tag:blogger.com,1999:blog-90142266757732132922024-03-13T08:45:30.700-07:00Gidan Novels | Hausa NovelsShafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zallaMuhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.comBlogger1047125tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-24794465774882959212022-02-12T05:30:00.001-08:002022-02-12T05:30:32.770-08:00WATA RANA Romantic hausa novels complete <p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEgnYRaeRkzRWXOrtSkBeFMRxMYyvgR_ksJNT8xLsFilm-MJsOiLfzoNpU8uUQvFMVVkaGjtrRvRDIlABpjZMIuYX0WZFhL-u1ZiD7g-VHKLl5kQSeakOMRgZg8A5XLTB1VV_N3O10PeCxxLDfxZ4OkCzJ6khAAtcCB74ZWlClP_huVI-XEHfxDjk8DE=s2286" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="WATA RANA Romantic hausa novels complete" border="0" data-original-height="1768" data-original-width="2286" height="309" src="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEgnYRaeRkzRWXOrtSkBeFMRxMYyvgR_ksJNT8xLsFilm-MJsOiLfzoNpU8uUQvFMVVkaGjtrRvRDIlABpjZMIuYX0WZFhL-u1ZiD7g-VHKLl5kQSeakOMRgZg8A5XLTB1VV_N3O10PeCxxLDfxZ4OkCzJ6khAAtcCB74ZWlClP_huVI-XEHfxDjk8DE=w400-h309" title="WATA RANA Romantic hausa novels complete" width="400" /></a></div><br /> Copied By<p></p><p>YAYA HAYAT </p><p> (admin </p><p> Hayat hausa novels</p><p>Hausa novels and fashion</p><p>Cool novel, makeup and kitchen1⃣</p><p>Cool novel, makeup and kitchen2⃣</p><p> AND </p><p>Cool novel, makeup and kitchen3⃣) </p><p><br /></p><p><br /></p><p> WHATSAPP NO:+2349030159301</p><p> WATA RANA !</p><p><br /></p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>© Haske Writer's Association💡</p><p><br /></p><p>1</p><p><br /></p><p>"Manya -manyan motoci ne na alfarma bakake wuluk kirar ( *Range rover*) sae kwaya daya tak ! Da ta kasance fara Sol wadda itace cikon ta biyar din hka kuma itace a tsakiya.</p><p><br /></p><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p>" A hnkali motocin ke shigowa cikin unguwar (Namadi Azikwe)" dake a garin Bauchi. Haka tsaddiyar unguwa ce ,cikin jeren gidajen masu kudi kosasshin ya'n siyasa manya-manyan ya'n kasuwa na Nigeria da wajen ta waya'ndda ake damawa dasu.</p><p><br /></p><p>Kae tsaye wani katon gida naga sunyi parking " tsayawa ,tsara gaban gidan xai daukeni tsayin minti biyar ban gama ba.yana da bakin rufi na zamani kalan rufin gidan da get din gidan duka baki ne. Haka a gaban gidan anyi wani irin Rubutu da farin fenti Mae dauke da sunan ( *Mrs. Sameer meera Estate*)" horn aka danna.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sauri mai gadi ya wangale katotuwar kofar gidan Kai tsaye motocin suka soma shigowa cikin harabar gidan wani bangare daban suka dosa inda aka kafa manya-manyan Rufuna Dan aje motoci kurum."</p><p><br /></p><p> Wanda a kalla mota takae kwara 10 a gurin ,tsawon minti biyu da tsayuwar motar ,da sauri wadan su irin mutane suka fito dai daga cikin motocin masu wata irin kira ,waya'ndda bature ke kira da(( body guard)).</p><p><br /></p><p>A kalla xasu kai mutum biyar cikin sassarfa suka nufi farar motar gefen barin dama dayan yasa ya bude marfin motar .</p><p><br /></p><p> Wani hadadden guy ne naga ya fito daga cikin motar yana cikin fararen kaya sol da kuma babbar Riga ya kafa hula akan sa haka kuma glass din frada ne a idonsa baki mai dihun gaske wandda ba'a hango kwayar idanun sa rufaffun talkami ne a kafan sa " sae a gogon hnnunsa wandda kudin sa yakai kimanin dubu Dari biyu da hamsin ."</p><p><br /></p><p>Kyakkyawa ne na karshe hka fari ne tas kamar balarabe yana da kirar maxa dogone mai ingirma jiki wato yana da fadeden kirji sae Dan karamin gemun sa da ya aza ." wandda yyi matukar kayata fuskarsa , hnnunsa yasa a hnkali ya cire babbar Riga gamida mikawa ,dae daga cikin yaran sa ...da sassarfa cikin takunsa na kasaeta ya nufi kofar shiga babban falon dake kallon gabas ..</p><p><br /></p><p>Abdul jabbar sameer meera kenan matashin saurayi wandda bai wuce shekara talatin da biyar ba a dunia ,wandda ya'mmata da yawa ke haukan so ...fans karku ga laifi na wollah koni Asmy ina cikin ya'mmatan dake da burin su mallaki Irin Mrs. AJ lolxxxxxxxx...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Body guard din dake biye dashi yyi saurin bude kofar falon ,ya shige manya -manyan mata na hango dam acikin falon da alamr akwae wani gagarumin taro da akeyi kowace tana cikin kaya na Alfarma ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dai daga cikin matan ta taho da fara'arta itama tana cikin shiga na alfarma ,haka gwala gwalai ne dam a ajikin ta tun daga kan Sarka ya'n kunne xuwa a warwaro.</p><p><br /></p><p>Sannu da xuwa my son!</p><p>Ta fada cike da tsantsan farin ciki haka ta amshi babbar rigarsa dake hnnu body guard din ya russuna ya bata cike da girmamawa , dai daga cikin kujorun dake babban falon na Alfarma mom ta samu ta xaunar da Dan nata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Gaba dae falon ya hau ihu ana masa kirari yehhhhhhh! Ango ! Ango! Ango kasha Mae ,a hnkali ya xare gilashin idonsa subhanalillahi ! Nan na kara tabbatar da kyawon Mrs .Meera wasu irin idanu garesa masu ban Sha'awa wandda bako wace hallitta keda irin suba. Wandda bature ke kira da (blue eyes) yana da Zara -zaran gashin ido haka yana da yalwar gira sosae wadda ta kusa gamewa ,Amma tayi masa masifar kyau!</p><p><br /></p><p>A tsakiyar goshin sa yna da tabon sallah wandda ya kara kaya ta fuskar sa hka tun daga saman bakinsa xuwa kasan sa gashine kwance baki wuluk sae kasan habar bakin sa Inda ya aza karamin gashi hka ya masa kyau sosae sabida Dan tsayin da yyi ,hancinsa mikakke har baka hka kanshi akwae tarin suma.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mom ta kalli Dan nata a karo na biyu ,ta sassauta murya hba Abdul jabbar meye hka??"</p><p><br /></p><p>Dan saki fuskar mna ,ranar farin ciki kowa na murna kai kuma ka tanke fuska kamar an aiko maka da sakon mutuwa."</p><p><br /></p><p>"Murmushi kadan yyi wandda ya bayyana fararen hakoransa farare tas ,mom na gaji ne shiyasa ynxu ma hka ina son naje na huta xanje nayi Abincika fa?..</p><p><br /></p><p>Tuku na mom sae xuwa anjima su sagir fah?".. Suna tareda friends din Aliya ko suna mgana akan yarda xasu tsara denern da xasuyi ohoooo!</p><p><br /></p><p>Ya Dan tabe baki nidae na fada masu baxan jeba mom ya kara sa xance gamida mikewa tsaye ,cikin fushi mom din ta Mike tsaye me kake nufi jabbar??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Meye abun fushi mom?? Ya fada cikin sanyi muryar sa nifa tun farko na fada masu baxan jeba ! So plzzzzz mom karki tilasta ni akan abunda xa'a xo a samu matsala !</p><p><br /></p><p>"Auren da kike so an daura so plzzzzz excuse meeeeee....</p><p><br /></p><p>Anan ya wuceta ,ya nufi wani bangare mutane sae tsokanar sa suke yi ..bai kulasu ba burin sa Kawae " A wannan lokacin yaje yaga kakarsa ya shiga ajikinta ko xaiji sauqin abunda yakeji a xuciyar sa..</p><p>WATA RANA !</p><p><br /></p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske writer's Association.💡</p><p><br /></p><p>2</p><p><br /></p><p>wani hadadden estate naga Aj ya nufa katon gaske hka xakayi mmki idan nace, duk fadin wannan gidan macce daya ke rayuwa ,acikin sa ,wato Hajia Asma'u mai kimanin shekara 70 a dunia tsohuwa mai ran karfe mai halin dattako ,duk da kasan cewar ita dai acikin gidan hka yasa aka xuba mata ya'n aiki mata zalla kwara biyar masu hidima a gareta .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sallamarsa ya shiga kayatatta cen falon Wanda aka kawata da kayan zamani ,ba kajin komae a katafaren falon sae karar Ac. Ga masu aiki nan birjik!</p><p><br /></p><p>Sae kai da kawo sukeyi yyi mmkin da bai samu hajja a wannan falon ba Dan yasan anan ne.gurin xaman ta "kai tsaye dayan falon ya nufa gabansa sae da ya buga hada ido da yyi da hajja a wannan lokacin sae ya'yanta da suke xaune a gefenta ganinsa yasa sukayi shuru da tattaunawar da sukeyi ,hka suka xuba masa ido sabanin kakar tasa da bata kalli ko inda yake ba balan tana tasan akwae halittar sa...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kanwar mahaifinsa kurum CE tayi karfin halin fadin kara so daga ,ciki abdul wato aunty salma.</p><p><br /></p><p>Har an daura auren kenan?" Ta tambaye sa gamida tsaresa da ido kuttttt! Ya hade wasu yawu masu dacin gaske."</p><p><br /></p><p>Karka kuskura ka karaso min cikin falo ,cewar hajja ka koma gurin matar da ka fito,cikin bada umurni take mganar fuskarta bbu alamr fara'a wani irin tashin hnkali ya shiga tunda yake da hajja bata taba irin fushi dashi hka ba ,tun kuwa tasowar sa har girman sa rau rau' yyi da ido ya kara kallonta idanunsa taf ! Da kwallah ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sassarfa ya isa gareta ya kankameta ajikinsa tamkar xai shige ciki ya Dora Kansa a bayanta "hka hajja ta dinga jin bugun xuciyar jikan nata.</p><p><br /></p><p> Na tuba hajja!</p><p>Nabi Allah ki yafe min Dan Allah fushin ki na azabtar dani ,nikaina bansan meyasa bana iya yiwa mom gardama ba " Aure anriga an daura addu'arki nake bukata."</p><p><br /></p><p>Kinfi kowa sanin bana kaunar Aliya !!.</p><p>Hasali ma ban taba sonta ba! Na yiwa mom biyayya kurum ne kasancewar ta uwa a gareni matar Uba" hka hajja ta dinga jin saukar hawayen sa a bayanta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Da kyar aunty salma ta samu ta jaye Abdul jabbar daga jikin hajja ta xaunar dashi dae daga cikin kujorun dage xagaye a falon saukar hnnun hajja yaji akan cheeks nasa hawayen idonsa ta shiga goge masa ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Granny!</p><p>Saurin daka taar dashi tayi karka ce komae a hnkali hajja ta kalli aunty salma ."salma a hada masa lunch da alamr bbu komae acikinsa .</p><p><br /></p><p>Hka aka cika gabansa da cima kala-kala tareda axa masa katuwar darduma tsakiyar falon sauko na ciyar da kai Abdul cewar hajja ta fada tana kallon AJ cike da so .</p><p><br /></p><p>Bbu musu ya rarrafo gurin hajja ya xauna tamkar yaro karami ,takun tafiya sukaji cikin falon kwas ! kwas!!</p><p><br /></p><p>Cikin wani irin sauti gaba dayan su suka mai da hnkalin su inda su kejin sautin.</p><p><br /></p><p>"Ido biyu yyi daita cikin wani tattausan less Wanda fadin kudinsa baxa fadi ba fuskarsa tasha make up!!</p><p><br /></p><p>Kallo daya zakayi mata kaga amarya ..bbu laifi tana da kyau na ban mmki..</p><p><br /></p><p>Kai tsaye ta tun karesu da sauri hajja ta dauke kanta itakam Allah ya gani bata son Aliya da jikanta ." nan ina tarbiya take??"</p><p> Wannan rashin tarbiya har ina ace amarya ta biyo ango har gidan su."</p><p><br /></p><p>Barka da gida hajja!</p><p> Aliya tayi saurin katse ma hajja tunani ,tareda yin masauki dae daga cikin kujorun dake ,xagaye da falon kannan mahaifinsa kuwa ko kallonsu batayi ba." Aunty salma da Aunty sadiya sae sakon harara suke aika mata Allah ya gani basa son Aliya da Abdul jabbar!</p><p><br /></p><p>"Jabbar !!</p><p><br /></p><p>I want to speak yhu in Private !</p><p><br /></p><p>Not now Aliya!</p><p>Muyi mgana xuwa anjima mganar yana da muhimmanci honey dama A......stop it !</p><p>I don't wan't to hear all of dis."</p><p> </p><p>I don't want 2 plzzzzz leave me a lone....ya fada in a angrily voice nasa ,just gooooooo out of my side "A fusace Aliya tabar part din na hajja cikin wani irin fushi...</p><p><br /></p><p>Asmy👛</p><p>WATA RANA !</p><p><br /></p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.💡</p><p><br /></p><p>3</p><p> Alh. Sameer meera haifaffen Dan garin Bauchi ne hka kuma dan siyasa Dan kasuwa yyi ya rika mukamai da dama ya rika mukamin senate Dan majalisa hka aka gangaro kan governor ya xauna a kujerar governor. "</p><p><br /></p><p>Bayan ya sauka ya fada harka kasuwan ci inda ya buda wani babban company na motoci da sunan sa ( *Sameer meera motors*)</p><p><br /></p><p>(( *Sameer meera petroleum*)) da sauran companies waya'ndda ake ji dasu a kasar nan Alh. Sameer meera yyi fice a kasar nan Nigeria da wajen ta hka mutunen mai tausayin gaske ,Sam Sam baya kyankyamin tallakka A kullum gidan sa cike yake dam da mutanen Arziki.</p><p><br /></p><p> Haka yana da manya-manyan gonakki wandda a duk shekara yake nome amfanin gona mai yawan gaske ,anan take ake lodasu a fita dasu kasuwan ci garuruwa daban-daban </p><p><br /></p><p>Masu karatu zakuyi mmki idan nace maku duk wannan dukia dake da Sameer meera ,shi daya ne dal A gurin mahaifinsa Wandda yake a matsayin da namiji ,sae mata kwaya biyu da suke bimasa sadiya itake bima Sameer meera akwae shekara 5 a tsakanin su sannan Salma wadda take bima sadiya ita kuma shekara 2 ne a tsakanin su " xo kuga yarda Dan uwansu ke nuna masu so tun suna yara Dan maifin sameer meera ya rasu tun yana da shekera goma sha takwas a dunia."</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Bbu laifi muha'd meera yabar masu dukia shema ba 'a hka yake bane shahararren Dan kasuwa ne ,hka ya mallaki gonakki " tun kaka da kakan ni bayan rasuwar mahaifin su ,mahaifiyar su Hajia Asma'u macce mai sanin ya kamata mai kokarin hada kan ya'yanta ta cigaba da basu tarbiya inda sameer meera a UK. Yyi karatunsa inda ya karatu a fannin kasuwanci...</p><p><br /></p><p>A gurguje Sameer meera yana da matar aure kwaya daya Hajia laila ,asalinta barabiya CE ya'r kasar misra A saudiya suka hadu da Sameer meera a nan suka fara soyayya bayan dawowarsa ,gida Nigeria ya tuntubi hajiar sa da xancen Duk da yana fargabar hajjah dinsa baxata amince masa ba ."</p><p><br /></p><p>Amma ga mmkinsa sae yaga tayi masa fatan Alkhairi hka ma su sadiya da salma lokacin ita sadiya tana aji shidda na secondary skull." Yyinda salma take aji ukku na secondary ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan Auren sameer da lailah ,ya daukota cikin ya'n uwan ta ya kawo ta garin Bauchi inda ya Gina wani babban Estate ,dake unguwar namadi Azikwe .</p><p><br /></p><p> Wandda shine suke ciki aurensa arxikinsa ya Dada habaka "yana rayuwa ne acikin gidan shida matarsa mahaifitarsa kanninsa ,shekara daya da auren sa aka samu cikin Abdul jabbar xo kuga tsananin son da Hajia Asma'u ke nuna ma Lailah bayan wata Tara ,ta haifi Dan ta namiji mai kama da mahaifiyar sa sak!!</p><p><br /></p><p>Dan a zahirin gaskiyya sameer meera bakin mutum ne sae dai yana da kyau ,Anyi shagalin suna anyi bidiri tamkar ba'a san xafin naira ba."</p><p><br /></p><p>Shekarar Abdul jabbar biyar A dunia lokaci daya aka yima Sadiya aure da wani ma'akacin banki abokin Sameer meera ne ,lokacin hidimar kula da Abdul jabbar ya dawo gurin salma wankan sa Abincinsa shirin makarantar sa gabadae salma keyinsa Dan yarda suke nuna ma Dan Dan uwan nasu So!</p><p><br /></p><p>Shekarar Abdul jabbar goma cif ! A dunia lokacin laila na da tsohon ciki a jikinta cikin bakaramin wahala yake bata ba ,bayan haihuwar ta da kwana biyu rai yyi halinsa bmutuwar ta girgixa sameer meera inda ta haifi kyakkyawar ya'rta mai kama da uban hka aka radawa ya'r sunan lailah Abdul jabbar shima mutuwar ta girgixa sa inda ya dauki son dunia ya daurawa Ya'r kanwar tasa ...</p><p><br /></p><p>Tun tana karama yake kiranta da Mimi..hka sunan ya cigaba da binta shekarar ta biyu a dunia ,ana shayar da ita madarar yara lokacin kuma Mr.sameer meera ya dauke Abdul jabbar ya kaisa UK. Karatu..</p><p><br /></p><p> *****************</p><p>Bayan shekara goma sha biyar. A hka Abdul jabbar ya cigaba da karatun sa a UK ...acan ya gama secondary skull inda ya fada jamia ,yna da shekara Ashirin A dunia yaxo Nigeria ya samu mahaifinsa ya aure wata ya'r kasar nupawa amma a Bauchi ,take rayuwar ta Hajia jummai Hka kuma lokacin mahaifinsa ya tsun duma cikin siyasa ,yarda yaga Hajia jummai na tsananin kulawa da Mimi ysa ya saki jiki daita wandda a zahirin gaskiyya a xuciyar Hajia jummai ba hka bane " tana son duka ta saye xuciyar ya'n gidan ne kafin ta fito masu da ainahin kalan ta na gaskiyya ."</p><p><br /></p><p>Sameer meera yana matukar son Hajia jummai musamman irin kyautatawar da take yiwa ,mima Dan a lokacin Aunty salma tariga tayi aure inda take auren Wani professor wandda Dan kano ne hka yana aiki a nan jami'ar Ahmad bello ...</p><p><br /></p><p>Jinin kanin mijin nata ko kadan bai hadu ba." Basa kaunarta hka ma mahaifiyar su Hajia Asma'u kawae dae kullum. Tana ma Dan ta Addu'a Allah ya karesa da sharrin mutum."</p><p><br /></p><p>Da na Aljan haka kuma a lokacin yana cikin tsakiyar siyasa , wannan xuwan da yyi Abdul jabbar yaga gata sosae gurin matar uban nasa ." da yake shi ba mutunen ne mai son hayaniya ba da kuma son fada komae nasa cikin sanyi yake yin sa haka yake tun yana karamin sa ..</p><p><br /></p><p>Da hajja tamasa complain din matar ubansa murmusawa kurum.yyi inda yake cemata hajja mom bata da matsala bakiga yarda takeson mima bane ,kawae dae keda su Aunty ne Baku fahimce taba.</p><p><br /></p><p>Baki so mom ta kawo maki jikoki ??</p><p><br /></p><p>A wasance xata jefesa da filo tace Allah ya raba Sameer dinta ."bata ma so mom ta haihu da Sameer ....ya kanyi daria yace hajja rigimar ki yawaaa garesa."</p><p><br /></p><p>Cikin hka Mimi ta shiga Aji daya na secondary skull..da hka shikuma Abdul jabbar ya koma UK.</p><p> ***********</p><p>WATA RANA !</p><p><br /></p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske writer's Association.💡</p><p><br /></p><p>4</p><p><br /></p><p>Abdul jabbar yana shekarar karshe A jami'r ta UK.inda shima yyi karatu a fannin kasuwan ci ne kwatsam yaji rasuwar mutuwar mahaifinsa "mutuwar da ta girgixa tunanin sa ta haifar masa da ciwon zuciya wandda sae da ya kwanta gadon Asibiti shekara biyu ya kamu da tsananin ciwon zuciya."</p><p><br /></p><p>Da kyar da Addu'a da sadaka Hajja tasamu jikanta ya dawo lpia wandda a shekarar da ya tashi ,sae da hajja tasa sukaje umra duka har mima lokacin tana aji 6 na secondary "</p><p><br /></p><p> Da yake shima Abdul jabbar ba banxa bane gurin Addinin Islam ya samesa sosae ,haka yyi ma mahaifinsa Addu'a da mahaifiyar sa sosae.</p><p><br /></p><p> Shekara ukku da mutuwar mahaifinsa ,ya koma UK. Ya cigaba da karatunsa Dan da yanxu ya gama shekarar sa hudu acan ya samu ya hada masters dinsa ,ya tattaro ya dawo Nigeria.</p><p><br /></p><p>A hka ya cigaba da jagorantar dukiar mahaifinsa ,haka kuma abun mmki dukiar sae kara habaka takeyi Dan Abdul jabbar kamar yafi mahaifinsa kwarewa akan harkar kasuwan cin ."</p><p><br /></p><p> Mom ganin bata aje ko kwae a gidan ba ,takara samun gurin xama ta cigaba da kula dasu Abdul jabbar ba wae Dan tana son suba hnya take nema ta samu ta kashe Abdul jabbar Dan ta cigaba da jagorancin dukiar tunda taga su Aunty sadiya da salma basu damu da dukiar ba uwa uba hajja suna gida daya amma sae tayi sati bata sa hajja a ido ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A ynxu hka shekarar AJ 34 A dunia duk wannan tsawon shekarun nasa baita ba kula wata macce ba da sunan so duk da kuwa ya'mmata sun sha sukawo masa hari ,hajja tayi fadan rashin Auren sa har ta gaji hka ma su Aunty sadiya .</p><p><br /></p><p> Akwae wata rana da aunty sadiya ke fada masa idan baifi tar da mata ba xata hadasa da ya'rta ta biyu wadda sa'annin junan suke da Mimi ,Rukaiyya haka kuma kawaye ne Mimi tana yawan xuwa gidan tayi kwana 2.</p><p><br /></p><p>AJ. Yakan yi daria haba Aunty sadiya daena hadani Da Rak! Mana hka yake kiran Rukaiyya karamar yarinya CE fa ni har yau ban ga matar aure ba ne shiyasa.</p><p><br /></p><p>Hka suka xuba masa ido Dan likitan sa ya tabbatar masu da cewa ciwon sa baison yawan damuwa ."</p><p><br /></p><p>A hka Abdul jabbar ya buda wani babban Asibiti da sunan mahaifinsa [Sameer meera hospital] haka ma makaranta islamiyya da na boko." Duka private ne.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kwatsama wata rana wata kawar Hajia jummai ta kawo mata ziyara dake xaune a garin Lego's ita da ya'rta Aliya ,Dora idonta akan Abdul jabbar shikenan ta rude da kyawon sa ...</p><p><br /></p><p>Suna a xaune take tambayar mom wannan pah?"</p><p><br /></p><p>Wae Abdul jabbar!</p><p>Dan maigida nane margayi mom yq xa'ayi ki shigar dani a gurinsa wallahi ya riga ya lashe xuciyata ina sonsa !.</p><p><br /></p><p>Ido waje mom ke kallon Aliya ,nan take mahaifiyar Aliya tayi kicin -kicin da rai meye hka Jummai?" Naga kin wani fiddo da ido.</p><p><br /></p><p>Ajiar zuciya mom ta sauke ,ba haka bane Hajia azumi yaron nan baya son Aure rayuwarsa haka ba'a so a takurama Rayuwarsa Dan yana da ciwon zuciya ko wane lokaci yana iya tashi uwar ubansa ma tayi fada ta gaji baran. Tana ni ..</p><p> </p><p>Mamar Aliya taja tsaki ,bansan yaushe kikayi sanyi ba hka ba jummai."</p><p><br /></p><p>Tunda Aliya ta tabbatar da tana son Mr.meera ai mu da talauci har Abada ke kanki xakiyi mmkin dukiar da xaki Tara anan gaba kawo kunnen ki kiji kawata.</p><p><br /></p><p>Anan Hajia jummai taba kawar tata kunne sae naga ta murmusa kai Azumi baki da dama to ynxu yaushe xa'a kawo min jibi insha allahu !</p><p><br /></p><p>Xakiga yarda Abdul xai xamar maki bawa sae abunda kikace nasan aurensa da Aliya cikin wata daya an gama komae..</p><p><br /></p><p>Gaba dayan su suka kyalkyale da daria har Aliya ..</p><p>OMG!</p><p>Mamy na!</p><p>Dan haka nake tsananin sonki I love yhu so much mamy !</p><p>Allah ya bar manke ....</p><p><br /></p><p>2 dayz letter .</p><p>Aka aikoma da Hajia jummai kulin mgani a Daren ranar tasaka ma AJ. Shi a abinci ,washe gari ta tunkaresa da mganar Aliya!</p><p><br /></p><p>Ga mmkin ta sae taga ya amince bbu gardama hka ta gargadesa akan kar ya fada ma hajja ya'n uwanta maxa tasaka aka je ne marwa Abdul auren Aliya a garin Lego's da yake ubanta bayer rabe ne yaga kudi nan take ya amince.</p><p><br /></p><p>Anan aka biya sadaki da komae ,hka mom taje Dubai itada Aliya suka hado lefe na gani na fada ."</p><p><br /></p><p>Har wannan lokacin Abdul jabbar baita ba tsayawa da Aliya ba Dan shi har ga Allah baya jin son Aliya ko kadan a ransa Dan dae baya iya yiwa mom dinsa musu ne kurum.</p><p><br /></p><p>Aliya irin yaran nan ne sangartattu gogaggun ya'n bariki hka idonta ya bude sosae akan kudi ..itada uwar ta!</p><p><br /></p><p>Sae dae muce Allah ya kyauta kurum.</p><p><br /></p><p>Anan mom ta shiga gayyatar manyan kawayenta da kuma ya'n uwanta ana gobe daurin Aure hajja taji lbr itada ya'yanta ko shi mijin Aunty sadiya yaxo mata da lbrn.</p><p><br /></p><p>Hajja tayi mmki sosae ,shiyasa ta kullaci Abdul aran ta.</p><p><br /></p><p>Ita kuma Mimi dama bata kasar tana kasar india tana karanta medicine "Dan shine burinta tun tana karama Wannan kenan))...</p><p><br /></p><p>Cigaban lbr.....</p><p>WATA RANA!</p><p><br /></p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.💡</p><p><br /></p><p>5</p><p> Da hka hajja ta shiga ciyar dashi kallonta kurum yakeyi har yau fuskarta akwae tarin damuwa acikinta hnnunsa yasa ya debo dakakkiyar sakwarar da taji Jan miya a hnkali ya isa kan bakinta daita hka ya tsareta da manyan idanunsa ,bbu musu ta buda baki ya saka mata da hka suka shiga ciyar da junan su."</p><p><br /></p><p>Aunty sadiya da Aunty salma na gefe suna kallon su soyayyar da hajja da Abdul jabbar sae Allah bayan sun kammala cin Abinci ya Dan kalli aunty salma da murmushi Aunty yaushe kika xo??</p><p><br /></p><p>"Daxun nan ta jirgi ma na biyo daga kano xuwa Bauchi jia da dare Aunty sadiya ta kirani take sanarda ni Aurenka " Ashe ka canja ya'n uwa bamu sani ba Abdul jabbar murmushi yyi a hnkali gamida cije leben sa na kasa hka ya kama kunnensa duka biyu ya langabe kansa yana kallon Aunt's din nasa am sowiee nayi laipi kaina bisa wuyana ni na isa na canja mahaifana !!</p><p><br /></p><p>"Aunty sadiya ta zabga masa harara nikam na fasa basa Rukaiyya ynxu kam Rukaiyya tafi karfinka kamata tsufa sae kai sae Aliya waya sani ma Age mate dinka ce.</p><p><br /></p><p> Shaye da toka yake kallon Aunty sadiya sae kuma ya Dan tabe baki ni mexan yi da Rak! Ae tayi min karama wollah A hnkali ya mike tsaye ya kallesu xanje na huta !</p><p><br /></p><p>Ya Dan subbaci goshin hajja I love yhu hajja ." murmushi tayi a hnkali gamida Shafa lallausar sumar kansa tareda fadin "bless yhu my child da sassarfa ya bar part din hajja .</p><p><br /></p><p>Hajja anan ta maida hnkalinta kan ya'yan nata ajiyar xuciya ta sauke yaron nan tausayi yake bani ,kunsan meyasa na kasa yimasa mgana?? Gabadan su suka girgixa kai lokaci daya hka suka xuba ma mahaifiyar tasu Ido idan muka nuna masa bama so ,xai daga hnkalinsa ne ina tsoron ciwonsa ya tashi ne kawae muyi masa fatan Alkhairi kurum.</p><p> Abunda nakeso ynxu Ku tashi yanxu Ku shiga wajen jummai cike da bin umurni suka mike dukan su xuwa side din mom.</p><p><br /></p><p>Yna kwance akan coach farar best ce ajikinsa sae bakin wandon Tree quarter wyar sa dake gefe tayi kara ganin sunan dake yawo akan screen wyar yasa yyi banxa da mai kiran.</p><p><br /></p><p>Karo na biyu wyar ya kara shigowa a fusace ya daga wayar meke kuma ya faru??"</p><p><br /></p><p> Sassauta murya sagir yyi kana Ina ne gani a gida ina ta Neman ka mom tace ka shigo amma ka fita ,ina son muyi mgana ina part dina ohkey gani nan zuwa ." datse wyar yyi cikin minti biyar sae gaya part din nasa da sallama ya shiga kira'ar Abdul Rahman Sudais kawae ke tashi a kayataccen falon nasa wandda aka kawata sa da komai fari Sol.</p><p><br /></p><p>Sagir ya xauna dae daga cikin kujorun dage xagaye da falon yana fuskartar abokin nasa "Remote ya dauka ya tsayar da karatun .</p><p><br /></p><p>Wai meke faruwa ne AJ??"</p><p>Da yake hka friends nasa suke kiran sa Nigeria da wajenta ga Aliya can tana kuka da sauri ya kalli friend din nasa .</p><p> Kana son ka sani ? Yyi mganar fuskarsa bbu walwala. Baxanje Dener ba !!👌🏿 shine kawae amma gobe su hajja xasu hada kayatattar waleema nipa kasan duk wannan bidi'ar baya gabana sageer!!</p><p><br /></p><p>So plzzz mubar ma wannan mganar haka na fadawa mom sagir xubama abokin nasa ido kurum yyi yasan halinsa fiye da sauran friends nasa idan yace no bbu mai sashi yyi haka ma idan yace yes bbu Wanda ya isa ya canja sa ."</p><p><br /></p><p>Sageer ya mike tsaye hannayen sa duka xube cikin aljihun wandon sa ohryt ." Ni xan tafi gida na huta !</p><p>Su barak suna hotel xuwa anjima dae xamu hadu anan yasa kai yabar sa batare da ya jira amsar daxai basa ba.</p><p><br /></p><p>Wya ya dga ya danna wa hajja kira akan A kawo masa ruwan Lipton.''</p><p>***********</p><p>8:30pm. Na dare dukan su suna a harabar gidan su biyar ne da alamr friends din AJ ne sageer barak farook jalal, Nura . AJ. Yana a tsakiyar su ya hade cikin wani tattausan bakin yadi da babbar Riga taji dinkin xamani wandda kudinsa xai kai kimanin dubu Dari da hamsin. Shigen baka ramin karbarsa yyi ba kasancewar shi mutum ne mai son shigen manyan kaya kana nan kaya ma bai fiye saka suba ."sae a lokacin zafi .</p><p><br /></p><p>Barak ya kallesa tom .ango kar kaje ka saki baki kana barci gobe flight din karfe goma zamu bi xuwa Abuja nida jalal hkama Nura xa yabar Bauchi xuwa kano ,sauran farook da Sageer xa'a barku tare ne kuci amarci koya kukace guy's?? "</p><p><br /></p><p>Gabadai suka kyal'kyale da dariar shakiyan ci yau gaka ga macce ,sae muga ya xakayi xuba mata ido xakayi ko yaya??" Tunda anki ba su Tina da leesa dama."</p><p><br /></p><p>Dunkule hnnunsa AJ.yyi da nupin yakai wa barak duka da sauri ya gofce ya naushi iska kai dai Dan iskane barak naga sanda xaka canja jalal yyi saurin amshe xancen da fadin nidai Ticket din Honey moon na nan na jiran Ku ko wace kasa kukeson xuwa mijin Aliya!!</p><p>Gaba dae suka kyalkyale da daria insha allahu soon xamuje honey moon. " Ku xauna nan a matsayin tuxuran ku mukam mun shige."</p><p><br /></p><p>Abdul jabbar ya fada yana gyara babbar rigar sa sageer ya duba agogon hnnunsa mukam suna bata mana lokaci muna so muje mu Hutu tunda ango ya hana aje dener!</p><p> Sageer yyi mganar yana kallon AJ.ta wutsiyar ido nidae ban hna kowa zuwa diner ba ."nidai kurum nace baxan ba."</p><p><br /></p><p>Wyar AJ.ce tayi kara yana duba kiran yaga aunty sadiya ce ,ya daga wyar Abdul kana ina??</p><p> Ganinan tareda su sageer kaxo ka dauki amaryarka a side din hajja mun gama .ohkey Aunty ya kalli su sageer guys sae.Allah ya tashe mu lpia xanje na dauki amaryata gabadae suka kalli juna tareda hada baki gurin fadin "Abun harda su kora da hali anan suka shige motocin su AJ.yana daga masu hnnu gamida sakar masu kayataccen murmushi har ya daina ganin su kai tsaye part din hajja ya nufa...</p><p><br /></p><p>_@t 10:50am.by Asmy b Aliyu_...</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p>6</p><p><br /></p><p>Masu karatu idan nace zan tsaya na fada maku haduwar part din Abdul jabbar meera xai daukeni tsayin lokaci ban gama ba amma bara na Dan takaita .</p><p><br /></p><p>Babban falo ne wandda komae nasa dark purple ne da white sae yana dauke da katon bedroom har kwara hudu acikin sa sae gefe kiching da katon store wandda yake lode da kayan abinci .akwae katon bene acikin falon inda xai daukeka side din AJ. Wanda komae nasa white ne ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Duka suna xaune a falonta itada friends dinta sae yaba gidan nata sukeyi billy CE tayi saurin katse ya'mmatan zip din Jakarta ta zuge ta fito da wata ya'r karamar kwalbar turare ta damka ma Aliya a hnnunta ,meye wannan??</p><p><br /></p><p>Cewar Aliya "ta fada tana ya tsine fuska.</p><p><br /></p><p>Murmushi billy tayi wannan xaiyi maki matukar amfani Aliya shixai daga darajar ki a gun mijinki basae na tsaya yimaki dogon sharhi ba keda kanki xaki bani lbr.</p><p><br /></p><p> Mun barki lpia sae xuwa gobe anan suka tafi suka barta nan ta mike tsaye ta fara zagayen gidan ,Wanda har lokacin bata ji motsin AJ. ba kai tsaye bedroom din ta ta nufa wandda komae na ciki lemon green ne kasan cewar tana son Abu green shiyasa mamin ta tasaka aka saka mata komae green.</p><p><br /></p><p>Kayan jikinta ta rage ,tareda Dora Dan karamin towel anan ta shige wanka.</p><p><br /></p><p>Yna kan sallaya da alamr ynxu ya idar da sallah kaidar sa kenan baya sallah Shafa,i da wutri sae xai kwanta barci ya daga kansa ya xubama agogon bangon dakin ido " karfe goma sha daya dae-dae na dare."</p><p><br /></p><p>"A hnkali ya Dan ja tsaki baya son ya shiga hakkin mutum ko kadan A rayuwar sa balanta na matar da take karkashinsa bedshoe dinsa ya saka kai tsaye ya nufi down stair xuwa side din nata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" hnnunsa ya aza akan kofar dakin yafi minti biyu a hka kafin ya tura kofar dakin wani sanyayyan kamshi ya daki hancin sa ,hada ido kawae da sukayi daita gaban sai da yyi wani irin buguwa tana cikin wata rigar barci Mae daukan hnkali maroon wandda ko cinyoyinta bata gama rufewa ba."</p><p><br /></p><p>A nan ya shiga karema halittar ta kallo Aliya irin fararen mutanen nan ne mara su kiba Amma tana da cikken kugu hka tana da cikar dukiyar Fulani ..murmushin mugunta ya saki lokaci daya Dan da alamr Aliya baxata iya da yawan bukatar sa ba ."Dan shi mutum ne Mae yawan bukata Dan haka ma yake azumin litinin da Alhamis.</p><p><br /></p><p>Tana ,tazar gashinta tana hangosa ta dressing mirror tana kallon yarda yake kallonta yau ne rana na farko da ya mata kallon tsaf!</p><p><br /></p><p>Bbu laipi tana da tsayin gashi sae dae kuma bai fiye baki ba.</p><p><br /></p><p>Sallama yyi gami da shigowa cikin dakin gaba daya a hnkali ta amsa batareda ta kallesa ba gefen bed yyi ma kansa masauqi sunfi minti biyu a hka ba wandda ya kara cewa uffan har Aliya ta gama dunkule gashin kanta guri daya taxo ta xauna gefen sa .kamshin turarenta ya kara fisgarsa nan take ya fara jinsa cikin wani irin ynayi .</p><p><br /></p><p> Kana bukatar wani abu ne??" Ta fada fuska bbu walwala Dan har lokacin fushi takeyi dashi ,ki hada min ruwan liptop haka Leda na nan a kiching ki gyara kayan dake acikin a katon faranti ki sameni A side dina.</p><p><br /></p><p>Yna maganar ne batare da ya kalleta ba itakuma tayi nisa gurin kallon kyakkyawan fuskarsa musamman bakin sa ,da yafi tafia da imanin ta da sauri ya mike tsaye har yakae bakin kofar idan xaki fito kifito da kayan sallar ki da hka ya Sakai ya fice daga dakin ..</p><p><br /></p><p>Murmushi Aliya tayi wandda tarasa ko na minene lokaci na farko kenan da yyi mata mgana mai tsayi a hka ,abun tambaya anan shine ko yafara Sonta ne??</p><p>A yarda yake mganar tamkar mganar yana masa wahala komae nasa burgeta yakeyi.itakam tana son Abdul jabbar tana addu'a Allah yabar mata shi har Abadan Abidin.</p><p><br /></p><p>******************</p><p>Da sallama tashiga bedroom din nasa da katon tire a hnnunta katuwar darduma ta shimfida masu anan ta hada masa ruwan liptop Tamika masa ya amsa ya aje bana shan Abu da xafi kibari kafin muyi sallah ya rage xafin nagode!!</p><p><br /></p><p>Da sauri ta dago tana kallonsa mmki baro -baro a fuskarta da Sauri ya dauke kansa baya son yawan kallo ,baiga abun kallo anan ba shi dama hka yake mutum ne wandda idan aka yiwa kyautata wa yana yiwa mutum godia ..hka ra'ayin sa yake.</p><p><br /></p><p>"Anan yaja su sallah raka'a biyu bayan sun idar ya rika kanta yyi addu'a sosae sa'annan ya fara jero mata tambayoyi game da Addini shuru tamasa tsoro mmki suka bayyana akan fuskarsa nan take kuma annurin fuskarsa ya canja a tsorace Aliya ke kallonsa ganin irin raxanar da tayi yyi saurin saukowa da fushinsa Allah ya gani cikin tsarin maccen da yakeso yana son maccen da tasan addini sosae Ashe ko akwae aiki ja agabansa anan ya shiga koyar daita cikin hikima da dabara bbu laipi ta kama hka itama tana mmkin ilimin Abdul jabbar hka."</p><p><br /></p><p>Gaya dae baya da matsala a rayuwar sa kudi sun xauna ta koina amma Sam Sam "baya da girman kai irin na wasu ya'yan masu kudin .</p><p><br /></p><p>Anan ya shiga shan ruwan liptop din tana gefe tana kallon sa a hnkali ya aje cup din hnnun sa yadan hadata da jikin sa ya dauko naman kaza ya fara ciyar daita ,subhanalillahi jin ta kurum ajikin sa sae da ta kusan xaucewa wani irin kamshi na mussaman jikinsa keyi itama a hka ta shiga ciyar dashi tayi mmki sosae taxata baxai Ciba.</p><p><br /></p><p>Minti goma sha biyar sun gama komae ta gyara gurin ta maida komae kiching dakinta ta koma kwantawar ta ke da wuya taji karar wyar ta Abdul jabbar ne!!</p><p><br /></p><p>Wata xuciyar take fada mata me kuma yake nema yanxu??</p><p>Dan a zahirin gaskiyya baxata iya jure waya'annan ayyukkan nasa ba dole ma ne gobe axuba mata ya'n aiki.Hutu taxoyi ba aeki ba ta Dan ja tsaki a karo na biyu kiran wyar nasa ya kara shigowa .</p><p><br /></p><p>Daukar wayar tayi batare da tayi mgana ba cikin sanyi muryar sa ya fara mgana kefa nake jira bae jira Mae xata fada ba ." ya datse kiran tabi wayar da hararar tana kwaikwayon mganar sa komae sae yyiwa mutane ya'nga dogon tsaki taja ..</p><p><br /></p><p>Anan ta rufe side din nata ta nufi up stairs.</p><p>Da sallama ta shiga dakin yana sanye cikin fararen pyjamas bakaramin kyau yyi mata ba itakam kyawonsa yana bata tsoro kanta a kasa ta tunkaresa baki shirya yin barci bane??</p><p><br /></p><p>Ya mata tambayr gamida riko hnnunta na dama wani irin shock sukaji lokaci daya "A hnkali ya hadata da jikinsa ya Dora kansa akan kafadar sa can ciki ya fara mganar ,ina son kamshin nan naki tabbas ta yarda namiji baya da kunya !!</p><p><br /></p><p>" A hka ya fara shinshinar ko wace gaba ta jikin ta yna sauke numfa shi kokarin turesa take amma ta kasa ya matseta ga gam ajikinta cak! Ya dauketa xuwa kan gadonsa ,nan take gaban Aliya yyi wani irin bugawa shike nan ta shiga ukku ta lalace billy takaeta ta baro wane irin turare ne ta bata hka??" Wanda xaesa Abdul jabbar ya fita haya cin sa hka Allah ya gani duk iskancin ta tana tsoron namiji yakae hnnunsa ajikinta kubarta kurum da son kudi da son rayuwa!</p><p><br /></p><p>Hnnun sa taji akan kirjinta a tsorace ta rike masa hnnu gamida kallon sa suna hada ido taga idon sa gaba dae sun canja tamkar ba Abdul ba meya faru kuma baby??" Ina son kamshin nan a hnkali ta maimaita sunan baby !!</p><p><br /></p><p>Lallae amma kuwa Allah ya tsinewa billy ko A mafarki bata taba tunanin AJ.xae hada jiki daita ba ."tunda ba sonta yakeyi ba Murya na rawa take fadin meye haka Abdul? Hnnun sa taji yana yawo akan kirjin ta runtse idonta tayi a hnkali tana jinta cikin wani bakon Al'amari Mae wuyar misiltawa."</p><p><br /></p><p>Romancing dinta yakeyi ta koina shikan sa mmkin kansa yake yarda ya kasa controlling din kansa."</p><p><br /></p><p>Jikinsa har rawa yakeyi A ranar bakara min wahala Aliya tasha a hnnunsa ba ,yasha zagi da Allah ya isa a Daren sumar ta yakae ukku AJ. Baisan ma tayi ba yana wata duniar."[truncated by WhatsApp "]</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.💡</p><p><br /></p><p>7</p><p>4:30@m. Yaga aika aikar da yyi mata lokacin ko motsin kirki bata yi hka wani bangare na xuciyar sa yana mmkin samun Aliya da yyi "A cikakkiyar budurwa can ciki ya fara kiran sunan ta cikin wani irin salo ya fara hura mata iska a kunnenta " Amma still bata motsi gaban sa ne ya fadi kar dae ace ya kashe ya'r mutane .</p><p> " cikin karfin hali ya sauko daga kan bed waige-waige ya shiga yi yaga ta inda xai hango ruwa acan ya hango ruwan "C way akan karamin center table ,budewa yyi ya xuba a hnnunsa tareda karanto duk addu'ar da ta fado bakin sa yana Shafa mata a fuska." Har kusan sau ukku doguwar ajiyar xuciya ta sauke tallabo ta yyi gaba dae xuwa jikinsa yna girgixa ta Aliya! Aliya!! "Are yhu ohkey ??</p><p>Ya fada cikin rikitacciyar murya ,kankame sa tayi tamkar xata koma acikin jikinsa kafin ta samu ta fashe masa da wani irin kuka Mae Sosa rai " cikin da sheshiyar murya ta fara fadin "Am not ohkey Abdul!</p><p><br /></p><p> " plzzz ka kaini gurin Mami Sabbatu ta shiga yimasa hka tana dukan chest nasa da karfi Shafa bayan ta ya somayi a hnkali alamr rarrashi shuru tayi tana sauke ajiyar xuciya gaba dae gashin kanta a hargitse yake "A hnkali ya zare ta a jikinsa tareda fadin yana xuwa bathroom ya nufa ya hada ruwan xafi minti biyar sae gaya ya fito tashi kije kiyi wnka."</p><p><br /></p><p>Ta yin kura xata mike ta saka masa ihu tareda koma wa da sauri ta dunkune kanta guri daya sannan ta saki kuka." Tsaye yyi yna kallonta aransa yake fadin akwae Aiki Sam Aliya bata juriyar kwanciya a shimfidar sa ,daukarta yyi cak ! Xuwa bathroom da taimakon sa ta samu tayi wnka bayan fitowarta shima ya samu yyi wanka koda ya fito bata dakin hka ya samu ya shirya ya saka farar jallabiya Dan baya so ya rasa jam,i ko kadan kae tsaye masallacin dake cikin gidan su ya nufa bayan idar da sallar bai tsaya yyi dogon azkar ba kamar yarda ya saba "yabar masallacin ganin halin da ya baro Aliya!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana murda kofar dakinta ya hangota dunkule acikin bargo bbu wata alama da ta nuna masa tayi sallah tattaki yyi xuwa gabanta ya fara danna mata kira Tana jinsa tamasa banxa Dan wani irin haushinsa " da takeji nasan kina jina kika yimin banza ki tashi kiyi sallah xuwa anjima xan kira Dr.fatyma zahra ta duba ki nan ma sharesa tayi abunda ya hasala AJ.kenan A fusace ya fisge blanket din da ta rufa dashi itama cikin fushi ta mike xaune wai meye matsalarka ne??" Matsalata shine ki kula da Addinin ki baxa mu shirya ba Aliya muddin kina wasa da addinin ki yana mganar ne cikin zafin rae anan yabar mata dakin gamida bugo mata kofar kafada ta daga alamr ko ajikinta ,ta koma ta shiga blanket abunta .</p><p><br /></p><p>***********</p><p>Kusan 7:00@m."Dr .fatyma zahra tayi parking din motar ta a dai-dai estate din AJ. " waya ta Ciro ta kirasa minti biyar ya sauko ya sameta tare suka shigo a gidan suna tafe suna lbr.Dr.fatyma zahra ma'akaciya ce kwararriyar Dr.wadda take aiki a karkashin (SAMEER MEERA HOSPITAL") haka tana daya daga cikin family dectors din sameer meera shekarunta baxasu wuce 24 years ba a dunia bata da aure ,shiyasa Allah ya dora mata son Abdul jabbar amma sai dae baima San tana yiba."</p><p><br /></p><p>"Ango kardae baka bi Amaryar mu A hnkali ba?? Murmushin sa mai kyau yyi kinji ki da wani xance zahra aiku dama mata kun fiye raki ne sae idan Abu bae sameku bane."</p><p><br /></p><p>Daria tayi lokacin da suka iso falon bissimillah xauna bara na dubata !</p><p><br /></p><p>Anan Dr. Faty tayi masauqi dae daga cikin kujoron tana bin koina da kallo ,gidan yyi mata kyau Allah sarki ko wacece wannan mai sa'ar auren Mr.meera ko wacece ita din Mae sa'ace.</p><p><br /></p><p>"Fitowar ta kenan daga wnka sae gaya ya turo kofar dakin nata saurin dauke kanta tayi akansa shima fuska bbu walwala ,Dan yaga alamr yarinyar nan naso ta raina sa kiyi sauri ki shirya ki fito ga Dr.nan taxo ta duba ki yna fadin hka bai jira Mae xatace ba yabar dakin.</p><p><br /></p><p> " Dan karamin tsaki taja sae da tabata kusan minti Ashirin kafin ta fito cikin wata ya'r bingilar Riga ta body hook mai katon Snake Ajikinta " hka kuma rigar da kadan ta wuce cinyoyin ta Mae hnnun supergaetti.</p><p> Tayi parking din gashinta a tsakiyar kae hka simple make up! Ne akan fuskarta ,sae ya tsine fuska takeyi Dr.Faty ta daga kai tana kallon ta tana mmkin ina Abdul ya samo wannan matar Dan ta tabbata da badan fari ba da sae bolaaa."</p><p><br /></p><p>"Kunya sosae AJ. Yaji yanxu Dan rashin tarbiya hka xata fito da wannan shigar da namiji ne A hka xata fito gabda AJ.ta xauna sae dae Dr.zahra ce tayi mata sannu da gidaa."</p><p><br /></p><p>A nan ta shiga aikinta Dan taga matar ta AJ.na tsananin ji da kanta tambayoyi ta shiga yi mata a ya'nga ce ta dinga bata amsa ,Dan wani irin haushinta take ji Wanda tarasa ko na minene Dr.Faty tayi rubutu akan wata takarda ta kalli AJ. Murmushi dauke a fuskarta .Mr. Meera ga drug's nan da xata bukata nan AJ,, ya amshi takardar yana dubawa godia yyiwa Dr.Faty tareda damka mata 20k. Har bakin motar ta ya raka ta."</p><p><br /></p><p>_Some hours latter_"</p><p><br /></p><p>Sae ga friends din AJ. Anan sukayi break fast gabadae ta tsane su su kuma sae Janta sukeyi da hira A hka sukayi shirin tafia sukayi mata Alkhairi na ban mmki bbu yabo bbu fallasa tayi godia ,Abunda yyi bala,in kular da AJ.kenan."</p><p><br /></p><p>"A air port barak ya kallesa gaskiyya matar nan taka bata da fara'a ko kadan kaga yarda take wani cin mgani kodae first night din Kane na jia ya shafe mu??"</p><p> Sabida haushi AJ.ko amsa barak baeyi ba suna nan tsaye shida sageer jirgin su ya daga xuwa Abuja yyinda Nura sae jirgin 12:00@m. Xaya bi...xuwa Kano.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*********</p><p>Ta hade cikin wani tsadadden less dark blue dinki Riga da skirt gaba dae ya kama jikinta tana xaune a tsakiyar friends din nata.ae wlhi billy ba abunda xance maki sae dae Allah ya isa!!</p><p><br /></p><p>Dama turaren na mugun tane kika bani kikasa nayi amfani dashi ,gaba dayan su suka kya'lkyale da daria to yah babe ?</p><p>Ya kk ga turaren?" Harara ta watsa mata ban sani ba!!</p><p><br /></p><p>"Ihu billy tayi kice jia kun kwana kuna aikin lada? Dogon tsuka Aliya taja ke Dan Allah bakida aiki sae wannan mganar ,plzzz mubarta kun san meye ta kalli sauran friends dinta kwaya biyu Feedo da Ummy nop sae kin fada??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mota nakeso Abdul ya bani?? Gabadan su suka hada baki wurin fadin mooooootah!!</p><p>Kwarae kuwa yana ga kowacen Ku ta zaro ido??"....har kuna mmkin irin baxai yuyu ba ma kenan guy's karku damu Ku zuba eyesss naku kusha kallo har skull na keso na cigaba anan ,tunda na baro Lego's baxai yuyu kuma nabar karatu na ba nayi bautar aure ,kutashi muje bangaren mom naga mami har 12 yyi bata xo ta duba ni ba ?</p><p><br /></p><p>"Gaba dayan su suka mike sukayi side din mom.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>★★★★★★★★</p><p>_2 week's letter_".</p><p>WATA RANA!</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.💡</p><p><br /></p><p>8</p><p> Yana cikin shigar bakaken suit coat wandda suka yi balain karbar sa yana rike da briefcase dinsa kai tsaye bedroom din ta ya nufa dae -dae lokacin da agogon bangon dakin ya nuna karfe Tara dae -dae na safe da sallama ya shiga dakin nata hango ta yyi tsakiyar gado tana sharar barci abunta tamkar wata matatta ,wani irin tsanar ta yakeji a ransa Sam Sam "Aliya bata San yarda xata kula da miji ba . musamman a gurin kwanciya xata nuna ma bata ma San abun da kake yiba.</p><p><br /></p><p> Tashin ta ya shiga yi ,A hnkali ta shiga motsi gamida doguwar mika kafin ta bude idonta akansa wani sanyayyen kamshi taji ya daki hancinta.</p><p><br /></p><p> Har kayi shirin fita office ne ??"</p><p>Ta tambaye sa gamida dirowa akan gadon ,gashin kanta duk a tarwatse."</p><p><br /></p><p>Ehhh xan fita!</p><p>Break fast fah?? Auhh Peter bae gama hada break fast din bane?" Ina justina batayi serving dinka bane?"</p><p>Lokaci daya ta shiga jero masa tambayoyi wani irin mugun kallo ya shiga aika mata dashi ,waye ne xai cimaki abincin ya'n Aiki ya'n Aikin ma Arna acikin tsarina bana cin Abincin waje kona ya'n Aiki ya kamata ki canja!</p><p><br /></p><p>"Shaye da toka take kallonsa gamida turo masa bakinta cike da shagwaba ,amma kasan aikin gidan nan baxan iya shi ni daya ba ko?"</p><p><br /></p><p>Duka hidimar nawa guda nawa ne?</p><p>Xaman aure fa kika zo ba hutu ba." Nidae na fada maki "ya kamata ki kiyaye haka kuma mgana na karshe kar Dan aikin da ya taka a part dina."..</p><p><br /></p><p>In kinga dama ki gyara kinga tafita a fusace ya bar mata dakin gamida bugo mata kofar ,anan ya tarar da ya'n aiki sae kai da kawo sukeyi duk inda ya wurga ,sae kaji ana fadin morning sir."</p><p><br /></p><p>Gidan hajja ya nufa yyi break fast hka ta tsaresa da tambayr ya kamata matarsa ta fara yimasa girki xuwa wannan lokacin " shidae bai ce komae ba yana gamawa yyi mata sallama ,Tsattsaye ya gaisa da mom .</p><p><br /></p><p>Body guard nasa suka amshi jakar hnnunsa xuwa mota."</p><p><br /></p><p>Drivern sa na ajesa a company dinsa ,body guard dinsa suka take masa baya xuwa katafaren offishinsa Wanda ma'aikatan gurin sae russunawa suke suna kwasar gaisuwa."</p><p><br /></p><p>Xaman sa keda wuya ..aka fara yin knocking ,shuru yyi yana duba tarin fales din dake xube a katon table din nasa ."</p><p><br /></p><p> Haka aka cigaba da kwankwasa kofar murya can ciki yake fadin "yes come in ..da sallamr sa ya shigo ya kwashi gaisuwa gamida mika masa wani fale ,Zubair hassan kenan wato P.A din AJ.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Anan ya shiga dudduba fale din ajiayar xuciya ya sauke ya dago dara -daran idanunsa gamida saukesu akan zubair.</p><p> Yaushe ne xa'ayi presentation din?" Jibi ne sir .ohkey zubair ka shiryamin meeting dasu xuwa 2:00pm. Na rana ohkey sir .</p><p><br /></p><p>Da haka ya juya yabar office din fitar sa keda wuya sae ga sageer ya shigo da alamr yanxu ne shigowar sa dama kuma sageer A karkashin sameer meera's company yake aiki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ango !</p><p>Ango kasha mai irin wannan kyau hka wae meye sirrin ne?"</p><p><br /></p><p>Shaye da toka AJ.ke kallon sageer ,bana son iskanci sageer kayi abunda ya kawo ka ."Auh nikake fadawa mgana.?" Tukuna dae ina Amaryar mu??</p><p><br /></p><p>A karo na biyu ya zabga ma sageer harara ka bani ajiyar tane ?"...Wlhi AJ.kana da matsala wae daga tambaya ban sani ba sageer!!</p><p><br /></p><p>"Get out of my office now!</p><p> Lokaci daya sageer ya kyalkyale da daria auh harda kora kuma karka manta nifa ne ? " sageer best friend dinka .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bbu shiri AJ. Ya jawo laptop dinsa ya shiga aiki Dan idan ya biyewa abokin nasa xai iya haukata sa ." fisge laoptop din sageer yyi ka aje wannan Mln mgana xamuyi .</p><p><br /></p><p> Sageer Dan Allah ka fitar min A office plzzzzz🙏. Naji xan fita amma ka saurareni first tukuna ina jinka ya fada fuska bbu walwala nan take shima sageer ya xama serious " wani sati xa'ayi onder sabbin motoci daga kasar England "ina ce kasan da wannan zancen??"</p><p><br /></p><p>Na san da xuwan su sae kuma meye??</p><p>Sae batun presentation ."wandda kai ya kamata ka yie sa ,kai na keso kayi sageer sabida jibi ina tunanin zanje Kano.</p><p><br /></p><p>"Angel xata xo Hutu..woww kace muna da manyan baki a gari nayi shekara biyu banga Mimi ba tom.Allah ya kaimu amma ba tafiar mota xakayi ba ko?"</p><p><br /></p><p>Ina tunanin ta jirgi xanbi xamu kwana daya sae mu dawo ,ina tunanin ma tareda Aliya xamu tafi taga gidan Aunty salma."olryt Allah ya kaimu amin ni bara na karasa office.</p><p><br /></p><p>Ohkey!!</p><p>Xuwa 2 dae xamu Shiga meeting olryt allah ya kaimu Amin amin."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>4:30pm.ya dawo gidan nasa A babban falo ya tarar da sarauniyar tasa ta hade cikin kana nan kaya Riga da wando "wanda gabadae kayan sun kama jikinta ,bbu alamr kallabi abisa kanta tana rike da wya tana operating daita ."kayan a fruit's ne Agabanta cikin wani kyakkyawn faranti tana dauka daya bayan daya tana ci a hnkali " kamshin mijinta kurum taji ta Mae da hnkalinta kofar falon cike da kewar mijinta tayi saurin isa gabansa tareda rungumesa "tana masa sannu da xuwa wani irin yar !!</p><p><br /></p><p>" yaji rabon sa da ya hada jiki da Aliya tun ranar first night dinsu."....karbar briefcase dinsa tayi ta sakala A right shoulder dinta ,tare suka nufi up stairs ."</p><p><br /></p><p>Ita ta fara bude kofar dakin wani sanyayyen kamshi yaji ya daki hancinsa ,dakin ya dinga bi da kallo Angyara sa an canja masa xanin gado.</p><p><br /></p><p>Kayan jikinsa ya soma ragewa yana kallonta waye ya gyaramin dakina??" Justina ce baki wangalau ya saki yana kallonta idan ransa yyi dubu to ya baci mena fada maki daxun da safe??"</p><p><br /></p><p>Meyasa bakya jin mgana ne?"</p><p>So nawa xan fada maki bana bukatar wani Dan Aiki ya shigo min a part dina ' this iz d first and the last Aliya ,da xan maki gargadi na karshe idan wani Dan Aiki ya kara shigowa a part din nan ranki xae baci.</p><p><br /></p><p>Shike nan na shiga ukku !</p><p><br /></p><p>Tunda na aure ka banda kwanciyar hnkali wai mekake so ne?"</p><p>Tafada cikin kunar rae .</p><p><br /></p><p>Yhu want 2 know??</p><p>Ya fada yana kare mata kallo fuskar sa bbu walwala "get out !</p><p>Kallonsa tayi cike da mmki, I said get out of my side !!</p><p><br /></p><p>Ya sake mai maitawa nan take idonsa ya juye xuwa bacin rae ."</p><p><br /></p><p>A fusace ta juya tabar masa dakin Stupid gal ' ya fada A xuciya anan ya shige bathroom ya sakarwa kansa ruwa. Yana fitar da wani irin huci yana tunanin matakin da xae dauka kan Aliya "tunda ya lura rarrashi da ban baki baya yie mata..</p><p>WATA RANA!</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p>9</p><p> Karfe goma dae dae na dare yana xaune akan soofa yana aiki da laptop dinsa kirar Apple da alamr wani aiki ne mai muhimmanci.</p><p><br /></p><p>Turo kofar dakin Akayi da sallama amsa sallamr yyi batare da ya kalleta ba gab dashi ta xauna ,tare da Jan karamin center table ta Dora cup tea din akae hka yaji kamshin turaren ta ya fara fisgar sa bbu shiri ya dago ya kalleta tana cikin wata irin rigar barci light pink ,wanda daita da bbu duka daya."</p><p><br /></p><p> Rigar barcin ba karamin karbar ta tayi ba ."kayi hkuri idan na bata maka rae tayi mganar gamida kama kunnenta duka biyu kayi hkuri ka yafemin Dan Allah .</p><p><br /></p><p> "Plzzzz mana !</p><p>Tayi mganar cike da kissa.</p><p><br /></p><p>Har lokacin bai kulata ba bbu shiri ta daura kanta a kafadar sa hka kuma ta riko hnnunsa tana murxawa a hnkali saukar hnnunsa taji a bayanta da sauri ta dago tana kallonsa kayi hkuri?"</p><p><br /></p><p>A hnkali ya daga mata kai alamr ya hkura.</p><p><br /></p><p>Nagode!</p><p>Ta fada cike da kulawa murmushi dauke a fuskarta ga lipton dinka." Hnnu tasa ta dauka ta basa ya amsa "A hnkali yace ...</p><p><br /></p><p>" nagode!</p><p>Tana gefen sa har ya gama shan ruwan liptop dama kuma cikin shirin barci yake .</p><p><br /></p><p>A nan saman jikinsa ta fara barci xuwa sha daya na dare ya rufe laptop dinsa A wannan lokacin wata irin matsanaciyar sha'awar ta ke Addabar sa hnnunsa ya saka ya dauketa tamkar wata baby doll"</p><p><br /></p><p>Xuwa kan bed ta rierikesa sosae tamkar wadda xa'ayiwa kwacen sa da kyar ya samu ya banbare hnnun ta akan wuyan sa gamida gyara mata kwanciyar ta.</p><p><br /></p><p>Kae tsaye toilet ya nufa alwalah ya dauro anan ya tada sallah Shafa,i da wutri.</p><p><br /></p><p>Sae kusan sha biyu saura yyi shirin barci A hnkali yazo ya kwanta gab daita gami da jawota a jikinsa A hnkali ya lalubi bakin ta ya fara Aika mata da wadan su irin saquna masu wuyar misiltawa tamkar a mafarki Aliya ta dinga jin bakon Al'amari.</p><p><br /></p><p>"A tsorace ta bude idonta dae-dae lokacin da AJ.ke kokarin rabata da ya'r ficikar rigar barcin ta ."</p><p><br /></p><p>Kokarin xare jikinta take yi cikin nasa ya riketa ga gam." Ya hana ta koda kwakkwaran motsi.</p><p> </p><p>"Wani irin salo ya shiga nuna mata wanda nan take Aliya ta manta kanta ." da ganan kuma suka Lula duniar ma'aura ta .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Washe gari_"....</p><p><br /></p><p>_yau yyi mmkin kyakkyawar tarba da ya samu a gurin Aliya gaba dae ta canja da kanta ta hada masa special break fast "haka ta hada masa ruwan wanka ,ita ta taimaka masa ya shirya har suka yi break fast A tare_..."</p><p><br /></p><p> _tare suka shiga part din hajja bayan ya gaisa da hajja itama Aliya ta gaisheta bbu yabo bbu fallasa hajja ta amsa ta maida kallon ta akan Abdul jabbar ya mganar xuwa kano dauko lailah?_""..</p><p><br /></p><p>_gobe ne hajja !_</p><p>_"Amma kasan dani xa'ayi wannan tafiyar ko?_"</p><p><br /></p><p>_A lokacin AJ. Yana tsaye hnnayen sa duka xube cikin aljihun wandon sa yana cikin wani tattausan yadi sky blue_"...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_wanda ba karamin karbar sa yyi ba rage tsawon sa yyi a hnkali hba granny kina hka xakice xaki bimu nan fa da kwana biyu kawae xaki ga Mimi na roke ki grandma kibar wannan tafiyar a jirgi xamu tafi ba'a mota ba nayi maki Alkawari kwana daya Mimi kurum xatayi A kano_..""</p><p><br /></p><p>_shike nan bbu damuwa yawwa my sweetheart "Dan haka sonki ke dada karuwa kullum a ruhina ina sonki hajja!_"""</p><p><br /></p><p>_nima hka yaro na!_</p><p>"Allah yyi maka albarka amin hajja ta.</p><p><br /></p><p>Da hka yyi mata sallama har lokacin Aliya na gefe tana sauraren su wata irin tsanar hajja takeji A ranta yarda taga Abdul jabbar yana kula daita tasan ko rayuwar sa xai iya bata.</p><p><br /></p><p>(Mtsw....)</p><p>Tayi tsakin da bata ma San fitowar sa ba da mmki AJ. Ya juyo kanta keda waye kk tsaki?</p><p><br /></p><p>Kaina ne kiyi min ciwo ki koma gida ki huta kibar ni na karasa da kaina ,xanje na. Gaisa da mom ."</p><p><br /></p><p>Nop !</p><p>"Kabar shi muje na taka maka dama kuma ina son naga mom.</p><p><br /></p><p>Tare suka shiga part din na mom."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_MA'U_....</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p>10</p><p> Masu aiki ne birjik ko ina Sae kai da kawo sukeyi yau yyi mmkin da bae samu mom a falo ba dai daga cikin aikin masu aikin gidan ya tambaya.</p><p><br /></p><p>Salame!.</p><p>Na'am Alhaji! Ta russuna ta kwashi gaisuwa matar da ya kira da salame shekarun ta xasu ba hamsin baya ."</p><p><br /></p><p>Da sauri AJ.yace ta mike tsaye Mom fah?</p><p>Tana bedroom bata jin ddi ne !</p><p>"Tashin hnkali nan take AJ.ya rude bata idar da fada masa ba ya nufi bedroom din nata da sassarfa Aliya na A bayan sa bakin ciki kamar meye ,,itakan ta shiga ukku hka Abdul kebawa ya'n gidan nasu kulawa harda mom" wadda a zahirin gaskiyya bata son sa a xuciyar ta a fili kurum take nuna hkan.</p><p><br /></p><p> Dole ma ta kira mamin ta a waya ya kamata su tashi tsaye."</p><p><br /></p><p>Ta masa mganar skull da sabuwar mota ya nuna mata ma baya son xance ....tunanin ta ya katse a daidai lokacin da suka ,fada bedroom din na mom da sauri AJ ..ya karasa gurin gadon nata tana dunkule acikin blanket "hka an saka mata drip ' da sauri ya rika hnnunta wanda baya da komae mom!</p><p><br /></p><p>Yyi mganar cikin raunaniyar murya da kyar ta daga ido ta kallesa sabida tsananin zazzabin dake addabar ta ." </p><p><br /></p><p>Murya can ciki take fadin baka fita bane??"</p><p><br /></p><p>Batare da ya bata amsa ba "yake fadin mom meya sameki ?</p><p>Meyasa ba asanar dani ba ya fada fuskarsa cike da tausayin ta ,murmushin karfin hali tayi gamida damke hnnunsa karka damu dear zazzabi ne kurum."</p><p><br /></p><p>"Waye yaxo ya duba ki?" Dr.yaqub ne anan ya Ciro wyar sa yana Neman layin Dr.yakuq yyi sa'a kuma ya samesa fita waje yyi yana waya akan meya ke damun mom dinsa."</p><p><br /></p><p>Anan yake masa bayani akan ciwon sugarn tane keson tashi amma idan ta kiyaye hkan baxai sake faruwa ba!</p><p><br /></p><p>Ajiar heart ya sauke gami da huro iska mai xafi a bakin sa.</p><p><br /></p><p>Mom ya jikin ?</p><p>Aliya tayi mganar fuska bbu walwala ,da murmushi mom ke fadin ae tasamu sauqi da hka Aliya taja gefe ta xauna tana chart da wyarta.</p><p><br /></p><p>Dae-dae kuma lokacin AJ.ya shigo a dakin ya karaso gab da mom ,kallonsa mom tayi me Dr.ya fada maka??</p><p><br /></p><p>Lumshe idonsa yyi a hnkali kafin ya bude su akan mom din tasa ,mom meyasa kike yawan cin duk abunda baya baki lpia ga lpiar ki ??" Na daina My son abincin ne namu bayamin ddi ne wata rana!</p><p><br /></p><p>Olryt."</p><p>Ya kalli drip din wanda rabi kurum yyi mom break fast fah?</p><p>Murmushi tayi karka damu my son yanxun nan salame xata shigo dashi...</p><p><br /></p><p>Dai-dai nan salamen ta turo kofa ta russuna ta aje katon faranti ta kalli mom Hajia bara na taimaka maki kici Abincin...</p><p><br /></p><p>AJ..yyi saurin daga mata hnnu no hka ma iz "ohkey mun gode!</p><p><br /></p><p>Aliya!</p><p>Firgit git tayi tana kallon sa xoki taimaka wa mom taci abinci mana." A zuciya Aliya ta kallesa ranta idan yyi dubu to ya baci. "</p><p><br /></p><p>Ga ya'n aiki in banda rainin hankalin Abdul jabbar Sae itace xata ciyar da mom ." karo na biyu ya sake yin mganar!</p><p><br /></p><p>Naji ta fada a yatse ne sa'annan ta maida hnkalin ta kan chart din da takeyi , abunda yyi balain fusata sa kenan...</p><p><br /></p><p>Baki da hankali ne wai?</p><p>Yyi mganar cikin tsawa ,mom ta sassauta murya yima ta a hnkali my son " mom kinsan bana iya jure wannan abun tun farko keki ka kawo yarinyar nan yanxu gaya nan tun kafin aje koina da haka ake tunanin ni Abdul jabbar xan sota ??"</p><p><br /></p><p>"Ina har Abada!! na dai yie xaman hkuri ni na tabbata (WATA RANA !) Zuciyata xata samu wadda take so ina mafarkin hkan mom wadda Sae kinyi Alfahari daita nina fada maki mom ....</p><p><br /></p><p>A xuciya Aliya ta mike wani irin bakin ciki ya ziyarci zuciyar ta ,haka hawaye suka dinga malala akan fuskar ta haka ta dinga ciccika tana karawa " idan Akwae abunda Aliya tafi tsana a dunia shine....AJ. Ya rabi wata macce da ayi mata kishiya gara kowa ya mutu wlhi a xuciya tabar dakin da gudu tana goge hawayen idonta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Jikin mom qlau yyi sanyi ta maida hnkalin ta kan AJ.wanda yabi bayan Aliya da mugun kallo gami da yin Dan karamin tsaki...</p><p><br /></p><p>My son!</p><p>Rinan nun idonsa ya dago yana kallon ta bacin rae ne tsantsa acikin su ka dinga hkuri da Aliya Dan Allah har ynxu yarinya ce ,baece komae ba ya bar dakin baijima ba sai gaya tareda salame..</p><p><br /></p><p>Anan yyi mata umurnin ta ta taimakawa mom din tasa taci Abinci ya kalli mom ,ni xan wuce office plzzz idan da matsala ki kirani mom ya fada yana kallon ta ."</p><p><br /></p><p>Murmushi tayi masa tana yimasa Allah ya kiyaye daga hka ya fice daga dakin ....</p><p><br /></p><p>"A office ma kasa zama yyi Sae waya kan waya yake yi akan ya jikin mom din nasa yna cikin wannan yanayin kiran Angel nasa ya shigo " A sanyaye ya daga wyar ..</p><p><br /></p><p>Cikin kasalalliyar murya yake fadin ..</p><p>"Angel!</p><p><br /></p><p>Yayana baka nema na ko??</p><p>Takarasa mganar A shagwaban ce bbu alamar ma kayi missing dina ni kawae ke haukata !</p><p><br /></p><p>Nop!</p><p>Angel waye ya fada maki?"</p><p>Nayi kewar ki sosae Anan suka cigaba da hirar su..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan dawowar sa office gaba dae gurin mom din nasa ya tare shike jinya duk da ta samu sauqi haka ma hajja taxo ta dubata ,Aliya kuma tun safe bata kara leko mom ba.</p><p><br /></p><p>Sae kusan karfe goma AJ.ya dawo gidan sa koda ya dawo bai nemi Aliya ba Dan har lokacin fushi yake yi daita...jin yayie xuwa wannan lokacin tamkar ya fasa tafiyar daita.</p><p><br /></p><p>Dan an riga an yanki ticket ne kurum." Haka kuma an gama komae , kwanciyar sa yyi batare da ya leka part dinta ba.</p><p><br /></p><p>Itama bangaren Aliya fushi ta hauyi dashi....</p><p><br /></p><p>(Washe gari........)</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>11</p><p><br /></p><p>Karfe 8:00@m na safe ya tura kofar dakin nata wanda tsaye take ajikin mirror dressing tana shirya kanta karar bude kofar da taji shi ya dawo da hnkalin ta jikin kofar ido biyu sukayi dashi yana cikin manyan kaya na captani ruwan kasa haka ya kafa hula kalan kayan ,ba karamin kyau yyi ba.</p><p><br /></p><p>Saurin dauke kanta tayi akansa bata reda ta kara kallon inda yake ba." Ki shirya da wuri jirgin karfe 9;00am. Xamu bi bai jira mai xata fada ba yyi ficewaer sa xuwa estate din grannyn sa.</p><p><br /></p><p>"Sallama yyi a babban falon karar T.V. yaji bbu kowa a falon sae tashar sunan t.v. dake aiki kai tsaye bedroom dinta ya nufa nan ma bata nan mmki ya cikasa to ina ta shiga ne??</p><p><br /></p><p>Karar bude kofa yaji da sauri ya maida hnkalin sa jikin kofa granny ce murmushi tama sa harka shirya kenan?"</p><p><br /></p><p>"Ajiyar heart ya sauke oh my world!</p><p>Daga ina hka granny " ina kiching muna ta kokarin hada Karin kumallo nida laraba.</p><p><br /></p><p>Meya faru kuma?</p><p>Yana shagwabe fuska to ba keki ka tsorata ni ba!</p><p><br /></p><p>Gyara xaman gilashin idonta tayi wanda ke karama idon nata lafia oya muje kayi break fast nasan shiya kawo ka ban San yaushe wannan matar taka xata canja ba anan kuma granny ta shiga banbamin fada shidae biye daita yake kurum.</p><p><br /></p><p>Allah ya kawo maka wata matar kirkin wadda xata cikamin gida da ya'yanka!</p><p><br /></p><p>" murmushi mai kyau yyi amin my sweetheart mekika tana darmin ne?"</p><p><br /></p><p>Yyi mganar gamida xaunawa akan kujerar denning table ,koko ne da kosae!</p><p>"Ya tsine fuska yyi kai gaskiya ni baxan ci ba ya fada gamida harde hannayen sa akan kirjinsa ya wani bata rae.</p><p><br /></p><p>" A mallan gari da yawa !</p><p>Kuma da kake xuciya akan baxaka Ciba." Yau shi nake sha'awar ci ga ruwan lipton nan kasha sae ka hada da wainar kwae.</p><p><br /></p><p>Suna break fast yana mita granny dae sae shan kokon ta take tana gamawa da kosae ..</p><p><br /></p><p>8:30@m.</p><p>Yama granny sallama akan idan sun isa xaikira ta anan ta masa fatar Allah ya kiyaye ,hka ma mom yau bbu laipi taji sauqi tare suka shiga da Aliya ta hade cikin wata doguwar rigar material marron sae Dan yololon mayafi da ta aza wanda dashi da bbu duka daya."</p><p><br /></p><p>Sae wasu uban hill dake a kafarta kalar handbag " nata bbu laipi tayi kyau ,nan tayiwa mom ya jiki anan AJ.ya kara jaddama ya'n aiki akan su kula da mom nasa da kuma granny dinsa."</p><p><br /></p><p>Idan akwae matsala su neme sa da hka yayiwa mom sallama drivern sa ya jasu xuwa air port da sauran tawagar body guard nasa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A mota sai kiran sageer yake baya shiga ,har lokacin da jirgin su ya daga xuwa kano ."</p><p><br /></p><p>**********</p><p>Sosae Aunty salma tayi farin ciki dasu sae nan nan take dasu itakam Aliya duk a takure take ,Suna xaune gaba dae a Falon na aunty salma wanda baifi awa daya ba jirgin su Angel nasa ya sauka.</p><p><br /></p><p>Wae aunty ina Nana ne?</p><p>Murmushi Aunty salma tayi ,tadan harare sa a wasan ce sae yanxu kasan daita sowiee aunty na sha'afa ne aikin San ya'r gidana ce.</p><p><br /></p><p>Tana gidan kanwar Abban su kwanan ta biyu yau acan saleem kuma yana Abuja. Kasan mahaifin nasu da tsastauran ra'ayi akan boko mussaman A boarding skull."</p><p><br /></p><p>Hka yana da kyau Aunty uncle jafar yyi tunani mai kyau.</p><p><br /></p><p>Uffan dae Aliya bata cema su ba sae hirar su sukeyi a tsakanin su ana saura minti talatin jirgin su ya sauka gabadai suka nufi air port din.</p><p><br /></p><p>"A wannan lokacin AJ.sae duba agogon hannun sa yake ,ya kagara yaga ya'r tilon kanwar tasa rabonsa daita shekara daya kenan har karfe biyu dai dai na rana ya buge bbu alamr saukar jirgin su abun da ya saka AJ.cikin matsanaciyar damuwa da wasi-wasi kenan 2:10pm...jirgin su ya sauka.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Murna kamar meye a wajen AJ. Gaba dae ya rasa na tsuwar sa burinsa kawae yyi tozali da ya'r kanwar sa Aliya na lura dashi sae dae ta kallesa ta tabe baki gamida dauke kae."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Matashiyar budurwar ce ke saukowa daga matattakalar jirgin " A tamfar sharaton ce ajikin ta kalar xubin brown da ratsin light pink ajikin ta dinki Riga da zani ne xanin single sae rigar wadda ta iso har gwiwarta an yimata dinki da wasu irin stones work." Wanda ba karamin dacewa sukayi da Zubin atamfar ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Medical glass ne A idonta haka din kyakkyawa ce ajin farko tana da manyan idanu masu ,daukar hnkali kallo daya xakayi mata kaga tsantsar kamar da sukeyi da AJ. Ta koina kanwar tasa shi ta debo."</p><p><br /></p><p>Sae Dan karamin veil brown wanda ta sakalo sa tun daga bisa kai ta sakalo sa a wuyan ta babbar trolley ce take jaye daita ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Matashiyar budurwa .mai kimanin shekara goma sha Takwas A dunia." Masu karatu ba kowa bace wannan illah (LAILAH SAMEER MEERA"))..</p><p><br /></p><p>Tafia kurum take taga inda xata hango ya'n gidan su nan take yanayin fuskar ta ya sauya tamkar tayi kuka wato ma .Yah Abdul din baixo ba. Bbu granny bbu mom bbu Aunty's dinta.</p><p><br /></p><p>Tunanin ta ya katse dai dai lokacin da taji saukar hnnunsa akan Fuskar ta." Hka taji kamshin jikinsa wanda tasan wannan tabbas yayan tane.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ihun murna tayi ya janye hnnunsa akan fuskar ta tayi arfa dashi ihu tasa keyi A karo na biyu tayie hugging dinsa sosae tamkar xata koma ajikin sa.</p><p><br /></p><p>Wayyo ddi yayana!</p><p>"Ashe xaka xo?</p><p>Oh my Allah ! Gaskiyya" Am very very happy kasan cewar ka anan.</p><p><br /></p><p>"Murmushi dauke A fuskarta ta subbaci goshin sa ,tareda fadin " by d way I miss yhu yayana!</p><p><br /></p><p>Murmushi ya sakar mata ,tareda fadin by d way I love yhu my "Angel muryar Aunty salma ce ta daki dodon kunnen ta sae lokacin ta kula daita tsabar murnar ganin yayanki kin manta dani oh sorry my Aunt nan tayi hugging dinta tana murna ,Anan ta maida hnkalin ta kan Aliya wadda bata Santa ba gaba dae dan bbu wanda ya fada mata Yayan nata yyi aure."</p><p><br /></p><p>Karaso wa tayi gurinta murmushi dauke a fuskarta ,Dan Mimi harga Allah ta dauka Aliya ya'r uwar mijin Aunty salma ce hnnunta ta bata na dama "A ya'n gace Aliya ta mike mata hnnunta na dama sukayi shaking hands.</p><p><br /></p><p>Lailah sameer meera" </p><p>Nyc name"</p><p>Thank yhu .</p><p>Cewar Mimi still bata saki hnnun Aliya ba ."hka tana jiran taji sunan ta .</p><p><br /></p><p>Aliya tagano nufin ta murmushi tayi mata" "Aliya Abdul jabbar meera!</p><p>Nyc 2 meet yhu ,cikin rashin fahimta Mimi ta saki hnnun ta da sauri kallon yayan nata tayi lokaci daya cike da mmki..</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>12</p><p><br /></p><p>"Haka aka cika gaban Mimi da cima kala-kala amma ta kasa taba komae gabadae hnkalin AJ. Na akan kanwarta sa.</p><p><br /></p><p>Yayan ta yyi Aure bata sani ba. Wannan wane irin Aure ne??"</p><p><br /></p><p>Aliya ce tayi saurin katse mata tunani meya faru Mimi ??" Ko bakiyi murnar ganin yayan naki bane,gashi kin kasa taba komae cike da kissa Aliya ta fara serving dinta bbu yarda ta iya hka ta fara cin abincin sama -sama lallai tana bukatar ta kebe da yayan nata.</p><p><br /></p><p>Kadan taci tacema Aunty salma ta koshi murmushi Aunty salma tayi oya mu shiga ciki kiyi wanka. Yah Abdul kaji rani naje nayi wanka akwae mganar da xamuyi daga mata kae kurum yyi Dan yasan mganar dake yimata yawo acikin xuciyar ta anan aka barsa shida Aliya.</p><p><br /></p><p>Honey!</p><p>Cewar Aliya ido ya xuba mata ina son ka kaini gidan wata friend dina dake nan</p><p>Sokoto road."</p><p><br /></p><p>Kibari sae xuwa anjima." Nura nake jira fita xamuyi nan take Annurin fuskarta ya canja Dan xaku fita da Nura shine baxaka kaini inda nakeso ba haba Abdul ,wannan wane irin Abune?</p><p><br /></p><p>Sae kasa wani ya kaini idan fitar ne baka son yi dani ta karasa mganar fuska bbu walwala."..</p><p><br /></p><p> "Shawara ne kike bani ko kuma umurni ,duk abunda xuciyar ka ta raya maka ta karasa mganar A zuciya ..</p><p><br /></p><p>Karar wyar sa ta katse sa Nura ne mai kiran yana dagawa ohkey gani nan fitowa ya kalli Aliya ki fadawa Aunty salma mun fita da Nura sae mun dawo baki wangalau ta saki tana kallon sa ."</p><p><br /></p><p>Yasa kai yyi ficewar sa batareda ya jira amsar da xata basa ba.</p><p><br /></p><p>Ta fito cikin Riga da wando na English west waya'ndda sukayi matukar yimata kyau ,kanta bbu Dan kwali sae tudun gashinta dake tsakiyar kanta wandda ta kama da riboom bata da cikar gashi sae uban tsawo da santsi.</p><p><br /></p><p>"Aliya!</p><p>Da mmki Aliya ta dago kanta tana kallon Mimi dake famar danna wya." Batareda ta kalleta ba take tambayar ta yah Abdul pah?"</p><p><br /></p><p>Kutumar uba!!</p><p>Aliya tayi mganar aranta lallai yarinyar nan bata da mutunci xata ko gyara mata zama dae-dae nan Aunty salma ta fito Ina kuma Abdul din yyi ne??</p><p><br /></p><p>Cewar Aunty salma." Mimi ta tabe baki shi nakeso na sani Aunty ,Aunty ya Dan fita ne shida Nura nima ynxu xanje nan sokoto road xan shiga motar haya ne.</p><p><br /></p><p>Yah Abdul !</p><p>Where Are yhu??" Ta karasa mganar a shagwaban CE shine ka tafi baka jirani ba." Dif ta kashe wayar hawaye suka xubo akan cheeks nata Aunty salma na mata mgana bata ko kulata ba tayi kan stairs da gudu kallon mmki Aliya tabita dashi ..</p><p><br /></p><p>Murmushi Aunty tayi Mimi kenan ya'r rigimar Abdul jabbar ,bansan ya xakiyi idan kikayi Aure ba!</p><p><br /></p><p>Nan aunty salma ta mai da kallonta kan Aliya " bara nasa driver ya kaiki in yaso daga baya shi Abdul din yaje ya dauko ki ohkey "Aunty nagode.</p><p><br /></p><p>★★★★★</p><p>Misalin karfe shidda da rabi na yamma dae-dae lokacin da motar su AJ. Ta shigo unguwar Ahmad bello way" dae dae lokacin wata wata bakar motar frado ta shigo cikin rashin sa'a AJ. Ya Dan bugi motar ."</p><p><br /></p><p>Nan take yaja burki suna salati da sauri yaa fito daga .motar ... "</p><p><br /></p><p>Macce CE matukiyar motar ,tana cikin shigar body hook bakin skirt ne ajikinta da kuma rigar su mai ratsin baki da fari Mae dogon hnnu ,glass din farada ne a idonta baki wuluk!!</p><p><br /></p><p>Gyalen bakar a baya ne tayi rolling din kanta dashi black beauty ce haka kyakkyawar gaske tana da manyan idanu masu daukar hnkali ,bbu wata kwaliyya akan fuskarta amma akwae pink janbaki akan labban ta Wanda ya kara kawata fuskarta ."</p><p><br /></p><p> Dogon hancin ta kuma tamkar Kara's ba'a sata a layin dogaye hka ma guntaye.</p><p><br /></p><p>Fitilar motar taga ta fashe glass din idonta ta cire ta maidashi kan goshinta ,kai wane irin makahon mutum ne ?</p><p><br /></p><p>"Ta fada A tsiwance maganar da tayi shiya bani damar hango fararen hakoran ta wandda acikin Su Akwae hauren makka ajikin su wandda bakaramin kyau yyi mata ba tana mgana dimple na fita a fuskarta ..</p><p><br /></p><p>Shikam AJ. Gabadae ya rude daganin wannan matashiyar budurwa kasa cemata uffan yyi shikuma Nura yana a mota dama cewa yyi baxai fita ba.</p><p><br /></p><p> Karo na biyu ta karaso a gaban sa a fusace mln bakaji ina mgana!</p><p>Nan ma shuru yyi mata yadda take mganar ma Abin burgewa ne.</p><p> Karar wyar ta taji dama tana hnnunta kallo daya xakayi mata kaga babbar wya dibawar da xatayi taga mai kiran nan take ta rude tashin hnkali baro-baro ya bayyana akan fuskarta."</p><p><br /></p><p>Hnnu ta aza akae batare da ta daga wyar ba." Nashiga ukku !!</p><p>Yah Anas na kirana a wya kasheni xaiyi wani mugun kallo take bin AJ. Dashi kaga hasarar da kajamin kayi shuru baka cemin komae ba kuma ka tsaya kana kallona da manyyun idonka!</p><p><br /></p><p>Wae halama kai kurma ne ?" Tayi tambayar tana zabga masa harara dae-dae lokacin Nura ya karaso gurin ganin har ynxu Nura yana kallonta ya zabga mata harara itama hararar sa tayi taja tsaki dama nasan xa'a Arina kace min da wannan mugun mutumen kk murguda masa baki tayi kafin ta maida kallonta kan AJ." Baxan yafe mka ba!!</p><p><br /></p><p>Yanxu ma kaci sa'a ina sauri da wlhi Allah sae na Tara maka jama'a Allah ya hada mu dakai ((WATA RANA!)) "Sae ka biyani Amin AJ. Ya bata amsa murmushi dauke A fuskarsa kadaina murmushi kyawun ka baxai gigita ni ba!</p><p><br /></p><p>" A fusace Nura ya daga hnnu xai zabga mata mari a xuciya AJ.yyi saurin rike masa hnnu da kabarsa ya mareni da ya tattaro ma Kansa masifa da bala,i yau da kasan ka taba "Asma'u Omar omra." Takara sa xancen tana binsa da mugun kallo ta murguda masa baki gamida Jan dogon(mtsw....)) Ta tada motar tabar gurin da shegen gudu ..AJ. Yabita da kallon SO" Aransa yake fadin (DRAMA QUEEN) suna. Da xuciyarsa ta bata kenan. Mganar Nura ta dawo dashi hnkalin sa.</p><p><br /></p><p>"Meya sa baka barni na mata shegen duka anan ba? Nura yyi mganar cikin kunar rae ,wlhi albasa batayi halin ruwa ba. A hka AJ. Ya lallashi Nura xuwa mota Sae masifa yakeyi...</p><p><br /></p><p>★★★</p><p>Ana bude mata get din gidan nasu ta hango motar yah Anas ! Da kuma daddy !</p><p>Xuciyar ta Sae da ta kusayin bindiga Dan tsoron abun da xai biyo baya jiki sanyaye tayi parking cikin sanyin jiki tayi sallama falon ido biyu sukayi da daddy !</p><p><br /></p><p>Da kuma yah Anas dake binta da mugun kallo gwiwowin ta ta xube A kasa dae -dae nan maman su ta shigo falon."</p><p><br /></p><p>Wani mugun kallo daddy yake yimata.</p><p><br /></p><p>Wanda yasa hnkalinta masifar tashi "Ashe ke babbar ya'r iska ce ban sani ba?" Iskancin naki har yakai ki dauki motar da nake hawa ki fita dashi .....cikin rawar murya ta fara mgna kayi hkuri daddy wlhi ba laifina bane ,shikenan nagode bani key din motar.</p><p><br /></p><p>Jiki na bari ta mika masa ..Anas ka kaita a store ka rufe kar Wanda ya bata Abinci a yau har Sae ta fada min daga ina take.</p><p><br /></p><p>Hawaye suka xubo a idonta Dan Allah daddy kayi hkuri daga gidan suna nake....gidan sunan ubanki!!</p><p><br /></p><p>Daddy yyi mganar A fusace kai Anas ko bakaji abunda nace bane?</p><p>Gadan-gadan yah Anas yyi gurin ta da sauri ta rarrafa gaban daddy ta rirrike kafafunsa Dan soyayyar ka da manxon Allah sallallahu alaihi wassalam kayi hkuri daddy!</p><p>Na tuba !</p><p>Daddy nabi Allah "baki tuba ba Asma'u har Sae na aurar dake ,haba mana daddy nice fa Asma'u mai sunan yayar ka!</p><p><br /></p><p>Fisgota yah Anas yyi tana ihu ya nufi hanyar store daita ,Sae famar ba yayan nata hkuri take hka tana kwalawa Maman su ....</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>13</p><p>"Nura dama kasan yarinyar nan " yama abokin nasa tambaya batare da ya kallesa ba Dan hnkalin sa duka yana kan driving" A kufule Nura ya kallesa unguwar mu daya sae kuma meye?"</p><p> </p><p> "Dan murmushi AJ.yyi hba mana Abokina Dan Allah ka sauko hka nan kasan mata ya'ntattali ne ,banda wannan shaidaniyar yarinyar Nura yyi mgana a zuciya."</p><p><br /></p><p>Har cikin ransa AJ.yaji Kalmar ta shedanci da Nura ya kirama drama queen dinsa."</p><p> Kadaina kiranta shaidaniyya mana! Da mmki Nura ya kalli abokinsa ya bata rae sabida baka so aga laifinta ba."</p><p><br /></p><p>AJ.yaushe ka canja??"...ba hka bane Nura ba laipin ta bane nawa ne ,ohkey ! Nan Nura ya shiga nodding din kansa. " Daga lokacin Nura yaja bakin sa yyi shuru Dan ya lura Abokin nasa akwae sakar da yake yi aransa".</p><p><br /></p><p> "Yana son yaji Karin bayanin Asalin drama queen dinsa".</p><p> Yana gudun kar Nura ya tuhume sa ,Dan haka yaja bakin sa yyi shuru amma ya dau Alkawari " WATA RANA !! Sae ya nemota .</p><p><br /></p><p>Dae-dae lokacin da sukayi parking "a dai dai lokacin kuma Aliya ta fito dga cikin wata mota (406) nan take ynayin AJ. Ya canja ya dai hngo macce da na miji a gaban motar wadda namijin shine matukin motar sae a side dinsa macce yyinda Aliya ta fito a bayan motar.</p><p><br /></p><p>" wa nake gani kamar Aliya AJ. Bai kulasa ba ya shiga dannawa mai gadi horn ,haka aliya ta hango motar tasu AJ. Amma ko ajikinta sae ma bin motar da tayi da harara."</p><p><br /></p><p>Ya ina tambayar ka kayimin shuru ??" Cewar Nura car key dinsa yabasa ,da dare xan shigo unguwar Ku da haka AJ." Yyi gaba yyinda Nura ya saki baki ,wangalau yna kallon Abokin nasa ."</p><p><br /></p><p>A falo ya tarar da Aunty salma da maigidan ta da kuma Autan ta sameer wandda suke kira jeniour da fara'a Mijin Aunty salma ya tari AJ' har ka dawo kenan??"</p><p><br /></p><p>Nan sukayi musabaha dae-dae kuma lokacin Aliya ta shigo Anan ta gaida mae gidan Aunty salma." Dama tareda madam kake kenan??</p><p><br /></p><p>Ehhhhh uncle tare muka zo Aliya ta nufi up stairs ainahin bedroom din Aunty salma yyinda AJ. Ya cigaba da hirar sa Da uncle jabir da kuma Aunty salma." </p><p><br /></p><p>Aunty wae ina Angel ta shiga ne??"..</p><p><br /></p><p>Tana barci ne agogon dake sakale A hnnunsa ya duba barci hka yamma yyi fa sosae hop tayi sallar la'asar ta kwanta ,sae da tayi ma tayi shirin barcin ta fitine mu da rigima kuma ba."</p><p><br /></p><p>Murmushi AJ.yyi nasan laipina aunty uncle jafar yyi dariar su ta manyya ina ruwan mimi har yau ganin kanta take yarinya uncle bara naje na watsa ruwa naga magrib yna gabatowa " Anan ya haura sama ya shiga daki mae kallon na Aunty wandda nan suka sauka hka ya samu Aliya da ya'r bingilar Riga ta shan iska xuwa lokacin har tayi wanka tana xaune ne akan soofa tayi crossing leg's " dinta wya takeyi kasa-kasa tana jin karar bude kofar ,tayi saurin fadawa mamin.. Xasuyi mgana xuwa anjima " bae kulata ba ya rage kayan jikinsa ya nufi bathroom saurin shan gabansa tayi ,yna daure da brown din towel a kugunsa" sumar jikinsa baka wuluk ..</p><p>Hka ta kwanta luf daita gwanin Sha'awa.</p><p>Lpia ??"</p><p> Ya fada yna kallonta "Am sowiee xan hada maka ruwan wnka ."</p><p> " sae aka fada maki bana da hannuwan hadasu ,plzzzz matsamin a hnya.</p><p><br /></p><p>Yyi mganar bbu wasa a fuskarsa daure fuska tayi gamida yin folding din hnnunta akan kirjinta ,baxan matsa ba !</p><p>Tayi mganar cikin fushi tunda muka diro garin nan kake wulakanta ni wae menayi mka ne A rayuwa?"</p><p><br /></p><p>Hawaye suka xubo akan idonta "nan take jikin AJ.yyi sanyi ta gefenta yabi ya wuce abinsa ,wani irin kuka taji yaxo mata da gudu taje ta fada kan bed" baxata iyaba ba wlhi baxata iya jure wannan wulakan cin nasa ba."</p><p><br /></p><p>Mganar mamin tace ta fado mata Arae Aliya shifa na miji Dan tattali ne dole ki aje duk ,wani girman kai naki ki tarairaye sa tamkar yaron goye dole kiyi hkuri da wani wulakanci nasa ,mun basa Dan lokaci ne "kafin mu dawo kansa dolene kiso duk abunda yakeso.</p><p><br /></p><p>" da hka ta dinga tuna mganganun mamin ta kusan minti goma sha biyar ya kwashe "A toilet kafin taji motsin bude kofar toilet din....</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p>©Haske writer's Association...</p><p><br /></p><p>14</p><p> Karfe Tara har da rabi na dare muna cin Abincin Daren da Aunty salma ta girka nida ita da kuma Mimi Wanda bakajin komae sae karar cokula muna cikin cin Abincin ne mukaji kararrawar (door bell)).</p><p> Mimi ce ta doshi kofar ta bude, Abdul jabbar ne hnnunsa duka biyu cikin aljihun bakin wandon sa da kuma farar T.shirt mai guntun hnnu wadda ta Dan kamasa sae naga yyi min kyau sosae acikin shigen duk da kuwa bai fiye son kananun kayan ba.</p><p><br /></p><p>"Yah ina kashiga tun daxu? Cewar Mimi dake rike da hnnunsa na dama sallama yyi a falon kafin yace Mimi kya bari na xauna tambaya hka,ko matata bata damuba baranta na ke ya karasa mganar cike da xolaya nan take ynayinta ya canja A zuciya ta juya ta koma wajen cin Abincin ta.</p><p><br /></p><p>Auh fushi ma kikayi??</p><p>Sharesa tayi Aunty salma tayi daria ina ruwan Mimi kai kuma Abdul baka kyauta ba ta damu dakae shiyasa ta tambayeka tun daxu take Neman layinka " ix not Available to Aunty bagani ynxu na dawo ba.</p><p><br /></p><p>Aliya ce tayi saurin mikewa tayi masu sae da safe yyinda Mimi tabita da harara .</p><p><br /></p><p>"Angel.</p><p>Ya kirata cikin wani irin sauti ta turo baki batareda ta kalli inda yake ba,ayi min afuwa ina unguwar su Nura nan ma banxa tamasa Cikin sanyin jiki ya kalli Aunty salma Aunty kice tayi hkuri ta kulani mana.</p><p><br /></p><p>Bbu ruwana wannan tsakanin Ku kunfi kusa kaga tafia ta anan Aunty salma ta fice...ya rage daga shi sae ita .</p><p><br /></p><p> Ta kallesa shaye da toka na xuba ma Abincin?" Tunda naga matarka bata damu daka ci Abinci ba ko baka Ciba ,takarasa mganar tamkar xatayi kuka murmushi yyi ya dawo gabda kanwar tasa hnnunta na dama ya rike kina fushi dani Mimi taya xa'ayi naci Abinci."</p><p><br /></p><p>Tun saukar ki kasar nan kike fushi dani gayamin meye laipina kiga yarda xan hukunta kaina." Jikin ta qlau yyi sanyi taji tausayin yyn nata ya kmata ,serving dinsa tafara yi tukuna sannan kanta tashiga basa Abinci."</p><p><br /></p><p>Sunfi minti goma a hka kafin yace mata ya koshi Anan ta dauko masa best drink dinsa wato maltina...</p><p><br /></p><p>Kiyi hkuri Mimi ba laipina bane ,mom keson na Auri Aliya hasalima ban taba sonta ba.</p><p><br /></p><p>Da mmki Mimi ta dga ido tana kallon yayan nata. "</p><p><br /></p><p>Anan AJ.ya bayyana mata komae to ita kuwa mom meyasa ta dage akan lallae lallae sae ka auri Aliya.?"</p><p><br /></p><p>Tom..Allah ya sa hka shiya fi xama alkhairi amma nikam bros gaskiyya matar nan taka bata yimin ba." Ina jin baxamu shirya ba ,murmushi AJ. Yyi dolema tayi miki tunda matar yayan kice , nan kuma suka canja hira xuwa na school dinsu anan ya biye mata da kallon pics din friends dinta A waya.</p><p><br /></p><p>Sae kusan sha daya saura minti goma suka bar falon."</p><p><br /></p><p>********</p><p>"Washe gari muna gama karya kumallo mukayi shirin tafia Air port Wanda jirgin karfe goma xamubi xuwa Bauchi.</p><p><br /></p><p>Mimi sae murna take kamar meye ji take tamkar tayi tsuntsuwa ta ganta A Bauchi tare da mom dinta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wannan murna fa haka Angel?".. AJ yyi tambayar wa kanwarsa Yah Abdul na kagara naje naga granny dasu mom ne ..daria AJ .yyi to Idan bamu samu flight din safe fah?"</p><p>Nan take yanayin ta ya canja sae ayi tafiar a mota nafiki son mu isa da wuri Angel ina da minti karfe "3 na yamman nan a yau kuma motocin mu xasu iso ,woooowwwww kace xan xabi dya aciki.</p><p><br /></p><p>" yaushe na canja mki mota da kike mganar canja wani??"...</p><p><br /></p><p>Kai yah AJ.shekara 2 fa yanxu Angel kina da rigima ne ,mexakiyi da mota keda ke karatu."</p><p><br /></p><p>Ni dae plzzzz bros ,xan Dan jima shi yasa ba sae na barwa rukayya nawa ba ." Angama my Angel idan aka kawo sae kowa ya xabi dai daya, keda Aliya....hugging dinsa tayi tana tsallen murna.</p><p><br /></p><p>"Murna kamar meye hka bakin Mimi yaxama A ranar Aunty sadiya da yah saifullahi da kuma Rukaiyya ya'nyata kenan manya ,harda su a air port gurin tarbonta ,granny mom narasa da Wanda xan fara runguma kai tsaye wurin granny nayi na kankame ta sosae ina dariyar farin ciki itama daria tayi ,Anan na shiga gaisawa da mutanen gida gaba dayan mu muka nupi gida yah AJ.da ya nufi office Wanda ya saifullahi ne ya dauka sa A motar sa.</p><p><br /></p><p>" mom tarasa inda xata sa kanta da tsananin murnar ganin Mimin ta ,Estate din granny aka nufa duka har mom ,yyinda Aliya tayi part dinta Abunta.</p><p><br /></p><p>Bata kara jin hayaniyar suba.sae bayan magrib da mom ta shigo tayi mata sannu da xuwa bbu yabo ,bbu fallasa Aliya ta amsa ,daganan bata kara kallon mom ba hasalima tashi tayi ta shigewar ta daki.</p><p><br /></p><p>Washe gari .....</p><p>Suna gama break fast AJ ..ya kira Aliya a wya Dan tana dakinta ,shi kuma lokacin yna tareda Angel nasa."</p><p> "Cikin wata bingilar rigar body hook ta fito ,da kadan ta wuce gwiwoyin ta dark blue kanta kuma da hula red " ta roba ,jeki canxo kayanki kixo xamu fita Mimi baki iya gaisuwa bane?"</p><p>AJ .yace da kanwar tasa ina kwana!</p><p><br /></p><p>"A yatsine Aliya ta kalleta kin tashi lpia??"</p><p><br /></p><p>Da haka ta juya ta koma ciki yah Abdul bari naje na dauko hijab da handbag dina "daga can xanje gidan su Aunty sadiya ohkey.....</p><p><br /></p><p>Aliya da AJ.a gaban mota sae kuma Mimi dake baya ta damesa akan ina xasuje ??"</p><p><br /></p><p>Ki xuba eyes naki kurum" kisha kallo, A company sameer meera motor's taga sun tsaya itama Aliya takasa boye murnarta ,wowwww sweetheart karka cemin mota xan xaba?"</p><p><br /></p><p>Kwabe baki yyi ya kalleta ko bakya sone?"</p><p>Batasan lokacin da ta rungumesa ba ,sae godia take ,xuba masa gaba dae ta rude Mimi ta Dan ja tsaki aranta tace taga mota manyya gayyar mayu "duk ta wani bi ta rude ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Motoci ne kala biyu baka da kuma Ruwan toka a gefe" kirar *4matic*" E350 , AJ. Ya kalli Aliya yace ta fara xaba nan take Aliya murna ya karu A hnkali ta fara xagayen motan tana duddubawa ,karshe ta dauki bakar car key yabata sannan ya mikawa Mimi dayan key din.</p><p><br /></p><p>Angel ki dauki "Ash din nan ta amsa tana tsallen murna .....</p><p><br /></p><p>Tom.kuxo mu tafi xuwa anjima sae akai maku su gida ko ,why not yanxu mu Dan Dana yah Abdul ..hohoho!</p><p>Angel kina dae bari ayi setting nata sa'annan kuma ayi mata full tank ...</p><p><br /></p><p>Da haka ya juya dasu gida yna aje Aliya Mimi ta axa rigima akan lallai sae ya kaita gidan Aunty sadiya .....hka ya juya kan motar suka nufi gidan Aunty sadiya dake unguwar fariah suites..</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu...</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>15</p><p> Tare suka shiga gidan Aunty sadiya shigar su falo suka isko Rukaiyya na tikar rawa cikin Riga da Wando na English west".</p><p><br /></p><p>Aunty Rukaiyya ga yah AJ. Nan na kallonki cewar safeeya wadda itake biwa Rukaiyya cak! Ta tsaya hka takasa juyowa ,kunya gabadai ta rufeta jin tayi anyi hugging back nata hka taji ihu a kunnenta Wanda tasan Mimi ce da gudu ta kwaci kanta ta gudu...</p><p><br /></p><p>"Safeeya tayi daria wadda shekarunta baxasu wuce sha ukku ba Ina wuni yah AJ.lapia qlau safeeyatu yah kk.?"</p><p><br /></p><p>Toro baki tayi a hnkali tana buga kafafun ta a kasa ni Allah yah AJ.kai daine ke batamin suna ,Dan Allah ka daina karkasa Kamal yaje skull ya fada Dan karamin kaninta kenan."</p><p><br /></p><p>"Dariya AJ.yyi gamida rike baki eyeeeh cikakken sunan ki fane ,ta turo baki cike da shagwaba ni bana son wannan sunan nafison,ka kirani da Safeeya na.</p><p><br /></p><p>" Ni baxan iya da surutun kiba .plzzzzz,ina Mamy ?" Mami tafita olryt da haka ya Ciro waya ya dannawa angel dinsa kira ni xan tafi ..</p><p><br /></p><p>Tareda Rukaiyya suka fito ta xuba katon hijab kamar ba ita ce ke rawa a daxuba.</p><p><br /></p><p>"Ina wuni yah AJ."</p><p> Hararar ta yyi yaushe kk xama haka Rak??" Shuru tayi takasa basa Amsa ,wannan katon hijab fah??"</p><p><br /></p><p>Nan ma banxa tamasa ,Dan ta gane yana Neman tsokana ne kurum."</p><p><br /></p><p>"Olryt ..tunda baxaki Amasani ba kinga tafia ta sai da yakai kofa sannan ta daga murya plzzzz,,yah AJ. Kabar mana Mimi na kwana daya Dan Allah !</p><p><br /></p><p>" Na barta Ku xauna kuyi ta gulmar mutane ,baxae yuyu ba ki shirya xuwa anjima dake xanxo na tafi kiga amarya tunda na lura bakida kirki tunda nayi aure,baki taka gidana ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sabida hka ki shirya xuwa anjima tare xamu koma ,xan turo driver idan ban samu dawowa ba." </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Naji xanje amma ni baxanje gurin matar ka ba!</p><p>Da gudu ta nupi up stairs ,yana kwala mata kira bata kulasa ba hka Mimi ta juya tabi bayanta.</p><p><br /></p><p>_Some Times latter_.....</p><p> "Gaba dae Ahlin sameer meera suka shirya xuwa " umra cikin watan axumin Ramadan dama kuma hka sukeyi duk shekara ,satin su biyu suka dawo.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_"Ranar wata lahadi kwanan su biyu da dawowa mamin Aliya taxo Bauchi._""</p><p><br /></p><p>_inda suka kebe itada uwarta da kuma mom,Hajia Azumi bansan meke damun Aliya ba,gabade yanxu ta janye jikinta dga gareni ba dole ba jummai Aliya tana son Abu baxaki iya tursasa Abdul yyi mata ba Alhalin ya daukeki kamar uwa "Aliya tana so ta koma skull sau nawa ,zatayiwa Abdul jabbar mgana?_"""...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Nazo da shawara wadda a ganina itace mafita tunda yanxu sunyi 6 month da aure hka kuma bbu Wanda xae gane da sa hnnun mu acikin batar Abdul ni naxo da mafita!_...mafitar kuwa shine anan ta bude Jakarta ta fito da wani kullin mgani ta .mikawa mom" jiki na rawa ta karba ,ki saurareni da kyau kiji jummai kuskure daya xai rusa mana shirin mu...</p><p><br /></p><p>Kece xakiyi wannan Aikin jummai Hka bokana ya tabbatar min. Wannan garin mganin xaki xuba wa Abdul jabbar cikin Abun shan sa ,ma'ana lemu hka ."</p><p><br /></p><p>_muddin Abdul yasha bokana ya tabbatar min da xaibar gidan nan xaibar dukiyar sa komae nasa ma'ana xaiyi nisa daku wandda baxai kara dawowa ba har sae idan mu muka sa aka dawo dashi ...kinga xuwa lokacin mun xama shahararrin masu kudi dukiar sa sae yarda mukayi dashi ,na tabbatar kuma bakin kowa xai rufe ba Wanda xai kara tambayar sa kowa xai cigaba da hidimarsa "Aliya xata cigaba da juya companyn sa da dukiar sa gabaki daya" kowa xai dawo karka shinta." Akwae layar da boka yabani wadda yaman umurnin nayi rame mai xurfi nasaka ta aciki ,Wanda bbu Wanda xae kara tamabayr Abdul "hka bbu Wanda xai kawo mana matsala ,tundaga kan lauyoyinsa ,komae nasa da kuka sani. Wannan aikin boka ya tabbatar min yna da hadarin gaske ...dolene a kiyaye."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_mom ta sauke ajiyar xuciya kinyi tunani mai kyau ,Jummai xan dauko Dan yayana ya taimakawa ,Aliya xamufa samu kudi da yawa ihun murna Aliya tayi wlhi mom kinyi A rayuwa_""...daga goben nan xan xama billionaire ,murmushi mugunta tayi.</p><p><br /></p><p>_wani irin gumi yaji ya hada haka kuma yaji lokaci daya wani irin xaxxabi ya rufesa mom!_"""</p><p><br /></p><p>_Ashe ya dde tun daxu A kofar shiga dakin mom ,dama yana so yabata wasu takaddu ne dai daga cikin filayen daddy Wanda daddyn ya mallaka mata kwaya biyu."_..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kai tsaye part din hajja ya nufa tana xaune A falo tana kallon tashar sunna TV..</p><p><br /></p><p>Ganin Abdul jabbar a rikice yyi balain dga hnkalinta tana tunanin meya dga masa hnkali hka? "Haka tana tsoron tashin ciwonsa, cikin karfin hali ta mike tsaye mmki tsoro suka dirar mata ,ganin hawaye a idonsa wani nabin wani...jagwaf ! Ya fada kan kujerar ta hka ya dafe kansa ,dakyar ta bude baki ta fara tambayar sa cike da tashin hnkali [Truncated by WhatsApp]..</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.</p><p>16</p><p><br /></p><p>*This page goes to yhu khansa'u Muhammad Isah tnx for d " care And the support Writing*...#one love#.</p><p><br /></p><p>"Aza kansa yyi akan kafadar ta haka hajja ta dinga jin saukar hawayen sa ,cikin sanyin murya da nuna soyayyar ta a garesa ta fara mgana ynxu Abdul jabbar dama akwae abunda xaka boye min?" Ashe ban isa nasan damuwar ka ba."</p><p><br /></p><p>Girgiza kansa yyi ya rike hannayenta ga gam ,tamkar xata gudu tabarsa cike da tashin hnkali ya fara yiwa kakar tasa bayani abunda ya faru da tattainawar dasu mom keyi mmki tsoro lokaci daya ya kama hajja ,Dama nasan akwae ((Wata Rana !)) Da gaskiyya xatayi halinta Abdul jabbar kasan nasha fada mka haka jummai ba mutunniyar kirki bace nasan da haka tun ubanku na Raye ynxu meyayi saura ?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ki saurareni granny kibar komae a hnnu na nayi maki alkawarin xan gyara komae taya ya Abdul jabbar gaba dae zuciyata neman take ta tsinke kana ganin xasu barka ne ?"</p><p><br /></p><p>Idan a wannan hanyar basuyi nasara ba xasu samo wata ne ."</p><p><br /></p><p>"No granny baxasu yi ma nasara ba baxan sha duk Abunda xai fito dga hnnun suba." mafita daya itace xanbar garin nan na Dan wani lokaci kinga xasu fahimci nasha kenan ,baka da hnkali dukiyar ka xaka bar masu ,A'ah granny " ki saurareni" very cerefully kinga sageer shine manager a company na ko ba hakaba ,kinga idan bana nan xai iya yin settling din komae."</p><p><br /></p><p>Zan basu damar su samu miliyan ko biyar ne ,granny ta bata rae kana da hnkali ni wannan shawarar batayi min ba ."kiramin commissiona ya'n sanda kaga yarda xa'a aikasu gidan yari no granny xan dawo daukar fansa tane ,plzzzz ki taimakeni ba wasu kudi fane xasu samu ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kinga Aliya gobe xata hau kujerata ta office ,xata hau matsayina .."mata fa ne ba wata kwakwalwa suke dashi ba "kuma basu San komae ba kuma ga sageer nasan xai iya jure wulakanci Aliya ." indai akan companyn mune ,xan kira sageer xamu hadu mu tattauna A yau komae dare.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Banki taka ba Abdul jabbar ina xaka tafi ynxu kabar ni ? Ina xaka nufa oh granny ba nisa xanyi ba xan xauna acikin Nigeria ne bazan fita ba xan xauna wani gari hka . naje nayi rayuwar ko wta biyr ne hka.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ina kenan??"</p><p><br /></p><p>Dafe kansa yyi granny baxata taba fahimtar sa ba. Kano ya fada mata hakane Dan ta kwantar da hnkalinta shi kansa baesan inda yakeso xuwa ba ,ynxu xan kira aunty sadiya nayi mata bayanin komae itada mijinta har ma Aunty salma ,dama Mimi ce kurum matsala ta kuma ta koma skull xuwa lokacin da xata dawo nayi settling din komae."</p><p><br /></p><p>Uban tagumi hajja ta buga sae famar binsa take da kallo A gabanta ya kira Aunty sadiya yyi mata bayanin komae ,itama Aunty sadiya ba karamin mmki tasha ba hka itama hnkalinta ya tashi matuka "sae dae jin xai koma kano da xama na Dan wani lokaci yasa hnkalinta ya kwanta nan take ta dinga tsinewa mom."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A yinin ranar yna tareda sageer hka ya kashe wayoyin sa duka ,a part din granny yaci Abinci rana da dare sae karfe Tara dai dai na dare yyi shirin wucewa part dinsa nan ma granny hnkalinta yakasa kwanciya " hnnunsa na dama tarike idan xaka shiga gidan ka ka karanta duk addu'ar da taxo bakin ka kadae gane ya subbaci goshinta gamida Dan rungumota a jikinsa yafi minti biyu a hka sannan ya saketa yaja mata kofar ya nufi gidansa..."</p><p><br /></p><p>"Acan kuma bangaren mom har xuwa wnnan lkcin bata ga Abdul ba tayi mmki sosae ,hka kuma taji woyoyinsa a kashe ,Dan haka ta hada msa ruwan Lipton da Dan karamin flasks ta xubesu sa'annan ta zuba mganin akae ta bawa Aliya akan idan ya dawo " tayi kokarin taga yasha tunda taga yau bata gansa A part dinta ba" ta tabbata rashin kunyar sace ya motsa.</p><p><br /></p><p>★★★★</p><p>"Da sallama ya shiga bbn falon gidan hka ya dinga jin karar T.v. kwance take akan doguwar coach tana sanye cikin sleeping dress Riga da Wanda red " wando iyakarsa cinyoyinta hka ya kama cinyoyinta sosae sae ya'r fingilar rigar su wandda iya karta cibiyar ta haka Rabin breast nata. Duka a waje."</p><p><br /></p><p>Kamshin ddi yaji ya xiyarci hncin sa ,haka yyi kamar baigan ta ba da gudu taxo tayi hugging dinsa sosae tamkar xata koma cikin cikinsa, I miss yhu so much " my sweetheart, ina ka shiga ina ta Neman ka tun safe??"</p><p><br /></p><p>"Jaye ta yyi a jikinsa muna tare da sageer ne shiyasa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" ohkey muje kayi wnka hka taja hnnunsa tamkar wani yaronta har master bedroom dinsa.......</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Xata tayasa rage kayan jikinsa yyi saurin katseta tareda cemata ya gode da kansa ya Cire kayan ya kalleta ,kifita ki jirani xan shiga wnka yyi haka ne Dan bayason ganinta a tare dashi xuwa wannan lkcin."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kusan karfe goma ta koma dakin nasa ,ta iskosa yana ta Aiki kan laptop nasa kirar Apple "dan karamin center table taja ta aje cup tea din ina ta jiran ka kai Ashe ka dde da shiryawa " ta Dan tabe baki ganin bai kulata ba."</p><p><br /></p><p>Ga ruwan Lipton nan mom ta kawo mka ,ta ta jiranka baka shigoba shiyasa tabiyoka dashi ,ynxu sabida Allah ruwan Lipton din ma sae mom ta hada mka "ina matsayin matarka wnnan ae sae kasa ta hadani da mamina ,tace bna mka komae.</p><p><br /></p><p>" gaskiyya honey kadae na yimin hka ,tun farko ae kekika bata rawarki da tsalle banga laipin mom ba Dan ta hadamin ruwan lipton saunawa xan bukaci ki hadamin kice bakya iyawa bakida lpia "ko ki kawomin banxan uzurinki ,toki barni na huta plzzzz..</p><p><br /></p><p>Ya karasa mganar a zuciya tsoro ya kamata Mae kuma ya fusata sa hka??"</p><p><br /></p><p>"A tsorace ta dawo gab dashi ta xauna tareda Dora hnnunta akan kafadar sa tana tsoron karyace baxai shaba duk barikinta yau Sai taji yamata wani irin kwarjini duk da Abdul jabbar din mutunne marar son hayaniya da tashin hnkali."</p><p><br /></p><p>"Am sorry idan na bata mka nayi alkawari xan gyara kuskurena kaji mijina!</p><p>Tayi mganar cikin sanyi murya."</p><p><br /></p><p>Na baka Abaki ??</p><p>Ta tambayesa gamida daukar cup tea din har takae bakin sa yyi saurin dauke kae tareda Amsa naji na hkura kawae ki koma dakin ki xansha."</p><p><br /></p><p>"Ta langabar dakae tana Shafa sajen fuskarsa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" promise me?'</p><p>I promise bkinta ta aza dae -dae nasa ta fara xagaye lips dinsa hka tana huraa masa ,iskan bkinta cikin wani irin salo ta hade bkinsa da nata ta fara kissing dinsa romantically "tareda Shafa kowace gaba ta jikinsa A hnkali AJ ..ya riko kugunta shima ya shiga tayata burin Aliya a wannan tym.din yafita hnkalinsa kurum yasha ruwan Lipton din nan ,tayi sa'a taga ya fara enjoying dinta.</p><p>[11:7:2017/at 10:6@m.by Asmy b Aliyu].</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu...</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p>17</p><p><br /></p><p>Sun dauki minti goma sha biyar a hka lokaci daya kuma ya hnkada ta gefe kai tsaye ya Mike xuwa toilet bayansa tabi da kallo ..</p><p><br /></p><p>"Ya kwashe fiye da minti Ashirin A toilet tana nan xaune sae gaya ya fito daure da towel a kugunsa Ajiyar heart ta sauke honey kar Lipton din nan yyi sanyi pah?"</p><p><br /></p><p>"A gabanta yyi shirin barci mikewa tayi tsaye ,kije ki rufo kofar falon a gabanta ya dauki cup tea din murna fal a ranta tana barin room din nasa da sassarfa ,ya nufi toilet ya juye Lipton din cikin sink " ya aje cup din kan center table .</p><p><br /></p><p>Ya xauna gefen bed ya dafe kansa ."</p><p><br /></p><p>Dae -dae lokacin Aliya ta dawo hnkalinta ta maeda kan cup tea din ,taga bbu komae da alamr yasha kenan ,baka da lpia ne??"</p><p><br /></p><p>"Ta fada tana leken fuskansa ,kaina naji yna ciwo Dan murmushi tayi mgani ya fara aiki kenan kasha mgani ka kwanta ohkey xansha yanxu nan ya haye kan gadonsa yaja bargo..</p><p><br /></p><p>Ya kashe fitilan dakin yabar marar Haske ((Dim light))..</p><p><br /></p><p>" tafi minti ukku a hka da haka tabar dakin nasa gamida rufo masa kofar .tana isa daki ta kira mom A wya cike da murna take fada mata ae yasha itama mom murna ta hauyi....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Washe gari_....</p><p><br /></p><p>"Yana dawowa sallar Asuba misalin karfe biyar da rabi yah shirya luggage's dinsa.</p><p><br /></p><p>_car key dinsa ya dauka na frado ya kwashe duka muhimman document's dinsa ,har lokacin Aliya bata San meke faruwa ba tana can tasaki baki tana kwasar barci ,mota ya kaisu ya dawo_".</p><p><br /></p><p>"_gidan hajja ya nufa Lokacin tana xaune akan sallaya tana azkar kamar yarda tasaba ya shigo da sallama ya xauna gab daita hka tasamu ta takaita azkar din Dan tasan bayada isasshen tym." Haske ya fara fitowa Anan yake gaisheda Hajja ta amsa jiki sanyayye ,ya lura da haka sae ya basar hajja xan kama hanya."</p><p><br /></p><p>Sosae hajja ta nuna damuwar ta Nasiha tashiga yimasa A duk inda ya tsinci kansa kada ya kus'kura ya kusanci zina ko wani aikin alfasha " Da sanyin jikinta ta mike tsaye kai tsaye kiching ta nufa sae gata tafito dauke da katuwar kula da kuma flask Dan karamin da cup tea mika masa tayi ..</p><p><br /></p><p>Meye wannan hajja dambun na mane nayi mka wannan kuma ruwan Lipton ne ,ko kan hanya xaka iyasha Allah yakae lpia da haka ta juya xuwa dakinta .</p><p><br /></p><p>_"hka idonta ya cicciko da kwallah jikin AJ. Qlau yyi sanyi ,haka yaji xuciyarsa bbu ddi aje kayan hnnunsa yyi ya rungumeta sosae a jikinsa sun dde a hka plzzzz hajja karki daga ma kanki hnkali muje daki na rakaki ki kwanta kina bukatar Hutu granny_"..</p><p><br /></p><p>_A hka ya rikata xuwa bedroom dinta ya taimaka mata ta kwanta kan gadonta yaja mata blanket a hnkali ya rage tsawonsa ya subbaci goshinta tareda fadin I love yhu granny._</p><p><br /></p><p>_ya juya yabar bedroom din nata wannan shine karo na farko a rayuwarsa da xai nisanci granny haka ,dama kuma shi tafiye -tafiye basa cikin tsarin rayuwarsa tun dawowarsa ,daga kasar waje baitaba yin tafia haka ba_"</p><p><br /></p><p>_hajja bayansa ta zuba ma ido har ya wuce da sassarfa cikin takunsa na kasaita_".....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_ya dde xaune a mota kafin yyi karfin halin saka mata key body guard nasa xasu biyosa ya dga masu hnnu da mmki suka kalli junan su ,Dan wannan shine karo na farko da ya taba fita shi daya batareda suba."_</p><p><br /></p><p>"Indae a moto ne meke damun maigidan sune? Da haka maigadi ya wangale masa get ya fice da mugun gudu....</p><p><br /></p><p>★★★★★</p><p><br /></p><p>" Bayero university kano......</p><p><br /></p><p>"Yammata da samari ne keta kai da kawo hka kowa yana harkar gabansa wasu suna sauri su shiga lecture wasu kuma sun fito ...</p><p><br /></p><p>" Asmy Kinsan halin mutum men nan wae dole nikam sae kinga Emran a ynxu?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kinga rahama idan baxaki tsaya nagan sa ba kawae kiyi tafiyan ki sally kuma munyi wya suna kan hanya."</p><p><br /></p><p>Kwana nawa banga Em." Ba Dan Allah ki tausayamin mna Rahama ! wadda naji an kira da Rahama ta saki baki wangalau tana kallonta tana cikin Riga da skirt na Atamfa sae Dan yololon mayafin da ta yafa akanta sae kuma handbag dinta kalan veil dinta.</p><p><br /></p><p>Ita kuma Asmy tana cikin shigar rigar body hook dark blue Mae tsayi sae boy friend jacket dinda ta Daura a kai baka itama ta robace sae bakin mayafin da ta aza akanta irin na rolling din nan wandda ya tsaya dae dae kafadun ta. talkamin kafanta irin rufaffun nanne (kwaba shoe)" dark blue black beauty ce kallo daya xakayi mata kaga kakkyawar karshe. Tana rike da long book A hnnunta tana dubawa ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asmy !!</p><p>Kina da matsala yau kin jamana hasarar shiga class" tayi mganar tana jifanta da mugun kallo, itakam hnkalinta gaba dae baya kan Rahama ta xuba eyes nata kurum taga inda king din nata xai fito..</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>18</p><p><br /></p><p>"A hnkali motar ke nufowa wurinsu gaba dae suka maida hnkali akanta wadda tayi balain tafia da imanin su kirar((Toyota Priusde Anaconda))".. Baka wuluk sae sheki take ba'a hngo wandda ke cikin motar sabida gaba dae rufe take da bakin tinted."</p><p><br /></p><p>Saleema ce ta fara fitowa dga motar ganin ta yasa Asmy sakin wani kayataccen murmushi ,cikin shigar Alfarma sally ta iso gurinsu '....wani hadadden guy ne ya fito dga side din driver yna cikin shigar kananan kaya brown din T.shirt ce a jikinsa Mae dogon hnnu ta Dan kama sa kadan kasancewar yau garin na kano tamkar a sauke da ruwan sama sae wandon Jean's milk Wanda ya Dan kama sa ,black beauty ne ba wani kykkyawa bne Emran sae dae akwae Aji na karshe ya tara wata irin suma akansa wadda taci kudi gurin gyaranta.</p><p><br /></p><p>"Rufaffun tallamine a kafansa bakake na maza ,sae glass din frada bki dake mnne a idonsa ,dogone sosae hka bayada yna da jiki Dan ko kusa ba'a sashi layin marasa su kiba."haka kodan ba bbu tarin gashi akan fuskarsa kamar yarda wasu samarin keyi.</p><p><br /></p><p>"Emran hasheem kenan cikakken saurayi wandda baxai wuce shekara a kalla ishirin da biyar ba A dunia Hutu da jin ddi da ya samu yasa ya koma wani irin ingarmar mutum tamkar Dan shekara Talatin a dunia."</p><p><br /></p><p>"Hannnayen sa duka xube cikin Aljihun wandon sa ,yana binta da wani irin kallo duk da glass din dake manne a idonsa bai hanata kasa gane yna kallonta ta ba.</p><p><br /></p><p>Cikin takunta na kasaita ta nufi gurinsa hannayen sa ya bude mata ,tana xuwa ta shige jikinsa rugume juna sosae sukayi yyinda Emran din ya sauke wata nauyayyiyar ajiyar zuciya ,lokaci daya Rahama ta dauke kanta akan su hka ranta taji ya baci idan da sabo ta saba ....Dan Abun Asma'u kullum kara karuwa yakeyi."</p><p><br /></p><p>"Itace ta fara jaye jikinta cikin nasa ,tayi folding din hnnunta a kirjinta ta Dan jingina jikinta da mota sa'anan kuma ta bata rai sosae tamkar baita bace mai fara'ar nan ta daxu ba."</p><p><br /></p><p>Sae Abun ya basa daria duk da kuwa yasan laifinsa."</p><p><br /></p><p>"Karasowa gab daita yyi yadan sun kuyo yna leken fuskarta " cikin wata hadaddiyar murya ya fara mgana meya faru kuma baby na??"</p><p><br /></p><p>Da alamr bakiyi missing dina ba." Ya karasa mganar yna kallonta ,kauda kanta tayi wani gefe sa'annan ta fara mgana a shagwaban ce bakai bane sabida Allah minti nawa kasan mun dauka anan ,xakaje kayi xamanka ynxu kasa munki Attending din wannan lecture din ,kuma kasan malamin nan ba yada kirki takara sa mganar tamkar xata saka masa kuka."</p><p><br /></p><p> "Dan murmushi yyi idan da sabo ya saba da wannan rigimar ynxu xasuyi wasa da daria lokaci daya kuma sae ta birkice masa ,Am sowieee plzzzzzz sweetheart wlhi laipin saleema ne ta tsaya jiran dad ne kowae xata karbi wasu kudi daga hnnunsa .A nesa ta hango wasu yammata sun xubawa Emran ido ,nan take taji ranta ya baci ta juya tana kallonsa sae taga gaba dae hnkalinsa na kanta shaye da toka ta kallesa ,ka tafi gida xuwa anjima ka dawo idan mun fito dga lecture " xan kiraka make kafada yyi alamr baisan xancen ba."</p><p><br /></p><p>"Xan jiraki ni dae yyi mganar a shagwanban ce " A zuciya tayi gaba a bunta tabarsa anan dama su sally sun karasa "A department yana kwala mata kira bata koma saurarensa ba ,shima a zuciya ya juya ya shige motar sa ya mata key yabar cikin skull din.</p><p><br /></p><p>" A yinin ranar hka suka kare lecture's bata kula kowa ba ,suma friends din nata sun gane tayi fada da hero din nata kamar yarda friends dinta ke kiransa Wato Rahama da kuma sally Wanda kanwar Emran din ce.</p><p><br /></p><p>Sae 4 suka gama lecture draver ta tsaya jira itada Aunty Zulfa'u wadda tana shekarar ta na karshe ne. duk da kasancewar unguwar su daya da Rahama hka layin su daya ,itama drivern ta yaxo ya dauketa.</p><p><br /></p><p>Akai akai Asmy ta shiga tsaki ganin har ynxu sallau driver bai karaso ba ,Aunty zulfa da ta hasala tace wae ubanwa waye sa'anki dakike famar jawa mutane tsaki??"</p><p><br /></p><p>Ta Dan turo baki tana kallon ,yayar tata Toni sabida Allah dake nake xakibi ki sakawa mutum ido takara sa mganar cike da rashin kunya."</p><p><br /></p><p>"Kwafa zulfa tayi xaki sani ne bari mukara sa gida dai- dai nan sallau ya karaso Gaba dan su suka shiga side din baya gaskiyya Mln sallau ka dde ,cewar Asmy yi hkuri Asma'u sae da naje nasha mai Aunty zulfa tace Dan Allah daena kula mahaukaciyar mukara sa gida.</p><p><br /></p><p>" ke dai ce mahaukaciya wlhi bani ba."</p><p><br /></p><p>Ta fada cike da tsiwa zulfa takai mata mari tayi saurin dafe kuncinta mln sallau sae famar basu baki yake bakin Asma'u yaki ya mutu haka suka isa gida suna gama parking tari ga zulfa fitowa."</p><p><br /></p><p>Da gudu ta karasa cikin gida falo ta saki jakar karatun ta aza hnnu akae ta saki ihu dai-dai nan yah Anas ya fito shida Abbansu."</p><p><br /></p><p>"Wata uwar tsawa yah Anas yyi mata ke mahaukaciyar inace?" Kuka ta saka Abba ya karaso yna tambayr meya faru ?"</p><p><br /></p><p>Dae -dae lokacin Aunty zulfa ta karaso cikin kuka ta fara mgana Abba ka daukar min driver ni na gaji da shiga mota daya dasu Aunty zulfa bbu abunda suka iya sae cin zalina." Ta fada hawaye na xubar mata nan Abba ya juya kan Aunty zulfa ke Zulfa'u meya faru??"</p><p><br /></p><p>Anan ta fadawa Abba komae ,nan ya juya kaina Asma'u bakida gaskiyya meyasa bakya yiwa yayunki biyayya?"..Abba in....saurin katseta yyi idan bakibar wannan halin naki ba baxamu shirya ba..anan yasa kai ya fita yah Anas yabisa a baya sae famar dokamin harara yake na murguda masa baki tareda saurin dauke kaina dakin mama na nufa ,yyinda Aunty zulfa tayi dakin su...</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>19</p><p><br /></p><p>"Alh.Umar Aliyu omra haifaffen Dan garin kano ne A kano aka haifesa anan yyi karatu hka acikin kano ya girma ,mahaifinsa ya rasu tun kafin yaxo dunia sae mahaifiyarsa da ya tarar Da kuma yayarsa Asma'u Wanda daga ita sae shi...</p><p><br /></p><p>Yana da shekara goma Allah yyiwa mahaifiyarsa Rasuwa ,lokacin baima San kansa ba yyinda rikonsa ya dawo hnnun kawun sa shida yayarsa Asma'u tana gama secondary skull aka aurar daita,ga wani chairman na local government."</p><p><br /></p><p>Barin Asma'u gidan Umar yaga rayuwa a gidan kawun nasa da tsangwama ,ga matan kawun nasa rasuwar kawun su Asma'u ta dauke Omar rikonsa ya dawo nta ,karatun sa da girman sa A hnnun yayar tasa yake kasancewar mijinta Dan siyasa ne yana sonta sosae ,haka yyi karatunsa a Jami'ar ahmadu bello dake xaria A fannin Economic computer"...</p><p><br /></p><p>"A hka ya samu Aiki " A pilgrim ,yana da matar aure daya Hajia hadiza shekara daya da aurensu ta haifi Anas ,yana cika shekara biyu aka haifi Aliyu Wanda suke kira Haidar ,shima shekarar sa biyu aka haifi Abdul hameed."</p><p><br /></p><p>Daga nan kuma shuru shekara hudu ,Shuru daga Aliyu kwatsam Mama ta samu ciki nan Alh.Omar ya dinga Addu'ar Allah ya basa macce yasa suna yayar sa Asma'u wadda bata taba haihuwa ba. (Blood cancer)"..</p><p><br /></p><p>Shine Ajalinta mutuwar tashigi Alh.Omar duk tsawon wannan shakarun bata taba haihuwa ba." Haka arzikin Alh.Omar ya bunkasa tun yana Aiki a karkashin pilgrim ,duk shekara sae yaje hajji ko omra anan ne ya samo sunan Alh.Omar omra."</p><p><br /></p><p>Matar sa na haihuwa aka samu shema'u haka dae Abba ya rada mata inda yace idan Allah yabasa wata xaisa mata Asma'u xokiga yarda yayunta ke nuna mata so shekara biyu akayiwa shema'u kanwa wato Zulfa'u anan yah Hameed ya samu abban su Abba har yau baka yiwa mai sunan umma takwara ba?"</p><p><br /></p><p>Wato yana nufin Asma'u tun kafin rasuwarta dama Abdul hameed ne nata shine mai sunan mijinta ,Abba yyi murmushi karka damu Abdul hameed idan maman ku ta sake haihuwa sunanta Asma'u ko bayan raina."</p><p><br /></p><p>Shuru shuru hadixa bata kara samun cikiba shekara shidda har sun fidda rae sae ga cikin Asma'u nan suka Shiga murna Allah yasa Maman su tasamar masu kanwa macce ,cikinta na shiga wata Tara tayi doguwar na kuda wadda bbu Wanda yasa ka ran hadiza xata rayu ,bata taba shan wahalar haihuwa ba irin wannan kwana biyu tana na kuda.</p><p><br /></p><p>"A yinin na ukku ne ta haifi katotuwar ya'rta mai kama da ubanta sak! Dan duk cikin ya'yansa Asma'u ke diban kama dashi sauran kuma duk mahaifiyar suce kasan cewarta bafullatanar Adamawa ce..</p><p><br /></p><p>An sha shagali sosae A bikin Asma'u hka yayunta na nuna mata so hka ta taso cikin gata da kulawa a kowane fanni...</p><p><br /></p><p>Da yake Hajia hadiza ma'akaciya ce hka kuma kwarrrar likitar mata anan asibitin Mln aminu kano ,ita da kanta tayi addu'a Allah ya tsayar mata da haihuwa hka Asma'u ta xama auta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Barin ta biyu ,bayan yaye Asma'u haka ya'yan su Anas da Aliyu a tare suka shiga mkaranta tun daga primary har secondary da yake kusan Kansu daya ,Anas a fannin pilot ya karanta yyinda Aliyu ya karanci fannin soja ,sai ya hameed Wanda yake sha'awar likita ,sae Aunty shema wadda ta karanci law Shekara daya dagama makarantar ta a jami'ar Ahmadu bello dake Zaria ,sae Aunty zulfa dake shekrara karshe Anan b.u.k . kano sae ni Auta Asma'u wandda A tashi na nayi fitina,rigima da Neman tsokana ba kadan ba ,haka nasamu gata ta kowane fanni sae dae duk da wannan gatan nawa baisa iyayenmu suka kasa bani tarbiya ba ,Dan bana mantawa a gidan mu ko kana jami'a baka daina xuwa islamiya ko sauka Littafai Dari Dari kuwa xakayi sai idan kayi aure ne ko kasamu Aiki....</p><p><br /></p><p>Ina da shekara goma A dunia Abba ya kara Aure da wata malamar makaranta Zainab ,xaman su da mama Abun Sha'awa tamkar mamace ta haifi Aunty amarya dama haka muke kiranta haihuwar farko ta samu y'ah macce akayiwa mama takwara hadiza ana kiranta Afra sae kuma kaninta mai sunan Abba ana kiransa sageer </p><p>.</p><p>Da ganan itama haihuwar shuru ,bangama secondary skull ba.Abban mu yyi ritaya ya koma kasuwan ci inda ya buda manya-manya shaguna a nan kasuwar kware ,bbu abunda baya xubawa a shagon tun daga kan kayan cosmetic ,wanda shago daban ne ya ware sae kuma na atamfa da Le'ss da sauran kayan mata bbu laipi arxikin Abba sae bunkasa yake yyi fice sosae haka ya wadata iyalinsa sosae duk da ritayar da yyi A ma'aikatar pilgrim baisa duk shekara ya kwashe iyalinsa suje omra ko aikin hajji hatta da sageer dake karamin mu dashi ake xuwa.</p><p><br /></p><p>Harda su yah Anas da ya Haidar dake da aure harda ya'yah bibbiyu ,duk shekara sae sunje harda iyalansu ...acikin yayuna kakaf nafi shiri da yah hameed shine kadae ke sona su kuma gabadan su cin zalina suke musamman yah Anas da yabi ya tsaneni kasan cewar ,nikaina nasan bana jin mgana haka inada daukar mgana sosae ina girma kamanni na sak na mahaifina hka gabadae nice baka a gidan mu...gaskiyya duka yayuna sun fini kyau ,idan na bata ma yah Aliyu rae a wata rana yana kirana da Kalmar da sai nayi kuka na yini ina zazzabi wato ya'r baka kuma mummuna natsani Kalmar A rayuwata Abba yyi fada har ya gaji da haka aka Samar min Admission anan jami'ar Bayero inda na dage akan lallai irin karatun Abba xanyi wandda duk gidan mu bbu wandda yyi kalan sa ,wato (Economic computer))... Kusan tare muka shiga skull da Rahama ,tun muna yara tare muka taso gida daya ne tsakanin gidan mu da nasu.. "</p><p><br /></p><p>Isalamiyar mu daya haka iyayen mu amminan junane ,Yayan Rahama daya ne yah Al'ameen wandda Dan sanda ne kusan sa'a suke da yah Aliyu Dan abokinsa ne ,sai Rahama sa'annan Aysha muna shiri sosae da yah Al'ameen har ya'n gidan mu ke ganin sona yakeyi ,acewar su duk da shima kyakkayawa ne ajin farko na kanyi daria nace aini police basa burgeni kudae jinin mu yaxo dayane.</p><p><br /></p><p>Sam-sam halin mu baizo daya da Rahama ba Dan ita macce ce mai sanyi yyinda ni nake da zafi ko fada aka tareta Nike sayewa islamiya da makaratar boko har girman mu kuwa ......iyakarmu wata 3 a jami'ar Bayero Aka kawo wata student mai suna saleema ,itama ajin mu daya jinin mu yaxo dya haka rawar kanmu daya....kwatsam Emran ya fado acikin rayuwata wandda ya sauyamin duniata da tunanina wandda A sanadiyar sa na fara samun matsala da mahaifina ...........</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p>20</p><p> "Haduwar mu da Emran ya samo A saline yaje daukar kanwarsa saleema ,to ranar dama ni daya naxo skull aunty zulfa bata da lecture ranar.</p><p><br /></p><p>Muna fitowa sae ga kiran mama wae nashiga adai daita sahu sabida xata Aiki Mln sallau yakaiwa Abba abincinsa " A kasuwa ,hka naji tamkar nayi kuka sabida ba abunda nafi tsana a rayuwata kamar na shiga motar haya gashi rahama itama bataxo ranar ba sabida bata jin ddi,muna tsaye da saleema taga ynayina ya canja anan take tambaya na meya faru nan nake shaida mata akan driven mu baxai samu damar xuwa ba.</p><p><br /></p><p>Ki bari mu wuce dake mna Asmy nima driven nke jira.</p><p><br /></p><p>" da farko naki amincewa da hkan sae da ta nuna min bacin ranta sa'annan bamu jima ba sae ga motar gidan su maimakon muga driver sae mukaga sabanin hka ,Emran ne saleema ce ta bude man side din baya.</p><p><br /></p><p>Yyinda ta bude na gaban ,ta shiga Nan na daga ido na gaishesa "muna hada ido sae da gabana ya fadi ya amsamin tamkar ansa sa a dole ,naji haushi ba kadan ba."</p><p><br /></p><p>Yah Emran saukar yaushe??"</p><p>"Daxun nan tare muga dawo da senior da matar sa hirar su sukeyi sama-sama ina jinsu ban shiga hirar tasu ba Dan da alamr guy din nan xaiyi jin kae.</p><p><br /></p><p>Har kofar gida suka ajeni nayi godia na fito daga motar ,nashige gida abina.</p><p><br /></p><p>" kwana biyu da faruwar hka kullum sae mun hadu da Emran "A makaranta . yakae sally ko xai daukota ,abunda na lura dashi shine yana jin kansa da yawaa..</p><p><br /></p><p>Sae Naji na fara tsanarsa a raina .wandda bansan dalilin tsanar ba hka kurum Naji baimin ba wata rana muna hirar sa da sally nake cemata nikam yayanta baiyi min ba ya cika ji da kansa ,tayi daria Abunta baki dae fahimce sa bane kawae Asmy amma wlhi yah Emran yana da sauqin kai sosae anan to take bani tarihin ya'n gidan su mata 3 ga daddyn su dayan ta rasu hka itada Emran sune a daki daya ,momyn suce ta ukku a gidan suna da yawaa sosae a gidansu A takaice.......</p><p><br /></p><p>Emran shine babba a dakinsu sae saleema sadiya da kuma sadiq gabadae maxan gidan su basa karatu a Nigeria har nake tambayar ta meyasa shi baya karatu shine take fadamin ya fara A Cyprus "ya kuma dawo wae bayason skull din."</p><p><br /></p><p>Ynxu kuma malesia yakeso nayi daria lallae yayan nan nki dan rainin hnkaline.</p><p><br /></p><p>"Mun fara shiri da emran ne lokacin da akayi wani bikin Aure a gidan su bna mantawa sally tabarni a dakinta ta shiga side din momyn su kwatsam ,saiga emran ya fado dakin da sallama na Amsa fuska bbu walwala ."</p><p><br /></p><p>Asma'u ya gida ??"</p><p>Yarda ya kira sunana Naji sunan har araina ,A hnkali na dago muka hada ido da mmki shi din ne ,wani irin kallo yake yimin wandda na kasa fassara sa."</p><p><br /></p><p>Yaki dauke kansa akaina sae nice nayi saurin dauke idona."</p><p><br /></p><p>Zoben hnnu na nashiga wasa dashi ,baxaki amsani ba sabida kin tsaneni "da Sauri na dgo na kallesa karo na biyu ni yaushe nace na tsaneka sabida Allah?" Nayi mganar gamida turo baki abunda yaba sa daria kenan karo na farko da nafara ganin dariar sa kenan haka na koma tamkar wata shasha ina kallonsa ,ya tsagaita da dariar tasa bansan lokacin da na fada masa ka cigaba da daria wlhi kafi kyau." Make kafada yyi naki wayon.</p><p><br /></p><p>Murmushi nayi mai kyau wandda sae da kumatuna suka lotsa ,dae dae kuma lokacin sally ta dawo ganin yayan nata a daki tasha mmki ."</p><p><br /></p><p>"Bros yah??"</p><p>Tayi mganar gamida aje katon tray a hnnunta qlau ,nida kawar nan taki mna tana jin kanta da yawaa.</p><p><br /></p><p>"Daria sally tayi auhh wae Asmy ita din."</p><p><br /></p><p>Xan fita idan ta tashi xuwa gida ki kirani ni xan maidata ,hka ysa kai ya fice dga dakin nan nabi bayansa da kallo ,Ashe duk yadda na fassara sa ba haka bane.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kaini gida da Emran yyi ya amshi digit,dina daga nan kuma muka fara wata irin soyayya dashi ni kaina nasan ina son Emran ina yimasa wani irin so wandda bantaba tunanin ni Asmy xanyiwa da namiji Shiba a rayuwata ,haka lokaci yaja kwanakki suka shude A gaban kowa bana iya boye son emran Rahama tasha yimin Nasiha akan na rage wannan son da nake masa kar wata rana yazo yyimin illah dan ba lallai bane A rayuwa ka samu Abunda kakeso nakan ce da Rahama kina tunanin Akwae ( WATA RANA !)) Da xata xo wadda baxan iya samun Em dina ba?" Plzzzz Rahama ki daina yimin wannan bakin dan Allah ,bance Ku Rabu ba Asma'u na daice ki rage rawar kae Akansa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yawan cin maganga nun da kanwar tata kemata kenan a yawancin lokutta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wasa-wasa muka kwashe wata biyar da emran batareda kowa ya sani ba a gidan mu iyaka muyi wya ko mu hadu A skull ko yawancin lokuta ,idan ina kewarsa naje gidan su har dakinsa na barci ...wannan shine babban kuskuren da na fara Aikatawa a rayuwata na yarda da soyayyarsa fiye da zaton mai karatu nayi ammana da bbu wata macce Azuciyar emran saeni Asma'u Umar omra ." tunda muka hadu dashi ban kara kula wani da namiji ba ko friends dina maza na kyale kowa kasancewr Emran mutun ne mai kishin gaske ,haka nima yna da saurin daukar xafi muyi fada mu shirya haka rayuwa ta cigaba da tafia sannu a hnkali hallayya na ya fara canjawa. Bna jin shakkar emran ya taba jikina ko a ina ne nariga nagama yarda dashi ..</p><p><br /></p><p>Wannan kenan Atakaice.....</p><p><br /></p><p>"A ranar fushi na hauyi da kowa a gidan emran ya kirani baya kirguwa naki na dagawa ,haka shima ya shareni mun hadu " WhatsApp na aza dp. Wani friend dina nasan kuma xaiji haushi dan haka na Daura sa akai kuma nasan xaiyi mgana ne.</p><p><br /></p><p>"Nan naga ya fara typing...."</p><p><br /></p><p>"Da alamr mgana xaiyi min .</p><p>Sae can ya rubuto min plzzzz ki cire wannan pic din A dpn ki ,sharesa nayi ban maida masa reply ba .".</p><p><br /></p><p>Karshe ma na sauka gamida kashe wayan duka duk abunda xaiji haushi nasan nayi sa a ranar ,duk da ni kaina dauriya kurum nakeyi bana iya jure fushi da Em dina...</p><p><br /></p><p>★★★★</p><p><br /></p><p>" fitowar sa kenan da makulli mota a hnnunsa ta kallesa cike da fara'a sae kuma ina Abdul??" Cewar Aunty salma tana kallonsa cike da kulawa ,ya tsine fuska yyi xanje nan B.U.K . Aunty ina son na hadu da nura Kinsan acan yake lecturing ." kace yau xaka sha kallo ga ya'mmatan b.u.k !</p><p><br /></p><p>"Shaye da toka yake kallon Auntyn nasa ,me kuma ya kawo wannan mganar Aunty ??" ..karkisa na fasa xuwa Kinsan bana son yawan kallo hasalima na tsani hkan ke dae kiyimin addu'a Allah ya hadani da drama queen dita itace kurum "A zuciyar Abdul jabbar!</p><p><br /></p><p>Aunty salma tayi daria sabon salo Abdul jabbar yaushe kafara son wata a ranka??"..... Iz a long story aunty sae na dawo kiyimin addu'a ae kullum muna kanyin ta ...daxu ma hajja ta kira wae bata samun wyar ka ."</p><p><br /></p><p>"Oh gosh!!</p><p> Nama hajja laipi ba kadan ba ,idan na fita xan sae sabon layi xan kirata anan yama Aunty salma ya fice daga falon."..</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu ..</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>21</p><p><br /></p><p>"ynxu kuna ganin idan nakai masa Assignment din nan ba baxai nemi ya wulakanta ni ba mussaman idan yaga ina rokonsa.</p><p><br /></p><p>" Rahama baxan fa yarda ya wulakanta ni ba a banxa kefa ke nema Asma'u dole sae kin kai zuciyarki nesa sally ta karbe xancen da haka xakiyi Asmy ki kwantar da kanki ki rokesa ya karbi Assignment din nan ynxu muje muraka ki ki gansa a office dinsa ,haka gabadai suka nufi office din nasa badan xuciyar Asmy ta yarda da friend's din nata ba.</p><p><br /></p><p>"Dan a zahirin gaskiyya Bata son wannan Mln Nura din ya cika daukar kansa wata tsiya amma idan taga yarda yake shiri dasu Aunty zulfa sae abun yabata mmki har ta gano yadae tsaneta kurum ne kamar yarda itama ta tsanesa."</p><p><br /></p><p>Suna isa bakin office dinsa ga sunan sa nan radau a jikin kofar (Nura Muhammad kurfi")..</p><p>Samun kanta tayi da hararar kofa sannan ta tsaya cak !</p><p><br /></p><p>Da mmki Rahama da sally suka tsaya suma suna kallonta me kuma ya faru??" Lokaci daya suka jefa mata tambayr idan naje ya wulakanta ni baxan taba yafe maku ba.''</p><p><br /></p><p>Mun yarda sae da sukayi knocking aka basu ixinin shigowa sa'annan suka hada baki wajen yin sallama "wani haddadden kamshine ya bugi hancin su wani hadadden guy ne suka hango tsaye hka ya basu baya yna amsa wya cikin sanyayyan turancin sa da kuma muryar sa ,mai taba zuciya da ruhi dukan su bbu wadda bata shiga tunanin wannan wane irin haddadden guy ne haka Mln Nura ne ya katse masu tunanin su yana hakin ce akan kujera mai juyawa yana cilla bairon dake hnnunsa ,Ya masu kwarjini sosae Rahama CE tayi karfin halin fadin sir dama gurin ka mukaxo ..bayan sun gaishesa.</p><p><br /></p><p>" murmushi yyiwa Rahama meke tafe daku Rahama??"..</p><p><br /></p><p>Ya fada dauke da fara'a " A fuskarsa dama kuma yna shiri da Rahama sosae ,ganin yarda yake fara'a Asmy ta hareresa "A ranta take fadin mugu kawae..dama Asma'u muka rako ta kawo assignment nata ,sabida ranar da akayi submit bata nan nan take yanayin Nura ya canja kuke da bakinta kenan ita bata da baki?"...</p><p><br /></p><p>Dan haka Ku fita kubari tayi mgana jiki sanyaye suka fita yyinda aka bar Asmy tsaye hka taji tamkar ta bisu a zuciya dae-dae lokacin AJ ya kammala wyar da yakeyi juyowar nan da xaiyi idonsa cikin nata " ya raxana da ganinta amma ita ko a jikinta karshe ma dauke kanta tayi ...</p><p><br /></p><p>"Tsawa Nura yyi mata malama idan bakida abun fada ki fitar min a office kinyi min tsaye akai ,har cikin ran AJ.yaji tsawar Dan haka ya tsaya cak !</p><p>Yna kallon abokin nasa da mmki ....</p><p><br /></p><p>" wani irin bakin ciki taji ya mamaye ta hka ta samu ta lallashi xuciyar ta ta fara basa hkuri wani mugun kallo yake jifanta dashi na lura bakida tarbiya yarinyar nan ,Dan haka get out my office right now!</p><p><br /></p><p>"Kije a koya maki tarbiya sa'annan ki dawo gareni a fusace ta daga dara -daran idonta tana kallonsa ya hango tsantsar bacin rae acikin su yaji ddi a ransa da yaga ran nata ya baci ...</p><p><br /></p><p>Rasa tayi mai xata fada masa ba laifin sa bane laifin su Rahama ne ta juya a hnkali xata bar office din AJ.ne yyi saurin shan gabanta bani Assignment din naki?"</p><p><br /></p><p>Yyi matagana cikin wata irin murya mai cike da bacin rae."</p><p><br /></p><p>Kallon banxa tashiga jefa masa idan kana sonka da mutunci ka jayemin a hanya na wuce nafi karfin ya wulakanta ni wlhi kuma baisa ya wulakanta ni ba." Dan haka bana so !</p><p><br /></p><p>Kaji nace bana so!!</p><p>"Tayi mganar tana bude masa manyan idonta meyasa xaka kulata AJ. Ai girman kanta baxai bari tabaka ba ka barta kawae tsaki tayi tabi ta gefen sa ta bar office din a fusace."</p><p><br /></p><p>A fusace AJ.ya nufo gurin Nura anan ya fara balbalesa da bala,i haba Nura wannan wane irin wulakanci ne ka tsiro dashi ?"</p><p><br /></p><p>A gabana friends din yarinyar nan suka baka hkuri ka korasu waje kace sae da kanta ta baka shine xaka wulakanta ka haka?"</p><p><br /></p><p>Cikin fushi AJ. Ke mganar a wannan lokacin Wanda Nura yasha mmki ...murmushi Nura yyi hello relaz...wat did yhu say??"</p><p><br /></p><p>Look Nura ba lokacin wasa bane ynxu "dis ix d first & last tym da xaka kara wulakanta ta hka bana son kana mata tsawa ko fada ." bana son ganinta cikin bacin rae "</p><p><br /></p><p>Did yhu get DAT? This is d only problem only!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Baki wangalau Nura ya saki yana kallonsa ,me AJ. Ke nufi akan Asma'u haka Nura yaji ransa ya baci ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Am going to find d solution to my self I will find d solution."</p><p><br /></p><p>A fusace AJ. Yabar office din nasa kallon mmki Nura yabisa dashi..</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>22</p><p><br /></p><p> "Kai tsaye wajen friends din nata ta nufa da wani irin mugun yanayi hangosu tayi jikin motar Emran A tsaye daga nesa ya harde hannayensa a kirji yana kallonta ."</p><p><br /></p><p>Idonta ne suka kawo kwallah lokaci daya ji tayi tamkar ta juya sae kuma ta tsaya cak! Rahama ne da sally suka ida karaso gurinta hnkali tashe.</p><p><br /></p><p>Ya kukayi dashi??"</p><p>Cewar Rahama ganin kwallah a idonta yasa suka xuba mata ido Kallon su tayi ta dauke kai kai tsaye gurin Em dinta ta nufa batare da ta masa mgana ba ta bude side din baya ta shige sally ce ta masa mgana da ido akan yaje yabata hkuri.</p><p><br /></p><p>Daita da Rahama suka kalli juna anan suka shiga tunanin meye Mln Nura ya fada mata ta fito a hka?"</p><p><br /></p><p>Dukan su bbu mai amsar tambayr nan idan baita ce ta fada masu ba Hango AJ.sukayi ya fito daga office din shima ransa a matukar bace ,sae ynxu ne suke masa kallon tsaf kasancewar basu ga fuskarsa ba tun farko Duk cikin su biyu din bbu wacce bata tsorata da kyawun sa ba.</p><p><br /></p><p>"Musamman sally wadda ta tsaya karewa shigensa kallo yana cikin wani farin boyel dinki Riga da wando na captani ya aza hula baka haka talkamin kafafunsa rufaffune suma bakake sae agogon dake sakale a hnnunsa dagani kansa mai tsada ne ".....</p><p><br /></p><p>Har yafice dga gurin sally bata daina kallonsa ba. Nan take taji tana yimasa wani irin so wandda idan bata samesa ba xata iya rasa Rayuwa ta." To amma ta yaya ??" Da gani guy din nan xaiyi jin kai ji yarda ya'mmata ke binsa da ido ,Wanda ko tafiyan sa kurum abun burgewa ne."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wae meya faru ne habibaty?" Yyi mata tambayr cikin nuna damuwa daita ,bata kallesa ba balanta na ta amsa sa hawaye yaga suna fitowa a cikin idanunta nan take Emran ya rude ."</p><p><br /></p><p>"Duk dunia ba abunda yafi tsana irin yaga saukar hawayen Asmynsa shin meya taba xuciyar ta haka ?" Bata da zabi ta aza kanta kan kirjinsa ta fashe da wani irin kuka mai sauti haka ya dinga jin saukar hawayenta "A hnkali ya dinga Shafa bayanta alamr lallashi tunani take me xatayiwa Mln nura Wanda baxai taba mantawa daita ba A tarihin rayuwar ta??"</p><p><br /></p><p>Dagota yyi a jikinsa farin handkerchief,yasa yana goge hawayen idonta xuba masa ido tayi ganin duk yabi ya damu tana jin wani irin sonsa na huda duka ilahirin jikinta .samun kanta tayi da kwakwalo murmushi ganin yarda yake kallonta ko kadan bata son ganinsa A damuwa ."</p><p><br /></p><p>"Fadamin meya saki kuka? Kawae dai ina son nayi kuka ne shine kawae ,ba fushi ka hauyi dani ba kwana biyu ta fada tana Nuna masa ya tsunta biyu ✌🏽murmushi dauke A fuskarta.</p><p><br /></p><p>Karya kike Asmy fadamin meye matsalar?" Wannan karon cikin fushi yake mganar ,tafi kowa sanin halinsa idan yyi fushi bbu kyau fuskarsa ta tallabo da hannayen ta duka biyu.</p><p><br /></p><p>"Believe me !! Bbu Abunda ya faru ta fada tana kallon cikin idonsa ajiayar heart ya sauke fuskarsa ya hade da tata ta gano me yake nufi sae tayi saurin dauke kanta agogon hnnunta ta duba saura minti goma sha biyar su shiga lecture ,gobe xanje Abuja."</p><p><br /></p><p>"A Dan tsorace ta kallesa dama yasan abunda tafi tsana kenan taji xaiyi tafia xanje na karbo Visa ta ya fito tareda daddy xamu tafi jin mganar Visa yyi balain daga hnkalin ta batace komae ba tafice daga motar kallonsa tayi Anjima idan xan tafi islamiyya xan kiraka mu hadu a bayan layin mu." Tayi mganar cikin rawar murya bata jira mai xai fada ba tayi gaba abunta .."</p><p><br /></p><p>"A lecture hall din ta nufa kai tsaye acan ta tarar dasu Rahama mai makon ta karasa gurinsu sae tasamu gefe ta xauna basu da xabi suka nufo gurin ta anan suka shiga tambayr meya faru tsakanin ta da Mln nura bata boye masu komae ba ta fayyace masu abunda ke faruwa." Sun sha mmki sae dae ita a nata bangaren ta manta da hakan yanxu tafiar Em dinta ce matsalar ta ,sunyi kusan lecture har biyu amma bbu abunda ta fahimta burinta kawae ta isa gida ,yauma su Aunty zulfa basa da lecture ga mmkinta Maman su taga taxo daukarta tana cikin uniform dinta na aikin Asibiti ...</p><p><br /></p><p>Nan tayiwa friends nata sallama. Bayan sun gaisa da Maman su inda take fadin Rahama baxata shigo su sauketa a gida ba tunda unguwa daya suke ,kutafi kurum mama driver baxai ji ddiba .idan yaxo ya tarar da bana nan...</p><p><br /></p><p>"A hanya Dr.hadiza ke kallon ya'rtata wadda taga ta Dan fada batace komae ba Dan tasan fitinar Asma'u kurum nasa ta rame hka wandda ta rasa mai ya sauya tunanin ya'rtata a wannan lokacin..</p><p><br /></p><p>" gyaran murya tayi bakida lpia ne? Mama kaina keyimin ciwo idan mun isa gida sae kici Abinci kisha mgani sae ki kwanta anyya mama barcin nan xai yuyu kuwa?"</p><p><br /></p><p>Ina son naje islamiyya yau da kam yafi mki Dan duk ranar da daddy yasan kina shan ruwan tsuntsaye islamiyya baza kuyi haduwa mai kyau ba."</p><p><br /></p><p> "Yayan Ku ma ya dawo zuwa anjima sae kuje Ku gaishesa keda su Zulfa'u shaye da toka na kalli mama ,yaushe yah Anas din ya dawo??"</p><p><br /></p><p> Dazun nan munyi wya dashi lokacin ma suna hanya dganan taja bakinta tayi shuru da hka suka karasa a gida......</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Next page xuwa anjima insha Allahu."..</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>23</p><p> "Tana cikin uniform dinta na islamiyya ta nufi dakin Maman su anan ta tarar dasu Aunty shema da kuma Aunty zulfa dae-dae lokacin Mama ta fito daga toilet.</p><p><br /></p><p>" mama xan wuce islamiyya plzzz kidan bani Dari biyu nasa kati bana da canji Asma'u ki tambayi yayunki gasu nan maybe baxa'a rasa ba Aunty shema Dan Allah xan Dan samu Dari biyu?"</p><p>Dan Allah ta Dan marairaice cike da ladabi take mgana bana da nima ya'n 1k ne kurum aunty zulfa.?"</p><p><br /></p><p>Zulfa ta Dan harareta plzzz mana Auntyna Dan Allah ta fada a shagwabance ,Aunty zulfa ta jawo handbag "nata anan ta fitar da Dari biyr Dari biyu din da kk ce ita xaki dauka ki dawomin da canji na nasan halinki da rike canji mutum.</p><p><br /></p><p>" nagode Aunty zulfa na!</p><p>Anan tayi masu sallama fitowar takenan daga gidan su kai tsaye gidan su Rahama ta nufa.</p><p><br /></p><p>Momin su tasamu A falo anan ta gaisheta tana tambayar ta Rahama fah??"</p><p><br /></p><p>Tana ciki barci ma takeyi na Nada mata duka a baya a fiegice ta tashi xaune Tana raba ido ganina yasa ta dauki pillow ta jefe ni dashi bakida kirki Asmy ganinta da uniform yasa ,Rahama ta saki baki Tana kallonta ina xuwa hka??"</p><p><br /></p><p>Islamiyya mana amma a xahirin gaskiyya ba acan na nufa ba ynxu ina.son na hadu da Em.ne gama jakana ki tafi daita xanje na fara ganin Em.tukuna xan biyo bayan ki."</p><p><br /></p><p>"Asma'u kiyi ma kanki fada ban yarda da wannan Emran din nan ba ke kawae ke haukan son sa nidae banga wani so da yake yimaki ba."</p><p><br /></p><p>Naji mallamr kinga tafiata baxamu shirya ba muddin Rahama baxaki daena kushemin Em dina ba."</p><p><br /></p><p>Anan tafita tana yiwa Rahama mita gamida yima momi sallama "</p><p><br /></p><p>"Shagon Yusuf ta nufa Dan ta sae kati dae dae kuma lokacin AJ. Ya fito daga gidan su nura hangota yyi tana tahowa wya rike a hnnunta baki wangalu ya saki yana kallonta uniform din bakaramin karbarta sukayi ba tayi kyau sosae wani irin murmushi ya saki wandda shi kansa baima San yanayi ba nura ne ya kula dashi ,ganin inda yake kallo yasa ya zuba ma wurin ido saurin dauke kansa yyi...</p><p><br /></p><p>Har ta shige shagon Yusuf AJ.baidaina kallonta ba.</p><p><br /></p><p>Kallonsa ya maida kan nura dama tana xuwa islamiyya??" Tambayar da yyiwa abokin nasa kenan gaya a zahiri kana gani gaskiyya ina farin ciki da wannan rana kasan ina son macce wadda tasan addinin Islam sosae tabe baki nura yyi Mln mukara sa naga akwae hadari a garin...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana fitowa daga Shagon dae-dae lokacin da suka shige motar ga mmkin nura sae yaga ta nufi bayan layin su ,tsaki Nura yyi Ina maccen arziki anan waya sani ko yawon iskanci xataje aka fake da xuwa islamiyya."</p><p><br /></p><p>A zahirin gaskiyya AJ. Baiji dadin furucin da Nura yyiwa drama queen dinsa ba sae dae baice komai ba ya tada motar ,nura ganin yyi yabi ta bayan layi mekuma ya kaimu anan ga hanyr da Yakama ta mubi.</p><p><br /></p><p>Dae -dae kuma lokacin kuma Suka ga Asma'u ta shige cikin Wata mota kirar Siena wani irin burki AJ. Ya taka haka yaji ransa ya baci nura ya kallesa mai kuma ya tsayar dakai??"</p><p><br /></p><p>Nan take nura yaga yanayin sa ya canja daurewa yyi ya karasa gabda motar ,samun kansa yyi da fitowa daga motar ya karasa wajen motar Em.Tana xaune gaban mota da mmki take kallonsa tana son ta tuna fuskar."</p><p><br /></p><p>Mln lpia??"</p><p>Ta fada fuska bbu walwala."</p><p><br /></p><p>Lpiar kenan yabata amsa shima fuska bbu walwala ,xuwa islamiyar kenan??"</p><p><br /></p><p>Mmki tsoro suka bayyana akan fuskarta haka taga Emran ya zuba mata ido cike da tuhuma ,a zuciya ta fito daga motar Anan ta hango Mln nura ya harde hannayensa yana jikin mota yana kallon drama dinsu."</p><p><br /></p><p>"Wa'azi AJ. Ya fara yimata wani mugun kallo ta dinga aika masa dashi ,hka tayi saurin katse sa Sannu (MUMIN))"....</p><p><br /></p><p>Haka yaji sunan har aransa sae ka rike wa'azin naka bana bukata taja wani tsaki ta shige motar haka Emran ya tada motar ya badesa da kuraaa...</p><p><br /></p><p>" rike dariyar cikinsa nura yyi Yana mmkin abokin nasa da shiga rayuwar wannan yarinyar marar tarbiya ...</p><p><br /></p><p>Yana kula da nura bai kula saba yaxo ya shige motar ,nura baima idar da rufe kofa ba yaja motar a xuciya......</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>#######</p><p>Shi kuma wannan fah?"</p><p>Emran ya fada cikin fushi abunda Asmy ta tsana kenan ya daga mata murya waya sani na sansa ne A unguwar nan yake abokin yah hameed ne ,tafada ne Dan bata tari jin rigimar Emran ba ynxu.</p><p><br /></p><p>Yaushe xaka dawo ?"ina jin sae nayi sati daya shaye da toka take kallonsa ,gaskiyya yyi yawa daddy ne ya tsara hka bani ba." Ke kanki kin sani bana iya jure rashin ki yana mganar yana murxa hnnunta haka ta dinga jin sonsa hade fuskarsa yyi datata ,haka yaga ta lumshe idonta yana hango sonsa tattare daita ."</p><p> Bakinsa taji anata anan ya shige yimata wani irin romantic kisses ,hnnunsa daya cikin rigarta yana Shafa breast dinta ."</p><p><br /></p><p>Sae nishi suke fitarwa a hnkali sun dauki kusan minti goma a hka." Da kyar ya saita kansa ya gyara mata hijab dinta sa'annan ya manna mata kiss a gefen cheek nata tareda furta "I love yhu."</p><p><br /></p><p>"Anan ya fitar da 20k ya damka mata kiyi manage da wannan nasan baki da kudi xuwa anjima xan turo .maki kati nesa da islamiyya ya sauketa ,dakyar tabarsa ya tafi Dan yaga tana shirin yimasa kuka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Rahama tana ganin yanayinta ta zuba mata ido tamkar wacce aka aikoma sakon mutuwa" har aka tashi jikinta sanyaye yake."</p><p><br /></p><p>**************</p><p>BAUCHI..</p><p><br /></p><p>"Look belly baxaki gane bane amma idan nace maki banyi missing din Abdul jabbar ba nayi maki karya."..</p><p><br /></p><p>Ina son Abdul jabbar ya kara dawowa a cikin rayuwata a karo na biyu ,ban San ynxu wace irin rayuwa yakeyi ba a inda yake ba." Bansan mata nawa ke harinsa ba billy??"</p><p><br /></p><p>"Burina ya cika na zama hamshakiyar mai kudi wandda xan iya shiga cikin kowace irin hamshakiyar mai kudi " Amma wlhi billy jikina kawae ne anan ,zuciyata tana tareda AJ. Bansan wace irin rayuwa yakeyi a inda yake ba."</p><p><br /></p><p>Baisa ba da wahala ba a tsayin rayuwarsa ."</p><p><br /></p><p>Billy na fara damar abunda na aikatawa Abdul dina ,tafada kwallah ta taru a idonta."</p><p><br /></p><p>Hkuri xakiyi Aliya kici gaba da hkuri tun kafin aje koina kin fara karaya??"</p><p><br /></p><p>Yanxu fa iyaka 2 month kibari sae kin dawo Dubai sae ki tunkari mamin ki da xancen nasan xata saurare ki ,ynxu ki tashi mu fita wurin shaqatawa hka xai debe maki damuwar da kk ciki....murmushi Aliya tayi gamida rungume billy Dan haka nake sonki Kawasaki Allah yabar minke....[@t 6:26pm.by Asmy b Aliyu]...</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>24</p><p><br /></p><p>Bayan magrib tana xaune a main falo tana juya cornflakes dake xube a cikin bowl juyasa take da spoon "A hnkali ta kasa sha hka tayi nisa sosae cikin duniar tunani.</p><p><br /></p><p>"Aunty shema ta Dade sosae akanta tana kallo ikon Allah to ita wannan meye damuwar ta."</p><p><br /></p><p>Xaunawa tayi gabda ita gamida Dan dafa kafadan ta a Dan tsorace Asmy ta jiyo tana kallon yayar tata ajiyar zuciya ta sauqe kai aunty shema har kin bani tsoro wlhi ...hararar ta tayi ke meye damuwar ki ??"</p><p><br /></p><p>Bbu komae bbu komae ki xauna ki hau tunani murmushi yake tayi na fada maki bbu komae aunty shema ,Ina yah Faisal din har ya tafi ne??"</p><p><br /></p><p>Ya wuce yana ta Neman ki kuyi sallama."</p><p><br /></p><p>Jibi ma xasu kawo lefe washe da baki nake kallon aunty shema yehhhh kice muna da biki tashi tsaye tayi ta aje bowl din hnnunta ." ta shiga taka rawa ina hango ranar bikin ki keda Aunty zulfa ranar akwae bidiri uwa uba na yayana Abokina yah hameed."</p><p><br /></p><p>Shigowar Aunty zulfa ta katseta ke lpian ki kuwa?" Ta fada gamida bin Asma'u da kallo wadda take cikin shigar farin wandon 3\4 da kuma bakar shirt ."mai guntun hnnu sae manya -manyan kalaban dake reto a tsakiyar bayan ta."</p><p><br /></p><p>Aunty shema ta kwabe baki wae daga na fada mata Ya'n gidan su Faisal xasu kawo lefe jibi shine take wannan murna.".</p><p><br /></p><p>Gaskiyya Aunty zulfa kema ya kamata kexo ki tsaida gwanin ki ta fada shaye da toka hka tana turo bakinta gamida cinnosa."</p><p><br /></p><p>Harara tabita dashi gamida Jan dogon (Mtswww)".kanki akeji gulmamma "ni Dan Allah bani canji na xan aika a siyomin creadet ."</p><p><br /></p><p>Nan kuma Asmy ta marairace fuska Dan Allah aunty zulfa kiyi...cikin sauri zulfa ta katseta karki gayamin mganar banxa Asma'u karki kuskura ki bani hkuri ya mukayi dake??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wlhi Aunty zulfa na Dari biyu baya isata ,kuma dama data na siya cike da takaici zulfa Kebin kanwarta ta da kallo kwafa tayi tabar falon gwalo tayi mata caraf aunty shema ta kamata "rankwashi ta kai mata wayyo mama!</p><p><br /></p><p>Da gudu tafita daga falon xuwa dakin Maman su ,tun kafin ta xauna sai ga sageer ya shigo dakin mama." Da sallama.</p><p><br /></p><p>"Aunty Asma'u wae daddy yace kizo. Kwalalo ido waje tayi gamida dafe kirjinta hka ta Dora hnnunta akae wayyo na shiga ukku !🙆 mekuma ya hadani da daddy?"mama ta harareta waya sani wannan tsakanin ku kije kiji maana rashin jin mganar ki shike jamaki Ae.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" da sallama na shiga falon daddy Yana xaune dai daga cikin kujorun dake zagaye a falon yana kallon Aljazira Aunty zulfa na gefen sa.</p><p><br /></p><p>"Ido hudu mukayi dashi Naxo na xauna nima gefensa sannu da xuwa ,daddy yawwa sannun ki husna ya gida??"</p><p><br /></p><p>Lpia qlau ."</p><p>Sunan da yake yawan kiranta dashi kenan a yawancin lokuta ."</p><p>Ganin yarda yaga tanayi yasan bata da gaskiyya ko kadan."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Gyaran murya yyi meya hadaki da aunty ki kuma yau??"..</p><p><br /></p><p>Kame-kame ta shigayi sannan ta bude baki da kyar ta fara mgana Dan Allah daddy kayi hkuri ni kikayiwa laipi da xaki bani hkuri ,nan ta fada masa abunda ya faru ke kuwa Ma'u ana hakanan daga taimako ??"..</p><p><br /></p><p>Iyaka waya'ndda kika nema ta baki meye kuma na dauka gaba daya ki kashe ,daddy ganin nayi baxasu isa ba kuma ni bawae na dauka duka bane gobe idan aka bani na xuwa skull xan maida mata abunta Dari biyr din ma duka ." ta karasa xancen cikin fushi tana zabgawa Aunty zulfa harara .daddy kagan ta ko ?"</p><p><br /></p><p>"Tana hararata Dan tana marar kunya."</p><p><br /></p><p>Kyaleni daita zulfa auhh bakyason kudin kenan duka xaki maida mata da kayanta Ehhh ta fada tana turo baki gamida cinnosa."</p><p><br /></p><p>"Murmushi daddy yyi husna kenan ya'r rigimar daddy kenan kinyi fushi??"</p><p><br /></p><p>Ni bansan ina kika koyo wannan halin ba na fitina yayata Sam bata da fada hakama hadiza balanta nani..."</p><p><br /></p><p>"Ynxu dae ko a gaba karki sake yin haka iya waya'ndda kika tambaya su yakamata kiyi amfani dasu ,daddy dama haka take lashe moneyn canji ce aunty zulfa ta fada gamida yimata gwalo ,murmushi daddy yyi A'ah Zulfa'u karki wuce iyakar ki Auntyna ba lashi money canji bace ,ko ba haka ba Ma'u na daddy ya fada murmushi kwance a fuskarsa A shagwabe ta gyada kai oya jeki A bedroom dina ki daukomin 20k. Da murna ta nupi saman daddy bata jima ba sae gata ta fito da 20k ya'n Dari biyu-biyu bandir daya."</p><p><br /></p><p>Anan ya yaba kowace 5k yace asa credit hka yabawa Zulfa'u yace takaiwa shema'u nan ko Asma'u ta kalli mahaifinta shaye da toka Gaskiyya daddy karka bata ta girma pah?"</p><p><br /></p><p>Bata na da yaya faisal ba kasan iya kudin da ma yake bata muda bama da saurayi mu yakamata ka baiwaaa...ta karasa mganar cike da rigimaa".</p><p><br /></p><p>"Tsaki Aunty zulfa tayi tace daddy mungode Allah ya qara bude Lokaci dya Tabi zulfa da harara falon ya rage daga ita sae ,daddy Meyasa kikema ya'n uwanki haka husna??"</p><p><br /></p><p>Shuru tayi bata ba Daddy amsa ba ,haka yasa ya Mike tsaye nixan tafi masallaci tunda bakida Amsar tambayana kayi hkuri daddy idan ka dawo muyi mgana Allah ya kaika lpia ya dawo dakai lpia Amin amin husna tare suka fito daga falon nasu ,shi ya nupi masallaci itakuma ta karasa side din Maman su."</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>25</p><p>########</p><p>The following day." </p><p><br /></p><p>"Yau garin na kano antashi da ni,imar gaske haka garin yyi luf tamkar xa'a sauke da ruwan sama hadari ne sosae a garin yyinda hadarin ya saki tsananin sanyi misalin karfe 7:30@m.</p><p><br /></p><p>Na safe fitowa ta kenan daga wnka na nufi gaban mirror dressing ina goge jikina da da karamin towel din dake hnnuna."</p><p><br /></p><p>"Wyar Emran ce ta shigo dama kuma wyar na ajiye akan mirror dressing ,daga wyar nayi na kara a kunne na .</p><p><br /></p><p>Daga bangaren sa " yace .</p><p>Yah dae??"</p><p>Dae-dae yah kk qlau ynxu fa xamu kama hanya ,auh dama bata jirgi xakubi ba ?"</p><p><br /></p><p>"Nop !</p><p>Tafian mota ce amma da driver ko A'ah ni xanja daddy ohkey tom .Allah ya tsare hanya nima gani nan ina shirin xuwa skull ,xuwa 8:00@m. Muna da text Allah ya taimaka Ameen.</p><p><br /></p><p>Sae munyi wya ."</p><p>Ohkey tom.</p><p>Bye....</p><p>Bye-bye dire wyar tayi ta cigaba da shirinta a gurguje ....</p><p><br /></p><p>Gaban wadrop dinta ta tsaya ta tarasa wane kalan kaayaa xata sa Dan tsaki tayi(mtsww..) Tunda em dinta baya nan zaben kayan meye doguwar rigar abaya ta fitar da mahadinta ,anan ta shiga shirya kanta ."</p><p><br /></p><p>Tayi kyau sosae a cikin kayan duk da kasancewar ta bakar fata bbu kwaliyyar komae akan fuskarta turarene Jere akan mirror dressing dinta ,Wanda yafi kala goma" kusan kala biyr ta feshe ma jikinta ,Jakarta ta laptop ta dauka dan yau xasuyi using da ita a skull ."fitowar ta kenan kusan cin karo sukayi da Aunty zulfa Dan Allah mallama kiyi sauri karkisa na makara na murguda mata baki amma dae kinsan sae nayi break fast ko ??"</p><p><br /></p><p>Taf dijam!</p><p>Nice xan tsaya kiyi break fast ,wlhi kuwa sae dae yaje ya kaini ya dawo kinga tafiata tare muka nufi dinning area Anan na tarar da ya'n gidan suna break fast wandda suke xuwa skull Afra da sageer sae kuma aunty amarya da mama suma dama suna xuwa aiki ,nasan daddy kuma sae 10:00@m." Yake fita kasuwa.</p><p><br /></p><p>"Yah Anas na hango a tsakiyar su shima break fast din yakeyi nayi mmkin wannan sammako hka ,sae kace bayada iyali?" Kuma naji mama na fadin tare suka tafo dga Abuja yah Haidar kuma yana Lego's. "</p><p><br /></p><p>Anan na gaida mama da aunty Amarya na juya kan ya anas ,ina masa ina kwana ya harareni da ban kwana ba da xaki ganni ne?"..</p><p><br /></p><p>Baxan amsa ba kowa jia yaje yyi min ya hanya banda ke !!</p><p><br /></p><p>Na Dan turo baki naje islamiyya ne shiyasa tabe baki yyi tom ya karatun inace ana maida hnkali??"</p><p><br /></p><p>"Araina nace Dan kininbibi A fili kuma nayi murmushi nace Alhmdullh nan naja kujera na xauna Aunty zulfa da masifa ta kalleni ke bafa xan tsaya jiranki ba ,yah Anas kayi mata mgana " tun yaushe na tsaya ina jiranta ta tsaya kwaliyya da bata Lokaci. </p><p><br /></p><p>Kinyi break fast naki ni kuma ki hanani nayi nikam bbu mai hanani break fast ,baxan hana kiba amma ki dibesa ga cooler "sae kije can kici...</p><p><br /></p><p>Hba sae kace Wata baby gal."</p><p><br /></p><p>Hka ta shiga serving din kanta bata kara bi takan Aunty zulfa ba ,Muje zulfa na saukeki barni da marar kunya."ya Anas ya harareni na kauda kaina gefe suna fita na juyo kan Aunty Amarya.</p><p><br /></p><p>Waeni kam Aunty meya kawo Dan naki ne tunda safe gidan mu??"</p><p><br /></p><p>Wannan irin sammako hka tun kafin ,masu gida suyi break fast yaxo yawani cinye muna abinci meye amfanin Auren Aunty Amarya tayi murmushi Asma'u kenan meya hana ki tambayesa ,mama ta karbe xancen da fadin Atooh...</p><p><br /></p><p>"Dan Allah mama kina saukeni A skull kafin ki wuce hospital ,ban maki alkawariba ina drivern ku??"</p><p><br /></p><p>Dan Allah mana mama ke karki rokeni fah hka ta juyo gurin Aunty Amarya ta waeni shagwabe fuska aunty xaki saukeni Dan Allah ??"</p><p><br /></p><p>Ina nima sauri nake kae idan dae baka da moto a gidan nan kaji haushi ni yah hameed dina yaxo ya dawo ,na huta da shan wulakanci dama kuma hameed A Zaria yake aiki A babbar Asibitin ((SHIKA ))" dake Zaria.</p><p><br /></p><p>Ko ynxu sae ki kirasa kice ya dawo mama tayi mganar gamida mikewa tsaye tabar dinning area din."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A mota sae famar kiran Rahama nake ina tambayar ta malamin da xai yimana test ya shigo ta fada min bai shigoba amma tace nayi sauri."</p><p><br /></p><p>Wani ikon Allah har na isa skull na shiga lecture hall" baixoba sae kusan 8:30@m. Sae gashi Anan ya bamu test.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Misalin karfe biyu na rana muna capteria ,Na dukufa ga wayata ina chat a group din (Asmy b Aliyu novel's))"..</p><p><br /></p><p>Kamar ance na pita na kira Em a waya ina kiransa na farko bae dagaba."</p><p><br /></p><p>Nayi sa'a na biyu ya shiga maimakon naji muryarsa sae naji sabanin hka macce ce ta dauki wyar gabana naji ya fadi ,saurin kashe wyar nayi jin wani Abu ya tokaremin kirji meya hada Wyr Em. Da macce kuma??"</p><p><br /></p><p>Raina ne naji ya baci kusan minti talatin da faruwar haka sae ga kiransa ya shigo a wyana." Wani haushi ya kamani sae na dauka batare da nayi mgana ba."</p><p><br /></p><p>"My habibaty !!</p><p>Shuru na masa sae da ya kara kiran sunan sannan na amsa a dakile ,Cikin tashin hnkali yake tambaya ta meya faru??"..</p><p><br /></p><p>Em meya hada wyarka da macce??..</p><p><br /></p><p>" macce kuma? Look Em.karka raina min hnkali nakira ka macce ta daga wyar.</p><p><br /></p><p>Ajiar heart ya sauke wandda ta jiyo hkan "Am sowiee na manta munje gidan Abokin daddy na barwa zee zee wyar ne ,wacece kuma zee zee??"</p><p><br /></p><p>Ta fada rae A bace ya'r Abokin daddy ne."</p><p><br /></p><p>Badan ta yarda ba .yyi saurin kauda xance ,gamida dauko wta hirar ya test din ?"</p><p><br /></p><p>Hop tayi miki ddi?"</p><p>Tayi man ina saleema bata da kirki ko kirana batayi ba har ynxu gata nan xaune tana jinka."</p><p><br /></p><p>Hira kadan muka taba sa'annan mukayi sallama akan xuwa anjima xae kirani idan muka koma gida.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>★★★★</p><p>"Karfe Tara da rabi na dare ina kwance a dakina Kayan barci ne ajikina Riga da wando pink colour ,na shiga Instagram" naga Em na posting wasu pics shida wata na birthday ,da alamr birthday tayi tana da kyau dae dae da irin nata itama din black beauty ce sae dae yanayin pics dinta na fahimci guntuwa ce sosae ,kusan duka pics din tareda Em sukayi sa wani ajikinsa wani ta saka masa cake shima" yabata haka na dinga ganin pics kala-kala."</p><p><br /></p><p>Wani irin kishi naji ya rufeni hka naji raina yyi balai,n baci badae Emran yaudarata yakeyi ba??"</p><p><br /></p><p>"Na daga wya na kirasa kusan 5 miss calls bae daga ba."</p><p><br /></p><p>Haka na daure na kira sally kira daya ta daga bbu abunda ta fara fadi sae ..</p><p>Asmy dear yne??"</p><p><br /></p><p>Dae-dae sally ya mommy qlau take meya faru naji muryarki wani iri??"</p><p>Sally pics din waye naga Em na posting dinsu A Instagram?? "..</p><p>Tambayar sally taji wani iri sae da tayi Jim sa'annan tace zee-zee ce ya'r abokin daddy ne Friend dinsa ce ohkey sae da safe bata jira amsar sally ba ta datse kiran.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Friend dinsa ce!</p><p>Hka tata maimaita Kalmar a ranta." Taya akayi bata taba sanint ba ??"</p><p><br /></p><p>Wta zuciyr take fada mata sabida kishin ki baya so ki sani ,Whatssapp ta hau anan ta tarar da kan dp dinsa pics dinta ne.</p><p><br /></p><p>Haka yyi mata status Wanda ta ma kasa fahimtar kalmomin soyayya ne ko na minene ,Wanda tayi imani da Allah ba only friendship kurum suka tsaya ba ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hawaye masu xafi taji suna xuba akan fuskarta ,me Emran ke nufi badae yaudarar ta yake shirin yiba??"</p><p><br /></p><p>Sae da yasan xuciyar ta ta Riga tayi ammana dashi ,xae yaudareta a hka ta kwana tana kuka Mae tsanani Mae makon taji haushinsa sae ma kara jin sabon sonsa takeyi ,har xuwa wayewar gari bata kunna wyarta ba..</p><p><br /></p><p>*MA"U*😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>26</p><p> Washe gari....</p><p><br /></p><p>Da zazzabi ta tashi Wanda da kyar tasamu ta sallaci sallar Asuba yau bata samu wani dogon azkar ba ,haka kuma week end ne bbu skull ta koma ta dunkule kanta cikin blanket. "</p><p><br /></p><p>Har kusan karfe goma sha daya mama bataji motsin Asma'u ba suna ta cikiniyar tarbar bakin da xasu kawo lefen shema amma bbu ta ba alamrta."</p><p><br /></p><p>Mama aunty Amarya Aunty shema,da kuma Aunty zulfa duka suna a kiching suna ta aiki mama ta kalli Aunty zulfa yau meya hana Asma'u saukowa a kasa ??"</p><p><br /></p><p>Inajin ko break fast batayi ba cewar Aunty shema .</p><p><br /></p><p>Aunty zulfa ta karbe xancen da fadin kema mama kinsan halin ya'rtaki da barci da kuma son jiki maybe barci takeyi ."</p><p><br /></p><p>Amma Bara naje na dubata dae-dae nan kuma suka yi kicibis da Rahama ta shigo da sallama Anan ta gaishesu ,cike da girmamawa."</p><p><br /></p><p>Sa'annan ta kalli aunty zulfa ...aunty zulfa Asmy pah??"</p><p><br /></p><p>Nima ynxu xan nupi dakin nata tun safe bata lekomu ba tare suka nufi dakinta sunyi sa'a a bude yake hangota sukayi dunkule cikin blanket "..</p><p><br /></p><p>Rahama ta karasa gareta gamida sa hnnu ta yaye blanket din." Haka ta taba jikinta taji zau ,da A xamar ta tayi saurin janye hnnunta ."</p><p><br /></p><p>Ta juya kan Aunty zulfa wadda ta xuba mata ido "Aunty zulfa bata da lpia ne??..</p><p><br /></p><p>Cewar Rahama ina xan sani Rahama anan suka shiga tashinta can ta shiga bude idonta a hnkali hka sukayi biyu da kawar tata da kuma Aunty zulfa."</p><p><br /></p><p>"Bakida lpia shine kika ki sanar da kowa??"..</p><p><br /></p><p>Aunty zulfa tayi mganar ." cike da tausayin kanwar tata zazzabi ne kurum ki samu kiyi wanka ki fito mama ta dubaki ta baki mgani ko ayi maki Allura tana fadin hka tabar dakin gamida Ja masu kofa."</p><p><br /></p><p>Kallon Rahama tayi cikin murya mara sa lpia take fadin yaushe kk shigo??"</p><p><br /></p><p>"Yanxu nan kuma naxo na tarar da bakya jin ddi dama kuma xuwa nayi na fada maki Yah al'ameen ya dawo duk da nasan bakya rasa sani tunda kedin ya'r hnnun damar sace."</p><p><br /></p><p>Ya fada min tun jia yake Neman layin ki a kashe shiyasa ma na biyo sahunki."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da kyar ta yunkura ta mike tsaye Bara na shiga wnka Rahama jirani anan akwae mganar da nakeso mu tattauna akae ta fada cikin rawar murya."</p><p><br /></p><p>Rahama binta da ido kurum tayi anan ta gano akwae abunda ke damun kawar tata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mintuna kalilan kuma sae gaya ta fito daure da karamin towel wandda santala -santalan cinyoyinta duka a waje."</p><p><br /></p><p>"Komae bata Shafa ba sae body sprayn dinda kurum ta feshe jikinta dashi."</p><p><br /></p><p>English west ta Ciro Riga da skirt dark purple masu Rastin baki ajikin su ,Rahama itadae binta kurum take da kallo ."</p><p><br /></p><p>Mun sauka kasa mama ta dubaki Asma'u gaya bbu komae acikin ki cewar Rahama ,karki damu Rahama nasan matsalar ciwo na !! Em yana gabda haifar man da ciwon zuciya!!.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Subhanalliahi!</p><p>Meya kawo wannan mganar kuma Ma'u?? Rahama bana son zargina ya tabbata akan Emran ina tsoron rasa sa a rayuwata kinfi kowa sanin irin kaunar da nake masa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Rahama bansan Mae ke shirin faruwa dani ba ina yima sa wani irin sone wandda Allah kadae yasan yawan sa Anan ta shiga labartawa kawarta ta mai ya faru ,haka Rahama ta dinga hango tashin hankali acikin idanunta."</p><p><br /></p><p>Batayi Aune ba hawaye suka ziraro akan kuncinta haka taji xuciyar ta ma wani irin kuna hnnunta ta hade gamida xubewa agaban Rahama hawayenta kuma tamkar ruwan fanfo."</p><p><br /></p><p>Plzzz 🙏Rahama ki tayani shawo kan Em.tun jia nake Neman wyarsa yaki ya daga ki kiramin shi a wyarki ki tambayesa laipin me nayi masa??" Idan ya fada maki nayi alkawari xan basa hkuri plzzzz Rahama ki taimakeni ,baki wangalu Rahama ta saki tana kallon kawarta ta hka taji ranta yyi balain baci wannan wane irin balai ne wani irin sone take ma Emran din nan da take Neman xaucewa akansa."..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Shaye da toka Rahama ta kalli kawarta ta Dama kin daina rokona kin San bana son wannan Emran din tun farko baiyimin ba ." Asma'u idan mafarki kikeyi ya kamata ki farka.</p><p><br /></p><p>Emran ba son tsakani da Allah yake maki ba." Cikin daga murya da xafin rai Asmy ta katse kawar tata idan baxaki yimin wannan Alfarmar ba ki kyaleni da surutunki Mae haifar min da ciwon kai plzzz ...na Rokeki zanje na samu yah Al'ameen xan fada masa damuwa ta nasan xai fuskance ni hawayen idonta tayi saurin gogewa gamida daukar hijab dinta tayi hnyar fita dga dakin."</p><p><br /></p><p>Cike da tashin hnkali Rahama tasha gaban kawar tata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tabbas da tasan irin yarda yah Al'ameen ke sonta da baxata tunkaresa da xancen Nan ba."</p><p><br /></p><p>"Am sorry dawo kiji xan kira mki shi Anan ta daga wya tana Neman layin Emran " Ta fiso ta kirasa A wyarta da dae ta Fama ma yayan nata ciwon dake addabarsa shekara da shekaru."..</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>27</p><p><br /></p><p>Zubama kawarta ta ido tayi wadda ke famar Neman layin Em. Kusan kira biyu bae daga ba.Rahama ta kalleta "A sanyayye kinga bae daga ba wata kila baya kusa ne!!.</p><p><br /></p><p> " Ta fada tana kallonta Asmy bata ce komae ba ta jawo wyarta ta kunna ,Anan kuma ta dinga cin karo da test message's din Em.dinta na ban hkuri ne da kuma kalaman soyayya masu sanyaya zuciya."</p><p><br /></p><p>Fara'a sosae ta hauyi washe da baki ta kalli Rahama cikin wani irin farin ciki marar misiltuwa ta mika ma Rahama wyar anan ta shiga ,karanta sakon nasa, Wanda ta basa suna Kalaman yaudara."</p><p><br /></p><p>A zuciya ta mika mata wyar gamida Dan Jan guntun tsuka."</p><p><br /></p><p>"Rahama nayi farin ciki sosae ynxu ma na nemi ciwona na rasa ,muje naga yah Al'ameen Rahama ta tabe baki ynxu kuma mexaki fadama su mama?? kina nufin fada masu zakiyi kin tashi dga ciwon wahalalliyr soyayyar da kike yiwa wannan yaron ko kuwa??"..</p><p><br /></p><p>Wlhil azeem Asma'u watarana kunya kike bani yarda kk haukace akan wannan yaron dama ko kadan ,ba sa'an auren ki bane!!</p><p><br /></p><p>" Yah isheki Rahama!!</p><p>Asmy ta katseta cikin tsawa ke baki isa ki hanani son abunda xuciyata ke soba." Idan baxaki tayani son abunda na keso ba sae kija bakin ki kiyi shuru."</p><p><br /></p><p>"Dan shine kike min tsawa da ihu akae sae kace wata uwata??" Rahama ta fada cike da bacin rae ohkey ! Asmy na daina shiga sabgar ki keda wannan yaron Kekika sani Amma karki manta "A WATA RANA !! Sae kin tuna dani Mae fada maki gaskiya ce a koda yaushe anan tabar mata dakin a zuciya Allah yasa bbu wandda ya ganta da haka ta fice dga gidan rae a bace."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tana sawo kae kofar gidan su taci karo da yayan nata ganinta hka ya daga masa hnkali karasowa gurinta yyi Dan ba karamin ji yakeyi daita ba."..</p><p><br /></p><p>Rahama meya sameki hka??"</p><p><br /></p><p>A sanyayye ta kalli yayan nata tana tausaya masa ,tana tausayawa yanayin da zai shiga muddin yaji Asma'u na soyayya da wani .".</p><p><br /></p><p>Bbu komae yaya ina zuwa haka ??" Ynxu har akwae damuwar da xaki iya boyemin plzzz fada min meye matsalar??"</p><p><br /></p><p>Hnnunsa taja zo muje yah Al'ameen kaji hka tajasa tamkar karamin yaro har xuwa side dinsa ."</p><p><br /></p><p>"A falonsa sukayi masauki zuba masa ido tayi na Dan wani lokaci yah Al'ameen !!</p><p><br /></p><p>'Ta kira sunan sa cikin wata irin murya ."</p><p><br /></p><p>Na'am Rahama!." Ya amsata gamida zuba mata ido."</p><p><br /></p><p>"Mexai hana ka fadawa Asma'u irin dumbin kaunar da kake yimata ??" Ganin nayi boye-boye baya da Amfani ina tsoron karka rasa ta yayah!</p><p><br /></p><p>"Ta fada idonta cike da kwallah.'</p><p><br /></p><p>Meya kawo wannan mganar Rahama?? Ya fada cike da tashin hnkali anan ta labarta masa soyayyar da Asma'u keyi da yayan kawar su ...</p><p><br /></p><p>Nan take ta hango tashin hnkali acikin idanunsa ,sae dae yyi saurin kawar da damuwar sa karki damu Sistr xamuyi mgana daita xuwa anjima."</p><p><br /></p><p>"Da fara'a ta kallesa da gaske kakeyi yah Al'ameen??</p><p><br /></p><p>Daga mata kai yyi alamr Ehhh." Yawwa yayana Allah yabaka sa'a bana son karasa Asma'u baxan ma rasata ba Rahama "yah fada cikin wani irin yanayi .</p><p><br /></p><p>★★★</p><p>" An kawo lefe aunty shema saiti goma sha biyu kaya masha allahu ,sunyi kyau da yake shima Faisal iyayensa suna da kudi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Da karfe shidda na fito daga gidan mu xuwa gidan su Rahama nasan tunda banganta ba tayi fushi ne ."</p><p><br /></p><p>Dae-dae kuma lokacin na hango ya Al'ameen cikin mota da alamr fita xaya yi ,ganina yasa ya fito daga motar cike da farin ciki na karasa garesa da nupi na rungumesa ,Dan na jima ban gansa ba kasancewar bai fiye xuwa ba Dan "A sokoto yake aiki."</p><p><br /></p><p>Sae yyi saurin kaucewa yana daria kae kae my Ma'u ynxu kin girma sunan da yake kirana dashi kenan ."</p><p><br /></p><p>Sae nayi folding din hnnuna akan kirjina na bata rae gamida turo baki cike da shagawaba ,sae yyi daria wadda tasa naga yyimin kyau."</p><p><br /></p><p>"Dan yah Al'ameen karshe ne gurin kyau cikakken bafulatanin Asalin dogone sanbal haka yana da kaurin jiki sae kasumbar da ya Tara baka wuluk wadda takara yimasa kyau."</p><p><br /></p><p>Ko Rahama baxata Nuna ma yah Al'ameen kyau ba."</p><p><br /></p><p>Haba ke kuwa my Fulani gal!!</p><p>In banda ke da abunki wake fushi da babban yayansa ,to bakai bane ka hanani na nuna maka murnar ganinka "kin girma Ma'u na wannan sae su Afra ,yah Al'ameen meye sirrin ne wae??</p><p><br /></p><p>Naga ka aza tumbi gaskiyya yakamata ace xuwa wannan tym." Din kuxo Ku aje iyali kaida yah hameed ,Dan na tabbata bbu maccen da xata kiku...</p><p><br /></p><p>Daria Al'ameen yyi ya langabar da kansa yana kallonta shikam yana son komae nata yana son life style dinta ."baka taba ganinta cikin damuwa ,nikam tuni nayi mata! Amma ban sani ba ko xata soni ina tsoron tunkarar tane.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zaro ido tayi gamida dafe kirji wacece wannan ka fada min ita bata isa taki son yayana ba! Tayi kadan plzz fadamin ita naje na sameta komae take ji dashi dole ta saukesa ta kularmin dakai."</p><p><br /></p><p>"Zuba mata ido yyi ganin yarda take murna a ransa yake fadin kece Asmy amma bansan taya xan fahimtar dake hakan ba."</p><p><br /></p><p>Hy!!</p><p>"Hohoho!!</p><p>Wallahi da alama yah Al'ameen kana tsoron budurwar nan taka , ji yarda ka rude lokaci daya plzzz muko ma cikin gida dole yau sae ka fada min damuwar ka !!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta Amshi car key dinsa " ta shige motar ta gyara masa parking sannan taja hnnunsa suka nupi gidan su.[truncated by WhatsApp "].</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>28</p><p> "A cikin barandar gidan su sukayi masauqi bisa wasu fararen kujorun roba da aka kawata da wurin dama kuma anyi sune Dan zama.</p><p><br /></p><p>Tana xaune kan kujera mai fuskantar sa ta xuba masa ido ta kagu taji wannan wace macce ce Mae sa'a har yah Al'ameen ya kamu da tsananin sonta haka??".. Plzzz yah Al'ameen kayi shuru mana ka fada min ko so kake Abba ya dawo ya gammu anan??"..</p><p><br /></p><p>" Ai nafison ya dawo ya samemu anan nafiso ya ganmu atare dalili kuma na gaji da Jan ran da kike yimin plzzz Asma'u ki tsaida hnkalin ki guri daya." Cikin rashin fahimta take kallon yayan nata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nasan kin gane manufata da kuma dangantakar dake tsakanin mu amma duk sae ki dinga mayar daita wasa ,ynxu lokaci yyi da xaki fuskance ni duk da kinsan da ina sonki kike kauce hkan."</p><p><br /></p><p> "Asma'u ina sonki kibani damar na fadawa su Abba hkan ina son yaje ya nemar min auren ki gurin daddy ,duk da nasan bbu matsala tunda aminan juna ne da gaske nake kena ke son aura kece mafarkina kice ko mae nawa tun kafin kisan kanki nake dakon sonki bana jin xan iya rayuwar aure da wata y'a macce face ke...</p><p><br /></p><p>Asma'u yawan irin son da nake maki ,son da baki baxae iya furtawa ba ko fasaltawa duk yawan irin son nan da nake maki baxan maki dole ba idan bakya sona shi kenan amma ki sani baxan taba daena sonki ba."</p><p><br /></p><p>"Harko xuwa ranar da xan koma ga mahaliccina."</p><p><br /></p><p>"Ya kika gani xaki iya xama dani A matsayin abokin rayuwar ki Ehh ko A'ah? Bana tunanin idan na rasaki xanyi aure."</p><p><br /></p><p>Naji abunda kace amma mganar gaskiyya yah Al'ameen ina mai baka hkuri tuni nayiwa wani alkawarin Aurena!!</p><p><br /></p><p>Kayi hkuri kama cire batun aure a tsakanin mu ,Dan ina maka kallon wanda muka fito aciki daya ne mutsaya matsayin mu na abokai na fito na fada maka gaskiyya ne ,Dan bbu boye-boye a tsakanin mu.da fatan xaka fahimci mgana ta??...</p><p><br /></p><p>Idan kuma mgana ta ta bata maka rae kayi hkuri Dan bana son na bata maka rae. Tana gama fadin haka ta mike tsaye ni xan tafi gida."</p><p><br /></p><p>"Xaki iya tafia yabata amsa kai tsaye kayi hkuri da fatan ban bata maka raiba....waye ya fada maki?" Kan me raina xaibaci akan wadda bata damu da farin ciki na ba? Jin furucin sa tasan cikin fushi yake mganar ficewa tayi abunta amma tabbas bataji ddi ba ."wannan shine karo na farko da suka samu matsala da yah Al'ameen dinta....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>One week latter....</p><p>Bbu wata jituwa a tsakanin su bbu wandda yake Neman wani haka ya dauke kafa daga xuwa gidan su ,sae taje skull yake shigowa ya gaishe da su mama.ya juya abunsa haka Rahama tayi nacin dunia akan ya fada mata ya suka karasa yaki sanar mata karshe ma ya fada mata basuyi mgana ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bbu abunda ya dameta ,tunda ta shirya da Em dinta har ya dawo kuma sun cigaba da soyayyar su. Har ta manta da wani yah Al'ameen..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ranar laraba da yamma tana dakinta yau ake birthday din Em dinta batasan yarda xata fita daga gidan nan ba."</p><p><br /></p><p>Haka ta xauna a daki ta saka wannan ta kwance wanccan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>********</p><p>Sanda ta shigayi tana tafia a hnkali tana duba bayanta dae-dae ta kawo bakin get fita daga cikin gidan .</p><p><br /></p><p>Karaf!</p><p>"Suka ci karo."</p><p><br /></p><p>Da sauri ta ja da baya gamida zaro ido ,wani mugun kallo ya shiga aika mata cike da tsoro tayi jefa da talkamin dake hnnunta ."</p><p><br /></p><p>Gidan ubanwa xakije kuma??"</p><p><br /></p><p>"Cikin ina ina " tafara fadin anan gidan su Rahama xan shiga takara sa xancen cike da tsoron yayan nata ."</p><p><br /></p><p>Saukar mari taji akan cheeks nata wandda ya kusan xautar daita "wani irin ihu tasaka tamkar wadda aka rufe da duka hka ta falfala da gudu cikin gida." A tsakiyar falo ta baje "anan ta shiga ihu ,da gudu mutanen gidan suka fito jin kururuwar ta !!</p><p><br /></p><p>Mama ce ta fara fitowa cike da tsoro Aunty amarya ta biyo bayanta sa'annan su aunty shema dama su Afra na islamiyya ..</p><p><br /></p><p>" Tsaki aunty zulfa tayi "dae-dae lokacin yah Anas ya shigo cikin falon ,ganinsa yasa tayi bayan Aunty da gudu kae Anas lpia??"</p><p><br /></p><p>"Barni da ya'r iskar yarinyar nan Aunty kinsan daddy ya kafa mata dokar fita da yamma kun Masan fitar ta??"</p><p><br /></p><p>"Ya fada yana kallon mama fuska bbu walwala ,cike da tsoro mama ke kallon yah Anas ni yaushe xan San fitar ta gyaran wadrop din su Afra na sakata sabida mai Aikin su tatafi ganin gida." Shine har tasaci hanyar fita."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Lallae Asma'u kinyi nisa sae dae nace Allah ya shiryaki ."</p><p><br /></p><p>"Ae wlhi yah Anas kayi mata shegen duka cewar aunty shema."</p><p><br /></p><p>Cike da tsiwa na murguda mata baki ke kuma ina ruwanki gulmammu kawae bbu abunda suka iya sae gulma." A harxuke suka nufo ni duka yayun nawa ,su ukku yah Anas aunty shema,da kuma aunty zulfa wandda nasan bugun mutuwa xasuyi min na lafe bayan Aunty amarya.</p><p><br /></p><p>Anan tayi saurin dakatar dasu cikin daka masu tsawa.".</p><p><br /></p><p>Kibarni aunty na lallasa wannan marar kunyar cewar yah Anas cikin fushi yake mganar ,Anas bacemin daganan cikin bin umurninta yabar falon na bisa da harara caraf!!</p><p><br /></p><p>Suka hada ido da aunty."</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>29</p><p> Nayi saurin dauke idona akan Aunty na wuce dakina hka na xauna a daki har aka kira sallar magrib sae ga kiran Em. Ya shigo cikin rawar jiki na daga wyar ."</p><p><br /></p><p>Har yau baki samu pitowa ba haba Asmy kina Abu tamkar ba ya'r jami'a ba.</p><p><br /></p><p>Hajiar heart ta sauke kayi hkuri Em.kadai San yarda tsaron gidan mu yake ,amma insha allahu ynxu xan fito ina xamu hadu??"</p><p><br /></p><p>Kisa meni a gida mana kin San sae isha,i xa'a fara ohkey tom. Ka saurari xuwa na a ko yaushe ya kashe wyar saman bene ta dinga leken kasa kasancewa gabadae dakunan su suna a sama ita da aunty shema da kuma zulfa natane a tsakiya su mama kuma dama a kasa suke bbu kowa a falon kasa."</p><p><br /></p><p>"Da alamr suna wurin sallah sauri tayi ta koma daki handbag" Mae Dan girma ta samu ta xuba sexy dress nata." Da sauran kayan make up dinta.</p><p><br /></p><p>Dogon hijab ta samu ,ta xumbula har kasa haka ta dinga komae cikin sauri ."ta dauki wyarta da makullin dakinta ta rufe dakin da key."</p><p><br /></p><p>Cikin sauri ta sauko daga down stairs din har tabar falon bata hadu da kowa ,ba mai gadi kuma ya Shiga masallaci .....</p><p><br /></p><p>Sae da tayi nisa ta saki wata ajiyar zuciya a daidaita sahu ta nema sae unguwar su Emran."</p><p><br /></p><p>Ana ajeta ta daga wya ta kirasa ki shigo mana kai tsaye kiyo part dina ,anya Emran baka tunanin wani xai iya ganina ??</p><p><br /></p><p>Kasan fa gidan Ku da yawa oh my Allah !!bbu wandda xai ganki habibaty duhu fane !</p><p><br /></p><p>Ohkey tom."</p><p><br /></p><p>"Anan ma sae da maigadin su ya raina mata hnkali ,nan take ta kira Em ta hada sa dashi cikin gaggawa kuwa ya bude mata kofa gamida binta da kallo a zuciyar sa yake fadin Allah ya kyauta." Ya kuma kara shirya mana xuri'ar mu.</p><p><br /></p><p> "Tana shiga falon nasa aka dauke wutar lantarki dae dae kuma lokacin taji ya rungume ta duk da ta tsorata cikin muryar rada yake fada mata ke matsoraciya nine fah?"</p><p><br /></p><p>Ajiar heart ta sauke cikin shagwaba take fadin ka tsorata nine dae dae kuma lokacin aka tayar masu da generator."</p><p><br /></p><p>Haske ya bayyana daga shi sae farar singlet ce ajikinsa da kuma boxer Wanda ana hango cinyoyinsa Wanda gashi ya kwanta acikin su.</p><p><br /></p><p>Ta Dan ja baya kadan Ta kallesa Em. Ayi partyn nan da wuri kasan halin daddy ynxu ma dakyar na samu na fito ta fada cikin yanayin damuwa."</p><p><br /></p><p>Ynxu xamu tafi ae su T.K. ma suna ta kirana a wya nace tare xamu taho dake xomuje kiji hka yaja hnnunta xuwa bedroom dinsa ta xauna bakin gadonsa to kashirya mana ni xanje na shirya wurin sally."</p><p><br /></p><p>Zauna wa yyi gabda ita ki shiryawarki anan mana haka yyi kokarin cire hijab dinta ya kuma samu nasarar rabata da hijab din."</p><p><br /></p><p>"Dinki doguwar rigar atamfa ce a jikinta pitted gown"..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wadda ta kamata sosae har ana hango albarkatun kirjinta a waje ,aza kansa yyi a kafadar ta nan take taga yanayin sa ya canja kokarin tashi take ya hanata murya kasa-kasa yake fadin ina kuma xaki my habibaty??"</p><p><br /></p><p>"Kinsan fa mun dde bamu haduba tun kafin naje Abuja plzzz my habibaty yau ki daure ki bani kanki koda na rana dayane ,ki bani shi a matsayin birthday gift dina na cika shekara ashirin da shidda a dunia Em ..amma...shitthhhhh yyi saurin Daura yatsan sa akan labbansa hnnu daya yasa ya shiga xuge zip din rigarta tana ji tana gani takasa hanasa rabata da rigar yyi. ."</p><p><br /></p><p>Ya rage daga ita sae pant da brezia."</p><p><br /></p><p>Cikin wani irin salo ya kwantar da ita akan gado anan taga ya koma zindir haihuwar uwarsa ,Saurin kawar da kanta tayi tana ji tana gani ya fara wasa da jikinta haka ya samu ya rabata da breazia dinta Wanda pant din jikinta kawae ya rage bakinsa yakai kan na fulaninta."</p><p><br /></p><p>Ya fara shan su tamkar yasamu alawa lokaci daya Asmy ta firgice ta fara fita hayacinta jinta ta farayi cikin wani bakon yanayi... tabata da Em.yake baeta ba wuce iyakah ba irin haka."</p><p><br /></p><p> "Haka ya dinga Shafa kowace gaba ta jikinta ,gabadan su sun pita hayacinsu kokarin xare pant din jikinta yake wani karfi taji yaxo mata tayi saurin turesa ta rarumi hijab dinta cikin wani irin yanayi yake kallonta ,haka ta hango bacin rae tsantsa acikin idanunsa ,kayanta ta kwasa ta wuce bathroom ta kwashi minti talatin aciki sae gata ta fito cikin wata hadaddiyar Riga ta english west mai santsi dark green ,Wandda take da tsaguwa baya haka ta kamata sosae."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta Daura head baki akae simple make up kurum tayi tayi kyau sosae Amma fa ta hade rae sosae wasu irin uban hills ne akafan ta masu belt ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Shima yana cikin shigar bakaken suite coat yyi kyau" sae xuba kamshi yakeyi ,Rika hnnunta yyi sukayi waje batareda ya yaba da kwaliyyar taba."</p><p><br /></p><p>Suna a mota sae famar kiransa friends dinsa suke ,haka ya sharesu can kiran zee-zee dinsa ya shigo ya dauka murya kasa kasa ya soma mgana ganinan xuwa Zeey Barni kawae ina cikin wani haline."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Basu tsaya koina ba sae "A (RAIHAN HOTEL)).....suna gama parking ya fito daga motar batareda yyi mata mgana ba ,yyi gaba abunsa jikinta qlau yyi sanyi sauri tayi ta cimmasa tamkar wasu taurari haka suka jera suka karasa cikin hall din tamkar wasu taurari isowarsu ya suka anka saki wani slow music."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hango mutane sukayi maza da mata cikin hall din kowa sai sha'anin gabansa yakeyi ,Anan Mc.ya fara yimana kirari Haka su TK.suka karaso wurin mu suka bawa Emran big hug haka nima ya rungumeni tamkar yarda yyi ma Emran amma na lura ko ajikinsa hka naji raina ya baci sae dae nayi kokarin danne bacin raina."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Anan muka shiga gaisawa da mutane dae dae kuma lokacin Wata budurwa ta karaso gaban Emran tayi hugging dinsa tana cikin shiga ta alfarma!!</p><p><br /></p><p>"Tana dago kanta muka hada ido nan take gabana ya fadi. Tabbas itace taga yana posting din pics dinta " A Instagram....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Harara ta zabga min bansan lokacin da na mayar mata da martani ba sally taxo ta jani gefe ,ke ya'mmata kinyi kyau!</p><p><br /></p><p>........yaushe kk karaso tareda Em. Muka taho hankalinta ta maida kan Em Wanda zee zee ke famar yimata shisshigi ,Ranta taji ya kara baci ...</p><p><br /></p><p>Sally ta juyo da ita ke wai mekike kallo murmushi ta Dan kwakwalo bbu komae Anan aka yanka cake "maimakon taga Em ya fara bata sae taga ya bawa zee zee nan wuri ya kaure da ihu haka itama ta basa anan aka yankawa kowa nasa wani irin bakin ciki ya xiyarci xuciyarta me Emran yake nupi??</p><p><br /></p><p>" Dan ya wulakanta ta ya gayyace ta xuwa wannan wurin?"</p><p><br /></p><p>"Anan kowa ya kama gal friend nasa aka shiga tikar rawa itama Sally tuni ta nupi wurin T.K. ganin yarda Em.ke rawa da Zee zee yyi balain bakanta ranta ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nan kuma aka tsaida kida aka shiga ciye -ciye da lashe lashe ."</p><p><br /></p><p>Itadae Asmy Tana gefe tana kallon ikon Allah Karasawa tayi wajen Tk. Tana tambayar sa Emran fah?"</p><p><br /></p><p>Kai tsaye ya mata bayanin dakin da yake kae tsaye ta nupi dakin knocking ka tashi gayi shuru take ji haka taji xuciyarta na wani irin harbawa ."Wanda tarasa dalili ."</p><p><br /></p><p>Wata zuciyar take fada mata ta shiga kowae murda kofar dakin tayi a bude take tasa kai cikin dakin innalillahi wainna ilaihir raji'un abunda take maimaitawa kenan aranta Emran ne shida zee zee haihuwar uwarsa suna aikata masha'a ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wani irin karfi taji ya xomata gamida wata irin xuciya ta finciko zee zee daga kan gado ta sauke mata yatsunta biyar Nan emran ya nemi abunda xai suturce jikinsa dogon wandonsa ya mayar haka Asmy ta finciki hnnun zee zee ta turata waje ta datso kofar wani irin mugun kallo emran ke aika mata dashi ...</p><p><br /></p><p>" A hnkali ya xube jagaf! Akan doguwar coach din dake ,dakin Emran ina son xamuyi mgana !</p><p><br /></p><p>"Plzzz leave me a lone am not in d good moon " dole ka saurareni ynxu Em.!!</p><p><br /></p><p>Ta fada hawayen bakin ciki na xubo mata bai damuba ya kalleta ,I will talk to yhu latter." </p><p><br /></p><p>"Iam really disturb now!!</p><p><br /></p><p>Ynxu nakeso dole ka saurareni Dan wannan shine karo na karshe da xaka kara ganin fuskata a rayuwarka."</p><p><br /></p><p>"Ka shirya aurena yanxu??"...</p><p><br /></p><p>Kina son kiji ehhh tafada a zuciya ohryt !!</p><p><br /></p><p>Baxan aureki ba!! Meyayi saura Wanda ban sani naki ba ,Allah ya sauwake na aureki !</p><p><br /></p><p>" get out of my Room ya mike a xuciya ya finciki hnnunta yyi waje da ita ya turata a xuciya ya bugo kofar Manyyan kawae!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bin kofar tayi da kallo haka hawayen idonta sun kasa tsayawa ,da kyar ta mike tsaye tana jin saitin xuciyar ta yarda yake wani irin tafasa .....</p><p><br /></p><p>"Tafia take bata San inda xata ba haka tayi nisa sosae da hotel din ta duba wyarta taga kusan karfe goma da rabi na dare."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Daga nesa ya hangota tamkar a mafarki da karfi ya furta Drama Queen" saurin taka burki yyi ."</p><p><br /></p><p>Ganin mota ta tsaya gafda ita itama taja ta tsaya ,da Sauri ya fito daga motar Ganin sa cikin rawar murya ta Furta *MUMIN*!!!</p><p><br /></p><p>"Har a ransa yaji sunan xubewa tayi a gabansa tana xubar hawaye."</p><p><br /></p><p>Note!</p><p><br /></p><p>Ina mai Baku hkuri gobe baxan samu damr yin typing ba shiyasa yau nayi 3 pages Dan gobe ina busy.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*TEAM ABDUL-JABBAR MEERA*(( *Mr.AJ*))😘...</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>*"Sakon gaisuwa da fatan alkahiri ga masoyan wannan littafin naga sakunan Ku na gode itama Asmy din tana kaunarku a koda yaushe kamar yarda kuke kaunar ta ,haka kar big fan's dina su manta gobe ne pah Birthday dina haka ina gayyatar ku birthday party na ,da fatan xaku amsa gayyatana?" Bbu damuwa nasan xaku samu hallara idan ma wasun Ku basu samu hallara ba nasan manyyan masoyana xasu xo kamar su Ummy Aysha hajjace party zahra Munay Teema luff Aseey khaleel Autar Hajia Aysha Aliyu Garkuwa ,Ayusher Muha'd Da kuma queen Supy...kai duka masoyana nasan kuna murnar wannan rana ta gobe allah ya kaimu goben*.."😇</p><p><br /></p><p>_"Sakon gaisuwa da fatan Alkhairi ga ya'n group dina "wato Asmy b Aliyu novel's da kuma dandalin Asmy b Aliyu nagode da soyayyar Ku a gareni Allah yabar zumunci_"...</p><p><br /></p><p>30</p><p><br /></p><p>"Lokaci daya AJ. Hnkalinsa yaji ya tashi meya sameta haka? Ina tafito acikin wannan Daren??</p><p><br /></p><p>Bbu Mae Amsa masa tambayoyin sa face ita dake durkushe a gabansa ba, gabansa yaji ya fadi a karo na biyu badae biyar maza takeyi ba??"</p><p><br /></p><p>"Wata xuciyar tayi saurin kwabar sa no Abdul jabbar karka fara kayiwa " Drama queen dinka wannan zargin kasan ba halinka bane nan ,nan take yyi saurin kawar da tunanin aransa hnnu yasa da nufi ya rikota sae yaga tayi saurin ja da baya a tsorace hka lokaci daya ta mike tsaye."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dan allah ka taimakeni ka daukeni a wannan wurin koma ina kakeson kaini na baka dama kai koma kasheni xakayi nafi farin ciki da haka plzzzz " na rokeka ta fada gamida folding din hnnunta haka hawayenta suka kasa tsayawa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nan take yaji ta karya masa da zuciya da tasan yarda kukanta ke ta'basa ba da bata yiba hnnunsa yasa ya bude mata kofar motan bbu musu ta shiga ya rufe sannan ya zagaya ya shiga side din Driver " Mahaifina yyimin komae "A rayuwa tun ina ya'r kankanuwa ta har na kai wannan shekarun yana bani damata.</p><p><br /></p><p>" kana ganin nayiwa mahaifana Adalci a rayuwar su sakamakon jin mganar su da banayi sabida kawae son zuciya na da soyayya yau na tabbata yau so bala,i ne bana tunanin xan kara son wani A rayuwata na tsani maza na tsanesu ta rushe da kuka mai taba xuciya haka ta saka kanta ajikin cinyoyinta yana jinta bai hanata kukan ba."</p><p><br /></p><p>"Amma yarasa fahimtr Mae kalaman ta ke nufi??"</p><p><br /></p><p>Saurin taka burki yyi kiyiwa allah ki daina wannan kukan Na rokeki bakisan yarda kukan ki ke tabamin xuciya ba Ynxu fada min ina kikeson zuwa??</p><p><br /></p><p>"Dago idonta tayi tana kallonsa na ya'n mintuna ganin yarda yake kallonta tayi saurin dauke kanta cikin muryar kuka take fadin bansan mexan fadawa daddy ba da yah Anas ba nasan mumin baxaka cutar dani ba ko gidan ku ne ka kaini xuwa gobe sae na tafi gida ta fada hawaye masu xafi suka gangaro akan kuncinta."</p><p><br /></p><p>Girgixa mata kai yyi alamr ta daina kuka wani irin sonta yakeji xuciya da ruhi ji yake tamkar ya jayota jikinsa ya lallasheta ko xaiji saukin abunda yakeji to "Amma ina bbu halin yin hka.</p><p><br /></p><p>" Jiki sanyayye ya tada motar bata kara kallonsa ba ta dauke kanta gamida xubama titi ido."</p><p><br /></p><p>Nan gidan Auntyna ne komae xakiji na fada mata kawae kiyi shuru kina jina ??"</p><p><br /></p><p>"Daga kanta tayi alamr to..</p><p><br /></p><p>Kusan tare suka fito dga motar ita dai binshi kurum take aranta tana Addu'ar allah yasa ba mugu bane!</p><p><br /></p><p>" Falon yyi tsit sae karar T.V. yana gaba tana binsa a baya dae- dae kuma lokacin Aunty salma ta karaso daga falon ganinsu tare yasa ta tsaya cak !</p><p><br /></p><p>"Tana bin AJ da ido daga ina haka??" Na ta kiran wyarka bata shiga ,murmushi ya kwa'kwalo na Dan fita ne Aunty ga bakuwa nan na kawo xuwa gobe da safe kanwar Abokina ce biki taxo a garin nan kasancewar bata da kowa shiyasa ya kirani ya damka min Amanar ta cike da Fara'a Aunty salma ta mata sannu da xuwa ."</p><p><br /></p><p>Nixan tafi na watsa Ruwa karki damu Asma'u Aunty salma na da kirki kisaki jikinki nan ma gidane washe da baki Aunty ta kalleta kice sunan ya'ta gareki Da kuma sunan hajiar mu ....kauda kai kurum Asmy tayi haka ta kwa'kwalo murmushin dole.</p><p><br /></p><p>"Anan AJ. Yabarsu ya karasa masaukin sa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kusan karfe goma sha daya na dare ya dawo falon cikin farar jallabiya bae tarar da kowa a falon ba wya ya fiddo ya kira Aunty salma yah akayi ne Abdul jabbar??"</p><p><br /></p><p>"Cewar Aunty salma ina dakin Abban su Nana Bakuwar ka kuma tana dakina."</p><p><br /></p><p>Ohkey tom."</p><p>Saurin datse kiran yyi kai tsaye dakin ya nufa murda kofar dakin yyi da sallama hangota yyi kan Sallaya da alamr sallah ta idar Kan bedside drower ya xauna gamida Dan xuba mata ido ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kana son wani Abune??"Ta fada tana kallonsa girgixa kai yyi alamr A'ah kinki cin Abincin da Aunty ta kawo maki ko. Baiyi maki bane??"</p><p><br /></p><p>Ya fada cikin sanyayyar muryarsa bana jin yinwa ne ta basa amsa batareda ta kallesa ba."</p><p><br /></p><p>Baxai yuyuba.!!</p><p>"Tana mmkin karfin halinsa ,murmushi ta danyi kadan mexai hana ya yuyu mumin tunda ni ba y'arka bace da zakayimin dure."</p><p><br /></p><p>"Ta fada gamida dan turo baki girgixa kai yyi gamida sakin guntun murmushi baxata ta bata canjawa ba." Duk da kuwa tana cikin damuwa."</p><p><br /></p><p>"Nifa ki daina cemin *MUMIN*"...</p><p>Ba shine suna na ba koma dae meye sunan naka ni ina ruwana da na sansa kawae dae nasan kana da kirki ba irin Mln Nura muguba !!</p><p><br /></p><p>" Dan haka dole ka karbi sunan ka mumin tom.naji na karba kici abinci plzzz karki xauna da yinwa aciki tayi ma lpiar ki illah..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Karka wahalar da kanka plzzzz idan dae xan samu coffee xan iya sha shi kike son sha ne??"</p><p><br /></p><p>Saurin daga kanta tayi batareda ta kallesa ba "Angama my drama queen!!</p><p><br /></p><p>Ya mike tsaye gamida yin hanyar fita daga dakin " A sanyaye tabisa da kallo ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*TEAM DRAMA QUEEN*..🌹</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>_thank yhu for my beautiful birthday wishes! I fell grateful and Lucky to have so many amazing by my side ,I love yhu so much my biggest fan's bohoot -bahoot shukriyah!!_*One love*#.</p><p><br /></p><p>31</p><p> Hawaye masu xafin gaske suka sauko akan fuskarta tana jin ciwon abunda emran yyi mata har aranta haka tana jin zuciyar ta na yimata wani irin zafi.</p><p><br /></p><p>"Ya dde tsaye akanta wandda yakai minti biyu a kanta bata ma San ya dawo ba."</p><p><br /></p><p> Cup coffee ne rike a hnnunsa samun kansa yyi da durkusawa a gabanta kamshin turaren da taji shiya sa ta dago jajjayen idanunta da sauri sukayi ido hudu dashi,saurin goge idonta tayi tareda dauke kanta ."A kansa Drama Queen!!</p><p><br /></p><p>"Ya kira sunan ta cikin wata rikitacciyar murya bata kallesa ba ." bata kuma amsa masa ba baxaki amsa niba??"</p><p><br /></p><p>"Yah fada A raunane niba drama queen ne sunana ba kanme zan amsa ka??".. Saurin katseta yyi bana bukatar naji sunan ki da mmki take kallonsa yarda ya masa a daxu shine ya mata hakanan."</p><p><br /></p><p>"Am sorry da wannan sunan na sanki tun ranar da na fara Daura idanuna akanki." Ganin zae canja xancen zuwa wata manufa wadda itakuma ko kadan bata son wata alaka Mae karfi ta hadasu shiyasa taja bakinta tayi shuri ta mika masa right nata ,gamida karbar cup din hnnunsa."</p><p><br /></p><p>Godia tamasa batareda ta kallesa ba tsam "ya mike tsaye yyi mata sae da safe Dan yaga da alamr batason mgana."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_washe gari_"..</p><p><br /></p><p>Tafia suke a mota shuru ya ratsa a tsakanin su sae kira'ar Mln shureem dake tashi a motar kowane da tunanin da yake sakawa a ransa.</p><p><br /></p><p>"Gabda shiga layin gidan su tayi saurin tsaeda shi ganin motar yah Aliyu!!</p><p><br /></p><p>Sae da zuciyarta ta kusan tsinkewa hka yasa tayi saurin dakatar da AJ.</p><p><br /></p><p>" Ta kallesa hankalinta a tashe da kyar ta iya fada masa nagode . da haka ta balle marfin motar ta fito sauri sauri gudu -gudu ta tunkari gidan su zuba mata ido yyi yana zaune a mota yana kallon ikon Allah!</p><p><br /></p><p>"Har ta bace daganin sa doguwar ajiar xuciya ya sauke yana ayyanawa a ((WATA RANA !)) Xasu xauna a karkashin innuwa daya a matsayin ma'aurata masu tsananin son junan su."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Samun kansa yyi da Daura kansa akan sitari haka ya tsinci kansa acikin wani irin yanayi da kyar ya saita kansa ya Ciro waya ya dannawa Nura kira ."yana dagawa Tambayar sa ya somayi yana ina??"</p><p><br /></p><p>Jin muryarsa wani iri yasa Nura yace lpian ka kuwa??"..</p><p><br /></p><p>"Da sauqi dae ina gida amma xuwa 11 xan fita office ohkey gani nan karasowa ."</p><p><br /></p><p>Yana aje wyar ya nufi gidan su Nura.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dai dai lokacin da ta karaso kofar gidan su Taga yah Aliyu tsaye shida Yah " Al'amin lokaci daya kuma suka zuba mata ido ganin mugun kallon da yah Aliyu ke jifan ta dashi yasa ta fada cikin gida .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hango motar daddy tayi a parking space's da Alamr bai fita kasuwa ba sallama tayi a babban falo taci sa'a kowa na xaune a falon duka sunyi jugum !!</p><p><br /></p><p>"Ganinta yasa duka suka mike tsaye zubewa nayi a tsakiyar falo haka hawayen idona suka kasa tsayawa ,gabadae kunyar iyayen nawa ta gama lullubeni "...</p><p><br /></p><p>Shaye da toka daddy ya kalleni cikin daka min tsawa daga ina??"</p><p><br /></p><p>Har kingama yawon karuwan cin naki!!</p><p><br /></p><p>"Gabana naji ya fadi na kalli daddy na girgixa kai baki na rawa na bude baki da kyar nace Dan Allah daddy kayimin rai kaji kaina !!</p><p><br /></p><p>" wallahi sharrin shaitan ne da kuma zuciya Daddy abunda kake nufi bashi ya faru dani ba!</p><p><br /></p><p>"Ta karasa zancen cikin rawar murya Asma'u kin bani mmki sa'annan kin tozarta ni A idon dunia nayi tir da halinki wae yau ace ni da girmana da mutunci na ya'ta ta dauki kafa tabi wani da namiji A hotel !!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" kanki kika cuta Asma'u bamu ba mgana na ,"Na karshe dake na cireki daga makaranta idan itace tasa idonki ya bude haka bbu ke bbu zuwa jami'a nan da Sati biyu zan hada Aurenki keda Shema'u keda Al'ameen kafin nan xansa Aliyu yakaiki a bincika ki ko bakida cutar H.I.V. </p><p><br /></p><p>"Kar aje a cutar da yaron mutane duk da shi yaji ya gani xai iya kwasar ki " A haka bana son in kara ganin kafarki ta taka koda harabar gidan nan ne bbu ke bbu fita sae Ranar da mijinki yaxo ya kwasheki da kansa shashashar banza shashar wofi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hannu nasa akae na zunduma ihu haka kuma yasa nayi saurin mikewa " A tsaye Daddy kayimin Rai bana son Aure wallahi!</p><p><br /></p><p>"Nayi alkawari a wannan karon xan dinga jin mganarka amma wlhi bana son yayah Al'ameen tafada cikin ihu da hargagi Sakin baki daddy yyi yana kallon fitinar ta !</p><p><br /></p><p>Da gudu Taje ta kankame mama tana gunjin kuka mama nasan kexaki fahimceni kinfi kowa sanin ciwona kiyimin Rai ki fadawa daddy yajanye wannan auren bana son Yah Al'ameen bana kaunar s......jintayi an fincikota jikin mama Gamida bata tagawayen mari har. Kwa'ra biyu ..</p><p><br /></p><p>" Wanda suka kusa zautar daita ido biyu tayi da Yah Aliyu haka yana korarin cire belt din wandon sa Ya Al'ameen ne yyi saurin dakatar dashi Kabar sa ya dakeni din.".</p><p><br /></p><p>"Wallahi baxanyi wannana auren ba !! Tacire hijab din jikinta A zuciya Aliyu yyi cikinta ubanwa kike yiwa rashin kunya ko zaki mutu sae kinyi wannan Auren tun muna mu biyu ki dauki hijab dinki ki saka ki wuce muje Asibiti ayi maki gwajin kanjamau"..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wani sabon ihu ta Saki gamida bajewa a kasa Kalmar da tafi tsana kenan fiye da komae A dunia kururuwa ta hauyi masu haka lokaci daya ta haukace masu ,ni na fada maku bana da komae kunbi kun isheni shin Ku baxaku fahimci matsala ta bane??</p><p><br /></p><p>Ta fada cikin dasheshiyar murya anki a fahimta Cewar yah Aliyu yah Al'ameen ne ya fara lallashina akan na tashi mutafi wani banza kallo na dinga jefan sa dashi inajin tsanarsa A raina banyi aune ba naji saukar belt ihu na saka gamida zabura ,naje na kankame daddy haka yasa daddy ya dakatar da Ya Aliyu ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Fashewa nayi da matsanacin kuka daddy ka daina sona ko??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Na fada maku ba Abunda kuke zargina dashi bane ya sameni meyasa kowa ya kasa fahimta ta laipine na Riga na aikata "Amma ynxu anyimin hnkalin da koda kudi akace na kalli da Namiji .ban isa na kallesu ba."</p><p><br /></p><p>"Daddy nafika jin ciwon abunda na aikata inajin tsanar maza araina bana son wannan auren plzzzzzz..."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zubewa tayi a gabansa tana famar rokonsa Wani irin tausayin ya'rtasa yakeji Amma baxai nuna mata ba har sae ya nuna mata kuskurenta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Haidar Ka dauketa kuje Asibiti yana gama fadin haka yasa kai ya fice daga falon ,itama mama side dinta ta nufa cike da takaicin ya'rtata.''</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Duk wata kalan haukanki baxata tsorata ni ba .bbu daddy bbu mama lallasa ki zanyi kitashi muje da arziki ko na illataki !!</p><p><br /></p><p>Yyi maganar cikin fushi Abu ga soja bbu musu ta mike tsaye ta dauki hijab nata badan wae taji tsoron kalaman sa bane A'ah tanajin bakin cikin yarda mahaifan nata. Suka kasa yarda daita."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>To ina gashi wandda Akeso ta aura ta tabbata bayan aurensu sae taga wulakanci. Da tozarci amma ta kudiri aniyar bazata auri Al'ameen ba komae zai faru.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da gudu ta shige bayan mota yyinda Aliyu da Al'ameen ke agaban mota tana fatar Allah ya dauki ranta kafin sukai Asibiti.</p><p><br /></p><p>"Ta tsani maza bata son su bata kaunar su..</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>32</p><p><br /></p><p>"Fitowar su kenan daga Asibitin Mln Aminu kano yah Aliyu sae jifana yake da mugun kallo kinci arziki baki da cutarnan a jikinki sae a kiyaye gaba ban kulasa ba na shige mota abuna.</p><p><br /></p><p>" Daddy ya kira a waya ya masa bayani bansan dae me daddy yace ba sa'annan yyima motar key muka nufo gida.</p><p><br /></p><p>★★★</p><p><br /></p><p>"Yana kwance bisa gadon alfarma ya xubawa wyar tasa ido da suke vedio call da kanwar tasa Wanda a zahirin gaskiyya hnkalin sa baya kanta.</p><p><br /></p><p>" Yaya na!</p><p> Yes my angel ya fada haka ya zuba mata ido meke damunka ne A ya'n kwanakkin nan duk kabi karame??</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Murmushi ya kwa'kwalo idonki daene kiyi maki gizon haka!!</p><p><br /></p><p>"Are yhu fall in love wit some one else??"</p><p><br /></p><p>"Da sauri ya kalleta cike da mmki ,meyasa kikace haka??"..</p><p><br /></p><p>Gayanan ana ganewa A idonka plzzz karkaxo ka dagama kanka hankali Yaya kasan ciwonka bayason damuwa ko kadan " wani sati ya kamata kaxo India ta fada cike da shagwaba." Baxan samu xuwa ba Mimi sae dae ki kara hkuri.</p><p><br /></p><p>Cikin fushi tace Sabida matarka ta Riga ta gama dakai ko??..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>No ba haka bane Angel "Aiki yyimin yawa ne shiya sa kullum haka kake fada yanxu bansan meke damunka ba duk kabi ka canja ni na fada maka dole kaxo wani sati india xan hada ka da wani likita Dan ni Sam hankalina bai kwanta da kaiba."</p><p><br /></p><p>"Tana gama fadin haka ta datse kiran pic nata ya zuba ma ido dake kan screen din wayarsa Doguwar ajiar xuciya ya sauke."</p><p><br /></p><p>Bansan ya zanyi da rigimar ki ba Mimi banjin xanje india xuwa wani sati bansan wane hali Drama Queen dina take ciki ba.kwana biyu kenan yana xuwa skull nasu baita ba ganin ta ba haka unguwar su Duk lokacin da xasu tafi islamiyya sae dae yaga kannenta da kuma kawarta ."</p><p><br /></p><p>Wadda mgana wannan bata taba hadasa daita ba yarasa yarda xai tunkareta ya tambayeta ,haka yana ji ajikinsa Drama Queen bata cikin natsuwarta A cikin kwanakkin nan."</p><p><br /></p><p>Samun kansa yyi da kiran granny dinsa yana cikin kewarta ,kira daya ta dauka cike da murna jin muryasa kasa -kasa yasa Ta fara tambayrsa ko bayada lpia ne??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Idonsa yaji ya ciko da kwallah ." granny ina. Sonta bansan taya xan sameta ba ina bukatar ki kusa gareni ,acikin xuciyarsa yake mganar.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Abdul jabbar !!</p><p><br /></p><p>Na'am granny ! Meke faruwa ne ??" Bbu komae granny kawae dae ina kewar Ku plzzz kixo kano granny Dan Allah ya fada cikin muryar tausayi."</p><p><br /></p><p>"Ajiar xuciya ta sauke Anyya kuwa zuwan nan xai yuyu Abdul " matsalolin gidan nan sunyi yawa Abdul jabbar ynxu Aliya itake juya komae na gidan nan Abinci ma kokarin gagarata yakeyi duka ta kora ya'n aikina!</p><p><br /></p><p>Baka ga yarda nake Rayuwa bane kullum Sadiya ke aiko driver da abincina na break fast lunch,dener duk safiya ta Allah."</p><p><br /></p><p>Abdul jabbar sae addu'a idan da kaga yarda ake shigowa da manyyan Alhazzai a gidan Ku sae abun ya girgixaka kwanakkin baya korar kare Aliya tayiwa sageer A company dinku."</p><p><br /></p><p>Sae da kyar da sidin goshi sageer ya samu ta maidashi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bakaramin kokari sageer ya maka ba Wani irin bakin ciki Abdul jabbar yakeji a ransa ji yake tamkar yabar kano a yau yaje ga granny dinsa.</p><p>"Amma bbu damar haka Cike da lallashi ya fara mgana hajjata kwantar da hankalinki ki shirya kayanki gobe xakixo kano kiyi kwana biyu xanyi mgana da Aunty sadiya da haka ya datse wayar ...</p><p><br /></p><p>Tunani ya farayi a ransa baxai bar kano ba sae ya mallaki Asma'u a matsayin matarsa ta auro ,da itaje xaiyi amfani daita wajen daukar fansa ."</p><p><br /></p><p>*******</p><p>Shirye shiryen biki akeyi a kowane bangare ."</p><p><br /></p><p>Karfe Tara na safe na killace kaina A daki haka yyi dae dae sauran kwana bakwai bikin mu "A wannan lokacin duk wandda ya sani baxai shaida niba nayi baki na Rame na fita hayacina !!</p><p><br /></p><p>" Ya'n gidan mu bamae shiga sabgata kallon marar hankali ma sukeyi min Daddy yace a zuba min ido xan gaji da haukata ne na daina aure dae bbu fashi sae "An Daura ....</p><p><br /></p><p>Ko ynxu xaune nake a dakina ina risgar kuka da naga bbu abunda kukan xai tsinanamin haka kuma bbu mai lallashina na aza hannuna akan kai na shiga zunduma ihu" gamida ruguza kayan dakina ,tunda ga kan mirror dressing da kananan Abubuwa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Na shiga kwarara ihu da saurin karfina ina bubbuga hannuwana jikin bango jama'ar gidan jin ihuna gabadae sukayo dakina suna tunanin ko wani mugun Abu ya sameni ."</p><p><br /></p><p>Kallona suka tsayayi tamkar masu kallon talabijin ,Aunty shema taja tsaki gamida gallamin harara Ciwon haukan nata ya motsa kenan??"</p><p><br /></p><p>"Cewar Aunty shema aunty zulfa ta amshe xancen da fadin Da alamr na kara sakin ihu nace ina ruwanku munafukkai nikam anriga an gama dani Ancuce ni tunda aka hadani Aure da yah Al'ameen."</p><p><br /></p><p>"Uban waye ya cuceki??Cewar yah Anas Wanda ya ratso cikin dakin nawa ,da duk wandda ya hadani Aure da yah Al'ameen ido bude yah Anas ke kallonta." Wato uban namu ne ya cuceki kenan??...</p><p><br /></p><p>"Belt ya cire ya shiga jibagata dashi yana dukana wandda xankira da dukan mutuwa Wanda tunda Allah ya halicce ni ba'a taba yimin makamancin saba."</p><p><br /></p><p>Bbu mai kwatata a hnnun yah Anas Sae jin nayi an rike yah Anas gagam." Ana fadin yah Anas gani ka dakeni kadaina dukarmin kanwa karka kashemin ita tunda Ku bakwa sonta ni ina sonta !</p><p><br /></p><p>"Muryar (ABDUL HAMEED OMAR OMRA") naji tana yimin yawo a kwakwalwa ta Anan wurin kuma na fadi A some...</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>33</p><p><br /></p><p>"Hameed Omra ne yyi saurin tarota a jikinsa ya kalli Yah Anas hankali a tashe yace shikenan ka kasheta yah Anas!</p><p><br /></p><p>" Idan wani Abu ya sami kanwata bazan taba yafema kuba." Yah Anas yyi tsaki kanku akeji dama ae kalan haukan Ku daya indaan akuyan gaba tasha ruwa tana baya kesha.</p><p><br /></p><p>"A fusace Yan Anas yabar dakin gamida bugo masu kofar A hnkali ya kwantar daita kan gado da gudu ya sauka kasa yana kwalama shema'u kira cikin hargagi da kunar rae."</p><p><br /></p><p>"A tsorace ta fito lpia yah Hameed irin wannan kira haka ??" ya galla mata hara Dan Allah bani ruwa masu sanyi a fridge ." munafukan banza munafukkan wofi wlhi idan wani Abu ya sami kanwata baxan barku ba."</p><p><br /></p><p>"Ya fisgi gorar ruwan hnnunta ya koma sama da gudu mama bin Dan nata tayi da kallo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tallabo fuskarta yyi ya bude gorar ruwa gamida Dan xubasu a hnnunta yana Shafa mata a fuskar haka yana tofa mata ayautul kursiyu Ajiyar zuciya ta fara saukewa da karfi tafi minti biyar a haka kafin tayi nasarar bude idonta wandda suka kumbura gamida fuskarta da tayi sukutum!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asma'u sannu kinji." Ya fada cikin so da kulawa kokarin mikewa take ya hanata zubama ta ido yyi gaba dae ta canja ,tafita hayacinta sae kace ba Asmy ba ya'r gayu "yanxu ba wannan gayun...</p><p><br /></p><p>" Yayah Hameed!!</p><p> Ta fada hawaye suka gangaro daga idonta .Ina ka shiga??" tsawon wannan lokacin kabar rayuwata cikin wahala gaba dae gidan nan nasan ba'a kaunata kai kawae ke sona!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Plzzz karka bari Daddy ya auramin yah Al'ameen yi shuru haka Asmy taimakeni ynxu kiyi wnka yanxu xanje na hada maki break fast kinji karki damu bbu maiyi maki Auren dole muddin ina Raye."</p><p><br /></p><p>"Taimaka mata yyi ta Mike tsaye Yabar dakin itakuma ta rage kayan jikinta ta fada ban daki danbin umurnin yayan nata.."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka Hameed ya tube ya dawo daga shi sae Tree quarter da farar singlet ya fada kiching su Aunty shema sae gulmarsa sukeyi kasa-kasa suna daria mama ta dubesa me xakayi haka kiching Abdul Hameed ??"</p><p><br /></p><p>Idan wani Abu kakeso baxakayi ma su zulfa magana ba su hada maka meye "Amfanin su??...kibarsu kawae mama xan hada mata da kaina tunda bbu Wanda ya damu daita ni Ae na damu daita gani na dawo zan cigaba da kula da Abuta."</p><p><br /></p><p>"Daria Abun yabawa mama tabbas kaunar Hameed da Asm'au daga rabbil izzati ne badan sun fito ciki daya ba da sae tace Hameed din son Aure yakewa kanwar tasa."</p><p><br /></p><p>"Da haka Mama taja bakin ta tayi shuru hakama ,aunty taxo ta sami Hameed din A kiching tambaya dayace haka Amsa daya Dan haka suka xubama sa ido ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kusan kawae Shidda ya soyama kanwar tasa sa'anan ya soyamata Dan kalin turawa sa'annan ya hada mata Tea.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Daga kiching ya dinga kwalawa Zulfa'u kira sae gata da sauri ta shigo kiching din gani yaya!</p><p><br /></p><p>"Daukar min ki kai Dakin Asma'u bbu musu ta dauki kulan Dankalin da plat shin kuma ya dauki flask da cups nashan tea haka yaxo ya wuce mama ."</p><p><br /></p><p>Sau mazurai yakeyi yana hawa kan stairs Shema takasa rike daria cikinta ...tako kyalkyale da daria wayyo ! Cikina yau ga likita da shiga kiching ! </p><p><br /></p><p>"Hahhhhhhhh !</p><p>Kasa- kasa take dariar tata Dan tana tsoron yajita yaci kaniyar ta ,tana cikin shadda galila doguwar Riga tana parking din gashin kanta sae gaya sun shigo ."</p><p><br /></p><p>"Anan zulfa ta galla mata harara bata kulata ba ta maida hankalinta kan yayan nata sannu da aiki Yayana! Yawwa kanwata kinga yarda kikayi kyau ko kefa ,ynxu kika fito Ainahin Nana Asma'ul husna sak!👌🏿 " murmushi tayiwa yayan nata zulfa anan ta wuce tabar su bara naje nayi wanka naxo muyi break fast "..ni na hada mana break fast bama cin na gidan nan ." tunda basa sonmu ya karashe maganar yana kallonta." Murmushi mai kyau tayi Dan haka nakeson ka yah Hameed dina kuma abokina ina sonka yayah Hameed!</p><p><br /></p><p>"Yhu Are d best lovely brother in d World " murmushin sa Mae kyau yyi mata nima haka kanwata bara naje na watsa ruwa anan ya fice daga dakin tabi yayan nata da kallon so Tabbas tasan baxa'ayi mata wannan Auren ba tunda yah Hameed nata yana Raye."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>********</p><p>"Tare sukayi break fast da yayan nata anan dakin ta." bayan sun kammala ta kawalama mai aikin nasu kira taxo tattare gurin ,haka yah Hameed ya umurceta da taso suje Dayan falon daddy suyi magana mai'aiki ta Dan gyara mata dakin Dan yaga duk ya wani hargitse."</p><p><br /></p><p>Murmushi tayi gamida bin umurnin yayan nata ."..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Duk cikin yayunta tafi jin mganarsa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Suna xaune " A falon daddy karami ya fuskanci Kanwar tasa Dan yana son yaji gaskiyyar lamari kafin ya dauki mataki bata boyemasa komae ba akan soyayyar sa da Emran .."</p><p><br /></p><p>"Yah Hameed nayi da nasanin Em " A rayuwata nasan nayima su daddy laipi amma meyasa baxasu karbi uzurina bane??" Tunda a rayuwa bbu wandda baya kuskure kuma yaxo ya tuba."A kayiwa mahaliccin mu laifi ya yafe balanta na Dan Adam."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yah Hameed wannan hukuncin na daddy baiyi min dadi ba ko kadan bana bukatar wani da namiji acikin Rayuwata a halin yanxu burina baifi na koma makaranta ba ." Dama can Al'ameen ya taba fadin yana sonki??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tambayar da yayan nata yyi mata kenan,a kwanakkin baya nasan muyi mganar Amma.ban boye masa komae ba bana jin soyayyar sa yah Hameed A raina lokacin ma muna tare da Em." Ina ga yanxu da abubuwa suka rikice ....."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hawaye suka gangaro akan Kuncinta na tabbata koda baka goyon bayana yah Hameed baxanyi wannan auren ba sae dae kuyi gunduwa gunduwa dani ,ta sharbe majinar hancinta sassauta murya yyi Haba Nana ta bansan Asmy da kafiya hakaba." Kinga shi Al'ameen din yana sonki fa kuma xakiyi farin ciki a gidan sa na tabbata kodan Amintar mu dashi xai rikemin kanwata da Amana ! Kiyi hkuri Da auren nan.ki Rungumi kaddarar ki Nana Asma'u na tabbata "(WATA RANA!)) Zakiyi Alfahari da Auren Al'amin kinji Ma'u na!!</p><p><br /></p><p>Kuka na fashema da yah Hameed dashi lokaci daya na birkice masa ,ganin da gaske yakeyi ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Na rantse maka da Alllah Mr.Hameed Omra koda "Gunduwa -Gunduwa xakuyi dani baxanyi Auren nan ba nafiso Ku babbaka ni A gidan nan ta fada tana sharbar hawaye baki wangalau ya saki yana kallon Kanwar tasa baitaba ganin fitinanniya irinta ba ...ta Fiye rigima da yawa Sam mai sunan ta ba haka takeba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bbu musu Hameed ya langabar dakai yana kallon kanwar tasa murya kasa kasa yake fadin,Abun baikai can ba Mrs.Omra bbu wandda ya isa yyi miki dole."</p><p><br /></p><p>*"TEAM ASMA'U OMAR OMAR*....🌹</p><p>WATA RANA !</p><p>[Posted on 26 July 2017 .@t 8:30pm]</p><p>By~Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p>34</p><p><br /></p><p>"Share Hawayenki babbar yarinya daina zubar dasu kar Al'ameen yyi galaba akanki ." yah Hameed yyi mganar cikin taushin murya bbu musu ko na shiga goge hawayen idona."</p><p> "Wyarsa ce ta katse mana mganar da mukeyi."</p><p><br /></p><p>Daga wyar yyi ni gani ma A gida ohkey tom." Ganinan fitowa yah Hameed ya kalleni cike da kulawa ,xanje na dawo my Asmy kije ki kwanta ki huta zankira ki "A waya cikin shagawaba take fadin Yah Aliyu ya karbe wyar." Idonta taf da kwallah murmushi yyi karki damu zankira zulfa sae ta kaimaki wayar daga kai tayi har kofar babban falo ta rakosa ." dai dai kuma lokacin Rahama ta shigo Falon anan take gaisheda yah Hameed ya amsa cikin Sakin fuska."</p><p><br /></p><p>"Yana wucewa tace ke lpian ki kuwa?..Galla mata harara tayi da ban kwana lpia ba da baxaki gani haka ba." Aeni wallhi Rahama na maidake cikin ,makiyana irin su Yah Anas daria Rahama tayi kai haba Amarya kawallin ki face muje kiji yah Al'ameen ma ya aikoni Nan take yanayin ta ya canja ,Rahama taga haka Sae dae batayi mgana ba suka nufi dakin Asmy din."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>***********</p><p><br /></p><p>"Granny ta zuba ma jikan nata Ido na tsawon lokaci duk yabi ya rame ya fita hayacinsa Rak! Na gefensa Ta saka hannunta cikin nasa sae famar damunsa takeyi da tambaya Yah AJ.meya sameka haka bakada lpia ne??..</p><p><br /></p><p>" lokaci Daya yasha mur."nikam hajja meyasa kikaxo min da Rak ! Ne."Mae sa mutum ciwon. kai .cikin shagwaba da turo baki tace auh nice Mae saka ka ciwon kae??</p><p><br /></p><p>"Ae dole ce Abdul waini kam Salma meke damun wannan Dan naki kodae yyi Rashin lpia ne??"</p><p><br /></p><p>"Aunty Salma tayi daria Kin dai San halin sa hajja ko yana ciwo ina xan sani miskilancin sa yyi yawane ,kullum tamabayr da Abban su Nana keyi masa kenan yace bbu komae maybe yana missing Aliya ne!!</p><p><br /></p><p>" Nan take AJ. Yabata Rai Mikewa tsaye yyi ya nufi hanyar fita daga falon lokaci Daya hajja tabisa da kallo hka tana karantr duk wani motsi nasa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ajiar zuciya ta saki Alamun sun nuna Salma da gaskiyyar ki ba matarsa yake yawan tunani ba ." yau watansa nawa da rashin macce kowan nan kawae zae saka sa a wani hali."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ajiar zuciya Aunty Salma ta sauke Shina gani hajja ina tsoron yaxo ya fara Neman mata duk da nasan mayuwacin Abune Abdul jabbar ya kusanci zina ." Na karance sa tsaf!!</p><p><br /></p><p>"Harda Rashin macce na damunsa Hajja fa yyi ko'kari ba kadan ba ." Amma ni hajja ga shawara Mae xai hana A hadasa da Rukaiyya tunda A Bauchi take karatun ta."</p><p><br /></p><p>"Idan tasamu Hutu sae ta dinga zuwa kano hakane pah Salma kinyi tunani amma fa." Ni bana son na takurawa yaron nan duk da Rukaiyya jininsa ce nasan baxai kitaba. Amma gara a tambayi Ra'ayinsa hakane kuma hajja kibarni dashi xuwa anjima xamuyi mgana."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yawwa hajja yanxu kidan watsa ruwa sae ki huta xuwa anjima kinga tafiar motace kuka yi." Haka za'ayi Salma Allah yyi Albarka ya kara daukaka Amin.''</p><p><br /></p><p><br /></p><p> "Anan Aunty Salma ta hadama hajja ruwan wanka...</p><p><br /></p><p>********</p><p>Waeni kam Nura meke damun AJ. Ne??"</p><p><br /></p><p>Rukaiyya tayiwa Nura tambayr tareda folding din hnnunta a kirjinta .ta zuba masa ido da alamr shi take saurare .." Murmushi Nura yyi kunfi kowa sanin yayan naku ,Zurfin cikinsa yyi yawa ni ina tsoron ma ciwonsa ya tashi wlhi ni kanà yimin magana "A dunkule ya kamata kayimin bayani mana."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Bbu Abunda keda mun yayanku sae dae ya fada cikin Tarkon wata " Karuwa!!</p><p><br /></p><p>"What??</p><p>Rukaiyya ta fada cike da tashin hnkali meya hadasa daita ? Anan Nura ya fayyace mata komae ,Yana wahalar da kansa ne kurum dan yasan Hajja baxata barsa ya aureta ba !!</p><p><br /></p><p>Haba Nura ka daina ma danganta Aurensa da karuwa ,to wlhi yau za'ayita ta kare xanje na fadawa hajja."</p><p><br /></p><p>"Da sauri Nura ya dakatar daita karkiyi hka muje dakin sa muyi mgana kai tsaye dakinsa suka nufa ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana zaune A gefen gado Yana rike da karamin window size na photon ta ya ku'rama masa ido sun dde tsaye A kansa A fusace Rukaiyya ta fisge frame din pic din lokaci daya tabi pic din da kallo wata kyakkyawar budurwaace Ajin farko ta hadu ta koina black beauty ce haka kyakkyawar karshe ce Bata San lokacin da tayi watsi da frame din ba ya tarwatse A tsakiyar falon ...Kan wannan karuwar zaka nemi kashe kanka yah AJ.haba yah Abdu..........saukar mari taji A fusace A tsorace tabi yayan nata da kallo wandda idonsa yyi jajawur ,bata taba ganin fushinsa irin yau ba! Jikinsa har tsuma yakeyi yna so yyi mgana ya kasa Bakinsa sae rawa yakeyi " Anan kuma ya dafe saitin zuciyarsa dake masa Zogi Gaba dae Rukaiyya ta Rude." Tama manta da marin da ya zabga mata." Taga -Taga yaje zai fadi Nura ne yyi saurin Rikosa Numfashinsa dakyar yake fita sae ynxu Hawaye sukayi nasarar Zubowa a idonsa haka lokaci daya kuma ya lumshe Idonsa Da sauri Numfashin sa ke fita kafin ya tsaya cak!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Ma'u*🌹</p><p>WATA RANA!</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>35</p><p> "Likitoci biyar ne Akan sa suna kokarin ceto Ransa Sunfi Awa ukku akansa ,da dakyar sukayi nasarar samo kan matsalar Haka suka saka masa( oxygen) yayinda Hajja ta jingina da kofar (Emergency Room) da yake ciki haka tana hango fuskarsa cikin Oxygen da aka makala masa." Tana karanta duk Addu'ar da tazo bakinta."</p><p><br /></p><p>"Aunty Salma na xaune a gefe ta xuba ta gumi yyinda Rukaiyya hawaye suka dinga zuba a fuskarta bbu alamr tsayawar su ,tana tunanin duk ita taja masa shiga wannan halin Abban Nana ne mai karfin halin lallashinta shida Nura amma fafur taki ,sae da hajja ta daka mata tsawa."</p><p>.zakiyi mana shurune ko kuwa da ciwonsa zamuji shida ke kwance magashin cikin wani hali koda kukan ki ..kai Nura xoka maidata gida kama baki Rukaiyya tayi gamida xubewa a gaban hajja na tuba hajja baxan kara ba ,Dan Allah karki sa "A maidani gida hajja tayi tsaki gamida dauke kai ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dai-dai kuma lokaci likitatocin suka fito daga emergency room din" Babban su ne ya dubi mijin Aunty Salma yace ya samesa a office ,hajja najin haka ta mike tsaye tabi bayan sa itada Aunty Salma cike da tashin hnkali."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Gabadan su Xaune suke sun xubama Dr. Ido sunajin mae fada gyaran murya yyi sa'annan ya fara yimasu bayani kamar haka.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kusan Yana da ciwon zuciya ne??..</p><p><br /></p><p>Tambayar da Dr.basheer galadima ya jefo masu kenan cikin karfin hali Aunty Salma tace Ehhh Dr."</p><p><br /></p><p>"Kunsan da haka kuka fada masa Abunda ya girgixa sa har jininsa ya hau ,mugun hawa kuwa haka yyi sanadiyar tashin ciwon zuciyar sa kenan ,amma yanxu mun shawo kan matsalar Dan Allah ku guji yimasa maganar Da zata taba zuciyar sa ynxu gayanan ya haifar masa da wani ciwon kai na gefen kai daya ,domin yakan haifar da Harbin kwa'kwalwa har ya haifar da (Depression)...Dan haka a kiyayye saka shi acikin damuwa plzzzzz ,ciwon sa baya bukatar hnkali.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>***********</p><p>" Misalin karfe bakawae dai - dai na yamma Agogon Asibitin ya nuna dai dai lokacin da AJ.ya bude idonsa haka ya dinga bin dakin da Kallo ido hudu sukayi Da .dr. basheer murmushin Samun nasara yyi gamida Cirema sa Oxygen din da aka saka masa A hanci.</p><p><br /></p><p>"Sannu Abdul !</p><p>Cewar dr. basheer taimaka masa yyi ya Dan tashi xaune nan yyi ido biyu da Rukaiyya ,nan ya tuno abunda tacewa Drama Queen nasa harda fasa pic nata ganin irin kallon tuhumar da yake yimata tayi Saurin dauke kanta ." Dr. Basheer ya kalli Rukaiyya ina sauran suke? Yyi mata tamabayr gamida zuba mata ido cikin farin gilashin sa .A sanyayaye tace sun tafi massalaci ,ohkey ki zauna dashi zanje nima nayi sallar yyi hanyar fita yyinda Rukaiyya ta dawo kusa ga Aje har ta tana gogar tasa ,sa'annan ta Daura kanta a kafadar sa saurin tura ta gefe yyi gamida matsawa kusa daita A tsorace take kallonsa idonta cike da kwallah Bakida kirki Rak!</p><p><br /></p><p>Ya fada cikin muryarsa tamarasa lpia .."kema kin yarda da abunda Nura ya fada kan wani dalili nasa na banza zae Dan ganta matar da nakeso fiye da komae "A dunia da karuwa !!! kitashi ki fita bana son ganin ki A kusa dani ya fada cikin tsawa tsawa " A tsorace take kallonsa ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bakiji mai na fada ba kinenan ? " Hannunta tasa ta rufe masa baki haka hawaye na zuba a idonta girgixa masa kai tayi alamr yyi shuru Dan Allah plZz na rokeka karka dagama kanka hankali "A fusace ya fisge hnnunta kan Bakinsa ..</p><p><br /></p><p>" I said get out of my Room!!</p><p><br /></p><p>Kosae na nuna maki ta ido gamida jinyatar dake sa'annan Auchhhhhh!! Dafe kansa yyi jin wani irin wani a zababben ciwon kai na gefe daya ,dae dae nan su hajja suka turo kofar dakin Rukaiyya bata tsaya ba tafice a dakin Da gudu tana kuka yyin da Hajja suka karasa gurinsa A tsorace .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ya daga Jajjayen idonsa Yana kallon hajja Yana son yyi magana ya kasa Aunty Salma ta fita kiran likita da sauri...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*****</p><p>Nura ka taimakeni ka kaini gidan su Asma'u! Wae meke damun ki ne Rukaiyya??" kinsan kuwa wannan shaidaniyar?. na tabbata ko kallon ariziki baxaki samu" A wurinta ba .naji na dauka in dae xata saurareni indai xataji halin da Yah AJ. Yake nasan in dae Ita mai tausayi ce xata duba mgana ta Nura bana son ya rasata wllhi na Hakura da son Da nakeyi wa Yah AJ." Indae har zan samo masa farin cikin sa Aza kanta tayi a jikin motar tana shesshekar Kuka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*TEAM AJ." OR TEAM Al'Ameen*??".....🌹</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>36</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Gaba dae Ahalin Alh.umar omra suna a katafaren falon sa da misalin karfe Tara da rabi na dare.yyi gyaran murya sa'annan ya kalli Mama " ya fara da fadin ke Khadija kinji Abunda ya'yanki suka yimin ko ??"</p><p><br /></p><p>Mama da mmki take kallon Sa kamar ya ya'yana daddy."??</p><p><br /></p><p> "Ni dae na rokeka ka daina sanyoni cikin sha'ani Asma'u sabida ta Riga da tafi karfina ,shikuma Hameed din tunda bayajin mgana ta ya biye mata sae yaje yyi tayi ."</p><p><br /></p><p>"Rai bace mama ta mike tsaye zatabar falon yyi saurin da katar daita ya gano fushi tayi." Dawo kiji Khadija ,ae bamu gama mgana ba."</p><p><br /></p><p>"Bbu musu ta dawo ta zauna amma ran nan nata a hade Yah Anas ya gallama yah Hameed harara ina kallon yah Hameed din yyi murmushi gamida dauke kansa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Naji Abunda kace Abdul Hameed xan sassauta ma Asma'u da hukunci da na yanke Akanta amma fa Aure ne bbu fashi!</p><p><br /></p><p>"Da sauri Asmy ta kalli yayan nata gamida yin " rau rau da idonta. " </p><p><br /></p><p>"Ina Son ta kawomin wandda takeso din Xuwa gobe jibi xan hade Aurenta da na ya'n uwanta shi kuma Al'ameen sae ya auri zulfa ,Dan ni Asma'u ta gama zaman gidana ." cikin Tashin hnkali Asma'u ta bude baki da niyar tayiwa daddy magana Yah hameed yyi saurin,dakatar daita ." Hankali tashe take kallon yayan nata ..nan Yah Hameed yyiwa daddy godia yyinda hukuncin Da daddy ya yanke baiwa mama ddiba dasu ."Yah Anas ..."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin fushi yah Aliyu ke fadin Daddy Dan meye zaka biyema shirmen way'annan yaran ?? Kafiso ka faran tamasu kaji kunya a idon dunia??" Shin ya zakayi da Yaron nan Al'ameen da mahaifinsa??.. wannan ba matsala bane Babana! Nasan mahaifinsa xai fahimceni dashi kansa Al'ameen din ,zulfa'au kuwa nasan zatayi min biyayya!!</p><p><br /></p><p>"Da haka taro ya watse mama taja tsaki bayan fitar yaran ." Daddy ka daina biyema wannan yarinyar wlhi to yanxu ina xata samo miji nan da kwana daya??" Ina fa jin hirar da sukeyi da Rahama aranar shi saurayin ma wandda takeso yaudarar ta yyi Dan tuni ya samu wata!</p><p><br /></p><p>"A hnkali daddy ya kamo hnnun mama Yana murzawa a hnkali bansan Ki da fushi ba ." Nana Khadija ,Addu'a zakiyi mata su kuma ki zuba masu ido naga yarda zata samu miji nan da kwana daya ." tunda samun mijin wasa ne ba."daita da yayan nata ba hankali ne dasu ba daga waya ki kiramin zulfa'u bbu musu mama ta nemi layin Aunty zulfa anan ta sanar mata kiran daddy din nasu."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>******</p><p>"A can kuma dakin Asmy hnkali tashe take kallon yayan nata!</p><p><br /></p><p>" Idonta yyi Rau rau yah Hameed kaji daddy da wani sabon zance kuma??"</p><p><br /></p><p>Ta fada cikin muryar son tayi kuka."ni ina ruwana da wani namiji tunda nasamu 'ya janye zancen hadani da yah Al'ameen. "</p><p><br /></p><p>"Baza'ayi haka ba husna! Kin dae San halin Daddy ,ki lallaba cikin samarin ki kisamo wani din wandda kin kasan zae rikemin ke Amana!!</p><p><br /></p><p>" Hawaye suka silalo daga kan fuskarta Jin tayi mganar wani iri nabarki lpia kiyi tunani da kyau kanwata ." da haka yaja mata dakin fadawa tayi kan gado gamida Rushewa da kuka." Itakam ta shiga ukku!! Ynxu ya zatayi da daddy ??...."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>**************</p><p>Da misalin karfe goma sha daya na safe tafito falon cikin shigar "dinki Riga da skirt na Le'ss brown da Ratsin Milk a jikinsa ....sae Dan karamin veil milk Wanda ta yafa saman kanta handbag nata da hills shoes nata brown ne taci uban gayu sosae sae kace mai shirin xuwa Party " Sae uban kamshi take zubawa ,cikin takunta na yanga da Jan hnkali ta iso falon gaba dan su suke xaune "A falon yyinda AJ. Ke shan Ruwan Lipton hka hajja na gefensa" Kamshin da sukaji yasa sukayi saurin Dagowa Akanta."</p><p><br /></p><p>"Anan ta gaishesu batareda Ta kalli AJ ba shima ko kallo bata ishesa ba."..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Baxaki gaisheda Yayan naki da jiki ba??" Cewar hajja."</p><p><br /></p><p> ''A hnkali ta turo Dan karamin bakinta ta gaishe sa bai ko kalleta ba ,Kai kanaji bazaka amsa Gaisuwar kanwar taka bane??" .........Shaye da toka yake fadin bana Amsa gaisuwar marar kunya tabe baki ,tayi gamida dauke kae."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Aunty Salma ke fadin yau kaida Rak! Din naka angan Ku A Rana! Sae ina ya'rlelen Yah AJ??" Cewar Aunty Salma." Shaye da toka Rukaiyya ke fadin Fita zanyi zanje gidan wata friend dina ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Waye zai kaiki?". Cewar hajja ga yayan naki baya jin ddi.." Tareda yah Nura zamu fita jin tace Nura AJ.ya zuba mata manyan idonsa daganin yanayin kallon tasan na tuhuma ne ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hajja Aunty sae na dawo anan tafice da sauri Lokaci daya ,AJ.ya bita da kallo Yana mmkin ina xasu fita da Nura Dan shi yasan karya tayi bata da wata kawa a Kano."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dai dai kofar gidan su Asmy Nura ya faka motarsa ." yah kalli Rukaiyya da murmushi tom.kanwata Allah ya bada sa'a idan zaki fito ki kirani ta wya." Zan shiga gida.</p><p><br /></p><p>"Jiki sanyayye Rak ! Ta balle marfin motar kai tsaye ta nufi get din gidan su Asmy cikin takunta na kasaita " bata sha wahalar shiga gidan ba.."bbu laipi Aranta take fadin suma Ashe suna da kudi ,Amma duk da haka ko kafar Mr.meera family basu takaba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kai tsaye mai gadin gidan yyi mata iso xuwa shiga falon babban gidan sae da ya sadata da kofar sa'annan ya dawo bakin Aikinsa." Masu aikine ke kai da kawo sae Wata Hamshakiyar macce matar manyan wadda ke zube dae daga cikin kujerun dake zagaye da Falon tana Amsa wya."...</p><p><br /></p><p>"Da sallama Rukaiyya ta shiga dae dae lokacin da mama ta gama Amsa wyar,ta Amsa sallamr tata." Dauke da fara'a A fuskarta zubewa kasa Rukaiyya tayi tana kwasar gaisuwa." Mama ta Amsa cike da fara'a sun zauna Jim na ya'n mintuna mama tayi karfin halin fadin Ya'mmata sae dae ban shaidaki ba daga ina??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Murmushi Rukaiyya tayi haka ne momy ni kawar Asma'uce cike da fara'a mama ke fadin Ayya yi hkuri bara akaiki wajenta" Amma kafin nan bara nasa akawo maki Abun motsa baki."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Murmushi Rukaiyya tayi da kin. barsa momy wlhi na koshi kedae kisha koda ruwane bara nasa akaiki dakin Asma'u din sae a biyoki da Abun motsa bakin daga baya." Godia tayiwa mom.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tala!Tala!</p><p>Mama ta shiga kwalama mai'aiki kira da sauri Talan taxo ta zube gaban Mama gani Hajia nuna mata dakin Asma'u...sa'annan kixo ki dauki Abun motsa baki ki kaimata daga baya to hajia.anan Rukaiyya ta mike tsaye gamida bin bayan Tala kae tsaye up stairs suka nufa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sae da Tala tayi knocking kusan sau biyu shuru sae ana ukkun "A fusace Asmy ke fadin wae waye ne??"</p><p><br /></p><p>Cikin Rawar murya Tala ke fadin nice Asma'u dama bakuwa Hajia tace na kawo maki dogon tsuka taja ki shigo daita Mana."</p><p><br /></p><p>A hnkali Tala ta murda kofar Dakin gimbiyar tana kwance akan Gado Fuskarta bata ma kallon Kofa itakam Rukaiyya ta matsu tayi tozali da Fuskar wannan Asma'un da ta Rikita yayan nasu lokaci daya."wani fannin kuma kishi ne fal A ranta."..[Truncated by WhatsApp "Asmy b Aliyu novel's]..</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>37</p><p> </p><p>"Sanye take cikin wata farar Armless top da Red din 3quater,hka gaba dae bakin gashinta ya zubo a bayanta Wanda ya rufe mata fuska sallama Rukaiyya tayi A hnkali ta juyo da fuskarta tana fuskantr ta kallo-kallo suka farayi wa junan su na ya'n sakwanni " Cikin karfin hali Asmy ke fadin sannun ki da xuwa nuni tayi mata da Duguwar coach dake gefen gadonta almr ta xauna bbu musu Rukiayya ta zuuna gamida Dan bin dakin da kallo sa'annan ta tabe bakin ta.</p><p><br /></p><p>"Kafarta daya ta Daura akan daya ta shiga wasa da wyar hnnunta.</p><p><br /></p><p>" ki'rar galaxy 65 dinta anan kuma ta shiga ka'rema Asmy kallo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ko kusa bata da muni koka dan ta hadu ta koina sae dae kurum ita bakar fata CE ."</p><p><br /></p><p>Batasan meye AJ. Ya gani ajikin Asmy ba Wanda ita bata dashi ,Dan siririn tsaki tayi Wanda bata ma San ya fito ba.</p><p><br /></p><p>"Da yake Asmy din yar jin kai ce ,sae ta Dan jingina da bayanta kan bed din ta dauki pillow daya ta rungume a jikinta " sa'anan ta kalli Rukaiyya gamida sakin wani malalacin murmushi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dae-dae kuma lokacin Tala tayi sallama dauke da katon tray a hnnunta cike da cima kala-kala irin na tarbon bako dae haka .taja karamin center table gamida ajesa A gaban Rukaiyya har xata juya Asmy tayi saurin dakatar daita "tala ki zuba mata ko drink din mana''</p><p><br /></p><p>" Ta fada cikin hadaddiyar muryarta."</p><p><br /></p><p>Har tala ta dauki glass cup da nufin ta zubawa Rukaiyya lemun five alive ...tayi saurin dakatar daita tare da fadin kibarsa kurum idan nayi ra'ayi zan sha."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Abun ya kara kular da Asmy kenan ita wacece da zata shigo har gidan su A dakin barcin ta tana mata wannan gadarar ,malalacin murmushi ta saki Ok. Tala barta kurum da haka tala tasa kai ta fice....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Mae da hankali Rukaiyya tayi kan wyarta cike da jin kai da,isa.</p><p><br /></p><p>Sa'anan ta bude baki da kyar ta jefowa Asmy tambaya."</p><p><br /></p><p>"Dama kece keson Kashe yayana!!</p><p><br /></p><p>" Da dam ! Gaban Asmy ya buga jin tambayr wata iri.</p><p><br /></p><p>"Cikin dakewar zuciya take fadin ban fahimci zancenki ba." Kawata.</p><p><br /></p><p>Nasan kinsan menake nufi ??" Ban fahimta ba gaskiyya Idan nasan da zancen "y not na fito na fada maki tunda ba tsoronki nakeji ba......Duk da na fahimce cewa kedin kina ji da kanki kmr yarda nima nakeji da kaena ...kinga kuwa angamu a dace....Asmy ta karasa zancen Gamida kashe ma Rak! Ido daya ,iyakar kuluwa Rukaiyya ta kulu lallai wannan yarinyr cikakkar ya'r barki CE.!!</p><p><br /></p><p>" Gaskiyar Nura Dan ga alamomi nan sun nuna.".</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Girgiza kai Rukaiyya tayi cike da takaici ,Amma shi wandda kikasa a wani halin yafi karfin yyi maki karya Dan baki San waye shiba.??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tabe baki Asmy tayi cike da kosawa da zance waye shi kuwa in banda makaryaci dan nasan karya yyi maku."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin ku'luwa Rukaiyya ta mika mata wyar wannan ne zakice baki San saba.??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dan waro ido Asmy tayi ganin pic dinsa acikin gallery din Rukaiyya,A hnkali kuma ta furta " MUMIN."</p><p><br /></p><p>Ko kadan Rukaiyya bata fahimce taba."ganin yarda ta zuba ma wyar ido ta fahimci tabbas tasan sa ,mika mata wyar tayi cikin hade rae take fadin nikam bbu wata alaka tsakanina da wannan guy din."</p><p><br /></p><p>"Meya fada maki ne??" Asmy tayi mganar shaye da toka....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wani kallon Raini Rukaiyya tayi ganin take Asmy tagama Raena mata hnkali ta koina...Anan ta Ciro farar takarda da bairo ta danyi guntun note !!</p><p><br /></p><p>" Da harshen Turanci Ta aza mata akan cinyar ta ta Dan kalleta ni xan tafi babe Anytime Idan kina da Sha'awar kirana .."ga digits nan Zube ajikin takardar ,da haka tasa kai ta fice cike da mmki Asmy tabita da kallo har tabar dakin jin tayi Ranta ya baci."</p><p><br /></p><p>"Kallonta ta maiyar jikin takardar..."</p><p><br /></p><p>Idan har kinsan "HA'KKIN SO...zaki iya ziyartar yayana! Dan yana cikin matsanaciayr damuwa sabida Rashinki idan kinyi Sha'awa ga Digits nawa nan da kuma full Address na gidan mu." Duk cikin harshen turanci tayi maganar jujjuya takardar ta somayi haka tana nazarin maganganun Rukaiyya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Zaga dakin nata ta farayi ta saka wannan ta kwance waccen ,murmushi mai kyau ta saki Dan ta nemarwa kanta solution ..wata zuciyar take fadin toke Asma'u yana da kudin da zaki tunkaresa da wannan zancen??</p><p><br /></p><p>" Idan ba Rich man bane fa??" Tadan tabe baki Any way's ta Dan taga kafada Zata kawoma daddy Wanda takeso A yau badan wae Dan tana son Mumin bane ."ita kawae tasan abunda take sakawa da warwara a zuciyarta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>******</p><p><br /></p><p>Aunty plzzz kidan bani Aron wyar ki zan kira Yah hameed bbu musu Aunty ta mika mata wyar Anan ta shiga Neman layin yayan nata har ya tsinke bai dagaba." Karo na biyu ta kara danna masa call. Gabda xata tsinke yyi nasarar dagawa cikin magagin barci ,ya daga wyar." </p><p><br /></p><p>Yaya na! Jin muryarta yasa yyi saurin dirowa daga kan gado bbu shiri...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ya dae Asmy na!!</p><p>Ina son muyi mgana kana ina gani a dakina ."lpia ? Kawae ina son mufita akwae inda xamu tafi .olryt bari nayi wnka nayi break fast Allah yasa tafian alkhairi CE ??</p><p><br /></p><p>Cike da shagwaba gamida Dan turo baki plzzz,nidae kayi sauri sae ka fadawa Mama tare zamu fita kasan yau za'a saka su Aunty shema lallae kuma wae hardani Dan haka ba inda xan fita ni dae ka tayani shawo kanta." Karki damu jekiyi wanka ki shirya Dan ihu ta saki gamida yima yayan nata godia."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ajema Aunty wyar tayi Dan bata ma dakin lokacin ta fice...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kai tsaye dakinta ta koma ,ta cire kayan jikinta ta nufi toilet gamida sakarma kanta shower..........</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu...</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>38</p><p><br /></p><p>"Yah hameed tsaya anan!</p><p>Bbu musu yyi parking ina tunanin nan ne kofar gidansu.</p><p><br /></p><p>" cikin zolaya yake fadin kina ma tunani kenan??" Gidan su mijin da zaki Aura bakima sani ba."kae Asmy anya aljannu basu shafar manke ba??..</p><p><br /></p><p>"Cike da shagwaba da toro baki ta ba'lle marfin motar ,shima ya fito yana mata daria ki Dan saki fuskar mata qanwata!</p><p><br /></p><p>Karki bata kwaliyyarki kinga yarda kikayi wani irin kyau."</p><p><br /></p><p>"Kayataccen murmushi ta saki tana kara kallon kanta ta ,glasses din motar ba abinda tafi qauna irin a fada mata tana da kyau."</p><p><br /></p><p> Kanta ta shiga karema kallo tana cikin shigar,doguwar Abaya Golding sae kwaliyyar da akayiwa gaban rigar da wasu irin duwatsu masu qal'qalin gaske black &white sae Dan karamin veil wandda tayi Rolling din kanta dashi baki.</p><p><br /></p><p>"Haka akwae powder a fuskarta da kuma jan janbaki sae sae silver black" handbag "nata da kuma talkamin kafar ta waya'nda suka kasance plat shoe.</p><p><br /></p><p>Suma silver black sae agogonta na mata mai tambarin zyros,Golding " sae uban kamshi take zubawa tabbas tasan bbu wani namijin da xai kalleta batare da ya kara kallaba ,wani irin smilling ta saki Wanda ita kawae tasan meaning nasa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Anan ta karbi wyar yayan nata ta shiga zuba digit's din Rukaiyya kusan kira 3 tana mata bata daga wyar ba haka taji ranta ya baci, Hameed ya kalleta lpia ??"</p><p><br /></p><p>"A kufule tace taki ta daga wyar kanwar nan tasa tana jin kanta </p><p> Dama na fada mka ta fada A zuciya gamida ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> " Mika masa wyar cike da shagwaba ni muma juya zuwa gida na fasa.".</p><p><br /></p><p>Yarda tayi mganar ta baiwa yayan nata daria sosae ,hkuri zakiyi Asma'u plzzz,dan kara gwada kiran make kafada tayi sae dae kai ko zaka gwada."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Taja da baya gamida harde hannayenta a kirjinta ta wani bata rae "daria hameed ya tuntsere daita gamida rike ciki abunda ya kular daita kenan."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A hnkali ya tsagaita dariar gamida karasowa gurinta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kinga bamuda cikakken tym.Ma'u na ya kamata a aje jiji da kan nan na dan wani ,lokaci bata kulasa ba asalima dauke kanta tayi ba yarda ya iya Hameed ya kara gwada layin Rukaiyya sae akayi sa'a ta dauka jin muryarta yyi saurin mika mata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ohkey Ku jirani gani nan fitowa tana fadin hka ta datse wyar."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Shi kadae ne a falo da almr wya yakeyi bata kulasa ba tayi hnyar fita daga falon ,lokaci daya yabita da kallo...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cike da Fara'a Rukaiyya ta tarbesu har tana tsokanar Asmy " kinyi sa'a kuwa yayan namu na gida itadae Asmy murmushi kurum,tayi anan kuma Hameed ya saka maigadi ya dinga shigo da kayan jinya." Wandda dae ake zuwa duba marar lpia.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hka Rukaiyya tamasa jagora zuwa babban falon gida karo na farko da Asmy taji zuciyrta ta tsinke.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dae-dae kuma AJ ya gama wyar gamida mikewa tsaye ganinta sae da zuciyrsa ta harba zuba mata ido yyi har lokacin da yah hameed ya karaso cikin falon ya mikawa AJ." Hnnunsa suka ,gaisa duk da ko ya lura gaba dae hnkalin sa na wurin qanwar tasa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Lokaci daya ya Rude da kyar ya tattara natsuwarsa gamida baiwa Hameed din hnnu sukayi musabaha ,sa'annan suka nemi wuri suka zauna Rukaiyya ta nufi cikin dan kiran su hajja kallo daya AJ.yyima Hameed yaga tsantsar kamar da sukeyi da " Drama Queen dinsa ko ba "A fada masa ba yasan jininta ne.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Anan yah hameed ya masa ya jiki ya amsa da sauqi cike da jin nauyinsa itakam gimbiyr ko uffan batace ba." Dae dae kuma lokacin hajja ta iso falon Aunty salma kuma tafita da mijinta cike da girmawa Hameed da Asmy suka xube kasa suna kwasar gaisuwa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cike da Fara'a hajja ta amsa duk da bata shai dasu ba ,Amma har ga Allah taji tana kaunar yaran suna da tarbiyr duk da bata tababa ,akan tarbiyr kanawa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hajja budurwar Yah AJ ce tazo dubiya da kuma yayan ta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A tsorace Asmy ta dago kanta caraf idonta cikin na AJ ..shima duk da ya razana da kalaman Rak! Amma sae taga yyi mata kwarjini sosae saurin dauke idonta tayi akansa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cike da Fara'a hajja ke tambayr Asmy yaya sunan Jikar tawa??" Cikin sanyin murya Asmy ke fadin Asma'u!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ayya kice kedin takwarata CE ?? Hajja tarasa inda zata saka Asmy dan farin ciki itakam lokaci daya taji tana qaunar yarinyar.</p><p><br /></p><p>" Anan AJ yaja yah hameed zuwa falon baki dan shikam tambayoyi ne fa'l aransa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Anan kuma yah hameed ya dinga walwale masa komae ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Na yaba da hnkalinka Abdul jabbar !</p><p> Nasan zaka rike min kanwata da amana."</p><p><br /></p><p>"Karka damu da duk wani shirme nata ,dan munyi mgana ta fada min bata sonka! Amma idan zaka yarda zakuyi (CONTRACT MARRINGE)’'</p><p><br /></p><p>Na shekara daya ,haka take fadamin kaidae wuyar ta taxo hnnun ka na rokike ko Mae tace kace Mata Ehhhh." Dan har yau kurciya kedamun kanwar tawa bara na turo maka ita ya kamata yau kaje kaga Daddy."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kafin nan ka fara shawara da iyayenka ,shikam baki wangalau AJ.ya saki yana kallon ya Hameed murmushi ,Hameed yyi gamida Dan girgixa kafadar AJ ."karka damu naga soyayyar kanwata "A idanunka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Anan Hameed yasa kai ya fice daga dakin yyinda AJ .ya dinga juya maganganun sa A ransa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*********</p><p><br /></p><p>Sun kusa minti biyr zaune su biyu bbu wandda ke mgana a tsakanin su ,sae can ya fara mgana cikin hadddiyr muryarsa."</p><p><br /></p><p>"Ashe dama kinsan soyayyr ki na wahalar dani drama Queen!!</p><p><br /></p><p>Yyi mganar gamida zuba mata sleeping eyes ,nasa bata iya jure kallon cikinsu sae tayi saurin kawar da kanta ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sae kuma kayi Rashin sa'a ni bana sonka!!</p><p><br /></p><p>Mganar yaji har a zuciyrsa haka tataba sa sae dae yyi saurin basar wa Ae nasani bakya sona "Amma da zaki bani dama " da zan koya maki yarda zaki soni."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A zubure ta dago ta kallesa ta hararesa ,karkama sa ran Akwae "Wata Rana !! Da zan soka nima ynxu taimakonka naxo nayi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana mganar cikin dakewar Zuciya." Shikam murmushi ya shigayi hka yana jin wani irin farin ciki aransa ,yana son life style nata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ganinsa tayi agaban ta ya zube gwiwowin sa kasa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka baisa ta kallesa ba dan zuciyarta harbawa takeyi da sauri da sauri... ’' Dago idonki ki kalleni my drama Queen!!</p><p><br /></p><p>Yyi mganar cikin kasalalliyr muryarsa itakam muryar guy din nan na tafia da imaninta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dagowa tayi tana kallon cikin idonsa Amma sae dae meye?? Baxata iya jurewa ba tayi saurin dauke kanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wani irin smiling yyi Kin amince ina sonki??" Ko har ynxu baki yarda ba??...</p><p><br /></p><p>Shaye da Toka take kallonsa ni ka aje xancen so A gefe plzzz,,bana son jin Kalmar."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Na amince Zan aureka Amma abisa sharadi!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ya Riga da yasan kwanan zancen sae yyi mata murmushi " ina jinki Husna!!</p><p><br /></p><p>A tsorace ta daga kai tana kallon sa tasan duk dunia mutum daya ne keyi mata wannan sunan,Daddy sae kuma gaya ynxu mumin ya kirata dashi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kawar da kanta tayi duk da zuciyrta na tsananin halbawa ,da abun da xata fada Amma batasan ya xai dauki zancen ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Zan Aureka!</p><p>" Amma contract marriage.... Amma ban saniba ko kana da kudin da zan iya baka sharadi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta fada tana kallon sa A tsorace sae taga idonsa ka'r akanta ,,fada ina jinki......</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana mmkin karfin hali irin nasa murmushin mugunta ta saki "zamuyi auren shekara daya dakai " Amma fa bbu wani Abu da xai shiga tsakanin mu dakae na Auratayya ." </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana son su hada ido dashi takasa ,dan itama taji kunyar mganar.</p><p><br /></p><p>Sa'annan kuma zaka sani skull ina son karatu amma daddy ya datsemin lokacin da nake cikin son nayi karatun.</p><p><br /></p><p>Zaka sayamin mota !</p><p><br /></p><p>Wannan shine kurum idan kayimin wannan xan aureka Amma fa bayan shekara ,daya zaka sakeni!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Lallai ya tabbata mahaukaciyr kurciya ke damunta."To nikuma ya kikeso da Soyayyar ki??</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Ae A hnkali xakaji ka daina sona ne."musamman idan mukayi auren shekara daya da kai.</p><p><br /></p><p>Tom.naji my Queen idn muka cika shekara daya na sakeki waxae cigaba da biya maki kudin skull?"</p><p><br /></p><p>Idan kuma takaasan CE. Bana da kudin siya maki mota da na shiga skull fa??...</p><p><br /></p><p>"Nan take kuma Asmy hnkalinta ya tashi yaga alamr rudewa tattare daita ,na tabbata kana Aiki A wata nawa kk amsa salarin ka??" Lokaci daya ta jefo masa tambayoyin..........</p><p>WATA RANA !</p><p>By~Asmy b Aliyu[posted on 2 August "2017]</p><p><br /></p><p>39</p><p><br /></p><p>" zuba ma kyawawan labbanta ido yyi yarda ta jero masa tambayr lokaci daya.</p><p><br /></p><p>"Murmyshin sa mai kyau ya saki wandda sae da dimple dinsa suka lotsa samun kanta tayi dasa yatsan ta a wurin bai hnata ba sae ma ido da ya zuba mata " yana jin sonta ta koina na huda duk sansan jikinsa."</p><p><br /></p><p>"Ko Mae ta tuna sae tayi saurin janye yatsan ta wurin A tsorace cikin zare ido."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hka lokaci daya ta dauke kanta cikin sarkewar murya ta shiga fadin ,baka amsa min tambaya na ba.??"</p><p><br /></p><p>Yanayin yarda tayi mganar ta wani hade rae sai abun yabasa daria.</p><p><br /></p><p>Niba Dan boko bane !</p><p>Hasalima bana aiki "amma karki damu ko dakone xan iyayi indae xan faran ta maki rae ya fada yana kallon yanayinta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mai makon tayi mgana sae yaga ta Mike tsaye jiki a sabule hka ta fara tattaki har takai bakin kofar fita daga falon ,kenan baka da kudin da zaka sayamin mota??"</p><p><br /></p><p>Baka da kudin da zaka sakani skull??"...nikam na hkura baxan aure kaba!!</p><p><br /></p><p>Bata waiwayesa ba ta fice falon da gudu lokaci daya yabita da ido ,cike da kissima abubuwa da yawa akanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*******</p><p>Sosae hajja ta nuna murnarta akan Al'amari hkama Aunty salma,itakam Rukaiyya gefe ta koma ta zama ya'r kallo."</p><p><br /></p><p>Tana kwance A dakin Aunty salma ya shigo da sallamr sa hnkalinta na kan chart din da takeyi Ta amsa batareda ta kallesa ba ,Dan tun ranar da yyi mata tsawa a hospital ta fita sabgarsa ."</p><p><br /></p><p>Yasan laifinsa sae ya xauna bakin gado cikin zolaya yake fadin wae nikam menayiwa dear Rak ! Dina ne??"</p><p><br /></p><p>Ka'mshin turarensa ya fitine ta Mike zaune tana kallonsa yana cikin farar shadda ta kaftani ya kafa hula ,wadda ta da'ce sa samfarin shaddar kallo daya zakayi masa kasan yana cikin farin ciki." Shima kafeta da idonsa yyi masu gigitata ."</p><p><br /></p><p>"Rakkiya nazo ayimin ko zan samu??...Kawae ka tafiyan ka bana jin zan iya yin rakkiyr ta fada idonta taf da kwallah." Zuciyar sa yaji bbu ddi "Am sorry da abunda ya faru Asibiti nasan shine a mind dinki." Duk da bansan Rak !dina xata iya yin fushi dani har haka ba.</p><p><br /></p><p>"Am sowiee nayi làipi ina Neman Afuwa mgana na karshe nagode da gudummuwar da kk bada ,acikin soyayyata yana fadin haka yasa kai ya fice daga dakin ko bata fada ba ,tasan gidan su Asmy ya nufa " Hawayen bakin ciki suka zubo a idonta itakam tashiga ukku wannan wace irin wahalalliyr soyayya ce take yima yayan nata??" Tana fama da tsananin sonsa baima San tana yiba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>**********</p><p>"A can gidan su Asmy da misalin karfe Tara da Rabi na dare daddy ne ke tattaunawa da AJ .da kuma Abokinsa Nura sosae daddy ya yaba da hnkalin yaron haka ma sun gaisa da mama da Aunty itama mama tayi murna tabbas Addu'arta ta ka'rbu gun ubangiji irin mijin da take mafarkin ya'rtata ta aura kenan ,Daddy ya amince Akan gobe ya turo iyayensa da biki sauran kwana hudu karya damu kansa da wani lefe " tunda lokaci ya ku're cike da ladabi AJ ."ya russuna yana fadin A'ah daddy baza ayi haka ba ha'kkina ne nayi mata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dan haka karka damu ko zuwa jibi za'a kawo mata lefenta anan daddy ya shiga samasa Albarka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana can kudundume kan gadon mama wani zazzabi taji ya rufeta lokaci daya" Tunda suka baro gidan su mumin taji ta sare. " ko saka lallae da kyar da sidin goshi ta yarda aka saka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mama CE ta sameta a dakin kitashi ga ba'kin ki can A falon ba'ki cikin sanyin muryarta tamarasa lpia take fadin mama bana jin ddi ne!</p><p><br /></p><p>" Haka dae zaki lallaba ki tafi hijab ta nema ta saka da kyar ta nufi dakin bakin kamshin turaren da tafara shaka ne ya tabbatar mata da ko waye??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin siririyr murya tayi sallama" zuba mata ido yyi gabadae yaga yanayin ta ya canja gabansa ,yaji ya fadi Can nesa dasu ta zauna nura ya kalleta A Dan kaikace "Amaryar mu sannu da fitowa.."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Banza tayi masa shima nura yasan bazata amsa saba."tsam ya mike tsaye gamida kallon AJ.Wanda hnkalinsa gaba dae yana gurinta "A kufule yake fadin idan ka gama ka sameni A waje,bai jira amsar saba A fusace yabar masu falon."...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Ajiyar zuciya ya sauke husna meyasa kikeyin haka??" Ko kadan ba girman ki bane ya kamata ki manta baya ki tari gaba ,ko banza yanxu nura Abokina ne kamata yyi ki dinga basa girmansa gaya kuma yana matsayin malaminki."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Daga ido tayi tana kallonsa bazai gama laifin abokin nasa ba ,dake yimata kallon kashi sae itace zaya ga laifinta " shin meye nata aciki??........</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Samun kanta tayi da fadin kayi hkuri na daina haka idonta sunyi rau-rau ,murmushi mai kyau yyi mata "Da alamr baxai wahala wurin shawo kanta ba."</p><p><br /></p><p>Ya karaso wurinta Ya mika mata ledojin hnnunsa ,da mmki take kallonsa "meye aciki yana kallonta yake fadin duba ki gani chaculates ta fara cin karo dasu tsadaddin gaske" da kuma phones masu tsadar gaske har kwa'ya biyu."</p><p><br /></p><p>Iphone6 ta gani da Note5 ,baki wangalau ta saki tana kallonsa ina yasamu kudin siyan way'annan manyan wayoyi haka??" Shida yace bayada kudi ,ya katse mata zance. Zucin da takeyi ta hanyr fadin Yaushe zaku fara Events??"</p><p><br /></p><p>"Gobe ne!</p><p>Mexa kuyi goben??"</p><p><br /></p><p>"Kamu .kina so naxo ne??...samun kanta tayi da daga masa kae ,baxan samu damar shigowa gobe ba,husna xanyi tafia kinsan ni ba Dan nan bane."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zan dae wakilta abokina nura kafin na dawo ,da sauri ta katse sa idan bazaka samu damar xuwa ba shikenan bbu damuwa yarda tayi mganar ya basa daria matuka ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kibani Account number naki nasan zaki bukaci kudi, zan turo maka ."A hnkali take fadin nagode itakam binsa takeyi da ido tamkar ba mumin ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sun Dan taba hira daga bisanin yyi mata sallama ,gamida cika kannenta Da kudi "da kuma su Aunty shema haka ya tafi yana kara jadadda mata ta buda wayoyin akwae chargi aciki da sim card."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zai kuma kirata idan ya isa gida jiki sabule ta dawo daga rakkiyarsa hka ta isko su Aunty zulfa na jujjuya wayoyin kai ma'u ina kika samu wannan Rich man din haka??....</p><p><br /></p><p>Ita kam jinsu kurum takeyi afra ce ta shigo da gudu Aunty Asma'u wae kije inji daddy sae da zuciyrta ta kusan tsinkewa itakam ynxu tana tsoron kiran daddy "a sabule Ta nufi side din daddy tankar kazar da kwai ya fashema wa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Lokaci daya taji jikinta yyi sanyi.."[Truncated by WhatsApp "..]</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_"Mmn Haneef "(naja'atu bello Gusau)" where are yhu?? Your page is here my sweetest "Angel yaushe kk zama ya'r Gatan haske Writer's haka? Duk inda na juya acikin haske sae yabonki sukeyi....Kungiyr haske sunga sakonki sun gode Allah ,yabar so da kauna Dan haka wannan kyautar page naki ne ke kadae " We Luv yhu to sae dae muce Allah yabar zumunci_"</p><p><br /></p><p>40</p><p><br /></p><p>Batayi mmkin jin yarda mahaifin nata kemata Nasiha ba,itakam takasa fahimtr komae "Yah hameed nason mumin hkama daddy mama,tom wae me hakan ke nufi??" Tambayr da takeyiwa kanta kenan har ta baro gurin dady.</p><p><br /></p><p>*****</p><p>"Kwan'ce take a katafaren gadon ta sae juyi take ,A hnkali bbu almr jin barci." a idanunta."</p><p><br /></p><p>"Daga kai tayi ta kalli agogon dake manne A bangon dakin Sha biyu dae -dae na dare,dae dae -kuma lokacin." Taji baburet din wyar ta "zu'bur ta mike daga kwa'ciyr da tayi ....tana mmkin inda take jiyo karar wyar ,cikin sanyin jiki tayi nasarar ku'nna fitilar da'kin haske ya bayyana."</p><p><br /></p><p>"A can kan mirror dressing ta hangi wyar sae ynxu ma ta tuna da wayoyin.''</p><p><br /></p><p>" ko ba'a fada mata ba tasan mai kiran ,da sassarfa ta isa ta dauki wyr "sae dae ta tsinke " k'urama sunan ido tayi ,haka ta shiga maimata sunan "A ranta " *Husband Luv*...hka ta gani a rubuce samun kanta tayi da hararar sunan ,Kiran ya sake shigowa a hnkali ta zauna kan bed din gamida daga wyar."</p><p><br /></p><p>"Assallamu Alaikum ! ." sallama irin ta ."Addinin musulunci,ga masoyiyata Wanda zan aura nan bada da dewaba."</p><p><br /></p><p>"Muryar taji har cikin ranta Amsa sallamar tayi a ataikace ."</p><p><br /></p><p>"Waye masoyiyr taka??"</p><p>Nifa na fada maka.’' gaskiyya mumin I'am not in Luv with yhu!!</p><p><br /></p><p>"Ina ga Auren da zamuyi bawae na soyayya bane ,Kaima kana son na taimaka maka ne " Duk da har yau banji taimakon kaba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Plzzz na rokeka idan muna mgana kadaina sanya " *SO* "Aciki sabida I don't want to hear All of dis " Any more....yarda take mganr yasan cikin fushi takeyin ta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ajiyar heart ya sauke " cool down ."my drama queen duk meyayi zafi haka kuma ??" Daga magana !!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hawaye taji sun wanke mata fuska ita kanta bata da wani dalili da zata iya basa akan kin da takeyi masa " A matsayinsa na mai qaunarta, haka kurum ta tsinci kanta cikin Rashin son Sa." Haka kuma baya wuce nasaba da ya'rda EM."ya nuna mata halinsu na maza."</p><p><br /></p><p>"Husna!!</p><p>" Ya fada cikin sarkewar murya ."tana jinsa takasa amsa sa ka'rshema kashe wayr tayi duka."</p><p><br /></p><p>"Fa'dawa tayi akan bed gamida saka kuka mai tsuma rae."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Washe gari...cikin barci taji ana buga mata kofa tamkr za'a karyata jiki sa bule ta diro daga kan bed" jikin kofar ta nufa tana tambayr waye ne?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Muryar Rahama taji tamakr A mafarki jiki sabule ta bude ko'far kallo daya Rahama tayi mata ta dauke kae " kan soofa Rahama ta zauna."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ynxu kika tashi kenan??" Cewar Rahaama "shigowarki CE ta tasheni ."</p><p><br /></p><p>Ayya sowiee na takuraki da yawa ."</p><p><br /></p><p>"Smiling Asmy ta saki mai burgewa ,karma ko kinsan barcin bai isheni ba."</p><p><br /></p><p>Meyasa yau baki fita skull ba??" Kin manta ana bikin babban yaya ! Bancin haka kuma kinsan farkon "Semester ne.</p><p><br /></p><p>Hakane kuma so yah akayi ne??"</p><p><br /></p><p>Nan take Rahama ta hade fuska ,A tunanina Asma'u kawancen mu ya wuce haka bai kamata ba."Dan kinki yah Al'ameen nima ki kaurace min ba,wae sae jia nakeji mijin da zaki aura sun xo gaisuwa gurin daddy."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nan take Asmy ta rikice itakam kunyar Rahama takeji ,sae take ganin idan ta fada mata kamr cin fuskane ,tayi mata ." Ajiyar zuciya ta sauke kiyi hkuri My Rahama abun ne yazo bbu shiri,naso na sanar dake ."naga kina fushi dani ko kiranki nayi da wayr mama idan kikaji muryarta sae ki kashe." Kinfi kowa sanin matsalata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ta kama kunnenta duka biyu idan nayi laipi ki yafemin Aminiyata ..." Yarda tayi yaba Rahama daria ,naji na hkura nima nasan bazan iya fushi dake ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ynxu sae ki tashi kiyi wanka ga mai lalle nan ta iso."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Harta gama dasu Aunty zulfa ke ya'r mulki kina nan kina barci."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kwa'lalo ido waje Asmy tayi duk yaushe haka ya faru?"...A tohhhh." Ina zaki sani ya'r mulki kina can kina mafarkin "Prince charming dinki.daria Asmy tayi gamida shigewa bathroom.</p><p><br /></p><p>" *KAMU DAY"...*</p><p><br /></p><p>6:15pm.na yamma Amare ne na hango tsakiyyar ha'll cikin shigar Alfarma sun hade ,cikin weeding gown tasu ta "Amare Red sae silver head da suka saka akansu " sunyi kyau na ban mmki Angwaye ma ,Anko ne wato Faisal da Al'ameen cikin shigar wani Ash colour materia na maza yaji dinki ya'r ciki da babbr,Riga."</p><p><br /></p><p>"A wurin AJ kurum ne bayanan Amma ya wakilta Nura " wandda ya dinga yima Amarya Asmy watsen daloli da sauran ya'n uwanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka aka gama taro lpia aka watse."</p><p><br /></p><p>"Ban garen AJ .kuwa booking din flight sukayi shida Aunty sadiya zuwa " Dubai hado kayan lefen Asmy "tun ranar da sukayi wya bai kara Neman ta ba."</p><p><br /></p><p>"Amma Nura ya turo masa pics din Amryar tasa ,tayi kyau sosae hakama Aunty salma." Taje kamu ."itada yaranta sae dae bata ga Rukaiyya ba." Tasha mmkin Rashin zuwanta...</p><p><br /></p><p>"Ranar kuma AJ." Ya turo wakilansa Aka yanka masa sadaki dubu da'ri kamar yarda aka ya'nka na ya'n uwanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ranar Jumu'a akayi Arabian night ...aranar kuma aka kawo lefen Asmy " lefen da ya girgixata ,haka ya zama abun mgana cikin dangin "wandda kowa ya dinga fadin Albarkacin bakinsa." </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A can na hango ya'n group din Asmy b Aliyu suna duba lefen suna sabbatunsa." Irinsu Tawakkaltu Dr.zee jameela Jegawa "Surry Bauchi." Acan gefe na hango kawalli Munay rike da jakkar gwala-gwalai lolzzz lefe kan sae Wanda yagani Mr.AJ." ya nuna ma dunia Kaunace......lolz😋</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ranar Assabar kuma aka Daura auren "Shema'u Omar omra da Faisal Zulfa'u umar Omar da Al'ameen sae ,kuma takwara " Asma'u Omar omra da Abdul jabbar meera."daurin Auren da manya-manyan ya'n kasuwan gwamnati kosasshin ya'n siyasa suka ziyarta."</p><p><br /></p><p>Sae dae muce Allah yaba su zaman lpia."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sosae iyayen nasu ke masu Nasiha " inbada kuka bbu abinda sukeyi"..</p><p><br /></p><p>Misalin karfe 8:00pm.na dare Alh.omra ne ya shigo falon gidan yana ,"kwa'lama mama kira ."</p><p><br /></p><p>"Daddy lpia??"</p><p>Wae me ake jira da baza'a bawa kowace mijinta ya wuce daita ba??" Mama ta sassauta murya ina jin ko dener zasu tafi haka Hameed ya fada daga can sae kowace tayi gidan ta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mganar banza !</p><p>Kenan..." Inaa hameed din ya shiga ne.. ??"</p><p>Dae -dae nan hameed ya bayyana cikin bakaken suit ."Wanda sukayi balain karbarsa ,kafin yyi mgana yah Anas yah Aliyu suka karaso suma kusan shigarsu iri daya ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yah Anas yake fadin ka gafarce mu daddy." Mun nemi izinin yin haka a wajen mazajen sune ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yah Anas yah kalli Hameed jeka kace masu su fito ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" shema CE."A motar yah Anas itada Faisal a baya ."sae shi dake" A gaban motar yana jansu..</p><p><br /></p><p>Sae Aliyu da ya dauki zulfa da Al'ameen ...</p><p><br /></p><p>"Sae kuma Mr.Hameed omra Wanda ya dauki Asmy da AJ. Acikin sabuwar BMW M4 dinshi..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Angwa'ye ne ciki shigar wani bakin le'ss na maza mai tsadar gaske ,Wanda kudinsa zasu kai kimanin dubu Dari biyu da hamsin."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yyinda A mare suka hade cikin Wata irin wedding gown peach colour,Head dinsu da jakar hnnu hill's shoe duka Dark blue ne."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A haka suka dauki hanyr zuwa dener a kunne ya shiga rada mata." My drama Queen kinfi jia kyau !</p><p>"Dago kanta tayi ta zuba masa Golding,eyes dinta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sae taga yyi mata kyau fiye da kullum" haka kuma ta kasa dauke idonta akansa ,shima din ita yake kallo ." komae ta tuno sae kuma tayi saurin dauke kanta."</p><p><br /></p><p>Ta wani bata rae."lokaci daya ,duk yarda yaso su kara hada ido fi'r taki...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Note!</p><p>Plzzz my Real fan's "A saka Ummy Aysha cikin Addu'a tana rubuta Exam" ubangiji Rabbi ya basu ,sa'a "Wato marubuciyar.... *MIJINA SIRRINA!*🌹</p><p>WATA RANA!</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>41</p><p><br /></p><p>"Alhmdullhi dener ta ka'yatar anci Ansha Anyi rawa.karfe goma sha daya na dare." Kowane Ango ya dauki "Amaryarsa zuwa gidan sa.</p><p><br /></p><p>"Shema ce." A NNDC Quaters."</p><p><br /></p><p>Sae zulfa da take sultan Road."duk da ba'a kano zasu zauna ba." Mijin nata sokoto yake aiki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sae mrs.Meera da suke xaune."A lamido crecet."wandda kowane tym."zasu iya barin kano zuwa bauchi..."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Gaba dae gidajen su ba na rainawa aciki ." bata lokaci ne tsayawa tsara gidajen nasu." Sae dae kawae kuxo kallo Readers "idan kunyu Ra'ayin hakan."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Zuba ma " Mansion din da take ciki ido tayi haka tana jin qaunar mahaifanta."batasan da mexata saka masu ba qaunar da suka nuna A gareta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Gidanta Falo ukku ne aciki."..</p><p><br /></p><p>Sae 2 bedroom... Falon ta na farko kujurun sa dark blue ne haka ma fentin falon komae na falon dae blue.</p><p><br /></p><p>" sae na biyu Wanda ya kasance White &black na ukkun kuma Red ne hakama " dakunan barcinta.</p><p><br /></p><p>"Dakin barcinsa.komae black &white ne yyinda nata ya kasance blue & Red." Sae kiching da store ."A gefe.a takaice dae bbu abunda bbu na more ...rayuwa aciki Bangaren swimming pool daban ."hakama guarding...</p><p><br /></p><p>"Itakam gaba dae kudin AJ." Sun gama gigitata shine ranr yake "fada mata Baya aiki ...dole tasan Aikin da yake , wata zuciyr take fada mata hkn."</p><p><br /></p><p>"Karfe sha biyu da rabi na dare ya turo kofar dakin nata ,Dauke da madaidaicin Tire a hnnunta ." yaja center table ya Daura akai."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tana sanye cikin Riga da wando na barci ,masu kauri kalan sararin samaniya "... "Dan yau taji garin na Kano akawe sanyi ga hadari ya hadu wandda ya sakarda sanyi gaske." amma bbu alamr ruwa ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kallo yabita dashi itama din haka yana sanye cikin milk jallabiya mai ya'nkken hnnu.." Wadda ana hango gashin ki'rjinsa wandda yake kwance lu'f baki...gwanin Sha'awa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Gefen Gado ya zauna Ga abinci nan nasan zaki bukaci hakan ." sae kuma mekike so??" Kanta ta sunne a kasa ,tareda wasa da yatsun hnnunta ."yana son macce mai kunya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin siririyr muryrta ta." Take fadin bana bukatar komae."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A hnkali ta dago ta zuba masa ido ." murya can ciki." take fadin .MUMIN!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Sae da yaji tsikar jikinsa ta tashi wani irin yar yaji."...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kyawawan idanunsa ya zuba mata ,A Dan shagwabe take fadin Shine ranar kake fadin baka Aiki to duk ,waye yabaka kudin wannan hidimr.??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yarda tayi mganar tabasa daria sae dae baiyi daria ba ... smiling yyi bita dashi yana mata kallon So. " A banki na aro idan na fara aiki zan biyasu .."</p><p><br /></p><p><br /></p><p> "Zaro ido tayi gamida dafe kirjinta." Har yaushe xaka samu aiki?" har ka biyasu.." Wata rana ! Insha allahu .."Addu'arki kurum." Nake bukata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ko bazaki min ba.??" Mexai hana zan maka mana.</p><p><br /></p><p>Anan yyi serving dinta."ya fara ciyar daita gasashiyr kazar da Ya Anas ya siyama kowane "Ango ....yana bata yana kallon yanayin bakinta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kai bazaka ci bane?"</p><p><br /></p><p>"Da'ga kai yyi Alamr ehhhh.." Meyasa ??" Ta tambayesa ka'ro na biyu ...har aransa yaji ddin yarda take kula dashi haka."</p><p><br /></p><p>"Bana jin yinwa Queen.!!</p><p>Yyi mganar ,tamkar karamin yaro hakan yasa ta kya'lkyale da daria baki wangalau ya saki yana kallonta ." baeyi aune ba yaji hnnunta kan cikinsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kai mumin karya fa haram."ga cikin ka nan tamakr baka saka masa komae."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Runtse idonsa yyi A hnkali yana jin hnnunta acikinsa."...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Baiyi Aune ba yaji kazar a bakin sa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bude idonsa yyi A hnkali yana kallonta Dan har ya fara jin sa cikin wani ,yanayi." Itama ta lura da sauyawar da yyi .."baka da lpiane??" Tayi maganr cikin nuna kulawa A garesa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mikewa yyi tsaye. Queen zanje na kwanta kema da kin gama kiyi ,Addu'a kafin ki kwanta." Ya Dan russuna ya subabbaci goshinta."</p><p><br /></p><p>"Gud nyt!</p><p> " da sassarfa yabar dakin binsa tayi da kallo ,itama jin tayi kazar ta isheta ."Dan haka ta ture plate din gefe tareda ." tsiyaya fresh milk A glass cup tasha.."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mikewa tayi toilet ta nufa brush tayi gamida dauro ..Alwala shafa,i da wutri tayi sa'annan tayi nafila raka'a biyu sae kusan 1 ta kwanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A bangaren AJ. A daddafe yakai bedroom dinsa zubewa yyi A gado yana maida numfashi "... Dan yasan koxai mutu." Drama Queen." baza ta basa abunda yakeso ba."a haka xai ta lalabata kurum." Tunda ya lura tana da saurin sabo da mutane."</p><p><br /></p><p>"Shima nafilolin sa ya gabatar ,gamida bin lpiar gado."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*MA'U* ...</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu...</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.....</p><p><br /></p><p>42</p><p><br /></p><p>Washe gari.....</p><p><br /></p><p>"Karfe biyu na Rana hajja dasu Aunty sadiya suka ido gidan AJ. Da kulolin abincin su.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana xaune A falo yana waya da Mimi yaji ana danna ka'rrawar shigowa ,falon yana wayar ya nufi ko'far yana bude kofar yyi tozali dasu Aunty sadiya ,dakuma hajja."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Angel I will call yhu back." Baijira Mae zata fada ba yyi saurin datse kiran nata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Rungume hajja yyi tamkar wani karamin yaro ,hajja ta Dan turasa gefe ta wani bata rae ya langabar da kae yna kallon ta."</p><p><br /></p><p>"In a low tone .." Yake fadin plzzz saki fuskarki granny fushinki yna ban tsoro." Gaba daya suka saka daria hka suka rankaya zuwa falo."...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ina takwarar tawane ?" Hajja tayi mganar tana kallonsa ,yyinda Rukaiyya ta nufi denning side "ta aje kulolin da suka , taho dasu."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tana ciki hajja bara na dubata na lura ,hajja kinfi kaunar Queen akaina."......bbu karya acikin maganar ka tabbas ynxu nafison Asma'u dakae murmushi maii kyau ya saki ,gamida Shafa kyakkaywan sajensa ,bbu damuwa hajja banji haushi ba." Nama ji ddin haka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ya mike tsaye bara na duba maku ita." Kai tsaye dakinta ya nufa yyinda Rukaiyya tabisa da kallo ,hka taji idanunta sun ciko da kwa'llah."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tana tsaye Agaban mirror dressing ,tsayawa yyi cak ! A bakin kofar shigowa ya zuba mata ido tana daure da "Ash colour din towel Mae Dan girma hka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Jin tayi an rugumeta ta baya ."A tsorace ta bude ido tana kallon ikon Allah!...ta cikin madubi suka hada ido sae taga ya daga mata gira." </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wayyo mumin kasakar min nauyin ka plzzz..ta fada tana son yin kuka ,Cikin kunne yake rada mata .da gaske ??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kedin na tabbata kinfini nauyi." Uhm hmm.banyarda ba ."batayi auneba taji ya sureta sama ya fara zagaye dakin daita."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wayyo allah na!</p><p><br /></p><p>Dan Allah ka daina ." wani iri. Na keji ,ta kankamesa gagam" tareda tura kanta cikin fadeden kirjinsa." Tsayawa yyi cak ! Yana kallon yarda ta rufe idonta ." bakinta ya zubama ido .jin ya tsaya tayi yunkurin kwa'ce kanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ganin haka yasa ya direta a kasa." Amma sae dae me??". takasa tsayuwa." Baya -baya tayi zata fadi yyi saurin tarota."ta zube ajikinsa jagwaf" ..tana maida numfashi.'</p><p><br /></p><p>"Dariya ya soma yimata da almr yama manta dasu hajja dake zaune a falo ." fadawa tayi kan gado "tana maida numfashi haka ,ta zubama selling ido ." kwantawa yyi gefenta gamida tallabo fuskarta ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A shagwabe ta buge masa hnnu sae ga hawaye na zuba a idonta." Abunda ya daga hnkalinsa kenan."tambyr ta ya somayi hnkali tashe ,meya faru kuma?"..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bata kulasa ba ."A fusace ta sauka daga kan gado shikam "binta kurum yake da ido ,kayanta yaga ta Ciro kayanta ta shiga shirya kanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana gamawa yaga tana shirin walwale towel agaban sa."yyi saurin kauda kansa gamida mikewa tsaye ,kishirya su granny na jiranki "A falo da haka yasa kai ya fice."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*******</p><p><br /></p><p>"Cikin sanyinta ta nufo su hajja zuba mata ido yyi tana cikin ,doguwar Riga kalar peach mai ya'nkakken hnnu rigar body hook.CE." sae Dan karamin mayafi shima peach Wanda ta azo akanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sae kamshi na mussaman takeyi ,A hnkali AJ.ya lumshe idonsa ya lura tana son doguwar Riga a rayuwarta."haka kuma tana mata kyau."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Zubewa tayi agabn su tana gaishesu cike ,da kunya hajja sae tsokanarta takeyi jiki bbu kwari ta mike tsaye ta nufi hanyar kiching."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sae da ta Dan yi nisa ta kalli Rukaiyya ."Rak! Zo taimakeni Dan Allah ." cikin jin haushinta tabita da ido bbu musu ta mike tabi bayanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Drink's da snacks ta zuba a katon tire tabawa " Ruakiyya tace ta mika masu ,dae -dae kuma lokacin AJ. Ya shigo kiching din ."batayi aune ba taga ya jawota ajikinsa nan take ta hade Rae hada fuskarsa yyi da tata haka yana gogar ,hancinsa da nata."..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Lumshe idonsa yyi yana shakar kamshinta ,kafin ya bude idonsa a hnkali cikin wani irin yanayi yake fadin ".. Kinyi kyau my drama queen!!</p><p><br /></p><p>" ina son kamshin nan naki ta hararesa gamida dauke ,kanta wae mumin yaushe kazama hakane??".....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Da sauri ya saketa " Am sorry na daina."in a low tone "...yyi mganar.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" muje ki hadamin Ruwa nayi wanka hnnunta ya Rike ,A tsorace ta zaro ido."tana kokarin kwa'ce hnnunta cikin nasa girgixa mata kai yyi sae ta mairairaice ."murya to ka sakarmin hnnu mana."</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Baiyi musuba ya sakar mata hnnun da gudu tabar kiching din."anan yabita da kallon so."....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>************</p><p>"Asma'u nayi farin cikin shigowarki cikin Rayuwar Abdul jabbar." Kece kawae zaki xamr masa "Garkuwa wajen ya'kar makiyansa."....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Ita kam Asmy jikinta yyi sanyi sosae ta tausayawa mumin dinta." Anya kuwa zata iya wannan Aikin??"..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tamkar hajja tasan abunda yake ranta,tayi saurin katseta."gamida fadin karki damu Asma'u ,tunda basa taba tunanin kematar sace. " zasu dauka ke Bo'ss dinsa CE .na wani Dan lokaci fatana Allah ubangiji yabaki sa'ar lashe jarabawrki Amin hajja na gode.". Aunty salma ke fadin insha allahu plant din mu xai tafi yarda akeso....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nasan ya'rtawa bata da tsoro." Cike da jin kunya Asmy ta sunne ,kanta kasa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Anan kuma Aunty sadiya ta karayi mata Nasiha ,yyinda hajja tace nikam gobe zan bar kano." Ina sa ran zuwan ku a koda yaushe ." duk da yace zakuje Indian Mimi ta matsa masa ,da rigima murmushi kurum Asmy tayi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nima wannan karon zan bisa ,hajja."cewar Rukaiyya aunty sadiya tace ae kunfi kusa mukam gobe da izinin Allah zamubar kano." ....bayan la'asr sukayi shirin tafia yyinda Asmy ta cikasu da kayan Arziki sae samata Albarka sukeyi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Suna tafia sae kuma ga ya'n gidan su ."matan yayunta da wasu danginta ."</p><p><br /></p><p>.suma sae ana sallar magrib suka tafi....suna ficewa ta fada wanka."Wanda har lokacin bata hadu da AJ. Ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>★★★</p><p><br /></p><p>"Misalin karfe takwas na dare naji ka'rar dannan ka'rarrawar shigowa falon lokacin ma." Ina kiching ina cikin shigar,English west ." Riga da wando rigr mai hnnun supghaiti. Ruwan Zuma sae wandon Jean's fari Sol' Wanda ya kamani har ya fitowa da hips dina."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Karasawa nayi jikin kofar ,na bude mukayi ido biyu da wandda ke tsaye jikin ko'far sanyen yake cikin shaddar (Hilton))" sky blue kansa bbu hula ,sae naga yadan rame haka tamakr yana cikin damuwa."</p><p><br /></p><p>"Sae naga bbu fara'ar ko kadan akan kyakkayawan fuskarsa ."na basa hanya ya shigo Na amshi manyan ledojin dake hnnunsa ina masa sannu da zuwa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya amsa cikin wani irin yanayi a hadamin dener Queen ina jin yinwa."yarda yyi magnr yabani tausayi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Abinci yake ci .yana bata lbrn jibi zasubar kano zuwa India daga can zasu wuce Bauchi." </p><p><br /></p><p>Cikin zolaya take fadin "Kayi missing din Aliya kenan??" ,nan take taga yanayin sa ya canja."wani irin kallo taga yana binta dashi Wanda takasa fassara sa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wani irin faduwar Gaba naji lokaci daya." Banyie aune ba naji gaba dae ya jawoni a jikinsa ina jin yarda saitin zuciyrsa ke halbawa da sauri da sauri " lalubar bakina ya somayi "..A tsorace na ware manyyan idona akansa." Kmr jira yake na dago kaina ."yyi hanzarin sanya bakinsa Cikin nawa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ya soma kissing dina tamkar wani mahaukaci lokaci daya ya rude ya fita hayacinsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_*Asmy b Aliyu novel's*_....📚</p><p>WATA RANA ! [posted on 4 ."August 2017 @t 8:10pm.]</p><p>By~Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>43</p><p><br /></p><p> "Sae da suka kwa'shi fiye da minti goma a hka da kya'r ta samu ta kwaci kanta. " A hnnunsa ,da gudu ta nufi dakinta ...Cikin wani irin yanayi yabi bayanta da kallo ,hnnunsa ya saka Cikin sumar kansa "gamida brushing dinta da hnnu."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>...."Ana gobe. "Zasu tafi taje gida haka taje gidan su Aunty zulfa ."</p><p><br /></p><p>"Gurin Rahama ne kurum bataje ba ,sabida tayi tafia itada momyn su zuwa Zaria."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*"INDIAN*....</p><p><br /></p><p>"Mimi tayi murna da ganin yayan nata da kuma ya'r uwarta Rukaiyya ,Asmy ce kurum batasani ba ." sae da suka kebe da AJ.anan take tambayr sa ."</p><p><br /></p><p>"Yayah!..</p><p>Wannan fah?".</p><p>" she iz my wife and my life...</p><p><br /></p><p>Ido waje Mimi ke kallon yayan nata ."</p><p><br /></p><p>"But my darling brother how comes??..</p><p><br /></p><p>" Ta fada cike da rashin jin ddin xancensa,nan take mood din ta ya canja."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Folding din hnnunta tayi ,akan kirjinta ta wani bata rae haka nan take kwa'llah ta cika idonta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Meya kaika Yayah?" Meyasa kayi haka .."ka manta balain da ka shiga akan macce?"....zokiji my Angel ." zaunar daita yyi gefensa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Listing to me very carefully .".. My Angel bazan taba na dmar kasanceer drama Queen. Acikin rayuwata ba Mimi."</p><p><br /></p><p>"Did yhu know why??"</p><p>Cikin sanyi jiki ta girgiza kanta almr ."A'ahhhhhhh!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Asma'u ba irin matan da ake yiwa rikon saka saka bane ,tana da abubuwa da dama da na keson Abokiyr rayuwata dasu..."She was All d qualities and All d Attributes to be loved upon.. "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Anan ya zayyana mata duk yarda Auren su ya kasance,Abu daya yasan ya bo'ye mata " Contract marriage ."dinsu da Drama Queen."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wowwwww My darling brother ,nan Gaba kadan zakayi beautiful Relationship kaida .." *Drama Queen* dinka." Am so happy for yhu my own brother in d world."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nan take Mimi ta shiga nuna murnarta sae Rawar jiki takeyi da Asmy itakam ."Rukaiyya ta zama ya'r kallo tana son Yah AJ." Su tafi masauqin su ta kebe itada Mimi..."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Shesshekar kukan Rukaiyya ya ishi Mimi ,A fusace ta katseta wae nikam ,Rukaiyya meya faru kinki yimin bayani Komae ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin fushi itama Rukaiyya ta dakatar da Mimi." Meyasa zan fada maki damuwa ta?... Mimi kinfi kowa ,sanin soyayyar da nakeyi wa Yah AJ." Amma ynxu kina Murnar ya auri Asmy .....Hawayen idonta tashiga gogewa ,ohkey fine !....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nazata idan na kawo damuwa ta ." zaki fuskanci ni, zaki sharemin hawayena ,Ashe ba haka bane ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wanda kuke ciki daya shi kawae ne naki ." hnkalin Mimi yyi balain.tashi xubewa tayi a gaban ,Rukaiyya tarasa yarda zatayi daita ." hnnunta tasaka ta shiga gogema ta hawayen idonta ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Is ohkey !!</p><p>My dear sistr kiyi hkuri ki yafemin ,na maki alkawarin Yah AJ.xai soki zai Goya ya'yan da zaki Haifa ...I promise hnnu tabata sukayi shaking hand's...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" kukan farin. Ciki Rukaiyya ta fashe dashi gamida hugging din Mimi." </p><p><br /></p><p>"Tana zubar da hawayen farin ciki...."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kwanan su 3 india sukayi sallama da Mimi tamkar kar su rabu,harda kuka tayi .....suma cikin kewa sukabart a haka ta cika Asmy da tsarabar kananun kaya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>~~~~*BAUCHI*.....</p><p>"Jirginsu Na sauka A garin bauchi yaji wata irin natsuwa ta shigesa." Kalmr nan ta hausawa yake tuno wa daita ,inda suke fadin."kowa yabar gida gida yabarshi....</p><p><br /></p><p>Sageer ne yaxo daukarsu ."cikin tsananin farin ciki ,da kewar junansu suka Rungume junansu.",</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Lkci daya sageer ya juyo kan Asmy anan yake mata sannu da zuwa ." gidan Aunty sadiya suka nufa acan sukayi dener."</p><p><br /></p><p>Sa'annan Sageer ya daukesu zuwa dae daga cikin gidajen sa." Daren Ranar sunyi shi cikin Aikin yarda zasu bu'llowa su Aliya."</p><p><br /></p><p>Sae kusan 12:00pm.sageer yabar gdan suma wanka kurum sukayi sukabi lpiar gado...Dan sun kwa'so gajia sosae.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>.....Washe gari."</p><p><br /></p><p>Karfe goma na safe Sageer ya diro gidan kasancewr Week end ne."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Duka suna A falo AJ.na aiki da laptop cikin Tsokana Asmy ke fadin yau dae xakaje kaga Aliyan ka!</p><p><br /></p><p>" A fusace ya dago kansa yana kallonta lokaci ,daya ta tuntsire masa da daria shima sageer ya shiga tayata."</p><p><br /></p><p>"Ture laptop din ."yyi gefe ya rarumin pillows ya dinga watsa mata da gudu ta tashi A hka suka shiga zagayen ,falon....Anan yyi nasarar damkar ta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Lokaci daya suka fada kan coach ....maeda numfashi ta shigayi ,haka yasa ya tsareta da manyan idonsa.</p><p><br /></p><p>" Am sowiee plzzz Mr.Abdul jabbar Meera plzzzz kamin nauyi plzzz kaji mana. Tayi mganar A shagwabance."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dogon Hancinta yaja da karfi ni banyi fushi ba Mrs.Abdul jabbar Meera !! Ya fada gamida kashe mata ido dagota yyi oya jeki kiyi wnka ,tym.na tafia....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau zakije ki hadu Da Mrs.Aliya Meera ,drama Queen ." Am scared very scared tana da hadarin gaske.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta hararesa gamida rike kugunta duka biyu,ta maida kallonta da Sageer,Mr.Sageer kajama wannan friend din naka kunne." Ko ya mance nice bo'ss dinsa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Murmushi mai kyau AJ.ya saki gamida Shafa sumar kansa shima sageer din murmushi yyi......</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>®HASKE WRITER'S ASSOCIATION..📚</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>44</p><p><br /></p><p> "Manya-manyan motoci ne na Alfarma suke ta shigowa a harabar gidan Mr.Meera da Almr ana wani gagarumin Taro A yau."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>..........Tsaye take A hrabar gurin tana Amsa wya cike da masifa tana cikin Shigar Riga da wando way'andda suka karbeta sukayi mata kyau wandon Jean's ne baki sae kuma rigar T.shirt fara so'l Mae dogon hnnu .....Bbu alamr mayafi abisa kanta wasu uban hill ne a kafafunta kananan kitsone Na ghana Weaving.....wandda aka yishi da gashin doko Wanda yake famar reto a tsakiya bayan ta ,taci uban make up "akan kyakkyawar fuskarta sae kace mai zuwa gasar sarauniyr kyau ta dunia." Dan nikaina Asmy da ke dauko mako rahota tayimin kyau matuka."...</p><p><br /></p><p>Haka ta tsuke kunkurun ta da bakin belt ,haka yabaiwa mazauna ta damar fitowa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Billy ce takaraso gurinta Itama tana cikin shigar body hook" Riga da skirt."...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Aliya wat wrong with yhu?? Mekike yi anan ?" Lokaci yyi da zaki yanka cake ,kinki tsayawa guri daya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Am sorry billy ina jin kaina wani iri ne a yau duk da yau Ranar farin ciki ne a gareni ,kuma gashi har yau Haseen bai karasoba." Gaba dae wayoyin sa kashe."...ki fadamin mexanyi?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tayi mganar damuwa karara a fuskarta....</p><p><br /></p><p>Kibi komae A hnkali Aliya maybe baida chagi a wyansa,mukoma ciki mom na nemanki...."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>**********</p><p>"Tana cikin shigar wani material Fari ka'l Dan ubansu ,Wanda kudinsa xasu kai kimanin Naira dubu dari da hamsin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Doguwar Rigace " dinki A1 sae gaban rigar da akayi sa da wasu irin duwatsu masu Ado bakake masu,kya'kyalin gaske."</p><p><br /></p><p>"Faraen Vincci hi'll ne " A kafanta masu belt ....."sae Dan karamin veil da ta yane kanta dashi ,su uban kamshi take zubawa tabbas tayi kyau "duk da simple make up ne a fuskarta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Takun tafiyrta su AJ sukaji da sauri suka dago suka kalleta shima yana cikin Bakaken suit " ganin irin kallon da sageer kemata yaji kishi ya kamasa, da Sauri ya mike tsaye ya kalli Naila wadda itama Aiki zatayi tareda Asmy tana cikin uniform dinta na body guard na mata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Naila karbi handbag nata mana da sauri ,ta karasa gurin Asmy ta amshi jakar hnnunta "cikin Takunta na kasaita ta karaso gurinsa ......" Me kuma ya faru kawani bata Rae ??"..</p><p><br /></p><p>Bbu komae Drama Queen ! Lokaci na tafia ya fada ba tareda ya kalleta ba." Dan gaba dae kishi ya ,gama cikasa ....oh really,tayi mganar tana kallon sa." bai kamata kayi fushi ba hka zakaje ma Aliyan ka fuska A daure." Plzzz Dan saki fuskar mana."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Shi kam tuni sageer yyi gaba ,a tare suka fito body guard na take masu baya zuwa mota ...." A hka suka nufi gidan su Abdul jabbar."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*****</p><p>Baiyi mmkin motocin da ya isko birjik a harabar gidan nasu ba,Ya kalli Asmy cikin sanyi .."har zaiyi mgana komae ya tuna yyi sauri basar da zancen ,Anan ya manna mata bakin glass din Frada ..."dai dai lokacin da guards dinta suka bude mata marfin motar."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin takunta na kasaita ta fito tana karema ,gidan kallo Wanda ta radawa suna."Aljannr dunia mutanen dake A harabar gidan da yawa "..basu gane AJ ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka body guard's suka take masu baya ,zuwa kofar shiga gida."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Suna sawo kai dai-dai lokacin Aliya zata ya'nka cake mom "na gefenta granny da Aunty sadiya da kuma" Rukaiyya da sauran mutanen da Aka gayyataa da mazaaa da mata A gefe.....</p><p><br /></p><p>"An kawata Falon da flowers masu ban Sha'awa.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Ganin AJ ...A tsaye ya firgita mutanen dake cikin ,falon waya'ndda suka San sa ..."lokaci daya Aliya ta saki knife din hnnunta."</p><p><br /></p><p>Gaba dae ta Rude haka ma mom da sauran ,friends dinta cikin takunsa na kasaita ya dosheta sae xuba mata murmushi yakeyi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dae-dae inda wukar ta fadi ya durkusa ya dauka ,yana dagowa ya rugumeta kam" ajikinsa Happy birthday my Luv!</p><p><br /></p><p>"Hawayen farin ciki suka gangaro ,daga idonta Ta dago daga jikinsa tana tattaba fuskarsa ,Abdul Kaine kodai gixau kake yimin??" Ta fada cikin rawar murya gaba dae tagama Rudewa ...nine Aliya duba ki ganni ya manna mata kiss akan cheek's nata ....Dama kana Raye??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yes mana kinga ikon Allah ko ??" Come on Aliya yau Ranar kice karki daga hnkalin ki ,nine a gabanki cike da farin ciki ya rungume mom dinsa." Haka yabi kowa yana hugging dinsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kafin ya dawo Gurin Aliya "cikin wani irin farin ciki take Kallonsa Am so happy to see yhu my love I really miss yhu Abdul jabbar !!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tayi hugging dinsa ,can kuma ta sakesa ina kashiga tsawon watan ni haka??" Aliya iz a long story."</p><p><br /></p><p>Sae mun zauna." Wukar ya bata gamida taimaka mata ta yanka ,cake shine farkon Wanda tabaiwa cake ..."A baki haka shima ya dauka yabata nan ta baiwa granny da mom.."nan wuri ya dau Tafi ji kakeyi Raf! Raf!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Congratulation mrs. Aliya Meera Happy birthday to yhu!!</p><p><br /></p><p>Jin wata sanyyar murya ta daki dodon kunnenta yasa ta dago ,da sauri taji inda muryarta ke fitowa .....". A hnkali Asmy ke takowa gurin Aliya yyinda Naila ke take mata baya da kuma body guard maza guda biyu ...masu karfin gaske.."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wani kallo Aliya takeyi mata Na Rashin sani, cikin karfin hali tabaiwa Aliya hnnunta na dama." Itama Aliyar tabata." Am Asma'u Omar omra...Aliya Abdul jabbar Meera ,Asmy ta gyada kai sukayi shaking hand's tareda girgixa ma junan su kai."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asmy ta maida kallonta gurin AJ...anan kuma ta rufesa da Fada Mr.Meera wat Nonsense'ss is This??" Da dukiyar ce tawa ake ."celebrating haka??"</p><p><br /></p><p>Kudin nawa ake banzatar wa "kamr laidar fiya wata .....this is impossible !!</p><p><br /></p><p>" bazai yuyuba ....!! Takarasa mganar cikin Tsawr gaske anan ta umurci dayan gurads dinta ya kira waya Sauran su su tare mata kofar falo kar abar kowa ya fita."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Am sorry Mrs.Omra Dan Allah kibi komae A hnkali cewar AJ." Yyi mganar cikin girmamawa!!....A fusace ta juyo garesa gamida zuba masa manyyan idonta masu gigitasa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Idan Ran Aliya yyi dubu to ya baci ,Anan ta karaso gaban Asmy .....hii how dare yhu to speak my husband like DAT?"</p><p><br /></p><p>"Ina tunanin bakya dai daga cikin family member's na gidan nan so meye naki Aciki Dan an zubar da dukia ina tunanin kudin nan banaki bane nasa ne...." So wat do yhu want??</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Aliya tayi mganar gamida folding din hnnunta akan kirjinta ta zubama Asmy ido."..lokaci daya Asmy ta kya'kyale da dariar da yakara fusata Aliya." Itakan ta tasan tana cikin Tsaka mai wuya "daurewa kawae ne takeyi ko kadan bataso A fuskanci,Weaknesses dinta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Naji dukiyar mijinki ne A can lokacin Da ya wuce but not now!! </p><p><br /></p><p>Komae na mijinki a ynxu is belong To me.....baki ".. Wangalau ta saki tana kallonta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dariya Aliya ta kya'kyale daita." Gamida nuna Asmy da yatsan ta ."Are yhu out of your mind...??</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nan kuma Aliya ta maida hnkalinta kan AJ.wandda yagama Sandarewa A wurin,Abdul kana jinta wae gaba dae dukiyrka ta dawo hnnunta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"But Abdul jabbar ....sae kuma mganar ya sarke a bakinta takasa karasawa "...</p><p><br /></p><p>" Don't wrong Mrs.Aliya Abdul jabbar Meera "I will explain Everything but not now ! Sae lauyana yaxo...."</p><p><br /></p><p>Anan Aliya tayo kukan kura Akan ta ,saurin ja da baya Asmy tayi ...."plzzzz Mr.Meera Take crazy women And faraway"from me gagam "AJ ya riketa ..." Gaba daya ,tarikice masu tana fadin Asmy karya takeyi ...." A fusace AJ .yaja hnnunta zuwa bedroom dinta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wurgata yyi kan gado....am requesting yhu to stop dis Nonsense's drama Immediately."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Baki wangalau ta saki tana kallonsa hawaye na mugun zuba A idonta ,mganar Mrs.Omra gaskiyya ne inba so kike mubar gidan nan ba." Yyi mganar cikin fushi A gaggauce ta mike tsaye tana binsa da kallo ,A tsorace."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yes my property iz belong to her now! ." ba karya ta fada ba ,Aliya ta girgixa kai hawayen idonta na mugun zuba cikin rawar murya take fadin ."She is Run Everything & my happiness "layi ta farayi yyi saurin tarota nan take ta sumaa...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*TEAM...DRAMA QUEEN*".🌹</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>_word's can't Ever explain how much I love yhu sis *Zainab Bello Aliyu*"(ZEERO) so this page goes to yhu my lil sistr thank yhu so much for the love stay blessed my ya'r kanwa." Luv yhu more!_*one love*#❤</p><p><br /></p><p>45</p><p><br /></p><p>"Some hour's latter."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Duka suna zaune A babban falo sai ...Aliya CE a gefen AJ.kallo daya zakayi mata kasan tana cikin tashin hnkali " haka ma mom daka kalleta kasan ,A rude take..hajja da Aunty sadiya na A gefe."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yyinda baristr musa da sageer suna zaune waje daya." Da alamr Asma'u kurum akejira.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Takun tafia sukaji A hnkali suka maida kallon su gurin ,cikin takunta na daukar hnkali ta fara saukowa daga kan stairs yyinda. Naila ke take mata baya." cikin wata doguwar Riga ." body hook,orange &brank Mae dogon hnnu sae Dan karamin veil dinta orange." Wandda tayane kanta dashi..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Idon AJ.na kanta Aransa yake fadin ita wannan kullum cikin ,doguwar Riga ta body hook ko jallabiya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kujera mai hawan mutum daya ,ta hakince gamida crossing leg's dinta tana kallon mutanen falon daya bayan " daya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wani mugun kallo Aliya keyi mata....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Naila mikawa baristr musa Document's din hnnunki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cike da girmamawa "Naila ta isa gaban sa gamida Dan russunawa ta mika masa file's din hnnunta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin kwanciyr hnkali baristr musa ya shiga duba takardun dake ,cikin falon daya bayan daya." Tsawon minti goma ,baristr musa yana duba takardun...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ya dago yana kallon AJ. A fakaice Da ido ya masa alama ya Riga ya gane meyake nufi .." Ya mike tsaye gamida kallon family member's din sae dae kuyi hkuri ."wannan yarinyar tafiku gaskiyya takardu sun nuna hakan." Gabadai dukiyar Mr.Abdul jabbar meera ta dawo hnnun Mrs.Asma'u Omar omra."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana gama fadin hka yace na barku lpia sa'annna Ina Baku shawara karku gwada shari'a da Mrs.omra Dan bazaku iya ka'rawa daita ba." Nabarku lpia .."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin wani irin fushi Aliya tamike tsaye tana kallon AJ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Shima cikin daure fuska ya mike tsaye yana kallonta, duk kune kuka jazamin wannnan hasarar tsawon wannann lokacin da na dauka bana gida meyasa Baku nemeni ba?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Bayan haka kun saka dukiyata ta salwanta A Sanadin ki!! Ya fada yana nuna ta." Dan haka duk cikin Ku duk wandda yaji baxai iya zama dani ba."hanya A bude take."</p><p><br /></p><p>"Da sauri hajja ta katse sa .mekake fada haka Abdul jabbar karka ka'ra fadin haka ,A kowane irin hali zamu iya zama dakai."</p><p><br /></p><p>"A sanyayye mom ta karbe zancen da fadin Kayi hkuri da'na munsan bamu kyauta maka ba." Amma karka dauka da zafi my son."mun shiga tashin hnkali A ranshin ka." Hawaye suka zubo a idonta."mun Amince a kowane,irin hali zamu zauna dakai da ddi da rashinsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cike da wani irin farin ciki yyi hugging dinta."suna hada ido da granny tayi masa jinjina👍 ya mayar mata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A hnkali drama Queen ta mike daga zaunen da take ,ta maida hnkalinta kan AJ." Zaka zauna A karkashina idan zaka amince da sharadina??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Da sauri AJ.ya zube agaban ta komae kikace hka za'ayi."... Baki wangalau Aliya ta saki tana kallon sa ." yau Abdul jabbar ne zube agaban macce yana mata haka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Zakayi Aiki tare dani " sa'annan kuma gaba daya zan canja tsarin Aikin gidan nan ,Abu na farko shine ..."bana son ganin ma'aikata a gidan nan."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mutanen dake cikin gidan nan ,su zasu dinga aiki irin masu Abinci haka da share -share." Dan haka na sallamesu."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Driver kawae nake buka'ta da maigadi."..... Macce daya zan daukewa aikin gidan nan ,wannan tsohuwar wadda naji kuna kira hajja."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sauran matarka da Mahaifiyar ka zan basu Aiki."...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mahaifiyar ka itace zata dinga Abincin gidan nan gaba dae a kowace Rana.sau ukku!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" A firgice mom ta kalli Asmy sae taga tayi mata wani irin kwa'rjini da da sauri ta dauke kanta ."ta samu kanta da wani irin jin tsoronta.".........</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mrs.Aliya meera Ita zata cleaning clearing din part din nan dana hajja a kowa ce safiya,sau ukku kuma."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tafi Aliya ta farayi mata RAF! RAF!...yhu Are talking 2 much Mrs.Asma'u omra....nafi karfin na kaskantar da kaina Akan wata ..</p><p><br /></p><p>" Ta kalli AJ. Baxan iya zama cikin wannan gidan ba." Zan koma gaban iyayena !har ranar da zaka samu ,gidan kanka."ta share hawayen idonta ,Haka ba yana nufin na bar sonka ba."A kowane hali muna tare."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Folding din hnnunta tayi a kirji gamaida,tattaki gaban Aliya ...ohkey naji bayanin ki Mrs.Aliya meera hanya bude take zaki iya tafia fatan Alkhairi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin fushi Aliya ta goge kwa'llar idonta .I don't need your good wishes " Any more..... ,Amma kisa Aranki." (WATA RANA!)''zan dawo gareki na maki Alkawarin sae na dawoma da mijina dukiyarsa " mark my word's.just wait and watch....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Da gudu tabar falon tana sharar kwa'lla itama Asmy sama ta haye dama kuma A part din AJ.ta sauka da haka taro ya watse...."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kaida kawo tashigayi ,A tsakiyar falon .."jin tayi anyi hugging dinta ta baya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"MUMIN !</p><p>Aliya fa zata ba'ta mana plant dinmu." Karki damu my drama Queen." Bazata tafiba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da mmki ta juyo tana kallon sa,kamar ya sabida nafi kowa sanin halinta "Macce CE mai hadarin gaske ,Zan kula da duk takunta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da haka ya jawota jikinsa,ya hade fuskarsa datata hancinsa,na gugar nata." Zif din rigarta ya fara ja cikin hikima."nan take ta bata rae gamida kwa'ce kanta a hnnunsa ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Bana son wannan abun plzzzzz,mumin ina tunanin mun Riga mungama wannan magnr kai Abokina ne kurum."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin wani irin yanayi yake kallon ta cije lebensa na kasa yyi ."cikin sanyi yake fadin Am sowiee,da haka yasa kai ya fice daga part din nata...[truncated by WhatsApp]...</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>*here's a page in a honour of my dear big fan's and supporter's, khaleesar Haidar novel's pharty novel's Dandalin Autar Hajia ,Maska fan's Matan kwarai Dandalin Asy Khaleel ,Rumbun Asiya Basheer Aliyu Zeey Al'kaseem novel's And other's thank yhu for d Luv and support*"..ONE LUV#❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p> "SOME LOVE STORIE'S NEVER END!!😘</p><p><br /></p><p>46</p><p><br /></p><p><br /></p><p>In Aliya's Room....</p><p><br /></p><p>" katuwar Trolley dinta ta jawo ta shiga zuba kayanta a haka AJ."ya sameta Jikin ko'far dakin ya jingina ,gamida yin folding din hnnunsa A kirjinsa." Sae da tagama tsara kayanta tsaf !</p><p><br /></p><p>"Cikin katuwar trolley ta zuge zif .</p><p><br /></p><p>Dama tana cikin dinki Riga da skirt." Holand ce brown da ratsin ja ajikinta."</p><p><br /></p><p>"Dinki ya kamata sosae gaba dae Rabin kirjinta ,A waje yake Dan karamin veil ta dauka baki ...tareda zura plat shoe ,suma bakake da karamar handbag" dinta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Fuska daure ta tunkari ko'far fita daga dakin ,kallon ta yakeyi Aransa yake fadin tukuna Aliya fitarki a gidan nan ba yanxu ba ynxu ma Aka soma wasar."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Keme me ya hanata fita hka ya wani bata rai ,kabani hanya na wuce Abdul jabbar!!</p><p><br /></p><p>" tayi mganar cikin wani irin Sauti lumshe ido yyi gamida budesu A hnkali ya saukesu."Akan ta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin haddiyr muryarsa yake mgana ." yana fadin ,ina kike nufin zaki tafi Aliya??" So kike ki tonamin Asiri ne??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Meyasa meyasa bazaki yarda da qaddarar da ta afkar mana ba??"...kina da tabbacin haka zan dawwama ,Bakya tunanin "..WATA RANA! Arzikina xae iya dawowa ??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dama ba sona kikeyi ba?,kudine a gabanki bata da zabi tafada jikinsa gamida fashewa da wani irin kuka mai sosa Rai kar ka'ce haka Abdul ." kaima kasan dukiyrka baya gabana. Ni baxan iya jure kallon yarinyar nan A gidan nan ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wai ace yau ni Aliya zan zamar wa wata house girl ,taya kake tunanin zan iya irin wannan Rayuwa har na bautawa wata ba'kar yarinyar!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Har Aransa yaji zafin kalaman ta sae dae ya danne haka A hnkali ya dinga lallashinta ....wannan aikin nawa ni lokaci ne idan kika kwantar da hnkalin ki Aliya komae mai wucewa ne."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kina jin ina jin ddin Abunda tayine dole mu lallabata ,Dan na lura yarinyr nan bata da kirki."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A hka dae ya samu ya dinga lallabata gamida fadamata swttt word's masu ddi daga nan salon nasa, ya fara canjawa Dan shi kansa yasan A bukace yake "....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" WASHE GARI......</p><p>"Tunda safe sae ga mom a kiching ,Din part din su Aliya Dan Drama Queen tace bata yarda tayi girki part dinta ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Anan mom ta hade da Aliya itama tana gyaran falo cikin ku'nar rae kayan barci mane ajikinta " duk tabi ta wani hargitse .,da alamr barcin baima isheta ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mom tayi saurin Jan hnnuna zuwa kiching Aliya ta kalleta ,A kufule mom meyene??</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" sassauta murya mom tayi yi kasa da muryar ki Aliya."</p><p><br /></p><p>Mom ta fara fadin Anya Aliya bakya ganin Akwae wata kulalliya A kasa.??"...</p><p><br /></p><p>Kamar meye kenan?" Da alamr akwae wani Abu tsakanin yarinayr nan da Abdul jabbar haka nake suspecting .....Da sauri Aliya tayi saurin dakatr daita plzzzz mom kibar wannan mganar Dan Allah kinfi kowa sanin Abdul jabbar taya zakice akwae wani Abu tsakanin sa da wannan bakar yarinya " lokaci na zuwa da zan koya mata hnkali ynxu billy kurum nake jira." Kixuba ido kisha kallo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ba zanyi sati biyu cikin wannan wahalar ba,A hka tasa kai ta fice A sanyayye mom tabita da kallo.."girgixa kanta tayi gamida cigaba da ferar dankalinta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A wahale Ta dawo dakin dai -dai kuma lokacin AJ.ya tashi daga barci ,ganin yarda Aliya tashigo du'ke tamkar wata tsohuwa,yasan ta wahala.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" murmushin mugunta yyi gamida dirowa ,daga kan gadon." Ya karaso gabanta my Aliya!!</p><p><br /></p><p>"Ya fada cikin sigar tsokana A raunane ta dago ta kallesa, Wat wrong with yhu??</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" A sanyyaye Ta zube gefen gado hka kwa'lla ta taru A idonta Abdul nagaji ne ."Dan Allah kaxo mubar gidan nan tafada cikin. Rawar muryarta."..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Du'rkuso yyi a Agabanta gamida tallabo ha'barta am sorry my Aliya nasan nine na jazami ki hakan kiyi hkuri wata rana sai " lbr."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mikewa yyi tsaye ya bata hnnunsa na dama ta rika ya mikar daita tsaye ,muje muyi wanka kinga zan fita office yau " bansan ya halin yarinyr nan yakeba."....nima ina son na shiga skull ,da haka suka shige toilet Dan yin wnka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>************</p><p><br /></p><p>"Tana cikin parkin kanta aka turo ko'far dakin A Dan raxane ta juyo ,sukayi ido biyu dashi yana jingine jikin ko'far yyi crossing leg's dinsa, gamida folding din hnnunsa A kirji ,murmushi mai kyau ya sakar mata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana cikin shigar ka'ananan kaya wandon Jean's ruwan kasa da ba'kar T.shirt mai dogon hnnu mai maballai ajikinta ,sae talkamin kafarsa rufaffu suma ba'kakke sae kamshi yake zubawa." Sumar nan ta kwanta luf"...akan sa .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Turarren jikinsa sae fisgarta yakeyi ,good morning my drama Queen!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Dalla masa harara ta shigayi tamkar idonta zai sauko ka'sa jin shi tayi gaf ,daita." Ya amshi ribbon." Din hnnunta ya shiga tattara gashin kan nata bata hanasa ba ta sakar masa kan."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sae wani cin magani take tana turo masa Dan kyakkyawan bakinta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan yyi parkin, din kan nata A hnkali ya sa'kalo kansa cikin wuyan ta ya zuba mata ido ta mirror dreassing wae duk wannna. Fushin na minene my Husna!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Turesa tayi Ajikinsa ta koma kan soofa ta zauna ,dawowa yyi gaf daita zata mike tabar masa gurin Ya hanata ya rike damtsen hnnunta gagam" fadamin meye laipina ta Dan hararesa meye kuma laifin ka mijin Aliya! </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kafita ka bani wuri zan shirya plzzzz,naki wayon mexaki bo'yemin hnnunsa daya yasa yana ko'karin walwale towel din jikinta caraf ! Ta rike hnnun A tsorace."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin shagwaba ,take fadin Dan Allah wae meye haka mumin??" Shima ya kwaikwayi muryarta ke zan tambaya my drama Queen!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Na maki an tashi lpia kin wani shareni ,Aliya ya kamata kayiwa haka " cikin Rashin fahimtr inda ta dosa ya Dan yi murmushi kema ai hakkina ne na tambaye ki hakan."</p><p><br /></p><p>"Ta hararesa ni har ga Allah na yafe."...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Tayi mganar cike da tsabar yarinta A zuciyrsa kuma ya shiga tamabyr kansa ita wannan yarinya ko kishinsa takeyi ,cikin farin ciki yake fadin inko hakane yaji ddin hakan."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mikewa tsaye yyi ya nufi side ,din kayanta bara na zabawa madam kayan da zata saka ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Baijira mai zata fadaba." Ya nufi ,side din kayanta da Dan sauri ta bisa ta tsaya agabansa bai kulata ba ya cigaba da duba kayan da ya dace ,tasaka can idonsa suka hango masa Riga da skirt din Super wax" dinki Riga da skirt ,skirt din mai dinki 16 pieces ."sae kuma Riga da akayi yankan pieces itama Wanda akayi mata half gown"....wadda ta kawo dae -dae guwayyun ta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Atamfar kalar dark blue ce da ratsin orange&yellow ajikinta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Saka way'annan my Queen kinsan yau zamu fita office ,nifa baxan sasuba." Zasu dameni gaskiyya ta fada gamida hade rae."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>,shima hade ran yyi nisu nake so kisaka nagaji da kallonki acikin jallabiya's ,ina son naga matata cikin Traditional kaya." Dan haka dole kisaka ni mijinki ne umurni na baki sae dae idan baxaki bi umurnin nawa ba.!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yyi mganar fuska bbu walwala daukar kayan tayi A fusace xuwa toilet yafi minti goma ,yana jiranta ."sae gata ta fito tundaga nesa ya zuba mata ido ,yana kara jin sabon sonta a zuciyarsa ....bata kulasa ba ta jawo hill's shoe din ta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta xauna kan soofa ta fara ko'karin sakawa masu dauke da kalar dark blue zubewa yyi agabanta ." ya amsa ya dago ka'farta yana kiciyar saka mata talkamin sukaji ana knocking din ko'far....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*TEAM# "DRAMA QUEEN.❤*</p><p>WATA RANA !</p><p>By~Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p>47</p><p><br /></p><p> "Da sauri ya saki ka'far tata a hnkali ta mike ta nufi ko'far murya can ciki take fadin waye ne??...</p><p><br /></p><p>" madam nice muryar naila ce ta daki dodon ku'nnen ta .</p><p><br /></p><p>Ohryt!!</p><p>Naila jirani A falo ina zuwa ,da haka ta juya ta kallesa kafita gani nan xuwa kar matarka taga mun fito tare ,tayi mganar fuska bbu walwala ."</p><p><br /></p><p>"An gama my flower." Yyi mganar gamida mikewa tsaye hnnayensa duka xube cikin aljihun wandonsa ,Ta Dan hararesa niba flowern ka bace kadai san wadda take flower ka."</p><p><br /></p><p>"Tayi maganr cike da jin haushin sa ,wandda tarasa dalilin sa jawota yyi da karfi ta fado kan kirjinsa ware manyan idonta tayi akansa." Yatsan hnnunsa ya saka yana yimata tafiar tsutsa A fuska ,A hnkali ta lumshe idonta tana ka'rbar sakonsa." Cikin ka'rfin halinta ta turesa ,da sasarfa tayi hnyar toilet Cikin wani irin ynayi yake binta da kallo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>********</p><p>Mom ce tagama tsara komae A dinning,dae dae lokacin dramar Queen ke saukowa kan stairs din ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Itama dae -dae lokacin Aliya ta fito daga dakin nata cikin shiga ta alfarma." Batare da ta kalli inda Asmy takeba."</p><p><br /></p><p>Kai tsaye ta nufi dinning side."</p><p><br /></p><p>Kusan tare suka isa cikin ya tsine fuska Asmy ke fadin dame dame kk hada?" Ta tambayi mom fuska bbu walwala."cikin dakewar zuciya mom ke fadin Ruwan zafi ,da kuma Dan kali da kaza."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin fusata Asmy ke fadin wat??" Halama kudin banza nake dashi dankali da ruwan tea baxai isa ayi break fast dashi ba sae an hada harda kaza."..</p><p><br /></p><p>"Am sorry Mrs.Omar za'a gyara cewar AJ. Daga yau a kiyayye Abu daya za'a rinka yie."</p><p><br /></p><p>"Ki kiyaye ina break da bread da kifi da kuma bakin coffee ,hop zaki kiyaye?".. Da Sauri mom ta kada kae idan ina bukatar canji zan maki mgana ,zansa naila ta tsara Yarda za'a rinka Abinci..."</p><p><br /></p><p>Taja kujera ta zauna "ta kalli Aliya wadda ta lura ta ,cika fam." Mrs.Aliya meera Dan hadamin bakin coffee " ta fada tana operating da wyan ta batareda ta kalli side ,din Aliyan ba." </p><p><br /></p><p>"Da sauri AJ.ya mata alamr ta hada kurum,ya fada yana yimata magiya a fusace Aliya ta fara hadamata tana,gamawa ta tura gabanta.".</p><p><br /></p><p>Ta shiga ko'karin hada nata ,A yangace Asmy tayi saurin dakatar daita bana cin Abinci tareda kowa ,ko a gidan mu plzzzz kubarni na gama tukuna."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Aliya ta tsaya cak! Tana kallon ikon Allah suna hada ido da AJ.' Yyi saurin dauke kansa ,Tana kai cup din bakinta tayi saurin cire bakinta akai tareda kallon Aliya cikin fushi , " A fusace ta mike tsaye batayi mgana ba sae dae taji Asmy ta feso mata sauran coffee din cikin bakinta." Akan kyakkyawar fuskarta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ke jahilar ina ce??</p><p><br /></p><p>Bakida hnkali?</p><p><br /></p><p>Tayi mganar A tsawace haka ake baiwa mutane coffee a gidanku!!...</p><p><br /></p><p>" yhu are very stupind!</p><p> "Ta karasa mganar Cikin wani irin fushi ,kan Aliya na akasa haka fuskarta gaba dae ta ba'ci da bakin coffee " tunda taxo dunia bbu wandda ya taba wulakanta ta,irin Asma'u Omar omra."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tsaki Asmy tayi ta kalli AJ.a fusace Mln mutafi office ,baxan iya break fast a gidan nan ba." Ka fadama matar ka ta canja da'bi'unta da wuri "idan ba hka ba akwae matsala."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Naila fice muje ,suna barin falon Aliya tayi wani irin ihu gaba dae ta ture abincin dake kan dinning .." Hawayen bakin ciki suka xubo mata ,cikin sassarfa AJ.yabi bayan drama Queen dan ko takan Aliya bai biba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>******</p><p>Tana kuka tana fadawa ,billy abunda ya faru ." billy baxan iyaba ! Baxan iya barin sa har wani lokaci ba." ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Barin yarinyr nan A dunia shi kawae zaisa hnkali na ya kwa'nta shin kinga yarda AJ .."ke rawar jiki akanta??"...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Bakiga yarda take basa umurni ba."</p><p><br /></p><p>"Am sorry Aliya kiyi hkuri na kwana biyu mana ,amma xanxo ynxu kodan na ganta ....idan ta canci ta mutu sae mu Aikata ai bawani aiki bane kawata kibani nan da minti talatin gani nan....da haka ta datse kiran."</p><p><br /></p><p>Anan kuma ta shiga Neman layin ,mamin ta amma a kashe cikin kunar rae tayi jifa da wyar kan bed ." </p><p><br /></p><p>"Gaban mirror dressing ta tsaya gamida,ku'ra ma kyakkayawar fuskarta ido ..."</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p>48</p><p><br /></p><p>"Da sallama ta shiga falon na granny tana ko'karin cire shoe din ka'farta da nufin ta karasa cikin falon hajja tayi saurin dakatar daita."</p><p><br /></p><p>"Ba Sae kincire ba Asma'u ka'raso a hka cike da jin kunya Asmy ta ka'rasa falon na granny wadda ke xaune a kasa an shimfida mata katuwr carpet " anjera kayan break fast.</p><p><br /></p><p>...da sassarfa ta isa gurin hajja tayiwa Naila nuna, data cire mata shoes dinta cike da girmamawa ta du'rkusa a akasa ta zare mata talakamin kafarta ,cike da girmamawa ta zube a gaban hajja."</p><p><br /></p><p>"Tana kwasar Gaisuwa cikin jin ddi hajja ta amsa tana tambayr ta yata kwana??" Ya kuma rigimar Aliya??...murmushi mai kyau tayi wandda ya bayyana dimple dinta ,lpia qlau hajja masha allahu."</p><p><br /></p><p>"Kinyi break fast kafin ta amsa hajja AJ. Dake zaune dai daga cikin kujorun dake zagaye da falon, ya kalli hajja da lumsassun Idanunsa ." tayiwa matana wulakanci taya za'ayi ta iya break fast."</p><p><br /></p><p>"Ya fada gamida galla mata harara ,itama hararar tasa tayi ta Dan murguda masa baki ,kana da karfi basae ka rama mata ba?"...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" hajja tayiwa naila umurni akan ta hadawa Asmy tea nan ko tabi umurnin hajja ta hada mata .."AJ ma yace a hada masa tea.</p><p><br /></p><p> "A gefe kuma ta zuba chip's da soyayyen kwae a plate ,ta tura gaban Asmy mayafin kanta ta cire ta baiwa naila ."</p><p><br /></p><p>AJ.shima ya zube a gabanta ya saka hnnunsa na dama acikin plate din,dake shake da chip's da soyayyen kwae.'' Granny kiyi masa mgana ,karya samin hnnu ta rike hnnun nasa ,taana galla masa harara wadda batasan sarda take yimasa itaba."</p><p><br /></p><p>"Abdul jabbar, kabar takwarata tayi break fast mana......Kuna fa makara cike da marairaicewa ''yake fadin haba hajja nima fa banyi break fast ba, Hajja tayi murmushi tana jin wani farin ciki sosae aranta ,yi hkuri takwarata ci abunki kyalesa." Da haka dae suka shiga yin break fast ,Sae tsokanarta yakeyi.</p><p><br /></p><p>*********</p><p><br /></p><p>"Tana xaune Akan coach dinda ke office din ta zuba masa ido wandda ya dukufa wajen cika wasu file's, gaba daya yamai da hnkalinsa gurin baimasan tana kallonsa ba ga sanyi AC.amma ya hada uban gumi da alamr yyi matukar galabaita."</p><p><br /></p><p>"Dago kansa kenan caraf !!</p><p>Suka hada ido A tsorace ,ta dauke kanta Dan murmushi yyi gamida Aje bairo din hnnunsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ya zuba mata lumsassun idanunsa ,Kallon fah?? Ya fada gamida daga mata gira " shaye da toka ta Dan kallesa ni yaushe na kalleka??"...na kamaki ne kina kallo na Ae.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta tabe baki kanka akeji tsam ya mike tsaye ,ya nufo gurinta ido ta zuba mata komae nasa mai kyau , da alamr kina cikin kewa drama Queen ya zauna gafdaita A tsorace ta Dan matsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kafin yyi mgana sukaji knocking din kofa ,yesss come in.....ya fada A ya'ngace a zuciyrsa take fadin wannan mumin din akwae kininbibi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sageer ne ya shigo office din Ahhh...kace kana tareda madam Dan iska ,kake amsa min A ya'ngace ga form din na karbo "yau madam tasa na wahala rufe idonta tayi cike da kunya ." Amsar form din AJ. Yyi sageer ya juya zaifita ,AJ ya dakatar dashi."</p><p><br /></p><p>"Sai ina Kuma?? Zan koma office mana ,ya fada gamida kanne masa ido " murmushi yyi yana barin office din Ta kallesa da sauri Muga form din ta fada cike ,da farin ciki."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nan take ya wani hade rae bafa form din shiga skull bane!!</p><p><br /></p><p>...kaifa kayi alkawari mumin meyasa zaka fasa??" Ta fada cikin rawar murya..."shaye da toka yake fadin taya zan sakaki skull da na taba ki kadan zaki fara yimin Rashin kunya".kodan irin kiss din nan ba kiyi min baranta na samu hugging....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Batace komae ba ta aza kanta akan cinyoyinta ,bata ka'ra kulasa ba." Shima haka bai bi takanta ba ,ya fara jin haushinta sosae aransa ,na ganin yarda take nuna ki'nsa Ka'rarra take nuna masa ..."maxaunin sa ya koma ya cigaba da aikinsa ransa A bace yana cikin bukatar macce ,ga Rigimar Aliya ga rigimrta wadda bata da wani dalili haukar banza ce kurum" jin yyi mararsa tayi wani irin juyawa ,da hanzari ya aje pen din hnnunsa tareda dafe cikinsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>**********</p><p>"Kina ina?? Ina gida mana tom.naga masu gadi sun hanani shigowa." Ran Aliya yyi balain baci ,A fausace ta nufi bakin get Dan shigowa da kawartata....</p><p>WATA RANA!</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>49</p><p><br /></p><p>"Ganin Aliya na tunkaro gurinsu securities guard din suka sha jinin jikinsu ,Cike da masifa ta ka'raso gurinsu hka tana binsu da mugun kallo.</p><p><br /></p><p>" su wanene Ku da kuke tunanin hana kawata shigowa cikin wannan gdan ,karku manta gidan mijina ne wannan ." daya daga cikinsu ya fara magana ,cikin girmamawa yake fadin kiyi hkuri madama Mrs.Omar ce tayi mana umurnin kar wandda aka bari ya tako kafar sa daga gidan nan idan ba itace ta sanar mana da zuwan suba."</p><p><br /></p><p>"Wata uban tsawa ta daka masa kayi shuru!! Ka rufemin baki hnnu tasa ta bude get din A fusace taja hnnun Billy zuwa cikin gda."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sae da suka ku'lle a daki billy ta dubi Aliya waeni ki fadamin meyake faruwa ne??.....Aliya bata bo'yewa billy komae ba ta shiga bata lbrn ,abunda ya faru shuru billy tayi cike da jimami hka tayi shuru takasa magana.</p><p><br /></p><p>"Sae can ta sauke doguwar ajiar zuciya kinsan meye Aliya Anya yarinyar nan ba Asiri tayiwa Abdul ba."?</p><p><br /></p><p>Wani mugun kallo Aliya take bin Billy dashi ,A hnkali taja tsuka haba billy meya kawo wannan mganar mana ,wane irin asiri Kuma?" Kenifa yanxu nadaina wahalar kudina zuwa wajen malamman tsibbo."</p><p><br /></p><p>"Yarda zan dawo da dukiar Abdul hnnuna nake tunani ,kebani shawara ??" Aliya ta fada tana kallon billy ,shawara daya ce Aliya kiyi hkuri ki dauki cikin Abdul jabbar ina ganin komae zaizo da sauqi.."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A razane Aliya ta fito da ido waje tana kallon Billy sae kace ,ta fada mata wata mummunar kalma shaye da toka ta kalleta kinga mu daina wannan mganar shawarar nan bazata karbu ba." Canja wata nikam ban shirya haihuwa ba ,A dai irin wannan tym.din Dan haka canja wata shawarar..." Shawarar nan Aliya itace karshen wahalarki gdan nan kinsha fadamin yarda AJ.keson ya'yah why not!!</p><p><br /></p><p>"Kiyi amfani da wannan damar shawarar da zan iya baki kenan plan na gaba baxai mana wahala ba.".....</p><p><br /></p><p>Ranar da duk Abdul jabbar yagaji da Rashin haihuwarki zai kwaso maki kishiyane,wani irin kallo Aliya tayiwa billy wandda yasa ta dakata da zancen nata.</p><p><br /></p><p>" Tsam Aliya ta mike tsaye bbu maccen da zatayi kasadar shiga Rayuwar Abdul jabbar duk wadda ,tayi yunkurin hka zata mutu!! Ki rubuta ki aje billy ,zan duba shawarar ki jirani na watsa Ruwa ina son na shiga skull na duba Result nasan kin duba naki, wani sati za'ayi Resuming skull....da haka ta shiga cire kayan jikinta ta dora towel gamida shigewa toilet kallo billy tabi,kawarta ta dashi "haka tana juya maganganun kawartata Aranta."</p><p><br /></p><p>******</p><p><br /></p><p>"Cikin wani irin yanayi ya aza kansa akan desk yafi minti goma A haka.....A hnkali ya dago rinannun idonsa yana kallonta ,sae yaga hnkalinta na akan wyarta tattara file's din yyi guri daya."</p><p><br /></p><p>"Ya kalli agogon bangon dake manne a bangon office ,din 2:30pm." Tsam ya mike ya ka'raso gurinta ya mikaa mata form din hnnunsa ,fuskarsa bbu walwala can cikin wata murya yake fadin zuwa anjima ki cikasa ,zuwa Monday zaki fara zuwa skull.."ae batasan lkcin da ta daka tsalle ta Rungumesa ba takai mai kiss A baki sae fadin take tnx yhu so much mumin "jinta ajikinsa ,gaba dae ta Rudasa Dan shafama kansa lpia yyi saurin rabata da jikinsa ,Zamu biya country mall" ki zabi abunda kk so dan haka ,idan kin gama ki sameni A mota da haka yasa kai yafice daga office din itama handbag nata kurum,ta dauka tabi bayan sa tana jin wani irin farin ciki Aranta ,Wayar tace tayi ka'ra zubama screen wyar ido tayi ,murmushi Mae kyau ta saki ganin sunan yah Hameed .."</p><p>"Katse kiran tayi tanason sae ta isa mota ta kirasa tana kokarin sa wyar a handbag nata, haka ta cigaba da tafia.</p><p><br /></p><p>Tafia take bata kallon gabanta ,karaf taji ta fada kan mutum saurin tarota yyi ta fado akan jikinsa, Kyakkyawa ne ajin farko haka black beauty sae smiling yake zuba mata idonsu ka'r akan AJ." Wandda yake tsaye a gaban mota yana kallonsu.....jin yyi zuciyrsa na Neman tsinkewa.</p><p><br /></p><p>_@t 6:50Pm.by Asmy b Aliyu_.😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>50</p><p><br /></p><p>A hnkali ya saketa haka ta shiga kallonsa "A tsorace tamkar taga dodo ,murmushin sa mai kyau ya sakar mata gamida daga gira daya samun kanta tayi da dalla masa harara tayi gaba.." Hips dinta yabi da kallo ,hada kansa yyi da sitari.</p><p><br /></p><p>Wanda yaji sarda ta bude motar ta shigo baisa ya dago ya kalleta ba ,sunfi 5 mnt. A haka a sanyayye yyiwa motar key kallonsa ta shigayi tana son tayi mganar sae kuma ta sharesa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wani katon mall suka nufa suna isa yyi mgana da ma'aikatan wurin haka itama yamata umurnin zabar abunda takeso tunda ga kayan sakawa da sauran su na zuwa skull."</p><p><br /></p><p>"Anan ta shiga zabar hadaddun English wear's, sleeping dressings, masu tsadar gaske hka kuma ta juya kan Atamfa da laces hadaddun gaske haka tsadaddu ,handbag's da shoe's ma ta shiga zaba ,su ma'aikatan suka kwasa akaje akayi payment sannan aka bisu dasu a mota."</p><p><br /></p><p>Mgana wannan bata hadasu ba, a hnkali ta saci kallonsa taga hnkalinsa nakan tukin da yakeyi , Cikin sanyi muryarta take fadin kayi hkuri idan na bata maka rae Dan Allah!! </p><p><br /></p><p>"Ta fada cikin sanyin muryarta mekika yi min ??" Yyi tambayr batareda ya kalleta ba ,ni ba kiyi min komae ba ..da haka taja bakinta tayi shuru.</p><p><br /></p><p>"Basu tsaya koinaba sae wani hadadden gidan cin Abinci mai dauke da sunan ((sky crown)).</p><p><br /></p><p>Oder Abinci yyi masu haka ya shiga cin Abincin sa,da alamr shikam yana jin yunwa amma itakam yaga batada alamr cin Abincin sosae ,yana gamawa yajawo wya yana jiran ta idar ....itama bata ddeba ta idar.</p><p><br /></p><p>" daga nan (Sameer meera motor's ) suka nufa Anan Asmy ta saki baki tana kallonsa yarda mutane ke girmamasa" aranta take fadin lallae guy din nan ba karamin Handsome Rich bane."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Batayi aune ba taji ya riko mata hnnu yana murxawa a hnkali ,suna hada ido ya kashe mata ido daya gamida sakar mata murmushi ,ido ta zuba masa tamkar yau tafara ganinsa suna tsaye a hka sae ga sageer ya ka'raso cike da kunya take koka'rin kwatar hnnunta."</p><p><br /></p><p>Amma sae taga AJ.ya rike hnnun gagam." Hka ya fara yimata salo gamida fara murxa hnnun ,daga ina haka??" Cewar sageer AJ.ya Dan tabe baki ,Madam na kawo ta zabi motar zuwa skull.."sageer yyi murmushi haka yana da kyau."</p><p><br /></p><p>Madam Allah ya taimaka cike da jin kunya na amsa ,da amin haka muka jera da Sageer suna hira ' Anan muka karasa gurin da motocin suke a ajeye wasu Rufe da tamfal ,wasu kuma hakanan suke ya Dan russuna dai-dai kunne na Kizabi duk wadda tayi mki yyi maganar numfashin sa na sauka a wuyana."</p><p><br /></p><p>Shikam sageer gaba yyi yana mmkin Abokin nasa da bai iya boye son Asma'u a koina suka shiga."</p><p><br /></p><p>,Ta Dan turo baki ta kallesa da idonta masu kashesa."</p><p><br /></p><p>Ni bana son motar ta fada shaye da Toka, Kare matsa hnnunta yyi sae da ta Dan saki kara meyesa."</p><p><br /></p><p>Ta turo baki kawae dae ni mu koma gda."</p><p><br /></p><p>Jawota yyi a jikinsa yana kallon Dan karamin bakinta Mae gigitasa ,Idan bakiyi hnkali ba sae na tsotse bakin nan naki A tsorace ta kallesa wayyo !!</p><p><br /></p><p>"Mumin mutane fa na kallon ka ,daga kafada yyi sae meye ae ba haramun bane Kayi hkuri ka Cikani zan zaba ,kaji nan take yanayin sa ya canja " Amma daxu a gabana wani ya rungumeki bakice ya cika kiba ,sae ni saurin sakin ta yyi ya zuba hannayen sa A aljihun wandonsa ,ya koma ya jingina da jikin wata mota tamakr wani mai jin sanyi ." </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Murya can ciki yake fadin ki shiga ki zaba husna ,kinga garin akwae hadari sosae ya fada yana kallon sararin samaniya " to kazo ka zabarmin mana ! Sae ka bansan wacce nakeso ba!! Tayi mganar cike da yarinya ta gamida daga shoulders dinta.🤷</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yarda tayi mganar yasa ya zuba mata ido ,Kamar bazae yi mgana ba yyi gaba tana binsa A baya haka suka dinga ratsa motocin."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Haka ta dinga bin bayan sa ,da ido komae nasa yana burgeta batasan meyasa ba...??🤔</p><p><br /></p><p>Asmy b Aliyu.❤</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>*HEART & SOUL*❤</p><p><br /></p><p>51</p><p>Gaban wata benz-AG45 baka wuluk ,a hnkali taja ta tsaya motar tayi mata ta koina kallonta yakeyi da sezy eye's dinsa .ta maki wannan ??</p><p><br /></p><p>Daga masa gira tayi ,alamr ehhhhh...Sae ya Dan harareta ni kk dagama gira??"..</p><p><br /></p><p>Komawa tayi gefe ta harde hannayenta akan kirjinta ,gamida jinginawa jikin motar cikin siririyar muryarta take fadin,i'am sorry Mr.meera kaina bisa wuyana ,ta fada gamida langabar da kanta gefe tana kallon cikin kwayar idanunsa "Wanda take hango wani blue -blue acikin su."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tabe baki yyi gamida daga shoulder's dinsa Wanda ta lura dabi'arsa ce hakan.</p><p><br /></p><p>" Ana kawo masa key din motar ya mika mata bissimillah tayi ta bude motar yana tsaye yana kallonta komae nata burgesa yakeyi da kanta ta bude masa side din driver da ido tayi masa alamr ya shiga ,tana tsaye tana kallonsa ya shige motar .."yana duba lpiar ta tana tsaye tana kallonsa...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>1 month letter.</p><p><br /></p><p>"Hka rayuwa ta cigaba da tafia cikin wata daya abubuwa ,da yawa sun faru na shigar ta jami'ar bauch. State university ,haka ta dinga mulkin gidan AJ.duk da ynxu bata da wani tym." Haka kullum cikin fada suke da Aliya.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tsakanin ta da AJ.kuma tabasa matsayin sa na friend ,acikin wata daya ya ziyarci ,kasashe da dama fannin businesses dinsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ********</p><p>Yau ma kamar kullum tsaye take a tsakiyar dakinta ,daga ita Sae Dan karamin towel dinta sauri takeyi tana da lecture karfe 9:00@m.na safe naila ce ta hado mata tea da soyayyen kwae taja center table ta Dora ,mata akae ta Dan kalleta plzzz naila dan fitomin da kayana.</p><p><br /></p><p>Fitomin da Suite (Japaneses) ,da rufaffun talkami ,haka ta dinga bata umurni ta dauko kaza ,kaza tana gamawa ta Daura mata su akan gado."</p><p><br /></p><p>"Ta kalleta plzzz akaima hajja break fast dinta gani nan saukowa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cike da girmamawa naila ta amsa mata da to, farar powder kurum ta murxa A gaggauce ta shiga shirya kanta cikin dogon skirt baki da kuma dark blue din T.Shirt Mae dogon hnnu ta suit coat."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Gashin kanta tattara ta daure da dark blue din ribbon."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ta kalli mirror ta Dan turo baki gamida bata rae idan na dawo zansa naila tayimin ko manyan kalabane.''</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" kan bedside drower ta zauna ta dauki cup coffee din ta shiga ku'rbawa a hnkali turo kofar dakin akayi." </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana cikin hadaddun suite bakake na (Japanese's) da, bakin gilashin frada a idanunsa ,dakin nan take ya gauraye da kamshin Turaren sa na (FAAKHER MAHABBAH")...</p><p><br /></p><p>Narkakkun idanun sa ya zubamata Wanda baisamu wani isasshen barci ba sabida rigimar drama Queen dinsa Wanda takeji a ya'n kwanakkin nan ,Mr. AJ ...jirgin mufa xae daga nan da karfe goma na safe ,ya kamata ki fadamin abunda kk bukata ."?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ina jin sae nayi sati biyu gashi kuma Aliya zataga likita tun jia kike fushi dani bansan meye laipina ba."</p><p><br /></p><p>"Duk wannan mganar da yakeyi bata kulasa ba ta ,tsinci kanta cikin Rashin jin ddin tafiar sa Egypt " shida Aliya."</p><p><br /></p><p>"a hnkali ta dire cup coffee din hnnunta ko kallon wainar kwan batayi ba sae taji tama fice ,mata a rae.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" ka bawa Joseph ya karbomin malti naman,gongoni da juice'ss"</p><p><br /></p><p>"Dakin hajja AC. Ta ya tsaya acire a canja wani Duk wannan mganar da takeyi bata kallesa,ba itakanta tasan karfin hali kurum ." takeyi bataso su hada ido yaga weakness dinta.</p><p><br /></p><p>Asmy b Aliyu.❤</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>52</p><p><br /></p><p>Tattaki yyi zuwa gabanta a hnkali ta zauna kan soofa ta dauki dark blue din cover shoes,dinsa ta saka xubewa yayie dae -dae kafafunta ya dauki dayan shoe din ya saka mata,a dayan kafar nata "still bata kallesa ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Husna!</p><p>Yyi mganar cikin rawar murya ko kadan baya son yaganta cikin damuwa yana jin ciwon hakan."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dago ki kalli idona ki fadamin meye damuwarki??....</p><p><br /></p><p>Yyi mganar cikin taushin murya dago manyan idonta tayi ta saukesa acikin sexy eye'ss dinsa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cike da karfin hali take fadin bbu abunda ya sameni Mr.mumin wae meye damuwarka ne??"</p><p><br /></p><p>"Ta fada murmushi kwance a fuskarsa ta dubi agogon goal din dake manner a hnnunta ,ta mike tsaye mumin zan wuce skull ina da lecture " karfe Tara sae dae munyi wya."</p><p><br /></p><p>"Ta russuna ta subbaci goshinsa take care !! Ta fada cikin wani irin salo.",da sassarfa tabar dakin tana ko'karin maida kwallar da ta taru a idonta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>.......honey nifa nayi mmkin da matar nan tabarmu zamu tafi tare ,Dan naga tana da son kudi ne. Ba abun mmki bane aliya ,wani fanni tana da tausayi kuma na Riga na mata bayanin matsalarki ,sae kiyi mata godia ita zata dauki Responsibility din kula da lpiar ki." Itace ta hadaki da Dr .din da zakije ki hadu da shii..."</p><p><br /></p><p>"Ya kamata ki sameta kiyi mata godia,shaye da toka take kallon sa, hba Abdul jabbar kamar ni za'ace naje nayiwa yarinyar can godia yarinyar da ta gama wulakanta ni." Taci mutuncina tayimin abun da tunda uwata ,ta kawoni dunia ba'a taba tozartani hka ba."...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Allah ya kiyaye na bata hkuri wlhi bancire ran ." WATA RANA!! Arzikin ka ya dawo ba ."a kuma lokacin zan dauki fansar abunda tayimin.".</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dogon (mtswtttt) yaja bansan yaushe zaki canja ba Aliya !!</p><p><br /></p><p>"Misalin karfe goma driver yajasu zuwa air port ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ****** *******</p><p><br /></p><p>"Around 3:00pm.na rana ta fito daga lecture hall din ,nasu kallo daya zakayi mata kasan a galabaice take burinta kurum a wannan lokacin taisa gida ,tana karasawa gurin motar ta dae-dae lokacin wani Dan kyakkayawan saurayi ya karaso gabanta Wanda shekarun sa bazasu haura ashirin da biyr ba ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Rike marfin motar tayi ta kallesa murmushi dauke a fuskarta Ya aka yine farook??"</p><p>Shima murmushin yyi handouts ya mika mata Wanda xasu kai kimanin guda bakwae ,hnnu biyu tasa ta karba tare dayi masa godia canji naira Dari biyr ya mika mata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Girgiza masa kae tayi nadae gode."</p><p><br /></p><p>Farook karike Allah yabar zumunci ,murmushi yyi tareda yimata godia "back side ta bude ta saka handouts din dakuma handbag nata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" sallama tayi da farook ta shige motar ta tafice daga makarantar." Koda ta isa gida kai tsaye part din hajja ta nufa.''</p><p><br /></p><p>********* </p><p>Misalin karfe goma sha daya da rabi na dare ,tana zaune "A tsakkiyar gadonta cikin wata doguwar rigar barci dark purple Mae hawa biyu." Kanta bbu Dan kwalli sae kananun kalaban dake reto tsakiyyar bayanta .</p><p><br /></p><p>Tana aiki da laptop dinta taji karar wyarta ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mumin ne mai kiran tamkar ta sharesa ,sae kuma ta daga wyar bakiyi barci ba.??" Ya tambaya cikin sexy voice dinsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta Dan turo baki tamkar yana kallonta,banyi ba Assignment nakeyi ."daga shiga skull sae turawa mutum uban assignment's .ta fada a shagawabance,tana jin sautin murmushin sa ."daria tabasa sabida yarda tayi mganar.</p><p><br /></p><p>"Bbu damuwa my drama Queen! Dan nasan " yhu can't make it ,keep the flag flaying yanajin sautin murmushin ta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sae tayi saurin kauda zancen ta hanyar fadin ,Aliya fah??".....tana wanka amma sae gobe za taga likita ko ??maybe ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ya kamata mumin kuje tare a San meye matsalar ni kaina inason naga ya'yan abokina sun iso a dunia ,ajiar heart ya sauke kamar kinsan meye a zuciyata husna inason ya'yah kiyimin Addu'a Allah yasa muji alkahiri ." insha allahu zan tayaka da Addu'a.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tunda kinki bada damar a samu ta jikinki ba."</p><p><br /></p><p>Cike da jin kunya tayi saurin katse wyar.</p><p><br /></p><p>Lokaci daya yabi wayar da kallo gamida sakin kayataccen murmushi dae-dae lokacin kuma aliya ta fito daga bathroom din sanye da Rigar bathrobe,fara so'l lokaci daya tabisa da kallo.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*TEAM "DRAMA QUEEN..*❤</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>53</p><p> *****</p><p><br /></p><p>" shaye da toka take kallonsa ,cikin shagawaba take fadin honey bbu fa credit a wayana inason nakira mami.</p><p><br /></p><p>Kibari zuwa anjima Idan na fita zan turo maki sae ki kirata.Batare zamu fita ba?? Girgiza mata kai yyi batare zamu fitaba. Ganin likita kikazo ba yawo ba,nima businesses ne ya kawoni ,shaye da toka take fadin ynxu sabida Allah ni daya zanta zama a hotel" zancen kk so ya fada gamida mikewa tsaye ya dauki wayoyinsa ya zuba a aljihunsa yabar mata dakin ,cike da jin haushinsa tabisa da kallo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>1week latter.</p><p>★★★★★★</p><p>" Around 7:30@m na safe yana zaune a falo yana shan Ruwan lipton Aliya tafito cikin,shiga ta alfarma .kallo daya yyi mata yaga yanayin ta ya canja kusa dashi taje ta xauna ta kallesa "kamshin jikinta na fisgarsa ,Aje cup coffee din yyi ya kalleta kinyi break fast kuwa??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin sanyi murya take fadin nasha tea tabe baki yyi muje ,karmuyi late zuwa 8:00@m zaki ga Dr ." haka kawae na tsinci kaina da faduwar gaba." Ya kalleta ya kanne ido daya gamida Dan tabe bakinsa ,maybe mutuwa ma zakiyi."</p><p><br /></p><p>Yyi mganar kai tsaye a tsorace ta kallesa yyi saurin fadan yes ko kina mmki??" Idan tym.dinki yyi dole ki amsa kiran ubangijin ki!! Ko dae kinyi masa wani laipine ,da kk tsoron mutuwa??</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Agigice ta kallesa gamida ,fiddo ido tayi rau rau da idonta alamr tana son tayi kuka lallae AJ. Bayasonta wato yana fatar ma ta mutu??" Haushi ya kamata batace komae ba ta Mike tsaye ta nufi kofa,haka yabita a baya yana tsokanarta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zubama Dr.Muhammad Muhseen ido kurum yyi cikin wani irin yanayi yake kallonsa ,batareda Dr.Muhammad ya lura da hakan ba ya cigaba da yimasa ,bayani gaskiyya Mr.meera Akwae babbar matsala ."hakan sabida matarka ta dde tana zubar ,da ciki .bancin hkan kwayoyin da takesha na hana daukar cikin sun ma mahaifarta illah ba kadan ba." Wanda da wuyane ciki ya tsaya ga mahaifar tata. </p><p><br /></p><p>Zan rubuta maka wasu drugs' haka wandda insha allahu xa'a dace nan da 2 month sae Ku ka'ra dawowa ,duk wannan bayanin da yake yimasa baima jinsa cikin wani irin yanayi yaba Dr.Muhammad hnnu yyi masa godia a fusace yabar office din akan zuwa anjima zae dawo ya ka'rbi drug's din wandda shi baiga amfanin suba."Dan karshen rabuwar sa da Aliya yaxo baitaba tunanin rashin imanin Aliya har yakai haka ba."da zuri'a ma takasa hadawa dashi Allah kawae yasan cikin sa da ta zubar"zuciyarsa sae tafasa takeyi.haka idonsa ya kada yyi ja jijiyoyin kansa suka mimmike almr ransa yyi balain baci haka ya fisgi hnnunta zuwa mota ,cikin wani irin yanayi marar misiltuwa,tsoro gabadae ya dira a zuciyarta sae tunanin take me Dr.Muhammad ya fadawa AJ.bata taba ganin yyi fushi haka ba,gidan baya ya jefata tamkar wasu kayan wanki ya shiga motar a zuciya yyi reverse yaja motar da ka'rfi yabar harabar Asibitin. Cike da masifa take kallonsa wae Abdul meye haka ?? Baka da hnakali cikin fushi yaja wani irin burki ya tsaya sae da kanta ya bugu a tsorace ta rike kan nata gamida fadin wayyo Allah na!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kiyi min shuru ko in kasheki!! Yyi mganar cikin wani irin fushi haka ya cigaba da mugun ,gudu daita bata taba ganin tashin hnkali irin wannan ba gaba daya jikinta Rawa yakeyi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Suna isa harabar hotel din haka ya fisgi hnnunta zuwa Room din da suka kama." Yana bude ko'far ya wurga ta ciki gamida sa kafa ya daki ko'far ta rufe Ruf." A tsorace ta fara ja da baya 'cikin karfin halinta ta mike tsaye cike da dakewar zuciya ta fara binsa da mugun kallo wae Abdul wannan wane irin rashin imani ne?" Nifa ba baiwar ka bace!!</p><p><br /></p><p>"Tayi mganar cike da tsiwa saukar mari taji akan fuskarta haka ta kara jin saukar wani ,kamin ta Ankara ya hankada ta gamida shako wuyanta " hawaye na mugun xuba a idonsa ke wace irin macce ce a dunia??" Ya fada cikin daga murya da hargagi numfashinta taji yana barazanar daukewa gaba dae tsoro ya gama cikata ."banji zafin Abunda kikayi min abaya ba keda momy da uwarki ,nafi jin zafin wannann fiye da illar da kukayiwa zuciyata a baya! Ko kuna tunanin bansan ko Mae bane??</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kin cuceni Kin rabani da komae nawa,Dan farin cikin da yyi saura acikin Rayuwata kin kwa'ce wannnan shine son da kike fadar kina yimin ?? Yyi mganar cikin fushi..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yarda kike kashe ya'yana kema yau zan aikaki a lahira idan yaso ,na kaarasa rayuwata a gdan yari " zuciyarta taji tana Neman tsinkewa .samu tayi ta shammace sa gamida gantsara masa cizo a damtsen hnnunsa cikin karaji ya saketa ,gamida kallon wurin taji masa ciwo sosae Dan ta hado da fatar hnnunsa da gudu tayi hnyar bedroom "tana shiga ta dannama ko'far key sulalewa ,yyi akasa hawayen bakin ciki suka zubo masa ,yau koda Aliya diya'r goal CE wlhi yagama zama daita a matsayin mata."..</p><p><br /></p><p>" ku'rawa hnnunsa ido yyi Wanda jini ke ambaliya sosae tamakr ba'a jikinsa yake zuba ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"THE LOVE STORY'S NEVER END!.👄</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p>54</p><p><br /></p><p>"Cikin shesshekar kuka take fadin na shiga ukku na mami!! Kamshin dunia gaba daya bbu ddi haske ,ya koma duhu fari ya koma baki ." inason sa mami bazan jure rasa saba ,Dan Allah kiyi wani Abu akae na tuba mami wlhi bazan kara tsallake umurnin Abdul jabbar ba.</p><p><br /></p><p>"Cike da tashin hnkali take fadin mami Ashe yasan komae wlhi ya sani, cikin tsawa Hajia azumi ta katse Aliya ke dan Allah rufemin baki da shegen tsoro meya isa yyi ba abunda ya isa yyi mki sakin kine kike tsoro ki share hawayenki ki saurareni da kyau" zaman gidan Abdul jabbar daram."gobe tunda safe zan kama hanyar zuwa gurin boka,kafin Ku dawo garin nan komae zae dae-daeta. Cike da tsoro take fadin mami mekuma zakiyi masa?? Ta fada cikin Rawar murya mami inason mijina bana son abunda zae cutar dashi ,cike da lallashi Hajia Azumi ke lallashin ya'rtata bbu abunda zae faru dashi dota .wannan karon Ga kakarsa xa'a koma wanda komae Runtsi bazata yarda AJ.ya sakeki ba.wani irin ihun jin ddi ta saki tamkar ba itace ,ta shiga wani yanayi ba yanxu-yanxu."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"********</p><p> "Yana kwance A sabon Room din da Yakama yyi folding din hnnunsa a kirji yana kan selling kamar Mae tunanin wani Abu ." agogon bangon dakin ya kalla karfe biyu da Rabi na dare ,A hnkali ya sauke ajiyar zuciya dole gobe yabar Egypt ta fice masa a rae gaba daya ya kosa garin Allah ya waye Dan ya Riga yyi masu booking din flight din karfe goma na safe ,A daddafe ya shige toilet ya dauro alwalah gamida zuba milk din jallabiyarsa ya shimfida sallaya tareda kallon Alkiblar sa ,haka ya kashe wannan Daren batareda yyi barci ba ,yana kai kukansa ga mahaliccinsa akan Allah ya dae daita shi da Drama Queen dinsa." Ya kauda shaitan a tsakanin su.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wani mahaukacin bugu ta dingaji da misalin karfe Tara da rabi na safe dama kuma tana falo kwa'nce ,A tsorace ta mike zaune gamida zubama ko'far ido cike da tsoro ." A hnkali ta isa bakin ko'far murya can ciki take fadin wanene??" A tsorace tayi mganar ,Ubanki ne!!</p><p><br /></p><p>"Ya fada a tsawace wlhi idan baki bude ko'far nan ba idan nasa security guard's suka ba'lla min ita sae an kwashi gawarki sae na nuna maki na ciki zama Dan iska ,A hnkali taja da baya cike da tsoro ta bude ko'far jiki na rawa suna hada ido dashi yabita da wani mugun kallo ,wandda sae da fitsari ya kusan zubowa a wandonta ' nabaki minti biyr ki tattara tsumman kayanki ki sameni A harabar hotel ,wlhi tallahi idan kika haura koda second daya ne." Ya lankwasa ya tsunsa ,sukayi ka'ra haduwar mu bazatayi kyauba."</p><p><br /></p><p>Ya buga ko'far da karfi yyi gaba abunsa ,A tsorace tabi ko'far da kallo anya wannan Abdul dintane ?? ...A sanyayye ta koma bedroom ta fara ko'karin hada kayan su ,sae masifa takeyi mugu kawae baxa yabar mutum yyi Wanka ba." Balanta na yabari yyi sallah ,wlhi Allah xae sakamin xan ramane Allah ya kaimu gida lapia sae masifar ta takeyi."ita daya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>4 hour's latter.</p><p><br /></p><p>"Tana tsaye a kiching tana hada samosa Dan yau ita take sha'awar ci .,da misalin karfe 3:10pm.na rana kasan cewar week end ne, tana sanye cikin wandon bomshort,na blue Jean's da red din Top ,wadda ta sauka har gwiwarta Anyi mata Rubutun . *QUEEN'S*" A jikinta da farin zare tayi nisa sosae cikin aikinta sae wakar ta takesha ta Justin bebar Mae taken *Angel*,tana balain son wakar Jb. Wyar tace tayi ka'ra tana cikin nisahadin bin music din ,Dan tsaki tayi ta kalli screen din wyar ganin sunan da ke yawo akan screen din wyar A gaggauce ta wanke hnnunta cikin sink Wanda yagama cakudewa da fulawa.cike da jin ddi ta daga wayar batama lura da numbers da ya kirata dashi ba itadae kurum ta daga wyar. </p><p><br /></p><p>"Mumin!!</p><p>Ta fada a shagwabance gamida turo baki " tamkar yana gabanta ,mumin meyasa zaka kashe wya tun jia?? Tayi mganar shaye da toka ,am sowiie my drama Queen! Gamu a air port kixo ki dauke mu." Ta fiddo golding eyes nata ,da gaske kakeyi?? Cike da kosawa yake fadin bakima San da number da na kiraki bane kenan??</p><p><br /></p><p>"Da sauri ta kalli screen din wyar sae kuma ta cije lebenta na kasa' xan dae aiko da driver ya daukeku mumin ina busy ,Husna kenake so kixo ki daukemu nabaki nan da minti Ashirin banason ,musu da haka ya datse kiran" haushi ya kamata tabi wyar da kallo ..kafafunta ta fara bugawa a kasa tamkar Wata baby gal" me mumin din nan ke nufi ??.taji xata je daukarsa amma shi daya xata dauka sae dae Aliya ta hau motar haya bazata shiga motarta taba."da wannan tunanin ta nufi dakinta gamida kashe cooker ga's din.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_"Fatan Alkhairi Asma'u Abdul Jabbar_..❤</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>55</p><p><br /></p><p>"A hnkali tayi parking motar ta A gurin na mussaman da aka tana da Dan parking din motoci Acikin air port, din.</p><p>Cikin takunta na kasaita ta fito daga motar.</p><p> Tana cikin shigar Doguwar rigar Arabian gown ,dark blue a gaban rigar a masa ,ado da stones work masu kya'kyalin gaske,sae Dan karamin veil baki da tayi rolling kanta dashi glass din frada ne manne a idonta.</p><p><br /></p><p>Ta fito rike da wayr ta ,ta shiga Neman layin mumin haka ta cigaba da Neman layin batareda ya shiga ba ." juyawa tayi a hnkali ta fara tafia."</p><p>"Acikin Air port din duk inda ta taka ka'fa sae anbita da ,kallo abunda ta tsana kenan.</p><p><br /></p><p>" A hnkali taja tsuka cigaba da tafia tayi tana Neman layin mumin,</p><p>Jin tayi anyi hugging back nata.</p><p>A tsorace ta juya cikin wani irin salon ya riko waist dinta ya juyo daita tana fuskantar sa ,ya ka'ra manne ta a kirjinsa.</p><p>,har tana jin bugun zuciyarsa saurin kwa'tar kanta tayi gamida Dan ja da baya.</p><p>"Tana maida numfashi hnnun sa ya sa'ka gamida zare gilashin idanunta,suna hada ido ya kashe mata ido daya.</p><p><br /></p><p>Sae taga ya ka'ra yi mata wani irin kyau,</p><p>Yana cikin farar shadda dinki (Hilton)" bbu hula akansa ,sumar nan tashi ta kwanta luff"as usually ,tamkar</p><p>Ta larabawa harde hannayenta tayi akan kirjinta ta Dan hararesa gamida ,hararar sa.</p><p>Baka tsoron matar ka tagan ka,nan take taga ynayinsa ya canja juyawa yyi yabi wata hanya ,da sassarfa tabi bayansa tana kiran sunan sa ,</p><p>Banza yyi mata gurin Aliya taga ya isa ya dauki ka'ramar trolley dinsa ganin hka itama Aliya ta mike jiki sanyayye itama ta dauki jakar kayanta.</p><p>,suna hada ido da Asmy tayi saurin dauke idonta."</p><p>Tayi gaba abunta yyinda AJ .yake binta da ,mugun kallo Allah Allah yake su isa gida ,Dan sunyi wya da Aunty sadiya itama tana hnyar zuwa gdan.</p><p><br /></p><p>"Tana tuki tana kallon yanayin sa gaba daya, yabi ya hade rae a hka suka isa gda.</p><p>Aliya ce farkon fita shima xae bude ,marfin motar tayi saurin riko hnnun sa,na dama nan tayi tozali da bandejin dake manne ,A hnnun sa.</p><p>Cike da tuhuma ta kallesa,Alamr tambaya kwa'nce akan fuskar ta ,cikin sanyin murya take fadin mumin wae meke faruwa ne??</p><p>" Rabuwar mu da Aliya yazo husna kiyimin Addu'a Allah yasa haka shiyafi Alkahiri ,bana son ta ka'ra awa daya a gdana."</p><p><br /></p><p>"Gabanta taji ya fadi me mumin ke nufi ? Badae ya ruguza masu plant ba.,baijira mai zata fadaba ya ba'lle marfin motar yyi gaba abunsa,yyin da security's guard ,din suka kwashi kayan su suka nufi cikin gdan."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>,Da sassarfa ta cimmasa falo tasha gaban sa ."cike da tashin hnkali take fadin wae meke damunka??</p><p><br /></p><p>"Tayi mganar gamida bude masa, manyan idonta ,mekikaji na fada maki. Shima yyi mganar a tsawace I don't need her in my life any more...,saboda hka I want to divorce her.!.</p><p><br /></p><p>" A fusace ya ra'ba ta gefenta ya nufi up stair's.</p><p>Cike da tashin hnkali ta zube gwiwowin ta ,kasa.[Truncated by WhatsApp]</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p>56</p><p>Sae da ta murzawa ko'far bedroom din nata key sannan ta dauki wyar mamin ta,</p><p>Cike da tashin hnkali take fadin mami !! Ta fada cikin,rawar muryar ki kwantar da hnkalin ki Aliya na fada maki bazaki bar gdan AJ. ba kixuba eye's naki ,kisha kallo an turawa kakarsa baka'r aljanah."</p><p> Kwa'llar da ta taru a idonta ,tayi saurin gogewa da Dan yatsan ta,gamida sakin kya'taccen murmushi mami ,yaushe zaki kawomin ziyara?? Tayi mganar a shagwaban ce, zuwa jibi insha allahu .ajiar heart ta sauke anan tayiwa mamin nata sallama ,rage kayan jikinta tayi ta nufi bathroom.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*****</p><p>Gaba daya family member's din nasa ana a babban falo ,dama idan ana wani muhimmin taro anan sukeyin sa ,mom tunda ta shigo falon taji zuciyarta ta tsinke " cikin takun sa na kasaita ya shigo falon yana cikin shigar ka'nanun kaya ,</p><p>Farar T.shirt ce mai guntun hnnu ,da bakin wandon Jean's " fuskar nan tasa ko kadan bbu walwala ,itakam Hajja binsa kurum take da kallo Sallama yyi masu ga badaya suka amsa sa ,itakam Asmy gaba daya jikinta yyi sanyi."</p><p><br /></p><p>"Aunty sadiya ce ta bude taro da Addu'a cikin sanyin muryarsa AJ.ya fara kora bayani tun daga ranar da yaji Mom da Aliya na ko'karin zuba masa magani a Lipton,har kawowa ranar da yaji ya tsara plant akansu akan yasha ,da zuwan sa kano da Aurensa da Asma'u har plant din da suka hada dasu hajja dasu Aunty Sadiya Abu daya yasan ,ya boye contract marriage dinsa da Asmy."</p><p><br /></p><p>"Wandda wannan sirrin sane ,acewar sa.</p><p><br /></p><p>" Cikin fushi ya fara mganar ganin likita da sukaje ,shida Aliya akan abunda yace akan ta ,Dan haka mom na baki nan da minti talatin ki kwashe komae naki kisan inda dare yyi maki " Idan ba haka ba hukuma ce zata rabani dake, dukiar daddy an baki kason ki so ,bama bukatar ki acikin zuria'r mu ,sa'annan ya maida kallonsa kan Aliya wadda hawaye ya gama wanke mata ,fuska wani irin kishine ke cinta dama da kishiyarta take zaune bata sani ba." Dama kishiyar ta ce ta wulakanta ta haka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Aliya na sake ki !</p><p>Saki daya ,Allah ya haramta saki ,lokaci daya da wlhil azeem ukku zan baki ,amma kije I hate yhu Aliya ! I so much hate yhu!......saukar mari yaji akan kyakkyawar fuskarsa ,A tsorace ya daga manyan idanunsa yana kallon wadda ya masa, wannan aika aikar ,Ga mmkin sa grannyn sa yake gani tsaye a gabansa tana wani irin huci " karo na farko a rayuwarsa da kakar tasa ,takai hnnun ta jikinsa,Da sauri Asmy taxo tasha gaban hajja "Sae taga hajja nayi mata wani mugun kallo wandda takasa ,fassara sa."</p><p><br /></p><p>"Cikin fushi take fadin muddin Aliya tabar gdan nan to na Rantse maka da Allah ka'fata ka'farta ,hka kuma bbu ni bbu kai har abada ." haba Abdul yaushe zakayi hnkali ne?" Kodan irin son da yarinyar nan take yimaka ,yaci ace kayi mata afuwa "A tsorace ya fara jada baya ,rike da fuskarsa hka hawaye ke tsiyayowa acikin ,kwayar idonsa Aunty sadiya tayi saurin kallon Hajja a tsorace."</p><p><br /></p><p>Cikin rawar murya ta fara mgana hajja meye haka?" Daga mata hnnu tayi sadiya bana son doguwar magana ,nariga nagama mgana in kuma kuna ganin ban isa daku ba bissimillah ga fili ga mai doki ,tana fadin hka taja hnnun Aliya sukabar falon ,A hnkali yaji duniar na juya masa wani irin tsoro ya dirar masa a zuciya ,wandda bai taba jinsa ba tsawon rayuwar sa ,A hnkali aunty sadiya ta fara tunkaro sa."</p><p><br /></p><p>Yyi saurin dakatar daita ,plzzxzz aunty sadiya karki nufoni "shin menayi wa hajja a rayuwa ,da zatayi min wannan hukuncin ??" Ya fada yana ya'rfe hnnunsa ,da gudu Asmy taxo ta rungumesa ga gam" ga mmkin ta Sae taga ya turata da karfi baya -baya tayi zata fadi da Sauri Aunty sadiya tayi saurin tarota a tsorace,</p><p>"Da gudu yabar falon hawayen Idonta suka kasa tsayawa ,aunty plzzz ki tsaida sa kar yaje yyi ma.</p><p>Kansa illah plzzz ,ta fada gamida zubewa a gabanta tareda folding din hnnun ta.</p><p>Tana zubar hawaye.......@t 7:38pm.by Asmy b Aliyu😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p>57</p><p> "Tuki yake hawaye na mugun zuba a idonsa ,haka zuciyarsa na wani irin tafasa kai tsaye " Guest in din shi ya nufa dake New G.R.A."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kuka take kamar ranta zae fita Aunty sadiya na xaune a gabanta tana famar lallashin ta,itaama gaba daya jikinta,yyi sanyi wannan wane irin rikici ne ya same su haka?</p><p><br /></p><p>" layin sageer ta shiga nema baya shiga haka ta koma kan Layin mumin still a kashe.</p><p><br /></p><p>Aunty sadiya ce zaune a gaban hajja wadda ke shan kayan fruit ,a tsorace take kallon mahaifiyar tata ,cikin rawar murya da kwantar da kae take fadin hajja meyasa kikayi haka??" Anya kuwa hajja kice? Kinsan irin halin da kika saka Abdul jabbar yanxu?</p><p>Saurin dakatar daita hajja ,tayi sadiya sau nawa xan fada maki bana son yawan mganar nan nariga na gama ,mganar nan so in dae na isa dake kibar ta daga ynxun nan ,shi kuma baisa ya canja min mganata ba ..idan ya kwantar da hnkalin sa na tabbata "WATA RANA! Aliya zata cika gdan sa da ya'ya Allah ke bada haihuwa ga wandda yaso baisan sharrin likitoci bane ,ya'n karyane to ita Asma'un da yake so uban meye take jira ne."</p><p>Har yau da bata dauki ciki ba a gdan sa." watan su nawa da aure ae in adalci akebi ya sake su duka"..cike da jinjina al'amarin aranta Aunty sadiya ke kallon mahaifiyar ta bbu kwa'rin gwiwa tayiwa hajja sallama ,Dan bataga wurin zama ba ."wannan maganar tafi ka'rfin ta drivernta tayiwa wya akan yaxo ya dauketa Addu'a take aranta kar ciwon Abdul ya tashi."</p><p>Bbu komae hajja Allah yasan ya alkhairi nixan koma ,Allah ya kiyaye hanya ,da haka hajja ta maida hnkalin ta kan T.V.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tana tsaye a tsakiyar falonta sai zagaye falon take ga waya a hnnunta,ta dubi agogon bangon falon 8:30pm.na dare bbu lbrn AJ. Hankalinta yyi balain tashi batasan wane irin hali abokin ta yake ciki ba ,A hnkali ta saka bayan hnnunta gamida goge siriran hawayen . da suka xubo akan fuskarta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wyarta CE ta shiga ka'ra da sauri ta kalli screen din wyar ,</p><p>Sunan sageer ta gani cikin rawar murya ta daga wyar cikin fashewa da kuka take fadin sageer ina mumin ya shiga tsawon wannan lokacin ?".bae tabayin hka ba sageer bae taba kashe wayan saba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ta fada cikin muryar kuka Fadamin Asma'u meya samesa ??"... Da alamr sageer baesan komae ba ,anan ta zayyana masa abun da ya faru." shima tashin hnkalin sa ya ka'ru anan ya shiga kwantar mata da hnkali ki daina daga hnkalin ki Asma'u ba abunda ya samesa,sageer taya kakeso na kwa'ntar da hnkali na?"</p><p><br /></p><p>"Lokaci daya komae ya lalalace,mumin baya daukar shawara " ban San mexan yiba ,sageer "just Relax,bani minti goma sha biyar gani nan zuwa da haka,</p><p>Ya datse kiran."</p><p><br /></p><p>"Sageer kana ganin zamu samesa a guest in din nasa kamar yarda ka fada insha allahu."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Horn ya dinga dannawa da sauri buzu ya leko " ganin sageer yasa ya washe baki,ahhh maigida Kaine?" Uhmm ....Mln lado Abokina na ciki??" Dan jimm ,,lado,yyi saurin katse masa tunani sageer yyi da sauri lado yace ehhh maigida "tun kafin magrib yana nan ,amma yace duk wandda yaxo ka'r nace yana nan."</p><p><br /></p><p>amma tun da kai ba wanin bane,bissimillah haka sageer ya koma mota" yyinda Lado ya wangame masu ,katotuwar get din ya danna hancin motar tasa aciki."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A hnkali sageer ya sauke ajiyar zuciya ganin ,ko'far falon a bude " cike da faduwar gaba suka danna sallama falon Tozali sukayi dashi kwa'nce a tsakiyar falon" abunda suka gani yyi balain tsinka masu zu......!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>The Love store's never End!</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>58</p><p><br /></p><p>"Cikin wani irin yanayi suka nufi ,Shifa Royal hospital " suna isa Asmy ta ba'lle marfin motar da karfi ta fito,</p><p>Ta nufi cikin hospital din Agigice tana kwa'lawa likitocin kira da Sauri aka daukosa xuwa "Emergency, da sauri Asmy ta tari wani Dr.da yafito dakin da aka aje AJ.</p><p><br /></p><p>" Dector saurin katseta yyi tareda yin gaba Abunsa ,zafafan hawaye ne ,suka shiga gangarowa akan Fuskarta addu'a takeyi aranta Allah ya tada kafa'dun mumin.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kusan Awa hudu likitoci kusan shidda ne ." A kansa.</p><p><br /></p><p>" Around 10:30pm.na dare suna tsaye a kofar Room din da yake ,Dr.kamal ne ya fito yana share gumin da yake tsiyayo masa akan fuskarsa,</p><p>Da farin hankicif da sauri sageer yasha gabansa ,Dr. Kune kuka kawosa??"</p><p>Cikin hadin bakin ,lokaci daya Asmy da sageer suka amsa ma Dr.kamal lokaci daya " ganin sun amsa atare sae ya kallesu gamida sakar masu ,murmushi." Karku damu marar lpian Ku xae samu sauqi ,Amma yana buka'tar jini sabida ya zubar da jini da yawa,sakama kon Aman jinin da ya ka mayi tsawon wani lokaci,so ku biyoni office."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dama kunsan yana da ciwon zuciya kuka nemi daga masa hnkali ??,wani mummunan abune ya samesa da har za yyi fushi irin hka??" Da Baku yi gaggawar kawosa ,hospital ba da xae iya rasa rayuwar sa."Duk da rayuwarsa ba hannun mu takeba.,Amma a yanayin da yake ciki,da sauri Asmy ta katse sa "plzzz Dr.ka gwada jinina idan xae yimasa??</p><p>" tayi mganar cikin rawar murya hawaye na zuba a idonta.</p><p><br /></p><p>Saurin girgixa kai yyi baxa ayi haka ba Mrs.Meera sae idan ba'a samu na namiji ba,okey tom.Dr.ka gwada nawa mana,cewar sageer anan Dr.kamal ya hada sageer da wani likita suna barin office din Dr.kamal ya juyo kan Asmy sae taga yana yimata wani irin kallo wandda ta kasa fassara sa ,tsam ya taso kan kujerar da yake zaune Mae juyawa ya dawo gabanta gamida Dan rage,tsawon sa."</p><p>Bugun zuciyar ta taji ya ka'ru haka taji ka'mshin turaren sa ya cika mata hanci,masha allahu!! idan nace ke kyakkyawa ce zaki yarda??"</p><p><br /></p><p>"Yyi mganar cikin sexy voice dinsa mganar sa takeji har cikin ranta ,Dara daran idonta ta dago ta kalli cikin idonsa.....wasu irin kibiyoyi take hangowa acikin kwa'yoyin idanunsa,wandda bata taba ganinsu acikin kwa'yar idanun ko wane namiji ba " ko Emran da taso ta raini son sa a zuciyarta bata taba ganin idanun sa haka ba."mumin Dama ba'a mganar sa bata taba kallon cikin idonsa,kai tsaye ba ."A tsorace ta mike tsaye jikinta na rawa haka kirjinta na wani irin bugawa Wanda bata taba,jin makaman cin saba." A tsorace ta juya xata bar office din sae yyi saurin rike mata gefen doguwar rigarta."@t 8:30pm.by Asmy b Aliyu.</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>59</p><p><br /></p><p>"Tsam ya mike tsaye gamida ka'rasowa gabanta cikin raunayiyyar muryarsa Mae kasheta ,yake fadin plzzz karki tafi Dan Allah " Ya fada gamida zuba mata narkakun idanunsa.</p><p><br /></p><p>"Wat do yhu mean dector?? Ta fada cikin kakkausar murya ,kawae natsinci kaina a hka nima bansan meke damuna ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Plzzz I'am not in the good moon plzzz excuse mee, ka're tare ko'far office din yyi da mmki take kallonsa jikinta ko ina ,rawa yakeyi batason jin muryarsa ." bcoz muryar nasa na saka ta faduwar gaba da jin wani irin yanayi."</p><p><br /></p><p>"A fusace ta bude masa manyyan idanunta ,Are yhu out of your mind nifa matar aure ce ,baka tunanin shaidan ya shiga a tsakanin mu mun kebe ,Mu daya ." bbu abunda xae faru Asma'u bbu komae a zuciyar kamal sae tsaftattaciyr soyayyar ki plzzz kibani Dama ,cike da tashin hnkali ta daka masa wata irin tsawa cike da tashin hnkali take kallonsa,baka da hnkali baka da tausayi baka da imani,kai wani irin mutun ne ??" Mijina yana kwa'nce a gadon Asibiti kake waya'nnan mganar muguntar ka bazata taba'yin tasiri akaina ba ,idan Asibitin kakeso ,zamubar maka ynxun nan ba gobe ba!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hanyar fita ta nufa yyi saurin fisgota ajikinsa tana jin wani iri bugu da zuciyarsa keyi ya rikice jikinsa sae rawa yakeyi tsoro da mmki ya cikata ,bata taba haduwa da wannan kaddarar ba."</p><p><br /></p><p>"Karfinta tasaka ta turesa ,wani mugun kallo ta dinga watsa masa ,nan take hnkalinsa ya ka'ra tashi muddin baisa meta ba komae xae iya faruwa ." dashi wannan wace irin kaddara ce ta samesa haka ,meya kaisa son matar Aure kodan ya wulakanta ya'mmata da dama shiyasa wannan kaddarar ta fa'da masa..." A hnkali ta ra'baa ta gefensa ta wuce tana sharar kwa'llah ,A hnkali ya zube ka'sa tareda dafe kansa ....</p><p><br /></p><p>Ya kwashi kusan minti goma A hka da kya'r ya mike tsaye ya nufi Dan karamin fridge dinsa,key ya saka ya bude fridge din Kwalaben beer ne ,masu tsadar gaske kwa'ra daya ya ciro ya rufe fridge din da sassarfa ya nufi ko'far fita daga office din ,karo sukaci da Dr.Habib tsayawa yyi cak! Yana kallon Abokin nasa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ganin kwa'lbar beer A hnnunsa yasa ya kallesa ,A tsorace."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ina zakaje kuma kamal ??" Yyi mganar cikin Rawar murya ni kaina ban saniba." habeeb!! ina kuma zakaje da beer ,look kamal ka tsaida hnkalin ka guri daya ,kana da marar lapia A hnnu . kaga kuma yanayin da yake ciki shine zakaje kasha abunda xae saka ,</p><p><br /></p><p>" kafita hnkalin ka idan ka kashesa fah?? </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Enough is a Enough! Habib! Ya katsesa cikin wata irin mahaukaciyar tsawa!!</p><p><br /></p><p>zasu iya canja hospital bana jin zan iya dubasa." am sorry leave me a lone , </p><p>Da haka yasa kai ya fice daga office din A zuciya cike da tsoro da mmki Yabisa ,da kallo</p><p><br /></p><p> " duk yarda akayi akwae abunda ya faru haka kawae baxaiyi fushi haka ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tana tsaye a ko'far Room din taga yana tahowa cikin,takunsa na kasaita da sauri ta dauke kanta."</p><p><br /></p><p>" shima bai kalleta ba ya wuce abunsa." Amma sae da taji bugun zuciyarta ya ka'ru ina kuma zayaje??" </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ta tambayi kanta.</p><p>Shine kuma ka dai likitan zuciya a Asibiti nan ,kuma dr.Habeeb ya tabbatar mata dashi xaeje ya saka masa jini ynxu,</p><p> "Takasa daurewa da gudu tabi bayan sa tana Dan kwa'la masa kira....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*SHOCK LOVE*!!</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>60</p><p><br /></p><p>"Da sassarfa ya isa parking spaces dae-dae gurin motarsa yaja ya tsaya ,ganin tasha gaban sa." Baiyi aune ba yaga ta zabga masa mari akan kyakkyawar fuskarsa ,Marin tunda yaxo dunia bbu wani Wanda ya ta'ba yimasa makamancin sa.</p><p><br /></p><p>Cike da masifa ta cakumi ,wuyan rigarsa cikin kuka take fadin meka keji dashi ne??,</p><p><br /></p><p>meka dauki kanka idan mumin ya rasa ransa baxan ta'ba yafe maka ba saukar hawayen ta yakeji tamkar ana zuba masa Ruwan ,dalma acikin zuciyar sa.</p><p><br /></p><p>"A hnkali ta sakesa ta Dora kanta a jikin motar gamida fashewa da kuka sosae."</p><p> Gaba daya Kamal ya rude ya fita hayacin sa ,</p><p><br /></p><p>saurin bude back sit yyi ya saka beer din tareda rufe ma'rfin motar."</p><p><br /></p><p>Dago fuskarta yyi a tsorace tayi saurin ja da baya, karka ka'ra ta'bani da wannan haramtaccen hnnun naka."</p><p>Am sorry kinji ki daina wannan kukan Dan Allah ,</p><p>ya fada cikin cool voice nasa.</p><p><br /></p><p>"Muje na dubasa hawaye na zuba a idanunta ta kallesa kayi alkawari?? </p><p>"Ta fada cikin Rawar muryar ta ,idonsa na akanta a hnkali ya daga mata kai Almr Ehhhh''</p><p><br /></p><p> komae nata burgesa yakeyi gaba tayi yana biye daita har Room din da aka kwantar dashi ya Dan juyo ya kalleta,</p><p><br /></p><p> "kijirani anan da haka ya juya ya shige dakin .</p><p><br /></p><p>Yyin da ta juya ta nufi dakin sageer."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kusan 11:30pm.na dare ya shiga danna wani ,irin horn na fitar hnkali ,agigice Hassan maigadi ya Dan leko ganin kamal cikin wani irin yanayi ya wangale ,ka'totuwar get din ...</p><p><br /></p><p>.wani irin parking yyi ya fito a hnkali Sae famar layi yakeyi A hnkali Hassan ya ka'raso gurinsa cike da jimamin hali irin na kamal,</p><p>" bai rasa komae ba a dunia.,halinsa dayane da baya da kyau shine ,shan giya " A hnkali ya Rika sa xuwa part dinsa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Har dakin barcin sa ya Kaisa tareda Dora sa akan katon Royal bed nasa Mae black&white ,</p><p><br /></p><p>"har Hassan ya nufi ko'far fita cikin wani irin yanayi " Kamal yyi saurin fisgo Hassan Sae ga Hassan akan fa'deden ki'rjin kamal ,A tsorace Hassan ya bude idonsa "Fuskarsa ya fara shafawa </p><p>" cikin cool voice nasa ta mashaya ya fara fadin "Am sorry Asma'u karki gujeni ina sonki ina matukar kaunar ki!!</p><p><br /></p><p>" Soyayya ta bata karya bane,banta ba son " wata macce A dunia ba bayan ke plzzz ,karki gujeni kibani dama zan koya maki yarda zaki soni ,</p><p>"A tsorace Hassan ya janye jikinsa cikin na kamal ,yabar bedroom.din da sassarfa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*******</p><p>"Alh.Muhammad Alkali tsohon alkaline a jahar Bauchi kuma ,dan siyasa Wanda ya Rika muka Mae da ,dama Haka yana da dukia Mae tarin yawa da,matar auren sa.</p><p>Kw'ara daya ,Hajia Asiya Dan su kwa'ra daya a dunia dr.Kamal matashin saurayi mai kimanin shekara talatin da biyu A dunia ,</p><p>" Ga ba daya iyayensa sun dauki son dunia sun Daura masa kasancewar sa,</p><p>D'a kwara daya da Allah ya basu ."da ganan Hajia Asiya bata ka'ra koda yin ba'ri ba ."haka yasa suka dauki son dunia suka do'ra ma kamal tun yana karamin sa yake sha'awar zaman likitan zuciya, sabida Ammin sa na da ciwo haka iyayyen,sa suka taimaka masa ya cika burinsa." Na zama babban likita yyinda A indian ya gama karatunsa" </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wanda shi ya cikgaba da kula da mahaifiyar tasa,</p><p>kamal kyakkayawa ne ajin farko haka ruwan tarwada ne ,yana da manyyan idanu masu daukar hnkali haka yatara suma a kansa ,wadda ake kashe kudi sosae gurin gyaranta ,sumarsa sak !zubin sumar hausawa ne ,baka kirin mata da yawa sonso kamal ya'yan masu kudi ya'yan amininan Abban sa amma fi'r yaki asalima ya tsani maccen da zata nuna masa ,zalamar ta A fili iyayyensa sunyi fada har sun saka masa ido."</p><p><br /></p><p>Sae dae Addu'a akwae wata ya'r aminin Abban sa ,a Kaduna suke zaune sunan ta zaliha "tana matukar son kamal ,Amma shikuma bbu wadda ya tsana sama daita ,Tana yawan zuwa gidan su hutu sabida shi amma har ta ka'rasa hutun ta baya ku'lata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wani abun mmki Na kamal baya Neman mata ,bai ta'ba kusantar zina ba .</p><p>Halinsa dayane shan beer da itace yake Rayuwa tun yana A India har ka'wowa ynxu ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wanda iyayensa,basu Masan yana Shanta ba "tsawon shekera biyu kenan Sae maigadin gdan su" Wanda yake matuka'r tausayin kamal ba ,bayada wani mummunan hali wandda ya wuce wannan."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dan kamal akwae kirki baya kya'nkyamin talakka da kyauta ,abokinsa kwa'ra da'ya ne a duniya shine Dr.habeb bayada wani aboki Wanda ya wucesa ,Habeeb yyi balain sanin halin kamal fiye da iyayen da suka kawosa,A dunia.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Idan yace yes bbu Wanda ya isa, ya canja sa hakama idan yace nooo bbu Wanda ya isa yyi musu dashi." Lokaci daya Asma'u Omar omra ta fado acikin Rayuwarsa,</p><p>Tareda birkita masa tunanin sa kwata -kwata ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Shine mutunen da tafara tunkara da bukatar ta lokacin,da suka kawo AJ.hospital din ,Wanda kallo daya yyi mata yaji zuciyarsa tayi wani irin halbawa ,nan take ya rude gamida.</p><p>Rasa natsuwarsa .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>.******</p><p>" A hnkali yyi sallama A bban falon yana cikin shigarsa ta manyan likitoci ,kallo daya xakayi masa kasan baya cikin natsuwar sa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dattijuwa ce wadda shekarunta baxasu haura Hamsin ba A dunia ,Tana tsaye akan dinnig " Table suna jera kayan break fast "Tana sanye ne cikin medical glasses ,mai ka'ra mata gani ."</p><p><br /></p><p>"Ta kallesa Wanda yake ko'karin zama daya daga cikin kujorun dake ,zagaye da Falon saukowa tayi akan stairs din dinning din tareda ,Tahowa garesa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin sanyin muryarsa ,yake fadin sabahul khair my Ammi!!</p><p>Cikin murmushi take fadin ,sabahun Noor my son!</p><p>,da fatan katashi lpia??Qlau Ammi kayi shirin fita kenan?</p><p><br /></p><p>" daga mata kai yyi Almr ehhh kasan cewar kamal ,mutun ne marar son mgana ."ammi Abba fa??</p><p><br /></p><p>Yana sashen sa baita shiba, kaxo kayi break fast ynxu Salamatu "tagama hada mka break fast ,kamr tasan xaka fita da wuri ya tsine fuska yyi bana jin xan iya cin komae Ammi ,idan naje zansha coffee inajin kaina cikin wani irin yanayi,</p><p>Plzzz Ammi kiyi min Addu'a ya fada gamida sunkuyar da kansa kasa,</p><p><br /></p><p>" A hnkali Ammi ke ka're ma Dan nata kallo Tana matukar tausayin sa,baya taba fada mata damuwarsa ."</p><p><br /></p><p>Yana da zurfin ciki sosae insha allahu zan maka Addu'a da murmushi ya dago ,ya kalli mahaifiyar tasa gamida,</p><p>Fadin nagode My Ammi"</p><p><br /></p><p>Ka'rasowa yyi gabanta ya Dan russuna ya subbaci ,goshinta tayimai addu'ar Allah ya kiyaye hnya.</p><p><br /></p><p>"Har ya kae bakin ko'fa ya juyo ya kalleta plzz Ammi ki gaisheda Abba idan ya tashi barcin ,kifada masa nafita idan ya tashi,zan kirasa." Cike da jin ddi ta daga masa kae cikin sassarfa ya fice daga falon ,</p><p>Cikin takunsa na kasaita."</p><p><br /></p><p>Asmy b Aliyu Novel's😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu. "</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>61</p><p>"Around 8:00@m dae dae na safe ya turo ko'far dakin hangota yyi kan farar kujerar roba.</p><p>Gafda gadonsa ta Dora kanta gefen jikinsa tana barci ,wani irin kishi yaji lokaci daya ya rufesa.</p><p>" da Sauri ya juya gamida bugo ko'far dae-dae kuma lokacin AJ ya fara motsi,</p><p>Sannu "A hnkali ya soma bude idanunsa."</p><p> "Dake yimasa nauyi da kya'r ya samu,ya budesu duka fara kallon da'kin yyi.</p><p>Jin mutum kusa dashi ,ya maida hnkalinsa gurin zuba mata ido" yyi tayi rama sosae haka yaga hawaye na zuba gefen Cheek's nata .</p><p><br /></p><p>"Hnnunsa,yasa ya Dan kara kwan'to daita ajikinsa a tsorace ,ta bude idonta dama ba barci Mae nauyi bane" Dan kamal ya sanar mata kowane tym"...xae iya farkawa.</p><p><br /></p><p>"Ido biyu sukayi dashi A zabure ta tashi daga jikinsa tareda rike hnnunsa ,gagam cike da murna take kallonsa ,Murya ka'sa ka'sa ta furta mumin!!</p><p> " saurin Daura ya tsansa yyi akan kyakkyawan bakin ta almr tayi ,shuru cike da murna ta nufi office din Dr.kamal sallama tayi ta ji shuru,</p><p>Ba'a amsata ba yasa tayi knocking</p><p><br /></p><p> "murya can ciki yake fadin ,yes come in.......aranta tace Dan rainin hnkali bude ko'far office din nasa tayi ta tsaya A bakin ko'fa tana kallonsa ,yana ku'rba coffee shaye da toka take fadin plzzz kazo mijina ya farka</p><p>" tana fadin hka ta juya da sauri tabar office din"har tana hadawa da tuntube,</p><p>murmushi kamal yyi gamida Shafa sajen da ya kewaye kyakkyawan fuskarsa,tsam ya Mike gamida aje cup coffee din yabi bayanta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"'Ko'karin tashi yakeyi tayi saurin dakatar dashi karka motsa mumin kabari ,likita ya shigo mana, ya Dan kalleta cikin jin zafin ciwo nagaji da kwan'ciyar ne husna At all." </p><p>Sae taji ya bata tausayi hnnunsa,Na dama ta rike gamida hadewa ,da nata karka damu zaka tashi ynxu ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dai-Dai lokacin kamal ya turo ko'far dakin nasa cikin tsinkewar zuciya ya isa garesa da sauri Asmy ta saki hnnun sa,gamida Dan ja da baya ta harde "hannayenta a kirji tana kallon Kamal ,</p><p>Wanda ya fara duba AJ.cikin sanyi jiki " fuska bbu walwala kamal ya cire masa drip ,din hnnun sa.</p><p><br /></p><p>Ya kalleta ,shaye da toka yake fadin kiraka sa toilet yyi wnka koxae ji ka'rfin jikinsa tareda rama sallolin dake kansa,"daga baya sae yyi break fast.sae nabasa drug's nasa."</p><p><br /></p><p>"Batare da takallesa ba ta nufi AJ,Right hand nata tabasa alamr ya rika" zata taimaka masa ya tashi bbu musu ya Mika mata hnnun nata,</p><p><br /></p><p>"ga mmkinta sae taji takasa dagasa a shagwabe ta kallesa gamida turo baki kae dan Allah mumin kabar sakar min jikinka duka mana."...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Suna hada ido da kamal ,sae taga ya watsa mata harara itakam murmushi ta saki gamida kashe masa ido,daya</p><p> batayi aune ba taji AJ ya jawota gaba daya akan jikinsa</p><p> " ware Golding eyes ,nata tayi akansa "sae taga ya daga mata gira ,cikin murya Rada ya sunkuya dae -dae kunnenta " plzzzzz kidaina zama a gaban likita haka bana jin ddin yana kallamin ke .</p><p><br /></p><p>"kinemi hijab ki saka Dan Allah!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yyi mganar A raunane bakin ta tasaka dae -dae gurin bakinsa takama,leben sa na ka'sa</p><p>'</p><p> gamida Dan cizasa da gudu ta sauka jikinsa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" A zuciya kamal yabar dakin tabi bayansa da kallo gamida Dan ta'be baki "</p><p> ta juyo kan mumin ,yana ko'karin mikewa tsaye tayi saurin taimaka masa cike da mugunta ya sakar mata nauyinsa duka ,wayyo mumin!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Gaba daya suka zube kan bed lokaci daya,</p><p>shine a saman ta.</p><p>"</p><p> ware manyan idonta tayi a kansa dakyar ta buda baki tana fadin ,xaka karyani Dan Allah wlhi nauyi ne dakai duk da kana kwance a gadon asibiti,tayi mganar a shagwancen ,gamida turo bakinta,</p><p><br /></p><p>Cikin wani irin salo ya'ke fadin waye mai nauyin??..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" kai mana ta fada cikin sauke numfashi dakyar ,Rumfa yyi mata da fadeden kirjinsa yana kallon fuskarta ,wadda tsoro yagama cikata hnnunsa ya aza akan bakin ta yana masa tafiar tsutsa .</p><p><br /></p><p>"dae-dae lokacin kuma aka banko ko'far a hnkali ya maida hnkalin sa ,kan ko'far yaga waye mai wannan aikin?"</p><p>Bbu sallama ,bbu Neman izini a shigo kai tsaye ido biyu sukayi da Hajja da Aliya dake bayan ta ,dauke da babban basket......saurin dauke kansa yyi gamida mikewa ,tsaye a hnkali ya dago Asmy hnnunsa "...sakale cikin nata ya nufi hanyar bathroom daita.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" saurin shan gabansu hajja tayi a tsorace Asmy ke kallonta yyinda taga gogan nata ya wani,dauke kae gamida ba'ta Rai sosae......</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Thank's</p><p> for the impression."</p><p> and Advocated,</p><p>My Enormous fan's!😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>62</p><p> "Shaye da toka hajja ta kallesa ,muxo dubaka shine zaka wulakantani Abdul jabbar!.</p><p> ,yaushe ka sauya dabi'unka??" Cikin sanyi muryarsa ta marasa lpia yake fadin kiyi hkuri hajja inaso in watsa ruwa ne.</p><p><br /></p><p>Da hka yaja hnnu na batare da ,ya jira Mae hajja xata fada ba muka nufi bathroom jiki sa'bule Aliya tabi bayan su da ka'llo hka kwa'llah ta taru a idanunta ,cikin fushi ta kalli hajja tamkar wata sa'arta kina ganin ko kallona baiyi ba ."sabida ya tsaneni matarsa ,ta Riga ta gama mallakesa kema ynxu bayajin mganar ki .</p><p><br /></p><p>Nidae hajja kiyi wani abu akae idan ma da ,hali kisaka sa ya maidani a yau din nan ,cike da tsoronta hajja ke fadin karki damu ya'r lelena ."kibarni dashi ya fito wanka xae xo ya sameni ne.</p><p>............Yana ko'karin cire kayan jikina nayi saurin Rike masa hnnu A tsorace ya kalleni fuska bbu walwala yake tambayr ta minene kuma?"</p><p>Cikin sanyin jiki nake fadin kayi wnkan ka mumin ni xan koma na jiraka sae naje gida tukuna."</p><p><br /></p><p>"A hnkali ya shiga girgiza kai ban yarda ba husna,bana iya jure rashin ki kona second d'aya ne ......da Dan karfi ya fara mgana bana son na bude idona naga yarinyar nan A gabana ,kinga hajja taje ta wani kwaso min ita zanyi wanka naga Dr.yabani sallama cike da ba'cin Rae yake maganar kallonsa kurum nakeyi ,Nan na taimaka masa yyi wanka ,ya fito sanye da jallabiya still su Hajja na da'kin sae naga ya dauke kansa ,anan na shimfida masa sallaya ya kabbarta sallah."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cike dajin haushina Aliya taja tsaki muna ha'da ido ta zabgamin ,Harara tareda fadin ya'r kinin bibi kawae .</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Cike da ya'nga Aliya ta iso gurinsa dauke da plate ,shake da soyayyaen dankalin turawa da kuma cup coffee " Yana xaune akan gado ta xauna gabda shi har ka'fadar su na gogar ta juna gudun sa'bama mahaliccin sa,Dan yasan ynxu bbu Aure a tsakanin su.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yyi saurin matsawa cikin wata uban tsawa ya kalleta wane irin iskanci ne haka Dan Allah matsamin banxa kawae marar zuciya ", taji haushin kalaman sa sosae har Yana cikin ciwon baxae raga mata ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kai - kai Abdul ka shiga hnkalin ka marar zuciya ya wuceka ,</p><p>ga wadda keson ka sae wata kake famar bibiya wandda bata damu dakae ba."</p><p><br /></p><p>"Da sauri na kalli mumin wandda yyi saurin dafe kansa Yana fadin..</p><p><br /></p><p> washhhh,Ashhhhhh!! Da sauri na ka'raso garesa gamida rike kan nasa kiramin likita !</p><p><br /></p><p>" yyi mganar cikin cijewar baki ,</p><p>na juya kan hajja plzzz hajja kidaina irin haka a gaban sa Dan Allah bakya tsoron ciwonsa ,ya tashi ne?? Tayi mganar cike da nuna damuwa a fuskarta salati."Hajja ta shigayi lallai yarinyar nan wuyan ki yyi kwa'ri ni xaki fadawa haka??"kenan kinfini sanin ciwonsa.?</p><p><br /></p><p> "Bata kula Hajja ba A fusace ta fisgi Hanun Aliya tayi waje daita ....hajja na kwa'lama Asma'u kira bata saurareta ba sae da ta Hanka'da Aliya a waje...</p><p><br /></p><p>("Plzzz Manage This Page).</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>63</p><p> Baya -baya tatafi zata fa'di Allah ya taimaketa ta dafa ba'ngo A tsorace a kuma fusace Aliya ke kallon Asmy ,</p><p>ka'rasowa gurinta tayi gamida folding din hnnun ta akan kirjinta ,</p><p>tana mata wani irin murmushi Wanda yafi "kukan ja'ki ciwo ,wae ke mekika dauki kanki ne??</p><p><br /></p><p>" Kina tunanin haukan ki da banxar jahilcin ciki xae ta'ba tasiri akaina ??....</p><p>saurin girgixa kai tayi gamida sakin wani malalacin murmushi.</p><p><br /></p><p>" hnnun ta tasaka A kirjin Aliya wadda ta saki baki da ido tana kallonta " </p><p>idan da nice ke da tuni nabar Rayuwarsa ,</p><p>Dan nikam baxan iya Rayuwar aure da namijin da ya nuna min tsana ka'ra ka'ra kuma ya nuna baya yi dani."</p><p><br /></p><p>"Anya kuwa kinsan mutuncin kanki ?"</p><p><br /></p><p>" A matsayin ki na y'a macce ya nuna bayayi dake ,</p><p>Sae kibar Rayuwarsa duk wannan kya'n da Allah ya baki ,haba ka'wata </p><p>"Dan Allah kiyi tunani da Kwa'kwalwar ki mana hajja bata sonki da Alkhairi da tana sonki da bazatace ki koma Rayuwar Mr.AJ.</p><p>ba Dan wlhi wulakanci zaki cigaba da gani acikin Rayuwar auren ki ,Dan nisawa Asmy tayi gamida ya'rfi da hnnun ta.</p><p><br /></p><p>"Shafa fuskar aliya ta somayi cikin wani irin sallon, ta soma fadin "Am sorry Mrs.Aliya meera har Abada ,baxaki ta'ba komawa cikin Rayuwar Abdul jabbar meera ba.!!</p><p><br /></p><p> ." mumin nawa ne ni kadae ,ki Rubuta wannan ki aje acikin sakaryar kwa'kwalwar ki,</p><p><br /></p><p>Tayi mganar gamida bude mata manyyan idonta."</p><p> ."A fusace Aliya ta daga hnnu da nufin ta saukesa akan fuskarta Sae taji anrike hnnun Idonta sun ka'da sunyi ja ,Cikin wani irin fushi ta juya alakar kallon nata, ga wanda ya hanata aikata hka "wani hadadden saurayi tagani rike da hnnun ta ,cikin shigarsa ta manyan likitoci ,tamkar shi yyi kansa Dan kyau."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A hnkali ya saki hnnun nata ,meyayi zafi haka malama ."??</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Da zaki mari fuska Mae daraja haka harara Asmy ta dinga sakar masa ."A fusace ta juya ta koma Room din .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Taje xata hada masa Ruwan Lipton hajja tayi saurin dakatar dashi cikin tsawa ,dae dae lokacin Dr.kamal ya turo ko'far dakin </p><p>,haka baisa hajja tayi shuru ba." </p><p>Yarda kika turata a waje kema ya zama dole kibar Asibitin nan ,</p><p><br /></p><p>ynxun nan !! basae anjima ba ta amshi cup din hnnunta ta nuna mata ko'far fita mai makon ta fita Sae ta nufi gurin mumin dinta."</p><p><br /></p><p>"Ta sunkoyo dae-dae kunnesa tayi masa ra'da ,Wanda ni Asmy ban San me tafada wa mumin din nata ba ." </p><p><br /></p><p>"Da sassarfa tabar dakin idonta cike da kwa'llah jiki sanyayye Kamal yabita da kallo Yana jin haushin hajja a ransa akan meye ne xata dinga yimata tsawa haka??</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Billy a yau zan kawo karshen yarinyar nan."</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Dan nasan muddin tana cikin Rayuwar Abdul jabbar baxan ta'ba </p><p>samun saba har Abada."</p><p><br /></p><p> Tom.ynxu meye shawara Aliya??murmushin takaici Aliya tayi ."just wait and see ka'wata nan da minti Ashirin xakiji sa'kon mutuwarta ,</p><p><br /></p><p>Tana fitowa taci ka'ro da sageer ganin yanayin da take ciki yaja ya tsaya."</p><p>Mae makon Ta kulasa Sae yaga ta nufi mo'tar ta da gudu tana famar sharar kwa'llah batasan yaushe mumin dinta xaeyi farin ciki ba."??</p><p><br /></p><p> Ganin ta shige motar ta tayar dabara ta fa'dowa kamal ,shima motar tasa yyi ma key yabi bayanta."haka kurum ya tsinci kansa da wani irin fa'duwar gaba</p><p><br /></p><p>" jin yake kamar ya tsaida ita amma yasan baxata kulasa ba ."Haka ya cigaba dabin bayan ta.</p><p><br /></p><p>"Asmy b Aliyu.😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>64</p><p><br /></p><p>"Ringing din wyarsa ya dakatar dashi daga shiga da'kin ,gabansa ya fadi lokacin da ya ka'lli pic din dake yawo akan screen din wyar tasa,wannan karon baisan karyar da xae fada mata ba." Yasan halin Mimi tacika rigima ne dabin kwa'kkwafi ."A karo na biyu wyar ta shigo cikin sanyin jiki ya daga wyar."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Haba sageer wannan wane irin sabon wulakan cine?".... Sassauta murya yyi mekuma yyi zafi Mimi ?? Kasan meke faruwa fadamin kawae ne baxakayi ba ." na fada maka kusan kwana,ukku ina kiran wyar yah Abdul a kashe idan nayi maka mgana sae kace yana busy .” kullum kuma kai sai nayi wya da kai!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ka fadamin meke faruwa ,ko har da yau week end ba'a samun sa ??" Ajiar heart ya sauke wae meye hakane?" Karya kenan xan fada maki inaxan San dalilin sa na kashe wya ,tunda yau week end ne ."dole ne ka sani sageer tunda best friend dinka ne ,kuma brother In law dinka ne...naji ajikina akwae abunda kuke bo'yemin Any way ,xan shigo Nigeria soon sabida munsamu hutun ka'rshen shekara."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Da sauri sageer ya katse mata hanxari kin fasa xuwa Sudan din ne??" Yana nufin dangin Ammin su ,Dan tace wannan karon acan xatayi hutun ta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kae tsaye tabasa amsa ,da nafasa tana gama fadin haka ta datse kiran hnkali tashe ya fara Neman layinta amma A kashe." Jiki sa'bule ya tura kansa da'kin da AJ .yake ciki dauke da sallama a bakinsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Granny ya hanga gefensa tana basa ruwan lipton ,ko kadan bbu fara'a a fusakarsa anan sageer ke gaisheda granny ." ta amsa dauke da fara'a a fuskarsa."</p><p><br /></p><p>"Yawwa sageer tunda kaxo sae kaxo kayimin sulhu da wannan yaron, sae famar fushi yakeyi dani ." Tamkar ni na Daura masa ciwo,Dan murmushi sageer yyi tareda rike hnnun Granny daya.. Karki damu kanki da yawa Hajjan mu. "Kinsan halin maigidan naki,idan yana ciwo sae yabi ya fitinemu da rigimarsa." Ynxu dae driver ya mai dake gida ,tunda gani na iso ,zan cigaba daba abokina kulawa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tsam AJ.ya mike tsaye dawa xaka xauna ??" ni kam nagama,xaman asibitin nan,Ae kaji irin ta sageer cewar Hajja." Ta,ina ya ta'ba ganin anyi haka ?"ka sallami kanka batare da likita ya baka sallama ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Plzzz sageer muje ka rakani gun likita zan amshi takardar sallama" yyi mganar fuska bbu walwala." Baxai fa yuyuba AJ.baka gama jin sauqi ba ,ka hkura sae xuwa gobe haka."cewar sageer cikin fushi AJ.ya kallesa idan baxaka rakani ba ka daina yimin dogon sharhi malan."idan na isa gida ,sae Drama Queen tayi jinyar tawa a gida mana...nasan baxata ki hakan ba !</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Badan sageer yaso ba yace OK.tom jirani bara naje na amso takardar sallamr ka kaga mata na awaje ko kana son suyi ta kallonka da jallabiya?" Nasan ka tsani hkan shiyasa saurin dauke kae yyi ,murmushin samun nasara sageer yyi ya kalli hajja gamida kashe mata ido daya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>**********</p><p>Tuki take amma bata jin motar dai-dai lokaci daya taji motar tana Neman ."Kufce mata hnkali tashe kamal ke kallon Abunda ke faruwa ,wani gefen daban yaga motar ta ya'nka wandda bbu yawan jama'a a wurin filine ,fetel.".</p><p><br /></p><p>Sae dogayen bishiyoyi ,kafin wani lokacin ta saki sitarin motar haka motar ta cigaba da gudu tsoro da raxana taji yasa xuciyarta na wani irin harbawa." Cikin ikon Allah motar ta bugi wata bushiyya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wata ka'ra kamal ya saki gamida fitowa motar sa,a guje ya nupi motarta ta hka sauran dai dai kun mutane suka rufa masa, baya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hayaki motar ta farayi cikin tsoro da firgita.</p><p><br /></p><p>Yyi nasarar cirota daga motar ,gaba daya fuskarta ta jike da jini ,ko motsin kirki batayi ..." Lokaci daya kamal ya fashe da kuka wani bawan Allah dake tsaye a gabansa ya Dan russuna ."ya kai hnnunsa akan hancin ta ."bata numfashi cikin jajjayen ido kamal ,ya kallesa hawaye na xuba a idonsa baba ta mutu ko?" Yyi tambayr cikin rawar murya ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dan a lokacin gaba daya ,ya manta dashi likita ne.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cike da jimami tsohon ya girgiza kai sae dae hkuri yaro ."A tsorace ya shiga jijjigata yana kiran sunan ta tamkar wani zautacce haka ya ko'ma. Ya riketa gagam a jikinsa yana wani irin kuka baidamu da jikin dake xuba ajikinsa ba."</p><p><br /></p><p>MA'U..😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>65</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Da gudu ya fito daita da hnnu bbu alamr numfashi,A tattare daita.</p><p> " Haka ya shiga kwa'lama likitocin gurin kira tamkar,</p><p>Wani xautacce Habeeb ne yyi saurin tarar sa yyinda nurse kwa'ra biyu suka axata agado suka jata xuwa ."Emergency a gigice kamal ke fadin Habib kaje ka ceci Rayuwarta Dan Allah,ya karasa xancen cikin rawar murya. ." Jiki sanyayye Habeeb ya nupi Emergency "Anan ma ya gano doguwar sumace tayi ,sae inda goshinta glass ya Dan ta'ba nan take Dr.Habeeb yyi dinke mata gefen goshin nata. "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Allorori ya ha'da yyi mata .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana xaune a katafaren ofishin nasa, kujera sae famar juyasa takeyi xuwa wannan lokacin yyi wanka ya canja kaya bakin Jean's ne Ajikinsa da Blue din T.shirt ."</p><p><br /></p><p>Habeeb ne ya kallesa cikin,yanayi na tuhuma har yau bakace komae ba kamal?" Mai ya kawo wannan ha'darin ko kuma fyade kayiwa ya'r mutane.......!?</p><p>Cikin wani irin Fushi kamal ya katse Habeeb ya isheka haka Habeeb!!</p><p><br /></p><p>"Niba yaron ka bane ,da xakaxo ka tsareni da silly Question's dinka." Wae meye ma damuwar kane?</p><p><br /></p><p>Yyi mganar cikin kunar Rai ,shima axuciya Habib yake fadin dole na damu "ka kawo yarinya cikin wannan hali baka gudun sauran likitoci su tuhume mu?" Idan ni na Rufeka wlhi,wani baxai rufeka ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nace a fadawa family din yarinyar nan ka 'ki kusan Awa biyr yarinya bata San idan kanta yakeba." Ido kamal ya zuba ma Abokin nasa, Dan murmushin takaici ya saki ,Kana tunanin akwae wanda yafini jin ciwon halin da take ciki?."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dan cije lebensa na ka'sa yyi ban hana ka fadawa family nata ba " but not yet!</p><p><br /></p><p>To sabida wane dalili naka?"kasan xa'ayi ta nemanta fah?"tsaki kamal yaja Dan Allah "idan baxaka bata kulawa ba ka fadamin na nemar mata wani Asibitin..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tsaki Habeeb yyi gamida bar masa office din ,A hnkali ya maida hnkalinsa kan Agogon bangon dake juyawa a da'kin ,Karfe shidda da Rabi na yamma ." tsam ya mike tsaye ya shige toilet Dan ya lura lokacin sallar magrib yana kusan towa ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A hnkali ya kalli Aunty sadiya dake gefensa,ya Dan hade rae wae aunty yaushe drama Queen xata ,dawo ne??"... Tun safe rabonta da nan daga xuwa gida tayi wanka,Aunty sadiya dake gefensa xaune ta Dan ta'be baki akwae mmki kasani ko Hajja ta hanata tahowa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dan tsaki yaja gashi fa duka tabar wayoyinta anan, shima sageer tun sallar la'asr ban ka'ra sakasa a ido ba." Ya ka'rasa xancen cike da damuwa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Turo ko'far dakin da akayi yasa suka maida hnkalin su ga ko'far A rude yake kallonta ." ke Rak lpia??" Xaki shigowa mutane a haka?"ya yyi mganar cikin kulawa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Aunty sadiya ta daka mata tsawa,uban me kike yiwa kuka ?"tun farko banso xuwanki gurin nan ba."ke kika nace akan hakan,kinxo kuma xaki ishi mutane ka'ra saka kuka tayi mai Dan sauti."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Bbu shiri AJ.yyi saurin tsaida Aunty sadiya , gamida dirowa ,daga kan gado duk da bayajin ka'rfin jikinsa haka ya daure yaisa gabanta ,Dan kukanta ba'karamin azabtar dashi yakeyi ba ." yana jin kukan ta tamkar na Mimi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sassauta murya yyi .</p><p>Gamida dafa ka'fadunta ,</p><p>Hi!</p><p>Rak!.</p><p>Wat Wrong wit yhu?</p><p>" why are yhu crying.</p><p>Cikin Rawar murya Rak ke fadin yah Abdul "naga Asma'u a wani daki an Daura mata bandeji A...........</p><p><br /></p><p>_At 5:40pm.by Asmy b Aliyu_.</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p>66.</p><p><br /></p><p>Hi !</p><p>Rak wat did yhu say?"</p><p>Da gaske nake fada maka yah AJ.naga Asma'u kwa'nce tamkar bata da numfashi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Saurin katseta yyi ,jikinsa koina rawa yake a wane daki ?" Aunty sadiya ta kalli Rukaiyya cike da tuhuma ."Anya Rukaiyya kwa'kwalwar ki bata fara samun Matsala ba.?"Haushine ya kama Rukaiyya tana jin takaicin ,fada masu datayi gashi lokaci daya AJ.ya rude akan Rabin ran nasa."</p><p><br /></p><p>Jan hnnunta AJ.yyi kaini da'kin nagani Aunty sadiya ce tayi saurin dakatar dashi ."bara naje na dubo ka koma ka kwan'ta baka ganin halin da kake ciki ,saurin girgixa kansa yyi no Aunty baxan iyaba."da haka yaja hnnun Rak haka ,aunty tabi bayan su."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yana tsaka da cire mata drip yaji an banko ko'fa ......A tsorace kamal ya Dan juyo ,ganin AJ. A gabansa yasa yadan rude shikuma a gigice ya nufi gadon nata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hnnunsa na rawa yakai kan goshinta wanda yake ,daure da, bandeji ."Da rinannun idonsa ya dago yana kallon Dr.kamal cikin wani irin yanayi kamal ya mike tsaye ,hnnunsa zube cikin Aljihun wandonsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A fusace AJ.ya mike tsaye cikin fushi yake fadin meya sameta??" Meyasa aka bo'yemin ,</p><p>cikin karfin hali kamal ya soma yiwa AJ.bayanin ha'darin da tayi ...dae-dae lokacin kuma ta fara motsi A hnkali take fadin ."water! Water!</p><p><br /></p><p>Da sauri AJ.ya xube a gabanta ,husna !</p><p>Yyi mganar cikin rawar murya ."A hnkali ta furta mumin !!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ko'karin mikewa takeyi xaune,Dr.kamal yyi saurin dakatar daita."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" cikin sanyi murya yake fadin karki tashi ,</p><p>Fridge ya nufa ya dau'ko gorar Fa'ro marar sanyi ya mikawa AJ. ruwan ,da sauri AJ.ya ka'rbi gorar Ruwan."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Shi ya taimaka mata ta sha ruwan idonta na ka'nsa hawaye taji sun cika idonta ."</p><p> Tana jin tausayin kansu.. Aunty sadiya ta ka'raso gurinta tana mata sannu yyin da suka shiga jimamin Abunda ya faru...."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A Daren AJ.yana tare da Drama Queen nasa, Dan shi yama nemi ciwonsa ya Rasa." Kwanan ta biyu aka basu sallama."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>1 week ltr.</p><p><br /></p><p>"Dawowar ta kenan daga skull misalin karfe 3:00pm.na rana ga mmkin ta Sae taga motar AJ.a parking lot taji ddi sosae ,Allah ya azata akan mumin Allah yasa yabar ta taje birthday din Mrs.Modibbo."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ka'rar AC.kawae kakeji A falon haka taci gaba da tafia bata ji motsin kowa ba har ta hau up stair's ,tana tura ko'far dakin Dai-dai lokacin AJ ya fito daga wanka." </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Farin Towel ne daure a kugun sa ,Sae karamin da yake tsane gashin kansa dashi A tsorace ta juya masa baya gamida runtse idonta ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A daddare ta xauna gefen soofa gamida basa baya,murmushi ya saki irin na xaki sani ne!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" yaushe kk shigo ?"</p><p>Yyi mata tambayar in a low tone,ynxun nan ta basa amsa batareda ta ka'llesa ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Karasowa yyi gabanta ,xaki taimkeni ki shafamin Mae ?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kayi hkuri ka Shafa da kanka ni wanka ma xan shiga ,tana fadar haka ta mike tsaye " </p><p>tayi hnyar toilet batare da ta kallesa ba ."tana kai jikin ko'far ta Dan daga muryarta ,ka jirani na fito muyi lunch tare "tana fadin haka da gudu ta shige toilet gamida rufo ko'far "</p><p><br /></p><p>" da murmushi yabita a ransa yake fa'din "..she acting like a chil'd alway's.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Maroon tree Quarter ne a jikinta da farar vest wadda ta gama bayyana,siffar jikinta du'ka parking gashin kanta tayi tsakiyyar kanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Daga hnnunta tayi sama tana Addu'ar Allah yasa yabar ta xuwa birthday din Ummi modibbo,</p><p>Agogon bangon da'kin ta kalla karfe 4:20pm. Na yamma ."</p><p>dama ta Riga da tayi sallar la'asar tana jiransa ne ya dawo,daga masallaci."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Zagayen falon ta farayi da wyarta a hnnunta tana juyawa ."</p><p><br /></p><p> sallamr sa taji ganin yanayin fuskarta yasa ya ka'raso gurinta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hi Mrs.AJ.</p><p>Wat wrong with yhu ?</p><p>Dan shagwabe fuska tayi ,kamo hnnunsa tayi suka xauna kan kujera ." Right hand nasa ta rike tana murxawa a hnkali</p><p><br /></p><p> shikam kanllonta kurum yake haka ,gaba daya hnkalinsa na kan kirjinta."</p><p><br /></p><p>.....Fadamin meye matsalar ki ?" Yyi mganar gamida kallonta ,</p><p>A tsorace ta fara mgana dama Mumin kawata ce xatayi birthday party shine....</p><p>Sae kuma tayi shuru kallonsa ta shigayi ,kina son kibata gift ne??"</p><p><br /></p><p>"Ina son naje birthday dinta ne wandda xa'a fara ka'rfe 8:00pm.na dare ,za'ayisa ne ....</p><p><br /></p><p>"saurin katseta yyi karkiyi tunanin xan barki kije ,ya fada gamida mikewa tsaye.</p><p><br /></p><p> hnkali tashe ta mike tsaye,haka ta ba'ta rae meyasa?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sabida kina matar Aure!!</p><p>Ya bata amsa,kai tsaye."</p><p><br /></p><p>Idan Baka yarda ba Sae mutafi tare tayi mganar shaye da toka."</p><p><br /></p><p>"Are yhu out of your mind?"</p><p><br /></p><p>Yyi mganar cikin ba'cin rae ,am not going anyway and yhu to ......yana gama fadin haka ya ra'ba ta gefenta ya fice cike da ba'cin rae...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*TEAM DRAMA QUEEN.👯*</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>67</p><p><br /></p><p>"Tana ganin wyar Mrs.Moddibo Amma ta kasa dau'ka sabida tana jin kunya ka'rshema kashe wyar tayi duka gamida turata ka'san filo.</p><p><br /></p><p>Kusan karfe ,Tara da rabi na dare ya shigo da'kin nata jin tayi an xauna gaf daita ,lokacin tana kwa'nce kan bed tayi Ruf da ciki Runtse idonta tayi." Dan bata mason mgana dashi a wannan lokacin haushinsa,takeji.</p><p><br /></p><p>"Husna !</p><p>Ya kira sunan ta murya ka'sa ka'sa."</p><p>Tana jinsa,ta masa banxa.baxaki amsani ba fushi kk yi ??"</p><p><br /></p><p>Nan ma shuru tayi masa, kiyi hkuri ba Dan niba.,kitashi ko tea ne kisha kinji my Asma'u A hnkali ta mi'ke xaune batareda ta kallesa ba ,Ta mika masa hnnunta Almr yabata cup tea din ,hawaye yaga ya cika mata ido ."jikinsa yyi sanyi Qlau ko ka'dan bayason ya ganta cikin damuwa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Daura cup tea din yyi Akan bed side ,drower cikin wani irin yanayi taji ya jawota ga ba'daya ajikinsa." Tana jin yarda yake sauke ajiar zuciya "A hnkali yake ko'karin lalubar ba'kinta ta gano nufinsa ,sae tayi saurin janye fuskarta.</p><p><br /></p><p>" hannayen sa yasaka ya ta'llabo fuskarta ,plzzz karkiyi min irin wannan horon Husna,</p><p>"Yyi mganar cikin rawar murya saurin kwa'ntar da kanta tayi akan fa'deden ki'rjinsa bata iya jure ganin sa ,cikin wannan halin gaba daya tausayin sa,</p><p>Takeji.</p><p><br /></p><p>Saukar hnnunsa taji akan bayanta ,cikin wani irin salo yake Shafa bayan nata wata, baby pink Riga ce ajikinta ta barci."</p><p><br /></p><p>Wadda ga badaya ,cinyoyinta sun gama bayyana ta kamata ta Rigar haka tayi mata kyau."cikin saukewar numfashi yake Shafa. Bayan nata.</p><p><br /></p><p>"Kafin ya samu ya ha'de bakin sa ,da nata wani irin romantic kisses ya'ke mata wandda ta ka'sa fassara sa."</p><p><br /></p><p>Sunfi minti goma a hka ,cikin sanyi jiki ya zare jikinsa cikin nata lokaci daya,</p><p>Haka ya mi'ke tsaye gaba daya yanayin sa ya canja tamkar wani mashayi."</p><p><br /></p><p>Da brown eyes ,dinsa ya kalleta cikin sa'rkewar murya yake fadin kisha tea ka'fin ki kwa'nta karki manta kiyi Addu'a sae da safe ,yana fadin haka yyi saurin barin da'kin jiki sanyaye tabisa da kallo.</p><p><br /></p><p>★★★★</p><p><br /></p><p>Da misalin ka'rfe biyu da Rabi AJ.ne xaune shida Sageer Akan Dinning side ,suna lunch haka suna tattauna matsalar da ta shafesu."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sukaji ka'rar talkamin kwa's! kwa's! Cikin wani irin taku ,tom dama ya dauka Asmy ce Dan bata dawo skull ba." Yana da'ga idonsa akanta sae yaga sa'banin hkan." Lokaci da'ya ya mi'ke tsa'ye shida sageer.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tana cikin wani uban leshi maroon colour dinkin Riga da skirt ya kamata sosae ,wandda da kya'r take da'ga ka'fa tayi tafia acikinsu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana janye da ya'r ka'ramar Trolley dinta." Da kuma Gucci handbag dinta."wasu uban Hill's ne a kafanta suma cmpanyn Gucci." Glass din Frada ne manne a idonta." Cikin takunta na kasaita ta nufi hnyar side dinta."</p><p><br /></p><p>"AJ. Yyi saurin ka'rasowa gabanta .</p><p><br /></p><p>Hi !! "wait a second!.</p><p>Yyi mganar,cikin kakkausar murya ,ina zaki tafi …?</p><p><br /></p><p>" A hnkali ta cire gilashin idon nata,murmushi da'uke a fuskarta .Ayyo my dealing Hus.....sauren katseta yyi a tsawace niba mijinki bane ,kin gane ko "so mind your language ki fa'damin meya kawoki gida na??</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" A hnkali ta dire trolley bag nata ,ta isa kan coach ta xauna tareda da'ura ka'fa daya kan daya ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Do yhu really want to know mr.Abdul jabbar meera?",tayi masa tambayr gamida ka'fesa da manyyan idonta."</p><p><br /></p><p>Asmy b Aliyu novel's.😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>68</p><p> "</p><p>Hello commissioner!</p><p>"It's Abdul jabbar meera speaking!</p><p>" ina bukatar isassun ya'n sanda ynxu matar da tayi ko'karin kashe matana ,ta dawo .."OK ina jira da haka ya datse kiran.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana koka'rin yin magana ,yaji muryar hajja Akansa wadda tuni Aliya ta tura mata message a wya,</p><p><br /></p><p>" baxataje koina ba ina mai baka umurnin ka kira wandda kayi. Mgana dashi ,A wya ka fa'da masa karma yaxo ."idan ya tako kafa'rsa acikin gidan nan to tabbas kuwa xa'a kwashi ya'n kallo."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A haukace ya juyo kan Hajja ,meyasa xan xauna daita ??" Akan meye xan xauna da Annoba ,acikin gidana!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Meyasa kikeyin haka granny ,idan ka maidata da'kin ta ae an xauna lpia."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bazaiyu yuyuba granny!!</p><p>Enough !is a Enough ,hkurina ya ka're baxan iyaba , ta kurawar yyi yawa idan Aljani suka tura maki ,Dan su ha'damu nixan yi mganin sa da ikon Allah ."</p><p><br /></p><p>Dan wannan ba hajja ta bace wadda ,ke tsananin sona da kaunata ."Akan mexan xauna da matar dake Neman Rayuwata ,ko ta halin yaya ."I don't even like her any more..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"So get out of my house right know!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yyi mganar A tsawace,duk wani kalan haukan dake ,bisa kanka xan saukesa ne ." yau nikake fa'dawa Aljani ne abisa kaina ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sageer ka fa'damata ta fita ynxu. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kafin nayi lossing control dina ,Hajja ce taji kanta na juya mata baya-baya ta tafi xata fa'di AJ.yyi saurin tarota."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A rude yake fa'din granny gaba daya ya Rude ,Daukarta cak !yyi xuwa up stair's Yana tofa mata duk Addu'ar da taxo bakinsa.sageer ne yyi ko'karin kiran family doctor a wya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Aunty sadiya ,abunda yafi ki dauketa xuwa gidan ki gobe malaminta ,xae fara xuwa cikin sha'rbar kwa'llah Aunty sadiya ke fa'din yaushe zamuyi farin ciki ne?" Komae ya canja duk son ibadar hajja a yau ba'ta iyayin Azkar mai tsayi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tana xaune akan soofa ,A hnkali take juya wyarta ta ta kalli Agogon bangon da'ki Dan tsaki taja kar'fe takwas da rabi, na dare Agogon bangon da'kin ya nuna.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dan tsaki tayi ,Billy nason ba'ta mata plan.tana cikin wannan yanayi wyar hnnunta tayi ka'ra.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Hello billy!</p><p>Where Are yhu?</p><p>Ina kan hanya ."kiyi sauri ki ka'raso nima ina kan hanyar xuwa wajen tsinanniyr can Wanda xanje na gabatar da aiki na nakarshe ,wandda mutuwa ce ko Rayuwa cikin biyu xa'ayi da'ya Dan wlhi baxan bar wannan matar ta Rayuwa ba...kiyi sauri ynxu xan gabatr da Aikin nawa." Yana gidan Aunty sadiya itakuma inajin Almr motsinta ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ok tom.</p><p>Sae kin ka'raso.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wani dogon ka'rfe ta dauka kakkar'fan gaske ta nufi ko'far fita daga da'kin murmushi dau'ke A fuskarta.[Truncated by WhatsApp]</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>69</p><p>A hnkali ta fa'ra saukowa akan stair's wya ce sa'kale a kunnenta da almr tana "Amsa call ne mai muhimmanci."</p><p><br /></p><p>"Saukar wani dogon Abu taji A tsakkiyar kanta kafin ta Ankara an turata tun daga kan stair's na 3 xuwa ka'sa haka ta dinga gangarawa ,jini na zuba ajikinta har ta sauka akan stair's din ,kwa'nce take cikin jini bbu Almr motsi a tattare daita ." Da'ga dogon ka'rfen Aliya tayi Akanta dai -dai tsakiyyar cikinta."sae taji an Daka mata tsawa cikin murya mai ka'raji .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Stop it Aliya!!</p><p><br /></p><p>Da gudu ya ka'rasowa gurin ya tallabi kan nata da jini ke fitowa Yana shiga ta gefen kunnen ta ga ba'daya ya rude ." ya rasa mai xai yyi .Ya ka'sa Rike hawayen idonsa duk dauriyar sa ."sae gashi suna sauka A kan Cheek's nasa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin zare ido Aliya ta yarda dogon ka'rfe jikinta koina rawa yakeyi ." bata taba ganin AJ.hka ba ,A hnkali ya saukar da kanta a ka'sa ga ba'daya fararen kayan sa sun gama lalacewa ,</p><p>"Cikin wani irin fushi ya shiga tun'karar ta a tsorace take ja da baya ,gidan ubanwa zakije kuma??" Wlhi kema yau sae na kasheki ,wani irin riko yyi ma gashin dokin dake reto,A tsakiyar bayanta Jan ta ya shigayi A tsakiyar falon Yana ba'll da ita Yana marinta ,ihu take tana fadin Axo aceceta xai kasheta."</p><p><br /></p><p>Amma bbu mai jin ihun nata ,shaketa yyi sae da ta fara ,</p><p>Hango mutuwar ta ,ya isa hka mr.Meera!" A haukace ya juya inda yakejin sautin mganar ya'n sanda ne fiye da goma tsattsaye ,Sageer ne yyi saurin ka'rasowa gurin Abokin nasa ...da kya'r ya ban'bare hnnunsa jikin Aliya wadda ta gama galabaita ."</p><p><br /></p><p>"Ga da'ya Shatin hnnun sa ya kwanta akan jar fusktar wadda ta gama kumburewa,da mugun bugun da AJ.yyi mata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kabar komae A hnnunsu ,gasu sun ka'raso muyi ko'karin kai ,Asma'u Asibiti Dan ceton Ranta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin sabulewar jiki ,AJ ya xube ka'sa akan gwiwonsa,ya fashe da kuka lokaci daya. "</p><p>Sageer wane irin Asibiti kuma ta Riga ta ka'sheta ."</p><p><br /></p><p>Wat should I do now! </p><p> "Yyi maganr cikin rawar ,muryarsa karka cire rae da Rayuwarta nayi alkawari xan taimaka maka ta hanyr shigar da *Haske*" Mai yawa acikin Rayuwarka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Anan jami'an tsaro suka tusa keyar Aliya a gaba tana kuka tana ihu,haka baisa suka saurara mata ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Likitoci fiye da biyr ne akanta sun saka mata wasu irin na'urori akanta ,</p><p>Kwa'nce take sam'bal bbu Almr numfashi a tattare daita koda Dan ka'ramin ya tsanta baya motsi ,Dr.saif ne ke ko'karin jawo numfashinta wandda har yau bayi nasarar hkan ba." Saurin likitocin kuwa,</p><p>"Darewa sukayi cike da tsinkewar ,Al'amarin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Sun Riga sun baiwa Kansu da wuya ta Rayu.</p><p><br /></p><p>"Har washe Gari bbu Almr wata nasara ,AJ.da sageer A tsaye suka kwa'na bbu likitan da ya masu ,bayani har ynxu haka bbu wandda yyi masu umurnin su shiga da'kin da take ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ta jikin window kurum suka iya hangota.</p><p><br /></p><p>" Around 7:00@m.Dr.saif ya nufi da'kin da take AJ.yyi saurin shan gabansa ya tsaresa Da jajjayen idanunsa ,Yana masa kallon tuhuma.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>MA'U.😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>*Take Note !*#</p><p>"*Naji sa'kon masoyan wannan nvl ,masu kirana a waya masu min mgana ta pc duka ina godiya da nuna soyayyar Ku A gareni ." wasun Ku sunyi mganar akan na samu na ka'rasa (Wata Rana!)kafin sallah wandda baxai yuyuba ka'rasa sa acikin kwa'nakkin nan Dan lbrn yana da tsawo ina mai Baku hkuri akan baxai yuyu ba."sae dae xuwa bayan sallah haka kuma wannan shine last page wanda daga garesa baxan koma typing ba sae bayan sallah idan Allah ya nuna mana da fatan masoyana zasuyi min uzuri Allah ya ha'damu da Alkahirin sa Allahumma Ameen!👏🏼</p><p><br /></p><p>70</p><p>"Nan take Dr .Saif ya rikice ganin yarda fuskar AJ.ta xama lokaci da'ya cikin sanyayyr muryarsa yake fa'din Dr.yaya jikin nata? Ta farfado?? Tambayoyin da ya jerowa Dr.saif kenan lokaci daya.."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Muje office nayi maku bayani Mr.meera wata ki'la xaku fahimceni."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Jiki sayayaye ya masu iso gurin sauran likitoci gaba da'yansu suka,hadu...Gaskiya Mr.meera matsalar matar ka babbace ,Dan tun jia bbu Alamr wata nasara Kamar yarda kunka kawota hka take,shiyasa ma mukaji tsoron sanar dakai ." Sabida ganin yarda ka damu akan jikin na matarka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Amma karka damu zan ha'daka da wani babban likita dake Asibitin *Shika*" dake zari'a Dr.jayyed Wanda na tabbata da ikon Allah xa'ayi nasara ..."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Jiki sanyaye ya kalli sageer idonsa ya ka'da yyi ja Wanda har baka hango fari acikin su,yana son yyi mgana sae dae ya kasa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Jikinsa ga badaya rawa yakeyi harta da yatsan sa,na hnnu."sageer ne yyi saurin Rikasa karka yima kanka illah Abdul ."kayi Addu'a kurum Allah yaba matarka lpia ,zanje nayi mana booking din jirgi zuwa zari'a Dan baxai yuyu aje a motaba."ka'da kai kurum yakeyi batareda yaba sageer Amsa ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_ZARI'A_"..</p><p><br /></p><p>Abdul hammed omra ne shida Dr.jayeed ke tattauna shafewar tunanin Asma'u Omar omra,Wanda ke kwa'nce sam'bal acikin wani da'kin na musamman An jona mata wasu irin da'urori akanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Numfashinta ya dawo dai-dai ,Barci takeyi hnkalinta kwance,tamkr bbu wata matsala tattare daita."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sanye yake cikin ya'di na kaftani dark green ,wandda yyi matukar kar'barsa ." kansa bbu hula sae dae suman nan tasa tasha gyara ,takwanta tamkar ta larabawa ."As usual ."sae kamshi yake zubawa kallo da'ya xakayi masa kasan baya cikin natsuwar sa ,</p><p><br /></p><p>Hameed omra ne yabisa da ka'llo ,ina kuma xuwa haka?" Xan koma hospital ne sauran Awa daya ,cif ta fa'rka tamkar yarda Dr.jayyed ya fa'da hohoho!</p><p><br /></p><p>."Abdul jabbar baxaka tsaya Ko tea ne kasha ba."tun safe bbu komae acikin ka."</p><p><br /></p><p>Haka sageer ya fa'damin ,idan ka kwantar da hnkalin ka komae zaizo mana da sauqi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>."Hannayen sa xube cikin aljihun wandonsa,</p><p><br /></p><p> "A hnkali ya lumshe ,idonsa ya hurar da iska,mai xafi a bakinsa."</p><p><br /></p><p>Baxan iyaba hameed.!!</p><p>"Komae bana jin ddinsa,nidai mutafi ka ajeni karta farka bama ku'sa yyi mganar in a low tone...</p><p><br /></p><p>girgixa kai Hameed yyi bbu inda xaka sae kasha ko'da coffee ne."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ni surikinka ne dole kabi abunda,nakeso idan ba haka ba sae yaga AJ.yyi murmushi .</p><p><br /></p><p>Wanda tunda suka zo zari'a hameed baiga ."murmushin AJ.ba Am sorry kaina bisa wuyana."</p><p> my brother in law,karkace zaka rabani da Rayuwata.!! </p><p>Wanda nasan hka xaka fa'da ,murmushi Hameed yyi gamida mi'ka masa cup coffee ."ni na,isa na Rabaku ai kae da Asma'u Omar Omra Zaku Rayu acikin. Inuwa da'ya a wata Rana!!</p><p><br /></p><p>" Ina hango maku kyakkyawar Rayuwa anan ,gaba."maxa shanye na ka'ra cikama wani cup ,</p><p>sosae Zancen na Hameed yabaiwa AJ.daria ,</p><p>baisan lokacin da ya murmusaba." Gamida ka'fa cup din A bakinsa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asmy b Aliyu 😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Assoe..</p><p><br /></p><p>71</p><p><br /></p><p>Ya'na ko'karin danna kansa da'kin da take wyarsa,ta katse masa hanzari ." kallon wyar yyi Angel nasa, kekiran sa kuma da lambr Nigeria."mmki sosae ya bayyana ,akan fuskarsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Da sallama ya da'ga wyar ,tattausan muryarta yaji ta dira a dodon ku'nnen sa." Yah Abdul!!</p><p>"Yes Angel ,yah Abdul ina ka shi gane??" Tayi mganar A shagwabance,</p><p>Na kira wyan sageer kashe."</p><p><br /></p><p>"Yaushe kk shigo Nigeria??"... Dan Jim tayi yarda yyi mata tambayr,</p><p>." lokaci da'ya ta rude ,a shagwabance take fadin ,mun fasamu hutun,</p><p>Ka'rshen shekara Amma fa a sudan kika ce ,zakiyi sa.</p><p>Meyasa kk canja?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>."zamuyi mgana latter yah Abdul kasan kuwa hajja na,hospital ." tana meera hospital."nasani ,</p><p>Wai ina ka shigane?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ina Zari'a ,wata tambyr zata jefo masa yyi saurin katseta ,</p><p>Mimi muyi mgana,xuwa anjima ynxu ina busy."baijira mai xata fa'daba yyi saurin datse kiran gamida kashe wyar duka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Lokaci da'ya Mimi tabi wyar ,da kallo kafin ta maida kallon ta ga Rak! Wadda ta tsareta da ido." Dan tabe ba'ki tayi mena fa'da maki."dama nasan hka xai faru ,ynxu kwata-kwata yah Abdul baya baki ku'lawa fiye da yarda yake baki Acan ba'ya ynxu son da yake maki da kulawar da ya'ke baki ya koma gurin matarsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Akwae mmki Ace yah Abdul hajja na kwa'nce a gadon Asibiti ace wae baiwani da'ga hnkalin saba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Na tsani matar sa ,cike da jin haushin yayan nata mimi tayi jifa ,da wyar ta akan soofa."</p><p><br /></p><p>A hnkali ta xauna a gefen bed ,tana juya mgan ganun Rak! Aranta ,tabbas hkane kulawar da yayan nata yake ba'ta a wancan lokacin ynxu ya ra'ge sosae ."ynxun ma kamar baiji ddin dawowar taba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>********</p><p><br /></p><p>"Yana xaune a gefenta yana rike da hnnunta na dama,</p><p>Yyi zurfi sosae wurin yimata addu'a,xuwa wannan lokacin."</p><p>."jikinsa yyi sanyi da'gowar nan da yyi yaga ,idonta ka'r akansa wani irin kallo take masa tamkar,</p><p>Yau tafara ganinsa."hka ta rike hnnun sa gagam tamkar ,</p><p>Wadda,xa'a kwa'ce mashi Cike da murna yake fa'din Alhmdullhi!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ga mmkin sa sae yaji itama tana fa'dar Alhmdullhi!!</p><p><br /></p><p>" ga ba'daya ya Rude fuskarsa ya matsa gaf da tata,yana daria farin ciki hawaye na zuba a idonsa ." My drama Queen Are yhu OK.??</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Itama dariar ,tayi gamida fa'din my Drama Queen Are yhu OK?", dai-dai lokacin Dr.Hameed omra ,da Dr.jayyed suka shigo da'kin da suke."</p><p><br /></p><p>*BARKA DA SALLAH!!*🌹</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>72</p><p> AJ.na ko'karin sakin hnnunta ta rike hnnun sa ,gagam idonta taf da kwa'llah ." Dr.jayeed ne yyi saurin fa'din karka damu Mr.meera ,matar ka bata iya tuna komae ynxu sae a hnkali tunda kaita fa'ra bu'de ido ta gani a ynxu ,Tamkar Kaine uwarta !</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kamr yarda kasan jariri idan Aka haifesa ,xa'a dinga dawainiya dashi ." hka itama matarka zaka dinga yimata ,</p><p>Zata dinga kwaikwayon abunda kakeyi ." har xuwa lokacin da tunanin ta xai dawo."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Jiki sanyayye AJ .yabi Dr. Jayeed da rinannun idanunsa,cikin kasalalliyr muryarsa yake fa'din har xuwa wane ,lokaci xae dauka??"</p><p><br /></p><p>"I don't know ,Mr.meera kajira lokaci kowane,tym</p><p>Tunanin ta xai iya dawowa dae-dae sae dae mukam mu bamusan lokacin ba,</p><p>Xamu dau'rata akan wasu drug's wandda da ikon Allah xa'ayi nasara."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Itakam Asmy duk wannan bayanin,da Dr.jayeed yake takasa fahimtr sa hnkalinta gaba ,da'ya yna kan AJ.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cike da jimami hameed Omra ke kallon,kan'war tasa ,yana yiwa Kansu jimamin abunda yasame ta,Wanda koda derection dinsa bata ka'lallaba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wata Nurse ce ta shigo Dr.jayeed ya dubeta plzzz Khadija taimaketa ,ki kaita toilet tayi wanka." Cike da girmamawa khadija ta nufi Asmy."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>."AJ yyi kar'fin halin mikewa daita tsaye ,still hnnunsa na cikin nata Cikin sanyin jiki AJ ya nufi hnyar toilet daita nurse na biye dasu." A tsorace take kallon nurse wadda,taga tana bin bayansu."</p><p><br /></p><p>K'ofar toilet din yaja ya tsaya gamida sakin hnnunta,A raunane take kallon sa ."shiga ciki Asma'u kiyi wanka ,zaro ido tayi gamida ma'ke ka'fada ,Almr baxata ba kenan,</p><p>Dr.jayeed da Dr.Hameed na tsaye gefe suna kallonsu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Fuska bbu walwala yake fa'din kina son natafi na barki anan kenan?"..</p><p><br /></p><p>Saurin girgiza kai tayi ,hawaye suka ba'llike a idonta,gyaran murya Dr.Jayeed yyi mexai hana kayi mata wnka ,Mr.meera!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>." Wani irin fa'duwar gaba yaji lokaci da'ya a hnkali ya lumshe idonsa,yana jin yarda zuciyrsa ke zafi ."ba wnkan ne, baxai iyayi mataba."ko da'ya yana gudun abunda ,xaije ya ganine ,</p><p>Wandda xae hanasa zaman lpia.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>."A hnkali ya bu'de idonsa ,da suka ka'da cikin da'ka tsawa yake bata umurni akan ta shiga toilet Nurse yama umurni ,akan taja hnnunta su shiga cike da tsoro take kallon sa,har suka shige toilet still idonta na akansa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yana jin xafin tsawar da yyi mata ,bbu wandda yace masa uffan tsakanin dr.jayeed da Hameed omra barin da'kin sukayi ,A daddare ya xauna gefen bed gamida da'fe kansa. Da hnnayen sa duka biyu."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>."Taya ma xa'ace baxae dau'ki mummunan mataki ,Akan Aliya ba ae kotu ce xata Rabasu daita."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Baisan tsawon lokacin,da ya da'uka cikin wnnnan yanayin ba,sae jin ka'rar bu'de toilet ,da'ga Blue eyes nasa yyi gamida xuba mata ido,tana dau're da farin towel a jikinta ka'to ."</p><p><br /></p><p>"Tsayawa tayi cak!</p><p>Tana kallon sa,A tsorace tana tuno tsawar ,da yyi mata da'zu."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wani irin tausayinta yakeji,nurse yama mgana akan tafita xae idar da shiryata,gamida yimata godia."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana fita ya matsa inda take ,yana ko'karin riko hnnunta."sae yaga ta da'uke kanta,</p><p>Almr fushi tayi murmushi mai kyau yyi ,ya jawota jikinsa ,duka ra'da ya shigayi mata a kunne ,</p><p>Am sorry kinji ."baxan ka'ra yimaki tsawa ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dago kanta tayi ajikinsa ,tana kallon fuskarsa,tana son tayi mgana sae dae batasan Mae xata fa'da ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ya'gane nufinta sae ya ha'da hancinsa da na'ta yana gogawa ,cikin wani irin salo." Sae yaga ta lumshe idonta ,ganin tsayuwar xata gagaresu,ya dau'keta cak ! Ya nufi gado daita sae ya'ga tana murmushi,</p><p>Wanda ya rasa ko na minene shima mu'rmushin ya shigayi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asmy b Aliyu😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>73</p><p><br /></p><p>"Yana bata tea sukaji an tu'ro ko'far da'kin ,</p><p>Mimi ce itada Rak !</p><p>Da gudu Mimi taje tayi hugging yayan nata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A hnkali ta xauna gafdashi ,ta Dan kwanto akan ka'fadarsa ,cike da shagawa take fa'din yaya baxan iya jiranka ba shiyasa muka biyo ta jirgi nida Rak ,ta fa'da tana kallon yanayin fuskarsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Murmushi dauke a fuskar Rak ta ka'rasa gafda Asmy ta da'fa ka'fadar ta ,Sistr in law yaya jikin naki??"..</p><p><br /></p><p>A tsorace Asmy ke kallonta tamkar taga abun tsoro ,jiki na Rawa tayi saurin shigewa jikin AJ."ta cinna kanta a cikin fa'deden ki'rjinsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Shaye da toka Mimi ke kallon yayan nata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yaya Abdul meya sami Asma'u hka take tamkar ba tasan mutane ba."....fuska bbu walwala ya ka'lli Mimi waye ya Baku izinin xuwa zari'a?? Yyi mganar fuska bbu,walwala ."xatayi mgana yyi saurin dakatar daita ,kutashi kuje masaukin mu ,ynxu xansa driver ya kaiku ya ka'ra sa mganr fuska bbu walwala."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A zucia Mimi tayi hnyr waje ,hka Rak tabi bayanta cike da ba'cin rae."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Suna fita ya kira Hassan driver a waya yace yaxo ya da'uki su Mimi xuwa cikin kaduna da ya'ke suna da gda a Kaduna."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A Hnkali ya da'go da fuskarta a jikinsa,Sae fa'mar gumi takeyi A hnkali ya sassauta murya kidaina tsoran ,mutane kinji habibaty!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" way'annan coursing sister's dina ne kuma tare zamu xauna dasu,na fa'da maki ki rage wannan tsoron."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A shagwabance,ta kallesa gamida tu'ro masa Dan kyakkyawan bakinta ,cikin cwt voice nata,</p><p>." take fa'din ba wannan da'yan bace taxo ta wani aza head nata akan ."shoulder naka ba."</p><p><br /></p><p>"Ta fa'da hawaye suka zubo,akan Cheek's nata ba'ki wangalau ya sa'ki yana ka'llonta ka'fin ya saki tattausan murmushi ,gefen Cheek's nasa ya lotsa a hnkali tasa Dan ya'tsanta a gun tana dannawa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana murmushinta mai kyau,dogon hancinta yaja,har Sae da tayi ya'r ka'ra ya rike fu'skarta da hnnnayen sa ,duka biyu ."cikin muryar ra'da ya'ke fa'din My wife fuskar nan taki ta fiye ba'ki da yawa ."ya kamata na xauna nayi maki make up ! Akanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A hnkali ta sauke hannayen sa akan fuskarta,</p><p>" yaya mutafi gida Dan Allah zama a gurin nan bbu ddi." Shaye da to'ka ya'ke kallonta ,ba yaya bane sunana,kina jina ."naji da'xun nan da'ya daga cikin sister's dinka" tace maka yaya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nan take taga yanayin fuskarsa ,ya sauya Sae taji duk bataji ddiba." Saurin kwantar da kanta tayi akan cinyarsa,shuru ya ra'tsa a tsakanin su ,Ra'da ya shigayi mata a kunne."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kinsan meye sunana?</p><p>Girgixa kai tayi ,</p><p>*Habiby!*</p><p><br /></p><p>Saurin tashi xaune,tayi ta washe bakinta dama shine sunan ka,? Yana da ddi ." a hnkali ya da'ga ma'ta gira oya to fa'da naji."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ya'tsanta ta da'ura a bakinta ta da'ga kanta sama, alamr tunani dan murmushi,</p><p>Ya saki da alamr ta manta tunda ya'ga tayi hka." A hnkali ta kallesa ta Langaba'r da kai gamida ba'ta rae ,na manta ka tunamin."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>."sunan xaiyi min wuya ,ta fa'da gamida ki'fta idonta murmushi ,mai kyau ya saki ."HABIBY !!</p><p>"Xakice,</p><p><br /></p><p>Yehh na tuna ta fa'da gamida clapping hnnunta,cike da jin ddi,tamkar wata baby gal!</p><p><br /></p><p>Oya said it.!</p><p><br /></p><p>" yyi mganr,cike da jin ddi yatsan ta tasa a baki ,tayi Ra'u ra'u da ido ,na manta kuma."tunamin.!</p><p><br /></p><p>Har ya "bude baki xaeyi mgana tayi saurin rufe masa ,baki da tattausan,hnnunta ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yehhhh !! Yehhhh !!</p><p><br /></p><p>Na tuna ,Habibyy!!</p><p>Ta fa'da cike da jin ddi ,da ya'r dariar sa yake kallonta ,har abada baxata canja ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Komai nata,na ya'rane yana son life style nata,duk da tana cikin Rashin tunanin ta,</p><p>."Halinta yana nan ,</p><p><br /></p><p>."A hnkali ya ka'lli agogon dake manne a hnnunsa,</p><p>Ya mike tsa'ye hannayen sa ,zube cikin aljihun wandon sa."</p><p><br /></p><p>Habibaty !</p><p>"Ba'ra naje naga Dr.jayeed inason ya bamu sallama a yau."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tana ko'karin fa'dar abunda ya gama fa'da ynxu ya sunkuya ya bata ,light kisses a tattausan la'bbanta ,ba sai kin fa'da ba jirani ina xuwa da haka ya kunna mata game a wayar sa,</p><p><br /></p><p>Kijirani ynxu xan dawo,Hnkalinta na kan waya ta da'ga masa kai kurum."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ba da'ga kai xakiyi ba Allah ya kiyaye xaki ce,A hnkali take fa'din Allah Sae kuma ta da'ga tana kallonsa da almr ta manta na ka'rshen ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Oya yi game naki bari naje na dawo yana fa'dar haka ,ya juya yabar da'kin xuwa office din Dr.jayeed.[Truncated by WhatsApp]</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p>74</p><p><br /></p><p>Suna xaune a sit din baya ,yyin da da'yan body guard dinsa ke jansu A mota."....yyinda Queen din nasa ,ta wani shige a jikinsa tamkar wadda ,za'a rabata dashi .</p><p>Hello sageer insha allahu gobe muna hanya ,ta jirgi xamu biyo ka'ga ya'r rigimar ka sae da ta biyoni,</p><p>Tsaki ka'dan sageer ya'ja dama ae kai ke sangartata ."</p><p>Gaba'daya Mimi ta canja bansan meke damunta ba ,Sageer ya ka'rasa mganar in a low tune.</p><p><br /></p><p>_ynxu hka fa fushi ta hauyi dani ,maza ya kamata kashigo da wuri fah,cewr sageer ina tunanin Aliya xa'a shiga da ita ko'ta har sun da'uki lauya_",insha allahu so ya ya'r rigimar taka??" A hnkali AJ ya Shafa kan Asmy ya sa'ki lallausan murmushi,gatanan surutun baya kanta yau ,da ynxu ta fa'ra maimaita abunda nake fa'da.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_A gaisheta ohryt xataji,da haka sukayi hanging call din_".</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Zaune suke a babban falo sunyi kaca-kaca dashi Mimi na sipping juice a glass cup,yyinda Rukaiyya kecin Egg roll's." Da sallama ya shiga babban fa'lon hnnusa,na cikin na Asmy Wanda sae bin koina,take da ka'llo .</p><p>Kallo da'ya xakayi mata kasan,a tsorace take ciki -ciki Mimi ta amsa,da sad face nata ."</p><p><br /></p><p>"Gaban su ya ka'raso ,cikin nuna kulawa akansu yake fa'din kunci abinci kuwa?" Mimi aranta take fa'din ina xakasan munci abinci kana tareda wananna, manyar."</p><p><br /></p><p>Ta'fada tana bin Asmy da harara kafin tamaida idonta,akan Darling brother din nata.".....Dan tsaki AJ yaja ya ka'llesu kuje kuyi wnka kuxo muyi dener.' Dan lokacin kusan ka'rfe takwas da Rabi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da hka yaja hnnun Asmy lokaci,daya suka bita da harara,cike da ba'cin rae Rak tamike tsaye hawaye suka ba'lle a idanunta ta nufi up stair's da Dan gudu."tsaki Mimi taja bakiga mashan wahala ba yarinyar ni zan xauna ina son maso wani ko sageer da muke soyayya ,ae baxan xa'ke akan soyayyar sa haka ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>******</p><p>Tana xaune a gefen soofa ,ya ba'lle botin din rigarsa ,yabr farar vest da dogon wandon Jean's ,yadan kalli inda take yaga tayi kwa'nciyrta bafa barci xakiyi ba Queen wnka xamuyi ,Muyi dener sannan ki kwa'nta ya fa'da gamida saukoda dogon wandonsa,na Jean's yana gama cirewa ya ka'raso gurinta ,oya taso kigani yinwa nakeji ,ya fa'da a shagwabance,</p><p> "Yarda yyi mganr sae yabata daria ,shiya taimaka mata ta cire doguwar rigar jikinta.ya Rage daga ita sae bra da pant."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Jayowata A jikinsa yyi yana shinshinar wuyanta, lumshe,idonta tayi da'yan hnnunsa na rike da ku'gunta da'yan kuma yana ko'karin ba'lle bran nata shafata yake koina yana sauke numfashi,gaba da'ya AJ.ya gama fita a hayacinsa dakya'r yaja hnnun ta zuwa toilet.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*WATA RANA !*[Update 7September _2017_by Asmy b Aliyu]</p><p><br /></p><p>75</p><p><br /></p><p>" A hnkali suke saukowa ,dga kan stairs din ,shiyana cikin bakin wando na Tree Quarter da red din T.shirt Mae guntun hnnu ita kuma tana cikin rigar body hook, wadda take Half gown fara so'l kanta cikin hular net pink colour hnnun sa,sa'rke cikin nata............Mimi ce xaune akan soofa' dake xagaye ,da falon xuwa wannan lokacin tayi wnka ,kayan barci ne a jikinta masu da'n kauri ,tayi nisa sosae cikin chart dinda take taji an fisge wyr ,a fusace ta da'ga manyan idonta karaf ,cikin na yayan nata." Asmy mexatayi inba da daria ba ,daria take sosae abunda ya k'ular da Mimi kenan ,Cikin shagwaba hka idonta taf da kwa'llah take dan turo ba'kinta." Wat wrong wit yhu Angel ??"Ya fa'da yana kallonta,ko'karin amsar wyarta takeyi ya hanata."oya taso muje Aci abinci Rak fa ya fa'da gamida Jan hnnun Asmy ya nufi dinning side,tana kumbure-kumbure tabi bayan su,oya yi serving dina bbu musu tayi serving nasa, ga mmkin ta sae taga bashi keci ba Asmy yake baiwa a baki,ina tambayr ki Rak kinyi min banza." Bata jin ddi ne ,tayi mganar a takaice meke damunta ??" Zuciyr Mimi sae halbawa takeyi,tana son ta fa'da masa gaskiyya Amma tana tsoron yayan nata."tasha ji A bakinsa baxai ta'ba son maccen da ta'buda baki ta'ce masa tana sonsa ba."itakam ya xatayi ,tana matukar tausayawa ya'r uwar tata."</p><p><br /></p><p>"Hii!</p><p>Yyi clapping hannayen sa,akan fuskarta firgigit tayi tana kallon sa,mekike tunani kuma?,Anya kuwa lpian ki Qlau Angel ya fa'da gamida da'n Shafa gefen wuyanta ,yana ko'karin kai Abinci a bakin Asmy sae yaga ta ture hnnun nasa,A fusace ta mike tsaye ,ta nufi up stair's da Dan gudu,ko waiwayen su batayi ba,zuciyr sa na halbawa yabita da ido yana ko'karin tashi caraf! Mimi ta rike, masa hnnu idonta,taf da kwa'lalh cikin muryar son tayi kuka take fa'din ynxu Yah Abdul kadaina sona ko??" Kafison matar ka akaina ,saurin girgixa kai yyi ba haka bane ,mimi kin dae san Asma'u tana cikin wani hali........dole a tausaya mata sanadina ta shiga wannan halin,meyasa kika canja meyasa kika daina sonta? ?" Nasan kiji Rashin lpiar Asma'u a bakin Sageer ,Meyasa baxaki tausaya mata ba Mimi,yaya kaima Abun tausayine,ji yarda karame lokaci da'ya da ynxu,Auren gida kayi da haka na faruwa??" Murmushi mai kyau ya saki bbu wandda ya isa ya ke'tare gaddarar sa A rayuwa Mimi,</p><p>Na Fahimceka ,yah Abdul Anan tayi serving dinsa,tashiga basa abinci duk da cin Abincin kurum yakeyi hnkalinsa da tunanin sa ga ba'daya yana wurin Asma'u........shi ya raka Mimi zuwa da'kinsu koda ya shiga da'kin nasu ,Rukaiyya na a Toilet nan yyi masu sae da safe kai tsaye da'kinsu ya nu'fa yana tura ko'far da'kin ya hangota kwa'nce akan soofa ,ta dunkule guri da'ya da sassarfa ya Isa gurinta......cikin raunanniyr muryrsa yake fa'din Habibaty!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Banxa tayi masa,hka yaji tana sauke Ajiar xuciya a rikice ya da'gota hawaye yagani ja'ge-ja'ge akan fuskarta ,nan take AJ.ya Ru'de jawosa jikinsa yyi sae ko'karin kwa'ce kanta take tana turasa da ka'rfi gagam...........ya'riketa Meya faru my Queen ya fa'da cikin Rawar murya ,tana dukan kirjinsa tana fa'din bakai bane,Ka'ki bani abinci ka'tsaya kana kula wannan Angel din ta fa'da hawaye suka ka'ra gangarowa a idonta."....... Sae yanxu ya ga'no rigimar Shafa bayanta ya fa'rayi a hnkali sa'annan ya shigayi mata " Ra'da a kunne ,koni Asmy banji me Mr.AJ.ya fa'dawa Mrs.AJ.ba sae naga lokaci da'ya ta kya'kyale da daria tana cinna kanta cikin fa'deden kirjinsa,cakulkuli ya fa'rayi mata sae kya'lkyalar daria takeyi ajikinsa tana zillo ya'rda ta sakan kance ajikinsa ,Mood din AJ. Ya fa'ra canjawa ." Daukar ta yyi cak ! Xuwa kan gado ,hnnun sa ya sa'ka ya kashe wutar da'kin yabr marar haske A hnkali ya fa'ra kissing din wuyan ta yana "Shafa na shanun ta,sae nishi takeyi ." da almr ta fa'ra sabawa da wannan karatun nasa ,ya tsaya cak ! Yana kallon ya'rda ta lumshe ido dan murmushi ya saki ya cigaba da romancing dinta, da hka ya samu ya cire rigar jikinta ,koina na jikinsa Rawa ,yakeyi ga ba'daya ya fita hayacinsa,bakinsa ya ha'de danata sae tsotsa yake tamkar ya samu swt, itama ta Rikesa gagam" tana ka'rban sakunan da yake aika mata dasu,yafi minti Ashirin Akanta ,sa'nan ya iya kya'leta komawa ,gefe yyi gamida yin ruf,da ciki yna mae da numfashi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sun da'uki minti biyr A hka ,sa'annan ya da'gata cak !! Zuwa toilet.</p><p><br /></p><p>*Writing & Posted by Asmy b Aliyu*.💖</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>76</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sanye take cikin nighty gown dinta ,light orange wyr dake hnnunta take wasa dashi ,ta xubama Rukaiyya ido wadda tayi kwa'nce ruf da ciki tun lokacin da ta fito daga wanka ta'ki kula Mimi ,ko kayan barcin ma takasa sakawa ,daga ita sae Dan ka'ramin towel ajikinta Wanda Rabin mamman nata duka a waje." Da kuma santala-santalan cinyoyin ta ,A fusace Mimi ta fisge wyr hnnun Rak wadda tayi nisa a chart din da ta'keyi ,badan tana jin ddin sa takeyin sa ba Dan kurum ya ra'ge mata zafin ciwon dake addabar xuciyr ta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wat wrong with yhu Rukaiyya ?" Ni na maki laipi da ,xaki hau fushi dani ."ina fa'damaki fushi bashine mganin matsalar kiba."kitashi musami solution ,Dan bakiji ya'rda yakejin yarinyr nan a ko'kon ransaba."da almr xae iya sa'bawa da ko'wa harni da yakeji dani kuwa." Seriously na tsani yarinyr nan ka'ro na fa'rko a rayuwata! Da naji natsane ta I just I hate her ,I really hate her,da sauri Rak ta mike daga kwa'ncen da take ,ta kalli Mimi meya faru kuma?"anan Mimi ta kwa'she komae ta fa'da mata ,A tunani na Mimi mexai hna ki tunkari sageer da zancen maybe xae iya saurarar Sageer."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin zarowar ido take fa'din Rak wat wrong wit yhu ,Are yhu out of your mind.??" Cikeda jin haushin kalaman ta tayi saurin katseta ,kinga Mimi idan baxaki taimakeni ba ,kirabu dani nixanyi ma sageer mgana."baki wangalau Mimi ta saki tana kallon haukan Rak! Aranta take fa'din lallai so sone ,OK gaki gashi amma wlhi komae ya fa'ru kada ki kuskura ,kiyi kuka dani ."bakisan waye sageer bane ,shiyasa abunda yah Abdul yakeso shi ya'keso baxae ta'ba fahimtar kiba !...........ni na fa'da maki haka ,so mark my words ,tana gama fa'din hka ta dauki da'yan pillow ta koma kan soofa ,tayi kwa'nciyr ta gamida manna eirpice akan kunnen ta." Cike da takaice,Rukaiyya ke kallon Mimi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_the following day#_</p><p>"Sanye take cikin wata doguwar rigar armless, dark pink,ka'farta sanye cikin Vinci hill" black sae kunnen ta da'ke sa'kale da ya'n kunne diamond da sa'rkarsu sae dau'kar eyes..........sukeyi ,simple make up ne akan fuskarta ,sae Dan ka'ramin veil da tayi rolling kan ta dashi black colour Mae da'uke da wasu irin duwatsu a jikinsu masu,ra'tsin pink colour." Tun daga kan stairs ,kallo ya koma Kansu." Yyin da AJ.yake sanye cikin black trouser, da yellow din shirt ."Wanda tayi balain ka'rabarsa ,sae agogon dake manne a right hand nasa, kirar Rolex.. "Sunyi kyau sosae."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Da Dan murmushi Mimi ta ka'rasa tayi hugging yayan nata, gamida fa'din good morning my darling brother how was your night??" Hop yhu sleep well,a hnkali ya da'go daita a jikinsa murmushi da'uke a fuskarsa ,cike da far'a yake fa'din my night was splendid ,my Angel I enjoyed it so much." Gud my own brother in d world am glad to hear DAT."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A hnkali ta sa'kesa tayi hugging Asmy ,morning my Sistr i n law ,Mimi muka'rasa dinning flight din karfe goma,xamubi." Xuwa Bauchi dae -dae nan Rak ta ka'raso cikin shiga ta alfarma sae kamshi ke tashi a jikinta." Right hand nata. " ta mikawa AJ ,ya rika hnnun nata." Morning my Rak ! Yyi mganr yna kallon ta morning 2 Yah Abdul ya jikin naki ??" Hop kin samu sauqi ,nasamu sauqi ....ga ba'dayan su suka nufi dinning ,Rak ko kallo Asmy bata isheta ba." egg Roll,da toast bread sukayi break fast dashi sae kuma farin Coffee, suna gamawa driver yajasu xuwa air port ,Wanda tun ka'fin a isa Asmy ta fa'ra barci ajikin AJ." Cikin drug's din da take using dasu akwae Mae sa barci."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Take note !</p><p>Kuyi manage ,da wannan gobe baxan samu damr yin typing ba ina busy....✍🏻</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>©Haske writer's Association..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>77</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sageer ne yaxo da'ukan su a air port ,har lokacin Queen din tasa na manne dashi a mota ." sageer sae tsokanar ta yakeyi bata kulasa ba ,AJ.yaja dogon hancinta bakya ji ,Abokina namaki mgana shima kika wani sharesa,? Yyi mganr yna kallon cikin idanun ta ."itama kallon cikin idonsa takeyi yyi saurin hura mata iskan bakin sa ,A hnkali ta lumshe idonta gamida kanta acikin chest nasa, duk abunda ke faruwa idon Mimi da Rukaiyya na Kansu ,bbu Wanda ya ka'ra fadin uffan har suka ka'raso a parking lot ,yana gama parking hajja aunty sadiya aunty ,salma suka ka'raso gaban mota da ,sassarfa AJ.ya ba'lle marfin motar batare da ya jira Guard dinsa ba ." ya Rungume hajjan saa, cike da farin cikin samun lpiar ta ." A hnkali ya dago ya subbaci goshinta ,kwa'llar farin ciki ta tsaya ,akan kwa'yr idonsa I love yhu so much my granny nayi farin cikin samun lpiar ki ina godia ga Allah mahaliccin mu. "Hka AJ.ya koma tamkr karamin yaro a gaban su,hka yyi hugging Aunts nasa cike da farin ciki..."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hajja ce ta ka'rasa gurin Asmy wadda ke ra'kube a jikin mota ,tana masu kallon rashin sani cike da tsoro hajja na kai hnnunta jikinta tayi saurin kaucewa a tsorace tareda furta nooooo!! Da ka'rfin bayan AJ.takoma ta lafe idonta taf da kwa'llah jikinta koina karkar wa yakeyi ,dama su hajja sun San matsalar AJ.yyi masu bayani a wya so basu wani damuba ." dama sun San hka xata kasance ,ga badayan su suka nufi cikin gda yyinda akabar Sageer da Mimi a waje ,sae famar cika takeyi tana batsewa ."A hnkali ya sassauta murya wai meya samu gimbiyr tun a air port take famar cin mgani ,fadamin ynxu kuma meye laifina??" Ya fa'da yana binta da kallon so ,folding din hnnunta tayi akan kirjinta ta wani ba'ta rae tana turo dan kyakkyawan bakinta ."Mae ka'rama fuskanta kyau 'cike da shagawaba ,take fa'din bakai bane ."kadaina sona ynxu kaida ya Abdul kuyi ta ma mutum fa'da ,,Am sorry my lady nayi laipi kaina bisa wuyana." Bakida da'ukar uxuri ne Mimi kona fa'da maki uzurina bakya ya'rda ,da kinkira wyana kinji busy shikenan sae ki hau fushi baxaki tsaya kiji dawa nake mgana ba." Shikenan komae ya wuce ynxu tayi mganr a shagwanbe ,shima murmushi yyi oya muje ciki ,kice anjima nashigo ta'di tadan hararesa tana ,murguda masa baki ,niki ke harara nodding kanta tayi "gamida Kwasawa a guje ,Dan bawani babban aekin sa bane ya cafkota."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tsayawa yyi cak ! Yana kallon fuskokin da bae kaunar ya gansu a rayuwarsa, Aliya mamy da kuma mommy " cike da mmki yamaida kallonsa gun su Aunty sadiya tambayoyi fal 'abakin sa ,meya kawo Aliya anan ita dake rufe cikin cell,Aliya na ganin sa ta rarrafo gabansa ,lokaci da'ya ta rame tayi wani irin ba'ki ku'raje duk sun ba'tamata fuska ,Zaman cell na sati daya rak! Shine ya canja ta haka? Lallae Dan Adam ba abakin komae yake ba." Zuciyar sa sae wani irin tafasa takeyi ,hnnunsa da'ya dafe da goshinsa nan take idonsa ya ka'da yyi ja ,jiniyoyin kansa sun fito ra'dau a goshinsa almr ransa yyi balain ba'ci ,hnnu Asmy kurum yaja ya nufi up stair's ,Aunty sadiya na 'kwa'la masa kira bai bi tako kanta ba ,yna shiga master bedroom din nasa ya murxawa ko'farsa key ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A sanyaye Aunty sadiya ta kalli hajja ,kinga irin abunda nake fa'da maki ko hajja ,nasan baxae ta'ba yafe masu ba." Tun fa'rko banso kika tilasta sageer yayo belin Aliya ba. "Naso kibari Abdul jabbar ya dawo ,kiyi mgana dashi ta fahimta ,bana son wannan fushin nasa." Granny batace komae ba a sanyayye ta zauna da'ya daga cikin Sofa's din dake jere a falon ido taf ,da kwa'llah Aliya ta rarrafo gaban hajja ta kama ka'farta kiyimin rae Hajja ,wlhi na tuba nayi nadama sosae sharrin zuciya ne bana da ku'din da xan ka'ra da AJ.akan shari'ar nan ,nasan ka'rshena baiwuce gidan yari ba Dan haka nayi nadama."hka nayi niyyar amsa laipina a ko'to mami ce ta da'ge akan dau'kar lauya hka tace duk na kuskura na amsa ,laipina sae ta tsinemin ." hawayen da suka gangaro a idonta ,ta da'n share cikin shesshekar kuka take fa'din Hajja nasan kina da zuciyar imani tunda ,har kika fito dani acikin cell kikayi ko'kari kika janye sharia ,da zamuyi a ko'to ,da ka'rfin ki da Aljihunki ,hajja masu xuciya irin Ku ka'lilan ne a dunia nayi maki alkawari idan Abdul jabbar ya yafemin ,xan bar rayuwarsa xan koma ga Allah a karshe xanje na shimfida ,kyakkyawar Rayuwa."ta ka'rasa maganr tana gunjin kuka." Mae ta'ba zuciya." </p><p>Tsam ,hajja ta mike tsaye ta nufi up stair's kowa binta yakeyi da ido."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yana gama cire kayan jikinsa ya Daura towel a kugunsa ,ya juyo daniyr ya cire mata nata kayan ,ya hangota tsakkiyr gado tayi tsaye rije da kugu tana kallon tangamemen ka'ton pic dinsa ,Wanda ke manne a bango da'kin ta kurawa pic din ido , tamkr mai tunanin wani Abu ,da azamr sa ya cimmata kan gadon sae taji anyi hugging dinta ,ta baya ya da'ura kansa a wuyan ta,cikin muryar ra'da yake fa'din mekike kallo ,Dan murmushi tayi tana mutsu-mutsun kwa'ce kanta daga ri'kon da yyi mata ." sae ya juyo daita tana fuskantar sa ,gashin kirjinsa ,ta kura ma ido wandda yake kwa'ce lu'f hnnun ,ta da'ya tasa tana shafawa wajen cike da sha'war son tayi wasa ,dashi tsikar jikinsa yaji tana tashi a hnkali ,ya kalleta a kasalance wanka xamuyi Queen taso muje ma'ke ka'fada tayi tareda kwantar da kanta a jikinsa ta cigaba da wasa da gashin kirjin nasa ,jin tana so ta nemi da'ga masa hnkali yyi Saurin daukarta cak ! Xuwa toilet ka'fa yasa ya tura ko'far toilet din .</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Team Drama Queen*.💖</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>78</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Doguwar rigar body hook ce ajikinta ,red colour mai yankakken hnnu." Har ka'sa kanta cikin hular net black ,hijab ya da'uko mata dogo har ka'sa ya taimaka mata ta sa'ka ,ya kalleta yace oya kiyi sallah la'sar ." nima ynxu masallaci na nufa ,yyi mganar yana kallon idanun ta ,kafin tayi mgana sukaji bugun ko'fa daga ba'kin ko'far Hajja ke fa'din Abdul jabbar! Kaxo ka bu'deman ko'fa ransa yaji ya ka'ra ba'ci ya rasa maike damun hajja ,anya kuwa malamin nan ba yaudarar sa yyi ba ,dakyar in Aljannun nan sun bar kan Hajja ." Asmy na kabbarta sallah ya nufi ko'far a hasale yasa key ya bu'de ko'far kallo da'ya yyi mata ya da'uke kansa ,cikin tausasawar murya ,take fadin Abdul jabbar my dear kaxo muyi mgana,cikin ha'de rae yake fa'din in dae mganar su xakiyi min ka'rma ki fa'ra kije duk abunda kikeso na amince shikenan amma banason,na dawo masallaci nagan su acikin gidana ."xatayi mgana yyi saurin ka'tseta granny plss ,ya'fada gamida ha'de hnnayen sa guri da'ya idonsa ya ka'da yyi ja,ta hanyar balcony dinsa yabi xuwa masjid Dan baya maso ,yako ma falon yyi tozali ,da fuskar da'ya daga cikin su."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ganin yarda take saukowa akan stair's din ,yasa suka ka'raya Aunty sadiya ce." Tayi saurin xuwa ta rikata,kinga Hajja plss ki daina ,dagama kanki hnkali da yawa ki kyalesa kurum nasan wata rana ,Abdul jabbar xae sauko Dan kansa basae kin tilasta masa yafiya ynxu -ynxu ba ."jiki bbu kwa'ri su momi da Aliya sukayi masu sallama."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>."Misalin ka'rfe kusan shidda na yamma ya shigo gidan kai tsaye up stair's ya nufa ka'ro sukaci da Rukaiyya ,Ta Dan tsaya tana kallon sa ,yah AJ.Ina kashiga ne??" Fuska da'ure yake kallonta ,Dan yaga alamr yaran nason rainasa rana tsaka ,meye matsalar ki ?? Yyi maganar fuska daure tadan ta'be baki kamr yarda ta lura .......he is not in d good mood itama sae taxama serious ,dama Hajja ce tasa na kawowa matar ka Abinci ina shiga ,ta wani fasamin ihu sae kace mahaukaciya." Ni wlhi haukan Asma'u tsor.........Rak!! Ya 'fada da ka'rfi gamida daka mata wata irin tsawa ,wadda bata ta'ba tunanin yayan nata ya iyata ba." Am warning yhu for d last tym.kika ka'ra kiran matata ma Haukaciya ,xan mareki ,cike da jin haushinsa ta sauka down stairs da gudu tana kun'kuni .........wani dogon tsaki yaja ,tura ko'far da'kin yyi A bakin ko'fa ya sameta ma'kure ta ha'da kai da gwiwa ,tana jin ka'rar bude ko'fa ta da'go idonta da suka ka'da sukayi ja,da almr taci kuka har ta gaji hnkalin sa yyi balain tashi ,tana ganin sa ,ta Mike da sauri taxo ta rungumesa gagam ,yana jin bugun zuciyr ta." Da sauri da sauri .....da'go kanta yyi fuska cike da damuwa ya sassauta murya a hnkali my Queen meya saki kuka??" Ta share hawayen idanunta ,cikin rawar murya take fa'din Dan Allah ka'rka ka'ra barina ni da'ya Habiby wlhi tsoro nakeji ta fa'da Gamida ka'ra tusa ka'nta ajikinsa ,ka'ra riketa yyi gamida da'n buga bayanta alamr rarrashi,duban sa yakai kan center table " Ya'ga kololin Abincin da Rak ! Ta ka'wo masu dolema ya tashi ,Tsaye yaxama dole yadinga saka Asmy jikin Hajja,dan baisan ya'rda xayayi daita idan ya fita office ,jibi da'go fuskarta yyi ajikinsa ,harshensa,</p><p>."Ya sa'ka yana lashe hawayen idonta ." daina kukan Hkanan my Queen , baxan ka'ra tafia na barki ba ,oya muje kici abinci cikin nan naki najin yinwa ,ya fa'da gamida kai hnnun sa akan shafaffiyar marar ta ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>."Around 9:00pm.na dare,</p><p>Mimi ce taxo up stair's </p><p>da gudu tana kwa'lawa yayan nata kira ,da ka'rfi ga ba'daya agigice take ..."jin muryar Mimi yyi saurin tura Asmy gefe dake jikinsa da sauri ya diro akan gado ya isa ko'fa da gudu xuciyarsa na harbawa kusan ka'ro sukaci Yah Abdul!!</p><p>Mimi irin wannan ,kira hka fa lpia? Yah Abdul Hajja,Agigice yake fa'dar mai yasamu Hajja gashi can ta.....bata ida ka'rasawa ba ya ra'ba ta gefenta da gudu ya'ke sauka daga down stair's "......A hnkali Mimi ta maida kallonta kan Asmy mugun kallo tabata gamida binta da tsaki ..."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Family doctor ne yagama dubata ,har ya Daura mata drip ,gamida yimata allurar bar'ci Har mota AJ.ya ra'kosa yana ka'ra Jadda da masa ,akan su kula da ,tashin hnkalin ta ." Da kuma kiyaye cin Abincin ta har da ulcer,na damunta musabaha ,sukayi yyinda AJ. Yake fa'da masa insha Allahu ,xaya kula da hakan yana nan tsaye ,har motar Dr.Ahmad tafita daga get din gidan su jinginawa yyi ajikin wata mota ,ya ha'rde hannayen sa akan ki'rjinsa yyinda ,Ya da'gan kansa a hnkali gamida ku'rawa sararin samaniya ido ,wadda taxama ba'kikirin ha'dari ne sosae agarin lo'kaci da'ya yaji ,marar sa tayi wani irin juyawa bbu shiri ,yyi saurin sa'ka dayan hnnun sa gamida da'fe gurin." Tareda karanta duk addu'ar da taxo ba'kinsa ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A daddafe ya ka'rasa cikin fa'lon nasa akan sofa ya xube yana maida numfashi a hnkali."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>B.Aliyu✍🏻</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu..</p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>79</p><p><br /></p><p>"Yafi minti goma ,dunkule a hka hnnun sa na acikinsa ,dakyar ya daddafa ya nufi up stair's tafia yakeyi yana layi ,ko gabansa baya gani dakya'r ya tura ko'far master bedroom din nasa ." hangota yyi can tsakiyar gado tayi Ruf da ciki ga iska na ka'da fararen labulayyan ,dake jikin windows ,dakyar ya samu ya Rufesu Ruf !! A hnkali ya hau kan gado gamida jawota duka ajikinsa ,sae yaga tana ture masa hnnu a fusace ta mike xaune shaye da Toka take kallon sa idonta taf da kwa'llah yana so yyi mgana ,ya kasa sae rawar sanyi yakeyi dakyar ya furta ."kiyi hkuri my Queen kiyimin rae xan rasa raina wlhi ,karki hukuntani a wannan hanyr baxan iya cigaba da rike wannan Alkawarin na'ki ba ya'r ka'ra ya sa'ka gamida da'fe marar sa da duka hnnun sa duka biyu ,lokaci da'ya kuma sukaji wata irin ka'rar tsawa gamida saukewa da Ruwan sama masu ka'rfin gaske a tsorace ta shige jikinsa ,jikinta koina Rawa yakeyi hka yaji jikinta da mugun zafi sae kakkarwa takeyi tana tuttusa kanta,cikin ki'rjinsa lokaci da'ya kuma ta fashe da kuka mai tsuma xuciya."hnnunsa yasaka cikin rigar ba'rcinta a hnkali yana Shafa bayanta." Hka yana hura mata iskan bakinsa ,a kunne cikin wani irin salo ya'ke shinshinar gefen wuyanta ." da hka ta fara amsar karatun nasa ,duk da xaxxabin dake Neman Rufeta ya Riga ya sabar mata da ,hakan sosae karatun nasa kemata ddi A hnkali yake tafiyar daita cikin wani irin salo ,soyayyar ta zallace acikin kwa'yar idanunsa." Ga ba'daya sun fita hayacinsu sae nishi sukeyi Harshen sa yana akan ra'men cibiyarta Romancing dinta yakeyi sosae tana tayasa ,duk yabi yafita hayacinsa kayan jikinsa ya samu ,ya cire duka "kafin ya cire ya'r ficikar Rigar barcinta anan AJ.ya ka'ra gigicewa ,yafi minti Ashirin akanta ." A hnkali ya dauketa cak xuwa Toilet dae -dae lokacin da Agogon bangon da'kin ya nuna ka'rfe goma sha da'ya na dare, Ruwan sama ake zabgawa sosae ,yanayin yana yimasa ddi sosae ." tana xaune a gefen gado daure da Dan karamin Towel a jikinta,sae rawar sanyi takeyi. " tana cikin wannan yanayin ,yafito sanye da Rigar wanka ash colour " murmushi yyi a hnkali ganin yarda take rawar sanyi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Set din kayanta ya nufa ya ciro mata dugywar Riga marar nauyi ,white colour ha'de da hijab na sallah ,oya taso asaka muyi sallah cikin da'n Turo baki take ." kallon sa Habiby wane irin sallah kuma Dan Allah ,nayi sallah fa da'xu yarda tayi mganar yabasa daria ,ra'ge tsawo yyi ." gamida tallabo ha'barta yana kallon kyawawan idanunya ,wannan daban ne my Queen !! Yana kuma da lada ,tsayawa tayi tana kallon sa tamkar me karantar wani Abu a fuskarsa ,ladar meye ?? Yaji tajefo masa tamabyr lokaci da'ya ,rasa yyi Mae xae fa'da mata ba'kinsa ya Dan kai gaf da nata ." yadan kama ,lebenta na ka'sa ya Dan ciza cike da shagawaba take fa'din Auch!! Tareda rike ba'kinta kukan shagwaba ,tasaka masa da sauri ya da'katar daita." No no my Drama Queen pls don't crying kinji ni Allah baxan yardaba sae na Rama OK." Gashi ki rama ,tako kama ba'kinsa ta ciza sae da AJ ."ya sa'ki ka'ra sakin bakin tayi da sauri ta'mike tsaye tana masa daria gamida Dan tsalle ,Bae kulata ba ya mike tsaye ya nufi set din kaya'nsa ya Ciro nighties dinsa milk masu kauri ,ya saka anan ya jasu sallah."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ture cup tea din tayi a gefe da ido yabita meya faru kuma na ko'shi sanyi nakeji ,ta fa'da gamida kwantar da kanta a ka'fadar sa ta takure guri da'ya ,a hka yagama shan Ruwan Lipton dinsa ,gamida shan magani ,kashe wutar da'kin yyi gamida barin marar haske ....... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" wasa yakeyi da kirjinta ,sosae yana mata wani irin romancing kisses Mae wuyar misiltawa ,ganin yau salon na habibyn nata ,ya fa'ra canjawa sae ta fa'ra yimasa kuka tana tutturesa." Amma ina AJ.baima San tanayi ba ,Dan yakai ga'bar dabaxai iya barin taba." AJ." Baibar Drama Queen din nasa ba,sae da ya maida ita cikakkiyar macce amma fa yasha ihu kuka da majina da cizo ka'rshe some masa tayi ........[Truncated by WhatsApp].</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>80</p><p><br /></p><p>A around 5:00@m na asuba dakyar yyi mata ,wanka har lokacin dakyar take fitar da numfashi kuka takeyi masa mai cin rae ta'ki barinsa yako da Rikata ne ,gaba da'ya ta haukace masa,idonta sun kumbura sabida tsabar kuka har muryarta,bata fita.........suna gama sallar asuba ta dunkule guri da'ya a saman Capet din sallah ,sae rawar sanyi takeyi." Xaune kurum yyi ya zabga uban ta gumi yasata gaba ,yana kallonta ."Albarka yake samata wani gefe na xuciyrsa kuma, yana da ya danin Abunda yyiwa Queen nasa ,A round 6 na safe ya da'uki car key cak ! Ya da'gata xuwa mota sae ko'karin sauka take ajikinsa da ka'rfin tsiya ka'rfinsa yasa duka ya matseta akan fa'deden kirjinsa bbu musu ta kwa'ntar da kanta a ki'rjinsa gamida fa'she masa da kuka mai Sosa xuciya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kai tsaye Sameer meera hospital ya nufa daita ,yana gamà parking cikin ,sanyin jiki ya fito daga motar,side dinta ya dawo ya bu'de ma'rfin motar a hnkali..........kanta na cikin cinyoyinta Yarasa yarda xaeyi daita ,kukanta ba ka'ramin Sosa masa xuciya yakeyi ba,hnnun sa yakai a kan ka'fadar ta a fusace a kuma tsorace ta janye ,cikin dasheshiyr murya take fa'din ni bana so katafi ka kyaleni ta fa'da zafafan hawaye na xuba akan kuncinta ." A hnkali yake fa'din am sorry to fito muje kiga likita kinji ,ya fa'da tamkar yana tsoron yimata mgana."...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A hnkali ta fito daga motar ,tana da'ga ka'farta da'ya ta kwa'la wata irin ka'ra bbu shiri AJ. Ya rikota a gigice yana da'go kanta tuni ta suma da'ukarta yyi cak xuwa cikin ,hospital hnkalinsa a tashe duk inda ya wuce ma'aikata sae kwasar ,gaisuwa sukeyi ko kallon su ,bayayi balan tana yabi takansu."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dr.phartyma zahra sae kallon yanayin ,sa take gaba da'ya yabi ya susuce ."sir kajima amaryar mu da yawa fa sae da akayi mata dinki,sir meyasa bakabi A hnkali ba ??" Lokaci da'ya Dr.zahra ta jefo masa tambayr samun kansa yyi da jin kunyar ta ,kansa na akasa cikin sexy voice nasa mai kasheta ,yake fa'din Am sorry Dr.nayi laifi da haka ya tsuke ba'kinsa yyi shuru ,ok tom.karka damu xuwa ka'rfe goma hka na safe xata fa'rka na mata Allurar barci ,wannan matan naka ,tana da Ra'ki duk da hka." Murmushi mai kyau yyi gamida Shafa sajensa,A hnkali ya da'go kansa yna kallonta ,murya can ka'sa ya'ke fa'din Really??batace komae ba ta dauke kanta ,ya kamata kaje gida ka huta ,girgixa kai yyi gamida jingina kansa jikin kujera ..."ya lumshe idonsa na da'n wani lokaci ,sa'annan ya budesu A hnkali baxan iyabane ,Dr.Rayuwata na kwan'nce a gadon Asibiti bbu lpia ,ina mganar wani barci .........."hkan da yace ,yabata daria kayi hkuri katafi na maka Alkawarin ,xan Kular maka daita har ka dawo ." bayason Jan mgana ne ,cikin Rashin kuxari ya'mike tsaye ya Dan kalleta ,A hnkali ya furta thank for d care ....."Allah yabr xumunci Amin tace tana kallon sa ,cikin takunsa na kasaita ya ka'rasa gaban gadon nata ,A hnkali ya sunkuya ya subbaci la'bbanta gamida furta I love yhu my Queen!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tsaye Dr.pharty tayi tana kallon su cike da sha'awa ,tayi folding hnnun ta akan kirjinta murmushi da'uke a fuskarta ,take fa'din Eyeeeh Mr.AJ. bbu ko irin ya'r kunyar nan??"......... Cike da jin kunyar ta ,ya nufi ko'far fita daga da'kin cikin sassarfa ,da murmushi tabisa gamida girgixa kanta tana son personality's din Abdul Jabbar meera."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" sanye yake cikin fararen ka'ya ka'l na captani, ,sae ka'mshi yake xubawa Ruwan Lipton kurum yasha ga'badaya hnkalinsa nakan drama Queen nasa ,......Hajja wat wrong with yhu # Are yhu out of your mind bakifa da lpia kice dole sae kinbini hospital ya fa'da fuska a ha'de ,bbu abunda ya shafeka ni nasamu ,sauqi Mimi maida hajja gida ,?itakam daria abun yabata ,nan ko hajja ta galla mata harara tareda ,ka'ra gyara xamanta a set din na ba'ya AJ.tamkar yyi kuka yake kallon hajja ,A fusace ya shiga motar yyinda Mimi ke xaune a driver side ya ,fisgi motar da ka'rfi Mimi sae daria takeyi ka'sa ka'sa."itakam hajja sae banbamin fa'da takeyi....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dukan su suna tsaye akanta da misalin ka'rfe goma da kwa'ta ,yyin da Mimi ke xaune akan farar kujerar Robar dake da'kin tana chart abunta." Kallo da'ya xakayiwa AJ. Kasan yaana cikin tashin hnkali ......."Hajja sae addu'a take tofa mata tana xaune a gefenta ."sannu A hnkali ta fa'ra motsawa gamida fa'din Ruwa ! Ruwa ! Cikin dasheshiyr muryarta ,da sauri AJ.ya fita kiran Dr.zahra har yana ha'rde ka'fa baki wangalau Mimi ,kebin yayan nata da kallo............gamida girgixa kanta ba'ajima ba sae gashi tareda Dr.Pharty ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cire mata drip din hnnun ta ,tayi idonta na kanta ,A hnkali Dr.party ke fa'din akaita toilet tayi brush ,daganan sae break fast ko sir." Sae tayi sae abata ruwa tasha." AJ. Yaxo xae ta'bata tayi saurin buge hnnun ,sa gamida furta no da ka'rfi sassauta murya yyi kiyi hkuri xan tamaika maka makine xuwa toilet cikin murya kuka take ,fa'din I don't wanted, ta fa'da cikin muryar son tayi kuka bayan granny ta koma ,ta boye fuskarta ..........."AJ.yaji ransa ya ba'ci Juyawa yyi yabar da'kin dakyar Dr.pharty ta taimaketa xuwa toilet ,yyinda Granny tabisu da ka'llo tana kallon yanayin tafiarta ,murmushi mai kyau granny ta saki wandda ni Ma'u na rasa ko na menene.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Team Drama Queen. "*💖</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p><br /></p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>81</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Granny ke bata tea ,da'n tsagaitawa ,tayi tana kallon hajja ku'rawa fuskarta ido tayi tamkar Mae son tagano wani Abu akan fuskar tata ." tana tunanin ina tasan fuskarnan."Amma ta ka'sa tuna komae ,sae data shanye ,Dr.zahra ta taimaka mata tabata mgani ,tarasa mai xata ce mata ." sunan da taji Habiby na kiranta dashi ,ta Dan tuno ,Cikin sanyi muryarta ta'ke fa'din Thank yhu so much granny!,da haka ta gyara kwanciyarta gamida runtse idonta ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ka'rfe Tara da rabi na dare ya shigo sashen na hajja ,Hajja na a falo agajiye ya zube akan sofa da kallo hajja ,tabisa ." murya a sarke ya gaisheta ,ta amsa cike da kulawa anan yake tambayr ta tasha maganin ta ,amsa tabasa da tasha." Yana son ya tambayi Queen dinsa ,sae dae yana jin kunyar hajja baxae iyaba ,itama bata ka'ra kulasa ba Dan ta lura ya'n miskilancin suna bisa kansa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin sanyin jiki ya mike tsaye direct master bedroom ." din hajja ya nufa ,da kallo tabisa hka murmushi da'uke a fuskarta...."A hnkali ya mu'rda ko'far bedroom din ,tana xaune akan sofa tana game da wyar hajja jin ka'rar bude ko'fa tayi saurin da'go kanta ganinsa ,yasa gabanta ya fa'di a tsorace ta mi'ke tsaye A hnkali ta shiga jada baya , tsaye yyi a bakin ko'fa yana kallon yanayin ta ,gaba da'ya a tsorace take ." Am sorry plss ya fa'da gamida rike kunnu wansa du'ka biyu ,da sauri ta juya masa baya ,hawaye suka ba'lleke a idonta ,jin tayi anyi hugging back nata ." wannan lokacin kya'lesa tayi ,A hnkali ya saka'lo kansa ta wuyanta ,cikin wani irin salo ,yake fa'din did yhu love me??" Yana fa'da yana ka'ra matseta a jikinsa ,yes I love yhu Habiby plss cikani mana yhu are hunting me ,." Cike da wani irin jin ddi yyi saurin juyo da fuskarta ,yana fuskantar ta ,shaye da toka take kallon sa ,gamida folding din hnnun ta akan kirjinta tana kallonsa ,so wat now?? Gabada'ya rudewa ,yyi jin wae Asma'u na son sa jin hka yake tamkar a mafarki amma ,kuma lokaci da'ya jikinsa yyi sanyi jin ba'a hayacin ta ta fa'da masa hkan ba ."Dan ko xa'a kasheta batasan ma'anar Kalmar ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cike da sanyi gwiwa ,ya xube akan sofa ,A hnkali ta xauna gefensa "tallabe fuskarta tayi da hannayenta biyu,tana kallonsa , </p><p>Hii !</p><p>Can yhu see me??..........................ta masa tamabyr ta wani ha'de rae oya tashi mutafi gida ,ya fa'da yana kallon fuskarta ,no I don't want to go with yhu !! ,ta fa'da da ka'rfi ......"A kuma tsorace ,Cikin son tayi kuka bana son abunda kakeyimin ni nadawo gurin granny bana son wurinka." Dae -dae lokacin Hajja ta turo ko'far da'kin da suke ,Asmy na ganinta tayi saurin mikewa tsaye ,ta koma a bayanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Granny ki fa'damasa ,I don't want to go with him......ni banason wannan abun da yak.......saurin Rufe mata ,baki hajja tayi shikam AJ.jin yyi tamakr ya nutse cikin ka'sa Dan kunyar hajja , A hnkali AJ.ya mike tsaye ya nufi bakin ko'far fita batareda ya ka'lli hajja ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Habiby*!!</p><p>"Asmy ta kira sunan sa a hnkali kayi fushine ??" Tayi masa mganar cikin fuskar damuwa , pls am sorry ka'ji ka kwan'ta akan sofa ,ni da granny mu kwanta ,akan bed plss don't go........ta fa'da a raunane,da sauri yabar room din yyinda ,Hajja tabisa da kallon tausayi ,kafin ta juya da kallonta akan Asmy ." nan take hajja ta ba'ta rae ganin hka jikin Asmy yyi sanyi lokaci da'ya ." fa'da hajja ta fara yimata ,waye ya fa'damaki ana fa'din irin wannan Abu ki daina bbu kyau ,idan baso kikeyi nayi fushi dake ba ."kina jina habibynki he is your husband!! </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cike da mmki Asmy ta xauna gefen gado jiki sanyayye take kallon granny ,tana maimaita mganganun granny aranta ,habibyna husband nawa,haka tata damun kwa'kwalwarta,bbu abunda ta iya tunawa me Kalmar ke nufi ,hka yasa ya sakar mata wani irin ciwon kai ......." Haka yasa ta kwana da zazzabi..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>★★★★</p><p>*_One month latter_*..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"AJ. ne xaune a katafaren office dinsa around 2:00pm.,aikin cika wasu takardu yakeyi yyinda Queen nasa Ke akan soofa tasaka ka'ton plate agabanta mai dau'ke da banana ,sae ci takeyi da sauri ,a sanyayye ya da'ga yana kallonta ya rasa meyasa a ya'n kwanakkin nan ta dami kanta dacin Aiba ,bata minti goma bataji aiba a ba'kinta ba ,duk tabi ta ya mutse ko abincin ,kirki bataci ga rigima Abu ka'dan xaeyi mata ta haukace masa,ynxu -ynxu ga saurin fushi...." Yana cikin wannan tunanin wyarsa ,da take game dashi tayi ka'ra ,ganin sunan da'ke yawo akan screen din ya'sa ta dan ha'rari wyar gamida turo ba'ki tacika ba'kinta da banana ,ta kallesa xubamaa ta ido yyi yanason yyi daria ,sae dae ya gimtse ,karta Tara masa jama'a wake kirana a waya."?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A shagwabe take fa'din ba wannan Angel din naka bace ,ni bana sonta ya'rda tayi mganar cike da yarinyata." ,tasowa yyi yaxo gabanta gamida ka'rbar wyar." Sae ga kiran Mimi ya sa'ke shigowa ,</p><p><br /></p><p>Hello Angel !!</p><p>Wat!</p><p>Yyi mganar da ka'rfi cike da tashin hnkali OK wane hospital?" Ganinan xuwa ,hnkalinsa a tashe ya datse kiran nata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>B.Aliyu✍🏻</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu</p><p><br /></p><p>Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>82</p><p><br /></p><p><br /></p><p>."Queen ya kamata mutafi ,ya fa'da yana harha'da file's batareda ya ka'lleta ba ,cikin shagwaba ,take fa'din ni gaskiyya baxanje ynxuba." Sae na tashi daga barci ,a natse ya juya yana kallonta." Na barki A office kenann,pls kirufamin Asiri Rak ! Ce batajin ddi ynxu hka ,suna hospital xanje na saukeki a gida ,sae na wuce hospital ."tashi tayi xaune tana turo da'n karamin ba'kinta bananan ta ta ba're ta cilla rabi a baki sae da ta canye ta kallesa ,nifa tare xamuje hospital gaskiyya baxan xauna a gda ba ,tayi mganar cike da shagwaba." Dason tasaka masa kuka har ta fara ruwan hawaye ,saurin durkusawa yyi agabanta no.......karkiyi kuka dan Allah ,yafada gamida sassauta muryarsa ."to naji baxan yiba ,xamuje tare ...??" Kallonta yyi gamida girgixa mata kai ,baxan je dakeba Queen kiyi min barci na rasa yaxan yi da'ke tunda naga alamr duk ,inda na fita ,dake kafin mu isa kin bin'gireman A mota kina ba'rci tamakr wata kya'sa ,nikuma kinyimin nauyi da yawa ,ynxu kin wani xama ya'r lukuta ae ,kuwa kamar jira take ya gama ta ture ,plate din hnnun ta sauran ayaba ,ta zube a ka'sa ta fa'sa masa kuka tana do'ka kafafunta ka'sa saurin Rufemata ba'ki yyi da ta'fin hnnun sa,fisge kanta tayi ." tana kallon Ayabanta data zube a ka'sa hawaye suka gangaro mata akan fuskar ta." Kanta ta da'ura akan sofa ta fashe masa da kuka mai cike da shessheka,baki wangalau yasaki yana ka'llonta ,sassauta murya yyi yana lallashi dakya'r ta hankura ,da kansa ya tsincemata sauran Ayaban Wanda bata wuce kwa'ra ukku ba cikin kwa'ra goma." Ya mika mata ,mikewa tsaye tayi ta ka'ra gyara zaman hijab,nata ." plate din banana nan ta na hnnun ta ta ka'llesa shaye da to'ka to mutafi mana."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"OK tom.baki aje plate din ba,bakya jin kunya kifita dashi ,hka ana kallonki ??" Turo ba'ki tayi ni bbu wani kun'ya xan ka'rasa cinye abuna ne a mota." Ajiar heart ya sauke da ka'rfi wannan ,Drama Queen din baxata barsa ya huta ba." Kullum wasu sabbin behervious take tsirowa dasu ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>~~~~~ Habiby! Yes !!</p><p>"Ya fa'da hnkalinsa nakan tukinsa , mubiya ta ." sky crown zanci *BANANA CAKE*!!</p><p><br /></p><p>"Tayi mganar tana kallon sa , da kuma meye?? Shikenan kurum" gyada kae kurum ,yyi." Kai tsaye ."sky crown ya nufa daita tana a mota yaje ya ka'rbo mata banana cake ,tun ka'fin su isa gida yawunta ke ,tsinkewa gashi ."ya hanata taci a mota Allah -Allah take su isa gida taji banana cake a ba'kinta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yana gama sallar azzahar ya canja kaya xuwa ka'nanan ka'ya farar Riga ce ajikinsa white da maba'llai ajikinta sae ba'kin wandon Jean's ,yana ko'karin fesa turarensa tayi saurin Rike masa hnnu ,pls karka fesamin wannan ,turaren bayada ddi ,tsayawa yyi yana kallonta ,towel milk ne a jikinta ga gashinta a jike ,sae handryer "din dake a hnnunta, A hnkali ya dire kwa'lbar turaren ya fuskance ta , ohhh yes come on what should I do now mrs.Drama Queen??" ,turarenta ta da'uko ta mika masa bodysprayn mai dauke da sunan ,Amirul uduh ." baxan Shafa turaren mata ba." Na fita anayi min daria ,ba're baki tayi xata sa'ka masa kuka yyi saurin amsa ya fesa ,OK gashi murmushi tayi gamida ka'rba,so what now mrs.Disturb?? A shawabe ,take fa'din kashafamin mai mana ,Bbu musu ya xaunar daita gefen gado ,ya walware towel din jikinta ." ya dau'ko mayukkan da take using dasu ,da nufin ya Shafa masa,aeko ta fasa masa ihu gamida rufe hancinta plssss karka ,buda ni bana son su ....."ka shafamin wandda kake using dasu,A hnkali ya da'ga kai cike dabin umurninta ,ya dauko nasa yashiga shafa mata." Lokaci da'ya ya ka'fe kirjinta da ido ,gaba da'ya jikinta ya canja ganin hnkalinsa ya koma kan na shanunta ,tayi saurin rufesu da towel ...."daria mata basa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kafin katafi ka ha'damin orange juice mana ,nan ko ya ha'de rae xansa josef ya ha'damaki ,bubbuga ka'fafunta ta farayi ni wlhi bana son nasa." Baxan ha'da maki ba ,yyi mganar cikin xa'fin rae idan bakyason na Josef kinga ,tafiata baxan iya da wannan banxar rigimar naki ba mai sa'ka mutum ciwon kai , a fusace yyi hanyar fita gamida Jan dogon tsaki ." fa'dawa tayi akan bed gamida sa'ka kuka mai tsuma rae......[ _posted&Typing on 13 September 2017 story and writing by Asmy b Aliyu_]😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>©Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>83</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kusan ka'ro sukaci da Dr.Kareema macce Mae tamkar ,maza shekarunta ,xasu kai kimanin Arbain ,da biyr a dunia tana da'ya daga cikin doctor's din da'ke rike da hospital din Mr.meera ,hka Ana ji daita sosae , tana da'ya daga cikin waya'ndda AJ.ke matukar girmamawa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tana cikin farin glasses dinta ,mai ka'ra ma idonta gani farar lapcoat ce ajikinta, da kuma hijab fa'ri Ah a'ah sae ynxu ka ka'raso kaida akace tun da'xu kana hanya ,tayi mganar tana kallon sa,cike da girmamawa yake gaisheta ,cikin fa'ra'a ta ka'rbi gaisuwar tasa ." Tana son halin Abdul jabbar duk da Asibitin nan tasa ce hka baisa shi girman kai ba." Da'gowa yyi yana kallonta ,Ehh Aunty lokacin ina office ne ,sae da na ko'ma gida ,murmushi tayi to ya madam din??" Hop tasamu sauqi ,Da sauqi Aunty kareema ." ya langabar da kae yana kallonta ,inason na kawota wurinki gaba da'ya tabi ta canja ,batada aiki sae rigima dacin banana ko yaushe ,murmushin farin ciki Aunty kareema ,tasaki bbu damuwa xanxo har gda na dubata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>."Anan kuma ta juya hirar tasu xuwa matsalar Rukaiyya ,Abdul jabbar Rukaiyya Nada wannan matsalar tun wuri kuka ka'sa fahimtar ta ,sae da Abu yyi nisa hka." Lokaci da'ya yaji fa'duwar gabansa ya ka'ru a tsorace ya'ke kallon Aunty kareema cikin,rawar murya ya'ke fa'din Aunty meya samu Rak din ne??" Ajiar heart ta sauke A hnkali take fa'din muddin xata samu abunda takeso xata dawo normal ,jininta ma dakya'r muka samu ya sauka sauran bayani xakaji sa a bakin family member's dinka." Tare suka shiga room din da Rukaiyya ta'ke A sanyaye ya da'ga ido yana kallon waya'ndda sukayi cirko -cirko akanta."Hajja Aunty sadiya da kuma Mimi ,kallo da'ya xakayi ma fuskokin su kasan suna cikin tashin hnkali A tsorace ya ka'rasa gadon da Rak take kwance ,drip ne daure a right hand nata ."sae barci takeyi lokaci da'ya ta rame ta fita hayacinta." Da'yan hnnun ta ya dauka ya da'ura akan ki'rjinsa ,A hnkali ya maida kallonsa kan hajja ,cikin sanyin murya yake fa'din granny meyasa mu Rak hka??"Lokaci da'ya ta rame ta fita hayacinta.' Granny kuyi min bayani mana pls ,meye amfanin dukiata ,A hnkali Mimi ta ka'raso gurinsa tareda ,da'fa ka'fadar sa hka idonta ya ciko da kwa'lla baiyi aune ba yaga ta fashe da kuka mai ta'ba xuciya gaba da'ya hnkalinsa ya tashi da sauri ya sauke hnnun Rak ,ya mike tsaye yana fuskantar Mimi ,sae yaga ta juya masa baya tana share hawayen idanunta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> lokaci da'ya yaji jikinsa ,yyi sanyi a hnkali ya fuskance ta plss Mimi ki fa'damin wae meye matsalar Rak ne ." A sanyaye ta da'ga kanta tana kallon fuskarsa,damuwa ne ka'rara acikin idanunsa,Amma tana jin tsoron fa'da masa batasan ya zae da'uki xance ba."Am sorry yah Abdul I don't have d courage to tell yhu dat.................but why Mimi plss go straight to d point am hearing yhu ,Cikin rawar murya take fa'din idan na fa'damaka baxakayi fushi ba yah Abdul ,kayimin Alkawari ina tsoron Abunda xae biyo bayane I don't want to lost yhu Any more.....akan halin da xaka shiga." Ta fa'da hawayen idonta ,suka cigaba da malala bata da ka'rfin da xata hanasu xuwa ,cike da tashin hnkali ya rike duka ka'fadunta pls Mimi ka'rkiyi kuka ki tsaida hawayen nan naki Dan Allah ,I don't want to see your Tear's dae-dae wannan tym.din plss yimin bayani I promise yhu I want to be strong, OK.........ta fa'da araunane gamida goge hawayen idonta ,Yah Abdul!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>."takirasa cikin Rawar murya ,Jin yyi zuciyarsa na Neman tsinkewa a hnkali ya lumshe kyawawan idanun sa ,na tsawon wani lokaci."sa'anan ya bu'desu tareda ,ka'feta da manyan idonsa har lokacin ,Hajja da Aunty sadiya na tsaye suna kallonsu ,yayin da kowanen su da abunda ya'ke sa'kawa acikin xuciyarsa ." yah Abdul ciwon Rukaiyya Nada nasaba ne dakae!! Lokaci da'ya ya rude gamida fiddo da manyyan idonsa ,waje ni kuma??" Yes yah Abdul ,she fall in Luv with yhu ,shekaru da.....nooo Mimi stop this nonsense drama ,before I lost my control ,yyi mganar cikin wani irin yanayi Mae wuyar misiltawa ,nan take ya sa'ka hnnuwan sa biyu ya ru'fe kunnuwan sa ,hka yaji da'kin na juya masa da duniar ma baki da'ya A hnkali ya shiga ja da baya ,hawaye na mugun xuba a fuskarsa gaba'daya jikinsa ka'rkarwa yakeyi ............da gudu Mimi ta ka'rasa gabansa tana ko'karin rikosa plsss yah Abdul listing to me dan Allah karkayiwa kanka illah ,tana ko'karin saka hnnunta ta rikosa yyi saurin katseta cikin da'ka mata tsawa ,I don't want to listing don't toch me I don't want to listing to yhu any more..........A fusace yabar Room din ko waiwaye bbu anan Mimi ta zube tana wani irin kuka mai Sosa ran duk, mai saurare[ _@t 12:30pm.by Asmy b Aliyu_].</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p>"I dedication dis page in honour to each and every special member's of Asmy b Aliyu fan's club....</p><p>Tnx for d love & support written naji ddin ka'sancewa acikin wannan group din Ubangijia Allah yasa mu amfana ,da juna# one love💕</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>84</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" A hnkali ya da'ura kansa akan sitarin motarsa ,yana jin yarda xuciyar sa ke ta'fasa idonsa sunyi wani irin ja ,yafi ka'rfin minti goma shabiyar a hka ..........."dakya'r ya ya lalubo lambr Sageer ya danna masa, kira bugu da'ya ya da'ga wyar Sageer kana ina ??" Yarda Sageer yaji muryar abokin nasa cikin wani irin yanayi yaji gabansa ya fa'di gani nan isowa ,yana fa'dar hka ya datse kiran dan bayason Sageer yajefo masa wata tambayar ,Dan xuciyar sa ."gaf take da ta fashe.....Da kya'r ya iyayin parking a parking lotttt din gidan su Sageer ,yau baima samu damar zuwa gurin umman Sageer ba ,direct Side din Sageer ya nufa A bakin kofar shiga ya tarar da Sageer dga shi sae farar singlet,</p><p>Da ba'kin wandon Tree Quarter ajikinsa gorar ruwan c .way ne a hnnunsa ,xubama abokin nasa ido yyi baibi kota kan ,Sageer ba." Ya ra'ba ta gefensa ya shige ciki kan sofa ya xauna ya ,dafe kansa hka lokaci da'ya idonsa ya cicciko ,da kwa'lla................jiki sanyaye Sageer ya da'fa ka'fadar AJ.jin hnnun Sageer akan shoulders nasa ,yyi saurin mikewa ,tsaye gamida fa'din noooo ,Sageer I don't want to be strong any longer ,I don't want to any hop anything iz finally over now Sageer !! Ya fa'da hawaye na mugun zuba a idonsa , gaba da'ya hnkalin Sageer ya ta'shi bai ta'ba ganin abokin nasa hka ba." Bbu mai iya fuskantar matsalata Sageer ,bbu mai sopporting dina ,bbu Mae sharemin hawayena ,bbu Wanda xan iya fa'dawa matsalata ......"Am all alone ,Sageer banida bangon da xan jingina bbu Mae duba matsalata ,iyayena sunyi min Nisan da baxan iya tunkarar su da matsalana ba." Rashin iyaye ,shiyasa kullum ,nake fuskantar matsaloli acikin rayuwata." Ka fa'damin mexanyi Sageer ,gaba da'ya Sageer ya Ru'de a hnkali ya taimaka masa ya xauna ,akan soofa iz OK Abdul jabbar .............fa'damin meye matsalar nayi maka alkawari xan gyara ,komae a hnkali ya girgiza masa kai baxaka iyaba."Sageer ynxu fa'damin wae duk wannan tashin hnkalin na meye ne??" Namiji dakae ka xauna ,kana kuka tamakar wani macce ...................."dakyar ya iya ba Sageer lbrn abunda,ya fa'ru a hospital ,shurun su granny yana nufin sun Amince na auri Rukaiyya....."but tayaya Sageer ,?? Basa ganin halin da Asma'u keciki ne ,basa tausaya mata tana cikin wannan halin ayi mata kishiyya ,ba'ayi mata adalci ba Sageer ,hka ancuceta da yawa."ba wannan bane Sageer ,taya kamar ni xan auri Rak! Yarinyr da nake tunanin mun fito ciki da'ya daita ,tayaya xan iya zaman aure daita."?? Hka xalika bbu soyayyarta ko di'go acikin xuciyana bayaga ta ya'n uwantaka.!!,ka fa'damin Sageer taya xan iya zaman aure daita??"Anya bbu cutatarwa ,acikin zaman mu ??" Idan husna ta dawo tunaninta mezan fa'da mata ....."lokaci da'ya hkurina ya ka're nayi breaking promise nata." Xan iya jure rasa komae nawa banda Rasa Asma'u itace duk wani solution na rayuwata!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Taimako da'ya xakayi min Sageer ka'je ka da'ukomin husna ,bana son na ko'ma gidan ,xan shirya fitar mu zuwa wata ka'sa na wani lokaci dan baxan iya dau'kar wannan Ka'ddarar ba......" Da sauri Sageer ya rufe masa ba'ki karka ka'rasa AJ.kayi saurin tubar ma Allah ,kaddarar mutum tana iya baiwa mutum komae ,a rayuwa samu ko rashi..."Alkahiri ko sharri kayi fatan Allah yabaka ka'ddara maikyau ,yabaka ikon ya'rda daita nasan ((Wata Rana)) xakayi alfahari ,da ka'ddarar ka." Wani mugun kallo ya'ke bin Sageer dashi ,A fusace yake fa'din ,yhu ask me to fight for my right .........nagaji dajin wannan Wata ranar ,Sageer kaida hajja kullum.wata Rana har sae yaushe xan cigaba da jiran hakan??" Fa'damin a wannan ka'ron baxan ka'rbi maganganun kaba."Alfarma na nema ,idan baxakayi min ba .......na nemi wani yyi mganar yana ka'llonsa da jajjayen idonsa ,A hnkali Sageer ke kallon Abokin nasa ,yarasa yarda xaeyi dashi ............Ajiar zuciya ya sauke OK." Xanje naxo maka daita amma fa ,duk abunda ya fa'ru ka'rkayi kuka dani ka fa'rayinsa ,da kanka." Cike da tsokana ,Sageer ke fa'din ni bansan me Rak ! Ta gano tattare dakai ba."take maka irin wannan ,son me akeyi da namiji mai rigima irinka!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ya'r karamar mgana kana shirin Mae data babba ,da ka'rfin tsiya car key ,ya dauka dake kan center table ." yyi gaba yana ma AJ.dariar shakiyanci ,baiko kulasa ba ya gyara,kwanciyar sa akan soofa haka kawae ....."yake jin kansa cikin wani irin kadaici ."Lokaci da'ya kuma yaja dogon tsaki yana jin Tsanar Rak! Aransa ,anan ya dinga tuno irin ,shisshigin da take masa,da kuma yarda lokaci da'ya taxo ta fa'ra Nuna ma Asmy wata irin tsana wandda ,yarasa ko ta minene......"wannan karon baxae yarda suyi yarda sukeso ba ."komae xae fa'ru ya fa'ru hka xae basu mmki ne .</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>B.ALIYU✍🏻</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>©Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>85</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ahnkali aunty sadiya ta da'gar da Mimi tsaye ,wadda ke durkushe a ba'kin ko'fa tana shesshekar kuka." Hawayen idonta Mimi ta share ta kalli granny cikin raunanniyr murya ynxu granny kina ganin halin da Rukaiyya ke ciki baxaki iya conversing ."din yah Abdul ba ,ta fa'da gamida nuna Rukaiyya da hnnun ta." Basan meyasa ya Abdul yyi hka ba,bansan meke damun kwa'kwalwarsa ba."dama ni nasani a wannan karon xamu sha fama,saboda wannan matar tasa gaba'daya tabi ta haukatasa bbu Abunda ke cikin kwa'kwalwarta sae tsabgegen hauka zalla ,bansan meyasa ya'ke son xama daita ba A hka."cikin kunar rae Aunty sadiya ta amshe xancen ,da fa'din kika sani ko asiri akayi masa.......................yau nasha mmki da Abdul jabbar ya nuna min ka'rara bayayi da Rukaiyya ,koda ya'ke ba abun mmki bane ,nasan Rukaiyya ba ajin sabace in banda munxama jini da'ya da mahaifinsa wannan hanya baxata ha'da Rukaiyya da Abdul jabbar ba.."no Aunty sadiya kidaina fa'dar hka Dan Allah in harko ya fifita ba're akan Ya'r uwarsa xae tafka babban kuskure A rayuwasa ,ga ba'daya yah Abdul ya canja baya kula dani kamar yarda ya'ke yimin Acan ba'ya gaba'daya anbi an magance sa ,an haukatasa lokaci ,A wannan ka'ron wlhi baxan ya'rda ba ."no matter wat !!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mimi tayi mganar da ka'rfi gamida ya'rfi da hnnayenta ,Hajja tanisa Mimi kiramin driver a wya ya maidani gida ,OK granny anan Mimi ta shiga Neman layin driven hajja."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kusan tare sukayi parking da sageer ,da kuma driven hajja ." haka sageer yabi yah Rude lokaci da'ya da sauri ya ba'lle ma'rfin motar ya tunkari motar hajja ,dakansa ya bude mata ma'rfin motar ,tana fitowa daga motar ya russuna ya kwa'shi gaisuwa ,wannan ka'ron hajja ciki-ciki ta amsa gaisuwar sageer ta ka'ra gyara xaman gilashinta idonta." Cikin daburcewa sageer ya shiga ,ya'n kame-kame sarae hajja tana lura dashi bayada gaskiyya ,Hajja ya mai jikin?"...da sauqi bata mutuba ,koda kuka gudo a asibiti."Dan murmushi sageer yyi ,Ya gano hajja fushi tayi dashi kenan Fushin AJ.ne ya shafesa." A hnkali ya Shafa sumar kansa ,ba hka bane Hajja munxo Neman sulhu ne ,baxan saurare kaba." Sageer ka ko'ma kaxo da Abokin naka nan da minti Ashirin idan ba hka ba." Nixan kwa'she komae nawa nabar garin nan nida Asma'u tana fa'din hka ,ta juya tayi tafiarta yyinda body guards din AJ ke take mata baya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>..."Hnkali tashe sageeer ya shige motar sa hka yyiwa motar key da gudu ya fita daga cikin gidan A hnya sae kiran lambar AJ.yakeyi bata Shiga..."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Team Drama Queen or Team Rak?*### nidae na'ce uhmmm.. !!🤔</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>86</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tsaye yasame sa ." A tsakkiyar falon yana kae da kawo ,wannan ka'ron ya cire T.shirt din da'ke jikinsa.jiki sanyayye sageer ya fa'da akan soofa yana maida numfashi ,Da kallo AJ.yabisa yana ga kadawo hnnu biyu ko dama wasa da hnkali kayimin??" Yyi mganar shaye da ,toka idan kaji Abunda ya fa'ru zuciyar ka xata iya tarwatsewa sabida tashin hnkali ,ynxu bbu dogon bayani sageer ya mike tsa'ye ya kallesa kaxo mutafi ,wani mugun kallo AJ.yabi sageer dashi lokaci da'ya ina kenan??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Meera Estate,look sageer banason rainin hnkali ,na fa'da maka baxan je wannan gidan ba ,in fa'da maka komae yasa ."bari ka'ji granny da Drama Queen naka." Gari xasu bari anan ya masa bayanin komae sosae hnkali AJ.ya tashi ka'fin sageer yakae ko'fa har yakae ,hka xaka fita bbu Riga daga kai sae singlet ??"Ina wannan kunyar take yau ?,akwae fa mata a gdan nan ,bae ko kula sageer ba ya nufi mota yyin ,da sageer ya bisa motar da T-shirt nasa sae dariar shakiyanci ya'ke yimasa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Granny habiby ne ya ba'ta maki rae ??,OK kibarni dashi xae xo ya sameni ne....murmushin ka'rfin hali hajja tayi tana matukar son Asma'u hka wani fannin tana ,tausaya mata halin da tashiga." Sanye take cikin wata doguwar rigar English wear's ,fara Mae ra'tsin ba'ki ajikinta sae Dan ka'ramin hijab fari Mae bakin leshi............"plat shoe ne a kafanta, a hnkali take sipping so'bo juice a glass cup sallamr AJ.sukaji ,cikin takunsa na kasaeta ya shigo fa'lon yyinda sageer ke take masa baya tamaka'r wani basarake." Glass din frada ne manne a fuskarsa,Wanda ba'a hangen kwa'yar idanunsa." Bbu Wanda ta amsa sallamar sa,</p><p>tsakanin Granny da Drama Queen nasa, hka ya hango manyyan Jikkunan su a tsakiyyar fa'lon wato har sun ha'da luggage's nasu ?........Abun daria yabasa tsayawa yyi tsakiyyar fa'lon yarasa waxae tunkara cikin su Shahada ,yyi ya nufi granny dinsa,ya xauna gaf daita gamida kamo "Hnnunta na dama saurin fisge hnnunta tayi ,Hajja mekuma ya fa'ru ? Yyi mganar A shagwaba'nce ,Hajja ta maida kallonta gurin Asmy ,Queen yiwa wannan Habibyn naki mgana I don't want to talk to him....Any more so kice yabar ni,itama shaye da to'ka Ta ka'raso gabansa gamida cire glasses din idonsa , Kalleni nan habiby..........tayi mganar cikin basa umurni bbu musu ya da'ga sexy eye's nasa, yana kallonta A hnkali ta ri'ke kugunta kabaiwa Granny hkuri kamata laipi shine ,xaka wani gudu oya bata hkuri Shi gaskiyyar ,tayi masa Yawa.................... yatsanta ta sa'ka ta ta'bo kyakkyawan hancinsa ,gamida da'ga masa gira da Sauri ya da'uke kansa akanta ,Shaye da to'ka ya ka'lli granny folding din hnnunsa ,yyi duka biyu ." Am sorry my granny!!,yawwa granny kin hkura??"Asmy ta fa'da cike da fara'a tana kallon Granny ,saurin girgixa kae tayi tukuna dae Queen,dole yabi Abunda nakeso ,so granny meke nan?? ..."A wannan ka'ron batasan meke fa'ruwa ba ,da sauri ya fisgi hnnunta xuwa up stair's ,Dan bayason ta jefoma Granny wata tambayr."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wae mekakeyi hakane habiby? Ta fa'da shaye da to'ka gamida fisge hnnunta,cikin nasa cike da kunnar rae ya'ke kallonta." Ae baxaki ganeba ,suna planning akan mijinki ya auri wata ba........" Ba'ki wangalau take kallonsa ,me mganar sa ke nufi....." my husband planning to get Marriage to some one else,As how habiby?? I don't understand yhu,kijirani anan ina xuwa karki ya'rda ki sauko a down stair's kina jina?" Idan kika sauko ,xamu ba'ta baxan Ha'da maki orange juice ba ,no xan tsaya anan mana ......."kar'kace baxaka ha'damin Orange juice ba ,xanjira ka anan I promise yhu OK .......da haka ya fice daga Room din ,gamida murxawa ko'far key....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asmy b Aliyu.👌🏻</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>©Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>87</p><p><br /></p><p>A hnkali ya'ke saukowa daga down stair's ,lokaci da'ya sageer da Hajja suka bisa da kallo ya wani ha'de rae ,sofa mai fuskantar Hajja ya xauna yyi crossing leg's ,ya tsare gda..............Hajja ta nisa ta sassauta murya tamkar Mae tsoronsa,baxan tilastaka ba Abdul Jabbar akan ra'ayin kaba." Amma nasan idan Mimi ta shiga wannan yanayin ,zakaji ddi ne?</p><p><br /></p><p>"Ko ita Rukaiyya din dan ba ciki da'ya kuka fito daita bane??" Ynxu ka'sa sadiya da Salma na ganin laifina ,suna ganin Kamr nice bana son ka Auri Rukaiyya ,</p><p>Bama hkan ba Rukaiyya ya'r uwarka CE ,ka auri ba're barantana ya'ruwarka muddin ka'ki Auren Rukaiyya kiyayya za'ka jawoma Asma'u ,ganin son da kake nuna matane ya'sa baka kaunar Rukaiyya , ina baka shawarar ka daure ka auri Rukaiyya muddin ,ka aureta xa'ka basu ku'nyar sune ,kasan komae xae fa'ru baxan ta'ba kin Asma'u ba." Koda Asma'u xata dawo tunanin ta ,ba lokaci da'ya xa'a sanar daita Aurenka ba." Sae komae ya lafa , Ido jajur ya'ke kallon hajja ya ra'sa Mae xae fa'da ha'da Ido sukayi da sageer yyi saurin girgixa masa kae almr ka'rya yi musu da Hajja ............." Saurin da'uke kansa yyi cikin Rawar murya ya'ke fa'din Hajja idan , iyayenta da yayunta suka sani ,Anya baxa suyi tunanin kamar nagaji da zama da husna bane shiyasa na ka'ra Aure Inajin kunyar Mamansu Asma'u idan ta ki'rani a wya har rasa abun fa'da nakeyi Anya granny bbu son kae aciki..."?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hajja tayi saurin girgixa masa kae ,ka'rka damu da hakan kasamu surukkan ki'rki a rayuwa ka'kara godewa Allah ." Asma'u tafito gdan dattako.", sadaukarwar so xa'kayi Abdul jabbar ,sadaukarwar tana da girma A soyayya ,tana baiwa mutum darajr da bai ta'ba tunanin sa'muba A rayuwa."kabarmin komae A hnnu na Allah yyi mka Albarka tsam ,ya mi'ke batareda ya ka'ra kallon granny da sageer ba ya nufi up stair's da gudu,sageer xae bisa hajja tayi saurin da'katar dashi ka'barsa hka sageer nasan ynxu baxae saurareka ba." Kaje kurum Ku fa'ra shiri nan da sati biyu bi'ki insha Allahu Allah ya ka'ra ka'reku da ka'riyarsa jiki sanyayye ,sageer ya Amsa ma hajja ,nan yyi mata sallama."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nan hajja ta da'ga wya ta kira Aunty salma ,tana fa'da mata idan tana da ha'li gobe ta shigo Bauchi ." Anan ta kira Aunty sadiya ,tace tana Neman ta xuwa dare..........Ta amsa da to."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Misalin ka'rfe 10:00pm.na dare yana xaune akan soofa ,yana using da laptop na'sa yyinda Queen ke gefe tana ba'rci knocking ya'ji yasha mmki ,yes come in................. Ana mu'rda ko'far da'kin ya zuba ma ko'far Ido Mimi ce tsaye a bakin ko'fa da sauri ya da'uke kansa akanta ya cigaba da aikinsa ,A hnkali ta ka'raso gabansa ,sannu da aiki yah Abdul ciki-ciki ya amsa ,Ya Abdul dama mgana nakeso muyi da kae a tsorace take mganar." A hargitse ya da'go da kansa ya jefeta da wani mugun ka'llo wandda sauran ka'dan fitsari ya zubo mata a wando, ynxu ba lokacin mgana bane ,kibari sae da sa'fe Yah.......shittttt ya da'kamta tsawa ,Kina damun Queen tana barci bana son mgana da'ke plsss get out ya'fada cikin Fushi bbu shiri Mimi ta juya tabar room din da gudu ,tsaki ya'ja gamida ture laptop din ,gefe dae-dae lokacin Asmy ta bu'de idonta gamida yin mika A hnkali kallon ta ta mayar kan'sa ,Da sauri ta mi'ke xaune cike da shagwaba ,ta matso gafdashi ."Habiby xanci Pizza yinwa,nakeji plsss Queen ka'rki dameni dan Allah kibarni da Abunda ya addabi Rayuwata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nan ta'ke tasha To'ka mekake nufi??" Ni Allah pizza nakeso tayi mganr gamida mi'kewa tsa'ye da'ga rinannun idonsa ,yyi yna kallon ta "Idan bai la'llabata ba ynxu sae ta nemi Da'ga masa hnkali Right hand nasa ,ya ba'ta baxan bayar ba ta fa'da gamida folding hnnunta akan ki'rjinta tana turo masa dan Ka'ramin ba'kinta baxaki ci pizza ba kenan ,xanci mana tom....zokiji yyi mganar in a low tune................." Bbu musu tabasa right hand ,nata A hnkali ya ja'wota ya xaunar daita kan cinyar sa ,gamida ture laptop nasa A hnkali yakae hnnunsa kan marar ta yana shafawa ,cikin muryar ra'da ya'ke fa'din ynxu Sabida Allah Queen ina zaki sa'ka pizza a wannan cikin in banda ,tsabar rigimarki A fusace xata fisge jikinta cikin na'sa ya Riketa gagam ya hanata motsi ,da'ya hnnunta ta sa'ka gamida dukan Kirjin sa da ka'rfi ni dan Allah kasake ni ,nibana mason Pizzar lokaci da'ya kuma ta fa'she masa da kuka, baki wangalau ya sa'ki yna ka'llonta kukanta yana ta'basa ,da sauri ya fa'ra lallashinta sorry Am sorry kinji my Lady oya jeki nemo Ka'ya masu kau'ri da hijab Acikin closer na'ki muje Eateries ya fa'da gamida gogen hawayen idonta." Am sorry I love yhu !! Yyi mganr A shagwabance, cike da jin ddi Ta sauka daga jikinsa ,Dan tsalle ta'yi Tana daria Sa'annan ta kallesa ,daganan Habiby xa'a biya shan ice cream ko ??,da'ga mata kae kurum yyi OK ........kajirani na watsa ruwa to ,tayi mganar shaye da to'ka A hnkali yace to my Queen cike da jin ddi ta shige toilet. Agogon bangon da'ke manne a da'kin yaxuba ma ido ka'rfe goma har ta gwafta ,saboda tsabar rigimarta ynxu su fita da dare....shingida'wa yyi gamida lumshe ,idonsa yana jin fitowar Drama Queen din na'sa....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_Ma'u_*.👄</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>88</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kae tsaye Aroma Restaurant suka nufa, yana ka'rabar mata pizza suka wuce Jifatu ,Ya siyamata ice cream ,sae kusan sha biyu saura suka nufi gida ............Anan main falo ta xube ta cire hijab dinta anan ta bu'de robr ice cream caraf ya rike hnnunta." Ki fa'ra cin pizzar first sa'annan ,kisha ice cream din na'ki shaye da toka ,take kallonsa Ice cream kurum xansha pizzar kuma sae na tashi barci ko gobe da safe sae nabar sa a fridge,</p><p>Sakar mata hnnu yyi A hnkali sa'annan ya lumshe idonsa ,bae ka'ra kulata ba ."</p><p>Sae da tayi Rabin roba ta juya ,tana kallonsa Wanda idonsa a rufe suke amma ba ba'rci yakeyi ba."</p><p>"Kai baxaka sha ice cream din bane?? A hnkali ya bude idonsa ,yna kallonta." Tsam ya mike tsaye hnnayensa xube cikin Aljihun wandonsa,</p><p>Ya ka'lleta nixan je na watsa Ruwa idan kin gama ,ki sameni A master bedroom. "Saurin ture robar Ice cream din tayi tana Dan turo ba'ki to kajirani mana ,ni tsoro nakeji kiyi hkuri wanka xanyi kafin ki gama ni banyarda ba kajirani na gama ,nima xanyi wnka mna tayi mganar shaye da toka..............." Bae ka'ra kulata ba A hnkali ya xauna akan soofa ya cigaba da kallonta sae shan ice cream dinta ta'keyi tana wani lumshesu yana nan xaune ,roba biyu ta shanye...........</p><p><br /></p><p>2dayz letter. "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sanye ya'ke cikin ba'kaken suite da ba'kin glass din frada ,a idonsa sae kamshi."ke tashi ajikinsa,</p><p>Kallonta kurum ya'keyi sae ko ka'rin da'ura Dan kwalin less takeyi ta ka'sa ,murmushi kurum yyi da sassarfa ya nufi gurinta hannayen sa ya zagaye ,da kugunta ."yyinda ya zura kansa Acikin ka'fadunta suna ha'da ido ta cikin mirror dressing,ta wani ba'ta rae sae kiciniyr ture hnnunsa take ,cikin sexy voice nasa ya'ke fa'din minene kuma??"</p><p><br /></p><p>"Rau -rau tayi da ido cikin ,yanayin shagwaba take fa'din Dan kwa'lin ya'ki dauruwa kamar ya ??" Baki daurasa da kyau bane shiyasa,A hnkali ya saketa ta juya tana kallonsa ,to amsa dauramin mana ta fa'da gamida mika masa dan kwalin ,Amsa yyi ya xaunar daita kan kujerar mirror ya ,shiga nada mata dauri tamkr wani macce,</p><p>Lokaci da'ya ta kya'lkyale da daria lah Habiby kuma daurin yyi kyau ,Allah daga yau kae xaka dinga dauramin dankwali murmushi ,yyi ya dauki mayafinta Mae shige da less din yabata ,sa'annan ya juya side din talkami da jaka ya ,dauko colourn da ya da'ce da kayan ,</p><p><br /></p><p>Kai tsaye ,part din hajja suka nufa hnnunsa ,na cikin na'ta sallama sukayi a babban falo Hajja ta amsa gamida binsu da ido ba ka'ramin kyau,</p><p>Sukayi ba tana xaune akan ka'tuwar carpet an cika gabanta ,da kayan marmari .........................A hnkali ya xube agabanta cike da girmamawa ,ya'ke fa'din sannu da gida My Granny ,ta amsa cike da fara'a sa'annan itama Asmy ta'ce sannu da gida my Granny A hnkali ta amsa ,tana rike hnnunta ka'fin ta maida kallonta kan AJ." Amma bada ita xaka tafi ba ??" Shaye da toka,ya'ke kallon hajja ,mexae hana Hajja baki wangalau ta sa'ki tana kallonsa,</p><p>Anya kuwa Abdul Jabbar bbu abunda, ke damunka ta fa'da gamida daura hnnunta ,akan Fuskarsa ,da sauri ya ture hnnunta bbu Hajja ,xakaje ka gaida surukkan ka .........shine xaka wani ja'ata da sageer ya kamata kutafi nasani ,Hajja xae sameni a can ne ."Ka'ra tun guri na nuna masu muhimmancin tane,har ita Rak ! Din dan naga tana wani taken Rashin kunya ya fa'da gamida mikewa ,tsaye yana kallon Asma'u wadda hnkalinta ya koma akan banana sae shan Abunta takeyi ,</p><p>Kurum da almr batasan xancen da sukeyi ba."Ajiar zuciya hajja ta sauke ,</p><p>Bbu laipi Allah ya kae lpia,Amin ya amsa Mimi fa??"</p><p><br /></p><p>"Ya fa'da yana kallon Hajja ,suna can suna shirye -shirye kaima kasan wannan tym.din baxaka ganta ba." Mrs.Banana na tafia ta na barki kenan?" Ya fa'da gamida tsareta ,da kyawawan idanunsa, da sauri ta mike ,tsaye Dan Allah kar ka tafi mana ."Amma kabari Hajja tasan min naje a mota ,naci bananan ."ta ka'rasa xancen dauke da shagawaba ,A fuskarta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kallonsa ya maeda kan Hajja ,ni dole mane ynxu mu biya meera hospital ,Aunty kareema ta duba,</p><p>Min ita Hajja Wannan cin Ayaba yana bani tsoro ,</p><p><br /></p><p>." Hajja batace komae ba ,sae wani irin murmushin farin ciki da ta saki ,Allah dae ya saukar lpia .....................yana son yyi mgana tayi saurin katsesa sae kun dawo Allah yasa,</p><p>Muji Alkahiri granny kixubamin A plate mana."</p><p><br /></p><p>Baxafa kijemin da Wannan abun,A mota ba xatayi mgana."ya dauketa,</p><p>Cak! Xuwa mota sae dukan kirjinsa tana masa, kukan shagwaba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kai tsaye meera Hospital suka nufa ,Haka yata kiran wyr Aunty Kareema bata da'gaba Wanda yarasa,dalili yna gama parking ya hango motar ,Mimi A harabr hospital din gabansa yaji ya fa'di lokaci da'ya......</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asmy b Aliyu.👌🏻</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>89</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hangosa da mimi tayi sae da zuciyrta ta kusan tsinkewa ,da sauri taja body guard din da suke tare ,ga Ya Abdul nan xuwa kayi saurin karasawa idan yace. " tare muke kace masa A'ah ,kaxo karbar min saqone ,cike da girmamawa ya amsa da to."yyi gaba da sauri yyinda itakuma tabi wani side da sauri ,xufa sae tsiyayo mata ya'ke ta koina ,tana cikin Wannan hali kiran Rak ya shigo da gaggawa ta da'ga cike da murna ,Rak ke fa'din yap babe??"</p><p>Kidae bari ynxu naga yah AJ. Ya shigo hospital din nan ,wat?? Rak tayi mganar in a shork."</p><p><br /></p><p>Come down Amaryar ya AJ." Baifa gannni ba Mimi ta fa'da tana wani smiling da ido,anan ta fa'da mata yarda ta fa'dawa body guard nata." Shewa Rak tayi nyc Job tawan ,sae kin ka'raso kinsan yana hnyr xuwa hka Ya fa'dawa mama xae xo ya gaisheda Abba plzzx ki ka'raso da wuri OK."gani nan ya kukayi da Dr. Sae na ka'raso xakiji komae daga nan sallama ,sukayi juyawar nan da xatayi idonta cikin na Asmy sae da ta raxana kallon da ,taga tana yimata cikin dakewar ,xuciya Mimi tayi folding hand's nata a kirji tana kallonta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin sexy voice ,nata take fa'din ."wat happen Drama Queen, mekikeyi anan? Bancin ynxu naji habiby na tambyr drivern ki ,inda kike kenan ka'rya kikayi masa??"Asmy tayi tambyr bbu almr raxana akan fuskarta,mmki ya kusan kashe Mimi ,A fusace take fa'din meye na'ki aciki munafuka??" Fiddo ido waje Asmy tayi ,mekuma yyi xafi Angel nifa na tambaye kine kurum...............dan Allah rufemin ba'ki kuma wlhi idan kika sake ,yah Abdul yaji Wannan ni dake ne ta fa'da gamida yimata kallon banxa sa'annan ta sa'kin dogon tsaki ,tayi tafiar ta da ido Asmy tabita tana juya maganganun A kwakwalwarta ,caraf taji an rike mata hnnunta ,ina kika shigane ,oya zomu ka'rasa ciki ga Aunty kareema nan ta iso,tirjewa ta shigayi tana turo dan ka'ramin ba'kinta nifa baxan jeba."Habiby bana son Allura ,tayi mganr ido taf da ,kwallah."</p><p>Ba allura fa xatayi mki ba ,dubaki kurum xatayi ,toni lpiata qlau ni dan Allah ka kyaleni ,tawani fisge hnnun ta,na fara tunani kaxo kasa na manta,ynxun nan fa naga An...........baijira Mae xata fa'daba yyi sauri daukarta cak ! Xuwa office din Dr.kareema Mae aikata ,sae kallon su akeyi cike da sha'awa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>."One hour .</p><p><br /></p><p>Aunty kareema ,ta shigo fuskarta dauke da fara'a take kallonsa ,Aunty Wannan fara'a hka fa??" Bani takardar Nagani meye aciki??"</p><p>."Ya fa'da gamida mika hnnu da nufin ya amsa ,tayi saurin bo'ye takardar A bayan hnnunta,</p><p>Ta girgixa masa kae A'ah Daddy baxa'ayi hka ba!!</p><p><br /></p><p>"Jin ta kirasa da daddy lokaci da'ya ya rude ,pls aunty Kareema ,fadamin mna na ka'gara naji minene??" Yyi mganr cike da shagwaba,meye Albishir nawa??"ni koma mekikeso ,xan baki ,harda Queen din naka ?" Ta karasa zance ,</p><p>Cikin tsokana ,da sauri yace Aa'h banda my wify..."Daria Aunty kareema tayi ,gamida mika masa,result...cikin sa'kan biyu sae gaya ya fiddo ido,waje lokaci da'ya ya mike tsaye ,tsoro mmki suka bayyana akan innocent face,</p><p>Dinsa ."Hamadala yyiwa Allah ,cikin wani irin farin ciki ya fa'di yyi sujada ,agaban Aunty kareema."sae da ya dauki tsawon mintuna a hka." Ya da'go kansa cikin kwa'llar farin ciki ya xube agaban Aunty kareema ,gamida rike kafafunta,</p><p>Gagam ."</p><p>Aunty kareema mekikeso na ba'ki a duniar nan fa'damin menene,na maki alkawarin xan mallaka maki shi muddin inada ka'rfin baki shi."cike da jin ddi Aunty kareema ,ta da'gosa ,tasa hnnunta ,tana share hawayen ,idonsa."</p><p><br /></p><p>"Haba kanina kaxama namiji ,mana tayi mganar tana xaunar dashi akan,da'ya daga cikin chair's din dake ofishin ,</p><p>Bbu abunda ,nakeso ka kula da Asma'u da cikin ,dake jikinta gobe xamu tattauna akan ,yarda xaka kula da cikin nata,</p><p>Maigida yana kan hanyr dawowa gari ,inason nabar Asibiti ynxun nan ...." Murmushin kasaita ya sa'ki nagode Aunty ,kyautar kujerar hajji keda maigida,Sauran kyauta da'ya xan aiko da Driver ,amma fa gobe ,xan buga saka mako a ko'far gidan ki dan jin yarda ,xan kula da babyn namu , daria tayi gamida yimasa,godia anan sukayi sallama ." ya nufi Room din da Asma'u take ,ta ha'da kae da gwiwa tana shesshekar kuka, jin tayi an rungumota."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da jajjayen idonta ,ta da'go tana kallonsa, hka ta kafesa dasu jin yyi zuciyrsa na Neman ,tsinkewa xaeyi mgana tayi saurin dakatar dashi ganmida fisge kanta daga rikon da yyi mata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A fusace ta tabr room din hnkalinsa ,lokaci da'ya ya tashi shin ko Asma'u tadawo hnkalinta ne??"Amma Aunty kareema ,bata fa'damasa hka ba."baitaba ganin fushinta ,hka ba tunda tarasa tunanin ta."numfashin sa yaji yana ,shirin daukewa .............</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Masu karatu mekuke Tunani ynxu??" Shin Asma'u tunanin ta ya dawo kuwa ??" Mudai je xuwa ,daga ya'r mutan Zamfarawa."😘</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>90</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Layi ta farayi ta tafi luuuuuuu......xata ,fa'di AJ.yyi saurin tarota Wannan ka'ron batayi ko'karin kwa'tar kanta ba sabida ,jirin dake dibarta. "Ta dauki minti goma A hka ,sannan tayi yunkurin kwatar kanta." ga bada'ya AJ.ya ru'de wae meye ne Queen yimin ,bayani mna??" Fa'shewa tayi da kuka ,gamida kaima kirjinsa ,duka bakae bane ,kabarni a wurin waya'nnan doctors din ni banason su ,kaga abunda sukayi min ,Murmushi yyi gamida ,sauke ajiar xuciya Mae ka'rfi am sorry ya fa'da cikin rawar murya ,harshen sa ya fiddo yna lashe hawayen idonta,cikin muryar ra'da ya'ke fa'din kiyi shuru mna sae kace ba big girl ba."A shagwabe ta sauka daga jikinsa ,ni big girl ce mana kai dae ne ba big boy ba."tunda har ka iya tafia kabarni ,A hnkali ya langabar da kansa ,gamida rike kunnuwan sa duka biyu ,Ya zuba mata sexy eyes nasa."Am sorry nayi laifi baxan ka'ra ba."</p><p>"A hnkali ta shagwabe ,fuska gamida yin folding hnnun ta,akan kirjinta tom.naji amma da sharadi ,tayi mganr shaye da toka fa'damin menene shara'din ,Idan muka ko'ma gida xakayi min Alale ta gwangwani ,Mae manja da yaji, ido waje AJ.ke kallonta." Ni yaushe na iya Wannan Abun Queen ,A fusace ta kallesa baxakayi ba kenan??" Ganin yanayin ta yyi saurin amsawa ,da xanyi mna idan mukaje gdan Aunty sadiya ,xan sa'ka su Rak suyi mki."nan ta'ke ta aza Hnnu akae ta fa'sa masa ihun kuka ,da sauri ya fisgota xuwa jikinsa,dan xata iya Tara masa jama'a ,ko'karin sauka take daga kan cinyrsa ,ya riketa sorry idan munje nida kaina xanyi miki ,shaye da toka take fa'din da dae ya'fi kam ni bana son Wannan Rak din ,ni kai nakeso kayimin ......................angama my Queen to mutafi mna,ta fa'da gamida sauka akan jikinsa,Ajiar heart ya sauke."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"**********</p><p>Tana cikin wani Red &black Lee's Mae zanen manyan flowers ajikinsa ,dinkin Riga da skirt ne ,wandda suka xauna dae -dae jikinta hka sun ka'rbeta ba ka'dan ba Abu ga farin mutum,Taji light make up na xamani, mimi ce ke ko'karin na da'mata ,dauri d ,Amma fa xaki saka mayafi ,kinsan halin ya Abdul idan ya'ga Wannan dinki xae CE ya matseki ne ,Shaye da toka Rak ! Ta kalleta mekike nufi??" a gida fa yaxo kuma Kwana nawa ,ya rage ya xama mijina ??" Ni Wannan kunyr ta Yah Abdul tana bani mmki wlhi ,Amma komae xae xo ka'rshe xanga ya xa yyi a gurin first night ,daria mimi tayi ina tausaya maki Rak !! Irin su ya Abdul hmmmmmmmm.....daria ,Rak ta kya'lkyale dashi ka ra'sa mna ,mimi xatayi mgana ,Kanwar Rak din ta shigo Mae suna Fareeda wadda baxata wuce shekara goma sha hudu ba,A dunia "Aunty Mimi wae Ku fito inji Mama ga Yah Abdul nan ya ka'raso A gaggauce ,Rak ta mikee tsa'ye jeki muna xuwa Fareeda ,</p><p>Da hka Fareeda ta juya ta fice, Mimi tabi Rak ! Da mugun kallo meye hka ,dan Allah kixama big girl mana ,kija ajinki ,Wae duk ina Wannan Ajin na'ki ya'ke Rak??"</p><p>Wata rana ,kina ban Haushi ,gaskiyya ki canja ,baxaki gane yarda nakeson saba ne ,Mimi muje ki ta'kamin wani mugun kallo tabita ,kijrani Anan xanje naga dawa ya'xo naji ance shida ,Sageer xasu zo amma A asibiti nagan sa,da matar sa."</p><p>Kijirani ina xuwa ,da hka Mimi ta fice a daga da'kin Jiki sanyaye ,Rak ta tsaya gaban madubi tana kallon kanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Asmy ce xaune a gefensa ,yyinda suke gaisawa da Aunty sadiya ko Aunty ,sadiya bata ji ddin Yarda Abdul jabbar yyi ba." Shida yaxo gaisuwar ,surukkai da ganawa ,da Rukaiyya meye na kwa'so Asma'u ,</p><p>Da gudu mimi taje ta xaunawa gaf da yayan nata,duk da bakaramin zafi tajiba, ganin sa da Asmy." Kanta ta daura akan kafadar sa gamida sakala ,hnnun ta cikin nasa,</p><p>Yaushe ka isone ya Abdul??"...........................ynxun nan Angel ,bbu ruwana ,dake ynxu idan xaki fita bana ma sani sae dae naji a bakin ,Hajja bbu komae ae"</p><p>Nasamu Queen dina ya fa'da yana kallon Asmy ya'ce ko my Queen ??"cike da jin ddi Asmy ta gyada kanta." Murmushin ya'ke mimi tayi duk da taji zafin mganar ya Abdul ba kadan ba,</p><p>Ae dama ya Abdul kadaina sona, tun ranar da ka Auri Asma'u tayi mganr A shagwabe,murmushi kurum yyi batareda ya ka'ra kulata ba."</p><p><br /></p><p>Aunty sadiya ,ta nisa ke mimi ina Rukaiyyar ne,??"ita baxata fito su gaisaba?" OK.Aunty bara na ,dubata da hka Mimi ta nufi Room din su Rak!! Nan Aunty sadiya ta ka'lli AJ." Wae ya mganr Ha'da lefe ne? Biki sauran Kwana goma." ,komae na gurin Granny Aunty sadiya daita ,xakuyi mgana ,yyi mgana gamida,jefa ya'nkakken Apple abakin sa."</p><p><br /></p><p>.."Ya kamata xuwa jibi ka shirya fitr mu dubai ,dan ha'do lefen ,Lokaci ya gabato Aunty sadiya Mae xae hna Aunty salma ta ha'do A kano hakan xae fi sauqi ,Qlau jikin Aunty sadiya yyi xanyi tabbas ta ya'rda AJ.bayason Ya'r tata ,ace duk kudinsa a kano xa'a ha'da lefen matar da xae Aura."</p><p>Cikin ka'rfin Hali ta kalli Asmy gamida mikewa ,tsaye xomu shiga ciki Queen noo....Aunty dama kin kya'leta anan ,kurum ko xaki bita Queen?? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>."Da sauri ta da'ga kae almr Ehhhh ,da sauri ta tashi tabi bayan Aunty sadiya ,dai-dai lokacin Rak ! Ta ka'raso cikin fa'lon da siririyr sallama a bakinta." a yangace ya amsata,koshi dan taxamar masa ,dolene ,cikin takunta na kasaita ,sanyayen kamshi ne ya ziyarci hancin AJ. Dara-daran idonsa ya da'ga gamida zuba ,mata ido ." da sauri ya dauke kansa ganin irin shigar da'ke jikinta ,Wanda dakyar ,take tafia cikin kayan ,Rabin manmanta duka ,a waje ................................cikin Rawar murya ta gaishesa ,batareda ya kalleta ba fuska a daure ya amsa,</p><p>Shuru ne ya biyo baya ,Agogon hnnun sa ,ya kalla ."Ina mimi ne??"</p><p>Tana ciki oya jeki k kirata,Daga nan ki tabbata kin fito da Hijab".....yyi mganr yna kallon yanayin fuskarta ,</p><p>Ba'a ddeba ,sae gata da mimi Wannan ka'ron dan siririn mayafi ne,Wanda ya tsaya iya kafadun ta,</p><p>Ga maxaunan ta nan A fili ...." bawani Abu bane,Queen xakuyi ma Alalen gwangwani ,xanje massalaci na dawo naga Amfara kiraye-kirayen sallar la'asr idan na dawo xan sameku a kiching naga ya'rda Akeyi ,Rai a ba'ce mimi ke kallonsa ka'fin tayi mgana ,ya fice daga fa'lon ,yyinda Rak ! Hawayen ba'kin ciki suka silalo akan fuskarta." Kenan kwa'liyyan ta ,ya zama na banxa??" Da gudu ta nufi part din maman su tana ,kwa'la mata kira."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>B.Aliyu✍🏻</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>91</p><p><br /></p><p>Da sauri Aunty sadiya ta tashi tsa'ye a tsorace take fa'din ke lafia?" Anan mimi ke fa'damata abunda ya ,fa'ru. Sosae ran Aunty sadiya ya ba'ci to inashi Abdul jabbar din ya'ke ne?? Ya tafi ,massallaci ku xauna anan kujirani bara nasa indo ta ha'damata ,ka'ryar iskanci ya'keyi bai isa ya wulakantaki ba wlhi ,muddin ina Raye ,aure kuma bbu fa'shi anan Aunty sadiya tasa kai ta fice dga, da'kin tana banbamin fa'da gamida kwa'lama Mae aikinsu kira Mae suna Indo....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>30 minute letter."</p><p>"Har indo tagama ha'da alalen dai-dai lokacin AJ.ya shigo da'ga fa'lon kai tsaye kiching ya nufa anan ,ya samu indon na zuba alalen cikin Ya'r madai daiciyr kula ,dan tsayawa yyi yana kallonta,jin takun tafia yasa,indo ta da'ga kanta xuwa ba'kin ko'fa ido biyu ,sukayi da AJ.cike da girmamawa ta xube ka'sa tana kwasar gaisuwa ,alama yyi mata da ta mike tsa'ye waye ya ha'da Wannan ,ka'fin tabasa Amsa sae ga Rak ta shigo ,da sauri ta ka'rbe kular da'ga hnnun indo ,tabata umurni akan tafita waje ...............................mgana mukeyi ,da ita shine xaki ce tafita??" Yyi mganar yna kallonta a tsorace take fa'din to mexaka fa'damata ya Abdul ??" Gani nashigo mna ka tambaye .""taka'rasa mganr cike da ku'nkuni da sauri indo ta fice dga kiching ,din baice komae ba ya canja salon xancen ,da fa'din Har kun gama kenan ,Ehhh muna tajiran ka baka dawoba." Wlhi kuwa naje wajen wani friend dina ne anan bayan Layin Ku." </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Alale kwa'ra biyu kurum ,taiya ci ta ture plate din da'ga gabanta ,ta kalli AJ .shaye da To'ka anya Habiby kai kayi Wannan Alalen??" Da sauri AJ.ya'ke fa'din Nina yi my Queen meya Faru?mimi da Rak lokaci da'ya suka kalli juna yyinda gaba da'ya mood na Rak ya canja, dan ' danon sane wani iri ae ."ni nayi mana my Queen ,baxaki iyadar da canye Ragowar bane .?? Ya fa'da yna kallonta ni na ko'shi kawae dae a ha'damin Orange juice tayi mganar,A shagwabance." OK tom.xa'a ha'da maki ynxun nan ,mimi plss Ku ha'da mata Orange juice ,lokaci da'ya mimi tamike tsa'ye itada Rak ! Hnyr kiching suka nufa" .......</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ran Rak ! Baka'ramin ba'ci yyi ba ,meya ya Abdul ke nufi??" Mimi kam sae kiciniyr ha'da orange juice ta'keyi ,da kallon takaici Rak ,tabita wae mekike nufine??" Girgixa kae mimi tayi ,baxaki ganebane Rukaiyya ,har sae ranr Dana ma'ki nisa na koma skull ,anan xaki ga'no ranata ,komae ya Abdul ya sa'kaki akan Wannan matar kiyi masa mna." Karki ta'ba nuna gaxawarki ,ni kinga ynxu na samu solution matsalar, kawae Ku zuba Eyes ,naki kisha kallo ammafa ba yau ba." Sae ranr dinnern Ku na maki Alkawari ,Asma'u xatayi bankwana da Rayuwar yah Abdul jabbar."</p><p><br /></p><p>."mekike nufi mimi? ,wani malalacin murmushi,mimi ta sa'ki baxan sanr dake ba ,da sauran lokaci Anjima xan ko'ma gurin Dr.ismai,l akan yyi wa'tsi da wanccan plan din dama asali ni tun can baiyimin ba." Ga wani ya samu cikin Ruwan sanyi."da hka suka cigaba da ha'dama Drama Queen Orange juice,</p><p><br /></p><p>"Xuwa ka'rfe 8 na dare AJ. Yaga baban su Rukaiyya,Wanda hka kurum ya samu kansa,da jin kunyr Uncle din nasa." Wanda ada can ba'ya bbu Wannan kunyr ,</p><p>Bayan fitowr su ne sageer sae daria ya'ke yimsa."Anan ya tsagaita da dariar ya ka'llesa Ka kira Amaryar ta'ka mu tattauna mana." Dan mimi ta'ce xasuyi dinner,</p><p>Shaye ,da to'ka AJ.ke ka'llon sageer bana son iskanci sageer ka'rkasa yaran nan su Rainani plss na ro'keka mu rufe Wannan lectures din,dan ba sauraren ka xanyi ba." Duk abunda kaga ya dace ,kaxauna dasu dama ae kae cikin su kake,</p><p>Hba Ango meyayi xafi hka tsa'ki AJ yaja anan ya shiga yyiwa ,Aunty sadiya sallama." </p><p>A gidan yabr Sageer shida, mimi suna tattauna yarda bikin xae kasance,</p><p>********</p><p><br /></p><p>"Ha'r aka fa'ra biki bbu Ango bbu alamrsa ,harkokin gabansa,kurum ya'keyi yyinda mimi suka cigaba da hidimarsu ,Haka dangin suka ci'ka gida ." Ynxu AJ ."baima fiye dawowa a gda ba." Sabida Jama'a ,</p><p>Cikin waya'nnan kwanakkin ,kusan kullum ta're suke fita da Asmy office,yyinda Hajja keji da Jama'a."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>**Ranar Jummu'a da misalin ka'rfe biyu da Ra'bi na Rana ,Bayn an sauko da'ga ,sallar Jummu'a dubban mutane suka shaida ,daurin Auren Abdul jabbar sameer meera ,da kuma Rukaiyya basheer Lamido ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*** *** ***</p><p><br /></p><p>."DINNER PARTY!##</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>92</p><p>*_ZARANDA HOTEL_*!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Su ukku ne xaune cikin wata ba'kar jeep wadda ,taji tinted, Amarya na sanye ,da Wedding gown ,ta meterial bak'i Mae da'uke da wasu irin duwatsu Golding ,ajikinta ." sae head din da ya kasance red ,tayi kyau sosae yyinda Asmy ke cikin ,farar wedding gown ."</p><p>Yyinda head din kanta ,yake Read " tasha make up sae uban smiling take ,zubawa hnnunta na cikin na Mr.Meera yyinda gogan ya'ke cikin milk din suite "............waya'ndda sukayi balain ,dacewa dashi amma fuskarnan bbu alamr fara'a ko'kadan Sae surutu ,Queen na'sa ke xubamasa yyi mata banxa ,A hnkali ya jingina ba'yansa A sit ya lumshe idonsa." </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A hnkali ta'ke ta'kowa gurin mo'tar cikin shiga ta alfarma ,dark blue wedding gown, ce ajikinta ,da Head red sae wasu uban hill's suma red ,A hnkali ta bude side din da Rak ! Ta'ke da sauri ta da'ga kanta ,ganin mimi ce ,ya'saka ta sauke ajiar xuciya da ka'rfi A hnkali Rak ta fito dga ,motar yyinda mimi ke tattare gown din Amarya" kae tsaye AJ.da Queen suka fito ,Nan mimi ta iso gabansa ,Ya Abdul kabani Asma'u kae kuma ka ka'rasa cikin ha'll kae da Amarya!! Ta fa'da murmushi dau'ke a fuskarta." Fuska bbu walwala ya'ke fa'din Amma kinsan dae ya'rda ta'ke ko??" Ya Abdul Ango da Amarya ake buka'tar su shiga Ha'll tare ,</p><p>Plss mimi ka'rki ba'tamin rae ya fa'da rae a ba'ce idan baxamu shiga hka ba."kinga tafiata ,A fusace ya juya xuwa mo'ta ganin yyi an shagaban sa,da'gawar nan da xaeyi sukayi ido ,biyu da Aunty salma wadda itama ,tana cikin shigar Alfarma." Mekake nufi??"</p><p><br /></p><p>"Yau ma dan ba'kin ciki baxaka iya nuna ,murnar kaba" sabida an aura ma'ka makiyarka,</p><p>Abdul jabbar kabani mmki ,dama Abunda Aunty sadiya ke fa'da gaskiyya ne,</p><p>Da sauri sageer Ya'ke fa'din Ayi hkuri Aunty munyi laipi xamu gyara ,tsaki Aunty salma .............."tayi gamida ,Jan hnnun Asma'u ido taf da kwa'lla Asmy ke ka'llon AJ." Ko ka'dan bataso ana yimasa ,Fa'da Hka Aunty salma ,taja hnnun Asmy xuwa cikin Ha'll din." Yyinda AJ.xuciyrsa kamar xa'ata fa'she dan takaici." Badan ya'so ba ,Ya tsaya ya jera tareda Amaryarsa ka'rshe ma mannawa ,idonsa ba'kin glass yyi Wanda ,ba a hngo kwa'yar idanun ta'sa </p><p>Sabida zallar ba'cin rae.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hka bride mate's suka bi bayansu, nan fa DJ.ya sa'ki cool music ,masu daukar pics,nayi masu Vedioting na'yi.</p><p>" har aka Rakki Ango da Amarya ,a maxaunin su yana son yyi mgana da sageer ,</p><p>Bbu halin hakan.Anan mc.keyiwa Ango da Amarya ,sannu da xuwa ................hnkalinsa ga bada'ya yana kan drama Queen na'sa ya ra'sa ta inda xae hangota.".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin kankanin lokaci ,aka fa'ra gudanar da,Event yyinda sageer yabada tarihin Ango a takaice yyinda Mimi,tabada na Amarya " Anan aka ta'so Amarya da ango a tsakiyyar Fili , tsayawa yyi cak! A tsakiyyar filin sae waige -waige ya'keyi A hnkali ya'ji anyi hugging back na'sa kamshin da ya'ji ya gane ko wacece ,da sauri ya dawo daita gabansa,Cike da kulawa ,Ya jawota ajikinsa ,yyi hugging na'ta lokaci da'ya suka sauke wata irin ajiayar xuciya,</p><p>Tamkar sun dde basu ,ga junan su ba ,lokaci da'ya ta sa'kesa ,suna ha'da ido suka sa'karma junan su wani,kayatattacen murmushi ,A hnkali kumatun ta su'ka lotsa dimple nata ya bayyana,Dan ya'tsan sa ya sa'ka aramen, dae -dae lokacin DJ.ya sakar masu Indian cool song."</p><p><br /></p><p>_*Aaj dil sharyanaa*_!!</p><p><br /></p><p>Ma'soyan AJ .idan kuna son Song ,din acikin firm din holiday akeyinta,sae ku nema."😊</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> ,lokaci da'ya ta fashe da dariya shima ya'r daria yyi ,Hnnu ya ba'ta suka ta'fa lokaci da'ya ,</p><p>"Duk Wannan abun da'ke fa'ruwa mutane ,</p><p>Tsayawa sukayi suna ka'llonsu cike da burgewa ,</p><p>Wannan wacece ta sa'ka Ango nishadi ,lokaci da'ya tunda aka fa'ra program ba'aga dariar Ango ba." Sae ynxu nan wuri ya dau Ihu da ta'fi Raf! Raf!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Masu pics ,sae xuba masu pic's sukeyi masu vedioting,</p><p>Ma hka ." A hawayen ba'kin ciki ke shirin gangarowa a idon Rak ,ba shiri tayi saurin Mae dasu,</p><p>Kar mutane su fahimci halin da take ciki Anan AJ.ya shiga ,yiwa Asmy watsin daloli haka ya juya kan Rak yana yimasu ." ya'mmatan gurin nan aka fa'ra gulma ,Queen tayi sa'ar samu ha'dadden Gentle man irin AJ."</p><p>Dan maxa irin su AJ.kadan ne a dunia,</p><p>.............................ya'rda ya'ke nuna so Akan uwargidan sa,tamkar baya ma Amaryarsa rabin-rabinsa,</p><p>Sa'banin wasu maxan da suke wulakanta uwargida,</p><p>Idan xasuyi sabon Aure." Nidae asmy na'ce tom.Allah ya'sa maxajen mu su za'ma irin AJ.Wanda a koina ,zasu shiga a fa'din dunia ,zasu nuna ma ma'cce so hka xasu iya yin Adalci a tsakanin matayensu,Allahumma Ameen,...............</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mimi yhu are hidden somting from me ,Nagano hkan Wannan murmushin ,da kikeyi na mugunta." </p><p>"Relax Rak wat wrong with yhu,?? Ga'ki Amarya kinbi kin da'gama kanki hnkali,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" A hnkali mimi ta Ciro ,wasu drug's a handbag,na'ta Ta zube a hnnun ,Rak " oya karanta bayan ,kwa'llin jiki na rawa rak ,ta shiga dubawa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin rashin fahimta,ta da'go tana ka'llon ,Mimi ban Fahimta ba?? Yimin bayani ,Wannan drug's sinadari biyu ne ,acikin su na da'ya .....................Sha'wa ,na biyu yana bugar da mutum sosae ,cikin biyu dole ayi da'ya kodae ta kwanta ,da wani kotabar cikin hotel din nan,na kira za'ki a waya ,ya takemin kan shegiya da mota !! Ynxu kin fahimta.?? " ta fa'da tana kallon Rak , Cikin ,da murna Rak ! Tayi hugging mimi ,thank yhu so much my best Darling Sistr in d world I love yhu so much,</p><p>Good Job!</p><p>Mimi ,anan sukayi sharking hand's lokaci da'ya suka kya'kyale da daria ,</p><p>Anan Mimi taxuba drugs ,cikin orange juice. "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ga sageer yana,xuwa tanan." jeki ji da Yah Abdul naga baya ,tareda Waccen manyyar gata can gurin Aunty salma." Da sauri mimi ta nufi wurin ,dauke da murmushi a fuskarta."</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>93</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kusan 3 cup glasses tasha na Orange juice ,tana shirin xuba na hu'du da sauri Mimi ta dakatar ,daita murmushin mugunta mimi ,tayi nooooooo............my sweetheart hka ma ,ae is okey cikin ba'ta rae Asmy ke fa'din meyasa my Angel??" Tayi mganar cikin sanyin murya Hka tana wani lumshe ido,</p><p>Da'fa ka'fadarta tayi sorry kibarsa hka."</p><p>A hnkali Asmy ta do'ra kanta akan table ,</p><p>Tana jin kanta cikin wani irin yanayi ,da'ga lokacin bata ka'ra mgana ba."tsayin minti goma ,tana cikin Wannan ynayin jin tayi komae na'ta na juyawa haka."ta fa'ra ganin dishi -dishi ga wurin da ta'ke bbu kowa,Cikin muryar son tayi kuka ,ta da'fe marar ta,</p><p>Tana kiran sunan Angel a hnkali." Shuru taji,cikin wani irin yanayi tamike ,tsaye tafia ta'ke dakyar ,ta nufi hnyr fita dga cikin hotel din."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kusan cin ka'ro sukayi da sageer ,A firgice ta'ke kallonsa ,nan ta'ke taji zuciyarta na Neman tsinkewa." Kar dae sageer ya ganota ne??" Saurin sae ta kanta tayi ,shikuma ganin ya'rda ta ru'de lokaci da'ya yasan bata da gaskiyya ,</p><p>Ina kika fito hka??" Yamata tamabayar yna kallonta,</p><p>Dan murmushi tayi kaina ke nema sweety ,xo muje ka'ji ta rika hnnun sa,yyi saurin kwa'ce hnnun sa,</p><p>Xan dan fita nan ,wajen hotel akwae wanda nakeson gani..............................lokaci da'ya hnkalin mimi ya tashi ,shikuma sageer sanin halinta ya'sa ya fa'da mata hkan ,dan da alamr akwae abunda ta'ke bo'ye masa." dai -dai lokacin AJ. Ya iso hnkalinsa a tashe ,Anan ya'ke tambayr mimi Queen fa??" Kusan zuciyarta tsinkewa ne batayi ba,</p><p> Banganta ba Ya Abdul??" Tayi mganar ,tana kallonsa ,Hnkali tashe AJ." Ke kallon sageer plsss,sageer ina jin ,feeling strange ajikina."</p><p><br /></p><p>"Kwantar da hnkalin ka ,muje can muduba Cewar sageer gamida nuna wasu fararen kujeru ,kusa ga wasu flowerse,</p><p>Saurin dakatar dashi mimi ,tayi mexae kaita acan sweetheart .........mudae je ciki mu bincika ,ya Abdul kae kaje kaji da sauran Friend's naka ,da amaryarka. Kar Aunty salma ta neme ka." Ba'ki da hnkali mimi ,kai tsaye wajen fararen kujerun batareda ,ya ka'ra bin tasu mimin ba." Shima sageer bin bayansa yyi ,</p><p>Yayin da akabar mimi cikin tashin,hnkali gumi." Ka'ryo mata ya'keyi ta koina." Hnkali tashe ta da'ga waya ,tana Neman layin Rak!</p><p><br /></p><p>"Bbu inda basu duba ba,Acikin hotel din bbu alamr Queen dinsa, lokaci da'ya jikinsa yyi ,sanyi a hnkali ya daura kansa, ajikin mo'ta ,mexae hna mu fita da'ga cikin hotel din ,muje mu tamabayi security ,mna."</p><p>"Anan sageer keyi masu bayanin ,basu ga fitowar wata yarinya ba ?" Wadda shekarunta baxasu ,wuce shekara goma sha takwa's ba a dunia ,anan AJ.ya'ke fa'din kalan kayan da'ke jikinta."</p><p> Anan wani ,kema AJ.bayanin ya'ga fitar ta ,wandda bata fi minti biyr da fita ba,sunyi ko'karin tsaidata ,bata sauraresu ba,kuka ma takeyi." Lokaci da'ya AJ. Ya'ji kirjinsa ,</p><p>Na wani irin bugawa ."sageer yyi ka'rfin halin jawo motar ,dakya'r AJ ya iya shiga motar suka fice ,da'ga cikin Hrabar hotel din da gudu..............</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Fatan Akhairi sis Atika bello Aliyu ." so much Luv yhu ,my best Sistr in d world ## Asha kindirmo lpia_.😊 </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_*TEAM DRAMA QUEEN*_.💝</p><p>WATA RANA!</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_Take note_*!!</p><p>"Am sorry guy's kunji ni shuru 2day'z ana bikin sistrna ne, shiyasa kuka jini shuru kwa'na biyu amma ynzu Alhmdullh ,angama biki Amarya na bada gaisuwa ,ga duka masoyan Asmy b Aliyu." One luv#</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>94</p><p><br /></p><p>" Tunda ya'ke a rayuwarsa,baeta ba tsintar kansa cikin tashin hnkali irin na yau ba." Zuciyarsa tamakr xata ,fito sabida tsananin fargaba ,A hnkali sageer ya sassauta murya ,oh common pls AJ." Kowa yasan how yhu ,.must be feeling ,hkuri xakayi kayi addu'a." da sauri Sageer ya ta'ka burki sakamakon ,Hango Asmy xaune a gefe titi ta ha'da kae da gwiwa,da sauri AJ." Ya ba'lle marfin ,motar haryana har'de ka'fa ya ka'rasa gurinta ."</p><p>Jin an ta'bata yasa ,ta da'go da ka'rfi idonta sun ka'da sunyi wani irin Ja ,ta wani hargitse lokaci da'ya da azamar ta tamike tsaye ,tayi saurin fa'dawa jikinsa ,ta dannan kanta acikin kirjinsa , tana girgiza kae hka ta rike ku'gunsa jikinta koina ka'rkarwa ,ya'ke yyinda hawayen Idon AJ." Suka ka'sa tsayawa ya ka'ra rungumeta,</p><p>A hnkali ya ka'lli sageer ,wandda yyi folding hnnunsa a kirjinsa ,yana kallonsu murmushi dau'ke a fuskarsa,</p><p>Shima AJ.murmushin yyi yna goge hawayen idonsa,</p><p>A hnkali ya da'gota dga jikinsa ,Hi my drama Queen Are yhu okey ??, A hnkali ta kae hnnunta ajikin suit coat nasa, tana ko'karin Cireta ,cike da mmki da tsoro ya'ke kallonta ,hannunsa da'ya yasaka ya rike hnnun nata yna kallonta a tsorace hka yamae da kallonsa,</p><p>Kan sageer ,lokaci da'ya yaji ta fashe masa da wani irin ku'ka tana ko'karin fisgen rikon da yyima hannayen ta,</p><p>"Alama sageer yyiwa ,AJ. da ya sa'keta cikin sanyin jiki AJ. Ya saketa ."</p><p>A hnkali ta Da'ga kafafunta , Dan yafita tsawo nesa bakusa ba ,tana ko'karin Ha'da bakinsa da na'ta ya daka mata wani irin mahaukaciyar tsawa!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Stop it Asma'u !!</p><p>,Ya fa'da cikin wani irin fushi hka lokaci da'ya ya hankada ta gefe,</p><p> Cikin rashin sa'a Ta bugi wani ka'ton dutse ,da'ke gefen hanya ,Kanta ya Dan bugu A hnkali jini ke fita a goshin ta."</p><p>Da sauri Sageer yaxo xae kamata AJ." Yyi saurin dakatar dashi daukarta yyi cak! Zuwa mota batareda ya ka'ra kallon, sageer ba." </p><p>Sageer kuma Sae fa'da ya'ke masa bai kulasa ba ,</p><p><br /></p><p>......"wani irin kuka Asmy keyi tana da'fe da goshinta ,da'ke famar xubar jini ,Haka ta matse kafafuwan ta guri da'ya tana juya kanta ,farin Hankicif ya sa'ka ya daure kan na'ta AJ. Ya rasa meza yyi mata ta daina wannan kukan."</p><p><br /></p><p>Bae san meyasa ,ta canja lokaci da'ya ba bae San meyasa take wasu abubuwa tamkr baita ba." Yna hango sageer Tsa'ye ajikin mo'tar Wanda ya ka'sa shiga ,motar Saurin da'ga glass AJ ." yyi A hnkali ya jawota bayada za'bi ya ha'de bakinsa da na'ta lokaci da'ya jikinta ya sa'ki wani irin romantic kisses ,ya'ke yimata a hnkali ya'ke blowing kowace ga'ba ta jikinta ,Sae ajiar zuciya ta'ke saukewa da ka'rfi tana mi'ka sun da'uki minti ,goma a hka a hnkali ya zare ba'kinsa cikin nata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>........kuka ta ka'ra fashe masa ,dashi gabansa lokaci da'ya ya fa'di tunanin ya'ke meke damun Queen dinsa??" Anya aljannu basu shafeta ba.??"........Idan yaciga ba da biye mata komae xae iya faruwa shikansa ka'rfin hali ya'keyi yana jin ,kunyar Sageer ,</p><p>Wya ya Ciro ya kira sageer ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Cikin sanyin jiki sageer yaja mota zuwa sameer meera hospital ,</p><p>Yyinda ya ka'sa ha'da Ido da abokin. Nasa ." Itakam ,Drama Queen kanta na acikin cinyoyinta tana, famar rere kuka tamakr ranta,xae fita.[Truncated by WhatsApp].</p><p>WATA RANA!</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association.</p><p><br /></p><p>95</p><p><br /></p><p>"Bbu abunda kakeji,a bakinsa sae Kalmar innalillahi wainnah illaihir raji'un,idon nan nasa sun ka'da sunyi ja ga'ba da'ya yafice dga hayacinsa lkci da'ya." da kyar yasamu ya sae ta numfashinsa,</p><p>Sallamr Dr.Fatyma Zahra yaji dakya'r ya amsata ,ka'llo da'ya tayi masa tasan yna cikin. "Matsanaciyr damuwa,</p><p>Tanajin tausayin Abdul Jabbar ,har azuciyrta yyinda wani ban'gare tafi tausayawa Rayuwar Asma'u na halin da tashiga."</p><p><br /></p><p>"A hnkali ta zauna kan kujerar ,da'ke fuskantarsa.</p><p><br /></p><p>Cikin raunanniyar muryarta ta ki'ra sunan sa ,bai amsa ba sae dae kurum ya zuba mata pleading eye's nasa, wane juice Asma'u tasha hka??" Cikin rashin fahimta ,ya'ke kallonta." Kallon da taga yana yimata ,yasa ta fahimci bai fahimceta ba." Gaskiyya Abdul Jabbar matarka ,tasha lemu Mae drug's din Sha'awa aciki Wanda shine ya jefata acikin wannan halin,amma ynxu Alhmdullh anyi mata allura ,tayi aman juice din du'ka hka tasamu ba'rci ,sae dae akiyaye ga'ba sabida lpiar Dan cikinta."tsoro mmki lokaci da'ya suka dira a zuciyrsa,</p><p>"Ya'rasa ma wane kalan tunani xaeyi amma tunanin sa ,</p><p>Ya'fi ka'rkata wa'ye yabaiwa Queen Juice ??"......................... Tamabayr da ya'keyiwa kansa ,kenan amma ya ka'sa samun amsarta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Na'gode Dr. Zahra ,amma ina son na wuce daita gda, ya za'ayi??" Yyi tambayar yana ka'llon tsadadden agogon diamond din ,dake manne ."A right hand nasa,bbu laipi sir duk yadda kagani ,Amma fa ta'fara barci kana ganin bbu takura aciki ,insha Allahu xan kiyayaye duk wani motsi na'ta da hka sukayi sallama da Dr.Zahra yyinda sukabar hospital din da misalin ka'rfe goma sha biyu ,da Rabi na da're kai tsaye Guest in..............dinsa sageer ya nufa dasu,Dan yasan yau aunty sadiya da Aunty salma bazasu barsa ba." Dan ya ka'she wayoyinsa du'ka gudun karsu nemesa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wanda ,yaji ddi da ba yau Rak! Xata ta're ba ."da baisan waxae kular masa da Queen ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"The following day........</p><p><br /></p><p>''Kusan karfe biyu da rabi na rana yafito cikin Riga da wando na captani wabangari Mae sararin ,samaniya ." ya ka'fa hula Wanda ta dace ,da kalan shigarsa sae kamshi ya'ke zubawa,</p><p>Kallonsa ya maida kan sarauniyar tasa ,wadda keshan Cornflakes ,Queen !!</p><p>"Ya kira sunan ta cikin sanyin muryarsa,shaye da to'ka ta da'go tana kallonsa,</p><p>Gamida turo masa Dan karamin ba'kinta." dan murmushi yyi dan yasan laipinsa,</p><p>Kyakkyawan sajensa ,ya Shafa."gamida sa'kin kayataccen murmushi Ayimin afuwa dan Allah ya kamata agama shan wannan abun,nasan ni mai laifine ka'r a hukuntani ta wannan hanyr ,plss yyi mganar gamida langabar da kansa ,yna mata ka'llon so .....................naji na hkura amma za'ka biya a siyamin Gwaiba.' Tayi mganar tana ka'llonsa,naji my Queen angama ,murmushi tasaki lokaci da'ya gamida fa'din thank yhu my habiby!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Shiya taimaka mata ta sa'ka hijab na'ta hnnunta ,na cikin nasa suka nufi mo'ta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>***********</p><p>Hajja yanxu kina ganin Abunda Abdul Jabbar yyi ya kyauta??"cewar aunty salma,batareda ta jira amsar Hajja din ba ta cigaba ,da mgana Ace Dan tsabar wulakanci da rainin wayo tun jia babusa bbu alamrsa ,</p><p>Wannan wane irin Abune??"keda kika isa dashi sae ki kirasa ki fa'damasa,da ka'rfe biyr na yamma za'a kawo masa amaryarsa hka dangin ubanta suka tsara.</p><p>Sallamrsa ce ta ka'tse Aunty salma,Hajja kurum ce ta amsa sa yyinda,Aunty salma ko ka'llonsa batayi ba." Da gudu Asmy taje ta xauna gafda Hajja ,ta aje ledar Gwaibarta a ka'san carpet ta dan kwanta ,a ka'fadar Hajja cikin sanyi murya take fa'din Granny nayi kewarki ,da yawa." Shafa kanta hajja tayi cike da kulawa ,take fa'din nima hka my Queen ina kika shigane??" Dan murmushi ta sa'ki Granny wannan Habiby zaki tambaya." Tana da'go kanta ,anan Hajja ta lura da bandeji da'ke manne a goshinta,</p><p>Hnnunta takai wurin ,cike da damuwa take fa'din meya sameki hka??"</p><p>Hnnunta takae wurin gamida yin ra'u ra'u da ido wlhi Granny habiby ne?"</p><p>Yyi min tsawa ajia kuma ya.........da sauri Hajja ta ka'tseta ya Isa Haka muje na zuba ma'ki Fete ae zakici ko??"</p><p>Cike da murna ta'ke fa'din Ehhh ,xan cimana granny."</p><p><br /></p><p>Hnnunta taja,xuwa dener Area." Yyinda Aunty salma ,tabisu da ka'llon takaici."</p><p><br /></p><p>Shikam AJ.tunda ya shigo a falon ya'ke zaune akan carpet ,hka ya sunkuyar da kansa,a ka'sa."</p><p><br /></p><p>Mganar hajja ce ta dawo ,dashi Hayacinsa ,Meyasa meka Abdul Jabbar tun jia ka ka'ma wya ka ka'she kabar gurin dener batareda,ka fa'dawa kowa uzurinka ba.??" Shuru yyi ,</p><p>Hajja tanisa,cikin sanyi ya fa'ra yiwa hajja bayani ,Allah ya kyauta kurum ta iya fa'da gamida fa'din Allah ya tsare ga'ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zuwa ka'rfe Hudu inason ganinka,Amsa mata kurum yyi da to."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ku'san ka'rfe hudu da Rabi na ya'mma Hajja tasamesa A master bedromm na'sa ,tsaye tayi Tana ka'llon yanayinsa,</p><p>Wae. Mikake nufi katashi ka shiga wnka mna ,lokaci na tafiya Abdul Jabbar! Tamkar yyi kuka ya'ke ka'llon Hajja plss Hajja ,badole sae nayi wnkan nan na Al'adaba." Ki taimakeni dan Allah ,yyi mganar a raunane,</p><p>Kasan Allah sae kayisa,saura Rabin awa kaje ka taho da amaryarka ,tashi mutafi ." bayason musu da Hajja,</p><p>Ko ka'dan jiki bbu kwa'ri ya Mike ,suka nufi side na'ta dan acan xaeyi wnkan Angwanci."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Zaune ta'ke a main falo, tayi rashe-rashe kan carpet ,wata bingilar Riga ce ajikinta maroon colour half gown,Mae guntun hnnu,</p><p>Sae hular net white da tasaka akanta."sae cin wainar fulawarta take A hnkali ,wadda ta ba'de da ya'ji Mae tafarnuwa."</p><p>muryar Hajja taji akanta. akanta,da'ga ido tayi Tana kallonsu washe ba'ki tayi ganin Habibyn ta,</p><p>Cike da shagwaba,</p><p>Take fa'din habiby ina ka shiga ne ,ina ta nemanka??"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bae iya amsa taba ,ya shige master bedroom din Hajja da sauri ,da kallo tabisa.[ _@t 6:40pm.by Asmy b Aliyu_]</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>96</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sanye ya'ke cikin farar shadda da, babbar Riga da ya'r cikinta.</p><p>"Ya ka'fa hula black ,wadda ta dace da ka'lan dressing na'sa sae kamshi ya'ke zubawa,</p><p>Zaune ya'ke agefen royal bed din Hajja, kansa a ka'sa yana sauraren nasihar da Hajja keyi masa." A lkcin jin ya'keyi tamkar yyi ihu wani sashe na zuciyarsa ,</p><p>Tunanin Queen na'sa ya addabesa,</p><p>Yna tunanin ya'rda zasu Raba kwanciya ,that mean's Hajja ,ta dauke Asma'u dga garesa na tsawon sa'ti da'ya." Dan ka'ramin tsuka ya'ja ,</p><p>A hnkali ya'ke ka'llon hajja cikin sanyin muryarsa,</p><p>"Ya'ke fa'din plss hajja ki aramin Asma'u na yau dan Allah ??"</p><p>Saurin girgiza kae tayi ,baxai yuyuba." nasan ya'kake ji a ynxu daurewa,</p><p>Zakayi Allah yyi maka Albarka."</p><p><br /></p><p>Ka'je kaxo da amaryarka.!</p><p><br /></p><p>"Hajja ta ka'rasa mganar gamida mikewa,tsaye da shanyayyun idanunsa yabita ,da kallo tana fita ya'r rigimarsa ,ta shigo da sauri tamkar wadda aka Jefo."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A shagawabe ,ta xauna kan cinyarsa tana sauke numfashi,</p><p>Cike da shagwaba,da turo baki take ka'llonsa shaye da to'ka take fa'din ina zaka haka??" Dan Allah zan bika,tayi mganar gamida ,sakala hannayenta akan wuyansa,</p><p>Hnnunsa,</p><p>Yasaka ya zagaye kugunta,</p><p>Ya riketa gagam ,tamkar </p><p>Wanda xa'ayiwa kwa'ce."</p><p><br /></p><p>Cikin idanunta ya'ke kallo ,cikin raunanniyr murya ,ya'ke fa'din."Am sowiee my Queen nayi mki laifi kiyafemin ??",cikin turo ba'ki take fa'din ni na yafe Habiby dan Allah mufita ta're,kaji plsss!!</p><p><br /></p><p>"Xaeyi mgana ,tayi saurin sa'ka hnnunta ta rufemasa,</p><p>Ba'ki ka'rkace nooo plsss ,tayi mganar cikin rawar murya a hnkali ta kwantar da ,kanta akan shoulder nasa,</p><p>Tana sha'kar turaren jikinsa,.</p><p>Wata irin kasala ce ta rufesa ,lokaci da'ya tallabo fuskarta yyi da taffukkan hnnun sa."</p><p>Sae ya'ga guntun hawaye,</p><p>Akan fuskarta."</p><p>Yna iya jure komae banda zubar hawayen ta,</p><p>A hnkali ya lalubi bakinta cikin wani irin sa'lo ya'ke tsotsar harshenta ."</p><p><br /></p><p>Yna sauke numfashi da ka'rfi itama hka ka'rar wyarsa,</p><p>Ya katsesu,</p><p>Cike da kasala yyi saurin sakin bakin na'ta."</p><p>Da kya'r ya saeta natsuwarsa bae dauki wyarba."</p><p>Har ta ka'tse dan kanta,</p><p>Daita ya Mike tsaye tana,manne a kirjinsa."</p><p><br /></p><p>Cikin muryar son tayi kuka ,take fa'din zakaje dani na canja ka'ya ??"</p><p>Ina son wannan turaren na'ka wlhi dan Allah karkace ,</p><p>Bazaka dani ba....................Habiby!!</p><p><br /></p><p>"Ta fa'da hawaye ,suka silalo akan fuskarta." Dae -dae lokacin Hajja ta ka'raso cikin da'kin da sauri yyi hanayr fita,</p><p>A hnkali Asmy ta fa'da kan ga'do gamida fashewa ,da wani irin kuka."</p><p><br /></p><p>Hajja sae famar lallashinta,ta'ke tayi mata banza,Kanta tamakr xaya cire sabida ciwo. "</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Zaune ya'ke a falon Abban su Rukaiyya ,ya yinda ya'kemasu Nasiha du'kan su,yafi ka'rfin minti talatin yana masu Nasiha ,da Addu'a amarya Rukaiyya sae famar kuka ta'keyi tamakr ranta zae fita hka ya'n uwa da abokan ,Arziki suka sa'kata A motar AJ. Yyinda Aunty salma ta koma ,gefen kunnenta tana yimata,</p><p>Mgana ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mimi da Aunty salma ce suka bi motar su AJ ." A baya ,</p><p><br /></p><p>.A bangaren AJ. Kuwa ya kule kira'r Abdul Rahman sudais ,yyinda kukan rak ke tafasa,masa xuciya ." A hnkali ya gangara da motar gefen titi." Gamida ka'sheta ,</p><p>Sae kuma ya'ji tabasa tausayi,</p><p>Ya tuna itama Asma'u haka tata kukan nan,</p><p>Cike da tausayinta da lallashi,</p><p>Ya jawota ajikinsa ."yana dan bubbuga bayanta alamr rarrashi,</p><p>Lafewa ,tayi ajikinsa lkci da'ya tana sauke ajiar xuciya ,</p><p>Wani ban'gare kuma ,taji ddin ya'rda Yayan nata yanuna mata kulawa,</p><p>Fitinannen turaren jikinta,</p><p>Sae fisgarsa ya'ke cikin wani irin yanayi ,ya lumshe idonsa ,gamida gyaramata kwanciyarta ,akan kirjinsa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>By~ Asmy b Aliyu.👌🏻</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>97.</p><p><br /></p><p>Cikin kan'kanin lkci ya janye jikinsa ,cikin na'ta gamida yiwa motar key ta wutsiyar ido ta'ke kallon yanayinsa,</p><p>Gaba da'ya jikinsa a sanyaye ya'ke komae har ya danna hancin motarsa ,</p><p>A sameer meera Estate bae ka'ra kallonta ba."hka baeyi mata mgana ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yna gama parking ,iyaye mata sukayi cirko-cirko a bakin motar suna jiran fitowar amarya ." wata kanwar Hajja ce tayi ka'rfin halin bu'de side na Rak! </p><p>"Ta fito daita A hnkali sae fa'din ta'ke tayi addu'a ta shigo da ka'far dama ,AJ.jin ya'ke tamkar ya sha'keta Dan takaici.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" kai tsaye side nata aka nufa ,daita nan Friend's na amarya suka ta'ke masu baya.'</p><p>Juyawa tayi xata bisu sae taji yayan nata ya'ce Mimi!!</p><p><br /></p><p>Cikin wata irin murya cak! Ta tsaya,hka taji zuciyarta na Neman tsinkewa,Addu'a takeyi Allah yasa yayan nata baigano plan dinta ba."A zuciyarta ta'ke fa'din ohhhh my Rabbi help me out."</p><p><br /></p><p>Cike da da'kewar zuciya ta ka'raso gabansa,gamida rike ma'rfin motar da da'yan hnnunta."</p><p><br /></p><p>."A shagawabe ,take fa'din sae yanxu ka tuna dani,tun wurin dinner bamu ka'ra haduwa ba." Ta fa'da gamida turo bakinta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Am sorry kinji ,yyi mganar A hnkali kekan ki kin sani ,</p><p>Baxan kyaleki ,hka kurum ba.''</p><p><br /></p><p>Dama ina son na shaida maki ,jibi zamubar ka'sar nan ta're Dake....................sosae ta nuna murnarta ,A fili tun ka'fin taji ko wace ka'sace,</p><p>Lallae ya Abdul dama yana son Rak ! Ya tsaya wahalar ,da Kansa a banza."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cike da murna ta'ke fa'din ya Abdul wace ka'sar zakaje Honey moon din??"tayi masa tambayar ,murmushi dauke a fuskarta."kallon rashin ,fahimta yyi mata."</p><p><br /></p><p>Wane irin honey moon kuma??"Indian nake maki mgana ,nayi bincike ,</p><p>Nagano akwae wani asibitin kwa'kwalwa ana dacewa,yarda naji ya'rda hospital din tayi fice,</p><p>Acan nake so nakae Asma'u so sae ki shirya tare zamu wuce ,ranar Laraba."</p><p><br /></p><p>Yna fa'din hka ya juya yabar Mimi cike da tashin hnkali Allah yaso bata shirya ,barin Nigeria ba yanzu." Kwa'lla</p><p> ta ta'ru a idonta,</p><p>Gaskiyyar Rak ne, yah Abdul yadaina sonta ,Asma'u kurum ce a birnin zuciyarsa ......da gudu ta juya ta nufi cikin gda."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta ko'far baya yabi zuwa side din Hajjaa Dan ya lura ,koina gdan da jama'a yasan ynxu hka Queen nasa ,na can A takure sabida yawan jama'a.</p><p><br /></p><p>Bae tsaya koina ba sae a master bedroom din,Hajja hamdala yyi da ya hangota kwan'ce akan soofa ,sae barci takeyi abinta tayi parking ba'kin gashinta da Jan riboon sae sheki ,ya'keyi tayi wani irin kyau,na mussaman ba'kar fatar ta sae sheki takeyi."</p><p><br /></p><p>"Ba'kin Jean's ne ajikinta pencil ,ya kamata sosae sae wata ya'r bingilar Riga pich colour Mae ya'n kakken hnnu tashan iska." Kokadan bayason ya katse mata barcinta,</p><p>Agogon da'ke manne da hnnunsa ya ka'lla kusan ka'rfe shidda ,da rabi na ya'mma A hnkali ya zauna dae -dae gurin kanta ,</p><p><br /></p><p>Kanta ya da'go ya do'ra akan cinyoyinsa ,cikin wani irin salo ya'ke huramata iskan ba'kinsa a kunne ,</p><p>Sannu A hnkali ta fa'ra motsi tamakr a mafarki takeji kamshin turarensa,</p><p>Saurin bude ido tayi ,zubur tamike zaune ." kallonsa tayi cike da murnar ganinsa ta rungumesa,</p><p>Gamida tura kanta cikin fa'deden kirjinsa ,A hnkali take lumshe ido tana budewa ."ina son kamshin nan Habiby!!</p><p><br /></p><p>"Murmushi yyi gamida lakaci hancinta.</p><p>Granny fah?</p><p>Yyi tamabayar yna kallon ,kyawawan idanunta,</p><p>Shaye da to'ka take fa'din suna babban fa'lo itada wasu mutane,sun cika gdan sun sa kaina yana yimin ciwo."</p><p>"Ta ka'rasa xance cike da damuwa" kae tsaye gurin closet ya nufa Ciro ,mata dogon hijab fa'ri har ka'sa ya sa'kamata cike da murna ta'ke tamabayarsa,</p><p>Inda zasu??" Bae amsata ba ,ya dauko plat shoes ya taimaka mata ta sa'ka yana rike da hnnunta,</p><p>Zuwa parking lot...........body guard's na'sane suka ka'raso gurin motar yyi saurin da'katar dasu,</p><p>Alamr dakansa xae fita." da hka Mae gadi ya bude masa get ,Hnnunsa da'ya na kan sitari da'ya kuma yana rike da hnnunta,yana wasa da yatsun hnnunta."</p><p>,wata irin azababbiyar Sha'awa ce ke addabar sa.</p><p>Yau bae san ya xaeyi da ya'r rigimar tasa ba.da hka yake ta tunani ,har suka isa guest in......dinsa, Queen sae surutu ta'ke masa." Yana gama parking ya fito dga motar ,ya fito side nata,</p><p>Da'yan hnnunsa ,ya sa'ka ya bude mata ma'rfin motar Mae makon tafito ,sae yaga ta ba'ta rae tana kallonsa,</p><p>Cike da Rigima take fa'din ni banzan shiga ,wannan gdan ba." </p><p>bana sonsa</p><p>,plzzz kazo muko ma</p><p>Gda."</p><p><br /></p><p>Kiyi hkuri my Queen xuwa anjima .</p><p>Ka'dan zamu koma."</p><p>Ba'anan </p><p>Zamu kwana ba.''</p><p>Promise meeee??"</p><p>Tayi mganar ,gamida zuba ,</p><p>Masa sexy eye's nata ."</p><p>a raunane ya'ke fa'din I promise,</p><p>Right hand nasa yabata ,</p><p>Takama sa'ananann tafito dga motar,</p><p><br /></p><p>Jinginawa ,tayi jikin mota gamida yin folding hnnunta ,cikin turo ba'ki take fa'din ,</p><p>Ni ka goyani nagaji da ,yawa bazan iya tafia ba."</p><p><br /></p><p>Bbu musa ya russuna ,ta haye bayansa ."</p><p>Cike da jin ddi A hka suka nufi aenahin ko'far shiga cikin gdan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A tare sukayi sallar magrib ,</p><p>Suna idarwa bata tsaya doguwar addu'a ba ta cire hijab na jikinta." Ta aje a gefe ta cire kayan jikinta."</p><p><br /></p><p>Kae tsaye side din ,da ake ajiye towel's ta nufa anan ta jawo da'ya ta daura ,</p><p>Wanda bae gama rufe mata cinyoyi ba."</p><p><br /></p><p>*Habiby*!!</p><p>Muje muyi wanka ina jin zafi ,</p><p>Kallonta kurum ya'keyi sae da ya gama addu'oin sa ,ya kalleta a natse,</p><p><br /></p><p>Kibari sae xuwa anjima muyi wanka gaba da'ya,shaye da to'ka take fa'din ni yanxu zanyi ,kaxo karaka ni, kae idan baxakayi ba .shikenan!!</p><p><br /></p><p>"Ganin tana son tamaida Abun rigima,ya cire kayansa shima yajawo ,towel ya do'ra a kugunsa."</p><p>Suka nufi toilet .</p><p><br /></p><p>"Tsayin minti go'ma ya daukesu a toilet ,sae gashi sun fito yana dauke daita tamakr wata,</p><p>Baby gal sae kya'lkyalar daria ,take akan gado ya shimfideta,</p><p>Yamata rumfa,da fa'deden kirjinsa,</p><p>Cakul'kuli ya'keyi mata ta koina ,</p><p>Sae ba'ngalar daria takeyi tana rokons ,akan ya daina dan Allah."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kwance ya'ke a gefenta yna Mae da numfashi kan ruwan,cikinsa ta haye ,itama lkci.da'ya ta shiga yimasa cakul'kuli fisgota ,yyi yna binta da wani irin ka'llo Wanda ,ta kasa fassara sa."</p><p><br /></p><p>''Cikin wani irin sa'lo ya'ke walwale towel din jikinta,</p><p>Gefe ya jefar dashi ."saurin shigewa tayi ajikinsa,</p><p>Cike da jin kunya harshensa ya saka acikin kunnenta." Hnnunsa </p><p>Da'ya kuma yana akan breast ,</p><p>Nata ."dganan salon na'sa ya fara canjawa ,wata irin zafaffar soyayya ya shiga nuna mata."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Afuwan da rashin samun update a koda yaushe,nayi tafia ne.....inda naje akwae da'n matsalar network ,sae kunyi hkuri._"����🏻</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>B.Aliyu😘</p><p>WATA RANA!</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association.. "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>98.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Lungu da sa'ku hajja ta Shiga neman Asma'u bbu ita bbu alamr ta,hnkalinta ba ka'ramin tashi yyi ba."</p><p>Hanyar da xata sadata da side ,din ba'ki taci ka'ro da Mimi ."da sauri ta dakatar ,daita.ta hanyar fa'din Mimi baki ganarmin Asma'u ba??"hajja tayi mganar damuwa ,dauke A fuskarta."</p><p><br /></p><p>Cikin zafin rae mimi kefa'din meye damuwarki akanta ne hajja??" Ko kema kinfi sonta ,da kowane??" Mimi takarasa mganar cike da kishi da son tayi kuka."</p><p>Meya kawo wannan mganar ,kuma lailah?"hajja ta fa'da tana kallon tana ka'llon ynayinta."plsss hajja leave me a lone bana son mgana ,</p><p>Da gudu ta ra'ba ta gefenta ta nufi side na'ta da ka'llon mmki Hajja tabita." Tashin hnkali ,yna nufin kenan Mimi ta fa'ra tsanar Asma'u kenan.?"abun da take gudu shi xae fa'ru ,laifin bana kowa bane ,sae na Abdul jabbar xae dawo ya sameta ne."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kusan ka'rfe goma da rabi ,ya kunno hanci motarsa,cikin Estate din sameer meera.'' Yna gama parking ya ka'she motar ,ka'llon side din da ta'ke yyi sae barci takeyi abunta." A hnkali ya kwantar da sit gamida lumshe idonsa ,tunani ya'keyi yarda xae bu'llowa Hajja,yasan a kullum shine Mae laifi........yafi minti goma sha biyar, A hka.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Daukarta yyi tamkar wata baby gal, kae tsaye ya nufi side din hajja ,Daita cike da fargabar ya'rda xae iya ha'da ido da Hajjan."da sallama yashiga ko'far baya,Dan yasan ta gaban cike ta'ke da mutane amma abun mmki ,sae yajita a rufe,</p><p>Cike da sanyin jiki ya juya.'' Da nufin yabar gurin sae yaji ance ina kuma zaka daita marar kunya!</p><p><br /></p><p>"Tsayawa yyi cak! Oya zoka ajeta ka ba'cemin da gani kafin na baka mmki ,hajja tayi mganar rae a ba'ce gamida nuna ma'sa hanyr ko'far jiki a sabule ya juya ,ya shige bae direta a koina ba ." sae a lallausan gadon Hajja ,</p><p>Ga mmki sae yaga tayi saurin bude idonta ,gamida rikemasa Kwa'llan rigarsa cikin son tayi kuka take fa'din ina kuma ,zakaje baka siyamin ice cream ba??"baece komae ba ya cire hnnunta dga wuyan rigarsa,</p><p>Yyi hanyar fita daga da'kin da harara ,Hajja tabisa har yafice dga da'kin ran sa a ba'ce.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"in a ...... Rukaiyya room.</p><p>Fitowarta kenan dga wnka,</p><p>Kae tsaye gaban mirror dressing ta nufa ,anan ta Shafa turaruka ,masu sanyi kamshi bayan tagama shafa Cream's din da take using dasu kae tsaye closet dinta ta nu'fa hnnunta ta sa'ka taciro gown din sponge Bob ,Half gown ta sae hular net white ."</p><p><br /></p><p>Kae tsaye ga'do ta nufa ,remote na Ac.ta dauka ta ku're volume. " ta dauki ha'dadden duvet dinta taja ta rufe jikinta ,tabar fuskarta kurum."</p><p><br /></p><p>Hnnunta ta sa'ka ta kunna bed light marar haske ,gamida ka'she wutar da'kin ,ka'rar wyar ta taji tamkar baxata da'gaba ,sae taga Darling Sistr na yawo akan screen na wyar." Cikin hanzari ta da'ga hello Mimi yne??"</p><p><br /></p><p>"Mimi harkin fara barci kenan??</p><p><br /></p><p>" Rak .....nop tukuna dae ,taya zan iya barci Mimi kema kinsan da wuya."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mimi....kina nufin har yanzu bae dawo ba??" Dan ta'be baki Rak tayi ,tamakr tana ganinta,ina xae dawo yna tare da ,Zuma dinsa."</p><p><br /></p><p>Ya'r ka'ramar tsuka taja ,kedae ki tabbata kinyi amfani da maganunnukkan da aunty salma tabaki." Kitabbar kin shasu,anan Mimi ta ka'tse wya .........dae -dae lokacin kuma taji ka'rar bude ko'far da'ga kae tayi gamida zubawa ko'far ido ,yana cikin fararen pyjamas Riga da wando,yyi kyau sosae acikin kayan lokaci da'ya taji gabanta ya fa'di kae tsaye ,taga ya nufota daukeda ,bakar Leda a hnnunsa."tsayawa yyi akan ta yana ka'remata kallo."</p><p><br /></p><p>Ta wutsiyar ido take kallonsa,ya'r karamar tsuka yaja, Allah yagani ancucesa wlhi !! Ba'aga wacce za'a ha'dasu aureba." Sae wadda ya'keyiwa ka'llon wacce suka fito aciki da'ya ,cikin kakkausar murya ya'ke fa'din nasan ba ba'rci kikeyi ba." Kitashi ga abinci nan kici ya fa'da gamida dire ledar akan bedside drower."</p><p>Still yna rike da kugunsa yana kallonta ,A tsorace ta bude ido tana kallonsa ,bbu shiri tamike zaune tana zare ido ,ba'lla mata harara yyi gamida sakin dogon tsaki ,ya juya yafice da'ga da'kin kifa kanta tayi a filo gamida sa'kin marayan kuka................</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Washe gari ....</p><p>Misalin ka'rfe takwas da rabi,taji ana buga mata ko'fa Dan tsaki ,taja gamida juya kwanciyarta ,</p><p>A hnkali kowaye ae sae yyi tayi bata gadamar budewa ,ba."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Juyawa yyi abunsa ya nufi Estate din Hajja ,duk da fushi ya'keyi daita Queen na gdansa ae dole yabuga mata sammako ,idan tagaji sae tabasa matarsa."</p><p><br /></p><p>Kicibis sukayi ,da aunty salma.''</p><p> da'n Jada ba'ya yyi sa'annan ya gaisheta ,cike da girmamawa ciki-ciki ta amsa sa."tana mmkin wannan uban sammako na'sa Wanda keda sabuwar amarya a da'ki!</p><p>"Rukaiyya fah?</p><p>Tayi masa mganar bbu walwala a fuskarta ,aransa yake fa'din ,ae sae kuyi tayi mana ,gaba da'yanku kunbi kun tsaneni akan mganar auren nan...........cikin sanyin muryarsa ,yake fa'din barci takeyi batace komae ba ta ra'ba ta gefensa ta wuce,da shanyayyun idonsa yabita da ka'llo."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Acan master bedroom ,din Hajja ya isko ana rigima da Asma'u sae kuka takeyi tamkar xata she'de takasa ,koda yiwa hajja mgana ne, kwance ta'ke akan cinyoyin Hajja da'fe da kanta tana jujjuyasa A Hnkali hka hawaye na ambaliya a fuskarta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Agigice AJ .ya ka'ra gurin Cikin rawar murya ya'ke fa'din granny meya sameta??"</p><p><br /></p><p>Ajiar zuciya hajja ta sauqe ina ,zan sani Abdul Jabbar tun daren jia ta'ke a hka."sae zantukka ta'keyi marar ma'ana narasa ,gane kanta."</p><p><br /></p><p>Da sauri AJ. Ya tallabo fuskarta ,</p><p>My Queen are yhu okey??"</p><p>Yyi mganar muryarsa ,A hnkali ta da'ga kyawawan idonta ,Wanda suka koma Red ,dan tsabar kuka ,cikin wata irin murya ta'ke fa'din Habiby !!</p><p><br /></p><p>"Kae na xae ciremin plsss ka cireman shi na huta ,Dan allah." Is OK Queen am right here daena ,kukan hka ya Isa."</p><p><br /></p><p>Hnnunsa,na dama ya daura kan goshinta gamida rike kanta ,da kyau a hnkali ya'ke karanto mata addu'oi.....................cikin wata irin ka'ra ta'ke fa'din MUMIN!!!</p><p><br /></p><p>"Gamida Rike hnnunsa da ka'rfi A hnkali ta'ke fa'din wayyo Allah na ! Kaena xae cire!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" lokaci da'ya AJ.yaji zuciyarsa,</p><p>Na Neman tsinkewa ."kiran wannan sunan ,yna nufin tunanin tane keson dawowa, agigice AJ.ke fa'din Hajja ta sumaaaaaaa.........!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"By ~Asmy b Aliyu.👌🏻</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>99</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Motar dr.Zahra nagama parking cikin estate din Mr.meera ,da sassarfa AJ.</p><p>Ya ka'raso gurinta gaba da'ya ya rude ya fita hayacinsa,</p><p>Lkci da'ya hnnunsa,yasaka ya bude mata ma'rfin motar ."</p><p><br /></p><p>Cike da tausayi tabisa da ka'llo lallae bakaramin so ya'keyiwa Asma'u ba." Kai tsaye part din Hajja suka nufa.''</p><p><br /></p><p>Dr.Zahra ce kurum ta ,nufi da'kin datake yyinda AJ. da granny suka tsaya a falon ...............Dr.Zahra tafi minti ashirin a da'kin kafin Dr.Zahra tafito daga da'kin ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kae tsaye ta tunkari gurinsu,</p><p>Anan ta zauna ,a raunane AJ. Kefadin Dr. Zan iya Shiga na ganta ,da sauri ta girgiza kae tukuna dae Sir."</p><p>Nayi mata allurar barci ,tunaninta ne keson dawowa a kowane lkci." Yaushe ne tafian Ku Indian??</p><p><br /></p><p>Gobe na'ke tunani tunda naga ,jikin na'ta ya tashi ."yna da kyau hkan,</p><p>Ya kamata kayi booking flight ,yau sir Dan ako wane tym.....tunanin ta xae dawo, yazama kuna tareda likitan kwa'kwalwa."ajiar heart ya ,sauke gamida ka'llon Hajja yaji mezata fa'da sae yaga ta kalli dr.party gamida fa'din angode insha allahu Dr."anan Dr.Zahra tayi masu sallama ,Har bakin mota AJ.ya ra'kata ya Ciro kudin da baesan iya karsu ba ,ya Daura mata akan sit ."godia tayi masa ,mae gadi ya bude mata get ta fice......</p><p><br /></p><p>"Wayarsa ya Ciro acikin aljihun wandonsa ,yana Neman layin sageer baya ,Shiga.''</p><p><br /></p><p>Juyawa yyi ya koma part din ,Hajja anan ya isko su Mimi suna break fast itada Rak! Kowacen su tasha ,gayu gamida ka'she dauri,</p><p>Cikin ha'din baki suka gaishesa,</p><p>Cikin ka'rfin hali Rak ke fa'din Yah Abdul kayi break fast kuwa??" Shuru yyi mata hajja ta amshe zancen da fa'din ina yyi break fast ,sauko Mae da break fast na'sa a ka'sa ki aza masa ka'tuwar carpet sae ki Daura masa ,akae nooo hajja data ma barsa,Fita zanyi ."</p><p><br /></p><p>Baka Isa ba !!</p><p><br /></p><p>Katsaya kayi break fast ,mna badan yaso ba ya nufi dinning ,ya zauna kusa da Mimi anan Rak ta shiga ha'da masa ,ba'kin coffee tare da aza masa wainar kwae akae ,Tura masa tayi agabansa ."</p><p><br /></p><p>A hnkali ya dauki cup coffee din ,gamida cemata thank for d care!</p><p><br /></p><p>"Murmushin tayi suna ha'da ido da Mimi ta ka'she mata ido saurin dauke kanta ,tayi ta wutsiyar ido take ka'llonsa,</p><p>Komae na'sa mae kyau ne,</p><p>Yana cikin break fast din ne wyarsa da'ke ajiye a gefe ta shiga ka'ra best friend yagani ,da sauri ya da'ga kiran ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hello sageer kana ina ??"</p><p><br /></p><p>OK ,gani nan zuwa </p><p>Zamuje muyi booking flight ,yau Queen bata da lpy serious ,nake fa'damaka ok. Sae na ka'arso.</p><p><br /></p><p>Katse kiran yyi hnkalin Rak !</p><p>Bakarmin tashi yyi ba ,A hanzarce ta mike tabar gurin ,da ido Mimi tabita kafin tamaida kallonta kan yayan na'ta wandda ya'ke sipping ba'kin coffee a hnkali." Shaye da to'ka take fa'din Yah Abdul da gaske gobe zamubar Nigeria?? Bae kalleta ba,yake fa'din da gaske mna Angel ya kamata kije kiyi shopping kayan ,da zaki bukata a yau." Hop akwae isassun kudi a account naki?" Idan bbu kisanar min ya fa'da yna kallonta."</p><p><br /></p><p>Cikin fushi ta dire ,cup tea din hnnunta ."</p><p>Ni gaskiyya yaya kabarni na ka'ra sati biyu kawae kayi tafianka."</p><p><br /></p><p>Kinsan bana mgana biyu,ae ya fa'da gamida mikewa ,tsaye kai tsaye main fa'lo na granny ya nufa ,acan ya tarar da Rak tana kuka yyinda Aunty salma kefamar rarrashinta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Fafur takiyin shuru ,tsawa taji an da'kama !</p><p>Ki rufemana baki da wannan kukan ,na'ki ko kitashi ki fita tsit ,tayi gamida kwan'tar da kanta ajikin Aunty salma ,</p><p>Tsaki yaja wlhi kuke sangarta yaran nan shiyasa sukeyin ya'rda suka ga dama."</p><p><br /></p><p>"Ya isheka hka!!</p><p>Aunty salma,tayi mganar cikin kunar rae ,da ba'kin cikin ka zataji koda rashin adalcinka.?" Xae yi mgana Hajja ,ta da'ga masa hnnu alamr yyi shuru baece komae ba ya juya ya fita rae a ba'ce ." </p><p><br /></p><p>Cikin kuka Rukaiyya ke fa'din ,basan menayiwa yah Abdul ba yabi ya tsaneni baya sona baya kau'nata aunty salma ka'lleni da kyau kigani meye aibuna meye ajikina ,da yah Abdul baya sona?"ta fa'da tana zubar hawaye ,share hawayen ki tsabar munafurci ne kurum ,da yyi ma'sa yawa ."baega abun so ba sae waccen ba'kar macce........."xanyi mganin sane,kibarni dashi ,kukan ta tacigaba dayi ,Aunty salma na famar bata ba'ki Hajja batareda tace uffan ba."tacigaba da sabgoginta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kusan ka'rfe biyar na ya'mma Sageer na tare da AJ. Kiran Mimi ya shigo a wyarsa,</p><p>Ya da'ga wyar gamida yin sallama.’'</p><p>Bata amsa sallamr ba kae tsaye ta'ke fa'din kana ina??"</p><p>Sae da ya ka'lli AJ ,yaga hnklinsa baya akan sa sa'nann yace na fita unguwa.'' Wannan wace irin tambaya ce? Haushi ya kamata ,bana da ikon na tambayeka ,kenan??" Sassauta murya yyi ba hka nake nufi ba,sweetheart fa'damin meya faru??"</p><p><br /></p><p>"Cikin rawar murya ta'ke fa'din ina son ganin Kane,dga nan zamu fita shopping ,ya'rda yaji muryarta yasan bbu lpia."</p><p><br /></p><p>OK.tom."</p><p>Bayan magrib yyi maki?"</p><p>Idan son ,samune ka'zo kafin lkcn ok tom.'' Sae naxo da hka ya katse kiran,</p><p>Ka'llonsa ya maida kan AJ."</p><p><br /></p><p>da alamr ya'r rigimar ta'ka bata sauko ba,kwa'fa yyi kar ta sako din ,iskancin Angel ya isheni,</p><p>Wasu sababbin behaviours ,ta tsiro dasu Wanda ada can bata dasu,</p><p>Daita da Rak!</p><p>Neman sukeyi su rikitani ,ka'ra na dauketa a ka'sar ,kafin mudawo naga ya'rda zaman mu za'yaa kasance."</p><p>Sageer ina tsoron ,ranar da Asma'u xata San Na auri Rak! Ba." Ina fargabar ranar.</p><p><br /></p><p>Komae xae fa'ru Asma'u baxata San matsayin Rak a gurina ba.! Sae ta haihu tukuna no matter wat! Xanyi ko'kari na da'tse duk wata hanya ,da xata ha'damu ,Ajiar zuciya sageer ya sauke batareda ya'ce uffan ba." Shikansa yna tausayin abokin nasa."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mimi kinsan AJ.idan ya'ce yes bbu Wanda ya Isa ya canja sa kawae kiyi hkuri kibisa ,tunda hutun Ku ya ka're,ban San mexaki xauna kiyi ba." Plsss ka'rki da'gama kanki hnkali !! xatayi mgana yyi saurin daura yatsansa a ba'kinta ,Hawaye ne suka Shiga ambaliya a fuskarta,</p><p>Muje na rakaki kiyi shopping,</p><p>Da kansa ya bude mata gaban mota ta xauna a da'yan side yyinda ya Shiga ba'ngaren driver.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> " yana rike da cup tea a hnnunsa, sae kallonta ya'keyi ta juya masa baya ,taki koda ka'llonsa baran tana ,tayi masa mgana yyi na'ci har yagaji Rashin mganar nan na'ta na Neman zautar dashi, da'ga wya yyi ya'kira Dr.Zahra kwa'ntar masa da hnkali tayi yyinda ,ta'ke fa'din ya kyaleta ,rigimar tace kurum irin ta masu ciki." Yna aje wyar granny ta shigo ta xauna gaf dashi,gamida da'fa ka'fadar sa.</p><p><br /></p><p>Kayi hkuri kaje ka kwa'nta kaga gobe flight din 12:00pm.xakubi ya kamata kaje ka kwa'nta kawo na ba'ta a sanyayye ya mika mata cup coffee ,murya a sarke ya'ke fa'din plss granny ki tabbatar da tasha bbu komae acikinta tun da ta tashi,Yyi mganar cike da damuwa."</p><p>Insha allahu ka'rka damu kaje kaji da Rukaiyya Dan itama sae da tasha allura bayan ,fitarka da'zu zazxabi ya rufeta ."A hnkali ya russuna ya subbaci goshin granny tnx yhu my love nagode ,da kulawar ki mu kwana lpy." Cike da tausayinsa ,tabisa da ka'llo har yafice daga da'kin."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Amsa ga tea ki kisha kinji takwarata,</p><p>Cikin ture ba'ki take fa'din Idan Shiya ha'dasa ,baxan shaba Granny ki ha'damin wani,kurum." Murmushi granny tayi bbu matsala indae xakisha ,dire cup din granny tayi a ka'sa gamida jawo Flak's ,ta Shiga ha'da mata wani ................yyinda Queen ta jingina bayanta da filo gamida lumshe,idonta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_TEAM DRAMA QUEEN_*.👄</p><p>WATA RANA.</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>100.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Acan tsakiyyar gado ya hngota dunkule ,Cikin blanket.dan tsaki yaja a hnkali yyi tattaki zuwa gaban gadonta." A hnkali yake kiran ,sunan ta tayi masa banza."hnnunsa ya sa'ka gamida fincike ba'rgon da ka'rfi Ihun kuka ta sa'ka ,masa da sauri ya sa'ka hnnunsa ya toshe... Mata ba'ki ke kiyi shuru nine,</p><p>Rinannun idonta ta da'go ,</p><p>Tana ka'llonsa suna ha'da ido tayi saurin kwantar da kanta ajikinsa." Jikinta zafi sosae ko'karin da'gata ya'keyi dga ,jikinta sae ta rikesa gagam."ta hnasa koda dogon motsi mmki tsoro ,suka rufesa lkci da'ya wani ban'gare na zuciyarsa ke fa'damasa ka kyaleta kurum hka AJ." bata da lpya ka tausaya mata.'koda na rana da'yane ,</p><p>A hnkali yake fa'din kinci abinci ne??"</p><p>girgiza masa kae tayi mezaki ci ??" Cikin muryarta ta masu zazzabi take fa'din bana iya cin komae ."kamar ya bakya cin komae baxae yuyuba,kixauna a hka cikin ki bbu komae da'gani naje na ha'do maki Tea koda ka'dan ne ma'ke ka'fada tayi ."tsawa ya daka mata!!</p><p>Bbu shiri ta janye jikinsa ,cikin na'ta kallon ta yyi yaga tana share hawayen idonta."A hnkali ya sassauta murya gamida fa'din am sorry baxan sa'ke yimaki tsawa ba.'' Jirani naje na ha'do maki tea ,a hnkali ta da'ga kanta alamr to." da ido tabisa har yafice dga da'kin gyara kwanciyar ta tayi ,tana sauke numfashi kadan-kadan mintuna ,kalilan sae gashi dauke da cup tea.</p><p>"Tashi kisha gashi na ha'do maki ,bbu musu ta tashi xaune ,ga mmkinta sae taga yakae cup din a bakinta Cikin rawar jiki ta bude ba'kin idonta na kansa,</p><p>Amma shikam yakasa koda ka'llonta a hka tasha Rabin cup ta janye bakinta ,da ido yabita ka'fin ya'ce ya isheki ne ??"</p><p>A hnkali ta da'ga kae alamr ehhh maganinki fah?"</p><p>Nasha da'zu bayan sallar ishai ,dauko nagani side drower ta buda ta fito masa dasu ."ya amsa ya duba ya maida ,kiyi barci nima zanje na kwa'nta kinsan gobe akwae tafia a gaban mu ,oya kwan'ta na samaki bargo ,idonta cike da hawaye ta kwan'ta yaja mata bargon dae dae wuyanta,</p><p>Hnnunsa ya sa'ka ya kunna bed light ,gamida ka'she wutar da'kin a hnkali yake furtama ta gud nyt.!</p><p><br /></p><p>"Da sassarfa yafice dga da'kin gamida rufo mata ko'far.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Lkci da'ya ta saki wani marayan kuka gamida cire blanket ,din da ya rufeta dashi lkci da'ya tayi cilli dashi agefe kanta ta sa'ka cikin cinyoyinta ta Shiga rai -rai kuka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Washe gari.....</p><p>"Yana dawowa sallar Asubah." diret ban'garen ta ya nufa yna tura ko'far da'kin ya hangota tana ba'rci a ka'san carpet gabansa ya fa'di lkci da'ya zuciyarsa ke raya masa ko fa'dowa tayi dga kan gado?" da sassarfa ya Isa gareta ,gamida zube gwiwowinsa,</p><p>Ka'sa tashinta ya shigayi a hnkali wannan ka'ron baiji wani zafi ajikinta ba." Sabanin jia."A hnkali ya Shiga tashinta .</p><p><br /></p><p>Rukaiyya!</p><p>"Rukaiyya!</p><p>'Sanyayyen kamshin tutaren jikinsa ne,ya cika mata hanci sannu A hnkali ta soma bu'de ido,sanye ya'ke cikin Ash colour din jallabiya ,Kinyi sallah ne? Saurin girgiza kae tayi alamr ah a'hh ,to tashi kiyi sallah daga yau karna ka'ra ganin kin kwa'nta a ka'sa kina jina ko??" Da sauri ta da'ga kae alamr to ,ganin yyi ta'kasa mikewa ,tsaye hka yasa shi taimka mata ko'far toilet ya ra'kata ya juya yabr da'kin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Misalin ka'rfe goma da Rabi na sa'fe yna rike da hnnun Rak ! Xuwa side din granny Wanda har ,lkcn jikinta bbu ka'rfi sanye ya'ke cikin suite coat pich colour ,da farar shirt ajikinsa ,wandda kayan sunyi balain ka'rbarsa ,suna danno ka'nsu cikin fa'lon caraf idonsa,</p><p>Cikin na Queen na'sa Wadda ke zaune akan carpet ,</p><p>Tana shan koko da kosae ,</p><p>Idonta na kan hnnunsa da ya'rike Rak dashi ,ganin idonta wurin yyi saurin sakim hnnun Rak!</p><p>" nan ta'ke ta dire ko'fin kokon." Ta wani ha'de rae ,</p><p>Jiki sanyayye Rak ta ka'raso cikin fa'lon taje ta xauna gafda granny tana ma'ta ina kwana!!</p><p><br /></p><p>"Cike da kulawa hajja ,ta amsa gamida tambayr ta jikinta anan ,ta amsa da tasamu sauqi ." tsam Asmy ta mike tsaye hajja ta ka'lleta kin koshi ne??"</p><p><br /></p><p>Batareda ta ka'lli hajja ba tabata amsa da Ehhhh ,tasa kai ta nufi master bedroom din Hajja,da ido AJ. Yabita ka'rasowa yyi ya xauna a gaban hajja ,anan ya gaisheta ,ta amsa ."gamida fa'din har kashirya kenan?"uhmmmm...wannan fa da'ke famar fushi hka ,kotana nufin har ynxu bata sauko bane?"ya fa'da cikin fuskar tausayi ,uhm wae Asma'u?</p><p>Ehhh mna Hajja tun jia take famar azabtar dani ,narasa meye laifina batasan yana keji bane."</p><p><br /></p><p>Ji nake kamr cikin jikinta ya dawo min,daria hajja tayi ,yyinda Rak ! Ta nufi side din Mimi cikin xafin zuciya."</p><p><br /></p><p>"Ruwan Lipton kurum ya iya sha ,gamida pancake kwa'ra biyu dasu yyi break fast ,zuwa 11 ya nufi side na Mimi anan ya samesu suna break fast itada ,Rak!</p><p>Murya a da'she ta gaishesa bae amsa taba ." yake fa'din ba'ki da lpia ne?"</p><p>Meka gani yaya?"</p><p>Tayi masa tambayr gamida ka'llonsa,kawae naji muryarki wani irine."cikin muryar rauni ta'ke fa'din bbu komae kawae ynxu na tashi ba'rci ne yakamata ki shirya da wuri ,flight din 12 zamubi."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Amsa masa kurum ,tayi da to.......Rak ce ta ka'llesa a ha'damaka break fast din??" nagode nariga da nayi a wajen hajja,</p><p>Kema ya kamata kiyi break fast Mae kwa'ri sa'annan kisha drugs na'ki gya'da masa kae kurum tayi ......yna fita Mimi ta ka'lleta ,yanzu meye abunyi sis ??" Shinake tunani Mimi bansan wane hali zan Shiga ba ,idan kuka tafi bbu ki bbu yah Abdul, Abun xaeyi min yawane!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta fa'da gamida goge ya'r kwa'llar da ta taru ,idonta da'fa kafadar ta tayi karki damu my sweetheart muna ,tare ba'ga wyaba." Namaki alkawari sae Asma'u tabar gdan yah Abdul komae rintsi ,ki rubuta ki aje biyayya kuma kicigaba dayi masa,sae anan Rak! Ta dan saki jikinta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tana ko'karin sa'ka Riga da wando na Pakistan ,kalan dark pink ,ya turo ko'far da'kin da sallama ciki-ciki ta amsa sa,anan ta walwale towel na jikinta ,tashiga sa'ka kayanta batareda ta ka'ra koda ka'llonsa ba." Saurin dauke kansa,yyi Ganin ta a hka ,yna Neman da'gamasa hnkali ,</p><p>Wanda ya lura ita ko ajikinta.</p><p><br /></p><p>Bayan tagama ,sa kayan ta tsaf ,</p><p>Ta nemi farin hijab Mae manyan flowers ajiki ta sa'ka fuskarta fayau bbu powder amma tayi kyau,</p><p><br /></p><p>Ganin tun da'zu idonsa na kanta ,</p><p>Yasa haushi ya kamata, A fusace ta nufi hanyar fita saurin fisgota yyi ta fa'do ajikinsa." Ya matseta a bango sae kiciniyr fisge kanta takeyi amma ta ka'sa ,da shayayyun idonsa ya'ke ka'llonta ,hawaye ne sukayi nasarar gangarowa akan face nata."</p><p><br /></p><p>da hanzari ya sa'ka harshensa yna la'sar hawayen nata,</p><p>Tana jin ya'rda Jikinsa ke rawa ka'rfinta ta tattaro du'ka ta turasa ,A tsorace ya'ke binta da ka'llo sae yaga ta fa'she da kuka ........ni wlhi ka'rka ka'ra tabani ,kaje wajen waccen Rak ! din ae da'zu ina ganin Kawani rike hnnunta."tayi mganar cike da kishi hawaye kuma ,tamkar an bu'de fanfo."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Anan yagano laifin sa ,am sorry kinji nayi laifi baxan sakeba.'' A hnkali ya zaunar daita gefen bed ,yna share mata hawayen idonta." Kwan'tawa tayi akan ka fada'rsa ,promise me habiby bazaka ka'ra ta'bata ba.?,,</p><p><br /></p><p>"Cikin muryar ra'da ya'ke fa'din naji na dauka ,anan ya tallabo fuskarta ,Ya aza bakinsa gaf da na'ta cikin kankanin lkci ya ha'de bakinsu guri da'ya cikin wani irin sa'lo ya'ke tsutsar ba'kin ta anan itama ta fara responding, hnnunsa ya sa'ka cikin bra na'ta yana wasa da Boob's nata sun dauki minti goma sha biyr a hka,cike da kasala ya zare ba'kin sa cikin na'ta ."</p><p><br /></p><p>Nan ta'ke idonsa suka juye,</p><p>Kwantawa tayi akan cinyoyinsa,tana maida numfashi."</p><p>Agogon da'ke makale da hnnunsa yabi da ka'llo 11:39am."</p><p>Kin ba'tamin wnka Queen muje part din mu muyi wnka ."lkci na tafia ma'ke ka'fa tayi lallabata ya shigayi dakya'r ta ya'rda kai tsaye part dinsu suka nufa,wnka sukayi gamida yin al'wallah ,wani farin yadi ne ajikinsa wandda ana hango fa'rar vest din jikinsa ,</p><p>'' yyinda Queen ke cikin ba'kar Arabian Abaya." Ta ya'ne kanta da ba'kin gyale.''</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A hka suka nufi airport ,tareda body guard's nasa da hajja dakuma Rak! Wanda har yau Rak bata daina mmkin canjin kayan da AJ. Yyi ba."</p><p><br /></p><p>Sha biyu da minti bakwae jirginsu ya da'ga zuwa ka'sar Indian ,yyinda Rak! Kefamar kuka tamkar ranta xae fita kae tsaye ta umurci daya'n body guard ya sauketa ,a gdansu granny tayi lallashi har tagaji....</p><p><br /></p><p>*************</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>KA'SAR INDIA....</p><p>WATA RANA!</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>101.</p><p><br /></p><p>Dr.petel ne ya amshi case din Asma'u ,wandda kuma a gobe ne xa'ayi mata aeki ,dan hka sukayi masauqi a wani kayayaccen hotel ,da'ke cikin birnin Mumbai.''</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kwana xaune yyi yna sallar samun nasara aekin da za'ayiwa Queen na'sa Wanda mutuwane ,ko Rayuwa kusan ka'rfe takwas na safe sukayi shirin zuwa Asibiti da dukkan abunda xasu bu'kata, Acikin taxi sae surutu take yimasa ,taga ya canja ya rame Mae yasa mesa??"</p><p><br /></p><p>"Shuru yyi yna wasa da kyawawan ,Hnnunta A hnkali ta do'ra kanta akan shoulder's nasa Idonta cike da kwa'llah plss Habiby kayimin mgana mna.''</p><p><br /></p><p>Cikin rawar murya ya'ke fa'din bbu abunda ya fa'ru my Queen kiyi addu'a Kurum.kinji ??" A hnkali ta da'ga masa kae almr to."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>10:00@m.</p><p>Aka shiga da ita operation,</p><p>Bbu wani saurin ka'rfi ajikinsa ,ya nufi massalaci,</p><p><br /></p><p>Ka'rfe biyu dae-dae aka fito daita zuwa da'kin Hutu ,Wanda anyi aekin cikin na'sara jiran farfa'dowarta kurum sukeyi ....................tun fitowar su ,Dr.petel ke neman layin wyar AJ. baya shiga,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sae kusan ka'rfe biyr yafito dga massalaci ka'llo da'ya zakayi ma'sa kasan yna cikin fargaba." Rana da'ya kurum yyi balain fita hayacinsa,</p><p>Cikin faduwar ga'ba ya nufi office din Dr .petel yna ka'ranto Addua'r samun nasara a ba'kinsa."...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da fara'a Dr.petel ya taresa cikin ,harshen turanci ya'ke fa'din ina yashiga ne??"wayoyinsa ,duka a ka'she Amsa yabasa ,da yna masallaci!</p><p><br /></p><p>"Murmushi Mae kyau yyi gamida baiwa AJ.hnnunsa na da'ma cike da Rashin fahimta Ya mika masa hnnunsa,Anan ya'ke tayasa ,murnar Anyi aekin matarsa cikin nasara kamar ya'rda suke tsammani!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>......Anan ta'ke AJ. Ya zube agaban Dr.petel yna maeyiwa ubangiji sujada ,yafi minti biyu A hka ,da sauri ya Mike tsa'ye yyi hugging Dr .tamkr ka'ramin ya'ro yna ma'sa godia , Anan ta'ke yyi masa kya'utar miliyan biyu ." washe ba'ki Dr.yyi cike da farin ciki yna ka'ra godewa ,AJ."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kusan ka'rfe goma da ,Rabi na dare yna zaune gban gadonta yna,karanta mata ummul Qur'an yaji ta fa'ra motsi A hnkali tana fa'din Ruwa murya ka'sa -ka'sa aje Al'Quranin yayi a gefe Anan ya Ciro wya yana kiran lambr dr.petel cikin minti biyr sae gashi ya shigo da sauri ya nufeta. "...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" A hnkali AJ.ya koma gefe gamida yin folding hnnunsa A kirjinsa acikin ransa ,sae Hamdala ya'keyiwa *Sarkin Sarakai*!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dr.petel yafi minti goma Akanta ,</p><p>AJ.yyiwa alma akan ya ka'raso ." cike da murna ya ka'raso gabanta ,Zuba masa ido tayi tamkar yau ta fa'ra ganin sa,</p><p>Cikin muryar jin jiki ta'ke fa'din Mumin zan sha Ruwa!</p><p><br /></p><p>,Da sauri AJ ya kalli Dr.petel cikin ha'rshen turanci ,ya'ke fa'din Dr.xa'a iya bata Ruwa?"</p><p>Dan ka'ramin pridge Dr.petel yasa hnnu ya bu'da ,ya dauko Ruwa aciki amma mara su sanyi......"ya mikawa AJ."umurni ya masa da akan ya da'go kanta ya taimaka mata tashaaa!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>,Ruwan tea kawae tasha dr.petel yyi mata Allurar samun Hutu."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>1 week letter !</p><p><br /></p><p>Zaune ta'ke akan soofa ,tana cin Apple A hnkali ta ka'lli AJ.Wanda ke famar aeki A laptop na'sa waeni mumin wane irin ciwone wannan nayi hka??"gaba da'ya sae nakejin jikina wani iri plss fadamin mna."Atakaice ya labrta mata ,ya'rda Aliya ta tu'rota akan stairs ."dakuma lossing memory na'ta da tayi ,na Dan wani lokaci."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A hnkali ta mike tsaye ,ta Isa gaban mirror dressing tana ka'rewa kanta ka'llo Dan bingilin skirt ne ajikinta Red naa body hook ,Wanda bae gama rufe cinyoyinta ba."</p><p><br /></p><p>Sae kuma farar vest ,mae Hannun supergerti.'' Kanta da hular net Red ,</p><p><br /></p><p>Amma fa naga jikina ya canja mumin !</p><p><br /></p><p>"Ba hka fatata ta'ke ba,naga nayi wani fresh ,ni fa'rin nan yna bni mmki Anya akwae jini Ajikina??"</p><p><br /></p><p>''Tayi mganar cikin fuskar damuwa,ido ya zuba ma'ta ynason life style na'ta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ka'rasowa yyi gabanta ,yyi hugging back na'ta gamida sakalo kansa ,cikin ka'fadunta,</p><p>Ya do'ra hnnayensa ,duka biyu akan cikinta yna shafawa A hnkali cikin muryar ra'da yake fa'din yakamata ki bada da'ma ,Hka drama Queen Acika wurin nan ,A hnkali ta turo ba'ki kamanta Contract marriage mukayi ni ban ya'rdaba Allah!</p><p><br /></p><p>Hasalima ,ni tsoron haihuwa nakeyi ."A hnkali ya saketa cike da sanyin jiki lkci da'ya yaji hnkalinsa ,ya tashi hnnunsa ta do'ra kan Kumatunta ,nikam bna son waya'nnan kumatun mumin ,ji ya'rda sukayi wani iri tamakr an hura balamm -balaaamm! ." ni Dan Allah muje asibiti ,A dubani A hnkali ya cire hnnunsa akan kumatunta ,cikin wani irin ynayi ya shige toilet!!</p><p><br /></p><p>Da ido tabisa ,da ka'llo tana mmkin sauyawar yanayinsa."</p><p>WATA RANA !</p><p>N@ Asmy b Aliyu.</p><p>Haske Writer's Association..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_this page is dedicated to yhu Guy's ,Hibbat Abubakar khaleefa ,Jamila Jegawa little Ummy Aysha Mmn nasiba Aunty maijidda musa Khadija Niger(my Granny) My dear Tawakalltu and mami Kebbi state,thank for d Luv and Affection #one love._*👄</p><p><br /></p><p>102</p><p><br /></p><p>A hnkali ya ku'nna fanfon da'ke jikin sink ya ta'ra hnnunsa hka ya dinga zubama fuskarsa ,Ruwa baesan ya xaeyi da Queen ba muddin tagano ,tana da ciki ajikin ta ,yafi minti goma sha biyr a toilet,</p><p>Koda yafito tuni tayi barci a tsakkiyar carpet, A hnkali ya dauketa ya maeda ta kan bed ,gamida gyara mata kwanciyrta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dai-dai lkcn wyarsa ,da'ke ajiye akan mirror ta fa'ra ka'ra ." dauko wyar yyi yna duba Mae kiran Rak! Ce har ga Allah ya manta da matsayinta a wurinsa ,Rabon dasuyi wya tun ranr da suka sauka a ka'sar India."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Palo ya ko'ma sa'nnan yyi picking call dinta."Wanda cikin siririyr murya tayi ,sallama gamida gaishesa amsawa yyi anan take tambayr sa jikin Queen yabata amsa da fa'din tasamu lpia."</p><p>Shuru yabiyo baya na dan, lkci ita bata saba ba ."uwa uba shi,Yah yaushe zaku dawo ne??"itakanta batasan lkcn da tambayr yafito abakin taba.'' Zuwa gobe insha allahu,cike da murna ta'ke fa'din Allah ya nuna mna yabata amsa ,da ameen agaisheda Queen idan tatashi barci plsss ,OK xataji katse kiran tayi ."lkci da'ya yabi wyar nasa da ka'llo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>NIGERIA.</p><p>"Ka'rfe biyr da rabi na ,yamma jirginsu ya sauka a air port ,ga mmkin sa sae yaga Rak ! Tana tahowa da gudu ,tana cikin wani red&black le'ss dinki Riga da skirt Wanda suka xauna dai-dai jikinta ,</p><p>Sae Dan siririn mayafi red ,Wanda ta yane kanta dashi ,da gudu tanufo su cike da farin ciki tana zuwa tayiwa AJ.kyakkyawan runguma ,gabansa lkci da'ya ya buga jin tudun kirjinta,</p><p>Hka jikinta na fitar da wani irin ka'mshi na mussaman baisan lkcn ,da yasaka hnnu ya zagaye ku'gunta ba." Haushi ya kama Asma'u ,kallon su kurum ta'keyi suna ha'da ido yyi saurin sakin Rak ! A tsorace,</p><p>Bata bi takan su ba taja trolley dinsu tayi gaba."AJ. Ya ka'lli Rak ! A sanyaye yakamata ki fa'ra kiyayewa Rak! Kinga dae Queen batasan komae akan Auren muba." Komae xaki gani ki kauda kai kina jina?"</p><p>A hnkali ta da'ga kai idonta cike,da hawaye insha allahu zan fahimtar daita.keda kanki kika zo daukar mune?..da'ga masa kae tayi alamr ehhhh,oya muje mota yana gaba tana a bayansa,har suka isa wurin mota ajikin motar suka hango Queen tayi folding hannunta akan ki'rjinta ,tawani ba'ta rae."hnnunsa ya sa'ka ya dauki trolley bag dinsu ,ya bu'de booth ya sa'ka ya ka'rbi car key din A hnnun Rak!,ganin yaki ka'llonta a fusace ta bu'de back sit ta xauna cikin sanyin murya ya'ke fadin dawo a gaba mana husna." bana da Ra'ayi !</p><p>"Tayi mganar cikin fa'da sae dae Rak! ta xauna a gaba."</p><p>Zaman shuru suka xauna a mo'ta har suka Isa ,gda tariga ko'wa fita dga motar kai tsaye part na Hajja ta nu'fa cike da sanyin jiki suka bita."</p><p>Cike da farin ciki ta Rungume granny ,gani na dawo my Hajja missing yhu so badly ,nayi kewarki da yawa Hajja ,ta fa'da cike da jin ddi Cike da farin ciki ta'ke fa'din nima hka my darling child, ina mijin na'ki ??" Ka'rki tambayeni shi Hajja I don't even want to talk to him........meyasa takwarata, yafiye son ka'nsa da yawaa Hajja kibarni dashi kurum.kuma ni ki fa'damasa gobe ka'no xanje ,ta ka'rasa mganar shaye ,da toka gamida zama ,da'ya dga cikin soofa's din da'ke zagaye da fa'lon. da'ga kai Hajja tayi tana ka'llonsa murmushi dauke a fuskarsa ,yaje yabata swtttt hugging, da sauri granny ta turesa,tabisa da harara mekayiwa takwarata,da'ga dawowa??" dan murmushi yyi gamida Shafa sajansa,Hajja bar takwarar nan ta'ki kurum tafiye rigima muje kicika min cikina ,yinwa nakeji ,ddin abun,dae matan suna da yawa idan wani ya ba'ta maka sae wani ya faran ta maka ,ko ya kikace my honey wife ,ya fa'da gamida daura hnnunsa,akan shoulder din Hajja yana wani irin murmushi,suna ha'da ido da Asmy ya ka'she mata ido da'ya dauke kanta tayi cike da jin haushinsa."</p><p>Turasa Hajja tayi a gefe ta ka'lli asmy wadda ke fa'mar cika tana batsewa ,Asma'u mexaki ci ne??"Hajja xanci ,Towon semo da miyr ya'kuwa, da kuma orange juice,angama anan Hajja ta kwa'lawa Taa'llah kira sae gata tafito oya ta'llah jeki ki ha'dawa Asma'u towon semo miyar ya'kuwa."anan ta'llah ta zube agaban Queen tana mata sannu da zuwa ,amsa mata kurum tayi da to rae a ha'de, granny yinwa nakeji plsss ki taimakeni mana ,yyi mganar a shagwabance ,ka'je kayi serving kanka mana gashi can a dinning. "Kae tsaye dinning side ya nufa,anan yyi serving ka'nsa sae da ya cika tumbinsa ,acan master bedroom din granny ya sami Asmy Wanda fitowarta kenan dga wnka." Abun ya'r hkane A maimakon kice na'zo muyi ta're harara ta ba'lla masa Allah ya kiyayeni,kasan dae wacce xakaje kuyi wnka atare.!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Matsowa gun ta yyi gamida fisgota zuwa jikinsa,mekika ce? Ya fa'da yna ko'karin walwale towel din jikinta ,ware masa many an idonta tayi ,shaye da to'ka take fa'din wae yaushe mumin kazama hka??" Wlhi ko ka'dan sunan mumin baidace dakai ba.'' A da'zun nan ka Rumgumi Rak! Agabana ,ko kunya bakaji ,ynxu kuma ka'zo zaka walwalemin towel,da wanine da ynxu ka fa'ra yimasa wa'azi wlhi bazamu shiryaba."</p><p>Muddin kana ta'ba wnnnan Rak! din tayi mganar,cike da kishi gamida fisge kanta da'ga rikon da yyi mata ta xauna gefen bed."Hawaye suka silalo akan fuskarta,lkci da'ya hnkalin AJ.ya tashi xaunawa gefenta yyi gamida jawota ajikinsa plss kidaina kuka, na daina lamoo tayi akan kirjinsa,tana shakar kam'shin jikinsa Mae sata nishadi yawancin lokutta.''ka'ra gyara mata kwan'ciyarta yyi ajikinsa,yna A hnkali kuma ya shiga walwale towel ,din jikinta ga mmkin sa bata hanasa ba.kamar ya'rda take hanasa a yawancin lokutta.''hka yaga Boob's nata sunka'ra cika sun ka'ra girma nan ta'ke ya rikice akansu sae remoncing dinta ya'keyi ta koina tana tayasa,itakanta mmkin kanta takeyi ya'rda take biye masa."</p><p>Wannan ka'ron abuka'ce ya'ke amma yasan halin Queen na'sa ynzu sae tarikice ma'sa ga mmkin sa sae yaga tana enjoying na'sa gaba da'ya tafita hayacinta sae tsotsar lips dinsa takeyi tamkar tasamu swt." Hka tana fitar da numfashi sama -sama da almr moment din yna mata ddi."A hnkali ta turo ko'far room din idonta ne ya hango mata abunda keneman tarwatsa mata zuciya ,A hnkali tashiga ja da ba'ya hawaye na mugun zuba a fuskanta."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Next page na'kane my best friend Ibrahim Al'mustapha(bab)" nasan kafi kowa kaunar nvl din *Wata Rana!*👌🏻</p><p>WATA RANA![posted on 14 . October ,2017 Story and Writing By~ B Aliyu.Last Episode.] Saturday#</p><p><br /></p><p>❤❣❤</p><p>*_Asmy b Aliyu novel's_*.</p><p>*_Dandalin Asmy b Aliyu_*!🤙🏽</p><p>*_B @Liyu Fan's club_*!!</p><p>Thank for d love and the support written! #One love.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Last chappy goes to yhu my best friend Ibrahim Almustpha(bab)my love for yhu is like Tear's from d sky thank for everything yhu are always in my heart ,Allah yabr zumunci_"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>103.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta're suka fito dga wnka kowane daure ,da towel a kugunsa, bayansa ta da'ne tana yimasa ihu akunne ,oh my world!! Mr.AJ. ka'rki batamin wnka na pls kinga na dauro ,Al'wallah ga kiran sallar magrib can anayi."lafewa tayi a bayansa,</p><p>Cike da shagwaba ta'ke fa'din uhm hmmmm! Ina son turaren nan na jikinka." Ka'ki kasaya min ,ta fa'da gamida ka're lafewa a bayansa tawani lumshe ido dan murmushi ,yyi idan ya biyewa husna ,sae ya rasa jam'in magrib rigimarta ,baya ka'rewa yaga alama."</p><p>Oya sauko kiji wani Abu ,na'ki wayon ta fa'da gamida ,ma'ke ka'fada sassauta murya ,yyi ba wayo bane Allah ,</p><p>A hnkali ta sauka dga kan bayansa .ta wani ba'ta rae to zauna mana anan ta xauna tana turo masa baki,</p><p>Mayukkan sa ya dauko ya shiga Shafa mata,sae da yagama ta tayasa ya Shafa na'sa kai tsaye closet ya nufa anan ya fiddo da milk din Jallabiyya,</p><p>Ya sa'ka itakuma ya fidda mata riga da Wando na Pakistan. "Da hijab na sallah shiya taimaka mata ,ta sa'ka kinji ana sallar magrib kiyi sallah nima massalaci na nufa ya nufi bakin ko'fa sa'annan ya juyo yna ka'llon fuskarta bbu Allah ya kiyaye ?? ka'ra turo masa ba'ki tayi murmushi yyi ciki-ciki ta'ke fa'din Allah ya kiyaye amsawa ,yyi da amin."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ni kayi Sauri ka dawo pepper soups xanci angama my princess anan yasa kae yafice kicibis ,yyi da mutum a center Palo ,kirjinsa yaji yna halbawa jin shesshekar ,kukan Rak ! A hnkali ,</p><p>Tana kwa'nce ne da'ya dga cikin soofa's din da'ke zagaye da fa'lon zubewa yyi agabanta ,yna kiran sunan ta a hnkali banza tayi masa kiyi hkuri nasan ni Mae laifine kiyafemin zanyi ko'kari na gyara komae a WATA RANA!!</p><p>Cikin muryar kuka ta'ke fa'din ni nagaji da jin wannan,Wata ranar a bakin ka abakin kowa ma,</p><p>Ni na hkura da soyayyar dama nika dae keson ka."ka sauwakemin na kama gabana."ta ka'rasa mganar gamida ka'ra fashewa da kuka Mae sosa rae yarasa ,yarda xaeyi daita ."OK naji kiyi hkuri ki tashi kishiga da'ki kinga ana kiran sallah idan na shigo da dare xamuyi mgana ,daga yau ka'r na ka'ra jin kin furta ,na sallameki ,ni dake Abadan dai,man ne, bakya so ."A WATA RANA kucika min gida da ya'ya keda Asma'u!! Tana ka'llonsa hawaye suka silalo akan fuskarta,dan yatsansa ya sa'ka ya share hawayen ,cikin rawar murya gamida sunkuyar dakanta a ka'sa ta'ke fa'din inaso mna ,yawwa ko ke'fa oya jeki a da'ki. Yna nan tsaye har ta shige part nata, doguwar ajiar zuciya ya sa'ki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A wani restaurant ya nufa ,ya siyi pepper soups ,da kuma pepper chicken sa'annan ya biya wani super maket, ya seyi foreign milk,sannan ya nufi gida Around 9 baiji motsin ko'wa a falo ba kai tsaye side din Rak ya nufa ya sameta da ya'r bingilar rigar ba'rci ajikinta .tana chart,a wyarta sallamersa ce ta ka'tseta Ta amsa taxo ta ka'rbi ledojin hnnunsa gamida dan ,russuwa ya'rda yna hango dukiar fulaninta ,ta lura bbu abunda yafi daukar hnkalin yayan nata ajikinta irin Boob's na'ta wani malalacin murmushi ,ta saki ganin hnkalinsa gaba da'ya yana wurin mur'ya ka'sa -ka'sa ta'ke fa'din kici abinci nixan je nayi wnka ,da hka ya juya ya fice daga da'kin."</p><p>"Kwance ya sameta a tsakiyar bed ,na'sa ta kure AC.laptop na'sa na gefenta da alamr amfani tayi dashi." A hnkali ya dire ledar akan center table ya nufi inda ,ta'ke wurin ya janye laptop din Pics dinsu ya bayyana shida Rak!</p><p>Na ranar dener,zuciyarsa yaji tana Neman tsinkewa."saurin rufe laptop din yyi yamaidata wurin zamanta.</p><p>Cikin bar'ci taji ana hura mata iska A kunne,</p><p>"Ka'ra matse filo tayi akan kirjinta,duk ta za'ta mafarki ta'keyi yatsun ka'farta ya cigaba daja cikin wani irin sa'lo a tsorace ta bu'de idonta ,ganin AJ.agabanta yasa tasha to'ka ,sae ynxu ??</p><p>Ta fa'da gamida tu'ro ba'ki Ehem.mmmmm ,na'je nemar maki pepper soups ne,toina ya'ke yinwa nakeji tun da'zu gayanan ,tashi kisamo plate a kiching ,tsam ta mike ta nufi kiching ,ganin wulgawar mutum ,ya'sa tafasa ihu saega AJ.ya fito a guje a tsorace Rak! Ke fa'din kenice fah!</p><p>" da mmki Asmy tabita da ka'llo ganin kayan da'ke jikinta sunyi balain daure ,mata kae ka'llonta ta mayar kan AJ.tana masa ka'llon tuhuma,sae yyi saurin dauke kan'sa juyawa yyi yabar gurin Mae makon ,taje ta dauko plate ,sae ta nufi side din na'ta batareda ta koma bangaren AJ ba."A hnkali Rak! Ta ta'be baki gamida da'ga kafada.</p><p>Ta dauki juice a fridge dakuma glass cup tayi gaba abunta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kwance ya sameta a main pal tana kuka,yna kai hnnunsa jikinta ,tayi saurin dakatar dashi ka'rka ta'bani ,wlhi ka'rkaxo kusa dani ban San hka kakeba ,mumin da ban sa'ki jikina har hkaba." Ashe imanin na'ka da Addinin na'ka a fa'tar baki kadai ya tsaya bae kae a zuciyaba."Hawaye suka silalo akan fuskarta ,wlhi bazan iya da wannan mugun halin na'ku na ma'za ba!</p><p>da'zu a laptop naka,naga pics na'ka kai daita,abun na munafurcine ,kenan wlhi bazan iyaba yanzu sabida tsabar rainin hnkali ka daukota ka kawo cikin gidana!ban ma sanda zamanta ba!</p><p>Zaiyi mgana ,tayi saurin dakatar dashi bana bukatar jin komae a ba'kinka mumin plss da gudu tanufi da'ki tana kuka gamida rufo ko'far zaune yyi gamida da'fe kansa,</p><p>Yana maimaita ka'mar</p><p>Innalillahi wainnah ilaihir raji'un." Yafi minti biyr a hka,sae da yaji zuciayrsa tayi sanyi yaje yna buga mata ko'fa yana kiran sunan ta yana magiya banza,tayi masa dama ya dameta da kira sae ta koma a toilet ta cigaba da kukanta,</p><p>Anan ta dinga tuno wasu abubuwa na shafewar,tunaninta Abu da'ya kwa'kwalwarta ta ka'sa fahimta auren AJ.da cikin jikinta."</p><p><br /></p><p>Ya'fi minti talatin yna buga ,mata ko'fa jiki sanyaye ya ko'ma side na'sa hka kowa ya kwana cikin ku'nci.yna dawowa sallar asuba ba'ngarenta ya nu'fa Sae ya tarar da ko'far da'kin nata a bu'de doguwar ajiar zuciya ya sa'ki, ga mmkinsa baiji motsinta ba."har toilet ya duba batanan ,nan hnkalinsa ya ka'ra tashi hango farar takardar yyi an daura akan pilo jiki na rasa ya warware ,takardar.</p><p><br /></p><p>_"kar kayi wahalar nemana Mr.Abdul jabbar sameer meera ,dan ni tuni na kama hnyar zuwa kano idan katashi tahowa sae kazomin da takardar sakina ,karka manta da'ma tun can baya bbu soyayya a tsakanin mu contract marriage ne?zaka iya tuna hka,bazaka burgeniba har sae ka Auri Rak !anan zan tabbatar da kudin *DANGIN JUNA NE! Na barka lpia_!!.</p><p>Dga Asmau Omar omra."</p><p>Duk da sanyin Ac.da'ke ratsa da'kin bai hanasa gumi ba gaba da'ya ya gigice yafita hnkalinsa ,da takardar yafita da hnnunsa ta'mkar wani zautacce hka,ya nufi bakin get yna kwa'lawa securities na'sa kira .ilya's ne yyi saurin ta'rarsa,</p><p>Bakaga fitar Queen ba?"</p><p>Am sorry oga munyi ko'karin mutsayar daita taki ta sauraremu ,hka munta Neman Layinka baya............saukar ma'ri yaji akan cheeks nasa, da sauri ilyas ya da'fe kuncinsa,</p><p>Sae yau na tabbatar da Ku sakarkarune hka bakwa iyayin komae AJ.ya ka'ra sa zancen cikin zafin zuciya."dame tafita da farar marsadez Benz na'ka ."</p><p>AJ baikara kulasa ba ya nufi side din Hajja."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kwance yayi ajikin Hajja ,yana zubar hawaye tamkar wani karamin ya'ro Hajja dakanta ta'ke driving fa?,bata tunanin cikin jikinta ina tsoro ina tsoron wani Abu yasameta.</p><p>Kitai makeni hajja,A hnkali hajja take shafar sumar kansa tana karanta ma'sa Addu'oi."</p><p><br /></p><p>"Kusan ka'rfe goma ,da Rabi a shigo garin na ka'no agalabaici ,Allah kawae ya kaita gda.'' Wanda tana kunno,hancin motar ta ta hango Hameed omra ,dakuma Abbanta.''</p><p>Dakyar ta ba'lle ma'rfin motar hka ta fara ganin dishi-dishi Hameed yyi saurin tahowa aguje ya tarota hka ta tafi luuuuuuuuuuuu.......taxube ajikinsa sumammiyya."</p><p>Mama da Aunty ne A fall sae ga Hameed ya sHugo,dauke da Asmy cikin wani irin ha'li lkci da'ya suka mike a tsaye a tsorace cikin ha'da baki suke fa'din meya sameta ??</p><p>"A lokacin bayada courage din amsa masu ,tambayrsu sae da yayiwa Asma'un masauki ,a master bedroom din mama ,anan ya dauko ruwa a fridge ya shiga Shafa mata." Mama da Aunty cirko-cirko sukayi suna ka'llon ikon Allah,,numfashinta ne ya fa'ra fita ,sama -dama kafin tasamu ya dawo normal ,anan hameed ya kalli mama idan akwae kaya'n aiki a gda a sa'ka mata drip tana bukatar bed rest."goma sha biyar da faruwar hka mama ta sa'ka mata drip ,hka yah hameed ya ha'da yyi mata tasamu ba'rci .."Jirgin ka'rfe goma na sa'fe sukabi zuwa kano shida hajja,dakuma Rak ,Abbane ya shigo sae famar fa'da ya'keyi akan baisan yaushe Asma'u xata daina wannan rashin hnkalin nata ba."anan mama ke tambayarsa meya faru??"shine ya'keyi mata bayanin ynxu suka gama wya da hajja,basu San da tahowar taba ,ga mijinta duk yabi ya da'ya hnkalin sa salati mama tayi gamida fa'din Allah ya kyauta kurum."dai-dai lokacin sukaji sallamr Aunty shema ,janye da wata kyakkyawar baby ,mai kimanin Wata go'ma sha biyu da sauri ta sa'ki hnnun uwar ta nufi Abba ,Abba ya da'gata sama."yna fa'din Hanan kinyi kiba da yawa,sae sokike na daukeki,anan Aunty shema ke gaisheda iyayenta,cike da kulawa suka amsa .</p><p>"2:00pm. Su AJ.suna gdan Aunty salma,Wanda hajja ta tsara hkan dakyar AJ.ya yarda hnkalin sa,duka yana kan Queen nasa." Zuwa ka'rfe 3 na rana suka nufi gdan su Asma'u hajja Aunty salma,da kuma Rak sae AJ.da'ke driving ."</p><p>Yah Anas ne yamasu Jagora,zuwa fa'lon Abba ,</p><p>Lkcin RANA tsakkkiyar ga'don mama tana shan damammiyar fu'ra da nono,</p><p>Ya'r Aunty shema na gefe tana barci mama ce ta shigo da'kin dauke da sa'llama a ba'kinta na amsa ,ina kallonta ta kalleni ,tana fa'din kizo ga mijinki nan sun iso."shaye da to'ka na ka'lli mama ina fa'din meya zoyi kuma??"mama tàbani amsa ,da fa'din ae sae kije ki tambayesa mana. " marar kunya ,kitafi tun ka'fin yayan Ku ya shigo yasameki kin dai San halinsa,</p><p>Ture kwa'non furar tayi agefe ,gamida ha'de rae Aunty shema ce ta shigo ,tana fa'din waini kam Anya . *Ma'u* bbu ajiar AJ .Ajikinki a tsorace ,nake ka'llon Aunty shema ,gamida zaro ido anan ta tuna tace idan ta'zo kano zata fa'dawa mama ta dubata tana jin sauyi ajikita"..........nan ta ka'lli mama gamida saukowa dga kan gado,tace mama dan Allah kidubani na ra'sa meke faruwa dani ina jin canji ajikina,kije kigama da mijinki tukuna."zuwa anjima zan dubaki.,hijab ta nema ta sa'ka dan tanajin yah Anas na kwa'lamata kira,</p><p>da sauri tabar da'kin na mama har tana ha'rde hanya."</p><p>Mama da aunty shema suka Bini da ido,Aunty shema ta maida ka'llonta kan mama ,tana fa'din wlhi mama Asma'u cikine daita .mama tanisa da fa'din munyi mganar da'zu da Abdul Hameed."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ganin mutanen da'ke zaune a fa'lon ya'sa tasha jinin jikinta,dan duka yayunta na a fa'lon suna ha'da ido da yah Anas ya kuwa ba'llo mata harara ............saurin dauke kanta tayi,A hnkali taje ta zauna kusa ga granny tana yimata sannu da zuwa." Tun shigowarta ,idonsa na kanta ,Anan ya Anas ya bu'de taron da addu'a ka'fin Abba ya fa'ra da fa'din dalilin Ta'ron ,Anan Abba ya fuskanci ya'rtasa yana mata bayanin abunda ,ya faru cikin hikima tun daga shafewar tunanin ta,har zuwa Auren AJ.da Rukaiyya ,</p><p>Anan kuma ya dawo yana Nasiha da ban ba'ki kukan ba'kin ciki ta fashe dashi."</p><p>An Riga ancuceta,an tona ,mata asiri wani irin ba'kin kishine ya lullube ma'ta zuciya lkci da'ya sae a yau ta ya'rda Iyayenta,</p><p>Basa sonta basa kaunarta!!</p><p>Bata ta'ba tunanin son AJ. Takeyi ba." Sae da taji sunan Rak ! A matsayin matarsa,Anan granny ta shiga lallashi kwan'tawa tayi ,ajikin hajja tashiga rera kuka mai tsayawa aran duk wani Mae saurare,kukanta ya'keji har cikin ransa Jin ya'keyi tamkr yajawota ajikinsa ya lallasheta, dama irin Wanann ranar yake gudu."</p><p>Da gudu ta fice, dga fa'lon tana ihun kuka ,tamakr ka'ramar yarinya bbu Wanda yyi ,yunkurin tunkarar ta."cike da mutunci da ka'rramawa Su Hajja su kayiwa,su mama sallama ."</p><p><br /></p><p>A fusace Abba ya tu'ro ko'far da'kin da ta'ke kwance,kodan cikin jikinki yaci ace kin shafawa kanki lpia ,bansan yaushe zaki canja ba!</p><p>Jin ciki ajikinta yasa tamike a zabure tana ka'llon Abban nata Tamkar wata zautattah."</p><p>Nashiga ukku Abba! Wane irin ciki kuma??"jiki sa'bule Abba yabar mata da'kin ,da gudu ta nufi hnyar fa'lo tana kwa'lawa Maman sukira na shiga ukku mama wae cikine dani?cike da jin haushinta mama ke fa'din ko abun kunya ne?</p><p>Hawaye masu zafin gaske ,suka sauko akan kuncinta ."A daddafe ta koma da'k gamida tsayawa agaban madubi ,hnnunta ta Daura akan cikinta ,Anan ta shiga tuno komae anan ta'kara tabbatar da zarginta ,tasha tamabayr mumin meayasa ta'ke jin canji ajikinta,bae ta'ba bata cikakkiyar amsaba."Hasalima gujewa tamabayarta ya'keyi mumin yariga yagama daita fa'dawa tayi akan gado tacigaba da kukanta tamkar ranta ,xae fita."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wani irin parking tayi a ko'far gdan shikuma AJ.a lokacin yake shirin Fita da mo'ta hngota bugun ,zuciyarsa ya ka'ru kashe mo'tar yyi yafito ,ya tunkareta lkcin da ta'ke ko'karin danna kanta cikin fa'lon da alamr batama ga AJ. ba jin kawae tayi anjawo hnnunta ,A fusace ta juyo taga wanene Mae wannan. Ka'rfin halin."Ha'da ido sukayi dashi aekuwa a fusace ta tura sa da ka'rfi baya yyi xae fa'di yyi saurin dafa bango yna ka'llonta a tsorace wani mugun ka'llo tashiga jefa masa bae kulata ba ."Ya dauketa cak !</p><p>Zuwa boy's Quarters ba,ki ta bu'de xata fa'sa masa ihu yyi saurin tura ba'kin sa cikin na'ta harshensa ta cafka gamida gantsara masa cizon da ya'kusan fitar dashi A hnkalinsa bbu shiri yyi saurin direta a tsakiyyar da'kin gamida kama ba'kinsa."</p><p>bata kula da halin da ya'ke ciki ba ta cakumi ,wuyan Rigarsa ,gamida fiddo ma'sa da manyyan idanunta."</p><p>Ina son ka amsamin ,Tambayoyin da zanyi ma wlhi idan kayimin ka'rya nafiso akai gawata a gdan ka!!</p><p>"Tana jin ya'rda saetin kirjinsa,ke bugawa alama ce ta nuna ciwonsa na iya tashi acikin kan'kanin lkci bata damuba."</p><p>Shin da gaskene ina da ciki?"</p><p>Ka'llonta ya'ke hnkali a tashe ,tambayar ka'nsa ya'ke shin a ina taji wannan zance?"..........Shuru yyi mata ,karfinta ta sa du'ka tana jijjigasa ka amsa min mna!</p><p>bbu wani saurin bo'ye -bo'ye Tamkar Mae tsoron Ha'da ido daita ,ya'ke fa'din am sorry Husna kina da ciki kiyafemin na'san na ma'ki laifi hka na ka'rya alkawarin dake............Saukar ya tsunta biyar yaji akan kun'ncinsa ,takara cakumar wuyan rigarsa ,hawaye na zuba a idonta ta'ke fa'din how dare yhu talk to me like DAT?</p><p>Ehemm oya tell me ?,mekuma yyi saura ynxu mekakeso ? Gaba da'ya ta haukace ma'sa matseta yyi a bango ,yarike ta gagam tamkar zata shige cikinsa ,jikinsa koina rawa ya'keyi fuskarsa ya samu ya ha'da datata ,hawayensa na zuba a fuskarta cikin sanyi ya'ke fa'din meyasa bakida yafiya ne Asma'u ?"</p><p>Dan'kin ga ina tsananin sonki Sae kiyi ta wahalar dani fa'damin sona ne bakiyi ko kuma yaya??"</p><p>Bu'de baki tayi zatayi mgana yyi saurin Daura ya'tsansa a ba'kinta Ka'llonsa ta tsaya yyi bata ta'ba ganin kwa'yar idonsa ,hka ba lkci da'ya taji jikinta yyi sanyi." Itakanta idan tace batason mumin dinta ,tayi ka'rya Abu da'ya kemata ciwo wae tanada kishiya ,</p><p>Did yhu love me or not??"amsa da'ya nake buka'ta daga gareki yanxu ,</p><p>Yamata tambayar gamida tsareta ,da shanyayyun idanunsa,lkci da'ya ta turesa I'am not In Luv with yhu mumin sabida kae macucine babban Makaryaci!!</p><p>'Ki'rjinsa ne yaji ya'masa nauyi ,ya bu'de baki yyi mgana Sae ga Aman jini sare-sare ido tafiddo waje aguje tayo ka'nsa Cikin rawar jiki ta da'go kansa ta Daura a cinyoyinta."</p><p>Yna son yyi mgana tayi saurin Daura tafin hnnunta ,</p><p>A ba'kinsa plss ka'rkayi mgana ,</p><p>Na rokike ta fa'da gamida fa'she masa da kuka,</p><p>Wlhi ina sonka,ina sonka mumin!!</p><p>Soyayyarka ajinina ta'ke ,</p><p>Dan Allah ka'tashi ka'rka tafi kabarni na ma'ka alkawari baxan ka'ra dagama ka hnkali ba."</p><p>"Hnnunsa ta da'go taga ya koma hka idonsa a rufe,</p><p>Wata irin gigitattar ka'ra ta'saka anan ta zube ka'sa sumammiyya.!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>2 days letter.</p><p>" bae San inda kan'sa ya'keyi ba,Asmy tayi kuka har Hawaye sun daina zuba a idonta." Sae na zuci,</p><p>Aunty salma,da Rak kusan tsinemata suka dingayi ,yyinda Wurin Granny kurum takejin sassauci." ,ga Abbanta yyi fushi daita."Hakama yaya Hameed dinta.</p><p>Rahama ,Kurum kedan debe mata kewà.''</p><p>A rana ta biyar ne, Mimi ta diro Nigeria ta sauka a kano."</p><p>Hnkalinta ya tashi ,kuka ta fa'she dashi,bata ta'ba tunanin idan bbu ,Yayan ta ba,baxata iya Rayuwa ba."tayi kuka Har taji bbu ddi.</p><p><br /></p><p>Hnnun granny ta Rike gagam tana wani irin, kuka Mae tsuma rae,Anan ta'ke baiwa granny Lbrn abunda tayiwa Asma'u itada Rukaiyya,</p><p>Salati tashi gayi yyinda Aunty salma,ta shiga jimami,</p><p>Dan ko a mafarki basu ta'ba tunanin su Mimi zasu iya aekata hkaba.!!</p><p><br /></p><p> Tabbas Abdul Jabbar Hkurinka yyi rana ,ga irin Ranar da nakejira kenan ta'zo Abunda nake jiye ma'ki kenan Salma keda Sadiya ,</p><p>Irin wannan ranar nake jiye ma'ku dama nasan A WATA RANA!</p><p>Zakuyi nadamar Abunda kuka aekatawa Asma'u itada Abdul Jabbar kamar ya'rda Asirin ALIYA ya to'nu itada Jummai yanxu Ku fa'damin wagari ya waya??"</p><p>Kuka Mimi ta'keyi tamakr zata shide yyinda itama Rak keyin na'ta Aunty salma Sae tsine masu takeyi anan ta da'ga wya takira Aunty sadiya ,tana fa'damata abunda ya fa'ru Salati Aunty sadiya ta do'ka ,tana fa'din mun shiga ukku salma ,ya zamuyi da Alhakin yarinyar nan?"</p><p>Wlhi kuwa Aunty sadiya ,sharrin zuciyane,ina jin kunyar ha'da ido da yarinyar nan."</p><p>Baki kaini ba Aunty sadiya ko a safiyar yau Sae da namata zagii na bugawa,a jarida.Allah dai dae ya kyauta kurum."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>2 weeks latter !</p><p>Alhmdullhi ya samu sauqi ,har suna shirin komawa a Bauchi."Aunty ,salma tanemi gafarasa da Aunty sadiya anan yayafe masu."Tareda Addu'ar Allah ya tsare gaba."</p><p>Itama Asma'u tanemi gafarar iyayenta ,Wanda Sae samata Albarka sukeyi.</p><p>da haka suka ko'ma kano dukansu ,Wanda mgana wannan bae Ha'data da mumin dinta ba.''</p><p>Hka kurum ya dau fushi,daita........tun A ka'no Mimi da Rak suka nemi gafarar sa ,anan yamasu gar'gadi akan kar hakan tasake faruwa,</p><p>Ynxu Wata kulawa ta mussaman ya'ke baiwa Rak!</p><p>Mussaman idan ya lura Queen na a wajen ."</p><p>Wanda Rak, kokada'n batajin ddin Abunda ya'keyiwa Asma'u..................su duka suna zaune akan dinning da dare,suna dinner Cak !AJ. Ya da'ga Rak!.ya xaunar daita kan cinyarsa,gabanta ya fa'di a tsorace ta'ke ka'llonsa.</p><p>Murmushi mai kyau ya sa'ki karkice komae my Love naga kina cin Abinci kamar kina shan mgani."</p><p>Xan baki a ba'kine ,ta Wutsiyar ido,ya'ke ka'llon Queen ta sunkuyar da kanta a ka'sa kwa'llah ta ta'ru a idonta.''..kishine taji ya rufeta ,da gudu ta nufi hanyr stair's. AJ.da Rak !</p><p>Suka ka'lli juna hnnu yabata ,suka ta'fa ihu Rak tayi Yehhhhhh!Wlhi Yaya Tana sonka!</p><p>Da sauri ta sauka akan jikinsa,cike da murna ta'ke fa'din plss yaya Abdul ka'je kasameta !ynxun nan kuwa Rak! Mikewa yayi a tsaye ya subbaci gefen kuncin Rak!</p><p>Gamida fa'din nagode Kan'wata hnyr part dinta ya nufa yyinda Rak! Tashiga gyara dinning din."</p><p>Yna mur'da ko'far da'kin yajita a bu'de yana sawo kan'sa suka cika'ro tana jaye da Trolley bag nata,</p><p>Tare hnya yyi bata kulasa ba.</p><p>Ta zagaya ta gefensa xata wuce,</p><p>Ya fisgota ajikinsa,kokarin kwa'tar kanta takeyi ya matseta ajikinta sassauta murya yyi gamida fa'din ina zuwa hka Mrs.AJ. meera,</p><p>Plss karabu dani banason mgana dakae !</p><p>Tayi mganar gamida fa'shewa da kuka ,how can I leave yhu my Queen ?</p><p>Ya fa'da gamida sakalo kansa cikin wuyanta yana shinshina ,Sae wani lumshe ido yakeyi lkci da'ya ta fashe masa da kuka hka tana ko'karin kwa'tar kanta."A hnkali ya lalubi bakinta ,ya fa'ra yimata wani irin hot kisses Dan yasan ,shine kurum *Weakness point* ,,na'ta wani irin Mahaukaciyar soyayya ya shiga nuna mata ,a wannan Daren </p><p>"Wanda Hnnun Asmy baxae iya rubuta ta ba." Fatan Alkhairi Kurum Asma'u Abdul Jabbar.👌🏻</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>3 year's letter.!</p><p><br /></p><p>Mimi ce rike da hnnun Muhammad sameer ,suna isowa a fa'lon ya sa'ki hnnun Mimi ,ya nufi nannyn sa wadda ,ke zaune akan soofa ,tana sipping juice acikin cup glass ,Nanny zansha !</p><p>Muhammad wannan ,da sanyi je Gurin Aunty Mimi tabaka ,marar sanyi."</p><p><br /></p><p>Mimi xaunawa tayi akan soofa din da'ke ka'llon Queen,dai -dai lkcn Rak! Tafito daukeda plate na Dan wa'ke Wanda yaji mai da ya'ji da tsohon cikinta Wanda ,dakyar ta'ke tafia sabida tsufa."gefen Mimi ta zauna,</p><p>Ta ka'lli Asma'u Ah a'hh Aunty Queen yaushe kika shigo ne?"</p><p>Ina zakisan na shigo kina can kina kwa'dayi."</p><p><br /></p><p>Aunty Queen plss kibani shawara mana ,Mimi tayi mganar a shagwabance,</p><p>Oh Mimi kibarni na huta mana,</p><p>Ynxu nafa dawo dga skull,dake da Auntyn Muhammad ,kun sakoni a gaba."</p><p><br /></p><p>"Ràk! </p><p>Ta dauki dan wake da'ya takai a baki sa'annan ta ka'lli Mimi oya fa'di minene muna jinki kanwarmu??"</p><p>Dan ta'be baki Mimi tayi ,plss kuzama serious mna naga kunason kumaida xance na wasa."</p><p>Sa'geer ne keson a tsaida date na bikin mu."</p><p>Eyeeh su Mimi ankusa shiga lalle,cewar Rak!</p><p>Daria Asmy ta kya'lkyale dashi,so mekika cemasa.?</p><p>Ina xan San mexan fa'da masa Sae kin fa'damin sabida Cancancarki ! *UWAR DA'KI*!!</p><p>Murmushi Mae kyau Asmy ,ta saki mai kyau ,gamida fa'din Sae Abban Muhammad ,ya dawo zamuyi mganar.kafa'da Mimi ta da'ga gamida Dan ta'be baki duk ya'rda kika gani ,MY DRAMA QUEEN!! #</p><p>"Takarasa zancen cike da zolaya da sauri ,ta dauki Muhammad ,zuwa side na granny suna mata daria. Ka'sa-ka'sa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>TAMMAT BIHAMDILLAH!#</p><p>" Anan ni Asmy na Aje alkalamina.✍🏻</p><p><br /></p><p>Alhmdullhi!</p><p>For making my book successful .Yah Allah ina rokonka ,da tsalkakan sunayenka,kuskuren dake cikin wannan lbrn.Allah ya yafemin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>SADAUKARWA!</p><p>*_I dedicated this book to my Sistr in law Zainab Abdullahi (Aunty Zeey)thank yhu for your support I'll love yhu Always like yhu do me,Allah yabar zumunci._"😘</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Special thank to special people's ,Asmy na Alfahari daku hka tana ka'ra kaunarku cikin zuciyarta *HASKE MAGANIN DUHU*!!</p><p><br /></p><p>1.Ummy Aysha.</p><p>2.Khaleesat Haidar</p><p>3.Fatyma Zahra</p><p>4.Hàjja CE</p><p>5.Mmn Abdul Shakur.</p><p>6.Ayusher Muha'd</p><p>7.Asy Khaleel</p><p>8.Billy Galadanci</p><p>9.Fazy Fàtion.</p><p>10.Safiya Huguma</p><p>11.Nusy Love.</p><p>12.missXoxo</p><p>13.Kubrace</p><p>14 Mmn Khady.</p><p>15.Afra Bhai.</p><p>16 .Aysha D/Sabo</p><p>17.Limrat</p><p>18.lilmera cut.</p><p>19.Mrs.Hafsat</p><p>20.Dijerh Berver.</p><p>I love yhu All Allah yabar ,zumunci.👏🏻</p><p><br /></p><p><br /></p><p>KUNA RAINA.</p><p>1.Munay</p><p>2.Teema luff</p><p>3.Eshaa Tsafe.</p><p>4.Maryam Muktar.</p><p>5.Aysha Aliyu Garkuwa.</p><p>6.S.A Azeez.</p><p>7.Rufaida Omar.</p><p>And Zeey yaborh."</p><p>Thank for d love and care."</p><p><br /></p><p>LITTAFAN MARUBUCIYAR.....</p><p><br /></p><p>1.Alkawari</p><p>2.Noorul Hooda.</p><p>3.Nadawo -Gareki</p><p>4.Wata Tafia</p><p>5. Adalili na.</p><p>6.Nida sakeena</p><p>7.Dangin Juna</p><p>8.Wata Rana!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asmy b Aliyu."📝✍🏻.</p><p><br /></p><p>*HASKE WRITER'S ASSOCIATION.*🤙🏽</p><p>Copied By</p><p>YAYA HAYAT </p><p> (admin </p><p> Hayat hausa novels</p><p>Hausa novels and fashion</p><p>Cool novel, makeup and kitchen1⃣</p><p>Cool novel, makeup and kitchen2⃣</p><p> AND </p><p>Cool novel, makeup and kitchen3⃣) </p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-91204107392777661222022-02-12T05:27:00.001-08:002022-02-12T05:27:09.435-08:00ZURFIN CIKI Complete Sabbin Hausa Novel 2022<p> </p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEi_pRNMLTkmM8R-anpyaMHc8zrVkX5b1XgFZh32H5goPESU6munJJvUabc5muEa3RtsEZEGFa70MTrlReXGuswm6Io_-8UfmrxLx7MhanQrMlE-mTSMYmK-h24ieCK2-Azh61lRCRoekinnv4dUhC9SZ1Xg-93HsTBFvtzyh1LA5XUVTNi9FaMVxsfg=s1914" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="ZURFIN CIKI Complete Sabbin Hausa Novel 2022" border="0" data-original-height="1464" data-original-width="1914" height="245" src="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEi_pRNMLTkmM8R-anpyaMHc8zrVkX5b1XgFZh32H5goPESU6munJJvUabc5muEa3RtsEZEGFa70MTrlReXGuswm6Io_-8UfmrxLx7MhanQrMlE-mTSMYmK-h24ieCK2-Azh61lRCRoekinnv4dUhC9SZ1Xg-93HsTBFvtzyh1LA5XUVTNi9FaMVxsfg=w320-h245" title="ZURFIN CIKI Complete Sabbin Hausa Novel 2022" width="320" /></a></div><br /><p></p><p><br /></p><p>Home / ZURFIN CIKI novels www.gidannovels.blogspot.com/ ZURFIN CIKI book 1 part 1</p><p>ZURFIN CIKI book 1 part 1</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 02:16</p><p>UUmmi tana tafe tana yan wakokinta, tareda gudu</p><p>hade da tsalle. cinikin ummi ne gudu, sam bata</p><p>tafiya a hankali.daga can gefe ta hango wata</p><p>yarinya wadda bazata wuce sa'arta ba.</p><p>tace,"yauwa,ga firdausin data tsokane ni" ta nufi</p><p>wurinta ,tasha gabanta ta rike kugu. "fiddausi wa</p><p>kike tsokana? fiddausi tace "ban tsokane ki ba</p><p>fa".cikin tsoro tayi maganar .ummi ta shako mata</p><p>wuya. ina jin lokacin da kika ce ummi tsiga.ban</p><p>ce ba inji fiddausi .ummi ta hankada ta tare da</p><p>cewa "Allah yaso ki." nikan garin da fiddausin tayi<span></span></p><a name='more'></a><p></p><p>ya tarwatse a kasa tace "kin gani ko? wallahi sai</p><p>kin biyani"ta soma kuka,ummi ta sheka da</p><p>gudu,sai gida. tana ajiye man gyadan data siyo ta</p><p>nufi ba daki don fitsari ya matse ta .umma dake</p><p>zaune tana fadin. "da mutum!da mutum!!" saida</p><p>ummi ta bude . Ganin yaya Abba tayi,da gudu ta</p><p>juyo ta fada dakin umma,jiki na bari bayan tayi</p><p>bol da dakakken yajin da umma ta daka zata</p><p>soya mai don cin abincin rana. sai kuma ta tuna</p><p>cewa bata tsira ba,don Abba tsaf zai binciko ta.ta</p><p>fito da gudu ta nufi dakin tsohuwa. tsohuwar tana</p><p>sallar azahar.ummi ta tsallake ta ta kutsa kasan</p><p>gado.nan ma tayi ciki da furar da tsohuwar keson</p><p>sha da zarar ta idar da sallah. Alhaji babba tasa</p><p>ya aiko mata da furar daga kasuwa.don tasha da</p><p>rana. Abba ya fito wanka ranshi a bace.dakin</p><p>umma ya nufa yana fadin "ummi ke ummi zonan"</p><p>Ya samu Umma tana tattara yajin da Ummi ta</p><p>zubar, tana fada. Ya ce, "Umma ban san irin</p><p>dukan da zan wa Ummi ba yau. Ta ce,"Abba ka</p><p>mata dukan mutuwa, na gaji da halin Ummi.</p><p>Yarinya sai ka ce 'yar fata? Ka dubata ta tafi</p><p>dakin Tsohuwa, don ta san zata hana a dake ta."</p><p>Ya ce,"Allah sai dai Tsohuwa ta yi ta fadanta,</p><p>amma ba zan barta ba. Ya juya zai tafi, suka ji</p><p>muryar Tsohuwa tana fadin. Ba zan yi fada ba, ka</p><p>kashe ta ka ji mai sunan Malam, ba na son ka</p><p>barta da rai. Ta dubi Umma" ke kuma Suwaiba</p><p>dama kin san ba za ki daraja sunana ba ki ka sa</p><p>a ka sa miki don kiji dadin ci min fuska?" Umma</p><p>ta ce," Ba haka ba ne Tsohuwa, Ummi ba ta yo</p><p>halinki ba. Ita fa rashin hankali ne da ita. Yayanta</p><p>fa ke wanka ta zo ta leka shi, nan kuma tazo ta</p><p>zubar min da barkono. Abba ya ce, "Umma don</p><p>Allah kiyi shiru ki kyale Tsohuwar nan, ai ita ta</p><p>6ata Ummin, duk abn da yarinyar nan tayi sai ta</p><p>hana a yi mata fada. Uhm duk fadanki yau sai na</p><p>dake ta, ba sunan ki ba in ma kece,"Tsohuwa</p><p>tasa kuka gami da salati. "Yanzu mai sunan</p><p>Malam ni ka ke fadawa haka?" ya ce, "An fada</p><p>miki." Umma ta ce, "kai Abba zan sa6a maka</p><p>jeka." Ta juyo wurin Tsohuwa, Don Allah kiyi</p><p>hakuri............... Maman Fiddausi ce tayi sallama</p><p>tare da Fiddausin suka shigo. Ran Maman</p><p>Fiddausin a 6ace, ta tsaya rike da gari a</p><p>hannunta ta dubi Umma. Ta ce, Umman Abba</p><p>dubi abn da Umminki tayi min don Allah, yarinyar</p><p>nan tayo nika da kyar," tun safe sai yanzu na</p><p>samu, amma ta zubar min." Abba ya ce, Kinga</p><p>halinta ko?" Tsohuwa ta ce, "Wannan ba matar</p><p>Bala ba ce?" Maman Fiddausi ta ce, "Ni ce." Ta</p><p>ce," To kije kije ki nemi wanda ya zubar da</p><p>garinki, Ummi ko fita ba tayi ba. Umma ta ce, "</p><p>Ta fita Tsohuwa, na aike ta siyan mai." Tsohuwa</p><p>ta ce," Tsokanarta a ka yi to. Umma ta amshe</p><p>abin garin ta zuba musu, sannan ta ce, "Don</p><p>Allah Tine kiyi hkr." Abba ya nufi daki. Sai da ya</p><p>shirya tsaf, sannan ya dauki belt ya nufi cikin</p><p>gida, dakin Tsohuwa ya shiga kai-tsaye kasan</p><p>gado ya nufa. Ya jawo ta, ta soma kurma ihu.</p><p>Daya ya lafta mata amma ta dane shi tare da</p><p>cukwikuye belt din tana ihu. Tsohuwa ta iso tana</p><p>dukanshi a baya, fadi take "Za ka kasheta ne?</p><p>Jama"a kuyo dauki. Haushin hakan yasa shi</p><p>damko kanta ya shiga zuba mata kola, ya</p><p>sirmiyota ya shiga lafta da takalminshi, tunda ta</p><p>hana belt din. Sai da ya mata tas, sannan ya fita</p><p>ya bar su, Tsohuwa na kuka Ummi na kuka. , Sai</p><p>da komai ya natsa ta leka ta jawo furarta don</p><p>tasha, sai ta ganta a zube. Ta ce, A" a ke ki ka</p><p>zubar min da fura?" Ummi ta ce, To ba shi ne</p><p>janyo ni ba Yaa Abban. Tsohuwa ta ce, "Ai ko sai</p><p>ya siyo min furata. Ta mike ta wuce Umma tana</p><p>rabon abinci, ta nufi soro in da dakin Abba yake</p><p>(Zaure) Ya fito yana rufe kofa, ta ce "Au za ka</p><p>fita ba? To ka sawo min furata da ka zubar. Ko</p><p>kallonta bai yi ba ya rufe kofarshi ya wuce. Ta ce</p><p>mishi "Aikin bana, in ba siyo min ba ubanka ai ya</p><p>dawo ko min dare ya sito min. Abba ya ce, Ku ku</p><p>ka sani. Ra ce, kaima ka sani, dan jakar uba. Ta</p><p>dawo ciki tana mitar ya cika bakin rai. Umma ta</p><p>ce, "Ina Abban? Tsohuwa ta ce, "Ya tafi, in bai</p><p>sai min furata ba ranshi zai 6aci yau a gidannan.</p><p>Umma ta ce "Ni bai ma ci abinci ba ya fita, ke</p><p>Ummi zo ki kira min shi, yunwa fa yake ji.</p><p>Tsohuwa ta ce, "Ba za ta kira shi ba, ya dake ta</p><p>sannan ta kira shi? Tunda bai barta taci da dadin</p><p>rai ba, shi ma ba ya ci ba.,, Umma tayi shiry,sai</p><p>haushin Ummi da take ji kamar ta shake ta ta</p><p>mutu. Ummi tayi wanka ta zura kayan Mkrnt,</p><p>tana saka sandal Umma ta ce, "Ina Ummi? Zo</p><p>nan." Ummi ta tafi tana cewa a ranta. "ALLAH</p><p>YASA DAKIN YAYA ABBA ZA TA AIKE NI, SAI NA</p><p>RAMA DUKAN DA YA YI MIN JIYA, DON YANZUN</p><p>DUK ME YA MIN SAI NA RAMA.........." Umma ta</p><p>katse mata tunani da cewa,"dauki shayin Abba ki</p><p>kai masa kada yayi latti,kai shayin ki dawo ki</p><p>dauki dankalin,yau shi kadai ma nayiwa dankalin."</p><p>Tace,"nifa?"umma tace "ke kina cin dumame</p><p>Abba ko ba ya ci,dan haka dan wanda ya rage</p><p>shi nayi wa." Ummi ta figi kayan tea din ta nufi</p><p>dakin Abba tana tura baki.tare da sallama bata</p><p>jira amsa ba,ta daga labule ta fada. Dabi'ar da</p><p>yake mata fada akai kullum,ya gama saka</p><p>singiletinshi kenan yana kokarin saka riga. Yace,</p><p>"wai ke wace irin majanuniya ce?ban ce miki in</p><p>kinyi sallama sallama sai na amsa za ki shigo</p><p>ba? sai kawai ta saki tiren,ruwan zafin ya zube</p><p>masa a kafa,dankalin ya watse kan rigar da zai</p><p>saka. tayo waje da gudu,sai dakin tsohuwa.ya</p><p>fito da sauri yana cewa,"umma ta kona ni! ta</p><p>kona ni!!" da sauri umma ta fito daga dakin Alhaji</p><p>babba,shima Alhajin na biye da ita yana fadin</p><p>"wacece ta kona ka?" Yace "ummi ce! ummi</p><p>ce!!."nan take Alhaji babba ya rike kafar yana tofa</p><p>mishi addu'a. Umma ta debo kullun kamu ta zuba</p><p>mishi,amma duk da haka sai da yan yatsun</p><p>kafarsa suka kumbura. tsohuwa ta fito daga daki</p><p>tana fadin,"kai ummi bata ji? wai ni meyasa aka</p><p>sa mata sunana?" Abba ya kalli tsohuwa cikin</p><p>takaici yace,"duk ba ke kike daure mata gindi ba?"</p><p>Umma ta shiga dakin tsohuwa ta janye kayan da</p><p>tsohuwa ta jera don kada aga ummi,ta janyota</p><p>tun daga dakin take kwallo da ummi har waje.</p><p>Alhaji ma yau har dashi aka zane ummi,tsohuwa</p><p>dai sai yan mitoci take yi,wai yanxu haka ma</p><p>bata sani bane. Abba dai ranar dai bai je</p><p>makaranta ba,haka nan da yamma sai da ya saka</p><p>ummi a dakinshi ya bata gwale-gwale sannan ya</p><p>zane ta. misalin hudu da rabi na yamma,Ahmad</p><p>abokin Abba yayi sallama a kofar gidan,Abba ya</p><p>amsa ya fito. Suna zaune kan dakalin kofar gidan</p><p>suna hira,sai ga ummi ta yanko da gudu tana</p><p>waiwayen baya. Ya ce,"zo nan."tazo yace,"kinyo</p><p>tsokanar fada ko?" tace,"a'a.yace in har tsokana</p><p>ki kayo zaki sani shegiya mummuna kazama. Ta</p><p>murguda baki,yasa takalmi ya jefeta,ta shige gida</p><p>sai ko ga wani yaro jiki duk kwata yayyanshi na</p><p>biye dashi. ya tambayesu,suka ce "ummi ce ta</p><p>jefa shi kwata"ya taso yaron har cikin gida ya</p><p>kamota dakin tsohuwa ya tsareta ta wanke ma</p><p>yaron jiki,ta kuma wanke kayan. sannan ya</p><p>zuzzuba mata kola a kai.tsohuwa tana ta yiwa</p><p>yaran fada,wai ita ma su daina tsokanarta Umma</p><p>ko lekowa bata yi ba,ya fito ya samu Ahmad yana</p><p>cewa "kayi hakuri na barka kai kadai." Ahmad</p><p>yace,"ba komai" sai Abba ya zauna sannan</p><p>Ahmad ya dube shi. Abba wannan kanwar taka</p><p>kuwa bata da Aljanu? Abba yace,"ba kowa</p><p>akanta,sai iskanci." Ahmad yace."a'a,kai dai ku</p><p>kaita ayi mata rukiyya." Abba yayi dariya,sannan</p><p>yace kasan Allah ba kowa akan ummi,saboda</p><p>Alhaji karami ya taba yin wannan tunanin. ya</p><p>dauke ta yakai ta rukiya bata da komai."Ahmad</p><p>yace tabdi!,gaskiya in ta isa aure duk wanda ya</p><p>aureta akwai aiki babba a tare dashi. Abba ya</p><p>ce,"wane mahaukaci ne ma zaya dibar ma kansa</p><p>ummi?"Ahmad ya ce,"sai ai muku hadin ggida..."</p><p>ya kaima Ahmad naushi a gefen ciki,Ahmad ya</p><p>kauce yana masa dariya. Abba ya ce,"ka cuce</p><p>ni,ace in auri ummi ai sai na hada kayana na bar</p><p>garin nan. nan. Ahmad ya s heke da dariya har</p><p>da rike ciki.sannan ya ce,"don me? Abba ya</p><p>ce,"to wannan yarinyar ba sai ta hada maka</p><p>gobara gida ba?gata kazama ga muni." Ahmad ya</p><p>ce,"kama dai kuke yi." Abba ya bata rai,"Ahmad</p><p>bana so.in har da gaske ina kamada ummi ba sai</p><p>na koma ciki an sake haifana ba. Don Allah ni</p><p>tashi ma ka tafi,don wallahi da don kai bane kake</p><p>fada min haka da sai munyi rigima,na tsani</p><p>ummi,bana sonta sam! Zaune suke a kofar gidan</p><p>Alhaji babba kan katuwar tabarma,sun jere abinci</p><p>suna ci. kullum Alhaji babba da Alhaji karami nan</p><p>suke zama tamkar tagwaye,suna matukar kama.</p><p>mafi yawancin lokuta ma kaya iri daya suke</p><p>sakawa,domin Alhaji babba duk kayan daya saya</p><p>tare yake sai musu. haka nan hula ko</p><p>takalmi,haka nan matansu baya</p><p>bambantawa.shima Alhaji karami duk da bai kai</p><p>samun babba ba yana koyi dashi. Alhaji babba ya</p><p>kalli karami yace,"Aminu ya zancen makarantar</p><p>bashir?" Alhaji karami ya dubi wansa ya ce,"Alhaji</p><p>bashi fa ya fadi jarabawa,jiya na tsare shi da</p><p>maganar sakamakon jarabawarshi yace bai duba</p><p>ba,saida yaji nace zan hada shi da Abba suje</p><p>sannan yace min yaje wai duk ya fadi. Alhaji</p><p>babba yace,"Ash sha! sai ya maimata shekara</p><p>kenan?"Alhaji karami ya ce,"to in ma ba zai</p><p>maimaita ba Alhaji shi ya sani,ba sahura ta bata</p><p>su ba? shi Abba ai ba haka yayi ba,ka dubi fa</p><p>yadda yaki aikin kanikancin nan,uwarshi ta zuga</p><p>shi wai yayi karatu kadai yayi aikin gwamnati.</p><p>kullum haka sahura take kitsa ma yaran."Alhaji</p><p>babba yayi yar dariyar takaici,sannan yace"in</p><p>banda abin sahura yadda kasan nan tamu ta</p><p>zama waye zaici alwashin aikin gwamnati? ina ce</p><p>masu digree ne ke yawo ba aiki?" "har masu</p><p>masters." inji Alhaji karami.ya tashi zaune daga</p><p>kishingidar da yayi,yace dubi misalin dan</p><p>abokinnan naka Alhaji buhari." Alhaji babba ya</p><p>ce,"kwarai kuwa,mas'ud ba.yanxu ma fa kasuwa</p><p>yake zuwa,sai yanxun yake koyon kasuwancin."</p><p>Alhaji karami ya ce,"to daya dora shi a kasuwar</p><p>fa tun farko?shi yasa na fada ma sahura ta bar</p><p>yara su hada da sana'ar hannu. Donni dai yaro</p><p>kamar bashir yanxun ba zan dauki kudina in ba</p><p>shi ba."Alhaji babba yace,"shi yasa kulum nake</p><p>kara son Abba,yaron nan da kanshi yace min in</p><p>kai shi shagon dinki. Har naki suwaiba ta</p><p>ce,"Alhaji ka kai shi in ya iya sana'ar hannu ko</p><p>bai samu aikin gwamnati ba zai rike kanshi da</p><p>sana'ar nan." Alhaji karami ya ce,"to ai kasan ita</p><p>suwaiba tasan abinda take yi.amma sahura sai</p><p>addu'a." Sallamar Abba ce ta katse su,ya zauna</p><p>can gefe sannan ya gaishe su,duk suka amsa tare</p><p>da tara hankulasu gurinshi. Ya mika ma Alhaji</p><p>babba kullin takarda tare da cewa "Alhaji gashi</p><p>maganin (ulser)ne" Alhaji babba ya amsa ya</p><p>ce,"Abba sarkin amsa magani, a gurin wa ka</p><p>samo wannan kuma?" ya ce,"Ahmad abokina na</p><p>raka ya amso ma babanshi,shine nace bari in</p><p>amso muku" yace to Allah ya saka da</p><p>alkairi."Alhajikarami yace"dame ake sha?" Abba</p><p>ya ce,"da madara peak." suka ce"to" daya mike</p><p>zai shiga gida Alhaji babba yace ya shige da</p><p>kwanikan abincin. yau kam Abba bacci yake ji da</p><p>wuri,don haka ya baro shagon dinkinsu wanda ya</p><p>kan kai goman dare a ciki ya nufo gida. Ya bude</p><p>dakinshi ya shiga ya cire riga sai singileti da</p><p>gajeren wando na jeans.ya nufi ciki don ya kama</p><p>ruwa ya kuma yi wa ummanshi sallama. tsakar</p><p>gida ya sameta zaune ta zabga tagumi,inda</p><p>abinda Abba ya tsana shine,yaga ummanshi cikin</p><p>damuwa. da sauri ya isa wurinta,"umma</p><p>lafiya?"ta dube shi "ina fa lafiya,ummi ce tunda</p><p>tayi sallar isha'i ta fice kusan awa guda zance</p><p>jiya ka mata dukan fita wasan dare?" Abba yace</p><p>"to wai me za'a yi wa ummi ne ta zama irin</p><p>sauran yara?" umma tace,"addu'a ce Abba,kuma</p><p>muna yi kullum." ya juya cikin bacin rai,layin su</p><p>Amina kawarta ya nufa,don bata wuce can.duk da</p><p>cewa Amina bata kaita rashin ji ba. can din kuwa</p><p>ya sameta,ta tara zugan yayan layi sai tsokanar</p><p>fada suke yi,ita ce shugaba. wata falwaya Abba</p><p>ya samu ya jingina yana kallonsu,don yana iya</p><p>tunkararta su diba da gudu. shi kam ba za ya iya</p><p>guje-gujen nan ba,duk wanda yazo wucewa sai</p><p>sun tsokane shi,wani su jefe shi,wani kasa zasu</p><p>watsa masa su gudu wani kuma rigarsa zasu ja.</p><p>c can wani shida budurwarsa sun zo wucewa ta</p><p>fizge ledar hannunsu ta watsar,sannan suka ruga</p><p>da gudu. tayo gurin da Abba ke tsaye bata zaci</p><p>da mutum a gurin ba,sai dai taji anyi caraf da</p><p>ita.sai da Abba ya zabga mata koso a tsakiyar</p><p>kai har tayi fitsarin wuya,sannan ya tasata har</p><p>gurin mutumin data yaga ma ledar. suna</p><p>tsugunne suna tsintar lemunsu da ayaba ya</p><p>ce,"malam ga wadda ta yaga muku leda." da</p><p>zafin nama mutumin ya mike,Abba ya</p><p>ce,"gata"mutumin ya shakota yace yau sai naga</p><p>ubanki." Abba ya ce,"ko kara ka kai gidansu nine</p><p>zan hukuntata,don haka gata na kawo maka</p><p>kanwata ce kuma naga lokacin data tsokaneka."</p><p>jikin mutumin yayi sanyi ya ce,"na gode bawan</p><p>Allah,taje taci albarkacinka." Abba yace "daka</p><p>nade ta." mutumin yace,"ba komai,ke kuma ki</p><p>canza hali ke mace ce." Abba yace nagode"</p><p>sannan ya tasa ta zuwa gida. Bokiti ya cika da</p><p>ruwa ya dora mata,,umma rasa bakin magana</p><p>tayi daya sanar da ita tsokanar daya tarar da</p><p>ummi suna yi. Daga karshe ta ce,"Allah ya</p><p>shiryaki,abind ya sameki kada ya sami sauran</p><p>dangi. Alhaji kuwa daya sameta dauke da bokitin</p><p>tana kuka tana fadin "yaya Abba na tuba,bazan</p><p>sake ba." ya ce,"uwata bakya ji ne fatan Allah</p><p>yashirye ki."ya nufi dakinshi.tsohuwa takaicin</p><p>Abba ne ya hanata fitowa tayi magana. nata</p><p>ganin,ummi bata wuce fita tayi wasa da</p><p>kawayenta ba,a cewarta ba laifi ba ne. amma an</p><p>bi an tsangwami yarinya,an hanata walawa.sai da</p><p>Abba ya gaji dan kanshi sannan ya sauke mata</p><p>ruwan. Sannan ya mammaka mata</p><p>takalmi,sannan ta shige dakin</p><p>tsohuwa.tsohuwana daga kwance ta dubeta.</p><p>"yaga dama ya kyaleki?kai mai sunan malam</p><p>akwai mugunta.zo ki kwanta." cikin kuka ummi</p><p>tace,"kayana sun jike,bokitin ruwa fa ya dora</p><p>min."tsohuwa tace,"barshi da halinsa,ace mutum</p><p>ba zai sake ba?" ummi tace,"ai sai na rama,shima</p><p>din sai yayi kuka."tsohuwa ta ce,"a'a,kada ki</p><p>soma zancen ramakon nan.kin san ko kin rama</p><p>ke ce zaki kwan ciki." ummi ta ce,nifa sai na</p><p>rama."tsohuwa ta ce,"baki gaji da shan wahala</p><p>ba kema da shegiyar gaddama,ga zanina nan</p><p>kikin raki ciro ki daura kizo ki kwanta." ummi tayi</p><p>lamo bayan tsohuwa tana tunanin dame zata</p><p>rama abinda Abba yayi mata jiya.har bacci yayi</p><p>gaba da ita waiwaye............. SULAIMAN shine</p><p>asalin sunan Alhaji babba,Aminu kuma shine</p><p>Alhaji karami. tsohuwa itace mahaifiyar su,kuma</p><p>su kadai ne yayan data haifa.Asalinsu yan</p><p>zamfara ne a kauyen daji a karamar hukumar</p><p>kauran-namoda. malam Idris mahaifinsu shine ke</p><p>zuwa yawon fatauci,har Allah ya zaunar dashi a</p><p>garin kano,da matarshi Habiba. sunzo da</p><p>yayansu guda biyu,sulaiman da Aminu.sun yi</p><p>karatun muhammadiyya mai zurfi,amma basuyi</p><p>karatun boko ba. sannan ya dora sukan harkar</p><p>kasuwanci,Allahya albarkaci kasuwancin Sulaiman</p><p>inda harkoki suka bude mishi cikin kankanin</p><p>lokaci. matsalar shi daya rashin boko,malam</p><p>idrisu mahaifinsu yana daya daga cikin wadanda</p><p>basu amshi boko ba lokacin da tazo. Don haka</p><p>sam bai saka yayansa ba.Sulaiman ya auri</p><p>Suwaiba wadda suka dauki watanni suna</p><p>soyayya,ita yar unguwar sheka makaranta ce.</p><p>Amma asalinsu yan Daura ne jihar Katsina.kafin</p><p>aurensu sai da yayi gini a unguwa uku gidaje</p><p>guda biyu iri daya. Ya ce Aminu kaninsa ya zabi</p><p>gida duk da cewa a lokacin baiyi auren</p><p>ba,wannan abu yayi wa mahaifisu dadi. yayi ta</p><p>shiwa Sulaiman albarka,don haka sai aka rufe na</p><p>Aminu,yayin da sulaiman ya tare a nasa da</p><p>matarsa Suwaiba. / ZURFIN CIKI book 1 part 2</p><p>ZURFIN CIKI book 1 part 2</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 21:40</p><p>Kwanci tashi 5yrs ta miqa suwaiba bata taba ko</p><p>batan wata ba. awannan yr ne mahaifinsu ya</p><p>cimma 1yr da rasuwa. saida aka watse makoki</p><p>danginsu na qauran-namoda suka koma. sannan</p><p>sulaiman yace da aminu, to ni xan dauki tsohuwa</p><p>in maida ta gidana,kai kuma aminu ka fito da</p><p>mata kayi aurenka dan mu xauna kusa da juna.</p><p>tsohuwa ta saka kuka tace wannan yaran nidai</p><p>da ka barni na xauna da gidan xai xama kufai.</p><p>sulaiman yace tsohuwa kiyi haquri, sai a saka</p><p>haya.aminu yace haka xa ayi. daqar tsohuwa ta</p><p>yarda dan tace ita wannan gidan mutuwane xata</p><p>rabata dashi, dan gidane me tsohon tarihi a</p><p>gurinta. ta ce gidan da mijinta ya rasu gidan da</p><p>ya kawo ta tun tanada jajayen sawunta. suka dai</p><p>lallabata. lkcn da aminu ya gabatar da sahura a</p><p>matsayin matan da xai aura, tsohuwa ta tuma ta</p><p>ce ba ta laminta ba, don kuwa kowa yasan</p><p>mahaifiyar sahura gun masifa. sanna sahurace ta</p><p>gajeta. aminu sai ya watsar da mgnn auran</p><p>gabaki daya har tsawan lkc. sulaiman yanata</p><p>roqan tsohuwa ta amince, dan ya lura aminu yayi</p><p>nisa. Ba yadda tsohuwa ta iya, dole ta amince,</p><p>aka sha biki ta tare gidan aminu. mai hali dai</p><p>baya fasawa, dan sahura batasan hulda da</p><p>suwaiba da surukarta, gashi daga kawota ko</p><p>2mth bata yiba ta kama fada da yan unguwa. a</p><p>cikin 3yrs sahura aka samu ciki. lkcn sulaiman ya</p><p>samu xiyarta qasa mai tsarki shida tsohuwa dan</p><p>sauke farali. sunyi addu'a allah ya bashi xuri'a</p><p>shida aminu.suna durowa gida suka samu lbrn</p><p>cikin sahura, murna a gun sulaiman tamkar</p><p>matanshi ne keda cikin.lkcn haihuwa tahaifi da</p><p>namiji murna gun yan uwa biyu ba'a magana,</p><p>anyi shagalin suna inda yaro yaci sunnan mahai</p><p>finsu wato idris shine suke kiranshi abba. Sannan</p><p>Ahaji Sulaiman ya biyama qaninshi kugeran</p><p>makka daga nan ne aka samu ahj Babba da ahj</p><p>qarami tun abba yana jariri ahj babba da</p><p>matanshi suke dawainiya dashi Sahura ba taso</p><p>saidai ba yan da xaitai da ita. domin alj qarami</p><p>na gama shirin fita xai saba shi sai gidan sai yayi</p><p>kukan nono ake maida shi, saidai tayi ta mitar</p><p>cewa anriqe mata yaro gidan,sahura dai in an</p><p>kawoshi bata isa taxoba dan tasan tsohuwa</p><p>tafita danja.duk da gugar xana da haibaici da</p><p>sahura take antayo ma suwaiba ta katanga ko</p><p>inta je gidan, baisa ta daina dawainiya da abba</p><p>ba. cikin hakane sahura wata ran sahura ta tashi</p><p>da xaxxabi mai tsanani da amai, shine taje asibiti</p><p>ganin likita ya tabbatar mata da tana dauke da</p><p>ciki.ko da ta fadama alj qarami ba qaramin murra</p><p>yayi ba ita kuma ta batarai, yace tunda abba</p><p>yana tafiyan shi ko ina ayaye shi. Da yamma</p><p>bayan yadawo kasuwa ya shiga gaida tsohuwa</p><p>shine yake gayamata xa'a yaye abba. tace</p><p>saboda me? ku barshi yayi 2yrs. sai yace ai uwan</p><p>tanada juna biyune, shi yasa, daman sha waran</p><p>da nakesan fada maki shine xanba yaya shi</p><p>kyauta har abada.tsohuwa tace kai amma ka</p><p>kyauta. Washegari da safe shine ma yayi ma</p><p>abba wanka tana kwance ya shirya shi, sannan</p><p>yace mata ta hada kayanshi duka dan xan kaishi</p><p>gidan ahj babba gaba daya. tace kana nufin kayi</p><p>kyauta dashi gaba daya? yace ea. tace tabdi!,ba</p><p>xai yiwu ba. infishari banxane kaxa tayi mana. su</p><p>wa yace kada su dage su samu nasu dan? nima</p><p>wahala nasha na haifi dan, ba shago na bude ya</p><p>fito ba....sam bai kulata ba, ya hada kayan yaran</p><p>ya fita. ya shiga gidan ahj babba da shi. dakin</p><p>tsohuwa ya shiga, nan ya samu ahj babba suna</p><p>gaisawa, yace yauwa, dama gurinka naxo yaya.</p><p>abba ya sauka daga jikin babansa yaje jikin ahj</p><p>babba da gudu, ahj ya dauke shi ya rungume. Ahj</p><p>qarami ya keqa ya kira suwaiba,ta shigo ta xauna</p><p>sai ahj qarami ya soma jawabi da cewa. tsohuwa</p><p>ina san ki xama sheda, yaran nan na ba yaya da</p><p>suwaiba har abada.ahj babba yasake rungume</p><p>yaran a jikinshi wani saban son shi ya ratsa shi.</p><p>idanshi suka kawo qwalla, suwaiba ta sa kuka</p><p>tace mun gode da wanna abu da ka yi mana.</p><p>Allah ya bamu ikon riqeshi da amana. ahj babba</p><p>yace bani da bakin da xan maka godiya, saidai</p><p>ince allah ya qara xumunci. ahj qarami yace haba</p><p>yaya dana nakane, saidai inasan abba ya xama</p><p>xaka kai daya. tsohuwa tace allah ya maku</p><p>albarka daku da yayanku, kaima allah ya baka</p><p>haihuwa. sukace amin. Sahura kuwa mijinta na</p><p>fita da yaro, itama ta xari hijabi ta nufi gidan</p><p>iyayanta, ta shaida ma mamanta cewan aminu</p><p>yayi kyauta da danta, kuma yaba mutanan da</p><p>basa qaunan ta. nan da nan uwar tahau masifar</p><p>cewan ba xai yuyu ba, ai dole ya baki danki.</p><p>shiko uban cewa yayi ai ikon sane, dan haka</p><p>baiga laifinsa ba dan yaba dan uwansa dansa.</p><p>sannan yace ,ta tashi ta koma. uwar tace ba xata</p><p>koma ba, ya ce ta xauna. bai sake bi ta kansu ba,</p><p>ya ci gaba da harkokinsa. shiko ahj qarami cewa</p><p>yayi baxai bita ba, lokacin da ya dawo ya samu</p><p>batanan, sannan bai fadama dan uwansa ba har</p><p>aka kwana. sukuma su suwaiba basu fahinci</p><p>sahura batanan ba dan ba hurda suke ba, saida</p><p>kukaxo cin abinki ahj qarami bai futo da kwanu</p><p>ba. sannan wan yace iyalin naka bata nanne?</p><p>yace yaji tayi, niko baxan bita ba. ahj babba yace</p><p>akan wani dalili ne? ahj qarami yace ban sani ba,</p><p>na dawo gida ban ganta ba. da safe ahj babba ya</p><p>tashi gaba sukaje gidan, sahura ba kunya tace</p><p>danta takesan ya dawo mata dashi, inhar yana</p><p>san xama da ita. Ahj babba yace, indai danta ne</p><p>xai maido shi. ahj qarami yace shi kuma inhar sai</p><p>an dawo da dan to ya haqura da auranta. kuma</p><p>na cikin ta ma inta haife shi xaixo ya ansa ya</p><p>qarama wansa inya so yaga yadda xatayi. duk</p><p>juyin da akayi yaqi yarda daga qarshe ma tafiyan</p><p>shi yayi. ubanta yace da ahj babba kaima jeka</p><p>yadda suka so haka xasu yi. satinta guda taka</p><p>abincin kirki gagaranta yake yi, ita kuma uwan ta</p><p>daina samun wani abu daga gun sahurar ke kawo</p><p>mata. dan haka suka yanke shawaran ta koma,</p><p>duk da haka saida ya shareta na kwana uku</p><p>sannan ya sakar mata. haka ta haqura saidai</p><p>tasha alwashin dun runtsi sai danta ya dawo</p><p>hannunta. sannan ta kulla sabuwan gaba da ahj</p><p>babba da suwaiba kuma tace duk tsohuwa ce</p><p>takitsa abin. abba yana samun kulawa tare da</p><p>tarbiya mai kyau.sahura ta haihu ta sake samun</p><p>da namiji aka samasa bashir, daga nan haihuwa</p><p>akai akai.. Tun abba yana qarami ya koyi wasu</p><p>halaiya na ahj babba. da farko, sallar</p><p>asuba,axahar, laasar, magrib da isha. ahj babba</p><p>kan tasa abba suje masallaci da rana kuma</p><p>umman sane ke turashi. ranan jumaa ahj na</p><p>dawowa gida dan ya tafi dashi. dan haka sallah</p><p>ta xauna ma abba da xaran lkc yayi xai fara shiri</p><p>yi. sannan ya iya sadaka dan dasunje yana bashi</p><p>kudi ya rabama almajirai ko yasa a asusun</p><p>masallaci. sai xumunci aduk lkcn da ahj babba</p><p>xashi xanfara yana tafiya da shi. ya tashi da san</p><p>iyayan shi matuqa bai taba sanin basu suka haife</p><p>shi ba. duk da cewan duk lkc da ya shiga gidansu</p><p>umman bashi takan cemai bafa umman kace ta</p><p>haifeka ba, nice na haifeka. riqonka muka basu. in</p><p>yaji haka sai yace allah kiyaye. sai ya baro gidan</p><p>ita kuma taita xakinsa. inya fadama umman shi</p><p>saitai murmushi ta rungume shi. ya ce aidai kece</p><p>ummata ko? ita kuma tace nice ummanka rabuda</p><p>ita kaji. abba yanada tausayi dan haka ya</p><p>taimaka ma ummanshi aikin gida. shekara sha</p><p>biyu ya sauke kur'ani.a lkcn ne ya gama pry ya</p><p>samu xuwa js1 Abba makarantan masu kudi ya</p><p>ke yi.ita kuma sahura duk yaranta ta batasu,</p><p>musamman bashir. duk lkcn da akace yaje</p><p>makaranta inyace ya gaji, saitace ya xauna kaje</p><p>gobe. ko ahj babba ya korashi sai dai ya labe</p><p>inya tafi shi kuma ya dawo. yafi san xuwa qwallo</p><p>ko shagon game. to hakama qannansa duk sun</p><p>dau irin tarbiyyan uwarsu. cikin haka wata ran</p><p>umman abba ta tashi da matsananciyan mura,</p><p>lkcn ahj babba yaje legos don taho da kaya. ahj</p><p>qarami ne yakaita asibiti bayan gwaje gwaje, an</p><p>gano ciki wata biyu da yan kwanaki. murna gun</p><p>ahj qarami tamkar yayi tsuntsuwa yaaje ikko ya</p><p>fadama ahj babba. suna isowa ya shiga gun</p><p>tsohuwa ya sanar da ita. nan take tasa kukan</p><p>murna.ita kuwa suwaiba tamkar mafarki, sai</p><p>kunya ta isheta. lkcn da ahj qarami ya fadama</p><p>sahura, sai cewa tayi um, bana an tabuka, ni dai</p><p>gani da cikin na shida amma sai yauxu ta samu</p><p>daya. ahj qarami yace kinji matsalanki, ke ba dai</p><p>kiji wani ya samu qaruwa ki taya shi murna ba,</p><p>sai dai baqin ciki. ta ja tsaki bakin cikin me</p><p>xanyi? tunda ni ga nawan. ciki mai laulayi</p><p>suwaiba ta samu, wanda duk abin da taci sai ya</p><p>dawo. wannan lamari ya daga ma ahj babba</p><p>hankali da abba, duk aikin gidan abba ke yi, ga</p><p>makaranta, ko an hanashi sai yayi.dan haka aka</p><p>dauko harira qanwar suwaiba, wanda mijinta ya</p><p>mutu. umman abba dai bata samu kanta ba saida</p><p>cikin yayi wata biyar. sannan ta samu sauki.lkcn</p><p>sahura tanada cikin wata bakwai, lkcn haihuwa ta</p><p>haifa mace, murna gurinta kamarme, dan sai</p><p>yanxu ta samu mace. safiyar talata umma ta</p><p>tashi da naquda, hankalin ahj da abba ya tashi</p><p>matuqa. duk da tsohuwa tana ta kwantar masu</p><p>da hankali, ranan abba ko makaranta bai jeba,</p><p>duk da san makarantansa, har suka dawo sallan</p><p>axahar shuru. ahj babba yace tsohuwa bari na</p><p>samo mota akaita asibiti. tace to. yana fita ba</p><p>jimawa ta haihu. ta santalo yarta mace mai</p><p>matuqan kama da ahj babba. tsohuwa tace da</p><p>abba,mai sunan mlm bi su ahj kace sudawo ta</p><p>haihu. dama harira tasa ruwan wanka lkcn da</p><p>suka xo ta fito daga wanka.nan aka wanke</p><p>yarinya yan barka sai xuwa suke amma sahura</p><p>saida aka. Sahura saida aka kwana sannan ta</p><p>shigo. ta dauki yar ta taba baki tace wannan yar</p><p>baqinqirin haka sai idanu daqwa daqwa. wata</p><p>mata da taxo barka tace ai wannan yar sak</p><p>abba,suna kama sosai. sahura ko kunya ta ce</p><p>basa wani kama da abba. da tasamu kyan abba</p><p>da tayi kyau, umma tayi ma matan alama da</p><p>haunu tai shuru. ranan suna taci sunan tsohuwa,</p><p>wato habiba, dan haka umma ke ce mata ummi.</p><p>abba yana ji da ita, saidai in yanasan tsoka nanta</p><p>sai yace dubeta ta ba ummata wahala, sai na</p><p>xaneki kika girma kika qi mata aiki. umma taita</p><p>masu dariya. tsohuwa ma naji da ita dan guta</p><p>take wuni. tunda ga kan ummi umma bata qara</p><p>haihuwa ba. abba yana aji uku suna qoqarin xana</p><p>(j.s.c.e)ya dage sai ahj ya saka shi shagon dinki.</p><p>ahj yace abba kabar batun dinkinnan ka tsaya a</p><p>karatunka. yace ahj nidai ina so kaga inna iya su</p><p>umma sun huta dakai dinkin su gidan laminde.</p><p>umma tace ka barshi yayi ahj sana an hannu ai</p><p>tanada dadi, kaga in ya gama bokon ba bai samu</p><p>aiki ba xaya riqe kanshi da sana anshi. ahj yace</p><p>to shi ke nan Ahj yace, to shi kenan, wane shago</p><p>ka ke san shiga inkai ka? yace, na can bakin titin</p><p>nan, in da kake saya na lemo. ahj yace shi kenan.</p><p>mafarin shigar abba gurin koyan sanaa kenan.</p><p>ummi ta taso da rigima, tsiwa tare da tsokana,</p><p>wanda yasa suka daina shiri da abba sam. abba</p><p>ne ya kaita makarantan boka da islamiya, kullum</p><p>yaje daukota sai ya raba fada ko ya bada hakuri.</p><p>umma kullum addua take fili da xuciya da lokutan</p><p>sallah, allah ya shirya mata ummi. ita kuma tata</p><p>kalan quruci yan kenan inta girma xata daina.</p><p>tsohuwa takance aini me sunana kingama min</p><p>komai, domin banasan ragon da, da in kai qara</p><p>gara akawo min na bada haquri. duk lkcn da tayi</p><p>wannan kalman sai sunyi fada da abba, dan cewa</p><p>yake ai dama tsohuwan nan tuni na ane kin daure</p><p>mata gindin ta siqa tsokanan yayan mutane. ita</p><p>fa mace ce ba namiji ba, shi kenan bata da aiki</p><p>sai dambe? tsohuwa takance batta tayi. tunda</p><p>ganan abba basa shiri da tsohuwa. ita kuma fati</p><p>yar sahura kamar ummace ta haifeta dan bata da</p><p>hayani. ummi kuma kamar sahura ta haife ta.</p><p>Wata rana abba ya ke cewa, umma da ace lkc</p><p>daya kuka haihu da umman bashir, allah cewa</p><p>xanyi kunyi canjin yaya. umma ta dube shi dan</p><p>me kace haka? yace sbd masifar ummi irinna</p><p>umman bashir ne, fati kuma ba ruwanta kamar</p><p>ke.dariya kawai take yi. kwanci tashi ummi ta</p><p>gama pry, lkcn abba yana shekaranshi ta qarshe</p><p>a jamia. yana karantan (mass comm)ne dan yana</p><p>san xama dan jarida. umma tasoshi da likita</p><p>amma yace baida raayi. tace kaga kai bakada</p><p>hayaniya abba aikin jarida na masu maganane.</p><p>yayi murmushi yace umma kenan. ummi ta samu</p><p>shiga aji daya a qaramar sakandare. maimakon</p><p>hankali abin nata sai gaba yakeyi. aduk lkcn da</p><p>tai laifi abba ya daketa sai tayi wani abun dan</p><p>tabashi haushi, da sunan ta rama. ahj babba ya</p><p>bude mai shago, tare da xuba mishi kekuna.</p><p>tsohuwa tace dakai wanine mai sunan mlm, saika</p><p>tafi da takwarana ta koya. abba yace ko a</p><p>kwafan shago na na ganta ba sai na karya mata</p><p>qafa ba. ummi ta murguda baki, sai daya tafi</p><p>sannan tace allah ya kiyaye inje wannan qaxamin</p><p>shagon nashi. Tsohuwa ta ce,"tafi can kema da</p><p>baki son ci gaba, in banda abinki da zaki kwantar</p><p>dakai ki koya in an tashi auranki basai a saya</p><p>miki keken ba. in kuma shi kika aura kinga</p><p>shikenan inya samo dinkin da yawa saiki taya</p><p>shi, ta ce"Allah ya kiyaye me xanyi da yaya</p><p>Abba,yayi ta cin xalina?ni bana son shi" Umma</p><p>dake gefe tana jinsu ta ce,"ke in kin samu kamar</p><p>Abban ma ai kinji dadi,shine zai ce mai zaiyi</p><p>dake? mara hali irinki." Ummi dai tayi shiru tasan</p><p>inta cika surutu kan Abba yanxun nan umma ta</p><p>doddoketa,umma tafi son Abba fiye da ita. watan</p><p>ramadan ya tsaya,duk daukacin musulmi sun</p><p>dauki azumi ranar da akai na uku Abba ya shigo</p><p>gida karfe daya saura. daga shago yake zaiyi</p><p>wanka yaje makaranta don yanada darasi karfen</p><p>biyun rana. Gidan shiru kowa na bacci,don haka</p><p>bai shiga dakin umman shi ba don baya son ya</p><p>tasheta ya shige bandaki. Da ya gama ya fito ya</p><p>nufi daki kamar ance ya kalli madafi, ummi ce</p><p>tsugunne tana cin abinci. ya tsaya yana kallonta,</p><p>dagowan da xatayi suka hada ido, yace ke! karya</p><p>axumin kika yi? ta toshe bakinta sannan nace</p><p>dan allah yaya kayi haquri. yace fito muje. ya</p><p>kaita dakinshi yasata gwale gwale. da xashi</p><p>masallaci ya kulleta ta baya. ya ce inyaso ki</p><p>tashi kafin na dawo, xan gane. yana fita tahau</p><p>binci ken abinda xata lalata mashi. ta ciro bidiyon</p><p>da yake kallo xata doka da qasa, sai taga kwalin</p><p>wani kaset tana kallon hoton jikin kwali, na</p><p>tsiraici ne. ta xare ido kicin mamaki, tace lalle</p><p>yaya abba, daman shi dan iskane? to kuwa xan</p><p>tona mai asiri. ta turashi cikin xaninta, da taji</p><p>motsin shi yana bude qofa sai ta koma inda take.</p><p>ya shigo ya kalle ta ya ce nasan kin xauna dan</p><p>kinga bananan. ya xauna bakin katifa, sannan ya</p><p>dubeta fuska daure. ummi meyasa kika karya</p><p>axumi? tace ba komai. yace tunda aka fara axumi</p><p>kike karyawa ko? tace yaune kawai yaya abba.</p><p>yace kinsan hukuncin wanda ya kasya axumi da</p><p>gangan. Tace eh an fada mana a islamiya, amma</p><p>mlm yace sai wadanda axumi ya wajaba akan su.</p><p>ya kalle ta cike da mama ki, a xuciyanshi yana</p><p>cewa, yanxu har yarinyan nan tasan akwai</p><p>wadanda axumi ya wajaba akansu? afili kuma</p><p>yace lalle ummi kina buqatan sa ido. dama</p><p>saboda bai wajaba akanki ba shiyasa kika karya?</p><p>to daga yau xansa maki ido, kuma xan fadama</p><p>umma ta sa maki ido. hakanan duk wani abu da</p><p>akeyi lkcn axumi an daina qyale ki, xaki ringa</p><p>sallar tarawi, ke har tahajjud sai kinyi shi. sannan</p><p>bayan axumi saikin rama wannan axumin. ya</p><p>xuba mata ranqwashi a tsakiyan kanta ,tare da</p><p>cewa tashi ki fita munafuka. daga dakinshi bayi</p><p>ta shige ta qara kallon kwalin, sannan ta maida</p><p>ta soke shi, tace sai na tona maka asiri. da dare</p><p>bayan angama bude baki, abba xai tafi tarawi ya</p><p>shigo dakin umma yace ina ummi? umma tace</p><p>gatanan kan kujera tayi sharkaf, wai yau taji</p><p>axumi. abba ya shiga ciki yana kallanta. yace</p><p>umma xaki yaudara ko yar rainin wayau, tafa</p><p>karya axumi daxu da rana na ganta tana cin</p><p>shinkafa. Yace shine kika xube wai ke kin sha</p><p>wuyan axumi ko? umma ta dube ta tana mamaki,</p><p>tace abincin da kike kinba almajirai da ma qarya</p><p>ne? ya dubeta yace biyu kenan ga larya axumi ga</p><p>qarya, xaki sani. tashi muje salla ko in ballaki.</p><p>umma tace allah ya shiryi halinki. abba yayi</p><p>dariya tare da cewa, kema dai umma yaxaki</p><p>amince da batun wai tac almajirai abinci, su basa</p><p>axumi ne, umma tace tunanin haka sam bai xo</p><p>min ba. saida ya sakata sahun salla, sannan ya</p><p>nufi gun maxa. bayan ya gargadeta da cewa in an</p><p>idar ta jira shi, inyaxo batanan sai ta sani. koda</p><p>aka idar da yaxo bata nan gurin ya kaure da</p><p>dambe da wata yarinya wai da suna sallah tana</p><p>bigeta. shine daga idarwa ta cakume yarinyan da</p><p>fada. bai tsaya sauraranta ba ya cire ta kalmi ya</p><p>shiga dukanta, sannan ya tasata xuwa gida. sai</p><p>da ta shige dakin tsohuwa sanna ya koma nashi</p><p>dakin. hakanan suka ta xuwa masallaci har</p><p>axumi yakai ashirin. Ahj ya kawo masu shadda</p><p>da leshi da atamfa na sallah ita da umman su</p><p>bashir da fati. ya suya masu takalma da mayafai,</p><p>abbane xai masu dinki, ran ummi baya son dinkin</p><p>abba, domin wanda take so bashi yake mata ba.</p><p>ta ce umma dan allah nidai a bani dinkina na</p><p>kaima laminde, yaya abba baya min ne kyau.</p><p>umma tace kije ki karbo da kanki. tace ai baxai</p><p>bani ba ne, xai dakeni. umma tace ai nafi san ya</p><p>dake kin, lamindan finshi dinki mai kyau tayi ne?</p><p>ummi tace nidai gara ita. tsohuwa tace ai banga</p><p>lkcn da mai sunan mlm xai faranta ma takwara</p><p>ba, kullun burinshi ya quntata mata. umma tace</p><p>tsohuwa ummi fa ba a mata gwaninta, inace dinki</p><p>in yayi mata har aro ake xuwa yi? ta dube ta</p><p>tace keda shine inya jiki kyayi biyu babu, yaqi</p><p>maki dinkin luma ya hana kayan bare kiba</p><p>laminde inga ta tsiya. qarfe dayan dare ya tura</p><p>dakin tsohuwa tana xaune a kan sallaya tana</p><p>addua, abba yayi murmushi. tsohuwannan kina</p><p>birgeni dama kina ibadan dare? ya kalla kan</p><p>gadonta, ummi taya dai dai tana ta bacci./ ZURFIN CIKI book 1 part 3 ZURFIN CIKI book 1 part 3 Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 21:42 Ya kalla kan gadonta, ummi taya dai dai tana ta bacci. Yace, ummi ke! ummi!! tashi. tsohuwa tana yi masa alama da hannu gami da gyaran murya, wai ya bar ummi maimakon haka ma sai ya dauki wani kofi nan gefansa da guntun ruwa a ciki ya watsa mata a fuska. ta farka firgigit, yace taso, da sauri ta tashi yace dauko hija binki maxa. ta dauka suna fita tsohuwa tana sallamewa. tace kai mai sunan mlm ka lafama yarinyan nan haka, wai axumi wajaba akanta yayi da xaka tasheta da tsohon darannan xuwa masallaci? yace kema in xaki, xo muje. ya tasata suna tafiya tana hada hanya suka tafi tahajjud. sai qarfe hudu na asuba aka tashi. ummi har kuka tayi saboda tsananinjin bacci, amma tana tsoran kar ta kama bacci yaxo ya same ta. tun tana layin bacci har ta gyagije. sakamakon tashinta da matan kusa da ita keyi. kafin kwana uku ta saba da sallan dare, lkc nayi xata farka. abba yana xaune ga dinki gabanshi amma yana can tunanin bushira, yarinyan da yake matuqan so ce. amma yana shakkan fada mata,dan iyayanta sunada kudu matuqa. kuma shine yakema duk yan gidansu dinki. Ahmad abokinshi da ke gefe kuma sai yayi murmushi, yasan tunanin bushiqa ne ke damun sa, dan haka sai ya ce, abba kasan allah, abari ya huce shi ke kawo raban wani. haka kuma ZURFIN KICI, ba xai kai ka gaci ba. ka fada mata kawai. abba ya ce hum ,ina tsoron kada ta ce bata sona, dan bansan ina xansa raina ba. ahmad yace daga ganin yadda take jin kunyanka tana sanka. abba ya kalli ledan da ke dauke da dunkunan su bushiran, yace ina xatan yau xasuxo amsan kayansu, dan tun jiya nace suxo.ahmad yace to in sunxo kayi qoqari ka fada mata mana, indai ba ragon namiji kake ba. abba ya tsurama qasa ido yana tunanin in sunxo mai ce mata? kusan awa biyu sukaje sukai sallan axahar, tungan motan ta tsaya yasan tasu bushurane. shi kadaine a shagon sauran basu dawo ba. bushura ta shigo da qannansu da yarsu aisha. ya taresu da faraa, suka gaisa kan bushura na qasa, sam bata iya kallan abba tela kamar yadda suke kiranshi. Ya tura masu kayansu suka duba sunata murna dan ya masu wadda sukeso. aisha ta aje masa cikon kudinsa kan table. har sun fita yagadai baxai iya hakuri ba, yace bushura xo gashi. ta juyo tana dariya taxo. yace bushura inasan na fada maki wata magana gashi kuna sauri ko? ta kalli motan tace fada min. yace kina sona? ta xare ido sannan ta ruga da gudu. gabanshi na faduwa, bata tsaya ba sai mota. ya kwantan da kanshi akan keken yace menene maanan gudun da yarinyannan tayi? ya tambayi kansa, qarfe uku sunada lecture, amma baya xatan xashi makarantan. ahmad ya dubi abba wanda daga ka dube shi xakasan yana kin damuwa. yace wai banaga sunxo ba? ko ba motan su bane? shiya bandawo ba nakuma hana yaran dawowa dan ku sasanta. abba yace um, inaga yarinyannan gara na haqura, dan bana san insa kaina cikin tunani. ahmad yace ban gane ba, abba yace, to naga daga tambaya tana sona, saita kwasa da gudu ta shige mota. ahmad yayi yar dariya sannan yace ,amsan ta baka. tana nufin tana sonka. abba ya harare shi kada ka maidani dan iska, ina ta magana ta xabga da gudune shine tana sona? yace jeka tambayi manya .yaci gaba da cewa kaine baka mata magana da hikimaba, ka fito mata kai tsaye baka sakaya ba. abba yace, kai nifa ka sanni ba ruwana da wata kwana kwana, idan abu yayi min bana kwana, inko bai min bama haka, ni ba ruwana. Ahmad yace sai xurfin kici ko? da ya aka shawo kanka ka fada mata,abba ya mike tare da kallan agogo, yace inada lecture. gida ya nufa dan shirin xuwa makaranta, har yayi kamar ya tambayi ummanshi cewa in ka ce ma mace kana sonta taji kunya ta gudu wai alamun so ne? sai kuma ya kasa, yana jin nauyi amma in bai samu wata manufa ba dole yaxo ya tanbaye ta dan baya boye mata komai.bushura yar ahj sale ce kwamishinan gona na wannan xamani, gidansu yana karkasara. danqareran gida ne ginin xamani, sun san abba ne sanadin dinki da yayi wa wata qawansu jamila.dinkin yayi matuqan birge su dan haka suka fara kawo masa dinki, tun ranan da ya fara ganin su bushura ta kwanta mashi a rai. to ashe ita ma yamata.shiyasa yau daya furta mata take ganin kamar anmata gafara da aljanna.wata xuciyar tace ,to yanxu da kika gudu in ya xaci baki sansane fa, nan take hankalinta ya tashi har tana rayawa ga abba can da wata.dan haka taga dolene ta koma gun sa inhar tana sansa. dan tasha ganin mata na masa tayin kansu in sunxo kawo dinki.nan ta soma tunanin wace dabara ce xatayi ta fita?saiko ta warware daya siket din kayanta cikin dare.da safe ta nunama momynsu tace mata telan ya manta bai hada wannanba,dama yace xai gwada nine kafin ya hada.momy tace direba ne xai kai mashi.bushura tace momx xaifa gwadani ne muje dai xa kaini.tace to kuje, bushura ta danyi gayunta suka tafi.saidai kash! bata samu abba ba ance mata yana gida. tace gidan da nisane, aka ce mata babu nisa,dan haka ta sa aka rakata.tacema direbansu tana xuwa telan na gida.gidan ba nisa. A qofar gidan su abba ta tsaya, sai ga ummi ta sheqo da gudu tana dawowa daga aike.ta tsaya tana kallan bushura, sannan tace lafiya?bushura ta dubeta. yauwa abba yana nan?budan bakin ummi sai tace yaje kashi ya fada a masai.bushura ta dafe qirji, yaushe? ummi tace oho.sai ga abba ya futo sanye cikin shadda bulu mai duhu yana ta qamshin turare.shawara ya yanke lkcn da yake xaune a shago kan cewa yaje gidan su bushura,tunda gidan kwamishina ba boyayye bane,suka hada ido da bushura,ta saki faraa sannan ta dubi ummi,kince ya fada ina? ummi tayi ciki da gudu.ya bita da kallo sannan ya kalla bishira,me tace maki?bishira tace, ba komai.saidai dariya da maganan ummin tabata.yace tunda baxaki fada min ba xomuje ki gaida ummana.cikin muryan jan hankali tace ina jin kunya.ta bude jakanta tace kamanta baka dinke wannan siket dinba.yace mugani,yaga yadda aka warware shi aka cire xaran da kyau. murmushi yayi dan yasan ya dinka siket din,kusan shinema na farkon dinki.ya gane yaran nata qila san ganinshi take san yi. Ya dinke siket din yana cewa"to amma sai dai ayi min izini inzo gida in kawo da kaina in na gama." tace haba dai,ya za ayi in taso ka?"ya ce,"ba komai,in dai anyi min izini sai inzo," ta ce,"to in maka kwatance?" ya ce,"a'a huta kada ki bata bakinki,nasan gidanku zanzo anjima bayan tarawih." ta ce,"to." sai mun zo" tace"ku dawa? ya ce,"abokina mana,kinga zo muje gurin ummana ku gaisa." Bishira ta bishi cikin jin kunya.tun kafin su shigo daman ummi ta shiga gurin umman da gudu tace mata"umma ga budurwar yaya Abba." Umma tace budurwa kuma? tace eh ai zama su shigo.daga nan ta kara kyallawa dakin tsohuwa tana fada mata. Umma dai jim tayi dan bata da wani burin da ya wuce ta baiwa Abba ummi,kuma da tasan har zai ga wata can da wuri haka data fada masa kudurinta,sa tay 'ZURFIN CIKI' gami da nauyin baki....... sallamar Abba ce ta katse ta ta ce,"shigo Abba." ya ce Umma bakuwa ce taxo gaisheki.Umma ta fadada fara'arta tace to shigo,ba dai surukar tawa bace?" ya ce,"ai ita ce kam" Bishira ta shigo tana sunne kai,ta gaida umma Umma ta ce,"masha Allah,Allah yasa rabon muce."Abba yana dariya ya ce,amin ummana."ya dubeta,"tashi ki gaida kakata." suka nufi dakin tsohuwa,umma ta jinjina kai .tabbas Abba nason yarinyar,in ta dubi yanda yake fara'a da zumudi. a fili ta ce,"Allah yayi mana zabin alkairi."ummi na kwance kanta na cinyar tsohuwa,sai ta kalli bishira ta tuntsure da dariya,lokacin da suke gaisawa da tsohuwa. Abba ya ce,"dariyar uban me kike yi?" sai ko ummi ta sake shekewa da dariya. ya nufota ya suri kafafunta,tsohuwa ta ce haba mai sunan malam yanxu in bata yi dariya ba kuka zatayi?" ya ce,Bishira tashi muje" Tsohuwa tace to yanmata mun gode ki gaida magabatan naki,sannan kiyi ta hakuri da halin wannan miskilin." Umma ta ce,"tsohuwa kodai kishi ne?suka yi sallama,ummi wadda tunda ya shureta ta rigasu fita sai ta dauki takalmi Bishiran guda daya takai soro (zaure). don haka da suka fito suka shiga nema ummi ta kule uwar dakin umma tana ta dariya tana lekensu. Abba ya ce,"ummi! ummi!!" taki amsawa ya nufi waje da niyar dubota don yasan ita ce zata dauki takalmin,sai ga takalmi a kofar shi. Don haka ya dauko kawai ya dawo ya bata umma ta ce,"ka kaita su gaisa da umman Bashir." Abba ya ce,"a'a ba yau ba."ya rakata wurin direbansu,kusa da shagonshi sukayi sallama da alkawarin zai zo washegari. yaje kuma bishira ta fada masa lallai tana sonsa sai dai tana tunanin iyayenta ko zasu amince? ya ce,to shi dai zai turo magabatansa su nemar masa izinin zuwa zance kamar yanda yake a shari'a Bishira tace a'a ya bari tunda yanxu shekarar farko take a babbar sakandare(s.s.1)ba za a bari ya dinga zuwa ba,amma zasu dinga haduwa gidan yarta dake na'ibawa. Abba baida zabin da ya wuce ya yarda da hakan tunda tace baza a barta yin tadin ba.sai dai fargabar shi kada nan gaba sunyi zurfi cikin soyayya ace ba za'a bashi ba. ta ce,"Babana bashi da matsala,amma momy dinmu ce abin tunani."Abba ya ce,"shikenan Allah ya shige mana gaba." soyayya ce mai karfi ta kullu tsakanin Abba da bishira,wanda har ummanshi da kanta tasan cewa Abba yana son yarinyar. Domin duk lokacin da zaije gurinta tana lura da zumudin da yakeyi,kazalikain tace ka gaida surukar tawa, bakinsa baya rufuwa. Don haka sai ta tattara batun ummi ta aje a gefe addu'a ce kadai bata daina ba.ana sauran kwana uku sallah.Abba ya siyo fenti yazo da mai fentin nana ak fente gidansu ciki da bai. Da yamma kuma ya kawo dinkunan su ummi da fati,ummi tasa ihu,sam irin dinkin da ta aro gurin kawarta Amina ba shi yayi mata ba,ya zai mata dink iri daya da fati? ya ce,"kin isa ki sani in miki dinkin da kike so?ta ce to ni dai bazan sa ba umma ta rafka salati tana kallon ummi ta ce,"ummi kina da hankali kuwa? kudi kika biya ko ko Abban sa'anki ne?" tace cikin kuka to ni umma ya zai min iri daya da fati? ya dubeta a fusace,"in kin bari na dauki kayannan wallahi bazaki sasu ba." Umma ta ce,"ni da zaka daukesu ma da naso"tsohuwa ta fito ta ce,"saboda me? akan wane dalili zaka amsar mata kaya?tunda baka mata wanda take so ba sai ka kyaleta." Da hannu Umma tayi mishi alamar yayi shiru,sannan ya fita waje.Abba ya kada kai ya fita. washe gari kuma ya shiga da me fenti har cikin gidan Alhaji karami,sahura tana daki lokacin da yake nuna ma mai fenti guraren da zaya fara. Ta fito daga daki ganin Abba sai ta hade rai sannan ta ce,"mune kashin baya? ai dama ka bar shi tunda baka mai da mu wani abu ba,mu ne dai baka so din mahaifanka. Ta dalilinmu zaka shiga aljanna,ba dalilin wasu banzaye ba da sauri ya nufi hanyar fita waje don baya son yaji zagin da zata yiwa Alhaji da Ummanshi. wannan na cikin dalilin dayasa baya son zuwa gidan Alhaji Babba da Umma,sune suka ci kashi da fitsarinsa. suka bashi tarbiya da ilmi,suka ci da shi suka shayar dashi.amma sam basa yi masa abinda umman Bashir ke masa. haihuwarsa ce kadai su Alhaji babba basu yi ba,sahura tana zuwa har shago tayi masa rashin mutunci,sannan ta ce ya bata kudi,ta ce ya ba bashir kudi ko ta aiko fati. Bai taba kin bata ba,amma duk da haka bai tsira daga zagin rashin mutunci ba.ta ce ya tare a gidan ummanshi komai nashike mata,wai da kuma sam ba haka bane. Umma bata taba tambayar shi sisi ba,haka nana duk lokacin da ya bata wani abu ko ya sai mata,sai tace ina na umman Bashir? kaje itama ka bata,in ko bashi da yawa ni naci girma ka bata. Ranar sallar idi kuwa ummi koda tayi wanka kin saka sabon kayanta tayi sai na bara. Lokacin da zasuje sallar idi,Abba ya fito daga wanka ya kalleta ina kayanki sabo? ta tura baki"ni baxan sa ba." Yace,"to zanga wanda zaki bi masallacin,kuma ki kara magana saina fasa bakinki."sai ta wuce kofar dakin tsohuwa,sannan ta ce,"to ai dai nima nasan hanya,kuma sai naje."ta fada dakin da gudu. ya bita bata san yaga tsohuwa lokacin da ta shiga wanka ba,bayan fitowarsa.don haka ya ritsa ta ya kwakkwada mata mari,sannan ya rike mata kunne. zan kara fada ki fada? ta ce,"a'a kayi hakuri." ya saketa ya wuce,ta zauna tana kuka. misalin karfe hudu na rana ,bishira ta iso shagon dinkin ita da direba,shagon a rufe.don haka ta ce su karasa gidan. Can dinma baya nan,amma sai ta fito ta shigj gidan dauke da tire babba cike da kuloli. cikin kunya ta gaida umma,ta kuma bada a aje masa.umma ta ce,"to ko ina Abba yayi? kila gidan su Ahmad yaje."umma ta ce,"ke uwar gudu ina yayanki?" ta ce,"nima na ganshi?" karar bude kofarshi suka ji,ta ce,"leka in shine kice yayi bakuwa.shine kuwa,jin cewa ga bishira ya shigo da zumudi. Umma tace ka kaita ta gaida umman bashir. yace to, ta fito ta tafi kicin ta bar masu dakin,ashe ummi tana uwar daki tana jinsu.ya ce,yanxun fa daga na'ibawa na ke,ina ta xumudi in ganki. tace,na xaci ba xa kaxo ba ne,nace bari inxo ni,dan baxan iya kai dare batare da idanuna sunganka ba.ummi ta toshe bakinta saboda dariyan da yakesan kufce mata,yace sai inga kamar bakya sona.bishira tace haba abba, in kace haka bakamin adalci ba.yace to wadannan kulolinfa me kika kawo min?ta ce bude ka gani.ya bude ya gani yace kai, lalle ashe ni dan gatankine? tace sosai ma.ya marairece murya yace to bani abincin a baki.ummi daga cikin dakin tace, la'ilaha illallahu.abba ya miqe da sauri.kafin ya ankara ummi tayi fitan bindiga tsakar gida tana fadin la'ilaha illallahu,dama yaya abba dan is....umma ta gwabe mata baki,bayan ta fito daga dakin ahj babba.ummi wadda inta s6a magana ko ana hanata sai ta kai aya.ta dafe baki,tace maci gaba da fadin,umma to kinji abinda yake ce mata ne? umma ta jefeta da takalmi tare da cewa,wai baxa kiyi min shuru ba? ummi tace,to fa cemata yayi xai bata abinci a baki,kuma daman xan nuna maki wani kaset da yake kallo. Abba ya riqe kai tare da cewa ummi in na kamaki xaki sani, kaset din wa kikaga ina kallo? tace na yan is....da gudu ya bita ,yayin da umma ta jefa mata murfin kwano,amma duk haka ko da ta fita waje saida tace masa sai na nuna ma ahj kwalin kaset din.take ya tuna da kwalin kaset din daya boye,wanda ya qwace a hannun bashir,kaset din tsiraici ne wanda laanannu sukayi.abba cikin takaici yace,kai ummi! kai ummi!! kinsan allah in kina wasa dani xa karyaki a banxa.ta ce to ba a dakinka na gani ba?yayi qwafa,allah ya sani ya tsani ummi kamar ya shaqeta ta mutu.sai ya samu kanshi da qin komawa gidan,kunya da nauyin umma yake ji,yasan dai ba xata kama xancan ummi ba,amma yasan xuciya da xargi,qila xuciyanta ta xargi wani abu.bashir ya fito daga cikin gidan su abba yace,yauwa bashir shiga gidanmu kace bishira taxo. Bashir rai bace ya shiga,dan yana jin haushi ya amsar me kaset.ya shiga umma na qofar kicin xugun tana tunanin halin ummi.bashir yayi sallama umma ta amsa.yace,abba ne yace in kira bira ne ni yace ne?umma tace gatanan ciki,taxo bakin qofa ta kalli bishira kanta na qasa tana mamakin ummi.yarinyan sam bata ji.umma tace kixo yana kira awaje.cikin kunya ta fita, yace da bashir rakata gun ummanka su gaisa.bashir yayi fara,a antynace ke nan?abba yayi murmushi. bishira ta xauna gaban ummansu bashir suka gaisa. bashir yace,budurwan abba ce. sahura tace,yau kika taba xuwa nan unguwan? kanta na qasa tace, xuwana biyu kenan.ta kalli bashir tace kaji ko? amma shine ko a turo ta nan gidan.nina haifi abba amma an gaje min shi.tace yarinya duba nan.bishira ta dubeta,ta dafe qirjinta ni na haifi abba nine uwansa.matan gidan can mai gidana ya bada shi a gunta,da ubansa da maigidan dan wa da qani ne amma sun gaje shi.bani da ikon sashi ko hanashi amma sun mallakemin shi. da muryan tausayi take maganar. Bashir yace, umma indai ya aurota xamu samu sauqi.bishira tace kada ki damu, insha allah komai xai warware. tace, to yan nan na gode.fati ta shigo ta gaidata cikin nutsuwa, bishira tace wannan qanwansa ce? umma tace eh, ai su ga sakamakon mugunta nan sun haifi yar muguwa mara jin magan. bishira tace, kai yarinyar bata ji. fati ta ce abba ya ce kixo.sahura tace kinji ko? shifa ko nan gidan baya qaunan shigo wa.bishira ta miqe ta balle jaka ta ciro sabbim kudi yan ashirin ko irgawa bata yiba ta bata, tace kinsaya goro.sahura tace harda abin arxiki?to an gode.bashir yace antyna inane gidanku?tace karkasana gidan kwamishinan gona.bashir ya raxo ido, nako san gidan,lalle antyna ina qara gaisuwa.bishiratayi dariya.abba na tsaye suka fito,yace mata to ki tafi xanxo amjima. tace baka kaini dakinka ba.ya girgixa kai, bai dace ba wannan ba mutunci bane,sam bai kamace yar mutunci suna xuwa dakin samari ba. bishira tace danme? yace sharia bata amince ba, damin duk lkcn da mutum biyu suka kebe,musamman mace da namuji. Abba yace na ukun su shedan ne. irin wannan yana haifar da xinace xinace a bayan qasa.tace hakane ta tafi.abba ya rakata har mota, bashir kuma tamkar maroqi, sai fadi yake allah ya tsare antina ki sauka lfy.bayan tafiyanta abba bai iya shiga gidan ba tunaninshi daya kada umma ta xargeshi.dan haka ya nufa gidansu ahmad.ya ba ahmad lbrn abinda ya faru.dariya ahmad yayi tayi.yace kai amma wannan ummin taku yar dirama ce. abba yace cikin takaici yanxu kai har kaga abin dariya?yaja tsaki yace allah na tsana ummi, namata muguwan tsana. dubi wannan yarfin da tai mani. ahmad yace xata bari, wata ranama ko ance tayi watace sam batayi ba.abba yace taf wannan yarinyan dawuya in xata taba yin hankali, duk wanda ya aureta ya auran ma kanshi fitina.ahmad sai dry yakeyi. da magariba ya shiga gidan,cikin saa ya samu ummi tana cin abinci.nan take ya kama hannun ta har saida tayi yar qara, yace muje ki dauko min kwalin kaset din da kika dauka, Umma tace, Abba na soma tunanin yarinyar nan tan da aljanu da gaske. abba yace hakama alhaji qarami yace, amma fa anje babu kowa akanta. ya saki ummi bayan ya ranqwasheta. sannan ya ce, in kika sake yarda ki kaga wani abu a dakina kika dauka sai na balla ki. washegari abba ya tasa ummi ya nufi gurin masu ruqiyya, amma da aka mata babu kowa a kanta kamar yadda ya xata. ya dawo ya sanar da umma,umma tace na gode allah.halinta ne ita kuma irinta kenan? yace irinta kenan umma,baxata canxaba saidai muyi ta mata addua, soyayyan abba da bishira ta bunqara,har dangin abba sun san da batun,sahura duk tabaxa ma dangi.sanadiyyan maganan da tayi ma bushiran na cewa an rabata da daxta. wata rana bishiran tace masa xata xo gaida ummanshi,yace to cikin xumudi sai tace, umman su bashir fa nake nufi, ba ance ita ce mamanka ba? abba ya ce inji wa? inji ummanka. abba yace sam, ummana ba xata fada miki ba sai dai ko ita umman bashir din. tabbas itace ta haifeni, amma ba itace ummana ba.tace dan me? nan take ya hada rai. Abba yace mata ba matsalanki bane, so ban so ki saka kanki ciki. nan take ta yarda da batun umman bashir.ta a mince qwarai umman da abba ke kira umman shine muguwa ce.kuma itace ta raba abba da umman shi.dan haka saita tsiri xuwa gun umman bashir, tare da yi mata kyauta.shiyasa suka saba sosai.duk xuwan da bishira xatayi sahura saita kukkushe umman abba, tare da yi mata sheri. dan kawai bishira ta tsaneta,kuma bata xuwa gunta koda taxo anguwan. abba bai taba sanin haka ba,ita kuma umma bata taba fadan mai ba, dan ummi ta taba fada mata cewan budurwan abba tana xuwa gun umman bashir kuma bata xuwa gunki. umma tace nida umman bashir duk daya ne intaxo gunta tamkan taxo guna ne. sai kuma habaicin da take jiyowa ta katanga sahura nayi.har ya kai umman abba na ganewa in bishira taxo, domin inxata tafi xakaji umman bashir tana cewa,to na gode yar albarka bakya gajiya da abin arxiki,ai ko baki kawo min komai ba yancina da kika fara qwato min kin biya ni. kuma ina tabba tan maki inkinga abba bai aureki ba baya ry/ ZURFIN CIKI book 1 part 4</p><p>ZURFIN CIKI book 1 part 4</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 21:45</p><p>Wannan furucin ke sa bishira na qara shige ma</p><p>sahura, duk wannan sha'anin da sukeyi abba bai</p><p>sani ba. wanci tashi abba ya samu digree,</p><p>sannan yaje kamp din shi a damaturu jihar</p><p>yobe.sati biyu yayi sannan ya dawo. cikin sati</p><p>biyun nan da baya nan ummi ta baxa iya</p><p>shegenta son ran ta, umma ta qosa abba ya</p><p>dawo saboda yanxune ta gane tsoran abba yake</p><p>sa ummi tayi mata aiki da aike.dan tasan in ya</p><p>sani baruwan shi da pushin tsohuwa,xai</p><p>nakadetane, amma ahj da umma duk abinda</p><p>ummi tayi daxaran xasu hukunta ta xata sa masu</p><p>kuka tace dan de aci mata xarafine.shi yasa suka</p><p>sakama ummi sunanta,sannan kuma suke</p><p>dukanta a gabanta,imba hakaba maisa basuyima</p><p>mai sunnan malan ba?dan dole suke qyaleta ,duk</p><p>da ummi ta soma tasawa amma sam bata yi</p><p>hankali ba. shekarun ummi sha uku tana js2</p><p>amma ko yaushe qara tirewa ummi keyi. addua</p><p>kurun sukasa agaba,kuma sunsan allah xai amsa</p><p>masu. Ranan da abba xai dawo ummi ta kama</p><p>yima umma aiki da aike, dan kar a fadama abba.</p><p>a ranan ne ummi taga wata alama da ta</p><p>tsoratata cikin fitsarinta. a rudenta da hauka ta</p><p>nufi gun umma tana cewa, umma na shiga uku</p><p>na, fitsarin jini nake yi. umma tace, wane irin</p><p>kuma fitsarin jini? ummi sai tsalle take tana fadin</p><p>ta bani ta lalace. umma tace ke xonan. ta jawo</p><p>ta xuwa cikin daki, tace ke yimin bayanin yadda</p><p>kika ga abin. ummi ta cire xani xata cire siket.</p><p>umma tace, ke dakata min bance ki nuna min ba,</p><p>yaya kalanshi yace? ko da tayima umma bayani</p><p>sai ta fahince girmane ya kama ta. dan haka sai</p><p>ta kamo ta ta xaunar kusa da ita, tayi mata</p><p>bayani game da abin data gani, sannan ta nuna</p><p>mata hadarukan da take ciki a halin yanxu. tace</p><p>ummi ki natsu kiyi hankali, kisani yanxu kinkai</p><p>wani matsayi wanda xakiyi taka tsantsa da</p><p>rayuwanki. hadari na farko shine wasan banxa da</p><p>maxa, kece mara hankali indai kin sama abokin</p><p>wasa ba ruwanki da maxane ko mata ke dai kiyi</p><p>wasa, Umma tace kisani yanxu xaki iya daukan</p><p>ciki, indai har kika bari wani namiji ya shiga</p><p>harkanki. ummi tayi xullo tace umma ciki irin na</p><p>bara'atun baito? umma tace, eh ummi tace</p><p>wanda har suka yar da yaran aka xo aka kama</p><p>su yan sanda? umma tace tabbas. ummi cikin</p><p>fargaba tace to ni umma baxan yi ba. ta soma</p><p>kuka, to a kaini asibiti a bani magani mana.</p><p>umma tace duk bayanin dana maki baki fahinta</p><p>ba? ai wannan kin dunga yinsa kenan har</p><p>qarshan rayuwanki, ko kuma in kinkai wani</p><p>mataki na tsufa. ummi tace, to shi kenan, yanxu</p><p>kuma inna yi wasa da maxa sai in xama irin na</p><p>bara'atu? umma tace qwarai kuwa. ummi tayi</p><p>tagumi tana tuna yadda suke tsokanan bara'atu</p><p>inta fito. suna cewa tayi cikin shege tayi cikin</p><p>shege! ta dubi umma tace xan daina ma yan</p><p>maxa magana. umma tace ki dinga maganarki da</p><p>kowa, kidai kula da kanki, sannan duk sokanan da</p><p>kikayi da xunubin da ki ka kwasa to fa ki sani an</p><p>bude maki fayel. Umma tace xunubinki xaki</p><p>samu,gashi bakya san sallar kan lkc, sannan ga</p><p>karya axumi.ummi ta sake tsurewa ,tare da fadin,</p><p>to ba tsohuwa tace min inna mutu baxa ayi min</p><p>hisabi ba,wai ni yarinya ce wai makarantan</p><p>annabi ibrahim xa a kaini.umma tace da kenan</p><p>kafin ki soma kalar wannan fitsarin, yanxun kam</p><p>in kin mutn xa a tambaye ki a cikin kabari,</p><p>tambayoyi uku masu sauqi, masu wuya agun</p><p>mara rabo.sannan xa a maki hisabi inkinyi mai</p><p>kyau kiga mai kyau. tayi tagumi, umma ta manna</p><p>mata tsumma a jikin pant. tace tashi kisa in</p><p>kuma kinje gun haukan guje guje ya fado mutane</p><p>sun gani shi kenan asirin ki ya tonu, kowa yasan</p><p>kin girma. ummi dai ranan lafewa tayi kan kujera</p><p>tanata tunani. tana kwance lkcn da ake hayaniyan</p><p>dawowan abba kannanshi ne suka shigo mai da</p><p>kayansa. qasa ya xauna a dakin umma, ya miqe</p><p>qafa domin duk a gajiye yake. umma tayi ta dire</p><p>mai abubuwan ci wanda tasan yanaso a gaban</p><p>shi. sannan ta ba fati kudi ta sayo mai lemun</p><p>kwalba, dariya yayi ya ce,ni dan gatane, shiyasa</p><p>ina can ina tunaninki ummana, har nace inama</p><p>ana tafiya da uwa da na tafi da ke.umma cikin jin</p><p>dadi tace allah sarki abba, niko ina nan ina maka</p><p>addua allaih ya baka abin da kaje nema,yace</p><p>ummana kenan. ummi dai tana jinsu sam baima</p><p>gantaba, sai can ya lura yace a,a kekuma lfy?</p><p>umma tace bata dan jin dadine. yace tabdi,lallai</p><p>kuwa ciwan nan yayi tsanani, ummi da ko a</p><p>gadan asibiti take bata daina halinta? umma tace</p><p>ai yanxuma nasan lafawa yayi ko ummi na?</p><p>ummi dai kallansu take yi. abba yace allah ya</p><p>yaye. suka ci gaba da firan su yana bata lbrn</p><p>camp tare da nuna mata hotunan da suka dauka.</p><p>yace dan ba kusa bane da kunje min kunyi kallo.</p><p>ummi da xata bayi sai tafiya take wani iri tare da</p><p>ware qafa. saboda rashin sabo. tsohuwa tace a,a</p><p>takwara lfy? ummi tace, fitsarin jinin nake yi.</p><p>umma ta fito da sauri tace ke ummi xo. tsohuwa</p><p>ta saka salati, tare da cewa yarinnan nan badai</p><p>faduwa kikayi ba. ummi tace nifa ban fadi ba</p><p>hakanan ya xo min. umma tayi mata daquwa</p><p>tace bayin kenan? tsohuwa tace ke suwaiba</p><p>yarinyan nan faduwa tayi? da yake umma ta</p><p>fahinci hausanta sai tace um,lkcn tane yaxo.</p><p>tsohuwa ta saka salati tace, ni habiba yau naga</p><p>abinda ya isheni? yarinyan yar shekaru nawane</p><p>kwata kwata. lalle xamani, to sai ayi axaman</p><p>aurad da ita. umma tace waxai kula ummi da</p><p>sunan aure ni suwaiba? ki kalla haukan data keyi</p><p>a gari. abba cikin daki yace umma wa tsohuwa</p><p>take cema ayima aure? umma tace ummi itama</p><p>cikin dariya. yace tabdi jam to wannan takwaran</p><p>taki waxai kwasa, ga muni ga rashin hankali.daga</p><p>bayi ummi tanata murguda mai baki tana cewa</p><p>eh din. Tsohuwa kuwa masifa ta hau yi,"gaka nan</p><p>mara mutunci a gabana kake zagin takwara?kai</p><p>mai sunan malam ka kiyaye ni" shi dai ya fita ya</p><p>nufi dakinsa don kintsawa,yana mamakin ummi</p><p>ta zama babba. Koda umma bata fada mishi ba</p><p>ya gane haka ne ta yadda tsohuwa tayi maganar.</p><p>tsohuwa ta dubi umma ta ce,"ki na daure ma mai</p><p>sunan malam gindi yana ci ma takwara kashi a</p><p>hannu,alhalin yana zaune a inuwarta.nan fa gidan</p><p>ubanta ne." umma ta bata rai matuka,ta ce</p><p>"tsohuwa ni da Abba da ummi duk daya suke a</p><p>gurina,don Allah kada ki kuma furta haka har</p><p>Abba yaji. kai ni da za a ce in zaba tsakanin</p><p>ummi da Abba,na rantse Abba zan dauka."bata</p><p>jira abinda tsohuwa zata ce ba,tayi ciki abinta.</p><p>tsohuwa ta gama yan mitocinta ta shiga daki.</p><p>Kwana biu kamar gaske,ummi an nutsu, amma</p><p>abinda ya takura mata na daukewa sai umminku</p><p>ta ci gaba da gashi, sai ma abinda ya karu. Abba</p><p>ya daga ido sama yana kallon wasu tsuntsaye</p><p>suna ta shawagi a sama, zuciyar shi tana cikin</p><p>matukar damuwa sakamakon sheshshekan kukan</p><p>da bishira keyi, bata san cewa ya fita damuwa da</p><p>tafiyarshi kaduna ba? in ma da don ta ita ne da</p><p>sauki tunda gidansu da waya zai iya zuwa</p><p>(telephone) na bakin titi ya kirata. damuwar shi</p><p>umman shi. ta katse shi "yanxu Abba haka zan</p><p>daina ganinka?" ya sake tausasa murya."haba</p><p>bishira, ina kano ina garin kaduna?" ta ce, "tabdi,</p><p>nifa dalilin kukana taron matan kaduna nake ji, an</p><p>ce kwarjini garesu. kawai kaje ka sa samu wata</p><p>ka manta da batuna." Yayi murmushi "bishira</p><p>kenan, kada ki dauka son da nake miki mai rauni</p><p>ne da har zan canza wata dake, ni dai ki min</p><p>addu'a." ta ce,"sam ban yarda da wannan zancen</p><p>ba, ni dai bari in kira antina mijinta zai iya</p><p>taimaka maka a barka kano." kafin ya ce komai</p><p>tayi ciki da gudu. yayi yar dariya. bishira tunda</p><p>ya ce kaduna aka tura shi duk ta damu. Anti ta</p><p>fito daga kicin, bishira ta ce, anti kizo inji Abba.</p><p>anti ta dubeta, "in zo?" bishira ta kama hannunta</p><p>"don Allah aunty taimako zaki mana, zo ki ji." 49-</p><p>suka xauna sannan abba ya gaidaa anti cikin</p><p>girmamawa.bishira ta dube shi ka fada</p><p>mata.abba yace me?tace anti kinga fa kaduna</p><p>aka tura shi,ni kuma wlh ba xan so yaje garin nan</p><p>ba.anty ta sa dariya.to yanxu so kike yaqi xuwa</p><p>ko so kike ya tafi dake? tace,ni so nake ki yima</p><p>abban nasir bayani,nasan ba xai rasa sanin wani</p><p>da ya sani ba.abba da anty suka sa dariya,yace</p><p>kamar yaya?tace yayi magana a barshi anan</p><p>suka sake tuntsira dariya.tayi fushi ta miqe fuuu</p><p>ta nufi cikin falon gidan.anty tace bishira tana</p><p>matuqan sanka,dan allah ka kula da ita.ya kalleta</p><p>ya sunkuyad dakai,yace nima anti ina santa,kuma</p><p>tuni nasa manya susan xancan,saboda in samu</p><p>natsuwa,amma tace tana jin tsoron</p><p>mamanta.anty tace eh to,dole taji tsoro dan ba</p><p>dole bane hjynmu ta yarda,amma shi babanmu</p><p>bashi da matsala.abba yace to ni dai xan tura a</p><p>kowane lkc,dan ahjna yayi min magana tun kafin</p><p>tafi ta camp. Din nan yake ta min zancan." Aunty</p><p>ta ce,"to in kun tashi fa ba gurinshi za'a tura</p><p>ba,gurin kaninshi ne dake jakara.amma kafin</p><p>hakan sai an nemi izinin Alhajinmu din." Abba ya</p><p>ce,"to ni ko wa zai shige min gaba gurin neman</p><p>izinin?"aunty ta ce,"Abban nasir zan sanar</p><p>dashi,insha Allahu har wannan din ma batun</p><p>(service)din naka zan mishi bayani." cikin murna</p><p>abba ya ce,"to na gode,Allah ya saka da</p><p>alkairi"anty ta ce,"ba komai" ta mike "bari in turo</p><p>ta don nasan tana can tana cika sai ka bata</p><p>baki." yayi yar dariya tare da cewa"to". ta zauna</p><p>tana kumbure-kumbureya ce"haba tawan har</p><p>yanxu baki huce ba?" ta sake kauda kai gefe,ya</p><p>ce"to shi kenan,yanzun dai na fasa barin</p><p>kaduna." ta dube shi da sauri,"ka fasa barin</p><p>kaduna fa ka ce?" yayi yar dariya"au na</p><p>manta.kece duk kin ruda ni,cewa zanyi na fasa</p><p>barin kano." ta share yar kwallarta,"to shikenan"</p><p>ya ce,"naji dadin kiran anty da ki ka yi.ina ganin</p><p>nan da yan kwanaki su Alhajinku zasu sanni,Allah</p><p>yasa ace an bani ke." Wayyo dadi,ta tuntsure da</p><p>dariya.abbana nawa,bana zaton cewa zaka kai ni</p><p>murna a ranar."ya mike zan tafi "ta ce tun</p><p>yanzun? to ka ce ina gaishe dasu umma." Ya</p><p>ce,"umma bata cin mike,kullum sai ta ci in gaishe</p><p>ki da kyau.amma ke kin ki zuwa gaida ta." ta</p><p>ce,"kasan fa ni bana iya sakewa da ita,nafi</p><p>sakewa gurin umman bashir." ya ce,"kunyarta ki</p><p>ke ji?" ta dan tabe baki tare da daga kafada kila.</p><p>ya ce,"ina mamakin yanda kika saba da umman</p><p>bashir,alhalin ummana tafi saukin kai." ta ce,"ga</p><p>wannan kanwar taka mara kunya." ya yi yar</p><p>dariya sabida tuno abind ummi ta musu. ya ce a</p><p>hankali,"zaki saba da halin ummi."ta dube</p><p>shi,"tun ranar dana soma ganin ummi din nan fa</p><p>ban taba jin cewa ina sonta ba." ranshi yadan</p><p>sosu,har ma ya gimtse fuska,amma baice kala</p><p>ba.lura tayi da canzawarsa.don haka sai ta ce"ka</p><p>min afuwa in na bata maka." nan ma bai amsata</p><p>ba.illa sai da safe. Tamkar Alhaji yasan yadda</p><p>abba suka yi da antin bishira,da safe Abba yaje</p><p>gaida shi ya ce,"babana zuwa yanzun ya kamata</p><p>a ce mun shiga maganarku da yarinyar nan."</p><p>Abba ya sunkuyar da kai tare da ce wa,"um,dama</p><p>gidan antinta da naje dazu munyi zancen,yanzun</p><p>dai su ce sai an nemi izinin shi baban nasu. ta</p><p>ce,mijinta zai masa magana,in yaso sai kuji ranar</p><p>da zaku je din." Alhaji ya ce,"to shikenan.Allah ya</p><p>kai mu.yanzu yaushe zaka tafi kaduna?" kafin</p><p>abba ya bashi amsa,ya ci gaba da cewa,ban so</p><p>ba sam da wannan yin nisan da zaka yi damu</p><p>Abba." Abba ya ce,"ina hasashen cewa za a barni</p><p>nan kano da yardar Allah,bisa ga taimakon mijin</p><p>yayar yarinyar da nake zuwa gurinta." Alhaji ya</p><p>ce,"to Allah ya yarda,sannan in an fada maka</p><p>lokacin da zamu gana da waliyyan nata sai ka</p><p>sanar dani." Abba ya ce,"to." Alhaji ya ce,"ina son</p><p>mu danyi bincike kan yarinyar amma mahaifinta</p><p>sannanne ne,anata yabonshi." Abba ya ce,"to."</p><p>Ranar juma'a da misalin karfe biyu da rabi Alhaji</p><p>ibrahim (wato abban nasir,mijin anty farida),ya</p><p>samu sirikinsa a gida. bayan sun gaisa ya</p><p>tambayi yan jikokinshi sai Alhaji ibrahim ya</p><p>ce,"suna lafiya.dama makasudin zuwan shi</p><p>ne,akwai wani yaro da ke zuwa gurin</p><p>bishira,yawancinan gidanmu suke zance. to</p><p>gaskiya na yaba da hankalin yaron,sannan ya</p><p>damu yana son ya turo iyayensa.to shi ne nace</p><p>bari in nemar musu izini tukun." mahaifin bishira</p><p>ya kalli surukinsa ya ce,"aisha ko bishira?" Abban</p><p>nasir ya ce,bishira ce." ya gyara zama. "bishira</p><p>ta gama sakandare ne?" Abban nasir ya ce,"ai</p><p>Alhaji ba yana nufin ayi auren yanzun bane,a san</p><p>dashi ne." Alhaji ya ce,"bana haka,ka sani sai dai</p><p>tayi abu daya,in karatun karatun,in auren to</p><p>auran. Ibrahim kasan wani abu daya? duk lokacin</p><p>da kasa yarinya ta soma tsayawa da saurayi</p><p>bayan tana karatu,musammanirin bishira irin</p><p>wadda tasan tsarina amma ta danne ta turo min</p><p>saurayi to gara ayi mata auren. Domin doguwan</p><p>soyaryannan bata da ma'ana,qarshe sai wata</p><p>shedana ta biyo baya,balantana bishira tana da</p><p>rawan kai.ya matsa kusa da wayan tangaraho</p><p>wadda aka jona ta ke amfani a daukacin gidan,ya</p><p>dannan nanbobin sannan ya kira hjy.ta amsa</p><p>daga sashanta,yace bishira na ciki? tace tananan,</p><p>yace ki turo mani ita,tace to.gaban bishira ya</p><p>badi,ganin mijin yarta a gidan dan tasan abinda</p><p>ya kawo shi.ta xauna can gefe tace,gani dady,ta</p><p>gaisa da abban nasir.mahaifinta yace nasan</p><p>kinsan dalilin xuwan ibrahim ko? kanta a qasa</p><p>tace,a'a. yace.yace to saurayin da ce xuwa gunki</p><p>ne yake san ya turo magabatansa,kuma nasan</p><p>kinsan da batun?sai dai inasan kisan abu daya</p><p>bana san doguwan soyayya,da xara nagama</p><p>buncike akan yaran wanda shari'a tace.inna</p><p>gamsu,to fa aurad dake xanyi kije can ki qarasa</p><p>karatun in kina so.ahj ibrahin yace yaran yace shi</p><p>ba dole sai anyi yanxu ba.nufin shi a amince</p><p>mashi.shi kuma xai jira har ta gama</p><p>makarantanta. ahj ya katseshi ta hanyan daga</p><p>mai hannu,ibrahin kaidai sheda ne bewan bana</p><p>haka, kuma ba a haka dani ko?yace auran yata fa</p><p>kakeyi,ka san tsarina.ibrahinyace na sani ahj.</p><p>yace yauwa,ina nan ban canxa ba.yace yanxu</p><p>abinda nake san ka dashi kafin na amince da</p><p>xuwan iyayan shi.ya dubu bishira yace kinasan</p><p>shi kin amince dashi? tace eh yace tashi ki tafi</p><p>angama.kai kuma inasan kashiga unguwa uku ka</p><p>binci komin labarin yaran da usilin shi.ahj ibrahin</p><p>yace angama.yace naso ace sai ta gana</p><p>karatu,dan sai anyi sa'a xata qarasa,anma hakan</p><p>xaifimin akan doguwan soyayya kafin inxo inajin</p><p>haushi.ibrahin ya miqe to ni xan tafi.ahj shima ya</p><p>yunqura xai tashi sai waya ta kama ruri dan haka</p><p>sukayi sallama anan. ummi ta shiga gida daga</p><p>makaranta take,akuyan umman bashir tagani ta</p><p>gani a gidansu tana masu barna a kicin da sauri</p><p>ta koma ta saka sakatan gidan,sannan ta</p><p>dawo.ta kama akuyan ta kaita bakin fanfo ta tara</p><p>kanta sai kuka akuyan take tayi. Umman bashir</p><p>ta jiyo daga gidanta,da sauri ta fita taxo tana</p><p>buga gidan tana mashifa.yan baqin</p><p>ciki,mahassada,yanka min akuyan xaku yi?san</p><p>ummi bata ji ba, dan gidan ba kowa. umma taje</p><p>sheka can gidansu,hta kuma tsohuwa taje</p><p>gaisuwa n mutuwa nan kusa dasu.saida taga</p><p>akuyan ta galabaita sannan ta janyo wata leda ta</p><p>daura mata a bindi,sannan ta saketa.akuyan ta</p><p>tashi da gudu tayi hanyan fita,tace shegiya gobe</p><p>kixo ki bude mana abinci kici.taje ta bude qofar</p><p>ta jiyo muryan umman bashir,dan haka sai ta cire</p><p>sakatar sannan ta dan sanmata qofan akuya tayi</p><p>waje da gudu.saboda ledar da ummi ta qulla</p><p>mata,sai take ganin kamar binta ake,dan haka ta</p><p>nausa cikin unguwa da gudu.umman bashir na</p><p>ganin akuyarta tayi fitan bindiga,sai tabi tana</p><p>cewa,ku taremin.ummi ta koma ciki tana</p><p>dariya.ita kuma umman bashir daqar ta samu aka</p><p>ruqo mata akuyan ta.aka kwance ledan taruqo ta</p><p>xuwa gida.sai masifa take, tana isowa qofar</p><p>gidan umma na RFIN CIKI book 1 part 5</p><p>ZURFIN CIKI book 1 part 5</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 21:54</p><p>Ita kuma umman bashir daqar ta samu aka ruqo</p><p>mata akuyan ta.aka kwance ledan taruqo ta xuwa</p><p>gida.sai masifa take, tana isowa qofar gidan</p><p>umma na isa. tace yar baqin ciki kun kama min</p><p>akuya kun jiqata xaku kashe min,ta ta allah ba</p><p>takuba.umma tace akuya kuma wani iri?ni bana</p><p>gidan dawowa ta kenan.ta ce kina nan muna</p><p>fuka.umma sai ta shige gida,amma duk da haka</p><p>sai da umman bashir ta bita har ciki tace sai ta</p><p>doke mace akan akuyan ta.umma ta shige daki</p><p>can qurya tasamu ummi a kwance,tace ke uwar</p><p>yan daukan magana, ke ce kika jiqa mata akuya?</p><p>umma tace cinye min abinci tayi.nan abba ya</p><p>riske ta tana ta tsine tsine.yace meya faru?tace</p><p>kai ja can ka bani guri,dan baka san darajata</p><p>ba,banda an raina ni yaya xa'a kama min dabba</p><p>a jiqa?in nai magana sai a maidani mahaukaciya</p><p>ko haquri baxa a ban ba.abba yace to kiyi haquri</p><p>in sha allah baxa a qara ba.tace baxan haqura</p><p>ba,tunda inta mutu nike da asara.umma tafito</p><p>tace to yanxu ya kike san ayi?ni dai bananan</p><p>ummi ce da wannan tsiyan wai ta sameta ta</p><p>cinye mata abinci. umma tace kinsan halin ummi</p><p>kuma nima haquri nake da ita.tace to ni baxan</p><p>iya haqurin ba.umma ta finciko ummi ta hanka da</p><p>mata.ta gata na ki rama mata.ta juya cikin daki</p><p>ta kama harko kinta.ba kunya ta kama ummi</p><p>tana ta jibga.abba takaicin mahaifiyan shi ya cika</p><p>mai xuciya,amma bashi da daman cewa ta</p><p>bari.shin baxa tai tunani ba takama yar matan da</p><p>tariqe mata danta riqon adalci da amana,tana</p><p>duka haka? sai data gaji dan kan ta sannan ta</p><p>fito.abba ma fita yayi cikin takaici,ummi kuwa</p><p>kuwa tayi tayi har tsohuwa ta dawo,ta sameta</p><p>xaune tana dirxan kuka. Dama taci karo da abba</p><p>a waje tace mai sunan mlm har ka dawo xaka</p><p>kuma fita?yace um.tace miskilin banxa saikace</p><p>mai ciwon hakori,ta riska ummi tana kuka,tace</p><p>umhum daman tunda naga ya fita yana ta</p><p>maxurai nasan yaci xalinci.kai na gaji da halin</p><p>mai sunan mlm.umma tace,ba ruwanshi.ummi</p><p>taqara satin kuka ba umman bashir bace taxo</p><p>tayi min duka.meki ka mata?wai din akuyan ta</p><p>taxo ta cinyemin abinci,shine na jiqata da</p><p>ruwa,shine taxo tamin duka kuma gashi banci</p><p>komai ba, ko qala bata ceba,ta juya sai gidan</p><p>umman bashir.ta sameta tana sinke kayan</p><p>miya.tace ke sahura saboda bakida mutunci shine</p><p>xakixo har gaban uwarta ki daka?sahura tace na</p><p>daketa,kamme xata jiqa min akuya?tace wane</p><p>shegen ne yace ki saki akuyan ki har taje taci</p><p>mata abinci?to kashedin ki mara mutunci da baki</p><p>san girman nagaba ba.bashir ya fito yace a'a</p><p>tsohuwa kidaina xagan mana uwa har cikin</p><p>gidanmu.tace iye!kaxone ka nuna min rashin</p><p>tarbinyan ka?nan har wata uwa gareka?nanfa sa</p><p>in sa ya tsarke a tsakaninsu.ummata juyo su</p><p>tarasa yadda xatayi,sai ga abba ya shigo.yauwa</p><p>abba shiga gidan can ka lallaso min tsohuwa taje</p><p>kasgedi ataba yar gwal dinta.ta dubi ummi tace</p><p>duk aka yar marajin can ni naji dadin dukan da</p><p>tayi mata,dan dukan algaki tayi.banda xalunci ya</p><p>xata kama dabba ta jiqa? abba ya fita ba tare da</p><p>yace qala ba. abba na shiga gidan bashir yana</p><p>tsigale tsohuwa tankar xai kai mata duka,abba ya</p><p>daga hannu ya wanka ma bashir mari,sannan</p><p>yace tsohuwa saankace da xaka dunga mata</p><p>wannan fadan.ya dubi umman bashir dan allah</p><p>kiyi haquri.sannan yaja hannu tsohuwa,shi kuma</p><p>bashir yana ta xagin abba yana cewa allah ya</p><p>isa. umman bashir ta ce abba tir da hauhuwan ka</p><p>tir!tir! kuma gab nake da in dagama ka nono.cak!</p><p>abba ya tsaya kalaman mahaifiyan shi sun shi</p><p>jeshi,a hankali ya saki hannun tsohuwa batare da</p><p>tasan ya tsaya ba.dan sababin da takeyi yaja</p><p>hankalinta.ya juyo har gabanta yace dan allah ki</p><p>yafemin ki ya femin.ba tareda ya jira amsan ta ba</p><p>ya fita. baiji muryan taba amma koda bata ya fe</p><p>maiba jikinta yayi sanyi.da yamma bayan su ahj</p><p>babba sun dawo kasuwa sai suka shiga dan</p><p>gaida tsohuwa.nan ta saka masu kuka suka rude</p><p>tare da fadin me aka mata?cikin kuka tace ni</p><p>sahura xatai ma rashin mutun ci tare da danta</p><p>bashir nan ta koro masu bayanin komai. Ahaji dai</p><p>sukai ta bata haquri,ahj qarami yace shi kam dole</p><p>ya cimata mutunci daga ita har bashir din.da</p><p>suka fito ahji babba ya ce kada gaje ka mata da</p><p>tsin hankali,nashihaxaka yi mata shi kuma bashir</p><p>ya girmama yayansa.abba kuwa yana fita sai ya</p><p>bar layin dan bacinrai,dakin ahmad yaje ya</p><p>kwanta duk da cewan ahmad din bayanan.tunani</p><p>yake tayi akan mahaifiyanshi,yadda ta runtse ido</p><p>da alkairin da umma da ahj suke mata.ahj qarami</p><p>cikin damuwa da takaici ya shiga gidansa,da</p><p>bashir ya soma yin karo,nan take ya rufeshi da</p><p>fada.sahura na ji ta taso cikin mashifa kada ya</p><p>xagan mata da,dan ya nemi tare mata</p><p>mutunci.ahj yace har wani mutunci ne dake</p><p>wanda xai kare maki?to da kinada mutuncin kin</p><p>tunkari mahaifiyata ki mata cin xarafi?tace har</p><p>gidannan ta shigo saboda na daki yar gwal</p><p>dinta,takan wannan wara mutuncin yarinyan xata</p><p>xo ta xage ni?umma tace ma ahj babba ka fito</p><p>gashi can fa ahj qarami rigima ta kaure</p><p>tsakaninshi da umman bashir.da qyar ahj babba</p><p>ya kashe wutan,abba da ya dawo yaji hayani ma</p><p>mahaifanshi sai ya qara barin layin sai can sha</p><p>daya na dare ya dawo ya kwanta,ranan ko abinci</p><p>bai ci ba.da safe yana gaban umman shi yana</p><p>fada mata kalaman da umman bashir ta masa</p><p>jiya,una ta ce ashsha,kai banji dadin wannan</p><p>kalaman na sahusa gare ka ba.saidai na gode</p><p>daka nemi yafiyanta,sannan ka kiyaye duk abinda</p><p>xaisa tayi maka munmunan furuci.dan bakinta</p><p>dafine a gareka.kada kaga cewan baka yimata</p><p>komai ba,to intayi ma mugun furuci sai</p><p>kamaka.yace xan kula,tace yauwa abba.saka</p><p>makon binci ke da mahaifin bishira yasa amishi</p><p>iri daya da wanda sirikinshi ibrahim yayi</p><p>mishi,ma'ana halayan kirki da mutuncin iyayanshi</p><p>da shi kanshi yaran.duk dadai ance masa ba</p><p>wasu masu hali bane?sai rufin asiri da suke da</p><p>shi.wannan bai dameshi ba tunda dai ance mashi</p><p>yaran yana neman na kanshi,sannan yana karatu.</p><p>to tunda tana sanshi ba ruwan shi. ya kira wayan</p><p>cikin gida ya kira hjy sai yaji sallamanta ta turo</p><p>qofa.yace yauwa dama ke xan kira.ta dire tire</p><p>mai dauke da kayan shayi akai,sannan ta xauna</p><p>tana gaishe shi. Ya amsa sannan yace ina jin</p><p>gobe masu neman auran bishira zasu je wajen</p><p>yaya a jakara. Hajiya zainu ta gyara zama,"ka ce,</p><p>bishira ko Aisha? ya ce bishira dai tayi yar dariya</p><p>yaushe bishira tayi saurayin da har zai turo? ya</p><p>ce,"a'a ba ki sani ba? ta ce,"na dai ji yanzun" ya</p><p>ce to na basu izinin turawa tun jiya tunda tana</p><p>sonshi babu ruwana da doguwar soyayyar nan</p><p>kin sani Hajiya zainu ta hade rai,"amma kana</p><p>sane da cewa ss2 zata je ko? ina laifin ta gama</p><p>sakandare? Tace ,"gaskiya ranka ya dade ka bar</p><p>batun auran bishira." ya dubeta,"kada ki damu</p><p>kanki fa.don kin san ba zan canza ba" ta bata</p><p>rai,to dan wanene? shima ya daure fuska dan</p><p>babanshine.ta mike a fusace ta fita sai dakin su</p><p>bishira. Lokacin suka farka daga baccin da suka</p><p>koma bayan sallar asubahi.ta ce,"ke bishira,ke ce</p><p>kika turo saurayinki gurin dadynku? wai yaushe</p><p>ma kika yi saurayin? Aisha tayi zaraf tace, momy</p><p>kin ma san wanene? hajiya zainu ta ce,"wanene?"</p><p>Aisha ta ce telanmu Abba din nan." Hajiya zainu</p><p>ta saka salati Abba tela? tela fa? Aisha ta</p><p>ce,"tela kuwa" hajiya zainu ta isa gurin bishira ta</p><p>rike mata kunne. "kece kika zabi auran tela? me</p><p>ya ci shi kansa bare ya baki? zai iya da</p><p>karatunki? wallahi tun wuri kije ki fada ma</p><p>dadynku bakya sonshi." Bishira ta ce,"nifa shi</p><p>nake so momy."hajiya zainu ta rufeta da duka.</p><p>washe gari su Alhaji babba da abokinsa Alhaji</p><p>sani,sai makocinsu malam ma'aru suka je</p><p>nemawa Abba auran bishira a jakara gidan Alhaji</p><p>musa wan mahaifin bishira. an amshesu hannu</p><p>biyu,sunyi magana ta fahimta an basu,kuma sun</p><p>karba.an yanka sadaki da dukiyar aure,sannan</p><p>sunce suna so za'a hada da yarta. Su Alhaji suna</p><p>ta godiya nan dai gemu da gemu suka rabu cikin</p><p>mutumta juna. Hajiya zainu ta dauki karan tsana</p><p>ta dora ma bishira,tunda tayi-tayi cewa ta janye</p><p>batun auran Abba taki,ta ce to bazan miki komai</p><p>ba.sannan in babu ta sameki kada ki ce kin</p><p>sanni,in ki ka zo nan gidan da sunan neman</p><p>taimako saina wulakanta ki. Duk bishira dai ta</p><p>yarda,nan aka sa rana kusan wata shida. Abba</p><p>ya iso kofar shagonsu da sauri don hangen da</p><p>yayi gurin ya cika da jama'a,yana zuwa sai yaga</p><p>ashe ummi ce tazo wucewa ta taba wani shagon</p><p>fale-fale ta taba sai yayi mata shocking. shikenan</p><p>ta tsaya tana jiran wa zai zo tasa shima ya</p><p>taba,can sai ga wani yaro,tace kai ka iya karatu?</p><p>yaron ya ce,"eh" ta ce karya kake in da gaske ne</p><p>nuna mun acan.da gudu yaro yaje ya dangwala</p><p>dan yatsa a kan A sai ko shocking ya debe shi ya</p><p>jefa kwata. Ashe yayan yaron na kallonta sai ko</p><p>ya biyota shine ta fallo da gudu ta fada</p><p>shagon,shi kuma y ce sai ya duketa. Abba ya</p><p>kalleta kallon tsana ya ce,"fito shegiya ya</p><p>hankado ma yaron ita ya ce ka mata dukan tsiya</p><p>yaron ya ce na hakura ta ci darajarka Abba ya ce</p><p>don Allah ka duketa,don wannan bata da wani</p><p>amfani daya wuce duka. yaron ya ce,ku dai ku ja</p><p>mata kunne don kar taje tasa dan wani a</p><p>matsala,ko ma ya rasa ransa,domin shocking zai</p><p>yi kisa nan da nan. Abba ya ce dama zai kasheta</p><p>ai da munyi murna.ummi ta kalleshi a ranta ta ce</p><p>sai kazo ka kashe ni. Bayan kowa ya watse na</p><p>nan yasata tsalle kwado. Ahmad abokin shi ya</p><p>shigo shagon ya ganta tana ta tsallen kwado ya</p><p>ce a'a Abba meye naka nasa mace irin wannan</p><p>horon? Abba ya ce kasan Allah da ace yarinyar</p><p>nan namiji ce da tuni na zuga an kaita gidan</p><p>horon yara,kaini da in kayi kisan kai babu laifi da</p><p>sai na ba yarinyar nan gamalan 20 tasha ta</p><p>mutu. Ummi cikin kasa-kasa da murya ta ce</p><p>nima da zaka mutu a dadina. Ahmad ya ce haba</p><p>Abba ya kake irin wannan maganar? ya dubi</p><p>ummi tashi ki tafi abinki.ummi taki tashi don</p><p>tasan in don Abba ne sai ta tashi ya ce ta sake</p><p>sabon lale don haka sai ta ci gaba da tsallan</p><p>kwadonta. kuma bata nuna kasalarta domin ya ce</p><p>sai taji jiki tukunna zai barta. wannan ya shigo ya</p><p>ce Allah sarki ai mata hakuri wannan ya shigo ya</p><p>ce don Allah a kyaleta.sai kurum ta saka kuka. da</p><p>kyar Ahmad ya shawo kansa har ya ce ta tashi</p><p>ta tafi.ya ce kuma inta yarda yazo gida ya samu</p><p>tayi wani laifim shi da ita ne.daf da magrib yana</p><p>sauri za shi masallaci sai ya ganta da dan tasi</p><p>tana kasa shi kuma yana tuko motar a hankali</p><p>yana ce mata an kusa gidan tana cewa eh. bata</p><p>lura da Abba ba saida ya ce ke ina zaki? da sauri</p><p>ta fice da gudu dan tasi yace ke yarinya zo nan.</p><p>Abba ya matsa gurin shi ya ce malam lafiya? dan</p><p>tasi ya ce yarinyar can ce ta taro ni tun daga</p><p>bakin titi.wai an aikota ta kira dan tasi za'a dauki</p><p>kaya zuwa wambai. nan na dibo fasinjan cikin</p><p>gari ne ma sauke su tare da basu hakuri,to da</p><p>mukazo hanya sai tace mun jaki ne za'a dauka</p><p>nace jakin lafiya? ya ya za'a iya saka jaki a tasi?</p><p>ta ce mun ita dai tashi aka ce mata ta taro,kuma</p><p>nayi-nayi ta shigo motar taki. Abba ya ce,kayi</p><p>hakuri karya takeyi,kanwata ce.wallahi bata ji.</p><p>dan tasi cikin takaici gashi ya sauke fasinjanshi</p><p>yajuya ya tafI. Abba ya nufi masallaci yana</p><p>kyalkyata dariya.don shi lamarin ummi tsoro ma</p><p>ya soma bashi jaki a tasi.kai shima dan tasin</p><p>mashiririce ne.banda haka tunda ta furta jaki ai</p><p>sai ya kama gabansa. yau bai ma bi ta kanta</p><p>ba.don yana sauri yaje gurin masoyiyar sa</p><p>bishira. Ummi ta shiga ajinsu na makaranta.kai</p><p>tsaye ta nufi kujerarta wadda babu wata yarinyar</p><p>data isa ta zauna duk ajin don suna matukar</p><p>tsoron ummi. Tun daga lokacin data bigi kirji ta</p><p>ce kujerarta ce,kowa ya sallama mata.malamai</p><p>ma da suka gaji da rabon fada cewa suka yi a</p><p>bar mata kujerar. duk makarantar babu wanda</p><p>bai san ummi ba,malamai da dalibai saboda</p><p>yawan fadanta da tsokana,har malamai bata bari</p><p>ba a tsokana. sun fita fitsari ita da kawarta</p><p>Amina,kafin su dawo malamin (social studies)ya</p><p>shigo. Amina ta ce ummi dubi har malamin(social</p><p>studies)din ya shigo. ummi ta ce,"ina ruwana,ko</p><p>wanene ma ni shiga zanyi abuna."Amina ta ce,"in</p><p>dai tica hassan ne gara mun juya don sai ya zane</p><p>mu." ummi ta ce,"tab ai gara dukanshi da in tafi</p><p>gida yanxun wannan mugun yaya Abban ya ci</p><p>zalina." sam ummi bata kalli malamin ba,sanda</p><p>take takai kujerarta,yayinda Amina ta labe ta</p><p>kasa shigowa,kamar cikin mafarki taji muryarshi y</p><p>ce,"ke daga ina ki ke?" ta dubi gurin da</p><p>sauri,"yaya Abba ne ya hade rai,fuskar nan tashi</p><p>babu annuri sai kace mai bada mugun labari. ta</p><p>tsorata matuka,ya ce" zo nan kiyi 'kneel down'."</p><p>jiki na bari ummi taje ta zube gaban allon.nan</p><p>take yayi mata bulala guda goma masu kyau.</p><p>take yan ajin suka shiga taitayinsu,don sunga</p><p>ummi tsiga tana kuka irin wanda bata taba yinsa</p><p>ba.don ko an duketa daurewa takeyi ta kuma</p><p>shanye dukan. sannan sabon malami dan bautar</p><p>kasa kamar yadda ya gabatar musu da Kansa</p><p>daga zuwa yayi wannan duka.lalle dole su</p><p>tsorata. ya ce,wuce ki zauna dakikiya mai idon</p><p>jaki.wannan kalma ta daga hankalin ummi,domin</p><p>taga yan ajin sun guntse dariya. ummi ta koma</p><p>kamar ruwa ya cinyeta a cikin ajin duk tsokanarta</p><p>ta tsiya,tsunguli wancan,shuri wancan,duk an</p><p>samu saukinta. taimako daya Allah yayi mata,duk</p><p>da halinta ta da kan daukar karatu.a zaton Abba</p><p>bata iya komai ba,tun da basa shiri. don haka</p><p>baya ko duba takardunta,islamiya ne yafi tsarata</p><p>don tashi hikimar fannin addininta ne dole a</p><p>matsa mata ta sani,boko kuma in bata yi ba ta</p><p>yiwa kanta. duk rubutun da Abba yayi ummi yake</p><p>ta dawowa ya ce ta karanta shi in ko ta mike sai</p><p>ta karanta shi tsaf.in da ta dan samu saukin shi</p><p>kenan. tun daga wannan ranar ummi alkadarinta</p><p>ya soma karyewa gurin yan ajin,domin in suna</p><p>fada shh da yazo ba bin ba'asi ita yake horawa.</p><p>sannan in ta duki wani kafin ya shigo.daya shigo</p><p>za'a fada mishi,don shine ya basu damar cewa</p><p>duk wanda ta taba in yazo a fada mishi. duk da</p><p>sun gano kanwar shi ce,gashi kuma wani lokaci</p><p>tsokanarta suke tunda ya ce mata ummi mai idon</p><p>jaki. sam bataji dadin zuwan Abba ba amma</p><p>tasha alwashin itama sai ta mishi abinda zaiji</p><p>bakin ciki kwatankwacin yadda taji. wata rana</p><p>Abba ya siyo wayar sadarwa, lokacin tana farkon</p><p>fitowa,yazo da ita gidan yana nuna ma su umma.</p><p>nan akayi ta mishi murna umma ta ce,"kai</p><p>Abba,kai da zancen aurenka ke karatowa ina kai</p><p>ina siyan wannan abar har kusan dubu ashirin ka</p><p>ce?" Yace umma amfani kai,kema xan sai miki ai</p><p>tunda nan gaba kadan xata sakko.ahj babba dai</p><p>yace xaya bani kudi in sayo musu shida ahj</p><p>qarami.ummi na wanke wanke tana kallan</p><p>su,wayar ta birgeta,irin wanda suke gani a cikin</p><p>fina finan indiya, ta xata yan sanda ne kawai</p><p>suke riqe irin wannan wayoyin.kai ko na bakin</p><p>titin nan da take ganin mutane na bugawa birgeta</p><p>yake yi,har ta tuna ranan da sukayi doguwan</p><p>tafiya sukaje phone book.suna xuwa suka tarad</p><p>ana layi,haka suka koma gyefe saida kowa ya</p><p>gama sannan suka shiga sunata latsa latsan</p><p>nanbobi suna karawa a kunne.saida wani mutun</p><p>yaxo ya kore su,bayan ya dundungure masu kai.</p><p>tayi murmushi, sannantace a ranta, allah yasa ya</p><p>sai ma umman su,ita ko ta samu abin latsawa.</p><p>daya nunama tsohuwa wayan tace shirman</p><p>banxa,inba qarya ba da wannan xaka kira wani</p><p>daga nesa?yace kn da a saudiyya kike xan kira</p><p>ki.ta ja tsaki tayi daki shiko ya fice nana</p><p>dariya.cikin satin ahj babba ya ba abba ya hada</p><p>masu waya da layi,ahj babba yafi kowa murna da</p><p>wayan, saboda shi mata fiyine. Wata safiya abba</p><p>ya shiga wanka, umma na kicin tana soya masu</p><p>dankalin hausa. zirif ta shige dakin abba tanata</p><p>danna danne,da taji motsin bayi sai ta aje ta yi</p><p>waje da gudu.saida ta tabbata ya shiga daki sai</p><p>tayi xirif da shige gida.lkc da taxo kawo mai abin</p><p>kari tasame shi yanata danna wayan,ya dubeta</p><p>kinxo kin tabamin waya ko?da sauri tace a,a.yace</p><p>munafuka,kece gashi kinyi min delete din duk</p><p>numbers din dake cikin wayan, muguwa. tace to</p><p>ni na shigone?ya harare ta yace fita, da ace ban</p><p>rubuta lambobin na aje ba da yanxun kin min</p><p>asara, muguwa kawai. ummi ta fita tana dariyan</p><p>mugunta,domin in da abin da tafi so bai wuce</p><p>taga bacin ran abba ba,kamar yadda tayi imani</p><p>shima burinsa kenan. umma ta lakato man xafi</p><p>tana shafama ahj a qafa tana murxawa.yace</p><p>yauwa suwaiba kamar kinsan tun daxu yakemin</p><p>kwankwatsa.daxidariya tace in dan tamu ne</p><p>kariqa ware ranaku biyu a sati kana hutawa.yayi</p><p>yar dariya,ina wani hutu da xanyi a gidan</p><p>nan,matsalar ummina kadai ta ishe ni.umma tayi</p><p>dariya,sannan tace ai ummi sai addu;a Ta canya</p><p>xancan da cewa,af na manta niko yanxu auran</p><p>abba yayi wata hudu nangaba?ya ce hudu ne da</p><p>yan kwanaki.tace tofa!gashi ni uwarsa banida ko</p><p>kobo,bari naxo na kama sana'a. ya tuntsure da</p><p>dariya,sannan yace sai yanxu kika san da</p><p>sana'a?itama dariyan tayi tace, in ba haka ba ahj</p><p>ranar biki ko an kirani bana amsa ba.yace gashi</p><p>kuma ke xaki mishi lefe.tace,to na shiga</p><p>aljihunka,in yaso in an soma sana'a sai in biya</p><p>ka.yasa hannu ya dago fuskanta yace sannu</p><p>sarkin wayau.suka sa dariya.yace in san muje</p><p>yaga gidajen nan na layin gabanmu,sai ya xaba</p><p>guda daya a baiwa masu hayar notice sai a gyara</p><p>shi.tace ya xabi na farkon layin dan yafi</p><p>kxau.yace amma bashida girma.tace ya ishe shi</p><p>daga shi sai matarsa fa?wanda ke cikin gidan ba</p><p>mata bixu ne dashi ba?yace to xamuje dai ya</p><p>xaba.sannan akoma kan lefe,tace allah ya saka</p><p>da alkairi,allah ya kaimu.yace amin.wayanshi</p><p>dake caji ta soma ruri,yace dauko min wayar</p><p>can.ta miqe tana cewa har naji tsoro,na kasa</p><p>sabawa da wayan nan.yace kuma gashi na kusa</p><p>bar maki ita. tayi dariyan jin dadi,tana</p><p>kallanshi.to ni wama xai dinga kirana?yace ni</p><p>mana,bana iya yi miki wata magana in na kira</p><p>abba na ce ya kawo maki,sai inga kamar yana</p><p>tsaye,inko taki ce dana kira sai ki kebe daga</p><p>jama'a muyi hiranmu. tayi dariya, daidai lkcn da</p><p>kiran ya sake shigowa,ya daga. ahj buhari ne</p><p>wanda ke sarin kaya gun shi daga kaduna.suka</p><p>gaisa yace ahj ka kira kan in dauka ta katse.ahj</p><p>buhari yace,dama ina san ince maka ne dan allah</p><p>gobe xan shigo,kasa ahada min kayan nan da</p><p>wuri.yace ba komai xa a hada.bayan sunyi</p><p>sallama umma tace ni abin da yake bani al'ajabi</p><p>da wayan nan, har kullum yanda xaka kira wani</p><p>daga nisan duniya,kuma kuyi xance radau.ahj</p><p>yace ci gaba kenan,wata rana ma sai kinga</p><p>fasahan data ninka wannan.tace haka ne.abba</p><p>yana xaune gaban ahj da safe bayan sun</p><p>gaisai,sai ahj yace abba ina ganin da yamma ko</p><p>xuwa dare kaje ka duba gidajen nan ka xabi</p><p>guda,saboda a ba su notice dan a gyara</p><p>didan.yace ahj ba sai naje ba duk wanda aka bani</p><p>yayi.ahj yace ummanka tace ka xabi na farkon</p><p>layin. cikin murmushi abba yace,ta shi</p><p>kenan,nima shina xaba domin duk abinda umma</p><p>ta xaba min shine xabina. tuni sahura ta fito da</p><p>anko,xaqewanta da nuna isarta akan bikin sai</p><p>kace ba dan fari ba. duk dangi sai surutunta ake</p><p>yi,har danginta.umma kan cewa tayi anko ba</p><p>shine damuwanta ba,dan haka sam bata bi ta</p><p>kansu ba.abba a cikin ajin da yake koyarwa,ummi</p><p>tana 2n gefe in da yayi mata maxauni a qasa,can</p><p>in da ba knwa sakamakon ganowa da yayi in tana</p><p>ajin ba a xaman lafiya,sannan babu me ikon xama</p><p>a kujeranta.yace,in ma ya sake ganinta ko a wace</p><p>kujera ce bas,xai ballata.rubutunda yayi take yi</p><p>ranta bace.ya kalli gun datake yace ke!ta dago ta</p><p>dube shi,yace xo nan.taje yace,amso min bulala</p><p>acan ajin.kafin ta dawo sai da ta duke wata</p><p>yarinya ta rugo.nan kuwa yarinyan ta biyo ta har</p><p>aji,abba kam daya amshi bulalar saida ya xaneta</p><p>tas.sam abba ya sama uni ido ko ta ina,ba</p><p>makaranta ba, ba gida ba.dan haka ta matsu yayi</p><p>aure ya bar gidan sannan ya gama service dan</p><p>shi ya qara gaba. tabbas lkcn auran sa xata yi</p><p>party.RFIN CIKI book 1 part 6</p><p>ZURFIN CIKI book 1 part 6</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 21:56</p><p>Tabbas lkcn auran sa xata yi party. Ummi party</p><p>xatayi na murnan barin gidan shi.ahj ya ba umma</p><p>wayarshi kamar yadda ya fada mata,ya ba abba</p><p>ya suya mata layin mtn kamar yadda ya fada</p><p>mata.ummi tafi kowa murna da wannan</p><p>wayan,domin in umma ta aje takan dauka tayi ta</p><p>latse latse,har dai ta iya abubuwa a wayan</p><p>saboda ta iya karatu.kwanci tashi bikin abba ya</p><p>rage saura yan kwanaki.duk gida biyun sai shirya</p><p>shirye suke,mu samman gidan amare saboda yan</p><p>mata biyu xasu auran.gidansu abba tuni ahj yasa</p><p>an masu fantin gidan biyun,gidan ango kuwa ya</p><p>sha gyara da fenti.ahj ya sabunta mishi qofofi da</p><p>wundunan gidan, batun lefe kam dama tuni ya ke</p><p>sayen xannuwanshi da kadan da kadan yana</p><p>kawo ma umma tana adanawa.dan haka ahj</p><p>karami yana kawo akwatuna umma ta fito da</p><p>kayan dan tasan me xa a qaro.sannan ya yaba</p><p>da hankalin abba.wannan ya nuna mishi cewa</p><p>abba xai iya riqe gidanshi.lalle sana'an hannu</p><p>tana da amfanh ga yayanmu a wannan xamanin</p><p>namu.umma tai mashi lissafin sauran abubuwan</p><p>da xannuwa da leshi xuwa shadda,tace ahj dan</p><p>allah adubo mana masu tsada, Ahj yace suwaiba</p><p>xan yi daidai qarfina,ba xan yi qarya ba dan sun</p><p>san cewa dana talaka ne,kuma suka ba shi.umma</p><p>tace,sai batun abin da xa a ci.yace suwaiba</p><p>kenan,saunawa xakimin lissafin kayan abincin?na</p><p>xata ma xakice kayan sawanku?umma tace suma</p><p>a kawo mana da wuri dan mu dhnka da wuri,ba</p><p>abba xan ba c saboda harkokin sun masa</p><p>yawa.saura sati uku biki aka kai lefe.hjy xainu dai</p><p>unguwa ma ta tafi a ranar,danginta na maigidan</p><p>su ne suka amsa.sai yatsina suke tare da raina</p><p>kayan da suka duba ma sai um da um suke</p><p>cewa,wata tace to an gode fa,tunda taji ta gani</p><p>mu menene namu?suka ba da tukuici, nan dai</p><p>yan kai lefe suka dawo jiki babu qarfi.koda suka</p><p>dawo suka sanar da umma sai tace ku qyale</p><p>su.mu dai mun yi daidai qarfinmu.umman bashir</p><p>kuwa da qannanta suka kai mata labari cewa,tayi</p><p>ina ko xa suyi maraba da kaya?suwaiba ta karbe</p><p>mishi kudi bada xuba kayan kirki ba,banga</p><p>laifinsu ba.ummi kam sai dibar ma umma kayan</p><p>abinci take a boye tana kaiwa gidan maman iman</p><p>maqotansu ne,matan suna shiri da ummi, don ita</p><p>rayuwar ummi dariya take bata,ta gwado shinkafa</p><p>ta kawo,taliya,ta tsiyayo mai,ta ce sauran kayan</p><p>miya da magi,har nama debowa zanyi. maman</p><p>imam ta ce lallai kawayenki zasu sha party.</p><p>ummi ta ce tab ai dole inyi party zan rabu da</p><p>alakakai sarkin mugancin duniya. maman imam</p><p>ta saka dariya,ummi ta kuma fita da gudu tana</p><p>fadina na tuna inda gishiri da maggi suke. daga</p><p>gidan amare anzo anga gidan amarya,nan ma sun</p><p>tafi suna mita,fadi suke "bishira batayi sa'ar miji</p><p>ba,wata ta ce ya aureta ne don kudin ubanta.</p><p>koda suka je suka fada ma hajiya zainu fasalin</p><p>gidan,daki uku ne duka falle dai dai sai kicin da</p><p>bayi a tsakar gida. kanwar zainu ta ce,"kai</p><p>gaskiya bishira bata yi dabara ba.hashimu dan</p><p>gidan Alhaji mansur ya jima da sanar dani ya</p><p>kamun bishira." hajiya zainu ta ce,"shi kadai?ko</p><p>yayan abokan babansu nawa ke sonta?tunda taki</p><p>tsayawa tayi karatu ta zabi ta auri tela,ba shi</p><p>kenan ba?dubi gidan ubanta amma ta zabi zama</p><p>a wani gida dakuna jere sai ka ce ajin</p><p>primary."lol. suka ce,"kwarai kuwa kamar ajin</p><p>makarantar gwamnati."ta ce,"shi kenan ai kaya</p><p>dai asai mata daidai tsarin gidanta ba iri daya za</p><p>a sai musu da Aisha ba." sun siyo sunje sun jera</p><p>komai ras,yanzun kam sai daura aure ya</p><p>rage,Abba da abokanansa walima kadai ya shirya.</p><p>can gidan ne suke ta bukukuwansu irin ma masu</p><p>hali.shi kam dai yasan yan'uwanta ba sonshi</p><p>suke ba. sam be je gurin shagalinsu ba. ranar</p><p>lahadi aka daura aure,misalin karfe goma na</p><p>safe,unguwar kam ta cika da mutane da motoci.</p><p>Abba da zugar abokananshi salisu yayan amare</p><p>yayi musu jagora cikin gidan. sun gaisa da</p><p>mutane sannan suka fito kowa fadi yake."kai</p><p>amma angon bishira zankadede dashi</p><p>tubarkalla."gashi Abba da iya daukar</p><p>wanka,tsafta ce dashi ga son kamshi. KAI MATA</p><p>IYAYEN GULMA. Can gidan ango ma anata</p><p>shagalin cin abinci, jama'a dangi da makota sa</p><p>gudunmawa suke ba umma tana a'a amma sai</p><p>ace ta rike sabida ita mutum ce mai kyauta.</p><p>umman bashir kam sai takaici take ji,kowa ya</p><p>shigo sai dai ya ce mata."Allah ya sanya</p><p>alkairi"kawai musamman ta shigo gidan don taga</p><p>ko ana ba umman Abba ne. Nan fa na fita ta</p><p>koma gida babu ko kunya tana ta masifa, fadi</p><p>take "lallai suwaiba,gudunmawar auran dana duk</p><p>ita ce ke karbewa? gaskiya naga sai dai amin</p><p>Allah sanya alheri a wuce,to da sake,ni na haifi</p><p>abuna ta bari sai ta tashi auran wannan</p><p>figaggyar yar tata sannan ta amshi bikin." ta</p><p>gama fadanta ta matsa,danginta suka soma yi da</p><p>ita,suka ce wa zai baki wani abu ke da ko dan</p><p>uwanki baki san ki bashi gudunmawa ba bare</p><p>kyauta.tsinanni yar rowarki ce taja miki."</p><p>kanwarta ta ce,"sahura sai dai ta ci na wani ba</p><p>dai aci nata ba,dama irinsu sun cika son banza."</p><p>ummi kam anci kwalliya an gayyato kawaye</p><p>anata party a gidan maman iman,an kunna rediyo</p><p>sai rawa suke yi,kafin a gama partyn an bige da</p><p>fada da dambe,da kyar aka rabasu,nan taro ya</p><p>watse. da misalin karfe takwas na dare,ango da</p><p>abokanshi sun taso sallar isha'i Ahmad ya ce don</p><p>Allah ango muje mu rakaka. ya ce,"Allah sai nayi</p><p>wanka."mukhtara ya ce,"gidan cunkus da jama'a</p><p>zakayi wanka?" Aminu ya ce,"don Allah malam</p><p>kazo mu tafi,in ma kifi zaka zama a gidanka."</p><p>Abba ya ce,"bari dai ku gani." a zaure suka ci</p><p>karo da ummi,ya ce,"ke jeki ki wanke bayi ki kai</p><p>mun ruwan wanka." ta sobare baki ta koma ciki</p><p>tana fadin. na dai kusan hutawa, masifaff. ta</p><p>wanke bayin sannan takai ruwan,yana shiga gidan</p><p>dangi sukayo kanshi,ga ango! ga ango!! abokan</p><p>wasa suka za na can zamfara suna tayi masa</p><p>tsiya. dan gidan ummanshi yau dai za a kwana</p><p>wani gidan ba na umman tashi ba.ya dai samu</p><p>ya shige wanka. bayan ya fito ya bude</p><p>dakinshi,ya shirya cikin wata shadda</p><p>mirror,lokacin su ake yayi.ruwan kasa mai duhu.</p><p>yasha hula mu hadu a banki ita ma kalar</p><p>shaddar,ya feshe jikinshi da kalolin turaruka.ya</p><p>shigo cikin gidan yaje kofar dakin umma. ya ce</p><p>umman tana nan.aka ce mishi tana dakin</p><p>Alhaji,yayi sallama a kofar falon Alhajin basu ji</p><p>ba,suna ta hira tsit ya yi lokacin da yaji umman</p><p>tana cewa Allah dai ya basu zaman lafiya da</p><p>zuri'a tagari. Amma har ga Allah naso Abba ya</p><p>auri..... ringing din wayar shi ce ta hana jin kowa</p><p>ummanshi ta ce,sai dai muryar Alhajin ya ce</p><p>wallahi suwaiba nima tsarina kenan. ahj yace ta</p><p>allah ya riga ya shirya ba ita ce matarshi ba.ya</p><p>daga wayar,ahmad ina xuwa mana. ba tare da</p><p>yaji abinda ahmad din xai fada ba ya katse</p><p>kiran,dan yaji haushi.yaso jin wacece iyayansa</p><p>suka so ya aura?ya sake doka sallama,suka</p><p>amsa.ya shiga ya xauna ya gaishesu,sannanya</p><p>dubi umma.dama naxo miki sai da safe ne.ahj da</p><p>umma suka yi yar dariya,umma tace to</p><p>abba,yanxu dai ka girma,dan allah kyawawan</p><p>halayenka dinnan kaci gaba da su.yace na</p><p>gode.ahj ma yayi masa nasiha,daga nan ya fita</p><p>jikinshi a sanyaye.da muwarsa me yasa umma</p><p>bata sanar da shi yarinyar da taso mishi ba</p><p>tuntuni?haka dai suka rankaya da abokanansa</p><p>dan xuwa dakin amarya. gidan kam tun daga</p><p>tsakar gida qamshi ke tashi.sun taradda</p><p>qawayenta biyu,ita kam tana lullube kan</p><p>gado.nan dai suka sayi baki akayi yan shaqiyanci</p><p>tare da barkwanci,sannan qawaye suka yi mata</p><p>sallama suka tafi,shima ya raka abokansa. ya</p><p>dawo ya xauna bakin gadan yana dubanta, itama</p><p>kallonshi take cike da so. sukayi ma juna</p><p>murmushi,ya janyo ledan kaxan da suka shigo da</p><p>ita. Ya warware takardar,y yago cinya ya mika</p><p>mata a baki,"ci,nasan yau kin wuni da yunwa</p><p>ko?" ta ce,"na koshi bana jin yunwa ma,ni kam</p><p>duk yau banji yunwa ba." ya ce,"ni ma haka,dama</p><p>yau bai da ce muci abinci ba."ta dube shi da</p><p>alamar tambaya a kwayar idanunta.ya ware</p><p>idanunshi. "taron da muka tara ko ina cike da</p><p>jama'a." yayi yar dariya sannnan ta bude baki ya</p><p>saka mata kazar.ta dan figa.haka yayi ta bata</p><p>tare da zuba mata juice a kofi shima yana bata.</p><p>ta ce,"to kaima ka ci." ya ce,nima ke zaki</p><p>bani."ta sunkuyar da kai don kunya sannan ta</p><p>dauka ita ma ta soma bashi. sai da suka yi</p><p>dam.sannan ya ce mata kije kiyi alwala kizo muyi</p><p>sallah. ta ce ai tun dazun nayi sallah.ya ce</p><p>wannan ta ma'aurata ce,zamu gode wa Allah</p><p>taare da rokonshi zuri'a tagari,da kuma fatan ya</p><p>tsare mu daga sharrin shaidan dama duk abin ki.</p><p>Ta fita ta dauro alwala,shi kuma ya kuskure</p><p>baki.shine yaja su sallar,raka'a biu sannan sukayi</p><p>ta addu'a,shi ne ma yake addu'ar ita kuma tana</p><p>cewa amin. bayan sun idar da sallah idar da</p><p>sallar,ya yi mata tambayoyi game da addini ta</p><p>sanar da shi,yayi mata yan gyare-gyare sannan</p><p>suka kwanta. sam Abba be daga kafa ba,a ranar</p><p>ya angwance abin shi.don haka yayi kwanan farin</p><p>ciki. da asubahi ya dawo masallaci,har lokacin</p><p>amarya tana ta shirga bacci ya zauna bakin</p><p>gadon yana kallonta.yasa hannunshi a gefen</p><p>kumatunta. "sleeping beauty" tayi mika sannan ta</p><p>bude ido,ya ce"a tashi ayi sallah ko?gashi sai</p><p>kinyi wanka ko?" ta ce,"eh." ya ce, "to tashi ki</p><p>gani gari ya soma haske." zani taja ta daura</p><p>daura ta nufi waje. da kallo tabi tsakar</p><p>gidan,sannan ta dawo dakin Abba.bazan iya jan</p><p>ruwa daga cikin rijiya ba. ya fito da sauri yaja</p><p>mata sannan yakai mata bandakin,ya dawo yayi</p><p>taja yana cika robobin ruwanta.sai da ya cika</p><p>mata komai,sannan ya koma dakin. lokacin ta</p><p>idar da sallah.ya dauko Alqur'ani mai girma ya</p><p>zauna gabanta,ya ce "madam zamuyi karatu." ta</p><p>dube shi tareda yatsina fuska,"wallahi bacci</p><p>nakeji."ya ce,"daure muyi ko aya biyar ce," ta ce</p><p>cikin shagwaba,"ni biyu." ya ce,"to bismillah,mu</p><p>fara ta sama ko ta kasa?" ta ce,"ni kam ko ta</p><p>ina, don haka sai ya soma mata daga bakara</p><p>yana yi tana maimaitawa,aya biyu kusan minti</p><p>ashirin ta ce, "zan kwanta." Ya aje kur'ani ya</p><p>kmama hannunta,zo muje kicin mu gani me zamu</p><p>nema.dan dole ta bishi zuwa kicin din.suka tsaya</p><p>suna kallm kayan, tukwane ne zuwa kuloli da</p><p>sauran tarkace,sai risho.ta dube shi cikin yanayin</p><p>tsausaya ma kanta. tace, sun qi sai min gas</p><p>cooker wai gidana ba flate ba ne bai dace da gas</p><p>cooker ba. ita ko anti aisha an sai mata, kayan</p><p>girkita ma duk yan chaina. tausayinta ya tsirga</p><p>ma abba, ya jawo ta jikinshi ya rungume, kada ki</p><p>damu bishira, duk abin da a ke sai ma yar gata</p><p>xan sai miki, matsawar Allah ya hore min. ya</p><p>janyo kwalin risho din ya ciro shi, ya hada yace</p><p>xan siyo lagwani da kalanxir kenan ko? tace eh.</p><p>ya miqe bari na dawo. tace to. ta nufi daki ta</p><p>fada kan gadanta taci gaba da baccinta, shi kam</p><p>gidansu ya nufa. tun daga nesa ya hango ahj</p><p>babba xai shiga dakin waje, in da aka sauki baqi</p><p>maxa, da alama ahjn ya hango shine shi yasa ya</p><p>tsaya a bakin qofar. abba yana cike da fara'a ya</p><p>rusuna xai gaida ahj shi kuma ya miqa masa</p><p>hannu, dan haka sai abban ya kama suka yi</p><p>musabaha. ahj yace Alhamdulillahi abbana, ka</p><p>xama mutun, sai ayi ta hakuri da rayuwa. abba</p><p>ya sunkuyar da kai yana tambayar kanshi ko</p><p>manya suna ganewa ne in kayi auratayya da</p><p>matanka? ahj ya katse shi da cewa, ya kwanan</p><p>iyalin taka? tare suka shiga gun baqin, yana</p><p>gaida su ya fito xuwa cikin gidan. yana leqawa</p><p>dakin umma bata ciki, sai baqi. wata uwani dake</p><p>matsayin abokiyan wasansu tace ango amarya ta</p><p>koro ka ne? yace, keni karki dame ni, ina umma</p><p>na? umma daga kicin tace, gani nan dana, xo</p><p>qyale su uwani. gurinta ya nufa yana cewa,kina</p><p>kicin ashe? tace, eh ina hada ma baqi abin kari</p><p>ne. yace kalli yanda duk suka yi mana kaca kaca</p><p>da gidan,wannan in sun tafi sai kin sha aikin</p><p>tsaftace gidan.tace to yana iya?dole in gyara in</p><p>sun tafi,ai arxiki ne ma xuwan nasu.abba yayi</p><p>dan murmushi,sannanya canxa maganan da</p><p>cewa,umma galan din kananxir muke so.tace,ga</p><p>ma kananxir din can da ahj ya siyo jarka babba</p><p>wai saboda biki.nace yaushe girkin biki xai yiwu</p><p>da kananxir?shine na aje shi.sai kadau galan ka</p><p>cika.yayi murmushi. Yace kai ahj akwai qoqari,</p><p>musamman lkcn bikin nan.umma tayi yar dariya</p><p>tare da cewa ko abinci fa baya iya tsayawa</p><p>yaci,in na masa magana sai yace bijin da guda</p><p>ina yaga ta cin abinci?abba ya girgixa kai,Allah</p><p>ya rama muku da mafificin alkairin da kuke</p><p>min,yasa ni ma in goya ku kamar yadda kuka</p><p>goya ni.tace amin abba ai muma kana yi mana</p><p>biyayya Allah yasa albarka a cikin auran, ya baka</p><p>yaya masu binka kaima.yace amin. ya isa gida da</p><p>kalanxir da lakwani ya samu ta koma bacci,dan</p><p>haka ya hada ya dora ruwan xafi ya juye cikin</p><p>plaks yaje ya ce ta shi mu karya. tayi juyi tare da</p><p>cewa sai an jima,dama tun jiya sun shigo da</p><p>biredi da kayan tea,shima sai ya sake</p><p>kwanciya.ya mannata jikinshi suka koma</p><p>bacci,goma da ishirin wayarsa ta tashe shi da</p><p>ruri. ya daga ahj ne ke san ganinsa qarfe sha</p><p>biyu.yace,ya sanme shi can kasuwa,ita ma ta</p><p>tashi.nan suka karya sannan yayo wanka ya tafi</p><p>kiran abba.kaya ne ya ba shi da kudin mota, yace</p><p>ya kawo ma baqi yan xamfara da xasu koma gida</p><p>yace ka tabbata ka dauki shatar mota har</p><p>Zamfara abba ya ce to.sai da ya samu motar</p><p>sannan yaje ya loda su suka daga,suna ta</p><p>godiya.yau satinsu daya cir umman shi ke kai</p><p>masu abinci,sannan ita kuma ya shigo da kayan</p><p>marmari,sai kaji ko tsire da balango.abba ya</p><p>shirya tsaf cikin qananan kaya xai tafi shago,yace</p><p>madam yau fa abinci xaki yi mana,kin san</p><p>abokaina su ahmad xasu xo muci abinci,in yaso</p><p>daga nan sai mu wuce gaisuwan surukai gidanku</p><p>a matsayin kina amarya wanda xaki soma girki</p><p>yau, me xaki dafa mana? ta tashi xaune duk abin</p><p>da ka ke so.dadi ya rufe shi,kowanne dai ki mana</p><p>fatana shine ki birge abokaina.tace an gama.</p><p>yace to bari inje xan turo yaran shago da abinci</p><p>da cefane tace to, har ya tafi kuma ya dawo</p><p>yace, xan biya in turo miki ummi,tace saidai in</p><p>fati.yace,ummi tafi fati hanxarin aiki fa.tace eh</p><p>nafi son fatin.kamar kullum sai da ya soma shiga</p><p>gun ummarshi suka gaisa ta tambaye bishira,</p><p>yace lafiyi lau.yaci gaba da cewa, yau nema xata</p><p>soma girki,nace na turo mata ummi tace wai</p><p>fati.umma tayi murmushi, sannantace kai ko</p><p>yaushe xata so a tura mata ummi umma tace ina</p><p>xata so a tura mata ummi? ita fa ba natsuwa</p><p>gareta ba.abba yace, duk da haka tafi fati</p><p>hanxarin aiki. umma tace,yanxu dai tura mata</p><p>fatin.ka ko sai kayan abinci?yace ina fa,yanxu dai</p><p>xan je bin wasu yan kudadena.tace ina xuwa</p><p>baqar leda ta ciro a cikin adakan suturunta,taxo</p><p>ta xauna sannan ta umurce shi da ya xauna.ta</p><p>miqa mashi ledan tace,kwance ka gani.abba ya</p><p>kwance ledan yana cewa menene a ciki ummana?</p><p>kudin da yayi arba da su su suka bashi amsa</p><p>yace,umma kudin nan fa?tace gudunmawa ce da</p><p>jama'a sukayi ta bani,ka gansu nan.yanxu ka je</p><p>ka siyi kayan abinci da su.abba yayi dariya,</p><p>sannan ya kullesu ya miqa mata tare da cewa.</p><p>Allah ya kyauta in amsan makh kudi, ki boye</p><p>abinki. tace bana son muyi ta jan magana</p><p>abba,kawai ka riqe kudin nan.muryan tsohuwa ne</p><p>ta katse su,inda take cewa yanxu ke suwaiba</p><p>hakan da ki ka yi adalci ne? yar gudunmuwar da</p><p>ki ka samu kiba mai sunan malam duka, ummin</p><p>fa? umma tace,to tsohuwa ummi me xatayi da</p><p>kudi yanxun?abba yace kai wannan matan sa</p><p>idan ki ya gota misali. Tace kai tafi can,ni rufemin</p><p>baki,ke kuma suwaiba da kike cewan haka ba kya</p><p>siyan mata yan tukwane da kwanonin nan na yayi</p><p>maigida cika duba ne ku ke ce musu ko ci bari</p><p>kallo? umma da abba suka sa dariya,tsohuwa ta</p><p>sake jin haushi ta ce eh dole ku min dariya tunda</p><p>kema kin xama shi,ai sai kiyi ta bashi naki ne ba</p><p>nawa ba.umma tace yi haquri tsohuwa, gani nayi</p><p>nan gaba muna sa ran abba shi ne xai ma ummi</p><p>kayan dakin ma gaba daya tace,me kika ce?tab</p><p>mai sunan mlm ne xai yi wa takwara wani abin</p><p>axo a gani?shi da ya tsaneta.abba yace,in lkcn</p><p>yaxo ke kya yi ma.ta tafa hannu cikin jin</p><p>matuqan takaici ta ce,a gayawa mai xuciya ba</p><p>mai dukiya ba,dan ko xan mata.ta nufi dakinta</p><p>tana fada.umma tace,tashi abba,dauki kudin nan</p><p>kaje. yace,wallah umma bari dai in dauka tunda</p><p>kin matsa,amma ba xan amsa duka ba.ya qirga</p><p>dubu uku,tace ka qara dan kusan dubu tara ne</p><p>kudin,yace haka ma ya isa ki adana sauran.tace</p><p>shi kenan. daga nan kasuwa ya wuce,ya sai</p><p>kayan abinci.bayan ya amso wadansu kudaden</p><p>shi ya hada ya kai mata. Sannan ya yi cefanen</p><p>kayan miyan rigijif da nama ya aika yaran</p><p>shago.dama kafin ya bar layin ya shiga gun</p><p>umman bashir ya gaisheta.da tana ta bace bacen</p><p>rai,sannan da yace umma ina fati? taje xata taya</p><p>bishira aiki ne.sai ta washe baki,tan bandaki.</p><p>yace to in ta fito ki tura mata ita.ya fice</p><p>abinshi.biyu saura ya iyo gidan,tun a tsakar gidan</p><p>yake jin qamshin shinkafa.ya isa kicin din tuni ta</p><p>sauke shinkafa sai miya.yace ki xubama yaran</p><p>shagona.ya dubi fati da ke yanka latas yace,in</p><p>kin gama jamin ruwan wanka a rijiya.tace to.yana</p><p>daki yana sa kaya yaji sallamar abokanshi.da</p><p>sauri ya fito, suna ta yi masa tsiya ango kasha</p><p>gyara, munxo dibar girki. abba ya bude musu</p><p>falo,falan yaji jeran samiru abin yayi na xamanin,</p><p>ga kujeru suka xauna suna yaba dukiyar da aka</p><p>xuba cikin falon.ya fito yace bishira ta saka hijabi</p><p>taje su gaisa.ya dauki abinci ya kai musu,sannan</p><p>yasa fati takai filet da ruwan sha,shi kuma ya</p><p>koma daki dan qarasa saka kaya.a xatam shi xai</p><p>samu sunyi nisa da cin abincin amma sai me?</p><p>dukkansu su shida kowanne filet din gabansa</p><p>shaqe da abinci da nama,ga cokali a</p><p>hannunsu,amma kowannansu juya abincin</p><p>yake,yace a,a kuci mana kai muke jira ka bude da</p><p>addua.tsaki yayi, yasan halin ahmad gun</p><p>xolaya,dan haka sai yace muktar kuci abincinku,in</p><p>kun bi ta ahmad xai ta bata mana lkc.cokali ya</p><p>dauka shima ya xauna kusa da sunusi ya ce mu</p><p>ci tare.take ya yatsina fuska tare da dawo da</p><p>abincin ya xube shi kan ledar yana tande</p><p>harshansa.dan danan gishirin da ya kama masa</p><p>harshe ya ragu,cike da kunya ya dubi abokanan</p><p>nasa suna ta dariyar da suke gimtse.da farko ya</p><p>dubi sunusi,wai gishiri ka qara ne?sunusi ya</p><p>ce,qila dai gishirin nan da bakin buhu ta</p><p>xufa.muktar yace dubi gaban rigata ni da shegen</p><p>kwandayi na tura nama a baki na tauna ya qwace</p><p>saboda tsananin qarfi ya dawo ya fado min</p><p>jiki.abba ya miqe cikin damuwa ya ce bari in</p><p>maku wata miyar. ahmad yace a,a duk yunwa</p><p>muka debo, inda yaji da mai a bamu muyi maneji.</p><p>abba ya fito xuwa kicin.fati ce xaune da nata</p><p>abincin tana ta juya cokalin. Abba yace ina</p><p>bishiran?taje daki.ya daga murya ya kirata,ta</p><p>amsa sannan taxo.ya dubeta fuska a daure ke</p><p>dama ba ki iya abinci ba shi ne ki ka toxarta ni</p><p>cikin abokaina?maimakon ki fada min? tace, to ai</p><p>fati ce nace tayi miyar, danni bansan yadda a ke</p><p>yi ba. haushi ya kama shi.ya dubi fati, ke dama</p><p>baki iya komai ba kema?shashasha, gara ki koyi</p><p>girki, dan duk macen da bata iya girki ba ba mace</p><p>ba ce.ya daka mata tsawa, tashi kije gidan</p><p>ummana ki ce ta baki abinci inji ni,ni da abokaina</p><p>ne.sallamar yaron shagon shi ne ta katse shi,ya</p><p>gaishe su sannan ya ce,naxo daukan abincin.ya</p><p>dubi bishira,kina da yaji?tace,eh gashi can cikin</p><p>kwalba da ummanka ta aiko min.ya ce,xuba ma</p><p>yaran nan yaji da mai.ta ce ai akwai miyar.yace</p><p>miyar ai ta xama guba.fati ta dauko abinci cikin</p><p>kula xata fita,yace wannan fa?ba aikenki nayi ba?</p><p>tace na ummanmu ne xan tafi mata da shi,ita ce</p><p>ta ce duk abin da a ka dafa inxo mata da shi, shi</p><p>ne yaya bishira ta xuba mata.abba baice qala ba,</p><p>sai al-ajabin halin uwarshi ya ke yi. Bishira ta ce,</p><p>kawo ita ma a kwashe miyar a xuba mata mai da</p><p>yaji. ya daka ma fati tsawa,kai mata haka ni ki</p><p>dauko min abinci gun ummana, minti uku na baki</p><p>in kin wuce biyar xa ki sani.da gudu ta fita tana</p><p>shiga gidansu ta aje bata tsaya yin surutu ba, ta</p><p>fita da gudu.dan wake umma tayi,Allah yasa tayi</p><p>da yawa,dan haka ta xuba musu ta dora ma fati</p><p>ba tare da ta tambeyeta dalilin aikowarshi ba. sai</p><p>dai a ranta tana ta saqe saqe tace,qila sun fasa</p><p>girkin ne,ko kuma bai kai kayan abincin ba.koda</p><p>fati ta kai musu dan waken nan suka baje suka</p><p>kwashi dan wake suna santi.bishira tana jiyo</p><p>shewarsu.abba na cewa ummana ta iya girki, bari</p><p>in xo in sa muku waigi.muktar yace, ka kai</p><p>amaryarka ta koyo girki.garzali yace,saboda irin</p><p>wannan matsalan kafin in auri yarinya sai na</p><p>tabbata ta iya girki.ahmad ya ce daya daga cikin</p><p>illar auran yaqan masu kudin nan kenan,</p><p>sangartattu ne basu iya komai ba tun da a</p><p>gidajensu ba sasu a ke yi ba.ado yace wasu ba</p><p>amma wasu suna saka yaransu.</p><p>vels / ZURFIN CIKI book 1 part 7</p><p>ZURFIN CIKI book 1 part 7</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 21:59</p><p>Ado yace wasu ba, amma wasu suna saka</p><p>yaransu,dan wani abokin wasanmu a kaduna ya</p><p>auri yar wani attajiri, ba kaga girki ba kala</p><p>kala.abba dai yana ta binsu da ido,har aka yi</p><p>kiran sallar la'asar suka fita xuwa masallaci,daga</p><p>can xasu wuce gaida surukai.bishirata dinga jin</p><p>haushi,wai abokan abba sunxo har gidanta sunci</p><p>mata xarafi.ummi ta fito dan xuwa gidan su</p><p>amina,domin akwai wata xainab da wai ta musu</p><p>gulma xasuje su.kirata har gida su dake ta.suna</p><p>xuwa kuwa suka tsaya a waje suna tunanin</p><p>yadda xa suyi ta fito,amina ta ce muje mu ce</p><p>mun xo gunta ne, inta xo rakiyan mu mu duke ta</p><p>mu gudu.haka kuwa suka yi,har ummarta tana ba</p><p>su quli quli,ita ga me qawayen yan tana rako su</p><p>tun daga soron gidan suka soma dukanta.sai da</p><p>ummanta ta fito sannan suka gudu.ta ce yar tata</p><p>kin san gidansu?xainab tace,na sani.ummar tata</p><p>ta taso ta.su kuwa su ummi suna fitowa sai suka</p><p>canxa hanya.amina tace dan allah muje gidan</p><p>amaryan abbanku,naji ana ta labarin jeranta an</p><p>ce kaya ne na uban gari. . Ummi ta ce,"duk da</p><p>son kirgan samirana ban taba zuwa ba,saboda na</p><p>kula ita ma yar rainin wayau ce kamar mijinta."</p><p>Amina ta ce,"ke dai muje inga samirun da aka ce</p><p>jajaye wai masu shida-shida" ummi ta ce,"mu</p><p>fara bi ta shagonsa in yana nan to sai muje,in ko</p><p>bayanan ba zani ba ya dake ni a banza." duk da</p><p>cewa shagon da gidan tsakaninsu da nisa sai da</p><p>sukaje suka duba sukaga yana nan,sannan suka</p><p>je. gidan shiru sunata sallama,ummi ta nufi wata</p><p>kofa ta tura,ta yafito Amina,"zoki gani nan ne</p><p>falon."suka kirge samiru tsaf,sannan suka fito. ta</p><p>window ummi ta leka nan ta hango bishira kan</p><p>gado tana ta bacci,suka je kicin suka leka suka</p><p>tura dayan dakin da ba kowa. nan ma sukaga ba</p><p>komai ciki,an dai shimfida ledar kasa an sa</p><p>manyan robobin ruwa. suka fito,ummi ta</p><p>ce,"gaskiya matar nan banza ce,dubi yadda</p><p>mukaje tana ta bacci." daga can suka sake zuwa</p><p>gidan wata amaryar don kirga samira,sai kusan</p><p>magariba sannan ta shiga.umma tana alwala ta</p><p>ce,"to tunkiya uwar tumbele,tun yaushe ki ka bar</p><p>gidannan sai yanzun kika waiwayo? sai kararki</p><p>da jama'a keta kawo min?to na gaji da</p><p>halinki,bari Alhaji ya dawo,wato tunda yanzu</p><p>babu Abba a gida shi yasa iskancinki ke son yafi</p><p>da." tsohuwa ta fito,"suwaiba da a ce ba a</p><p>gabana kika haifi takwara ba,to da zance ba yarki</p><p>ba ce,ba dama yarinya ta fita wasa?" umma ta</p><p>ce,"ban hanata yin wasa ba,amma tayi shi a gida</p><p>yawo ne bashi da dadi." tsohuwa ta ce,"a'a karki</p><p>wani fada ma Alhaji,ta daina ko takwara?" ummi</p><p>ta ce, eh.umma dan haushi ta shige daki ta barsu</p><p>anan. lokacin da su Abba suka je gidan</p><p>surukanshi an amshe su ba yabo ba fallasa,har</p><p>ma da zasu tafi aka basu (uniforms)din bishira na</p><p>boko wai ranar monday lallai ta tafi makaranta.</p><p>sun zaga gidajan danginta dake kusa,sannan</p><p>suka dawo gida.ya sameta tana fushi,shima</p><p>shareta yayi don yaji haushi barnar abincin da</p><p>tayi masa. dadin dadawa gidan nan yanda ya bar</p><p>shi haka ya tadda shi.ita kanta batayi wanka ba</p><p>ta kwanta tana ta uban bacci.fita yayi daga</p><p>gidan,sai goman dare sannan ya shigo ya rufe</p><p>gidan yaja ruwa yaje yayi wanka. sannan ya</p><p>shiga dakin,tsayawa yayi yana kallon gadon</p><p>mutsu-mutsu,sannan ga kaya nan duk a kai.ita</p><p>kuma tana kwance rike da wani littafi tana</p><p>karantawa. . Ya ce,"bishira wai me yasa bakya</p><p>son kakkabe gadonki? ta dube shi nifa duk na</p><p>gajine.tsaki yaja tare da cewa me kikayi da har</p><p>kika gaji? bani guri ni in gyara shimfidar zan</p><p>kwanta. shine ya kakkabe shimfidar sannan ya</p><p>kwanta.duk da ya cike da bukata amma haushi</p><p>ya hanashi kulata,sai ma baya da ya juya mata.</p><p>Abba yanada tsafta sosai,haka nan ma'abocin</p><p>son kamshi ne,duk da gyara gami da tsafta irin</p><p>na ummanshi wata ran har cin gyaranta yake</p><p>yi.sam baya so yaga ko ina rakwacan,yafi son</p><p>komai ya ganshi a muhallinsa. dole kullum shi ke</p><p>share gidan ya wanke ban daki,sannan da rana in</p><p>ya dawo ya dora abinci. litinin duk makaranta</p><p>suka koma daga dogon hutun kirismeti da suka</p><p>samu.Abba ya koma kan aikinsa na bautar</p><p>kasa.dan haka kusan tare suka fita da bishira ta</p><p>wuce makaranta shima ya wuce wurin koyar war</p><p>shi. . Ya rigata dawowa gidan,dan haka gajeren</p><p>wando ya samu ya shiga tsabtace gidan.sannan</p><p>ya dora dafa dukan taliya. uku da minti sha biyar</p><p>ta shigo ya dubeta ina kika tsaya? ta ce,ba ko</p><p>ina mufa makarantar mu biyu da rabi ake tashin</p><p>mu.dan ma na samu direban gidanmu da yazo</p><p>daukan kannena shine ya kawo ni. Abba y sake</p><p>had'e rai,motar gidanku? Bn baki kud'in mota</p><p>ba?Ta ce ka bani, ya ce to bn amnce ki sake</p><p>shiga motar gidanku ba. Ta ce,"kan me ? ya</p><p>harare ta ba tare d ya bata amsa ba,y nufi kicin</p><p>tabi bayanshi d harara,sannan ta shige d'aki. A</p><p>ganin Abba sam babu wani sauki da ya samu a</p><p>auranshi,nashi ganin wahala ya d'ebo ma</p><p>kanshi,kwanciyada ita ne kurum zai ce ya k'aru d</p><p>shi acikin auren. Ya shiga gidansu d</p><p>sallama,Umma ta amsa tana zaune kan sallaya</p><p>bayan ta idar d sallar Isha'i. Ta ce,Abba ba a je</p><p>an kwanta ba?ya zauna tare d d'an jan tsaki ta</p><p>ce,A'a ha,jikin ko garin? Ya ce,Umma gaskiya ni</p><p>abubuwa sun cud'e min,yarinyar nan tunda a</p><p>kawo ta sam ban huta ba. Umma ta saki dariya</p><p>"ka ji Abba d wani zance,dama ce maka a ka yi</p><p>ana bauta d hutu? Aure shi bautane. Ya ce,Tsaya</p><p>kiji fa ummata,kinga tun Asubahi in nayo Sallah</p><p>zan hau sharar gidan,in shirya in je gurin d nike</p><p>koyarwa. In dawo in dafa abnci,sannan in tafi</p><p>shago kuma don takaici in na zo kwanciya ni zan</p><p>kakka6e shimfid'a,ita bata iya komai ba ashe</p><p>daga gidan nasu.Ni fa har ta soma sure min......</p><p>"Kai Abba! Umma ta katse shi d sauri, kada in</p><p>kuma jin wannan furucin, kana hauka ne?yanzu d</p><p>fada min menene matsalarka?in dai abnci ne ka</p><p>bari zan diga aiko muku da shi. Ya ce umma ya</p><p>ya ma za a yi haka?Tab ai ba zai yi wu ba,Ta dai</p><p>zo ta koya sati d lahadi. Umma ta ce,To shi</p><p>kenan,tazo din.kayi ta hkr Abba,nasan ka kai ma</p><p>d zuciya,don Allah kada ka sake in ji wata</p><p>fitina,ka lalla6a matarka kuyi zamnku lfy. Abba</p><p>ya ce, To ko da ya sanar d Bishira cewa yana son</p><p>taje gurin ummansa ta koyo girki,sai ko ta tuma</p><p>ta ce ita ba zata je ba,dama dai gurin umman</p><p>Bashir ce, Ya ce,shi kuma gurin ummansa ya</p><p>turata,koda Asabar din tazo kin zuwa tayi,shi</p><p>kuma sai ya shareta ta ya daina girkinki. Sai dai</p><p>yaje gidn ummanshi yaci,hatta ranar litinin d suke</p><p>d makaranta bai dafa abncin ba da ya dawo a</p><p>galabaice da yunwa ta iso. Bashir ya ce, Ni har</p><p>fata nake wata rana 'yar sa' in'sa ta hadu ku</p><p>umma,wlh in mata shegen duka. Bishira ta ce,Ni</p><p>dai bata isa ba, in ma ita ce ta turo shi dn in</p><p>dinga zuwa gidnta to ba zanje ba. Haka suka yi</p><p>ta zagin umma,daga bisani Bishira ta mike ta tafi</p><p>dn kada ya dawo bata nan. Rashin iya girki ya</p><p>kawowa masoyan 2 rashin jutuwa,wanda ko</p><p>magana Abba bai cika yi mata ba. In ta zauna</p><p>tayi ta kuka tana mmk,me ta mishi ya juya mata</p><p>baya dan da nan? Yau kam abn ya yi kamar</p><p>kaurace mata ya yi daga dakin baccinta, ya dauki</p><p>filo ya tafi falo ya kwanta. Tayi ta kuka. Kasa</p><p>jurewa tayi ta mike ta bishi,kwankwasakofar tayi</p><p>kusan sau 3 ya ce "Waye?" cikin muryar kuka ta</p><p>ce, Ni ce, Abba don Allah ka bude. Ya kunna</p><p>wutar falon,sannan ya bude ta shigo ta zauna</p><p>kusa d shi, ta ce, Abba wai mi na maka ne ka</p><p>tsane ni? ka duba fa ko wata daya ban rufa</p><p>ba,kasan dai yadda a ka yi auranmu yanzun in</p><p>Mahaifana suka ji dariya za su Min. Amma ba</p><p>komai sai biredi ta samu ta k'asuma,d ya tafi</p><p>shago sai ta yafa mayafinta ta nufin gidn umman</p><p>bashir. koda tai sallama umman tana kan turmi</p><p>zaune suna ta ganzar rake ita d su bishir. umman</p><p>Abba ce ta aiko musu da shi don rashin Adalci</p><p>suna sha suna yi da ita. Suka shiga lale d zuwan</p><p>Bishira, ta kalli bashir 'Ina fushi da kai, shine</p><p>wato har yanzun ba ka zo ba ko? ya ce, Tab, sau</p><p>2 ina zuwa zan shiga gidan sai yaya Abba ya fito</p><p>ya ce min kina bacci, na gane nufinshi baya son</p><p>ina shiga masa gida,shi yasa na share.Bishira ta</p><p>ce Um, wannan Yayan naka halinshi sai shi,</p><p>yanzun ma fa fushi yake dani. Umma ta ce," A</p><p>kan Me kuma? wai shi dole sai nazo gurin</p><p>ummarshi na koyi girki, ai ko nace wlh ba ni</p><p>zuwa. Umman bishir ta rafka salati. sannan tace</p><p>'Naga ta kaina ni Sahura,kai Allah ya isa</p><p>tsakanina d Suwaiba. yanzun kuma ta gama d ni</p><p>ke ta sako a gaba, so take ta shiga tsakaninku?'</p><p>Abba ya kura mata ido, yasan abn d ta fada</p><p>gaskiya ne ya ce "Me na miki to?" ta kalle shi,"Ba</p><p>ka ma san abn d kayi min ba?Ta ga daya yanzun</p><p>fa kaurace min kayi. Ya ce ba kya gyara</p><p>gadonki,ni kuma na gaji d gyarawa. Ta saka tafin</p><p>hannunta cikin nashi zo muje in gyara.</p><p>Tausayinta ya ji,ya tashi ya bita yana kallonta</p><p>duk kakarin d ta yi dn t gyara ta kasa. Sai dai shi</p><p>ne ya gyara, Sannan ya janyo ta suka</p><p>kwanta.Sam bata d gardama ko nuna gajiyawa a</p><p>gurin ba shi hakkinshi na kwanciya. In zai zo sau</p><p>nawa ba ya damunta,gurin da ta ke birge shi</p><p>kenan. Amma ba wannan ba ne kadai namiji ke</p><p>bukata,Musammanirin Abba dan kwalisa. Wata</p><p>ranar Jumma'a bayan sun tashi daga mkrntr da</p><p>ya ke koyarwa,ya ce da Ummi ta jira shi zaya</p><p>aike ta gida. Kudin cefane ya bata ya ce taje ta</p><p>sai kayan miya d nama ta kai gidanshi, Sannan</p><p>ta tsaya tayi masa miyar tare d yi masa sakwara.</p><p>. Shi kuma zai je ya fada ma umma, dn yana son</p><p>d dunkunan wata amarya d yake son karasawa</p><p>ummi ta zun6uri baki bayan ta amshi kudin ta</p><p>wuce tana yankun-kunai, ya ce "Ke!" ta waigo "Zo</p><p>nan . ta dawo, Ya kama mata kunne, Kin san</p><p>kwana 2 bn ta6a lafiyarki ba ko?to kiyi abn d yau</p><p>zaki gwammace ba ki zo duniya ba. ya</p><p>rankwashe mata kai, Sannan ta wuce tayi ce</p><p>fanan ta nufi gidn Matar gidn tana zaune d kayan</p><p>mkrnt a jikinta,,Ummi ta mata Sannu harara ta</p><p>zuba ma Ummi, Ummi ko ta rama,sannan ta ce</p><p>"Mijinki ya ce in zo in yi mashi sakwara d miya.</p><p>"Bishira ta ce, To sai ki koma gidn ubnki ki dauko</p><p>tukunya d murhu b dai nawa ba, Ummi ta ce, To</p><p>ni dai gaskiya d ubana ba. Bishira ta taso tana</p><p>cewa Sai na wa? Ummi ta ce, Oho,amma ba</p><p>nawa ba. Za ta kai mata duka ta goce ta ajiye</p><p>mata kayan miyan ta ce " Gashi sai kiyi, kila ma</p><p>baki iya girki ba ne. Taje ta fadawa umma, Umma</p><p>ta ce "Ke ummi karya ki ke daga zuwa zata hauki</p><p>d zagi sai ka ce Mahaukacciya? To kije ki fada</p><p>wa Abban in ya so sai kuje tare ya fada mata</p><p>amma fa kada ki ce masa ta zage ki, ki ce masa</p><p>dai yazo ya fada mata zaki tayata. Ummi ko kyn</p><p>mkrnt ba ta cire ba ta nufi gurinshi,yana tsaka</p><p>dinki taje,Ummi sai ce masa tayi ta ce ba zam</p><p>mata girki d tukunya ba. Ya ce Muje gidn ganin</p><p>nan. "a kofar gida ta zauna tana jiranshi, sai d y</p><p>shiga sannan ta bishi. Tana tsaye tsakar gida</p><p>tana jin rigimar d suke yi.Bishira ta dage ita fa</p><p>babu mai yi mata girki d kayan aiki, shi kuma ya</p><p>ce tunda ba a koya miki girki ba a gidnku dole ne</p><p>in sa kanwata ta mini. Ta ce ya turo Fati</p><p>mana,wannan maran kunyar yarinyar mata</p><p>tarbiyya ba za ta zo mata gida ta zage ta ba.</p><p>Ran Abba ya 6aci, ya ce Ga ki nan mara</p><p>tarbiya,ina fada kina fada ina matsayin</p><p>mijinki.,Ummi tafi ki tarbiyya domin uwar d ta</p><p>bata tarbiyya ita ta bani har ki ka amince ki ka</p><p>aure Ni. Ta ce, Ta baka tarbiyya ko ta asirceka?</p><p>Ta mallake ka har baka ganin Mahaifiyarka d</p><p>gashi sai ita. Zancen ya soki Abba sosai Har ya</p><p>daga hannu zai mareta sai kuma ya fasa,ya juya</p><p>ya fita. Fatanshi Allah ya sa ummi bata ji ba,dn</p><p>yasan tsaf sai ta fada ma Umma. Tana zaune</p><p>gefen rijiya ya nufo ta,Ummi ina kayan Miyan?</p><p>tana nuna masa su tare d cewa 'Gasu ya</p><p>ce,Dauki ki kai ma ummana. Har ta kai bakin kofa</p><p>ya sake cewa "Ummi!"ta tsaya ya zo ya kalleta</p><p>Ummi kin ji me Bishira ta ce? Ummi ta dube shi</p><p>cikin ido,,sannan ta kalli hanyar fita. Naji duk</p><p>abnda ku ka ce,Ya lumshe ido "Ummi dn Allah ka</p><p>da ki fad ma Umma. Ta tsura mashi ido,bata</p><p>ta6a jin Abba ya yi mata magana cikin tattausar</p><p>murya ba sai yau tunda ta taso. Ta ce, "To." Ta</p><p>juya, yasa ke cewa Ummi. a waiwayo Don Allah</p><p>kin ji? kai kurum ta daga sannan ta fita Tafe take</p><p>tana Mmkn me yasa Abba baya son Umma taji</p><p>zagin da Matarshi tayi Mata? Hakika d taso</p><p>Sanar da Umma amma yanda ya yi 'yar Murya</p><p>yana rokonta sai t jure,koda taje gida bata sanar</p><p>d Umma ba. Cewa tayi kawai ya ce a ma barshi</p><p>sai dai cikin ranta ta tsani Matar Yaya Abba fiye</p><p>d tsanar d ta yi wa Abba. Shi kuwa Abba duk</p><p>wata hulda tsakaninnshi d matarshi ya dakatar d</p><p>ita,saboda yana son nuna mata matsayin umma a</p><p>gurinshi. In ya fita tn Asubahi bacce ke kawo shi</p><p>gidan,wanka ma cn gdn Umma yake yi sai ya ce</p><p>mata Bishira tana mkrnt. A cikin rana t 3 hnklnta</p><p>y gama tashi,taje t fadawa umman Bashir,ta aiko</p><p>yaje tayi ta fadan gami d zazzagnshi,ya bata hkr</p><p>y fita. Amma sam Bishira, bai canza mata ba. Sai</p><p>ma sabon salon d ya dauko na yn kaura daga</p><p>falon zuwa dayan dakin d babu kowa,dk kayn</p><p>sawanshi y tattara y koma can. Abba yana d zcy</p><p>g taurin kai,Umman Bashir ta ce,"Yanzun in kin</p><p>samu saukinshi to uwar goyonshi ki ka fada</p><p>mawa, km gwada ki gani za ki gane ta fini a</p><p>gurinsa. Sannan ki g aikin asiri. . Shi kuma zai je</p><p>ya fada ma umma, dn yana son d dunkunan wata</p><p>amarya d yake son karasawa ummi ta zun6uri</p><p>baki bayan ta amshi kudin ta wuce tana yankun-</p><p>kunai, ya ce "Ke!" ta waigo "Zo nan . ta dawo, Ya</p><p>kama mata kunne, Kin san kwana 2 bn ta6a</p><p>lafiyarki ba ko?to kiyi abn d yau zaki gwammace</p><p>ba ki zo duniya ba. ya rankwashe mata kai,</p><p>Sannan ta wuce tayi ce fanan ta nufi gidn Matar</p><p>gidn tana zaune d kayan mkrnt a jikinta,,Ummi ta</p><p>mata Sannu harara ta zuba ma Ummi, Ummi ko</p><p>ta rama,sannan ta ce "Mijinki ya ce in zo in yi</p><p>mashi sakwara d miya. "Bishira ta ce, To sai ki</p><p>koma gidn ubnki ki dauko tukunya d murhu b dai</p><p>nawa ba, Ummi ta ce, To ni dai gaskiya d ubana</p><p>ba. Bishira ta taso tana cewa Sai na wa? Ummi</p><p>ta ce, Oho,amma ba nawa ba. Za ta kai mata</p><p>duka ta goce ta ajiye mata kayan miyan ta ce "</p><p>Gashi sai kiyi, kila ma baki iya girki ba ne. Taje</p><p>ta fadawa umma, Umma ta ce "Ke ummi karya ki</p><p>ke daga zuwa zata hauki d zagi sai ka ce</p><p>Mahaukacciya? To kije ki fada wa Abban in ya so</p><p>sai kuje tare ya fada mata amma fa kada ki ce</p><p>masa ta zage ki, ki ce masa dai yazo ya fada</p><p>mata zaki tayata. Ummi ko kyn mkrnt ba ta cire</p><p>ba ta nufi gurinshi,yana tsaka dinki taje,Ummi sai</p><p>ce masa tayi ta ce ba zam mata girki d tukunya</p><p>ba. Ya ce Muje gidn ganin nan. "a kofar gida ta</p><p>zauna tana jiranshi, sai d y shiga sannan ta bishi.</p><p>Tana tsaye tsakar gida tana jin rigimar d suke</p><p>yi.Bishira ta dage ita fa babu mai yi mata girki d</p><p>kayan aiki, shi kuma ya ce tunda ba a koya miki</p><p>girki ba a gidnku dole ne in sa kanwata ta mini.</p><p>Ta ce ya turo Fati mana,wannan maran kunyar</p><p>yarinyar mata tarbiyya ba za ta zo mata gida ta</p><p>zage ta ba. Ran Abba ya 6aci, ya ce Ga ki nan</p><p>mara tarbiya,ina fada kina fada ina matsayin</p><p>mijinki.,Ummi tafi ki tarbiyya domin uwar d ta</p><p>bata tarbiyya ita ta bani har ki ka amince ki ka</p><p>aure Ni. Ta ce, Ta baka tarbiyya ko ta asirceka?</p><p>Ta mallake ka har baka ganin Mahaifiyarka d</p><p>gashi sai ita. Zancen ya soki Abba sosai Har ya</p><p>daga hannu zai mareta sai kuma ya fasa,ya juya</p><p>ya fita. Fatanshi Allah ya sa ummi bata ji ba,dn</p><p>yasan tsaf sai ta fada ma Umma. Tana zaune</p><p>gefen rijiya ya nufo ta,Ummi ina kayan Miyan?</p><p>tana nuna masa su tare d cewa 'Gasu ya</p><p>ce,Dauki ki kai ma ummana. Har ta kai bakin kofa</p><p>ya sake cewa "Ummi!"ta tsaya ya zo ya kalleta</p><p>Ummi kin ji me Bishira ta ce? Ummi ta dube shi</p><p>cikin ido,,sannan ta kalli hanyar fita. Naji duk</p><p>abnda ku ka ce,Ya lumshe ido "Ummi dn Allah ka</p><p>da ki fad ma Umma. Ta tsura mashi ido,bata</p><p>ta6a jin Abba ya yi mata magana cikin tattausar</p><p>murya ba sai yau tunda ta taso. Ta ce, "To." Ta</p><p>juya, yasa ke cewa Ummi. a waiwayo Don Allah</p><p>kin ji? kai kurum ta daga sannan ta fita Tafe take</p><p>tana Mmkn me yasa Abba baya son Umma taji</p><p>zagin da Matarshi tayi Mata? Hakika d taso</p><p>Sanar da Umma amma yanda ya yi 'yar Murya</p><p>yana rokonta sai t jure,koda taje gida bata sanar</p><p>d Umma ba. Cewa tayi kawai ya ce a ma barshi</p><p>sai dai cikin ranta ta tsani Matar Yaya Abba fiye</p><p>d tsanar d ta yi wa Abba. Shi kuwa Abba duk</p><p>wata hulda tsakaninnshi d matarshi ya dakatar d</p><p>ita,saboda yana son nuna mata matsayin umma a</p><p>gurinshi. In ya fita tn Asubahi bacce ke kawo shi</p><p>gidan,wanka ma cn gdn Umma yake yi sai ya ce</p><p>mata Bishira tana mkrnt. A cikin rana t 3 hnklnta</p><p>y gama tashi,taje t fadawa umman Bashir,ta aiko</p><p>yaje tayi ta fadan gami d zazzagnshi,ya bata hkr</p><p>y fita. Amma sam Bishira, bai canza mata ba. Sai</p><p>ma sabon salon d ya dauko na yn kaura daga</p><p>falon zuwa dayan dakin d babu kowa,dk kayn</p><p>sawanshi y tattara y koma can. Abba yana d zcy</p><p>g taurin kai,Umman Bashir ta ce,"Yanzun in kin</p><p>samu saukinshi to uwar goyonshi ki ka fada</p><p>mawa, km gwada ki gani za ki gane ta fini a</p><p>gurinsa. Sannan ki g aikin asiri. . Bishira t nufi</p><p>gurin umma t same t zaune tana yankan ku6ewar</p><p>miya. tun d a ka kawo ta yau ne rana ta farko d</p><p>ta zo. Umma ta ce, "A'a Maraba d Bshra. shigo</p><p>koda yake je ki gaida tsohuwa. Taje suks</p><p>gaisa,Tsohuwa ta ce Ke dai wannan yarinyar</p><p>kirkinki d sauki,a ce tunda ki ka zo unguwar nan</p><p>baki ta6a zuwa kin gaida iyayensa ba? Umma t</p><p>jiyo 6aram6aramar d Tsohuwa ke yi,d sauri tazo</p><p>ta ce Tsohuwa b laifinta ba ne, laifin Abba ne. Ba</p><p>sai ya kawo ta ba za tazo? Jin haka Bishira ta</p><p>samu bakin magana,wlh Tsohuwa laifinsa ne nayi</p><p>in zo ya ki,yanzun hk kararsa na kawo. in y fita</p><p>tn Asubahi sai dare bana sanin shigowarshi.</p><p>Yanzun ni tn jiya ma bn sa shi a idona ba,Umma</p><p>ta ce Shi Abban ne ke hk? Ta ce IIlahi kuwa, ni</p><p>bana son in je gidanmu in kai karanshi ne amma</p><p>shi baya gani,yanzun fa ya tattare y koma dakin</p><p>nan d ba kowa. Ran Umma ya 6aci, a irin</p><p>tarbiyyar da ta yi wa Abba bata zaci zai</p><p>wulaqanta mace ba, . Ummi tana shigowa daga</p><p>Islamiyya ta ce,maza d sauri shagon yayanki kira</p><p>mn shi. kan keke ta same shi yana t dinki, t shiga</p><p>d sallama,sauran yaran shagon ma suna t</p><p>dinki,ta ce yaya Abba Umma ta ce kazo yanzu.</p><p>Ya dube ta me ya faru?Ta girgiza kai,bn sani ba,</p><p>ta dai ce kazo. Take ya mike,ita km t fice d gudu.</p><p>A ranshi ya ce ko yaushi Ummi zata yi hnkl t</p><p>dinga tafiya irin t mata? Yana shiga gidn umma t</p><p>rufe shi d fada,ba tare d tambaye shi dalilin shi</p><p>na yi wa matarshi abn d yake mata ba. Ta</p><p>ce,"Maza gata nan dakin Tsohuwa kaje ku koma</p><p>gida ka bata hkr. kanshi na kasa bai ce kala ba</p><p>ya nufi dakin Tsohuwa. Ya dube ta Tashi muje.</p><p>Har daki suka shiga ya dube ta kiyi hkr. Ta ce, To</p><p>nima kayi hkr. Ya ce kin ga matar d ki ke zagi ta</p><p>baki gaskiya alhalin danta nake fushi. Ya ce ki</p><p>kula kici albarkacinta karki sake ki km fadin wata</p><p>mummunar magana a kanta,km hucewar da nayi</p><p>da hkrn d na baki kada ki zata dn kin isa</p><p>ne,umurninta na cika,ta ce to na daina. . Da dare</p><p>gidn Umma ya je ya bata hkrn dn yaga ta dau</p><p>zafi, ya ce, "Umma yarinyar nan bata kyautawa,</p><p>abn d take min ni d har zan kai wa yarta kara na</p><p>gaji. Umma ta ce, kada ka soma,kayi t hkr in</p><p>girkin ne matsalarku tunda bata son tazo ta koya</p><p>kai ai ka iya,sai ka ware lkc ka zauna ka dinga</p><p>koya mata kasa tayi kana kallo har ta iya. Ya ce</p><p>To, amma kin huce kin daina haushina,? Umma</p><p>ta ce , sam ban jin haushinka Abba raina yana</p><p>6aci ne in ji an ce ga laifinka, ya ce to na gode</p><p>ummata. Shawarar Ummanshi ya dauka,ranar</p><p>farko ya ce ta dora farar shinka fa sai da ya koya</p><p>mata yadda zata dafata kashi-kashi,harkala 4.</p><p>Sannan ya ce,tayi jajjage tayi tana wai-wai ita</p><p>duk ta gaji. Yana gefe zaune d wayarshi yana ta</p><p>Game sai d yasa ta tayi miyar komai yana nuna</p><p>mata yadda zata yi. Sai gashi kafin wani lkc</p><p>Bishira ta iya girki, gurin tuwo ne a ka danfi</p><p>samun matsala,sukai kwana 4 suna yi yana</p><p>gudaji. . Yanzu sun samu jituwa dk d dai abncin</p><p>ma ba ya samunshi kn lkc sai dai kuma fannin</p><p>tsafta.Duk da yakan zage ya gyara gidn d shara</p><p>kullum in ya dawo Masallaci ya wanke bayi</p><p>fes,cikin dakunan a nan matsalar take, sannan</p><p>jikinta ma bata son gyara shi. Cikin haka ta kamu</p><p>d laulayin ciki sun je asibti sun samu magunguna</p><p>dk d hk amai ko ruwa tasha sai y dawo, dk hnkln</p><p>Abba ya tashi y kira wayar Anti ya sanar d ita.</p><p>Da dare tazo dubata ita d mijinta suka zo,sun</p><p>same su Abba yana bata tea,ganin Anty,Bishira ta</p><p>soma kuka wai ita zata bi Anty. Anty ta ce A"a ki</p><p>zauna ga mijinki na kula d ke, ni dai bana zama</p><p>in kin je gidana ba zai miki dadi ba. Sunyi Murna</p><p>d Abba ya fada musu ciki ne, take Anty ta kira</p><p>Mahaifiyarsu ta fada mata. "Tabdi!" in ji hjy. tun</p><p>yanzun? To Allah ya raba lfy. Anty ta ce to sai</p><p>anjima,dn jin yadda hjyr bata yi murna d cikin ba,</p><p>km bata so Abba ya gane. Ta dubi Bishira, Momy</p><p>ta ce a gaisheki d jiki, Bishira ta ce ba za ta zo</p><p>ba?Rannan d muka yi waya d Anty Aisha ta ce</p><p>min ita ko Momy taje / ZURFIN CIKI book 1 part 8</p><p>ZURFIN CIKI book 1 part 8</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 22:01</p><p>Ni kuma sai naga ta min qanqanta. Ummi ta ce,</p><p>ahj kaima ka sai mota ne mu dinga shiga? ya ce,</p><p>to xan siya mamana, ki dunga min addu'a kinji?</p><p>umma ta ce, nayi murna abbana, ya yi abin</p><p>hawa. bari in je masa albishir. tsohuwa ta taba</p><p>baki, sannan ta ce, kullum burinku da tattalinku</p><p>na ne sunan mlm ne, ita takwara kun maida ta</p><p>baya. umma ta ce, sai na dawo. ta fice, dan</p><p>tasan tsohuwa da mita. abba yayi murna samun</p><p>abin hawa, domin da dan nisa in da ya ke xuwa,</p><p>waton makarantarsu ummi, in ya shirya ya kanxo</p><p>gidansu ummanshi ya dauki ummi su tafi. jwanci</p><p>tashi su ummi an shiga aji uku, lkcn abba ya</p><p>gama service din shi, ya amshi certificate. bayan</p><p>sun je sun yi faretinsu. dakin umma ya dire, ummi</p><p>tunda ya shigo take kallonshi da kayan yan</p><p>bautar qasa. ita kam kayan suna birgeta, ya dube</p><p>ta kallan fa? ta dauke kanta, sannan ta murguda</p><p>baki, umma ta nufi kicin tana dariyar halin ummi</p><p>da abba. dama ummin tana kwance kan kujera ne</p><p>tana wasa da wayar umma, yace ta ga me kyau</p><p>tana ta kallona, ba xa dai ki samu miji mai kyau</p><p>kamar ni ba. . Ba ta san lkcn da ta ce, tir, da me</p><p>kama da kai gara in mutu banyi aure ba. ya</p><p>dubeta da sauri sannan ya dauki hijab din umma</p><p>ya jefeta, tare da cewa, mummuna, qaxama gaki</p><p>mahaukaciya. wama xai aure ki? sai kn</p><p>mahaukaci dan umanki. ta hade rai tana</p><p>kallanshi, ya ce daina kallona me kama da</p><p>goggon biri, in kuma kika min wata magana in</p><p>xane ki. fuu ta tashi ta shige uwar daki. tana jiyo</p><p>hiransu da umma, in da yake cewa, naso a ce</p><p>ummi tana aji uku ne lkcn da xan bar</p><p>makarantantan mu bari tare, saboda sam bata ji.</p><p>gashi akwai mlmn da aka samu a makarantan ma</p><p>su bata yara, sannan tana da wata qawa da aka</p><p>kama da wani malami a bayin makaranta. sai da</p><p>taci duka sannan ta rabu da yarinyar. umma ta</p><p>daff qirji tare da cewa, na siige su ni suwaiba, to</p><p>ko amina ce qawan tata? abba ya ce, ba ita ba</p><p>ce. umma ta ce, hu-um, to makarantar boko dai</p><p>ba tilas, da yaro ya fada cikin irin wannan</p><p>rayuwar gara a bar bokm. abba ya ce, ina ganin</p><p>xan nemi koyarwa a makarantan, in naci sa'a an</p><p>daukeni to sai ta qarasa har lkcn. . Abba ya ce</p><p>Ina ganin zan nemi koyarwa a mkrntr in na ci sa'</p><p>an daukeni to sai ta ci gaba hr zuwa lkcn d zata</p><p>gama,sai in bar koyarwar. Umma ta ce,To hkn za</p><p>a yi. Ummi km daga cikn dk take mgn ita 1,ta ce</p><p>Da na shiga 3,ka ci gaba d koyarwa a mkrntrm ko</p><p>dai ka ci gaba d hn ni sakewa? In yana aji</p><p>numfashi mai karfi ma bana iya yin shi,Allah yasa</p><p>kada a dauke ka. Murna kmr me gurin Ummi d</p><p>taga an yi bakwai 2 Abba bai zo ba,hk na nufin</p><p>ba a dauke shi a mkrntr ba. . Don hk ta ci gaba d</p><p>tsula tsiyarta. Kwatam! a sati na 3 sai gashi ya</p><p>zo daukarta suje mkrnt,hr kuka sai d ummi tayi</p><p>don takaici. Daga dawowarshi km y dora mata</p><p>daga in d ya tsaya,d rashin mutunci,hr t soma yi</p><p>mishi fatan mutuwa,dn tana ganin matsawar</p><p>Abba yana raye baza ta ta6a jin dadin rayuwar</p><p>dny ba. Tunda cikin bishira ya samu t daina zuwa</p><p>mkrnt, Abba bai matsa mata ba,amma d yaga t</p><p>soma dan jin dadi,sai ya ce ta fara zuwa. . Haka</p><p>ta ke zuwan yau taje gobe ta ki zuwa ta ce ba a</p><p>komai hr lkcn biyn kudi yayi. Duk d tsadar mkrntr</p><p>hk Abba ya fige ya biya,daga bisani ma sai ta</p><p>daina zuwa, Abba ya kira Anty a waya ya fada</p><p>mata Bishira ta ki zuwa mkrnt. Yaya-yayi ta</p><p>ki,shi km gsky ta zo tayi mata fada,dn ba ya so</p><p>su momy suga laifinshi., Don ko d suka je</p><p>gaisuwar surukai sai d ta ce "Kada a katsewa</p><p>'yarta krt"Anti ta ce za ta zo. . Ai kuwa ranar d</p><p>Anty tazo taga ta kaici gidn Bishira,ko ina</p><p>datti,Falon d ta leka dk kura d yanar gizo-gzo.</p><p>Cikin dakin baccinsu kuwa ko ina yamutse d</p><p>kaya,bngo dk t tofe shi d miyau,sannan g wani</p><p>gwangwani madara gefenta ta kusan cika shi d</p><p>miyau. Gashin kanta rabi an tsefe shi rabi ba a</p><p>tsefe ba.jikinta fari sol tamkar bai ta6a ganin</p><p>ruwa ba. Anty t doka salati tare d cewa Bishira</p><p>me zan gani hk?Dan ubnki hk ki k dawo? Dubi</p><p>gdnk?dubu kanki? A kanki a ka soma ciki?nan t</p><p>zauna ta zageta tas, sannan ta taya t suka gyara</p><p>gidn suna yi tana fada. Ta ce Hk ki ka ga ina yi a</p><p>gidana?Ko sauran jama'a hk suke yi? Za ki sa a</p><p>zagi uwarmu a ce an sangarta ki alhalin aikin</p><p>gida dk a na sa ku.Sannan kin ki mkrnt,to ki sani</p><p>kanki zaki cuta dn kuwa dk ranar d mijinki y</p><p>zama wani abu 'yar boko zaya nema ya tafi d ita</p><p>cikin lamuranshi. . Zan km hada ki d momy.byn</p><p>sun gyara gidn t sata tayi wanka t dauki kaya</p><p>masu kyau t saka. Gwangwanin miyau tasa t tayi</p><p>jifa dashi,ta ce ki dinga saka sweet ko goro a</p><p>bakinki zanje nan d sati 1 zan dauko momy muzo</p><p>tare. kin san dai me zai biyo baya. Abba da ya</p><p>shigo gdn byn Isha'i dk d cewa dare ne sai d y</p><p>gane an tsaftace gdn,Domin kamshi tare d iskar</p><p>da ke kadawa a gdn sun bayyana hk. Dakin ta da</p><p>ya yi wa kaura yau kam hr bakin gado,ganin t</p><p>cikin kwalliya yasa shi cikin wani yanayi wanda</p><p>ya kwana 2 bai shiga ba. Ko abncin bai nema</p><p>ba,ya shiga caftar Syy,wnd ita ma dk d tana</p><p>laulayi tana ra'ayin hkn,don hk sai suka rankaya.</p><p>Kwana 2 ya dan samu sauki kazantar dn tana</p><p>tsoron momynsu tazo ta gani,sannan tana zuwa</p><p>mkrnt. Amma d momyn tazo tayi mata fada t</p><p>tafi,shi kenan sai ta koma gdn jiya,dama</p><p>Hausawa sun ce mai hali ba ya fasa Halinsa.</p><p>Haka dai hr cikin ya tsufa Umma tasa shi ya sayi</p><p>dk wani abu da mai jego da jaririnta za su</p><p>bukata. . Ita km ta daka yajin mai jego ta tanadi</p><p>sabulun salo zuwa Kwallin da za a sa ma jariri.</p><p>Wani dare Abba y kira Umma,Alhj ne y daga nan</p><p>y sanr d su bishira bata d lfy,yana ganin haiuwa</p><p>ce. Alhj d kns y raka umma hr gidn suka buga</p><p>Abba ya bude,suka shiga.Ranar Alhj y yi burin</p><p>mota,dmn d yana d mota yanzun sai su tafi</p><p>assibiti. Bishira bata d juriya,dn hk sai raki take</p><p>yi,tana fadin a kaita assibiti. A daddafe suka kai 4</p><p>dare Ahlj ya je ya taso abokinshi suka kaita</p><p>assibiti tare d su umma,karfe 8 na safe ta haifi</p><p>danta namiji. . Umman Bashir d taji sai ta hau</p><p>fadan me ya sa ba a sanr d ita ba?Alhj karami ya</p><p>rufeta d fadan cewa,ita wace irin mutum ce? Sam</p><p>ita bata son Alkairi ba,sannan ya fita ya yi wa</p><p>Alhj babba barka,dg assibti gdnsu iyayenta suka</p><p>wuce d ita ba tare d sun nemi shawarar mijinta</p><p>ba ko ta iyayenshi. Hjy ce ta bada wannan</p><p>umurnin,rai 6ace Abba ya zo gurin umma dn ita</p><p>ta baro gurin ne d iyayenta suka iso. Ya</p><p>ce,"dama umma umma haka akeyi sai a daukar</p><p>wa mu2m mata a tafi da ita ba tare da neman</p><p>izini ba?to gaskiya bazan yarda ba." umma ta</p><p>ce,"ka kyalesu, Allah ya raya.shi kenan, tafiya da</p><p>ita ba laifi bane tunda ita kadai ce a gidan ba mai</p><p>kula da ita matsalar dai da basu nemi izininka</p><p>ba." ya ce,"sai ka ce ba zamana take ba?</p><p>wankan gidan addini ne?dama fa niyyata in kawo</p><p>ta nan gidan ki lura da ita." umma ta ce,"to</p><p>yanxu dai hakuri kawai zan baka,ka bar</p><p>maganar." tayi ta lallashinsa har dai ya</p><p>hakura,amma shifa ya dau alwashin sai ya nuna</p><p>musu nasa ikon. umma ta hada abubuwan data</p><p>tanada suka tafi da makota.bayan sun shiga</p><p>gidan aka kai su gefen da maijego take. sun sami</p><p>dakin tamkam da jama'a nan dai suka zauna aka</p><p>gaisa,sa wani gani-gani ake musu ga talakawa.</p><p>umma ta ce,bishira ina ummar taku mu gaisa?sai</p><p>da ta yatsin fuska sannan ta kalli</p><p>kanwarta"sumayy a kije ki cewa momy ga</p><p>baki,koda yake kice mata yan gidan su Abba ne."</p><p>Hajiya zainu tana zaune da kawayenta da suka zo</p><p>barka, tana labarta musu rashin mutuncin dangin</p><p>mijin bishira dashi kanshi mijin. ta ce,"yau</p><p>kwananta uku tunda tazo gidan nan bashi ba</p><p>danginshi,kuma yanda bishiran take fada mana</p><p>laifin masu rikonshi wato wan ubansa da</p><p>matarsa. sun mallake yaron sai abinda suka</p><p>ce,hajiya nafi ta ce,"ku nuna musu kuskurensu ne</p><p>yanzu haka tunda kika ga sun mallake shi kila</p><p>shine mai dan samun gunshi suke ci." Hajiya</p><p>sabuwa ta ce"shi yasa auran talaka ko tsiya,yar</p><p>wajena Amina da tazo min da wani wai sun hadu</p><p>a ummara,koda na bincika sai na tarar likita</p><p>ne.karamin likita ubanshi dashi ya dogara na ce</p><p>ba dani ba." Hajiya zainu ta ce"ai gara shi</p><p>wannan fa tela ne." "TELA?" kawayen suka hada</p><p>baki, ta ce"au dama ku duk fadan da nayi lokacin</p><p>biki baku ji ba? tabi ta nace sai shi gashi nan</p><p>yanzun ya wulakanta mu." Ta dube su d</p><p>wulanqacin da ya fi Ki haihu kwana 3 tun dg</p><p>asibiti miji bai kuma bi ta kanki ba? Hjy Nafi ta</p><p>ce in bai zo don kowa ba ma yazo dn dansa.</p><p>Zainu ta ce Ina nan ina jira ko shi ko danginshi</p><p>domin........ Sumayya ce ta katse su da sallama.</p><p>Sannan tace momy wai kizo ga yan gidan su</p><p>Abba sun zo. su duka suka mike ita d kawaynta</p><p>suka nufi gurin su Umma. Hjy Zainu ta kalli gurin</p><p>d su umma suke,sannan ta kalli Bishira,</p><p>wadannan sune 'yan gdn Su Abban? Bishira ta ce</p><p>Eh ummar tasa ce gata nan. ta nuna umma Hjy</p><p>zainu suka kalli juna d kawayenta sannan suka yi</p><p>'yar dry wanda hkn ya kashe jikin umman. Tasan</p><p>cewa akwai wani tanadi d a ka yi mata. Hjy</p><p>Zainu ta ce d kawayenta ku mu zauna,aikin</p><p>zaune yafi na tsaye. Suka zauna. Ta kalli umma</p><p>Dama ko ina son ganinki,ke ce uwar goyon tasa</p><p>ko? ta ci gaba To gsky ba ki yi wa dnki tarbiyya</p><p>ba,sbd rashin mutunci a yi maka haihuwa amma</p><p>kwana 3 ba zuwa ba aike? Kuma sai yau za ku</p><p>kwaso kafa kuzo in 'yarki ce zaki so hk?umma</p><p>tayi shirun tana tunani, ta kuma rasa me zata ce</p><p>dn tund take ba a ta6a ci mata mutunci ba irin</p><p>wannan ba. Amma ita bata iya fada ba,dn hk sai</p><p>ta ce, To Hjy a yi hkr, bn san cewa Abba bai zo</p><p>ba,Amma zan tsawata mishi,dn kuwa bai kyauta</p><p>ba. Sai dai km shi ma bai so yadda a ka dauko</p><p>masa mata ba izininshi ba,dn ya same ni d</p><p>fushinsa ya ce min shi ba ya son wankan gidan</p><p>nan,sannan ba a yi shawara da shi ba a ka taho</p><p>d ita nan. kin ga km hkn bai dace ba..........</p><p>"Dakata min Hjy zainu ta katse ta Shi ne ya</p><p>haifar min 'yar d hr zan tsaya neman izininsa?</p><p>shi kuma a wa? Ramatu mokociyarsu ta ce "Miji</p><p>km hjy ai ba abn wasa ba ne. hjy nafi ta ce ko?to</p><p>ke kinji hjy Zainu tabdi!Tun farko kuskuran naki</p><p>ne da ki ka bar 'yarki tayi irin wannan auran na</p><p>rainin d tsiya. Umma ta ce d abokan tafiyarta</p><p>wadanda ko dan (ba) ba su ce ba, ta ce kuzo</p><p>muje"Ta dubi hjyr "Allah ya baku hkr.Hjy zainu ta</p><p>ce Ai ban ga gama maganata ba. umma ta ce,To</p><p>fadi ina jinki. Hjy zainu ta ce Sako ne zuwa ga</p><p>danki ki fada masa ba komai muke nema dg gare</p><p>shi ba,abn d ya siya ma na yaron dk mun canza</p><p>wasu sdb dk 'yan gida ne. Bukatarmu ya zo ya yi</p><p>wa yaronsa huduba,in km ya kai gobe za mu yi</p><p>masa d kanmu. umma ta ce Abba ya yi wa dansa</p><p>huduba,tn lkcn d a ka haife shi. Hjy Zainu ta</p><p>ce,To ai bai yi shawara d uwar yaron ba,ko d ya</p><p>ke ga ki dawa zaiyi shawara? Uwar d ta haife shi</p><p>ma bata zama komai ba, a dai ji tsoron Allah.</p><p>umma jiki ba karfi ta fito. Su Ramatu suka biyo</p><p>ta hr kuka sai d umma tayi dn takaici. koda taje</p><p>gida sam bata fada ma kowa komai ba,illa dai dk</p><p>wanda ke gidn yasan yau umma tana cikin 6acin</p><p>rai. Hatta ummi da bata d kn gado sai d tayi ta</p><p>tambayrta,umma baki d lfy ne?ta ce Eh,kaine ke</p><p>ciwo. Da ta zauna sai ta shiga tunani so take</p><p>lallai sai ta gane aibnta,ko kasawarta akn Abba.</p><p>Ta kasa fahimtar mallakr d a ke fadin tayi wa</p><p>Abba. Tana ganin nuna tsanarta ga Abba shi ne</p><p>mafitarta. Abba ne ya katse mata tunani d cewa</p><p>Ummana ina t zuwa ba kya nan. Ta dube shi g</p><p>mmknta ba ta iya bayya tsanarta g Abban,</p><p>maimakon hk ma sai ta samu kanta da cewa</p><p>Naje ganin jariri ne. Ya shiga ya zauna kusa d ita</p><p>t dube shi Yanzu Abba dm bn isa in fada maka</p><p>mgn ka ji ba?Dama kin zuwa kayi ka duba</p><p>matarka da danka? Ya shafa kai,Umma anjima d</p><p>dare zamu da su Ahmad ni haushi sukai bani. Ta</p><p>ce to ka tabbata yau din kaje,Sannan ko sun</p><p>nuna ma fushinsu naka kawai ka ba su hkr,Ya ce</p><p>to umma ta ce Na sanka d zcy ne. Ya ce to zan</p><p>kiyaye Umma. Ya kuma dabn ta ummata yau na</p><p>ganki a yanayi mara dadin gani. ta dube shi kaina</p><p>ke ciwo Abba na kuma sha magani. Da gaske</p><p>ciwo kanta ya dinga yi dn damuwa. Yace Allah y</p><p>kara sauki. Ya fita. Da Ahmad d Muktar suka</p><p>je,sun ci sa'a Alhjn yana gari. suka shiga suka</p><p>gaishe shi suka kuma yi wa juna barka. Sam ba</p><p>ruwanshi da matsala,Suka shiga ciki tare d</p><p>Sumyya,sn samu Aisha ta zo ita d mijinta.</p><p>Bishira km hade rai tayi lkcn d taga su Abba? Su</p><p>Muktar suka dauki jariri,sannan suka gaida mai</p><p>jego. ta amsa tana musu wani kallon daga ina?</p><p>Aisha ce taje ta sanar d uwar tasu. Nan ko ta</p><p>shigo ta samu su Abba d abokanshi. Ta shiga</p><p>zazzaga mishi masi fa,wai sai yau yaga damar</p><p>zuwa?Ai ta samu lbrn yadda yake wulaqanta</p><p>mata yarinya. ta ce km a bakin mahaifiyarka naji</p><p>kaji tsoron Allah ka talike a gurin uwar goyonka</p><p>sai yadda ta ce. to 'yata tafi karfinta. Abba sam</p><p>ba zai juri ji ba,dn hk ya mike ya fita. tana ta</p><p>cewa saurare ni ko waiwayowa bai yi ba. Su</p><p>Muktar dai suna ciki suna bata hkr ya kira wayar</p><p>Ahamad ya ce zan tafi in ba za ku fito ba. Ya</p><p>kashe ba tare d jiran asmar Ahmad din ba, hk</p><p>suka fito. Muktar ya ce Tabdi! lallai matar</p><p>gidannan bata d mutunci.Ahamd ya ce ka fada</p><p>ma mai gidan Mana. Abba ya ce Ni sai ma in</p><p>sakar Musu 'yarsu "Kul in ji Muktar, Kada kayi hk</p><p>Ahmad ya ce, Ashe hr umma suka yi wa rashin</p><p>mutunci dazu? Abba ya ce Ummata?Muktar ya ce</p><p>Eh, bayn fitarka take fada,Abba ya yi shiru dn</p><p>takaici. Gidanshi ya wuce,gado ya hau ya</p><p>kwanta. . Tabbas sun ci zarafin ummarshi,dn ya</p><p>ganta cikin yanayin da bai ta6a ganinta aciki ba.</p><p>Ko me dame suka fada mata?Umma bata</p><p>cancanci cin zarafi ba.Ranshi ya kai makura</p><p>gurin 6aci,ya rufe gidn ya nufi gdn su Umma.</p><p>Lkcn d ya shiga umma ta nufi dakin</p><p>Alhj,Sallamarshi ce ta tsaida ita,ya shiga dakinta</p><p>ta dawo ta shiga. Tana cewa Abba hr ka dawo</p><p>daga gurin ma su jegon?bai amsa ba,kanshi na</p><p>kasa,dmn sai ya samu kansa da jin kunyarta</p><p>sakamakon abn d aka mata sbd shi. Ta ce lfy</p><p>Abbana?Ya dube ta,maimakon amsa sai ya ce</p><p>umma me suka ce miki dazun d ki ka je gidn?</p><p>Tayi dn yaki ita a dole Murmushi , Na me Abba?</p><p>ya ce mamn bishira ta ce taci miki mutunci ko?</p><p>Umma tayi 'yar dry,sannan ta ce ko daya ta dai</p><p>fada maka hk ne dn kaji haushi. Ta ciga ba d</p><p>cewa,Abba dn Allah ka bi sannu hr t dawo...... Ya</p><p>ce umma na san sunci miki zarafi sosai "ZURFIN</p><p>CIKI' ne da ke umma shi yasa ki ka shanye,</p><p>amma yanayinki dazn y nuna.Umma b zan zauna</p><p>d matar d baya san darajarki, dk kuwa yadda na</p><p>kai sonta,ina ga zamanmu ba zai yiwa d bishira</p><p>ba. Umma ta ce "Kai! Kai!! kul na sake ji zanyi</p><p>fushi d kai me tsanani Abba,dk hakkinsu d ke</p><p>kanka matarka d danka ta ka sauke su,kuma</p><p>koyaushe kaje ka gansu, ba km na son su Alhj</p><p>suji wannan zancan. Ya ce yanzun hk zan zauna</p><p>umma cikin 6acin rai? Tunda na auri matar nan</p><p>bn huta ba,kema baki daina shan zagi ba? umma</p><p>ta matso kusa da shi ta dafa kafadarshi. Abbana</p><p>ka sani cewa ba a toru ka dny dn k huta ba,nawa</p><p>ganin duk wanda a ka haifa daga ran d ya diro</p><p>dny y gama hutu komai jin dadinsa,komai</p><p>kudinsa,ko mulki. Hutu daya ne in ka mutu ka</p><p>sadu d rahamar Allah,ita kuwa Rahama bata</p><p>samuwa g wanda bai bi Allah d manzo ba. Bn</p><p>Allah kuwa shine kada ka bata masa,kabi dukkan</p><p>abn d Manzonsa ya yi umurni,Sannan ka hanu</p><p>daga abn d ya yi hani. Aure bautar Allah ne Kum</p><p>sai kayi hkr sannan za ka yi bauta d kyau. hk dai</p><p>umma tayi ta wa Abba nasiha hr zcyrsa t sauka,</p><p>sannan sukayi Sallama. Washe gari misalin karfe</p><p>2,Abba ya dawo gida dg mkrnt d yake koyarwa,</p><p>dn suna ta shirye-shiryn jarabawa (J.S.C.E.) Su</p><p>ummi ne za su zana,wnk y fito sai ga wayr Alhj</p><p>ta shigo.Y daga cikin girmamawa. Bayn sun gaisa</p><p>Alhj ya ce Abbana kana ina ne? Ya ce ina nan</p><p>gida.Alhj ya ce kaje gidanmu ka amshi mukallin</p><p>dakina ka shiga kasa mukallika bude dirowar nan</p><p>tawa,zaka g wadansu ta kardu irin littafin nan na</p><p>rubutu. kabi a hnkl za ka g wani a samnshi an</p><p>rubuta Alhj Sale Jigawa,d ajami ne rubutun,maza</p><p>ka kawo min. Abba ya ce to.,Yana cikin duba</p><p>littattafan sai ya ga wani an rubuta wasiyya,dk</p><p>littattafan d ajami Alhj yake rubutu, Abba ya dauki</p><p>littafi ya bude shafin farko an rubuta........ Babi</p><p>Na Daya "Ni Alhj Sulaiman, nayi kudirin ko bayan</p><p>raina 'yata Habiba (ummi) zan aurar d ita ga dan</p><p>Idrisu(Abba). Da sauri Abba ya rufe littafin</p><p>gabnshi yana wata muguwar faduwa,ya sake</p><p>budewa ya kalli kwanan wata. Alhj yayi rubutun</p><p>ne ranar d a ka haifi ummi,Ya yi sauri ya maida</p><p>komai ya dauki wnd aka aiko shu yana zufa ya</p><p>kalle dakin ya maida wa umma makullin ya fita</p><p>da sauri Ya buga mashin can ya hango ummi</p><p>suna dambe da wani yaro an raba su ta tirje</p><p>kafafunta ba ko takalmi, mayafinta taci damara</p><p>da shi. Ya ce "Ke! tn dg nesa ta jiyo muryar</p><p>Abba,ya yi mata dakuwa ta kwashi takalmanta a</p><p>hannu ta yanka d gudu. Yabi ta da kallo hr ta</p><p>shige gida ya lumshe ido tare d fadin "Innalillahi</p><p>wa'inna ilaihin raji'un."Me ma ya kai shi bude</p><p>littafin wasiyyar Alhj Babba, Duk garin kano akwai</p><p>mutumin d ya tsana irin Ummi?? To fa! ku</p><p>biyomu a littafi na biyu </p><p><br /></p><p>rk ****ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com :-2**** ta dafa kafadata tana cewa kayi haquri mubarak na sani kana son nabeelah sannan itama tana sonka,sai dai kuma kayi kuskuren rashin bayyana soyayyarka gareta a sanda ta bukaci hakan,nayi kokarin dai- daita tsakaninku amma naji tsoron kada mutane suyi tunanin na aurar da nabeelah ga d'ana ba bisa son ranta ba sai dai bisa dole kasancewar ta girma a hannuna.......haka kuma yanzu bazan saka kaina cikin wannan matsalar taku ba amma zan goya muku baya bisa dukkan shawarar da kuka yanke,idan kuna nemana ku sameni a fallow*** na kalli nabeelah idona cike da hawaye na fara magana kamar haka'nabeelah ina sonki,kuma ina kaunarki, sai dai na kasance cikin irin mutane da sukan boye sirrin zuciyarsu,kiyi haquri ki gafarceni,nasan nayi miki laifi...nagode ki tashi ki tafi allah ya bada zaman lafia sannan allah yasa shine mafi alkhairi gareki........na miqe zan fita daga motar,ta kamo hannuna ta zaunar dani tana magana hade da wani kuka mai tsuma zuciya gami da sa tausayi kamar haka'yamubarak da farko na yarda kana sona amma yanzu na gane cewar soyayyar batayi tasiri a zuciyarka ba tunda har ka yarda zaka haqura dani kan wani ya aura,lallai na yarda baka kishina baka tausayina irin zaman da zanyi tare da wani namiji wanda ba kaiba,ka sani cewar zuciya ba zata aminci rabuwa da kaiba,jikina na haramtashi ga dukkan wani d'a namiji idan ba kaiba dan haka na qudiri niyyar mallakarka ka ta wane hali,yamubarak kayi kokari ka soni kamar yanda nake sonka,yamubarak kada ka bani kunya'*** na share hawayen dake zuba kan kuncinta,na kama hannayenta na kwantar da ita bisa kirjina,nabeela h ki amince da soyayyata gareki kada ki zargeni da komi sai alkhairi,nabeelah ina sonki kuma nine mijinki da yardar allah,da sauri ta tashi daga kan kirjina ta dafa kafaduna tana kallon fuskata,ta sumbaci goshina sannan ta rungumeni kan kirjinta tana cewa hakika farincikina ya karu,burina ya cika sannan alheri ya tabbata gareni.....amma *menene mafita? *da wane zance zamu tunkari abba? *sannan kuma lokaci yana da karanci garemu.... Na kalli nabeelah dake kan kirjina nace zaifi sauki muje wurin kawu aminu mu shaida masa halinda muke ciki...ni nasan me zan fada masa kuma zai yarda. *kai tsaye na tuka motar zuwa gidan kawu na tarar ya gama cin abinci yana gindin bishiya yana hutawa..bayan mun gaisa ya cigaba da magana kamar haka'lallai daga ganinku akwai matsala dan naga alamun damuwa gareku, shin ko baki son auren ne? Ya tambaya' na fara da cewa gaskiya kawu ita nabeelah ba wanda take son za'a bata ba,kawu yace wannan zancen banza ne dama shi yasa suke boye min to wallahi wannan maganar babu ita,ku tashi mu tafi gidan.... Na tuka mota har kofar gidan muka shiga shi kuwa kawu tun daga kofar gida yake ta fada..yana shiga su mama suka fito suna gaisuwa amma ko amsawa bayyiba ya cigaba da cewar'maganar auren nabeelah babu na soketa yanzu zata fada mana wanda take so kuma goben zan daura mata aure dashi...nabeelah ta kada baki tace'ya mubarak nake so' kawu yayi dariya yace au to ai shikenan ta kwana gidan sauki kuda dan iskanci abin na gidane ma kuke bata lokaci,to ai ni yanxu xan daura auren idan yaso kuje chan kuyi ta bikinku,sannan baba ya shigo yaji meke faruwa amma ba yanda zaiyi da kawu dan yasan halins doe qura ya zama waliyina shi kuma waliyin yamubarak aka daura auren*** take yamubarak ya daukeni muka tafi gidan kunshi daga nan ya kaini nayi kitso muka wuce gidan aunty nafeesat nayi wanka na saka rigar atamfa kaina ba dankwali na fito gareshi,wow nabeelah amma kinyi kyau,ya kamo hannu daga inda yake zaune gefen gadon,ya sumbaceni har saida numfashina ya dauke,ya kwantar dani kan gadon ya fara cire kayan dake.......hakika ban taba sanin haka yamubarak ya iya soyayyaba sai yau,lallai da tuni nayi asar miji,haka muka kasance cikin nuna kaunar juna har zuwaN CIKI book 2 part 1</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 2 part 1</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 22:05</p><p>Abba kwance kan gado,dare yayi nisa amma shi</p><p>ya kasa bacci sam.saboda matsalar da yake ciki</p><p>yanzun. domin kuwa matar shi in yaga bazai iya</p><p>ba sai ya sawwake mata,amma maganar auran</p><p>ummi koda Alhaji bai goya mishi ba bazai iya guje</p><p>mata ba. "yanzun menene mafita?"ya tambayi</p><p>kansa,wata zuciyar ta ce, "kayi shiru tamkar baka</p><p>ga wannan takarda ba,tunda ba wanda yasan ka</p><p>gani." a fili ya ce,"haka ne." ya ci gaba da</p><p>tunanin kila ma yanxun ya janye kudirinshi,tunda</p><p>yaga ummin bata da kan gado. don yaga rubutun</p><p>yayi shi ne tun ranar da aka haifi ummi,ko kuma</p><p>ranar sunanta. tunda gashi har da sunan ummi a</p><p>jiki.mafita kenan yayi shiru.wata zuciyar ta ce,"in</p><p>ko kayi haka kayiwa Alhaji da ummanka adalci?</p><p>koda yar su ba yar adam ba ce bai kamata ka</p><p>gujeta ba.ko don albarkacin son da suka nuna</p><p>maka. shin da ummi ta kasance mai jin magana</p><p>da nutsuwa,kuma mai tsananin kyau zaka</p><p>gujeta? Kada kayi zaton Alhaji yayi kudurin aura</p><p>maka yarsa ne don yasan zata zama mara ji,kayi</p><p>nazari. haka Abba yayi ta tunani har asubah</p><p>tayi,amma hukuncin da ya yanke shine yayi shiru.</p><p>sai dai ya janye batun rabuwa da matar shi,don</p><p>yasan yana sakinta zai zama mijin ummi,kai</p><p>batun nan hadiye ma cikinshi shine mafi dacewa.</p><p>dunkuna masu kyau yayi wa matarshi saboda cin</p><p>suna.haka yayi wa dan siyayya daidai karfinshi,ya</p><p>kawo ma umma. Taji dadi sosai nan ahj ya iske</p><p>su, shima ya shiga dakin umman ya xauna ya ce</p><p>a dauko masa abinci nan xai ci yau.ya dubi abba,</p><p>babana nayi sautun raguna xuwa qauye nace xa</p><p>a siyo nmanya.abba ya ce biyu?umma tace</p><p>hakan yayi.abba ai tuwan girma miyarsa nama,</p><p>aja rago daya xiqal a shiga wannan gida da shi?</p><p>abba yace,me xai hana tunda ban musu qaryar</p><p>arxiki ba sun san mu talakawa ne.ahj yace</p><p>xancanka dutse bacna,amma maganar ummanka</p><p>ita xa a bi, sannan xa a sai buhun shinkafa da</p><p>cefane a kai musu.ana gobe suna abba da</p><p>abokansa suka dira gidan da ragunan da kayan</p><p>mai jego da na yaro sannan ga kayan abinci. sun</p><p>samu anty a gidan,ta musu tarbar mutunci.da</p><p>yake abba xana waya da ita,ya fada mata komai</p><p>ta sani.hjy zainu da taji kukan raguna ta fito,anty</p><p>tace dan Allah momy kada ki musu magana,kin</p><p>ga shi da abokansa ne.da qar ta samu ta turata</p><p>sashin ahj,shi kuma murna yayi yace aje a daure</p><p>su.zainu tace ahj menene na numa farin ciki sai</p><p>kace ba ma cin nama?can ba xa a ka kada ba</p><p>dan kawai shagalin sunan, sannan tace harda</p><p>shinkafa suka kawo sai kace muna yunwa? nana</p><p>take ya hade rai tare da cewa,zainu kada dai ki ce</p><p>min kin sa an dawo da yarinyar nan gidan ne dan</p><p>ki kashe mata aure?tace haba dai. ya ce to hir</p><p>dinki dan bansan in kuma jin irin xantukan nan</p><p>yayi ma matarsa daidai arxikinsa. mu kuma mu</p><p>ma yarmu da jikanmu gwargwadan arxikinmu,in</p><p>ya fito daga gun mai jegon ki turo min shi,sbd mu</p><p>ji in da xa a yi sa sunan.tace ina xa ayi in ba nan</p><p>ba?ya dube ta an taba haka?ki dai turo minshi.ta</p><p>taba baki sannan ta wuce.lkcn da ta leqa dakin</p><p>abba da abokansa suna xaune,abba yana ta fama</p><p>da danne dannen waya,domin tun da suka shiga</p><p>ya qi ko kallan inda bishira take bare danta.tace</p><p>bishira ki eada musu in sun fito ahj na san</p><p>magana da su.ta wuce ba tare da jiran jin amsa</p><p>ba,ko amsa gaisuwan da abokan abba suke mata</p><p>bata yiba.bishira ta kalli abba wanda tana</p><p>hankalce da shariyan da yayi mata,tace kaji abin</p><p>da momy tace?sai lkcn ya dubeta me tace? yayi</p><p>maganar ne cikin tsare gida.dadynmu yana san</p><p>ganin ku. bai amsa ba,sai kurun ya tura mata</p><p>jakar kayanta,ki duba,ta xaxxage dinkuna ne na</p><p>gani na fada masu kyau,duk da xannuwan ba</p><p>masu tsada ba ne kala uku atamfa daya shaea</p><p>daya sai kuma leshi.sai ko kayan yaron.ta dube</p><p>shh an riga an sai mana kayan fitar</p><p>sunanmu.ahmad ya dube ta wannan din baki so?</p><p>tace ni bance ba.abba yace ku tashi muje.tace</p><p>ina san magana da kai.ya ce kiyi</p><p>maganarki.muktar yace kuxo mu fita ta dauki</p><p>yaran tare da miqa mashi ta ce ina lura da kai</p><p>rabon da ka dauke shi tun randa aka</p><p>haifeshi,alhalin mu kuma yana nan yana hana mu</p><p>baccin dare.kai kana can kana baccin ka.ta fadi</p><p>haka ne cikin sanyin murya.ya amshi dan tare da</p><p>cewa ai gara ya hanaku bacci tunda kunqi ku</p><p>kaishi gurin babanshi.ya tsura ma yaran ido,wata</p><p>qaunan dan ce take shigarsa.ta matso</p><p>jikinshi.abba ya kalli furkarta,ita ma kallansa</p><p>take,ta ce yanxu ko dan murmushin ka bana</p><p>gani.yace,in da kina san gani da baki dawo ghda</p><p>ba.yaci gaba da cewa na sha mamakinki</p><p>bishira,da har xa ki yarda ki dawo gidanku ba da</p><p>ixinina ba. kuma tun kafin ki haihu sai da na fada</p><p>miki ba za ki zo gida ba.Ta ce To Abba mony ce</p><p>ta ce sai an zo. Ya ce shi kenan ku zauna. ya</p><p>mike mata yaron ta amshe shi ta kwantar ta</p><p>kama mishi hannu. Abba wane suna ka sa masa?</p><p>ya ce Sunan Alhj babba. Da sauri ta saki</p><p>Hannushi . Sunan 'yan da? ya kalle ta Na zaci</p><p>zaki ce suna mara ma'ana,tund da ne da sauki.</p><p>ya fice. Haushin hali irin na Bishira ya ke ji.dn</p><p>son shi yasan tana matukar sonshi,amma bata</p><p>son yin biyayya ga abn d yake so. Ya samu su</p><p>Mktr sannan suka shiga gurin Alhj ya tambaye su</p><p>in d za a sa sunan,Abba ya ce a masallaci kusa d</p><p>gidn babnshi ne za a yi addu a. Amma tuni an sa</p><p>wa yaro suna Sulaiman.sunan babana. Alhj ya ce</p><p>Madalla Allah ya raya mana shi, ba sai mun zo</p><p>ba dn yanayin sanyi ne. Nan dai Abba d</p><p>abokansa suka tafi suna yabn Alhjn. An ci sunan</p><p>shima Abba shi d abokansa sun yi walima da</p><p>Azahar. matar abokinshi Bala ita ce suka bai wa</p><p>girkin ta yi masu. Mai jego taci gaba d wnk. Abba</p><p>kan leka su lkc zuwa lkc,kusan dk lkcn d yaje ba</p><p>su cika rabuwa d dadi ba sbd mgnr d hjy zainu kn</p><p>datsa mishi. Umma shi ma bata yi fushi ba tana</p><p>leka su dk d rashin sakar mata fuska d mai jegon</p><p>tare d mahaifiyar keyi. Ummi tana tafe tana 'yan</p><p>tsince-tsincenta,kmr yadda ta saba,sai ko taga</p><p>sim,take ta yarda dk wani abu d t samu t dauki</p><p>Sim din. Gefen zaninta t samu ta kulle,sannan ta</p><p>tafi,cikin jakr mkrntrta t saka.wata rana ta dauki</p><p>wayar umma ta shige daki,ta bude wayar ta cire</p><p>sim din ta saka wanda ta tsinto a cikin zani ta</p><p>soke wayar ta fito soro.Jikin dakin yaya Abba a</p><p>bakin kofar ta dauki lamar Abba da ya rbt sbd</p><p>masu zuwa nemanshi tana kira taji wayr tana</p><p>ringing. Ta kashe tana ta dry,hk tayi ta yi wa</p><p>Abba Flashing dg nan tayi gidn du Amina</p><p>kawarta,tana ba wa Amina lbrn abn d ta ke wa</p><p>Abba. Ta ce Amina nsn yanzun hk yana cn yana</p><p>jin haushi,shi yasa ki ka ga ina murna.Ta ce in ya</p><p>gane fa?Ummi ta ce Ai tsintar sim din nayi,Umma</p><p>kuwa ba za ta san na dauki wayarta ba,domin</p><p>yaya Abba da Alhjnmu kawai suke kiranta. Amina</p><p>ta ce Yadda za a yi ki kira shi ne in ya dauka sai</p><p>ki make murya ki canza suna. Ummi ta ce Tab,dn</p><p>in ci duka. Amina ta ce Dalla cn gane ki zai yi?</p><p>suka kira ya daga ummi ta sirantr d muryarta</p><p>tana fadin "Hello! Abba ya ce Ke wace ce ki ke</p><p>kiran layina? Ta ce Sunana '"Suhaila. ya ce</p><p>Menene ki ke kirana?Ina ma ki ka samu lambata?</p><p>Ta ce Gani nayi ni ma a cikin wayr. Tsaki yaja</p><p>Sannan ya kashe.Suka dinga tsuntsira dry. Amina</p><p>ta ce Sake kiranshi ki ce ma ke a kaduna ki ke.</p><p>Ummi ta ce Kai yin waya akwai dadi ni ina son</p><p>buga waya. Ta sake kira cikin Zafin rai ya ce Ke</p><p>lfy??kin dame ni fa!Ummi ta ce To tsaya mana</p><p>kaji ina son mu gaisa ne ni ina kaduna ne. Ya ce</p><p>To na gode. Sai ma ya kashe wayar gaba daya</p><p>suka yi ta kira a kashe. Tun daga ranar Ummi ta</p><p>samu in umma tana aiki ko tana bacci sai ta sace</p><p>wayar ta cire sim tasa nata ta kira Abba. Tun</p><p>yana kyararta hr ya daina ya koma rokon ta</p><p>daina kiranshi,dk a banza. Daga baya sai Abba ya</p><p>soma sauraronta, ranar kuma ta kira shi ne</p><p>misalin dayan dare,ranar taki zuwa dakin</p><p>Tsohuwa ta kwanta a dakin umma. umma kuma</p><p>dama dakin Alhj take kwana. A dai-dai lkcn ya</p><p>kwanta kadaici ya dame shi,ga garin yanayin</p><p>sanyi. wayar ta katse tunaninshi d yake yi na</p><p>matarshi zuwa yanzu ya haddace lambar Suhaila.</p><p>Ya daga ya ce "Hello ya ce Ke wai me ya hana ki</p><p>bacci?Ta ce Ni ba sunana ke ba,Ni sunana</p><p>Suhaila,kai fada min sunanka. Ya ce Abba Ta</p><p>danne dryr d taso kwace mata ta ce Abba ba</p><p>suna bane,Fada mn sunanka n gsky. Ya ce "Idris</p><p>Yadda ya fadi sunan sai da ta dage kwarai</p><p>sannan ta maida dryrta. Ya katseta d cewa Ina</p><p>ku ke a kaduna?tayi dim,dn dai bata san ko ina</p><p>ba a garin kaduna ba,ba ta ma ta6a zuwa ba.</p><p>Take ta tuno Amina sun ta6a zuwa unguwar</p><p>Sarki,dn hk ta ce "Unguwar Sarki. Ya ce, wai</p><p>shekaranki nawa? Ta ce Sha takwas. Ta sheka</p><p>masa karya.Ya ce Amma shi ne a ka ba kiwaya?</p><p>ta ce ta ka san wanene Babana? Ya ce A"a ta ce,</p><p>To shi ne mai bawa Gwamna shawara a jihar</p><p>kaduna. Abba ya ce Lallai, ki ce in nazo kawo</p><p>miki ziyara ba zan samun ganinki ba? Ta ce za</p><p>ka ganni mana. Ya ce To zan zo. Ta ce To, Ya</p><p>ce,Amma fa ina d mata ta haihu ne ta tafi</p><p>wankan gida. . Ummi ta ce Lallai to sai da safe.</p><p>Ya ce, Wa ke zuba miki kudi ne cikin waya?Ta ce</p><p>Babana mana. ita sai lkcn ne ma ta tuna cewa</p><p>ana saka kudi tunda ta ke kira bai taba kin zuwa</p><p>ba,aranta ta ce kila wannan ba a sa kudi. Sunyi</p><p>Sallama babu dadewa,wayar ta sake daukar</p><p>tsuwwa. Ga zaton Ummi Abba ne sai da ta daga</p><p>sannan taji muryar wani. Ya ce Da wa nake</p><p>waya? ta ce wa ka ke nema?Ya ce Me wayr. ta</p><p>ce Ummata ce kuma tayi bacci. Ya ce Yallabai</p><p>nake nema. Ta ce Ban san wani yallabai ba,kada</p><p>ka dame ni Ta kashe wayar tare da jan tsaki.</p><p>Sannan ta cire layin ta maida na umma Wasa-</p><p>wasa cikin kwanakin Abba ya soma damuwa da</p><p>lamarin Suhaila kaduna, lokuta da dama ya kan</p><p>kira layinta amma sai ya ji shi a kashe. Sam ba</p><p>ya samunta sai lkcn d ta kira shi,ko da ya yi</p><p>mata korafin hk,sai ta ce "Eh ita ce ke kashe</p><p>layin sbd ana damunta. Sun yi jarabawar (J. S.</p><p>C.E.)sakamako suke jira. dn hk yanzu tana gida</p><p>ko yaushe tsokana kuwa bata fasa ba. Kullum ita</p><p>d Amina cikin shirya yadda za su yi wa Abba</p><p>waya suke, kudin cikin layin ya kare,Abba shi ke</p><p>tura kati yanzun. Duk lkcn d Abba yazo gidansu d</p><p>ya ga ummi ya hade rannan yana muzurai,ita km</p><p>sai ta yi ta sheka dry,dmn tana tuno yadda yake</p><p>kwantat d murya a waya. Wata rana hr duka ya yi</p><p>mata sbd dryr d ta dinga yi daga sallamrshi a</p><p>gdn. Tsohuwa kam ranar yini tayi fada,wai ita za</p><p>ta bar gidan.Cin kashin d ake yi wa ummi ya yi</p><p>yawa. A ce rashin 'yancin yakai ko dry ba a son</p><p>tayi. Da kyar umma ta sha kanta t hkr. Wannan</p><p>ta kaicin dukn yasa ummi tace ita kam sa tasa</p><p>shi wahala. dn hk ranar gdn su Amina taje. suka</p><p>shirya yadda in ta kira shi zata ce yaxo Kd ta</p><p>ganshi, ummi ta ce mugu dama in yaje ya 6ace in</p><p>huta. Hakn kuwa ta fada mishi, a ranar d suna</p><p>waya. Ta ce '"Idris.dn Allah yaushe za ka zo ne?</p><p>Ya ce Tun yaushe Suhaila nake cewa zan zo</p><p>amma kin ki,to yanzun yaushe zanzo? ta ce kazo</p><p>Juma'a ya ce A"a zan dai zo Asabar,Juma'a</p><p>rabin rana ce. Ta ce,To sai kazo.Nan d kwana 4</p><p>kenan?ya ce Insha Allah,sannan ina son ki toro</p><p>min da adireshin dn gdnk,sannan ranar d zan zo</p><p>ki bar wayarki a kunne. Ta ce To." Ranar Asabar</p><p>misalin goma na safe Abba ya shigo cikin sabbin</p><p>kaya,ya yi matukar kyau tamkar sabon Ango.</p><p>Umma ta ce za ka je gurin su Maigida ne?Ya ce</p><p>A"a umma koda yake zan bi ta can.Kd zan je.</p><p>Umma ta rike baki "Kd,? Me a ke yi?ya ce sai na</p><p>dawo za ki ji.Ummi d ke wanke-wanke ta kwashe</p><p>da dry. Umma ta dirma mata dundu tare d</p><p>cewa,Ke wai ciwon dry ne y kama ki?Abba ya</p><p>dubeta cike da tsana. Ummi ba za ki shiga</p><p>hnklnki da ni ba?ta sunkuyar da kai tare d maida</p><p>dryrta ciki. Sannan ta ce Yaya Abba dn Allah ka</p><p>siyo min biredi,wlh biredin Kd dadi ne da shi.</p><p>Lkcn d Amina suka dawo ta sammin. Ya galla</p><p>mata harara,tare d fadin an ce miki nima bakauye</p><p>ne irinki?In ma ki ka sake min mgn sai na gabje</p><p>ki. . Ya kalli Umma Kada ki ce ma Alhj nayi tafiya</p><p>amma in na dawo zan fada masa. ta ce ,To" Allah</p><p>ya tsare. Abba ya fita. Ummi tana gama wanke-</p><p>wanke ta shige daki dn yin gyaran gado. Umma</p><p>na shiga kicin itama ta fito falo ta ciri wayr a caji</p><p>taje ta saka sim. Take kuwa kiranshi ya shigo, ta</p><p>daga ta matse murya kamar yadda ta saba, ka</p><p>taso ne? ya ce Ina mota mun kusa tasowa. Ki</p><p>turo mn adireshin. Ta ce Ba fa wahala,d kun</p><p>sauka tasha sai ka ce a kawo ka unguwar sarki</p><p>gidn mai ba Gwamna shawara. Ya ce Suhaila ma</p><p>su ba Gwamna shawara d yawa Ta ce Um to ai a</p><p>nan unguwar Sarki shi daya ne. Ya ce Ya sunan</p><p>layin?ta ra sa me zata ce,gabnta y shiga</p><p>faduwa.Ta samu kanta da cewa, Abuja Ya ce</p><p>Abuja kuma Suhaila?ko dai Abuja road? Ta ce Eh</p><p>gida mai lamba 6. ya ce To zan ci gaba da kiran</p><p>layin. ummi ta ce To," Ta zauna tana sauke</p><p>numfashi. Tab da ya dogata d ta bani,Sannan ta</p><p>saka dry murna take yau yaya Abba zai sha</p><p>wahala. Jefi-jefi ya kan kira ya ce sun zo gari,dk</p><p>lkcn d ya kira in ta ji ringing sai tayi bayi da</p><p>gudu, har Tsohuwa da suke zaune tare ta ce, ke</p><p>takwara gudawa ki ke ko atini ne? Ta yamutsa</p><p>fuska, sannan ta ce Bacin ciki ne. Tsohuwa ta ce,</p><p>To taso uwarki ta baki magani. Ummi ta ce ya yi</p><p>min sauki ma. Can kuma masu kiran layin suka</p><p>kara kira. Ummi tayi kofar gida ta daga wayar a</p><p>ka ce ke ina ki ka samu wannan wayar? Ta ce</p><p>Oho 'yan rainin wayau kada ku sake kirana. Ta</p><p>kashe wayar ta koma gida. Lokacin da Abba ya</p><p>ce sun shiga KD har ma sun kusa sauka, sai ta</p><p>cire layin ta ci gaba da harkokin gabanta ta</p><p>manta ma da labarin wani yaya Abba. KADUNA</p><p>Abba suna sauka a tashar kawo, ya sauka ya</p><p>shiga raba ido yana kallon garin kaduna. Yau ce</p><p>rana ta 2 d ya ta6a zuwa KD, daman sun zo</p><p>daurin auran wani abokin su bara waccan. Ya</p><p>kalli wani dan aca6a sannan ya yafito shi da</p><p>hannu. Ya iso yana cewa Ina za ka? ya ce</p><p>Unguwar Sarki. Dan aca6a ya ce Wane layi? Abba</p><p>ya ce Abuja Road. Ya dubi Abba Rigasa kenan,</p><p>unguwar Sarki babu layi mai wannan sunan.</p><p>Abba ya ce, Ina zuwa, bari dai in kirata. Koda ya</p><p>kira layin Ummi sai ya ji shi a kashe, yana ta kira</p><p>a kashe. Ya dubi dan aca6a ya ce, Kasan gidn</p><p>Mai ba Gwamna shawara? Dan aca6a ya ce, Hau</p><p>dai muje sai mu tambaya. Abba ya hau mashin</p><p>yana mai ci gaba da nemn layin Suhaila. Sun</p><p>zagaye unguwar Sarki layi-layi suna tambayar</p><p>masu gadi da 'yan dai-daikun mutanen da ke</p><p>giftawa kasancewar unguwa ce ta manyan</p><p>mutane, daga karshe dan aca6a yaba Abba</p><p>shawar ya tafi gida kawai. Don haka sun gama</p><p>zagayen unguwar Sarki har da makotanta, amma</p><p>ba su samu ba. Gida daya ne aka ce musu da</p><p>akwai Suhaila, amma yarinya ce ta goye. Kusan</p><p>karfe 3 sannan suka koma tasha,ya biya dan</p><p>aca6a, sannan yaje ya yi sallah. Zuciyarsa cike</p><p>da takaici sai yanzu yake Sallah. gashi ya kasa</p><p>samun layin Suhaila. kila ma tana sane ta kashe</p><p>wayr dn kawai ta tazarta shi. Ya tuna d zagin d</p><p>wani mu2m ya masa lkcn d suka tambaye shi ko</p><p>ya san ina ne gidan mai ba wa Gwamna</p><p>shawara? Mutuminya ce,mai ba Gwamna</p><p>shawara a kan me? Ma su ba da shawara suna</p><p>da yawa, ya sunan layin da ka zo? ya sunan mai</p><p>gidan? kama ina lambarsu? Abba ya ce, Lambr</p><p>kadai gare ni,km taki shiga.Mutumn ya ce,"Amma</p><p>kai soko ne,gashi kmar wayayye.Ya ja tsaki ya</p><p>wuce. Shi kanshi sai yanzu yaga wautarshi. ko</p><p>me ya kawo shi gurin yarniyar?Shida dai ba za</p><p>ya ce sonta ya keba,km ba ya ce ba sonta yake</p><p>ba. Wani ma ya zaci dn kudi ubanta yazo,shi kam</p><p>in ya koma shiru zai yi ko abokanshi zai ce musu</p><p>bai gane ba kawai,dn yabi ya fada musu lbrn</p><p>Suhaila,sun km san d batun zuwanshi gurinta</p><p>sarai,km yasan hlinsu za su maida abn na</p><p>tsokanarshi. Cikin matukar takaici suke tafe cikin</p><p>motar kaduna zuwa kani,sun zo kwanar Dangora</p><p>tsautsayi ya akfa musu. in da tayar motarsu guda</p><p>ta fashe. . Nan take motar ta bar hannunta ta</p><p>mulmula da su suna ta salati,nan aka kwashe su</p><p>xuwa asibiti.wasu sun mutu take,wasu sun yi</p><p>dogon suma.masu waya ta cikin wayarsu aka yi</p><p>ta kiran yan uwansu,shi ma abba a cikin wayarsa</p><p>aka kira lambar ummanshi da alhj da sauran su</p><p>aka shaida musu cewa mai wannan layin sun</p><p>samu hadari,kuma an kawo su asibitin mlm</p><p>aminu kano yanxu.iyakan rudewa su umma sun</p><p>rude,tsohuwa kam take cikinta ya kada ta soma</p><p>xagawa bandaki tana kuka tana face</p><p>majina.ummi bata gidan tana can gidan su amina</p><p>suna ta hira suna cin dariya ,tace bari in je in</p><p>qara sa layin in ya kira sai ince wayata chaji ne</p><p>sai yanxu nayi.sadaf sadaf ta shige daki,kan</p><p>kujera taga wayar,ta dauka ta saka sim din ta</p><p>cire wancan. tana kunnawa sakuna suka soma</p><p>shigowa. kafin ta bude ta duba sai ta jiyo muryar</p><p>tsohuwa cikin kuka tana cewa wannan yaro ashe</p><p>ajalh ne ya kira shi,ko me xashi yi kaduna?ni ban</p><p>sani ba.ummi ta fito da sauri tana cewa,tsohuwa</p><p>me ya faru?tace ba kina can gun yawanki na</p><p>tsiya ba.Mai sunan mlm da ya tafi kd sun tafka</p><p>hadari, yanxun haka suna asibitin mlm. ana xatan</p><p>shi ma ya mutu.ummi ta saki ihu,sam bata san</p><p>ta damu da dan uwan ta abba ba sai yau,ko tana</p><p>kukan ita ce sila?oho.kafin kice haka,lbr ya watsu</p><p>a unguwa abba ya mutu.cikin kuka ummi ta</p><p>tambayi tsohuwa ina ummata? tace tare suka</p><p>nufi asibitin da ummarku.taqi yarda ta jira</p><p>su.ummi tana jiyo ihun kukan umman bashir ta</p><p>xaga gidan.gidan ya rincabe da kuka,ummi fa</p><p>hankalinta ya qara tashi.matarsa ta iso da kuka</p><p>da yan uwanta a motoci.yayyantamaza suka nufa</p><p>asibitin.can kusan qarfe takwas su alhj suka</p><p>shigo.alhj ya ba mutane haquri,ya ce bai mutu ba</p><p>dogm suma yayi.kuma Allah yayi taimako ba</p><p>karaya.likitocin sunce xast duba shi xuwa gobe</p><p>su gani.nan ko jama'a suka dinga fadin</p><p>alhamdulillah.ummi ma tadan ji dadi a</p><p>ranta,sanna fa kowa ya tafi dama wasu sunce xa</p><p>stje yin sallah su dawo.saida suka koma sannan</p><p>suka taho da umma,ummi cikin kuka tace umma</p><p>da gaske bai mutu ba, umma tace eh bai mutu</p><p>ba,muyi magana dashi. . Umma tace in sha Allah</p><p>gobennan xai dawo gida. ummi tace to,umma</p><p>tace kinga wayata? gaban ummi ya fadi ta tashi</p><p>da sauri ta shiga neman waya,taci sa'ar ganin</p><p>wayar,sai dai bata san inda ta saka sim din ba</p><p>sai wanda ta tsinto ne a ciki.ummi dai tayi shiru</p><p>ta miqa ma umma waya. kusan qarfe goma sha</p><p>daya wayar abba da umma ta taho da ita ta</p><p>soma qara,umma ta dauka.alhj ne ya ce ina</p><p>wayarki ina ta kira ana cemin a kashe?una tace,</p><p>a ku6e take gata ma a hannuna.yace to inata</p><p>kira.tace qila faduwan da tayi daxu ne ta samu</p><p>matsala.yace to dama zance ne ki dafa masa</p><p>ruwan xafi a xuba a flask dan uwan matansa xai</p><p>kawo mu yanxun a mota xai amsa ya kai.ta ce to</p><p>alhj wayn xai kwana gunsa?yace bashir na nan</p><p>kuma matarsa anyi anyi ta qi tafiya shi yasa na</p><p>haqura xan dawo dan ba na xauna gun su ba ko?</p><p>umma tace amma yaya jikin nashi?ya ce da sauqi</p><p>yanxu ma yana son shan tea ne.tace to xan hada</p><p>harda wayar tasa inya so ma dunga kiran shi</p><p>kafin gari ya waye.ya ce yauwa ki</p><p>bada.Alhamdulillah abba jiki ba matsala. Don hk a</p><p>ka sallamo shi zuwa gd.kai tsaye gdn su umma a</p><p>ka wuce d shi. A salin dakinsa a ka gyara a cikin</p><p>kwana nan 3 ya yi ras sannan ya koma shago.</p><p>Bishira kuwa lkcn mahaifinta ya ce maza ta koma</p><p>dakinta,tunda ga abn d ya samu mijinta.Sun</p><p>dawo hr da tafkeken injin Janareto wai yaron ba</p><p>ya son duhu. Sannan ga kayan kallo d</p><p>saraunsu.TabbasAbba ya ji dadin dawowar</p><p>iyalanshi,dn dama yana cike d bukatarsu. Ranar</p><p>yini suka yi gyaran gd ita da 'yan uwanta,sai byn</p><p>magrib sannan ya shigo d tsarabobi.madara</p><p>tatacciya da kaji. Ya dauki dansa cikin jin dadi</p><p>yana kallonta cike da so da kauna,Nayi missing</p><p>din ku da yawa.URFIN CIKI book 2 part 3</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 2 part 3</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 22:08</p><p>Ai bama shiri. shi ne fa ya kawo ni mkrntr kwana</p><p>dn kawai baya son ganina. Suka yi ta mamaki.</p><p>Can jimawa ya dawo, sun fito rakiyar 'yan</p><p>uwansu Safiyya da na Khadija, suka ganshi tsaye</p><p>yana danne- dannen waya. Ya taho ya gaida</p><p>iyayensu duka,sannan suka koma gefe d ummi,</p><p>ya ce Ni ma zan tafi. Ta ce, Ya Abba ko fa</p><p>gaisawa ba mu yi ba. Ta karkatar da kai,Cikin</p><p>raunin murya tamkar mai shawagaba,ta ci ga ba</p><p>da cewa Ya Abba su Umma ba wanda ya ce a</p><p>gaishe ni? Sai hawaye suka soma zuba.</p><p>Hankicinshi da ke hannunta tasa tana sharar</p><p>kwalla.Abba yana da matukar tausayin mace. Don</p><p>haka duk da tsanar da ya yi wa Ummi sai da ya</p><p>tausaya mata.Ya tausasa Murya. Sun ce in</p><p>gaishe ki sosai, za ki ga gyada mai gishiri,</p><p>Tsohuwa ta ce a ba ki.Umma ta miki miya, ta</p><p>kuma daka miki yaji. Ta ce Na gode, Alhj me</p><p>yasai min?ya ce kayan tea ne da lemun kwali. Ta</p><p>ce Na gode. Tana ci gaba da share hawaye. Ya</p><p>mike Zan tafi. yasa hannu cikin aljihu ya ciro kudi</p><p>ya mika mata, ta ce A'a ya Abba ka bar kudinka.</p><p>Ya ce Ba ni ne na baki ba,Alhj Karami ne ya ce in</p><p>ba ki. Ta sa hannu 2 ta amsa tare d godiya.Sun</p><p>raka shi kusa da Gate ita da su khadija,sai kuka</p><p>Ummi ke yi. Bayan sun dawo dakinsu ne ta zauna</p><p>tana duba kayan da ya lissafo mata,duk ta gani.</p><p>Sai kuma saitin sabulun wanka da manshi da</p><p>turaransa da hodarsa duk na (Aloe vera.) Shi</p><p>kuma bai fada mata ko daga wa ba,ko ba komai</p><p>ta dai yi murna sobada tana da 'yan kuraje a</p><p>fuska,tasan kuma za su mutu. Sai kuma audagar</p><p>mata,tayi dan murmushi. . Tunda Umma taji</p><p>sallamar Abba ya shigo dakin ta bar komai tazo</p><p>ta zauna tana son jin lbrn Ummi. Abba ya fahimci</p><p>Haka,dn haka sai ya boye mata cewa, Ummi na</p><p>kuka hr yanzun. Ya nuna mata ai Ummi ta</p><p>kwantar da Hankalinta,km tayi hnkl dn ya bincika</p><p>ya ji ana ta yabonta. Umma taji dadi Sosai,Sai da</p><p>ya fara zuwa gurin Ummu,sannan ya je gida.Ya</p><p>samu Bishira tana zaune tana aikin nata,wato</p><p>Kallo. Tun da ta dawo daga wankan gida tazo da</p><p>janareto da kayan kallo,shi kenan ta sanu abn</p><p>yi.Kullum tana gabn (TV)da ta shi da safe in ta</p><p>kokarta shi ne ta dafa ruwan tea ko wanka ba za</p><p>ta yi wa dan ba,sai lkcn d man injin ya kare. Ya</p><p>nufi gurin injin ya kashe,dif din da ta ji komai ya</p><p>tsaya shi ne yasa ta zabura ta mike tana fadin</p><p>Ba dai har man nan ya kare ba? Ta fito da niyar</p><p>dubawa.Abba ta gani tsaye gabn injin yana bn</p><p>tsakar gidan da kallo cikin takaici. Ta ce Baban</p><p>Walid kashe min injin kayi??Ya ce Eh na kashe dn</p><p>Allah dubi gidanki?kalli wanke-wanke kuda na bi</p><p>dubi tulin wankin kayan Fitsarin yaronki. Dubi</p><p>kicin dinki,kuma ko da bn shiga dakinki da</p><p>wannan falon da ki ke kallo ba.na tabbata da</p><p>wanda ki ka dauke ko tsinkw a cikin sa.Kila ma</p><p>ba ki yi Sallah ba. Ta ce Dan karashe ne fa ya</p><p>rage min in gama kallon in zo in yi aikin.Haushi</p><p>ya sake kana shi,Sai kurum ya shige daki.</p><p>Tsakuwar da ya dora kafa a kai tasa tsigar</p><p>jikinshi tashi,sam ya tsani ya shiga daki ya dora</p><p>kafa kan datti. Ya dawo yasa takalmanshi ya</p><p>shiga da su,Walid yana kwance tun kayan da ya</p><p>bar shi da su da safe sune a jikinshi yana ta</p><p>bacci cikin fitsarin da ya shafka wanda ba wata</p><p>leda da zata hana katifar ta jike. Ko wankan safe</p><p>ma ba a mishi ba kenan.A fili ya ce,",Inna lillahi</p><p>wa'inna ilaihinr raji'un. ya juya ya nufi shagi. Ita</p><p>kam sai ta kunna injinta ta karasa kallonta,</p><p>sannanta tashi ta dora girki.sai lkcn ta ma Walid</p><p>wanka. Ta dan dauraye kwanukan da za su ci</p><p>abnci,wai ta gaji sauran wanke-wanken sai gobe.</p><p>Fati ta shigo,Bishira ta ce Yauwa Fatima naji</p><p>dadin zuwanki.shuga dakina ki gyara min gado,ki</p><p>dan yo min shara. Fati ta ce To. Ta shiga ita ma</p><p>duk shegiyar darin ce gurin kuiyar aikin,dn haka</p><p>ta dan birbira ta fito ta ce ta gama. Bishira ta ce</p><p>Yauwa dan dauraye min kaya can na Walid. Nan</p><p>ma tasan sama ta shanya. Bishira ta ce Yauwa</p><p>ta ga abnci nan kici.sai ki dauki na Ummarku ki</p><p>kai mata. Har Fati ta kai waje,Bishira ta kwala</p><p>mata kira. ta ce,Zo ki tafi da wannan galan din</p><p>na man fetir kije shagon Babn Walid kice ya taho</p><p>mana da shi,dn man ya kare. Koda Fati ta same</p><p>shi da galan ta fada mishi sako ya ce Ba zan siya</p><p>ba,Maida mata galan din. Ta tafi,Shi kuma ya ci</p><p>gaba da mita a zcyrshi. Yana fadin Na daina</p><p>sayan man tunda ba za a bari sai dare a kunnan</p><p>ba.Gidan Ummanshi yaje,ba ta nan ma taje</p><p>barkar Haihuwa. Ko dakin Tsohuwa bai shiga</p><p>ba,ya zauna nan falonta.Ya za kula ya zuba</p><p>abncinshi ya ci.sannan ya dan huta sai ya fita</p><p>zuwa gidan su Ahmad. Cam ya samu wasu daga</p><p>cikin abokanshi suka shiga hira. Ranar dai Abba</p><p>bai je gida ba sai misalin sha daya ko daya shiga</p><p>bai nemi matar gidan ba,ya dibi ruwa ya yi wanka</p><p>sannan ya shiga dakin. Ya lalibo makunnan wuta</p><p>ya kunna,dn Nefa sun kawo wuta. Tana kwance</p><p>irn banzan kwanciyarta da ta iya,dakin sai tashin</p><p>wani irin wari yake kamar na ruma,kamar na</p><p>fitsari ko na datti.Ya kalli ko'ina kullin kaya ne na</p><p>wanki ne,na gaga ne ciki da guri.Ranshi ya</p><p>baci,Ya kuma dubanta ga wata kiba da ta tafka.</p><p>Tun da ta haihu ta zama rusheshiya,gashi bata</p><p>son kama jikinta.Tsaki yaja,sannan ya dauki fiko</p><p>ya fita. kan doguwar kujera ya jefa filo,ya kwanta</p><p>a gajiye.Amma me?sai ya ji dora gadon bayansa</p><p>acikin lema.Da sauri ya mike ya kunna wuta.Duk</p><p>fitsarin yaron ne a kan kujerun dakin,dn haka sai</p><p>ya nufi dakin da takw aje tarkace ya kunna</p><p>wuta,shi ma dai duk shirgi. . Ya share Ya</p><p>shimfida ta barma ya kwanta,a ranar ya dauri</p><p>aniyar maida dakin ya zama nashi din-din-dn.</p><p>Don haka washegari yasa a ka zo a kayi masa</p><p>fenti,ya siyo kati fa ya yar da zanin gado,dk wani</p><p>abu nashi sai da ya kwashe su. Kafin wata guda</p><p>ya maida dakinshi cikakken daki,ya zuba dk wani</p><p>abu da yake bukata. kafin ya fita kullum sai ya</p><p>gyara dakinsa fes. ita kuma sam bata zuwa</p><p>dakin,sai dai in yana da lalura yaje can ya sauke</p><p>ya dawo. kazantarta kam ta kai in da ta kai,tunda</p><p>hr kayan kashi tana zube su a cikin daki. Ya gaji</p><p>yaje ya samu Anty ya fada mata,hr gidan Anty</p><p>tazo ta zazzageta,ta tasata suka gyara gidan,</p><p>amma ko a jikinta.Washegari ta ci gaba da in da</p><p>ta tsaya. Sam babu wanda zai ganta ya ce</p><p>haihuwarta daya. ¤¤¤¤¤¤ ¤¤¤¤¤¤ UMMI yau</p><p>ba wanda ya kaita murna,domin yau dai an basu</p><p>hutu..Sai dai tunaninta zata ko iya kai kanta</p><p>gida? Sunyi ban kwana bata da kudin mota, dan</p><p>duk tayi taba su safiya kudin gurinta, amma ta ce</p><p>yau ko da qafa ne xata gida.sun fito wajan mkrt</p><p>wata maryam tana cema,ki tsaya mota xato da</p><p>xata kaimu cikin kn.ummi tace baxan jira ba.sai</p><p>ga abba kamar daga sama,tsoro ya kamata karya</p><p>ce ta xauna gidan abokin sa da yace.hanka linta</p><p>ya tashi cikin in ina ta gaida shi ya amsa.ya</p><p>shiga mkrtn jim kadan ya dawo.hakan ta sha</p><p>alwashin yau ko da shiya saita je gida.shi kam</p><p>ma ya manta yai mata wannan maganan ma.ya</p><p>sabi akwatinta suka je suka shiga mota. abba</p><p>mamakin natsuwan ummi yake yi, ko da yake</p><p>baxai ce ta natsu ba, qila lafawa tayi.tundaga</p><p>soro ta saki jakanta da bokin tayi ciki da</p><p>gudu,cikin kuka tana kiran ummanta.umma ta</p><p>share do min tsohuwa tana cikin gida,kada tace</p><p>tayi rashin kara,sai tsohuwa ne ta tashi da sauri</p><p>tana fadin oyoyo takwara.suka qungume juna</p><p>tace to menene kuma na kuka?umma ta fito nan</p><p>fa ummi taje ta rungume ta.sai umma ta doje</p><p>tace bubi shirme,sakar ni ni.tsohuwa tace haba</p><p>suwaiba yarinya tana dokin, . Tsohuwa tace haba</p><p>suwaiba yarinya tana dokin ganinki amma ki</p><p>gwasale ta? abba ya ce daman nasan ba</p><p>natsuwan da yarinyan nan tayi,har ina</p><p>yabonta.dubi yanda ta xubarda kayan a soro.to</p><p>xaki debo su.tsohuwa tace bari ni in debo mata</p><p>tunda kai baka da tausayi.laile umma taga</p><p>canji,do min ummi dai tunda ta dawo ko qofar</p><p>gida bata fita ba,sai ko in an aike ta.sannan</p><p>yanxu ba gudu da tsalle tsalle bare tsokana.ga</p><p>aiki har girki ita kema umma komai.alhj yana</p><p>shan shayi da safe,ummi ta yi sallama ta shiga.</p><p>can gefen su umma ta xauna,sannan ta gaida alhj</p><p>ta gaida umma wanda ta saka alhj agaba tana</p><p>masa fira.wannan qa'idan umma ne bata barin</p><p>mijinta shi kadai,in har yana gida.alhj yace</p><p>suwaiba kinga ummina ko?laile abba yayi namijin</p><p>qoqari. yarinya ta natsu.umma tace Allah ya</p><p>amsa addu'an mu ka duba tsayuwan daran da</p><p>muka dunga yi bayan tafiyan ta kan cewa Allah</p><p>ya kintsa mana ita.alhj yace hakane,ummi dai na</p><p>jinsu tana murmushi.can tace alhj anjima xanje</p><p>gidan inna saratu in gaishe ta. qanwan sahura ce</p><p>da ke aure a kabuga.ya ce to ummi, xanba</p><p>umman ki kudin mota ko? ummi ta ce,to na</p><p>gode.ta miqe ta fita ta bar mahaifanta cikin farin</p><p>ciki jin dadin natsuwarta, suna godiya ga Allah</p><p>mai shirya bayinsa.lkcn da ta shirya dan xuwa</p><p>kabuga.sai umma tace ki kwana dan bana san ta</p><p>fiyan yamma,kabuga da nisa.tace to sannan ta</p><p>dauki kayanta kala guda, sannan ta fito.har xata</p><p>wuce sai ta shiga gidan alhj qarami,sahura na</p><p>ganinta ta hade rai,daman daqar take amsa</p><p>gaisuwan ummi tunda ta dawo.ummi ta gaisheta</p><p>a ciki ta amsa,sam ummi bata damu ba,tace</p><p>umma ina fati?ta yatsine baki tace tana gidan</p><p>abba,tace to inta xo ki ce mata naje kabuga sai</p><p>gobe xan dawo.umman bashir tayi tsaki,tare da</p><p>cewa ni yar aiken ki ne?ita dai ta wuce.tun</p><p>dawowan ummi suke shiri da fati kamar me,ko</p><p>yaushe suna tare suna fira.ummi tana mata</p><p>labarin mkrtn su.ita kuma fati tana bata lbrn</p><p>saurayin da tayi fahad,da irin son da take</p><p>masa.ummi tace tab,ni ko xanyi saurayi nafi san</p><p>irin ya abba...... . fati ta dubeta da al'ajabi kina</p><p>nufin ya abba kike so?ummi ta xabura tana fadin</p><p>tir, ko a mafarki Allah ya kyauta.ina nufin mai irin</p><p>hirarsa da tsafta.fati ta qyalqyale da dariya tare</p><p>da cewa ai na xaci shi kike cewa,inko ya ji kici</p><p>duka ummi ta ce,ai ni ba ma da shi nake ba</p><p>tab,shi da yayi auran so?kusan ko yaushe</p><p>yanayin hiran tasu kenan.ummi tana tafe</p><p>wadansu samari suka yi ta binta, sun shawo</p><p>kanta ta tsaya da kyar,kuma har ta masu</p><p>kwatancen gidansu. kwanaki uku bayan haka tana</p><p>ki shingide kan kujeran dakin umma,misalin</p><p>takwas saura ma dare.krtn wani littafi take yi na</p><p>hausa da fati ta ara mata,sam ita bata taba krnt</p><p>irin littafin ba,amma fati ta ce mata ta karanta da</p><p>dadi sunan littafin NAGA TA KAINA na</p><p>(sodangi).kasance wan wannan ne karo na farko</p><p>da ta taba krnt lbrn soyayya,sai abin ya</p><p>birgeta.amma nata ganin gwarxon sojan nan xai fi</p><p>dacewa a ce abba ne, jefi jefi takan kalli abba da</p><p>ke xaune kan kujera kusa da umma suna wani</p><p>xance da bata jiyo su. 'Amma tasan ko me suke</p><p>tattaunawa mai mahimmanci ne a gare</p><p>su.sallamar wani yaro ne ya katse su,umma da</p><p>abba suka amsa mishi a lkc gudu.yace wai ana</p><p>kiran ummi a waje inji wadansu.da sauri abba ya</p><p>kalla yaron,sam ba xai ce me yasa xance yaran</p><p>ya fadar masa da gaba ba.sai ya lumshe ido</p><p>sannan ya kalli ummi wadda kunya ta rufe</p><p>kasancewar yau ce rana ta farko da aka soma yin</p><p>sallama da ita.umma wadda kullum fatanta ummi</p><p>ta samu miji,sai tayi murmushi,sannanta ce da</p><p>yaron kace tana xuwa.abba ya dube ta da sauri,</p><p>umma kin san ko su waye?ta ce, a'a.yace ya</p><p>kamata a san ko su wanene dan kin san bata da</p><p>kan gado,kowa ma sai ta jajibo kuma ma duk</p><p>nawa ummin take da har xata soma tsayawa da</p><p>samari?umma tace,to abba ai gara ta kama</p><p>dahir, tana qare sakan dire ba sai ayi mata aure</p><p>ba?yace gaskiya umma gara ta dan taba krt,dan</p><p>yanxu xamani ne na krt.umma tace,tayi acan a</p><p>dakinta.ta dubi ummi tasgi kije.ummi ta miqe ta</p><p>fita.abba ya miqe shi ma,umma bari dai in gani</p><p>ma su kamun kai ne? umma tace to.., . Sun</p><p>gama gaisawa kenan sai ga abba ya fito.ganinsu</p><p>tsaye da ummi sai ya tsinci kanshi cikin wani</p><p>bacin rai.ya isa gun ya musu sallama, suka</p><p>amsa, sannan suka gaisa.yace daga ina kuke?</p><p>suka dube shi dayan ya ce lfy dai ko? ummi tayi</p><p>karaf ta ce yayana ne.anan suka sake gaida</p><p>abba.bai amsa ba, sai ma cewa yayi na tambeye</p><p>ku kai ma kana tambayana,wai lfy? suka ce,kayi</p><p>haquri,nan suka gabatar da sunansu.mai san</p><p>ummi shine nazir, abokinsa kuma sagir. sun 3a</p><p>masa cewa dukkansu daga kabuga suke.yace krt</p><p>kuke ko kasuwanci? sagir yace,eh krt muke,amma</p><p>muna taba kasuwanci a shagon mahaifinsa da ke</p><p>kwari.abba ya dan yi jim,sannan yace to kai ka</p><p>shirya aure ne?nazir yace eh to, nasan dai kafin a</p><p>tashi yi mata aure na shirya.abba ya ce, to ita</p><p>kam krt xata yi, kuma c ma buqatan ta hada krt</p><p>da soyayya. ya dubi ummi da fatan xaki sallame</p><p>su.ya juya gida.sagir ya ce, wannan wanki ne da</p><p>gaske? ummi tace qwarai kuwa. nazir ya ce to</p><p>yanxu ya kenan? kin ji abin da ya ce.ummi yayi</p><p>shiru tana tunani, ita fa basu kwanta mata rai,</p><p>tun randa ta hadu dasu,sam basu iya saka kaya</p><p>kalar yadda ya abba ke sawa ba.dan haka sai</p><p>tace, ina ganin xai fi mu haqura kada yaxo ni yayi</p><p>ta mun fada.nazir ya ce yanxun haka xaki ce?</p><p>ummi tace, um,sai da safenku.kada ku ja min</p><p>duka.sagir cikin jin haushi ya ce,ki xama</p><p>mangofak qarewan krt.sannan in kin gama wan</p><p>naki ya aure ki. ita dai ta shige gida.kusa da soro</p><p>ta iske umma da ya abba ta yo masa rakiya, tana</p><p>kuma ba shi aaki kan cewa yayi ta haquri,tace ina</p><p>fada maka ko yaushe ba fa fushi ko fada ne xai</p><p>saka matarka a hanya ba.lallashi da nashiha,ka</p><p>dunga koya mata giqki daka nutsu ka koya mata</p><p>ba gashi ka ce ta iya daidai gwargwado ba?abba</p><p>yace,hum lamarin yarinyan nan yayi nisa fa</p><p>umma,wankan jikinta ni xan koya mata? sallah fa</p><p>daga nake da ita.amma abin yaci tura.antynta</p><p>sau nawa tana xuwa tai mata fada duk a</p><p>cnxa,mkrtn ma ta qi xuwa.ni kuma da ce</p><p>ruwanta.umma cikin al'ajabi tace, sallah! sallai</p><p>ma bata san yi abba?abba yace umma baxan</p><p>mata sharri ba... Ta ce Tabdi,to kuwa ba kuwa</p><p>kazantarta ta wuce jiki hr d zcy. wannan ita ce</p><p>kazanta mafi muni. Don haka dole ne ka zage</p><p>damtse don ganin ta kama sallah,to menene</p><p>marabar arne d Muslmi in ba Sallah ba?Abba ya</p><p>ce Umma na mata nasiha na gaji. Ta ce To kasa</p><p>ta a mkrntr Islamiyya,kila ta ji tsoran Allah in</p><p>tana jin Wa'azi. Sannan ka dainga siyo mata</p><p>kasasuwan wa'azi.Abba ya ce Umma kaset nawa</p><p>na kawo mata bata sakawa,Kullum sai indiya da</p><p>Hausa fim,in naki sayan man fetur in tana da kudi</p><p>ta saya. In kuma ba a ta da shi sai ta dauki</p><p>ittafin Hausa ta dukufa.umma ta ce Allah ya</p><p>kyauta,kaje kayi ta hkr tare da addu'a. Ya kalli</p><p>Ummi,sannan ya ce ma umma,kada ta sake fita</p><p>gurin wadanan kananan yaran,sannan ya fita. A</p><p>daki umma take tambayar Ummi daga ina suke?</p><p>Ta ce um,Umma kyale su ni sam ma ba su min</p><p>ba. Umma ta ce to Allah dai ya miki za6i nagari.</p><p>Abba yana kwance a dakinsa ya yi lamo cikin</p><p>bargo,ya kasa amsa ma kanshi tarin tambayoyin</p><p>da ke yawo cikin kanshi. Haka tambayoyi suke</p><p>zuwa masa daya-bayan-daya ,me yasa ya damu</p><p>da lamarin Ummi??me yasa da a ka yi sallama da</p><p>ita ya samu kanshi cikin wani tashin Hankali? Me</p><p>ya sa ranar da zai je mata ziyara ya za6i ya sai</p><p>mata kayan kwalliya? A fili ya ce,don tana</p><p>kanwata.Zuciyarshi ta ki amincewa da haka. Me</p><p>yake shirin faruwa da ni ne? ya fada a fili. Ya yi</p><p>juyi zuwa rigingine,sannan ya dauki filo ya manna</p><p>a kirjinshi, ya ci gaba da magana shi daya. Bana</p><p>zaton cewa Son Ummi nake yi.don lkcn da na yi</p><p>tsananin Son Bishira bn ta6a samun kaina cikin</p><p>wannan yanayin ba. Kai Allah ya tsare ni da Son</p><p>ummi,wannan mahaukaciyar</p><p>yarinyar..........bugun kofarshi da a ke yi ne ya</p><p>katse shi. Murayar Bishira ce ta na cewa Babn</p><p>Walid!Babn Walid!! Ya bude kofar da sauri,ta ce</p><p>Walid ne ke ta amai. Ya fita ya dauki yaron daga</p><p>hannunta yana fadin Me zai hana shi amai,in ba a</p><p>ci sa'a ba har zawo sai ya yi,Saboda</p><p>kazantarki.Sam ba ki lura da me zai wawuro ya</p><p>tura bakinsa. Ta ce Yau fa bai ci komai ba,tun da</p><p>safe yake wannan aman.Ya ce shi ne ba ki sanar</p><p>da ni ba?Ya cire masa kayan jikinsa wadanda ya</p><p>ji suna ta doka karni.. . Ya isa igiyar shanya ya</p><p>ciri wasu yasa masa,sannan ya fita dashi.Wani</p><p>babban kyamis ya tafi da shi,mai kyamis din</p><p>likita ne,sai dai ba na yara ba ne,amma kowa</p><p>yazo sai ya duba shi.Nan dai ya masa bayani ya</p><p>ba su magunguna. Sha biyu dai dai ya dawo,tana</p><p>zaune tana kallo ya ce "A'uzubillahi,wai ke kallon</p><p>nan masifa ya zamarmiki ne?to ki sani na kusan</p><p>fita da kayan kallon nan. Ta ce,Tab,ka kaisu ina?</p><p>dadinta dai dafa gidan ubana a ka kawo su. Ya</p><p>ce ta za su koma gidan uban naki. Ta dafe kirji</p><p>"Zagina ka ke yi?ya dora mata dan a jiki "An</p><p>zage ki,ke din banza,kazama!yazube mata</p><p>maganguna ya fita. Ya jima zaune a kofar</p><p>gidanshi dafe da kai,yana tunanin shin wai shi</p><p>kadai ne bai yi sa'ar mata ba,ko kuwa duk maza</p><p>ne.Ya tuna abokanshi 2 da suka yi aure. Muktar d</p><p>Jamilu,sam ba su da wannan matsalar,duk lkcn</p><p>da yaje gidansu tsaf matansu,ga mutunci da</p><p>mutanta mutane. Shi kuma a cikin abokanshi</p><p>babu mai zuwa gidan sbd bata gainin kowa da</p><p>gashi. 'Yan uwanshi sai wanda ta za6a sannan</p><p>zata yi hulda da su. 'Yan garinsu kuwa can</p><p>¤ZAMFARA¤In suka zo kiri- kiri take nuna musu</p><p>kyama ga rowa,sam bata hulda da matan</p><p>abokanshi. Ya numfasa zai bi shawarar Umma ya</p><p>gani, amma gaskiya Bishira ba matar zama ba</p><p>ce. Tun da ya dawo sallarAsubahi dakinta ya</p><p>shiga tana ta shirga bacci. Walid kuma ya yi</p><p>faca-faca cikin kashi ya tausasa zuciyarshi ya ce</p><p>"Bishira! . Bishira!!Ya dan duki kafarta,sannan ta</p><p>tashi. Ya ce Ki tashi ki gyara masa jiki kiyi</p><p>sallah.Ta ce,Tab, me ya yi?ya ce, "kashi ya</p><p>yi.kurum sai ya ji ta ce Tab,wannan akwai dan</p><p>iskan yaro.Yanzun dan ubanka kashi ka min?</p><p>Sam bai san lkcn da ya watsa mata mari a baki</p><p>ba,cikin murya mai karfi ya ce "kada ki kuskura ki</p><p>sake ce ma dana dan iska!kar ki sake zagar min</p><p>yaro kada ki yi wa dana baki.Ba zan dauki</p><p>wannan ba. . Ta mike daga kan gadon tana kuka</p><p>Ni ka daka? wlh sai na rama. Kasancewar lebe</p><p>baya raina duka,sai jini.Nan da nan sai kumburi.</p><p>Ta cakumo shi,wlh sai na rama.Ya hankadata kan</p><p>gado ya bar gidan.cikin zcyrshi yana fadin</p><p>,"Wannan fitina da me tayi kama? Ita kam ruwa</p><p>ta dafa sannan ta wa yaron wanka, cukuikuiye</p><p>zanin gadon ta saka shi cikin baho,sannan tayi</p><p>kwaskwarima ta sabi danta baki suntum ta nufi</p><p>gida tana kuka. Mahaifinta bai nan yana</p><p>Abuja,Hjy Zainu ta kalle ta bayan ta gama kero</p><p>karyarta. Wai don yaro ya yi kashi ta ce yaron</p><p>bai kyauta ba shine ya hau ta da duka da zagi.</p><p>Hjy Zainu ta ce Amma wannan da muciya ya</p><p>dake ki ko?ta ce, Da hannu ne,nushina fa ya</p><p>dinga yi. Hjy Zainu ta ce Ai kin gani ba yadda ba</p><p>a yi ba ki tsaya kiyi karatunki kin ki,kin kafe sai</p><p>kin aure shi,wannan matsiyacin? Dama talaka</p><p>yana da wannan tsiyar.Yanzun za ki zauna mu</p><p>jiraZuwan Alhj,ba za ki koma ba.Ya dai baki</p><p>takardarki in yaso ki koma mkrnt.Su kuma su</p><p>dauki dan nasu. Bishira dai tayi shiru,zcyrta tana</p><p>jinjina rabuwa da Abba d kuma danata. Abba kam</p><p>gidansu ya nufa.Ummi ya soma cin karo da ita</p><p>tana sanye da doguwar rigar bacci,ta dora rigar</p><p>sanyu ta sakar ulu, a kai tana wanke baki da</p><p>busushi. Ta dube shi,mmkn ganinshi tayi a</p><p>wannan lkcn.Sai da ta dauraye baki sannan ta ce</p><p>masa sannu da zuwa,ya amsa a hnkl bai san mai</p><p>yasa ya kasa dauke idanunshi daga kanta ba,hr</p><p>ta gama alwala tayi addu a ta mike. Ta dube shi</p><p>da niyar yin magana,amma sai ta fasa don tana</p><p>tsoron kada ya daka mata tsawa. Ta daga</p><p>labulan dakin Umma zata shiga. Ya ce, "Ke!' ta</p><p>waiwayo cikin hada rai,domin ta tsani kiranta da</p><p>yake da ke!Ya ce Ummana fa?ta kalli dakin Alhj</p><p>Ba ta fito ba,,Ta shige ta zura hijabi ta tada</p><p>Sallah. Ya shiga dakin ya zauna,yana kallonta</p><p>tana Sallah zcyrshi tana nazarin Rayuwar</p><p>Ummarshi. Tun tasowarshi ya ke ganin kulawa da</p><p>kyautatawa da take yiwa Alhj Babba ga biyya,</p><p>sam bata wasa da dk wani abu nashi daga lkcn</p><p>da ya shigo gida ta gama sauraron kowa sai lkcn</p><p>da ya fita. Bai ta6a jin sunyi sa'in-sa ba bare ta</p><p>daga murya sama da tasa.Shin sauran matan ba</p><p>su fahimci irin wannan ladabi ba ne?Ummi tana</p><p>addu'a zcyrta cike da tunanin shi kuma ya Abba</p><p>me ya kawo shi da wannan sassafen? Muryar</p><p>Umma suka ji daga waje tana cewa,"Ummi in kin</p><p>idae ki fito ki share gidannan,ki wanke bayi,Ummi</p><p>ta ce To''. Sam Umma ba ta san Abba ya shigo</p><p>ba,dmn da ta ba Ummi umurni sai ta sake</p><p>komawa dakin mijinta, Ummi ta wanke bayi</p><p>kansu,sannan ta share ko ina na gidan, ta kunna</p><p>risho ta dora ruwan karyawa, sannan ta shiga</p><p>firar doya. Gyangyadi yake daga zaunw, Muryar</p><p>Ummanshi ce ta farkar da shi tana cewa, "A'aha!</p><p>ya bude ido cike da bacci.ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 2 part 4</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 2 part 4</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 22:10</p><p>"A'aha! ya bude ido cike da bacci. Ya kalle ta tare</p><p>da yin mika,ta ce "Lafiya"? Ya ce,Umma lfyr</p><p>kenan.Ta zauna da sauri Me ya faru Kuma? Yayi</p><p>dan tsaki,umma na gaji da auran nan ina ga</p><p>wannan karan xan yar da qwallon mangwaro in</p><p>huta ta quda. umma ta ce abba! abba!! me yasa</p><p>baka da haquri? ban xace ka haka ba abba,ina ce</p><p>jiyannan ka min alqawarin kawo qarshen duk</p><p>wata matsala tsakaninka da matanka?shin ban</p><p>fada maka hanyoyin da xaka bi ka xauna da</p><p>matarka lfy ba?ya kamo hannun ta,umma ba na</p><p>san bata ranki, ban san yadda xanyi da halin</p><p>yarinyan nan ba ne. jiya fa ina kwance taxo tace</p><p>min yarona amai naje kai shi kyamis,ina dawowa</p><p>na samu ta xauna tana kallon,ina mata magana</p><p>ta hayayyaqo min da asuba na tashe ta</p><p>sallah,wai dan yayi kashi shine ta hau xagin</p><p>yaron nan,wai dan iska. ni ko na bige mata baki</p><p>har da cukume ni da dambe fa.umma tace kaine</p><p>harda duka abba? dukan mace?ta xuba tagumi</p><p>tana kallon shi,ya ce umma xaginshi fa tayi,kuma</p><p>kin san dai ba kyau uwa ta dinga xagin danta.dan</p><p>ba haka kikai min tarbiyya ba.kalli rashin ji irin na</p><p>ummi, amma ban taba jin kin ce mata yar iska</p><p>ba.tace to ba sai ka xaunar da ita cikin tsanaki</p><p>ba?? . Yayi shiru a xuciyarshi fadi yake umma ba</p><p>xata fahinta ba.tace, tashi kaje ka bata haquri, ka</p><p>lallasheta.matafa sai haquri,kasan da qashin</p><p>haqarqari aka yi su,dole ka ganta a karka</p><p>ce.saidai nasiha da lallashi,da xaran ka ce kan</p><p>dole xaka miqar da ita,sai ta karye.nan dai ta yi</p><p>ta ma abba fada, har sai da shi kanshi yaga</p><p>cewa eh,yayi saurin fushi.dan haka ya miqe ya</p><p>nufi gida da nufin bata baki.sai dai kuma kash!</p><p>lkcn da yaxo tuni tana gidansu.ya dawo ya sanar</p><p>da umma, tace to dole sai alhj yaji kenan.ta shiga</p><p>gun alhj yana shirin fita. yace yau dai suwaiba</p><p>akwai abin da ya dauke miki hankali daga kaina</p><p>ko? tace, me kagani? yace tunda kika fita ban</p><p>kuma jin duriyarki ba, hatta karin kumallo yau</p><p>uwata ce ta kawo min.ko taya ni shafa mai yau</p><p>ban samu ba, tace uhum, abba ne in gaya maka</p><p>na gani hankalinshi a duk tashe, matsala ce suka</p><p>samu da matarshi,wai ta yi yaji.alhj yace,yaji?</p><p>umma tace eh wai a ce kamar abba bai san</p><p>yadda xai yi haquri da mace ba, alhj yace ina</p><p>abban?ta ce yana daki yana karya wa. Ya ce kira</p><p>min shi.abba ya xauna ya xayyane ma alhj komai</p><p>duk abubuwan da ke faruwa wanda take</p><p>masa,hatta batun sallah da bata san yi duk ya</p><p>fadia.alhj yayi shiru,can ya ce in ko haka ne ba</p><p>qaramin haquri kake yi ba, amma kaje xamu je</p><p>gidan.abba ya ce, ni dama xa a baita can dana</p><p>huta.alhj yace ba xa ayi haka ba haquri dai xa ka</p><p>ci gaba da yi.xuwan su alhj biyu gidan amma ba</p><p>suyi dace ba ance musu mahaifinta baya nan.</p><p>antynta kuwa ta kira shi a waya ya ce yana nan</p><p>xuwa gidanta.da dare suka je da ahmad sun</p><p>same ta ita da mijnta,anty ta tare su cikin fara'a</p><p>aka kawo musu kayan shaye shaye.nan dai abba</p><p>ya fada mata komai.ya qara da cewa ban sani ba</p><p>ko dan ni talaka ne shi yasa bishira bata ji</p><p>maganata? anty tace dame ka gaxa mata?</p><p>iskancintane kawai, wai bishira har da rashin</p><p>sallah,xa ko taci qaniyarta gun alhj.mijin anty</p><p>yace,tabdi lalle kana haquri nan dai suka ci gaba</p><p>da hira har mijin antyn yayi mishi alqawarin cewa</p><p>ya kawo takardunshi.MD din gidan rediyon</p><p>tarayya na jihar kd, amininshi ne. Amininshi ne</p><p>tun da abn da ya karanta kenan za a sama mishi</p><p>aiki.Abba ya yi ta godiya. Bai san da wane baki</p><p>zai gode ma mijin anty ba,tun daga nemna auran</p><p>Bishira yake taimakoshi, darajar su shi da Anty</p><p>da Alhjn su Bishiran yake hkr da halayanta. Ya zo</p><p>ya sanar da su Umman,Sun yi murna hr Alhj ya</p><p>ce dole ne in in masa godiya. Umma ta ce To</p><p>Abba ka gani fa,ta dailin matarka gashi zaka</p><p>samu aiki,ka yi ta hkr fa. Abba ya ce Umma ba fa</p><p>ta dalilinta ba,in Allah ya rubuto zan samu ta</p><p>hanyarshi sai ki gani,ko ban santa ba Allah ya</p><p>kawo sila.Ta ce To yanzun dai ita ce Silar,Allah</p><p>yasa albarka.Sai dai ba zan ji dadin tafiyarka</p><p>garin Kd ka barni nan ba. Ya ce Umma ko ni</p><p>tunda ya ce kd ke kurum ni ke tunan.Umma tayi</p><p>Murmushi,Allah ya maka za6i na alkairi,dk in da</p><p>za ka je.Amin Ummata. Mahaifin Bishira ya dawo</p><p>kuma Alhj ya tasa Abba sun je in da aka kirata</p><p>gata ga shi ga kuma iyayensu. Abba ya jero duk</p><p>laifunkanta bai rage ko daya ba. Sannan ya ce,shi</p><p>ma yana son ta fadi tsakani ga Allah me yake</p><p>mata wanda ba ta So?Nan fa a ka ce ta fadan,</p><p>sai ta shiga Kame-kame, Wai in ya shigo gida sai</p><p>ya yi ta fadace-fadace sannan ba ya zama a gida</p><p>sai tayi bacci,km ga abnci ta dafa amma sai ya</p><p>amso na Ummarshi ya c. Alhjnta ya daka mata</p><p>tsawa."Yi min shiru,yaushe ki ka bar musulunci?</p><p>Ba kya sallah ko?sannan ki bude baki kina zagar</p><p>masa da a gabansa?Ya bige miki baki kin kwaso</p><p>kin taho gida,to a miki uban me?ya dubi Abba</p><p>"Idiris me yasa ma ka mata duka ba?Ai ke babu</p><p>abn da ya dace da ke irin duka. Maza ki kakkabe</p><p>mayafinki ki koma gidanki,bana son in sake</p><p>ganinki da sunan yaji a gidana, . Zan wulakanta</p><p>ki. Kuma game da batun sallah dk lkcn da bata yi</p><p>ba ka dakar min ita ni na saka,batun tsafta kuwa</p><p>kada tayi,ka nemi mata ka aura ka barta da</p><p>tsiyarta. kai dk lkcn da ka samu matar ma zan</p><p>biya maka sadakinta ko 'yar wanene.Sai a lkcn</p><p>Alhjn Su Abba ya yi magana. Hakuri za ka yi</p><p>ranka ya dade,Allah ya saka da Alkairi bisa</p><p>karamcin da a ka yi mana,kuma insha Allah ba za</p><p>su sake ba. Abba ma ya yi godiya,sannan suka</p><p>masa sallama.Ita ko Bishira mayafi ta dauko tana</p><p>kuka suka tafi. Hjy Zainu ranta ya 6aci,taso a</p><p>kashe auran don dama bata son Abba sam,kafin</p><p>zuwan iyayen Abba da shi kansa Abban ta</p><p>fadawa mijinta karairayi,kamu ransa ya 6aci. Ya</p><p>kuma daukar wa kansa alkawari in ya bincika ya</p><p>tarar haka ne dukanta da zaginta yake ba tare da</p><p>ta masa laifin komai ba?sai yasa an raba auran.</p><p>Amma da yaji batun Abba gata a gurin bata musu</p><p>ba,sai ranshi ya baci da ita, har dai batun sallar</p><p>nan.dn haka ya bincike yana da kyau ayi shi,kada</p><p>ka yanke hukunci da maganar gefe daya,wannan</p><p>shi ne adalci. Bayan sun dawo Abba ya rakata</p><p>gida ya zo gurin Alhj da ya ce ya dawo yana</p><p>jiranshi. Alhaji ya masa fada cewa dk in da tara</p><p>tayi to ya kansace a gida. Sannan fadan da ta ce</p><p>yana yi in ya shiga shi ma ya daina,haka ya</p><p>dinga zama yana cin abncin.Abba ya ce to.Umma</p><p>ma da ya shiga suyi Sallama nan dai ta kara</p><p>masa fada tare da nuna mishi hanyoyin da zai bi</p><p>ta ce kuma cikin satin nan yayo mata rijistar</p><p>Islamiya tunda da ita a kusa. Ya shiga ya same</p><p>ta zaune bakin gado tana ta fushi,ya zo ya zauna</p><p>kusa da ita.Yasa hannunshi ya kamo nata,sannan</p><p>ya kira sunanta bata amsa ba bata kalle shi ba</p><p>ya ci gaba da mgn. Kin san dai ina sonki ko??ta</p><p>dube shi Da ba kafin a zuga ka.Ya ce wa zai zuga</p><p>ni? ta ce Wa kuwa in ba Ummar taka ba. Ya yi</p><p>tsam ya ji haushin maganarta sosai,amma sai ya</p><p>danne kada ki zargi Ummata tana sonki kin ki</p><p>fahimta ne kawai.amma mu bar zancan kiyi hkr</p><p>akan abubuwa da nike miki. ki yafe min nima na</p><p>yafe miki. . Ya jawota zuwa jikinshi,hr gobe ina</p><p>sonki sosai.Ranta ya yi sanyi don mata na son</p><p>wannan kalma daga mazajensu. Ya kira sunanta</p><p>ta dube shi cikin ido suke kallon juna,ya ce kin ya</p><p>fe min?ta daga gira,kina sona hr yanzun?Ta kara</p><p>mannewa a jikinshi "Ina sonka sosai ma.Ranar</p><p>dakin shi suka kwana,kuma ranar ce rana ta</p><p>farko da suka soma kwana a dakin nasa. Washe</p><p>gari tunda ya dawo Masallaci ya soma akin share</p><p>gida,lungu-lungu ya gama ya wanke bayi kan su</p><p>sannan ya yako ta da kyar ta tashi ya ce tayi</p><p>sallah ta yiwa yaro wanka. Tayi Sallar,wankan ta</p><p>kuke wai akwai sanyu,sai ranar ta daga. Ya ce,To</p><p>t dafa musu ruwan zafi su karya.Shi kuma ya</p><p>fitar da wankinshi yana yi ya gama ya ce ta fito</p><p>da duk wankinsu ita da yaron.Tsawaya ya yi yana</p><p>kallon tilin kayan,amma gudun kada suyi rigima</p><p>sai ya yi shiru ya ci gaba da wanki. . Ya cire</p><p>kayan yaron da zannuwanta hr ma zanin gado</p><p>wadanda yaron ya yi kashi ta aje su suka</p><p>bushe,,wasu kayan hr da tsutsotsi. Ya kira ta ya</p><p>ce "To kalli kayanki hr da tsutsotsi,wanna n ya</p><p>dac fisabilillah?samo leda ki kwashe su,ba zan</p><p>iya wanke su ba,in kuma za ki wanke to. Nan ta</p><p>samo bako ta kwashe takai gurin bola,ya ce</p><p>Bishira tsafta cikin addini ce,Annabi (S.A.W)ya ce</p><p>Babu mai shiga Aljanna sai mai tsafta. Don Allah</p><p>ki dinga kula,ke kanki za ki ji dadi in har ki ka</p><p>tsaftace ko'ina na gidanki.Ta tura baki ta wuce.</p><p>Ranar haka ya yini wanki kayan yaron dk sun</p><p>dafe kaya masu tsada da kyau irin wadanda a ka</p><p>sai masa daga gidan iyayenta,ranar dai ko shago</p><p>bai je ba. Cikin satin dai babu laifi suna ta</p><p>shiri,kuma tana daurewa tana yin tsaftar</p><p>jikinta,haka nan yasa ta wanke kai tayo kitso. sai</p><p>dai ita gani take dk an takura mata,amma tana</p><p>jin dadin yadda ya sakar mata fuska kamar</p><p>farkonauresu. Mitar da take masa kullum ya</p><p>daina dadewa a waje,ita don Allah ya zauna a</p><p>gida suyi hira. Ranar dai saiya gwada zama tun</p><p>da ya dawo sallar Isha'i ya shigo gida. Tana</p><p>zaune ba riga ya ce,Wai Bishira kayan kwalliyarki</p><p>sun kara ne? ta ce,Me ka gani?ya ce,Rabon da in</p><p>ga kwalli a idonki tun kina amarya bare dan jan</p><p>baki. . Taja dan tsaki "kwalliyar me zan yi sai</p><p>kace wata budurwa?Da dai nayi.Ya ce kin ji wani</p><p>shirme kuma,ban da ke ai matar aure me miji a</p><p>hannu ita ce da yin kwalliya. Ta ce, To ko ma</p><p>nayi ba zama ka ke ba.Ya ce "To yau dai gani na</p><p>zauna,kuma ina son a sheka min kwalliya. Ta</p><p>dube shi Gsky sanyi ba zan iya yin wanka yanzun</p><p>ba.Shiru ya yi yana kallonta,can sai ta zame ta</p><p>kwanta,sai kuma bacci. Ya yi murmushi.Dubi</p><p>matar da ta ce wai ba na zama a gida. to yau na</p><p>zauna amma kalli yadda ta bingire tana shirgar</p><p>bacci. Ya mike ya fice.cikin takaici korafin banza</p><p>kenan take yi tunda ba ta san yadda za ta yi fira</p><p>da mijin ta ba. haka dai abba yayi ta hakuri don</p><p>baxai yiwu ya ce shi kadai zai dauke mata duk</p><p>aikin gidanta ba. sai dai yayi wanda zai iya,amma</p><p>duk wanda ya shigo gidan shi ko ba a fada ba</p><p>yasan matar gidan kazama ce ta bugawa a</p><p>jarida. ummi tana zaune gaban umma,fuska</p><p>shabe- shabe da hawaye.ta rikewa ummar</p><p>hannu."kinji don Allah umma kice wa ya Abba ya</p><p>dawo dani garin nan.wallahi bana son makarantar</p><p>kwana,ni dai bazan koma ba."umma ta ce "haba</p><p>ummi xuwa yanzu ya ci ace kin saba da</p><p>makarantar" ta ce,"umma bazan saba da rashinku</p><p>ba....."karaf a kunnen Abba. ya ce,"to sai ko ki</p><p>shirya sabawa,don wata rana ma aure zaki yi."</p><p>umma ta ce sosai kuwa. tsohuwa dake zaune a</p><p>kofarta,tana jinsu ta sako baki da cewa,"ku dai</p><p>lallasheta,karatun nan fa da ake ta matsanta</p><p>mata bana ganin manzo bane." Abba ya ce</p><p>mata,"in ji wa? kin ji ki,to ana neman aljanna da</p><p>karatun boko kuma ana neman wuta." ta ce,"kai</p><p>ni raba ni da shegiyar karya tunda bata so a</p><p>barta." Abba ya dubi ummi,"kada ma kiyi za ton</p><p>maganar tsohuwa za tayi wani tasiri,gara ma ki</p><p>shirya komai gobe da wuri zamu wuce." ta dube</p><p>shi,"don Allah ya abba." ya mike ki shirya da</p><p>yamma zanzo muje (sahad store). ya dubi umma</p><p>na tafi. . Ta ce,"abba bamu ko gaisa ba,ya mutan</p><p>gidan?" ya ce,"suna lafiya,sauri nake in karasa</p><p>wasu dinkuna,saboda gobe bana nan jibi litinin</p><p>zanje interview da gidan radiyo da talabijin na</p><p>(c.t.v) ta ce,"a'a ka samu anan din ne?" ya</p><p>ce,"eh bana fada miki ba da aka tura takarduna</p><p>can sai suka ce gurin da zasu saka ni akwai wani</p><p>wanda suke jin dadin aikinshi a gurin? don haka</p><p>zasu turo ni kano,suna ganin ana bukatar irina.to</p><p>shine mijin anty ya fada min to yanzu sun kirani</p><p>ranar litinin zasu min (interview).ummi dai na</p><p>jinsu bata ba kukanta ba.abba na ficewa umma</p><p>ta ce tashi kije kiyo kitso ummina,kin ji? dakyar</p><p>taje ta dawo.umma tana yankan kubewa wayarta</p><p>ta shiga ruri,ta dauka Abba ne.ya gaisheta ta</p><p>amsa,ya ce ummana ummi fa ta shirya? umma</p><p>takai duba cikin daki inda ta hango unmi nade</p><p>kan kujera tunda ta fito wanka. Tace can cikin</p><p>kujera,wai sanyi take ji.yace sanyin lfy kuma? ta</p><p>shirya ta sameshi gida,umma tace to gatanan</p><p>xuwa sukayi sallama.umma tace ke ummi fito</p><p>man in kin gama shirin.ummi tace umma nifa</p><p>sanyi nake ji,ina ganin xaxxabi ne xai</p><p>kamani.tace to ku biya ta kyamis kusai</p><p>magani.tsohuwa tace ke yi kwanci yanki, dole ne</p><p>fitan? umma ta miqe tana cewa, yanxu in ban je</p><p>ba da yaxo xai fara min masifan shi ne. ta shirya</p><p>ta fuce rai a bace.a nutse ta ke tafiya har daf da</p><p>qofan gidan ya abba. sallama taji anyi mata.wani</p><p>matashi ne suka gaisa, ya tambaye ta nanne</p><p>gidansu? tace a,a lafiya?ba tare da bata lkc ba ya</p><p>fara xayyane mata manu fanta,santa yake kuma</p><p>da aure,tace kaga mlm sai anjima.ta shige gidan</p><p>abba shiko ya kafe yaqi tafiya.da sallama ta</p><p>shiga gidan,qaran inji baisa aji sallaman ba,dan</p><p>haka ta jingina da rijiya tana kallan tsakar</p><p>gidan.mamakin daya yadda mace daya a gidan ta</p><p>kasa gyara gidan.sai kace gidan namiji, namijin</p><p>ma qaxami. . abba ne ya fita wanka sanye da</p><p>jallabiya fara.ya aje bokitin ya dube ta. yace ki</p><p>siga ciki mana, ai tana falo.tayi</p><p>sallama,bishiratana xaune da baso tana kalan tv,</p><p>ganin umma ta daga labule sai ta hada rai tare</p><p>da cewa lfy? ummi tace ina wuni. bishira tace</p><p>lau, nace lfy? ta fada hadi da xare ido. ummi tace</p><p>ya abba ne ya ce na xauna anan na jira shi. tace</p><p>baxa a xo nan adame ni ba, ehe dan kallo nakeyi.</p><p>ummi ta ja tsaki tare da sakin labulan, ta koma</p><p>ta jin gina da rijiya.bishira ta fito.ke sarkin rashin</p><p>kunya wa kike ma tsaki? ummi ko kallanta batayi</p><p>ba.sannan tace baki isa kixo min har gidana</p><p>ba,kice xakimin rashin kunyan da kika saba.abba</p><p>ya jiyo hargowanta ya fito, yana qoqarin saka t-</p><p>shirt baqa akan faran singiletin shi,wandan jeans</p><p>ne mai laushi blue.yace,menene? tace, wannan</p><p>mara kunyan yarinyan nanne xata sameni har</p><p>dakina tamin tsaki.oa dubi ummi dake kallan</p><p>qasa tamkar bata san me akeyi ba. yace ke</p><p>ummi, ta dube shi da sauri,xan bata maki rai</p><p>kinsan bana san raini ko? tace nifa ya abba</p><p>banfa yi mata komai ba kawai fa.ya daga mata</p><p>hannu,yace banasan ji. yace na fada maki dai</p><p>bana san raini. takaicin duniya ya isheta,ta</p><p>sunkuyad da kai cikin qunan rai.wanna shine</p><p>gaba kura baya damisa.bishiqa kam sai ci gaba</p><p>da mita take, shiko abba tuni ya koma dakinsa da</p><p>qarasa shiri. ya fito fes, sam baxaka ce mijin</p><p>bishira bane.qamshin turaransa ya karade gidan</p><p>ya daga labule.ni na fita. tace sai ina? xan kai</p><p>ummi ta sai duk abinda xata nema dan gobe xata</p><p>koma mkrt. ta tabe baki. ya dubi ummi wadda ke</p><p>cika tana batsewa,sannan ga sanyi alamun</p><p>xaxxabi yana damunta.yace muje ko? ta dube shi</p><p>sannan ta bishi.a qofar gida ya iske wannan</p><p>saurayin,yace lfy, ko kana jiran wanine? saurayin</p><p>ya ce wata yarin....sai ya hango ummi,dan haka</p><p>ya katse batun da cewa yauwa gatanan. . abba</p><p>ya kalleta ke uwar rore rore wannan ke yake jira</p><p>ko? ummi tace oho mashi, bina yake tayi.abba ya</p><p>ce, kayi haquri dan samari,ba aure xa a mata ba,</p><p>krt takeyi. yace nima din bawai ina nufin yanxu</p><p>bane.ya ce na fahince ka.to ka bari sai nan</p><p>gaba,ina nufin in auran yayi sai kaxo ko???? Ya</p><p>dubeta ranshi bace,ke kuma wuce muje.suka bar</p><p>shi nan tsaye yana kallansu.yaga kishi qarara a</p><p>idon abba.yace wannan ba wanta bane shima</p><p>santa yake.ya raya aransa shima yayi gaba abin</p><p>shi.shi kam abba suna tafe yana yi mata fada,wai</p><p>tabi ta sakar ma maxa fuska kowane gaja sai ya</p><p>xo yace yana santa.maimakon ta tsaya tayi</p><p>krtnt,xamani na ilimi,ita dai ta qi kula shi,har</p><p>yanxu takaicinta abin da matarshi ta mata,kuma</p><p>ya nuna ya goyi bayanta.wayarshi tayi ringing,ya</p><p>kalli ummi muje shago na mashin din</p><p>nacan.sannan ya daga wayar,ita tana tafe ne</p><p>amma sam bata jin dadi.da yake tafiyanta yanxu</p><p>tamkar tana jin tausayin qasa take yinta,sabanin</p><p>da da sai dai tayi gudu,shi da ke tafe yana waya</p><p>ya riga ta isa.gefe ta tsaya ya shiga shago bayan</p><p>ya gama amsa wayar.ahmad abokinsa yaxo xai</p><p>shiga shagon ya ganta tsaye.tace ina yini ya</p><p>ahmad? yace lfy lau yar daru.daman haka ya kan</p><p>ce mata.ya shiga shagon yana</p><p>waiwayanta,abbana barma yan shagon sallahu</p><p>wasu kayan da xa a xo dauka,ahmad ya shigo.</p><p>suka tafa,sannan suka gaisa.ahmad yace naxo ne</p><p>in fada maka anjima xamu shiga gidan su hafsa</p><p>dan gaida iyayenta,sai dai kuma ganin ummi ya</p><p>sani jin wani abu.anya ba xan dawo gida da</p><p>neman aurena ba?a rude abba ya ce wace ummi</p><p>kenan? ahmad ya ce qawarka mana.abba ya ce</p><p>dan Allah saki xancen nan kada ma ta jiyo ta</p><p>raina mu,me ka gani naso a gun ummi? dan Allah</p><p>kada ka cta min rai. . ahmad yace, allah in xai</p><p>yiwu, nutsuwan ta birge ni .abba ya ce to ba da</p><p>ni xa aci amanar hafsa ba.ummi kuwa dan Allah</p><p>ka bar xancenta.yaea ahmad yaga abba ya sha</p><p>mur ya tsare gida,dole ya saki batun.suka yi</p><p>sallama ya tafi,abba na cewa sai yaxo da</p><p>dare.yasa yaron shagon ya goge mashi mashin</p><p>din sannan ya tada,ya kalli ummi fuskarshi daure</p><p>xo ki hau.itama tata fuskar a daure take.tahau</p><p>suka tafi,iskar dake kadata tasa xaxxabin dake</p><p>san kamata ta qaru.ya kafe mashin dhn ya</p><p>kalleta,muje mana.ta bishi suka shiga cikin sahad</p><p>store din.tsaye tayi tana kallanshi yana diba</p><p>kaya.da alama na iyalanshi yake diba,dan taga ya</p><p>soma da pampas. Hannuwanta harde a qirjinta</p><p>tana kallan shi,kome nashi yana birgeta.ya</p><p>waiwayo ya dubeta, tsayuwarme kike yi a nan da</p><p>ba xaki dauki abinda ya kawo kiba? ta rasa me</p><p>xata dauka,sai kurun ta dauki makilin ta riqe a</p><p>hannu,ya gama diban abin da yake so,sannan ya</p><p>aje gaban masu amsar kudi.ya dubeta,bakya</p><p>buqatar komai kenan? ta nuna mishi makilin din</p><p>hannunta,tana murxa shi.ya harareta baxa ki</p><p>dauki komai ba,kina da kayan tea dasu complex?</p><p>tace a,a.y2e to ki tsaya kada ki dauka.ya soma</p><p>dibo mata saitin sabulan nan daya taba sai mata</p><p>na aloe vera,dan yaga duk kananan qurajen sun</p><p>mutu.sannan ya hada mata da audugar mata</p><p>guda biyu.ya kai table.lkcn ta dauki madara da</p><p>milo ta kawo.yace wawiya,dalla matsa ki bani</p><p>gu.yaje ya qara tsinto mata ,sanna akayi musu</p><p>total ya biya.suka fita.kafin sukai gida haqoranta</p><p>sun s6a haduwa,gashi tana ta takurewa,yace</p><p>lfy,wani irim xama kika yi haka?tace,sanyinake</p><p>ji.tana magana muryarta na makyarkyata.wani</p><p>dan asibiti ya nufa da ita nan kusa da unguwansu</p><p>aka dubata. Wurin allura,nan fa a ka soma</p><p>daga.Ta ce,ita kam bata san allura.Abba ya daka</p><p>mata tsawa da cewa,Allurar ce abn tsoro?Na</p><p>gane sam ba ki son ki koma mkrnt,a gobe ne</p><p>kuma sai kin koma duk abnki. Ta ce, Naji zan</p><p>koma amma yanzun kam dn Allah Ya Abba kada</p><p>amin allura.Nurse dai sai kallonsu take yi tana</p><p>dariya. kwai Ummi sai ta soma hawaye ita fa har</p><p>ga Allah bata son allura.Nurse ta ce,To ka rike ta</p><p>mana ko ba Amarya ba ce?Naga shagwabar tayi</p><p>yawa. Abba ya ce,Me? cikin tsawa ya yi</p><p>maganar,hr sai da Nurse din ta tsorata,ya ce</p><p>kanwata ce fa,kin ga wannan kucakar tayi kama</p><p>tayi kama da Amare? Nan take Ummi taji ta</p><p>muzanta,sannan km ta tsorata da irin tsawar da</p><p>ya yi,ba ta san lkcn da ta shige a ka yi mata</p><p>allurar ba. Ta fito tana sharar kwalla suka koma</p><p>gida. Sai dai tana hada kayanta a Jaka,Sannan ta</p><p>ga wadannan sabulun da kuma audugar,kenan shi</p><p>ne dama ya sai mata wancan?ko me yasa ya sai</p><p>mata kuma hr da augugar mata? . wata zuciyar</p><p>ta ce,kila dn yaga Umma bata san kan abubuwan</p><p>zamani ba sosai.A fili ta ce,kai umma tasan</p><p>audugar mana. Haka dai ta ci gaba da tufka tana</p><p>warwarewa,hr ta gama shirya kayanta. Yau kuma</p><p>a bayan Tsohuwa ta za6i kwanciya,da dn komai</p><p>ba sai dn suyi hirar yaushe gamo. Sai dai</p><p>Maimakon hira sai ta tsunduma a tunani,ta bar</p><p>Tsohuwa tana ta zance ita daya. Fitarsu da Ya</p><p>Abba ta tsaya mata a rai,ita tayi ta tunowa tana</p><p>murmushi.Sai dai bata Son tuna lkcn da ya yi wa</p><p>Nurse din nan tsawa dn ta ce ko ba amarya ba ce</p><p>kom me yasa zai mata Tsawa? ita kam kalamn</p><p>Nurse din nan sun birgeta,shi kuma daga ganin</p><p>yadda ya yi tsawar nan kalamn ba su masa dadi</p><p>ba.......... wai takwara bacci ki ka yi ne?Muryar</p><p>Tsohuwa ta katseta,ta ce,Idona biyu Tsohuwa.Ta</p><p>ce, Tunanin me ki ke yi ne haka?Ummi ta ce</p><p>"Um" ina tuna gobe yanzun ina can.Tsohuwa taja</p><p>tsaki,Ai mai sunan Malam ya san takan mugunta.</p><p>UMMI dai ta ce "Um.Tsohuwa kuwa sai yi take</p><p>da mai sunan Malam.Tun Ummi naji tana "Um",</p><p>hr zcyrta ta soma tsanar kalaman Tsohuwa. Sai</p><p>dai bata da damar ta katse Tsohuwa tunda dn ita</p><p>take yi,bata da mafita da ta wuce ta bar</p><p>dakin,don haka ta suri butar Tsohuwa,wai zata je</p><p>kewaye(bandaki). Shi ma Abban da ke kwance a</p><p>tsakar dakinshi kan kafet ya tada kai da</p><p>katifarshi,ban da tunanin fitarsu ta dazun ba abn</p><p>da ya keyi. Sai dai damuwarshi daya,me yasa</p><p>samari da dama suke kawowa Ummi hari?Me</p><p>yasa ya ke jin zafin haka?Zuciyarshita amsa da</p><p>cewa,ka so ko ka ki kana Son UMMI."a fili ya</p><p>furta "Haba dai so,Allah ya tsare ni." Tun misalin</p><p>tara Ummi ta gama shirinta tsaf,cikin kayan</p><p>mkrnt mai ruwan hoda,mai gida-gida.Da kuka ta</p><p>bar gidan yau ma. Haka nan kuka take hr suka</p><p>isa mkrnt,ta samu Khadija hr tazo,dn haka tare</p><p>suka kwashe kaya.Kafin Abba ya tafi sai da ya yi</p><p>mata fada kwantankwacn wnda Umma tayi</p><p>mata.Waton ta kula d kanta,kuma tayi abn da ya</p><p>kawo ta,waton krt.Sannan ba ya son tayi</p><p>kawance d yaketa shari'a.irin wanda wasu</p><p>watsatstsun yaran ke yi.(Allah ya shiryesu).</p><p>Sannan ya jadadda mata batun ibada,sannan ya</p><p>kawo kudi ya bata,ta ce Umma fa ta riga ta bani.</p><p>Ya ce,"Ki kara."ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 2 part 5</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 2 part 5</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 14 Dec 2016 - 22:12</p><p>Umma fa ta riga ta bani. Ya ce,"Ki kara."</p><p>Rayuwarta a mkrnta wannan karon ba laifi,sai dai</p><p>fa hr yanzun ta tunu da gida sai tayi kuka. Su</p><p>Safiyya suna mmkn yadda Habiba take da</p><p>matsanancin nacin gida. ******** Abba ya shigo</p><p>gidanshi dauke da ledajin kayan miya,da sauri ya</p><p>dire su kofar kicin ya nufi Bishira da ke kofar</p><p>bandaki tana shara amai. Ya kama ta,"lafiya?Me</p><p>ki ka ce? Sai da ta gama aman sannan ya karasa</p><p>da ita ta wanke baki da fuska a cikin bayin. Ya</p><p>ce,Ba ki d lfy ne?Ta soma Hawaye, Ka gani ko</p><p>Babn Walid,kila fa ciki ne da ni.Tun wancan Satin</p><p>ya kamata in ga al'aldata amma shiru. Ya ce, To</p><p>menene na kuka? Yi shiru,Allah ya inganta.Ta</p><p>harare shi Dana fa bai shekara ba.Ya ce,To dole</p><p>ne sai danki ya shekara sannan Allah zai baki</p><p>wata kyautar? Ta soma kuka,Ni dai zan je a</p><p>ciremin ne. ya hade fuska,Ban yarda da haka ba.</p><p>Ganin ta tada hnklnta tana cewa "Dama Hjyrsu ta</p><p>ce mata tabi a hankalu ta ki ji gashi nan yanzun</p><p>tana da wani ciki. Ya ce To kada ki damu kin ji?</p><p>Zamu je asibtin dn a tabbatar da cikin kafin a san</p><p>abnyi. Da za suje asibiti shi ne ya dage sai da</p><p>tayi wanka,dn d farko kaca-kaca ta dauko</p><p>mayafi, ya ce sai tayi wanka ta canza tufafi.</p><p>Gwajin farko ya tabbata tana da ciki,nan ta shiga</p><p>kuka. shi kanshi ya damu domin bai so ciki</p><p>yanzun ba.A son ranahi sai an yaye yaron kafin</p><p>wani cikin. Amma ba shi da ra'ayin</p><p>zubarwa,nashi ganin kyautar Allah ce,dn haka ya</p><p>amsa ya kuma gode. Ya lallashe ta da cewa,ta yi</p><p>hkr su amshi kyautar Allah dn haka wani na nema</p><p>da kudi bai samu ba. likita ya ce,Kada ta</p><p>damu,taci gaba da bai wa danta abnci tana hada</p><p>mishi da nonon,a hnkli zata yaye shi bana farat</p><p>daya ba. Bayan ya kaita gida ya kuma</p><p>lallashenta,saiya nufi gurin Umma. Bayan sun</p><p>gaisa,ta tambayi iyalanshi ya ce "Daga asibiti ma</p><p>muke da Bishira." Umma ta dube shi da</p><p>sauri,Waye ba lfy? ya ce, Ita ce.Sai kuka ma take</p><p>yi wai dn an ce tana da ciki. Umma ta ce, Ikon</p><p>Allah, to Allah ya inganta.Sai dai kuma kada</p><p>Walid ya sha ciki. Abba ya ce,likiya ma ya yi</p><p>mata bayanin yadda za ta yi masa,hr ta janye shi</p><p>daga nono cikin hikima.Umma ta ce, Da za ta</p><p>yarda ma an kawo mana shi nan. ya ce,Ai dama</p><p>nan zan kawo shi da zarar an yaye shi Umma.</p><p>Sam bai fada ma Bishira nufinshi na baiwa Umma</p><p>Walid ba,dn yasan ba zata ta6a laminta ba.Sai</p><p>dai itama tasan dole hakan zai yi. Don haka ta</p><p>garzaya gurin Umman Bashir ta shaida mata</p><p>cewa sunje asibiti,dk ta fada mata komai,sannan</p><p>ta ce ita danta take tunani kada ya dauka ya</p><p>kawo wa Ummarshi ita ma a mallake mata yaro.</p><p>Umman Bashir Ta ce Wannan a zaune take,sai</p><p>dai in ko ba a kai shi ba.Amma ki bari daga kin</p><p>kula ya daina damuwa da nonon ki janye shi,zan</p><p>zo in taho da shi wurina. Bishira taji dadi tare da</p><p>cewa, Hakan dai yafi. Sabuwar kazanta ta</p><p>samu,Bishira dk abn bi bangon daki an tofe da</p><p>yawu.Rashin wanka sabo,kai abn nata sai</p><p>addu'a. Ibada kuwa ba a mgn,domin dai tuni ta</p><p>aje Sallah a gefe,Azumi dai tana yi amma in ta</p><p>sha bata ramawa.Allah ya shirye wanda ya 6ata.</p><p>Abba ya dai yanzun tuni ya yafe abincin</p><p>gidansa,matsawar ba shi da kanshi ya girka</p><p>ba,don kuwa dama can shi mutum ne mai</p><p>kyankyani. In zata fita takan wanke kafafunta ta</p><p>dauki kaya ta saka,sai ka rantse tayi</p><p>wanka.Amma da zata matso kusa da kai,nan za</p><p>ka ji kauri na tashu da karni da kuma wari. Dole</p><p>ya hkr da laluranshi ta aure a gurinta,domin in</p><p>yaje shimfidarta ba zata ki ba,amma wari da</p><p>zarni suna hana shi yin komai cikin nutsuwa. In</p><p>kuma dakinshi ya kirata ko bata kwana ciki ba</p><p>har gari ya waye yana jin warin jikinta a</p><p>shimfidarshi don haka lokuta da yawa yake</p><p>hakura da ita. *********** . Ummi tana kwance</p><p>kan gadonta,yayin da Khadija da Safiyya suke</p><p>zaune bakin gadon Safiyyan wadda ke kallon</p><p>Ummi. Hirar masoyinta take basu,Safiyya bata ko</p><p>gajiya da zancensshi. Khadija ta ce,ita ma da</p><p>zata taho har kuka nata Saurayin ya yi. Sai lkcn</p><p>Ummi ta dube su,"kuka Khadija?Khadijata</p><p>ce,"Riris Kuwa. Ummi ta ce, Hu'um ba namijin shi</p><p>yasa nike da za6i a kan irin mijin da zan aura.</p><p>Safiyya ta ce,"ke banza,dk cikin so ne. Ummi ta</p><p>ce Ban damu da sai namiji yaso ni ba,in dai ya</p><p>tara abubuwan da nake so ga namiji to zan yi</p><p>amfani da kasantuwata 'ya mace in koya mishi</p><p>Sona. Khadija ta tashi ta dawo kusa da Ummi,Kin</p><p>san me ki ke fada?Koda yake sanar damu yadda</p><p>ki ke son mijinki ya kasance? Ummi ta ce "Na</p><p>farko mai son Addini,Mai Ilimi duka 2,mai hakuru</p><p>,sannan yana da saurin fushi,mai kuzari da</p><p>kwarjini. Ma"abocin tsafta da tsantseni,wandadk</p><p>tufafin da yasa sai sun kar6e shi,mai biyayya ga</p><p>iyayensa,sannanmai kula da gidansa,baki mai</p><p>tsare gida,ga yawan Ibada, Safiyya da khadija</p><p>suka kwashe d dry,Khadija ta ce, Ina za ki samu</p><p>dk mai wadannan lissafin da ki ka yi??? Safiyya</p><p>ta ce, Kuma fa bata gama lissafin ba ke ba ki ji</p><p>ana cewa dan Adam tara yake bai cika goma ba?</p><p>Ummi ta ce,Akwai shi,Ya Abbanmu haka</p><p>Halayansa suke. Yanzu ma da ni ke lissafin shi</p><p>na ke kallo a idona.Khadija ta ce,To ba dan</p><p>uwanki ba ne da shi kenan kin samu a gida.Ummi</p><p>ta ce,Wuu fitina Road,wannan ya mugun tsanata,</p><p>ina son dai me irin halayarshi ds</p><p>dabi'unsa.Khadija ta ce,Har da kamaninsa? Ummi</p><p>ta ce,sosai ma. Saitaga sun sa dry.Safiyya ta ce,</p><p>Malma shi ki ke so,kuma dk yanda a ka yi ba</p><p>shakikin ki ba ne,da aure a tsananinku. Umma</p><p>tayi Shiru tana kallonsu,Khadija ta ce,Habiba</p><p>kenan,wai har saurin fushinshi tana so. Ummi ta</p><p>6ata rai tare da cewa,Tunda kun kasa fahimtata</p><p>shi kenan.Ya zan yi in ce ina son Ya Abba yana</p><p>da matarsa? SAfiyya ta ce,ke dai in da aure</p><p>Tsakaninku kada ki tsaya "ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com, kizo a</p><p>karshe kina da kin sani. Ummi ta ce,A bar</p><p>zancen. 32... Sai dai kuma a daran ranar ta</p><p>tsinduma duniyar tunani.Tabbas zuciyarta da</p><p>shisshiga take,tunda ta rasa wanda zata so sai</p><p>Ya Abba. Wanda ya yi mata muguwar tsana.Afili</p><p>ta ce,Duk kauce-kauce da kewaye-kewaye ba za</p><p>su kai ni ba,Ya Abba nake so. Hawaye Suka</p><p>soma sintiri daga idanunta. Wannan lkcn ziyarar</p><p>da yazo Abba da Umma d Tsohuwa da Alhj</p><p>Karami dk suka zo. Dadi ya kashe Ummi,ta rasa</p><p>jikin wanda zata fara fadawa don dadi. Alhj</p><p>karami ta soma kamkamewa sannan</p><p>Umma,Tsohuwa kam ai tana manne jikinta hr</p><p>suka zo tafiya.Shi ko Ya Abba yanzun kunyarshi</p><p>take ji,dn haka tunda suka gaisa mgn bata kara</p><p>hada su ba. Sai dai jife-jife suna satar kallon</p><p>juna,in sun hada ido sai ya dan daure</p><p>fuska.Safiyya da khadija sun gaisa da su sannan</p><p>sun yaba da yadda a ke ji da Ummi. Da za su tafi</p><p>kuwa Ummi kuka Tsohuwa kuka,sai da Abba ya</p><p>ce ba za a sake zuwa da su ba,Sannan Ummi tayi</p><p>shiru.Sun tafi sun barta d kewarsu,Kamar yadda</p><p>suma suka tafi suna kewarta. ********** . Bishira</p><p>da kanta ta dauki Walid ta kai ma Umman</p><p>Bashir,domin ta san zai kai ma Ummanshi ne.</p><p>Abba ya rufe ta da fada lkcn d y tambayi dan ta</p><p>ce ta yaye shi ta kai ma Umman Bashir. Ya ce To</p><p>je ki dauko mn yarona,dn ba can nayi niyyar kai</p><p>shi ba,Ta rike kugu,kaje mana da kanka,tunda ba</p><p>ka son zamn danka hannun mahaifiyarka to ni ba</p><p>zan yi saken da Mahaifiyarka tayi ba a ka raba ta</p><p>da danta ina fata ka fahimci karatuna? Kallo</p><p>kurum ya bita da shi,sannan yaja tsaki tare da</p><p>cewa,Dube ki kmr wata Bauna,jiki sai tsami yake.</p><p>Ta ce,Eh dk abn da zaka ce kace. Ya juya ya fita</p><p>rai 6ace. Umma ya Samu ya fada mata, ta ce, To</p><p>menene na bata rai Abba? Can din da nan ba dk</p><p>daya ba ne? ai ba za su cutar da shi ba. Ya ce, ki</p><p>fahimce ni Umma,ba ina nufin zai cutu ba</p><p>ne,amma can da yara kanana,nan kuma babu.</p><p>Sannan......... ...... Sai kuma ya yi shiru tare d</p><p>cewa,Shi kenan. Umma ta ce,Yauwa bana son</p><p>kana daga murya kan abn da bai kai ya kawo ba.</p><p>Allah ya raya mana shi ya kuma sauketa lfy.</p><p>Abba Ya ce Ameen. Gidan (T.V)sun kira Abba sun</p><p>masa (intervier)da kusan wata 2,dmn ya cire ran</p><p>samun akin, ko da yaje suka ce sun dauke shi</p><p>aiki. Abn d yasa suka yi jinkiri daukarshi,suna</p><p>canza tsarukan aikin ne sannan sun sake</p><p>tantance ma'aikatansu. Litinin Abba ya soma</p><p>zuwa aiki kmr yadda a ka bukata,dakin watsa</p><p>labarai a ka kai Abba. Sam bai samu matsala</p><p>ba,dk d shi na mai yawan surutu ba ne,amma a</p><p>cikin sati 1 ya goge da aikin,km an yaba da yadda</p><p>yake watso labarai. Yana yi da Hausa minti sha</p><p>biyar da turanci minti sha biyar,ana sakawa karfe</p><p>7 na yamma. Abba ya kama aiki cikin sa'a nan</p><p>da nam sai farin jini cikin abn d bai fi wata ba ya</p><p>nemi izinin a bashi fili koda mint 15 ne don</p><p>gabatar da wani fili da ya yi masu don matasa.</p><p>filin yana kiran shugabannin matasa na</p><p>unguwanni suna hira da su akan halin da matasa</p><p>suke ciki na shaye- shaye da sace-sace da kuma</p><p>rashin sana'a. Da turanci a ke shirin,sannan a kan</p><p>baiwa sauran matasa na gida su bugo waya su</p><p>fadi nasu ra'ayin,game da abin da ya kawo</p><p>hakan,da kuma hanyoyin da za a bi don magance</p><p>su. Haka nan ya kan samu lkc ya shiga cikin</p><p>matasan musamman ma su shaye-shayen da</p><p>marasa sana'a dn jin ra"ayoyinsu,da dalilan</p><p>fadawarsu cikin harkar. Kafin wani lkc filin ya yi</p><p>suna kuma kullum yakan tallata filin kan cewa ya</p><p>kamata Gwamnati ta dauki nauyi filin don yana</p><p>taimakawa mata wurin inganta rayuwar matasa.</p><p>Cikin ikon Allah sai gashi Gwamnati ta yaba da</p><p>filin,ta dauki nauyin shirin kuma an sa shi hr</p><p>fannin Radiyo. Lallai Abba ya shigo da kafar</p><p>dama,Sannan hukumar gidan Radiyo tayi Matukar</p><p>farin ciki da zuwan Idris Aminu Idris,wannan</p><p>Ma'aikata. Sannan sai Abba ya zama wani sabon</p><p>tauraro wurin Al'umma,dk in da a ka ganshi ya</p><p>zama abn kallo. Matsalar shi daya gidanshi,in ka</p><p>ganshi a waje Sam ba za a kayi tsammanin haka</p><p>zaka samu gidanshi ba,Dattin ya karu,musamman</p><p>da ya kasance yanzun ba shi da lkcn kanshi</p><p>ballatana ya yi sammakon share gidan. Wankinshi</p><p>mai kaiwa yake yi,haka nan nasu ya ce ta dinga</p><p>kaiwa makota gidan wanki. Amma kafin ta hada</p><p>ta kai aiki ne ita dai tayi kallo ko a shiga makota</p><p>hira. Sam Abba ko adreshin Zai bada ya</p><p>gwammace ya bada na gidansu Ummanshi dn ba</p><p>ya so aje gidanshi ************* . Kwanci tashi</p><p>Ummi suna ta fana da jarabawa zuwa (SS2) cikin</p><p>ikon Allah suka gama. ranar da aka yi musu hutu</p><p>kamar ta sani bata tsaya jiran Abba ba,Ta nufo</p><p>gida. Shi kuwa lkcn suna kici-kicin kai Bishira</p><p>asibiti zata haihu,amma yana sane da cewa yay</p><p>Ummi zata dawo kuma hnklinshi na can. Motar</p><p>wani Salis Abokin aikinsa ya aro ya kai su</p><p>asibitin ita d Ummanashi. Bayan ya ba d dk wani</p><p>abu da suke bukata ya ce Umma za shi dauko</p><p>ummi. Umma ta ce,Ka barta tukunna in matarka</p><p>ta sauka lfy gobe sai kaje tunda tana mkrnt ne.</p><p>Ya yi-ya yi Umma ta ki,dole ya hkr. sai bayan</p><p>la'asar sannan ta haihu,Nurse ce ta zo tayi musu</p><p>albishiri an samu 'ya mace. Bayan an kintsa</p><p>uwar,sannan a ka kaita dakin hutu,su kuma a ka</p><p>kawo musu 'yar.Nurse din da ta kawo 'yar ta ce</p><p>d Umma ke ce Mamanta? Umma ta ce,'Eh."Nursr</p><p>din ta ce "kazantar yarinyar tayi yawa,kafin ta</p><p>haihu sai da likita ya korata ta yi wanka,muka yi</p><p>mata aski ko'ina jinkinta datti. Gsky Mama</p><p>mijinta yana kokari,yanzun kuje ku dafa ruwan</p><p>dumi ku kawo mata tayi wanka. Abba ya yi tsaki</p><p>ya ce, kin ji ko Umma,Allah ya kara.Umma ta</p><p>ce,Yanzun kaje gida ka dauki babban filas dina ka</p><p>shiga wurin Umman Bashir ka ce Mata ta dafo</p><p>ruwan Zafi,daga nan ma sa ji haihuwar. Yana</p><p>shiga gidan tun daga zaure ya jiyo Muryar</p><p>Tsohuwa tana cewa,Naji shiru-shiru kin ga dai hr</p><p>yanzu. Yana saka kafa a tsakar gidan muryar</p><p>Ummi ta daki dodon kunnanshi.in da ta ce,Kila</p><p>kuma ta haihu yanzun. jinin jikinshi ya tsinke dn</p><p>jin Muryae. Ya nufi dakin.Tana zaune tana shan</p><p>rake. Ya dubeta, ita ma shi take kallo dn tunda ta</p><p>diro ba wanda take muradin Gani irin shi,cikin</p><p>sanyi murya ya ce,Ummi ke da wa ki ka taho? Ta</p><p>sunkuyar da kai,Ni da wasu 'yan mkrntrmu ne</p><p>muka dawo. Ya ce '"Good,tashi ki dafa ruwan zafi</p><p>ki zuba a babban flask. ya dubi Tsohuwa da take</p><p>ta tambayarshi ko mai dakin nashi ta sauka? Ya</p><p>ce, Eh ta haifi 'ya mace. Tsohuwa cikin takaici ta</p><p>ce,Sai yanzu kaga damar bani amsa?Dan</p><p>walakanci kawai? Kai mai sunan Malam ka gyara</p><p>halinka. Abba ya ce,Yi hkr Tsohuwa dk na gaji</p><p>ne,Nan kuma ina yi wa Ummi mgn. Ta ce kana</p><p>mata fadan ka dai. Ya ce,Tsohuwa wai ni hr</p><p>yanzun ba zan wanku a wurink ba game da</p><p>Ummi? ta ce, Ina fa zaka wanku?Har abada mai</p><p>sunan Malam kai ba me kaunar takwara bane. .</p><p>Yace to naji a bar maganar yanzu dai kishiyarki</p><p>ta haihu.an samu ya mace.tace Allah ya raya</p><p>mana. Yana jingine da bango yana kallon ummi</p><p>tana ta shige da ficen daura ruwan zafi.komai</p><p>cikin tsafta da natsuwa take yi. Sai da tasa</p><p>ruwan zafi ta wanke flask din kasancewar anjima</p><p>ba'ayi amfani dashi ba.ta tafasa ruwan tazo ta</p><p>bashi,ya ciro wayarshi ya mika mata. "sa min a</p><p>caji naga nepa sun kawo wuta" ummi ta jona</p><p>waya sannan ta ci gaba da girkin dare don tasan</p><p>Alhaji bai cika son wani abu da dare ba sabanin</p><p>tuwo. Ta gama wanka sannan tayi sallar</p><p>magariba tana kwance gadon tsohuwa tana</p><p>tunanin abba. Tsohuwa nata lazimi in tayi</p><p>magariba bata tashi sai tayi isha sannan taci</p><p>abinci.ummi ta tuna wayar da yaya abba ya bata</p><p>ajiya. Da sauri ta tashi tare da cewa "ke tsohuwar</p><p>nan anzo tayaki hira kin share mutane" ta mike</p><p>ta nufi daki ta dauko wayar ta kunna HEHE KIN</p><p>MANTA YAYA ABBA KENAN?" Sakwanni ne sukai</p><p>ta go slown shigowa sannan sai kira tashin farko</p><p>data daga wayar muryar mace taji, ta ce "dawa</p><p>nake magana" wadda ta kira ta ce "ina mai</p><p>wayar?" ummi tace "dq matarshi kike magana,ke</p><p>din wacece?" waccac n ta ce "in yazo ki</p><p>tambayeshi? yasan me lambar." nan da nan sai</p><p>ummi ta samu kanta yana juyawa,tayi tsakita</p><p>kashe.ta shiga duba sakonnin da yawansu na</p><p>mata ne masu sonshi,daidaikune na maza masu</p><p>nuna yabawar aikinsa.hankalin ummi ya tashi</p><p>ganin yadda mata suke farautar abinda take</p><p>tsananin so.ta kashe wayar cike da nadamar</p><p>kunnata Hankalin Ummi ta samu kanta yana</p><p>juyawa,tayi tsaki ta kashe.Ta shiga duba</p><p>sakonnin da yawansu na mata ne ma su</p><p>sonshi,dai-daiku ne na maza ma su nuna</p><p>yabawar aikinsu. Hankalin Ummi ya tashi,ganin</p><p>yadda mata suke farauta abnda take tsananin So.</p><p>Ta kashe wayar cike fa nadamar kunnata. Sintiri</p><p>ta dinga yi a tsakar dakin,Sallamarshi ce ta, katse</p><p>ta.Ta amsa ciki,sannan ta zauna ba tare da ta</p><p>kalle shi ba. Ya ce,Bani wayata da abinci 'yan</p><p>asibiti. Ta mike ta dauko masa abncin,sannan ta</p><p>bashi wayar.sai dai tana yin komai ne fuskarta</p><p>daure. Ya ce,Lafiya na ganki wani iri?ta dago ido</p><p>ta kalle shi,ta sake tsuke fuska. lfy lau.Ya ce,shi</p><p>kenan na tafi Sam bata tanka ba. Yana fita ta</p><p>mike a kujera,so takeyi a lkcn ta samu makanta</p><p>mafita,shin ko dai ta tare shi ne ta fada masa?</p><p>wata zuciyar ta ce,In ko ya dinga kwallo da ke</p><p>sai kin rasa mai cetonki. Ta tashi tare da</p><p>cewa,Bari kawai in fada ma Tsohuwa.Zuciyarta ta</p><p>sake rayawa.Tsohuwa fa ba zata yarda ba, domin</p><p>kullum tana bada shaidar tsanar da Ya Abba ya</p><p>mata,ta koma ta zauna. Sai ta samu kanta da</p><p>fashewa d kuka,tana fadin wannan wace irin fitina</p><p>ce ta same ni?me yasa zcyt ke son tozarta ni?</p><p>Me yasa zata so wanda ya tsane ta?Ta mike ta</p><p>shige uwar daka. Gado ta hau tana son ta lallashi</p><p>zcyrta,dn ta daina son Ya Abba. Shi kuma yana</p><p>tafe a mashin zcyrshi na mitar bata gaji da ganin</p><p>Ummi ba,yadda take ta kai kawo ya ke gani a</p><p>idonshi. Lkcn da ya kai musu abnci me jego ta</p><p>gyare,dama ta zubar d jini ne shi yasa suka ki</p><p>sallamarta,sukace sai da Safe. Ya samu kannanta</p><p>sun zo da wata 'yar Babnsu.Sun gaisa an yi 'yar</p><p>hira sannan suka ta fi lkcn ya dauki 'yar ya yi</p><p>mata kallon sosai. Ya dubi Umma kin san</p><p>yarinyar nan da wa take min kama?Ta ce,A'a.</p><p>Bishira ta tsare shi da ido,ya ce lkcn d Ummi na</p><p>karamarta sak wannan. Umma ta ce,Kana nufun</p><p>d Ummi take kama?ya ce,"Eh,Bishira ba kunya ta</p><p>ce,Allah ya kyauta ni 'yata bata kama da wata</p><p>can wai ummi. Umma tayi saurin cewa,Dama</p><p>zolayarki yake ba suyi kama ba.Shi kuma ya</p><p>kalleta.Ko ki so ko kada ki so yarinyar nan sak</p><p>take kama d Ummi. Ya mika ma Umma ita,yana</p><p>ci gaba da fadin Maman Walid kina bani</p><p>mmki,kina zaton zan ki raba 'ya'yanku d Ummi?</p><p>Ya girgiza kai"Sun hadu hr abada ,domin in kin</p><p>tsaga jikin 'ya'yanki dole za ki ga jinin Ummi. to</p><p>ya ya ma ki ke tsammanin zan so wanda ba ya</p><p>son Ummi? Ta ce, "Oho! Ni ba ka sona kenan?To</p><p>in da na gode ma Allah dk dyniya ta san cewa</p><p>Ummi bata kaunarka.dk da kana wanta.Ba ita ba</p><p>ce silar kariyarka?ko an kashe ka ma bata da</p><p>asara. Umma ta ce,'Abba jeka ban son in kuma</p><p>jin bakinka in na isa. / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 2 part 7</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 2 part 7</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:16</p><p>Ta samu an saka ranar auren fati da saurayinta</p><p>Fahat,nan fa Alhj ya ce dama ke ni ke jira uwata</p><p>ki dawo. A masu sonki ki fito da daya a hada</p><p>auranku da 'yar uwarki Fati. Hankalin Ummi ya yi</p><p>matukar tashi,ranar kasacin abnci tayi. Da suka</p><p>zauna da Umma a daran ta ce Umma baki fada</p><p>ma Alhj bani da tsayayyen saurayi ba?Umma ta</p><p>kalleta,ba shi yasa na ce Kitsada ba,amma ba kya</p><p>son fita. Duk kin bi kin kori masu sonki Abba na</p><p>daure miki gindi,kin san dai Alhj ba yarda zai yi ki</p><p>wani ci gaba ba,gara ma kin yi kokarin fidda miji</p><p>kafin lkcn da ya dibar miki,in ki ba haka ba ya</p><p>daki da mai rabo. Ummi tasa kuka ranar,kwana</p><p>tayi tunani hr ta yanke shawarar zata fada ma</p><p>Alhj Ya Abba take so. Da safen taje hr dakin Alhjn</p><p>ta gaishe shi,ya ce uwata naga kamar bakinki da</p><p>magana ko?Ta dube shi "Eh,a'a ba komai.Ta</p><p>mike,dakin Tsohuwa ta shiga ta haye gado ta</p><p>soma kuka. Tsohuwa ta dubeta a rude,Takwara</p><p>ke da waye,? Nasan ba zai wuce me sunan</p><p>Malam ba,dn shi ne kadai ke hana ki sukuni. A</p><p>ran Ummi ta ce,shi ne kam,amma ba irin wanda</p><p>ki ka sani ba. Amma a fili sai ta ce,Tsohuwa Alhj</p><p>ne wai in fito da miji,kuma abn da ke damuna ni</p><p>ba wanda na ke so. Tsohuwa ta ce, "Au, shi ne</p><p>abn kuka?To bari kiji bana ba zan goyi bayabki</p><p>ba,dn da ubanki ya ji ta tawa da yanzyn kina da</p><p>diya 2 in da rabo. Amma mai sunan Malam ya ce</p><p>za ki ci gaba da krt,yamzun ko tun da Allah ya</p><p>kawu mu angama wannan kaddararriyar mkrnt ba</p><p>sai aure ba? Ga Bunta nan hr an yi baiko, to rana</p><p>guda za a yi shi in muna cikin masu rai. FUU</p><p>Ummi ta fice,ta shiga dakin Umma tana tunanin</p><p>wa zata fada ma matsalarta?kamar an tsikareta</p><p>ta dauki mayafi zata fice. Umma ta ce, "Zo nan,</p><p>ina za ki? ta ce "Wurin Fati. Tana shiga Bashir</p><p>zai fito . Ya ce Yauwa Ummi ina son magana da</p><p>ke. Ta dawo baya ya fita kofar gida ita ma ta</p><p>fito,suka tsaya ya ce "Ummi gaskiya dama ba</p><p>wani abu ba ne, ni dai na tsinci kaina da sonki.</p><p>Ummi ta dafe kirji da sauri."Sona?" ya ce kwarai</p><p>kuwa, dn haka za ya ki ka gani?ta dube shi,sam</p><p>babu wata alama da ke nuna cewa dan uwan Ya</p><p>Abba ne. Ta girgiza kai "kayi hakuri kawai Ya</p><p>Bashir,wlhy zuciyata ta jima da kamuwa da son</p><p>waninka." ya ce, Me ki ke nufi?Kin fi son bare da</p><p>ni jininku? Ummi ta ce,"Ni dai na fada maka." Ya</p><p>ce, "To kin fada min,ni kuma zan fada wa su</p><p>Alhj." Gabanta ya fadi. Shi kuma ya yi tafiyarsa, .</p><p>Sabon tashin hankali kenan. Sai damuwa ta</p><p>lunku,bata ta6a marmarin zamn mkrntr kwana ba</p><p>sai ranar. Ta rasa me zata yi taji dadi,gida ta</p><p>koma cike da nadamar fitowa,ta zauna a falon</p><p>Umma ta soma kuka. Umman tana dakin mijinta</p><p>ya yi karin kummali. Sai da ya fita sannan Umma</p><p>ta maido hankalnta ga lamuran gidan, kan kujera</p><p>ta samu Ummi ta nata rera kuka. Umma ta ce</p><p>"Ke Ummi lafiyanki? Abun ya soma zama iya</p><p>shege,daga cewa ki fito da miji sai ki tsira kuka?</p><p>To ina ganin kwadantaki zamu yi muci. Ummi ta</p><p>ce, "Ni fa ba kukan da nike yi ba kenan,ni fa Ya</p><p>Bashir ne fa. Umma ta ce Bashir me,? kiranki aka</p><p>yi? Gara daya da ke ki. ta ce ba fa dukana ya yi</p><p>ba wai cewa yai wai fa yana sona. Tab,Allah ya</p><p>tsare ni. Umma dn Allah bana sonshi,gaban</p><p>Umma jikinta a mace ta ce "Tabdi,ai ko in Alhj ya</p><p>ji wannan zancan ta zauna. Ummi ta sake</p><p>firgicewa, cikin kuka ta ce Da na shiga 3 Umma,</p><p>ya ya zan yi ne don Allah?Umma ta ce,"Mafita</p><p>daya ce ki fidda wani kafin zancan yaje wurin</p><p>Alhj. Yinin ranar Ummi ta rasa mafita Addu'arta</p><p>daya,Allah ya turo mata ko ma waye a daran yau</p><p>ta ce ya turo iyayenshi. Wayar Umma tana</p><p>hannunta,ta rubuta text ta goge yafi sau 20 da</p><p>niyyar ta tura ma Ya Abba cewa tana</p><p>sonshi,amma da ta tuno da irin dukan da zai zo</p><p>gidan ya yi mata in ya karanta sai ta share. Ita</p><p>dai ta san shi kadai take so. Tayi Sallar Istihara</p><p>kusan sau 3,amma hr yau zcyrta na nan makale</p><p>da son Ya Abba. Don bayan Isha'i kuwa a ka aiki</p><p>kiranta, ai tare da dan aike suka fita. Wani</p><p>saurayi ne wai shi Sahabi,dan unguwar ne Kuma</p><p>sana'ar aca6a yake yi. Na dai manta. Suka gaisa</p><p>ya gabatar da kanshi sannan ya fada mata dalilin</p><p>zuwanshi ba tare da wani nazari ba,ta ce ta</p><p>amnice. suka yi sallama ta dawo gida,umma ta</p><p>tambaye ta wanene?Ta fada mata,sai dai Umma</p><p>bata gane shi ba. Can jimawa Bashir ya aiko</p><p>Kamal kaninsa wai Ummi tazo,ta ce kaje ka ce</p><p>masa ba zan zo ba,ya sake aiko shi cewa in bata</p><p>zo ba shi zai shigo. Umma ta ce mata tashi kije.</p><p>Ummi hr d kuka ta fita,dn a rayuwarta ta tsani</p><p>Bashir,sbd yanda ya raina Umma. Kuma ba ya</p><p>ganin kowa da gashi sannan tana ganin in hr ta</p><p>auri Bashir zai mata tsakani da auren Abba. Tana</p><p>zuwa ta same shi zaune a dakalin kaofar gida,ta</p><p>isa gurishin. Ya Bashir kiran me ka ke min? Ya</p><p>ce,kin sani kema. Ta ce Ya Bashir dn girmn Allah</p><p>ka bar ni ba,Usaina gidan kurma ce buduwarka</p><p>ba? Ya ce Da ba, ya ci gaba da cewa,Ummi ina</p><p>sonki so na hakika nayi mamakin yadda lkc daya</p><p>zcyta ta kamu da sonki,to wai dn Allah ni me</p><p>yasa ba ki sona? ta ce Ya Bashir ina da wanda</p><p>nake so tun farko..........kamar daga sama suka ji</p><p>muryar Abba yana cewa,Kai Bashir me ka ke</p><p>fada? ya ce sonta nake. Abba sai da wayarshi da</p><p>ke hannunshi ta kwace ta fadi don figici,bai bi</p><p>takan wayar ba ya isa gabn Bashir ya ce, In ka</p><p>kuma furta kalmar so ga Ummi sai na maka</p><p>matsiyacin duka,ke kuma hr da fitowa kin zo tadi</p><p>ko? kafin tayi magana ya ce,Bace min daga nan.</p><p>Bashir ya ce,Amma ai ba laifi ba ne don nace ina</p><p>sonta? Abba ya bige mishi baki tare da cewa In ji</p><p>wa ya ce maka ba laifi ba ne?Bashir ya ce,An</p><p>haramta aure tsakaninmu ne? Abba ya cakumo</p><p>wuyan rigarsa Ni ne nan na haramta haka,kuma</p><p>kar in kara jin wannan mgnr. Bashir ya fige ya</p><p>nufi gida yana fadin cewa Yau zan samu Alhj da</p><p>mgnr. Ina ruwanaka da zaka ce ka haramta min</p><p>sonta? . Abba jikinshi hr 6ari yake dn tashin</p><p>hankali, yasan in mgnr taje teburin Alhj to ta kullu</p><p>yanda yake mishi mgnr hada auran Ummi da Fat.</p><p>Har ya saka kafa a zauran gidan su Umma,sai</p><p>kuma ya fasa ya dawo ya nufi gidan su Bashir</p><p>din,yana saka kafa a zauren gidn Alhj Krm na</p><p>fitowa. Don haka sai yaja baya,Alhj ya fito ya</p><p>ce,A'a Abba ne? Abba ya ce "Eh ni ne. Ya gaida</p><p>Mahaifin nasa,sannan Alhj ya tambaye shi cewa</p><p>Babn naka yana gida? Gaban Abba ya yi</p><p>mummunan faduwa,ko dai Bashir ya fada wa</p><p>mahaifinsu ne? Alhjn ya ce ko ba ka ji ba?Abba</p><p>ya ce "Eh a'a ban riga na shiga gidan ba. Alhjn</p><p>ya ce To bari in ganshi. Nan jikin Abba ya jike da</p><p>zufa. Da azama ya shiga gidan. Mahaifiyarsu tana</p><p>alwala ya ce Umma ina Bashir? ta dube shi</p><p>Lafiya ba ko sallama? ya ce Nayi ba ki ji ba ne?</p><p>ta amsa sannan ta ce lfy ka ke nemanshi? ya ce</p><p>lfy lau. ta ce Yana daki,shima na ganshi ya shigo</p><p>a fusace. Abba ya nufi dakin. Bashir na zaune kan</p><p>katifar idonshi na kasa yana girgiza kafarshi ta</p><p>dama,Abba ya shiga ya ce,Bashir nazo ne in sake</p><p>gargadinka a kan Ummi,sai dai naga hr kayi</p><p>kuskuren fada ma Alhj krm ko,? Bashir ya mike</p><p>ya daga sauti Ban fada mishi ba,amma ina da</p><p>niyya. Ina sonta babu wanda kuma ya isa ya</p><p>hana ni sonta. Abba ya kashe masa fuska da</p><p>mari. Sai suka ji muryar Mahaifiyar tana cewa,</p><p>Kara mishi Abba,ka cika dana. Ta shigo dakin hr</p><p>gabn Bashir ta ce, Ni za ka tozarta? kayi kuskure.</p><p>Ai da in ga ranar aurenka da Ummi gara naga</p><p>gawarka kwance yafi min sauki. Abba da Bashir</p><p>suka dubeta a rude. Ta ci gaba da cewa Bashir</p><p>kai ma kasan ba zai ta6a sa6uwa ba ne in hada</p><p>jini da Suwaiba,kafi kowa sanin kin da nike</p><p>mata,zan iya daukar ranta ba don tsoron hukuma</p><p>ba. Kuma hr dny ta nade ba zan ta6a kaunarta</p><p>ba,kai ko fatan alheri ba zan ta6a mata ba. Ta</p><p>kalli Abba, Baka ta6a faranta min rai ba irin</p><p>yau,dama nasan cewa dole wata rana ka bayyana</p><p>dana in dai kai jinina ne,na gode Allah da yasa ka</p><p>zama mai kishina Kuma ka wanke dukkan</p><p>laifukan da ka min a baya da ka nusar da ni</p><p>Bashir na shirin jefa rayuwata a cikin garari,da ba</p><p>ka mishi mgn ba yaushe zan san yana shirin jefa</p><p>ni cikin bala'i. . Abn da Umma bata sani ba shi</p><p>ne,tuni Abba ya yi mutuwar tsaye,hnklshi ya</p><p>ninka na Bashir tashi,dn haka Bashir ya riga shi</p><p>fita daga dakin. Da kyar Abba ya dago ido ya kalli</p><p>Umma,ta ce Daina damun kanka shi ma din ko</p><p>ba don Allah ba zai dawo hanya,duku-dukayau</p><p>sati guda fa kenan da naje kauye na saida 'yar</p><p>Akuyata guda daya sannan na bada kaji 2 ga</p><p>Bokan kuka sbd a min akin da Ummi ba zata</p><p>samu miji ba. Sai kuma a ce ko satin bai rufe ba</p><p>dana na cikina ya zo ya ce yana sonta? Da sauri</p><p>Abba ya dafa kirji Umma Boka! Boka ki ka ce</p><p>Umma? Inna lillahi wa'inna ilaihin raji'un,Umma</p><p>kin san cewa zuwa gurin Boka shirka ne ga</p><p>Allah? kin san duk wanda ya mutu a shirka Allah</p><p>ya yi alkawarin kona shi a wuta?Umma kina cikin</p><p>hadari............ta kaste shi. Kai Abba!Ni ce nake</p><p>cikin hadari?Ni ce Allah zai kona a wuta? ya ce,</p><p>umma bana nufin haka, ina fada miki ne ki kiyaye</p><p>da zuwa gurin Bokaye makaryata,macuta 6arayin</p><p>Imanin Jama'a. Na ranste miki da girmn Allah</p><p>umma Bokaye 'yan wuta ne,matsawar ba su tuba</p><p>ba. Ta ce, Kai ni rufe min baki,da za ka ce karya</p><p>ne sau nawa suna min asirn kuma yana ci. Ba</p><p>gashi nan da ya min na kada Ummi ta riga Fati</p><p>samun miji baga Fatin ta riga samun ba? ummi</p><p>kuma ba ta d masoya. Abba ya ce, Umma kin ga</p><p>karya ko? wa ya fada miki Ummi bata d masoya?</p><p>ta ce, To me yasa ba wanda ya tsaya? Ya ce, Ni</p><p>dai Umma ki bar zancan nan a wurina, Bashie zai</p><p>bar Ummi ko yana so ko baya so,dn haka na</p><p>hada ki d girmn Allah kada ki koma gidan</p><p>mishieikin Bokan nan. Ta ce, Ba zan koma ba in</p><p>hr zaka raba Bashir da alakakai din yarnyar nan.</p><p>Ya ce Na miki Alkawari. ta ce, Shikenan. Ya fice</p><p>jiki babu karfi.URFIN CIKI book 2 part 8</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 2 part 8</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:18</p><p>Kasa shiga gidan su Umma ya yi,haka nan ya</p><p>manta sam da batun motar da yazo da ita a</p><p>kofar gidan Umma. Ko Bishira bata san cewa ya</p><p>shigo gidan ba,tana can jarabar kallonta na</p><p>tsiya,ya rufe gidan ya nufi dakinshi. Ranar mu2m</p><p>5 bacci sai dai 6arawo,Umman Bashir kwana tayi</p><p>saka da mugun zare. Umman Abban ma juyi</p><p>kurum take yi hr Alhj ya gaji ya ce,Yau dai sai</p><p>juyi ki ke yi. ta ce Na kasa bacci Alhj. Ya ce,</p><p>Tashi to kiyo alwala kizo ki kama sallah,in kina</p><p>da damuwa ne sai ki fada ma Allah. Umma bata</p><p>tsaya ba,ta tashi. shi ko Abba wani matsanancin</p><p>ciwon kai ne ya hana shi sallah. Ya dai yi</p><p>nasarar yin alwala da ya shiga daki sai jiri. Dole</p><p>ya kwanta rigingine tare da dafe kanshi da</p><p>hannuwa guda 2,sunan Allah yake ta kira dan</p><p>neman dauki. Ita ko Ummi dirshan ta zauna tana</p><p>kuka,hr sai da hawayenta suka kafe,idanunta</p><p>suka shiga zafi,kanta ya soma sarawa gefe daya.</p><p>Ita ma ringingine ta kwanta tare da lumshe</p><p>ido,Istigfari kurum take yi tare da hailala,shi ko</p><p>Bashir mafarkai ne suka hana shi bacci,dk</p><p>mafarkan na Ummi ne. Da safe da matsannancin</p><p>zazzabi ya farka,dn haka bai iya zuwa Masallaci</p><p>ba,da kyar ya yi alwala.yana idar da sallah ya</p><p>kundundune cikin bargo. Matsanancin ciwon kan</p><p>da Ummi ta tashi dashi ya firgita 'yan</p><p>gidan,Musamman Umma wadda ta same ta</p><p>kwance a tsakar daki da safe. Ganin fuskarta a</p><p>kumbure ya tsorata Umma,hr sai da ta kira</p><p>Alhj.Nan fa Alhj ya dauko wayarshi ya shiga kiran</p><p>Abba,kan cewa yazo ya kaita asibiti. Sai dai tayi</p><p>ringing ya kai sau 10 amma ba a daga ba. Alhj ya</p><p>ce Ina yaron nan ya shiga ne?kuma ga motarshu</p><p>a kofar gidan nan,na ganta da asubahi da na fita</p><p>Masallaci. Umma ta ce,Tao Allah yasa dai lfy.</p><p>Har karfe 8 Alhj na neman layin Abba shiru ba a</p><p>dauka ba,ga Ummi rike da kai tana ta salati</p><p>Umma ta ce,Alhj ko Bashir za ka sa ya duba shi?</p><p>Alhj ya koma daki ya dauki hula ya nufi gidan</p><p>Abba. Gidan a kulle ya same shi,dn haka ya dinga</p><p>bugawa.Abba na jiyowa amma ba zai iya tashi</p><p>ba,haka dk ringing din da wayarshi ke yi yana ji</p><p>ya kasa tashi ne. cikin bacci Bishira taji bugun</p><p>gida ya yi yawa,ta tashi ta bude. Da Alhj suka yi</p><p>ido 2,ya ce lfy ba ku tashi ba? Ta ce Mun tashi.</p><p>ya ce Ina maigidan naki? ta ce Ina ga ya fita,bari</p><p>in duba. Ta juya ta nufi ciki. Alhj ya cika da</p><p>mmk,ya za a ce wai mace bata san fitar mijinta</p><p>ba? Anya wannan matar tasan darajan mijin?</p><p>Tunaninshi ya katse lkcn da ta dawo tana cewa</p><p>Alhj yana kwance ba shi da lfy. Alhj ya bita yana</p><p>cewa Ba shi da lfy,amma ke ba ki sani ba?Wanna</p><p>wane irin zama ku ke yi ace kina matarsa amma</p><p>ba ki san cewa ya tashi ba lfy ba? Bishira ta ce</p><p>To ai shi ne bai kira ni ya fada min ba. Alhj ya ce,</p><p>Allah ya kyauta. ya nufi dakin. Abba na kwance</p><p>ya kundundune cikin bargo sai rawar sanyi yake</p><p>yi. Alhj ya yi Sallama ya shiga dakin ya rusuna ya</p><p>daga daidai fuskarshi ya janye bargon ya ce,</p><p>Abbana ba ka ji dadi ba? Abba ya bude</p><p>ido,idanunshi jajir,ya ce Abba kaina ne tamkar zai</p><p>6alle. Sai zazza6i tun daren jiya. Alhj ya ce,Ikon</p><p>Allah Yau kuma abn da na wayi gari da shi</p><p>kenan? Ummi ma na can kwance da ciwon kan,to</p><p>tashi. Shi yasa nake ta kiranka don ka kaita</p><p>asibiti amma da ka daga ba. Yanzu tashi in za ka</p><p>iya ka kira Ahmada abokinka sai ya kai ku</p><p>asibitin. Abba ya ce To Wayar Ahmada din a</p><p>kashe don haka sai Alhj ya ce "Af, na tuno da</p><p>Bashir,kintsa bari in je muzo naga mator can</p><p>kofar gidanmu ko?Abba ya lulubo makullin motar</p><p>yaba Alhj., Zani kawai Umma ta daura ma</p><p>Ummi,sai ta zura mata hijabi,suka shiga bayan</p><p>mota su 3 da Umma da Alhj,sukaje gidan Abba</p><p>suka dauko shi. Bishira taso zuwa amma suka ce</p><p>ba wuri ta bar shi kawai. Asibitin kudi ne kuma</p><p>likita guda ne ya duba su. Ummi dai hawan jini</p><p>ne don ita a ka fara dubawa. Gado likitan ya</p><p>bata,sannan Abba ya shiga shima likitan ya ce</p><p>jininsa ya hau,amma ba kamar nata ba. Nan ya</p><p>roki likitan cewa kada ya fada ma iyayensu abnda</p><p>ke damunsa,ya rubuta mishi magunguna kawai.</p><p>Likitan ya ce Ba komai. Amma me ya ke</p><p>damunku kai da sister dinka ciwonku iri daya</p><p>kuma ya kama ku a lkc daya? Abba ya ce Ba</p><p>komai lalura ce kawai a ka kaddara ta same su</p><p>lkc daya.Da Abba ya fito sai ya ce ma su Alhj</p><p>Zazza6i ne. sai dai shi kanshi ya ji mmkn</p><p>ciwonsu iri daya. Yana jingine da bango a dakin</p><p>da a ka ba Ummi gado,yayin da Bashir ya tsaya a</p><p>gabn gadon Umma tana zaune a kan kujera. Alhj</p><p>krm d Bbba suka shigo tare da Likitan ya kalli</p><p>Abba Yarona kana bukatar bacci ga. Abba ya ce</p><p>To yanzun zan tafi gida. Ya iso kan Ummi wadda</p><p>a ka daura ma ruwa,ya ce ku barta ta huta bata</p><p>bukatar hayaniya,don haka ku rage daga cikin</p><p>dakin. Alhji ya ce, To mun gode. Suka tafi suka</p><p>bar Umma. A mota Alhj ya ce da Abba,ka fada a</p><p>wurin ainkan? ya ce, Eh abokin aikina ya kira ni</p><p>kuma na fada masa. Alhj ya ce,To shi</p><p>kenan,yanzun sai muje can gidanmu zaka fi</p><p>hutawa... .Yanayin aikinku ne ba ka samun bacci</p><p>ko? eh kurum Abba ya ce,amma shi yasan</p><p>tunanin Ummi ne ya ke hana shi bacci da</p><p>matsalolin da yake hangowa. Yinin ranar yasha</p><p>bacci,sai kusan 4 ya tashi ya yi Sallah,ya ji dadin</p><p>jikinshi. Bishira tana gidan Umman Bashir wai ita</p><p>da tazo jinyar miji,tana bata lbrn wai Abba bai</p><p>fada mata ba shi da lfy ba,ya kira Alhj yazo yana</p><p>ta min surutai wai mijina ya fita ban sani</p><p>ba,meye- meye? Umman Bashir ta ce, Da Allah</p><p>kyale su,don wani sabon iskanci ma wai Bashi ne</p><p>ke son Ummi. Bishira ta mike zumbur tare da</p><p>cewa, Bashir fa ki ka ce Umma? Hu'um,lallai da</p><p>wani abu. Bashi da ya tsani Ummi shi ne zai ce</p><p>yana sonta? Umma ta ce, Sannu 'yar albarja,ashe</p><p>kin fahimta,? Tabbas nasan ke za ki fahimta,to in</p><p>gaya miki Bashir ko yau da safe fa sai da muka yi</p><p>ta dashi. Dubi yadda Bashir ke min biyayya amma</p><p>yau ina fada yana fada. wai hr da ce min shi bai</p><p>ga wani mugun halin Suwaiba da nike fada</p><p>ba,tana min alkairi amma ni kullum ina binta da</p><p>sharri. Kai dai jin wannan zancan ka san ba yin</p><p>Bashir ba ne,don haka na ce masa ba komai</p><p>nasan ba yin ka ba ne. Bishira ta ce,Tabdi,Umma</p><p>sai kin tashi tsaye. Ta ce ke dai bari ai ina cikin</p><p>wani hali shi kanshi miji naki sai na nema masa</p><p>taimako. Don wannan ciwon nashi ban yarda shi</p><p>ba, kuma lkcn daya. Fati ta shigo gidan da</p><p>sallama,ta shiga dakinsu ta canza kaya. Umma</p><p>ta ce,sai ina? ta ce Ya Abba ne ya ce in zo in</p><p>canza kaya zamu je asibiti wurin Ummi. Bishira</p><p>ta mike ya farka ne? Ta ce Eh hr ya yi wanka da</p><p>sallah Umma ta ce Bari in same shi bai gama jin</p><p>sauki ba zai tafi wurin wata can kema banza</p><p>mara kishi kin taho jiki Na 6ari,Fati ta ce,Umma</p><p>don Allah ki daina irin wannan abubuwan,wlh</p><p>Umman su Ummi bata yin haka Bishira ta fita</p><p>tana fadin Ai Ummi yanzun ita ce uwar Fati, don</p><p>bata jin mgnr kowa sai ta Ummi,tunda ta dawo</p><p>mkrnt. Sun samu Tsohuwa ma hr ta shiga</p><p>mota,shi kuma Abba yana jingine a jikin Motar</p><p>yana sanye da shadda (Sky blue) Rigar 'yar 3</p><p>Quarter kanshi da hula. Bishira ta ce,Babn Walid</p><p>hr ka tashi? ya dube ta,sannan ya kai idanunshi</p><p>kan fati Shiga muje. Bishira taja baya Ina ba in</p><p>da za ni. Ya kalleta ke Kuma ke da wa? Wa ya</p><p>fada miki da ke nake? yaja tsaki. Ta iso Ummar</p><p>tasu Abba ka hakura mana da wannan tafiyar. Ta</p><p>ce Naji sauki Umma. Tsohuwa ta ce, Mai sunan</p><p>Malam ka shiga don Allah mu tafi. cikin sauri ya</p><p>fada mota suka wuce. Yana yi wa Umman nuni</p><p>da Hannu wai yana zuwa. Tsohuwa ta</p><p>ce,Kinibibin banza ne da wannan matar taka mai</p><p>sunan Malam kana bukata kara aure,me a ke da</p><p>kazamar mace? Abba ya ce, Tsohuwa sha</p><p>kuruminki zan sake aure,ke ce ma za ki bani, Ta</p><p>ce, Ni a wa zan shiga maka ga . Bishira ta fita</p><p>tana fadin Ai Ummi yanzun ita ce uwar Fati, don</p><p>bata jin mgnr kowa sai ta Ummi,tunda ta dawo</p><p>mkrnt. Sun samu Tsohuwa ma hr ta shiga</p><p>mota,shi kuma Abba yana jingine a jikin Motar</p><p>yana sanye da shadda (Sky blue) Rigar 'yar 3</p><p>Quarter kanshi da hula. Bishira ta ce,Babn Walid</p><p>hr ka tashi? ya dube ta,sannan ya kai idanunshi</p><p>kan fati Shiga muje. Bishira taja baya Ina ba in</p><p>da za ni. Ya kalleta ke Kuma ke da wa? Wa ya</p><p>fada miki da ke nake? yaja tsaki. Ta iso Ummar</p><p>tasu Abba ka hakura mana da wannan tafiyar. Ta</p><p>ce Naji sauki Umma. Tsohuwa ta ce, Mai sunan</p><p>Malam ka shiga don Allah mu tafi. cikin sauri ya</p><p>fada mota suka wuce. Yana yi wa Umman nuni</p><p>da Hannu wai yana zuwa. Tsohuwa ta</p><p>ce,Kinibibin banza ne da wannan matar taka mai</p><p>sunan Malam kana bukata kara aure,me a ke da</p><p>kazamar mace? Abba ya ce, Tsohuwa sha</p><p>kuruminki zan sake aure,ke ce ma za ki bani, Ta</p><p>ce, Ni a wa zan shiga maka gaba a baka ku taru</p><p>kai da matarka ku halakata?Duk da Abba yana</p><p>jin jikinshi gim, sai da ya dar dara,sannan ya ce,</p><p>Sai ka ce ma su yankan kai? Tsohuwa kuma da</p><p>za ki ce na cika zcy yanzun ba ga mata nan ina</p><p>da ita ba tana kawo miki karan ina dukanta ne?</p><p>Tsohuwa ta ce Tabdi,ni yaushe ma wannan</p><p>guzumar matar taka zata zo guna da sunan kawo</p><p>min kara? Ban da ma haka ni bani shi da mara</p><p>kunya. Ya ce, sai Ummi ko? koda yake ita ai</p><p>takwararki ce shi yasa lkcn da tayi tata rashin</p><p>kunya ta zama 'yar lelanki. Tsohuwa ta ce ai</p><p>wannan ba kuciya ba ce? Yanzun ko kai ba ka fi</p><p>ta hankali ba.Abba da fati suka sa dry. suna isa</p><p>dakin suka samu Umma suna waya da Alhj,Ummi</p><p>kowa hr lkcn bacci take yi. Abba ya jingina da</p><p>bango yayin da Tsohuwa da Fati suka je suka</p><p>tsaya a gabn gadon. Sunyi Sallama da Alhj shi</p><p>ma ya kira ne ya ji ko Ummi ta farka. Ta ce</p><p>masa ba ta farka ba,kuma Likitan ya ce an fi son</p><p>tayi baccin. Nan suka gaisa tare da tambayar mai</p><p>jiki,Abba kallon Ummi yake,yau daya duk ta fyade</p><p>kmr ta yi sati,sonta da tsananin kaunarta ne</p><p>suka sake mamaye ko'ina na jikinshi. Ya kalli</p><p>Umma wadda ke tambayar nashi jikin, ya ce da</p><p>sauki. Sannan ya kalli Ummi tare da cewa Umma</p><p>wai dame Ummi ta fara? Umma ta ce kamar ya</p><p>ya? Ya ce mmkn ciwon Ummi nake,wai hawan</p><p>jini?Dama can bata da lfy ne? Tsohuwa ta amshe</p><p>da cewa, ko kai ai kasa mata hawan jini,irin</p><p>tsanar da ka mata Mai sunan Malam ai ta isa.</p><p>Abba ya ce Don Allah Tsohuwa ki daina mgnr</p><p>nan. Ya dubi Umma yana me kara maimaita</p><p>tambayarshi. Ta ce ko kusa ai kasan Ummi bata</p><p>cika laulayi ba ma,lalura ce dai yanzun bata ga</p><p>babba ba ta ga yaro,amma mafari daga yi mata</p><p>zancen aure shi kenan take ta kuka. Abba ya ce</p><p>to don Allah Umma ku barta da zancen nan,ina</p><p>krtn take so tayi kayanta,don gudun hawan jinin</p><p>nan kada yakw tashi akai-akai. Tsohuwa ta ce</p><p>Don kawai kada jinita ya hau sai a zura mata ido</p><p>kada tayi aure?ai ko lallai sai dai kada jininta ya</p><p>sauka. in ya hau,aure ya haifeta dole tayi shi,in a</p><p>kasarmu ce ta Zamfara wane ita. . Abba ya ce</p><p>Muje in kai ki gidan Tsohuwa. Ta ce ban tafiya,</p><p>sai naga dama Umma da fati suna ta musu dry.</p><p>Nan dai Abba ya fita yaje wurin likitan ya amshi</p><p>takardn maganin,dn da farko bai rubuta ba</p><p>magaungunan ba. Kwanan Ummi 3 a asibiti a ka</p><p>sallem ta. Abba ya kwashe su zuwa gida.</p><p>Saurayinta Sahabi zuwanshi 2, kuma sun je da</p><p>mahaifiyarshi. sai lkcn ne ma ta mishi kallon</p><p>tsaff,sam ita ba sonshi take yi ba,sai dai gara shi</p><p>da Bashir. Kuma ta lura Bashir din da gaske yake</p><p>yi. Domin kullum zai zo safe da yamma,haka nan</p><p>yakan dan tsaya hr yafi Abba wanda ke zuwa sau</p><p>daya hr tana cewa ina ma yadda Bashir ke nuna</p><p>tausayinshi a gare ta Abba ne. An shuri sati 2 da</p><p>sallamo ta kuma ta warke sarai,sai dai fa hr</p><p>yanzun Alhj yana nan kan bakanshi,ganin Bashir</p><p>na son takura mata sai ta daina fita. Abba ya</p><p>kira Basshir shagonshi wani yammaci,ya sake</p><p>fada masa ya rabu da Ummi sai dai yau da</p><p>lallashi yazo masa,. Ya ce Bashir ka ga</p><p>mahaifiyarmu bata sonka da ummi,dn haka ka</p><p>hkr ka nemi wata,na maka alwashin kashe ko</p><p>nawa ne dn yin hakan zai faranta ran Umma.</p><p>Bashir ya yi 'yar dry,sannan ya mike tsaye Ya</p><p>Abba kenan! kana tsammanin ni wawa ne?nasan</p><p>ba don Umma ka ke fafutukar in bar Ummi ba</p><p>kana yi ne don kana sonta. Gaban Abba ya</p><p>fadi,cikin saurin baki Abba ya ce,In ji wa ya fada</p><p>maka? Allah ya kiyaye. kai ka san Ummi kanwa</p><p>na dauke ta. Bashir ya kakki cikin idon</p><p>Abba,sannan ya ce,"Haba Malam,fadan da ka ke</p><p>da kalaman da ka ke furtawa suna nuna kishinka</p><p>ne karara. Dubi cikin idanunka,kishinUmmi ka ke</p><p>yi. don haka sai ka hkr ka bar min ita,domin ka</p><p>san ba wanda zai fi girgiza Umma tsakanina da</p><p>kai irin ka. Ya nuna Abba da yatsa, Za tafi bakin</p><p>ciki ka zama mijin Ummi fiye da ni. Abba ya daga</p><p>hannu ya falla mishi mari Bashir ya dafe wurin</p><p>sannan ya kalli sau 'yan shagon wadanda marin</p><p>ya janyo hankalinsu. Don farko ba su san abn da</p><p>a ke tattaunawa ba.Bashir ya ce, ka mare ni?</p><p>Abba ya ce, Zan kara maka,ko za ka rama ne?</p><p>Bashir ya ce, Ba zan rama ba,amma zan fada ma</p><p>su Alhj yau dinnan ina son Ummi. ya fita fuu.</p><p>Abba ya zauna ya rike kai yana huci. shi kam</p><p>Bashir ya kudurci niyyar fada wa iyayensu yau</p><p>dinnan. Abba ya kira wayar Umma ta daga suka</p><p>gaisa lkcn karfe 6 na yamma ya ce, Ummi fa? ta</p><p>ce Gata can kwance. Ya ce Ba dai jikin ba? ta ce</p><p>A" aikin karance-karancenta take. Ya ce, Ba ni ita</p><p>Umma. Umma ta kwala ma Ummi kira,ta mika</p><p>mata wayar tare da cewa "Yanyanki ne ke son</p><p>magana da ke. Yau ce rana ta farko da suka yi</p><p>waya a matsayin shi na Abba,ita kuma Ummi, in</p><p>an debe lkcn da suka yi waya a matsayin shi na</p><p>Abba ita kuma Suhailat. Tayi sallama cikin sanyi</p><p>murya can kasan makoshinta ya amsa tare da</p><p>runtse ido sakamakon tsigar jikinshi da ta tashi.</p><p>Ya ce "Ummi ta ce Na'am yaya. Ya ce "Kina son</p><p>Bashir? ta raunana murya. Yaya am sorry to say</p><p>bana son shin gsky. Ya ce To yau kam zai sanar</p><p>da su Alhj cewa yana sonki,in kina san kida</p><p>wanda ki ke so to ki gabatar da shi kafin shi ya</p><p>rigaki. Takaici ya kama ta, kamar ta ce, Ni kai na</p><p>ke so.......ya ce kina jina? ta ce,To Ya ce, kin san</p><p>in su Alhj suka ji ba ki da mafita,Ummi ta ce To</p><p>ni fa bani da wanda nake so shi ne ban san</p><p>yadda zan yi ba. Ya ce, shi kenan matsalarki ce.,</p><p>ya kashe wayar. Ummi tayi shiru tana tunanin</p><p>mafita,ko dai ta hkr ne ta aure Bashir din? kai a'a</p><p>to kuma gashi wanda take so ya ce matsalarta</p><p>ce. Can dai ta yanke yadda zata yi,don haka ta</p><p>kosa Alhj ya dawo. Tun kafin suje wurin cin abnci</p><p>ta same su a dakinshi su da Umma,ya yii wanka</p><p>yana kokarin fita sallar magriba. Ta ce Alhj dama</p><p>wanda ya ke zuwa gurina ne ya ce in fada muku</p><p>iyayenshi za su zo. Dadi ya kashe Alhj ya ce To</p><p>to dan nan unguwar ne? ta ce Eh ya ce To</p><p>madallah dama wannan yaron na sabon titi din</p><p>nan Suwaiba wanda kwanaki nake fada miki</p><p>nasan ubansa a kasuwarmu ya ke? Ta ce Naji</p><p>wanda ya soma zuwa wurin Ummi? ya ce Shifa,</p><p>Uban danai masa zancen naga dansa wurin 'yata</p><p>sai cewa ya yi auran gida za su yi masa,ko ni na</p><p>so hadin nan sai dai Allah bai so ba. Ya kalli</p><p>Ummi Yaushe za su zo? ta ce Ya dai ce in</p><p>tambaya ne. Alhj ya ce To Allah ya kawo su. Da</p><p>dare Sahabi yazo ta ce Sahabi an ce in maka</p><p>mgn ka turo ya ce Alhamdulillah, dama ina son in</p><p>miki mgn sai ina tsoron kada ki ce ya yi wuri don</p><p>haka gabe zan turo. Bashir yazo ya zauna gabn</p><p>Alhj suna cin abnci ya gaishe su. Suka amsa ya</p><p>yi shiru yana tunanin ta ina zai fara? Alhj Babba</p><p>ya ce ya ya Bashir akwai wata matsala ne?Ya ce</p><p>Am dama ina son in ce ni dai ina son Ummi ne.</p><p>Ummi kuma?Alhj karami?Ya ce Eh Alhj Babba ya</p><p>ce Ta amma ya aka yi kayi nauyin baki hr a ka</p><p>ba wani dama? Bashir ya ce Alhj Wanene? Alhj</p><p>karami ya ce Sai ka san shi? koda ba a tambaya</p><p>ba, ba zan ba da goyon baya a baka Ummii ba,</p><p>tashi ka bamu wuri. Abba ya ce, Bashir je ka ci</p><p>gaba da addu'a Allah yasa Ummi ta zam</p><p>rabinka,zan so haka dn na jima ina son zumuncin</p><p>nan. Iyayen Sahabi sun zo kuma an basu hr ma</p><p>an tsaida ranar daya fa ta Fati. Tun daga ranar</p><p>Ummi kullum cikin kuka take wanda iyayenta</p><p>suka kasa gane nufinta. Bashir bai daina cin</p><p>alwashin sai ya auri Ummi ba, dn haka kullum</p><p>cikin aiken kiranta yake. Ban da haka ma ya</p><p>maida hnkl kan sana'arshi tunda ubansa ya mishi</p><p>gorin wa zai ba shi mata ya ki tsayawa sana'a</p><p>nashi ganin in ya rike sana'a r za a ba shi. Abba</p><p>kuwa ya ji ya yi ma gidan wai don ya goge Ummi</p><p>a ranshi. Anya "ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.comN nan zai kai su? .</p><p>Sai mu hadu a littafi na Uku don jin yadda za a</p><p>kare. ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 1</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 1</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:21</p><p>Na Halima Abdullahi K/Mashi 1... Abba ya fito</p><p>cikin suit bakake, yayi kyau matuka hatta</p><p>takalminshi sawu ciki baki ne, tamkar wani black</p><p>America. Igiyar wuyan ta zauna tsam, sai kamshi</p><p>yake. Dakin Bishira ya nufa ya daga labule, ta</p><p>dago ta kalle shi yayi matukar birgeta. Tana</p><p>alfahari da shi matsayin mijinta, ya ce "Kin</p><p>shirya?" ta ce,, "Zuwa ina?' Ya ce, "A'a, jiya fa na</p><p>sanar da ke ki shirya da wuri zamu je asibiti ki</p><p>gaida Ummi". Ta watso mishi wani kallo uku</p><p>saura kwata, tare da cewa "Ko garin nan ba a</p><p>sanyi ba zan fita gaida wata can Ummi ba bare</p><p>da sanyin nan." Ya ce, "Dalili ta mike tsaye "Ciwo</p><p>bai kai mutuwa ba, da mutuwa ya yi tazo ta min</p><p>gaisuwa?" Takaici ya turnu'ke Abba, da yake</p><p>sarkin dankara magana ne, sai ya ce "To ita ta</p><p>kashe shi da zata miki gaisuwa?" Ta kule da</p><p>bakin ciki ta zabga mishi harara "To ai kasan ni</p><p>na dora mata ciwon, don haka dole in je</p><p>gaisheta." Ahankali yake tukin, kira'ar Ahmed</p><p>Suleiman ce ke tashi wadda ya yi murya biyu</p><p>cikin sanyin murya. Wayarshi d ake gefe ta soma</p><p>ruri. Ya kali fuskar wayar, Hajiya Nina ce, don</p><p>haka ya ci gaba da tukinshi, kusan kira na bakwai</p><p>sannan ya daga. Ta ce, "Lokacinka ne za ka iya</p><p>yin duk yanda kaso, amma kafin kazo hannuna</p><p>wacce shawara ka yanke?" ya ce, "Ta me?" Ta</p><p>ce, "Au, ka manta kenan? To ba damuwa za ka</p><p>zo yau ne ko sai an dauko ka?" 2.... 'Yar dariya</p><p>ta kufce masa, "Ki sa a dauko ni sai ka ce wani</p><p>karamin yaro? In kin ci gaba da bibiyata za kiyi</p><p>nadamar hakan." Ta ce, "Ko kuma kai kayi ba, na</p><p>baka awa goma ka kawo kanka in ko ka 'ki, hum!</p><p>Za a kawo ka." Abba yaja tsaki "Yanda ki ke</p><p>zatona na wuce haka". Ta ce, "Idris Aminu Idris</p><p>raina ya biya da kai, kuma dole sai na cimma</p><p>hakan, jarumtarka din nan ta sake bige ni, kasan</p><p>dalilin da yasa na ce nan da awa goma? In ka</p><p>lissafa zai baka bakwai na yamma. Daidai lokacin</p><p>da ake watso mana labarai ina kwadayin ina tare</p><p>da kai, lokaci guda kuma ina kallonka cikin TV</p><p>kana feso turanci, kasan ina son muryarka ga shi</p><p>ka gwanance da iya tsara turanci, sai ka ce</p><p>yarenka. Kada in cika ka da surutu sai mun hadu</p><p>anjiman". Ta kashe wayarta. Abba yayi kokari ya</p><p>tsaida motar shi a gefen titi a hankali ya furta</p><p>"Allahumma ajir ni fi musibati..." ya kifa kansa a</p><p>jikin sitiyarin motar, yana tunanin wai shin ba za</p><p>ta sauya masa a halin da yake ciki ba? Wata</p><p>zuciyar ta ce in tasan kana cikin wani halin ko? A</p><p>haka ya isa gurin aikinsa, tunda suka shiga dakin</p><p>daukar labarai, abokanshi suka gane yana cikin</p><p>wani hali duk da bai kasance mai yawan magana</p><p>ba, amma yau ba kamar kullum ba. Salis ne ya</p><p>kasa hakuri, don haka bayan an gama daukar</p><p>labarai da kyar sun je su yi sallar Azahar suna</p><p>zaune wata Bafulatana da ke kawo musu fura ta</p><p>kawo. 3..... Dama shi Abba bai cika shan fura da</p><p>rana ba, yafi shanta da dare, don haka siyan</p><p>kurum yake yi. Bayan yaje gida sai yasha, amma</p><p>ranar ya ce mata ta bar shi kawai, ta jiya ma</p><p>tana nan bai sha ba. Da ta tafi Salis ya dube shi,</p><p>"Idris ba ka da lafiya ne?" Ya ce, "A'a me ka</p><p>gani?" Ya ce "Ba yanda ka saba ba, duk kwanakin</p><p>nan na lura kana cikin damuwa". Abba ya dube</p><p>shi amma ai kasan nayi rashin lafiya ko? Salis ya</p><p>ce dakata Idris kada kaga kamar na matsa maka</p><p>sai na ji cikinka, ko kusa ba haka ba ne. Ni</p><p>mutum ne mai saurin karantar duk dan Adam din</p><p>dana zauna kusa da shi na awa daya bare kai da</p><p>na zauna da kai tsawon lokaci, muna kuma ci</p><p>gaba da zama. Idris na fahimci kana da matukar</p><p>'ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com' dalili kenan da yasa ban ta6a</p><p>damuwa da in tambaye ka matsalarka ba.</p><p>Sannan dalilin 'ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.comN' da naga kana da</p><p>shi ne yasa har kwanakin baya na kawo maka</p><p>matsalata da iyalina. Alhamdulillahi ka bani</p><p>shawara kuma nayi amfani da ita, kuma naga ci</p><p>gaba, matsalolina sun ragu". Abba yayi dan</p><p>murmushi. "Wai kana nufin saboda ina da</p><p>'ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com' ne kaga ya dace ka sanar da ni</p><p>sirrinka?" Salis ya ce "Kusan haka ne, don me</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com ya iya hadiye magana, sai dai a ganina</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com wataran zai iya fadawa halaka, ko</p><p>wata gagarumar matsala". Abba ya dube shi,</p><p>"Wace irin halaka? Salis ya ce, "Me ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com sai</p><p>ciwon zuciya ya kama shi yana muku-muku da</p><p>matsalarshi, wani ma har ya mutu da ita ba</p><p>wanda ya sani. Amma in abu na cinka ka samu</p><p>wanda ka yarda da shi mai amana ka fada masa</p><p>zaka ji dan dadi". Abba ya ce, "To kai tunda baka</p><p>da ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com, kenan bai dace ka ji matsalar ba?"</p><p>4....Salis ya tuntsire da dariya, "Ta nan ka 6ullo?</p><p>Ai dama ka sani ba ina son yabon kaina ba ne,</p><p>a'a duk surutuna nasan abinda nake fadi". Abba</p><p>ya ce, "Salis na gode da kulawarka, matsalata ko</p><p>ka ji ta nasan shawarar da za ka bani bata wuce</p><p>ka ce in yi hakuri ba, ni kuma ba wannan ni ke</p><p>son ji ba. Salis ba komai nake yiwa 'ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com'</p><p>ba, yawanci in ina da matsala nakan tunkari</p><p>Ummata ne kuma ta warware min komai. Saboda</p><p>na taso da wannan koyin da ta min, yanda na</p><p>shaku da ita ko su Alhajina ba mu shaku haka</p><p>ba". Salis ya ce, "To me ya hana ka fada mata</p><p>wannan karon?" Abba ya ce, "Ba zan iya ba, sai</p><p>dai in za ka samo min mafita ban da hakuri, to in</p><p>fada maka". Salis ya ce "In sha Allah ba za arasa</p><p>mafita ba". Nan Abba ya bai wa Salis labarinshi</p><p>da Ummi tun farko har zuwa yau. Salis ya</p><p>numfasa, sannan ya ce "Kaga illar 'ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com'</p><p>ko? Ummin ma taka ce amma kana nema ka</p><p>rasata, ai ba mafitar da ta wuce ka samu</p><p>Ummarka ko Alhajinka ka fada musu muradinka".</p><p>Abba ya ce, "Tabbas haka ce mafita, sai dai idan</p><p>na aikata haka abu biyu za su faru, na farko na</p><p>zubar da mutuncin Alhajina, domin babu girma,</p><p>sun ba da 'ya ba tare da wani dalili ba ya ce ya</p><p>fasa. Sannan haramun ne neman aure cikin aure".</p><p>Salis ya ce, "Haka ne, to hakurin kawai zaka yi".</p><p>Abba ya ce "Ai mun yi ban da bada hakuri ko?"</p><p>Salis ya saki dariya, sannan ya ce "To kayi</p><p>addu'a". Abba ya mike tare da fadin "Ka tayani</p><p>da addu'a". Daga nan ya shiga dakin, Filin Don</p><p>Matasa na Hausa, don likkafar shirin tayi gaba</p><p>yanzu har na Hausa yana gabatarwa. Kullum</p><p>sake kar6uwa shirin yake a gurin Jama'a.</p><p>5......UMMI Tana kwance kan doguwar kujera,</p><p>yau kwana hudu kenan bata saka Abba a idonta</p><p>ba. Tamkar Umma ta san abinda ke ranta, sai ta</p><p>tsinkayi Umma na cewa "Yau kwana uku ne ko</p><p>hudu rabon Abba da gidan nan, sai dai ya kira mu</p><p>a waya. Alhaji dai ya ce, yana zuwa gunsa</p><p>kasuwa". Ummi ta ce, "Nima yanzun nake tunanin</p><p>haka". Ta miko ma Ummi wayarta da ke gefenta.</p><p>"Lalubo min shi in ji". Da ta soma /ringing/ sai ta</p><p>mika mata. Ya dauka suka gaisa ta ce "Abba ko</p><p>dai na maka laifi ne?" Ya ce, "Umma me a ka yi?"</p><p>Ta ce, "Tsaf, ka dauke min kafa, wanda kullum</p><p>komai saurinka sai ka biyo". Ya ce, "Ina nan</p><p>zuwa Ummata, kina raina duk inda nabi, harkoki</p><p>ne suka taru suka sa ni gaba". Ta ce, "Ni kuma</p><p>sai na ke ganin kamar don ba mu dauki</p><p>shawararka ba ne ta game da karatun Ummi shi</p><p>yasa ka". Ya ce, "Umma ba haka ba ne, zan shigo</p><p>da zarar na dawo". Ta ce. "To". Sam shi batun</p><p>shi yayi ba, sai dai baya son yazo ya ga Ummi</p><p>domin da ya ganta yake neman kwanciyar</p><p>hankalinsa ya rasa na tsawon lokaci. Amma</p><p>yanzun kalmar Salis ta karshe daya fafa masa da</p><p>za su rabu a gurin aiki ita yake tunawa. Dafa shi</p><p>ya yi tare da cewa "Miste Man shawara ta</p><p>karshe, ka nunawa kanwarka kana sonta a fili".</p><p>Ya ce "Tab, wannan shi ne me wahalar ai,</p><p>furtawa Ummi kalmar so. Zubar da kai kenan".</p><p>Ga shi ba sonsa take ba, duk yanda mace ke</p><p>girmamaka da zaran ka ce kana sonta shi kenan</p><p>ka zube a idonta. Musamman in kai ke sonta ita</p><p>ba ta sonka, wata ma har da rashin kunya zata</p><p>tsula maka, a fili ya ce, "Ina, ai ba zan ta6a gigin</p><p>bari ta san ina sonta ba". Daga kasan zuciyarshi</p><p>yaji an ce za ko ka sarata. Sai da ya yi sallar</p><p>Isha'i sannan ya yi wanka ya saka kananan kaya,</p><p>ya fito da nufin gidan su Ummarshi. Bishira ta</p><p>bishi da kallo, daga ganin fita zai yi ta fito da</p><p>saurinta tana cewa "Baban Walid! Baban Walid!!."</p><p>Ya tsaya, ta dube shi "Ina za ka?" Ya ce "Gidan</p><p>su Umma". Ta ce, "Ba wani gidansu Umma, kai</p><p>dai kurum tadi za ka je". 6.... Dariya ta su6uce</p><p>masa, sai da ya dara sannan ya ce "To in ma</p><p>tadin zan je ya za ki yi dani?". Ta ce, "Tab!, ai na</p><p>rantse maka kayi kadan. Kullum kuma ina 'kara</p><p>fada maka kai mijin mace daya ne rak!" Ya ce, "In</p><p>ji ki ko?" ta ce, "Eh." Ya ture ta gefe tare da cewa</p><p>"Da sauki tunda ba fadin Allah ba ne". Yayi</p><p>ficewarsa ya barta nan tana ta masifarta. Kan</p><p>dakalin kofar gidan, Ummi ce zaune da Sahabi</p><p>suna hira, duk da cewa Sahabin shi kadai ke ta</p><p>surutanshi Ummi na can duniyar tunanin abinda</p><p>zuciyarta ke so. Tun daga nesa ta shaki kamshin</p><p>turaransa, zaraf ta mike tsaye. So take ta kalli</p><p>fuskarshi amma ya dauke kanshi daga gare su.</p><p>Haka nan ya share sannun da zuwan da ta ke</p><p>mishi tare da shigewa cikin gida abinsa. Sahabi</p><p>ya ce, "Ya Abba na nan kuwa kwana biyu na rabu</p><p>da ganinshi?" Ta dauke kai sannan ta ce "Zan</p><p>tafi gida". Ya ce, "Haba Ummi, zuwana fa</p><p>kenan?" Ta dube shi. Ji take tamkar ta sheka</p><p>mishi mari, ta ce "To kaina ciwo yake yi, sannan</p><p>kuma ga Ya Abba yazo baya son ina dadewa a</p><p>waje". Ya ce, "To shi kenan sai gobe?" Ta ce,</p><p>"Don Allah kada kazo gobe, ka bari sai jibi". Ya</p><p>ce "Za ki azabtar da ni, ba zan iya kwana biyu</p><p>ban gan ki ba." Maimaikon taji dadin kalmar, sai</p><p>taji takaici ya mamayeta. A ranta ta ce,, "Tunda</p><p>ga gyatumarka ba". Ya ce, "In zo goben don</p><p>Allah?" Cikin muryar tausayi yake maganar, ta ce</p><p>"To shi kenan". Ta soma tafiya, ya dan tako ya</p><p>biyo ta tare da cewa "Sahibata mu kwana lafiya"</p><p>A kagare ta ce "Uhum". Ta samu Abba suna hira</p><p>da Umma, ta tura mishi kular birabisko tana</p><p>lallashinshi ya ci, tayi sallama Umma ce ta amsa.</p><p>Ta shiga idanunta kan Abba, ta zauna a kujerar</p><p>da ke fuskantarshi. Umma ta ce "Har Sahabin ya</p><p>tafi?" Ummi ta ce "Eh". Ta tsura ma Abba ido</p><p>tare da cewa, "Ina kwana Ya Abba?" Umma ta ce</p><p>"Wane irin kwana kuma Ummi da wannan daren?"</p><p>Ta ce, "Au, zan ce ina yini?" Ya amsa tare da</p><p>kallonta, "Lafiya". Ya mayar da dubanshi ga</p><p>Umma. "Umma Matar Ahmad fa ta haihu". Ta ce,</p><p>"Eh, ba jiya ka fada min ba a waya? Me ta samu</p><p>ne?" Ya ce, "Mace ta haifa, gashi ta sha wuya".</p><p>Umma ta ce, "Allah Sarki, to Allah ya raya mata,</p><p>zan je in dubota in mata barka gobe". Ya ce,</p><p>"Allah ya kai mu, ai Ahmad yayi dacen mata ba</p><p>kamar ni ba. A da Umma bana tunanin sake aure,</p><p>amma yanzun ina ganin dole sai nayi mata biyu".</p><p>Umma ta ce, "To ba dai yanzun ba duk nawa ka</p><p>ke kuma yaushe kayi wancan?" Ya ce, "Umma ke</p><p>dai ki min addu'a, ban samu irin macen data dace</p><p>da ni ba". Ta ce, "Ina maka addu'a, Allah ya</p><p>shirya maka matarka." Abba ya ce, "Ko ta shiryu</p><p>sai nayi aure insha Allahu". Ta ce, "Abba ni ko</p><p>gani nake ba ka san wadda za ka aure din ba</p><p>itama da nata kalar halin zata zo, sai su taru su</p><p>ruda ka". Ya kalli Ummi wadda ya lura da kallon</p><p>da ta tsare shi da shi kamar tana son jin abin da</p><p>yake fada ne. Ya maida idanunshi kan Umma.</p><p>"Na yarda da tarbiyar wannan yarinyar da nake</p><p>son aure yanzun, duk da yarinyar bata sona tana</p><p>girmamani". Umma ta ce, "Har ka samu kenan,</p><p>'yar gidan waye? Ummi kuwa tuni makoshinta ya</p><p>bushe, ta zaro idanu tana son ji wa kuma Abba</p><p>ke so? 7:....Ya kalli Ummi ganin yadda ta zaro</p><p>ido ya ce "Ke ni ke fadama wa ki ka zaro ido ki</p><p>ka tsare ni da su?" A hankali ta lumshe idanu</p><p>sannan ta maida kanta kan hannun kujera, ya</p><p>fuskanci Umma "Ba 'yar unguwar nan ba ce",</p><p>matsalar da yarinyar bata sona". Umma ta ce,</p><p>"To ka bar ta mana ka samu mai sonka? Yo in</p><p>haka ne ma ka ce gara matar taka ta gida, don</p><p>ita tana sonka". Yayi shiru zuwa can ya ce</p><p>"Umma in dai zan sameta zan aureta a haka".</p><p>Umma ta ce, "Kayi addu'a, ina ko mamakin mene</p><p>ne ta gani na 'ki a tare dakai Abba?" Ya ce cikin</p><p>'yar dariya "Umma ai ba dole ba ne sai ka birgke</p><p>kowa". Ummi ta mike jiri na dan dibanta ta shige</p><p>ciki. Zance ya dada watsewa, ta furta bayan ta</p><p>fada kan gado, ni ina son shi shi kuma ashe yana</p><p>can ya zarme da son wata. Ranar ta raba dare</p><p>tana kuka daga karshe ta soma ba kanta</p><p>shawarar ta samu Abba ta ce a fili dama</p><p>shisshigi ne irin na zuciyata Ya Abba ba irina</p><p>yake so ba. Shi kuwa zuciyarshi ta soma zargin</p><p>wani abu a kan Ummi, irin yanda ya ga tayi</p><p>kamar hankalinta ya tashi da batunsa. In ko haka</p><p>ne zai fi kowa murna, wata zuciyar ta ce ka sani</p><p>ko tsabar jin gulma ne yasa ta kafa maka ido duk</p><p>da haka yasha alwashin bibiyarta. Sun taso daga</p><p>sallar Juma'a shi da su Ahmad gidan budurwar</p><p>Tukur suka dosa, wayar Salis ta katse shi. Wani</p><p>aiki ne ya taso dole ya koma gurin aiki. Ya sauke</p><p>su a unguwar shi kuma ya nufi gurin aikinshi.</p><p>Karfe biyar ya baro gurin aikin da nufin yada</p><p>zango gidan Ummanshi. 8.... Yasan yau juma'a</p><p>duk yanda aka yi zai samu abinci na musamman,</p><p>don al'adarta ce girkinta na juma'a daban ne,</p><p>tana girmama ranar da abincin da ta san mijinta</p><p>zai yi farin ciki da shi. Haka nan ta kan yi</p><p>kwaliyyar musamman, shi yasa yake kara</p><p>kwadayin aura Ummi, ya san zata dauki wannan</p><p>tarbiyyar. Matasa guda uku a tsaye gefen titi cikin</p><p>fara'a da murna suka tsaida shi, ya saba kusan</p><p>kullum sai irin haka ta faru. Matasa kan tsaida</p><p>shi suna ma su nuna jin dadi da ganinshi, a gaisa</p><p>su wuce. Wasu kuma su amshi lambarshi har da</p><p>ma su son adireshinsa, yanzun ma sai ya tsaya</p><p>zai fito, tsum! Yaga sun bude motar sun shigo.</p><p>Biyu baya daya gaba, ya ba su hannu suka gaisa</p><p>su duka. Na gaban ya ce. "Mai matasa ai muna</p><p>jin dadin taimakon da ka ke mana. Ya kamata a</p><p>baka Sardaunan Matasa". Daya daga baya ya ce</p><p>"Sarkin Matasa gaba daya zamu ba shi, don yana</p><p>kokarin gurin binciko matsalolin matasa". Abba</p><p>ya yi murmushi tare da cewa, "Na Gode". Dayan</p><p>da bai yi magana ba sai ya ce "Amma mai</p><p>Matasa ka san da wannan matsalar?" Abba ya</p><p>waiwaya da nufin jin karin bayani, sai ko ya fesa</p><p>mishi wata farar hoda a fuska. Take nan atishawa</p><p>da tari suka tirnike shi. Ya soma mutsuka</p><p>idanunshi bakinshi na furta "Inna lillahi wa'inna</p><p>ilaihir raji'un". Kafin 'yar sakwanni kanshi yayi</p><p>din, kuma ya fita daga hayyacinsa. Suka tuka</p><p>motar suka tashi dashi. * Farkawa ya yi tamkar</p><p>wanda ya tashi daga bacci, a hankali ya bude ido</p><p>tangaran a kan silin, irin na masu hali. Kwan</p><p>lantarki irin na kasaitattun gidaje ya daki</p><p>hancinshi. Nan take ya shiga tunanin me ya kawo</p><p>shi nan? ba 6ata lokaci ya tuna duk abinda ya</p><p>faru, da sauri ya tashi zaune yana fadin "Inna</p><p>lillahi wa'inna ilaihir raji'un". Ya ci gaba da kallon</p><p>dakin, cikin tangameme ne yana dauke da</p><p>tafkeken gado da sauran saitin shi. Sai kafet din</p><p>tsakar daki da kayan kallo, ga kuma kofofi guda</p><p>biyu. Ya tambayi kanshi da cewa me ya kawo ni</p><p>nan? me matasan suke nema a gurina?" Take</p><p>muryar Hajiya Nina ta fado masa, inda take cewa</p><p>"Za ka zo yau din ne ko sai an dauko ka?" ya</p><p>girgiza kai tare da cewa, Lallai wannan makirar</p><p>matar ce tasa aka mi shi haka". 9... Nan take ya</p><p>soma karanta addu'ar neman tsari. Daya daga</p><p>cikin kofofin ta bude, ya kure idonsa gurin da</p><p>kallo, matar ta shigo sanye cikin doguwar riga</p><p>baka mai ma6allai a gaba. Fara ce kyakkyawa,</p><p>shekarunta suna tsakanin Talatin da takwas zuwa</p><p>arba'in da biyar, domin kyawun nata sun 6oye</p><p>shekarunta, ta baza gashi a kafada. Tsura mata</p><p>ido yayi yana son tuna inda ya ta6a ganinta,</p><p>domin tabbas yasan fuskar. Muryarta ce ta katse</p><p>shi,"Dama nasan zuwa yanzun ka farko, kuma ka</p><p>gama nazarin yanda aka yi kazo nan. Kila ma</p><p>tunda kana da kamannin ma su basira ka hararo</p><p>wadda tasa a ka dauko ka". Ya ce, "Kwarai</p><p>kuwa". Lokacin ne ya tuno inda ya santa, wato</p><p>Hajiya Zabba'u ce matar shaharraran Attajirin nan</p><p>Alhaji Uzairu wadda a ke nuno ta a TV da Jaridu</p><p>tana taimakon talakawa da Marayu. Wadda ake</p><p>labarin tsoron Allahnta da gudun duniyarta,</p><p>wadda ta gina Masallatai da Makarantun Addini</p><p>ma su dama. Ya girgiza kai cikin matukar</p><p>mamaki, ta ce "Ka gane ni kenan?" Ya ce (Cikin</p><p>karfin hali) "Lallai mutum mugun ice. Wannan shi</p><p>ne Allah a baki shaidan a zuci". Ta ce "Kai ne na</p><p>biyu da ka furta wannan kalmar, sai dai bana fata</p><p>ka zama na biyu da ya bakunci inda na farkon ya</p><p>tafi. 10.... Ta tako a hankali ta dunfaro shi, ya</p><p>matsa baya cikin zuciyarshi yana korar shaidan,</p><p>'yar dariya tayi. "Nutsu Idris ko ince Abba. Ba</p><p>fyade zan maka ba". Ya dubeta da sauri, "Eh haka</p><p>nace, in na son hakan zan maka, amma ba</p><p>hakanne burina ba". Ta zauna bakin gadon, "Ka</p><p>zo mu daidaita, in kana tsoron ciwo zan baka</p><p>makari, sai dai ina so ka sani bana dauke da</p><p>wata cuta". Ya ce, "Karya ki ke, kina dauke da</p><p>mummunar cuta". Ta ce "In ka tashi daga dan</p><p>jarida ne, ka koma Likita zan baka dama ka</p><p>gwada ni". "Ya ce ba ki bukatar gwaji don ga</p><p>ciwonki nan a fili ciwon zuciya". Ta ce, "Sam ba</p><p>ni da ciwon a zuciyata, to in ma ina da shi me zai</p><p>dameka tunda ba dauka za ka yi ba". Ya sake ja</p><p>da baya ya ce, "Zuciyarki ta kamu da ciwon zina.</p><p>Ta yi duhu dumdum! har bata iya ganin</p><p>gaskiya...". "Ta daga mishi hannu, "Dakata min,</p><p>ban tambayeka labarin wa'azi ba, domin in shi</p><p>nake son ji ina da kaset-kaset kala-kala zan saka</p><p>na ji". Ta mike zuwa wata durowa ta bude, dauri</p><p>uku ta dauko ta aje gaban madubi na 'yan dari</p><p>biyar-biyar sababbi dal! Ta ce, "Wannan za ka</p><p>sha mai ne sannan kasa kati, kuma in ka kwantar</p><p>da hankalinka zan canja maka mota, zaka je</p><p>Makka. 11.... Sannan idan naga kana bin</p><p>umarnina zaka yi suna a aikin jarida fiye da duk</p><p>wani dan jarida da ka sani a kasar nan. Kai zaka</p><p>taka duk wani matsayi da dan jarida ke takawa".</p><p>ta sake nufoshi da tausasa murya. "In kabi yanda</p><p>nace ba kai ba sake kwana a talauci..." Ya</p><p>katseta da fadin, "In naki fa?" Ta hade rai tare da</p><p>zuba mishi ido, "Shima kallonta yake, sai a</p><p>lokacin ya ga tsufanta ya bayyana. Ta juya mishi</p><p>baya tana 'yar tafiya, sannan ta ce "Am sorry to</p><p>say". Ta juya ta dube shi "Za ka mutu". Gabanshi</p><p>ya fadi, amma sai ya yi karfin hali ya ce "In na</p><p>mutu sai me? Dama can mutuwa zan yi ko ba ki</p><p>kashe ni ba. Kuma ni na san ba zan wuce iyakar</p><p>ajalina ba, murnata daya zaki sauke min nauyin</p><p>zunubaina". Ta matso kusa da shi "Ka san</p><p>matasa nawa ke shiga malamai kawai don su yi</p><p>hulda da ni? In ka dade muna hulda shi ne muyi</p><p>wata biyar, sau daya na rike saurayi har tsawon</p><p>shekara daya don yana da hankali". A zuciyar</p><p>Abba ya ce "In fa na daka ta matar nan zan mutu</p><p>ban auri Ummi ba. Sannan ba Allah a ranta bare</p><p>taji nasiha, yanzu bari yabi ta hikima". Ya ce,</p><p>"Saboda me suke shiga malamai don suyi hulda</p><p>da ke? Sannan daman duniya tasan ki kina</p><p>haka?" Ta ce, "Ko kusa, sun sanni a Hajiya Nina</p><p>sai in mutum ya zo ya ganni, in ya sanni to in bai</p><p>sanni ba duk daya. Sudai burinsu kudin". 12......</p><p>Abba ya ce, "Nikam ba zan iya wannan huldar</p><p>ba". Ta ce, "Kada ka bari taurin kai yaja ka</p><p>nadama irin wadda waninka ya ta6a yi. In kana</p><p>da sha'awa in baka labarinsa don ya zamar maka</p><p>Ishara". Shirun da Abba ya yi shi yasa ta ci gaba,</p><p>domin alamar yana son ji kenan. Da a ce zan fadi</p><p>sunanshi zaka sanshi, wani malami daga cikin</p><p>Malaman garin nan, haka nan yanda na ganka a</p><p>TV kana labarai na kwadaita da kai, shima haka</p><p>na ganshi a TV yana wa'azi kuma zuciyata ta</p><p>yaba. Na neme shi ya zo kuma shi na fada masa</p><p>ni ce Zabba'u ban 6oye masa ba. Sai dai nuna</p><p>masa nai aikin rabon zakka zan ba shi, ma'ana</p><p>kudi ne masu yawa ban san yadda zan fidda</p><p>musu zakka ba. Da jin haka sai ya taho, nan</p><p>dakin na kawo shi, sannan na fito mishi da</p><p>maitata fir! ya shiga jawo min ayoyi na numa</p><p>masa cewa ba zan hakura da abinda zuciyata ke</p><p>so ba. Don ban ta6a 'kin cika mata burinta ba,</p><p>shi kuma ya fir ya ki ya nemi ya gudu na bashi</p><p>guri ya dan ci abinci na nuna masa mishi kuskure</p><p>ne ya ce zai gudu. Don gidan nan duk masu tsaro</p><p>ne har da ma layin gaba daya. Da sauri za a</p><p>kama ka a matsayin dan fashi, sannan in ka yi</p><p>kokarin shigo da jami'an tsaro lamarin to, zaka</p><p>kwana ciki. Domin duk a hannunmu suke, amma</p><p>Ustazun ya ki shan ko ruwan gidan nan, gashi ya</p><p>min shame-shame zai mutu don yunwa. Ba arziki</p><p>na saka aka fita da shi kuma aka kai shi gidan</p><p>karuwai a ka ba su na sakar musu kudi suka sa</p><p>shi a daki. Nasa Malamina ya karasa min shi,</p><p>sannan na sa karuwan suka kira 'yan sanda kan</p><p>cewa ga wani ya zo gurinsu amma kwananshi ya</p><p>kare a nan. To dama iyalanshi suna ta nemanshi</p><p>an sace shi nan fa suka dauke shi, na san yanzu</p><p>ka gane kowane Malami ne tunda labarin ya yadu</p><p>a cikin garin nan da ma wajen shi". CIKI book 3 part 3</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 3</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:24</p><p>Abba ya ce "Lokacin da muke cin abinci tare,</p><p>Umma ta ce, lokacin da ka ke bata dai, Abba shi</p><p>ne ya fara baki abinci a baki. 20..... Watanki</p><p>hudu, da kin hango shi za ki soma daga hannu,</p><p>Abba ya ce Umma na fa goya Ummi a bayana.</p><p>Lah, goyo? In ji Ummi. Umma ta ce, "Goyo sosai</p><p>kuwa, suka sa dariya, Umma ta ce, "Shi yasa in</p><p>naga yanda ku ke rashin shiri a tsakaninku</p><p>yanzun sai in ta mamaki. Don tun ba ki fita a</p><p>tsumma ba Abba ke rainonki, tun ba ki fi wata</p><p>hudu ba, ki ka tantance muryarshi. Haka nan</p><p>sunan shi ne ki ka fara iya fadi a duniya. Abba</p><p>yana goya ki kin sha yi masa fitsari da kashi da</p><p>tumbudi, wanka da wanki duk Abba ya miki</p><p>Ummi. In ko na aike shi ko zai tafi Makaranta to</p><p>sai da wayo da dabara. Ke har an kai lokacin da</p><p>kin yarda in tafi unguwa in bar ki gurin Abba, in</p><p>ya dawo Makaranta tun daga soro zai soma miki</p><p>wakar da yake miki. Ummin Abba da Alhaji,</p><p>Ummin Umma da Tsohuwa, da kin ji haka za ki</p><p>dibi rarrafe ki nufi gurinshi, kuma duk kudin break</p><p>dinsa zai debo miki tsaraba. Umma na bada tarihi</p><p>Ummi ta zuba ma Abba idanu cikin wani irin</p><p>yanayi da ba zata iya tantance shi ba, shi kuwa</p><p>lokacin ne ya dawo mishi, ido ya yi dan murmushi</p><p>tare da cewa "Allah sarki da na tuna ranar da aka</p><p>yaye Ummi, Umma tayi dariya ta ce, "Ranar tare</p><p>kuka kwana kuna min kuka wai in yi hakuri in</p><p>baki nono". Wata sabuwar kauna da so Ummi taji</p><p>ya rufe ta na Abba, har kwalla ta cika mata ido,</p><p>ta ce "To Ya Abba me yasa ka daina sona?" Ya</p><p>ce, "Ummi ban daina sonki ba, kanwata kiriniyarki</p><p>ce ta hada mu fada dama, yanzun kuma kin</p><p>daina ko?" Ta daga kai alamar eh, Umma ta ce</p><p>"Labarin yanda ku ka kaunaci juna mai tsawo ne,</p><p>kusan kullum sai mun yi labarin da Alhaji". Ummi</p><p>ta kalli Umma shi ne ba ku ta6a bani labari ba?</p><p>Ta ce ba gashi kin ji ba, Tsohuwa tayi sallama,</p><p>suka amsa. Ta ce, "Kai me sunan Malam me ya</p><p>faru da kai? Nan ya warware musu komai, suka</p><p>yi ta al'jabi. Umma ta ce "Ni 'yasu, yanzu haka</p><p>mata suka maida aure ba a bakin komai ba?"</p><p>Kuma ka ce matar aure ce, Abba ya ce dama z</p><p>aki san kowa ce ce za ki ji mamaki fiye da haka,</p><p>don dai kurum na rufa mata asiri ne in taci gaba</p><p>to can gabanta hadu da mai tona ta. Su Alhaji</p><p>suka shigo da sallama, nan suma aka ci gaba da</p><p>jajanta batun, Alhaji Babba ya ce, "Babana ina ga</p><p>dai rahoto za mu kai gurin 'yansanda". Abba ya</p><p>ce, "Alhaji tuni manyan shuwagabannin gurin</p><p>aikinmu suka shigo da hukuma, in Allah ya yarda</p><p>dolenta ta bar ni, Alhaji Karami ya ce, "Addu'a dai</p><p>ita ce z aka kara rikewa, Allah ya ja mana gaba".</p><p>Suka ce Amin. 21... Ranar su Alhaji a tsakar gida</p><p>suka ci abinci anata hira, Ummi dai kallonsu take</p><p>yi amma zuciyarta na can duniyar tunanin labarin</p><p>da aka bata. Ashe har yanzu Ya Abba na sonta,</p><p>Allah ya sa haka har yanzun. Sai kusan sha daya</p><p>Alhaji ya matsa wa Abba ya tafi gida. Abba ya ji</p><p>dadin hirar musamman in ya waiwaya idanunshi</p><p>suna kallon Ummi ta mai 'kuri da ido, Umma ta</p><p>ce, "Ka gaida 'yan gidan". Ya ce "Za su ji, har ya</p><p>kai soro Ummi ta ce Alhaji da an raka shi kada a</p><p>kara sace shi fa, duk suka sa dariya". Abba ya</p><p>dawo yana cewa, "Umma kun rage man fetur</p><p>kuwa? Na san yanzu na gidan ya kare tunda ba</p><p>shi da yawa, bana son kuma sai na sake daukar</p><p>galan na fita". Alhaji ya ce, "Na shigo da mai</p><p>dazu duba nan soro na aje shi, Ummi ta sake</p><p>cewa Ya Abba ka ce Alhaji su rakaka gida, yayi</p><p>'yar dariya kada ki damu Ummi, ina yin addu'a</p><p>Allah zai kare ni. Yau kam Ummi ta dade bata ga</p><p>daren da farin ciki ya hanata bacci ba irin yau.</p><p>Haka nan shima Abba zuciyarshi fes Ummi ta</p><p>fahimci dama can santa yake, da alamu ba zai</p><p>sha wuya gurin shawo kanta kuma cikin</p><p>karammin lokaci. 11 HAJIYA NINA Ta kalli</p><p>matashin, sannan ta kalli jaridar hannunshi ta ce,</p><p>"Me ya'ki kai fa ba jakadan azriki ba ne, a duk</p><p>lokacin da na ganka sai gabana ya fadi,</p><p>musamman in kazo min da jarida". Yayi 'yar</p><p>dariya "Hajjaju makatu sallah Makka Sallah</p><p>Madina, ni dai kin san ba ilimin nan gare ni ba, in</p><p>da z aki tsare ni in karanta ban iya ba, ni dan</p><p>sako ne. Muftahu ne mai siyo duk wata jarida da</p><p>ya ga ta shafe ki, ta amsa ta bude cikin azama,</p><p>hoton Abba ta gani gabanta ya fadi, ta ce dan</p><p>jarida shege ne, yaron nan tallatani zai yi? Ta</p><p>soma karanta labarin zufa tana karyo mata, har</p><p>ta gama. Kafa kurum take karkadawa tana</p><p>tunanin abin yi, murna daya tayi da bai tona ma</p><p>duniya cewa ita ce Hajiya Zabba'u ba. Amma duk</p><p>da haka ba zata bar shi ba, koda yake ta ga</p><p>manyan 'yan jarida na kokarin shigowa ciki, ta</p><p>kai hannu ta dauko daya daga cikin wayoyinta ta</p><p>danna kira. 22.... Jim kadan aka daga ta ce,</p><p>"Karamakallu barka da warhaka, ya amsa da</p><p>Ranki ya dade lafiya dai ko?" Ta ce, "Malam ba</p><p>lau ba, kana ji? Ina yaron da nake baka labari</p><p>dan jarida? Ya ce, Naji. Ta ci gaba, Yaron nan</p><p>kaga yanda ya yayata ni a duniya? Sai na koya</p><p>mishi hankali, da ni zai ja?" Malam ya ce, ya ma</p><p>ki ka ce sunanshi? Ta ce Idris, ya ce To zan kira</p><p>ki anjima, kada ki dauki wani mataki tukunna sai</p><p>na gama bincikena duka. Ta ce an gama. Sintiri</p><p>tayi ta yi tsakanin dargajejen falonta zuwa</p><p>barandar shakatawarta, lokacin da taji rurin</p><p>wayarta tayi tsammanin Malamin ne, sai data</p><p>duba taga Aminiyarta ce Haiya Attine. Ta daga da</p><p>cewa, "Hello Attinen bishasha ya aka yi ne? Ta</p><p>ce, Zabba haka kwallon dan iskan yaron nan zai</p><p>miki? Ta ce, Hum! Ke dai bari Aminiyata, yanzun</p><p>nan na gama karantawa a jarida ban ma san</p><p>hukuncin da zan yanke ma yaron nan ba. Attine</p><p>ta ce, sa su Adda su tura shi Jami'ar mi'kakku</p><p>mana. Hajiya Zabba'u ta ce, "Ai kuma na riga na</p><p>kira Teacher ya ce in saurare shi". Attine ta ce,</p><p>"Eh to kin yi dabara ma, kya iya sa Teacher din</p><p>ma ya tura ba tare da an zargi kowa ba". Hajiya</p><p>Zabba ta ce, "Kin san jami'an tsaro suna cikin</p><p>maganar tsundum! Don haka dole in yi taka tsan-</p><p>tsan, guri daya yaron ya yi min kyan kai, da bai</p><p>fada ma duniya Zabba'u ita ce Nina ba." Attine ta</p><p>ce "Eh yayi wannan adalcin, yanzun bari muji ta</p><p>bakin Teacher". 23.... Shikam Malamin duk</p><p>lamura sun kasa masa daidai, sai kusan karfe uku</p><p>saura, sannan ya kira ta da rawar jiki ta dauka.</p><p>Ya ce, Hajiya? Ta ce, Na'am ya ce ki tattara ta</p><p>batun yaron nan ki watsar domin yanda naga</p><p>al'amuran to fa in mun matsa ba zamu kai labari</p><p>ba. Haka nan allura zata tono garma game da</p><p>damuwar malamin nan, sannan asirinki zai tonu a</p><p>gurin maigidanki. Tsaki taja don maigidana</p><p>Malam nasha fada maka ban 'ki ya ji ba, tunda</p><p>shi ne sanadin komai, tafiya kullum daga waccan</p><p>kasa zuwa waccan, kullum cikin bakin yawon</p><p>neman kudi. Sam baya biya mini bukatata ba</p><p>dole in nema ba? Yarana biyu cal a duniya duk</p><p>sun yi aure su ne kawai zan ji kunyar su sani,</p><p>don haka in zai yiwu ka sa Aljanu su tsotse min</p><p>jinin matsiyaci. Malam ya ce, "Ba zai yiwu ba, ina</p><p>ce tun lokacin da ki ka zo min da batunshi kafin</p><p>ma ki sa a dauko miki shi sai d ana fada miki</p><p>yaron yana da kariyar da take kare shi daga</p><p>Ubangiji. Yaron ma'abocin kyautata Sallah ne,</p><p>tare da yin Azkar, yana da makarin da Aljanu ba</p><p>za su iya tunkararshi ba... Dakata Malam, ta</p><p>katse si duk addu'arshi ya kai Malam ne, kuma</p><p>muka ci nasara a kanshi? Ya ce kila shi Malamin</p><p>kwananshi ya kare dama ke ce sila shi ko</p><p>wannan da sauran shan ruwansa. Ta ce, "Kai ne</p><p>sila dai daina jingina min mutuwarsa, ya ce ko</p><p>kin ki dole ki dauki nauyin zunubin mutuwar</p><p>Malam". Yanzun kuma ta wannan sai ki wamu</p><p>wani don ni ba zan matsa lamba a kan al'amarin</p><p>da Aljanu suka nuna tsoronsu ba, tsaki taja</p><p>sannan ta kashe wayar. Har gari ya waye ba ta</p><p>daina tunani ba, haka nan bata yanke matsaya</p><p>ba. Gidan Aminiyarta Attine bishsha ta nufa, sun</p><p>tattauna sosai sannan suka bukaci sukai koken</p><p>ga wasu Malaman. Sai dai guri uku zancan iri</p><p>daya ne, wato ta bar shi kawai, yayin da guri</p><p>biyu suma zancan su iri daya ne, sun ce zata ci</p><p>sa'ar kashe shi amma asirinta zai tonu zata rasa</p><p>ran 'yarta daya kuma zai yiwu tayi zaman Jarun.</p><p>Ta ce, "Wannan akwai shegen yaro, shi yasa da</p><p>na ce zan sa Aljanu su dauko shi ya ce min yana</p><p>da makaminsu? Daga karshe ta ce na bar shi</p><p>mara rabo". Attine ta ce da dai yafi shi yasa tun</p><p>farko in naga wanda zai ja min aji ni ke watsi da</p><p>shi in nemi wani. Kai jama'a sai kace aikin Allah</p><p>menene amfanin zinar ma da har ake shiga</p><p>Bokaye dominta? Allah ka tsare mana Imaninmu,</p><p>amin. 12 24.... Ummi tana zaune zata wanke 'yan</p><p>kayanta na ciki, ta zubo omon cikin ruwa tana</p><p>faman karkadawa, tana 'yar wakar da ke sata</p><p>nishadi. Sam ba ta ji sallamar Abba ba, yana</p><p>jingine yana kallonta, tana fadin, Akwai wanda na</p><p>ke so, amma kunya naso, ya wanke ni da soso</p><p>dan Yayana. Ta tsoma sikyat dinta da fant da</p><p>'yan bireziyoyinta farare ne ta soma cudawa tana</p><p>maimaita wannan baitin wakar, shi kadai ta iya.</p><p>A jikinta taji cewa ana kallonta, ta waiwaya da</p><p>sauri, idanunta tsaf cikin na Abba, sai ta samu</p><p>kanta da sunne fuskarta cikin cinyoyi. Ya ce,</p><p>"Kunyata ki ke ji ne Ummi?" Ta dago da dan</p><p>murmushi, "Sannu da zuwa Yaya Abba". Ya ce,</p><p>"Yauwa dama kin iya waka?" Tsohuwa daga daki</p><p>ta cafke, tun da ta samu wannan wakar sai ka ce</p><p>me hadda, kullum Abba ya isa kofar Tsohuwa</p><p>suka gaisa. Ya dawo kofar Umma yana tabayarta.</p><p>Ummi ta ce, "Taje Hotoro sunan kanwar Umman</p><p>Bashir da ta haihu, ya manta fa matarshi ma ta</p><p>na can, Tsohuwa ta fito tana cewa, ai Ummanku</p><p>ta juri wulakanci. Waccan haihuwar da Zilai</p><p>kanwar Sahura tayi tas a ka zageta a gidan</p><p>sunan, amma yau ta koma. Abba ya ce, "Ummata</p><p>tayi nisa a zumunci, Allah zai bata lada" Tsohuwa</p><p>ta ce, "Ai sai tayi ta yi, in dai shisshigi ne ba</p><p>kwarjini". Ta dubi Ummi, wai wankin me ki ke yi</p><p>ne har yanzun ina nan ina jira ki yanke min</p><p>farce". Ta hango kayan Ummi na daura ta ce,</p><p>"Kai ni wannan zamani naku yana bani mamaki,</p><p>ace 'yammata suna saka rigar mama? Kunya ta</p><p>cika Ummi saboda Abba da ke gurin. 25.... Abba</p><p>ya ce, "Kin ji tsohuwa, lokacinku da namu daya</p><p>ne? Ku lokacinku kai bai waye ba, ta aje 'yar</p><p>kujerarta ta zauna. Tir da wannan wayewar taku</p><p>ta zamani, yarinya ta fadi a gaban iyayenta har</p><p>ta shiga sa tara mama bata kama dakin kanta</p><p>ba? Mu kuwa da wata ma ba sai tayi haihuwa</p><p>goma ba ma ta sa ran mama ba. Abba dariya ta</p><p>ishe shi yayin da Ummi kunya ta hanata shanya</p><p>kayan ta matse ta aje. Abba ya ce, "Yanzun</p><p>Ummi har wani girma tayi, shekara sha takwas</p><p>kurum ce fa, bata ma cika ba. Ta ce "Mu lokacin</p><p>sha biyu sha daya yarinya ta kama dakinta.</p><p>Ummi ta zanua ta soma yanke ma Tsohuwa</p><p>'kumba, tana cewa To dai nima na kusan tafiya in</p><p>huta gorinki. Abba ya matso, "Ummi don Allah in</p><p>tambaye ki mana? Ta tsaya da yanke 'kunbar</p><p>tana kallonshi, ya maimaita tambayar da gira ta</p><p>bashi amsa ya ce kina ko son wannan Sahabin?</p><p>Ta maida kanta ga yankan 'kunbar duk jikinta da</p><p>hannunta suna dan rawa, a zuciyarta ta ce, "Kai</p><p>ne kadai zuciyata ke so, amma a fili sai ta ce,</p><p>Um, ya ce Yaya hausar um?" Tayi kokarin</p><p>saisaita hawayenta, sannan ta ce Eh, jikinshi yayi</p><p>lakwas, Tsohuwa ta ce, "Zancan banza, in bata</p><p>sonshi zaka daga batun auren ne?" Ai ko tana so</p><p>ko bata so tunda ta kawo shi zance ya kare, ka ji</p><p>mai sunan Malam da zancen wofi. Ya ce,</p><p>"Tsohuwa ni fa ba wani abu na ce ba, kin ga ma</p><p>dai bari in tafi abina. Ummi ina Azimi yau, zan zo</p><p>in yi buda baki anjima. Ta ce, "To." Tsohuwa ta</p><p>ce, "Wai kai ba ka da gidan mata ne kullum kana</p><p>la'ke a nan? Tsoron ta ka ke ji ne da zaka kasa</p><p>lankwasata ta yi maka girki?" Ya ce, "Na nan</p><p>nake son ci Ummi kam tana can duniyar tunani</p><p>tana tambayar kanta shi kenan ta rasa Abbanta?</p><p>Son da da yayi mata da ca dama ba na aure ba</p><p>ne, na 'yan uwantaka ne? Kai ko dai ta fito ta ce</p><p>Abba take so, gaskiya ita fa Sahabi ba sonsa</p><p>take ba. Kusan wata daya kenan rabon da ya</p><p>samu biyan bukata daga matarsa, don gaskiya</p><p>baya iya zuwa dakinta saboda kazanta da kuma</p><p>datti da wari da zarni da 'karni ba za su bar shi</p><p>ya samu cikakkiyar biyan bukata ba. In ta zo</p><p>dakinshi ma jikinta tashi yake, a haka yake</p><p>maneji, amma in iskancinta ya motsa har yanga</p><p>take mishi (Mtsw! Allah rabamu da kazaman</p><p>Mata). Shi kuma yana da wani hali, duk yanda ya</p><p>matsu in har ya nuna mata bukatarshi ta 'ki sai</p><p>ya hakura ya roki Allah ya shiryeta, shi kuma ya</p><p>kare shi da fadawa sharrin zina. 26.... Bai zaginta</p><p>ko ya ce zai nuna mata karfin shi, ko ya ce zai</p><p>tsaya rokonta, shi yasa yake yawan yin Azumi.</p><p>Ummi ta ce, "Umma ki kawo kudi in siyo kwai in</p><p>soya ma Yaya Abba doya, ya ce zai zo shan</p><p>ruwa. Ta ce, "To je ki kasan filo ki dauko, amma</p><p>fa sai kin yi azama don an kusa kiran sallah. Ta</p><p>ce, "Ai na dafa ruwan shayi, sannan na masa</p><p>kunun tsamiya, doyar ce kawai, ta ce "To sai da</p><p>ta gama komai sannan tayi wanka tayi sallah.</p><p>Riga da siket na leshi tasa fari tas, bata damu da</p><p>yin fenti da dare ba amma yau tayi ta feshe</p><p>jikinta da turare wanda shi ne ya sai mata.</p><p>Sallamarshi ta jiyo suna gaisawa da su Umma, ta</p><p>fito ya bita da kallo, kin yi kyau kanwata, Umma</p><p>ta ce yau za ku hoton ne? Ta ce kila, Abba ya ce</p><p>shi yasa ki ka yi kwalliya haka? Ba ta ce komai</p><p>ba sai dai ranta bai so ma maganar da Umman</p><p>tayi ba. Suna hira da Umma ta shirya misi abinci</p><p>ta koma kan kujera ta dauki littafi lokaci-lokaci</p><p>idanunta suna kan Abba. 13 Suna hira da Umma</p><p>ta shirya mishi abinci ta koma kan kujera ta dauki</p><p>littafi, lokaci-lokaci idanunta suna kan Abba. Shi</p><p>ma haka ya ce wai ni littafin nan da ku ke nacin</p><p>karatunshi dame kuke karuwa? Umma ta ce, Ai fa</p><p>gara ka tambaye ta, don ban ga abinda ta ba</p><p>muhimmanci ba irin wannan littafin. Ummi ta cem</p><p>ina karuwa sosai Umma suna koya mana tarbiyya</p><p>yyanda zamu tafi da rayuwarmu cikin tsarin</p><p>Addini da al'adarmu. Abba ya ce amma basa</p><p>koya tsafta da biyayya, Ummi ta ce suna yi sosai</p><p>ma, ya ce Umma ni naga jarabar karatu irin na</p><p>Bishira amma kullum mugayen halayenta bayyana</p><p>suke yi. Ummi ta ce ni ko har addu'o'i zuwa girki</p><p>kala- kala ina koyo, Umma ba rannan nayi</p><p>dafadukan kwakwa ku ka ce ya yi dai ba?" Ta ce,</p><p>"To ki dai dinga daukan na kwarai kina yarda na</p><p>banza, Abba ya ce in haka ne d agaske zan samu</p><p>lokaci in zo ki karanta min in ji, ta ce "To." 27.....</p><p>Umma ta yi 'yar dariya ta ce, "Sai ka ce ba ka da</p><p>aikin yi? Ya ce, "Allah Umma da gaske nake yi</p><p>don in ji wacce irin koyarwa suke yi, marubutan</p><p>ko ko sai shirme?" Kiran sallar Isha'i ne yasa</p><p>Abba mikewa, ita kuma Umma ta tafi kicin don</p><p>shiryawa su Alhaji Abinci. Ummi kam sun bar ta</p><p>cikin takaicin tafiyar Abba don dai bata gundura</p><p>da shi. * Alhaji Ya kalli Umma, wai yau bikin</p><p>yaran nan saura wata nawa? Ta ce, "Wata ko</p><p>kwana dai?" Yau saura kwana talatin da shida,</p><p>ban ga kana motsi ba? Alhaji bikin nan zai</p><p>mamaye mu, ya ce "Yanzun ya za a yi da batun</p><p>kaya?" Ta ce, "Ni da cewa nayi ga Abba sai yaje</p><p>ko kuje ku za6a musu kaya masu kyau a siya,</p><p>kada a ba kafintoci in ba a yi sa'a ba har lokacin</p><p>yayi ba a gama ba". Ya ce, "To zan sa shi ya tafi</p><p>da su kawai su za6a". Ta ce, "Sai kayan girki na</p><p>dai sayi tukwane da risho, sai kuloli". Ya ce, "Duk</p><p>da haka uwata zan sa ta za6i wasu kayan."</p><p>Umma tayi dariya tare da cewa, "Allah ya kara</p><p>budi, nan dai suka yi ta lissafin kudi. Da safe</p><p>Alhaji ya kira Abba a waya ya sanar da shi cewa</p><p>ya dauki su Ummi suje su za6i irin kayan da suke</p><p>so, duk da cewa zancan ya doki zuciyarshi amma</p><p>ya ce "To." insha Allah zamu je, suka yi sallama.</p><p>Sam baya son ya ji batun auran su Ummi, baya</p><p>son rasata, kuma yana ji a jikinshi cewa zai same</p><p>ta. ** ** 28.....Yammacin ranar Asabar La'asar</p><p>lis garin yayi dan sanyi Abba ya nufi gidansu don</p><p>daukan su Ummi zuwa kasuwa. Jikinshi sanye da</p><p>farin yadi mai shara-shara, har ana iya hango</p><p>fara kar din singiletin da ke ciki ta manne a</p><p>jikinshi. Kamshin turarenshi ya cika dakin Umma</p><p>wanda ba shiga yayi ba daga bakin kofa suka</p><p>gaisa. Ya ce, "Ummi su fito don Ummi ce ke</p><p>shiryawa tuni Fati ta fito, ya matsa kofar</p><p>Tsohuwa suka gaisa, sannan ya ce "Umma sai</p><p>mun dawo. Ya nufi waje yana fadin su Ummi su</p><p>mishi sauri. Sun fito za su duru a baya Abba ya</p><p>ce Ummi ta dawo nan gaba, ta zauna ranta</p><p>dagule don ita bata bukatar wani za6i tunda ba</p><p>wanda take so zata aura ba. Haka nan ta</p><p>fuskanci Abba yau yana cikin wani irin yanayi,</p><p>kila daga gida aka 6ato masa rai, nata tunanin</p><p>kenan. Shi kam takaicin zuwa za6on kayan ke</p><p>damunsa, ya kalli wayarsa da ke ruri ya daga,</p><p>Salis ya ce kana ina ne? Ya ce ina nan</p><p>unguwarmu zan kai kannena ne za su za6i kayan</p><p>daki. Ya ce, "Ta ina zaku bi? Abba ya ce kai kana</p><p>ina ne? Ya ce ina nan kusa da asibitin Malam,</p><p>bari in jira ka a jikin gidan man nan, Abba ya ce</p><p>"To." Salis ya kalli yarinyar da Abba ya ce Ummi</p><p>koma baya ya ce, "'Yammata sannunku, suka</p><p>gaishe shi ya yi murmushi ke ce Ummi?" Ta ce,</p><p>"Eh, ya ce ya su Umma?" Ta ce lafiya lau, ya</p><p>maida dubansi ga Abba wanda ke tuki cikin</p><p>nutsuwa ya ce, "Idris akan batun yarinyar nan ne</p><p>don Allah ka daure muje gidansu yau". Gaban</p><p>Ummi ya fadi. Abba ya ce, "Don Allah Salis ka</p><p>bar batun yarinyar nan, kai dai kasan halin da</p><p>nake ciki game da wata". Salis ya ce, "Me yasa</p><p>ka amsa kana sonta, kuma har kana daga waya</p><p>duk lokacin da ta kira ka?" Abba ya ce, "Shike</p><p>nan za mu je da yamma tunda wancan na rasa</p><p>madafa". Salis ya ce kuma fa da hakan zai fi</p><p>maka. Ummi gashin jikinta duk ya mike, suna fitar</p><p>da zufa lumshi ido tayi luf a kan kujera ta kwantar</p><p>da kai, Salis ya waiwaya ya dubeta, yaya dai? Ta</p><p>yi dan yake, "Ba komai." . 29.... Sun je gurin</p><p>kujeru da gadaje, Fati tayi ta ruwan ido yayin da</p><p>Ummi ta koma ta jingina a kujerar da ta zauna.</p><p>Abba ya dube ta. "Ke wanne ki ka za6a? Ita ta ce</p><p>wancan farin". Ummi ta yatsina fuska, "Nifa bani</p><p>da za6i, duk wanda ku ka ga yayi". Salis ya ce, "</p><p>Idris yarinyar nan ina zaton tana sonka, naga</p><p>tunda muka yi maganar zuwa gurin wata ta</p><p>canza yanayi. Abba ya ce, "Kyaleta ba wani ya</p><p>dubeta ba, ke Ummi tashi ki za6a mu ji</p><p>farashinsu, sauri muke. Ta ce, "Ya Abba cikina ke</p><p>ciwo, ka za6ar min don Allah". Ya ce, "Salis ita</p><p>ma a bata farin kawai ko? Salis ya ce, "A daukar</p><p>mata mai ruwan madaran, mai shagon ya ce sun</p><p>fi tsada, Abba ya ce ka daukar mata su. Sun</p><p>koma gefen kujeru nan fa Abba ya ce dole sai ta</p><p>za6a, nan ma wanda ta za6a a ka ce sun fi na</p><p>Fati tsada, suka ji farashinsu su sannan ya ba da</p><p>wani abu suka tafi. Ya sauke su a gida, Fati sai</p><p>ba Umma labari take yayinda Ummi ta shiga</p><p>kuka, Umma ta ce ke kuma lafiya ki ke kuka?</p><p>Ummi ta ce "Umma ni bana son in yi auren nan,</p><p>bana son in bar gida. Fati ta ce, "Shi yasa naga</p><p>tun a gurin shagon kina ta 6acin rai? Umma ta</p><p>ce, "Shirmen banza da wofi, sai ki tayi. Ta fice,</p><p>Fati ta ce Ummi ke kin cika son damuwa. Menene</p><p>na damuwa? Kila ma kina nan unguwar.ovels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 5</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 5</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:29</p><p>ummi sannu da zuwanku, nan sukayi masa</p><p>gaisuwa yace ummi kaisu ciki. 36.. Zainab tace a</p><p>ranta wato ma ummi yafara gani, a fallon su</p><p>umma suke don nan ta fara kai su, tace umma</p><p>wanan ce zainab, wannan kuma matar abokinshi</p><p>salis, umma tayi masu sannu da zuwa sanna tace</p><p>ummi ta kaisu dakin bishira, sun shiga sun yi</p><p>mata gaisuwa, bishira tace ke ko gaisuwa baki zo</p><p>min ba koda yake bai dame ki ba, ummi tace</p><p>nima ana ta zuwa min gaisuwan ne a gd, duk yan</p><p>dakin suka kalli ummi, sahura tace ke asuwa?</p><p>Bishira tace ita a mahaifiyar shi, ummi tace</p><p>zainab kuzo muje, tun daga lkcn zainab tasa a</p><p>ranta akwai matsala a wanan familyn din, basu</p><p>jima ba suka yi sallama, inda ummi ta rakasu</p><p>daga can itama ta wice gd, suna shiga soro</p><p>shima ya shigo yace badai tafiya zakuyi ba? Ya</p><p>kalli ummi sun sha ruwa ma kuwa?ummi wadda</p><p>dama idanunta na kanshi ta amsa mishi da</p><p>idanu. Yace yama akayi kuka gane gdn zainab</p><p>tace yaya salis ne yakawo mu, ya kalli matar</p><p>salis yace madam mun gode fa,tace bakomai</p><p>Allah ya jianshi, sam ummi batasan lokacin da</p><p>furucin ya fito mata ba, sai dai taji tace ya abba</p><p>duk ka rame baka cin abinci ko? Shi kanshi yayi</p><p>mamaki don haka ya ya tsura mata ido, sai taji</p><p>kunya ta rufee ta saita kau da kanta daga</p><p>kanshi,don kada su zargeta. Kayi hkr naji wani</p><p>malami yace duk wanda yaranshi kananan uku</p><p>suka rasu to zasu ceceshi ranar gobe. Kaga ynz</p><p>kafara da daya,matar salis tace ai koma dayane</p><p>indai kayi hkr kayi tawakkali,ummi ta kalle shi</p><p>tace to kaji ma,yace ummi nifa tuni na</p><p>dangana,ta sake tausasa murya to meyasa baka</p><p>cin abinci? Ya tausasa murya wadda dama take a</p><p>dusashe yace ummi inaci,tace ya abba baka fa</p><p>yin karya,yace to yau zanzo inci a gabanki, ya</p><p>kalli matar salis wadda ke murmushi, in naci a</p><p>gabanta saita yarda ko? Tace tabbas! 37..Zainab</p><p>wadda takaici ya cikata tace da matar salis anty</p><p>nifa natafi, abba ya dubeta zainabu nagode ki</p><p>gaida su mama sai nazo,batare da ta tsaya ba</p><p>tace to, ummi ta musu sallama itama ta tafi gd.</p><p>Zainab ta dubi matar Salis bayan tafiyar Ummi,</p><p>ta ce, "Duk da son da na ke ma Idris din nan ba</p><p>zan aure shi ba". Matar Salis ta ce dalili? Zainab</p><p>ta ce, "Bana zaton ko matarshi ta gida da ya</p><p>aura ya aje yana sonta irin yanda yake son Umiin</p><p>nan". Abin nasu yayi yawa. Dubi yanda ya manta</p><p>da ni, ta ita kawai yake yi. Matar Salis ta ce, kin</p><p>ji ki da wani shirme, ita da zata yi aure?" Zainab</p><p>ta ce, "Abinda ke tausar zuciyata ke nan in na</p><p>tuna cewa zata yi aure, amma kai naga ji ba zan</p><p>iya ba, haka suka tafi tana ta bai wa yarta</p><p>labarin yanda Abba ke ji da Ummi. Kamar yadda</p><p>Abba ya ce zai zo cin abinci da dare yazo, Ummi</p><p>ta saka shi gaba wai sai ya cinye wake da</p><p>alayyaho da kifin da ta dafa masa. Da kyar ya</p><p>cinye plate din farko ya ce "Ummi na koshi kin ji?</p><p>Ta daure fuska tana kallonshi, shi ma ita yake</p><p>kallo yana dan murmushi. Ya ce, "Ina ma a ce</p><p>tun da da haka muka yi sabo, Ummin cikin</p><p>kwanakin nan kin lura cewa muna shiri". Ta</p><p>harare shi, "Kana zaton na manta da irin dukan</p><p>da ka yi ta min ne? Shi ma ya harare ta tare da</p><p>kwaikwayon muryarta. "Kina tsammanin zan</p><p>manta da irin tsokanar fadanki ne? Ko zan manta</p><p>da Suhailar Kaduna...?" Kafin ya rufe baki tuni ta</p><p>yi uwar daka da gudu, shi kam dariya yayi ta yi</p><p>yana cewa ki zo mana Ummi, kin fitowa tayi har</p><p>sai da ya bar gidan. Duk lokacin da suka kasance</p><p>tare kowannan su yana mantawa yana da wata</p><p>matsala. Saura kwana uku daurin auransu,</p><p>lokacin dangi sun soma zuwa, musamman 'yan</p><p>Zamfara. Ummi da Abba hankalinsu ya kai</p><p>kololuwa gurin tashi. Ranar ya ziyarci Zainab wai</p><p>ko zai samu 'yar nutsuwa. Bayan sun gaisa ta</p><p>sake mishi gaisuwa, shi kuma ya mata bangajiya,</p><p>dama tun da aka yi rasuwar bai zo ba. Ya ce</p><p>"Zainab ina ganin da an gama hayaniyar bikin</p><p>Ummi zan turo". Tayi shiru bata yanke ma kanta</p><p>shawarar matsawar ya cikata da zancan Ummi</p><p>yau kam za su yi ta ta kare. Jin tayi shiru ya ce</p><p>kina jina Ummi... ta katse shi da sauri, "Ba Ummi</p><p>nake ba Sorry Zainabu. Ya ci gaba bakina ne ya</p><p>saba da kiran Ummi, da yake daga ni sai ita ne a</p><p>gidan. Yanzun haka auran nan da zata yi ina cikin</p><p>tsananin kewarta...Zainab ta ce ina Idris? Don</p><p>Allah ni na hakura ka je ka auri Ummi, Abba ya</p><p>dubeta cikin tsananin mamaki. 38.. Me ki ke</p><p>fada? Me Salis ya sanar da ke? Ta ce Idris duk</p><p>wanda ya san so, minti biyar in ya zauna da ku</p><p>zai san kuna tsananin son junanku kuma ni na</p><p>tambayi Salis cikinku daya? Ya ce min A'a tun</p><p>daga nan nasan cewa ku masoya ne, ta nufi</p><p>hanyar gida, da sauri ya sha gabanta. Zainabu</p><p>kada muyi haka da ke, wallahi auranki zan yi. Ta</p><p>ce, "Eh ai na san aurena zaka yi, amma ba sona</p><p>ka ke ba, don Allah ban hanya sonka in zai yi</p><p>ajalina ba zan aure ka ba, ya kauce ta wuce, ya</p><p>bita da kallo har ta shige. Jiki ba karfi yake tuka</p><p>motar har ya iso gida, kukan Muhibba ya jiyo don</p><p>haka ya nufi dakin. 21. Jiki ba karfi yake tuka</p><p>motar har ya iso gida, kukan Muhibba ya jiyo don</p><p>haka ya nufi dakin. Bishira na zaune ta zuba</p><p>tagumi tunanin danta take, ga Abba sam baya</p><p>sakar mata fuska, ya ce "Lafiya Mamina take</p><p>kuka?" Ya shiga ya dauketa Bishira ta ce, "Rigima</p><p>cee kawai, ya nufi kan madubi inda ya hangi</p><p>pampers ya dauki guda daya ya nufi dakinshi da</p><p>ita. Bishira ta biyo shi itama ta zauna a gefen</p><p>katifa kusa da shi, cikin sanyin murya ta ce,</p><p>"Abban Walid don Allah kayi hakuri, ya ce me a</p><p>ka yi? Ta ce, "Gani nayi kana ta fushi, ya ce ni</p><p>bana fushi wannan kadan kenan ki ka gani daga</p><p>cikin sakacinki, na tabbata kin fini jin bakin cikin</p><p>mutuwar yaron nan. Musamman da ki ka zama</p><p>sanadi, amma don batun yawo ni na daina miki</p><p>fada, kiyi tayi illa dai zan nemo wadda zata dinga</p><p>lurar min da gida. Ta ce me ka ke nufi? Ya ce</p><p>aure zan yi". Ta doki kirji tare da fadin, "Aure?" ya</p><p>ce, "Eh". Ta soma kuka haba Baban Walid, wane</p><p>laifi na maka da zaka yanke min irin wannan</p><p>mummunan hukuncin? Ya ce, "Don Allah fita, ta</p><p>ce sai ka fada min dalilin yin auranka, ba za ka</p><p>bar ni in ji da rashin dana ba ko? ta mike an</p><p>zugo ka an ce kayi aure, to bisimilla. Ta fita ta</p><p>zari mayafi tayi gidan Umman Bashir. Abba ya</p><p>rungume 'yarshi ya yi laf a kan katifa shawara ya</p><p>yanke zai tura magabanshi gidan su Zainabu ba</p><p>tare da ya sake bi ta kan Zainabun ba. * Umma</p><p>ta leko dakin Tsohuwa, Ummi kin san na ce miki</p><p>kizo ki kwashe kayanki daga dakina ki adana su</p><p>ko? Kin san dai yau duk na nesa za su iso, ki cire</p><p>wadanda za ki bada. Tsohuwa ta ce, "Suwaiba</p><p>yarinyar nan ina kallonta jiya bata runtsa ba,</p><p>sannan da Asubahi a zaune tayi sallah. Umma ta</p><p>shiga dakin warwas take a kan gado, Umma ta</p><p>tasheta zaune Ummi ciwon kai ta keya ga jiri da</p><p>ta ke gani daga zaune. 39.. Umma ta ce taso ki</p><p>dan watsa ruwa ki karya, mikewar da zata yi sai</p><p>ta sulale a kasa sumammiya, nan suka dau</p><p>salati, Toshuwa kam kuka ta saka. Alhaji ya fito</p><p>wanka kenan ya ji Umma na salati, don haka</p><p>dakki ya shiga ya dauko waya ya kira Abba</p><p>lokacin yana kokarin shiga wanka. Alhaji ya kira</p><p>shi, jin cewa Ummi ba lafiya zari mukullin mota</p><p>ya fito. Sai da suka kai asibiti sannan ya lura da</p><p>silifas ya fito da jallabiyarshi ta wanka, Lkitan ma</p><p>bai zo ba lambarshi suka amsa Abba ya kira shi.</p><p>Ya duba Ummi sosai da kyar suka samu</p><p>numfashinta ya dawo, sun daura mata ruwa</p><p>sannan aka kaita wani daki. Likitan ya ce su zo</p><p>ofishinsa, Ya kalli Alhaji ya ce, "Gaskiyar magana</p><p>yarinyar nan tana bukatar kulawarku, ciwonta</p><p>baya son sakaci. Jininta ya hau ya wuce matakin</p><p>da zata iya samun mutuwar 6arin jiki. Su Alhaji</p><p>suka dauki salati,, ya ci gaba da cewa yanzun dai</p><p>addu'a zamu ci gaba da yi. Allah yasa in ta</p><p>farfado kada wata matsala ta biyo baya. Sannan</p><p>ya basu takardar magunguna". Alhaji ne ya amsa</p><p>don Abba fita yayi ya koma dakin da Ummi ke</p><p>kwance. Idanu ya zub amata, sam bai san cewa</p><p>kuka yake ba, sai da Alhaji ya shigo ya dafa shi</p><p>tare da cewa, "Haba Abba ba girmanka ba ne</p><p>kuka. Addu'a za ka yi Allah ya bata lafiya". Ya</p><p>share hawaye. Alhaji don Allah kada ka sanar da</p><p>Umma abinda Likitan ya ce, Alhajin ya ce ai</p><p>dama ba zan fada mata ba. Bari in je sai tazo ga</p><p>takardar maganin inta zo sai ka siyo, ya ciro kudi</p><p>ya mika ma Abba, Abba ya ce a'a da kudi a</p><p>jikina. Alhaji ya ce ka amsa ka kashe kudi cikin</p><p>kwanakin nan ina sane da duk lokacin da na ce</p><p>kazo ka siyo wani abu sai kawai in gan ka da shi</p><p>ban da kayan dakin da ka siya musu, Abba ya ce</p><p>ai ina da shi ne. Bayan fitar Alhaji Abba yaja</p><p>kujera ya zauna ya zabga tagumi tare da tsura</p><p>ma Ummi ido, a zuciyarshi fadi yake ALLAH ka</p><p>tashi yarinyar nan lafiya, Allah kasa kar ko ina na</p><p>jikinta ya nakasa. Alhaji ya fada wa Umma an ba</p><p>Ummi gado, don haka ta shirya su wuce. Abba ya</p><p>tashi ya nufi ofishin Likitan, bayan ya kwankwasa</p><p>Lokitan ya ba shi izinin shiga, ya same shi yana</p><p>rubuce-rubuce. Ba tare da ya dago kai ba ya ce,</p><p>"Zauna sai da ya kai aya rubutunshi sannan ya</p><p>dago kai ya kalli Abba "Ba dai mai jikin ba ce</p><p>ko?" Abba ya ce, "a'a ina son ne nima agwada</p><p>nawa jinin, Likitan ya ce kana jin jikinka ba dadi</p><p>ne?" Abba ya ce, "Eh da har yasa a dauko fayal</p><p>din Abba kuma ya tasa ya dauki abin gwaji.</p><p>Bayan ya gama ya zaunar, ya tsare Abba da ido</p><p>wai kun yi gadon ciwon nan ne? Abba ya ce,</p><p>"A'a, Likitan ya ce, "Jininka ya hau, sai dai ba</p><p>sosai ba. Kila don kai namiji ne kana kokarin</p><p>kauce ma abubuwa. Zan rubuta maka magani na</p><p>sati daya, kuma ka dinga kokarin yin bacci a kalla</p><p>na wa shida kada ka dinga yawan tunani. Kaga</p><p>kanwar nan taka, sai sa'ar gaske zata tashi</p><p>lafiya. Ku dai cigaba da addu'a, zata yi bacci na</p><p>tsawon awa tara ko goma. Ina son daidai lokacin</p><p>da zata farka ya kasance ta soma dora ido a kan</p><p>wanda suke shiri ko wanda ta fi so a cikin</p><p>mahaifanta ko danginta, Abba ya ce "To."</p><p>Lokacin da ya koma dakin su Umma sun zo har</p><p>da tsohuwa, nan Abba yake fada musu abinda</p><p>Likitan ya ce game da farkawa in tayi. Koda bude</p><p>bakin tsohuwa sai cewa ta yi ai ko dai ba a bar</p><p>mai sunan Malam ba, tunda an ce wanda suke</p><p>shiri, don in taga mai sunan Malam karasawa</p><p>zata yi. * 22. Duk da ana cikin wani hali sai da</p><p>su Alhaji suka murmusa. Abba kam daure fuska</p><p>yayi yana kallon Tsohuwa, Umma ta ce, "Ai da ne</p><p>Tsohuwa. Yanzun shiri suke tunda ta daina rashin</p><p>jinta". Likitan ya shigo ya sake musu bayani</p><p>kamar yadda ya yi ma Abba, sannan ya ce su</p><p>bata guri kada zantukansu ya farkar da ita a</p><p>samu matsala. Suka fito, Umma ta ce da Abba ya</p><p>tafi gurin aikinsa, su Alhaji ma suka fita tare da</p><p>Abba. Fati ta je gidansu Sahabi dan uwansa yana</p><p>kankarar rake a kofar gida, inda yake saidawa ta</p><p>tambayi Sahabi. Yaron ya ce mata ya ffita, ta ce</p><p>To in yazo kaa ce masa Ummi tana asibiti ba</p><p>lafiya, an bata gado. Karfe uku ya iso asibitin</p><p>hankali a tashe, sun gaisa da Umma ta raka shi</p><p>dakin, hankalinshi ya tashi da ganin Amaryarshi</p><p>kwance a gadon. Abba kam yana gurin aikinshi</p><p>amma hankalinshi na Asibiti, su Alhaji ma duk</p><p>nan suka nufo, Abba sai da yayi magriba sannan</p><p>ya shigo asibitin. Jikinshi babu karfi, bai matsa</p><p>sai yaga farkawar Ummi ba ne saboda yasan da</p><p>gaske ba shi ne ya dace idanunta su soma arba</p><p>da shi ba, ya samu su Umma da su Alhaji.</p><p>Sahabi da abokansa duk suna gurin, ya gaida su</p><p>tare da tambayar ko ta farka? Umma ta ce har</p><p>yanzun dai shiru. Ya nufi cikin gurin Likitan suka</p><p>gaisa, ya ce Likita har yanzu ba ta farka ba. Suka</p><p>jera zuwa dakin, Likiran yana cewa cikin wannan</p><p>dan takin zata farka, In sha Allahu. Sun shiga</p><p>takin tana dan motsi suka nufi gadon Abba ya ce</p><p>Ummi. Likitan ya daga mishi hannu alamar yayi</p><p>shiru ita kam daidai lokacin mafarkin Abba take</p><p>wai suna tafiya ya rike mata hannu sai ga</p><p>Sahabi. Yana zuwa ya kama hannunta tana</p><p>tirjrewa, sai janta yake zai fita da ita, Abba yana</p><p>tsaye yana kallonsu. Ita kuma sai kiran "Ya Abba!</p><p>Ya Abba!! Take yi. Likitan ya kara kunne gurin</p><p>bakinta ya dagowa yayi ya dube shi. "Waye Yaya</p><p>Abba?" Abba ya ce ni ne. Liitan ya ce, matsa</p><p>kusa, ya kama hannunta. Ummi. A hankali ta</p><p>bude ido. Ya Abba! Ya abba, zan sha ruwa, ya ce</p><p>to ya kalli likitan za ta sha ruwa, Likitan ya ce,</p><p>"A'a bari ta dan kara warwarewa tukunna. Likitan</p><p>ya kama kafafunta ya dan matsa, sannu ko. Ta</p><p>kalle shi, kin ji zafi? Bata yi magana ba ya dauki</p><p>allira ya 6are ya dan soka mata a tafin kafa ta ja</p><p>kafafunta alamun taji zafi. Ta yunkura zata tashi,</p><p>Ya abba zan tashi, ya tayar da ita zaune. "Likitan</p><p>ya ce Alhamdulillah, Abba ya kalli likitan, ba</p><p>matsala kenan? Ya ce, Ina zaton haka insha</p><p>Allah, Abba ya ce "Alhamdulillahi, ya jinginata da</p><p>jikinshi, sannu Ummina. 41.... Alhaji ya shigo</p><p>yana cewa, "Ina Abba ne?" ya ganta zaune a'a ta</p><p>farka ne? ya kama hannunta sannu uwata. Ta</p><p>kalle shi. "Ina Ummata?" ya ce, "Bari in kira miki</p><p>ita". Yaje ya sanar da su, sun shigo da murna.</p><p>Sahabi ya iso gaban gadon. "Sannu Ummi". Ta</p><p>kalle shi sai ta kwantar da kanta a kafadar Abba,</p><p>"Ya Abba ina son in wanke bakina". Ya ce, "To</p><p>bari in siyo miki Maclean din". Ta ce, "A'a kada</p><p>kaje". Ya gyara zama "To shi kenan." Umma ta</p><p>ce, "Me ta ke so?" Abba ya ce "Baki zata wanke".</p><p>Umma ta ce "Ai nazo mata da maclean da</p><p>burushin nata, don nasan ita gwanar wanke baki</p><p>ce". Nurse ta kawo wani dan kwano na silba</p><p>Ummi ta wanke baki da taimakon Abba. Likitan</p><p>ya ce, a bata tea mara zafi sosai, sannan a bata</p><p>magani. Takaici dan'kam a zuciyar Sahabi, irin</p><p>wannan shigewa da Abba ke matar da zai aura</p><p>tayi yawa. Kai shi fa wannan Yaya Abban bai</p><p>masa ba ma, don yana daure mishi fuska ko</p><p>gaida shi yayi d kyar yake amsawa. Shi fa tun</p><p>ranar da a ka ce mishi Ummi ba cikinsu daya da</p><p>Abba ba ya ji ya tsane shi. Umma ta ce, "Abba</p><p>an kira Isha'i. Sahabi kaje kai ma ka huta yaran</p><p>nan tun tuni ya ke nan". Abba ya kalle shi, "Ya</p><p>kamata ka tafi haka ko?" ya kalli Ummi sannan</p><p>ya dan rusuna "Sannu Ummi". Ta ce, "Yauwa"</p><p>"Innata ta ce in gaida ki da jiki, ni zan tafi sai da</p><p>safe. Me zan kawo miki?" Abba ya dube shi a</p><p>kule., "Don Allah Malam kaje ba za ta iya cin</p><p>wani abu yanzun ba". Umma ta ce, "Abba". Ya</p><p>kale ta, sai ta girgiza mishi kai alamun ya bari.</p><p>Sahabi jiki a sanyaye ya fice tare da cewa "Umma</p><p>sai da safe". Ta ce, "To Sahabi, ka gaida Innar</p><p>taka". Da ya fita ta kalli Abba "Wannan ba</p><p>halinka ba ne kada in kuma gani". Ya ce "To</p><p>Umma". 23. Su Alhaji sun yanke shawarar daga</p><p>auran Ummi a darua na Fati kawai, ita sati biyu</p><p>masu zuwa sannan ta murmure sai a daura nata.</p><p>Gidan su Sahabi sun ji haushi musamman</p><p>Innarshi, sun kashe dan abinda suka tattala don</p><p>bikin amma gashi an daga, su kam da an daura</p><p>auren in ta murmure sai a yi bikin. Sahabi ya</p><p>shigo gidan ranshi a 6ace, ya kalli Mahaifiyarshi,</p><p>"Inna wai sun ki a dauram?" Ta ce, "Sun ki, dama</p><p>ai gaddamar dan yau ce. Ban da shegiyar</p><p>gaddama ga 'ya can da a ka baka a daura ka</p><p>gaddame, to yanzun ina ranar abin da aka mana?</p><p>Gida duk dangi sun cika amma wai a daga biki,</p><p>mu kuma karamin karfi ne da mu, bare mu ce nan</p><p>da sati biyu zamu sake kashe kudi". Sahabi ya</p><p>tuna abinda Abba ya masa a asibiti, shi ne dalilin</p><p>da bai sake zuwa asibitin ba, yaja tsaki. "Kin san</p><p>Allah Inna ni kaina sai yanzun nake jin haushin</p><p>kaina da na ki amincewa da Badariyya. Mu zuba</p><p>musu idanu in za su sake kawo mana cikas sai</p><p>kawai in koma gurin Badariyya." Inna ta ce, "In</p><p>da tun jiya kamin zancan nan da tuni yau ba a</p><p>fasa daura auranka ba an ma da Badariyya". Ya</p><p>ce, "Kiyi hakuri Inna mu ga nufin su". * 42... An</p><p>sha shagalin bikin Fati kuma an kaita gidanta.</p><p>Ummi jiki Alhamdulillah, Abba kullum in zai je aiki</p><p>sai ya biya. Haka nan in ya dawo gida wanka</p><p>kawai zai yi ya tafi, wataran sai goma ko sha</p><p>daya. Abokanshi suna ta zuba duba Ummi, ita</p><p>kanta da lokacin zuwanshi ya karato ta dinga</p><p>kallon agogo ke nan tana kallon kofa. A zaman</p><p>asibitin nan Umma ta gama karantar su tsaf.,</p><p>matukar son juna suke yi, sai dai taji takaicin da</p><p>sai yanzun sonsu ga juna ya bayyana. Lokacin da</p><p>ya kasance an riga an bada Ummi ga wani sai</p><p>dai ta ci gaba da addu'a Allah yayi za6i na</p><p>alkairi. Bashir yayi murna da fasa auran Ummi,</p><p>dama a fasa gaba daya. Yana fitowa dakinshi ya</p><p>ji Ummarsu tana cewa, "Kin san Allah Tasalla,</p><p>uwar yaron nan da zai auri Ummi zata ga bakin</p><p>ciki, don mallake mata da za su yi. Tana ji tana</p><p>gani sai yanda suka yi da shi. Kuma ba yanda</p><p>zata yi sai Allah ya isa". Tasalla ta ce "Ban da</p><p>halin mutanan yanzun ba da sai na fada mata ba.</p><p>Kin san makotanmu ne ta baya, gashi su ba karfi</p><p>ba. Sahabin ne fa ke rike da gidan, kin san shine</p><p>Babban a gidan". Sahura ta ce, "Don Allah Tasalla</p><p>ki taimaka ki fada musu, don ko in har aka yi</p><p>auran nan in suna cin abinci sau uku ne a rana,</p><p>to za su koma dau daya". Tasalla ta ce "Ai ko</p><p>zanje". Tana fita Bashir ya dawo kusa da</p><p>Ummarsu ya ce, "Umma dama da kanki ki ka je,</p><p>saboda za su fi yarda tunda sun ga ke kina da</p><p>danganta da gidan". Ta ce, "To in Babanku ya ji</p><p>fa?" Ya ce "Umma ai in kin fada musu ai kwa6ar</p><p>su za ki yi, sannan kada kije a kan lokaci, kije ana</p><p>gobe daurin auren". Ta ce, "Saboda me?" Ya ce,</p><p>"Saboda su Alhaji Babban suji haushin rashin</p><p>fada musu da wuri". Ta ce, "Haka za a yi, kuma</p><p>in an fasa Malamai zan shiga don a hanata auran</p><p>ma kwata-kwata". Ya ce, "Kada kije wurin</p><p>Malamai yanzun tukun". Ta ce. "Ai dama sai an</p><p>natsa". * Abba ya fito cikin suit bakake, yayi kyau</p><p>matuka hatta takalminshi sawu ciki baki ne,</p><p>tamkar wani black America. Igiyar wuyan ta</p><p>zauna tsam, sai kamshi yake. Dakin Bishira ya</p><p>nufa ya daga labule, ta dago ta kalle shi yayi</p><p>matukar birgeta. Tana alfahari da shi matsayin</p><p>mijinta, ya ce "Kin shirya?" ta ce,, "Zuwa ina?' Ya</p><p>ce, "A'a, jiya fa na sanar da ke ki shirya da wuri</p><p>zamu je asibiti ki gaida Ummi". Ta watso mishi</p><p>wani kallo uku saura kwata, tare da cewa "Ko</p><p>garin nan ba a sanyi ba zan fita gaida wata can</p><p>Ummi ba bare da sanyin nan." Ya ce, "Dalili ta</p><p>mike tsaye "Ciwo bai kai mutuwa ba, da mutuwa</p><p>ya yi tazo ta min gaisuwa?" Takaici ya turnu'ke</p><p>Abba, da yake sarkin dankara magana ne, sai ya</p><p>ce "To ita ta kashe shi da zata miki gaisuwa?"</p><p>Ta kule da bakin ciki ta zabga mishi harara "To ai</p><p>kasan ni na dora mata ciwon, don haka dole in je</p><p>gaisheta." Ya ja tsaki tare da cewa, ballahaza</p><p>wadda bata san mutuncin mijin auranta ba". Ya</p><p>yakice labulen ya wuce yana jiyo ta tana cewa,</p><p>"Ba dai za ni ba ko me za ka ce". Ranshi a 6ace</p><p>ya isa asibitin, Ummi na zaune kan gado ta kosa</p><p>Abbanta yazo, ko karyawa ta kasa yi, yana</p><p>sallama suka hada ido. Nan ta ke ya ji ya manta</p><p>da duk wani bakin ciki da ya taho da shi, ya isa</p><p>bakin gadon fuskarshi dauke da murmushi. Itama</p><p>murmushin take yi, ya ce. "Ummi ya ya jikin?" Ta</p><p>ce "da sauki". Ya Abba kayi kyau sai ka ce</p><p>Manajan Banki". Umma ta saka dariya, shi ma ya</p><p>yi 'yar dariya, "To ko bankin zan koma?" Ta ce,</p><p>"A'a kafi kyau da dan jaridanka Ya Abba, balle in</p><p>kana turancinn nan a labarai". Ya lakuci</p><p>kumatunta "Ko kwanwata?" Ya juya ya gaida</p><p>Umma, Umma ta ce "Ka zo katafi gurin aikinka</p><p>fa". Ya ce, "Umma sai sha daya yau zanje gurin</p><p>aiki". Ta ce, "Ni na ma kosa a sallame mu". Abba</p><p>ya ce "Ai kila a sallame ku yau. Likitan ya shigo</p><p>ne?" Suka ce "A'a. Suna cikin karyawa Likita ya</p><p>shigo ya same su, ya kuma kafa mata dokokin</p><p>daina tunani, daina shiga duk wani abu da zai sa</p><p>ta cikin damuwa. Rage shan gishiri tare da</p><p>samun isassen bacci, ya kuma gargadi su Umma</p><p>su dinga nisantar 6acin </p><p>Home / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com novels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 6</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 6</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:31</p><p>Rage shan gishiri tare da samun isassen bacci, ya</p><p>kuma gargadi su Umma su dinga nisantar 6acin</p><p>ranta. 26. 43... ABBA Ya kwaso su ya maida su</p><p>gida, cikin satin Ummi ta murmure. Sahabi na</p><p>zuwa sai dai da sun gaisa yake tafiya.</p><p>Mahaifiyyarshi ma tazo, amma Bishira da Sahura</p><p>ko le'ke, Bashir ma yana ta sintirin zuwa. Ganin</p><p>haka Alhaji ya ci gaba da shirin biki, mutan kauye</p><p>dai dama an ce kada su dawo, Ummi dai bata</p><p>maida hankali ga komai ba. Ta ce ma Umma zata</p><p>je gidan Fati, Umma ta ce To sai ki je gurin</p><p>Sahura ta kwatanta miki. Abba ya same su suna</p><p>zancen, don haka ya ce ta shirya zai kaita ya</p><p>ajiyeta in ya tashi aiki sai yaje ya daukota. Yanda</p><p>ta samu Fati da Angonta ana ta ji da juna abin</p><p>ya tsokanota, sai dai ta kasa ganin dacewar</p><p>soyayyar da Sahabi. Da mijin Fati ya fita Ummi ta</p><p>ce, "Oh, Fati cikin kwana takwas dubi yanda ki ka</p><p>yi kyau". Fati ta ce, "Amma ban rame ba?" Ummi</p><p>ta ce "Eh to, kin dan rairaye". Fati ta ce, "Kai ai</p><p>dole, gaskiya ina koduwa, wallahi ba ya barina in</p><p>huta". Ummi ta ce, "Da me?" Fati ta ce, "Dallacan</p><p>ki gane mana". Ummi ta ce, "Wai da me? Allah</p><p>ban gane ba". Fati ta ce, "Ai ke sokuwa ce, gurin</p><p>kwanciya mana. Ummarmu ta samu ta dirka min</p><p>kayan sha na mata, gashi nan nazo ina ta shan</p><p>wuya". Ummi ta zaro ido, "Da wahala ne?" Fati ta</p><p>ce, "Tab, ai kin kusa kema za ki ji". Tsoro ya cika</p><p>Ummi. Ta ce, "Zan ce ma Umma ni dai kada ta</p><p>bani wannan kayan matan". Fati ta yi ta dariya</p><p>tare da cewa, "Ke yanzun sai ki iya wa Ummanku</p><p>wannan zance?" Ummi ta ce, "Sosai ma". Fati ta</p><p>ce, "Ko ba ki sha ba yarinya sai kin sha zafi, ana</p><p>kawo ni ko dan kwana daya bai raga min ba".</p><p>Ummi dai ido ya raina fata. Koda Abba ya zo</p><p>daukarta duk ta damu. ** ** 44..... Tasalla ta</p><p>samu uwar Sahabi ta fada mata cewa, in dole ne</p><p>sai danta ya auri Ummi, to ta amso mishi karya</p><p>tambaya. Don kuwa wata rana sai ta taso ta</p><p>ganshi ko da a hanya ne ta rasa samun hakan.</p><p>Inna ta tsure ta ce, sai a fasa babu dole, ita</p><p>dama tuni abin ya sire mata. Ana gobe daurin</p><p>aure gidan su Ummi suna ta shiri Ummi na ta</p><p>kuka, wannan karon ba Umma ba har Alhaji da</p><p>Tsohuwa sun kule da wannan iskancin da Ummi</p><p>ke yi. Alhaji ya ce "Ki sani uwata, wannan karon</p><p>ko kin tsokalo ciwon nan naki auren nan dole ne</p><p>babu fashi. Idan yaso jinin naki ya tashi ya ta6o</p><p>sama ba zan kuma daga auran nan ba". Lokacin</p><p>da Alhaji ke wannan fadan Abba yana gidan yana</p><p>zaune dakin Umma yayin da Ummi ke gefanshi</p><p>tana rusa kuka. Umma ta shigo ya ce "Umma</p><p>don Allah ki lallashi Alhaji a dan daga bikin nan</p><p>mana". Abba bai ta6a ganin ranar da Umma tayi</p><p>mishi irin wannan kallon da ta masa yanzu ba</p><p>tun tasowarshi. Sannan bata ta6a daka masa irin</p><p>wannan tsawar ba ta ce "Kai! Abba shiga</p><p>taitayinka, me yasa yanzun ka canza, ko kai ba</p><p>za ka hukunta Ummi ba da irin wannan yaro da</p><p>hankalin da take mana? Don gidansu kanta a ka</p><p>soma aure? To wannan karon ba za a daga bikin</p><p>ba, in yaso ta mutu, ke ko mutuwa ki ka yi</p><p>gawarki can gidan mijinki za a je a miki sutura".</p><p>Tsohuwa ma daga can tana yo nata fadan tare da</p><p>dauko tarihe-tarihen da tana cewa, "Lokacinsu</p><p>kaza-kaza". Abba ya sake kallon Ummi,</p><p>matsanancin kukan da take yi yana daga mishi</p><p>hankali, ya mike tare da kama hannunta, "Zo</p><p>muje". Ya bude mazaunin direba ya ce ta shiga,</p><p>shi ma ya koma ya shiga motar ya tasheta, tafiya</p><p>kawai suke ba tare da ya san in da suka dosa ba.</p><p>Kukan Ummi na tsikararshi, sun yi tafiya mai nisa</p><p>sannan ya tsaya a hankali cikin wata irin murya,</p><p>ya ce "Ummi ki fada min gaskiya kina son</p><p>Sahabi?" Ta dago ta dube shi, "Ni bana son shi".</p><p>"To me yasa ki ka fito da shi?" cikin dasasshiyar</p><p>murya ta ce, "Ba ni da yanda zan yi ne, saboda in</p><p>ban za6i Sahabi ba za a bani Bashir". Ya ce, "To</p><p>ke yanzun fada min wa ki ke so?" Gabanshi ya</p><p>shiga faduwa don tsoron kada kunnenshi ya ji</p><p>mishi ta ce wani ba shi ba. Ta kuro shi da ido</p><p>tamkar ta ce kai, amma sai take ganin in ta fada</p><p>mishi haka dan shirin da suka soma yanzun zai</p><p>wargaje, kila ma sai ya hada mata da duka. Wasu</p><p>zafafan hawaye suka gangaro kan kumatunta,</p><p>daidai lokacin da yake cewa "Ko dan digo ki ka ji</p><p>son ko waye a ranki kada ki rufe min". 45... Ta</p><p>girgiza kai "Ba na son kowa Ya Abba". Cikin wani</p><p>irin yanayi ya dubeta, "Shi kenan, sai ki je ki</p><p>hakura da Sahabin a sannun kin so shi". Cikin</p><p>kuka ta ce, "Ya Abba Allah ni bana son shi, kai to</p><p>ka hada ni da ko waye mana". Ranshi 6ace ya</p><p>dubeta cikin tsawa ya ce, "Ki rufa min baki tunda</p><p>ba ki ta6a son kowa ba ki zauna da wanda ki ka</p><p>za6i zama da shi. In da kina son wani ne to da</p><p>sai in cije in tunkari su Alhaji, tunda kuwa babu</p><p>sai in ce musu me?" Ya fada mota, ya koma kofar</p><p>gidan. Koda ya tsaya tafi minti uku sannan ta</p><p>fito, yana kallonta maimakon ya wuce gida sai</p><p>kawai ya nufi gidan Maman Iman makociyarsu da</p><p>suke shiri da ita. Shima kanshi na kan sitiyarin</p><p>motar har ttsawon shudewar wasu dakiku,</p><p>sannan ya nufi gida. 27. Misalin karfe tara</p><p>Umman Bashir ta rangada sallama a tsakar gidan,</p><p>Innar su Sahabi ta amsa tare da fadin "Shigo".</p><p>Sahura ta shiga tana tambayar "Ba kowa dai ko?"</p><p>Inna ta ce "Shigo mu kadai ne". Bayan sun gaisa</p><p>ta ce "Ba ki sanni ba ko?" Inna ta ce, "Eh."</p><p>Sahura ta ce, "To ni dai tsakani ga Allah zuwa</p><p>nayi in ba ki shawara bisa ga yarinyar da danki</p><p>zai aura. Tsakani ga Allah yarinyar ba ta da</p><p>mutunci, sannan iyayenta za su mallake miki da,</p><p>don ni kaina ya faru da ni". Sahura don makirci ta</p><p>soma rishin kuka. "Dana maigidana ya ba su riko,</p><p>ina sheda miki wannan zance 'yar uwa yanzun</p><p>tsakanina da shi sai ido, sun makkale shi komai</p><p>shi yake musu, ni ko da nayi wahalar ciki da</p><p>nakuda sai na tashi a banza. To da yake an ce</p><p>ciwon 'ya mace na 'ya mace ne, shi ne nazo in</p><p>sanar da ke. Amma in kin ji haushi kiyi hakuri".</p><p>Ta yunkura zata mike. 46... Inna ta ce, "Zauna</p><p>'yar uwa, na gode. Nima fa tuni auran nan ya fice</p><p>min a rai, dama da naga shi Sahabin ya dage ne</p><p>sai kuma suka aiko gobe azo za a daura aure sai</p><p>na hakura". Kafiin Sahura tayi magana sai Sahabi</p><p>ya doka sallama, Inna ta ce "Yauwa zo nan". Ya</p><p>nufo ta "Zauna kaji ma kunnenka". Ya rage</p><p>tsawo, Inna ta ce "Baiwar Allah ya ki ka ce?" Nan</p><p>Sahura ta soma zuga sharri, ta kara da cewa</p><p>"Yaro ina ga ma za ka san dan nawa da suke riko</p><p>Abba a ke ce masa". Cikin saurin baki ya ce, "Na</p><p>san shi". Ta ce, "To dana ne da asiri suka amshe</p><p>min shi, sai dai Allah ya isa". Ya tuna irin halayen</p><p>da Abban ke nuna mishi. Yaa jinjina kai, sannan</p><p>ya dubi mahaifiyarshi "Inna to da Kawu yayo</p><p>binciken halayan iyayenta ai ana ta yabon</p><p>halinsu". Inna ta ce, "Kin ji shi ko? To bari kaji,</p><p>kwanaki ma Tasalla da ke bayan layin nan tazo</p><p>ta fadan irin wannan matsalar ban kama ba ne</p><p>don na asanta da shegiyar karya. To kuwa an yi</p><p>biyu ba zan bari ai na uku ba, don haka a daran</p><p>ta tabbatar ma da danta an fasa gobe ya wuce</p><p>gurin Badariyya a daura, su kuma in sun ji shiru</p><p>sa ba wani can". Cike da murna Sahura ta koma</p><p>gida. * Maman Iman tayi lallashin duniya amma</p><p>Ummi ta ki yin shiru, ga zazza6i tamkar wuta a</p><p>jikinta. Sai kusan sha dayan dare sannan Maman</p><p>Iman ta rako ta gida, lokacin Umma tana ta</p><p>neman layin Abba a kashe. Ta ce, "A'a sun dawo</p><p>ne yanzun ni ke neman Abba in ji suna ina ne?"</p><p>Maman Iman ta ce, "Tun dazu tana gidanmu</p><p>zazza6i da ya rufe Ummin, na bata magani ta 'ki</p><p>sha". 47... Umma ta ce "Rabu da ita kar Allah</p><p>yasa tasha, aure dai gobe babu fashim dubi irin</p><p>yanda a ka sa gidan su yaron nan wancan karon</p><p>suka kashe kudi gurin yin girki da sauransu ba a</p><p>yi bikin nan ba. Yanzun a kuma dagawa daga</p><p>lokacin da muka samu?" Maman Iman ta ce, "Ai</p><p>ba zai yiwu ba, sai dai a bi ta da lallashi". Umma</p><p>ta ce, "Mun daina lallashinta tunda ko mun</p><p>lallasheta aikin banza ne". Maman Iman ta ce,</p><p>"To Allah ya kaimu gobem bari in shiga gida sai</p><p>mun shigo aiki da safe". Umma ta ce, "To sai da</p><p>safe". Ummi tana shiga dakin Umma taga baki</p><p>kwakkwance, ta ce a ranta "Mayu, don kalata sai</p><p>da wasu suka dada zuwa". Tana fushi da</p><p>tsohuwa amma duk da haka dakin ta nufa, ta</p><p>kwanta a bayanta don ita tuni tayi bacci. Nishin</p><p>kukanta ya farkar da Tsohuwar, kala bata ce</p><p>mata ba, sai sauka tayi ta shimfida a kasa ta</p><p>kwanta, sannan ta ce "Aniyarki ta biki Takwara".</p><p>Wannan dare gurin Ummi da Abba wani dare ne</p><p>mai cike da bakin ciki da tashin hankali, ko Sarkin</p><p>sata bacci ranar bai samu galaba gare su ba.</p><p>Dukkan su a kan kunnansu aka kira sallar farko,</p><p>Abba ya mike cikin rangaji, jin jikinshi yake yi</p><p>tamkar iska ta dauke shi saboda rashin karfi.</p><p>Ruwa ya diba ya watsa, wanka sannan yayo</p><p>alwala don yin nafila, addu'a yake Allah yasa</p><p>hakan shi ne mafi alkairi a gare shi. Da ya dawo</p><p>Masallaci kwanciya yayi amma baccin ya ki bai</p><p>fita ba sai kusan takwas. Koda yaga Bishira</p><p>zaune a tsakar gida tana karatun littafin sam bai</p><p>ji haushin rashin zuwanta gidan su Umma ba.</p><p>Nashi ganin duk wanda yaje tamkar yana murna</p><p>ne da rasa Umminshi da yayi, ita kuwa da gadara</p><p>ta fito don ya ji haushi, bata je ba yana son sanin</p><p>halin da Ummi take ciki amma ba ya ra'ayin</p><p>zuwa gidan su Umma. Shagonshi ya bude ya</p><p>shiga ya dan zauna har zuwa tara, yana kallon</p><p>lokacin da Jama'a suka yi ta dafifin shiga layinsu</p><p>don halartar daurin auran. Kurum sai ya samu</p><p>kansa da tare dan Aca6a ya hau ba tare da ya</p><p>shaida masa inda za su ba. Koda dan Aca6an ya</p><p>tambaye shi ce masa ya yi mu je. 48.... Ita ko</p><p>Ummi ranar zaune tayi sallah ta koma ta kwanta,</p><p>duk kaikawon ai da 'yan shewe-shewen da jama'a</p><p>dangi da makota tana jin su. Sai dai makoshinta</p><p>ya bushe ga zufa da ta rufeta, duk da yanayin ba</p><p>na zafi ba ne. Karfe goma daidai shi ne lokacin</p><p>daurin auran, layin ya dinke da jama'a, Alhaji</p><p>ranshi a dame don bai ga Abba ba. Ya kalli Alhaji</p><p>Karami, "Ina Abba ne?" Alhaji Karami ya ce,</p><p>"Abokan aikinshi ga su can sun zo ba a ganshi ba</p><p>son daukan daurin auran". Alhaji ya ce, "Su dauka</p><p>mana nasan yana nan tafe". Har sha daya ana ta</p><p>jiran 'yan gidan Ango shiru, su Alhaji suka tashi</p><p>dan aike gidan don a ce ana jiran wakilan ango.</p><p>Amma sai a ka dawo musu da sako wai sun fasa,</p><p>kalmar da ta rikita Alhaji ta tashi hankalinsa. Ga</p><p>jama'a an tara, Alhaji Karami ya ce wadannan</p><p>akwai kananan mutane." Daidai lokacin da muryar</p><p>wani Maroki ta ratso dodon kunnuwansu da</p><p>cewa, "Alhaji ku hanzarta Jama'a sun gaji da</p><p>jira". Alhaji ya dubi Alhaji Karami, "Aminu a daura</p><p>da Bashir". Alhaji Karami yayi shiru, can ya ce "A</p><p>daura da Abba". Alhaji Babba ya ce, "Ina zuwa".</p><p>Ya fito daga dakin Abba na da inda suke yin</p><p>shawarar, ya ratsa mutane ya ce a yi masa</p><p>magana da Suwaiba. Umma ta fito daga kicin ta</p><p>same shi a dakinsa yana tsaye yana kai-kawo ta</p><p>ce lafia? Ya ce Gidan ango ne shiru, an bisu sun</p><p>ce sun fasa. To shi ne na ce me zai hana a daura</p><p>da da Bashir? 49... Umma ta ce a daura da Abba.</p><p>Ya ce, "Haka ma Aminu ya ce. To ni ban ga</p><p>Abban ba ma, amma bari muje Allah yasa hakan</p><p>shi ne mafi alkairi". Take a nan a ka daura auren,</p><p>Habiba da Idris Alhaji Babba ya kirgo sadaki ya</p><p>mika. Alhaji Karami Waliyinta ya amsa, mutane</p><p>na ta al'ajabin yanda lamarin ya sauya. Umman</p><p>Bashir kuwa Bashir din ne ya shiga gidan hankali</p><p>a tashe yana fada mata cewa da Abba a ka</p><p>daura. Nan ko ta hau bala'i da zage- zage. Ummi</p><p>ko tunda ta jiyo guda na alamta mata an daura</p><p>aure, sai ta birkice ta shiga kowa da</p><p>numfashinta. Fati da ke kusa da ita tana</p><p>lallaminta ita ce ta kwala ihu, ba shiri aka yi</p><p>asibiti da Amarya. Fati ta shiga gidansu da kuka,</p><p>nan ta taras Ummansu tana bala'i sai lokacin ta</p><p>ji da Abba a ka daura. Ta ce da Ummar su to</p><p>menen ba shi ke nan ba? Umma ta hau zaginta</p><p>tare da cewa, kar ki ga kin yi aure sai in miki</p><p>shegen duka, Fati dai ta fice ta bar gidan. Sam</p><p>Umma bata ji dar da ciwon Ummi ba, wannan</p><p>karon don haka ma bata bi su Asibiti ba, da</p><p>kanwarta Saratu a ka tafi. Likitan yayi ta fada</p><p>lokacin da yake yi mata allurai, a kuma bata gado</p><p>Umma ci gaba tayi da kula da bakinta. Yayin da</p><p>zuciyarta take fara kar, ta sani kuma tayi Imani</p><p>Allah ba ya tozarta addu'ar bawansa, matsawar</p><p>bawan yayi hakuri tare da dogewa. Haka nan in</p><p>baka samu biyan bukatarka nan duniya ba lallai</p><p>gobe kiyama zaka tarar da abinka. Ta jima tana</p><p>rokon Allah yasa 'ya'yan nata biyu su zam miji</p><p>da mata su haifa mata jikoki masu albarka. Suma</p><p>su Alhaji suna ta sallamar baki sai dai yanzun ba</p><p>wanda ya damu ya gani irin Abba. Fatanshi Allah</p><p>yasa Abban yayi farin ciki da wannan hukunci da</p><p>suka yanke. Salis kuwa burinshi ya zama shi ne</p><p>mutum na farko da zai wa Abba wannan albishir</p><p>sai dai ya kira layin Abba sama da sau hamsim</p><p>bai daga ba. Abinda bai sani ba shi Abba ma gida</p><p>ya bar wayar, haka suka gama dauke-daukensu</p><p>yayi hira da Jama'a da kuma iyayen Ango da</p><p>Amarya don jin ta bakinsu a kan yanda auren ya</p><p>juye zuwa na zumunci. Haka nan suka tafi ya</p><p>samu abin sawa a Taskar labarai, burinshi yanzu</p><p>shi ne ya je ya nemo angon. 28 50.....Abba kam</p><p>kofar dan Agundi ya yada zango gidan su Mansir</p><p>abokinsu, shi ne kurum cikin abokan Abba da bai</p><p>yi aure ba. Yana isa kofar gidan Mansur na</p><p>fitowa za shi daurin auren, wani dan layinsu a</p><p>Gwammaja suka gaisa. Abba ya ce "Bari in dan</p><p>kwanta a dakinka". Mansur cikin mamaki ya ce,</p><p>Lafiya? Abba ya ce lafiya lau. Yana kwance dakin</p><p>Mansur idanunshi suna kallon agogo, zuciyarshi</p><p>tana raya yanzun abar sonshi ta zama matar</p><p>Sahabi. Sai dai bai san dalilin da bugawar</p><p>agogon karfe sha daya daidai tazo gwame da</p><p>bugawar zuciyarshi ba. Zuciyarshi ta fada mishi</p><p>cewa wannan alamu ne na an kammala daurin</p><p>auren. Wasu hawaye ne suka biyo ta gefen</p><p>idanunshi suna sauka a kan filon. Yini zur yana</p><p>dakin in lokacin sallah yayi sai ya fito kofar dakin</p><p>yayi alwala har duhun Magriba ya gabato. Ya fito</p><p>tare da kulle dakin, don Mansur bai dawo ba,</p><p>kuma dama ya ce ba zai dawo da wuri ba. Gidan</p><p>nashi ba kowa lokacin da ya shiga, kai tsaye</p><p>dakinshi ya wuce, ban da idanunshi da suka kai</p><p>kan wayarshi ya manta ma yana mallakinta. Ya</p><p>kai hannu ya dauka, bai ji mamakin yawan</p><p>missed calls din da ya gani ba, kiran Salis ya</p><p>sake shigowa. A kasale ya daga, muryar Salis ta</p><p>ratsa dodon kunnanshi, fadi yake yana</p><p>maimaitawa Ango- Ango. Abba cikin sanyin</p><p>murya ya ce "Salis ya haramta a gare ka ka</p><p>zolaye ni a halin da nake ciki. Sanin kanka kai</p><p>kadai ne kasan yanayin da nake ciki". Salis cikin</p><p>zumudi ya ce, "Kana nufin ba ka sani ba?" Abba</p><p>ya ce, "Me?" Salis ya ce "To bani goron albishir in</p><p>sanar da kai". Abba ya ce, "Don Allah Salis kada</p><p>ka min karya". Salis ya ce, "Ina rantsuwa da</p><p>wanda ya yi mu Ummi matarka ce, da kai a ka</p><p>daura. Ina ka shige lokacin da al'amarin ya canza</p><p>salo?" Abba ya mike zumbur. "Ka fa rantse Salis!"</p><p>cikin dariya Salis ya ce, "Wai har yanzun ba ka</p><p>sani ba? To ka aje min goron albishir dina". Abba</p><p>yasa hannunshi a baki ya gatsa, zafin da ya ji ne</p><p>ya tabbatar da mishi da ba mafarki yake ba. 51...</p><p>Ai sai ya katse wayar ya zube yayi sujjada ya fita</p><p>tsakar gida yana furta "Alhamdulillah." Ruwa yaja</p><p>ya watsa ma jikinshim sannan ya yi alwala.</p><p>Sabuwar shadda ya saka kalar kunkumadi, ya</p><p>fesa turare sama da kala hudu. Hula da takalmin</p><p>bakake, ya nufi Masallaci, daga can za shi gidan</p><p>su Umma don jin karin bayani. Bayan sun idar da</p><p>Sallah, mutane suka yi ta masa murna, nan ya</p><p>hadu da su Alhaji kawai yau sai ya samu kansa</p><p>da kunyar Alhajin. Alhaji ya ce, "Ubana ina ka</p><p>shige duk yau?" Ya rasa me zai ce, sai in-ina</p><p>"Am...na kwanta ne bana jin dadi". Alhaji yayi</p><p>'yar dariya, "Kai dai ka ce kana taya kanwarka</p><p>fushi don mun ce ba zamu daga aure ba, to ba</p><p>mu daga ba amma Allah cikin ikonsa ya sauya</p><p>lamarin". Abba tamkar bai san komai ba, ya ce</p><p>"Alhaji me kuma ya faru?" Alhaji Karami ya</p><p>karaso gurin su yana cewa, "Kai Abba ina ka</p><p>shige ne?" Abba ya dube shi "Nan dan Agundi na</p><p>shiga". Alhaji ya ce, "Oho, shi yasa aka yi ta</p><p>nemanka. To ka ji kuma yadda lamari ya sauya</p><p>ko?" Alhaji Babba ya amsa tare da cewa, "Shi ne</p><p>nake massa bayani, wato Abba iyayen yaron nan</p><p>Sahabi muka yi ta jiransu su zo gurin daurin</p><p>aure, wai ashe su sun fasa. Amma ba su shaida</p><p>mana ba har bin su fa nasa aka yi, gashi mun</p><p>tara jama'a kawai sai Aminu da Ummanka suka</p><p>ce a daura da kai, da ni na ce a daura da Bashir".</p><p>Dadi ya lullu6e Abba irin wanda bai ta6a ji ba,</p><p>Alhaji ya ci gaba da cewa, kayi hakuri mun kara</p><p>maka nauyi ba tare da mun ji ra'ayinka ba". Abba</p><p>cikin matukar murna ya ce, "Haba, ai ko ba 'yar</p><p>uwata ba ku ka daura min aure da ita zan aminta</p><p>bare jinina. Nagode". Sun ji mamakin yanda Abba</p><p>yayi murna, duk da sun san biyayya irin tashi ba</p><p>zai 'ki ba, tare suka rankaya gidan su Umman, so</p><p>kurum yake yaga Ummi. Ba mutane sosai, don</p><p>haka har ciki ya kutsa, sai dai suna hada ido da</p><p>Umma sai ya ji nauyinta, ta fada da fara'a. "Ina</p><p>ka shige Abba?" Yayi dan murmushi, ta ci gaba</p><p>"Sai kuma ka ji yanda abu ya kasance?" Ya ce,</p><p>"Na ji Umma, Allah yasa haka shi ne alkairi". Ta</p><p>ce, "Amin, Insha Allahu". Tamkar ya tambayi ina</p><p>Ummin, amma ya kasa. Umma ta ce "A baka</p><p>abinci ko?" sai lokacin ya tuna da batun abinci,</p><p>amma baya gabanshi, ya ce "Na koshi Umma".</p><p>Ta ce, "To ga na 'yan asibiti can in kayi isha'i".</p><p>Da sauri ya ce "Wa ke asibiti kuma?" Ta ce,</p><p>"Ummi ce, ko 'yan daurin auran ba su watse ba</p><p>don ka ji yarintar nan ta hau farin suma don</p><p>haushi ko leka su ban yi ba. Tana can it da</p><p>Saratu sai Tsohuwa da ta matsa yanzun Alhaji</p><p>Karami ya kai ta". Jikin Abba ya yi sanyi, kenan</p><p>tsabar rashin sonshi ne ya saka Ummi suma? Ya</p><p>ce Umma bani abincin asibitin. Sai da yaje</p><p>gidanshi ya dauko dan mukullin motar, a</p><p>zuciyarshi yana tambayar kanshi ina kuma</p><p>Bishira tayi ne? Zai bude motar kenan muryar</p><p>Bashir ta dakar da shi, "Kaci nasarar samun furen</p><p>zuciyata, amma ka sani ka kulla abota da rashin</p><p>zaman lafiya a novels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 7</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 7</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:33</p><p>kulla abota da rashin zaman lafiya a gidanka". *</p><p>52..A fusace abba ya dubeshi"xansa yan sanda</p><p>su rufe min kai inhar zaka cigaba da kiran matata</p><p>da furen zuciyarka,rashin zaman lfy kake cewa?</p><p>An dade ba'ayi yaki abgdn ba kullum,bashir yace</p><p>oho dai ni zanta zuga umma abba yaja tsaki</p><p>tareda shigewa motarshi. Bashir yashiga gdnsu</p><p>inda su ummanshi dasu bishirabke zaune jugum</p><p>jugum tamkar masu zaman makoki,bishira tabi</p><p>bashir da kallo lkcn dayace ga ya abba ya can a</p><p>waje yashiga mota ya kure wanka,kila ma asibiti</p><p>zaije ana fada maku yanaso kuna wani tilasta shi</p><p>akayi,bishira cikin dasahhshiyar murya tace aiko</p><p>da bala'i don ko bazan yarda ba,umman bashir</p><p>tace sha kutuminki bishira,barni dasu zan</p><p>maganinsu, bishira tafita fuu,amma saidai. Kafin</p><p>ta isa gurin motar tuni ya, Cilla yabar mata</p><p>hayaki. Da innna saratu kanwar umma ya soma</p><p>cin karo a asibitun suka gaisa,tace ashe kuma</p><p>haka abu ya zama? Yace eh"nima dana dawo</p><p>dazu nasamu lbrin,tace Allah yasa hakan shine</p><p>mafi alkhairi,abba yace ameen inna,ya mai jikin?</p><p>Tace dasauki,yace bacci take? Tace a'a ta farka</p><p>tun kusan karfe uku,koda fatima ta fada mata</p><p>yanda abubuwa zuka zama,tayita yan koke</p><p>kokenta,gaban abba yafadi****tabbas ummi ba</p><p>son shi take ba inba hka ba meye na kuka? Ya</p><p>kalli inna bari in karasa,tace to kaje tshuwa na</p><p>ciki,a ranshi yace jaraba road,yasan dai ko yane</p><p>sai tshuwa tayi mishi surutu,yana tura kofar</p><p>tareda salama suka hada ido da ummi,sun kure</p><p>juna da kallo,kowanne nason ya fahimci ya dan</p><p>uwansa yadauki abin"tshuwa ta katse su dacewa</p><p>to zakin fama sai ynz kaga daman zuwa? Ya</p><p>dubeta eh" ai eh ace? To me kikeso ince,tace to</p><p>madalla ai na dade da sanin halinka,kuma da ace</p><p>iyayenku sunyi shawara dani lallai da baza suyi</p><p>wanna hadin ba Domin na tabbata kai zaka</p><p>karasa takwara don baka kaunarta, haushi ya</p><p>cika abba abba yana kallon tsohuwa yana tuna</p><p>amsar data dace da ita, ummi kuwa tsura mishi</p><p>ido tayi tana son jin me zaice,yace kamar kin</p><p>sani,tace ahaf shiyasa tausan yar nan kebani</p><p>tausayi, ta soma matsar ido,yace nima yakamata.</p><p>ki tausayamin tnda cusa min ita akayi,ummi</p><p>takoma ta kwanta lakwas tareda hakikancewabl</p><p>kalaman abba sako ne zuwa gareta,matar cushe</p><p>kuma bata daraja,to inaso kasan wani abu</p><p>guda,duk randa naji wani abu daidai da</p><p>wulakanci, toba kaiba har iyayenka saisun san</p><p>naje makura. 52..Dazun nake gaya masu basun</p><p>hada kai sun kulla auren nan ba,duk randa suka</p><p>kuskura sukazo min da batun warwareshi saina</p><p>basu mamaki,abba ya tabe baki tareda kallon</p><p>ummi wadda takasa jurewa tashiga rera kuka,ya</p><p>isa gaban gadon,"jikin ne ummi? Tayi shuru,kinci</p><p>abinci? Nan ma ta share,sai kurum ya nufi wurin</p><p>likitan zuciyarshi na kuna bako shakka kukan kin</p><p>shi ummi keyi,sun zo da likita ya shiga yimata</p><p>fadan kukan da takeyi,a cewar likitan kukan illa</p><p>ne ga lafiyarta,tshuwa ta kalli likita dan nan dole</p><p>ta koka a dauke ka ahadaka da wanda baya</p><p>kaunarka"abba cikin takaici yace subhanallla! Don</p><p>Allah tshuwa kibarni inji da abinda ke</p><p>gabana,tace ina ruwana da abinda ke</p><p>gabanka,likita yayi dariya yace mama yakamata</p><p>ki koma gd haka,abba yace bari inkaita</p><p>indawo,tace ban binka da can dani kazo? Abba</p><p>yace nahuta,likita yayi dariya,da kyar suka lallaba</p><p>tshuwa ta tafi da inna saratu,abba yaja kujera ya</p><p>zauna gaban gadon,bayan fitan likita Idanu ya</p><p>zuba ma ummi,godiya yake ma Allah a zucin shi</p><p>daya amsa addu'ar shi yabashi abar sonshi,itako</p><p>kai ta dukar a ynz takasa tantance kukan farin</p><p>ciki take ko takaicin kalaman ya abbanta? Wani.</p><p>Dan zare dake jikin hijabinta take wasa dashi,a</p><p>zuciyarta kuma tambayoyi ne da fuska data jefa</p><p>masa su,ya katse ta kinci abinci? Ta daga kai</p><p>alamun eh" yace to yakamata ki dangana da</p><p>kukan haka kisani ni kaina da ina nan bazan bari</p><p>su alhji su daura maki aure da wanda bakiso ba.</p><p>53..Da sauri ta kalleshi,yace. amma inkin yi hkr</p><p>zansame su zamu san yadda zamuyi,ta lumshe</p><p>ido a zuciya tace tab! Ai rabamu sai mutuwa,zan</p><p>juri duk wani ki dazan gani daga gareka,ya</p><p>katsxeta kina zance a zuci fadi abnd kikeson</p><p>cewa,tayi tagumi tareda kallonshi,ya abba yakanfi</p><p>dacewa sa dan sanda ne ba dan jarida ba,sbd</p><p>yanada saurin nazartar mutum,to amma meyasa</p><p>yakasa gane tana son shi? Yayi murmushi,zanso</p><p>inji abnda kikeb saqawa azuciyarki ko kinn samo</p><p>mafita ne? 29. Zancan mafitar nan tana bata</p><p>haushi, don haka saita canza zancen da cewa,</p><p>tambaya zan maka guda biyu, ya dan yi shiru.</p><p>Nazari yake, wace irin tambaya zata masa? Kila</p><p>zata tambaye shi ne ko zai amince ya sahale</p><p>mata auranshi, ya dubeta amsa daya zan ba ki in</p><p>kin yarda, ta ce To dama zance ne ya ka ji</p><p>lokacin da labarin sauyawar lamari ya zo gareka?</p><p>Ya kura ta da ido, ya tambayi kansa a zuciya, me</p><p>yasa take son ji@ yayi dan yake, yi tambayarki ta</p><p>gaba, ta tsura mishi ido. Yanzun yaya za ka yi da</p><p>maganar Zainab? Ya yi 'yar dariya, wacce amsa</p><p>ki ke so a ciki? da sauri ta ce ba ni wannan</p><p>amsar. Ya ce, "Kiin manta ni mijin mace hudu ne?</p><p>Ta zaro ido kamar ya ya? Ya yi kokarin danne</p><p>dariyarsa, sakamakon yanda ya ga ta zarana. Ya</p><p>ce, "Ina nufin bayan Zainab har da wata, Ummi ta</p><p>hade rai sannan ta zame ta kwanta cike da dana</p><p>sanin tambayar. Abba ya yi mamakin kishin</p><p>Ummi gare shi, ita da ba sonshi take ba? Ko da</p><p>yake an ce mace ko bata son namiji in dai mijinta</p><p>ne ta tsani ta ganshi da wata. Duk da haka ya ji</p><p>dadin yanda ta nuna kishinta a kanshi, da ya tuna</p><p>da Bishira ya ce tab, wata fitinar tana can tana</p><p>jirana yau. Sam Ummi bata kara magana ba, shi</p><p>kam Abba waya ma yake tayi Inna Saratu ta</p><p>dawo, don haka ya mike ya kalli Ummi. Zan tafi</p><p>ba tare da ta dago ba ta ce, sai anjima. Ya tafi</p><p>yana waiwayonta bayan ya wa Inna Sallama. Kin</p><p>shiga gidanshi ya yi sai kusan sha biyu a nufinshi</p><p>lokacin Bishira tayi bacci, sannan yaje ya sai</p><p>mata wayar da layi don yasan tana son waya.</p><p>Kudinshi kenan ma ya kwashe ya sai mata, bai yi</p><p>wani motsin kirki ba don kada ta farka, ya bude</p><p>dakinshi ya shiga ya fito yana jan ruwan wanka</p><p>kenan ta fito daure da zani a kirji. Jikinta ko dan</p><p>kwali babu, gaban Abba ya fadi ta ce, "Munafukin</p><p>Allah, annamimi dama ashe abinda kuke shiryawa</p><p>kenan? To ka sani dole kasa ke ni don ba zan iya</p><p>zama da Ummi ba, Allah ya kiyaye in hada miji da</p><p>wannan 'yar yarinyar, tunda kai baka ga ai baya</p><p>ba". Ya sassauta murya, "Haba Bishira, wannan</p><p>abin fa Allah ya kaddaro za a yi haka, matar</p><p>murtum kabarinsa. Ta ce, "To wannan ajalinka ce</p><p>tunda wancan ya ki shi ne kai a ka cusa maka.</p><p>Ya bar jan ruwan ya kama hannunta suka nufi</p><p>dakinta, tana ta masifa. Ya ce, kibar maganar</p><p>yanzu dare ne duk makota suna ji za su yi, kuma</p><p>banga bain da zai sa ki daga hankalinki ba. Kin</p><p>san dai ina sonki ko? Ta yi shiru tana kallonshi,</p><p>ya ce ina zuwa. Yaje dakinshi wayar ya dauko</p><p>mata, ga wayarki. Ta ce, "Eh don ka toshe min</p><p>baki k? to bana so, ita wa ya san abinda ka sai</p><p>mata? Ya ce, ya ki ke wannan maganar? Ban sai</p><p>komai ba ko lefe ma tukunna. Ta mike tare da</p><p>jefa mishi kwalin wayar, Ga tsiyarka nan</p><p>matsiyaci, dole ka saka min da haka, tuni a ka</p><p>gaya min tsiyar talaka na tafe. Haushi ya kama</p><p>Abba ya dauki wayarshi ya tafi ya maida yazo ya</p><p>dau ruwanshi yayi wanka, yana jiyo kukanta da</p><p>duk zage-zagen da take yi. Shi kam katifarshi ya</p><p>fada tare da rungume fito yana tunanin ranar da</p><p>Ummi zata maye gurbin filon. 30. Har an tada</p><p>sallah a Masallaci lokacin da ya farka, ya jima</p><p>bai yi irin wannan baccin ba, da hanzari ya fito</p><p>ya nufi ban daki don alwala. Abin mamaki Bishira</p><p>ce zaune kan kujera a kofar dakinta, matar da sai</p><p>ta kai takwas bata farka ba, amma yau bala'in</p><p>kishi ya hanata bacci. Ta ce, "Eh na fito a ba ni</p><p>takardata na gama zama da kai, ko in da take bai</p><p>kalla ba ya ci gaba da abinda ke gabanshi, ya</p><p>nufi Masallaci yana jinta tana ina nan ina jira ba</p><p>zan zauna ba. Haba, gaskiya naji na tsani</p><p>yarinyar ashe mijina zata aura, tsaki ya yi ya</p><p>bude gidan ya fice. Har gari ya soma haske yana</p><p>cikin masallacin, tunanin zuwa gidan yake, daga</p><p>karshe dai ya fita da niyyar zuwa gidan</p><p>Ummarshi. Wata zuciyar ta tambaye shi da cewa,</p><p>tsoron ta ka ke ji ne? Kar ka zama soko dai a</p><p>gidanka. A fili ya furta cewa, tunda na bita ta</p><p>lalama ta ki, bari in koma mata ta zafin, ida din</p><p>me? Sai ya sauya hanya zuwa gida rai 6ace,</p><p>fuska daure ya shiga gidan, tana ta kai-kawo a</p><p>tsakar gida. Ta dumfaroshi sai ka ce sabon</p><p>kamun hauka, daga ganinshi ta dinfaroshi. "Ka</p><p>ban takardata ba ni ba zama da kai, tafiya zan</p><p>yi". Ya harareta "Sai da takarda za ki tafi? Lallai</p><p>ba ki ji tafiyar ba. To ba zan bada takarda ba,</p><p>don ki sani, sai dai in kotu za ki kai can Alkali ya</p><p>baki". Ta nufo shi da zummar shako masa kwala,</p><p>ya ce Kina ta6a ni sai na zane ki, in yaso ki tafi</p><p>da hujja". Ganin yanda Abba ya bude mata wuta</p><p>sai taja baya, Ka isa ka zane ni, ai da ka san ka</p><p>dake ni, don ko sai ka sha dauri. Ya nufi dakinshi,</p><p>wanka ya fito yayi sannan ya yi shirin tafiya aiki,</p><p>amma har lokacin tana nan, ga 'yarta ta tashi</p><p>daga bacci sai kuka take yi. Ta dauke ta ta goya,</p><p>ta shiga dakinta can kuma ta sauke 'yar tasa</p><p>kaya ta fito ta dauraye fuska da kafa ta goya 'yar</p><p>tasa kaya ta fito taja kofar tana fadin." "Tafiya</p><p>zan yi". Ta fito ta same shi yana goge gilashin</p><p>motarsa na gaba. Ta ce, Tafiya zan yi sai an</p><p>kar6ar min hakkina". Murmushi ya saki, sannan</p><p>ya kalleta, ta ina za ki bi in rage miki hanya? Ta</p><p>dawo ta duki motar, Ba zan shiga wannan</p><p>gwanganin motar ba, kai ne bakon mota. Kafi</p><p>kowa sanin daga gidan da na fito, ko motar zuwa</p><p>cefanen gidanmu tafi wannan tsarri. Ya ce.</p><p>"Gurinki ko? Ni ai bani da wadda ta fita tunda</p><p>bata gidan naku nike hawa ba. Sannan kuma</p><p>tunda ba za ki zo in rage miki hanya ba shi</p><p>kenan sai naga sammaci. Ya shiga motar ya</p><p>tasheta yayi gaba, ba tare da ya saurari abinda</p><p>take cewa ba. Ta isa gidansu cikin tashin hankali,</p><p>Hajiya Zainu ta saurare ta tsaf, sannan ta ce "Kin</p><p>dai ga abinda a ke fada miki, kina ganin ba zai</p><p>faru ba ke so ya rufe miki ido, to yanzu an zo</p><p>gurin. Bishira ta ce, "Ai na gane komai yanzun,</p><p>Momy nayi nadama. Ta ce, "To zan tsaya miki</p><p>matsalata Babanku, yana nan a gari na kuma san</p><p>za su zo iyayen Abba. Amma wannan karon shi</p><p>kanshi Babankun zan iya ja da shi, Bishira taji</p><p>dadi sosai, don kuwa duk son da ta ke wa Abba</p><p>yanzun kishi yasa ya koma 'ki. Gidansu Umma</p><p>yaje a gurguje suka gaisa, ya kwashe su da Alhaji</p><p>da Alhaji Karami zuwa asibiti, a motar nema ya</p><p>ke fada musu cewa Bishira ta tafi gidansu Umma</p><p>ta ce a kan me Abba, me ka mata? Ya ce, "Ban</p><p>mata komai ba, ya fada musu duk yanda aka yi.</p><p>Alhaji Karami ya ce, Sahura ke zugata, itama ai</p><p>kwana tayi bala'in. Don haka kada kaje bikonta,</p><p>Alhaji Babba ya ce, "Ba za a yi haka ba, da dare</p><p>kazo muje, Abba ya ce To. Sun isa asibitin tana</p><p>wanka, sun gaisa da Inna Saratu ta fada musu</p><p>tana wanka, sannan likitan ya sallame su amma</p><p>sai sha biyu za su tafi gida, lokacin an karasa</p><p>mata allura. Abba can baya ya tsaya kusa da</p><p>kofar shigowa ya jingina da bango idanunshi suna</p><p>fuskantar kofar bayin, matuka ya kosa yaga</p><p>Ummi. Sanye da hijabi da zani daurin kirji ta fito,</p><p>da Abba suka soma hada ido, bai ta6a kallon</p><p>Ummi da sha'awa ba sai yau. Kamshin turaren</p><p>Abba ya ratsa ko'ina a dakin, ta zare idanunta</p><p>daga nashi, ta kalli Ummanta sannunku Umma.</p><p>Suka ce Yauwa. Ta gaida su sannan ta zauna</p><p>bakin gado tare da sunkuyar da kai, Alhaji Karami</p><p>ya ce, "Uwata jiki kuma ya yi sauki ko? Kanta na</p><p>kasa ta ce, Eh, ta kasa dago kanta, gani take</p><p>Abba ya cika dakin. Abban ya ce, "To ni zan tafi</p><p>don lokacin aikina ya kusa, Alhaji zamu je ne in</p><p>sauke ku? Suka ce To, Umma ta ce In an yi mata</p><p>Allurar anjima ma nemo mai Taxi. Alhaji ya ce, To</p><p>shi ke nan. Umma ta dubi Ummi ba za ki gaida</p><p>Yayan naki ba? Ta saci kallon Abban tare da</p><p>cewa, Au, ban ganshi ba. Ina yini? Ya ce, Umma</p><p>me yasa za ki rokar min gaisuwarta? Inna Saratu</p><p>ta ce, Kai Ummi da iya shege take, ina kallonta</p><p>shi ta fara kare ma kallo sannan ta kalli kowa</p><p>amma wai bata ganshi ba. Su Alhaji dai 'yar</p><p>dariya suka yi sannan suka fita, Abba ya bi su</p><p>tare da yi wa su Umma sallama. * 31. Bayan</p><p>fitarsu, Umma ta dubi Ummi fuska daure, ina</p><p>fatan baki nuna damarar nuna kiyayya ga Abba</p><p>ba ne? Ummi ta sunkuyar da kai, a ranta ta ce,</p><p>"Kin ji Umma da wani zance, ai ina zaton nafi</p><p>Mahaifiyarshi sonshi ma bare ku. "Amma a fili sai</p><p>ta ce, To Umma shi ma fa Ya Abban bai ce yana</p><p>sona ba, Umma ta ce Saratu ji ta da wani shirme.</p><p>Ina ce ita ce zata janyo ra'ayinshi gareta? Inna</p><p>Saratu ta ce, Kwarai kuwa, ta hanyar ladabi,</p><p>biyayya da girmamashi, musamman shi da ke da</p><p>matsalar mata. Ummi ta ce, Kuma ina tsoron</p><p>masifar matarsa ba dai guri daya zamu zauna ba</p><p>ko? Umma ta ce ina ruwanki da matarsa?</p><p>Sannan in ba ku zauna guri daya ba haya zai</p><p>kama? Umma ta ce ina ruwanki da matarsa?</p><p>Sannan in ba ku zauna guri daya ba haya zai</p><p>kama? Kada ma in ji kin kuma zan nan, Ummi dai</p><p>tayi shiru. Da dare Alhaji ya tasa Abba zuwa</p><p>gidan su Bishira, zuwan su ne ma Alhajin yasan</p><p>'yarshi tayo yaji, cikin 6acin rai ya kira wayar</p><p>Hajiya Zainu ya ce su zo ita da Bishira. Ba tare</p><p>da ya jira amsarta ba ya aje wayar, ba tare da</p><p>yasan abinda ya faru ba ya shiga ba su hakuri.</p><p>Hajiya Zainau taje dakin su Bishira ta kira, suka</p><p>nufi sashen Alhajin tana mitar cewa munafukai</p><p>sun zo kenan, ai za'ayi ta bari muje mu ji. Suna</p><p>shiga Alhajin ya kalli Bishira, "Me ki ka zo min ki</p><p>yi a gida? Ta ce, Daddy cin amanata ya yi, aure</p><p>fa ya yi da yarinyar da suka tsane ni. Alhajin ya</p><p>daukin da ke gabanshi na plastik ya jefe ta da</p><p>shi, auren shi ne cin amana don uwaki? Hajiya</p><p>Zainu ta ce, "A'a Alhaji, zan cen gaskiya a duba</p><p>hakkinta itama, ya ya za a dau 'yar da bata</p><p>kaunarta, iyayenta basa kaunarta a ba shi.</p><p>Sannan ta yi magana ya hauta da zagin iyaye?</p><p>Ya ce, "Ke yi min shiru ban tambaye ki ba". Ya</p><p>kalli Abba, Ya abin ya faru? Ban ji ta bakinka ba?</p><p>Nan dai Abba ya fadi komai har ta taho, daidai da</p><p>cewa tazo ya rage mata haya da abin da ta ce</p><p>duka. Alhajin ya yi tsaki ya dubi Alhaji Babba, irin</p><p>wannan ai ba a biyo su, tayi ta tafiya sai dai</p><p>nima in ba zata koma gidanta ba, to ba gidana</p><p>ba. Ya zura hannu cikin aljihu ya ciro rafar 'yan</p><p>dari bibbiyu, Ga shi Abba, dama nayi maka</p><p>alkawarin baka sadaki duk lokacin da ka nemo</p><p>aure. 57..... Abba ya ce, "A'a ka bar su ai an riga</p><p>an yi. Mahaifin Bishira ya ce, "Ni nayi alkawari.</p><p>Suka yi godiya. Ya kalli Bishira, Ko ki bi mijinki,</p><p>ko ki bar gidana. Hajiya Zainu ji take tamkar ta</p><p>shake Abba. Ta ce, "Haba Alhaji, gaskiya ban</p><p>yarda da wannann hukuncin..." Ya katse ta da</p><p>cewa, Ke! Da Allah fita anan. Su Abba suna shiga</p><p>mota Bishira na fitowa da kukanta, dole ta zo ta</p><p>shiga motar. Alhaji Babba ke ta bata baki har</p><p>suka kai gida, shi kam Abba da suke sauke Alhaji</p><p>ya yi nasu gidan, suna shiga ta soma zantuka. Ba</p><p>za ka ta6a samun kwanciyar hankali ba a gidan</p><p>nan har abada, ba dai ka matsa an dawo da ni</p><p>ba? Abba ya yi murmushin mugunta, ai ni</p><p>wannan yajin naki naji dadinsa, gashi har na</p><p>samu gudunmawa, kin ga sai naje kasuwa in</p><p>soma darzo wa Amarya zannuwan lefe. Ya nufi</p><p>dakinshi ya barta nan tsaye tana zage- zage,</p><p>lefen banza, in ma uban lefe ne kai da ita sai na</p><p>koya musu hankali. Kusan goman dare Ummi</p><p>tana kan doguwar kujera, addu'a take yi Allah</p><p>yasa Abba yazo ta ganshi kafin tayi bacci. Can</p><p>kasan zuciyarta kuma kishi ne don tasan sun je</p><p>gidansu Bishira ne biko ganin Alhaji ya shigo shi</p><p>daya sai ta debe tsammani da zuwanshi. A ranta</p><p>take raya cewa yanzun haka suna can suna cin</p><p>soyayyarsu, kamshin turaren shi ne ke mata gizo</p><p>a hanci. Amma sai kunnuwanta suka tsinkayi</p><p>sallamarshi, a hankali tamkar ba ya son a san ya</p><p>shigo. Umma tana ciki? Tambayar da ya yi kenan</p><p>ba tare da ya jira ta amsa sallamar ba, ta tashi</p><p>zaune da sauri a'a tana gurin Alhaji. Ya shigo ya</p><p>zauna ta ce, "Sannu da zuwa". Ya amsa yana</p><p>kalonta, ta sunkuyar da kai, gabanta ke wata irin</p><p>faduwa. Shi kam ji yake tamkar ya manne ta a</p><p>jikinshi, sai dai yana jin nauyin hakan tunda ba</p><p>suyi wannan sabon da ba rin haka zata faru</p><p>tsakaninsu ba. Dakin yayi shiru, ita tana wasa da</p><p>yatsunta shi kuma yana kallonta, can ya ce</p><p>"Ummi". Ta dube shi "Yaushe za ki tare? Ta ce,</p><p>Nima ban sani ba, sai yanda su Umma suka ce.</p><p>Ya dauko kwalin wayar da ya sai ma Bishira ta</p><p>jefe shi da shi ya ciro wayar ya hadata da batir</p><p>din bayan ya 6are sim din ya saka. Ummi dai</p><p>tana ta kallonshi, ya manna chajar a jiki, ya mika</p><p>ma Ummi jona min can, ya nuna mata soke din</p><p>da ke bayanta. Ta amsa cike da sha'awar wayar</p><p>duk da bata nuna hakan ba sannan ba ta ce kala</p><p>ba. Ya ci gaba da cewa, "Karfe nawa a ke kashe</p><p>inji? Ta ce, har yanzu ba a canza daga yanda ka</p><p>ke kashewa ba. Ya ce, "Sha daya zuwa sha biyu?</p><p>Ta ce, "Eh, ya ce in har zuwa wannan lokacin ba</p><p>kiyi bacci ba to ki cire in an kashe, ki kunna ko da</p><p>yake in dai ke ce ba sai na ce ki kunna ba. Ta</p><p>dago ido ta kalle shi, ya ce, Eh kunnawa za ki yi</p><p>ko za ki musa ne? Don kin fi ni ma sanin kan</p><p>waya. Ta ce, Wayar Umma kadai na iya kunnawa,</p><p>sai taka. Ya ce, Oho, cikin dan murmushi, na za</p><p>ci ba za ki fadi tawa ba in tuna miki lokacin da</p><p>kika kunna tawa. Haka nan don tsabar iya sarrafa</p><p>wayarki tun kina 'yar karama ki ka tura ni garin</p><p>Kaduna. * 58....Haka nan don tsabar iya sarrafa</p><p>wayarki tun kina 'yar karama ki ka tura ni garin</p><p>Kaduna. Ta zuba fuskarta cikin tafukan</p><p>hannayenta, sam bata son Ya Abba yana tada</p><p>wannan zancen, Umma ta shigo da sallama tana</p><p>cewa, Yuwa Ummi, ina ki ka sa min 'yar kwalbar</p><p>turaren nan? Ummi ta dago fuska, "Cikin jakarki</p><p>ta rataye. Umma ta dubi Abba, "A'a ha, yaushe</p><p>ka shigo? Ya ce Ban jima sosai ba. Ta zauna ya</p><p>gaisheta, sannan ta ce masa dama Alhaji yanzu</p><p>yake ce min zaman me Ummi ke yi a gidan nan?</p><p>Ya zaci tun daga asibitin zata wuce dakinta,</p><p>Ummi ta turo baki. Umma Alhaji ya gaji da ni</p><p>sosai, suka kalle ta, Umma ta ce, Ji wani shirme,</p><p>me ya yi na gajiya? Ta ce To dubi fa daga cewa</p><p>an fasa aurena sai da ya matsa ya daura min</p><p>aure. Sannann kuma yanzun wai ya zaci daga</p><p>asibiti zan tare? Abba ya ce, Ai yana daki yi</p><p>hanzari ki same shi don shi ya san amsarki ba</p><p>Ummata ba. Umma ta ce, "Wallahi daga nan suka</p><p>share Ummi. Ta kalli Abba ta ce, "To kawai</p><p>yanda za a yi gobe ka kwashe kayanka daga</p><p>dakinka sai a kai na Ummi din kawai. In yaso</p><p>zuwa yamma ko Saratu da sauran makota sai su</p><p>rakota. Abba ya kalli Umma, ni da so nayi a dan</p><p>yi kwaskwarima a gidan kafin sannan na dan</p><p>samu na sai ma Ummin Zannuwa. Umma ta ce,</p><p>"Zancen wofi, yanzun tsirara take yawo? Kawai in</p><p>kana da fenti a hannu a goga a kawo ta haka, in</p><p>babu ma dai goben nan zata tare don ba zan</p><p>amince ran mijina ya 6aci ba. Abba ya yi</p><p>murmushi, to shi kenan Umma da safe kafin na</p><p>fita zan nemo masu aiki ina da fenti da siminti</p><p>sai ayi 'yar kwaskwarima shi ke nan. Dama ga</p><p>kudi nan da Mahaifin Bishira ya bani, wai dama</p><p>ya yi min alkawarin biya min sadaki. . 59...</p><p>Umma ta ce, "Yanzun Alhaji ya gama bani labari,</p><p>Mahaifin yarinyar nan mutumin kwarai ne, don</p><p>Allah Abba ka rike yarinyar nan ko don darajar</p><p>mahaifinta. Ummi ta ta6a baki, kishi ya motsa.</p><p>Abba ya ce "In sha Allahu Umma nima abinda</p><p>nike dubawa kenan, ni ke hakuri da ita. Ta ci</p><p>gaba da cewa, Sannan kada kaga Ummi yar</p><p>uwarka ce ka ce zaka fifitata, sam ba zan yarda</p><p>da haka ba. Kayi adalci a tsakaninsu ka dinga</p><p>addu'a Allah ya hada maka kansu. Ya ce, "In</p><p>Allah ya yarda Umma zan kula. Ta ce, "To maza</p><p>ka tashi ka tafi gurin iyalinka. Sam bai ma dace</p><p>ka fito ba, kamata ya yi a ce ka zauna gida ka</p><p>kara ba matarka baki, ya cee To Umma. Ta mike</p><p>tana cewa, tashi maza. Ya mike yana kallon</p><p>Ummi, yayin da ita kuma ta juya fuskarta cike da</p><p>6acin rai. Ya ce, Ummi ki fa kunna in an kashe</p><p>injin? Sam ba ta tanka ba don haushi, sai da ya</p><p>tafi sannan Umma ta dubi Ummi. Ki tashi ki</p><p>kwanta don gobe ki tashi da wuri, kiyi duk shirin</p><p>da ya dace saboda babu daga kafa a tarewarki</p><p>gobe. Ki ta fasha-fishenki ba zamu kuma yarda</p><p>da kalace-kalacen ciwonki ba, ta tafi abinta. A</p><p>zaton Umma, Ummi tana fushin ba zata tare ba</p><p>ne, ita ko haushinta korar mata miji da Umma</p><p>tayi ya tafi gurin kishiyarta. Koda ta kulle kofar</p><p>ba ta shiga uwar dakin ba, nan kan doguwar</p><p>kujeta ta mike abinta. Jira ta ke a kashe Injin ta</p><p>kunna waya. Abba ko kafin ya isa gida sai da ya</p><p>fita titi ya fanshi kaji guda biyu da madara mai</p><p>tsafta.I novels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 8</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 8</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:37</p><p>Jira ta ke a kashe Injin ta kunna waya. Abba ko</p><p>kafin ya isa gida sai da ya fita titi ya fanshi kaji</p><p>guda biyu da madara mai tsafta. 60...Sai dai</p><p>yana shiga gidan ya iske mahaifiyarshi da matar</p><p>tashi suna ta zage- zage. Ya nufi gurinsu, Sahura</p><p>ta ce, Sai yanzun suka barka ka taho? Ya ce,</p><p>"Umma dama ban dade da zuwa ba". Ta ce, "Ina</p><p>ta aiken kazo ina nemanka shi ne ka 'ki zuwa</p><p>saboda ka maida ni 'yar iska ko? Ya ce, A'a</p><p>Umma ba a fada min ba. Sannan aiki ne yasha</p><p>kaina... Ta ce, "Rufe min baki, ai baka daga kafa</p><p>da zuwa gun Suwaiba. To saurare ni da kyau ka</p><p>ji, nazo ne in fada maka cewa ka rubuta saki ka</p><p>ba wannan 'yar iskar yarinyar. Ya ce, Kiyi hakuri</p><p>Umma, ki bari sai a hankali. Bishira ta ce, Umma</p><p>yana sonta fa, jin ku kawai nake. Maganar Bashir</p><p>gaskiya ce da ya ce da shi a ka shirya hakan.</p><p>Umman Bashir ta ce, "Dama Abba kaima son</p><p>Ummi ka ke yi? Ya ce, Umma ba zan ki Ummi ba,</p><p>in kun yi la'akari da kaunar da iyayenta suke</p><p>nuna min. Amman wallahi ban san komai game</p><p>da auranmu ba, ta ce kana nufin kan dole a ka</p><p>daura muku aure ba don kana sonta ba? Abba ya</p><p>yi dan jim, ta ce kai nake sauraro, don ta tafi sai</p><p>ya ce kusan haka dinne, itama kuma ba sona take</p><p>ba. Umma ta ce, Ina ruwana da bata sonka, in</p><p>bata so iyayenta ai suna so. Ni dai bukatata</p><p>yanzun kada ka bari ta tare, sannan ko kusa kada</p><p>taga fuska a gurinka. 33. 61... Umma ta ce, "Ina</p><p>ruwana da bata sonka, in bata so iyayenta ai</p><p>suna so. Ni dai bukatata yanzu kada ka bari ta</p><p>tare, sannan ko kusa kada taga fuska a gurinka".</p><p>Ya dan yi shiru yana tunanin wannan irin lamari a</p><p>zuciyarshi ya ce, bari kawai in lalla6ata, zan yi</p><p>yanda ki ka ce sai dai kuma in su Alhaji suka sa</p><p>kawo ta ni ba zan iya ja da su ba. Sannann ke</p><p>kanki bana so a ce ke ki ka sa ni in ma Ummi</p><p>rashin mutunci, amma ki bar ni da ita in har ta</p><p>yarda ta tare a nan gidan. Bishira ta ce, "Tab, ba</p><p>ko zata tare a nan gidan ba". Umma ta ce "A'a ki</p><p>bari in sun matsa ta tare a nan din ta tare, gara</p><p>suna kusa muna kallon irin zaman da za su yi.</p><p>Can gefe ba sai su rinjaye shi ba". Bishira ta ce,</p><p>"Umma na tsani shegiyar yarinyar nan ne, bana</p><p>son in ganta ko cikin mafarkina, bare a zahiri".</p><p>Sahura ta ce, "Bishira na ce ki nutsu ki bar komai</p><p>a hannuna, in ma zan hada da Bokaye ne ba</p><p>Malamai ba in sha Allahu sai kin dara a gidan</p><p>nan. Ta ce, "To Umma, Sahura ta ce, Yauwa ke</p><p>dai ki zuba ido, Abba dai yana tsaye yana</p><p>kallonsu. Sai lokacin yayi magana, Umma dare fa</p><p>yayi, ta ce to muga ledar hannunka, ya mika</p><p>mata. Ta buda ta gani, "A'a kaza? To ku zuba</p><p>min nawa". Ya mika wa Bishira, Ki dibarwa</p><p>Umma. Ya nufi dakinsa yana jin sallamarta tana</p><p>fadin ta wuce, ya fito ya ce "To Umma sai da</p><p>safe, ya rufe gidan ya koma dakinsa. Da ya shigo</p><p>gidan ne da niyyar lallashin Bishira, amma yanda</p><p>abubuwan suka zama sai ya ji ba ma ya son</p><p>ganin Bishiran. Zantukan Bishiran da na</p><p>Mahaifiyarshi sun saka shi cikin tunani, lamo ya</p><p>kwanta a kan katifa yana ta harsaso irin zaman</p><p>da za a yi a gidan. Anya kuwa ba zai kama wa</p><p>Ummi haya ba? Cak! Hasken wutar dakin ya</p><p>dauke tare da tsayawar Injin. A fili ya futa, Mai</p><p>ya kare kenan, sai da ya yi shirin bacci ya</p><p>kwanta tare da manne filo a kirjinshi, sannan ya</p><p>dauko wayarshi ya kira layin da ya hada cikin</p><p>sabuwar wayar da ya ba Ummi. 62.. Gabanta ne</p><p>ya fadi, lokacin da taga lambar Ya Abba suna</p><p>rawa a fuskar wayar, ta haddace lambobinshi tun</p><p>shekarun baya. A fili ta ce, kenan ma ya hada</p><p>wayar ba yau ya soma hada ta ba, ta sake yin</p><p>lamo a kan gado tare da janyo filo ta manna a</p><p>kirjinta. Ta daga wayar lokacin tana daf da</p><p>tsinkikewa, can cikin makoshinta tayi sallama. Ya</p><p>amsa, tsigar jikinsa a tashe sakamon jin muryarta</p><p>tana ratsa jikinshi, ya ce "Ummi, ta ce Na'am Ya</p><p>Abba. Ya ce, "Kina son ki tare goben? Ta lumshe</p><p>ido, ba ni da za6i Ya Abba, duk yanda ku ka ce.</p><p>Dadi ya cika zuciyarshi. To shi kenan ki tare</p><p>goben, zan yi parking tun Asubahi sai in sa mai</p><p>fenti yayi kafin in tafi aiki. Ta ce, "Ba an ce in</p><p>mutum ya yi aure ana ba shi hutu ba? Ya yi 'yar</p><p>dariya, "To ni ba ki ga yanda auren nawwa yazo</p><p>daga sama ba? Amma duk da haka in na nemi</p><p>hutun za a bani, ta ce kayi aikin kama kawai ba</p><p>sai ka nemi hutu ba.. Ya katseta, "Don ba a sona</p><p>shi yasa ba a damu na amshi hutu ba? Ta ce,</p><p>"Ba nufina kenan ba, naga kana matukar son</p><p>aikinka ne". Ya yi dan murmushi "Kin dai</p><p>wayance kawai, to yanzun haka zaki tare babu ko</p><p>dan kunshi bare gyaran kai irin na Amare? Koda</p><p>yake ba aure so ba ne. Cikin muryar shagwa6a ta</p><p>ce, "Ya Abba ka daina, ya ce me zan daina? Kana</p><p>cewa bana sona, ai kai ma ba ka sona... Ya dan</p><p>yi shiru, yanda ta ke shagwa6ar ne ta tsuma shi.</p><p>Ya ce, ok, to goben sai kije ki gyaranki ko? ta ce,</p><p>"Umma ba za ta bari in fita ba, amma me yin</p><p>fulawa za ta iya ta mini". Ya ce, "To ina ne a ke</p><p>gyaran gashin? Ta ce, "Cikin gari ne, ya ce kin</p><p>san gurin? Ta ce, "Eh, amma ban ta6a yi ba, ya</p><p>ce to ki bari zan shigo gidan kafin na tafi aiki zan</p><p>ce Umma ta bar ki, ta ce "To." Suka dan yi shiru.</p><p>Can ya katse shirun da cewa, "Me ki ke tunani?"</p><p>"Yaushe?" "Yanzun." Ta dan musukuta, "Ina</p><p>tunanin yanda abubuwan za su kasance gobe.</p><p>Yanda har za'a yi fenti, sannan a jire kuma in tare</p><p>duk a gobe". Ya ce "Duk mai sauki ne, ni kuma</p><p>kin san tunanin da nake yi yanzun? Ta ce, "A'a,</p><p>ya ce gobe kamar yanzun muna tare... da sauri ta</p><p>katse wayar, me Ya Abba ke son fada? Ta kashe</p><p>wayar sannan ta kudundune. Ita ma yanzun ya</p><p>jona mata wannan tunanin, a fili ta furta gobe</p><p>kamar yanzun me ya ke faruwa? Shi kuwa sai ya</p><p>ji haushin kansa sakamakon furucin da ya yi har</p><p>ta yanke wayar, wani gefen kuma sai ya ga kila</p><p>don bata sonshi ne shi yasa har ta ji haushin</p><p>furucin nashi. Kila ma yanzun tana can tana kuka</p><p>in ta tuna gobe tana gidansa, dare ya tsala amma</p><p>ya kasa bacci, don haka sai ya mike yayo alwala.</p><p>Sallah ya shiga don kara nuna godiyarsa ga Allah</p><p>da ya bashi Ummi tare da rokon Allah ya kimsa</p><p>mata sonshi, daga karshe ya roki hadin kan</p><p>matansa. 34 63..Yana wanka da safe ya jiyo</p><p>muryar mum dinsa harta zo gdn, a zuciyarshi</p><p>yace innalillahi wa inna ilaihir raji'un, yana fitowa</p><p>tace wurinka nazo, Bashir yazo ya fada min cewa</p><p>yau za'a kawo fitsararriyar yarinyar nan ko? Abba</p><p>cikin damuwa yace umma nima bansani ba, tace</p><p>munafiki kasani, bari kaji ko an kawota ko</p><p>magana bance ta hadaku da ita ba, kai in ma</p><p>kaje girin munafukan iyayen nan nata su ka ce</p><p>yau zata tare kace saika shirya. Bishira tace</p><p>umma bazan yarda ta tare ba, bai sai min komai</p><p>ba, ya kalli Bishira to itama na sai mata wani</p><p>abun ne? Sahura tace to ina ruwan wani da baka</p><p>sai mata ba? Abba yace toni bani da kudi ma,</p><p>Bishira tace to kudin jiya da babana ya baka fa?</p><p>Umma tace fito dasu, yace umma dama fa kudin</p><p>sadaki ne ya biya min, kuma naba alhji karami</p><p>waliyyinta sai dai ki je gun shi ki amsa, tace don</p><p>kasan bazan tunkareshi bane shi yasa to tana</p><p>binka bashi, zaka chanza mata kayan daki, ka sai</p><p>mata zannuwa sannan ka bata jari, yace umma</p><p>banyi alkawari ba, in dai na samu kudi kuma ta</p><p>kwantar da hankalinta to xan mata, ya nufi daki</p><p>yabar su nan sunata zantukan su. Lkcn daya</p><p>shiga gdn su umman shi, ummi tana linke kaya</p><p>tana sakawa cikin jaka, yana daga bakin kofa ta</p><p>dago ta amsa sallamar shi ta kalle shi, ya kalli</p><p>kayan sam zuciyarshi bata mishi dadi, ya nufi</p><p>wurin umma don yana son neman alfarma abar</p><p>ummi zuwa dan wasu kwanaki don yana so ya</p><p>dan gyara gidan, rashin galihun zai yi yawa, ba</p><p>lefe kuma gida ba gyara? Yayi sallama suka</p><p>amsa, bayan ya gaishe su, ya dukar da kai yace</p><p>alhji dama nazo ne neman alfarma, suka ce</p><p>alfarman me? Yace inaso ne kudan bar ummi</p><p>zuwa nan da sati daya, sannan na gyara gdn,</p><p>kuma nayi mata sabbin dinki, alhji yace ba kana</p><p>da fentin ba? Kaje kasa a goga, sai ka biyo ta</p><p>kasuwarmu ka amshi zannuwa, abba yayi shuru</p><p>umma tace koda wani abu bayan nan? Yace a'a,</p><p>umma tace to an daga maka zuwa gobe, yace to</p><p>umma da alhji nagode, ya mike ya zai fita, yace</p><p>am umma ummi tace zata je gyaran gashi, suka</p><p>yi dariya su kace ai wannan ikon kane, yace to na</p><p>tafi alhji sainazo kasuwar, ummi ta jera masa</p><p>kayan karin kumallo koda ya leka dakin sai tace</p><p>ya abba ka shigo ga break, yace ummi zanyi latti,</p><p>tace to da yunwa zaka tafi? Yace akwai shayi a</p><p>can, tace come on ya abba zoka karya, ya kalli</p><p>agogo minti biyar gareni, ta dau copi ta tsiyayo</p><p>kunu ta mika masa, ya fara kurbar kunun, ta zubo</p><p>kosai a plate tarike a hannunta dauka kaci, ji take</p><p>tamkar ta bashi a baki, tsohuwa ta dago labulen</p><p>dakin, tace zura masa a baki za kiyi? Ummi tace</p><p>kada ya kware tsohuwa, an hana yin magana in</p><p>ana cin abinci, toshuwa tace tafi can da cusa kai</p><p>ba kwarjini, abba ya dire kofi tareda mikewa yace</p><p>ummi saina dawo, ki bari da dare zan kai ki</p><p>gyaran gashi, yasa hannu a aljihu ya zaro yan</p><p>dari binbiyu guda biyar ya bata, tayi godiya ya</p><p>ciro dari yaba tshuwa yace yar sa ido kema kiyi</p><p>kotso da wannan, ta rike baki tana fadin wannan</p><p>yara da munafunci suke, ya fita yana murmushi</p><p>ummi tace a dawo lfy, ya sake waiwayo wa ya</p><p>kalli ummi, suka saki murmushi, 35. 64....</p><p>Tsohuwa da ke bin su da ido ta ce, "Kai ban</p><p>yarda da ku ba Takwara, dama can ke da me</p><p>sunan Malam soyayya ku ke? ---- Umma da ta</p><p>tsinci zancen bayan fitowarta daga dakin Alhaji,</p><p>ta ce "Ya a ka yi?" Ta ce, "Suwaiba ina ga</p><p>yarannan tuni kallonmu kawai suke. Sai wannan</p><p>salo suke wa juna, sannan ga Takwara ciwon</p><p>barin gida shiru, ina ga dama ciwon nan na mai</p><p>sunan Malam ne." Umma ta saki dariya tare da</p><p>cewa "Allah yasa haka ne. Ummi kam cikin daki</p><p>ta kule zuciyarta zallah dadi. Misalin karfe biyu</p><p>Umma ta dan kishingide baya, ta idar da sallah,</p><p>tsuwar wayar da da Abba ya ba Ummi ajiya ce ta</p><p>farkar da ita. Ta ce, Ummi me ke tsuwa a dakin</p><p>nan? Wannan dai ba wayata ba ce. Ummi da ke</p><p>tsakar gida ana mata zanan fulawa ta ce, Lah,</p><p>Umma Ya Abba ne ya bani ajiya. Kila ma shi ne</p><p>ya kirata, ta dubi wadda ta yi mata zanen fulawar</p><p>ta ce Sabira don Allah shiga ki dauko min a kan</p><p>gado. 2missed call ta gani, ta ce kash! Sai gashi</p><p>ya sake kira, kafin ta daga sai da ta leka dakin</p><p>tsohuwa ta hango ta kwance a gadonta. Dama a</p><p>kofar dakin Tsohuwar take ta biyo inuwa ta daga</p><p>wayar tare da sallama, ya amsa cikin dokin jin</p><p>muryarta. Ina ki ka shiga ne? Ta amsa a can</p><p>cikin makoshinta, ana min fulawa a tsakar gida</p><p>wayar kuma tana daki. Ya ce, Ok ana miki zanen</p><p>fulawar ne? Ta ce an ma ganin har ya fara</p><p>bushewa ya saki murmushi tamkar yana gabanta.</p><p>Ana yi miki me kyau? Ta ce, Eh yayi kyau sosai,</p><p>ya ce Good, zan dawo kamar karfe uku saboda</p><p>zan kwashe kaya za a yi fenti a daki, so kin ga</p><p>ba zan samu kai ki gurin gyaran gashin da wuri</p><p>ba. 65... Don haka sai mu bar shi zuwa dare ko?</p><p>Ta ce, "To Ya Abba, ehm za a dafa maka wani</p><p>abu ne? Dadi ya lullu6e shi amma saboda</p><p>burinshi na kimanta Bishira a idonta sai ya a'ah.</p><p>Na hutar da ke zan ci na Antynki Bishira,</p><p>maganar ta soki ran Ummi har ta kasa magana,</p><p>ya fahimci hakan don haka sai ya kawo zancen</p><p>da cewa sai nazo. Ta tura baki tare da cewa</p><p>uhm, tana kashe wayar ta shiga kunkunan cewa</p><p>in yaso kaci abinci gidansu bana ta ba. Tsohuwa</p><p>da ke sauraronta ta sheka dariya tare da cewa,</p><p>ba dai ke kin ce me sunan Malam ba? Sai ma kin</p><p>je gidanshi yarinya ban miki baki ba amma za ki</p><p>raina kanki. Ummi ta cafke cikin jin haushi ta ce,</p><p>wai to Tsohuwa da za ki ce na ce Ya Abba cewa</p><p>nayi ina sonshi? Kuma da su Alhaji suka jona ni</p><p>da shi da naki har da ke za a dinga cewa ban yi</p><p>biyayya ba. Tsohuwa ta ce, Raba ni da gulmarki,</p><p>kina sonshi ai ni ba yarinyar goye ba ce, kina</p><p>waya kina kashe murya, san nan ciwoce-</p><p>ciwancanki duk sun lafa. Sai wannnan rawar kai</p><p>ki ke, to ki sani me sunan Malam dai ya aure ki</p><p>ne don dole, matar cushe kuwa ba daraja take</p><p>ba. Ummi ta ce, "To nima dai ai ba sonshi ni ke</p><p>ba, ni dai tsohuwa don Allah ki daina samin ido.</p><p>Ta mike, Na ma bar miki kofarki. Ta nufi kofar</p><p>dakin Alhaji tana kunkunai. 36. 66... Sai dai duk</p><p>da haka kalaman tsohuwa sun tsaya a ranta,</p><p>matar cushe bata daraja, Ya Abba kan dole ya</p><p>aureta, lallai zancen tsohuwa abin dubawa ne.</p><p>Abba ya shigo gidan uku da doriya, tare yake da</p><p>yara guda biyu, dayan zai mishi dan face-face,</p><p>dayan kuma zai masa fenti. Sune suka taya shi</p><p>kwasar kaya, bai samu Bishira a gidan ba, kila</p><p>tana gidan Ummanshi, ko makota. Sun kama</p><p>aikinsu shi kuma ya shiga kicin don ya dan dafa</p><p>abinda zai ci. Bishira gidan Anty ta tafi kuka take</p><p>wiwi wai ita fa ba za ta iya zaman gidan nan ba,</p><p>ta ce "Aunty Farida tunda kuna shiri da Baban</p><p>Walid ki ce masaya sawake min". Anty Farida ta</p><p>tsura ma kanwarta ido, tausayin Bishiran ya</p><p>cikata. Tabbas kishiya bata da dadi koda</p><p>mahaukaciya ce bare mai hankali. Sai dai ita bata</p><p>da ikon da zata hana ayi kishiyar koda kuwa</p><p>mijinta ne ke son yi, don sunna ce ta mai tsira da</p><p>Aminci. Bishira ta katse mata tunani da cewa,</p><p>dubi fa Anty hatta Dady yanzu yafi son Baban</p><p>Walid fiye da ni. A gabana ya dauki kudi yaba</p><p>baban Walid, a halinni kara na kai a kar6ar min</p><p>'yancina, kuma Momy zata yi magana ya hanata</p><p>cikin tozartawa. Hakan da Daddy yayi ba zubar</p><p>min da kima yayi ba, har da ita Momy? Yaushe</p><p>Baban Walid zai sake ganin darajarta? Anty</p><p>Farida ta sauke ajiyar zuciya, ta ce "Bishira Dady</p><p>bai zubar miki da mutunci ba, illa kara tarairayo</p><p>miki mutunci da yayi daga ke har Momy. Kuma ni</p><p>ba zan ce mijinki ya sake ki ba, haka nan ba zan</p><p>ga laifinshi ba, domin aure sunna ce ta Manzon</p><p>Allah (S.A.W), sam ba zan yi fushi da wanda ya</p><p>raya Sunna ba, koda mijina ne. Kiyi hakuri</p><p>kanwata koda bani da kishiya nasan akwai zafi,</p><p>amma kema kina da laifi, dube ki fa. Yanzu</p><p>Bishira wa zai gan ki ya amince ke kanwata ce ta</p><p>hudu? Zato za a yi ke yayata ce, kin saki kin yi</p><p>ragwaf, nonuwa har ciki haihuwa biyu jal, dubi</p><p>yanda tsabar datti yasa fuskarki da dokin wuyanki</p><p>zuwa bayanki duk kyasbi ya miki riga. Da kin</p><p>zauna kusa da mutum wari ki ke tashi, hakora</p><p>sun miki yalo, kai mijinki fa ya yi kokarin ba</p><p>kowane zai dauki hakan ba. Duk ba ki kalli laifinki</p><p>ba sai don ya kara aure yanzun? Ina ce kwanaki</p><p>garin shegen gantalinki ne ki ka bar danki a gida</p><p>ya fada rijiya ya mutu? To hatta Abban Nasir ce</p><p>min ya yi da shi ne ba zai yarda ba, saboda haka</p><p>ki dawo hankalinki ki zubar da kazantar nan ki</p><p>kama Ibadarki. Bishira ba kya jin kunya a ce ba</p><p>kya sallah? Kuma a tare da haka kina da wannan</p><p>kazantar ki ke kaurace ma shimfidar mijinki.</p><p>Kwanan baya ya kira ni a waya ya sanar da</p><p>nicewa kin ce min ina wari, don haka ni kuma na</p><p>ceya tafi gurin mai tsafta mai kamshi. Shima fa</p><p>Anty magana yake dankara min don ba kisan</p><p>halinshi ba ne. Anty ta ce, "Bishira kina cikin</p><p>hadari, ga kin sallah sannan ga kauracewa miji ki</p><p>kwana Mala'iku suna tsine miki. To daidaita</p><p>sahunki, ga mijinki dan kwallisan dan Jarida mai</p><p>farin jini, ki kalli yanda in yana gabatar da</p><p>shirinsa yanda 'yammata kan kira su ce suna son</p><p>lambarsa. Amma ke kina sakaci da shi, ki dubi</p><p>yanda wata mata ta kawo masa hari kwanaki da</p><p>a ce ya yarda ke ba za ki san kina da kishiyar</p><p>waje ba. Ki shiga taitayinki zan dai miki taimako</p><p>daya in kinamince za ki natsu. 67.... Bishira ta</p><p>ce, Anty taimakon me? Ta ce, "Zan samu Momy</p><p>su taimaka su canza miki kayan daki, sannan</p><p>Dady ya ba mu kujerar Makka ni da ke da Aisha.</p><p>To sai ya ce tunda ke kin ki kwantar da</p><p>hankalinki ki kwantar da na mijinki to ya fasa</p><p>naki, mu harmun yi passport. Bishira ta zaro ido,</p><p>da gaske Anty? Anty ta ce, Allah da gaske. To</p><p>yanzun shi ne ni ke son in ce muje mu ba shi</p><p>hakuri kila ya amince. Bishira ta ce, Tashi muje</p><p>Anty don Allah, Anty ta ce kin tambayo zuwa can</p><p>ne? Bishira ta ta6a baki, nifa ko nan din ban</p><p>wani tambaya ba, wallahi gidan ne bakikkirin</p><p>nake ganinshi. Anty ta ce, "Ki dinga addu'a, kishi</p><p>yayi miki yawa. Sannan ki daina fita ba tare da</p><p>izinin mijinki ba, duk in da ki ka je har ki dawo</p><p>Mala'iku suna tsine miki. Don haka yanzun tashi</p><p>ki tafi gidanki, ni zan samu Hajiya da Dady yau</p><p>din nan kuma in sha Allah za amiki gyaran dakin,</p><p>sannan tafiyar za ta kasance tare da ke. Bishira</p><p>ta ce, Na gode Anty, amma don Allah ki barni na</p><p>dan huta a nan gidan duhunsa nake gani, don ba</p><p>ki ji yanda ni ke ji ba ne Anty ko da dana Walid</p><p>ya rasu ban ji kunci irin wannan ba. Ta sake</p><p>rushewa da sabon kuka wiwi, Anty kallonta kawai</p><p>take ta ma rasa me zata ce. Wayarta ta ciro</p><p>daga chaji ta shiga kiran layin Abba, lokacin ya</p><p>kira kananan kannanshi su Kamal suna ta fito da</p><p>kayan dakin Bishira saboda ayi fenti har an gama</p><p>nashi dakin. Wayarshi da ya ajiye a kan windown</p><p>dakinshi ta shiga ruri, ya duba, Anty ce. Ya daga</p><p>tare da sallama, ta amsa ya gaida ta cikin</p><p>girmamawa da mutuntuwa, ta amsa da fara'a</p><p>sannan ta ce, "Abba ga Bishira nan tazo tana</p><p>kuka, kuma ta ce min ba ka san ta fito ba". Ya</p><p>ce, "Eh haka ne, ta ce don Allah in baka wani abu</p><p>ina son ganinka. Ya ce To zan zo Anty, amma</p><p>yanzu ina aiki ne kayan dakin ta muke fita da shi</p><p>za a yi mata fenti ne, ta ce To ko da dare ne</p><p>haka, ya ce to zan zo. * 68.... Ummi tana ta zuba</p><p>ido ganin Abba amma shiru har a ka yi Magriba</p><p>tayi wanka tayi sallah. Tana zaune har Isha'i tayi</p><p>daga Masallaci shima ya nufo gidan su Ummi,</p><p>lokacin Ummi tana bakin gado tana 'yan shafe-</p><p>shafenta.Ta juyo Abba suna gaisawa da su</p><p>Umma, ta shirya cikin leshi mai ruwan lemun</p><p>tsami, da dan mayafinta fari haka takalminta. Ta</p><p>fito tana zaune kan kujera, ta ce "Sannu da zuwa.</p><p>Za ka ci abinci?" ya ce, "Da sauri haka ba muko</p><p>gaisa ba?" Ta zauna ina yini? Ya ce, lafiya lau. To</p><p>na kawo abinci? Ya ce, daga gida fa nake, ina da</p><p>kuma mata. Ummi ta ta6a baki, oh, haka ne ashe</p><p>kana da mata, gani nayi da matar taka ka ke</p><p>zuwa cin abincin daga nan ta lafe a kujera tare da</p><p>hada rai. Ya mike muje ko? itama ta mike, ya</p><p>kalle ta da wannan mayafin za ki? Ta ce, eh, ya</p><p>ce a'a dauko hijabi ba zan lamunci yafa wannan</p><p>dan mayafin ba. Ta kalle shi kamar ta ce ai</p><p>matarka tana yafa irin shi sai kuma tayi shiru ta</p><p>nufi uwar daki don dauko hijabi. Shi kuma ya nufi</p><p>waje, ta yi wa su Umma sallama sannan ta fito.</p><p>Yana tsaye jikin mota ya ce, ina wayar nan? Ta</p><p>ce, "Gata nan a hannuna ya yi dan murmushi</p><p>yace mayyar waya dama nasan sai kin dauko har</p><p>yanzun cikin haushin maganar shi ta dazun take</p><p>yi. Don haka bata kula shi ba, ya shiga motar ya</p><p>bude mata gefen kusa da direba ta zauna cikin</p><p>fushi. Lura ya yi da hakan, don haka sai ya ce ba</p><p>ni tamata ta ce so nake in loda mata kudi. Ya</p><p>guntse baki don kada yayi dariya, ganin yanda</p><p>tamiko mishi wayar cikin hanzari gata Allah yasa</p><p>bacewa nayi a bani ba. Ta juyar da kai tana</p><p>kallon titi, shima bai sake cewa kala ba har suka</p><p>shiga cikin gari. Ya dube ta, wane shagon zamu?</p><p>Ta ce, duk wanda kaje, ni sanin wani saloon nayi?</p><p>Shagon wata mata ya kaita kusa da inda yake</p><p>aski, sun samu shagon Musulma ce 'yar</p><p>Maiduguri.Shamsy belloRFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 9</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 3 part 9</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:40</p><p>nayi? Shagon wata mata ya kaita kusa da inda</p><p>yake aski, sun samu shagon Musulma ce 'yar</p><p>Maiduguri. 69.... Abba ya ce mata ga Amaryata a</p><p>gyara mata kai duk da ba wai gashi ne da ita ba</p><p>ya yi kyau sosai ko nawa ne zan biya. Mai</p><p>shagon tayi 'yar dariya, zan mata yanda ka keso</p><p>ya dubi Ummi wadda ta samu kujera ta zauna</p><p>fuska daure. Ya ce, "Kanwata zan tafi nayi aski</p><p>nima, daga nan sai na dauki matata daga unguwa</p><p>na kaita gida, sannan ta san in har ta bude baki</p><p>to kuka ne zai kwace mata, don haka sai ta yi</p><p>shiru. Ya fita yana 'yar dariya, mai shagon</p><p>Yagana saloon ta ce, "Kai kanwata kun dace fa,</p><p>kuma da alamayana sonki sosai.Ta kalli mai</p><p>shagon hawayen da take makalewasuka zubo, ta</p><p>ce "Anty ina so a nan, dubi fa abinda yake</p><p>min.Komai sai ya ce min matarsa, matarsa, ko</p><p>inaruwana da matarsa? Yagana ta ce, "Yana da</p><p>matane? Sam bai yi kama da mai mata ba.Ummi</p><p>ta ta6a baki ta ce, "Yana da mata da yakeso ni</p><p>bana sonshi, baya sona, iyayenmu ne sukahada</p><p>mu.Yagana ta ce, in ma ke ba kya sonshi shi kam</p><p>yanadauke da tsantsar sonki a idanunshi n</p><p>fuskancihakan. Ummi ta ce, "Anya kuwa? Bana</p><p>zaton yanasona ne, in kin ce yabi iyayenmu ne</p><p>zan fi yardadon shi din mai biyayya ne.Yagana ta</p><p>tura mata kujera, zauna in soma miki,sai da ta</p><p>fara gyara mata kai sannan ta ce, "In mamijinki</p><p>ba ya sonki to kuwa ba za a yi wuyarshawo kai</p><p>ba.Ummi tayi murmushi tare da kallon fuskarta</p><p>tamadubin da suke fuskanta, ki ke gani Anty? Ta</p><p>cesosai kuwa, ki tarairaye shi da kyau, kin san</p><p>shinamiji dai dan shauki ne da son nishadi.</p><p>(((KWARAI KUWWA!!!)))Ga kuma son tarairaya</p><p>kamar jaririn yaro, ummi tace, "To zan yi hakan in</p><p>har yin hakan zai sa ya soni.Yagana ta ce, "Zai</p><p>so ki, zan so kiyi gyaran jiki dafata, Umi ta ce,</p><p>kamar ya ya? Yagana ta ce, kayanmata zuwa</p><p>gyaran fata, wanda za ki sha don 'karinni'ima.</p><p>Ummi tayi shiru, don bata son irin</p><p>wannanzantukan.Ta ce, "Kin yi shiru, Ummi ta ce</p><p>Ummana ta ce bata son in sha komai, tunda ni</p><p>budurwa ce, in je wamijina da ainihin halittata.In</p><p>yaso daga baya sanin saboda 'yan garinmu sunzo</p><p>da shi daga Zamfara. Yagana ta ce, Hakan</p><p>mayana da kyau, domin Amare da yawa suna</p><p>shanwahala sosai kasancewar ba su saba</p><p>ba.Sannan mazajen ba su bambance ainihin</p><p>yandamatan suke. Ummi cikin gundira ta ce, Gara</p><p>ma nagyara fatar.Yagana ta ce, "Wancan ma za</p><p>ki neme shi, ko nangaba Ummi ta ta6a baki, ni</p><p>dai fada min na gayarnfatar.Ta ce, "Ina sai dawa</p><p>in kina so zan baki kije gida kihada kiyi zan hada</p><p>ma angon lissafi da shi Ummita ce, ba ni sai da</p><p>suka gama a ka gyara matagashi fes, sannan ta</p><p>dauko kayan ta shiga lissafamata kamar haka:-1.</p><p>Man Zaitun2. Lalle3. Kurkur4. Madara ta ruwaZa</p><p>ki hada su guri daya ki kwa6a, sannan ki</p><p>shafejikinki da su kafin shiga wanka, in ya bushe</p><p>idan zaki shiga wankan sai ki murje shi tas,</p><p>dukwadannan 'yan kurajen na fuskarki za su</p><p>mutu,jikinki ya yi laushi da sheki.Ga kuma wani.1.</p><p>Sabulun Ghana2. Dettol3. Zogale4. Farar</p><p>AlbasaZa ki hada Sabulun Ghanada da Dettol da</p><p>garinzogale, da farar albasa, ki hada su ki kir6a</p><p>kimurmule shima a jikin za ki ringa shafawa.Da</p><p>fuska kafin ki shiga wanka, zan bar ki da biyunin</p><p>sun amshe ki ma sun ishe ki. Yanzun ko inwanke</p><p>miki kafa? 39. 70.... Ummita ce, "Ina tsoron kada</p><p>yazo kuma kudin shi ba su kai ba, Yagana tayi</p><p>'yar dariya, kina tausayinsa ne? Ki daina tausayin</p><p>mijinki shi ne zai amfana da gyaran da duk za ki</p><p>yi. Ummi ta ce, "To wanke mini".Ta hada kayan</p><p>wankin kafa ta ce yarana ke yi amma zan miki da</p><p>kaina. Sai kuma taga zanen fulawa. Ta ce, "Au,</p><p>an riga an yi zanen fulawa ma ba dama ayi,</p><p>Ummi ta ce, Ohi ni na manta ma, to ki fada min</p><p>yanda zan dinga gyara kafar, ta ce To bari in ba</p><p>ki mai sauki ma. 1. Man kwaka 2. Man shanu 3.</p><p>Man Zaitun Ki samu man kwakwa da man shanu</p><p>da man zaitun ki hada man kwakwa da man</p><p>shanu guri daya, ki shafa da dare da safe. Ki dan</p><p>gasa kafar sannan ki wanke ki shafa man zaitun,</p><p>za ki ga yanda kafafunki za su yi tamkar ta jariri.</p><p>Ko ki yi na ruwan ko kumba, lalle ki hada su guri</p><p>daya ki shafa a kafafunki da dare. Da safe ki</p><p>wanke ki shafa man ridi, wadan nan kurum in kin</p><p>rike su za ki ba wani labari, Ummi tace zan</p><p>kiyaye in sha Allah. Shi kuma Abba yana fitowa</p><p>daga shagon aski kai tsaye gidan Anty ya nufa,</p><p>ya samu Bishira Anty ta matsa mata tayi wanka</p><p>ta bata kaya ta saka. Ta kira mai kitso tazo tayi</p><p>mata ta sata ta shafa turaruka. Tunda Abba ya</p><p>shigo yake kallon Bishira, sun gaisa da Anty,</p><p>sannan ta ce dama dai na ce kazo ne don Bishira</p><p>ta baka hakuri. Sannan in maka tuni da yin adalci</p><p>a tsakanin matanka, kuma na yi wa Bishira fada</p><p>sosai. Ta dubi Bishira, ki ba shi hakuri, Bishira ta</p><p>hada rai tare da turo baki, ta kalle shi cike da</p><p>tsananin jin haushin shi. Kayi hakuri ya ce ba</p><p>komai dama ni ban yi fushi dake ba, a zuciyarta</p><p>ta ce, ba ka isa in baka hakuriba, albarkacin ina</p><p>son zuwa Makka ne da kuma canjin kayan dakin.</p><p>Ya yi wa Anty godiya ta ce ma Bishira gobe da</p><p>wuri kiyi parking din duk kayan ki a waje da mun</p><p>zo sai mu shirya miki. Bishira ta ce, Allah dai</p><p>yasa su yarda, Anty ta ce,"Za mu su yarda in</p><p>Allah ya yarda. Ta dauko wasu kayan sawa da</p><p>sabbin kuloli ta ce ma Bishiran je kisa a motarku.</p><p>Abba ya ce, "Kawo in kai, Anty na gode sai</p><p>anjima, ta ce To Abba ayi ta hakuri". Ya ce, Ba</p><p>komai, Insha Allahu. Suka biyo shi a baya tana</p><p>kara jawa Bishira kunne kan cewa in har ta</p><p>kuskura ta ji wata magana ta 6ullo ta rashin</p><p>mutunci sai ta fasa tsaya mata a kan maganar</p><p>aikin Hajji ko Dady ya amince sai tasa ya janye.</p><p>71.... Sun shigo mata Muhibba tana baya tana</p><p>'yanwutsil-wutsil dinta tamkar kurame, haka suke</p><p>tafiyar. Ta zaci su nufi gida sai taga sun nufi</p><p>cikin gari. Bata tambaye shi ina za su ba, har</p><p>suka isa inda yayi parking ya dubeta, Madam ina</p><p>zuwa, hum kawai ta ce. Ya bude baya ya dauko</p><p>Muhibba ya sa6a a kafada ya nufi shagon saloon</p><p>din. Daidai lokacin sun kammala komai, Ummi ta</p><p>zari hijabinta da niyyar rufe kanta, Yagana ta ce</p><p>a'a kanwata bari ya gani don ya biya ni 'yan</p><p>kudina. Abba bai zaci Ummi tana da gashi ba,</p><p>domin dai acikin Hausawa 'yan Arewa za a iya</p><p>saka Ummi acikin ma su gashi. Yayi laya-laya a</p><p>dokin wuyanta baki sidik. Yayi murmushi, lallai</p><p>kin gyara da kyau. Nawa ne kudinki? Ta fada ya</p><p>ciro ya bata, sannan Ummi tazari hijabinta.</p><p>Mamaki take, Gida ya koma ya dauko Muhibba?</p><p>Yamiko mata ita, Ga 'yarki. Ta amsheta. Yagana</p><p>tace, yarinyar tana kama da ku. Abba ya ce, "Ai</p><p>'yarmu ce, suka yi mata sallama suka fito. Ummi</p><p>da Bishira a tare gabansu ya fadi lokacin da suka</p><p>ga juna. Bishira ta kauda kai yayin da Ummi taja</p><p>baya daga mazaunin kusa da direban da ta nufa,</p><p>ya bude mata baya ta zauna tana rike da</p><p>yarinyar. Ya tada motar suka dauki hanyar tafiya</p><p>kowanne zuciyarshi da abinda take karantowa.</p><p>Ummi tunaninta Abba ya je ya zo da matarshi ne</p><p>don yanuna mata shi fa matarshi yake so. Ita ko</p><p>Bishira nata ganin wulakanci ne na karshe da ya</p><p>dauko ta yazo da ita gurin wannan karamar</p><p>yarinyar. Shi ko Abba addu'a ce a zuciyarshi</p><p>Allah ya hada masa kan matansa, sai kuma ya</p><p>soma tunanin ina zai soma zuwa? Nashi ganin in</p><p>ya kai Bishira gida ya sauke ya tafi kai Ummi bai</p><p>mata adalci ba. Amma ya kula Ummi tana fushi</p><p>kuma yaso ya lallasheta, yana cikin wannan</p><p>tunanin ya tuna dawayar nan. Ya kalli wayar a</p><p>gefanshi. Dan murmushi yayi da ya tuna lokacin</p><p>da ta dangwarar masa da wayar don ya ce ta</p><p>matarsa ce. Yanayin yanda Ummin ke nuna</p><p>kishinta yana birge shi, koda bata sonshi tana</p><p>kishinshi sannan bata masa raini ko rashin</p><p>kunya. Kofar wani gidan saida gasassun kaji da</p><p>ire-iren kayan kwalam ya tsaya. Ya kalli Bishira</p><p>Madam mu shiga ko? Ta ce, "A'a ni fa ba zan fita</p><p>ba, ya ce To bari in dawo, ya nufi ciki. 72.. Ta</p><p>waiwayo ta dubi Ummi, ta ce "Ba ni 'yata</p><p>fitsararriya. Ummi ta mika mata tare da cewa</p><p>nima ai ba cewa nayi a bani ba, ta ce "Kar dai ki</p><p>min rashin kunyaki bar ganin an jona ki da mijina</p><p>ki zata za ki hada sahu da ni. Ummi ta ce, "Sai</p><p>dai kada a kuma in dai batun hada sahu ne, kuma</p><p>ban damu don mijinki ba bai sona ba, tunda ni ina</p><p>sonshi. Bishira cikin daga murya ta ce, oho?</p><p>Dama sonshiki ke yi? Yanzun na gane da nufi aka</p><p>yi. To ki sani kin sai ma kanki masifa da bala'i.</p><p>Ummita ce, "Kin ga bala'inki can, daga nan</p><p>batakara magana ba ta bar Bishira na ta masifa.</p><p>Tundaki ka za6i ki auri mijina zan shayar da ke</p><p>ruwan dana sani. Sai kin gwammace zama a</p><p>kurkuku fiye da gidan mijina, daidai lokacin Abba</p><p>ya dawo da ledoji guda biyu. Bishira bata yi shiru</p><p>ba sai zagin Ummi take yi,"'Yar iska, 'yar daba...</p><p>tsawa Abba ya daka ma Bishira, tare da cewa ba</p><p>ki ji kunya ba da ki ke zaginta amma bata kula ki</p><p>ba? "Ta ce, "To ka ji abin da ta ce min ne? Tsaki</p><p>yaja tare da daukar wayar da ta aje yasa a ledar</p><p>Ummi, sannan ya tada motar. Kofar gidan su</p><p>Umma ya tsaya, Ummi wadda dama ta kosa tazo</p><p>gida, ta bude motar ta fada gida cike da takaici.</p><p>Ya kashe motar sannan ya dauki ledarta ya kalli</p><p>Bishira, Ina zuwa. Kala bata ce ba. Illa baki da ta</p><p>cije, kirjinta na yin wata irin suya. Ban da tana</p><p>tsoron Anty kada ta fasa zuwa gurin Dadynsu da</p><p>tuni ta shago Ummi ta nadi 'yan kayanta. Dakin</p><p>Umma ta shige, Ummar tana shirin fitowa Ummi</p><p>na shiga, ta ce kun dawo? Ummin ta hadiye 6acin</p><p>ranta."Eh, mun dawo Abba a ya shiga gaida</p><p>Umma sannan ya mika ma Ummi ledar, gashi kin</p><p>manta Ummi ta amsa tare da cewa, an gode.</p><p>Umma ta ce, "Me ku ka siyo in ce dai ka sai ma</p><p>Bishira? Ya ce, "Eh na sai mata, kaza ce fa</p><p>Umma ba wani abu ba". Ta ce, "To shi ke nan</p><p>maza ka koma gurin su, yace "To. Tana fita ya</p><p>kalli Ummi akwai waya a cikin zan kira ki, kuma</p><p>bana bukatar ki kashe min waya. Ummi ta ciro</p><p>wayar da sauri, ta dibe shi ba wayar matarka ba</p><p>ce? Ya ce, "Eh tata ce, ta mika mishi cike da</p><p>kunan rai, ga abinku ka kira ni da layin Umma. Ya</p><p>ce, "Ke ce za ki cigaba da rike ma mata</p><p>tawayarta, ba tare da ya jira jin me za ta ce ba</p><p>yana murmushi, Ummi ta kasa gane cewa ita ce</p><p>matarta shi. Ko kallon kazar bata yi ba illa dai</p><p>tayi duk wasu abubuwan da ta saba yi kafin ta</p><p>kwanta, sannan ta kunna wayar tana tsammanin</p><p>kira. 73..... Shi ko Abba koda yazo Bishira tana</p><p>ta mitar don tsohon wulakanci an zo da ita an</p><p>shanya ta, bai ce mata kala ba illa dai motar da</p><p>ya tada suka nufi gida. Gidan duk kaya saboda</p><p>bai maida ba da a ka gama fentin, ya dauki</p><p>tsintsiya ya share dakin, sannan ya shimfida</p><p>katifa ya fito inda take zaune bakin Rijiya.</p><p>Muhibba tayi bacci tana rungume a jikinta, ya ce</p><p>kawo ta, ta mike a fusace ta nufi dakin ba tare</p><p>data bashi 'yar ba. Ya bi bayanta, so kurum yake</p><p>ya lallasheta ba wai don tsoronta ba sai don</p><p>tausayinta, yasan mata kan kishi za su iya yin</p><p>'yar karamar hauka. Wasu ma sai sun yi babbar</p><p>kuma bai dace ana nuna kishinsa ba, shi kuma</p><p>yana nuna ko 'in kula a gare ta, gefen katifar ya</p><p>zauna ya lalubo hannunta ya rike cikin</p><p>nashi."Bishira!" ya ambaci sunanta cikin sanyin</p><p>murya, bata amsa ba kuma bata dube shi ba, ya</p><p>ci gabada cewa, "Bishira ban ga abin damuwa ba.</p><p>Ko damata uku a ka daura min aure da su bare</p><p>daya, inkin yi la'akari da irin son da nake miki ke</p><p>kin san Bishira ba kiyayya ta hada mu ba. Kina</p><p>manta wannan ne? Ta dago ta dube shi ta dan</p><p>soma saukowa, yayi murmushi har yau ban daina</p><p>sonki ba, ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta turo</p><p>baki sai kace 'yar yarinya. To ai na sha jin a ana</p><p>cewa so daya ne tak, ya cehaka ne, ta ce "To</p><p>tsakanin ni da Ummi wa ke keyi wa? Da sauri ya</p><p>ce ke, ta ce Allah?Ya sake tausasa murya, haba</p><p>Bishira ya ki ke wannan zancen kema kin sani,</p><p>kuma don Allah na roki ki in muna tare ki daina</p><p>min zancen Ummi, ke kadai ce za6i na. Bishira</p><p>taji dadin wannan kalamai, don haka sukaci</p><p>namansu suka kwanta, ya bukace ta a nan masai</p><p>da ta ce kaje gurin Ummin mana. Ya ce, "Na ce</p><p>in muna tare bana son kina min zancenta. Sai dai</p><p>in kina son ci gaba da horon daki ke min ne.</p><p>Haba Bishira, ko tausayina bakya yi?An fi wata</p><p>uku kina haramta min halas dina. Kullum sai dai</p><p>ina azumi sai ka ce gwauro? Yajawota jikinshi, ya</p><p>rungume da kyar dai ya samu yadan rage</p><p>matsala, sai dai ita ma ya lura tayi missing</p><p>dinsa. Suna kwance har kusan sha daya saura</p><p>tuni ita tayi bacci, shi kam daman so yake tayi</p><p>bacci yakira Ummi. Ya mike yaje yayo wanka</p><p>sannan ya nufi dakinshi. Yaja katifarshi ya kai</p><p>dakin, sannan ya kwanta akai, ya kira Ummi</p><p>lokacin bacci ya soma figarta. Ringing din ne ya</p><p>farkar da ita, sai da ta kusa tsinkewa sannan ta</p><p>daga, kafin ta amsa sallamarshi sai da tayi wata</p><p>doguwar hamma.Ya ce, "Ke baccin ki ma ki ke</p><p>alhalin na ce zan kira ko? Ta ce, "Amma ka san</p><p>bacci ba ya jira in ya zo,ni kuma ba zan iya yiwa</p><p>bacci gardama ba". Ya ceto sarkin iya zance, yayi</p><p>nufin zolayar ta. Yanzun dai na soma tunanin kin</p><p>soma sona, gabanta ya fafi, sam bata son ya</p><p>gano hakan yanzu. Tafi son sai lokacin da shima</p><p>ya soma sonta. Ya katse mata tunani, hasashe</p><p>na haka ne? Ta ce, ko kusa, mene hujjarka da</p><p>fadin haka? Ya gyara kwanciya. Na farko naga</p><p>ana ta kishina, sannan tun da a kadaura aure da</p><p>ni sai ciwo ya kame kansa, kuma nalura kina ta</p><p>zumdin tarewa a gidana.Ya saki 'yar dariya,</p><p>yasan ya cika mata ciki da takaici, shiru tayi</p><p>nazari take wacce amsa zata bashi, ko dai wayar</p><p>zata kashe? Tamkar ya shiga zuciyarta, sai ya</p><p>ce.... 41 Tamkar ya shiga zuciyarta sai ya ce,</p><p>"Koda wasakada a kashe waya. Ranta ya sake</p><p>6aci, ta ce Ya Abba ka tafka kuskure da kayi</p><p>zaton ina sonka,sam ni bana wani kishinka. In</p><p>don ka ce wayar matarka ce na ce ka rike abinka,</p><p>sanin kanka ne ba ma shiri da matarka, kuma duk</p><p>abinda ka ce nata ne dole na guje shidon ba zan</p><p>dauki wulakanci ba. Batun ciwo kuma daka ce</p><p>tunda aka daura mana aure ka neme shi ka rasa</p><p>dama bani na dora makaina ba, kaima ina naka</p><p>hawan jinin ya tafi? Sannann kuma wane zumudi</p><p>na nuna na tarewa a gidanka, Ya Abba ka sani</p><p>yanda a ka tilasta maka aurena, to ni ma fa dole</p><p>tasa na hakura. Amma ka rike a ranka bana wani</p><p>sonka bani kamarina ina sonka, kalaman nata na</p><p>karshe sun burgeshi har sun sa shi yin da ya</p><p>sanin tsokale zancen. Sai kuma ya canza salo da</p><p>cewa, haka dai ki ka ce amma ina da ja mu dai</p><p>bar zancen, shin dazun kafin ki soma wannan</p><p>tunanin me ki ke yi? Ta danyi shiru tana</p><p>tambayar kanta. Dama mutumin nan haka ya ke?</p><p>Oh yanzun dabara zai min sai ya gano ko ina</p><p>sonshi dole, to kuwa bazai ji ba, ya katse ta da</p><p>cewa ban san ki da karya ba. Ta ce, ina tunanin</p><p>irin ukubar da zan sha a gidanka ne ta</p><p>wulakancin da zaka min, ya yi shiru zuciyarshi</p><p>tana cewa yarinyar nan ba ta san irinson da ka ke</p><p>mata ba ai ta ma dauke ka mugu kenan. A fili sai</p><p>ya ce, "Kuma fa kin yi tunani, Allah yabaki ikon</p><p>daukar ukubar da zaki sha tare kuma dajure</p><p>wulakancin da na tanadar miki goben Ummi. "Ya</p><p>fadi, wai dama da gaske wulakancin zai mata.</p><p>Gyara kwanciya kawai tayi bata kara cewa komai</p><p>ba, kuma bata da nufin cewa wani abu, yasa taji</p><p>haushi sosai, don haka sai ya tausasa muryarshi.</p><p>"Ummi kina ji na?" Uhm" Kurum ta ce, don ya</p><p>gane tana jin shi. Alkawari ta dauka ba zata sake</p><p>cewakala ba, tunda ya hanata kashe wayar. "Ba</p><p>ni da nufin miki..." Sai layin ya yanke daga</p><p>gefanshi, ta ce, "Gara ma haka". Tana kokarin</p><p>kashe wayar gaba daya kiranshi ya sake shigowa.</p><p>Tsaki taja kafin ta daga, kuma a ciki ta amsa</p><p>sallamarshi, sannan cikin murya mai kamar zata</p><p>rushe da kuka ta ce "Ya Abba ni fa bacci nake</p><p>son in yi". Ya ce, "Sam ba wani bacci da za ki iya</p><p>yoa sai tunani". Ta ce "To na ji, ina son yin</p><p>tunanin please".Ya ce, "Tunanin me za ki yi".</p><p>Cikin gundira ta ce,"Dole in yi tunanin yanda zan</p><p>kare kaina daga wulakancinka, don bana</p><p>tsammanin zan dauka" .Ya ce, "Wasa nake miki</p><p>fa." Ta ce, "Uhum, ban amince da cewa wasa ka</p><p>ke min ba, don na tabbata mu ba abokan wasa</p><p>ba ne".Ya ce, "To shi ke nan bari in bar ki kiyi</p><p>tunanin, amma tunanin yanda za ki faranta min</p><p>za ki yi". Muryar Bishira ce ta katse shi. "Oho! Ai</p><p>tun da na farka ban ganka ba na san ana nan</p><p>ana cin amanata". Ya kashe wayar da sauri, duk</p><p>da dai Ummi ta riga ta jiyo muryar Bishiran. Sai</p><p>dai bata fahimci me Bishirar take cewa ba,</p><p>ringingine tayi tare da dora filo a kirjinta, tunani</p><p>take yi wane irin zama za su yi? Koda bata da</p><p>amsa ta kudurce har abada ba za ta dauki</p><p>wulakanci ba, a shi ko a matar shi. Sai dai</p><p>alkawari ta dauka ba za ta musu raini ba,</p><p>matsawar ba su suka 6ullo da hakan ba. *</p><p>************************************** Shi ko</p><p>Abba rigima suka dinga yi da Bishira cikin tsohon</p><p>daren wai ya cuce ta ya kwanta da ita yazo yana</p><p>hira da wata banza. Kila ma ya saba kwanciya da</p><p>Ummin ne yau bai samu dama ba, Abba ya ce kin</p><p>so kanki in ki ka yimin wannan zaton, don ban</p><p>ta6a nemanki ba, kafinki shigo gidana, ko na</p><p>ta6a?"Ta ce, "Don ka san dai ni ba fuska". Da ya</p><p>gaji da iya korata ya rufe kofar ya koma can</p><p>dakin. 40. 74... Washegarin ranar, ga mamakin</p><p>Ummi tun misalin karfe goma jama'asuka cika</p><p>gidansu, a ka dora abinci. Can kuma saiga yaran</p><p>shagon Abba da dinkunan zannuwan daAlhaji</p><p>Babba ya sai mata.Ranar Abba bai shigo gidan</p><p>ba a waya ya kiraUmma suka yi magana, zuwa</p><p>karfe uku angama yiwa Ummi jeren dakin da yake</p><p>yana da girma yacinye komai tsaf.Fitar 'yan jere</p><p>babu jimawa sai ga Anty Farida dakannasu motar</p><p>tana da kaya tana biye da su, gadoda kujeru a ka</p><p>canzo mata.Suka jera mata sannan suka lodawa</p><p>motar na dasuka dauki hanya suka koma, Abba</p><p>kam yana gurinaiki amma zuciyarshi tana</p><p>gida.Fatanshi Allah yasa yana zuwa ya tarar an</p><p>kaimishi Umminshi, kawayen Bishira da</p><p>makotansu'yan jam'iyyarta duk sun shigo gidan</p><p>sun hadu saizugata suke yi tare da nuna mata</p><p>koda wasa kadata sakar ma Ummi fuska, kuma in</p><p>ta mata takamata ta duki 'yan kayanta.Suna</p><p>gidan a ka kawo Ummi, 'yan kawo Amaeyakam</p><p>suna jiyo habaici da zagin da su Bishira ke yi,don</p><p>haka suka ce kada a kai musu yarinyar.Inna</p><p>Saratu da Inna Harira suka ce ai kuwa sai</p><p>ankaita.Ba ko kunya Bishira ta zabga musu</p><p>harara lokacinda suka fada mata cewa ga</p><p>kanwarta sun kawomata, don Allah su zauna</p><p>lafiya tare da Aminci.In yarinyar tayi ba daidai ba</p><p>ta sata a hanya... takatse su cikin tsawa da</p><p>mikewa tsaye. "Don Allahku fice min daga daki</p><p>amanar kishiya? Har wai muzauna da aminci ku</p><p>ke cewa?Tayi 'yar dariyar yake "Kun yi kuskure,</p><p>ai batacanza daga sunan ta na kishiya ba, kuma</p><p>kowa yasan kishiya abokiyar gaba ce."Inna</p><p>Saratu ta ce, "Baiwar Allah jahilan mata sunesuke</p><p>yin irin wannan tunanin, amma ga masu ilimisuna</p><p>koyi da gidan mai tsira da Aminci</p><p>(S.A.W)ne".Bishira ta ce, "To kawai dai ki ce min</p><p>jahila ki huta,bari ku ji ba za n ba ku a 6oye ba,</p><p>zama ne za muyi shi na rashin mutunci, na kowa</p><p>ya iya allonshi. Don ina kishin mijina, kuma zan</p><p>nuna". Tirkashi! Lallai akwai daru kenan. To</p><p>masu karatu ku biyo ni cikin littafi na 4, kumana</p><p>karshe domin jin yadda za ta kasance atsakanin</p><p>Bishira da Ummi da kuma Oga kwata-kwata wato</p><p>IKI book 4 part 1</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 1</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:42</p><p>Inna harira tace, Allah ya kyauta ku tashi mu tafi.</p><p>Suka mike Suka nufi dakin ummi. Duk da ummi a</p><p>da bata tunanin tana da lokacin bishira, yanxu</p><p>kam dole tasan zaman da zasuyi. Su inna saratu</p><p>suka ce ma ummi duk abinda zatayi don allah</p><p>kada ki kulata. Suka ce tayi harkokin gabanta tayi</p><p>biyayya wa mijinta shine abunda zai fisheta.</p><p>Ummi tace To amma a zuciyarta bata tunanin</p><p>zata zuba ido a rainata. Suna tafiya fatima ta</p><p>shigo yiman sallama, ummi tace don allah fati ki</p><p>dan tsaya ni kadai fa zan zauna a dakin nan. fati</p><p>tace wayace kada kisan kawaye? Ummi ta ce</p><p>wane kawaye, auren da a ka daura cikin yan</p><p>mintina? Fati tace, Yau zakiji abinda mata kaji.</p><p>Ummi ta damko mayafin fati, ni fa inajin turo, wai</p><p>da gaske da wahala ko kina tsokanata ne? Fati</p><p>ta kamo kunnen ummi tayi mata rada. Ummi ta</p><p>zaro ido tare da cewa, Da gaske? Fati ta sheke da</p><p>dariya tace sai nazo jin batun. Ummi tace sirrine</p><p>ya za'ayi in fada miki sirrina? Fati tace au ni</p><p>shine na fadamaki nawa ko? Ummi tace kinyi</p><p>haram da kika fada fati tace, "ke kuma kinji</p><p>haram ko? Suka sa dariya. Duk yanda ummi taso</p><p>fati ta tsaya amman taki, don haka sukayi</p><p>sallama. Fati ta shige dakin bishira don yi mata</p><p>sallama. Bishira tace, fati fitar min daga daki</p><p>bana wasa dake, tunda kema naga kin koma</p><p>jam'iyar waccan yar iskar, fati ta fita, cikin ranta</p><p>tana cewa ba zanki yar uwata ba don kishinki na</p><p>banza tayi tafiyata. Ummi tsuru tayi tanaji tsoron</p><p>abinda fati ta fadamata, amman sai wata zucia</p><p>tace keda ba sonki yake ba kila ma bazaibi ta</p><p>kanki ba, sannan ta samu yar natsuwa. Abba ya</p><p>fito zai nufi gida sai kuma ya fasa ya nufi super</p><p>market, ya siyo audugar mata yana tsammanin</p><p>gobe ne zata tashi da al'ada a lissafinsa. Tun</p><p>sanda ta soma bai taba mance ranar ba, haka in</p><p>ya chanza mata lokaci duk yana lissafe. Ya sai</p><p>masu yan kayan masarufi sannan ya fito, gida ya</p><p>nufa amman gabansa yana faduwa kila har</p><p>yanxun ba a kai ummi ba. Da yayi fakin sai kuma</p><p>ya nufi gidan su umma duk kowa ya watse. Yayi</p><p>sallama tsohuwa tana alwala ta amsa. Umma</p><p>daga kicin ta amsa, tsohuwa tace "wane kinibibin</p><p>kuma ya kawoka mai sunan malam? Bayan an</p><p>kai maka ita? Yace kaji tsohuwa da wata magana</p><p>da gurin ummi nake zuwa? Ni gidan mu ne. Tace</p><p>kadaiji shi, takwara dai kada inji kada in gani, don</p><p>nace mata duk abunda kuka mata tazo ta</p><p>fadamin. Yarinyar nan tana kuka wiwi tabar gidan</p><p>nan. Umma cikin dariya tace "toh ai tsohuwa in</p><p>don Abba baza ayi fada ba, ummin ce dai abin</p><p>jama kunnen. Tsohuwa tace 'a' a daina zancen</p><p>nan suwaiba kada ma ya samu nayi. Abba yace"</p><p>Toh bari in zo in hada maki kayanki mu tafi can</p><p>don kada wani ya zafin cewa. Kinga kyafi tare</p><p>mata. Tace ina gana nan din ma zanji. Yace</p><p>Alhaji sun shigo kuwa umma? Tace A'a basu</p><p>shigo ba. Yace toh bari in isa gida. Tace toh</p><p>Abba ummi ma dazun aka rakata. Don allah Abba</p><p>ka kara hankuri a kan na da, sannan matarka</p><p>kuma kada kace zaka nuna mata bambanci a kan</p><p>ummi yar uwarka ce. Ka kwantar mata da hankali</p><p>ka mata adalci, sannan kada ka bawa ummi kofar</p><p>da zata raina bishira. Yace zan kiyaye insha allah,</p><p>kuma don allah umma ki kara mika godiata gurin</p><p>alhaji. Tace haba Abba yaya kake fadin haka?</p><p>Alhaji ai mahaifinka ne karka dinga kallon</p><p>alakarka da ummi. Yace haka ne duk da haka dai</p><p>a min godia, tsohuwa tace yaki godia ya samu</p><p>mata a sama don rashin imani mai sunan malam</p><p>ko gyauto bai sa mata ba, toh kasani tana binka</p><p>bashin lefe. Abba Yace umma ni dai na wuce.</p><p>Umma cikin dariya tace "Toh Abba. Yace tsohuwa</p><p>ni nayi gaba, don in na cika tsayuwa a nan kila</p><p>mu dambace, Tsohuwa tace kai dai jeka na baka</p><p>amana ya tafi yana dariya. Koda ya kai kofar</p><p>gidan sai ya bude mota ya dauki kayan</p><p>masarufinshi ya nufi cikin gidan salam dai duk da</p><p>jarumta irin tashi gabansa ne ke faduwa. Bai san</p><p>wace irin masifar bishira ta tanada ba. Ya shiga</p><p>da sallama. Bishira tana zaune akofar daki tana</p><p>goye da muhibba, amman bata amsa ba. Duhun</p><p>magriba ya soma dan daf da a kira sallah a ke,</p><p>yace bishira ya ba a tada inajin ba? Tace tunda</p><p>kazo yanxun ai sai ka tada kai. Da kafin wata</p><p>tazo ai baka taba zuwa kace a tada inji ba. "Abba</p><p>ya kalleta a zuciyarshi Yace" mata kenan masu</p><p>manta alhaji. Ya aje ledodin hannunshi ya nufi</p><p>injin. Bishira ta mike ta nufi ledodin tana fadin</p><p>Tun yanxu a aka shigo mata da kazar, alamun ba</p><p>za'ayi ada ba kenan. Ni lokaci na sa wuraren tara</p><p>ya shigo ina lissafe da komai, ta bude ledodin sai</p><p>taga kayan masarufi d kuma audugar mata. Tsaki</p><p>taja tare da dangwarar dasu yana kallonta da ya</p><p>kara mai ya tada injin sa yazo ya kwashe ledodin</p><p>ya shiga falonta.vels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 2</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 2</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:44</p><p>Kujerun da aka chanza mata masu kyau, amman</p><p>a ran abba yace ya basu sati biyu. Ya cire riga ya</p><p>fito yana son yayi wanka ne kafin a kira sallar</p><p>magana,yaja ruwa da sauri da sauri yayi ban daki</p><p>ya fito ya shiga falo ya kwalama bishira kira.</p><p>Tace minene kake damuna? Yace ina aka kai min</p><p>akwatuna na? Tace tace ina kuwa gasu can a</p><p>kicin da sauri ya fito, kicin din lafia? Ya tsaya</p><p>yana kallonta bani da mutuncin da za'a sa min</p><p>kayana a daki? Tace ni da aka guji dakina da</p><p>kayan a kace ni kazama ce, me zaisa in sake</p><p>kaine? Daga baice komai ba ya nufi kicin ya</p><p>kwaso akwatuna shi da takalmin shi ya kai</p><p>falonta. Bai tsaya chanza kaya ba, ya nufi</p><p>masallaci don zai rasa sallah. Bai baro masallaci</p><p>ba sai bayan isha'i amman bishira tana zauna.</p><p>Ummi kam ta kasa fitowa don tana kyankyamin</p><p>ban dakin, gashi al ada ta sameta da yamman</p><p>nan, sannan duk tanajin abin da sukeyi da</p><p>matarshi. Ya shigo gidan ya chanza kaya sabi fil,</p><p>ya feshe jikinsa da turarukkanshi wayar shi ta</p><p>soma ringing ya daga salis ne. Yace aboki in ba</p><p>sallama akwai daga hannu ko? Kace an kai maka</p><p>rabin ranka koda ba zamu rakaka ba ai kayi</p><p>mana sallama. Cikin dariya Abba yace na yafe</p><p>salis yace To Allah ya bada zaman lafia. Suka yi</p><p>sallama zai aje wayar kenan sako ya shigo. Ya</p><p>duba ummi ce da wayar nan da ya bata ajiya</p><p>cewa tayi, ina da matsala, ina bukatar taimako.</p><p>Gabanshi ya fadi, sai kuma ya tuna kila al'adar</p><p>ce, don haka sai ya saka hularshi ya dauki ledar</p><p>audugar ya nufi dakinta. Har lokacin bishira nan</p><p>zaune inda take, tace au tun daga yanxu za'a</p><p>soma rashin adalcin? An dauki leda an nufi</p><p>dakinta? Sam baiko waiwayo ba, yayi sallama ta</p><p>amsa tare da gyara mayafinta, ya shiga suka kalli</p><p>juna Cikin ido zukatansu sukayi fari kal. Cikin</p><p>taushin murya yace, wane taimako kike bukatar?</p><p>Ta lumshe ido sannan ta juya masa baya domin</p><p>kunya ta rufeta. Yace To karba ya mike mata</p><p>ledar ta waiwayo ta ansa da hannu biyu. Mamaki</p><p>ya cikata ganin audugar, ya yayi har ya san tana</p><p>bukatar audugar kuma a ina yake sanin lokacin</p><p>al'adarta har idan ya chanza? Tace nagode yayi</p><p>dan murmushi nima ina godia. Ya juya har ya</p><p>daga labule tace "Em na ce....." ya waiwayo yace</p><p>kika ce mi? Tace don allah inason maganin</p><p>wanke bayi ne, tayi maganar Cikin kyankyami,</p><p>sakamakon irin dattin da tagani a bandaki tare da</p><p>gamsa kuka. Yayi murmushi wane iri kikeso?</p><p>(IZAL) yace ai akwai amman yanxu Bai kamata ki</p><p>shiga wankin bayi ba. Tace zan wanke in dai</p><p>akwai. Yace bari in wanke maki, da sa tace a'a</p><p>yaya Abba zan wanke. Falon ya koma ya cire</p><p>rigarshi ya shiga jan ruwa. Bishira tana zaune ta</p><p>mike ina badai abokitaina ba, in zaka kwashe</p><p>mata rijiyar kwashe, amman a juye ko in baras</p><p>kuma in dai ruwan da za'ayi amfani dashi ne</p><p>kakeja, To kesani nima duk lokacin da zanyi</p><p>amfani da ruwa saika dibar min, ehee. Ummi ta</p><p>fito da bokitai don duk tana jinsu, tazo wurin</p><p>Cikin sanyin murya tace, Ya Abba don allah ka</p><p>bari in ja ruwan nan. Ya kalleta, take ya manta da</p><p>duk bakin Cikin da bishira ta kunsa mashi.</p><p>Yanxun daga zuwa saiki fara jan ruwa? Ummi</p><p>tazo ta kama igiyar gugar, ai ba zama nazoyi ba,</p><p>Ya Abba bauta nazo yi, Aljanna sai an dage. Ya</p><p>saki dariya bishira ta dakatar dashi da ce wa</p><p>"Karuwanci za'a gwadaman? Ta daga ruwan da</p><p>ya zuba a bukati zata watsama ummi, yace kina</p><p>watsa mata zan baki Mamaki. Cikin tsawa yayi</p><p>maganar ta tsaya cak da bokitin yace, Sakarya</p><p>mai kishin hauka. Yaci gaba da jan ruwan yana</p><p>zubawa abokitan da ummi ta fito dashi. Bishira</p><p>ta aje ruwan sannan ta hankadar dashi a kasa,</p><p>Bai ko kalleta ba. Ya zuba ruwan sannan ya fito</p><p>da izal da omo. Daki ummi ta koma ta dauko</p><p>tsinsiyar da aka sai mata don wankin bayi, kin</p><p>tafiya Abba yayi tana wankewa yana zuba mata</p><p>ruwa har sai da taga bayin yayi yanda take</p><p>bukatar sannan ta hankura. kyankyami jikinta</p><p>takeji don haka taje ta hada kayan wanka har</p><p>lokacinzurfin Ya Abba yana wurin rijiyar. So take</p><p>ya matsa taja ruwan amman yaki, don ya lura</p><p>bishira shi kadai take shakka zata iya zartar da</p><p>komai kan ummi. Shine ya sake zuba mah ummi</p><p>ruwan wanka, sannan ya coge har ta gama ta</p><p>fito rufe da hijabi tayi dakinta, sannan ya dauraye</p><p>jikinsa yaje ya maida kayanshi ya nufi wane.</p><p>Bishira tana nan wurin kofarta ta kasa zaune ta</p><p>kasa tsaye, bakinta kuma Bai fasa sambatu ba</p><p>sai kace sabon kamun hauka. Fadi take kuma a</p><p>zo a biyani duk basisikan da nike, ehee. Kuma in</p><p>yarinya tamin in murji bukina. Ummi kam ta</p><p>gyara jikinta tsab ta saka sabbin kaya ta feshe</p><p>jikinta da turarokan da umma ta sai mata. Tunda</p><p>ba lefe aka mata ba bare ta samu kayan shiga.</p><p>Kan doguwar kujera ta mike, salam yanzu taji</p><p>yinwa tana tsammanin rabonta da abinci tun</p><p>karin safe. Ta shafa Cikin ta ina ma umma na</p><p>aiko man da abinci. Ta furta a fili WAYA nan ta</p><p>jawo tana tunanin sanar da Abba cewa tana jin</p><p>yunwa. Sai wata zucia ta hanata wannan ba</p><p>girman amarya bane. don haka ta share ta bude</p><p>shafin game tana ta bugawa. Sai sha daya Abba</p><p>ya shigo gidan, ya rufe gidan. Nufinshi ya wuce</p><p>kai tsaye dakin ummi, amma sai ya tuna da kazar</p><p>da ita bishira ya sawo mata. Duk da baya tunanin</p><p>ta karba ga mamakinsa tana tsaye a tsakar daki</p><p>har yanxu da daurin kirji take. Wannan ya nuna</p><p>batayi sallah ba, bare wanka. Ya mike mata wata</p><p>harara ta zabga masa banaci, ya juya batare da</p><p>yace mata kala ba, ta biyo bayan shi, A bani</p><p>basussukana da nike bi malam. Ya nufi dakin</p><p>ummi taba biye dashi, ummi ta turo kofa dama</p><p>yana kokarin tura kofa dama yana kokarin tura</p><p>kofar bishira tana rike masa riga ta baya. Ya</p><p>waiwayo Cikin zafin nama zai wanka mata mari</p><p>sai taci sa'a ta tsugunna, Cikin azama ta yunkura</p><p>tayi baya da gudu. Banda tsaki da yaja Bai ce</p><p>komai ba. Ya shige dakin ummi da sallama, ummi</p><p>bacci ya dan dauketa saboda gajiya. A kan kujera</p><p>take da waya a hannunta. 4rm Shamsy bello</p><p>balarabe.IKI novels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 3</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 3</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 00:48</p><p>Niyyarta yau sai taji komai, don haka ta kai yarta</p><p>ta kwantar, dai dai lokacin ne abba ya fito don</p><p>kashe injin. Sake fitowar da tayi ne taganshi zai</p><p>koma. Wayan cewa tayi da daukar buta ta shiga</p><p>bandaki, shi kuma ya shiga daki ya kulle kofa,</p><p>tazo ta manne jikin kofar. Fitar abba shine yaba</p><p>ummi damar saka kayan baccinta, don bata iya</p><p>bacci da kaya masu nauyi. Fargabarta yaya</p><p>kwanciyar tasu zata kasance? Kan kujera ta</p><p>zauna tare da kwantar da kanta a hannun kujera.</p><p>Shima abba yana da jin zafi don baya iya bacci</p><p>da kaya sai da gajeran wando kurum, idanu ummi</p><p>ta kulle lokacin da taga ya abba ya soma cire</p><p>tufafinsa ga hasken cocilar da ya kunna. Filo ya</p><p>dauka ya jefa Kan doguwar kujera ya kwanta</p><p>rigingine, ganin haka sai ummi ta mike ta nufi</p><p>gado addu'a tayi sannan ta lumshe ido har bacci</p><p>ya dauketa. Fuskarta cike da murmushi zuciyarta</p><p>cike da godia allah yau gata dakin ya abba a</p><p>matsayin matarsa. Abu daya ya rage mata shine</p><p>ta koya masa yarda zaya sota. shima farin ciki</p><p>ne a ranshi yayi da idanuwanshi sukayi kuri a Kan</p><p>gado yana hango ummi ya ta zama halalinsa Abu</p><p>daya ya rage shine ya koya mata sonsa. Bishira</p><p>data labe bata jiyo komai amman kunnuwanta</p><p>suna jiyo mata magana kasa kasa,,hawaye na</p><p>zuba a idonta batasan iya adadin awanin data</p><p>dauka a kai ba. Koda ta koma daki juyi kawai</p><p>take a gado. Abbanta abun sonta yana can</p><p>kwance da wata, watar ma makiyiyarta wadda ta</p><p>tsana. Wata zuciya tace kije ki watsa masu man</p><p>petur wata tace ki bari da safe ki caka masu</p><p>wuka babu abinda bata rayaba har asubahin</p><p>farko. Labule ta daga ta shiga leke taga ko zasu</p><p>fito, lokacin ne kuwa abba ya fito yaja ruwa a</p><p>bokitai yayi wanka da alwala. Ba zata gane ko</p><p>wani Abu ya faru tsakaninsa da ummi ba don</p><p>wanka al'adarshi ce Koda bai dauki najasa ba.</p><p>Nafila ya shiga yi da rokon allah yasa ummi ta so</p><p>shi, ya kuma hada masa kansu. Koda zai tafi</p><p>masallaci bai tashi ummi ba tunda yasan ba</p><p>sallah zatayi ba. Bishira ta fito tasa kujera kofar</p><p>daki ta zauna, saboda tashi bai bar ummi bacci</p><p>ba, don haka ta tashi in tana al'ada yini take</p><p>wanka gaba daya sai ta tah ktankyamin jikin ta.</p><p>Ta fito da bokitai duk ta cika d ruwa, Bishira tana</p><p>kallonta sai da ta wanke bayi tas, sannan tayi</p><p>wanka. Sauri take tayi kwalliya don a cikin</p><p>nasihohin da umma tayi mata a safiyar da za'a</p><p>kawota gidan miji tace kada ta sake mijinta ya</p><p>ganta cikin kazamin yanayi. Kuma kada ta bari ya</p><p>shaki wari daga gareta, tayi shafe shafenta.</p><p>Atamfa ta saka riga da siket mai ruwan hoda</p><p>hoda da ruwan kwai. Daurin dan kwali ta kafa</p><p>sannan ta feshe jikinta da turaruka masu kamshin</p><p>gaske, sannan ta shiga gyaran dakin duk da ba</p><p>datti yayi ba. kayan da abba ya cire ta ninke don</p><p>da jallabiya yake zuwa masallaci, sannan ta dau</p><p>kujera ta kishingida saida gari yayi haske sannan</p><p>ya nufo gida. Tsaki bishira ta jamashi maimakon</p><p>amsa sallamar ta kara da cewa an girma ba'a</p><p>san an girma ba, an kwana da yar ciki abin</p><p>kunya. Ai wallahi baka cika dan halas ba da ka</p><p>auri yarinyar datayi sanadin kulleka kaci duka har</p><p>aka ballaka ba. Ya kalleta dalilin kenan da ban</p><p>cika dan halas ba? Tace eh baka cika ba, yace</p><p>toh jeka naji ni shege ne, in don dai na auri ummi</p><p>ne, tace munafuki dama can kana sonta. Ya sake</p><p>wai wayoowa yace so kuwa mai tsanani. Takaici</p><p>ya cikata ta daga murya allah ya isa munafuki.</p><p>Ya nufi dakin ummi wadda ke sauraren duk</p><p>abunda ake. A cikin ranta tace ina ma son da</p><p>gaske ne? Tasan ya fada don kawai yaba</p><p>matarsa haushi. Da sallama ya daga labulen,</p><p>ummi ta amsa tare da tashi daga kishingida da</p><p>tayi, ya zauna tare da lumshe ido. Lokacin daya</p><p>kuma ya shaki kamshin turarukan data fesa. Ya</p><p>kalli Fuskarta labbanta da yake matukar so sun</p><p>sha jambaki ruwan hoda. Take abba ya manta da</p><p>duk wata damuna koh kalma marar dadi da</p><p>bishira ta fada masa. Daga inda take zaune ta</p><p>dan rankwafa don girmamawa tace ya abba ina</p><p>kwana? Lafia qalau ummin abba ya bakon wuri?</p><p>Ta lumshe ido saboda jin dadi sunan daya fada</p><p>mata. Alhmdllh ya sake karkatawa yana kallonta</p><p>sosai yace to masha allah, yanxu kinsan minene?</p><p>Ta tattara hankalinta gareshi tace a'a? Yace kiyi</p><p>hnkr nasan a al'adar ta hausawa amarya ta Kan</p><p>yi sati daya cir ba tare data yi ko cangal ba. Toh</p><p>hnkr zakiyi kinga ke tun daga kawoki jiya kin</p><p>soma da wanki toilet. Sannan yanxu ma ina son</p><p>ki ciro rishonki a hada shi a sa kalanzir mu karya.</p><p>Kin dai ga yanayin yanda matar gidan take</p><p>gudanar da nata kishin. Ummi ta gyara zama ta</p><p>tuna nasihar ummanta da tace in zaki yima</p><p>mijinki magana kalaman ya zamana kin zabo su</p><p>ne ba wai kin sakesu ba. Ta kalle shi, shima ita</p><p>yake kallo, tace ya abba don wannan ne kake ban</p><p>hnkr? Yayi murmushi tare da lumshe ido ya kuma</p><p>budesu lokacin guda, a yaran soyayya yana nufin</p><p>eh, itama ta fahimci yaren don haka taci gaba da</p><p>cewa. Ya abba ni dama ba zama nazo ba, neman</p><p>aljanna nazo kuma zanyi komai don na sameta.</p><p>Don haka kadaina bani hnkr umurni kawai zaka</p><p>bani. Tun daga tsakiyar Kan abba har zuwa</p><p>babban yatsansa sai da ya motsa, don sanyin</p><p>muryar da ummi tayi amfani da ita tare da</p><p>kyawawan kalaman ta. A zuciyarshi yace tabbas</p><p>ummi haihuwar ummanshi ce, duk rainon umma</p><p>dole zai zama daban ciki ya'ya. Ya kalli ummi</p><p>allah yayi maki albarka tace amin. Ta mike ya</p><p>bita da kallo taje gurin da a ka shirga mata</p><p>kayan aiki ta zakulo risho yace to muje kicin dinZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 4</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 4</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 01:13</p><p>Ta mike ya bita dkallo tje gurin da aka shirge mta</p><p>kayan aiki ta zakulo risho yce to muje kicin din.</p><p>Tkarya murya, ya Abba amin afuwa, bna son in</p><p>shiga kicin din can kmin hakuri insa rishona</p><p>akofar daki. Ykalleta, bazai tkura mta ba domin</p><p>ysan duk wnda yzauna da umma dole zai zama</p><p>me kyankyani, yce indai zai miki kiyi kawai , in na</p><p>smu ynd da nke so dga baya sai ayi miki kicin a</p><p>gurin, tce ngd. Shi kan da kanshi yfito darisho yn</p><p>budewa ya hadashi, tafito da tukunya tanufi rijiya,</p><p>ta dauraye sannan tazubo ruwa.Bishira kuwa</p><p>dma tazo talabe duk tji maganganun dsu kayine,</p><p>jin abba zai fito da risho sai ta gudu daki. Sintiri</p><p>ta dinga yi tna magana ita kadai, wato abban</p><p>walid nece mazai ce anga irin nawa kishin?</p><p>Yarinyar dya ce bsonta yke ba dole akayi masa</p><p>shine har ysoma kai mta gulmata. Har dawani shi</p><p>mata albarka , tunda uwarta ta kitso mata ynda</p><p>zata ce ai dole yashi mta albarka, to ni ya tsine</p><p>min kawai. Ummi ta amshi galan din kalanzir din</p><p>dga hannunshi tre da cewa ya abba kawo inzuba</p><p>zai ce ta barshi kenan wayarshi ta soma ruri,</p><p>yadaga. Anty ce, suka gaisa tce tna son yin</p><p>magana da bishira ya mike ytafi kaimata ummi</p><p>kam ci gbata yi dasa kalanzir dinta takunna</p><p>rishon tdora ruwan zafinta takoma daki, shima</p><p>yna bt wayar ydawo. Anty tce bishira dm na kira</p><p>kine inji bakuwar dta kwana a gidan da safennan</p><p>kin bta abin kari ko? Bishira tahade rai tamkar</p><p>tana gabanta, anty tome mexan bta, ina ruwana</p><p>ma da ita? Dazunnan fa suka gama gulmata wai</p><p>har yna ce mta tye hakuri tdai ga irin mtar gidan.</p><p>Anty tce hauka kike tyi shi ysa ai dole yce haka.</p><p>Ynzun dai sai ki tashi kibsu abin kari, hka da rna.</p><p>Karki sake yarinyar nan ta dora tukunya sai byan</p><p>sati daya, kina jina ko? Bishira tace to bdan</p><p>zancan ykai ranta ta amsa ba. Sai don tunanin</p><p>kada zancan zuwa makkanta yafasu . Sunayin</p><p>sallama ta aje wayar tre da cewa, koda uwarta</p><p>tke ywo bzan dfa mta abinci ba. Sai da ummi ta</p><p>wanke flas din shayin sannan tazuba ruwan, falon</p><p>bishira yje ydauko kayan shayin dbiredi. Tace,</p><p>itama kakai mta ruwan zafin. Yce ta dafa, ygama</p><p>yashirya tsaf don zuwa gurin aiki, harbakin kofar</p><p>daki tarakashi. Yce, ummi naroke ki koda bishira</p><p>tna zaginki ne don Allah kda ki kulata, sambana</p><p>ganin laifinta don nasan sboda sona tkeyi. Nan</p><p>da wni lokaci komai zai daidaita. Ummi tce kada</p><p>kadamu insha Allah ba abin dazai faru, allah ya</p><p>tsare yace amin nagode. Dakin bishira yaleka ya</p><p>amshi wayarshi, sannan yce mezakuyi drana?</p><p>Tzabga mishi harara, ina ruwana dawani abinci.</p><p>Ya aje mata dari hudu. Gashi kusai nama nasan</p><p>akwai komai ko? Tsaki taja, gara maka dauki</p><p>kudinka don bzan dafa ma munafukai suci suji</p><p>dadin zagina. Yakalleta, Allah yganar dke. Tdg</p><p>murya yganar dakai dai maci amana sainaga</p><p>bayanku. Bki yataba kafin yafita, baice mata kala</p><p>ba. Ummi ta kinkimi akwatinan kayan abba dya</p><p>kawo mt tgyara msu mzauni, sannan takwashe</p><p>'yan kofunan dasuka sha tea ta wanke. Sannan</p><p>takoma dki tna jin wsu kawayen bishira sunzo</p><p>sunata habaice dazage-zage, ummi bt fito ba</p><p>bare ta tanka. **** **** Bashir abin duniya ya</p><p>ishe shi, ykasa sukuni sbd son ummi, yzuga</p><p>ummanshi sun kai suka gidan su sahabi don</p><p>afasa auran anfasa kuma duk da hk ummin</p><p>tzama btashiba. Jinshi yke tamkar ykashe abba</p><p>don tsana, don hka koyaushe cikin zuga umma</p><p>yke dan kawai tatsani Abb. Guraran sha biyu</p><p>ummi bacci yasoma dibanta sai tji muryar</p><p>umman bashi akofar dakinta tna cewa ina ummin</p><p>tke munafauka, fitsararriya tadaga labulan kofar</p><p>tarike. ummi takalle ta. Kin kalle mi mna 'yar</p><p>makirai. Kin bar smun zman lfy a gidannan, kuma</p><p>uwarki ko tn tsafi dbakin kare dbakin dodo sai</p><p>kinbar gidan dana. Ke inzan tafi dazani daya</p><p>mtsawar bokaye da 'yan bori suna nunfashi kin</p><p>smun nutsuwa agidannan. Bishira tace, umma</p><p>shima munafuki ne shida yce bai sonta amma</p><p>dazun haryi dni sukayi. Umman bashir tce shi</p><p>Abba kimasa uzuri, duk abinda ykeyi byin knshi</p><p>bne, anriga an rikita shi, bakya ganin shi duk</p><p>afirgice yke? 'yar bori tafada min komai, ynzun</p><p>karya tambaya muke nema. Bishira tce duk dhaka</p><p>ma ynso, ai ance asiri yan tarad dahali. Umman</p><p>bashir tce hk ne, shi dinma ai ubansa zaici ba</p><p>dagin kafa. Ummi datna zaune kai duke, sam</p><p>zantukansu bsu dme tba, abu dya yagirgizata</p><p>btun asiri. Bta son ashiga tsakaninta da mijinta</p><p>tun kafin su fara son juna. Saidai kuma dta tuna</p><p>da addu'o'inta da takeyi bta fsa yi ba. Ga Azkar</p><p>safe dayamma, saitasamu ntsuwa tsan Allah</p><p>yafisu.ovels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 5</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 5</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 01:33</p><p>Umman bashir tagama jarabarta tafita, karfe daya</p><p>drabi Abba ykira wayar dke hnnun ummi tdaga.</p><p>Cikin girmmawa tce, snnu da aiki ya Abba, ina ftn</p><p>kn cikin koshin lpy? Yyi murmushi cikin jindadi</p><p>yce, lpy nke ummi, am...in... Dama zan cene kin</p><p>ci abinci? Tce A'a, amma bna jin yunwa, dnaji</p><p>yunwa zn sha tea ai, kda kdamu kai fa kci? Yyi</p><p>dan tsaki, tsiyar bna cin abinci awaje ummi,</p><p>abincin umma kdai ke min dadi, Allah ys zki gjeta.</p><p>'yar driya ummi tayi, insha Allahu sai mna fita.</p><p>Yce anya kuwa? Tce insha Allahu ai nace. Kin</p><p>gma mgna yafadi tre dyin murmushi mai sauti,</p><p>yawwa bari in kirata ta turo miki da abinci, tce to</p><p>ngd. Yce, nima na gode, sai ndawo. Tce, to Ya</p><p>Abba kdawo lpy, ka kula min dkanka. Tkashe</p><p>wayar, yjima yna kallon wyar tre dmamakin ynda</p><p>ummi ta iya zantuka masu kwantar dahankali, irin</p><p>wdanda bishira da ta ba ta shekaru bta iya ba.</p><p>Ykira lyin ummanshi suka gaisa, yce ummana don</p><p>Allah kitura ma ummi abinci, umma tce, kan wani</p><p>dlili Abba? Tci gba dacewa, tbdijam!, bza ayi hk</p><p>dniba. Abba ymarairaice murya, don Allh ummana</p><p>yunwa tke ji. Umma tce, ta tashi tdora mna?</p><p>Abba tsaya kaji, dadai wta ce can kke aure ba</p><p>ummi ba sai na aika mta, amma ynzun ga</p><p>uwargidanka agidan shi kenan sai in aikamata da</p><p>abinci? Wannan ba gsky bne, sannan zgin da ake</p><p>min ai sai ya linku yfi nada, yce umma duk wnda</p><p>yzageki rshin fhimta ne. Kuma fana baiwa bishira</p><p>kudin cefane amma tki tdafa musu abinci, tce kila</p><p>tgaji ne, shiyasa bta dfa ba. Ita ummi dba saita</p><p>amsa tdafa musu ba? Yce, amma dai umma</p><p>tsakani da Allah kowacce amary bsai ta kwana 7</p><p>bsannan tke fara dfa abinci? Umma tce, ai ba</p><p>addini bne al'ada ce, don takama girki ai ba laifi</p><p>tyi ba, yce, shikenan umma tunda kin hna sai</p><p>anjima, tce mujima dayawa. Shiru abba yyi yna</p><p>tunanin mgangnun umma, ysan gsky tfada, amma</p><p>dmuwarshi ummi dbta ci komai ba. Ykalli agogo,</p><p>saura kusan awa 2 ytashi, wayarta yske kira,</p><p>tdaga yce ummi kisha tea din umma bta da</p><p>abinci kfin ndawo. Tce, to ya Abba, kkusa</p><p>dwowane? Yce, sai nan da awa 2. Tce to Ya</p><p>abba, sai ka iso. Bta wni sha tea bdon bta jin</p><p>yunwa sam, tshi tayi tasake kakkabe dkinta don</p><p>mutane suna tshigowa ganin dki yra dmanya. Tas</p><p>tkakkabe ko ina tafito tshare tsakar gidan lungu</p><p>dasako, bishira lokacin mbata gidan wsu yra</p><p>dsuka shigo tbasu kasko suka smo mt rushi</p><p>tzuba turaren wuta mai kyau dkamshi. Tnayi tn</p><p>kallon agogo, saura minti ashirin yaya Abbanta</p><p>ydwo ta wanke byi tsake wnka, sannan tdibar</p><p>masa ruwan wanka shima ta aje akofarta. Trufe</p><p>kafin ya iso, tshiga dki tna ta shafe-shafenta, sai</p><p>lokacin bishira ta shigo gida. Tna rike da 'yarta</p><p>akafada, ita kanta 'yar ba amata wanka ba bre</p><p>uwar, tkwabe hijabi trataye, sannan tzauna akofar</p><p>dakin tna kallon tsakar gidan. Duk da ita knta</p><p>gurin ybta sha'awa, amma bki ta taba tre dcewa,</p><p>wahalalliyar bnza. Ummi tayi mtukar kya cikin</p><p>wando da riga nawani ydin dshi Abba ydinka mta</p><p>a babbar sallar dta gbata. Tasaki gashinta sosai</p><p>tyi wani daurin dankwalin da ita ce ta iyashi</p><p>amma gshin nta duk yna wje. Tfesa turarukanta</p><p>sannan tfada kan kujera, tkalli agogo minti goma</p><p>takaru akan lokacin dya fada mta. Zuciyarta tdan</p><p>dmu tkosa sosai ta gnshi bta ki yzauna agida tyi</p><p>ta kallonshi tre da sauraron muryarshi ba. Sai</p><p>dkusan minti 20 sannan Ya Abba yshigo, tsayawa</p><p>yyi yna kallon tsakar gidan, yau kam farin cikine</p><p>ya mye gurbin bakin cikin dyake ji aduk lokacin</p><p>dya shigo gidan ykalli tsakar gidan. Kamshin irin</p><p>turaren wutan da umma ke cika gidanta dashi ne</p><p>yke shaka. Ysaki murmushi tre dyin sallama,</p><p>bishira dke zaune dabas atsakar gidan maimakon</p><p>ta amsa sallamar sai tsaki taje dogo tre da cewa.</p><p>Aikin bnza. Kallonta kurum yayi ranshi ya baci.</p><p>Bai cemata kala ba ynufi dkin ummi, tyi nisa cikin</p><p>buga game. Sallamarshi ceta sata yin jifa da</p><p>wayar akan kujera tamike tdaga labulan daidai</p><p>lokacin dyke cewa inshigo? Ta amsa sallamar</p><p>dwata murya wadda bta san ma tna da ita ba,</p><p>suka kalli juna cikin ido, lokaci 1 suka ski</p><p>murmushi tmika hannu kafadarsh rtaye da wta</p><p>jaka wadda bda ita yfita ba. Ya salubo jkar ymika</p><p>mt tre dcewa, kirike dakarfi, tce to, sannu</p><p>ddawowa. Yshigo rike da leda ahannunshi yzauna</p><p>tre dcewa. Yauwa, tnufi robar ruwa data dauraye</p><p>jug din data tnda don shi kadai, tzubo ruwa tzo</p><p>dakofi tadauraye kofin snnan tzuba ruwan tmika</p><p>msa tre dsake cewa, sannu dkokari. Ydubeta,</p><p>yauwa kema sannu dkokar, dud da byajin kishi</p><p>dole ne ysha ruwan, ybude bki ysoma shan ruwa.</p><p>Sai yaji ruwan yfi duk wani ruwa dyasha a tsayin</p><p>rayuwarshi gardi dkuma dadi, ydubeta ido lumshe</p><p>dama ruwan amare dadin shi dabanne?? ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 6</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 01:37</p><p>Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa,</p><p>yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire</p><p>takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan dan</p><p>teburin da aka aje don dora abinci ko kofi. Tazo</p><p>takwashe tkalman tkaisu kusa da kofar fita tyi</p><p>musu ajiya mai kyau, sannan tadauko dan twul</p><p>tshare kasar gurin. Ykalleta, yi hkuri nshigo miki</p><p>dki datakalmi ko? Tce bkomai aranshi yce nsaba</p><p>shiga dakin bishira da tkalmi. Yjanyo ledar dya</p><p>shigo da ita tre dcewa ummana tki aiko miki da</p><p>abinci ko? Tace, kyi mta mgnane? Ya ciro take</p><p>away din yasiyo mata, zo kici, ai dole ta bmu na</p><p>dare, zan jene in tsaya mata. Ummi tdubeshi,</p><p>anty bishira fa ka bata nata ne? Yyi mta banza,</p><p>tduba ledar tga guda daya gakuma wnda yciro</p><p>mata. In kaima anti bishira? Ydaka mta tsawa tre</p><p>dharararta, ke! Ban aike kiba, tatsaya tna</p><p>kallonshi, meye ruwanki da mtata, kin fini snin</p><p>meye kamata nayi kenan? Yja dogon tsaki tare</p><p>djanyo jakar dta dora mishi akan gado, jikin ummi</p><p>yyi sanyi. Ta tuna damaganar da umma acikin</p><p>nasihar dta mta, kda kizama dga cikin mtan</p><p>dsuke btawa mzajensu rai. Hakan yna sawa miji</p><p>yatsani matarsa, kiyi tka tsantsan kinsan hlin</p><p>abba yna dsaurin fushi. Dsauri ummi tasulalo dga</p><p>kujera. Don Allah kyi hkuri ya abba, ban san</p><p>zakaji haushi ba. Ydubeta fuska daure, hwaye</p><p>ygni sun cika idonta yace, kda ki sake hawayen</p><p>nansu zubo, tsa ytsunta tdanna idnunta, tshi ki</p><p>zauna ki dauki abinci kici. Tzauna tarike abincin</p><p>tkasa ci. Ykalleta suka hda ido cikin ido, tariga</p><p>shi mgna kayi hkuri Yaya Abba, tausayinta</p><p>ykamashi amma sai ydake. Bnason kisake mgna</p><p>akan abinda yshafi mtata kinji ko? Da sauri tce,</p><p>bzan kra ba. Yyi dan murmushi ci abincinki.</p><p>Tasauke wta irin ajiyar zuciyar dhar ya klleta da</p><p>ido ya tmbayeta lpy? Dabaki tfurta lpy lau, yce ci</p><p>abincinki. Ummi tdauki abinci tn ci, jefi-jefi tna</p><p>kallonshi, shi kuma yna ta kokarin kunna laptop,</p><p>don ymantar da ita. Yce, kinsan menene wannan?</p><p>Ta a'a yace computer ce, agurin aikinmu aka rba</p><p>mna. Ummi tace, kyauta? Yce A'a za'aringa</p><p>cirewa acikin albashinmu, mtso kigani. Tdan</p><p>mtsa inda zta iya kallowa, ykunna yna nuna mta</p><p>abubuwa, yce ai nsan ki zaki iya sarrafata, tce</p><p>wai, bazan iya ba Yaya Abba. Yce, nima sai</p><p>nshiga mkarnta akwai tnan cikin gri zan shiga nyi</p><p>diploma, salis shi tuni yyi. Ummi tce amma gshi</p><p>ynzun mkana sarrafata, yce ina dan hwa ta office</p><p>dinmu ai tce tayi kyau Allah ysa albarka yce</p><p>amin. Ykashe komai ydauki take away din ynaci.</p><p>Sannan yce, bri infita. Tdube shi itakam bta son</p><p>yfita don umma tce mta tzama mai tsare mijinta</p><p>dga zaman majalisa koyawo. Indai ba mkarnta</p><p>yke zuwa ba, yma ztayi thana shi fita tatambayi</p><p>knta, tdube shi cikin tausasa murya. Ya Abba hka</p><p>zka fito bkayi wnka ba? Tmike gruwa nan nadiba</p><p>bari inkai mka, shima ymike. Sai anjima zanyi</p><p>ummi, ynzun shago nke sn zuwa. Akwai wsu</p><p>dinkuna da za a amsa yau ina son ingako yaran</p><p>sun gama snnan inson in yanka wsu dunkunan</p><p>ciki har dnaki, koda yke saina gwada ma tukunna.</p><p>Tce, tokadan huta mana ynzun faka dawo, ygane</p><p>bta son yfita ne, don hk yce kda kidamu dg shago</p><p>ba inda zanje. Har bkin kofa tarako shi tarike</p><p>labule, to sai kdawo, yce to, ynzun mbai kalli inda</p><p>bishira tke ba, yyi wje. Datsaki traka shi tre</p><p>dcewa, girma dai yfadi warwas, murmushi yyi mai</p><p>sauti yfice abinshi. Ita kuwa sai thau zntuka,</p><p>kinibibi a auran mka miji sannan a nuna anfi ka</p><p>sonshi, yrinya lokaci nabaki. Ummi dai sai tkaro</p><p>kofarta, koda dre abinci daidai cikinta bishira tyi</p><p>taci tba 'yarta shiko Abba bai shigo gidan basai</p><p>bayan sallar isha'i. Byan yje sun sha dirama da</p><p>umma, tce itafa bta yi abinci dsuba, yce umma</p><p>gskiya toki bmu na babanmu. Tyi driya, kasan</p><p>abin dakake fada kuwa abba? Inbaku abincin</p><p>mijina? Ai kuwa bkwaci ba. Tsohuwa tace, kai ina</p><p>mtarka ita bazata dafa fa? Kodon tsoronta</p><p>fakakeji ko? Abba yce eh bazata dafa ba ina</p><p>ruwanki ke tsohuwa kin cika sa ido. Tce, nasa</p><p>din, ai gskiyane kowa ysn uwargida ke yin girki</p><p>harsati guda. Abba yce, to mu tsarinmu bhka bne,</p><p>tkwashe da driya. Bwani tsarinku bhaka bne kila</p><p>ma kinyin girkin tyi, yce oho dai bza kiji bdai, tce</p><p>jeka intayi tsami mji. Umma dke tsheka driya tce,</p><p>abbana zoka dauka gashi nan yce, yauwa</p><p>ummana mungode, tce abba bka shiga gidan</p><p>nanne? Yce wai gurin umman bashir? Tce eh, yce</p><p>ina zuwa mna, tce todon Allah kadinga shiga, nan</p><p>yyi musu sallama ytafi. Lokacin dya shigo gidan</p><p>dindim! Sai daya tda injin, aranshi cewa yake yi</p><p>lallai mta dakíshi, jimatar dko darana tada inji tke</p><p>yi amma ynzun don kda wtan tga hske ko tji iskar</p><p>fanka shine taki tadawa.I novels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 7</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 7</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 01:41</p><p>Ya aje kular kofar dakin ummi yaleka dakin</p><p>bishira, tana kwance kan gado, itafa bata jin cewa</p><p>zata dazama dakishiya, dole cikin biyu ayi daya,</p><p>kota tada ballin dazai saketa komuma tanemi duk</p><p>wata hanyar daza akori wannan 'yar iskar</p><p>yarinyar. Yashiga dakin, muhibba daketa wasa</p><p>akan gadon da baya zaton tun da aka kafashi</p><p>tasake kakkabe shi, yace hibba. Yarinyar ta</p><p>waiwayo cikin murna tanufo ubanta da dan</p><p>gwaranci, bishira tasa hannu tasuri 'yarta yace,</p><p>bishira duk wannan abin daki keyi fabashine</p><p>mafita agare kiba. Ki kwantar da hankalinki ki</p><p>nutsu ki kama girmanki, yarinyar nan zata biki</p><p>amma in kin zabi akasin haka kece zaki koko....</p><p>Kai malam! Ta katse shi, bafa wata sauran</p><p>magana fanasan komai, ni yanzun saki kurum nafi</p><p>muradi, ya ce sakin lafiya? Ni yanzun ma na</p><p>soma sonki, tadaga mishi hannu tare da daga</p><p>murya, nikuma nadaina sonka, karya ne makace</p><p>kana sona kuma kanason waccan banzar. Dole</p><p>acikinmu akwai wadda kafi so. Abba yace to ai</p><p>kece, ke nafi son kuma ita tasan haka, kalmar</p><p>tashi tadan sanyaya mata zuciya. Don haka bata</p><p>sake magana ba, yace kina bukatar wani abu ne?</p><p>Tace don Allah nidai ka fita kawai, yace to na</p><p>fita. Ummi lokacin tana canza kaya zuwa riga</p><p>dazani na leshi, sosai tayi kwalliya tamkar</p><p>kasureta ka ruga don kyau. Fuskarta sake ta tari</p><p>Abbanta dasannu dazuwa, ita ce tasa musu</p><p>abinci kowa da plate dinshi, amma sai ya aje</p><p>nashi yace suci nata. Dama taso yin hakan amma</p><p>tana tsoron kada ya gwasaleta, sai da sukayi</p><p>dam sannan yace bari yayi wanka tatashi takai</p><p>masa ruwan wanka tadawo. Kafin ya fito ta sake</p><p>gyara ko ina, jallabiya mai gajeran hannu yasaka</p><p>mara nauyi ya wadata jikinshi da turaruka tana</p><p>kallonshi cikin sha'awa. Taso taimaka mishi tun</p><p>agurin shafa mai, amma tana tsoron kada yaga</p><p>zakewarta, don haka tashare tare da cewa</p><p>dasannu za azo gurin. Ysake cewa zai koma</p><p>shago, tace haba yaya Abba yanzun kuma?</p><p>Yadauko tape dinshi nagwada mutane, zo in</p><p>gwadaki, har da kayanki zan yaka yanzun.</p><p>Yarannan 'yan shiriritane, badon naje dazun ba</p><p>dasun sani nasaba alkawari, dinkunan su kawai</p><p>suka yi tayi suka aje wanda nabasu. Ummi</p><p>tabata fuska, ya tausasa murya, come on zo in</p><p>gwada ki, bazan jima bakinji ko? Tatashi taje</p><p>gabanshi ta tsaya. Sai dai mamakinta duk</p><p>dunkunan da Ya Abba ya sha yi mata abaya bai</p><p>taba gwadata basai yanzun? Koya manta yanda</p><p>yake mata ne? Tsawon siket din ta ya soma</p><p>gwadawa, tana tunani sai taji ratsawar dan</p><p>yatsansa tare da tape din a kwankwasonta, duk</p><p>da cewa dariga ajikinta saida hakan yasa taji</p><p>wani yanayi ajikinta. Har ma takalle shi, haka nan</p><p>ya auna hips dinta da kirjinta, shi kanshi ya shiga</p><p>wani yanayi alokacin, haka nan yakoma shagon</p><p>cike dakewarta. Kayan bacci tasaka ta kwanta a</p><p>gadon tana da yakinin bazai mata komai ba,</p><p>tunda yasan bata sallah. Har kusan goma da rabi</p><p>tana jiran shigo warshi shiru, waya tadauka ta</p><p>rubuta mishi sako da cewa. Ya abba don Allah</p><p>kadawo ni dai tsoro nake ji. Ya karanta yayi</p><p>murmushi, azuciyarshi yace, don ita ya kwafe,</p><p>yayi dunkunan yana son kudin don ya sai mata</p><p>akwati da kayan shafa zuwa kayan ciki. Share ta</p><p>yayi sai kusan sha daya darabi sannan yatashi</p><p>tare da sallamar yaran, haka nan itama sai daya</p><p>hado mata duguwa rigarta ta shadda wadda</p><p>dama anriga anyi sirfani ajikinta. Dakin bishira</p><p>yasoma lekawa, bacci yadauketa sosai agefen</p><p>gadon take da alamun baccin yazo mata ba cikin</p><p>shiri ba. Abba yayi murmushi tare da cewa, wa ya</p><p>fada miki ana cin bashin bacci? Ina zaton matar</p><p>nan jiya bata runtsa ba, yau gashi yazo ba shiri.</p><p>Har ya gyara mata kwanciya itama 'yar ya gyara</p><p>ta amma bishira bata farka ba, don haka yakashe</p><p>mata wuta yafita. Yaso kashe injin amma garin</p><p>da zafi gashi basu kawo wutar nepa ba, gidan</p><p>yarufe yazo ya tura kofar ummi data rufe. Karar</p><p>kofar ne ya farkar da ita amma bata motsa ba,</p><p>tun daga kofar yatsaya yana kallonta, can</p><p>tsakiyar gadon takwanta bata dora kanta saman</p><p>filo ba. Amma tana manne da filo daya akirjinta</p><p>fuskarta yake kallo, a jikinta taji kallonta yakeyi.</p><p>Kusan minti 4 sannan ya aje ledar hannunshi.</p><p>Shirin bacci yake amma yakasa daina kollonta,</p><p>shikanshi yana mamakin wannar jarababben son</p><p>dayake ma ummi, duk da dakewar dayake don</p><p>kada yabada kanshi amma sai yadinga jin wani</p><p>abu yana fisgarshi. Tamkar yafito mata da zallan</p><p>sonshi gareta, tsoronshi inta gano kila tarainashi.</p><p>Kadan-kadan takan bude ido ta saci kallonshi, sai</p><p>daya gama komai a tunanin ta ya kwanta a</p><p>gadon amma sai taga yadauki filo yakwanta a</p><p>kan kujera. Haka suka rayu har tsawon sati daya,</p><p>ranar yabar dakin ummi ranar kuma tasoma salla,</p><p>ita ko bishira satin nan tayi shine tamkar</p><p>mahaukaciya sabon kamu. Ranar kuma da abba</p><p>yadawo dakinta bata runtsa ba shima bata barshi</p><p>ya runtsa ba, daga bisani dole yabar dakin</p><p>yakoma falonta yakwanta. Haka gidan yaci gaba</p><p>da kasancewa, in Abba yafita ummi bata da</p><p>sauran sakewa saboda zagi da habaicin bishira.</p><p>Wani sa'in har da kawayenta, ko makota 'yan</p><p>jam'iyarta su shigo suyi tayi, ummi bata kula su.qnovels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 8</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 8</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 01:50</p><p>Duk abinda bishira zatayi kada takulata. To ita</p><p>duk bawannan bne damuwarta ba, damuwarta</p><p>ynda Abba sam yaki nuna sha'awarta gare shi,</p><p>duk dayasan tana sallah, hka nan duk lokacin</p><p>dakwananshi yajuyo kanta sai dai ya jefa filo</p><p>akan kujera ya kwanta. Takasa gane ma'anar</p><p>hakan, tun tanajin dadin ynda bai nemeta ba</p><p>saboda tsoronsa da take harta dawo tasoma jin</p><p>haushi. Ita ma fa mutum ce cikakka mai lafiya,</p><p>sannan tana kwana daki daya da san kacecen</p><p>abun sonta ya ya ba zata damu ba? Sai dai tayi</p><p>wa kanta alkawarin a yau in zasu shekara ahaka</p><p>ba za ta taba yi masa tallar kanta ba ma'ana</p><p>baza takai masa kanta ba. Sai dai zatayi masa</p><p>kyale- kyale taga karshen girman kai, ta kosa su</p><p>hadu da fati don ta bata sakon kananan kaya</p><p>tasiyo mata don ta bata labarin cewa ta kwashe</p><p>su a wambai. Kwananta goma taso ma girka, duk</p><p>tsawon kwanakin nan abincin siyarwa dana</p><p>umma suke ci, domin bishira taki dafa abinci.</p><p>Ranar da zata fara girki ta haukata gidan da</p><p>kamshi, tuwon shinkafa miyar shuwaka, tasan</p><p>Abba nason tuwon shinkafa. Tun kafin ya dawo</p><p>yamata waya ta aika shagonshi, 'yan shago sun</p><p>ci suna santi, haka nan ya gayyaci abokansa</p><p>kofar gida ya shimfida musu tabarma suka ci tare</p><p>da lemu, zobo da kunun aya. (reall ehem tazubo</p><p>mun nawa na koma 1 site ina kimtsa cikina lolx)</p><p>ga nama ya wadata a ciki, abba yaji dadin yanda</p><p>abokanshi sukayi ta santi, safiyar ranar kuma</p><p>kunun gyada ta musu da kosai. Duk wannan</p><p>abincin da ummi keyi bishira ko a harshenta ta ki</p><p>ci, cewa ma tayi ita fa kowa tayi girkinta don</p><p>baza ta ci abincin ummi ba. Kuma ba shegiyar</p><p>dazatai wa girki, hakan yayi wa ummi dadi don</p><p>nata ganin ta bakin tsohuwa ce, da ta ce ko kwai</p><p>bishira tadafa shine dai dai a cikin bawo to baza</p><p>ta iya ci ba bare wani abinci. Sun zauna tsawon</p><p>wata daya ahaka ummi bata taba leka ko kofar</p><p>gida ba, tana kewar ummanta gara ma tsohuwa</p><p>duk ranar juma'a in tadawo masallaci takan biyo</p><p>gidan taga takwararta. Dakinta Abba yake</p><p>yagama karyawa ya shirya zai tafi aiki, ummi ta</p><p>kalle shi tana son tambayar zuwa gidan umma</p><p>tna jin tsoro. Ya dubeta kamar kina son cewa</p><p>wani abu ko? Ta ce am dama inaso inje gida in</p><p>gaida su umma, yajuyo yadubeta suka hada ido.</p><p>Gabanta yafadi, ta sunkuyar dakanta, yace a'a</p><p>tadaga ido takalle shi, wani kunci taji aranta, ga</p><p>matanshi nan yini take garari a layi bata ko</p><p>tambaya amma ita ta tambaya shine ma zai</p><p>hanata? Ya dauki jakar shi, ta mike ta rakashi</p><p>har tsaka gida tare da yi masa addu'ar Allah</p><p>yatsare, yini tayi da takaici dama haka mata suke</p><p>ji in an hana su zuwa anguwa? Daran ranar zai</p><p>koma ga bishira don haka bata san dawowarshi,</p><p>tana kwance kan doguwar kujera tana karanta</p><p>littafin hausa ( naleka muku kozanga sunan</p><p>littafin amma bangano mukuba) kamshin turaren</p><p>shi ne yasa tasan yashigo, don littafin yadauki</p><p>hankalinta. Ta amsa sallamar daya sake yi tare</p><p>da mikewa zaune, yana sanye da kananan kaya</p><p>tamkar wani dan saurayi, yayi kyau a idonta</p><p>kamar ta rungumeshi. Tace sannu dazuwa yace</p><p>yawwa, dauko mayafinki muje tazura takalma</p><p>bayan tagoge sannan ta ciro mayafi, yace a'a</p><p>dauko hijabin. Ta maida ta dauko hijabi tafito</p><p>sannan yakulle kofar, saida suka fita waje sannan</p><p>yadubeta, hannu rabbana zakije musu? Tace yaya</p><p>Abba toni bani da kudi ai. Sukabi ta wani super</p><p>market suka sai sabulai da turare, akafa suke</p><p>takawa sannu ahankali suka jero duk da cewa</p><p>bawata hira suke ba, Abba ne yake amsa waya</p><p>jifa-jifa na jama'a masu sonshi. Tun daga nesa</p><p>suka hangi mahaifansu suna cin abinci a inda</p><p>suka saba. Alhaji babba dakarami. Cikin zumudi</p><p>ummi ta ce, yauwa gasu alh. Abba yaje haka</p><p>zakije musu da rawar kanki ko? Cikin shagwaba</p><p>tace, wanne rawar kai nayi toni yaya Abba? Yace,</p><p>na gani kinayi kamar zaki kwasa da gudu, kafin</p><p>tayi magana sun iso gurin dukkansu suka zube</p><p>akan tabarmar daga gefe. Abba ne yasoma cewa,</p><p>sannunku alh. Alh. Yace, a'a kune? Alh karami</p><p>yace, uwata harda ke? Tace, eh ina yininku?</p><p>Sukace lpy lau. Alh. Karami yace, uwata kunanan</p><p>lpy ba wta matsala ko? Ta ce, ba komai alh..</p><p>Yace to Allah yyi maku albarka, ya azurtaku da</p><p>'ya'ya ma su albarka wadanda kuma zasu biku.</p><p>Abba yace amin suka hada baki da Alhaji babba,</p><p>alh babba yaci gaba da cewa, Abba ya hakurin</p><p>shirmen ummi kuma? Ince dai bawata matsala?</p><p>Abba yakalleta mun gode Allah alh, amma bwata</p><p>matsala, ummi tamike dazumudi bari a karasa.</p><p>Tun daga soro take kwala ma umma kira. Umma</p><p>tce, A'a muryar wa nake ji haka? Ummi tashigo</p><p>da gudu ta cakume umma, tsohuwa tafito tana</p><p>fadin lale. Dakin tsohuwa tasoma shiga suka</p><p>gaisa sannan tadawo dakin umma, sun gaisa</p><p>umma tasake mata nasiha, ummi tace umma ni</p><p>matsalata daya matarsa. Kullum saitayi min</p><p>habaici tana zagina wata rana r harda kawayentaRFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 9 ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 9 Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 01:54 Ita ko bishira gidan su umman bashir ta tafi dakuka wiwi, tace Abba yamata duka takan sun taka hakkinta sun fita ranar girkinta. Tayi magana ummi ta mata tsaki shi kuma yazo yazo yahauta da duka, umman bashir tace duka! Duka akan ummi? Tabdi, tashi muje gurin wadanda suka daure masu gindi. Umma na kokarin shiga daukin alhaji taji sallamarsu sama-sama, gabanta yafadi ta amsa tare da dawowa baya. Sahura tace to suwaiba, abinda kuka shiirya yasoma tasiri. Abba yayi wa bishira shegen duka saboda 'yarku, umma tace haba sahura, yaya ki ke irin wannan maganar? Mu ne zamu sa Abba ya cutar da iyalinsa? Sahura kiyi nazari. Alhaji yafito, me yafaru ne ni kejin hayaniya suwaiba? Umma tace, oho. Sahura tace, bishira fada musu. Nan bishira ta shaida masu yanda ta tsara ma umman bashir, alhaji yadaga waya yakira Abba, Abba yana dagawa alhaji cikin zafi yace Abba maza kazo yanzun duk in da kake. Abba yace to alhaji, ummi ta mike zan bika tsoro nake ji ni daya, cikin zafin rai yace abin daki ke tsoro ya cinye ki, ya fita fuuu. Cirko-cirko ya same su a tsakar gida, sai muryar sahura kake ji tana rashin mutunci. Alhaji karami yadawo gidan shi sai ya jiyo muryar sahura a can gidan, ya nufi gidan don haka kusan tare suka shiga gidan da Abba. Alhaji cikin bacin rai yafada Abba da fada, abba bai katse shi ba har sai daya kai ga tambayarshi cewa me yasa yayi mata duka? Yace, banyi mata duka ba alhaji marinta kawai nayi, umma ta ce mari kawai ne Abba? Alhaji karami yace, to kan wane dalili ma zaka mare ta? Abba ya koro musu komai, ya kara da cewa, wannan har zata ce an mata tsaki, zata yi duka ni wane irin zagi ne bata min ina hakura darajar iyayenta? Ya nuna ta, wallahi in kika kai ni bango zaki koma gidanku don bazan iya ba na gaji, nan kuma su alhaji suka shiga bashi hakuri. Ita kuma suka bata rashin gaskiya, sai dai duk da haka umma tai masa fadan kada ya sake daukan ummi ranar girkin bishira ya fita da ita, yace to. Umman bashir taja bishira zo muje ai dama nasan baza suga laifin 'yar su ba. To wllh marin da yamiki ki tabbata bashine. Ko nan da yaushe ne ki rama shi kan ummin, in ba haka ba duk da banice uwar data haife kiba sai na tsine miki. Alhaji karami yace, to katuwa mara lissafi, ke dai kinji haushin rayuwarki, to ki sani duk randa ta rama duka akan ummi ni kuma akan ki zan rama wa ummin inga ta tsiya. Alhaji babba yace, kada kai ma kazama su mana aminu. Tsohuwa tace, gskiya ne, in har tazama silar dukan ummi itama sai ya mata taji. Umma tace, a'a duk abin ba zai kai haka ba insha Allahu, kai dai abba kayi ta hakuri sannan kadaina sa hannu kana dukan mace. Yace, umma dukana fa tayi, sai kace wani soko zan tsaya mce tna dukana, umma tace, to ai tace ummi taje duka, yace ummin 'yarta ce? Alhaji yace, tafi gidan kahadasu kayi masu nasiha, Abba yace ai baza ta tsaya ba, wannan yarinyar fa sai dai addu'a ni in nagaji kawai hakura za ayi, umma tace bana son jin wannan zancan, alhaji karami yace ai gskiyarshi ne, shi yasan irin zaman dayake da ita. Alhaji babba yace, ai kuma darajar mahaifinta za aduba, da mutuncinsa, Abba yace ai dama alhaji ni banda mahaifinta da tuni nayar da kwallon mangwaro na huta da kuda. Umman tace je ka gida Allah ya kyauta. Nan dai ya musu sallama yanufi gida. Ummi da gske tsoro ne da ita, da rana in ba kowa bta damuwa, amma da dare tfi son tdinga jiyo motsin bishira koda habaicin dta sabayi mata. Soro taje ta tsaya tana yi tana leka waje, can ta hango bishira, don haka takoma daki ta kullo kofa aranta ta ce kada tazo tayi min duka. Ummi tna jiyota lokacin data shigo tana cewa wllh kan yarinya zan rama marina, wannan dole ne koba dade saina ramashi. Abba kan bai nufo gida ba, shagonsa ya wuce lokacin goma ta gota, yaran sunyi shirin tafiya, don haka ya amshi makullin ya shiga shagon saman teburin da suke yin yanka da guga ya hau ya zauna. Tagumi ya zuba hummu biyu tare da sauke wata ajiyar zuciya mai karfi, me yasa ummi ta furta kalmar data tuna mishi cewa bata sonshi? Sakankancewa dayanda ummin kenuna mishi yasa shi jin kamar sonsa take ashe dai shi yake shermenshi. Ya tuno wani labari yaya tabaji na wani mutum da aka ara masa mata wadda bata sonsa, tazo tazauna dashi tsawon shekaru kuma tayi masa biyayya matuka. Ga 'ya'ya sun haifa yaran sun yi girma sosai, suma sun zama magidanta, sai wata rana mutumin nan suna hira da matar, yace oh, wance dafa ba kya sona, yanzun gashi harmun tsufa kin manta dawata kiyayyah. Tadubeshi, inji wa yace maka na manta? Biyayya kurum nake maka amma har gobe bana sonka. Abba yajinjina kai, lallai dole ne ya nutso, yadaina tunanin ummi tana sonshi kokuma zata soshi, shidai da kaddarar sonta tafada mishi sai yayi ta addu'a Allah ya bashi hakurin jure zama da ita ahaka. Bai san adadin lokacin daya dauka awaje ba kuma baisan adadin tunanin dayayi ba. Daga karshe yarufe shagon yanufi gida. Ganin yanda garin yayi tsit shine yasa shi kallon agogon hannunshi, daya da minti shabakwai, lallai lokaci yatafi. ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 10</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 10</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 01:55</p><p>Yanufi dakin bishira aranshi yce da wanda yake</p><p>kinka gara mai sonka ko mahaukaci ne. Gdon</p><p>yahau tagefe ya kwanta suka saka muhibba</p><p>atsakiya, ummi kuwa duk tsawon lokacin nan</p><p>tkasa bacci domin bata ga shigowarshi ba. Idonta</p><p>biyu har sai daya shigo ta leka ta windo tana</p><p>kalloshi har yashiga dakin bishira ya rufo kofa,</p><p>sannan ta kwanta tare dayin ajiyar zuciya. A fili</p><p>tace ina ga fa har dani alaifin nan, amma bari</p><p>gari yawaye inba shi hakuri durkusa ma wada ai</p><p>ba gajiyawa bane. Bishira tafarka cikin dare taga</p><p>Abba kwance hannunsa na dama dore kan jikin</p><p>'yarsu, ta tsura mishi idanu tana son mijinta</p><p>sosai. Ban dahaka data kaishi koto ya bata</p><p>takardarta koda mahaifinta xaimata baki</p><p>sanadiyar haka, amma shi yanzun yadaina sonta.</p><p>Takai hannu tadora a kumatunshi, ahankali</p><p>yabude idanu, suka kura majuna ido yace bishira</p><p>me yasa kike yin abinda zai samu mu samu</p><p>sabani bayan kinsan sone ya hadamu?</p><p>Idanuwanta suka kawo ruwa, Abba dane ka soni</p><p>kaji dani har alokacin ina ganin ba Wata mace</p><p>data kai ni dacen gwanin iya soyayya. Amma</p><p>yanzun duk ka zuba ni a kwandon shara har kana</p><p>marina saboda ummi. Ya ce, a'a ba sbd ummi na</p><p>mare kiba, saboda kin dukeni ne amma kiyi</p><p>hakuri. Banason kina zubar da kanki a gurinta,</p><p>yawan fadanku zai sa raini ya shiga tsakaninku,</p><p>ni kuma ba zan so ta rainaki ba. Kuma da kin</p><p>kwantar da hankalin ki ummi fa ba wai tana sona</p><p>bane, ita fa an matsa ma tane, kuma su umma da</p><p>kike zagi na rantse miki masoyan kine. Ta ce</p><p>tokai kana son ummi ne ? Ya dan yi jim, sannan</p><p>ya ce ai dai kin san yanda auran namu da ita</p><p>yakasance bagatatan bai dace ace kinma tsaya</p><p>yin wannan tambayar ma. Tadan yi shiru, zancen</p><p>nan ya shige ta bakamar yanda ta zata da farko</p><p>ba, ko dadin baki zaimata? Sannan ta tuno da</p><p>ranar da fati tazo. Ta labe taji koza suyi</p><p>zancenta sai taji suna ta hirarsu, acikin harar fati</p><p>ke cewa wai kuwa ya kuka kaya ne ummi? Nasan</p><p>yanzun ai kin warke, kema kin goge. Ta ce</p><p>damefa? Fati tace, a'a ki gane mana, batun</p><p>kwanciya. Ummi tace, kin san cewa yaya Abba ko</p><p>gadona bai taba kwana ba? Fati tace kai haba?</p><p>Ummi tadinga yimata rantsuwa, tuno da wannan</p><p>sai bishira ta yarda mijinta ma baya son ummi,</p><p>don haka sai ta saki murmushi. Yace, tunanin me</p><p>ki ke yi? Tace da ina ga kamar dadin baki kake</p><p>min, amma dana tuno naji ummi tana fadama fati</p><p>wai baka taba ko kwanciya a gadonta ba, bare ka</p><p>hada jiki da ita sai na yarda. Abba ya zaro ido, a</p><p>ina kika ji suna zancan? Ta ce, a'a tazo mata</p><p>rakiyane naji suna maganar a soro. Abba ya</p><p>girgiza kai. Bishira tace, kuma da gske hakane,</p><p>yakai hannu yakama nata tafin hannun, wannan</p><p>wani sirri ne tsakanina da ummin. Ynda ba zan</p><p>fada mata komai tsakanina dake ba, haka itama</p><p>zan sakaya nata sirrin, tadai fahimci hakane, don</p><p>haka sai ranta yayi mata dadi har ma ta baiwa</p><p>Abban kanta a daran. Ynda taga yna rawar jiki ya</p><p>tabbatar ma ta ba wani angwanci da yayi, don</p><p>haka zuciyarta fes ta wayi gari. Duk da cewa</p><p>abba ya tashe ta cewa taje tayi wanka harda</p><p>Allah yahadata amma tayi niyar baza tayi hakan</p><p>ba sai gari yayi haske. Ummi ta fito don tanuna</p><p>mata cewa Abba ya kwana da ita. Bishira an dafa</p><p>ruwan tea an kai falo sai wannan rawan kai ake</p><p>yi. Sai data lura ummi ta dauko tsintsiya tasoma</p><p>sharar gidan kamar yanda tasaba, sannan tafito</p><p>da buta aka nufi bandaki, kai ko dankwali babu</p><p>aka yiwanka aka fito. Gashi yna ta digar ruwa,</p><p>ummi ta fahimta kuma tagane cewa tayi hakan</p><p>don ta nuna mata ne. Kuma taji zafi aranta</p><p>kamar ynda bishiran taso, ta amma azuciyar ta</p><p>sai tace na banza jiya nan yakora miki mari.</p><p>Lokacin da abba ya shigo gidan tagama shara</p><p>tana kwashewa, bai ko dubeta baya shige falon</p><p>bishira, kan ummi yasake daurewa, me yake</p><p>faruwane haka da zafi? Ta tambayi kanta. Data</p><p>koma daki tagumi ta zabga tana tunani ita da</p><p>suka yi kaca-kaca ma sun shirya bare ni? Kamar</p><p>tabi shi har falon bishiran ta gaida shi, amma sai</p><p>tafasa. Tazuba ido taga zai bar gidanne ba tare</p><p>daya leko dakinta ba? Sun gama karin</p><p>kumallonsu tsaf yayo wanka don tafiya gurin aiki,</p><p>sai dai kayan dazai saka suna dakin ummi. Ya</p><p>fito yanufi dakin. Ciki- ciki yayi sallama ita kam</p><p>tsoro ne ya tsirga mata, tasake tambayar kanta</p><p>mekuma yafaru? Ta amsa tare da gaida shi. Nan</p><p>ma a ciki ya amsa, yadauki kayan sai dazai fita</p><p>sannan yace ba kya bukatar komai ko? Tayi</p><p>karfin halin cewa sugata ceta kare. Ya dube ta</p><p>furka tsuke me yasa baki fada minba? Ta ce, na</p><p>manta ne, yace to sai kije gurin bishira da dibar</p><p>miki inzan dawo na siyo. Ba kya neman komai da</p><p>rana ko? Tace a'a sai nama kawai ya daga</p><p>murya, kullum ne ya zama dole a saka nama a</p><p>abinci? Jikinta har bari yake don tsoro, ta ce a'a</p><p>yaja tsaki ya fita. Ummi tasaka kanta cikin cinya</p><p>tana furta 'inna lillahi wa inna ilaihir raji'un.'</p><p>hawaye suka soma yi mata sintiri.KI novels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 11</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 11</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 01:57</p><p>Dadi tamkar yakashe bishira don tna labe tana</p><p>jinsu afalon ya saka kya yashirya tsaf, sannan ya</p><p>nufo dakinta don dauka jakar laptop dinshi. Jin</p><p>sallamarshi tayi mza tashare hawaye sannan ta</p><p>amsa, yshigo ya dauko dari biyu ya aje mata</p><p>akan gdo, ga kudin maman nan kura, kada fati</p><p>tzo kifada mata baki kudin nama kullum tunda</p><p>har kin iya shaida mta cewa ban tba kwana</p><p>agadonkiba. Kin kosa inkwanta dakene? Yadauki</p><p>jakar yarataya sannan yayi mata wani kallo sama</p><p>dakasa, to banga gurin kwana agadon naki ba.</p><p>Hakanan banga abin kwanciya ajikinki ba, yafice</p><p>yabar ummi tsaye tazaro idanunta cikin matukar</p><p>al'ajabi da kunya. Ina ya Abba yaji zancen nan?</p><p>Kodai fati ceta fada masa? Wata zuciyar tace fati</p><p>baza ta iyayi masa zancan nanba saidai in</p><p>ummarsu tafada mawa ita kuma tafada masa.</p><p>Inko hakane fati batayi mata adalci ba, ai hira ce</p><p>irinta aminta tsakaninsu, gashi ta bata kunya har</p><p>tasa ya Abba naganin tazaku. Tokuwa tasha</p><p>alwashin nuna mishi bahaka take nufi ba, afili</p><p>tace Allah yabamu rai da lpy. Sai kuma tasoma</p><p>kuka. Bishira tafadi kan dadi ashe gara data fada</p><p>masa zancen dataji suna yida fati, gashi yanzun</p><p>yayi mata rana. Lallai labe yayi mata amfani sai</p><p>kawai tasabi 'yarta tazari mayafi tafice makota,</p><p>yau kan tana da labari mai dadi sai yawon raba</p><p>shi take bata manta ko kalma daya. Sannan</p><p>darana tazo tahau kici-kicin dora girki, lokacin</p><p>ummi tafito don yin alwala, ita ko karyawa batayi</p><p>ba don tawuni da takaici ya Abba. Tana kallon</p><p>yanda bishira tazubu kayan miya tana jajjagawa</p><p>batare data wanke ba hancin kawai ta cire. Ummi</p><p>tayi alwala tashige daki, ranar har dare ummi</p><p>bataci komai ba, duk da tanajin yunwa. Zantukan</p><p>abba kawai kemata yawo a kwanya. Tayi kuka</p><p>harta gaji fuska ta kumbura. Tun uku yadawo</p><p>baiga ummi ba, bishira tagabatar masa da abinci</p><p>dakyar yayi cokali uku. Dama yazo dafura, yasha</p><p>sannan yanufi shago, yini yayi yana tunanin</p><p>kamar bai kyauta ma ummi ba, amma yana</p><p>mamakin yanda ummi ta iya cewa bai hau</p><p>gadonta ba. Kenan inyahau din dakuma abinda</p><p>yabiyo bayan hawa gadon duk zata ringa fesarwa</p><p>ne? Kai yafaji haushin abu biyun nan dacewa</p><p>bada sonta aka daura masu auran suba dakuma</p><p>fada ma fati sirrinsu. Saidai duk dahaka zuciya</p><p>da idanunshi suna matukar kewar ganin ummi,</p><p>sai shida yadawo gidan. Ruwan wanka ya diba</p><p>yanufi bandaki, man shafawarshi dasauran su</p><p>suna dakin ummi, don haka yakalli bishira. Bari in</p><p>dauko kayana can dakin ummi kozaki dauko min?</p><p>Tace, bazan jeba kaje da kanka. Tana kwance</p><p>kan doguwar kujera lokacin kanta yana matukar</p><p>sarawa, don kuwa yanda yayi sallamar da kyar</p><p>itama dinda kyar ta amsa. Saidai ita badon</p><p>wulakanci tayiba, saidai don yanda take jin</p><p>jikinta. Yashafa mai tare da feshe jikinsa da</p><p>turaruka. Idanunshi suka sauka kan darinshi biyu</p><p>daya aje mata. Yakalleta, ke ina abincin da kika</p><p>dafa? Batare data dubeshiba tace, bandafa ba.</p><p>Yace sbd me? Tace banjin yunwa, kaikuma naga</p><p>ba anan kake ba, baki ya taba yasa kaya yafice.</p><p>Har tayi sallar isha'i lokacin tasoma jin jiri, amma</p><p>bata da niyar shan ko tea tanajin ya shigo ya aje</p><p>mata ledar ta kusan minta 30 kafin tataso tazo</p><p>tatura kofarta. Sannan taduba ledar, nama ne</p><p>balango yaji albasa da tumatiri, sai sugar da</p><p>madara, nan ta aje su tayi kwanciyarta afili tace</p><p>natabbata kurar kenan indai naci maman nan.</p><p>Bacci yadauketa can kusan ukun dare fa yunwa</p><p>fatakai yunwa, kowa yasan yunwar dare yanda</p><p>take jigata bawa, a gigice ummi ta tashi tahada</p><p>tea tahau sha da gaggawa. Tagama kamar taci</p><p>naman sai kuma tafasa ( tamiko min ninkuma</p><p>nayi fuska nacinye au namanta madawani azumi</p><p>lolx) ta kauda kayan ta koma ta kwanta, aikonan</p><p>fa cikinta yahau hautsinawa. Dagudu tatashi</p><p>tanufi fita tana bude kofa kafin takai bandaki</p><p>tasoma sheka amai, tun bude kofarta abba</p><p>yafarka dasauri yafito. Riketa yayi ganin yanda</p><p>take sheka amai kamar zata amayar da hanjin</p><p>cikinta, sai sannu yake mata. Data gama yajanyo</p><p>ruwa ya wanke mata fuska ta kuskure baki.</p><p>Yawanke gurin gurin tana gefe tsugunne, cikinta</p><p>da kanta sai ciwo sukeyi tana mikewa sai jiri.</p><p>Nan tafadi ragwaf, shine yadauketa tamkar ya</p><p>dau jaririya don rashin nauyi yace duk kece kikayi</p><p>makanki sanadin wannan matsalar. Don kina</p><p>fushi saiki yiwa abinci yaji, ai gashi nan kema</p><p>kina ji ajikinki, kan kujer yadorata ya cire mata</p><p>siket din atamfar dake jikinta, don duk sun jike sai</p><p>na ciki. Yajuyata zai zage mata zif din rigar tana</p><p>son ta hana amma bata dawani karfin hanawa.</p><p>Tanaji tana gani abba yacire mata riga, gashi ko</p><p>best bata saka ba sai breziya. Takai hannuwanta</p><p>tarufe kirjinta. Shikam ganinta ahaka yasa tsigar</p><p>jikinsa tashi, tun daga karamin yatsansa har</p><p>tsakiyan kansa ruf da ciki ta juya tayi, shi kuma</p><p>ya kunna mata fanka yafita. Zaune ya samu</p><p>bishira atsakiyar gado, ta kalle shi da tuhuma, me</p><p>kaje yi dakinta? Yce amai naji tanayi shiyasa</p><p>nafita, bta dlpy ne, tsaki taja sannan ta kwanta.</p><p>Shi kam bai runtsa ba, kunnanshi da hankalinshi</p><p>suna can, dga bisani madayaga baccin yaki sai</p><p>yatashi yayi alwala yasomayin nafila. Dazai tafi</p><p>masallaci yske lekawa yaga IKI novels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 13</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 13</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 02:05</p><p>shikenan yanyun bata dawani aji agurin Abba</p><p>ummi da tsoron allura sam taqi tsayawa jiya ma</p><p>don agalabaice take Nurse din tace ke dai</p><p>shagwaba ta miki yawa A ce allura ma kin kasa</p><p>tsayawa kefa mace ce Wata rana ma haihuwa</p><p>zakiyi ummi fa taki tsayawa nurse tazo tace ma</p><p>Abba taki tsayawa abba yaleka dakin allura</p><p>menene haka ummi tsoron alluran ki yayi yawa</p><p>kitsaya mana Tadube shi fuska a shagwabe ya</p><p>Abba dazafi nikam na hakura da allurar nan Abba</p><p>ya shiga dakin ya kalli nurse din zo kimata ba</p><p>zanyi asarar kudina ba Ummi bata ankara basai</p><p>jinta tayi atsakiyar kirjin Abba shi kanshi sai jin</p><p>wani abu yayi yataso daga tafin kafarshi zuwa</p><p>tsakiyar kanshi Har yayi baya dasu tamkar zasu</p><p>fadi to bare ummi wadda jikin nata ya dauki rawa</p><p>Ya kalli nurse dinda idanuwanshi wadanda suka</p><p>canza kala nan da nan zo kiyi mata Yadaga</p><p>hajabinta tare dazame zanin daidai inda za ayi</p><p>mata allurar shigar allurar ta saka ummi cewa</p><p>wash tare da sake makalewa jikin Abba Don kuka</p><p>tasaka wanda daga jinshi kasan shagwaba ce</p><p>zalla ya lumshe ido lokaci daya ya kuma budesu</p><p>nurse din tace kai ke kam kin cika shagwaba</p><p>Abba ya dora yatsunshi guda adaidai gurin da</p><p>akayi allurar yana murza mata tare da rada mata</p><p>'sannu' akunnenta Rekicewa tayi sannan ta</p><p>kwace jikinta daga gare shi wani yanayi ta tsinci</p><p>kanta mai girgiza bawa Ya sauke ajiyar zuciya</p><p>sannan yace mu tafi suna cikin mota dukkansu</p><p>sunyi shiru Abba kasala ce da muradin matar shi</p><p>yasa shizama hakan Ita ko ummi mamakinta ba</p><p>yau Abba yasoma taba jikinta ba can baya yasha</p><p>rike ta yazane ta, yasha rungumeta ayi mata</p><p>allura, bata taba jin irin abinda taji yanzun ba Ta</p><p>jingina da kujera tare da lumshe ido sai take ta</p><p>tuno yanayin dataji lokacin daya mannata</p><p>ajikinshi. Tsayawar motar ne ya sata bude</p><p>idanunta, azatonta gida suka zo,sai taga ashe</p><p>gurin kayan kwalama ne Ya kalleta, ina zuwa Ya</p><p>fita ya nufi zuwa ciki jim kadan ya fito da ledoji,</p><p>kaji ya siyo da madara mai tsafta, har da</p><p>kankarar dayaji tana tambayar umma yasai</p><p>musu. Tace, gama fa kankarar umma tasai mana.</p><p>Bishira ta cika fam don takaici, kamal kaninsu</p><p>Abba yaduba mata ko ummi tana gidan umma, ya</p><p>fada mata bata nan. Ta tabbatar suna tare, ta</p><p>cema umman bashir tunfa safe suka fita tare</p><p>umma tace tun safe wane iri? Tace wai bta da</p><p>lpy yaje kaita asibiti Umman bashir tace Allah ya</p><p>tashe mu lpy Goben nan zan tafi kauye dama</p><p>gobe ta ce indawo gaje 'yar bori, ina fada miki</p><p>ummi dakanta zata bar gidan basai ance mata</p><p>ba. Bishira tace dahaka zata faru zanfi kowa farin</p><p>ciki, umman bashir tace kece aida shegen kyamar</p><p>'yan kauye bakison mutane Matsalarki kenan da</p><p>ace zaki jure muje tare kiyi kwana 2 'yar bori da</p><p>bokan tsauni zasu cika miki aiki Bishira tace</p><p>zanje umma. Biyan bukata ai yafi dogon buri</p><p>umma tace taki turo minshi ince masa sha'ani</p><p>zamu don kada yace zai hana, bishira tace to.</p><p>Sun sameta agidan ummi tayi dakinta da ledar ta</p><p>shikuma yashiga gurin bishira. Ranar daya dawo</p><p>dakin ta kuwa tayi kyau cikin doguwar rigar</p><p>shadda ruwan kunkumadi, tun yana kallon ummi</p><p>asace harya kasa dauke idonsa Ummi talura ta</p><p>birgeshi sosai don haka tazauna bakin gado tana</p><p>fuskantarshi hira ce suke yi jifa- jifa itace ma</p><p>tasoma sako zancen Ya Abba zance ma alhaji</p><p>yasai min TV nagaji dazama shiru Abba yace a'a</p><p>banason haka ina sane zansai miki, tace to</p><p>Bishira dake labe ta girgiza kai aranta tace ashe</p><p>za ayi bala'i duk randa yakawo TV ai itama ai</p><p>iyayenta suka sai mata. Tace to yaya abba</p><p>inason makaranta ya aje laptop din daya soma</p><p>budewa yamaimaita kalmar makaranta? Ta ce eh,</p><p>yace sai nayi tunani Ummi ta marairaice tunani</p><p>ya Abba? Kai dakake son inyi karatu? Yace</p><p>shikenan haka sukayi ta hira har lokacin</p><p>kwanciya ummi tayi shafa'i da wuturi tayi shirin</p><p>baccinta takwanta Abba yau yakasa nutsuwa</p><p>tamkar yaje ga ummi, amma girman kai ya</p><p>hanashi. Ranar sama-sama yayi bacci sau biyu</p><p>yna fita yana watsa majikinshi ruwan sanyi kozai</p><p>dan samu nutsuwa. Har lokacin daya tafi gurin</p><p>aiki bashi da wani kuzari. Ranar fati tazo lokacin</p><p>bishira ta tafi badadinta, ummi tahau fati</p><p>damasifa tare da fada mata yanda sukayi da ya</p><p>Abba. Fati ta rantse tamaya kan cewa ba wanda</p><p>yasan zancen nan don bata fada ma kowa ba,</p><p>sukayi ta tunanin ta ina ne zancan nan yafita?</p><p>Fati tace to ko kiyi hankali koda Anty bishira tana</p><p>miki labe? Ummi tayi shiru tna nazari, can tadubi</p><p>fati Bazan zargeta ba, domin ban taba ganinta ba</p><p>amma zansa ido fati tace gara kisa kam yanzun</p><p>harzuwa yau baku sasanta ba? Ummi tace aini</p><p>bana bukatar sasantawa dashi tunda yace baiga</p><p>gurin kwanciya agadona ba Fati tasaka dariya ke</p><p>dai kada kicika baki,ummi tace kedai mu bar</p><p>wannan zancen inbaki kudin kayan don Allah?</p><p>Tati tace kibani dan bnida matsala mijina she ne</p><p>yakaini nasai nawa zance yakaini insai miki</p><p>kinason wanduna Ummi tace kinjiki da siket zaki</p><p>debo min Ai har gajerun wanduna ki kwaso min,</p><p>wulakanci zanyi a gidan nan.vels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 15</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 15</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 02:12</p><p>Saidatayi sallah sannan tazauna gaban madubi</p><p>duk da shirin bacci take yi Saida tashafa manta</p><p>da hoda sannan tadan goga jan baki. Tafesa</p><p>turarenta ta isa gurin kayan baccinta dake cikin</p><p>dirowar dora akwati, ta dauko duguwa tazira</p><p>sannan takama karshen kitsonta tahada su guri</p><p>daya ta tufke. Zata ha gado yace, ga nama kizo</p><p>muci. Ta fada gado tare da jan filo ta dora kanta</p><p>da kirjinta sannan tace nama saikace wata kura?</p><p>Dazun fana danci amiyar danayi. Yace nida na</p><p>siyo shine nazama kuran ko? Tace, a'a ya Abba</p><p>kaine ranar nan naji kace kura. Kullum ake cin</p><p>nama? Yayi murmushi aranshi yace, ok nan na</p><p>rama ne kenan, sannan yace toshi kenan bari in</p><p>ajiye miki naki. Nan tayi kwanciyarta. To 'yar</p><p>gidan tsohuwa, yafada danufin zolaya, tace kai</p><p>kuma dan gidan ummanka. Cigaba yayi dashiga</p><p>yanar gizonsa, ita kam a gajiye take bacci</p><p>yasoma fizgarta. Lokacin dayazo shima ya</p><p>kwanta akan gado, ta bude ido lpy Yaya Abba?</p><p>Ya dubeta tsakaninsu mutum daya zai iya</p><p>kwanciya. Wace irin tambayace wannan mutum</p><p>da dakin matarsa da gadonta atambaye shi lpy?</p><p>Tatashi zaune, gani nayi ba guri agadona, yayi</p><p>shiru, wato ummi bata barin bashi, ta tsura mishi</p><p>ido tana jira jin mezaice. Yatashi zaune, idanunshi</p><p>akan lebunanta, toni dai ga guri na samu, ta</p><p>sulale itama takwanta rigingine tare dajan bargo</p><p>tarufe rabin jikinta. Shima hakan yayi, ummi</p><p>fargaba ce tasa tanemi bacci tarasa, shikam</p><p>addu'ar bacci yakaranta sannan yashafa</p><p>yalumshe idanu. Duk su biyun bacci sama- sama</p><p>sukayi koda Abba baisamu nasarar kama kayan</p><p>ummi ba amma aranshi yace wannan sharar fage</p><p>ce. Dasannu za'a kai ga muradi, ko washegari</p><p>daya kwana adakin dai bawani cigaba sai sake-</p><p>sake Abban yayi tayi azuciyarshi, na cewa</p><p>yakauda wata kunya ya fito mata amutum, amma</p><p>yakasa hakan. Musamman yanda yaga ummin</p><p>tana da shegen wayo, ba kamar yan yazata ba.</p><p>Sannan gashi ta iya yin ado irin na tsokana.</p><p>Hakan yasa duk ranakun girkinta Abba yana</p><p>zumudi amma yakanyi kwanan rashin sukuni.</p><p>Wata jumma'a tsohuwa ta riski ummi da irn</p><p>wannan shiga tariga da gajeren wando, ta kawo</p><p>mata ziyarar data saba inta dawo masallaci.</p><p>Salati tasaka tare da cewa, yarinyar nan kece</p><p>haka kinzamo sai kace arniya? Ummi ta tashi</p><p>tsaye tayi juyi tare da cewa. Ynzun tsohuwa ban</p><p>birge kiba? Ta ce kitson naki ne kurum yamin</p><p>kyau, amma wannan shiga dame tai kama? Kuma</p><p>shimai sunan malam yakasa hanaki koke ma</p><p>yasoma tsoron nakine? Ummi ta tuntsure da</p><p>dariya, ba tsorona yake jiba, shine ma yake son</p><p>kayan don shine ma yasai minsu. Tsohuwa tace,</p><p>oho! Eh lallai ta mike Allah ya taimaka, duk abin</p><p>ku dai baza ki koma baturiya ba, ummi tace oho</p><p>dai ke dai kuma baza ki iya wannan ba. Tace,</p><p>Allah ya tsare nida wannan shiga, ummi ta dauko</p><p>dari biyu ganin tsohuwa ta mike, nizan tafi in dan</p><p>zazzaga in ziyarci jama'a. Ummi ta kama</p><p>hannunta ta saka dari biyun, gana goron</p><p>jumma'a, Allah ya hadamu aladan ziyarar. Suka</p><p>fito tana cewa. Ke kullum nazo sai kin bani kudi</p><p>ummi, to Allah ya shi muku albarka, Allah kuma</p><p>yasa ki sauko lpy. Murmushi ummi tayi duk 'yan</p><p>gidan su kallon mai cike suke mata. Duk hirar</p><p>nan tasu bishira najinsu, ta cika tayi fam. Dama</p><p>Abba yana kwana da ummi? Ashe shine yake sai</p><p>mata kananan kaya? Ashe har tana da ciki shine</p><p>yamata karyar cewa baya sonta? Tana dawowa</p><p>raka tsohuwa, bishira ta kalleta, karamar yarinya</p><p>ta iya karuwanci, dube ki. Ummi ta kalleta babba</p><p>fa ya rike girmanshi inba haka ba inhau in taka,</p><p>kuma niba karuwa bace, kema kalle ki. Ta taso</p><p>zan zane kifa? Ummi ma tadaga murya. Sai kace</p><p>wata 'yarki? Ba ki isa ba. Bishira tazo zata</p><p>shakota, ummi ta daka tsalle taja baya. Karki</p><p>sake ki taba ni. Nan fa gidan ya kacame, bishira</p><p>sai ashar take zugama ummi, tana kiranta 'yar</p><p>matsiyata. Ummi tace, banga kamannin masu</p><p>arziki ba a jikinki, nan makota suka shigo yin</p><p>rabo. Ummi ko tana fada mata take ramawa, abin</p><p>da yafi yiwa ummi ciwo datace ummanki</p><p>matsafiya, nasan komai saboda bakin asirinta ne</p><p>sahabi yafasa aurenki aka mannawa mijina. Don</p><p>shima ya fada min ba ya sonki, har yanzun bai</p><p>taba kwanciya dake ba. Ummi tace, kazama mara</p><p>sallah me labe, kina labe min akofan don bakin</p><p>kishi, kuma insha Allahu sai Allah yasakawa</p><p>ummata tunda kika ce tana asiri. Maman amir</p><p>kawar bishira tuni taruga takira umman bashir,</p><p>sai dai cikin sa'a tanazuwa Abba nayin parking.</p><p>Ganin yanda mahaifiyarshi tashiga gidan cikin</p><p>hanzari haka shima agurguje yafada gidan, ranshi</p><p>yayi mugun baci yanda yaga gidan cike da</p><p>jama'a. Ga bishira mutum biyu sun rike ta tana</p><p>zambarmar asake ta ta lallasa ummi, ga ita kuma</p><p>ummi tsaye akofarta kanta babu ko dan kwali ta</p><p>sha gajeren wando ya dan gota gwuiwarta da 'yar</p><p>riga tana maida martani. Yace ma matan dasuka</p><p>rike bishira, ku saketa suka sake ta ya daka mata</p><p>tsawa da karfi, duk ku fice min daga gida,</p><p>magulmata tunda duk yawanku kun kasa sasanta</p><p>su. Sum-sum suka wucesuna tabe baki, duk</p><p>dahaka bishira bata daina magana ba.ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 16</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 16</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 02:14</p><p>Haka umman bashar batasan yarda komai ya faru</p><p>ba. Amman ta shiga zagi da tsine ma ummi har</p><p>da ce mata karuwancin ne ya motsa, ai dama</p><p>nasan tun kafin kixo gidan nan kinsan maza.</p><p>Bishira ta ce umma wllhi ga babban mai laifin</p><p>nan, muna funtata sukeyi duk ire ire wadannan</p><p>kayan na jikinta shiya sai mata su, ni bai siyo</p><p>min ba. Na gaji da hakuri ana cutata gwara</p><p>yaban takarda ta. Umma tace daina fadin ya baki</p><p>takarda insha allahu saidai ita ya bata, Abba</p><p>yayima bishira wani kallo tare da cewa ki tafi</p><p>mana sai me? Yarda kika gaji da ni nima Haka na</p><p>gaji da ke, ya kalli ummi yace ke kuma mi nake</p><p>fada maki kullum? Itama cikin fushi tayi magana</p><p>toh shikenan saita ta zagina tana ma ummata</p><p>sheri don ita kake so? Bishira ta cafke dama ai</p><p>ya fadaman baya sonki. Ummi ta kalleshi ko zai</p><p>kare kanshi, amman baya kokarin Haka saima</p><p>kara zaro mata ido da yayi yana cewa. Ni kike ma</p><p>ihu ummi? Zuciya tazo mata wuya nata ganin an</p><p>daketa ne kuma an hanata kuka. Shi kanshi ya</p><p>tozarta ta da ya fadama kishiyarta baya sonta.</p><p>Duk da tasan da haka ta kalli bishira cikin daga</p><p>murya tace, an fada maki na damune don baya</p><p>sona bana son ya soni don nima bana son Shi....</p><p>Mari Abba ya sakar ma ummi da bayan hannu,</p><p>kalmar da ya tsana kenan, zafi yakeji a Zuciyarshi</p><p>ko tunowa yayi da ummi bata sonshi. Daki ummi</p><p>ta fada, ta fada kan gado tana kuka, ya kalli</p><p>bishira kije gidan ku sai nazo, umman bashar</p><p>tace ba inda zataje kuma in ka sake na samu</p><p>labarin ta tafi saina debe maka albarka. Tasa kai</p><p>fuuuu ta fice, tunda ka dauki hukunki mai kyau ka</p><p>duki marar kunya ai naji dadi. Bishira ma taji</p><p>dadin haka, Shi kuwa ba don su yayi ba zafin</p><p>furta bata sonshi ne yasa ya daketa. Yana shiga</p><p>dakin ummi lokacin ta mike tana kuka, ta dauko</p><p>zane ta daura tana kuka sosai. Ta zari hijabi ta</p><p>zura zata fita, yace ina zaki? Taki sauraronshi</p><p>zata fita ya rikota, ina zaki nake? Tayi magana</p><p>cikin daga murya cikin muryar kuka tace gidan</p><p>ubana kai kuma ka zauna da warda kakeso,</p><p>tunda ya mareta nan ya gane bai kyauta mata ba,</p><p>don yasan ba dole bane ta fahimce Shi, sai ya</p><p>samu kanshi da jawota ya rungume. Duk da suna</p><p>cikin bacin rai Duk kansu saida sukaji wani irin</p><p>yanayi. Yace kada kiyi yaji ummi kinsan dai koh</p><p>kinje su umma fada zasu maki. Cikin sanyin</p><p>murya yayi maganar, kan ummi ya sara, ta kwace</p><p>daga jikinshi ta sake fadawa kan gado. Sabon</p><p>kuka ta saki, ya zauna bakin gado ya kamo</p><p>hannunta ta sarke ya tsunshi da nata ya dan</p><p>matsa, ummi! Ummi!! Tashi kiji, cikin kuka tace</p><p>mi zanji yaya Abba, kawai ka rabu dani, ni baka</p><p>man adalci ba. Ya za'a yi kaje kana fada mata ni</p><p>baka sona kasa tana man gori, umman bashar</p><p>harda ceman wai ni nabi maza. Ya sake kwantar</p><p>da murya yace ki yarda ni ban fadama bishira</p><p>cewa bana sonki ba, kuma batun umma kisashi a</p><p>gefe kawai don ni nafi kowa sanin halinki. Nafi</p><p>kowa sanin tarbiyar umma na... Duk da haka ai</p><p>baka kare kanka ba lokacin da take fada ba,</p><p>ummi ta katse kiran da yake mata, yasan ummi</p><p>sarai yanzu kam bazata saurari komai ba, koma</p><p>ta saurara zata ta kalubatanshi ne, don haka sai</p><p>yace to Tashi ki bani abinci. Kin Tashi tayi don</p><p>kanta jinsa take kamar ya fado, mi kewa yayi ya</p><p>fita, ya rasa sukuni, koda yaje shago kasa yin</p><p>komai yayi, sai murza hannunsa da ya mari ummi</p><p>yake. Ya ciro wayarsa ya kira ummin tayi ta</p><p>ringing kusan sau 3 kafin ummi ta daga yace</p><p>haba ummi, inata kira kayi banza dani? Shiru dai</p><p>tayi bata tanka ba, ummi cikin disashiyar murya</p><p>tace, dama haka ne, sai an kwance ma mutum</p><p>zane kasuwa azo gida ace za'a daura masa. Sai</p><p>ta kashe wayar. Daga nan gidan umma ya nufa,</p><p>tace anya Abba lafiyarka kuwa? Naga Duk ka ya</p><p>mutse. Ya zauna suka gaisa yace umma ina fa</p><p>lafia, dazun bayan sallar jumma'a ina iso wa gida</p><p>da yunwa sai kurum na samu gidan tam d</p><p>jama'a. Ummi da bishira na tarar suna ta zage</p><p>zage har aka samu wata shedaniya taje ta kira</p><p>umman bashar. Umma tace subhanallah! To ya</p><p>akayi yanzu? Yace tarwatsa taron nayi, nasan</p><p>koda ban tsaya bin bahasi ba ummi ce mai</p><p>gaskiya. Domin bata kula bishira, Duk yarda akayi</p><p>ta kure ta ne. Tsohuwa daga can gefe tace, wai</p><p>bayan zuwa na gidan sukayi fadan? Abba yace</p><p>oho ni ban masan mafarin fadan ba. Umma tace</p><p>kai wannan abu allah ya dai dai ta maka su.</p><p>Amman kyanshi kana zuwa ummin ya kamata</p><p>kayi wa fada, koma ka zane ta, don itace karama.</p><p>Abba har suna hada baki da Tsohuwa gurin fadin</p><p>"Haba dai". Abba yace umma in itace da gaskiya</p><p>kuma ai na zalinceta, yanzun da haka fushi take,</p><p>Duk na tsorata bana son fushinta, sai taki cin</p><p>abinci. Don allah umma bari in kira maki ita ki</p><p>bata hnkr, umma tace ba zan bata hnkr ba, abinci</p><p>kuwa kada allah yasa taci. Sai dai ayi tunanin</p><p>abinda ke cikin ta, Tsohuwa tace, wannan</p><p>sakaryar matar taka dama na lura fada takeji.</p><p>Sanda nayi sallama tana zaune amman amsawa</p><p>ta gagareta, don haka ma ko gaisheta banyi ba</p><p>na wuce. Ita kuma takwara ka hanata saka</p><p>wadannan kayan na arna. Abba yace, su ake yayi</p><p>Tsohuwa, Tsohuwa tace, tafdi lallai yayi ya zama</p><p>banza. Abba yake cewa Don allah umma ga nmbr</p><p>bari in saka maki a waya, ya dauki wayar umma</p><p>ya saka mata lambar wayar da ke hannun</p><p>ummin, yace umma na roke ki lallasheta ba wai</p><p>fada zaki mata ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 17</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 17</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 02:17</p><p>Duk jumma'a abba yana dawowa gida</p><p>musamman in ranar girkin ummi ne don cin</p><p>abinci na musamman. Jumma'a biyu kenan bata</p><p>fado kanta ba sai wannan, don haka tun alhamis</p><p>taje ta yarfo kitsonta, ta biyo ta gidan su gurin</p><p>tsohuwa tazo. Don haka suna gaisawa da umma</p><p>tace gurin tsohuwa nazo. Suka shige daki tace da</p><p>tsohuwa nazo ne indan samu dan wani sirrin.</p><p>Tsohuwa tace, name ummi? Ta ce na gyaran jiki</p><p>mana. Fati tace min kwanaki kin fada mata wasu</p><p>abubuwa. Tsohuwa ta ce, ja'ira, kinga uwar bari?</p><p>Dama nace zaki same ni ina kyakkyawan zamana,</p><p>bada ina fada miki kina sharewa ba? Ummi tace</p><p>haba tsohuwa banaso aji mu yanzun dai ki bani</p><p>shawara sannan ki fada min abinda zanyi inja</p><p>hankalin mijina. Ta ce, toda farko ki dinga kula da</p><p>jikinki ta hanyar rufe shi ruf, kada kibar kofar</p><p>iska. Banda tafiya ba takalmi, iska tana shiga</p><p>tanan kuma mace narage ni'ima banda zama ba</p><p>dankwali inso samu ne hatta tsarki ki daina yi da</p><p>ruwan sanyi, ki dinga yida ruwan dumi. Sannan ki</p><p>amshi bagaruwa gurin ummarki ki dinga shiga</p><p>inkin tafasa da alif dakuma saiwar mata, sannan</p><p>inkinyi al'ada kin gama kinyi wanka toki dinga</p><p>matsa farin miski a ehem dinki. Sannan ki samu</p><p>saiwar kankana, saiwar zogale, kanunfari,</p><p>mazarkwaila dazuma amma kisa kanunfari</p><p>dayawa sai ki dafa su su dafu kullum kisha kofi</p><p>biyu safe da yamma. Sannan ki aya garinta,</p><p>kwakwa ma kiyi garinta, dabino ma kiyi garinsa,</p><p>sai ki dinga diban cokali bibbiyu ki zuba amadarar</p><p>ruwa sannan ki zuba zumarki mai kyau kisha, sai</p><p>ki samu kuma gwanda, kankana, abarba, zogale,</p><p>citta, lemun tsami, ki markada su kisha. In anan</p><p>maki katsaya yarinya zakiji ki kin cika cindum</p><p>daruwan ni'ima sai kin samu martaba ta</p><p>musamman agurin miji dan zaijiki kin fita daban</p><p>da dukkan sauran mata. Ki hada da biyayya</p><p>tsafta da kuma iya tsara girki mai dadi. Ummi</p><p>tace, toni yanzun yaya zanyi nasamu saiwoyin</p><p>nan? Tace, bari zanba matar ado dake yawan</p><p>zuwa kasuwar qauye zata zo miki dasu. Amma</p><p>su gwanda gasu nan bakin titi ko shi sai kice ya</p><p>siyo miki, zogale kuwa baki rasa shi gurin</p><p>ummarki, har da cittar da alif din da bagaruwan.</p><p>Ta ce to, ta tafi gurin umma ta amsa har taje</p><p>gida bata daina mamakin tsohuwa ba, ya akayi</p><p>tasan duk wadannan hadin matan? Tun ranar</p><p>alhamis din ta soma aiwatar da darussan da ta</p><p>debo daga tsohuwa, safiyar jumma'a ranar zai</p><p>bar dakin bishira. Ya fito tana sharar tsakar gida</p><p>ta gaidashi, ya amsa da fara'a, tare dawani kallo</p><p>mai fassarar in ba keba. Cikin muryar data adana</p><p>don shi kadai tace, ya abba ina son in je ayi min</p><p>zanen fulawa. Yace jiya kin fita yau kam a'a.</p><p>amma ki aika akira mai zanen tazo ta miki. Ta</p><p>marairaice, towa zan aika yaya abba? Yace aike</p><p>ni, ina ne gidan? Tace layin su umma ne yace to</p><p>za'azo ai miki. Bishira tafito daga daki tazabga</p><p>ma ummi harara, Tare dacewa kisisina. Abba</p><p>yakalleta, kema sai tayi miki. Tace bana bukata,</p><p>aikin banza, shikam yafice. Ummi kuwa tace gaba</p><p>da aikinta, ita ko sai tasa kujera tazauna tana</p><p>sakin zantuka, eh don kwalliyar tabanzanta tunda</p><p>ba a iya biyawa miji bukata. Allah dai yasa ya</p><p>fada min komai, to ni me zai dame ni don 'yar</p><p>aiki kawai na dauki yarinya. Tashare min gida,</p><p>tayi wa mijina abinci, daga nan fa? Saita saki</p><p>shewa, ummi ta ce aranta yau zan bambance</p><p>miki. Birabiskon shinkafa tayi da miya, ta wadata</p><p>birabiskon da kayan lambu, miyar ta dauki nama</p><p>da bushasshen kifi. Sannan ta hada musu kunun</p><p>aya yaji dabino da madara, ta aikawa ummanta</p><p>lokacin da kamal yazo daukar na ummarsu.</p><p>Tasheka wanka taci doguwar rigar shadda koriya</p><p>mai duhu, ta kafe dauri tamkar yau ne daurin</p><p>aurensu. Ga fulawar da yaje ya biya akazo aka</p><p>zana mata. Tanajin rigimar muhibba tafito tazuba</p><p>mata adan kwano tazaunar da ita akofar falon</p><p>mamanta. bishira tafito kicin baki tasaki tana</p><p>kallon ummi da tazo wucewa harda bangazar</p><p>ummi, nan ko kamshi ya bude ta na turarukan da</p><p>ummi ta fesa. Abba yana yin sallama ummi tafito</p><p>da sauri, oyoyo yayana, bishira tana daga kicin</p><p>dinta tana kallon su. Ummi ta rungume shi,</p><p>sannu dazuwa sahibina. Ta amshi ledar</p><p>hannunshi dajakar, yace yauwa sannu babyna</p><p>tace inazan kai ledar? Yace akwai ta bishira aciki</p><p>ki ciro. Ta mika mishi ledar ta wuce dajakar</p><p>dakinta. Ya mika wa bishira lemo da abarba da</p><p>yayo musu tsaraba sannan ya wuce danasu,</p><p>awulakance ta aje. Yana shiga ummi tadan karo</p><p>kofar yanda bishiran zata iya lekensu sosai ta</p><p>gefen kofan. Ta cire masa hula ta aje akan</p><p>madubi sannan ta kunna fanka. Ta shirya masa</p><p>abinci, yauni zan baka har ka qoshi. Haka suka</p><p>yita baiwa juna abaki har suka qoshi. Yakamo</p><p>hannunta mai qunshi yana ta sumbata, wai kamar</p><p>kada su goge. Kumatun shi ta shafa nima yau</p><p>kamin kyau, koda yake dama kai me kyaune, ina</p><p>sonka ya abba sosai. Cikin jin dadi ya mannota a</p><p>jikinshi, nima ina sonki, ina manta kowa da komai</p><p>in muna tare, tace ina tsoron kada wata rana ka</p><p>juya min baya. Ya saqalo hunnuwansa cikin nata</p><p>ina fata in mutu kafin lokacin. Ummi tasomayi</p><p>masa wasu irin darussa wadanda tasan yana</p><p>saurin tada sha'awarshi nanda nan kuwa tasa shi</p><p>fita hayyacinsa yakama surutai. Ummi ta tabbata</p><p>bishira tana wurin ta labe, don haka tai murmushi</p><p>ta bishi suka tafi duniyar ma'aurata. Bishira</p><p>tamkar tayi hauka sai kawai ta fado dakin tana</p><p>fadin, maciya amana, har yanzun ba afita daga</p><p>lokacin girkina ba munafiki. Abba ya tashi sannan</p><p>yaja riga yasaka, ok dama kina labewa ne kiji</p><p>sirrinmu? Da taga ya sauko da zafin rai saita</p><p>gudu dakinta. Yabita yamata tatas, kuma ya fada</p><p>mata cewa tazo ta shiga dakin ta zauna ba labe</p><p>ba, yanzun zai komane yaci gaba daga inda ya</p><p>tsaya. Tayi ta kuka gashi ba damar zuwa gurin</p><p>umman bashir dole ta tafi gidansu. Shi kam abba</p><p>shareta ya yi kosu umma bai fadawa ba. Sabuwar</p><p>soyayya ma ya balle agidan, su ci abinci tare,</p><p>wanka tare, su fita yawonsu a qafa ko amota. In</p><p>yana gurin aiki bini- bini ya kira waya, ita kuma</p><p>ko yaushe cikin kirkirar girki da kwalliya tare da</p><p>dadadan kalaman dazata fada masa take.ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 18</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 18</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 02:19</p><p>Ummi tayi alalar gwangwani ta sauke kenan sai</p><p>ga aunty farida da yake tunda akayi auren ummi</p><p>batazo gidan ba. Har daki ummi ta shiga suka</p><p>gaisa tayi masu addu'a zama lafia, tayi mata</p><p>nasihar zama da miji. Umman taji dadi tare da</p><p>kwadayin ina ma bishira take da halin yayarta, ta</p><p>zuba alala ta kaima aunty falon bishira. Ta isko</p><p>su tana mata fadan kaxanta, cikin murna aunty</p><p>ta anshi alalar taci bishira ta cika fam. Tun tana</p><p>jurewa har tace aunty ai kin zubar min da kima,</p><p>ya ya za'a yi ki anshi abun kishiya kici. Aunty ta</p><p>kalli bishira fuska daure tace ke da ita akwai</p><p>bambamci ne? Bishira tace aunty bambamci ma</p><p>nifa jininki ce ita fa? Aunty tace a musulunci fa?</p><p>Bishira ta hade rai tana kallon aunty, taci gaba</p><p>da cewa, A musulunci tama fiki don tana sallah,</p><p>Haka nima ina sallah, kefa kin faru? In kin soma</p><p>sallar to kin shigo cikin mu ni da ita. Domin</p><p>addinin mu ya nuna muna dukkan musulmi dan</p><p>uwan musulmi ne. Inji mai tsira da aminci. Haka</p><p>zan iya cin abincinta banci naki ba don bakida</p><p>tsafta. Ta daka mata tsawa tashi don allah</p><p>malama kije kiyi wanka, ki wanke duk jirwayen</p><p>nan naki kafin In daukeki da motata. Da zasu tafi</p><p>har kudi aunty farida taba ummi, ummi kam</p><p>godiya ta dinga yi. Haka nan da abba ya shigo ta</p><p>nuna masa tace ai abba ya ciri tuta a zuri'arsu,</p><p>halin mahaifinsu ne da ita. Wata rana aunty ta</p><p>bugo ma abba waya cewa aisharsu ta haihu don</p><p>allah ya fadama bishira koda ya iso gida ya fada</p><p>mata nan ta shiga murna. Washe gari tace zata</p><p>gida tama mahaifiyarsu barka. Sannan taji randa</p><p>zasu abuja wurin aisha. Yace ta shirya ya</p><p>sauketa, ta samu aunty tazo nan dai sukeyi wa</p><p>juna barka, mahaifiyarsu tace dubi yar uwarki sai</p><p>yanxu ta haihu gwanin shawa. Amman kinje kin</p><p>gwarje miji ma yayi maki kishiya, dubeki kamar ba</p><p>yar gidan nan ba. Aunty tace mummy ai ita taso</p><p>ta zama Haka, tunda kaxanta ce sana'arta.</p><p>Hajiya zainu tace ni wani lokacin bana ganin</p><p>laifinta a kaxanta, don a gida bata saba aiki ba.</p><p>Laifinta daya a gurina wannan abba data nace ta</p><p>aura, data tsaya ta gama karatunta ta auri wanda</p><p>zai dobo mata yan aiki komai saidai ayi mata</p><p>tana daga zaune, amman ta likema talakan tela</p><p>wanda bashida ko sisi. Aunty ta katse mamarsu</p><p>da cewa In tana da yan aiki shine har wanka</p><p>zasuyi? Ta cire dan kwalin dake kan bishira kalli</p><p>fa mummy har kanta zasu wanke mata. Mummy</p><p>tace aiki gida ya mata yawa, yaushe har ta gyara</p><p>jikinta? Aunty tace kawai mummy kina goyon</p><p>bayanta ne. Bishira tace aunty mummy ta</p><p>fahimta kece baki fahimta ba saboda kina da yan</p><p>aiki. Mummy tace duk ba kece kika yima kanki ba,</p><p>ga kishiya an maki, bishira ta tabe baki nima duk</p><p>nadama ta isheni. Kuma shi da matar duk bana</p><p>raga masu. Don ban damu ya sakeni ba, yaji ne</p><p>dai nace na daina, daddy ko nazo cin mutuncina</p><p>yake gabansu. Mummy tace kin man dai dai.</p><p>Haka yake bishira kullum cikin tsokanan hayaniya</p><p>da ita da miji ko kishiya. Amman ummi yamxun</p><p>bata kulata Domin umma ta gargadeta. Bishira</p><p>bata bar gidan ba saida mummy ta zugata</p><p>Sannan tace mata jibi kizo za a kai su innarku</p><p>yin barka abuja kije ki dan huta kafin suna.</p><p>Bishira tace daman ban taba zuwa ba, ko anyi</p><p>suna sai na huta. Aunty tace kada ku yanke</p><p>hukunci ba tare da sanin mijinki ba kije kiji ta</p><p>bakinsa. Bishira ta ce ina ruwana da yardarsa</p><p>aunty. Haka kuwa data dawo ta shiga tattaro</p><p>kayan ta dake jibge a gefen gadonta, don ita zane</p><p>ko yau a aka dinka shi In tasa ta cire duk In da</p><p>tayar kafin ta dauke shi yaji jiki. Wani ma saita</p><p>goge ruwa ne, kamu ne, duk kyan zani saita goge</p><p>tsakar daki dashi. Ranar dama abba dakinta</p><p>yake, tace mashi jibi zamu abuja Inji mummy.</p><p>Taso ya dan sai mata zani sabo wanda zata</p><p>danci suna ya dinka mata. Yace akwai wani leshi</p><p>dan sai maku yana shago, Tun wancan satin</p><p>naso In zauna In dinkashi da kaina don mai tsada</p><p>ne. Tace nawa ka siyeshi, yace dubu biyar ko</p><p>wane daya, bishira ta tabe baki. Na zaci zakace</p><p>sha biyar wai dubu biyar, yace matsalata da ke</p><p>rainuwa yace bari zansa a dinka maku gobe ashe</p><p>sunan har yazo? Tace a'a jiya pha ta haihu, ya</p><p>sake kallonta jiya? Shine zaku tafi jibi? Tace eh</p><p>mummy ce tace mu tafi jibi. Yace a'a kibari sai</p><p>ana gobe suna kije. Kafin lokacin ma na samu</p><p>wasu kudi da nike sa rai. Sai na sai maki kayan</p><p>barka zanen maman da kayan baby. Bishira ta ce</p><p>gaskia gobe zamu tafi, In ka sayi kayan barkar ka</p><p>aika dasu can wurin mummy yan tafiya Ranar</p><p>suna su kai mata. Abba yace nifa ban amince da</p><p>tafiyar nan gobe ba. Ban yarda ba. Bishira ta ce</p><p>ba wai ina neman yardarka bane, ina fada maka</p><p>umurnin da mummy ta bani ne, ko ka mance</p><p>mahaifiyata ce? Mamakinta ya cika abba, yace</p><p>mahaifiyarki ita zata baki izinin tafiya ko ni?</p><p>Umurnina da nata yanzu wanene...? Bishira ta</p><p>katseshi kada kayi ganganci hada kanka da</p><p>mahaifiyata, ita ta haifeni ta raineni har ka ganni</p><p>kace kana sona Sannan ka dinga kokarin</p><p>kwatanta kanka da ita? An fada maka kowa</p><p>baisan darajar mahaifiyarsa ba irinka? Abba ya</p><p>mike ni ne bansan darajar mahaifiyata ba? Tayi</p><p>shiru yace nagode Kuma suna na hanashi ma</p><p>gaba daya. Zan gani Kuma Bishira ta ce zako ka</p><p>gani.ls / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 19</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 19</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:14</p><p>Duk ummi tana jiyo su amman bata fito ba, tana</p><p>ta mamakin yarda bishira batasan darajar</p><p>aurenta ba, bare tasan girman miji. Ranar da</p><p>zasu tafi kuwa ko a jikinta ta dibi tsummanta ta</p><p>nufi gidan su, Duk ta fadama mummy yarda</p><p>sukayi. Mummy tace kinman dai dai talakan</p><p>banza shine zai hada kanshi dani, tafiya zakiyi in</p><p>yaso in kika dawo ya ce baya auren. Abba ya</p><p>dawo ya samu dakinta a rufe, ummi na daka</p><p>sakwara a kofar dakinta yace ina bishira? Ummi</p><p>tace ina ga ta fita, don ina daki bansan fitarta ba.</p><p>Ya daga waya ya kira aunty yace bishira tazo?</p><p>Aunty tace bata fada maka zasu tafi abuja bane,</p><p>Abba yace ta fadaman amman nace a'a sai ana</p><p>gobe suna zataje, ya kwashe komai ya fadama</p><p>aunty. Aunty tace kayi hnkr don allah idan ta</p><p>dawo da kaina zan hadata da daddyn mu, Abba</p><p>yace kiyi hnkr aunty na gaji da halin bishira inga</p><p>wannan karo gwara kowa ya huta ni da ita. Aunty</p><p>tace kayi hnkr Abba yace sai anjima ya kashe</p><p>wayarsa. Zama yayi kan kujera dakin ummi yace</p><p>gaskia wannan karo bazai fadawa kowa ba ya</p><p>gama auren bishira. In bai nuna mata kurenta ba</p><p>nan gaba zata masa abunda yafi wannan don</p><p>Haka yabar komai sai ta dawo. Ummi kam</p><p>batason ya rabu da matarsa, amman kam saida</p><p>taga tarairaya cikin kwanu kan nan matsalarsu</p><p>daya, Abba yace ummi kodai asibiti zamuje ne,</p><p>ummi tace muce masu mi? Yace muyi masu</p><p>bayani mana, ummi tace a'a. Yace to muje mu</p><p>fadawa umma, ummi ta zare ido yanxu sai kama</p><p>umma wannan zancen? Yayi murmushi. Ai da zan</p><p>iya mata wannan maganar da tuni na mata,</p><p>asibiti ma abunda yasa banson zuwa sai likita ya</p><p>bukaci ganin wurin. Ni kuma ina kishin wani</p><p>namiji ya kallan mi al'aurarki, ummi tace nima ai</p><p>shine, ya sake janyota jikinshi. Yanzun Haka</p><p>zamu zauna? Shine nakeson in fada maka naji</p><p>kana ka gaji da aunty bishira kila zaka saketa ne.</p><p>Toh don allah ka rabu da ita tunda ko ka saketa</p><p>sai ka auri wata. Tunda nasan zama Haka bazai</p><p>yiwu ba. Ta soma hawaye ya shiga lallashinta</p><p>yace Allah zai yaye masu. Haka sukaci gaba da</p><p>rayuwa cikin kwanakin da bishira bata nan, ummi</p><p>tanason kalolin wasanin da Abba ke mata,</p><p>amman da yaso kwatantawa ko allah ya amshi</p><p>addu'a su ta warke saita kwace jikinta ya hau</p><p>bari tayi ta kuka. Don Haka sai ya hnkr da</p><p>bukatarsa amman ya takura sosai, kuma yana</p><p>ganin dole yabar batun bishira yanxu don Haka</p><p>ya jaye batun saki amman sai dole ya nuna mata</p><p>kurenta. Ranar data dawo kwananta takwas</p><p>Ranar ma bata da niyar dawowa sai da aunty ta</p><p>kira mahaifinsu ta sanar dashi, ya kirasu a waya</p><p>ya zagesu tas gaban mahaifiyarsu harda mai</p><p>jego. Tace bishira ta dawo shine ya kira Abba da</p><p>waya ya bashi hnkr yace Duk irin wannan ta faru</p><p>ya kirashi ya sanar dashi. Abba ya shigo da T. V</p><p>guda 2 daya ya kai dakin ummi, daya ya kai falon</p><p>bishira wanda ya yanke kwadon. Ummi tayi ta</p><p>murna bishira kuma ta daki Duk rashin kunyarta</p><p>gabanta sai faduwa yake, batasan ya zasu</p><p>kwashe ba. Sai da taga baiko kalleta ba daga ita</p><p>har yar sannan ta dan saki jikinta, tasan ba zai</p><p>tsaya a fushi ne in taci sa'a. An dauki sati guda</p><p>Abba baya ko kallon inda bishira ta ke ko Ranar</p><p>girkinta sai dai yayi kwanciyarsa a falonta. Duk</p><p>da yana bukatarta Haka kuma ya janye yan</p><p>wasanin da yake da ummi don wahalce yake</p><p>bacci, ita kuma sai ta damu don ya saba mata</p><p>sai tayi tunanin ko laifin tayi masa ne. Ita kam</p><p>bishira ganin zura ido ba zai kaita ba, don Haka</p><p>ta sauke zafin kai ta iske Abba a falonta wani</p><p>dare harda kukanta take bashi hnkr. Wai sherin</p><p>shedan ne ba zata sake ba, Abba ya dubeta mi</p><p>kikayi? Tace nidai ka yafeman, yace ashe kinsan</p><p>kinyi ba dai dai ba? Ai inda ke ce saikin kara,</p><p>amman bari kiji na rantse maki duk kika kara</p><p>zuwa wani wurin bada izinina ba wllhi sai kinsha</p><p>mamaki. Tace na yarda, abun mata da miji nan</p><p>dai suka sasanta, hakan nan dakin ta ya kwana,</p><p>suna shiri cikin satin don bishira ta fahimci mijnta</p><p>ita kadai a matarsa, yarda yake rawar jiki lokacin</p><p>kwanciyarsu. ***ummi na zaune idonta kan tv</p><p>Abba take kallo yarda yake watso turanci cikin</p><p>kwarewa. Kullum kara sonshi take, ta kwantar da</p><p>kanta a hannun kujera, kusan sati guda kenan</p><p>tana lura da Abba. Baya son ko taba hannunta</p><p>sannan ga wani shiri da yake da matarsa, sai dai</p><p>yazo yaci abinci ya dauki laptop dinsa ya raba</p><p>dare. Inko yazo kwanciya saidai ya juya mata</p><p>baya sabanin kwanaki da yake mata makwanci da</p><p>hakarkarinsa, lokacin tasan babu inda keda dadin</p><p>kwanciya ga matar aure irin hakarkarin mijinta,</p><p>sam bata iya bacci sai tunanin abunda tayi masa,</p><p>amman yau din nan zata tmbysa ko laifi tayi</p><p>masa, Bayan yaci abinci yayi wanka ta dauko mai</p><p>zata shafa masa ya amsa da murmushi yace</p><p>barshi kawai nagode, ta dawo ta zauna, zaya fita</p><p>tace ina zaka ya Abba, yace aski zani, ko zaki</p><p>rakkani tace eh yace taso muje. Suna tafe suna</p><p>hirar aikin shi, yace An koma kirkirar wani filin</p><p>kuma An saka shi ciki, yanxu abubuwa zasu kara</p><p>mashi yawa. Sun isa babu layi An suma mashi ya</p><p>mika mata wayoyinsa guda biyu tana danne</p><p>danne kira ya shigo. Nan take ta hade rai ganin</p><p>sunan dake jiki zainab dina, ya tmbyta da ido</p><p>waya kira ta sake hade rai, sannan ta mika masa.</p><p>Ya kalli sunan zainab sannan ya daga cike da son</p><p>ya zolayi ummi yace zainabuna. Can bangaren</p><p>Duk da kallaman Sun mata dadi tace da ba</p><p>amman yanxu ta wani ce. Yaya salis ya kawo</p><p>maka katin aurena? Yace eh yabani tace ya</p><p>amarya? Yace gata bari in bata ku gaisa, ummi ta</p><p>kauda kai tare da jan tsaki, yayi dan murmushi</p><p>yanason yanda ummi ke nuna kishinsa, salon da</p><p>take wurin kishinta daban ne. Yace zainab Wai</p><p>tana gaisheki, zainab tace to ina amsawa. Ka</p><p>gaida umma sannan ka sai masu anko kalla biyu</p><p>ne. Abba ya naji ko kalla goma ne zan saya tace</p><p>to gobe kazo gidan mu nan ake sai dawa. Ya kalli</p><p>ummi yasan kadan ya rage ya kaita bango. Ya</p><p>danne dariyar da ta taso masa yace gobe kikeso</p><p>nazo gidanku zainab? Tace eh don gobe za'a</p><p>kawo wasu kayan, yace to zanzo, ummi ta zaro</p><p>ido ta mika tsaye dai dai lokacin da aka gama</p><p>askin. Yayi sallama da zainab din sannan ya</p><p>shiga karkabe jikinsa. Ummi kam tuni ta kai bakin</p><p>kofa. Ya sallami mai askin ya isketa Sun jera</p><p>yanxu ba kamar daxun da suke fira ba. Sun kusa</p><p>layinsu yace muje mu gaida su umma tace ni</p><p>bacci nakeji baice komai ba, Sun iso hijabi kawai</p><p>ta cire ta kwanta, yace Wai lafia don zainab ta</p><p>kirani tun dazun kin kasa sukuni?URFIN CIKI book 4 part 20</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 20</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:17</p><p>Ummi ta taba baki, Allah yakawo ta lpy. Ya ce ni</p><p>ban soba gsky. Sbd ke ummi tadafa kirji, sbd ni?</p><p>Ni ya abba, kada kasa duniya ta zage ni, Tare fa</p><p>nasameku? Yace to ni dai kada kiga kamar da</p><p>son raina, tace don Allah ya Abba kabar zancen</p><p>nan. Kaje kagyar mata dakunanta don su kamal</p><p>bazasu iya ba, yanufi gurinsu ganin kamar ya</p><p>damu yasa itama taje tasa musu hannu don dai</p><p>ya saki ranshi, sun gyara tsaf ummi ta goge</p><p>sannan ta rufe dakin. Har magriba bishira bata ji</p><p>an ce za'a maida taba, sai ta dauki wayar</p><p>kanwarta ta kira shi wai yazo don Allah</p><p>yadauketa. Tsakanin mata da miji sai Allah, nan</p><p>ya tausaya mata yace zaizo, kafin ya isa sai daya</p><p>sai mata waya irin dai ta hannun ummi. Har cikin</p><p>gidan ya shiga suka gaisa da babanta, yayi</p><p>murna sosai yayi tawa Abba godiya, tare da ba</p><p>shi hakuri yace yasan yanda ta horu zai gata</p><p>canza da yardar Allah. Yasa aka turo ta yayi</p><p>mata nasiha, sannan ya gargadeta da cewa inhar</p><p>ta bari mijinta yakawa kararta zatayi mamakin</p><p>abinda zai mata. Tace, insha Allahu baza ta kara</p><p>ba, yakawo kudi yaba Abba, da kyar ya amsa ita</p><p>kuma ya bata wasu zannuwa acikin leda, yace su</p><p>raba da abokiya zamanta. Taje tayi wa hajiya</p><p>zainu sallama suka tafi, tamkar baquwa haka ta</p><p>koma, sai kace basu taba zaman aure da Abba</p><p>ba, nauyinsa take ji. Suna tafe ya ciro waya ya</p><p>miqa mata, tasa hannu ta amsa yace taki ce, tayi</p><p>ta godiya yace ba komai. Sallamarsu tasa gaban</p><p>ummi faduwa, ta dake ta fito ta amsa, wani kishi</p><p>ya tasho mata amma saita danne. Ta kalli bishira</p><p>tare dayi mata sannu dazuwa, ta amsa tana</p><p>kallon ummi tayi kyau tagoge daga ka ganta</p><p>kaga wayayya 'yar gatan miji. Ta dauko makullin</p><p>dakin ta ba bishira, abba kuma ya nufi dakin</p><p>ummi. Bishira ta dinga kallon yanda abba ya</p><p>gyara gidan yaja gini ta gefen ummi yayi mata</p><p>falo da kicin, sannan tsakar gidan an gyare shi da</p><p>tiles. Haka bandakin su yagyara shi, nan dai</p><p>bishira ta shiga dakinta ta zauna bakin gado tana</p><p>yi wa allah godiya tare dayi wa kanta alkawarin</p><p>har abada bazata ta kara yin yaji ko ta janyo</p><p>abinda zaisa mijinta ya sake ta ba. Ummi tana</p><p>kan gado tana karanta wani littafi yazo ya zauna</p><p>bakin gadon bata ko kalle shi ba don haushi take</p><p>ji. Sai take ganin kamar rawar kai yake yi da</p><p>dawowar bishiran, kuma tuntuni yana zuwa gurin</p><p>ta ya boye mata. Yace madam ina son in yi</p><p>magana da ku ne ke da bishira, ummi tace ina jin</p><p>ka, yace can zaki zo muje. Tace, gsky nagaji, kayi</p><p>maganar da safe. Yagama gano kishi ne ke</p><p>damunta, don haka yayi murmushi yace yanda</p><p>kikace hakan za'ayi. Ya fita kamar minti 30</p><p>yasake shigowa ya aje mata leda tare da cewa</p><p>saida safe aciki tace Allah yabamu alheri. Yana</p><p>tafiya taje ta banko kofarta, yau kam bacci ya qi</p><p>idanun ummi sbd tayi sabon bacci a haqarqarin</p><p>Abba. Dukkan filolinta ta rasa wanda zai maye</p><p>mata madadin haqarqarin mijinta, ynzun yancan</p><p>da wata tasan yanda yake wannan rawar jikin</p><p>ynzun ya manta da batunta. Tarasa me yake</p><p>mata dadi, littafin datake karantawa kuwa sam</p><p>bata fahimtar abinda ke ciki. Hka ta dinga zubda</p><p>hawaye har nisan dare, ganin bata da wata</p><p>mafita, tashi tayi ta bude kofa lokacin 2 saura</p><p>taje tayo alwala tazo ta kama nafila. Abba jin</p><p>bude kofarta ne yasa shi leqowa ta window</p><p>aranshi yaji tausayinta don yasan bata iya bacci</p><p>sai ajikinshi, ita bata san ya leqo ba don ko</p><p>hanyar dakin bata ishe ta kallo ba. Yakalli bishira</p><p>wadda bacci yayi gaba da ita ya tausaya mata</p><p>sosai yanda tayi tarawar jiki alokacin</p><p>auratayyarsu dazun. Yadauko wayarshi yarubuta</p><p>ma ummi sako. KI KWANTA KIYI BACCI BABY,</p><p>TARE DA QISIMA CEWA KINA LAFE</p><p>AMAKWANCINKI (WATO JIKINA) INA CIKE DA</p><p>KEWAR LEBUNANKI Tana sallah taji shigowar</p><p>saqo amma bata yi ko marmarin dubawa ba, haka</p><p>tai sallah har zuwa lokacin da bacci yasoma</p><p>fizgarta. Tayi adduo'o'i sannan ta kwanta, saida</p><p>asubahi ne datayi sallah sannan ta karanta, dan</p><p>tsaki taja tare da cewa, Karya kawai, kishi yasa</p><p>ta fadin haka don tasan Abba sosai baya boye</p><p>mata komai ynzun. Sai dai abinda yasake qular</p><p>da ita da asubahin nan yanda tana fita shi kuma</p><p>ya fito wanka, duk da tasan dole wani abu yafaru</p><p>tsakaninshi damatarsa, amma sai taga tamkar da</p><p>gayya ya tsaya don tafito taganshi. Tna idar da</p><p>sallah ta dora ruwa akicin dinta, tadafa ruwan tea</p><p>taje kicin din bishira tadauko flask tazo ta wanke</p><p>ta zuba musu ruwan zafi taje kofar bishira tayi</p><p>sallama bishiran ce ta bude ummi tamiqa mata</p><p>tare da cewa an tashi lpy? Cikin sakin fuska tace,</p><p>lpy lau, nagode. Ummi ta ce ba komai takoma</p><p>dakinta ta kulle kofarta don yau bata da darasin</p><p>safe. Abba ma yau bada wuri zai fita ba, don</p><p>haka yadan samu baccin safe sai 8 yayi wanka</p><p>ya karya, sannan yanufi dakin ummi. Kofarta tana</p><p>rufe, ya kwankwasa ta share sai can dai dataji</p><p>yaqi tafiya sannan tazo tabude. Takalle shiya yi</p><p>kyau cikin kananan kaya, ta kauda kai tare da</p><p>cewa, an tashi lpy? Yace lpy lau, kin karya? Tace,</p><p>um'um sai anjima, zata rufe kofar yace,</p><p>makaranta fa? Tace sai karfe 2 nake da darasi.</p><p>Ta maida kofar ta rufe, yayi dan murmushin</p><p>takaici sannan yafita. Kwananshi 2 dakin bishira</p><p>yayi niyyar dawowa dakin ummi, don ya kosa</p><p>yadawo ya lallasheta bazai iya daukar wannan</p><p>shariyar da take mishiba. Tsakaninta da bishira</p><p>lpy lau amma shi sai tana wani share shi. Ya</p><p>shigo da zumudi zai nufi dakinta, tamiqe cikin</p><p>fara'a daga wanke-wanken da take yi ta amshi</p><p>ledar hannunsa da jakar laptop ta nufi dakin</p><p>bishira. Shida bishira suka bita da kallo, ganin</p><p>zata shiga bishira tace ummi yau ai dakinki yake.</p><p>Ummi tace injiwa? Anty bishara ai kullum ke ce</p><p>dashi har sai kin rama duk kwanakin da kika</p><p>dauka agida. Kinga kenan kusan wata goma sha</p><p>daya kenan. Abba cikin sauri yace ke</p><p>mahaukaciya ce? Ina ki kasamo wannan fatawar?</p><p>Ta kalle shi, sannan tashiga dakin ta ajiye ta fito</p><p>taqara kallonshi gurin malamai, yace to ban</p><p>yarda ba, don haka zanci gaba dayi muku kwana</p><p>bibbiyunku, ummi tace to ni na yafe mata nawa</p><p>kwanakin bishira tace nagode ummi. Haushi ya</p><p>cika Abba, amma shi bazai dauki wannan horon</p><p>da ummi take shirin yi masa ba. Yadawo dakin</p><p>bishira a fili yafurta kema saina baki haushi zakiyi</p><p>dakin sanin wannan furucin. Sharewa yayi yaci</p><p>gaba da kwana dakin bishira tare da nuna kulawa</p><p>ga bishiran. Ummi ta jure duk da duk daren Allah</p><p>sai taci kuka ta gode Allah, sannan tashiga zargin</p><p>cewa shi ma ya Abban dama can yana son</p><p>tarewa dakin bishira, inba haka bame zaisa yayi</p><p>saurin yarda kuma yayi ta nuna mata soyayya?</p><p>Ganin ummi tana yi tamkar bata damu ba yasa</p><p>shi qa rajin haushi, yadawo da yamma suna</p><p>zaune kowa A qofarshi. Ummi tayi kwalliya cikin</p><p>qananan kaya, bishira kuma tana sanye da leshi,</p><p>karatun littafi bishiran keyi ita kuma ummi tana</p><p>yin gyaran qumbunanta. Bawai suna wata hira</p><p>bane amma suna kula juna sosai musamman</p><p>bishira tana son su saba da ummi. Ummin ce.</p><p>bata cika son fitowa ba, bishira ta tashi ta masa</p><p>sannu dazuwa tare da amsar kayan hannunsa</p><p>don yanzun tana koyi da ummi gurin kyautatawa,</p><p>ummi ta kalle shi sannu dazuwa, ya amsa da</p><p>yauwa baby. Yakalli bishira sweety zanyi wanka,</p><p>tace to, takai masa ruwa yashiga dakinta, sai</p><p>tazo tace masa takai nan k sweety zanyi wanka,</p><p>tace to, takai masa ruwa yashiga dakinta, sai</p><p>tazo tace masa takai nan kuma yajanyo bishira</p><p>jikinshi. Ba wai yana da bukata bane, amma don</p><p>ya shaqar da ummi sai ya banko kofar, qaran</p><p>kofar ne yasa ummi kallon gurin dakin. Ta duqar</p><p>dakai taci gaba da abinda take yi, kusan minti</p><p>arba'in suka fito, Abba ya matsawa bishira wai</p><p>suyi wanka tare, tace ni bazan iya ba akwai ummi</p><p>dama da dare ne inajin kunya. Kuma kada taga</p><p>kamar cin fuska ne, yace kenan don kada ki bata</p><p>mata rai ni mijinki bazaki faranta min ba ko? Dole</p><p>ta bishi suka shiga bayi. Baqin ciki yasa ummi</p><p>tashi tashige daki, kuka sosai tayi daga nan bata</p><p>fito ba sai magriba, tanayin alwala tarufo kofa,</p><p>washegari ma qin bude qofar tayi daga alwalar</p><p>asubahi. Abba yayi ta raba ido ya ganta amma</p><p>bata fito ba, yasan fushi take, ya kira wayarta</p><p>taqi dagowa yayi mata saqo cewa in zata</p><p>makaranta tafito inkuma sai darana ta bude ta</p><p>amshi kudin mota. Tana gama karantawa tayi</p><p>wuri da wayar ba tare data bashi amsa ba, haka</p><p>ya tafi. Bishira ta qwanqwasa ma ummi ta bude</p><p>suka gaisa, tace naga baki fito bane ina fata lpy?</p><p>Tace lpy lau bacci ne, tace yau baza kije</p><p>makaranta bane? Ummi tace, zanje sai sha biyu.</p><p>Bishira tace kinji dadinki ni gashi nan ina tayi</p><p>masa zancen karatun amma ya share ni, ummi</p><p>tace inkin matsa zai yarda, tace ko za ki dan sa</p><p>min baki? Ummi ta riqe baki, ni a wa? Ke da yake</p><p>hannunki ai ke ce zai saurara, ni kin zo ne ma ki</p><p>zage ni. Bishira tace wane irin zagi? Ni dama ki</p><p>amshi mijinki ummi don gangar jikinshi ce kawai</p><p>agurina, amma ruhinsa yana gurinki. Ummi ta ce,</p><p>ngd da zagi, bishira ta ce zancan gsky ne ba</p><p>wani zagi. Haka suka yi ta rayuwa cikin kwanakin</p><p>ummi kam har rama tayi shima Abba ya rage</p><p>walwala don wanda yasan kan kula da shi</p><p>kamarta. Yayi missing din abincinta. Amma ya</p><p>gaji bazai jure ba. Ya tuna bishira tace masa zata</p><p>ta yini gidan ummanshi. Don haka yana gama</p><p>muhimman abubuwan da zai yi agurin aikin</p><p>yanufi gida. Ummi tana shirin tafiya makaranta ta</p><p>dauko jakarta sai kurum taga mutum kamar an</p><p>jeho shi. Ta daure fuska tamkar bata taba dariya</p><p>ba, yace ummi nagaji kin ji ko, na gaji da wannan</p><p>horon naki. Laifin me nayi miki? In don na dawo</p><p>da bishira ne sai in saketa, duk ba kece kika</p><p>takura min sai na dawo da ita ba? Ummi tace, ni</p><p>karka doran jakar tsaba kasa kaji su bini, ka saki</p><p>matarka sbd ni? Ba ruwana. Yace, to ki dawo</p><p>yanda kike, kuma ki janye batunki na wai kin</p><p>haqura dani, niban haqura ba. Ke ma kuma nasan</p><p>dole ki kasa kanki, ummi ta ce ni ban damu ba,</p><p>ya ce qarya ne gashi nan duk kin rame? Ya</p><p>canza daga fada zuwa lallashi, ummi don Allah</p><p>na roqeki mu koma kamar da, haba bebyna. Ya</p><p>lalubo hannunta ta qwace, don Allah ka tafi kada</p><p>bishira ta dawo ta same ka anan ta zargi wani</p><p>abu. Haushi yakamashi sosai, ya daga murya da</p><p>qarfi, kin san Allah ummi zan hadaki da umma, ta</p><p>nufi hanya fita, nikaga kada kasa ni yi latti don</p><p>lokaci yayi nisa. Ya ficiko ta ta dawo ba zaki</p><p>makarantar ba, ke an ma daina karatun tunda yafi</p><p>ni. Ta zubar da jakar da hijabi ta nufi gado shi</p><p>kuma ya fita cikin zafin rai, gidan su umma yaje.</p><p>Bishira tana dakin umma tana sallah yabi umma</p><p>kicin, umma gurinki nazo, ta dube shi lafiya</p><p>Abba? Ya turo baki, alamun ranshi bace baki,</p><p>yace umma ki sallami bishira, tace kamar yaya?</p><p>Yace taje can gidan ko muyi maganar agabanta?</p><p>Tace, kyale ta muje dakin babanku. Abba ya fada</p><p>ma umma komai da ummi ke masa, tun dawowar</p><p>bishira ran umma ya baci tace ka barni da ita.</p><p>Banda shashancin ta da ita kadai take son</p><p>azauna? Baga bishirar nan ba gidan nan ta gane</p><p>kuskurenta ko yau yarinyar nan sai da tace in</p><p>yafe ta nace ni dama ban riqe ta da wani abu ba.</p><p>Shine ita zata qirqiro fitina? Yace, umma ai ba da</p><p>bishira take yi ba dani take yi, tace to zata gane</p><p>kurenta da dare kuzo kai da ita. Umma ce ta kira</p><p>ta awaya tace tazo ita da abba, jikinta ya mutu</p><p>don tasan qararta aka kai, tana idar da sallar</p><p>isha'i taje gidan. Can tasamu abba, nan ko umma</p><p>ta rufe tada fada, koda tsohuwa ta jiyo tazo</p><p>umma tafada mata komai sai ta shiga fada. Wai</p><p>ai kishi halas ne, ke suwaiba tsakani ga Allah ko</p><p>ke bazaki so kishiya ba, bare ita yarinya. Abba</p><p>yace to gata nan ita ce fata dame ne nida batun</p><p>in dawo da bishirar, yanzun na dawo da ita kuma</p><p>ni abin ya qare akaina? Nan fa umma tayi mata</p><p>tatas, ta kuma sata anan ta ba Abba Haquri, aka</p><p>kira shi awaya ya fita. Umma ta samu dama</p><p>taqara yi mata nasiha da cewa, in bnda shirmenki</p><p>yaushe zaki bar ladanki, hanyar aljannarki kice</p><p>kinyi fushi da ita kin barwa kishiya? To kada in</p><p>sake jin haka, ki riqe darajarki da mijinki, ke</p><p>ganinki da ita. Ta jima tana bata shawara kafin</p><p>Abba yadawo suka nufi gida. Ya shiga gurin</p><p>Bishira ya fada mata cewa yau gurin ummi zai</p><p>kwana, nan ya bar ta da kewa yanufi gurin ummi,</p><p>tamkar yaune daren farkonsu hara sukai rayuwa</p><p>s / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 21</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 21</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:19</p><p>Kwanci tashi asarar mai rai, shekara ta zagayo</p><p>lokacin bishira da tsohon ciki, Abba nason yara</p><p>don muhibba taqi dawowa tafi son umma dole</p><p>suka haqura suka bar mata. Ta haifi 'yarta</p><p>budurwa tubarkalla ranar suna ta ci sunan sahura</p><p>inda suka sa mata walida. Ummi nason yara, don</p><p>haka in tana gida to tana manne da walida, Abba</p><p>yana damuwa da rashin samun cikin ummi,</p><p>wanda ita ummin ta barma Allah komai. Shekaru</p><p>uku sun sake biyo baya, lokacin Bishira ta sake</p><p>haihuwar habiba takwara Abba yayi wa ummi.</p><p>Tsohuwa an qara tsufa, 'yan rigingimu sun qaru</p><p>tace ita Abba yama takwara amma bata son ya</p><p>duke ta irin yanda yayi wa ummi. Abba kullum</p><p>qara son ummi yake, umma ta matsa masa sai</p><p>da yayi qoqari ya sai fili rabin filoti tace kuma a</p><p>rage ciye ciyen dadin nan agina shì. Haka kuwa</p><p>ya gina flat mai daki hudu, daya ummi daya</p><p>bishira, sai nashi sannan na yara. Yayi qoqari</p><p>gurin gyaran falon ita kuma ummi ya canza mata</p><p>kayan daki don bishira an canza mata daza su</p><p>tashi agidan su. Yace tabishi bashi in ya samu</p><p>zai bata kudi amadadin kayan daya saima ummi,</p><p>tace ta yafe. Ummi dake karantar (BUSSINESS)</p><p>har ta hada (H.N.D) dinta kuma tayi bautar qasa.</p><p>Abba dai yace baza'ayi aiki ba amma ya yarda</p><p>tayi kasuwanci, Alhaji babba ne ya bata jari inda</p><p>take saro kaya zannuwa, lesuna, takalma zuwa</p><p>jakunkuna. Abin ya amsheta don har kayan aure</p><p>tana hadawa, tana yin saqo irin su kwatano da</p><p>chaina, india, pakistan ko dubai, ta hanyar wani</p><p>wan kawarta. Haka kawai ummi ta samu kanta</p><p>da zaban abinci, yawan bacci kasala da dai</p><p>sauransu, sam bata san takamaiman lokacin</p><p>al'adarta ba. Don bata wani lissafi in yazo shi</p><p>kenan in bai zo ba bata damu ba tama cire ranta</p><p>daga batun ciki. Abba ya kalli nonuwanta, baby</p><p>kwanan nan kirjinki ya cika sosai, gashi kinyi</p><p>haske ko kin canza mai ne? Tace yaya yaushe</p><p>kazama likita? Yace, ummi kin fa canza shirya</p><p>muje asibiti, ta ce ya Abba don Allah ka bar ni</p><p>nagaji dazuwa asibiti. Yace, to ni zan je inya</p><p>tambaya game da yanda ki ka canza. Cikin jin</p><p>haushi tace sai ka dawo. Ga yara atsakar gida</p><p>sun ishe mu, yace ni naki nake qawar in gani</p><p>nasan addu'ar da nike yi bazata fadi kara banza</p><p>ba, sannan ga qoqarin danake yi, shiru ta masa.</p><p>Dagaske yake yi yaje yayi wa likita bayani, yace</p><p>yadai kawo fitsarinta. Sai da suka yi tsiya da qyar</p><p>bishira ta lallasheta ta yarda ta bada fitsarinURFIN CIKI book 4 part 23</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 23</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:22</p><p>Sam bishira bata damu da barin mijinta da zatayi</p><p>gurin ummi ba, tunda ta jima da sanin cewa</p><p>ummi bata da wani ammafni. Wannan ne ma</p><p>yasa tasha alwashin in taje zatayi addu'a Allah</p><p>yakara toshe ummin kada ta warke sam, tunda</p><p>umma Bashir ta fada mata duk addu'ar da tayo</p><p>kafin ta dawo an karba mata. Ta kuma kara bata</p><p>shawara ta roko musu rigima suyi tayi har su</p><p>rabu, Bishira tace duk zata roko. Ko ranar da</p><p>zasu tafi sai da ta yi wa ummi habaici, kawyenta</p><p>sun shigo wato makotansu a tsakar gida take</p><p>fada musu cewa mijinta kurum take tunani. Wai</p><p>zai sha wahala kafin ta dawo. Wata cikin su tace,</p><p>wahalar me ga shi da amarya? Ta ce amaryar da</p><p>ta ke a toshe, ai bata da ammfani. Ummi duk</p><p>tana ji, takaicin duniya ya isheta sai dai ita zata</p><p>so ace bishiran take ta roko ma kanta shiriya ko</p><p>Allah zai sa ta dawo ta kama sallah. Dayar tace,</p><p>to Bishira ki roko mata sauki mana, cikin zolaya</p><p>tayi zancen, Bishira tace ba abinda zai kaini</p><p>makka in roko ma kishiya abin arziki. Ummi ta</p><p>fito ta ce Anty Bishira zai fi kyau ki roko ma</p><p>kanki shirya ko in kin dawo kya fara sallah da</p><p>tsafta. To ban san ma yanda zaki kwashe da</p><p>ibadar ba ko za a karba tunda ba yin sallah ki ke</p><p>ba. Ta taso fuuu, kawayen suka reketa suka ce</p><p>kyaleta bakin ciki ne. Abba ya fito wanka yana</p><p>cewa, Ok, za kuyi na bankwana ko? Yana da kyau</p><p>hakan. Ummi ta koma dakinta. Tun bayan tafiyar</p><p>Bishira Abba ya shiga takura musamman irin</p><p>wannan lkc na sanyi. Ya dawo da yiwa ummi 'yan</p><p>wasanni da ya daina, sai hakan yakara sa shi</p><p>damuwa don haka ya shiga lallashin ummi ta</p><p>fadawa umma....... Kuyi hkr da typing din banda</p><p>lafia sstr dita nake sawa tana maku.els / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 24</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 24</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:24</p><p>Tace ita kam ba zata iya ba ranar wata juma'a</p><p>suka tafi da nufun su fadama umma matsalarsu,</p><p>sai dai har zuwa bayan isha'i da abban yazo don</p><p>su tafi sun kssa sanar da umman komai, har</p><p>sunyi sallama abba yayi kunar bakin wake yace</p><p>umma ta fada maki matsalarta? Umma tace wa?</p><p>Yace ummi tace a'a suka koma suka zauna. Abba</p><p>kanshi na kasa Yace umma dama bata da lafiya</p><p>ne? Umma tace mike damunta kuma? Yace ummi</p><p>fada mata. Ummi ta sunne kai cikin cinya tare da</p><p>cewa shiya fada. Cikin sa'a aka kira wayarshi,</p><p>nan yayi waje ya barsu, umma tasa ummi saita</p><p>fada. Ummi ta rasa ta inda zata dauki zancen,</p><p>umma ta soma yi mata fada har tsohuwa ta leko</p><p>tambaya take lafiya ba sunyi sallama dama basu</p><p>tafi bane? Umma tace wai bata da lafiya ne,</p><p>kuma ita da abban sun kasa fadaman shi yayi</p><p>waje, ita kuma ta kunshe kai cikin cinya wai injira</p><p>ya dawo ya fadaman. Tsohuwa taja hannun</p><p>ummi zuwa dakinta, suka zauna bakin gado ta</p><p>riko hannunta. Takwara fadaman abunda ke</p><p>damunki. Ummi ta sunkuyar da kai ta kasa</p><p>magana. Tsohuwa tace inda baki fadaman ba</p><p>akwai wanda zai taimaka maki ne? Tunda naga</p><p>duk yarda mijinki yake da umman ku ya kasa</p><p>fadamata to abun mai girma ne. Ummi ta daure</p><p>tace "Gabana ne fa a toshe....." tsohuwa ta rafka</p><p>salati, sannan tace yannan badai angurya ba?</p><p>Cikin tsoro ummi Tace, ni ma ban sani ba ko</p><p>shine. Salati tsohuwa ne ta jawo hankalin umma</p><p>tazo dakin da sauri. Tsohuwa Tace ina ga</p><p>yarinyar nan angurya ne a gabanta. Umma Tace</p><p>shine don wauta daga ke har abban kukayi shiru,</p><p>dubi tsawon watanin da kuka dauka, tsohuwa</p><p>Tace yanzun yaya za'ayi umma tace ni ina nasan</p><p>yanda za'ayi, ai ni na zata yanzun babu masu irin</p><p>wannan ciwon. Rabon da inji labarinshi tun muna</p><p>yan mata. Tsohuwa Tace kai nima na jima banji</p><p>ba, amman kinsan dama wanzamai ke aikin.</p><p>Alhaji ya dawo daga sallar isha'i yaga abba tsaye</p><p>a waje, Yace a'a babana dama baku tafi ba, Abba</p><p>yace eh yanzun zamu wuce, ya biyo bayan Alhaji</p><p>suka shigo suka riski zancen dasu dasu umma</p><p>keyi. Alhaji Yace lafiya? Umma Tace yaran nan</p><p>ashe zaune suka da lalura, tame inji Alhaji, umma</p><p>Tace angurya ce ashe ta fito ma Ummi wai suka</p><p>zaune. Alhaji yace meye kuma angurya Tace wani</p><p>abu ne dake toshe mace. Nan fa suka shiga</p><p>tattauna yanda za'a shawo kan abin, tsohuwa</p><p>Tace wanzami za a kira ya yanka mata. Alhaji</p><p>yace to gobe zai kira wanzami. ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 25</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 25</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:26</p><p>Abba da jin haka sai ya fito, kishi fal da</p><p>zuciyarshi, ya ce umma wanzami kuma? Ta ce</p><p>eh, aikin sune. Yace gsky umma ba za a kai ta</p><p>gurin wani wanzami ba , bagara muje asibiti ba.</p><p>Tsohuwa ta ce, kaci gdanku da asibiti komai ku</p><p>ce asibiti to wannan ba aikinsu ba ne. Abba ya</p><p>ce, Nifa gsky ba xa a kai min mata gurin wani</p><p>wanzami ba, umma asibiti zamu. Yanzu kai ya</p><p>waye wanzamai ba duka suke dafa kayan aikinsu</p><p>ba, haka kawai taje ta hadu da wata cutar? Alhaji</p><p>yayi murmushi yasan kishi ne ke damun Abba, ya</p><p>ce Babana kada ka damu, goben sai kuje asibitin,</p><p>in sun ce ba su san shi ba to sai a zo a yi na</p><p>wanzam ko ? Kunya ta kama Abba, Sam ya</p><p>manta Alhaji yana gurin ya ce to Tsohuwa ta ce</p><p>kuje in kun je ma dawowa za Ku yi dan me taurin</p><p>kan tsiya. Abba ya ce naji kin ji ummi taso muje</p><p>gda Tsohuwa ta ce oho dai, kuyi ta tafiya in dai</p><p>akayi mata aikin ai dole ka barta ta warke . Alhaji</p><p>da umma dai dariya sukayi ta yi musu, shi kuma</p><p>yayi musu sallama, ummi kam kasa magana tayi</p><p>don duk ta tsorata. Suna fita ta rike hannun Abba</p><p>gam tana cewa. Don Allah ya Abba kada kabari</p><p>wanzam yayi mini aikin nan, zan ji zafi. Ya</p><p>rungumota, Ba zan amince ba wani ya ganmin</p><p>al'aurar mata, likita ma mace zan nema ko nawa</p><p>zan kashe . Ummi ta ce, to zan ji zafi ya Abba?</p><p>Ya ce, made ki damu, in asibiti ne kila suyi miki</p><p>allurar kashe zafi amma in wanzami ne ina za ya</p><p>ga wata allura yayi mini. Ummi sarkin tsoro ranar</p><p>kwana tayi cikin damuwa, washegari kuwa tun</p><p>bakwai suna asibiti. Babban asibiti suka je sun</p><p>yanki kati likita me kula da fannin mata aka tura</p><p>su. Mata dayawa suna ta kallon su ummi</p><p>musamman yanda Abba ke nan-nan da ita,</p><p>sannan wasu sungane shi kasan cewar shi dan</p><p>jarida mai farin mini. Wasu mazan kuwa sai zuwa</p><p>suke suna gaida shi. An kirata dakin ganin likitan,</p><p>ta mike zata Shiga Abba shima ya mike, wata</p><p>Nurse ta ce, malam jira mana, ya ce ai duk Mu</p><p>biyu ne bamu da lfy, ya shige likitan namiji ne ba</p><p>yanda ya iya dole ya yi masa bayani likitan yayi</p><p>ma ummi tambayoyi in da duk ta bashi amsa/ ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 26</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 26</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:27</p><p>Sannan ya bukaci ta kwanta kan gado ya saka</p><p>safar hannu, juya kai abba yayi don gaskia ranshi</p><p>ya baci, lallai ya kamata mata musulmai su dage</p><p>suyi karatun likitanci don su taimaki yan uwansu</p><p>mata. Sai da likita ya gama dubata sannan ya iya</p><p>dubansa, likita yayi wani rubutu ya mika abba</p><p>tare da cewa, an baku gado zayi mata aiki gobe</p><p>ko jibi. Abba yace likita zan iya sanin wane ciwo</p><p>ne wannan? Likita yace tsirone dake fitoma mata</p><p>dai daiku. Sam abba bai fahimta ba don haka yayi</p><p>mashi sallama. Umma ce a wurin ummi tana</p><p>shan magani kafin ranar aiki inda abba</p><p>hankalinshi ya rabu biyu rabi gurin aiki rabi garin</p><p>ummi. Don ma umma ta koreshi da so yayi ya</p><p>rika kwana, addu'a kam yana yinta. Ranar da</p><p>za'ayi aiki abba hankalinshi duk tashe. Yana</p><p>zaune bakin gadon da take kwance ita kuma tana</p><p>can ana aikin. Wayar umma ce a hannunshi yana</p><p>ta danne danne, ba don nishadi ba don kawai ya</p><p>rasa me zaiyi. Dript ya shiga yana ta bin abinda</p><p>ke ciki, mamaki ya cikashi lokacin da yaga irin</p><p>text din da ummi tasha rubuta mashi don ta tura</p><p>ma abba, sai kuma ta fasa. Tamkar cikin mafarki</p><p>abba ya rika karanta sakwanin dama ummi tana</p><p>sonshi ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com ne tayi? Ya sake bude wani</p><p>rubutu cewa, Ya Abba ina sonka, ina kaunarka</p><p>duk wani motsi na numfashina kara sonka nake,</p><p>ka tausaya mun sonka zai zama ajalina, duk</p><p>ciwon da nakeyi na sonka ne. Ko na rantse ba</p><p>zanyi kaffara ba, in kaji haushin kalamaina ka</p><p>yafeni, nasan ni ba ajinka bace, amman ka daure</p><p>kace kana sona koda bada gaske bane. Gama</p><p>karanta sakon yayi dai dai da dawowa da ummi</p><p>dakin, da sauri suka nufeta idonta biyu saidai</p><p>daga gani tasha azaba. Tayi wujiga wujiga. Abba</p><p>ya kama hannunta cikin matsanancin sonta da</p><p>tausayi. Sannu suka dinga yimata, nurse tabasu</p><p>magungunan da za'a rika bata, umma kuma ta</p><p>dauki wayarta don sanar da alhaji an gama aikin.</p><p>Abba yasa bakinshi dai dai kunnenta yace ina</p><p>sonki ummi, ina matukar sonki. Duk da tana cikin</p><p>wani hali taji kalaman nasa har a tafin kafarta.</p><p>Ta bude jajayen idonta ta dubeshi, ya sakale</p><p>hannunshi cikin tafin hannunta ya hade su. Ta</p><p>girgiza kai dai dai lokacin da nurse din ta sake</p><p>shigowa tace ga kayanta, ya amsa zaninta ne da</p><p>siket da sauransu. Tace ka barta tayi bacci kafin</p><p>ta tashi zafin gurin ya ragu, kila zuwa dare a</p><p>sallame ku. Umma tace to mungode. Nurse tace</p><p>yarinyarki nada dauriya, anyi mata allurar kashe</p><p>zafi bata kama jikinta ba amman bata yimuna ihu</p><p>ba. Likita ma ya yabata da kokarie ta, Abba ya</p><p>kalli ummi cikin tausayi. Sai gurin karfe ukku ta</p><p>farka wurin kam ya dan lafa da radadin, abba ne</p><p>yaje gida ya dafo masu abinci sannan ya nufi</p><p>wurin aikin shi. Don ranar bada wuri zashi ba.</p><p>Tunda ummi ta farka take ta kokarie tunowa shin</p><p>kalaman da taji cikin mafarki ne ko kuwa ido biyu</p><p>ne? Bakwai na dare likita ya shigo ya kara duba</p><p>ummi sannan yace suna iya tafia gida. Ya basu</p><p>maganin sha sannan yace ta rika shiga ruwan</p><p>zafi da dettol. Umma ta kira abba ta fada masu</p><p>batun sallama. Yace su jirashi yana zuwa. Ummi</p><p>tace da ummansu su alhaji pha? Tace sunxo kina</p><p>bacci harda ummanku sahura.els / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 28</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 28</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:30</p><p>Bansan lokacin dana dauka ina rigimniya da sonki</p><p>danqare a zuciyata.Ummi da ban sameki ba da</p><p>tuni bana garin Kano domin lokacin yanke</p><p>shawara nayi in nemi canjin aiki zuwa wata jihar</p><p>har yau ban daina yiwa Salisu addua ba wanda</p><p>shine mutum na farko da ya soma tsegunta min</p><p>kin zama mata gareni So, Ummi baya raina</p><p>abinda yake so da nayi zaton zubar da kima ne in</p><p>furta maki kalmar so musammam in na tuna ke</p><p>baki soma, zurfin a so bashida wani amfani don</p><p>na sha wahala.Ba zan Qara boye dimbin son da</p><p>nike maki ba Ummi ko gaban wa zan nuna kina</p><p>jina matsala? Ummi wadda ke zaton mafarki take</p><p>sai taji bakinta yana furta wayyo dadi Ya Allah</p><p>kada ka farkar dani in har bacci nike Abba yace</p><p>ciji yatsanki zakiji zafi Ummi nine Abban ki mai</p><p>sonki wanda ya reneki tun kina zanen gobe.</p><p>Hawaye suka soma zubo mata cikin muryar kuka</p><p>tace Ya Abba da gaske kana sona? Nafi zaton</p><p>tausayina yasa ka furta haka, Amma koba gaske</p><p>ba ne na gode kuma naji dadi Amma ka sani Ya</p><p>Abba ina sonka mai tsanani sai tasa kuka. Yace</p><p>ummi yi shiru, in kukan takaici ne kukan ya kare.</p><p>Nima na jima ina sonki jiya naga sakonki a wayar</p><p>umma da kike rubutawa mai dauke da nuna sonki</p><p>gareni. Sai ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com ya hanaki, don allah ummi</p><p>kada ki koma ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com a sona, ki zazzage min</p><p>duk irin sonki gareni. Ummi tace yau kam ji nake</p><p>kamar a mafarki. Sun nutsa a cikin hirar so suna</p><p>ta baiwa juna labarin halin da suke shiga a baya,</p><p>a lokacin daya ganta da wani namiji yace</p><p>hankalinsa yayi mugun tashi. Sai lokacin daya</p><p>fuskanci bashir na sonta, ita kuma Tace ta tsani</p><p>koh mace ta kira layin shi, zainab kuwa data</p><p>samu labarin ta kamar ta mutu. Tace ko bishira</p><p>bata kishi kamar yarda take kishin zainab, sunyi</p><p>nisa basu san sun kwana zance ba, sai da ummi</p><p>taji kiran sallah. Tace ya abba kaji abunda naji,</p><p>yace sallah ake kira naji, kin sani kwana zance.</p><p>Ban gaji dajin muryarki ba amarya tah. Ummi</p><p>tace gari yayi saurin wayewa kaje kayi muna</p><p>godia ga allah ta hanyar nafita, yace to matata.</p><p>Hamdala ta rikayi har bacci ya dauketa, muryar</p><p>umma taji tana cewa ummi ki tashi kiyi wanka ki</p><p>gasa jikinki. Tana zaune cikin baho wanda umma</p><p>ta zuba ruwan dimi da dettol, tsohuwa ta shigo</p><p>cikin bandakin. Ummi tace don allah tsohuwa fita,</p><p>tace don allah ja can anki a fita din, ta saka</p><p>hannu cikin ruwan wankan ummi dake gefe a</p><p>bokiti. Tace ina suwaiba? Ai karo mata ruwan</p><p>zafi, wannan ruwa yaushe zata gasa jikinta, idan</p><p>da dan tawul dauko in danna mata jikin. Ummi</p><p>tace nidai tsohuwa ki barshi don allah, sai kace</p><p>wata mai jego? Tsohuwa tace tafi can kuda baku</p><p>san darajar jikinku ba. Wannan rawar kan da mai</p><p>sunan malam keyi idan ba'a gyara kiba saiki ba</p><p>sai zance ya dawo baya, idan anyi magana ku</p><p>yan zamani kuce bamu waye ba. Alhali ku</p><p>wayewarku itace kwalliya amman jiki ba'a san a</p><p>gyara ba, umma tazo ta kara mata ruwan zafi a</p><p>cikin bokiti. Tsohuwa tace yau a sawo bagaruwa</p><p>a tafasa ruwan shigar tata da ita don tayi saurin</p><p>warkewa. Kuma ko ina zai hade, in kin koma</p><p>gidanki kin kwana biyu ki dinga hada bagaruwa</p><p>da alim kina tafasa su kina shiga.IKI novels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 29</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 29</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:31</p><p>Umma Tace xa'asiyo tafita tabar su ummi</p><p>nacewa to tsohowa kije mana tace bantafiya sai</p><p>naga yanda xakiyi ganin ummi tabata lokaci nan</p><p>tsohuwa ta dauki tawul din tashiga nadar ruwa</p><p>tana dannama Ummi, Ummi tanacewa itadai</p><p>abata tayi da kanta. Tsohuwa tace gaddamace</p><p>daku ya'yan yau kinga duk macce dake rufe</p><p>jikinta tafita daban damasu tallar jiki. Ita macce</p><p>anfison a sameta ko yaushe da dumi a jikinta,</p><p>yawo babu takalmi ko a tsakargidane yana</p><p>ragewa mace dumi sbd sanyinda ke ratsa tafin</p><p>kafarta har ni'ima yana ragemata. Sannan zama</p><p>atantagaryar suminti shima yana rage mace, da a</p><p>ace zaku gane kunga masu saka hijabinnan da</p><p>safa? bakaramin wayo suke yimukuba. Inda za'a</p><p>banbance za a samu sunfiku ni'ima da kyau fata,</p><p>don haka sai kin dage Ummi dai tayi shiru, amma</p><p>aranta cewa take wannan tsohowa ko ina tasan</p><p>wannan duk bayanin? Filo aka ajewa Ummi ta</p><p>zauna tana karin kumallo, duk takosa taga</p><p>abbanta, koda ta tsinkayi sallamarsa tamkar</p><p>tamike ta taroshi. Amma dole yaje yagaida su</p><p>alhaji, tsohuwa tace aefa mu kuma bana munga</p><p>takanmu don nan zaka dinga likemana. Yace</p><p>dadin abundai nima nan gidan ubanane, da</p><p>uwata. Umma tana kicin tanamasu dariya. Tunda</p><p>ya zama idanunsu sunsarke da juna sun kasa ko</p><p>magana Ummi ce tayi karfin halin lumshe ido</p><p>sannan tabude tace sannu daxuwa. Tasowa yayi</p><p>ya tsugunna kusa da 'its, yajikin babyna?sunan</p><p>yamata dadi, naji sauki bari in kawomaka abun</p><p>karinka. yamika mata tafin hannunsa tasaka nata</p><p>yahadasu ya yasarke, murya kasa kasa yace</p><p>barshi na' amso. Ta kula abba mutum ne maison</p><p>wasa da tafin hannu. Ita kanta tanason hakan da</p><p>akwai wani sako da tafin hannu ke isarwa acikin</p><p>duniyar ma'abota so, kila wannan dalilin ne yasa</p><p>abba ke kashema tafin hannusa kudi da mayukan</p><p>da ke saka laushin hannu har ita mah ya</p><p>saimata. Koda umma ta shigo Ummi tayi kokarie</p><p>amshe hannunta amman abba yaki saki, kuma a</p><p>hakan ya karya. Umma kasa zaman dakin tayi</p><p>domin a baki abba yake ba Ummi abinci, umma</p><p>nafita taceels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 30</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 30</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:33</p><p>Daren ranar duk suna kan kujera doguwa a dakin</p><p>umma ya bude mata laptop wai yana koya mata</p><p>kanta kwance a cinyarsa, umma ta shigo dakin</p><p>tsohuwa tace tsohuwa zaifi kyau mu sallami</p><p>yaran nan na gaji da ganin wannan aiki nasu ai</p><p>tasamu sauki. Tsohuwa tace suwaiba ina laifin ta</p><p>kwan goma ma, umma tace anya zasu kwan</p><p>goma nan? Gobe bakwai guda ta koma dakin ta,</p><p>tsohuwa tace shine nan. Abba yace Ummi kinfa</p><p>samu sauki ba zakizo mu koma gidan mu ba?</p><p>Tace su umma ne zasu maidani ai nima ya abba</p><p>inason in koma yace yau nan zan kwana in sunga</p><p>haka sun kuramu, Ummi tace ya abba kayi hnkr</p><p>kada ka kwana, shine yace kin yarda goma inxo</p><p>mutafi ko ba sanin su umma? Tasa dariya tace</p><p>taf inajin kunya bazan iya binka ba yace to kuwa</p><p>zan kwana a nan. Suna cikin haka umma ta leko</p><p>tace abba bazakaje gida ba yanxo fa sha biyu</p><p>saura, yace umma nima nan zan kwana. Ta rike</p><p>haba nan din lafia? Yace to umma nima ba gidan</p><p>mu bane? Ummi tace dama yafi umma kada yaje</p><p>wani abu ya rudashi, umma tace a'a abba tashi</p><p>ka tafi insha allah gobe Ummi zata koma yayi</p><p>murmushi tare da cewa nagode umma.nan dai ya</p><p>tattara yanashi yanashi ya tafi gida cike da</p><p>kewar matarshi, itama Ummi lamo tayi a gado.</p><p>Bayan umma ta gama yimata fada ta bari ta</p><p>warke taki ko, sai cewa tayi umma ni fa na</p><p>warke. Umma ta kalli Ummi cike da mamaki tace</p><p>yaran yazo saidai a barsu. Shiyasa akace idan</p><p>macce ta isa aure ayi mata a huta. Ita kam Ummi</p><p>tana ganin a barta tabi mijinta ta faranta mashi</p><p>shine abinda yafi dacewa don yanxu ba inda ya</p><p>kai mata dakinta dadi bacci. Duk da kashedin da</p><p>tsohuwa tasa abba dakinta tayi mashi na cewa</p><p>ya bar Ummi sai ta kara sati kafin yace zai</p><p>kulata da sunan auratayya, bai sa abba jin zai iya</p><p>ba. Don haka koda ta fada mashi cewa yayi kadai</p><p>da huruminki da wanda ba naki ba duk sai kin</p><p>shiga? To nidai ki lafa man haka. Ya fice a dakin.</p><p>Ita kuma tana ta fadanta tana cewa "Na shiga din</p><p>dan neman yaro, da kyar ya barta ta kara kwana</p><p>biyu ya afka mata don shi hkr sa ya kare, ta</p><p>nuna mashi ita fa tsoro take ji kada ta wahala, ya</p><p>lallasheta yace ba wani wahala. Ummi tana son</p><p>faranta ran mijinta. Don haka ta jure duk da</p><p>yarda yazo mata ba sauki, sai dai tasha albarka</p><p>kuma ta kara samun wani matsayi na</p><p>musammam a gunsa. Cikin satin ta zama yar</p><p>lelenshin kafin sati biyu ta hardace duk wani</p><p>darasi da abba yake koya mata, abba jinsa yake</p><p>kamar wannan lokacin ne ya fara rayuwar</p><p>angoncinsa. Sam ya manta yana da wata mata</p><p>uwa duniya saida Aunty ta kirashi tace lafia baya</p><p>kiran matarsa sai ga abba da girman shi ya girba</p><p>karya. Wai ya kira ya kasa samunsu Aunty ta</p><p>yanda tunda farkon tafiyarsu yana kiransu sun</p><p>gaisa da bishira tana tmbyrshi ina hibbarta? Sai</p><p>lokacin ya tuna kwana biyu bai ganta don tana</p><p>gidansu umman bashir, amman sai yace tana</p><p>lafia in yaje zai kirata taji gwarancin yar tata.</p><p>La'asar sur suka jero ita da abba don su dan</p><p>zaga kurum. Sun shigo gidan ahmad da muktar</p><p>duk basu rabu ba saida sukaji sun saba da ummi.</p><p>Don ita haka take yana da wuya kayi zaman awa</p><p>guda da ita bakaji ta kwanta maka a rai ba. Abba</p><p>yaji dadi yarda Ummi ta nuna kauna ga matan</p><p>abokanin nasa, yasan bada jimawa ba matansu</p><p>zasu zama kawaye kamar yarda yaso da bishira</p><p>amman taki. Daga can suka nufi layin su gidan</p><p>su umman bashir Ummi tace su fara shiga su</p><p>dauki muhibba abba yace bazata yarda dake ba.</p><p>Ummi tace zata yarda muje a ran abba tsoro</p><p>yake gada umman bashir ta gwasaleta Ummi, sun</p><p>sameta tana shara da sauri Ummi ta amsa ta</p><p>soma sharewa hakan ya faranta ran abba sai dai</p><p>da ya kalli umman bashir yaga tana hararar</p><p>Ummi, saida ta gama taxo ta zauna suka gaisa</p><p>abba na rike da hibba tayi kaca kaca da kunu</p><p>gashi duk ya dunkule dama ko lokacin da bishira</p><p>tana nan haka zakaga yar duk kazanta. Ummi ta</p><p>bude post dinta ta cire dari biyu guda biyu ta</p><p>mikawa umman bashir gashi umma kin sai goro</p><p>saida ta tabe baki ta amsa babu ko godia, sai dai</p><p>abba cikin jin dadi yace angode, da hibba taki</p><p>binsu Ummi tace kamal xo ka siyo wa hibba</p><p>alawa, kinga baba kamal baya nan xo muje in</p><p>sayo maki. Cikin sa'a sai taxo zasu fita sai ga</p><p>bashir dauke kai yayi tare da jan tsaki daya shiga</p><p>gidan sai ya hau umma da fada Wai ta daina</p><p>barin Ummi da wannan abba suna zuwa in ba</p><p>haka ba zasu kawo mata wani asiri. Umman</p><p>bashir tace suta zuwa ma indan ta nine mi jiya</p><p>tayi bare yau, ka gansu dari hudu yanxu ta bani</p><p>don haka bazan hana zuwa ba amma fa ina nan</p><p>yarda nake bazan canza ba, suna shiga gidan su</p><p>umma kicin ta wuce ruwan zafi ta zubu ta cude</p><p>muhibba tas, ta wanke mata kai ta chajeshi ta</p><p>shafeta da mai nan ma basu jima ba suka nufi</p><p>gida zanen umma ta ansa ta goye muhibba, shine</p><p>ya bude dakin bishira duk kayan yarinyar sun rine</p><p>da datti, Ummi dai ta zazzaba yace .ba maidata</p><p>za'ayi ba, Ummi tace ta dan kwana biyu mana.</p><p>Yace tana fitsari fa. Ummi tace kasawo muna</p><p>pampers Yace shikenan duk da ya nuna bayaso</p><p>yarinyar ta zauna gurinsu amman yaji dadi sai</p><p>lokacin bacci daya shigo ya shigo da pampers din</p><p>ta saka mata Sannan ta kwantar da ita can gefe</p><p>ta azama mata pillo guda haba guda baya, su</p><p>kuma suka kwanta a nasu makwancin suka</p><p>cigaba da soyewa. novels / ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 31</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 31</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:36</p><p>Ummi tana son yara don haka hibba ta dinga</p><p>samun gata, satinta guda umman bashir ta dinga</p><p>jaraba sai an dawo da ita. Wai kwadayi ne don in</p><p>bishira tadawo ta bata tsaraba, amma koda ta</p><p>tafi da hibban yarinyar sai taqi sai kuka har dasu</p><p>amai. Dole aka dawo da ita, don alhaji karami</p><p>cewa yayi atattara mata kayanta duka inyasake</p><p>samun an maido da ita sai ya saba ma umman</p><p>bashir. Hakan da babbar sallah abba yakashe</p><p>musu kudi ita da hibba, sai dai duk abinda yasai</p><p>ma ummi to ya aje ma bishira nata. Ita kam tana</p><p>can duk addu'arta akan ummi ne, kafin ta dawo</p><p>ummi tafita, don haka data dawo da kwarin</p><p>gwuiwarta ce wa bazata samu ummi agidan ba.</p><p>La'asar sakaliya, direban gidansu ya iso da ita</p><p>gidan kamar yanda mahaifinsu ya umarce shi</p><p>cewa in ya dauko su kada yaso dasunan, ya dire</p><p>kowa agidanta. Kasancewar unguwa uku suka</p><p>soma zuwa sai anty ta taya bishira diban kaya</p><p>su shiga. Daidai kofar dakin bishiran abba na</p><p>kwance rigingine, 'yar T-shirt ajikinshi fara kar.</p><p>Dawandon jeans gajere iyaka gwuiwa. Ummi</p><p>kuma dogon wando ne irin mai kama jikin nan</p><p>dariga mai kamar singileti kanta yasha kana nan</p><p>kitso, tayi filo da kirjinshi yana bata labarin wata</p><p>mota da yake son yabada tashi yayi ciko. Ita</p><p>kuma tana ce masa ya dai je ya shawarci umma,</p><p>muhibba kuwa tana ta faman wasa da sabbin</p><p>kayan wasanta da ummi tasai mata. Ita ma cikin</p><p>'yar shimi mai kyau, kanta kuwa ummi tayi mata</p><p>kitson (3 in 1). Sororo bishira ta tsaya tana</p><p>kallonsu, sam bata tsammaci a irin addu'ar</p><p>datayi zata dawo ta samu ummi agidan ba. Basu</p><p>ganta ba saida anty tayi sallama tare da cewa, ya</p><p>naga kin tsaya? da sauri suka waiwayo duk suka</p><p>mike. Gaban ummi yayi wata muguwar faduwa,</p><p>amma duk dahaka cikin fara'a ta nufe su, bishira</p><p>ta hade rai matuqa sannan taqi ko kallon ummi</p><p>ta nufi 'yarta. Anty kam cikin fara'a suka gaisa da</p><p>ummi harta zage jakarta dake kafadarta tabawa</p><p>ummi wani dan agogo mai kyau. Nan dai ummi</p><p>tayi ta godiya shima abba ya mata godiya. Abban</p><p>ne ya shigar mata da kayan daki, ummi tana</p><p>cewa anty kin mana dawowar bazata, dakin fada</p><p>da an share miki dakin. Nan ma bata tanka ba,</p><p>ummi dai data gaji dayi mata sannu bata amsa</p><p>ba sai kurum ta nufi dakinta, zuciyarta babu dadi,</p><p>tasan yanzun ya Abba zai raba jin da yake da ita</p><p>zuwa su biyu. Bishira tayi kyam tana ta qamshi</p><p>don anty baza su barta tazauna masu da qazanta</p><p>ba, ga haqorin makka an sako ana ta qwambo.</p><p>Ranar dakinta Abba yakwana, yanda bata ga</p><p>wata rawar jiki daga gare shi ba tayi zargin ummi</p><p>tasamu lafiya. Hakan ya qara dagula mata lissafi,</p><p>tayi rabon tsarabarta daga kawayenta sai</p><p>maqota, don ko umman bashir daga zam-zam</p><p>bata qara mata komai ba. Dama tana cike da</p><p>haushin umman data bari ummi ta daukar mata</p><p>'ya gashi nan muhibba ta liqe ma ummi. Hakan</p><p>ya shaqar da umman bashir har tace amaida</p><p>mata zam-zam dinta ita bata sha. Wato don taje</p><p>makka shine zato zo ta canza hali? Ita kuma</p><p>bishira ta amsa tare da cewa, ai ba ita ta aike ni</p><p>makkan bada har sai tazabi abinda zan bata.</p><p>Ummi ko zam zam din ba abata ba, kuma ko</p><p>ajikinta. Abba kam shita kawo masa dogayen</p><p>riguna da T-shirt masu kyau, amma su anty ne</p><p>suka matsa mata sai ta saya. Ranar daya dawo</p><p>daga dakin bishira ummi tana fashin sallah gashi</p><p>yanuna yana dalarura alokacin. Sai tace ta yafe</p><p>masa yau dagobe yaje gurin anty bishira, yace</p><p>A'a tace ba haramun bane nina amince, yace</p><p>nasani. Shiba yason sai yatafi tafara damuwa ko</p><p>tazo tana jin haushinsa, tace ba komai saida</p><p>yatafin kuwa har kuka tayi don kishi. Amma</p><p>tabawa zuciyarta hakuri tasan wata rana wannan</p><p>jarumtar datayi zata zame mata alkhairi. Ita ko</p><p>bishira koda yazo mata sam bata damu ta</p><p>bincika ba, tunda taga ba girkinta ba, saima ta</p><p>hau murna yayo satar kwana ya bata musamman</p><p>dataga dayayi wanka yakoma dakin ummi, haka</p><p>washegari. Don haka sai tashiga daga hanci har</p><p>da 'yan habaice habaice, kafin tadawo tun da</p><p>dama da namiji dan uwansa yake kwana. Tana</p><p>nufin ummi bata ba tayi masa amfanin komai</p><p>wannan yasa ummi ta daura aniyar cusa mata</p><p>takaici, aranta tace tunda cinikinki labe nikuma</p><p>zansa miki hawan jini. Kamal yazo daukar abincin</p><p>da ummi ta saba sawa yau har da kunun gyada</p><p>tayi. Bishira ta kalle shi, wai kai wannan abincin</p><p>na waye kullum kake zuwa dauka? Yace na</p><p>ummarmu ne. Ta taba baki, ummar nan taku</p><p>kwadayinta yayi yawa, ko kuwa itama asirin ya</p><p>kamata ne? Kamal kuwa yaje yafada sai ga</p><p>umman bashir agidan suna zage zage da bishira,</p><p>tana ce ma bishira dadin abin gidan dana nazo</p><p>kwadayin ba gidan ubanki ba. Marowaciyar bnza</p><p>ai dama ina da cikinki, lokacin da Abba yasai</p><p>maku TV, yace ki bani naki sai ki kace gara kiyar.</p><p>Bishira tace, Eh na hana TV aiba wani shegen ya</p><p>sai minba, ubana yasai min, kuma nace mai</p><p>kwadayin yarinyar daki kace uwarta mai asiri,</p><p>menene na amsar abincinta kici banda kwadayi?</p><p>Shiyasa kika bata 'yata ashe don asami abinci</p><p>ne, umman tasa kuka ni ke ke zagi? Yau ko abba</p><p>zai zo gidan nan zai zaba ko ni ko ke. Ummi dai</p><p>tana daki tana jinsu. (aranta tace dadi na da</p><p>gobe saurin zuwa). Bishira tace dama ya darajaki</p><p>ne shine za kice haka, yazo din nace mai kwadayi</p><p>harda rainawa na baki zam zam butulu duk</p><p>abinda na miki kin manta kece kika aikeni</p><p>makkan? Umman tace, zuwa makkan naki dashi</p><p>gara babu, don nasan da kyar ne in za akarbi</p><p>wannan aikin nani ke da bakya sallah arniyar</p><p>banza qazama. Ummi harda riqe ciki don dariya,</p><p>haka dai suka yi tayi wajuna gori har dai 'yan</p><p>kallon da suka taru suka soma bda haquri,</p><p>umman bashir tayi gida cikin kuka. Tagayawa</p><p>'ya'yanta komai su bashir dasunce sai sunje sun</p><p>zaneta umman bashir din tace barta ku barta</p><p>kawai bari abban yadawo. Da dare ta ritsa shi</p><p>agidan yasha mamakin wai yau mahaifiyarshi da</p><p>bishira ne suke fada yace hakane dama duk</p><p>zamantakewar da ba'a kafata don Allha ba wata</p><p>rana sai ta rushe. Nan yayi tawa bishira fada da</p><p>cewa uwarshi sa'arta ce dazata tsaya ta dinga</p><p>gaya mata magana? Nan fa aka sake kacamewa</p><p>har abba. Yakai ga kwasa wa bishira mari,</p><p>sakamakon irin rashin kunyar data rike qugu take</p><p>tsulawa umman bashir din. Ummi ganin abin yana</p><p>tsawo ta fita taja umman bashir tana bata haquri</p><p>ta zaci zata hantare ta amma sai taji tana cewa</p><p>ba komai ummi sakayya ce tunda na nuna ina</p><p>sonta dole tamin haka. Abba yace ummi tasa</p><p>mayafi taraka umma gida, hakan ya qara qona</p><p>ran bishira gashi yanda taga Abba ya bata rai zai</p><p>iya yin komai, dole ta koma daki tana cizon yatsa</p><p>tare da tunanin mafita. Ummi kuwa ahanya sai</p><p>lallashin umman take tare dayi mata alqawarin</p><p>cewa duk abinda take so ta tambayeta zata mata</p><p>shi tarakata har gida sannan tadawo. Sabon kuka</p><p>umman bashir tazauna tanayi, takaicinta yanda</p><p>bishira ta zage ta taci mata mutunci agaban</p><p>ummi, tashare ido tare dayin ajiyar zuciya a fili</p><p>tace dani take magana. Ynzun ummi tasan kishi</p><p>fiye da baya, don ta hau turbar ma'aurata kuma</p><p>tasan muhimmancin abinda ake yiwa kishi, don</p><p>haka zatayi komai na jan hankali don ganin taja</p><p>mijinta gareta. Kuma inta lura cewa bishira ta</p><p>maqale mata aqofar daki sai tayi ta jan abba da</p><p>wasanni, don ta quntata ma me labe. Amma</p><p>hakan baisa ta daina ba, don haka ta daura</p><p>aniyai saita mata abinda zata tona kanta ha abba</p><p>yasani. Duk jumma'a abba yana dawowa gida</p><p>musamman in ranar girkin ummi ne don cin</p><p>abinci na musamman. Jumma'a biyu kenan bata</p><p>fado kanta ba sai wannan, don haka tun alhamis</p><p>taje ta yarfo kitsonta, ta biyo ta gidan su gurin</p><p>tsohuwa tazo. Don haka suna gaisawa da umma</p><p>tace gurin tsohuwa nazo. Suka shige daki tace da</p><p>tsohuwa nazo ne indan samu dan wani sirrin.</p><p>Tsohuwa tace, name ummi? Ta ce na gyaran jiki</p><p>mana. Fati tace min kwanaki kin fada mata wasu</p><p>abubuwa. Tsohuwa ta ce, ja'ira, kinga uwar bari?</p><p>Dama nace zaki same ni ina kyakkyawan zamana,</p><p>bada ina fada miki kina sharewa ba? Ummi tace</p><p>haba tsohuwa banaso aji mu yanzun dai ki bani</p><p>shawara sannan ki fada min abinda zanyi inja</p><p>hankalin mijina. Ta ce, toda farko ki dinga kula da</p><p>jikinki ta hanyar rufe shi ruf, kada kibar kofar</p><p>iska. Banda tafiya ba takalmi, iska tana shiga</p><p>tanan kuma mace narage ni'ima banda zama ba</p><p>dankwali inso samu ne hatta tsarki ki daina yi da</p><p>ruwan sanyi, ki dinga yida ruwan dumi. Sannan ki</p><p>amshi bagaruwa gurin ummarki ki dinga shiga</p><p>inkin tafasa da alif dakuma saiwar mata, sannan</p><p>inkinyi al'ada kin gama kinyi wanka toki dinga</p><p>matsa farin miski a ehem dinki. Sannan ki samu</p><p>saiwar kankana, saiwar zogale, kanunfari,</p><p>mazarkwaila dazuma amma kisa kanunfari</p><p>dayawa sai ki dafa su su dafu kullum kisha kofi</p><p>biyu safe da yamma. Sannan ki aya garinta,</p><p>kwakwa ma kiyi garinta, dabino ma kiyi garinsa,</p><p>sai ki dinga diban cokali bibbiyu ki zuba amadarar</p><p>ruwa sannan ki zuba zumarki mai kyau kisha, sai</p><p>ki samu kuma gwanda, kankana, abarba, zogale,</p><p>citta, lemun tsami, ki markada su kisha. In anan</p><p>maki katsaya yarinya zakiji ki kin cika cindum</p><p>daruwan ni'ima sai kin samu martaba ta</p><p>musamman agurin miji dan zaijiki kin fita daban</p><p>da dukkan sauran mata. Ki hada da biyayya</p><p>tsafta da kuma iya tsara girki mai dadi. Ummi</p><p>tace, toni yanzun yaya zanyi nasamu saiwoyin</p><p>nan? Tace, bari zanba matar ado dake yawan</p><p>zuwa kasuwar qauye zata zo miki dasu. Amma</p><p>su gwanda gasu nan bakin titi ko shi sai kice ya</p><p>siyo miki, zogale kuwa baki rasa shi gurin</p><p>ummarki, har da cittar da alif din da bagaruwan.</p><p>Ta ce to, ta tafi gurin umma ta amsa har taje</p><p>gida bata daina mamakin tsohuwa ba, ya akayi</p><p>tasan duk wadannan hadin matan? Amma data</p><p>tuna cewa 'yar katsina ce sai tace ba mamaki.</p><p>Tun ranar alhamis din ta soma aiwatar da</p><p>darussan da ta debo daga tsohuwa, safiyar</p><p>jumma'a ranar zai bar dakin bishira. Ya fito tana</p><p>sharar tsakar gida ta gaidashi, ya amsa da fara'a,</p><p>tare dawani kallo mai fassarar in ba keba. Cikin</p><p>muryar data adana don shi kadai tace, ya abba</p><p>ina son in je ayi min zanen fulawa. Yace jiya kin</p><p>fita yau kam a'a. amma ki aika akira mai zanen</p><p>tazo ta miki. Ta marairaice, towa zan aika yaya</p><p>abba? Yace aike ni, ina ne gidan? Tace layin su</p><p>umma ne yace to za'azo ai miki. Bishira tafito</p><p>daga daki tazabga ma ummi harara, Tare dacewa</p><p>kisisina. Abba yakalleta, kema sai tayi miki. Tace</p><p>bana bukata, aikin banza, shikam yafice. Ummi</p><p>kuwa tace gaba da aikinta, ita ko sai tasa kujera</p><p>tazauna tana sakin zantuka, eh don kwalliyar</p><p>tabanzanta tunda ba a iya biyawa miji bukata.</p><p>Allah dai yasa ya fada min komai, to ni me zai</p><p>dame ni don 'yar aiki kawai na dauki yarinya.</p><p>Tashare min gida, tayi wa mijina abinci, daga nan</p><p>fa? Saita saki shewa, ummi ta ce aranta yau zan</p><p>bambance miki. Birabiskon shinkafa tayi da miya,</p><p>ta wadata birabiskon da kayan lambu, miyar ta</p><p>dauki nama da bushasshen kifi. Sannan ta hada</p><p>musu kunun aya yaji dabino da madara, ta</p><p>aikawa ummanta lokacin da kamal yazo daukar</p><p>na ummarsu. Tasheka wanka taci doguwar rigar</p><p>shadda koriya mai duhu, ta kafe dauri tamkar yau</p><p>ne daurin aurensu. Ga fulawar da yaje ya biya</p><p>akazo aka zana mata. Tanajin rigimar muhibba</p><p>tafito tazuba mata adan kwano tazaunar da ita</p><p>akofar falon mamanta.bishira tafito kicin baki</p><p>tasaki tana kallon ummi da tazo wucewa harda</p><p>bangazar ummi, nan ko kamshi ya bude ta na</p><p>turarukan da ummi ta fesa. Abba yana yin</p><p>sallama ummi tafito da sauri, oyoyo yayana,</p><p>bishira tana daga kicin dinta tana kallon su.</p><p>Ummi ta rungume shi, sannu dazuwa sahibina.</p><p>Ta amshi ledar hannunshi dajakar, yace yauwa</p><p>sannu babyna tace inazan kai ledar? Yace akwai</p><p>ta bishira aciki ki ciro. Ta mika mishi ledar ta</p><p>wuce dajakar dakinta. Ya mika wa bishira lemo</p><p>da abarba da yayo musu tsaraba sannan ya wuce</p><p>danasu, awulakance ta aje. Yana shiga ummi</p><p>tadan karo kofar yanda bishiran zata iya lekensu</p><p>sosai ta gefen kofan. Ta cire masa hula ta aje</p><p>akan madubi sannan ta kunna fanka. Ta shirya</p><p>masa abinci, yauni zan baka har ka qoshi. Haka</p><p>suka yita baiwa juna abaki har suka qoshi.</p><p>Yakamo hannunta mai qunshi yana ta sumbata,</p><p>wai kamar kada su goge. Kumatun shi ta shafa</p><p>nima yau kamin kyau, koda yake dama kai me</p><p>kyaune, ina sonka ya abba sosai. Cikin jin dadi</p><p>ya mannota a jikinshi, nima ina sonki, ina manta</p><p>kowa da komai in muna tare, tace ina tsoron kada</p><p>wata rana ka juya min baya. Ya saqalo</p><p>hunnuwansa cikin nata ina fata in mutu kafin</p><p>lokacin. Ummi tasomayi masa wasu irin darussa</p><p>wadanda tasan yana saurin tada sha'awarshi</p><p>nanda nan kuwa tasa shi fita hayyacinsa yakama</p><p>surutai. Ummi ta tabbata bishira tana wurin ta</p><p>labe, don haka tai murmushi ta bishi suka tafi</p><p>duniyar ma'aurata. Bishira tamkar tayi hauka sai</p><p>kawai ta fado dakin tana fadin, maciya amana,</p><p>har yanzun ba afita daga lokacin girkina ba</p><p>munafiki. Abba ya tashi sannan yaja riga yasaka,</p><p>ok dama kina labewa ne kiji sirrinmu? Da taga ya</p><p>sauko da zafin rai saita gudu dakinta. Yabita</p><p>yamata tatas, kuma ya fada mata cewa tazo ta</p><p>shiga dakin ta zauna ba labe ba, yanzun zai</p><p>komane yaci gaba daga inda ya tsaya. Tayi ta</p><p>kuka gashi ba damar zuwa gurin umman bashir</p><p>dole ta tafi gidansu. Shi kam abba shareta ya yi</p><p>kosu umma bai fadawa ba. Sabuwar soyayya ma</p><p>ya balle agidan, su ci abinci tare, wanka tare, su</p><p>fita yawonsu a qafa ko amota. In yana gurin aiki</p><p>bini- bini ya kira waya, ita kuma ko yaushe cikin</p><p>kirkirar girki da kwalliya tare da dadadan kalaman</p><p>dazata fada masa take. Duk lokacin datayi masa</p><p>zancen bishira sai ya ce, don Allah ta bar ta ta</p><p>huta, ummanshi kuwa 'yar bin qwaqqwafi sai da</p><p>tabi ta gano bishira bata nan. Don haka koda ya</p><p>shiga gaisheta sai tace kada ya yarda yaje yama</p><p>bata takardarta. Ita ko tana can uwarta tace ma</p><p>mahaifinta abba sakinta yayi, shi kuma yace to</p><p>sai tazauna tunda zaman gidan take so. Amma</p><p>su sani daga abinci sai ruwan gidanshi ya amince</p><p>tayi amfani dasu sai ko gurin kwana, amma bnda</p><p>wannan ko makilin dinshi ta taba bai yafe mata</p><p>ba, wannan hukunci yayi musu tsauri. Ko wata</p><p>bata rufa ba taji gidan ya isheta don hajiya zainu</p><p>taso maidata makaranta amma yace tagama</p><p>boko. Bishira na zaune ta zuba tagumi hajiya</p><p>zainu ta shigo dakiki tace tagumin menene kuma?</p><p>Tace, su sumayyah ne wai nace suyi ma muhibba</p><p>wanka sukace Allah yakiyaye. Wai tunda nazo</p><p>dakinsu ya lalace da kazanta, hajiya zainu tace</p><p>aiba karya suka yiba, don haka ma maida</p><p>yarinyar nan za ayi ke kuma ki koma gidan</p><p>antynku ko ki tafi abuja gidan aisha. Tace</p><p>baxanje gidan aisha ba, don itama bama shiri,</p><p>gara gidan antyn amma gsky ni abarmin 'yata</p><p>kuma fakinsan bai sakeni ba. Tace, inda ubanki</p><p>yasan ba saki bne da tuni bai kora kiba? Don</p><p>haka mubarshi haka amma batun 'ya nice zan</p><p>maidata. Ranar da ummi takira ummansu tafada</p><p>mata cewa bishirafa tuntuni tayi yaji amma Abba</p><p>yaqi zuwa, umma ta kira shi tace inya dawo gurin</p><p>aiki tana son ganinshi. To kafin yadawo ma saiga</p><p>hajiya zainu da direba tazo gidan su umma tadire</p><p>musu 'yar, sannan tashiga gidan umman bashir</p><p>tace, in kin haifi danki na halas ne ba shege ba to</p><p>kisa shi ya aiko wa 'yata saki. Umman tace zoko</p><p>kiga dan halas ne in yaso kuje ku nemi arne mara</p><p>sallah dan uwanta kazami kubashi. Nan fa zage-</p><p>zage ya tashi har su umma dasauran makota</p><p>suka shigo. Dakyar aka tura hajiya ta tafi, tace</p><p>kuma saita kira 'yan sanda anzo antafi da umman</p><p>bashir. Alhji qarami ma cewa yayi maza abba</p><p>Abba yarubuta takarda ya aika ma bishira.ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 32</p><p>ZURFIN CIKI www.gidannovels.blogspot.com book 4 part 32</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:37</p><p>Shiko alhji babba da umma suka ce a'a abari</p><p>qura ta lafa sannan aje. Koda aka kwana 2 abba</p><p>kin bin alhaji yayi sai wani abokinshi alhaji</p><p>yasamu suka tafi tare. Mahaifin bishira yaji</p><p>mamaki cewa ba sakinta abba yayi ba. Kuma bai</p><p>san sun maida 'ya ba, tadai ce mishi kunzo kun</p><p>amshi 'yarku, to yanzun tunda haka ne kunga</p><p>kenan bishira da uwarta basa son takoma gidan</p><p>mijinta ko? Su alhaji suka ce eh, yace to ku sa</p><p>shi ya rubuto takardarta ku kawo min, su alhaji</p><p>sukace ba za'ayi haka ba. Yace, to kuje ku barta</p><p>zata gane gidan ubanta bananne yadace tazauna</p><p>ba. Sukai godiya suka tafi. Harta koma gidan</p><p>anty farida mahaifinsu yace tadawo nan gidanshi</p><p>badashi take takama ba? Wato ta kashe auranta</p><p>zata je ta kashe na yarta dole ta dawo, tsohuwar</p><p>dake musu aiki yace ta koma gida tahuta amma</p><p>duk wata tazo ta amshi albashinta. Sannan yace</p><p>bishira itace zata dinga wannan aikin duka ita</p><p>kadai, lamarin yayi wa bishira tsauri da yawa,</p><p>gashi ba fita duk ta rame ta lalace ga tunanin</p><p>'yarta. Muhibba kuwa tana gurin umma, ummi</p><p>ma takan daukota sannan ummi tasamu nasarar</p><p>rufe bakin umman bashir, ta hanyar yi mata</p><p>kyautuka ko me sukace sai ta aika mata. Tasa</p><p>Abba ya canja mata gado don nata ya lallace,</p><p>sannan da fati ta haihu tasa Abba ya sai mata</p><p>garar abinci, ita kuma tasa zani da rigunan yara.</p><p>Nan fa sai ga sahura babu ko kunya tana shima</p><p>ummi albarka, ko bashir ne yakawo gulmarsu</p><p>ummi sai tace ai ita bata yo halin uwarta ba.</p><p>Tafi-tafi ma in ya kawo sai tace ai su umma da</p><p>ummi sun gane kuransu. Haba sahura kodai ki</p><p>gane kuranki? Abba yasoma damun ummi da</p><p>batun ciki, wai shifa yana tsoro kada su gaji su</p><p>umma, ummi tace su dai yi addu'a sunje asibiti</p><p>ba wata matsala, likita yace in rabonsu yazo zasu</p><p>haihu. Da kyar ummi ta shawo kan Abba ya</p><p>amince ta zana (JAMB) don ci gaba da karatu,</p><p>sannan ta shiga islamiya. Abba yayi kyau yayi</p><p>kiba ya kara gogewa, haka nan ummi duk wanda</p><p>yaganta saita birge shi, daka ganta kaga wayayya</p><p>wadda mijinta yasan da ita. Taci nasarar samun</p><p>(POLY) saboda bata samu abinda take so don</p><p>zuwa (UNIVERSITY) ba, sai dai ba tasha dokoki</p><p>kafin ta fara zuwa. Bayason kawaye baya son</p><p>abokai, irin wanda wasu matan keyi sannan</p><p>yadinka mata manyan hijabai, kuma banda hawa</p><p>acaba, inya samu sarari zai dinga zuwa da kansa</p><p>yana daukarta. Sai kuma gargadi na karshe kuma</p><p>da babbar murya, in har ya daina samun kular</p><p>datake bashi ta kowane fanni wai saboda karatu,</p><p>to kuwa za adaina karatun gaba daya. Tace,</p><p>insha Allah sai abinda yai gaba. Ya canja mota,</p><p>umma tayi ta fada wai tafi son yasai fili yayi dan</p><p>gidanshi irin na zamani yace za'azo gurin</p><p>ahankali kada ki damu umma. Bishira ta sulale ta</p><p>tafi na'ibawa gidan anty da kukanta wiwi don</p><p>Allah ta taimaka mata taba Abba hakuri ya maida</p><p>ta, wlh tagane kuskurenta. Anty tace, nifa bazan</p><p>iya kiran Abba ba don kin riga kin bmu kunya, sai</p><p>dai in ke ce zaki kira shi ga waya can. Ta dauko</p><p>ta kira, shikuma ganin kiran anty sai yayi parking</p><p>yadauko ummi daga makaranta, ya daga sai yaji</p><p>muryar bishira. Cikin kuka tana cewa, don Allah</p><p>abba nice, kayi hakuri indawo dakina, wallh zan</p><p>canza, yace ok baki riga kin canza din ba, to bari</p><p>inkin canza din sai muyi magana. Yakashe haka</p><p>tayi ta kuka tagama anty tabata wasu kayan</p><p>sawanta sannan ta tafi. In lokacin labarai yayi</p><p>haka take zuwa ta tasa TV tayi ta kallonshi tana</p><p>kuka, kullum kara sonshi take gashi yayi kyau</p><p>idanunshi sun qara haske. Wata ranar jumma'a</p><p>wuraran karfe sha daya ta saci jiki tanufi gurin</p><p>aikin Abba, yana fitowa dakin daukar labarai</p><p>akace wata tana nemanshi. Baiji wani mamaki ba</p><p>don mata kanzo neman shi wasu suce suna</p><p>sonshi wasu suce ganinshi kurum zasuyi don</p><p>yana birge su. Yana zuwa sai yaga bishira, nan</p><p>take ya daure fuska tamkar bai taba dariya ba,</p><p>duk da cewa acan kasan zuciyarshi yatausaya</p><p>mata. Ta tsugunna gwuiwa 2 tana rokonsa, yace</p><p>ke tashi kada ki janyo min mutane, jeki zanzo.</p><p>Koda ta tafi cikin murna shi ko harkokinsa</p><p>yakama. Shiru-shiru tana saka rai bashi ba</p><p>alamarsa. Nan kuma tashiga daukar waya</p><p>kannanta tana kiranshi, harma yadaina dagawa.</p><p>Wataran taje tasamu ahmad tana kuka, ahmad</p><p>yace taje zai ganshi. Rannan kuwa har gida</p><p>ahmad yiyi sallama da abba yashiga rokon Abba</p><p>ya maidota. Abba yace taje taroqi mahaifiyarsa</p><p>dasu umma insun yarda shikenan. Har gida</p><p>ahmad yaje ya fada mata, bata yi sanyi ba tanufi</p><p>gurin umman bashir. Umman tana zaune da</p><p>'ya'yanta suna shan farfesun kifin da ummi ta</p><p>aiko musu dashi, tana ganin bishira ta hade rai.</p><p>Tace, lapiya? Bishira tace lpy lau umma zuwa</p><p>nayi in roqi gafararki. Tace nime kika min? Tace</p><p>don Allah dai ki yafe ni, ina son indawo dakina</p><p>Abba yace sai kin hakura, tace oho, yanzun kin</p><p>yarda ina da kima agurinsa? To bari kiji bazaki</p><p>dawo ba, mai baqar rowa kince nimai kwadayi ke</p><p>kuma mai rowa ko? To kin gani wannan ummi ce</p><p>ta dafo mana ta nuna mata kular kifi, sanda</p><p>kinanan bana cin komai bansan dana yana samu</p><p>ko baya samu ba. Yanzun abin arziki iri-iri</p><p>kidawo ki toshemana kofar samu? Tace, wlh</p><p>bazan toshe ba, umman bashir tace dukda haka</p><p>dai bazaki dawo ba. Tayi takuka sannan tafita,</p><p>har zata wuce gidan su ummanshi sai ta tuna</p><p>kada suyi mata dariya sai tace baridai ta shiga.</p><p>Kyakkyawar karba umma tayi mata suka gaisa,</p><p>tazauna umma ta kawo mata ruwa ta amsa</p><p>tasha. Muhibba tana ta tsalle tsallenta kan kujera</p><p>zuwa jikin umma, umma tace ji hibba ki gaida</p><p>mamanki, ga mamakin bishira sai yarinyar ta</p><p>kalleta tace. Umma niba wannan bace ba</p><p>momina, momina sun tafi da babana zaya kaita</p><p>makaranta. Umma tace, wannan ma ummarki ce</p><p>yarinyar taruga dakin tsohuwa tana cewa, ita ba</p><p>ummarta bace. Bishira ta bita dakallo, yarinyar</p><p>tayi bulbul gata cikin shiga mai kyau da tsafta</p><p>kanta yaji kitso da 'yan duwatsu. Saita soma</p><p>kuka tana fadin mahaifiyata ta cuce ni, umma</p><p>tace a'a kece kika cuci kanki, inbaki dauki</p><p>damuwarki kin kai mata ba yaushe zatasan anyi?</p><p>To ynzun dai dubi 'yarki tana gudunki sbd bata</p><p>sanki ba, ina amfanin wannan? Tsohuwa tace</p><p>kukan wanikeji ta shigo tana kallon bishira cikin</p><p>mamaki tace. 'yar nan kece haka? Ciwo kikayi ko</p><p>ko duniya ce ta juya miki baya? Kai jama'a dubi</p><p>yanda kika kare kikayi bikinkirin. Ita da tadukar</p><p>dakai tare da cewa bnyi ciwo ba nidai nazo ku</p><p>yafe ni, sannan ku roqa min abba ya yafe min in</p><p>dawo dakina. Yace, bazan dawo ba har sai kun</p><p>yafe min, amma naje gurin umman bashir ta kore</p><p>ni tace bazata bari in dawo ba. Kuma gidanmu</p><p>wuya nake sha, kusan rabin aikin gidan nikeyi ga</p><p>qannaina duk sun raina ni. Umma tace, yi shiru</p><p>share hawayenki bari zaki koma. Tsohuwa tace,</p><p>ke dai kin cika sa kai a uku suwaiba, gashi abin</p><p>kirki bai karbe kiba. Kina yi ana zaginki ana zagin</p><p>'yarki, bishira ta ce wlh duk na daina, yanzu na</p><p>gane kune masu sona, umma tace ba komai.</p><p>Tadaga waya ta kira alhaji ta fada masa komai</p><p>yace to yana zuwa donshi ya qosa asulhunta</p><p>yarinyar ta koma dakinta saboda darajar</p><p>tsohonta. Yana zuwa yaji komai nan ya daga</p><p>waya yakira Abba, yace yana zuwa yana hanya</p><p>ne yace to ya same su gida. Abba yana shigowa</p><p>ganin bishira yahade rai ya zauna nan dai alhaji</p><p>ya hada su yayi musu fada da nasiha, sannan</p><p>yace baya son abba yace komai komai kuma ko</p><p>sun koma gida banda tashin tashina. Bishira tayi</p><p>ta godiya alhaji babba yace su tashi ashiga gurin</p><p>umman bashir din tana ganinsu tahau cewa alhaji</p><p>dakanka? Maimakon ace in zo? Umma tace, a'a</p><p>keda zamu zo baki hakuri ai mu ya dace mu</p><p>shigo. Nai dai alhaji yayi bata hakuri tace taci</p><p>albarkacinta na hakura, amma da sharadi inta</p><p>sake maimaita halin da tayi abaya ko taje ta</p><p>takurawa ummi tofa saita tabar gidan. Bishira</p><p>cikin kuka tace ta daina insha Allahu, nan itama</p><p>umman bashir din tace dasu umma su yafe mata</p><p>sharrin shaidan ne da qaryar barayin imani wato</p><p>bokaye da 'yan tsibbu suka ce ba komai. Nan</p><p>alhaji yace da abba yakai bishira gida, ba don son</p><p>ranshi ba yadauke tazuwa gida, sam bata damu</p><p>da daure fuskarshi ba, dadi da murna fal ranta.</p><p>Yana sauke tazai wuce tace, don Allah ka yafe</p><p>min sannan ka gaida min ummi, yace zataji. Tace</p><p>to yaushe zan dawo? Yace, duk lokacin dasu</p><p>alhaji suka zo gurin dadynku. Nan yatafi, ita</p><p>kuma ta shiga gida, hajiya zainu ta tsareta wai</p><p>sai ta fadi inda taje, tunda ta kira anty tace, bata</p><p>can. Bishira tace naje ba mijina da surukaina</p><p>hakuri ne, hajiya zainu tace ni dazai maida ki ai</p><p>sai nafi kowa murna. Na gaji da zamanki da</p><p>qazantarki, tunda babanku yaqi ki koma</p><p>makaranta yakashe miki kudi ki goge ko kya</p><p>samu mai kudin dazai aure ki, to gara kin koma</p><p>can kin qarata. Abba kam shi tunaninshi ta ina</p><p>zai soma sanar da ummi dawowar bishira? Don</p><p>baya son ko kusa hankalinta yatashi, baya son</p><p>wani abu yayi musu katsalandan a cikin</p><p>daddadan zamansu, don haka ya share bai fada</p><p>mata ba. Da dare alhaji da umma suka je, an</p><p>sasanta sannan suka taho da alkawarin cewa</p><p>gobe zata dawo dakinta. Washegari umma ta kira</p><p>Abba tace ya share ma bishira daki yau zata</p><p>dawo, yace umma nifa gsky dabata hankalina yafi</p><p>kwanciya. Sannan ina ta tunanin yanda zan</p><p>tunkari ummi da wannan zancen, umma ta riqe</p><p>baki tare da rafka salati, yace ynzun tsoron</p><p>ummin ka koma ne? Yace, a'a umma kin gata</p><p>sakankance ynzun hankalinta yakwanta sai kuma</p><p>taji nazo mata da zance dawowar bishira? Tace,</p><p>shi kenan nina fada mata. Awaya ta kira ummi</p><p>tafada mata cewa bishira zata dawo, duk datasan</p><p>cewa matar mijinta ce dama, amma sai da</p><p>gabanta yafadi. Umma taja mata kunne da cewa</p><p>kada taji kada tagani, abba ranar sai kusan sha</p><p>biyu zaije gurin aiki. Don haka yace kannanshi</p><p>suje su soma fito da kayan kafin yazo sunzo sun</p><p>fada ma ummi, ita ce ta bude musu dakunan don</p><p>abba ya canza makulli bayan tafiyar bishira. Abba</p><p>ya shigo tana zaune kan kujera sai tunani take yi</p><p>na irin zaman dazasu yi in bishira tadawo.</p><p>Yazauna tare dariko hannunta, tunanin me ki ke</p><p>yi? Takalle shi, halin rayuwa nake tunani, yace</p><p>yanzun umma ta kira ni jiya sun je gidan su</p><p>bishira wai yau zata dawo. Ummi ta taba baki,</p><p>Allah yakawo ta lpy. Ya ce ni ban soba gsky. Sbd</p><p>ke ummi tadafa kirji, sbd ni? Ni ya abba, kada</p><p>kasa duniya ta zage ni, Tare fa nasameku? Yace</p><p>to ni dai kada kiga kamar da son raina, tace don</p><p>Allah ya Abba kabar zancen nan. Kaje kagyar</p><p>mata dakunanta don su kamal bazasu iya ba,</p><p>yanufi gurinsu ganin kamar ya damu yasa itama</p><p>taje tasa musu hannu don dai ya saki ranshi, sun</p><p>gyara tsaf ummi ta goge sannan ta rufe dakin.</p><p>Har magriba bishira bata ji an ce za'a maida</p><p>taba, sai ta dauki wayar kanwarta ta kira shi wai</p><p>yazo don Allah yadauketa. Tsakanin mata da miji</p><p>sai Allah, nan ya tausaya mata yace zaizo, kafin</p><p>ya isa sai daya sai mata waya irin dai ta hannun</p><p>ummi. Har cikin gidan ya shiga suka gaisa da</p><p>babanta, yayi murna sosai yayi tawa Abba</p><p>godiya, tare da ba shi hakuri yace yasan yanda ta</p><p>horu zai gata canza da yardar Allah. Yasa aka</p><p>turo ta yayi mata nasiha, sannan ya gargadeta da</p><p>cewa inhar ta bari mijinta yakawa kararta zatayi</p><p>mamakin abinda zai mata. Tace, insha Allahu</p><p>baza ta kara ba, yakawo kudi yaba Abba, da kyar</p><p>ya amsa ita kuma ya bata wasu zannuwa acikin</p><p>leda, yace su raba da abokiya zamanta. Taje tayi</p><p>wa hajiya zainu sallama suka tafi, tamkar</p><p>baquwa haka ta koma, sai kace basu taba zaman</p><p>aure da Abba ba, nauyinsa take ji. Suna tafe ya</p><p>ciro waya ya miqa mata, tasa hannu ta amsa</p><p>yace taki ce, tayi ta godiya yace ba komai.</p><p>Sallamarsu tasa gaban ummi faduwa, ta dake ta</p><p>fito ta amsa, wani kishi ya tasho mata amma</p><p>saita danne. Ta kalli bishira tare dayi mata sannu</p><p>dazuwa, ta amsa tana kallon ummi tayi kyau</p><p>tagoge daga ka ganta kaga wayayya 'yar gatan</p><p>miji. Ta dauko makullin dakin ta ba bishira, abba</p><p>kuma ya nufi dakin ummi. Bishira ta dinga kallon</p><p>yanda abba ya gyara gidan yaja gini ta gefen</p><p>ummi yayi mata falo da kicin, sannan tsakar</p><p>gidan an gyare shi da tiles. Haka bandakin su</p><p>yagyara shi, nan dai bishira ta shiga dakinta ta</p><p>zauna bakin gado tana yi wa allah godiya tare</p><p>dayi wa kanta alkawarin har abada bazata ta</p><p>kara yin yaji ko ta janyo abinda zaisa mijinta ya</p><p>sake ta ba. Ummi tana kan gado tana karanta</p><p>wani littafi yazo ya zauna bakin gadon bata ko</p><p>kalle shi ba don haushi take ji. Sai take ganin</p><p>kamar rawar kai yake yi da dawowar bishiran,</p><p>kuma tuntuni yana zuwa gurin ta ya boye mata.</p><p>Yace madam ina son in yi magana da ku ne ke da</p><p>bishira, ummi tace ina jin ka, yace can zaki zo</p><p>muje. Tace, gsky nagaji, kayi maganar da safe.</p><p>Yagama gano kishi ne ke damunta, don haka yayi</p><p>murmushi yace yanda kikace hakan za'ayi. Ya</p><p>fita kamar minti 30 yasake shigowa ya aje mata</p><p>leda tare da cewa saida safe aciki tace Allah</p><p>yabamu alheri. Yana tafiya taje ta banko kofarta,</p><p>yau kam bacci ya qi idanun ummi sbd tayi sabon</p><p>bacci a haqarqarin Abba. Dukkan filolinta ta rasa</p><p>wanda zai maye mata madadin haqarqarin</p><p>mijinta, ynzun yancan da wata tasan yanda yake</p><p>wannan rawar jikin ynzun ya manta da batunta.</p><p>Tarasa me yake mata dadi, littafin datake</p><p>karantawa kuwa sam bata fahimtar abinda ke</p><p>ciki. Hka ta dinga zubda hawaye har nisan dare,</p><p>ganin bata da wata mafita, tashi tayi ta bude kofa</p><p>lokacin 2 saura taje tayo alwala tazo ta kama</p><p>nafila. Abba jin bude kofarta ne yasa shi leqowa</p><p>ta window aranshi yaji tausayinta don yasan bata</p><p>iya bacci sai ajikinshi, ita bata san ya leqo ba</p><p>don ko hanyar dakin bata ishe ta kallo ba. Yakalli</p><p>bishira wadda bacci yayi gaba da ita ya tausaya</p><p>mata sosai yanda tayi tarawar jiki alokacin</p><p>auratayyarsu dazun. Yadauko wayarshi yarubuta</p><p>ma ummi sako. KI KWANTA KIYI BACCI BABY,</p><p>TARE DA QISIMA CEWA KINA LAFE</p><p>AMAKWANCINKI (WATO JIKINA) INA CIKE DA</p><p>KEWAR LEBUNANKI. Tana sallah taji shigowar</p><p>saqo amma bata yi ko marmarin dubawa ba, haka</p><p>tai sallah har zuwa lokacin da bacci yasoma</p><p>fizgarta. Tayi adduo'o'i sannan ta kwanta, saida</p><p>asubahi ne datayi sallah sannan ta karanta, dan</p><p>tsaki taja tare da cewa, Karya kawai, kishi yasa</p><p>ta fadin haka don tasan Abba sosai baya boye</p><p>mata komai ynzun. Sai dai abinda yasake qular</p><p>da ita da asubahin nan yanda tana fita shi kuma</p><p>ya fito wanka, duk da tasan dole wani abu yafaru</p><p>tsakaninshi damatarsa, amma sai taga tamkar da</p><p>gayya ya tsaya don tafito taganshi. Tna idar da</p><p>sallah ta dora ruwa akicin dinta, tadafa ruwan tea</p><p>taje kicin din bishira tadauko flask tazo ta wanke</p><p>ta zuba musu ruwan zafi taje kofar bishira tayi</p><p>sallama bishiran ce ta bude ummi tamiqa mata</p><p>tare da cewa an tashi lpy? Cikin sakin fuska tace,</p><p>lpy lau, nagode. Ummi ta ce ba komai takoma</p><p>dakinta ta kulle kofarta don yau bata da darasin</p><p>safe. Abba ma yau bada wuri zai fita ba, don</p><p>haka yadan samu baccin safe sai 8 yayi wanka</p><p>ya karya, sannan yanufi dakin ummi. Kofarta tana</p><p>rufe, ya kwankwasa ta share sai can dai dataji</p><p>yaqi tafiya sannan tazo tabude. Takalle shiya yi</p><p>kyau cikin kananan kaya, ta kauda kai tare da</p><p>cewa, an tashi lpy? Yace lpy lau, kin karya? Tace,</p><p>um'um sai anjima, zata rufe kofar yace,</p><p>makaranta fa? Tace sai karfe 2 nake da darasi.</p><p>Ta maida kofar ta rufe, yayi dan murmushin</p><p>takaici sannan yafita. Kwananshi 2 dakin bishira</p><p>yayi niyyar dawowa dakin ummi, don ya kosa</p><p>yadawo ya lallasheta bazai iya daukar wannan</p><p>shariyar da take mishiba. Tsakaninta da bishira</p><p>lpy lau amma shi sai tana wani share shi. part 33 the end</p><p>Posted by Bashir Sani www.gidannovels.blogspot.com Fesan on 15 Dec 2016 - 14:45</p><p>Ya shigo da zumudi zai nufi dakinta, tamiqe cikin</p><p>fara'a daga wanke-wanken da take yi ta amshi</p><p>ledar hannunsa da jakar laptop ta nufi dakin</p><p>bishira. Shida bishira suka bita da kallo, ganin</p><p>zata shiga bishira tace ummi yau ai dakinki yake.</p><p>Ummi tace injiwa? Anty bishara ai kullum ke ce</p><p>dashi har sai kin rama duk kwanakin da kika</p><p>dauka agida. Kinga kenan kusan wata goma sha</p><p>daya kenan. Abba cikin sauri yace ke</p><p>mahaukaciya ce? Ina ki kasamo wannan fatawar?</p><p>Ta kalle shi, sannan tashiga dakin ta ajiye ta fito</p><p>taqara kallonshi gurin malamai, yace to ban</p><p>yarda ba, don haka zanci gaba dayi muku kwana</p><p>bibbiyunku, ummi tace to ni na yafe mata nawa</p><p>kwanakin bishira tace nagode ummi. Haushi ya</p><p>cika Abba, amma shi bazai dauki wannan horon</p><p>da ummi take shirin yi masa ba. Yadawo dakin</p><p>bishira a fili yafurta kema saina baki haushi zakiyi</p><p>dakin sanin wannan furucin. Sharewa yayi yaci</p><p>gaba da kwana dakin bishira tare da nuna kulawa</p><p>ga bishiran. Ummi ta jure duk da duk daren Allah</p><p>sai taci kuka ta gode Allah, sannan tashiga zargin</p><p>cewa shi ma ya Abban dama can yana son</p><p>tarewa dakin bishira, inba haka bame zaisa yayi</p><p>saurin yarda kuma yayi ta nuna mata soyayya?</p><p>Ganin ummi tana yi tamkar bata damu ba yasa</p><p>shi qa rajin haushi, yadawo da yamma suna</p><p>zaune kowa A qofarshi. Ummi tayi kwalliya cikin</p><p>qananan kaya, bishira kuma tana sanye da leshi,</p><p>karatun littafi bishiran keyi ita kuma ummi tana</p><p>yin gyaran qumbunanta. Bawai suna wata hira</p><p>bane amma suna kula juna sosai musamman</p><p>bishira tana son su saba da ummi. Ummin ce</p><p>bata cika son fitowa ba, bishira ta tashi ta masa</p><p>sannu dazuwa tare da amsar kayan hannunsa</p><p>don yanzun tana koyi da ummi gurin kyautatawa,</p><p>ummi ta kalle shi sannu dazuwa, ya amsa da</p><p>yauwa baby. Yakalli bishira sweety zanyi wanka,</p><p>tace to, takai masa ruwa yashiga dakinta, sai</p><p>tazo tace masa takai nan kuma yajanyo bishira</p><p>jikinshi. Ba wai yana da bukata bane, amma don</p><p>ya shaqar da ummi sai ya banko kofar, qaran</p><p>kofar ne yasa ummi kallon gurin dakin. Ta duqar</p><p>dakai taci gaba da abinda take yi, kusan minti</p><p>arba'in suka fito, Abba ya matsawa bishira wai</p><p>suyi wanka tare, tace ni bazan iya ba akwai ummi</p><p>dama da dare ne inajin kunya. Kuma kada taga</p><p>kamar cin fuska ne, yace kenan don kada ki bata</p><p>mata rai ni mijinki bazaki faranta min ba ko? Dole</p><p>ta bishi suka shiga bayi. Baqin ciki yasa ummi</p><p>tashi tashige daki, kuka sosai tayi daga nan bata</p><p>fito ba sai magriba, tanayin alwala tarufo kofa,</p><p>washegari ma qin bude qofar tayi daga alwalar</p><p>asubahi. Abba yayi ta raba ido ya ganta amma</p><p>bata fito ba, yasan fushi take, ya kira wayarta</p><p>taqi dagowa yayi mata saqo cewa in zata</p><p>makaranta tafito inkuma sai darana ta bude ta</p><p>amshi kudin mota. Tana gama karantawa tayi</p><p>wuri da wayar ba tare data bashi amsa ba, haka</p><p>ya tafi. Bishira ta qwanqwasa ma ummi ta bude</p><p>suka gaisa, tace naga baki fito bane ina fata lpy?</p><p>Tace lpy lau bacci ne, tace yau baza kije</p><p>makaranta bane? Ummi tace, zanje sai sha biyu.</p><p>Bishira tace kinji dadinki ni gashi nan ina tayi</p><p>masa zancen karatun amma ya share ni, ummi</p><p>tace inkin matsa zai yarda, tace ko za ki dan sa</p><p>min baki? Ummi ta riqe baki, ni a wa? Ke da yake</p><p>hannunki ai ke ce zai saurara, ni kin zo ne ma ki</p><p>zage ni. Bishira tace wane irin zagi? Ni dama ki</p><p>amshi mijinki ummi don gangar jikinshi ce kawai</p><p>agurina, amma ruhinsa yana gurinki. Ummi ta ce,</p><p>ngd da zagi, bishira ta ce zancan gsky ne ba</p><p>wani zagi. Haka suka yi ta rayuwa cikin kwanakin</p><p>ummi kam har rama tayi shima Abba ya rage</p><p>walwala don wanda yasan kan kula da shi</p><p>kamarta. Yayi missing din abincinta. Amma ya</p><p>gaji bazai jure ba. Ya tuna bishira tace masa zata</p><p>ta yini gidan ummanshi. Don haka yana gama</p><p>muhimman abubuwan da zai yi agurin aikin</p><p>yanufi gida. Ummi tana shirin tafiya makaranta ta</p><p>dauko jakarta sai kurum taga mutum kamar an</p><p>jeho shi. Ta daure fuska tamkar bata taba dariya</p><p>ba, yace ummi nagaji kin ji ko, na gaji da wannan</p><p>horon naki. Laifin me nayi miki? In don na dawo</p><p>da bishira ne sai in saketa, duk ba kece kika</p><p>takura min sai na dawo da ita ba? Ummi tace, ni</p><p>karka doran jakar tsaba kasa kaji su bini, ka saki</p><p>matarka sbd ni? Ba ruwana. Yace, to ki dawo</p><p>yanda kike, kuma ki janye batunki na wai kin</p><p>haqura dani, niban haqura ba. Ke ma kuma nasan</p><p>dole ki kasa kanki, ummi ta ce ni ban damu ba,</p><p>ya ce qarya ne gashi nan duk kin rame? Ya</p><p>canza daga fada zuwa lallashi, ummi don Allah</p><p>na roqeki mu koma kamar da, haba bebyna. Ya</p><p>lalubo hannunta ta qwace, don Allah ka tafi kada</p><p>bishira ta dawo ta same ka anan ta zargi wani</p><p>abu. Haushi yakamashi sosai, ya daga murya da</p><p>qarfi, kin san Allah ummi zan hadaki da umma, ta</p><p>nufi hanya fita, nikaga kada kasa ni yi latti don</p><p>lokaci yayi nisa. Ya ficiko ta ta dawo ba zaki</p><p>makarantar ba, ke an ma daina karatun tunda yafi</p><p>ni. Ta zubar da jakar da hijabi ta nufi gado shi</p><p>kuma ya fita cikin zafin rai, gidan su umma yaje.</p><p>Bishira tana dakin umma tana sallah yabi umma</p><p>kicin, umma gurinki nazo, ta dube shi lafiya</p><p>Abba? Ya turo baki, alamun ranshi bace baki,</p><p>yace umma ki sallami bishira, tace kamar yaya?</p><p>Yace taje can gidan ko muyi maganar agabanta?</p><p>Tace, kyale ta muje dakin babanku. Abba ya fada</p><p>ma umma komai da ummi ke masa, tun dawowar</p><p>bishira ran umma ya baci tace ka barni da ita.</p><p>Banda shashancin ta da ita kadai take son</p><p>azauna? Baga bishirar nan ba gidan nan ta gane</p><p>kuskurenta ko yau yarinyar nan sai da tace in</p><p>yafe ta nace ni dama ban riqe ta da wani abu ba.</p><p>Shine ita zata qirqiro fitina? Yace, umma ai ba da</p><p>bishira take yi ba dani take yi, tace to zata gane</p><p>kurenta da dare kuzo kai da ita. Umma ce ta kira</p><p>ta awaya tace tazo ita da abba, jikinta ya mutu</p><p>don tasan qararta aka kai, tana idar da sallar</p><p>isha'i taje gidan. Can tasamu abba, nan ko umma</p><p>ta rufe tada fada, koda tsohuwa ta jiyo tazo</p><p>umma tafada mata komai sai ta shiga fada. Wai</p><p>ai kishi halas ne, ke suwaiba tsakani ga Allah ko</p><p>ke bazaki so kishiya ba, bare ita yarinya. Abba</p><p>yace to gata nan ita ce fata dame ne nida batun</p><p>in dawo da bishirar, yanzun na dawo da ita kuma</p><p>ni abin ya qare akaina? Nan fa umma tayi mata</p><p>tatas, ta kuma sata anan ta ba Abba Haquri, aka</p><p>kira shi awaya ya fita. Umma ta samu dama</p><p>taqara yi mata nasiha da cewa, in bnda shirmenki</p><p>yaushe zaki bar ladanki, hanyar aljannarki kice</p><p>kinyi fushi da ita kin barwa kishiya? To kada in</p><p>sake jin haka, ki riqe darajarki da mijinki, ke</p><p>ganinki da ita. Ta jima tana bata shawara kafin</p><p>Abba yadawo suka nufi gida. Ya shiga gurin</p><p>Bishira ya fada mata cewa yau gurin ummi zai</p><p>kwana, nan ya bar ta da kewa yanufi gurin ummi,</p><p>tamkar yaune daren farkonsu hara sukai rayuwa</p><p>aranar. ** ** ** ** Kwanci tashi asarar mai rai,</p><p>shekara ta zagayo lokacin bishira da tsohon ciki,</p><p>Abba nason yara don muhibba taqi dawowa tafi</p><p>son umma dole suka haqura suka bar mata. Ta</p><p>haifi 'yarta budurwa tubarkalla ranar suna ta ci</p><p>sunan sahura inda suka sa mata walida. Ummi</p><p>nason yara, don haka in tana gida to tana manne</p><p>da walida, Abba yana damuwa da rashin samun</p><p>cikin ummi, wanda ita ummin ta barma Allah</p><p>komai. Shekaru uku sun sake biyo baya, lokacin</p><p>Bishira ta sake haihuwar habiba takwara Abba</p><p>yayi wa ummi. Tsohuwa an qara tsufa, 'yan</p><p>rigingimu sun qaru tace ita Abba yama takwara</p><p>amma bata son ya duke ta irin yanda yayi wa</p><p>ummi. Abba kullum qara son ummi yake, umma</p><p>ta matsa masa sai da yayi qoqari ya sai fili rabin</p><p>filoti tace kuma a rage ciye ciyen dadin nan agina</p><p>shì. Haka kuwa ya gina flat mai daki hudu, daya</p><p>ummi daya bishira, sai nashi sannan na yara.</p><p>Yayi qoqari gurin gyaran falon ita kuma ummi ya</p><p>canza mata kayan daki don bishira an canza</p><p>mata daza su tashi agidan su. Yace tabishi bashi</p><p>in ya samu zai bata kudi amadadin kayan daya</p><p>saima ummi, tace ta yafe. Ummi dake karantar</p><p>(BUSSINESS) har ta hada (H.N.D) dinta kuma</p><p>tayi bautar qasa. Abba dai yace baza'ayi aiki ba</p><p>amma ya yarda tayi kasuwanci, Alhaji babba ne</p><p>ya bata jari inda take saro kaya zannuwa, lesuna,</p><p>takalma zuwa jakunkuna. Abin ya amsheta don</p><p>har kayan aure tana hadawa, tana yin saqo irin</p><p>su kwatano da chaina, india, pakistan ko dubai,</p><p>ta hanyar wani wan kawarta. Haka kawai ummi</p><p>ta samu kanta da zaban abinci, yawan bacci</p><p>kasala da dai sauransu, sam bata san</p><p>takamaiman lokacin al'adarta ba. Don bata wani</p><p>lissafi in yazo shi kenan in bai zo ba bata damu</p><p>ba tama cire ranta daga batun ciki. Abba ya kalli</p><p>nonuwanta, baby kwanan nan kirjinki ya cika</p><p>sosai, gashi kinyi haske ko kin canza mai ne?</p><p>Tace yaya yaushe kazama likita? Yace, ummi kin</p><p>fa canza shirya muje asibiti, ta ce ya Abba don</p><p>Allah ka bar ni nagaji dazuwa asibiti. Yace, to ni</p><p>zan je inya tambaya game da yanda ki ka canza.</p><p>Cikin jin haushi tace sai ka dawo. Ga yara</p><p>atsakar gida sun ishe mu, yace ni naki nake</p><p>qawar in gani nasan addu'ar da nike yi bazata</p><p>fadi kara banza ba, sannan ga qoqarin danake yi,</p><p>shiru ta masa. Dagaske yake yi yaje yayi wa likita</p><p>bayani, yace yadai kawo fitsarinta. Sai da suka yi</p><p>tsiya da qyar bishira ta lallasheta ta yarda ta</p><p>bada fitsarin. Rungume likitan yaya lokacin da</p><p>yake fada masa ciki ne in dai har fitsarinta ne.</p><p>Afalo gaban bishira da yara abba ya rungume</p><p>ummi yana murna, ji tayi tamkar tsokana amma</p><p>ganin ya zauna yana ta buga waya yanata</p><p>yadawa ta amince cewa gske ne. Don haka ta</p><p>tashi ta shiga dakinta tayi alwala tazo tayi nafila</p><p>raka'a 2 cikin kuku take godewa Allah tare da</p><p>addu'ar ya raba lpy. Ya bata mai albarka.</p><p>Tsohuwa ma kuka ta saka lokacin da labarin ya</p><p>riske su. Ummi taga gata musamman daya</p><p>kasance cikin yazo da kumburi tayi sumtum. Duk</p><p>kowa ya tsorata sbd tunanin ko hawan jininta ne</p><p>ya tashi. ALLAH cikin Ikonshi data tashi haihuwa</p><p>saita santalo danta cikin gajeriyar nakuda, sak da</p><p>abba kwabo da kwabo. Rungume ummi abba yayi</p><p>don murna, sunan alhaji babba ya sake maida wa</p><p>kuma walid din dai suke kiranshi. Watan yaron</p><p>bakwai ummi ta sake rasa kanta, kuka wiwi ta</p><p>dinga yi shiko abba murna kamar yayi rawa.</p><p>Tasake samun da namiji inda yaci sunan alhaji</p><p>karami suka sa masa hibban. Haka suka ci gaba</p><p>da rayuwa cikin haquri da juna, tsakanin bishira</p><p>da ummi, bama irin bishira saboda abba baya iya</p><p>boye son ummi. Kan 'ya'yansu ahade ba kya</p><p>gane bambanci, bishira ta gane umma uwa ce</p><p>guda har da rabi, don haka hatta shawara saitaje</p><p>gurin umma kuma ko sabani suka samu da abba</p><p>gurin umma take zuwa. Ita kuma umma ta dauke</p><p>ta babu bambanci da ummi, don bata taba fada</p><p>ma ummi sirrin bishira ba. Sahura yanzun ta</p><p>yarda umma da alhaji sune rufin asirinsu, kuma</p><p>gatan Abba, bashi ma da yayi aure gidan dasu</p><p>ummi suka tashi nan ya zauna. Dangin bishira</p><p>yanzun sunga bishira ta samu natsuwa sun</p><p>sulhunta. Abba agurin aikinshi yana ta samun ci</p><p>gaba, lamuran sai godiya. Ummi tashafa addu'ar</p><p>da takeyi sannan tamiqe tana linke dardumar tace</p><p>kallon me ka ishe ni dashi ne ya Abba, yace ina</p><p>kallo ne na kusan samun da na uku wannan</p><p>karon takwara zan ma kaina. Ummi ta jefa masa</p><p>dardumar hannunta, daina min fata ni, yace ban</p><p>karanci likitanci ba amma ni likitanki ne. Ta fada</p><p>kanshi, ya rike fuskarta yana kallonta cikin ido,</p><p>ummi lokuta da yawa ina zama inta tuna da,</p><p>musamman in na kalli 'yan yaranmu wadanda</p><p>suke matuqar kama dani, tace me kafi tunawa a</p><p>baya? Yace, yanda kikayi ta kirana awaya kina</p><p>tsara ni suhaylan kaduna. Suka sa dariya. Ni kam</p><p>nafi tuna yanda ni da kai muka yi ta 'ZURFIN</p><p>CIKI' dason juna. Yace Allah yabarni da ke har</p><p>abada matata. Ta kwantar da kanta</p><p>amakwancinta ''Amin mijina''. Muma Allah ya bar</p><p>mu da masoyanmu har gidan aljanna, ya bamu</p><p>lafiya dazama lafiya. Ya zaunar mana da 'yan</p><p>uwanmu lafiya, Amin ya rabbi. ** ** ** ** Bayan</p><p>shekara goma naje nasamu yaya Abba nace</p><p>inason muhibba yace badamuwa yabani kyautar</p><p>gida da mota. Ummi kuma ta hada mun kayan</p><p>lefe saboda namijin kokarin danayi na rubuto</p><p>maku wannan littafin aka daura mana aure da</p><p>muhibbata muka tare muka cigaba da soyayya</p><p>fiye dasu ummi ma.</p><div><br /></div>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-49391156719073627572022-02-12T05:12:00.001-08:002022-02-12T05:12:55.350-08:00Sirrin-zuci Complete Hausa Novel<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEiltBXD8Hhz4hRF61VU677oy74-HycFBMUzzwA57iOW-q938jk-d7LepH1aQQvoxLmg8pkT9aJgPnvzht2-nZuMUFgfS8ziCQsoG-Q97Uh5eLaYryzGPVx66giU5sDcGnKsV-V2v1R9MFtVtXCszfqpuWZPe6zU0hF62cBAMvgUlTOOCfaQTLEvJGBw=s2286" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="Sirrin-zuci Complete Hausa Novel" border="0" data-original-height="1768" data-original-width="2286" height="309" src="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEiltBXD8Hhz4hRF61VU677oy74-HycFBMUzzwA57iOW-q938jk-d7LepH1aQQvoxLmg8pkT9aJgPnvzht2-nZuMUFgfS8ziCQsoG-Q97Uh5eLaYryzGPVx66giU5sDcGnKsV-V2v1R9MFtVtXCszfqpuWZPe6zU0hF62cBAMvgUlTOOCfaQTLEvJGBw=w400-h309" title="Sirrin-zuci Complete Hausa Novel" width="400" /></a></div><br /> 💧💧SIRRIN ZUCI........<p></p><p> </p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p>1 to 2</p><p><br /></p><p> البسم الله الرحمن الر حپم</p><p><br /></p><p><br /></p><p>================= Gidan Novels =====================</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Lumshe Ido yayi sannan ya budesu tar bisa kan wata karamar yarinya dake zanen yar galala ....</p><p><br /></p><p> Fito yayi da bakinsa a hankali ....da sauri yarinyar ta kallo sama tana murmushi tare tsalle tana daga mashi hannu ...</p><p><br /></p><p> Iska ya huro mata ...sannan ya daga mata hannu ....itama hannun ta daga mashi ....</p><p><br /></p><p> Wata tsohuwa ta fito daga wani karamin gida wanda duk unguwar babu talaka sama dasu ....</p><p><br /></p><p> Meenalle ...Meenalle. ..ta fara kwada kira ....</p><p><br /></p><p> Yar karamar yarinyar ta juyo da sauri tana bata fuska ...cikin shagwaba tace .....Kai kaka ke kullun sae ki batawa mutun suna ...nasha fada maki Meenal fa ake cewa? ...</p><p><br /></p><p> tsohuwar tace ...to naji sarkin hakuri zo muje ki sayo mana kwaki ko bakijin yunwa?</p><p><br /></p><p> Saman benen ta kalla. ..har yanzu yana tsaye ita yake kallo ...daga mashi hannu tayi tare da langwashe kai ...sannan taja hannu tsohuwar suka koma gida ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kudin ta karbo sannan ta sako hijab ta fito ...tana zuwa bakin kofa taja birki tare da dafe kirji ....hal ka ban tsoro ...ta fada hakoranta waje ...</p><p><br /></p><p> Hararanta yayi...ke kuma sarkin tsoro ko ...ya fada yana gyara mata hijab dinta ...</p><p><br /></p><p> Kai ...aikena fa akayi ...ta fada tana neman cire agogon dake makale a hannunsa ...</p><p><br /></p><p> Hannunsa ya janye don karta bata mashi...sannan yace ...Me zaki sawo?</p><p><br /></p><p> Baki ta tabe tana kokarin wucewa sannan tace ...kaini Kaka tace kabar sawo man komae ..wae ku yan yankar kaine ...kuma tace wae kaina zayayi tsada ...</p><p><br /></p><p> Dariya ya sake a hankali kafin yace mata. ..ni kuma kakata tace man indae mace na yawo to kasa ake rufeta ...ya fada idonsa na kallonta ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ido ta waro cike da tsoro ...da gaske Mai kamshi?</p><p><br /></p><p> Ganin ta tsorota ya saka yace ..eh mana ai bana so a rufeki shiyasa ma nace ki fada man in sawo maki ...</p><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p> Kamar jira take ya rufe baki tayi saurin mika mashi naira hamsin din da ta gama nannadewa ...</p><p><br /></p><p> Amsa yayi ..yace me zaa sawo. ..</p><p><br /></p><p> Kwaki na talatin sae sukari na ashirin ...ta fada a hankali ..</p><p><br /></p><p> kai ya girgiza kana ya tafi. ..har yayi nisa ta kwala mashi kira...ya juyo. .tace ...Dan Allah kace a maka arha ..kuma kayi sauri kar kaka tace na dade ...</p><p><br /></p><p> Kai ya daga mata sannan ya tafi ..</p><p><br /></p><p> Baifi minti goma ba ya dawo rike da manyan ledoji. ..tana hangoshi ta tareshi tana dariya ...</p><p><br /></p><p> Duka ledojin ya mika mata ya juya ...tayi saurin janyo hannunsa ..to ka tsaya mana na duba inda canji ba sae ka bani ba ...ta fada tana bata rai ..</p><p><br /></p><p> Dariya ta bashi sossae ..ya dawo suka shiga zauren gidan ...</p><p><br /></p><p> Zama tayi kasa ta zazzage kayan tsaf ...ido ta waro lokacin da ta daga katon gwangwanin madara ..tace ...Nawa ka sayo wannan ...ta fada tana kallonsa ..</p><p><br /></p><p> Naira biyar ...ya ce idonsa yana kallon karamin bakinta ...</p><p><br /></p><p> Uhmm saura arba'in da biyar kenan ta fada ...biscuit ta cigaba da fitowa da chocolate sae ledar cos cos da sugar sae lemuka kala kala ...duk wanda ta daga sae ta tambayeshu kudinsa ...daga wanda zayace biyu biyar sae na biyar ....har ta fito da tiyar garin kwaki ...</p><p><br /></p><p> Wannan nawa yake? ...</p><p><br /></p><p> Kura mata ido yayi ..sannan yace ...wannan a shagon wani abokina ya bani su ...</p><p><br /></p><p> Dariya tayi kana ta maida kayan tana kallonsa ...to bani canjina ...ta fada lokacin da ta gama maida kayan ...</p><p><br /></p><p> Ido ya waro ...wane irin canji kuma?</p><p><br /></p><p> Harara ta balla mashi ...sha biyar mana. .ba yanzu mukayi lissafi ba naira Talatin da biyar ka kashe ...</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi ..ya lalubi ajihunsa ...babu ko naira 500 bare kananan canji. ..</p><p><br /></p><p> dubu daya ya mika mata ...ta make kafada ...ni canjina zaka bani ....ta fada a shagwabe </p><p><br /></p><p> Dukawa yayi dae dae tsawonta ....kiyi hakuri Meenatou ...banda canji...kinji. ki bari anjima zanyi canji sae na baki ....</p><p><br /></p><p> aa Ni dae ban yarda ba ....muje a canzo su ...ta fada. .</p><p><br /></p><p> To naji shiga da kayan sae ki fito muje. ...ya fada idonshi a lumshe ...</p><p><br /></p><p> Ka gudar man da canji ...tace </p><p><br /></p><p> Hannunta ya kamo ...baran gudu ba ....ya fada har lokacib idonshi a rufe ...</p><p><br /></p><p> Shiga gidan tayi tana waigenshi ...aje kayan tayi ta fito da gudu ...kaka nata kiranta. ..amma ce mata tayi ....Kaka Kawata ta mutu ake kiranmu muyi mata addua ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Feedohm💞</p><p><br /></p><p> </p><p>.</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI......</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>3 to 4</p><p><br /></p><p> </p><p> Suna fitowa daga zauren Gidan ...dae dae lokacin mota ke horn kofar gidansu ....da sauri ya kalli motar sannan ya kalli kofar get din ...babu alamun mai gadi zaya bude ....hannunsa ya zame ya nufi kofar zaya bude ...</p><p><br /></p><p> Ka tsaya wallahi duk wayonka bara ka gudar man da canji ba ...ta fada lokacin da ta bishi da gudu ...</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi a ranshi yace ...Meenatou kenan ....</p><p><br /></p><p> Gate din ya bude sannan ya matsa jiki. motar ...na ciki ya rage glass din dauke da faraa ...yace</p><p><br /></p><p> Ma'aruf ...ina mai gadin ne ...</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi wanda ya zame mashi dabi'a sannan yace ...wallahi ban san inda ya tafi ba ...amma ko ma meye na tabbata baya kusa. ...ya saka hannun ya bude motar ....</p><p><br /></p><p> Dae dae lokacin Meena ta iso gurin tana sheshsheka ....</p><p> </p><p> Hararanshi tayi ...sannan tace ..wallahi yau ko'ina zaka shiga sae ka bani canjina dan ba asi ta yayeni ba ...na gaji mutun sae wayau ..dama ranar nan na biyoka canjin Biyar baka bani ba to yau sae ka hada man da ita ...don na gaji da wahala. ..ta karasa maganar kamar zatayi kuka </p><p><br /></p><p> Mutumin yafito cikon motar dauke da murmushi ...ya dafa kanta yace ...Mamata canjin nawa zaa baki ? </p><p><br /></p><p> Dariya tayi kana tace ...Abba canjin sha biyar ne biyar din wancen satin dana biyoshi amma ya gudu wae bayya da canji .....Au na manta Abba Ina wuni...</p><p><br /></p><p> Dariya yayi yace ...dama mamana ina zaki tuna idonki ya rufe da kudi ...Ma'aruf bawa mamana canjinta....</p><p><br /></p><p> Murmushi ..yayi yace ..Wallahi Abba banda canji kuma kasan halin Meenatou ...</p><p><br /></p><p> Shima dariyar yayi yace ...Mamana bata da wani hali mara kyau ...mu shiga gida sae yasamo Maki Canjinki ko mama..nima na gaji da cinye maki kudi kullun ....</p><p><br /></p><p> Dariya ta sake tana kallon Ma'aruf din ...hannunta Abba ya kama suka shige ciki...</p><p><br /></p><p> Da Sauri ta karbe kayan da wata kyakykyawar mata ta fito dashi daga kitchen ...sake mata tayi tana murmushi ...</p><p><br /></p><p> Yau Mamanmu ce a gidan mu ...Ta fada tana dauke da murmushi. ..</p><p><br /></p><p> Meena tayi dariya sannan tace ...Eh man ae mai kamshine ya cinye man kudi naira ashirin har da ta rannan ...</p><p><br /></p><p> Dafe kanshi ma'aruf yayi ...sannan yayi sama da sauri yana fadar ..Wayyo Meenatou kamar na cinye maki Million bara dole na samo maki canjin ki yanzu. .</p><p><br /></p><p> Matar tayi dariya tace ...Sae kuwa ka biya mamanmu canjinta yau ....zo kici abinci kafin. ya samo maki ....</p><p><br /></p><p> Girgiza kai tayi tana murmushi...na koshi..</p><p><br /></p><p> Abba ne yace. .. ai kuwa na kusa batawa da ke mamana </p><p><br /></p><p> Da Sauri ta matsa kusa dashi ...Abba me nayi ...</p><p><br /></p><p> Matar ta tareta tace ...da bakicin abinci kullun a gidansu Mai kamshi ..</p><p><br /></p><p> Ido ta waro ...In ci abinci ku sayar dani ? </p><p><br /></p><p> waye zaya sayar dake ...inji Abba ..</p><p><br /></p><p> Ni dae ba ruwana ...ta fada sannan ta fara kwalawa Ma'aruf kira ...Matar ta nuna mata inda yake ...</p><p><br /></p><p> Ta kuwa shige dakin da sauri ...lokacin da kyar ya samo naira sha biyar ...ya mika mata ...sae da kyar ya samu ta karba shima da kashedin da ta gansho sae ya biyata ko kuma ta cire mashi agogo ...</p><p><br /></p><p> To kawae yace mata don so yake ta barshi da wannan masifar canji ....sae da ya hada mata da sweet sannan ta tafi tana mita..</p><p><br /></p><p> Bayan ta fita ya dafe kai. ..sannan ya kwanta saman gado...shi kanshi yasan yau duk inda ta ganshi sae ta nunashi tana binshi canji ...iska ya huro ...sannan yace ...yau ba abunda zaya saka na fita indae ban samo naira biyar ba ....idonshi na lumshe fuskar dauke da murmushi ...bacci ya daukeshi ..</p><p><br /></p><p> ••°°</p><p><br /></p><p> Kunnenta Kaka ta rike ...wane shegene ya kiraku kuyiwa gawa addua ...</p><p><br /></p><p> Ido ta waro ...wallahi Allah kaka wa ...</p><p><br /></p><p> Bakinta ta buge....rufe man baki ke yanzu ko dabbobin gidannan ai sun bar kama rantsuwarki ..</p><p><br /></p><p> Baki ta turo waje ...tana kefta idanuwa ...</p><p><br /></p><p> Ma'aruf kika bawa kudin ya sawo maki ko? ....ta tambayeta tana kallonta </p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm*💞.</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI......</p><p><br /></p><p> 💞 </p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>4 to 6</p><p><br /></p><p> Ido ta waro waje ...Hauka nake da zan bashi...ae in fada maki kaka wani shago naje mai saukin tsiya komae naso naira biyar suke sayowa ..su fa ko daga kasar Dandiyana suke siyo kayansu ...ta karashe maganar hakora bude ..</p><p><br /></p><p> Gwagwanin madara ta dago tace ..naira nawa kika sayo wannan ? ...</p><p><br /></p><p> Shiru tayi tana tunanin nawa ma Ma'aruf yace mata ...da sauri tace Naira biyar ...ta fada tare da nunota da hannu ...</p><p><br /></p><p> Kwafa tayi sannan ta fito da wata naira biyar din ta miko mata ...kije ki sayo man irinta karba. ..</p><p><br /></p><p> Babu tantama ta karba ta fice da gudu ...daga zaure ta tsaya tana hangen saman benen gidansu Maaruf ...ganin baya nan ya saka ta sake murmushin jin dadi tare da fadar ...Allah ya soni da yanzuma sae yaci zalina. ..ta nufi babban shagon dake unguwar ...</p><p><br /></p><p> Cikin saa tana zuwa taga gwangwan madarar jere ...ta washe baki sannan tace a miko mata ...aka saka mata a leda ...ta fito da naira biyar ta mika mashi ..</p><p><br /></p><p> Mai shagon ya karba yace mai zaa baki da wannan ...</p><p><br /></p><p> Rufe ido tayi sannan tace a hankali ..Mai kamshi Ma ya iya cuwa cuwa ashema har da canjina yace naira biyar to bara na koma ya jama kanshi sae ya fito man da kudina ...? </p><p><br /></p><p> Sanna ta nuna wani karamin sweet aka miko mata ...ta juya ...mai shagon yace ke kawo kudin madarar mana ..</p><p><br /></p><p> Wani kallo ta mashi sannan tace ..wanda na baka fa ..</p><p><br /></p><p> Yaushe kika bayar ...ya tambayeta ...</p><p><br /></p><p> Malan Dallah biyar din da nabaka fa ka miko man canjin alawa ko bashi kake bina ..</p><p><br /></p><p> Tsaki yaja ya fizge ledar sannan ya nuna mata hanyar fita ..fice ki bawa mutane guri ..sakaran banza ..Ubanwa ke sayar da katon Gwangwanin peak naira biyar ..fice dallah ...</p><p><br /></p><p> Kuka ta sake gurin ...wallahi ba inda zanje sai kun biyani kudina ai bani nace ka tambayeni me zaa bani da biyar din ba ...gashi ka saka na kashewa kaka kudi kuma ka hanani abunda na saya .kuma dazu anan aka sayeta naira biyar din ...ni sae ka bani kudina kuma wallahi baran sake siyan komae ba anan ...</p><p><br /></p><p> Cikin tsawa yace ...zaki fice ko sae naci ubanki anan ...kaga marar kunyar yarinya</p><p><br /></p><p> Tsaye tayi gurin taki wucewa sae da ya dauko bulala ya biyota a guje sannan ta wuce tana kuka .....</p><p><br /></p><p> Tana shiga dakin ta fada saman cinyar kaka tare da sake kukan da babu digon hawaye ko kadan a idonta ....</p><p><br /></p><p> Cikin kula tsohuwar tace....Me kuma ya faru Meenalle. ..</p><p><br /></p><p> Kafa ta fara haurawa tana fadin ...ba kudin da kika aikeni bane naje shagon da zan saya babu sae na fito wata akuya ta fizgesu daga hannuna ...</p><p><br /></p><p> Murmushi tsohuwar tayi ..duk da tasan karya take....kuma ta tabbata bara ta kashe kudin ba ..sae dae ko faduwa sukayi ...</p><p><br /></p><p> Ta shafi kanta ...to yi shiru mana Aminatuta ...dan akuya ta fizge biyar ba sae kiyi hakuri tunda kin san dae baran maki fada ba ...banda abunki nima na wuce irin akuyar data fizge naki ta fizge hannuna ...yi shiru Meenalle share hawayen mana ...</p><p><br /></p><p> Kin shirun tayi sae ma sabon salon turje turje da ta sake ta hambare duk inda taso ido rufe kuma ko hawaye babu ....</p><p><br /></p><p> Saukar tsintsiyar kwakwar da taji a kafarta ya saka ta bude idonta da sauri tare da kallon kafarta. ..ganin ledar garin kwakin Da Ma'aruf ya sayo mata ta fashe gashi duk ya zube a kasa ya saka ta gane bannar da tayi ....</p><p><br /></p><p> Lokaci guda ta tuno da zafin tsintsiyar kwakwar kaka ta zuba da gudu ta fice daga gidan ...</p><p><br /></p><p> Tana jin Kaka na kiranta amma bata tsaya ba ta fice daga gidan ...</p><p><br /></p><p>°°••</p><p><br /></p><p>Tulin kayan wankine jibge gaban Yar mashiyar budurwar da bata wuce shekara 17 ba ....ta saka hannu tana daga kayan a yatsine tana kauda fuska gefe ...</p><p>. </p><p> Wata mata ta fito daga wani karamin daki ...tace Haba luba kiyi sauri ki wanke mashi mana su zaya saka ...</p><p><br /></p><p> Yatsina fuska tayi tace ...ni gaskia innarmu baran iya wankewa baba wannan kayan ba ...kaya sae wari suke ...ga kudi a kai mashi wanki ....ta mike tsam ta shige daki ...</p><p><br /></p><p> Ficiciyar Sallamar Meena ne ya katse mata hanzari ...</p><p><br /></p><p> Matar ta kalleta da faraa ....Su Aminatu ne a gidanmu ...</p><p><br /></p><p> washe baki tayi tana fadin ....Eh Man inna ..fada mukayi da Kaka na taho nan ...Mamata tana ciki? .ta tambayeta. </p><p><br /></p><p> Tana ciki Aminatu.....</p><p><br /></p><p> Da gudu ta fada dakin tana kwalawa Mamanta kira ....ta zaune saman darduma tana addua ....ta juyo tana kallonta har ta karaso ...bata tsaya gurin mamar ba ta wuce gurin wani dan karamin tebur ta dauki ayaba ta saka baki tare da lumshe ido ....da sauri ta budesu tace ..mama karki ga na rufe ido ba fa ki dauka wani abu ..ni ba Mai kamshin unguwar mu ba.. nake kwaikwayo kawae nayine naga ko zai man kyau ...kinsan dazu sae da yaci man zalin biyar muka rabu ...shi wannan shegen taurin bashine dashi kamar babansu Luba .. ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*.</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>7 to 8</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sallamar babansu luba ce ta katse mata sauran maganarta .....da sauri ta koma bayan mamarta....</p><p><br /></p><p> Ya shigo fuska daure ...Idonshi na kan Meena ...ya Nuna Nuna mamar da Hannu cikin daga murya yace ...Banda iskanci Rabi kina ji ina kwala maki kira kikayi shiru ...</p><p><br /></p><p> Dukar da kai tayi ...tace wallahi Malan banji ba kayi hakuri ...</p><p><br /></p><p> Yace ...baki ji gidan ubanwa ba ...sau nawa ina kiranki dan rashin mutunci har muryata ta dashe ..</p><p><br /></p><p> Meena tace. . .to tunda bata ji ba kuma ba shikenan ba . kai babansu Lubar nan ka cika masifa ...ko dan baka da ko sisine ? ....</p><p><br /></p><p> Mamar tayi saurin zaunar da ita tare da buge mata baki ....</p><p><br /></p><p> Girgiza kai yayi yana fadin ...owo Rabi har kin haifi diyar da zata fadawa mijinki magana ..to nima ina da yaron da zai mata dan banzan duka ....ya fice daga dakin</p><p>....Dafe kai tayi idonta cike da hawaye tace ...Nashiga Uku Aminatu waya ce ki zo gidannan ...ba na hanaki zuwa ba ...kinga yi maza ki fice ki koma gidan Kaka yanzun nan ....</p><p><br /></p><p> Ai kuwa da gudu ta fice dae dae zaune Musa( _babban dan Malan_)Ya shigo rike da wata doguwar bulala ..tayi saurin boyewa bayan kaure. ..yana shigewa gidan ta fice da gudu ta koma gidan Kaka .....</p><p><br /></p><p>••°°°••</p><p><br /></p><p> Wallahi Malan Kaka ce ta aikeni shi yasa na makara ...tafada tana daga hannu ...</p><p><br /></p><p> Babu Abunda Ya dameni da wadda ta aikeki ita bata san lokacin Islamiyya ba ...? </p><p><br /></p><p> Tace .. Lah Malan ai lokacinsu babu islamiyya ta tsofa ba ..</p><p><br /></p><p> Yace Aminatu Abubakar ki matso ba bugeki ki shiga aji ...don yau ba wani da uzurinki da zan karba .... </p><p><br /></p><p> Matsowa tayi ...yana daga bulalar ta matsa da sauri..hannu ya saka ya fizgota tare da zuba mata bulala a baya. ....wani tsalle tayi ta shiga cikin babbar rigarshi ta aza mashi cizo a kirji .....</p><p><br /></p><p> kokarin fiddota yake amma taki sakinshi ...da kyar ya samu ta fito lokacin ta sake mashi cizo yafi 5 .. shi kadae yasan azabar da yake ji ...idanuwansa sunyi jawur. ..yana ganin ta fito ya shige toilet din makarantar da sauri ya cire rigar ...duk inda ta cijeshi ta fasa shi ...wani karamin kwalla ya goge tare da yi mata Allah ya isa ...duk islamiyyar babu mai son dukan Meena saboda irin wannan abun shima yau tsautsayi yasa Headmaster yace yayi taren yan makara ...</p><p><br /></p><p> Sae da ya gama kananan kwallan shi sannan ya fito daga toilet ...Headmaster ya ganshi yace ...Ustaz Har ka gama dukan yan makaran ..</p><p><br /></p><p> Harara ya balla mashi ya wuce office abunshi ....daga cikin office din yana hango Meena nata wasanta ...Allah kadae yasan iya Allah ya isar da ya ja mata ...bai kuma fita ba har aka tashi ...</p><p><br /></p><p> ••°°°••</p><p><br /></p><p> Ganin motar gidansu Ma'aruf ta fito ya saka ta karasa gurin da sauri tana washe baki. ..</p><p><br /></p><p> Abba ta gani ciki ...yana ganinta ya sauke glass din ...ta gaidashi ...ya amsa mata cikin Faraa .</p><p><br /></p><p> Abba kaga Mai Kamshi har yau bai biyani bashina ba ...ta fada tana bata fuska ..</p><p><br /></p><p> Dariya yayi yace ...to ae mamana Mai kamshi baya lafiya. ..</p><p><br /></p><p> Ido ta waro ...me ya sami Maikamshina ? ta kareshe maganar kamar zatayi kuka. ..</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi ya fito daga motar tare da jan hannunta suka shiga gidan ...Mamanshi bata falo suka wuce dakinshi ....yana kwance yana bacci ...tana hangoshi ta janye hannunta daga Hannun Abba ta duka kusa da gadon da yake ...tana kallon fuskarshi ...fita Abbah yayi ...</p><p>Hannunsa ta damke tana kallon fuskarshi .sajen dake kwance a fuskar ta taba .....Mai kamshi ...ta fada a hankali ...</p><p><br /></p><p> Idonsa yana rufe amma ba bacci yake ba ....ta kara kiran sunanshi. ..ganin bai amsa ba ya saka ta sake mashi kara dae dae kunnenshi ...</p><p><br /></p><p> Da sauri ya bude idon yaji karar har cikin kanshi ...dariya ta sake ...sannan ta shafi wuyanshi ...saurin dauke hannunta tayi tana kallonshi shima ita yake kallo ..</p><p><br /></p><p> Mai kamshi jikinka Zafi ..ta fada kamar zatayi kuka ..</p><p><br /></p><p> Daga mata kai yayi tare da lumshe ido ...itama idon ta lumshe sannan tace. ..Amma mai kamshi wannan ciwon naka har da taurin bashi ke kara mashi yawa ...</p><p><br /></p><p> Dariya ta bashi yayi saurin janyo drawer dake jikin gadon ya fito da sabuwar naira biyar ya daura mata a hannu ...</p><p><br /></p><p> Baki ta washe tace. ..ka gani ko Mai kamshi yanzu ko mutuwa kayi babu bashin kowa akanka ...lokacin guda idanunta suka ciko da kwalla tace ...kuma ko bana so ka mutu Mai kamshina ...ta fada lokacin kwallar ya gangaro kumatunta ...</p><p><br /></p><p> </p><p>*Feedohm*💞</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI.....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p>================= Gidan Novels =====================</p><p><br /></p><p>9 to 10</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Zaune ya tashi tare da janyota ya zaunar da ita bisa cinyarshi ya share mata hawayen </p><p><br /></p><p> Yace ...ai mutuwa dole ce Meenatou ..</p><p><br /></p><p> Girgiza mashi kai tayi ..aa ni bana so ka mutu ...</p><p><br /></p><p> Shafa kanta yayi yace ...to kiyi addua meenatou Allah ya bamu tsawon kwana kinji ko ...Na furta maki Sirrin Zuci ...mai dadin saurare...</p><p><br /></p><p> Film din dake kunne a dakin ta maida hankali gareshi .....zuwa can ta mike tana washe baki ...tace Mai kamshi kaci abinci ...</p><p><br /></p><p> Film din ya kalla shima ciki wata budurwace take bawa saurayinta abinci abaki ...murmushi ya sake ya girgiza mata kai alamar aa ...</p><p><br /></p><p> Ta fice ...zuwa can sae gata da abinci cikin Plate ya kalleta da mamaki yace ...ina kika samo ...</p><p><br /></p><p> Baki ta washe gurin Mamanku naje nace zaka ci abinci ta bani ...</p><p><br /></p><p> Zama tayi saman cinyarshi ...tare da debo abincin a spoon ta mika mashi ...ahankali yace ..bana cin abinci da spoon sae da hannu Meenatou</p><p>Ido ta waro ..Kai mai kamshi dazu dana zo cizon malan na taba hammatarshi kuma wari take ....</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi ya bude ...wani abu ya tokare mashi makoshi baya kaunar Meenatou ta taba wani namiji duk da tana karama ....</p><p><br /></p><p> Shiga toilet ki wanke hannun ki fito ...ya fada a hankali ...</p><p><br /></p><p> Sae da ta bashi abinci sannan ta fice ...ya bita da kallon ....gida ta koma ta sakewa Kaka kusa sae tazo ta gaido mai kamshinta baya da lafiya ...</p><p><br /></p><p> Da farko kaka cewa tayi bara tazo ba amma da taga masifar ba mai karewa bace ta ziro Hijab ta biyota ...</p><p><br /></p><p> Mamar Ma'aruf taji dadi sossae sanna ta kara son Meena a ranta ...haka shima Ma'aruf murmushi kadae yake yi tare da lumshr ido har suka tafi ....</p><p><br /></p><p> Kasancewar an koma Boko kullun kafin ta tafi makaranta sae ta shiga ta ganshi ...ta bashi abinci .. sannan take wucewa haka idan ta dawo sae ta shiga ta bashi abinci ko da kuwa zata dade bata dawo ba to zaya jirata ....Abincin Rana tare suke ci ...tana bashi tana ci ...amma da anzo gurin nama nanne zancen zai canza salo ...don sae taci Yanka 4 kafin ta bashi guda ...idan kuma kazane to sae ta cinye tsokar sannan tace ya gashi ya cinye ...sae dae kawae yayi murmushi. yace ya koshi. ..haka zata sake mashi kuka sae yaci ...hakanan zaya danci abinda zai iya ya bar sauran kashin ...Har Allah ya bashi lafiya ....</p><p><br /></p><p>••°°</p><p><br /></p><p> Kaka nidae wallahi wannan wanke wanke wanken yayi man yawa ...ta fada cike da shagwaba ...</p><p><br /></p><p> harara ta dalla mata ...sae ki nemi wanda zaya tayaki ...</p><p><br /></p><p> Sallamar Ma'aruf ce ..yasa ta sake Murmushi tana cewa ...Yauwa Maikamshi zoka tayani mu gama na fada maka wata magana</p><p>Kaka tace ..bara ya tayaki ba dan kaniyarki ....Ma'aruf ko za zauna ka kyaleta ...ta shimfida mashi tabarma ..</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi yace ...barta na tayata Kaka naga kayan sun mata yawa ita kadae. ..</p><p><br /></p><p> baki ta washe ...Yauwa mai kamshina ..kayi wanke wanke sae in maka dauraya nafi iya dauraya kai kuma kafi iya wanke wanke ...</p><p><br /></p><p> Yana wankewa tana daurayewa har suka gama ..kaka na kallonsu cike da fata kala kala aranta ....</p><p><br /></p><p> Bisa tabarmar ya koma ya zauna ...zonan Meenatou ...ya fada a hankali. ..</p><p><br /></p><p> Kusa dashi ta koma ta zauna ta harde kafa tana kallonshi ....</p><p><br /></p><p> Wani karamin zobe na gold ya fito daga cikin jikkanshi ...ya zura mata a hannu ...</p><p><br /></p><p> Kallon zoben take ..tana kallonshi ..ni ka sawo mawa ? </p><p><br /></p><p> Daga mata kai yayi ...ta kare washe baki tace .... don kar na fadawa kaka kace idan aikeni na dinga karbowa kyauta a shago ...</p><p><br /></p><p> Ido ya lumshe sannan yace aa ...kinsan Zuciya ? </p><p><br /></p><p> Lallae ma Mai Kamshi tun muna primary one muka ganin zuciya ....</p><p><br /></p><p> Yace Good ...to ki aje wannan itace zuciyata ...</p><p><br /></p><p> Dariya take har da kwalla ...kai kuma wannan itace zuciyarka ...to nima bara na baka taea zuciyar ...ta kwance dankwalinta ta zare ribbon din dake kanta ta mika mashi ...</p><p><br /></p><p> Amsa yayi yana daga shi ...sannan yace na meye wannan ...</p><p><br /></p><p> Hararanshi tayi sannan ta saka hannu zata fizge ....to bani abuna tunda baka so ...</p><p><br /></p><p> Aa sorry Meenatou ina so mana ...wannan shine zuciyarki ? </p><p><br /></p><p> Eh man mamana ta bani shi da sallah ...ina sonshi ...</p><p><br /></p><p> cikin jikkarshi ya saka sannan ya mike ya ma kaka bankwana ya wuce ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Feedohm💞*</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI.....</p><p> </p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>11 to 12</p><p><br /></p><p> </p><p> Wani karamin yarone ya shigo office din headmaster yana kuka rike da ya gaggen littafi ...</p><p><br /></p><p> Ustaz ya kalleshi Yace..me ya faru kake wa mutane kuka...</p><p><br /></p><p> Yaron yace .Meena ce ta yaga man littafi ...</p><p><br /></p><p> Wani wahallalen miyau ya hade tare da shafa kirjinsa ...sannan yace ...Jeka Allah ya saka maka ...ya juya yaci gaba da duba lttafin dake gabanshi ...</p><p><br /></p><p> Wani sabon malamin da bai dade da zuwa ba ya kalli Ustaz yace ..Haba ustaz wane irin Allah ya saka mashi ...ya nuna yaron tare da fadin ..jeka kirata. . </p><p><br /></p><p> Bai fi minti biyu ba ta shigo da uwar sallama. ...Sabon malamin ya ce ta rage tsawonta ...</p><p><br /></p><p> Zama tayi tsakar office din ta mike kafa ....tsawa ya daka mata. ..babu shiri ta yi kneeldown din ...Kallon Ustaz tayi tace ...Ustaz Dan Allah kayi hakuri shi ya fara daukar man goriba ya cinye ..</p><p><br /></p><p> Da sauri Ustaz ya juyo yace. .Meena Abubakar bani na kiraki ....ya kakkabe riga ya fice daga office din ...</p><p>Sabon malamin ya bata punishment din wanki toilet din makarantar duka tare da share ko wane glass. ...tana kuka ta gama ko aji bata koma ba ta wuce gida ...</p><p><br /></p><p> Sae da ta bari lokacin tashin malamae yayi saboda suna tsayawa meeting kullun ...lokacin mangrib tayi kowa na sauri yaje masallaci sannan ta nufi hanyar islamiyya. ....tun kafin ta isa ta cika jikkarta da duwatsu ...</p><p><br /></p><p> Wani lungu mai duhu ta samu ta shige wanda ta san dole tanan sabon malamin zaya wuce ...Cikin saa sae gashi ya taho kanshi na kasa yana tafiya ....katon dutse ta samu ta saita keyarshi ta jefa mashi ....dafe gurin yayi ya juyo yace ...Uban waye ke yo jifa ...bai rufe baki ba ya kara jin wata a goshinsa har sae da jini ya zubo ....</p><p><br /></p><p> Tana ganin ya dafe gurin da sauri ta fito daga maboyarta ta kukan kura tayi ta shige cikin rigarshi ...rudashi tayi ta dinga sake mashi cizo tare da yakushi ta ko ina ...</p><p><br /></p><p> Da kyar ya samu ya babbareta ...tare da zubawa da gudu ...don duk tunaninshi aljanace ....</p><p><br /></p><p>••°°°</p><p><br /></p><p> Ustaz ya kalleshi cike da tausayi yace ...Malan isiya sae naji headmaster yace ka samu hadari jiya a hanyarka ta komawa ...</p><p><br /></p><p> Sosa kai yayi yace ...wallahi kuwa Ustaz ina saman mashin wani mai mota ya bangajemu ...</p><p><br /></p><p> Meena dake tsaye ta kalli ustaz tace. .Malan meye hukuncin mai karya...</p><p><br /></p><p> Dan wuta ...ya bata amsa don yanzu tsoronta yake ji ...</p><p><br /></p><p> to Malan isiya ma dan wutane ...jiya gabana akayi ...wata aljanace ta rotsa mashi cizo sannan ta shige a rigarshi ta yakusheshe ta ruga ...</p><p><br /></p><p> Wata dariya Ustaz yake har da dafe cikin sannan ya kalli malan isiya da sae yanzu ya gane wannan shegiyar yarinyar ce ta masa rashin mutunci ...</p><p><br /></p><p> Ustaz yace. ...Malan da mai motar ya bugeku sae ka fada kan aljanar ? </p><p><br /></p><p> Shiru yayi ...yana nan tsaye kuma duk yaron da yazo wucewa to Meena zata tareshi ta bashi labarin malan yayi karya yace hadari yayi alhalin aljana ce ta shige rigarshi ta yakusheshi ...wani ma har yadda aljanar tayi masa take nuna masu da bango .... yana tsaye da uwar palasta a goshi ...cikin dubara ya sulale ya fice daga islamiyya....Tun daga lokacin malan isiya bai kuma dawowa ba ...</p><p><br /></p><p>••°°°•• </p><p><br /></p><p> Mai kamshi ina irin wannan alawar daka sawo man jiya ...ka tunata ...ta fada rike da hannunshi tana murmushi ...</p><p><br /></p><p> Daga mata kai yayi ...na tunata ..</p><p><br /></p><p> Yauwa to ita zaka kara sawo man ...ta mika mashi wata rabin naira biyar ...</p><p><br /></p><p> Dan Hararanta yayi ...waye zaya amshi wannan rabin kudin ?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*.</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI......</p><p> </p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>13 to 14</p><p><br /></p><p> </p><p> Hararansa tayi ...Kai baka san yarda ake cuwa ba ...ai murdeta zakayi ka mika masu da sun baka sae ka rugo da gudu. ..</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi yace. ..Idan Allah ya kamani fa ..</p><p><br /></p><p> Washe baki tayi tace ...ai zan maka addua ya yafe maka tunda yana saurin amsar adduar mu ...</p><p><br /></p><p> To kawae yace mata ya juya ya koma cikin motarshi ya fice daga unguwar ...har ta bar ganinshi tana daga mashi hannu ...nan ta zauna tana zanenta a kasa. ...sae da tayi budu budu da kasa sannan ta koma gida ....</p><p><br /></p><p> Tana shiga kaka tace sae tayi wanka....rantsuwa ta hauyi wae mamarsu Ma'aruf ta mata wanka daga gidansu take ....kaka tace bata yarda ba. ....</p><p><br /></p><p> Turo baki tayi tace ...ni wallahi na gaji da wannan cacar kullun wanka ...</p><p>Kaka ta rike baki tace. ..yanzu dan kaniyarki Meenalle wankan ne wahala ....to ai kuwa indae kina nan gidan ki dinga irin wannan wahalar ..tashi tun kafin na taso ...</p><p><br /></p><p> Mikewa tayi ta nufi hanyar zaure tana amsa sallamar karya ...Girgiza kai kakar tayi tare da fadin Allah ya shiryaki Meenalle ....Zaure ta ci zamanta har sae da kaka ta fara gyangyadi sannan ta dawo ta kwanta kusa da ita ...</p><p><br /></p><p> ••°°°••</p><p><br /></p><p>Kai ta daga tana kallon benen gidansu Ma'aruf sannan ta fito tana tafiya tana kallon gidan ko zaya fito ya bata sakonta ....har ta bar unguwar bata ga kowa ba .....Ledar dake hannunta ta saka hannu ta fito da biscuit daya ta fasa ta ci rabi ta maida rabi ta kulle ...</p><p><br /></p><p> A bakin kofa ta tarad da Malan Musa mijin mamarta zaune ya kallon masu wucewa ....gaidashi tayi yaki amsawa. ..har ta shiga zauren ta dawo baya ta tsaya gabanshi ...</p><p><br /></p><p> Angon mamarmu ina wuni _Kamar yadda taji wasu mutane na kiranshi da can baya_...ta sake gaidashi ..</p><p><br /></p><p> Ko inda take bai kalla ba ...ta sake cewa ..kodae mamansu Luba ta ci maka Uwa shi yasa ka dawo nan ka zauna ...ta kefta ido daya ...</p><p><br /></p><p> Cakumota yayi ya hade da dakalin da yake zaune ...Uban me kikace ....ya fada da karfi. .</p><p><br /></p><p> Wani mutumin dake zaune nesa dashi ya taso ya amsheta tare da bashi hakuri sannan ya jashi suka tafi kasuwa dan gudun abunda zaya je ya dawo ...</p><p><br /></p><p> Miyan wahala ta hade sannan ta ida shiga cikin gidan ....</p><p><br /></p><p> Musa Ustaz ....ta fada lokacin da taga musan zaune tsakar gida daga shi sae gajeren wando ..kusa da Luba </p><p><br /></p><p> Harara ya banka mata tare da yin kwafa ....</p><p><br /></p><p> Kara cewa tayi ...su musa da luba ba magana. ..kunyi zaune kamar turmi ...</p><p><br /></p><p> Zanci Ubanki Meena ...Luba ta fada tare da tasowa ...dakin mamarta ta fada da gudu ...amma bata tsira ba sae da ta biyota ta mata zagin uwa da uba sannan ta fice ...</p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Meena dan Allah ki rufa man asiri kizo ki koma gidan kaka wallahi bazan iya da masifarki ba ...ke kamar jaka kowa ya bugeki amma bara ki natsu ba ...dan Allah ki zo ki shirya ki tafi ....Mamarta ta fada idonta taf da hawaye ..</p><p><br /></p><p> Ni Ba inda zan koma wallahi ..ai gidan ma bana baban Luba bane ashe na bakine ...ta turo baki ..</p><p><br /></p><p> Waya fada maki nawane Meena ki rufa man asiri. ....</p><p><br /></p><p> Shiru tayi taci gaba da baccin karya. .. .</p><p><br /></p><p> Can kuma ta mike kamar an tsikareta tare da kallon mamarta sannan tace ....ni mama waye babana ? .....</p><p><br /></p><p> Kallonta take sannan ta dauke kanta gefe guda tace ...tashi kije kiyi wanka kizo ki koma gidan kaka ....</p><p><br /></p><p> ••°°•••</p><p><br /></p><p> Tsaye yake ya harde hannuwanshi kofa gidansu Meena ya kurawa ido kamar yana kirga kasar gurin ...</p><p><br /></p><p> wayarshi tayi kara ya duba message ne ya shigo ...da sauri ya buda sannan ya sauko tare da daukar keys din motar ya fice daga gidan ....</p><p><br /></p><p> </p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI......</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 15 to 16</p><p><br /></p><p> </p><p> Office dinsu ya nufa ...yana zuwa aka bashi takardar tafiya karo karatu kasar indiya nan da wata biyu ake so ya tafi ...Course din na shekara 5 ne suna so ya zama cikkaken Pilot ....Karba yayi yakoma gida ...dama Abba ya dade yana nemar mashi sae akace sae gurin aikinshi sun saka mashi hannu ...sae yau ya takardar ta fito suka saka hannu ....Mamarsa ya bawa takardar sannan ya kara fita da sauri ....</p><p><br /></p><p> Meenatou. ..ya kirata ahankali ...</p><p><br /></p><p> Ta juyo cike da masifa tace ...kai me yasa ka cika cin zali na ...tun yaushe nake nemanka ka bani kudina shine ka boye dan kasan ka kashe man kudi ko</p><p>Dafe kanshi yayi tare da lumshe ido sannan yace ...Meenatou na nemeki bakyanan ..</p><p><br /></p><p> Baki ta bude tana kallonshi sannan tace ..ni dae bani kudina ..ta mika mashi hannu ..</p><p><br /></p><p> shiru yayi yasan ko ya bata kudin dake jikinshi bara ta amsa ba ...dan naira dari biyarce karama ciki ...a hankali yace ...banda canji bara na shiga gida na dauko maki ...</p><p><br /></p><p> Gefen rigarshi ta tace ...sae dae mu tafi a haka karka kuma guduwa ....</p><p><br /></p><p> Meenatou haka zaki rikeni kamar kin kamo barawo ..please ki sakeni kinji ..</p><p><br /></p><p> ta daure Fuska Allah mai kamshi idan kaga na sakeka to ka bani kudina ...</p><p><br /></p><p> Kaka ta leko tana mata dakuwa. ..Meenalle uwaki nace ...zaki sakeshi ko sae na fito ...</p><p><br /></p><p> kafa ta fara bugawa tana fadin ...kaka kudina fa ya cinye kusan sati guda ...ganin tsohuwar ta fito ya saka ta sake mashi riga tare da fashe da kuka ta zauna gurin ...</p><p><br /></p><p> Daukarta yayi da hannu yana bawa kaka hakuri ...ce mashi tayi ya sauketa kasa amma yayi murmushi ya shige da ita gida</p><p><br /></p><p> Falo ya zaunar da ita yana lallashi sannan ya dauko mata rabin biyar dinta ..dama tana aje saman mirrow ..ya bata tare da sweet din ....Haka Mamanshi ta shigo ta isketa tayi bacci saman kirjinsa ta wuce tana kallonsu ....</p><p><br /></p><p> ko motsin kirki kasa yi yayi gudun kar ya tayar da ita ...sae da ta dade tana bacci shi kuma yana kallonta sannan ta tashi .....gida ya rakata sannan ya bawa Kaka hakurin karta dake ta sannan ya fice ...</p><p><br /></p><p>*Meena*</p><p><br /></p><p>Diyace tilo ga alhaji Abubakar mai zinari </p><p>..wani hamshakin mai kudine a cikin garin kaduna ...Sunyi aure da Rabi'at..Auren soyayya ...ko shekara basu datse ba Allah ya albarkacesu da Meenatou ...Mahaifinta yana mutuwar sonta amma matsakar uwar Alhaji Abubakar bata san danta ya haifi diya mace don tace dawainiyace da wahala haihuwar mace ...Tunda Rabi ta haifi Meena zaman gidan Alhaji Abubakar ya zame mata zaman makoki ...kullun mahaifiyarshi tana gidan ...wulakancin yau daban na jibi daban ...har Meena takai wata Takwas. ..sae Uwar Alhaji Abubakar ta kawo wata diyar kawarta tace sae ya aureta ....sannan ya saki mahaifiyar meena ko ta tsine mashi ...suna kuka suka rabu ...Sannan mahafiyarshi tace ko bayan ranta kar ya neme su idan kuma ya nemesu bata yafe mashi ba .....</p><p><br /></p><p> Da dan kudin da ta samu ta gina gida ta ginawa mahaifiyarta kaka itama karamin gida ...gida daya suka fara zama da kaka tana rainon diyarta ...</p><p><br /></p><p> Meena nada shekara 5 Malan Sani ya fito yace zaya aureta ....lokacin yanada rufin asiri dae dae gwargwado ..sannan yana da mata daya mai suna Saratu ..itace mahaifiyar su Luba da Musa ....</p><p><br /></p><p> Ta aureshi ashe bata sani ba dan cacane ...dan haka duk abunda ya mallaka sae da ya kare gurin caca ...harta gidan da suke zaune sae da ya sayar ..sannan ya roketa suka dawo karamin gidan da ta mallaka ...ita da mamansu luba kuwa ...kowane yana daraja dan uwanshi ...matsalar tana gurinsu luba da Musa ...ko kadan basu da tarbiyya wanda sak halin Malan Sani ya biyo ...da yake rabi macace mai hakuri bata taba gayawa wani mutun cewa ga zaman da take gidan mijinta sannan bata nunawa kowa gidanta suke zaune ba ..da farko auren ya yarda Meenalle ta zauna gidanshi amma daga baya sae yace sae dae ta koma gidan ubanta ..haka ta mayar da Meenalle gidan kaka....lokacin da Meenalle tace mata gidantane tayi mamaki sossae dan bata san wanda ya fada mata ba ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm*💞</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 17 to 18</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mai kamshi wae ina kake samun kudin da kake rabawa mutane ....</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi yace ...Allah ke bani meenatou</p><p><br /></p><p>Dariya ta sake tare da tarba hannu sama tace. ..Allah ka bani kudi irin na Uncle Ma'aruf nima na dinga bawa mutane ...</p><p><br /></p><p> Kallonta yayi tare da fadin Uncle Ma'aruf a hankali ...</p><p><br /></p><p> Da Sauri ta kalleshi tace ..Mai kamshi kaji nace maka Uncle Ma'aruf ko ..haba nima yanzu na zama baby ...ina Musan gidansu Luba ..ka ganeshi? </p><p><br /></p><p> Uhm yace mata duk da bai sanshi ba ...</p><p><br /></p><p> Ta wash baki tace ...to shi naji yana cewa I love dinshi ta gaida mashi Uncle ..kila ko babanta yake nufi ko kuma i love you dinta itama ...uhm ohon mashi dae shima dae ya sani ...kuma yake ce mata I Kiss me wallahi ...in gaya maka Mai kamshi kamar a film dinnan daka kunna man rannan ....Ni kuma naga duniya ba kullun ake kwana gado ba. ...kasan ko jiya kaka kasa ta saukeni na kwana </p><p> </p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi tare da mikewa tsaye yace. . Meenatou tashi kije kiyi sallah ...</p><p><br /></p><p> Miyau ta hade sannan tace ..ni bana Sallah yau ..</p><p><br /></p><p> Ido ya waro gwanin shaawa yace ..Me yasa bara kiyi sallah ba Meenatou ...</p><p><br /></p><p> Sae da tayi dariya sannan tace ...yo malamarmu ta boko naji rannan tace wa kawarta wae bata yin Sallah nima kuma naga da kadan ta fini tsawo ...shi yasa nima nace banayi ..</p><p><br /></p><p> Tunda Take magana yake kallonta har sae da diga aya sannan yaja numfashi a hankali ..ya wuceta ...</p><p><br /></p><p> Hannunsa ta kama tare da rike kunne...Mai kamshi zanje nayi kaji? ..</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi tare da shafar gefen fuskarta yace ...Yauwa Meenatou ta ..kije kiyi zanzo na tambayi kaka ki rakani unguwa ...</p><p><br /></p><p> Wani uban tsalle da daka tare da rungumeshi cikin sabo ta dankara mashi cizo a hannu ...</p><p><br /></p><p> Da Sauri ta janye bakinta lokacin da ta lura da cizon da ta sake mashi</p><p>Idanuwanta suka kawo ruwa ta duka gabanshi tare da kallon kasa ....</p><p><br /></p><p> Meenatou ...ya kira sunanta a hankali ...ganin bata dago ba ya saka ya duka shima tare da dago kanta da hannunsa ..hawaye ya gani bisa fuskarta ...murmushi yayi sannan ya share mata hawayen ...</p><p><br /></p><p> Hannunta ta daura saman lebenshi tana kallon fuskarshi ...lumshe ido yayi tare da zura hannun cikin bakinshi ...kadan ya hade hakoranshi da hannunta ....ga mamakinshi sai ji yayi ta sake mashi ihu tare da murginawa kasa tana fadi ..</p><p><br /></p><p> Wallahi sae na rama ai ni ba da karfi na cijeka ba ....</p><p><br /></p><p> Dariya yake sossae sannan ya mika mata hannu yace ...Rama Meenatou ...babu kunya ta murje idonta ta dana mashi cizo sannan ta mike tana dariya ta shige gida .....</p><p>Dariya yayi ya shige masallacin kofar gidansu ....daya fito sae da ya shiga gida yayi wanka ya saka blue din shirt data fito da zaharin kyanshi tare da bakin jeans ...ya fito sae kamshi yake ...</p><p><br /></p><p> Daga zauren gidansu taji kamshinshi ta sake ihu tana kewaye zatayi wanka tana fadi ...naji kamshin mai kamshi bara na fito ...</p><p><br /></p><p> Ruwa ta shafawa kafafuwanta tare da wuyanta da hannunta sannan ta zubar da ruwan ta dauro zani ta fito ...</p><p><br /></p><p> Tsakar gida ta tarad dashi suna zaune da kaka suna fira. ..</p><p><br /></p><p> Kaka ta bita da kallon tuhuma. .nan da nan ta hau rawar sanyin karya tana fadin. ..kaka ruwan sanyi....dakyar na watsawa bayana don hannuna rawa yayi tayi. ..</p><p><br /></p><p> Aa Meenalle. ...kya ma fadi gaskia dan kaniyarki ..muje dakin ki gwada man bayan naki ...</p><p><br /></p><p> Bata fuska tayi tace ..na fara nonuwa fa ...</p><p><br /></p><p> tashi tayi ta bita da fada daki da gudu ....</p><p><br /></p><p> Ma'aruf da kusan suman zaune yayi ...bashi yayi magana ba amma kunya ta rufeshi ....da kyar ya iya tambayar kaka meena zata rakashi gidan mamarta ya gaida ta ...</p><p><br /></p><p> Taji dadi sossae tace ..ba komae Ma'aruf ko da duniyar zaka bari da Meenalle wallahi na yarje maka bara ka taba cutar da Meenalle ba ...ina fatan Allah ya nuna man girman Meenalle na nuna mata mijin da babu kamarshi a duniyarnan Ma'aruf...</p><p><br /></p><p> Dukar da kai yayi cike da kunya ....Meena ta fito taci uban jan janbaki duk fuskarnan duk tasha digon baki sae washe baki tayi ....</p><p>suna hada ido suka lumshe ido tare ...tayi saurin bude idon tare da warosu ...Mai Kamshi ? ...ta fada da karfi ...bafa kai nake kwaikwayo ba hakanan nayi abuna ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI...... </p><p> </p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>19 to 20</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A mota ta isheshi da surutu duk surutun akan babansu luba ya kare tana fada mashi shima babansu luba taurin bashine dashi ..wae idan ya karbi kudin mutane dakin mamarta yake boyewa. da anzo kiranshi sae dae yayi karya yace baya nan ...</p><p><br /></p><p> Har sae da taga an tsaya kusa da wata katuwar plaza a jiki an rubuta MIMA Plaza ...parking yayi ya fita ya zagayo ya bude mata. ...murmushi yayi tare da jan hannunta ....</p><p><br /></p><p> Kaya sossae taga ya jida sannan aka biyoshi dasu a baya ...sannan tun da suka shiga taga kowa yana bashi girma kuma bai biya kudi ba ...kasa hakuri tayi ta kalleshi tace ...</p><p><br /></p><p> amma Mai kamshi kai babban barawone..</p><p> ....</p><p><br /></p><p> Kallonta yayi ya tada mota sannan yace ..da nayi me kenan Meenatou ...</p><p><br /></p><p> Uhmm banda sata zaka shiga shago ka debo kaya ka fito bakq basu kudi ba ...ko bashi suka ba ...</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi yace ...eh bashi suka bani ...</p><p>Uhmm Allah to ya fito masu da kudinsu ...nima da kyar kake biyana bare wasu ..uhmm .. ta tabe baki ...</p><p><br /></p><p> Idan ban biyasu ba ai sun zo su kamaki don dake nayi kwatance .....ya fada hankalinshi naga titi ..</p><p><br /></p><p> Dadinta ma nasan gidanku sae in kaisu ka biyasu ....</p><p><br /></p><p> Dae dae gidansu Mamarta taga ya tsaya ta budeshi. ...mai kamshi ba dae labarin da na baka na babansu luba ba kazo zaka fada mashi ..</p><p><br /></p><p> Hararanta yayi ...yace ...kinsan baki so a fada mashi kuma kike fadawa mutane ..</p><p><br /></p><p> Dan Allah kayi hakuri mai kamshi wallahi rannan ma da kyar wani ya kwaceni gurinki. .kuma ma kai kadae na fada mawa da yan ajinmu ...</p><p><br /></p><p> Ki fito muje mana ...ya fice daga motar ...da sauri ta biyoshi tana rantsuwar bara ta kara bawa wani labari ba ....data isheshi yace mata ba za gaya mashi ba ...sannan ta kyaleshi ...sun gaida sossae da Mamarta sannan ya aje masu kayan da ya siyo masu ya tashi ...taji dadi sossae tare da godiya don dama tuni ta san shi ...</p><p><br /></p><p> °°••°° </p><p><br /></p><p> Kaka jiya kinsan me ya faru</p><p>....</p><p><br /></p><p> ya zaayi na sani Meenalle ....</p><p><br /></p><p> Uhm kema fa kar na baki labari kizo kici amanata yarda mai kamshi yaman gidansu mama ....ta fada a hankali ...</p><p><br /></p><p> Dariya tayi tace ...indae kinsan gulmar mutanece karki fada man nima amanarki zanci ...</p><p><br /></p><p> Shiru tayi ...zuwa can ta kasa hakuri tace ...Kaka babansu Luba fa dan iskane ! ..</p><p><br /></p><p> Meenalle kaniyarki nace ..tashi ki wuce ki bani guri ....sae ki saka a daure mutun yana gani ....</p><p><br /></p><p> ••°°••</p><p><br /></p><p>*Two month*</p><p><br /></p><p> Shiru tayi tana kallonshi ...a hankali tace Maikamshi ...</p><p><br /></p><p> Yaakae Meenatou ...ya fada idonshi na kallonta ..</p><p><br /></p><p> Zaka manta dani? ...</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi tare da dawo kusa da ita...Zuciyarshi ya nuna da hannu ...tare da lumshe Ido...kina nan ciki Meenatou ....ya furta a hankali</p><p>Zuciyarshi ta dafa tare da daura kanta a bisa tafi minti goma Sannan ta janye tana kallonshi ...idanuwanta suka ciko da kwalla ...tace ..Mai kamshi Ka dawo da wuri na dinga ganinka.. ...</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi ...zan dawo Meenatou amma kiyi alkawarin nima zaki sakani a taki zuciyar ...</p><p><br /></p><p> Da sauri ta janyo hannushi ta tura a rigarta ..tana fadin. ..taba kaji Mai kamshi akwaeka ciki Allah. ..da karfi zuciyarta ke bugawa ....janye hannushi yayi daga jikinta ya mike tsaye ....Tashi muje Abba na jirana a mota ...</p><p><br /></p><p> Hannunshi ta rike yana janye da ita ....har harabar gidan ...nan ne ta sake sabon kuka sae ya tafi da ita ...da kyar kaka ta cireta daga jikinshi ...shima idonshi ya kada yayi jawur .....</p><p><br /></p><p> Mamarshi ta dauketa ta dinga lallashinta ranar nan gidan ta kwana ...sae da daddare Tayi shiru lokacin Ma'aruf ya kira waya ...kuka ta sake mashi sae ya dawo ...lallashinta yayi sossae ...wayar na kunnenta tana kwance jikin Mamarshi bacci ya dauketa ...daga cikin wayar yake jiyo saukar numfashinta lumshe ido yayi ...sannan yaki kashe wayar ya daurata a kirjinsa..yana sauke numfashi ...ganin tayi bacci ya saka mamarshi ta zare wayar ...gani tayi har lokacin wayar na kunne .. wayar ta kanga a kunnenta tana jiyo bugun zuciyarshi ...Shafa kanta tayi tare da sumbatar kanta sanna ta maida mata wayar a kirjinta ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI...... </p><p><br /></p><p> 💞 </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞 </p><p><br /></p><p><br /></p><p>21 to 22</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Haka rayuwa ta cigaba da tafiya kullun da safe Ma'aruf zaya kira Mama AWaya ...haka itama Meena tana gama shirin makaranta zata shiga gidan ...bara ta fito ba har sae ya kira sunyi magana ...kullun idan suna wayar tambaya dayace yaushe zaya dawo ....sae dae yace maka nan ba da dadewa ....wata irin shakuwa ta kara shiga tsakaninsu ....haka Mama na kokarin ganin ta taimakawa da kaka da komae na bukata ...</p><p><br /></p><p> wani lokacin idan ya kira da daddare anan gidan take kwana rungume da wayar... </p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°•• </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gab da zasu gama primary lokacin Meena ta gama fadawa kaf yan makarantarsu cewa gidan mamanta babansu luba ke zaune ...duk inda ta zauna bata da labari sae na babansu luba....sannu sannu magana ta koma kunnenshi ....ranar sae da yayiwa Rabi wulakanci sossae dan har cewa yayi zaya daketa ...da kyar maman su luba ta shiga tsakani .. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Abokan cacarshi ya fadawa mawa wasu suka bashi shawarar indae yana so ya zauna cikin gidan dole ya dauki mataki ...in kuma ba haka ba to yana ji yana gani Meena zata girma ta fitar dashi cikin gidan ...hankalinshi yayi mummunan tashi domin wannan gidan shine rufin asirinshi ... </p><p><br /></p><p> A rude ya sami wani babban abokinshi wanda tare suke komae nasu ...shine ya bashi shawarar indae yana so ya gaje gidan to dole yasan yadda zai hada auren da Musa da Meena .... </p><p><br /></p><p> Shawarar ya dauka ...ya kuwa samu rabi da maganar ...daga farko taki amincewa ...amma daga baya daya sameta akan cewa ta nuna mashi bashi ya haifi Meena ba ...hakuri ta bashi amma ya tashi ya fice daga dakin ...tun daga ranar yake fushi da ita ...</p><p><br /></p><p> Rabi tana da ilimin addini kuma tasan darajar miji ga matarshi don haka har daki ta sameshi ta bashi hakuri sannan ta nuna ta yarda ... Da yake munafukine ranar soyayya kala kala ya nuna mata ...tunda ga ranar yakoma yana lallabata ... </p><p><br /></p><p> Ita da kanta ya tura ta sami kaka da maganar amma fifir taki yarda ...wasu malaman unguwarsu ya turo mata suka dinga mata sharhi akan Meena tare da bata baki ....da kyar suka shawo kanta ta yarda ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Bayan sun tafine Meena ta dawo daga islamiyya sanye da uniform ...tun daga zaure ta fara kwalawa kaka kira ... </p><p><br /></p><p> Kaka tace ..Meenalle ta yau kuma me aka samo ... </p><p><br /></p><p> dariya tayi ta zube bisa kafarta ...sannan ta kalleta tace ...Kaka Maikamshi yace ya kusa dawowa ...kinsan idan ya dawo ko ..uhmm kaka kenan ..ranar zan kwashi adashena na hada mashi abinci mai dadi kuma ba bashi zan mashi ba kyauta ...kinga ko ranar zan saka wadannan kayan Sallan da Mamana ta dinka man ...inyi kyau sossae wallahi ko ke bara ki ganeni ba ......Yana zuwa zance I Love you Uncle Ma'aruf..I Kiss Me Mo Uncle ...kinsan waya koyaman wannan turancin ? Girgiza kai ..kaka tayi a hankali ....tana kallonta ... </p><p><br /></p><p> Zama ta gyara sannan tace ...wani littafine na samu na kaiwa Mamansu kausar kawata ta koya man ...Allah ko Kaka Ina son Mai kamshi ... ...tashi tayi ta shige daki ta cire Unifoam dinta sannan ta dawo ta zauna tare da sake sabon surutu kuma duk kan Ma'aruf ...wanda kullun dama firanshi take ..</p><p><br /></p><p> ••°°•• </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Rabi na zaune daki babansu Luba ya shigo rike da goro a hannu ...gabanta ya zube mata sannan ya zauna yana washe baki ... Ga goron auren danki....ya fada yana dariya ... </p><p><br /></p><p> Zumbur ta mike ..tana fadin na shiga uku ni Rabi ...Aminatu Malan shekararta 12 kenan ..haba Malan ...wani kuka ta fashe dashi tare da dukewa gurin ..... </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mikewa yayi ya fice daga dakin tare da barin goran a kasa ....Musa ya shigo cikin babbar riga yana washe baki ... Dukawa yayi ya gaisheta yana washe baki ...kasa amsawa tayi har ya mike ya fice daga dakin yana tattare riga ...dakin uwarshi ya shiga ..Wanda itama sae yanzu take jin labarin ..kallonshi tayi sama da kasa ta wuce su tare da tur da halinsu ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Feedohm💞</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ...</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>23. to 24</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Cikin sauri Rabi ta fito daga cikin gidan Malan ...yana shingide bisa dakalin kofar gidan ...mutane ke zuwa tare da mashi murna ...bata kalli kowa ba ta tsayar da mai adaidaidata ...tasha tace ya kaita cikin saa ta samu motar kaduna mutun daya ake jira .....ta hau suka tafi ...</p><p><br /></p><p> °°••°°</p><p> </p><p> Kofar gidan Alhaji Abubakar ta sauka ...bakin gate taga motarshi da alama yanzu ya Dawo ...</p><p> </p><p> Yana hangota yayi saurin fitowa ya tareta ...Rabi dama kina raye ? ....ya tambayeta a rude ..</p><p> </p><p> tambayar ta sosa mata rai ...saurin daga mashi hannu tayi sannan tace ..Muna Raye ko muna Mace abubakar wannan ba damuwarka bane ...nazone na tuna maka da amanar Da Allah ya baka tana bukatar taimakon Ubanta Abubakar ..Idan har kabar Ameenatu ta wahala a duniya daga ni har ita sae Allah ya tsayar damu ya mana hisabi ....Wata takarda ta fito da ita daga jikkarta ta daura mashi saman motar ta juya sannan tace ....Duk lokacin daka shirya daukarta ka nememu ta nan Abubakar ....Bata jira cewarsa ba ta haye adaidaitar da ta kawota ....</p><p> </p><p> </p><p> bata isa gida ba sae wajen sha biyu na dare ....gidan kaka ta wuce ta buga masu gidac...cikin bacci Meena taji bugun gidan da yake bata da tsoro ta fito ta tsaya jikin kofar tace ..</p><p> </p><p> waye ke bugawa kamar barawo ...baka ga gidanmu bane ...to mugu idan ma kudin adashe na kazo nema to ban amso ba ...</p><p> </p><p> Ki bude Ameenatou ....</p><p> </p><p> Mama kene ...hala wani abu mugun babansu Luba ya maki ..kema dae Mama kawae kice ya fitar maki daga gida ...</p><p> </p><p> Ameenatou nace ki bude ko ....ta fada da karfi ..</p><p> </p><p> Da sauri ta bude tare da tsayawa tana kallonta ...amma mama banga wani ciwo a jikinki ba ....</p><p> </p><p> Shiru tayi ta shigo tare da rufe gidan da sauri ...kaka ta tada ...ta kalleta a dan tsorace tace ...Rabi lafiya da wannan daren hakan ? ...</p><p> </p><p> Da Sauki dae ...daga kaduna nake ...ta fada tana kallon meena dake zaune ta kura mata ido. .</p><p> </p><p> Gurin wa kika je kaduna yanzu rabi ...</p><p> </p><p> Gidan Abubakar Gwaggo can naje ..na tuna mashi da amanarshi ...na kasa Hakura gwaggo ko taimakeni ...idonta ya kawo ruwa. .</p><p> </p><p> Da sauri meena ta matsa tare da dafa mamanta tace ...Mama Shi Abubakar din zai taimaki babansu luba ya sakeki ne ? ...</p><p> </p><p> A a Ameenatu babanki ne ..shine mahaifinki ...ta fada da sauri ..</p><p> </p><p> taba baki tayi ..su babana manya ni bana sonshi ..mai kamshine komae nawa...babana baya sona bai taba zuwa ya dubani ba ..amma mai kamshi yana sona ..ni bani da wani baba ...</p><p> </p><p> Kina da Ameenatu babanki yana sonki karfinshi aka fi ....ta fada hade da dafa ...</p><p> </p><p> Ba wani Mama ...baya sona ...nima bana sonshi ...ya taba zuwa ya kaini makaranta kamar yarda babansu sauran kawayena yake kaisu ...ko ya taba man kayan sallah ...Duka ba Ma'aruf yake man ba ...shike kaini makaranta idan an koroni ya har goyani yake idan ina kuka ya man komae ...shi kadae na sani arayuwata cikin maza ...sae ke da kakata ...kawae ki bar maganar babana ....kwanciya tayi bata sake cewa komae ba ...</p><p> </p><p> </p><p> °°••°°</p><p> </p><p> Meenatou ...ya Fada Ahankali ...</p><p> </p><p> Rufe idonta tayi sannan ta bude ...</p><p> </p><p> Bara ki amsa ki ...ko bakya jina ...ya kara fada ahankali ..</p><p> </p><p> Yaushe ka dawo ...ina son na ganka Mai kamshi ..dan Allah ka dawo ...ta fada cikin kuka ....</p><p> </p><p> duk ya rude bai taba jinta ahaka ba koda take mashi kukan ya dawo kullun ba irin wannan kukan bane ...na yau yasha banban dana kullun ...asalin kuka take mashi mai shiga zuci ....</p><p> </p><p> Zan dawo Meenatou ...zan dawo gobe kinji ko ...kiyi shiru please Meenatou nima na so nazo na kara ganin inga ya kika zama Meenatou ....Kiyi Hakuri gobe zan dawo ...ya fada cikin lallashi ...</p><p> </p><p> Da gaske Mai kamshi ...ta fada cike da doki ...</p><p> </p><p> Da gaske Meenatou..kin tuna Ranar da zamuje gidan Mama dake ...ya fada cikin wasa ...</p><p> </p><p> Uhm na tuna Mai kamshi ..ina lissafawa shekara 3 da sati 5 yau ...ta fada tana murmushi kamar yana ganinta ...</p><p> </p><p> sae da yayi dariya sannan yace ...kin tuna abunda kika fadawa kaka. ..</p><p> </p><p> Aa ban tuna ba ...ta fada a hankali. ..</p><p> </p><p> ya shafi sajensa yace ...a wancan ranar Meenatouta ta fadawa kaka cewa ta fira kirgar dangi ..to na tabbata ...</p><p> </p><p> da sauri ta kashe wayar tare da rufe fuska ...Mamansa na ganinta tayi murmushi tace ...aa su mamana an fara kunya kenan .</p><p> </p><p> </p><p> </p><p> Wayar ta kara ringing amma har ta tsinke bata dauka ba ....text ya turo ...dan lokacin Meenatou na js one. .kuma babu abunda ba zata iya karantawa ba ...</p><p> </p><p> _Please Meenatou ki daga wayan baran sake cewa komae ba_</p><p> </p><p> reply ta mashi tace ... _Uhm Uhm sae da safe Maikamshi_</p><p> </p><p> Yana ganin text din yayi murmushi sannan ya tura mata </p><p> </p><p> _Wow Meenatou ta fara hankali ...am Very Happy na kusa Furtawa Meenatou Sirrin Zuci ..._</p><p> </p><p> tana karantawa ta yi murmushi tare da mikawa Mamanshi wayan ...kin karba tayi tace mata. ...</p><p> </p><p> Jeki da Ita mamana taki ce ..dama bari mukayi ki gama primary sannan ....</p><p> </p><p> tsaye tayi rike da wayar ta kasa koda motsin kirki ....</p><p> </p><p> °°••°°</p><p> </p><p> Babansu Luba ya shigo cikin dakin tare da nunata da hannu ....Dan Iskanci Rabi shine kika wucemu shekaranjiya ko gaisuwa babu ...sannan ma da zaki fita ubanwa kika tambaya .....</p><p> </p><p> Ganin bata kulashi ba ya saka yace ...kuma ki shirya Musa yace yana bukatar matarshi nan da wata biyu ..kije ki sanar da innarki ku shirya duk abunda ake bukata na samo masu gida a kauye ...acan zasu zauna don bazan cuci yaro ba ace sae nan da wasu shekaru zai tare da matarshi ...tunda har ya nuna yana bukatarka ...don haka kuje ku shirya ni na gama koma ....</p><p> </p><p> </p><p> bata ce mashi komai ba har ya karaci fadanshi ya tafi don kanshi ....</p><p> </p><p> </p><p>*Feedohm💞*..</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI .....</p><p> </p><p> 💞</p><p> </p><p> Na Feedohm 💞</p><p> </p><p> </p><p> 25 to 26</p><p> </p><p> </p><p> Tun da asuba Meena ta bar gida ...inda take adashen kudin taranta ta nufa ..tana zuwa ta karbo kudinta sannan ta shige wani shago ....shinkafa ta sawo dan kwati ....Tare da gwangwani biyu na wake...Cefane tayo tare da namanta na dari biyu ...</p><p><br /></p><p> Wani karamin littafi ta dauko tana karantawa ...alalan shinkafa tayi kokarin yi tare da miyar wake. ..ba laifi tayi kokari don duk inda bata ganeba zata ruga da gudu gidansu Ma'aruf ta tambayo mamanshi. ...ta dawo ...nan da nan gida ya fara kamshi ...bayan ta gama ta dauko wasu kwanukan kaka sababbi ta zuba ....sannan ta kai markaden kunnun aya ta hada mashi ...kaka ta gwada mata yarda zatayi har ta gama ..duk kwadayi irin na Meena bata ci ko yankar nama ba .....</p><p><br /></p><p> Wanka ta shiga tayi ...wannan karon wankan gaskia da gaskia tayi ...tana shafa vasline Ma'aruf yayi Sallama ....wata kara tayi tare da fitowa da gudu ta makalleshi ....</p><p><br /></p><p> tsigar jikinshi ta tashi yar. ...don daga ita sae zani .....kokarin zameta yayi cikin wayau don gani yake yanzu yana iya daukar zunubi indae zaya yarda ta dinga hade jikinsu. ...</p><p><br /></p><p> Galala ta tsaya tana kallonshi ...lumshe ido yayi a hankali...hakan ya kara mata damar kare mashi kallon ...</p><p><br /></p><p> a hankali tace ...Mai kamshi ya zama ba indiye .....</p><p><br /></p><p> Uhmm Meenatou fa ? ...ya tambayeta ....tare da kura mata ido ...</p><p><br /></p><p> murmushi tayi sannan ta dauko tabarma ta shinfida mashi ...tana fadin ..</p><p><br /></p><p> Mai kamshi Allah yasa dae yadda na bar surutu kaima kabar cin zalin .....</p><p><br /></p><p> Ya zauna yana fadin ...ayya Meenatou har yanzu baki bar surutu ba .....</p><p><br /></p><p> Da gaske na daina ...yanzu Allah idan na rantse har kaka na yarda ....ta fada tare da shigewa daki ..</p><p><br /></p><p> Kaya ta sanyo sannan ta fito. ..lokacin har ya mike zaya tafi ....</p><p><br /></p><p> Bata fuska tayi tana kallonshi ....murmushi yayi yace ...zan koma gida Meenatou ko tsayawa banyi na gaisa da mama na fito ....</p><p><br /></p><p> Cikin shagwaba tace ...uhm uhm ni dae ban yarda ba ...</p><p><br /></p><p> Ido ya lumshe. .Meenatou kin canja komae ya canza daga gareki Sossae ...kyanki ya fito kamar bake ba Ameenatu ....</p><p><br /></p><p> Nidae ka zauna dan Allah ....ta fada a hankali ...</p><p><br /></p><p> yanzu zan dawo .....mamaki sai ganin hawaye yayi a idonta. ..</p><p><br /></p><p> Ya Salam ....ya fada a hankali ...Meenatou wallahi yanzu zan dawo ..</p><p> </p><p> To ka cire takalminka kaje kadаwo ...</p><p><br /></p><p> Na tafi ba takalmi Meenatou ...ya fada a hankali..</p><p><br /></p><p> To muje tare sae mu dawo ....ta langwabe kai ...sallama yayi da kaka sannan suka tafi ...</p><p><br /></p><p> ••°°••</p><p><br /></p><p> Wallahi Abubakar koda rana daya ka sake man maganar Rabi ..to zan daga maka nono ...Ta fada a fusace ...</p><p><br /></p><p> Kuka ya fashe dashi tare da dafa guiwarta ta yarje mashi yaje ya dauko Meena amma fir ta kiya daga karshe tashi tayi ta bar mashi Falon .....yafi Awa zaune gurin ...duk lokacin daya bude ido Rabi yake hangowa tare da jinjirar diyarta lokacin da take kuka zasu rabu ...hannu ya saka ya share hawayen tare da fadi. ...Allah sarki diyata ina sonki ...Hannu ya daga Sama yace ...Ya Ubangiji Allah ka saukar da zuciyar Mahaifiyata na karbo diyata na nuna mata gatan da baa taba gwadawa wani shi ba Allah ka kare man Aminatu Ya Allah .....hawayen dake idonshi suka idasa fitowa ...ko yaya Aminatu ta koma. ...ya fada tare da mikewa shima. .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ••°°••</p><p><br /></p><p> Baki ta turo tana fadin ...wae mai kamshi babansu kausar ya bani dog (kare) amma kaka tace bara na karbo ba ...wae mala'inkun rahama basa shiga gidan dake da kare ....</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi yace ...to kiyi hakuri mana Meenatou ...</p><p><br /></p><p> Kafada ta make sannan tace ...To Dan Allah mai kamshi ba idan na tara karnukan da yawa ba sae ka dauko man mota ba na kaisu lagos a saya a bani kudin ....kuma banda bakin ciki irin na kaka ba sae na ajeshi a zaure ba ....idan mala'ikun sunyi niyar zuwa ko ta katanga ba sae su diro ba...tunda katangar gidan mu ba irin taku bace ...ko na baka ka aje man ? ....</p><p><br /></p><p> Dariya ya sake sossae tare da mikewa ya dauki hanky dinshi ....gam ta rike hanky din tana kallonshi ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ki saki Mana Meenatou ....ya fada a hankali ..</p><p><br /></p><p> Uhm uhm. ..ka bari na wanke maka wallahi na iya ..kuma da kyau zan wanke maka ....ta karbe hanky din daga hannunsa ....</p><p> </p><p> girgiza kai yayi tare da sanya takalmi yana fadin ....Idan kaka ta gama baccin kice mata nazo muyi bankwana amma zan dawo ...</p><p> </p><p> Da gaske dae komawar zakayi Maikamshi ...ta fada kamar zatayi kuka ...</p><p> </p><p> Meenatou ba mungama wannan maganar ba tun dazu ...nace maki saura 1yr na gama na dawo baki daya ..mu zauna tare mu rayu a tare ko Meenatou ...karkiyi kuka kinji ko .....ya rike hannunta yana kallon cikin idonta ...</p><p> </p><p> kanta ta sadda kasa tana kokarin hade hawayen dake neman zubo mata ....kwantar da kanta tayi bisa cikinsa tana shakar kamshinsa ....</p><p> </p><p> Ji yayi wani sabon lamari na neman hargitsa mashi tunani ...yayi saurin janyeta tare da ficewa daga gidan</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm*💞</p><p>.</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ......</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>27 to 28</p><p><br /></p><p> </p><p> Zaman dirshan tayi gurin tare da hade kai da guiwa tana kuka .....</p><p><br /></p><p> Haka shima tunda ya koma gida kasa samun natsuwa yayi ...wani zafi zuciyarsa ke masa ..har Mamanshi sae da ta mashi magana amma yace mata bakomae ....</p><p><br /></p><p> Kwanciya yayi ...yaki hada komai ...sae da Mamansa ta shigo dakin da kanta ta hada mashi jikkanshi ...lokacin Abba na cikin mota yana jiranshi .....</p><p><br /></p><p> Bayan sun gama bankwana da Mamanshi sannan ya shiga gidan kaka da sauri. ...</p><p><br /></p><p> kaka na tsaye tana kwashe shanya ...tace ..Ma'aruf ba dae Tafiyar bace ko ...</p><p><br /></p><p> Murmushin yake yayi yana raba ido cikin gidan tare da fadin ...Har ma mun fito Kaka ...ina Meenatou ? ..</p><p><br /></p><p> Meenalle ...ta kwala mata kira ....amma shiru bata amsa ba ...aje kayan dake hannunta tayi ta leka daki amma bata ciki ....dawowa tayi tana kwala mata kira shiru duk gidan ba inda bata leka ba amma Ba Meenalle. ..tayi mamaki sossae don tasan bata aiketa ko ina ba ...sannan lokacin data fito ta ganta tsugunne tana kuka ....</p><p><br /></p><p> dawowa tayi inda ta barshi tana taba hannu ...tace...kaga Ma'aruf wallahi bata gidan bansan inda ta tafi ba ....</p><p><br /></p><p> Wani abu ya tokare mashi kirji ...duk irin daurayi irinta Ma'aruf sae da yaji hawaye na neman zubo mashi ...</p><p>Lumshe ido yayi tare da ciro wani karamin abu mai shape din heart da envelope daga cikin jikkarshi ya daurawa Kaka bisa hannu tare da fadin ...Na Meenatou ne Kaka....ya fice kamar kwae ya fashe mashi a ciki.....</p><p><br /></p><p> Yana fita aka bude mashi mota ya shige ba tare da ya juyo ba ko sau daya ...daga karshe ma kanshi ya daura saman cinyar Abba ...</p><p><br /></p><p> Tana daga bayan gidansu tun da taga ya Shiga gidan kaka tasan tafiya zayayi dole ...ta rabe jikin bango tana kuka ita kadae. ..har fito ya shiga mota tana kukan ...tana ganin an tada motar ta fito da gudu tana kuka da karfi ...motar tabi da gudu .....tana daga hannu. ...</p><p><br /></p><p> Karo tayi da mutun da yasaka dole ta tsaya daga bin motar ......</p><p><br /></p><p> Tsinka mata mari yayi tare da fizgarta yayi gidan kaka da ita ....bata dago bare tasan wanda ya mareta ...kuka take har idonta ya bushe ....</p><p><br /></p><p> Suna shiga gidan kakar mutumin yayi wurgi da ita tsakar gida ...da sauri kaka ta fito daga daki tana kiran lafiya kuwa ...</p><p><br /></p><p> Turus tayi ganin musa cikin gidanta ....Meenalle ta kalla gefe guda kwance a kasa idanuwannan sunyi jawur da fuskar .....da sauri ta matsa tare da dagota </p><p><br /></p><p> Meenalle ina kika je. .me ya sameki Meenalle ....ta fada duk ta rude ...</p><p><br /></p><p> Ma'aruf dina ya tafi kaka. ..ya kuma tafiya ya barni ...kaka kice mashi ya dawo dan Allah ....ina Sonshi Kaka ....ina so ya zauna tare dani ...ta rungumeta tare da fashewa da wani sabon kukan</p><p>Kiyi Hakuri Meenalle zaya dawo kinji ko ...dan Allah ki bar kukan karki karya man zuciya nima ...ta fada lokacin da itama idonta ya kawo ruwa. ..</p><p><br /></p><p> Kutmar uban can ...kina matana kina son wani don Uwarki. ...musa ya fada da karfi ...</p><p><br /></p><p> Ba Meenalle ba har kaka sae da ta firgita suka dago suna kallonshi .....ya nuna Meenalle da hannu yace. ....Ki tashi muje dan Uwarki tun kafin na maku shegen duka ku duka biyu. ....</p><p><br /></p><p> Meenalle ta kalli kaka tace ...da gaske yake kaka ....</p><p><br /></p><p> Rashin amsar data bata yasa ta dan fahimci wani abu ...don tasha ganin ana yiwa kananan yara aure a kauyensu Kaka lokacin da sukaje wani biki tun ma kafin ta kai haka </p><p><br /></p><p> </p><p> Kaka ta nunashi da hannu ...Kai Musa ko ubanka bai isa ya nuna man hannu ba bare kai ...</p><p><br /></p><p> Gurin Meenalle ya nufo da sauri kaka ta tareshi ...hannu ya saka cikin rashin imani ya buge tsohuwar tare da jan Meenalle kamar kayan wanki ya fice daga gidan ....</p><p><br /></p><p> Duk mai adaidatar daya tsayar baya tsayawa sae da kyar ya wani ya tsaya ya shigar da ita sannan ya shiga ....</p><p><br /></p><p> Kuka kawae take ...amma ba kukan abunda ya mata ba ...aa kukan dukan da yama kaka da kuma kukan rashin Ma'aruf. ....</p><p><br /></p><p> Ba gidan Malan sani ya wuce da ita ba aa tasha suka nufa ...</p><p><br /></p><p> Duk abunda yake kallonshi kawae take ita kadae tasan abunda ke ranta ....yana cewa ta shiga mota ta shige babu matsala ....</p><p><br /></p><p> wani gari aka ajesu ...sae da suka hau mashin sannan suka shiga kauyen .....wani karamin gida mai cike da jamaa yan tarar amarya suka nufa ....tun daga kofar gidan ta gane danginsu Babansu Luba ne don daga ganin hancinsu zaka gane ...</p><p><br /></p><p> Ji tayi ana ga amaryar musa ....ta kuwa kalli gefenta taga sae washe baki yake. . </p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>SIRRIN ZUCI.....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>29. to 30</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Duk abunda suke kallonsu kawae take har kowa ya watse ya barta ita kadae ....</p><p><br /></p><p> Dakine da tabarma shinfide sae tukunyar ruwa ...zoben dake hannunta take murzawa ta kurawa kofar ido ...zuwa can ya shigo sae uban wari yake ...tayi saurin goge hawayenta tare da maida hannunta baya ....</p><p><br /></p><p> Gefe ya zauna ya kura mata ido yana washe baki yace ...Meena an kawo maki tuwo ko ...</p><p><br /></p><p> Harara ta balla balla mashi tace aa ...Babansu Luba aka kawo man ...</p><p><br /></p><p> da yake sakarae ne bai san darajar iyayenshi ba sae washe baki yayi yace ...Danshi dai yanzu yazo ...ya matso kusa da ita ...</p><p><br /></p><p> Matsawa tayi tana hararanshi tace ...bansan iskanci wallahi.. kai musan nan dama dan iskane ...ta murguda baki. ...</p><p><br /></p><p> Tashi yayi ya cire riga ...ta kalli kirjinsa duk da yanzu ta bar cizo amma ba abinda zai hana ta cije wannan shegen ba ....ta fada a ranta. ..</p><p><br /></p><p> kafin ya ankara tayi kukan kura ta fada saman jikinshi ai kuwa ya fada kasa ya bugu ....ta dankara mashi cizo ta saka hannu ta murde abun fitsarinshi da karfi .....wani kara ya sake don tabbas yaji azaba sossae ...</p><p><br /></p><p> Tana ganin ya fita hankalinshi ta mike da gudu ta fice daga dakin ...</p><p>Lokacin da ya dawo hankalinshi ya fara nemanta yana sabbatun Sae yaci Uwarta ...babu inda bai duba amma bai ganta ba. ...</p><p><br /></p><p> Meenalle tana cikin gidan kuma duk neman da yake tana kallonshi bayan wani rumbu. .....har ya gaji da neman ya koma daki ....</p><p><br /></p><p> Nan gurin tayi baccinta ....tun da asuba kuwa ta farka ....ta leka dakin yana kwance kamar gawa.... alwala tayi tayi sallah ...sannan ta fita ta debo kaikayin gero ta zo ta zuba mashi ruwa ta koma ta sheka mashi ....kamar aljana kafin ya gama hauka kaikayin ta koma inda ta kwana ta lafe .....</p><p><br /></p><p> Sae da safe sannan suka hadu. ... ya bita zaya daka yana zagi ...ta kuwa fice daga gidan da gudu .....shima binta yayi amma ya kasa kamota dole ya kyaleta amma ya dauki aniyar duk lokacin daya kamata sae ya mata dan uban duka. ...</p><p><br /></p><p> Bata dawo ba sae dare ...lokacin tayi kawaye yara da yawa kamarta ....tare sukayi wasa sannan tabi wata gidansu taci abinci ....kasancewar kauyen scattered ne shi yasa ba kowa ya san kowa ba ...wani gidan ma bara kayi tunanin akwaeshi cikin garin ba ...don tafiyace ba karama tsakanin gidajen ....</p><p><br /></p><p> Tana dawo ...ta leka dakin ta make murya tace ...Kai Shege Musa .....</p><p><br /></p><p> ya taso kamar mahaukaci amma kafin ya fito har ta boye inda ta kwana ....bai ganta ba ...haka ya karade gidan har ya hakura. ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Bayan kaka ta mike gidansu Musa ta nufa tarad da Malan Sani kofar gida ....duk abunda ya faru ta fada mashi amma sae ce mata yayi ai matar musa ..kuma yana da ikon ya kaita duk inda yaso ...</p><p><br /></p><p> Tana jin abinda ya fada ta shige cikin gidan ta sami Rabi zaune bama tasan abunda ke faruwa ba ....ta hauta da fada ta inda ta shiga ba tanan ta fita ba ...sannan ta fada mata har da dukan da musa ya mata ....</p><p><br /></p><p> Ran Rabi idan yayi dubu ya baci ...fita tayi ta samu Malan sani a zaune ...</p><p><br /></p><p> Ina kuka kaiman diyata Sani ...ta fada cikin tsawa ...</p><p><br /></p><p> Mijinta ya dauke abunshi ..ko bada saninki akayi auren ba ne ? ....shima ya fada cikin harguwa. .</p><p><br /></p><p> A ranan dai anyi ba dadi tsakaninsu ...sae ranar ya fahimci wacece Rabi sannan zata iya komae akan diyarta ...dan cewa tayi ma sae ya saketa amma fur yaki sakinta ....</p><p><br /></p><p> Bata koma gidan ba taja hannun kata suka bar unguwar ...babu irin neman da basuyi wa Meenalle ba amma babu labarinta ...hakanan suka hakura suka dawo ....</p><p><br /></p><p> ••°°••</p><p><br /></p><p> Ma'aruf duk wani kuzarinsa ya tafi kullun ka ganshi cikin damuwa yake ...duk yan matan dake juyi gabanshi yanzu sun shiga taitayinsu don sun gane jiran kowa yake yaci mashi mutunci. ....</p><p><br /></p><p> Abokanshi kuwa sunyi tambayar duniya kullun amsa dayace ....karsu dameshi .....mutun daya kawae yasan labarin Meenalle .....</p><p><br /></p><p> Yau ma kamar kullun ya kira Mama ..yace ta bada wayar akaiwa Meenalle ....</p><p><br /></p><p> Cikin lallashi tace mashi ..An kai Meenalle boarding school .....</p><p><br /></p><p> Tunda ya yanke wayar ya fitar da sim din bai kuma kiran wani ba a nigeria. ...Su Abba sunyi neman duniya amma wayar bata shiga ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm*💞.</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>31 to 32</p><p><br /></p><p> </p><p> Watansu Biyu da aure amma Musa duk ya kare yayi baki dama abunka ga bakin ....fitinar meenalle ta bi ta dameshi kullun da irin muguntar da zata mashi sannan sau daya ya taba kamata ya daketa ...shima ya wahala gurin dukan don duk sae da ta yakuceshi ta cijeshi .....shi bai ma daketa ba kamar yadda ta wahalar dashi .....</p><p><br /></p><p> Sannan ma duk ta gama zubar mashi da mutunci ga mutanen kauyen ...duk gidan da ta zauna bata da labari sae nashi dana ubanshi ....daga inda zata ce Babansu Musa dan iskane yara yake wa iskanci a garinsu sannan kuma dan cacane ...alhalin bata taba ganin yana iskanci ba ..gara ma cacar ta fadi gaskia ....</p><p><br /></p><p> Idan kuma ta shiga wani gidan sae tace Babansu Musa barawo ...don tsabar karya irinta meenalle har cewa take ya taba dirawa gidansu Maikamshinta ya sace masu jarkar mai ja....</p><p><br /></p><p> Haka idan ta kuma shiga wani gidan su kuma tana iya ce masu ...Musa Mijinta dan iskane su yi kaffa kaffa da yaransu ....</p><p><br /></p><p> Mutanen kauyen duk sun yarda don sun tabbata meenalle bara tayi masu karya ba a tunaninsu. ...</p><p><br /></p><p> Idan kuma Labarin kirki ya tashi ...to labarin mai kamshine ...wani sa'in ta fadi gaskia wani sa'in kuma har da karya. ..duk kauyen ba wanda baisan Maikamshin Meenalle ba ...haka ba wanda baisan yana da taurin bashi ba</p><p>Har labarin irin ciwon da taurin bashi ya sake mashi ba sae da taba yan kauyen ...</p><p><br /></p><p> Lokaci guda tayi farin jini a kauyen kowa sonta yake ...duk inda ta gifta sae kaji ana Meenallen Maikamshi ...sae ta washe baki....haka mamanta da kakarta kowa ya sha labarinsu ....har fada masu take ...kakarta da tana da wani buje duk ya yage ...ita ta sace bujen ta yarda don ta gaji dashi .....</p><p><br /></p><p> Musa kuwa duk wanda ya ganshi da yaronshi to zaiyi kokarin ganin ya raba su</p><p>Don kar ya bata masu yara ...kauyen ya isheshi .... yaje har gida ya fadawa Malan sani halin da yake ciki ...</p><p><br /></p><p> Rufeshi yayi da fada akan shine ya kyale Meenalle ...amma amsar da ya bashi ita tayi matukar girgizashi ...don ce masa yayi ...yana matukar son Meenalle ....</p><p><br /></p><p> Yafi Minti ashirin kafin yayi magana.. . yace mashi to yayi hakuri zaya sake nema mashi wani gida acan kauyen dangin uwarshi ....haka ya koma gida jiki a salube. ....</p><p><br /></p><p> Amma yana zuwa kofar gida yaja burki don ganin Meenalle ta tara mashi yara sun cika gidan wae yan kwana ta debo yara sunfi Ashirin ...dole ya zauna kofar gida anan yayi bacci ....</p><p><br /></p><p> Da Allah ya taimakeshi yaran duk suka koma gidajensu zasuyi kalaci ....ya shiga gidan jiki a sabule ya sameta sae wanka take tsakar gida ta saka karamin siket duk ya jike ya bi mata jiki ...ta dan fara kirgan dangi ga kuma hips da take dasu dama can .....tayi jawur kamar baa kauye take zaune ba .....</p><p>Kamar sakarae haka ya zauna yana kallonta har sae da ta gama sannan ta juyo tana kallonshi tare da watsa mashi harara. ...tace ..</p><p><br /></p><p> Kai Musa lafiya kake kallona kai dai mayena ne wallahi .....</p><p><br /></p><p> Bakomae Meenalle ...ya fada da sauri. ..don bala'in tsoronta yake tare da sonta yanzu ..</p><p><br /></p><p> Tabe baki tayi ta shige daki ....ta sanyo kaya sannan ta fito ta zauna kusa dashi tana washe baki .... </p><p><br /></p><p> Tace ...Musa bani hamsin ...</p><p><br /></p><p> haka ya ciro yana kyarma ya mika mata ...ta fice tana mashi ....awara ta saya taci sannan ta shige gidan kawayenta suka fito wasa .....</p><p><br /></p><p> ••°°•• </p><p><br /></p><p> Kaka da kanta ta koma gidan Alhaji Abubakar amma sae aka ce mata an kwantar dashi asibi ...haka ta dawo bata samu ganinshi ba ...don ta tabbata shi kadae zaya iya kwatarma Meenalle Yan'cinta ......</p><p><br /></p><p> Abban Ma'aruf ma da kaka ta fada masu da cewa yayi zaya shigar da kara ...amma wani amininshi ya bashi hakuri tare da lallabarshi ...indae ya shigar da kara to duniya zata dauka yana son kashe auren ne don Ma'aruf ya aureta ....haka ya suka hakura amma basu yarda Ma'aruf ya sani ba ...kawae sun barta a cewa Meenalle ta tafi boarding school ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Feedohm💞*</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI ....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Ban ma san me zan fada ba ...am speechless wallahi ...duk irin godiyar da zan maku bara ta gamsar dani ba na fahimci kun yarda da ina tare daku ....Nagode sossae Allah ya bani ikon faranta maku ...ina yinku sossae ...Thanks For your support and cares .....08066598868 Shine real number na ta yanzu wadanda ke fadar bana masu magana wancan number da suke messages na bar amfani da ita ..*</p><p>💞</p><p><br /></p><p>33 to 34</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Haka Musa ya tattara kayanshi da Meenalle suka koma kauyen Ruhogi can cikin zariya .....acan ma Meenalle cikin Kwana kadan ta zama yar gari ....kasancewar gida daya suka zauna da dangin Uwarsu musa ....</p><p>Cikin wata biyu zaman ruhogi ya fi karfin Musa ..ga kuma wani bala'in son meenalle da yake ...ko mi tayi mashi baya iya ko da mata maganar banza ne ....abunda ta fada a wancen garin sae ma ya zama wancen garin da suka baro yafi mashi dadin zama ...dan a ruhogi cewa ta dinga yi ko rosu akayi saboda Musa dirawa yake gidan matan aure yana kwartanci ...sanna ga muguwar satar awaki da yake masu ...har cewa take wae ya dira gidan maigari ya shiga dakin amaryarshi mai garin ya saka aka mashi mugun duka ...sannan abincin mutane yake sacewa idan sun aje a waje kafin su shigar dashi gida ....</p><p><br /></p><p> Fitinar Meenalle ta isheshi dole ya tattarota ya maidota gidan malan sani ......</p><p><br /></p><p> Ranar da suka dawo garin kuwa. ..kafib keftawar ido suka nemi Meenalle suka rasa ....gidan kaka ta koma ...acan ta iske Mamanta da kaka zugum ...</p><p><br /></p><p> Ranar sunyi murna sossae da ganinta ...rabi ta rungumeta tana tambayarta rayuwarta ...bata boye masu komae ba ta basu labari ..sunsha dariya sossae sannan duk wani takaici dake zuciyarsu sae da ya fita ...don ko ba komae sun tabbata Meenalle ba inda zata shiga a cuceta ....</p><p>Daga nan gidansu mai kamshi ta shiga ...ta tarad da ba kowa gidan sun tafi Umara su duka ...sannan Ma'aruf kuma bai dawo ba ...haka ta dawo tana share hawaye ...anan gidan kaka ta kwana ...</p><p><br /></p><p> Tun da Safe sukaji sallamar mutane ...Kaka ta fita tana binsu da Kallo ...ko baa fada mata ba tasan Malan Sani da dansa ne suka dauko masu yan Sanda ...</p><p><br /></p><p> Ta kallesu tace ...Bayin Allah Lafiya kuma ...</p><p><br /></p><p> Wani daga cikinsu yace ...idan munje office kunyi bayani ....</p><p><br /></p><p> tace to Allah ya kaimu lafiya ...ta shiga ta dauko hijabi ...tare suka fito da Rabi da Meenalle ......</p><p><br /></p><p> a Police Station akace wae ana tuhumarsu da sacewa musa mata. ....daga kaka har rabi kasa rufe baki sukayi saboda maki ...</p><p><br /></p><p> Meenalle ce ta kwashe da dariya tace ...ni ba wanda ya saceni ...Musane yace na je gurin kaka wae zai sa babanshi ya rude saboda a yana binshi bashi. ....</p><p><br /></p><p> Dan Sanda ya kalli dayan yace mata. ..Kece Meenalle ...</p><p><br /></p><p> Ta daga mashi kai tana washe baki. ...yace. .kece matar tasa. ....nan ma daga mashi ...</p><p><br /></p><p> Tace. ..haka nima naji ana fada. ..amma kasan ko ..ina kazar nan da ake sawowa amare to ni ko ita baa bani ba ...kai ko kumshi ma baa man ba. .ina dae jin wannan auren na irin su shegu Musa ne. ....</p><p><br /></p><p> ya Kalli Rabi yace zasu iya ganin Uban Meenalle ....</p><p> </p><p> aa tace mashi. .....sae gasu musa sun shigo .....nan dae aka bawa musa matarshi sannan aka ce su kaka su koma gida. .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ••°°•• </p><p><br /></p><p> Alhaji Abubakar na zaune a office dinshi ...babban amininshi Alhaji Sadee ya shigo ....ya dade tsaye yana kallonshi kafin ya dafa kafadarshi....</p><p><br /></p><p> Alhaji Abubakar wae lafiya kake kuwa. ....</p><p><br /></p><p> Gumi ya goge sannan ya dago idanuwanshi sunyi jawur yace ...ba komae Sadee ..</p><p><br /></p><p> Zama yayi saman kujera yace ...A tunani Abubakar yanzu mun zama daya ....duk wata damuwarka ni ya dace na santa. ..ka dubi girman Allah ka fada man meye Matsalar. ...Sirrin zuci ...baya da wani amfani har sae an fito dashi an warwareshi .....</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi ...nan take ya fada mashi duk abunda yake faruwa dangane da diyarshi tilo da mahaifiyarshi ta hanashi dauka ..sannan yanzu yarinyar na bukatar taimakon Mahaifinta. ....</p><p><br /></p><p> Ajiyar zuciya yayi sannan yace. ..lallae Abubakar kana cikin damuwa. ..amma me yasaka tun farko baka fada. man ba ?</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Feedohm*💞</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>35 to 36</p><p><br /></p><p> </p><p> Shin Abubakar Aminatu ba jininka bace ? ...ya tambayeshi cikin natsuwa </p><p><br /></p><p> Tabbas Jininace Sadee kana sane ko da hajiya ta sakani auren Lami bamu taba samun haihuwa ba sannan ba kwanciyar hankali nake samu ba ...babu kwanciyar Hankali ina kake tunanin samun zuri'a ...</p><p><br /></p><p> In Kuwa Aminatu jininka ce to tabbas itama tana da hakki akanka ba mahaifiyarka kadae ba. . Abubakar dole mubi umarnin Mahaifanmu indae bai sabawa Musulunci ba ....shin barin diyarka kana tunani baka sabawa Allah ba ...tunda aka haifeta ka taba zuwa ka ganta. ..kana sane da cinta shanta tufafinta yana wuyanka ....</p><p><br /></p><p> Shiru Abubakar yayi sae uban gumi dake kyeto mashi ....</p><p><br /></p><p> Sadee ya cigaba da cewa ...Aminatu Diyata kamar yarda take diyarka ...bani address din Aminatu zanje ni na daukota na riketa kamar yarda na rike Ahmed da Mus'ab ....zan daga darajarta har sae mahaifiyarka ta hankalta ....</p><p>Sannan ba zan baka Aminatu ba har sae mahaifiyarka ta rokeni akan hakan ...inaso wannan ya zama sirrin zuci ...daga ni sae kae sae matata .....</p><p><br /></p><p> Tabbas duk abunda Sadee ya fada gaskia ...Aminatu nada Hakki mai girma gareshi ....Takardar da Rabi ta bashi ya laluba ya mikawa Sadee .....bai ce mashi komae ba ya fice daga office din ....</p><p><br /></p><p> kasancewar dare ya kusa ya saka ya koma gida ...acan ya sami matarshi Mai suna Saadiya ya fada mata komae dangane da matsalar Amininshi ...</p><p><br /></p><p> Mace ta gari. ...nan take ta goya mashi baya tare da bashi karfin guiwar abunda yake shirin aikatawa .....</p><p><br /></p><p> Tun da Safe suka shirya tare da Babban danshi Mus'ab suka nufi garin su Meenalle ....basu sha wahala ba suka gane gidan Malan Sani ....nan sukayi parki g Mus'ab ya fita daga cikin motar .....</p><p><br /></p><p> Meenalle na tsakar gida tana ta uban bala'in Malan Sani yacewa Mamanta yar iska .....malan na duke bai ce mata komae ba har sae da ya gama alwala sannan ya nade babbar riga ya biyota da gudu ...ta kuwa kwaso a guje. ..a bakin kofa tayi karo da Mus'ab dake ta faman sallama .....tureshi tayi ta wuce da gudu ...ya bita da kallon ....</p><p>...</p><p><br /></p><p> Gidan kaka ta nufa ....a hanya ta tsaya ta gama wasanta sannan ta wuce ...tana shiga gidan taja birki tana fadi ...</p><p><br /></p><p> Kai Aljani bakae ne na baro gidansu Luba ba ....</p><p><br /></p><p> Mus'ab da tunda yaga yarinyar ta kwanta mashi a rai ...yace ..bayan wasa kika tsaya a hanya ...</p><p><br /></p><p> Kilbibi ...ta fada kafin ta gaida Alhaji Sadee dake ta faman kallonta ....</p><p><br /></p><p> sannan ta kalli Mus'ab tace ...to mujiya sae a daina kallona kuma ko ....ta murguda baki ...</p><p><br /></p><p> Murmushi ya sake mata yace ....Meenalle da alama kina da dadin zama</p><p>Ta shige daki abunta ...Alhaji Sadee bai boye komae ba ya fada masu komae dangane da yadda sukayi da Alhaji abubakar......nan da nan ya kirashi a waya sukayi magana da kaka ...dan. Rabi cewa tayi bara ta amshi wayar ba ...</p><p><br /></p><p> Kaka ta kira Meenalle ta fada mata zaa tafi da ita ...amma kememe taki yarda sae tayi bankwana da Ma'aruf idan ya dawo sannan suzo zata bisu ....da lallashi sannan ta bisu ....</p><p><br /></p><p> Suna tafiya Musa na zuwa yazo daukar matarshi ...kallon banza suka mashi sannan sukace ya duba inda ya ganta ya dauka ...daga karshe ma kaka bori tayi tace sae ya fito mata da Meenalle ...haka ya tafi jiki ba dadi ....</p><p><br /></p><p> </p><p> *Feedohm*💞</p><p>SIRRIN ZUCI......</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>37 to. 38</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ina Labarin Ma'aruf ....Bai kuma kiran iyayenshi ba har sae da ana saura kwana biyu ya dawo ...shima magana dayace ..shin Meenatou sunyi hutu ta dawo gida ....</p><p><br /></p><p> Abba yace. ..aa Ma'aruf Mamana bata dawo ....</p><p><br /></p><p> Abba ka fada man gaskia. ..kodae Meenatou ta rasune kuke boye man ...idonshi ya ciko da kwallah ..</p><p><br /></p><p> Calm down Ma'Aruf Meenatou bata rasu ba kaji ko ...yaushe zaka dawo ...</p><p><br /></p><p> Jibi Abbah ...ya fada tare da kashe wayar ....</p><p><br /></p><p> Raliya ta dafa mashi kafada tare da tausasa murya ...What wrong Ma'aruf .....ta langwabe kai</p><p>Fuskarta ya kalla sannan ya kalli kafadarshi ..da sauri ta janye hannunta daga jikinshi tare da zama bisa kujeran dake facinng dinshi...</p><p><br /></p><p> Ta kura mashi ido har tsawon mintina sannan ta sauke ajiyar zuciya ..tace. ..Ma'aruf please meke damunka ...</p><p><br /></p><p> ya juyar da kai gefe guda tare da fadin ...Tashi kije Raliya ....</p><p><br /></p><p> Haba Ma'aruf tafiya fa zamuyi atleast ka tsaya muyi magana da. girman Allah ...</p><p><br /></p><p> Ido ya lumshe tare da mika mata wayarshi ....drop your number zan nemeki ....</p><p><br /></p><p> Wani dadi taji don ta dade tana jiran wannan rana sae yau Allah ya bata ...jikin kyarma ta karba tare da saka mashi number. ....</p><p><br /></p><p> Thank you Ma'aruf you completed my life....am very happy ....ta fada dauke da murmushi ...</p><p><br /></p><p> Idonshi ya lumshe ya nuna mata hanya ...amma ta tsaya tana fadin ...please Ma'aruf muyi pictures mana ...</p><p><br /></p><p> To the hell of you and ur bullshit pic ....ya fada cikin tsawa tare da nuna mata hanya ...</p><p><br /></p><p> Haka ta wuce tana waigenshi ...</p><p><br /></p><p> _Raliya Saad yar nigeria ce cikin garin kaduna tazo karatu india itama tunda ta kyalla ido taga Maaruf take binsa bai taba tsayawa ya mata magana in ba yau ba Raliya irin matannan ne Yan bariki duk abunda take so sae tayi yarda tayi ta sameshi ...Yar guntuwa ce ..sae dae tana da hips amma ba irin cikkakar matan nan bane ..haka tana da gashi dae dae gwargwado amma duk da haka tana karawa dana doki ..sannan farace tas da ita ...tana dauke da kananan ido kamar yar china_..</p><p><br /></p><p>================= Gidan Novels =====================</p><p>°°••°°</p><p><br /></p><p> Su Meenalle tun da aka sauka gidan Alhaji Sadee take washe baki ganin gidan mai kyau ... Hajiya Saadiya ta mata tarba mai kyau ..kamar ita ta haifeta ...</p><p><br /></p><p> Suna zaune bayan mangrib Alhaji Abubakar yayi sallama ya shigo ...tunda ya shigo yake kallon Meenalle. ..har dae ta kasa hakuri ta matsa kusa da Hajiya Saadiya tare da zungurinta ....</p><p><br /></p><p> Lafiya Meenalle ...ta fada tana kallonta</p><p><br /></p><p> Bata fuska tayi tace ..to tunda na zama yar gayu ba sae adaina ceman Meenalle ba ....ta kifta ido ..</p><p><br /></p><p> Tayi murmushi tace to yaakae Aminatu. ...</p><p><br /></p><p> Baki ta washe tare da nuna mata Alhaji Abubakar tace ...Kinga wancan sae kallona yake da idanuwanshi kamar na magen gidansu kausar... oh na manta ban baki labarin kausar ba ko ...Haba Itama kawata ce in gaya maki kullun mamarsu Idan tana girki sae ta barbada wani abu a ciki ...ai ko nace zan fada wa babansu kausar sae ta bani naira hamsin tace kar na fada ..in gaya maki da kaka ta aikeni na yarda kudin sae naje gidansu kausar din nace zan fada tana barbada magana....rannan da naje ta bani kwakwa da dabino tace dan Allah kar na kuma zuwa gidansu ...sae nace mata to na tafi ....</p><p><br /></p><p> Hajiya tayi dariya tana kallon Alhaji Abubakar ..sannan tace mata ...Ni kam naga kamar kuna ma kama Meenalle ...</p><p><br /></p><p> Kai ta juyar tana fadin ...ki nemi Meenalle. .....Sanna ta kurawa Alhaji Abubakar ido tace ...Kuma kamar da gaske dan dae shi kamar yana shafa jan baki ..shi yasa lebenshi yayi ja ....ni kuma nawa hink ne ....kinga na fishi haske ..wae bashine yazo nema gurin Wancen ta nuna Alhaji Sadee .</p><p><br /></p><p> tace ...tashi ki matsa ki gaidashi ....</p><p><br /></p><p> Ta mike ba gardama ta isa gurinshi </p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI ......</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>39 to 40</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Maimakon ta gaisheshi ...sae lekewa tayi gefen fuskarshi tace mashi ....Ka daina kallona ni matar musan gidansu Luba ce ...kasan waye Musa ? ..</p><p><br /></p><p> Girgiza mata kai yayi ...tace ..Kai yanzu duk girmanka baka san Musa ? ..Uhmm to Dan Mijin Mamata ne. ..In Gaya maka Sunan babanshi Sani wae sae ace in dinga jin kunyarshi ni kuma nace bazan ji kunyar ba ..kasan me yasa?...</p><p><br /></p><p> Nan ma girgiza kai yayi tare da kamo hannunta ...tayi saurin janyewa tana hararanshi ...sannan tace ...</p><p>Ranar jumaa mamansu Luba tayi alala ...kasan Mayen alala ne ..aiko ya ci sossae ya dinga banka mana tusa mai shegen wari ..nima kasan cikina ya kumbura naje zanyi kashi haba can naji babansu Luba yana zawo da karfi ...aiko tunda lokacin na daina jin kunyarshi</p><p>Dariya ta bashi sossae ...gata kyakyawa da ita sannan ga surutu da saurin shiga rai ....ya dade tana bashi labarin musa. ..amma sam ya kasa yarda da zancen wae an mata aure ...haba ubanwa ya isa ya aurar man diya tana karama ...ya fada a ranshi .....sannan ta zuba mashi labarin mai kamshi sossae ...ayadda take bashi labarin yaji yana son ganin yaron ...don har zoben da ya bata sae da ta nuna mashi ....</p><p><br /></p><p> Dan zaman da yayi da ita ta shiga ranshi sossae sae wajen karfe Sha daya na dare sannan ya tafi ...shima sae da Sadee ya mashi da kyar sannan ya tafi ....cike da kewarta ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ••°°••</p><p><br /></p><p> Mus'ab ya shigo rike da ledar chocolate ..Meenalle na zaune saman carpet da duwatsunta tana yar carabke ...</p><p><br /></p><p> Ya samu guri ya zauna yana kallonta tare da mika mata ledar ta amsa tana kallonshi tace ...Kai dae Mayenane Allah ...dan kawae kana samo man chocolate da yanzu na maka rashin kirki ....</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi mata yace ..har kin iya wani rashin kirki ....</p><p><br /></p><p> Harara ta balla mashi tace. ..kai Malan ni mai kamshi kawae nake kyalewa a garinmu. ..</p><p><br /></p><p> Wae waye wannan mai kamshin Meenalle ...</p><p><br /></p><p> Baki ta washe ..ta fito da zoben dake hannunta tace ...Shi wata irin zuciya gareshi ..ka ganta nan shi ya cirota tana ta jini shaaa...ya saka man a hannu sannan ya saka wani abu ya kulle hanjinshi dashi don kar ya fado kasa ...abun gwanin ban tausayi ......</p><p>ta mayar da zobenta a hannu....</p><p>Ni kuma kasan me na bashi ? ...</p><p><br /></p><p> Ya girgiza mata kai yana murmushi ....</p><p><br /></p><p> Nima zuciyata na bashi amma ni da reza na cirota tana ta jini sae da aka kaini asibiti fa .....nasha wahala sossae kamar zan mace ...ranar da ya tafi ko ..ranar Shege Musa ya daukeni .....</p><p><br /></p><p> Tayi dan karamin tsaki ta mike tsaye. ...nina yi tafiyata tunda ko sannu bara kace man ba ...ta shige dakin hajiya saadiya. .....</p><p><br /></p><p> Kwanciya yayi saman carpet din tare da rufe idonshi yana murmushi</p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°•• </p><p><br /></p><p> Ranar da Ma'aruf ya dawo kamar zayayi hauka daya samu labarin wae an wa Meenalle Aure ?,...Abunda ya dinga maimatawa kenan ....Shin waye Meenalle ta aura ....Bata san yana mutuwar sonta ba ....kuka ya dinga yi ..kamar karamin yaro ...a ranar ya tsani duk wata mace .....</p><p> </p><p> Abba da ya fada mashi sae da yayi dana sanin fada mashi da yayi .....</p><p><br /></p><p> Tun safe ya bar nigeria ....Ya koma india ...don bara ya iya cigaba da rayuwa a gurin ba </p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ......</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>41. to. 42</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Meenalle zo ki mikawa Mus'ab Wannan jug din....Momma ta fada ..</p><p><br /></p><p> Da gudu ta amsa ta shige part dinshi ....yana ta game abinshi ta dire mashi saman cinyarshi ...sannan ta bi falon da kallon ....</p><p><br /></p><p> Hannunta ya janyo ya zaunar da ita barinshi ....Me kike kallo .....</p><p><br /></p><p> Tabe baki tayi tace ...wani gulma na gani ...</p><p><br /></p><p> falon ya bi da kallo sannan yace ...ina kika gani ..</p><p><br /></p><p> wani frame ta nuna tare da fadin ...in ba gulma ba komae na dakin maikamshi sae ace sae an kwaikwaya ....</p><p><br /></p><p> fuska ya bata don ya gaji da labarin Ma'aruf Yace ...Karki kuma man maganar maikamshi anan ...</p><p><br /></p><p> Harara ta balla mashi tace ..don kasan ya fika kyau? ..</p><p><br /></p><p> Cikin tsawa yace ...zan bata maki rai wallahi kika kuma fadin sunanshi anan</p><p> </p><p><br /></p><p> Baka sonshi ne don ya fika tsada? ..ta fada a hankali. .</p><p><br /></p><p> Eh bana sonshi ....shima ya fada ...</p><p><br /></p><p> Idonta ya ciko da kwallah ..sannan ta fara tafiya da baya da baya zata bar dakin ....har ta kai kofa ta tsaya tare da fadin ...Karka kuma man magana ba ruwana da kai ...nima bana sonka ..Bana Sonka tunda baka son Maikamshi .. ....ta fice da gudu tana kuka .....</p><p><br /></p><p> Da sauri ya bi bayanta ....a corridor ya tarad da ita ta hade kai da guiwa tana kuka ...tsugunnawa yayi ...</p><p><br /></p><p> Meena ....ya kira sunanta a hankali ...</p><p><br /></p><p> Banza tayi dashi ....lallashinta ya cigaba dayi amma bata kulashi ba ...so take yace yana son mai kamshinta amma shi ya kasa .....</p><p><br /></p><p> ••°°•• </p><p><br /></p><p> School bag din dake hannunta ta yarda a kasa tare da dukewa tana kallon Momma .....</p><p>Mus'ab ya shigo falon yana ganinta duke yayi sauri zubewa gabanta ...Meena me ya faru .....</p><p><br /></p><p> Momma na zauna tana kallonsu bata ce masu ķomae ba don tasan Halin Meenalle. ..</p><p><br /></p><p> Duk ya rude yana tambayarta amma taki bashi amma ....kamar ya mata kuka ganin yanayinta ya canza ..Please Meena Meke damunki ...</p><p><br /></p><p> Sae da taga dama sannan ta dago tana hararanshi tare da fadin ...Kaini karka dameni ...</p><p><br /></p><p> Ya kwantar da murya . .ba damunki zanyi ba Meena kinji ...fada man zakiyi abunda ke damunki ...</p><p><br /></p><p> Kaini ciwon ice Cream ke damuna .....ta fada tana turo baki ...</p><p><br /></p><p> Mtss ya saki tsaki tare da mikewa. ....takaicin tsakin ya sakata ta fashe da kuka. .....yayi sauri dawowa yana fadin ...tashi ki cire unifoam dib kizo muje</p><p>Bai rufe baki ba ta mike da gudu ta fada daki ....bata fi minti Goma ba ta fito sanye da doguwar riga da karamar hijab ....</p><p><br /></p><p> Hannunsa ta rike ...Suka fice ...</p><p><br /></p><p> </p><p>Ice cream ta kwasa a gurin tare da chocolate kala kala ...sannan suka dawo gida ...bakin gate din gidan tace ya tsaya ....ta fice ta shige wani gida dake facing dinsu ...binta kawae yayi da kallo har ta rufe kofar sannan ya shiga gida ...</p><p><br /></p><p> Tayi Sallama yafi biyar amma ba wanda ya amsa mata... dage labulen falon tayi ta shiga ...mutane zaune a falon da alama magana suke ....</p><p><br /></p><p> ta tsaya tsakiyarsu tana kare masu kallo...wata yar budurwa da ta kasa daurewa tace mata ...Ke lafiya ...</p><p><br /></p><p> Harara ta watsa mata tare da kara yin sallama da karfi ....</p><p><br /></p><p> Wae lafiya ko bakya da hankali ne .....budurwar ta sake fada tare da tasowa ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Bata kulata ba ta sake yin Sallama ....wata daga cikinsu ta amsa sallamar ...sannan Meenalle tace ...Ni makarantarmu an hanani kula wanda bai amsa sallama ba ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI.....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p>43. to 44</p><p><br /></p><p> </p><p> wata tace amma bai hanaki shiga gidan mutane ba ..? ..</p><p><br /></p><p> Kallonta tayi ..itama budurwace tana kwance jikin wata daga ita sae bra da pant. ...</p><p><br /></p><p> Ido ta waro sannan ta sake kallon wadda ke tsayen itama duk uwar darin ce.... duka yan matane gidan su kusan 8 amma babu mai kayan kirki. .</p><p><br /></p><p> Miyau ta hade ta samu guri ta zauna tsakiyar tafalon sannan tace ...Ina Mamanku ...</p><p><br /></p><p> Wata daga cikin yan matan ta taso ta zauna kusa da ita tare da dafa ta tana kallonta .....sannan tace ...Ya sunanki ...</p><p><br /></p><p> Keni sunana Meenalle a garinmu anan kuma Meena ...Maikamshi kuma yace man Meenatou ...kinsan duk yafi iya fadin sunana ...shi kuma wancen kilbabben yace man wae Sweet Meenah. ..kinsan ai kilbabben da nake nufi ko?</p><p>Hannunta ta kama tace .. meenah ...</p><p><br /></p><p> Harara ta balla mata ...tace wancen Mayen nawa fa ..ai mayena ne Allah ...ke ni dae bara na tafi ...dama zuwa nayi naga ko zan samu kawa ..sae na ga kuma duk baku sa kaya yan iskane ....ta mike ...</p><p><br /></p><p> Da Sauri ta janyota ta fado jikinta ...tare da matseta a kirjinta...nan da nan idonta ya canza kala ta saka hannunta cikin pant din Meena tana shafata. .</p><p><br /></p><p> Hannun Meenah ta buge tana kokarin kwace kanta. ...amma ta kasa .....kuka ta sake mata tana zaginta tare da kai mata duka amma duk abanza ....</p><p><br /></p><p> Wata ta taso tace. ...Ruky meye haka ki kyaleta bana so ...</p><p><br /></p><p> harara ta sake mata ...ina sonta ne ...</p><p><br /></p><p> Nifa. ...ta tambayeta a fusace ...</p><p><br /></p><p> Idan na gama da ita zanji dake ...ta fada ta shiga ba da shafa. ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Duk falon ba wanda ya kulata kowa harkar gabanshi yake ....daga karshema budurwar daukar meenalle tayi ta shigar da ita daki ta rufe dakin ta cire mata kaya tsaf ...ta dura mata wani abu a baki ....tun daga lokacin Meenalle bata kuma sanin inda take ba ...har sae da ta gama Shafeta tsaf tare da daukarta pic sossae sannan ta fito dakin ta rufota ...</p><p><br /></p><p> °°••°°</p><p><br /></p><p> Mus 'ab kuma tunda ya shiga gida hankalinshi ya ki kwanciya don basu harka da mutanen wancen gidan ...bama su san juna ba...amma wani sashen na zuciyarshi ya tuna mashi Meenalle face ..kila ma ta dade da sanin mutanen gidan sae kawae ya aje mata kayan da suka sawo a dakinta ya shige dakinshi ya kwanta. ...</p><p><br /></p><p> Bata Farka ba sae kusan Laasar ...jikinta ta duba babu kaya wani miyan wahala ta hade tare da share hawayen da suka zubo mata ...ita dae taji seniors na fadin lesbian ...amma bata taba ganin anyi ba ..</p><p>To ko shine wannan ...ta tambayi kanta ...aiko baza manta ba Ustaz ya taba fada masu duk wanda ke lesbian baya shiga aljanna</p><p><br /></p><p> Hawayen ta share ta saka kayanta sannan ta fito har lokacin suna zaune ....tana fitowa budurwar ta taso tana fadin </p><p><br /></p><p> Baby har kin tashi .....</p><p><br /></p><p> Bata ce mata komae ba ta rabe ta fice daga falon ....kwado ta gani sagale jikin kofar ta janyo kofar da sauri tare da rufesu ta baya .....ta tafi da keys din ..</p><p><br /></p><p> Bata fadawa kowa ba abunda ya faru ...haka bata kuma bin ko ta kofar gidan ba ....tun daga lokacin ta hankalta da shiga duk gidajen unguwar .....</p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Dafe kanshi yayi tare da lumshe ido ...Again Raliya ForGod sake me ya kawoki gidan infact me ma ya maidoki nan kasar bayan kin tafi..</p><p><br /></p><p> zama Tayi tare da goge hawayenta ....Ma'aruf Kaine ka maidoni ...bazan iya rayuwa babu kai ba ..Ma'aruf dad dina baya lafiya...amma na baroshi nazo gunka please ka amsheni </p><p><br /></p><p> Tausayi ta bashi don yana ganin yarda take son dade dinta kuma ita kadae ce dashi ....ya lumshe ido tare da zama a kujeran dake facing dinshi ..Me ya sameshi ...ya fada a hankali ....</p><p><br /></p><p> Paralysis ya kamashi ....</p><p><br /></p><p> Ya Salam Raliya ..Allah ya bashi lafiya ...amma raliya ki fahimceni bawae nayi rejecting naki ba san raina ..wallahi Zuciyata tuni tana gurin Meenatou ..ko da na aureki bazan baki farinciki ba ...</p><p><br /></p><p> Na yarda Ma'aruf indae zan zauna dakai. ...please wacece Meenatou zan zauna da ita ka hada mu ...</p><p><br /></p><p> Kinga Meenatou can ...ya nuna mata wani frame dake makale jikin bangoshi ....</p><p><br /></p><p> Sauri tashi tsaye tayi tana nuna Photon. ..Waccen Yarinyar ce Meenatou da kake fada ....waccen yar iskar yarinya ...</p><p><br /></p><p> Tsawa ya daka mata ....Tare da nuna mata hanya ...fice man daga gida ..</p><p><br /></p><p> Indae akan waccen yarinyar ce wallahi sae ka rabu da ita ...komae nake so duniya sae waccen shegiyar yarinyar ta kwace man ...bazata yiyu ba wallahi ...wannan karon bazan bar maki ba ....</p><p><br /></p><p> Ta fice daga gidan da sauri ..mota ta shige ta fizgeta da karfi ta bar unguwar ....</p><p><br /></p><p> </p><p> *Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💧💧SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>45 to 46</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Dome Hotel din da suke zaune ta nufa. ..Ruky na kwance bisa gado tare da Precious. ..tajanye mayafin da suka rufa dashi ..</p><p><br /></p><p> ...Ruky muga phone dinki please ....ta fada da karfi</p><p><br /></p><p> Idonta na rufe ta lalubi Phone din ta mika mata ...</p><p><br /></p><p> amsa tayi ta koma falo tana bincikar wayar ....Gallery ta shiga ta fara scrolling pictures din dake cikin ....</p><p><br /></p><p> Murmushi tayi tare da marking din pictures din da take bukata ta tura a tata phone din sannan ta mayar mata ...ta sake fitowa ..</p><p><br /></p><p> Gidan Ma'aruf ta koma ...falo ta iskeshi ...yana ganinta ya mike kamar zaki yayo kanta</p><p>Uban me kika zo nema Kuma. ..ya fada lokacin daya shakare mata wuya ....</p><p><br /></p><p> Da kyar ta mayar da numfashi tare da mika mAta mashi wayarta .....da kyar ta buda baki tace ka duba ciki zaka Meenatou ..</p><p><br /></p><p> Sakinta yayi ya amshi wayar ...jikinshi ya fara kyarma ganin photon Meenalle tare da wata babu kaya jikinsu .....</p><p><br /></p><p> Karya kike raliya ...Ba Meenatou bace forcing dinta akayi ....Why ...ya fada da karfi ...</p><p><br /></p><p> Wayar ya tandara da kasa tare da sulalewa gurin ...ko'ina jikinshi kyarma yake ...da hannu yake nuna mata kofa amma taki fita ...kasa controlling kanshi yayi ya mike tare da shakaranta ....sae da kyar ta samu ta kwaci kanta ta fice da gudu ...</p><p><br /></p><p> .kamar mahaukaci ya fara wurgi da kayan dake tsakiyar falon yana kuka ....</p><p> </p><p> Why Meenatou .... ..Me yasa haka . ...rayuwar da nafi tsana fiye da komae. ...Rayuwar da karuwa mai bin maza ta fiku daraja ....shin bara ki barni da bakin ciki daya ba Meenatou...sae kin hada man da wannan mummunan rayuwa ba kyasona Meenatou ....Me yasa kika bari na tsaneki Meenatou? ....na tsaneki Meenatou ..na tsani duk wata mace yanzu. ....haka ya dinga sabbatu shi kadae. .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Alhaji Sadee ya dauki Meenalle kasancewar Weekend ne ..gidan Mahaifiyar Abubakar ya nufa da ita. .kasancewar ta sanshi sossae ya saka ta amsheshi hannu biyu ....</p><p><br /></p><p> Ina ka samo wannan kyakykyawar yarinya haka tubarkallah ....ta fada tare da janyo Meenalle ta zaunar da ita gefenta ...</p><p><br /></p><p> Alhaji Sadee yayi murmushi yace. ..Diyar Kanwata ce Hajiya shine na daukota ...</p><p><br /></p><p> Meenalle ta kalleta ...gata dae tsohuwa amma taci kwalliyarta. tace ...tsufa dae yayi shawagi ...ni Kakata bata abun yara amma ke tsohuwa dake kin shafa jan baki ....</p><p><br /></p><p> Sadee ya tashi yace bara yaje ya dawo zaya bar Meenalle anan ....tace mashi to ...</p><p><br /></p><p> Tunda ya tafi take ta mata uban surutu kamar dama sun saba ....nan da nan tashiga ranta ...sae bayan isha'i ya dawo ya dauketa kamar karta tafi haka hajiya taji ...don cewa tayi ya bar Meenalle amma yace tayi hakuri zaya dinga kawota suna gaisawa ....</p><p><br /></p><p> Ranar koda Alhaji Abubakar ya shigo gaidata ...sae da ta mashi firar Yarinyar da Sadee ya zo da ita ....uhm kawae yace mata. ....</p><p><br /></p><p>Duk bayan kwana biyu Sadee zaya sauki Meenalle ya kaita gidan Hajiyar Abubakar. ...</p><p><br /></p><p> Sannu sannu shakuwa ta shiga tsakaninsu sossae wanda in har aka dade Meenalle bata je gidan Hajiya ba to da kanta zata taso tazo ta ganta ta koma ....</p><p><br /></p><p> A lokacinne Hajiya ke fadawa Abubakar tana Shaawar yarinya kamar Meenalle ...har take fada mashi ..da yanzu Aminatunshi tana nan da takae kamar Meenalle ko ta fita ...</p><p><br /></p><p> Cewa yayi shima bai sani ba .....</p><p><br /></p><p> Akwae lokacin da tace mashi ko dae zaya nemi Rabi ya karbo diyarshi don tana bukatar ganin jinin danta ..tunda har yanzu bai kuma samun Haihuwa ba ...</p><p><br /></p><p> Nan ma ce mata yayi bai san inda suke ba ....</p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>47 to 48</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>°°••°°</p><p><br /></p><p> Kwanci tashi ba wuya har Meenalle ta gama Secondary school ...</p><p> Alokacin ne Mus'ab ya fara nuna mata abunda ke ranshi ...amma fur taki yarda ...har ta manta da wani aure a rayuwarta ...duk wata zaa kaita garinsu gurin su kaka da mamanta har lokacin mamanta bata koma gidansu Musa ba ....haka Musa ya kasa Hakura da Meenalle kullun cikin bala'i yakewa ubanshi ya nemo mashi matarshi ...su duka hankalinsu ba kwance ba ...</p><p><br /></p><p> Wani zuwa da tayi har bangazar musa tayi amma sam bai ganeta ba ...don kwata kwata ta canza hutu da jin dadi sun canzata. ..bara ka taba cewa diyar hausawa bace</p><p>Duk zuwan da zatayi sae ta shiga gidansu Ma'aruf haka zaa ce mata baya nan sannan babu mai numbershi tunda ya tafi bai nemi kowa ba ...haka zata ci uban kukanta har ta taho ...</p><p><br /></p><p> Shima mus'ab kokarin cusa kanshi yake amma hakan bai samu ba ......</p><p><br /></p><p> Lokacin da waec and neco. ta fito a lokacin Alhaji Abubakar ya ce zaya fitar da ita kasar india karatun lawyer ....Alhaji Sadee ya yarda don har lokacin bata san waye ubanta ba ....</p><p><br /></p><p> Cikin saa ta samu Visa cikin sauri ...Su biyun suka kaita indiya tare da mika amanarta gurin wani lecturer amininsu dake can ....</p><p><br /></p><p>°°••°° </p><p><br /></p><p> Batayi wata uku ba ta goge wata wayewa tazo mata ta kara kyau da diri duk wanda ya kallu meenalle alokacin sae ya kuma kallonta</p><p>Kyakykyawa first class ...duk fadin makarantar ba wanda bai san MMA _Meenat Ma'aruf Abubakar_ ...</p><p><br /></p><p> Sun fito daga lecture su kusan Uku a jere ...Shamy ta dauki ihu tare da fadin ....Wow *Mr M*...da sauri suka kalli wani ginin dake kallon makarantar .....</p><p><br /></p><p> Yana rike da glass cup hannushi guda dauke da magzine sannan idonshi sanye da farin siririn glass ....</p><p><br /></p><p> Feena ta daka uban tsalle tana fadin Yaushe ya dawo ...</p><p><br /></p><p> Shamy tace jiya sajan Sadam ke fada man ...Kai *Mr M* ji yanda ya kara uban kyau ....Wallahi Ina mutuwar kaunar ...nayi missing dinshi wallahi.....kissing hannunta tayi tare da Nunashi</p><p><br /></p><p> Sae lokacin Meenalle ta da ido ta kalli wanda suke maganar akae ....</p><p><br /></p><p> Tafi minti ashirin tana kallonshi har sae da soofy ta buga mata littafi a kai sannan ta sauke ajiyar azuciya</p><p>Soofy please meye real name dinshi ....ta fada a hankali ...</p><p><br /></p><p> Tsayawa sukayi suna kallonta cike da mamaki. .....karo na farko kenan da suga Meenalle a wannan yanayin ....kamar tayi kuka tace....Please i need to know ....</p><p><br /></p><p> Shamy tace ...lallae MMA har kin kamu da sauri haka ...ina cika bakin ?...injin yau kin yarda akwae mutumin da yafi Maikamshin kyau ....</p><p><br /></p><p> Please ku fada man dan Allah ...ta kwantar sa murya ...</p><p><br /></p><p> Soofy tace ...kyaji da gulmarki yadda kike da class wancen babanki ne a wannan fannin ...sunanshi *Mr Ma'aruf* .....</p><p><br /></p><p> Ihu ta kurma ta ruga da gudu dakinsu ........</p><p><br /></p><p>Feedohm💞</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI......</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>49 to 50</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Wae Meena me ya sameki kike ta murna ko dae Dady zaya zo .....Shamy ta tambayeta. ..</p><p><br /></p><p> Ido ta waro tare da lumshe ido. . Sirrin Zuci ne ..ba bukatar ku sani .....tana gama fada ta shige toilet ...wanka tayi sannan ta fito ...ta dade tana shafe shafe ...sannan ta dauko wani sabon turare cikin jikkanta ta fesa ta dauko kayan fulani ta saka tare da takalmi mai tsinin ...babu abunda bata saka ba cikin kayan fulani har abunda suke daurawa a kai sae da ta daura ....ta fito ....su shamy suka bita da kallon mamaki har ta fice daga makarantar ...</p><p><br /></p><p> Ba tare da shakkar komae ba ta shige gidan Mr Ma'aruf ....</p><p>.</p><p> Da Sallama ta shige falonshi ....ba kowa ciki sae kamshi dake tashi .....bisa kujera ta samu ta zauna ....ga wani tafkeken hotonshi manna jikin bango a gefen dama. ...tana kara juyawa ta hango abunda ya saka dole fararan hakoranta suka fito ...photon Meenalle ne kafe a gefen haggu anyi rubutu da gold a jiki ...Meenatou ...amma duk ya farfashe..</p><p><br /></p><p> Bata fuska yayi lokacin daya shigo falon ....</p><p><br /></p><p> Me kike bukata ...ya fada lokacin da ya dauki remote ...</p><p><br /></p><p> Shiru tayi tare da kura mashi ido ...jin shirun yayi yawa ya saka ya dago da kanshi .</p><p> </p><p> Suna hada ido yayi saurin janyewa ....</p><p><br /></p><p> Hanya ya nuna mata tare da fadin ...idan kallo ya kawoki ga kofar da kika shigo a bude .....</p><p><br /></p><p> zuwa nayi mu gaisa dakai ...kullun Sae na ganka amma baka taba ko da kulani ba irin dan kallon ma da akeyi a kauda fuska idan an kamaku baka yi man ...ko baka kula mata ?..</p><p><br /></p><p> Ido ya dago yana kallonta sannan ya maida kallonshi ga tv ....</p><p><br /></p><p> Allah sarki ashe magana kadan kake kayi shiru ....ta sake fada a hankali .....wae ma dan rowa ko ruwa bara ka bani ba nazo gidanka...ko ka bani baran karba ba....Mai rowa dae dan wuta</p><p><br /></p><p> Da sauri ya kalli photon Meenalle ..ya tuna lokacin da tazo gidansu ta zauna tana zuba mashi surutunta .. yana rike da ice cream take ce mashi...Gidanku fa nazo Mai kamshi dan rowa bara ka bani ko ruwa ba ..ni bana ma shan abunda kake sha..ko ka bani so daya kawae zan sha ..shima sae kace man please sannan. ...Maikamshi me rowa fa dan wuta ...</p><p><br /></p><p> itama photon ta kalla tare da kallon fuskarshi ...ga mamakinta sae taga hawaye na zuba ....</p><p><br /></p><p> Da sauri ta dawo kujeran dake kusa dashi tana kallonshi cikin rawar murya tace. ..nayi wani abu daya bata maka raine Mr Ma'aruf?..please ka yafe man ...</p><p><br /></p><p> wannan karan ma da sauri ya kalleta ...kije please ..ki tafi ...ya fada a hankali ...</p><p> </p><p>A hankali ta mike ta juya tana tafiya kallo ya bita dashi ...yana ganin zata juyo yayi saurin dauke kanshi ....</p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Har kusan sati daya bata kuma ganin Mr Ma'aruf ba inda yake zama .suna fitowa daga lecture ta ...ta bar su Shamy ta shige gidanshi ...</p><p><br /></p><p> Falo ta zauna tana jiranshi ...amma har kusan minti 39 bai fito ba ...sae dae tana jin nishi sama sama yana fitowa daga dakin dake facing dinta .....tun yana fitowa a hankali har ya fara fitowa da karfi ....zaune tayi tana son taje ta duba kuma tana tsoron ...</p><p><br /></p><p> Jiki ba karfi ta mike tana Sanda ta tura dakin ...Ganinshi tayi kwance kasan tiles ...hannunshi rike da kirjinshi ....da sauri ta ida bude dakin ta dago kanshi tare da daurawa saman kafarta tana girgiza shi ...</p><p><br /></p><p> *Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI.....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>51 to 52</p><p><br /></p><p> Mr Ma'aruf me damunka ...ta fada a rude ...</p><p><br /></p><p> Lunshe ido kawae yake ...ya kasa budesu gaba daya....sannan bakinshi ya kasa furta wata kalma</p><p><br /></p><p> Kuka take iya ranta ..tare da girgiza shi tana kiran sunanshi ....</p><p><br /></p><p> Jin kukan yake cikin ranshi ..sannan so yake ya bude idon yaga wacece amma sam ya kasa ......</p><p><br /></p><p> Ma'aruf ka tashi dan Allah ....</p><p><br /></p><p> Please Ma'aruf ka bude idonka don Allah ka kalleni ...nice Meenallen Maikamshi ..ka tashi bana so na rasa ka wannan karan ....</p><p><br /></p><p> Yana jin Lokacin data fadi Meenalle kokari yake ya bude idonshi ...amma ya kasa ..bakinshi kawae yake motsawa. ..ita kadae ke iya jiyo sautin ..Meenatou ...da yake fada ....</p><p><br /></p><p> Rungumeshi tayi tana kuka ...sannan ta fice daga dakin ganin baya numfashi ta kira security dinshi suka sakashi mota aka wuce dashi asibiti .....</p><p><br /></p><p> Emergency aka shiga dashi ...abu na farko da aka fara bukata shine jini .....Har lokacin Meenalle kuka take .....</p><p><br /></p><p> Amma tana jin ance zaa kara mashi jini ta mike tace a debi nata ...</p><p><br /></p><p> Doctor yace ..Madam baa Fiye dibar jinin mace ba ...amma akwae jinin fresh anan sae a sanya mashi ...</p><p><br /></p><p> Aa Ku debi nawa ku saka mashi na yadda ...ta fada tana kuka. ..</p><p><br /></p><p> Kiyi hakuri ..wanda muke dashi normal yake ...</p><p><br /></p><p> Bana so a gauraya mana jini da na wani ...koda jinina idan kuka diba zaya kare na yarda ki dauka indae Ma'aruf zaya tashi ....</p><p><br /></p><p> Ganin ba yarda zaayi da ita ya saka aka auna nata cikin saa tana da isasshen jinin da zata bashi ...nan da nan aka kwantar da ita gadon da yake kusa da nashi aka diba .....</p><p><br /></p><p> Kafin a saka mashine suka dibi nashi jinin jikinshi aka auna sannan aka kara mashi da na Meenalle ...</p><p><br /></p><p> </p><p> Har 10 dare bai farka ba ...secutity din yace ta tafi zaya kula dashi ...amma hararan data zabga mashi itace amsarshi ....</p><p><br /></p><p> Anan ta kwana ...ganin har da asuba shiru ya saka taje ta samu nurse din tana kuka ta fada masu ...ce mata sukayi karta damu zaya iya tashi ko da yaushe tayi hakuri ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>°°••°°</p><p><br /></p><p> Duk wani test da zaa mashi an gama ...doctor ya kira Meenalle kamar yarda tace mashi ita matarshi ce ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Bayani ya mata mijinta nada Kidney problem ( _Nephropathy_) kuma yayi attacking dinshi sossae dole a saka shi adjoining room zuwa wani lokacin kuma baa bukatar kowa yaje inda yake akwae nurse. din da zasu dinga kula dashi ...idan kuma har lokacin da suka yankar mashi baiyi ba to gaskia sae dae ayi mashi transplant na kidney ...</p><p><br /></p><p> Yarda ta dinga kuka ...shi kanshi likitan sae da yayi nadamar fada mata ...</p><p><br /></p><p> Wata nurse ta tambayi doctor din ko mai ke saurin kawo ciwon ...</p><p><br /></p><p> Rashin bacci na saurin haifawa da mutun ciwon koda ...ke har ciwon sugar da ciwon zuciya duk rashi isasshen bacci na kawosu .....amma indae mutun zaya samu isasshen bacci to lalurar zata iya gushewa ...idan kuma har tayi illar da sae an mata aiki to bayan anyi insha Allah zata gushe ...</p><p>Harta ta ruwa gurbatattu zaka iya daukar ciwon koda ...don haka ya kamata mu dinga kula da rayuwarmun ....</p><p> </p><p> Sannan rashin shan isasshen ruwa ..mussaman lokacin zafi. ...sannan rike fitsari. ..shima yana nakasa koda ...sannan yawan cin gishiri...sannan yawan cin nama shima yana kawo matsalar koda ....haka kuma yawan amfani da magungunan saukaka zafi ko antibiotics ..sanna yawaita shan lemuka masu gas ...kamar coca cola ...lacasera da ire irensu ..</p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Kwananshi 5 A gurin amma ko fardadowa baiyi ba ...duk da an hana kowa zuwa gurinshi amma Meenalle na makale ta glass kullun ...abinci ma sae da likitan yayi mata da gaske take ci ...</p><p><br /></p><p> Maganar makaranta kuwa ta manta da labarinta .....sae a kwana na 6 ne Ma'aruf ya fara bude idonshi ....lokacin tana tsaye inda take zama ta hango yana motsa bakinshi .....</p><p><br /></p><p> Da sauri ta matsa gurin .tare da dafa glass din gurin tana hawaye mai dauke da murmushi ....</p><p><br /></p><p> ..Meenatou ..yake fada a hankali .... Why Meenatou ? Me ya maidoki rayuwa. .ko kinzo kiyi proving abunda kike aikatawa ...Karki kuma zuwa inda nake ...i hate you Meenatou ...Bana son ganinki ...kin cutar da zuciyata da yawa...idan ina ganinki baran iya rayuwa ko kinzo ki kasheni ne Meenatou ..na rokeki karki bari idona yayi tozali dake in dae har soyayyar yarintarki gaskiyane ....hawaye ke bi ta gefen idonshi kamar an bude fanfo ...yayinda da kirjinshi ke sama da karfi</p><p><br /></p><p> Baya tayi da sauri ta jingina da bango ...kanta ya fara juya mata ....</p><p><br /></p><p>*Feedohm*💞</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI.....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p>53 to 54</p><p><br /></p><p> </p><p> Da Gudu ta fice daga asibitin ...dakinsu ta koma ta fada saman carpet tana kuka ....su shamy dake nemanta sukayo kanta suna tambayar inda taje ..ganin ba magana zata masu ba ya saka suka kyaleta sae ta koma ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Bata koma Asibitin ba sae da ta tabbatar ya koma bacci ..sanna taje tana lekenshi tana hawaye ...ji tayi an dafa kafadarta ta juyo da sauri.</p><p><br /></p><p> Ganin Nurse din dake taimaka mashine ya saka ta goge hawayen ...</p><p><br /></p><p> Kiyi hakuri Mrs Ma'aruf ..mijinki zai samu sauki Soon ....</p><p><br /></p><p> daga mata kai tayi tare da share hawayen ...taji dadi sossae ko ba komae yau an kirata da Mrs Ma'aruf .....</p><p><br /></p><p> Murmushi tayi mata sannan tace ..doctor yana bukatar magana dake ....</p><p><br /></p><p> Binta tayi suka shiga office dinshi ...ya zaune da uwayen takaddu gabanshi ....yace ta zauna ....</p><p><br /></p><p> Mrs Ma'aruf nasan dae ke musulmace ..kuma zaki yarda da kaddara mai kyau ko mara kyau. ....</p><p><br /></p><p> Kallonshi kawae take tana hawaye ...so take ya fada mata kai tsaye abunda yake son fada ...amma sae da ya mata waazi da yake balarabene sannan ya fada mata gaskia sae sun wa Ma'aruf dashen koda ..don duk yarda suke tunanin abun ya wuce nan .....</p><p><br /></p><p> Tun da yake maganar take kuka har ya gama sannan yace dole ta kira yan uwanshi domin ciki wani zaya bashi kidney daya ...</p><p><br /></p><p> Meye amfani doctor? </p><p>.komae zaa bukata na yarje a cire nawa indae Ma'aruf zaya tashi ...ko da zuciyata a cire a saka mashi ..Doctor nafi sonshi da kaina a duniya ...ku shirya duk abunda zaa kashe zanje na kawo ...ina so ayi mashi aiki ya samu sauki da wuri ....tana gama fadar haka ta mike tana kuka ...</p><p><br /></p><p> Dady ta kira tace tana bukatar kudi masu yawa ...babu musu ya turo mata 10 million. ..da ta ga kamar bara su isheta ba ta fitar da sarkar gold dinta da Alhaji Abubakar ya sawo mata da wata sallah ...ta sayar naira million 5.5</p><p>Wanshekare da safe ta hada kudin ta kai masu ...naira million 9 kadae suka amsa suka bata sauran. ..ko a ranar sae da doctor yayi encouraging nata aka ta kira wani ko mahaifiyarshi ta bashi wanda baya da wata damuwa a tare dashi ...amma ta saka mashi kuka ...dole suka fara preparing cire tata daya a saka mashi ...duk wani aune aune da yakama suyi sae da sukayi ...suka tabbatar idan an cire tata daya wadda aka barta zata iya fuctioning sossae a jikinta ...sannan aka shiga dasu dakin tiyata .....</p><p><br /></p><p> </p><p> *4 Hours*</p><p><br /></p><p> Aka fito gangaro su sannan aka kaisu adjoining room su biyu aka jerasu ......</p><p><br /></p><p> Ta fishi jin jiki sossae don har sae da ta kwana biyu bata farfado ba ...shi kuwa kwana daya ya farka. ..tana kwance kusa da gadonshi ...ya kura mata ido. ...har doctor ya shigo. ....</p><p><br /></p><p> Ya mashi alluran da ya kamata sannan ya fice don baa cika son a takura masu da magana ba ....</p><p><br /></p><p> </p><p> Ranar da ta farka tana bude ido suka hada ido ...murmushi ya sake mata tare da lumshe ido ...ita murmushin ta maida mashi ..sannan ta kawar da kanta gefe guda ta goge hawayen dake neman zubo mata .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Lokacin da likitan ya shigo ..ya sameta ta farka shi kuma yana bacci ....</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi mata yace ...Congrat Mrs Ma'aruf ...yanzu hankali ya kwanta ya samu sauki ko ...</p><p><br /></p><p> Murmushi tayi ta lumshe ido....a haka ya mata allura ya fice ...</p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Satinsu biyu acikin asibitin suka samu sauki ...sae dae har lokacin suna daure da belt don sae yayi wata shidda zaa cire ....</p><p><br /></p><p> Haka har lokacin Ma'aruf bai san taka maimai wanda ya bashi kidney ba. ..don tun kafin ayi aikin ta roki Doctor din da kar ya fada mashi ita ta bashi ....</p><p><br /></p><p> Meenalle na kwance bisa gado Ma'aruf ya fito daga toilet dinshi sanye da jallabiya ...kallonta yayi dauke da murmushi yace ...</p><p><br /></p><p> Fateema ya jikin ... _kamar yarda ta fada mashi sunanta_</p><p><br /></p><p> Murmushi tayi tace Alhamdulillah....</p><p><br /></p><p> Good ...ga abinci nan an kawo ki tashi kinji ko ...</p><p><br /></p><p> Tashi tazo yi amma ta kasa ...ya matso tare da dagota ta ya jingina ta da kirjinshi kafin ya dauko filo ya saka mata abayanta ya janye jikinshi ...yana fadin Sorry Sister kinji</p><p>Zama yayi yana bata abincin har sae da ta dauke kai sannan ya tashi yayi sallah ....</p><p><br /></p><p> Da yake ya fita lafiya kuma doctor yace mashi tare akayi masu aiki. ..shi yasa yake tausayinta da yaga shi har ya samu sauki amma ita ba wani sauki sossae ....</p><p><br /></p><p> A wani bangaren na zuciyarshi ...yana jinta sossae matsalar ya riga ya saka mata tsanar soyayya ....</p><p><br /></p><p> Idan tana bacci bashi iya dauke idonshi a kanta ...haka idan yana bacci bata iya dauke idonta daga kallonshi ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ana Gobe zaa sallamesu ...doctor ya shigo ....Ma'aruf yayi ta rokanshi akan kar ya bar asibitin sae ya fada mashi wanda ya bashi koda ...</p><p><br /></p><p> Doctor ya saci kallon Meenalle yaga idonta na kanshi ...sannan ya mai da kallonshi ga Ma'aruf ....yace ...gobe zan fada maka ...ya fice ...</p><p><br /></p><p> Yana fita ta bi yanshi ta sameshi da kuka kar ya fada mashi ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yace Mrs Ma'aruf mai yasaka baki san yasan ke kika ceceshi? </p><p><br /></p><p> Bakomae doctor dan Allah karka fada mashi ..</p><p><br /></p><p> wannan ba hujja bace Aminatu ...dole a nuna mashi wanda ya bashi ...</p><p><br /></p><p> Zaa nuna mashi amma bani ce zaa nuna mashi ba doctor</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p>55 to 56</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Me yasa bake ba Aminatu Abubakar? ...sannan wacce kike so a nuna mashi ...</p><p><br /></p><p> Doctor ni zan kawota ..kawata shamsiyya ita nake so ka nuna mashi ..ka taimakeni ...ta fada cikin kuka. .</p><p><br /></p><p> Me yasa to Mrs Ma'aruf?..</p><p><br /></p><p> Wannan Sirrin zuci ne ....</p><p><br /></p><p> Wayarta ta fito ta kira Shamy tace ta zo ta yanzu ta mata kwatancen asibitin da suke .....</p><p><br /></p><p> bata fi 10 mints ba sae gata ...tana zuwa doctor ya mata bayanin abunda suke so tayi ...</p><p><br /></p><p> </p><p>Dadi kamar ya kasheta don dama tana mutuwar son Mr Ma'aruf ..kuma ta tabbata idan aka ce ita ta bashi to babu abunda bara ya iya yi mata ba ....don doki kasa barin asibitin tayi sae da wata nurse tace mata baa kwana ba wani dalili sannan ta tafi ...</p><p><br /></p><p>°°••°° </p><p><br /></p><p> Murmushi ya sake yana kallon Meenalle sannan yace ....yau zan huta da tashin dare da kukanki ..</p><p><br /></p><p> Hararansh tayi lokacin da take neman maida hawayen da suka zobo mata tace ...ni kuma zanyi kewarka ..</p><p><br /></p><p> Nima ai zanyi kewarki Fateema wasa nake maki kinji ko ...karki bari hawaye ya kara fitowa daga kyawawan idanuwannan ..</p><p><br /></p><p> Lumshe ido tayi tace ...Da Zan iya da tuni na tsaidasu Ma'aruf ......</p><p><br /></p><p> Yauwa ga doctor nan ...ya fada lokacin da ya mika mashi hannu ...lokaci guda kuma ya bata rai yana cewa ...ya na ganka kai daya ..tana ina ? </p><p><br /></p><p> Doctor yayi murmushi tare da daga murya yace ...Mrs Ma'aruf ...</p><p><br /></p><p> Da sauri Meenalle ta kalleshi lokacin da gabanta ya yanke ya fadi ...ganin ya kira wata da sunan da ta dade tana mafarki...Sunan da tun tana karama ta so ta amsa sunan ...hawaye suka zo mata. ..tayi saurin Mikewa daga kujeran da take ta juya da niyar ta bar dakin...</p><p>Hannunta taji an rike da sauri. ..ta juyo tana kallon Wanda ya rike mata hannu ....</p><p><br /></p><p> Kanta ta sadda ta kasa cigaba da tafiyar ganin Ma'aruf rike da hannunta. ...</p><p><br /></p><p> Ina zaki Fateema bara ki tsaya kiga wadda ta taimakeni ba ...lokacin da lumfashina ya nemi ya bar jikina dalilin wata?....ya fada yana kallonta</p><p><br /></p><p> Shamy ta shigo taci uwar kwalliya ...</p><p><br /></p><p> Meenalle ta girgiza kai tana toshe bakinta ...</p><p><br /></p><p> Ma'aruf yace ..Doctor baka ga wata yarinya ba Wadda ta kawoni Sunanta Meenatou ..ko ba ita ta kawoni ba ... </p><p><br /></p><p> Doctor ya nuna Shamy yace ..Shamsiyya ce ta kawoka kuma ita ta baka kidney dinta daya ...bansan wata mai suna Meenatou ba anan ...</p><p><br /></p><p> Da sauri Meenalle ta kwace hannunta ta fice daga dakin tana kuka. ...Ma'aruf duk dokin ganin wadda ta taimaka mashi da yake ..sae da ya yunkura zaya bita amma doctor ya tareshi ....lumshe ido yayi duk da ba karan kukan yake ji ba amma yana jin zafin kukanta a ranshi ....</p><p><br /></p><p> Gurin Shamy ya juyo yana mata godiya sae washe baki take</p><p>Yace ...kin taimaki Rayuwata Shamsiyya ..banda bakin da zan gode maki ...amma ina neman Alfarmar ki aureni a lokacin ne zan nuna maki tsantsar godiyar da nake maki ....</p><p><br /></p><p> Mr Ma'aruf. ..ta fada lokacin da take washe baki ...da gaske zaka aureni ...</p><p><br /></p><p> daga mata kai yayi yana kallon gadon Meenalle ...</p><p><br /></p><p> Shi daya kamata ya nuna zakewa amma itace ta nuna zakewa a gurin ...</p><p><br /></p><p> Tare suka koma gidanshi...sae rawar kai take mashi ...kokari yake ya sakata zuciyarshi amma ina ..babu wani babi face na Meenalle ....</p><p><br /></p><p> Sae dare ta tafi shima sae da ya lallabata sannan ...</p><p><br /></p><p> Da safe ya yanki ticket ....sannan ya kira Shamy sukayi bankwana ta bashi address din iyayenta ya tafi akan bara ya dawo ba sae angama maganar komae akansu ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI ....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Godiya ba adadi gareku .....💞_</p><p><br /></p><p>57 to 58</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ina labarin Musa?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da musa ya matsawa Malan sani lamba sae an nemo mashi matarshi ...</p><p><br /></p><p> Malan sani ya rasa yarda zayayi ...gashi abokanshi na bashi shawarar ya shigar da kara don Uwar Meenalle da kakarta su suka boyeta ....</p><p><br /></p><p> Alokacin baida ko sisi ga musa ya addabeshi ...dole ya sayar da gidan da suke ciki _Gidan Rabi_...ya shigar da karar ...</p><p><br /></p><p> Su kaka na zaune tsakar gida aka kawo masu sammaci daga kotu ....</p><p><br /></p><p> Wae ana tunanin sun sace matar Musa ....ana nemansu ranar litinin akotu ...</p><p><br /></p><p> Haka suka shirya suka tafi kotu da safe ...aka karanto masu da karar da akayi akansu ..tare da tambayarsu sun san da zance ...</p><p><br /></p><p> Kakata ta murje ido tace bata san da zancen ba kuma sae an fito mata da diya ....</p><p><br /></p><p> Da Alkali yaga kamar zaa rainawa kuto hankaline sae ya kori karar .</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Da yake akwae kudin gidan sae Malan sani ya daukaka kara tare da daukar lauya ....</p><p><br /></p><p> Lokacin da suka shiga kotun ...anan ne aka rufe kaka don ana tunanin ita ta sace kaka ...aka rufeta sati biyu a sail ....</p><p><br /></p><p> Ran Rabi in yayi dubu ya tashi ...taje har kano tasami Alhaji Sadee ta fada mashi</p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Meenalle tun da ta koma hostel ba abunda take sae kuka ....Friends dinsu sunyi lallashin duniya amma taki kulasu </p><p><br /></p><p> Kwata kwata rayuwar garin ta fita ranta. ...haka shamy bata da Labari sae na Ma'aruf ...wata sa'in idan suna waya sae dae Meenalle ta bar gurin tana kuka .....Sannan taki fadawa Shamy din dalilin da ya saka take hakan ...</p><p><br /></p><p> Sae a hankali sannan ta fara komawa dae dae har ma ta fita lecture ...</p><p><br /></p><p> Da marece ta fito daga lecture ta daga idonta ta kalli benen Ma'aruf kamar yadda take kullun ...suka hada ido ....alama ya mata da ta jirashi yana saukowa .....gurin tayi tsaye kanta na kasa har ya karaso ...</p><p><br /></p><p> Dariya ya sake bayan ya leka fuskarta tare da lakutar Hawayen yakae baki ....Bara naji ko hawayen nada zakine shi yasa basu wahalar fitar ....</p><p><br /></p><p> Murmushi tayi ta saka hannu zata share ...yayi saurin saka hanky dinshi ya share mata yana girgiza kai ......</p><p><br /></p><p> Guri ya samu ya zauna ...yana tambayarta ...Meke faruwa Fateema ...ko har yanzu baki warke ba ....</p><p><br /></p><p> Girgiza mashi kai tayi tare da juyawa bangare guda ....</p><p><br /></p><p> To me yasaka kike kuka ? ...Wani ne ya sakaki kukan? ..ya sake fada a hankali yana leken fuskarta ..</p><p><br /></p><p> Kamar tace Kaine Ma'aruf ...amma ba dama ...sae dae girgiza mashi kai tayi ...</p><p><br /></p><p> To kiyi hakuri kinji Fateema ...bana son ganin hawayenshi ko kadan ...kin koma gida bayan kin warke? ...</p><p><br /></p><p> Nan ma girgiza mashi kai tayi tare da share hawayen dake binta .....</p><p><br /></p><p> Kinci abinci ? ....ya tambayeta lokacin da yake kallon bakinta ...</p><p><br /></p><p> Uhm ...tace mashi ..</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi yace ban yarda ba. ..tashi muje kinji ko ...kamar kin taba zuwa gidana can baya ...kece ? </p><p><br /></p><p> Daga kai tayi tana murmushi ....</p><p><br /></p><p> Hararan wasa ya sake mata yana fadin. ..lokacin kinje kallona ne ko kinje ki saka man ciwon da zamu hadu asibiti .....</p><p><br /></p><p> bata ce komae ba sae murmushin da tayi..wanda har hakoranta suka bayyana</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI ....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Godiya ba adadi gareku ..... Wadanda suka man magana ban mayar masu ba ...su gafarceni ba yarda na iya ne ....💞_</p><p><br /></p><p> *Wannan page din kyautane ga Masu Yara kanana Allah ya raya Mana ku bisa turbar addinin musulunci ya saka masu tausayi da imani🙏🏻*</p><p><br /></p><p>57 to 58</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ina labarin Musa?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da musa ya matsawa Malan sani lamba sae an nemo mashi matarshi ...</p><p><br /></p><p> Malan sani ya rasa yarda zayayi ...gashi abokanshi na bashi shawarar ya shigar da kara don Uwar Meenalle da kakarta su suka boyeta ....</p><p><br /></p><p> Alokacin baida ko sisi ga musa ya addabeshi ...dole ya sayar da gidan da suke ciki _Gidan Rabi_...ya shigar da karar ...</p><p><br /></p><p> Su kaka na zaune tsakar gida aka kawo masu sammaci daga kotu ....</p><p><br /></p><p> Wae ana tunanin sun sace matar Musa ....ana nemansu ranar litinin akotu ...</p><p><br /></p><p> Haka suka shirya suka tafi kotu da safe ...aka karanto masu da karar da akayi akansu ..tare da tambayarsu sun san da zance ...</p><p><br /></p><p> Kakata ta murje ido tace bata san da zancen ba kuma sae an fito mata da diya ....</p><p><br /></p><p> Da Alkali yaga kamar zaa rainawa kuto hankaline sae ya kori karar .</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Da yake akwae kudin gidan sae Malan sani ya daukaka kara tare da daukar lauya ....</p><p><br /></p><p> Lokacin da suka shiga kotun ...anan ne aka rufe kaka don ana tunanin ita ta sace kaka ...aka rufeta sati biyu a sail ....</p><p><br /></p><p> Ran Rabi in yayi dubu ya tashi ...taje har kano tasami Alhaji Sadee ta fada mashi</p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Meenalle tun da ta koma hostel ba abunda take sae kuka ....Friends dinsu sunyi lallashin duniya amma taki kulasu </p><p><br /></p><p> Kwata kwata rayuwar garin ta fita ranta. ...haka shamy bata da Labari sae na Ma'aruf ...wata sa'in idan suna waya sae dae Meenalle ta bar gurin tana kuka .....Sannan taki fadawa Shamy din dalilin da ya saka take hakan ...</p><p><br /></p><p> Sae a hankali sannan ta fara komawa dae dae har ma ta fita lecture ...</p><p><br /></p><p> Da marece ta fito daga lecture ta daga idonta ta kalli benen Ma'aruf kamar yadda take kullun ...suka hada ido ....alama ya mata da ta jirashi yana saukowa .....gurin tayi tsaye kanta na kasa har ya karaso ...</p><p><br /></p><p> Dariya ya sake bayan ya leka fuskarta tare da lakutar Hawayen yakae baki ....Bara naji ko hawayen nada zakine shi yasa basu wahalar fitar ....</p><p><br /></p><p> Murmushi tayi ta saka hannu zata share ...yayi saurin saka hanky dinshi ya share mata yana girgiza kai ......</p><p><br /></p><p> Guri ya samu ya zauna ...yana tambayarta ...Meke faruwa Fateema ...ko har yanzu baki warke ba ....</p><p><br /></p><p> Girgiza mashi kai tayi tare da juyawa bangare guda ....</p><p><br /></p><p> To me yasaka kike kuka ? ...Wani ne ya sakaki kukan? ..ya sake fada a hankali yana leken fuskarta ..</p><p><br /></p><p> Kamar tace Kaine Ma'aruf ...amma ba dama ...sae dae girgiza mashi kai tayi ...</p><p><br /></p><p> To kiyi hakuri kinji Fateema ...bana son ganin hawayenshi ko kadan ...kin koma gida bayan kin warke? ...</p><p><br /></p><p> Nan ma girgiza mashi kai tayi tare da share hawayen dake binta .....</p><p><br /></p><p> Kinci abinci ? ....ya tambayeta lokacin da yake kallon bakinta ...</p><p><br /></p><p> Uhm ...tace mashi ..</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi yace ban yarda ba. ..tashi muje kinji ko ...kamar kin taba zuwa gidana can baya ...kece ? </p><p><br /></p><p> Daga kai tayi tana murmushi ....</p><p><br /></p><p> Hararan wasa ya sake mata yana fadin. ..lokacin kinje kallona ne ko kinje ki saka man ciwon da zamu hadu asibiti .....</p><p><br /></p><p> bata ce komae ba sae murmushin da tayi..wanda har hakoranta suka bayyana</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>59 to 60</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Haka kawae yake jin farinciki idan yana tare da ita ...tare suka jera har cikin gidanshi ...ya dauko mata abinci ..tare da lemon ..sannan ya zauna yana tsokanarta har ta koshi ....</p><p><br /></p><p> Komae nata na burgeshi ...bata tafi ba sae da ta gyara mashi gidan sae kamshi yake sannan ta tafi ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Bayan ta tafi ya kira Shamy ya mata bayanin komae ...yace mata duk wata magana an riga an gamata ...iyayenshi sunje gidansu an kuma bashi ita .....</p><p><br /></p><p> Haka ta koma hostel Meenalle na kwance ta fada kanta sae hauka take ..ta kusa zama matar Mr Ma'aruf ....</p><p><br /></p><p> Kamar saukar aradu Meenalle ke jinta ...har ta gama ta haukanta bata motsa ba ...sae da ta leko fuskarta tace mata ...You're not happy MMA</p><p><br /></p><p> Am very happy Shamy ...Allah ya sanya albarka ...tana gama fadar haka ta fice .....</p><p><br /></p><p> Ma'aruf dinne yazo ya kira Shamy ...tana zaune bisa wani dutsi tana hango su....sae wannan iyayi yi Shamy take .....</p><p><br /></p><p> Dukar da kanta tayi daga barin kallonsu ...motsi taji a bayanta ...ta dago a tsorace ....Ma'aruf ta gani ya harde hannuwa ya zuba mata ido ....</p><p><br /></p><p> Saurin juyar da fuskarta tayi tana kakaro murmushi ...</p><p>Fateema. ..ya kira sunan a hankali ...akwae abunda ke damunki kawae baki so na sani ....</p><p><br /></p><p> Allah ba komae Mr Ma'aruf kawae kaina ke ciwo na fito na sha iska. ..ta fada tana murmushin yake ..</p><p><br /></p><p> A nan zaki huta ...? ..ta so muje na kaiki inda ciwon kan zaya tafi kinji ko ..? ..</p><p><br /></p><p> Shamy ta iso gurin tare da dafa Meenalle tana fadin ...Hubby wallahi mu kanmu bamu san Meke damun MMA ba ...</p><p><br /></p><p> Ido ya waro ..dama kin santa ne ..</p><p><br /></p><p> Yeah friend dinta ce... Shamy ta fada tana murmushi .</p><p><br /></p><p> Tashi muje to kinji ko ...ki bar nan gurin akwae sanyi da yawa kinji ko ...rigar sanyin dake jikinshi ya ciro tare da rufa mata ...sannan Shamy ta dagata suka jero tare ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ma'aruf ..yace su shiga mota bara su tafi a haka ba ...Shamy mai miji aka shige gaba ....ta glass din yake kallon meenalle ...duk wani motsi da zatayi a idonshi take ...yaso ace itace ta bashi kidney don ya masifar tausayin yarinyar ...sannan kallonta yake Meenalle komae tayi burgeshi take ....</p><p><br /></p><p> Wani guri ya kaisu ...ya masu shopping sossae ...aka saka a bayan mota ...sanna ya dauko wasu kananan ledoji guda biyu ...ya mikawa Shamy daya ..ta karba tana godiya ....</p><p><br /></p><p> Sannan ya mikawa Meenalle guda ...ta saka hannun dama zata karba ...ya kurawa zoben dake hannunta ido sannan yaki sakin ledar ....</p><p><br /></p><p> Da Sauri ta janye hannun ta maidasho baya ...</p><p><br /></p><p> Yaso ya ce ta fito da zoben ya gani amma sae wata zuciya tace mashi ba abunda yake tunani bane ...don yanzu tuni zoben yamata Meenalle kadan ...haka ya kauda tunanin zoben a ranshi ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>°°••°°</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Lokacin Alhaji Sadee na tunanin case din karamine ...ko Alhaji Abubakar bai fada mawa ba ...ya shirya ya tafi ...</p><p><br /></p><p> Ranar da sukaje kotun ..Alkali ya tambayi Rabi shin da saninta aka aurar da Meenalle .....</p><p><br /></p><p> Rabi tace eh da saninta aka aurar da Meenalle ..</p><p><br /></p><p> Alkali ya tambaya ..shin ko ubanta ya san da auren ? ..</p><p><br /></p><p> Tace. ..aa ubanta baisan da auran ba domin ba gurinshi ta tashi ba. ...</p><p><br /></p><p> Alkali yace a kira mashi Wadanda aka daura auren gabansu ....babu shamaki malan sani ya kirawo har wanda ya daura auran ...Alkali yace aure ya dauro kuma ba wanda zaya warware auren ba tare da wata kwakwkwaran hujja ba ..</p><p><br /></p><p> Alkali ya nemi a kira Meenalle ...Alhaji Sadee yace sam bata kasar ...</p><p><br /></p><p> Alkali yace to nan da sati biyu a kawo Meenallen ...sannan aka sake kaka suka tafi da ita ..</p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Hajiyar Abubakar ta tasa Abubakar dole sae ya karbo diyarshi don tana bukatar ganin jikarta ...</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi yace shi yanzu baisan inda zai ga su Rabi ba ....sae dae tayi hakuri ...</p><p><br /></p><p> Kuka ta saka mashi amma ya tashi ya fice daga gidan ...</p><p><br /></p><p> Lokacin tayi nadama sossae ...kuma Meenalle ta bar mata son diya mace ...don ta gane Rahamace ...itama so take ta ga jikkarta ko da ace musakace bama mai lafiya ba ...</p><p><br /></p><p> </p><p>*Feedohm💞*</p><p>SIRRIN ZUCI......</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦Talented writers forum💦</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>61 to 62</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Alhaji Sadee ya kira Meenalle yace ta taho gida nan da sati biyu ...</p><p><br /></p><p> Taji dadi sossae ko ba komae dama garin ta isheta ...</p><p><br /></p><p> Ranar ta fito zata tafi asibiti ...taga motae Ma'aruf inda yake ajeta idan yazo gun Shamy ....</p><p><br /></p><p> Hanya ta canza tayi uban zagaye ...ta fice daga School din ...Taxi ta tara ta kaita asibitin ..</p><p><br /></p><p> Tana zaune doctor na mata bayanin yarda zata kula da lafiyarta idan ta koka gida ...kanta na bisa table din doctor din .</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Magunguna ya rubuta mata ...wanda zatayi amfani kafin ta dawo ...mika hannu tayi zata karba taga an karba ....</p><p><br /></p><p> Lumshe ido tayi ba tare da ta dago ba ....kujera yaja ya zauna kallon doctor din ...</p><p><br /></p><p> Ya jikinta ...ya fada tare da kallonta ...</p><p>Alhamdulillah ...bata da matsala ...doctor ya fada ..</p><p><br /></p><p> Lafiya lau kuma ta zo asibiti ...Ya kalleta. ..Fateema ki fadawa doctor abunda ke damunki ...</p><p><br /></p><p> Babu komae ...ta fada ahankali ...</p><p><br /></p><p> Doctor yace ...Tazo ne tana so ta koma gida shine na rubuta mata maganin da zatayi amfani dashi ...sannan bara tasha wani ruwa ba sae swan har tsawon wata shidda ....</p><p><br /></p><p> Ido ya lumshe sannan ya mike. . tashi muje Fateema. ..</p><p><br /></p><p> Ba musu ta mike suka fice tare da yi ma doctor din godiya. ...</p><p><br /></p><p> Gaban mota ya bude mata sannan ya zagaya ya shiga .....kura mata ido yayi yana karantarta ...</p><p><br /></p><p> Fateema. .....</p><p><br /></p><p> Kamar tace mashi Meenatou dae ..amma babu dama ...sae dae ta juyo da fuskarta gefenshi idonta na rufe. ..</p><p><br /></p><p> Ba da wata manufa ba ya kamo hannunta ya rike. ..Fada man meke damunki ...</p><p><br /></p><p> Girgiza kai tayi idanuwanta suka ciko da kwalla ...</p><p><br /></p><p> Babban yatsanshi ya saka ya share kwallan ...sannan ya tada motar hannunta na rike cikin nashi suka fice daga asibitin .....</p><p><br /></p><p> Kafin ya maida ta makaranta jikinta ya hau rawar sanyi ...</p><p><br /></p><p> Ya shafi wuyanta ...ya dauki zafi kamar wuta ...kwantar mata da sit din yayi baya ta kwanta ...sannan ya wuce da ita gidanshi ...tun kafin su isa ya kira Shamy yace ta tarad dashi gidanshi .....</p><p><br /></p><p> Suna isa ya yi Parking ya fita ba tare da ya mata magana ba ya dauketa ya shigar da ita gidan ...dakin shi ya kaita ya kwantar da ita saman gadon ...</p><p><br /></p><p> Sannan ya fita ya shiga kitchen ya hado mata coffee ....lokacin da ya dawo idonta a. rufe ...sae yayi zaton ko bacci take ...ja aje coffe din ya gyara mata kwanciya sannan ya rufe ta da bargo ya fita daga dakin ya koma falo ..</p><p><br /></p><p> Yana fita ta bude idonta tare da tashi zaune ..tana kallon dakin ...duk kusurwar dakin hoton Meenalle ne ...wani photon ma bata san inda ya dauketa ba ....</p><p>Kanta ta daura saman cinyarta tana kuka ....hannu ta saka ta janyo pillown dake gefenta ....</p><p><br /></p><p> Ribbon din da ta bashi tun tana yar yarinya ta gani cikin wani glass cover an Rubuta _*My Heartcherry*_.. _*They say you only fall in love once, but that can't be true... Every time I look at your Pictures, I fall in love all over again Meenatou*_</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Glass din ta dinga shafa tana hawaye ...ita kadae .....Motsin magana ta taji ya saka ta yi saurin komawa ta kwanta ..</p><p><br /></p><p> Tana jin lokacin da yake cewa Shamy ta shiga dakinshi friend dinta na ciki .....</p><p><br /></p><p> Ta turo dakin ta shigo tana fadin ..Meena meke damunki . .ta zauna bakin gadon tare da dago kanta. ...</p><p><br /></p><p> Ayya ...me kike wa kuka kuma ...dan Allah ki daina Meena ...tashi ki sha magani zaki samu sauki ....ta fada kamar zatayi kuka ..</p><p><br /></p><p> Ma'aruf ya shigo yana tambayar ta farka ...amma sae ganinta yayi jikin Shamy tana kuka. ...</p><p><br /></p><p> Bara ya iya jin kukan ba shi yasa ya juya da sauri ya fice daga gidan ....</p><p><br /></p><p> Da kyar Shamy ta samu tayi shiru ta hada mata ta hada mata Coffee sannan ta bata maganin da Ma'aruf din ya bata ...ta koma tayi bacci ...</p><p><br /></p><p> Shamy ta kira Ma'aruf din tace yana ina. ..</p><p><br /></p><p> Ce mata yayi ...Ina Fateema ...</p><p><br /></p><p> Da yake ta san Fateema yake cema mata ...sae tace mashi tayi bacci ..</p><p><br /></p><p> Ya sake ajiyar zuciya yace gashinan zuwa. ......</p><p><br /></p><p> ko da ya dawo ce mata yayi ta tsaya su kwana anan ta kula da ita ....</p><p><br /></p><p> Murna tayi don ko ba komai yau zasuyi fira sossae da shi ...</p><p><br /></p><p> Amma sae taga hankalinshi sam ba gareta yake ba. ...duk minti biyu ..zaya leka dakin yaga ko ta tashi ...</p><p><br /></p><p> Meenalle kuwa ta dade da tashi amma taki bude idonta ...tana jin lokacin da suka shigo da shamy ya daga bargon tare da shafar wuyanta yaji ko zazzabin ya sauka ...</p><p><br /></p><p> Shamy ta wani hade rai tana fadin Meye zaka wani tabata bayan ba aurenta zakayi ba ...ni bana son wannan wulakanci ..</p><p><br /></p><p> Shima daure fuska yayi yace. ..bakya ganin bata lafiyane. .</p><p><br /></p><p> Don bata lafiya sae ka tabata har da wani lumshe ido ..me kake nufi ...</p><p><br /></p><p> Bai ce mata komae ba don baya son ganin fushinta ...sae towel daya mika mata tare da fadin ...please ki jikashi ki dinga goga mata a jikinta ..</p><p><br /></p><p> Hararanshi tayi tace..tunda har ka iya taba wuyanta wannan ma bara ya maka wuya ba...</p><p><br /></p><p> Kwantar da murya yayi yace. . Please Shamy kiyi mata mana. .friend dinki ce fa ...</p><p><br /></p><p> Bafa zanyi ba ..ta fada kai tsaye ..</p><p><br /></p><p> Ok ...to fita ...ya nuna mata kofa ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>?</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI ......</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦Talented Writers Forum💦</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>63. to. 64</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tsaye tayi tana kallonshi cike da mamaki ...tunda take bata taba ganin ya daure mata fuska ba sae yau ...kullun cikin lallashinta yake ...</p><p><br /></p><p> Tsawa ya daka mata lokacin da ya fito daga toilet rike da bucket a hannu ...</p><p><br /></p><p> Baki ji abunda nace maki ....Get out ...ya nuna mata kofa ...</p><p><br /></p><p> Fita tayi a fusace tare da banko masu kofar ...shima karamin tsaki yaja ...sannan zauna gefen gadon tare da cire bargon .....</p><p><br /></p><p> har ya kai hannu zaya daga mata riga ya tsaya cak yana kallon fuskarta ...mikewa yayi ...ya rasa ta yaya ma zai mata ...tana jinshi sae dukan hannunshi yake ...sannan ya mike ya fita daga dakin ...he decide yaje asibiti ya kira wata nurse tazo ta mata ya bata kudi</p><p><br /></p><p> A falo ya wuce Shamy zaune ta kasa fita daga gidan ....tana ganin ta fito ta tareshi ...</p><p><br /></p><p> am sorry Habibi ...</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi tare da kallonta bai ce mata komae ba ...</p><p><br /></p><p> Kayi hakuri Please bara naje na mata kaji dan Allah...Please Hubby ...</p><p><br /></p><p> Kofar dakin ya nuna mata tare da zama kujeran falon ....</p><p> </p><p> Da Sauri ta shiga dakin. ..ta tarad da Meenalle zaune tana goga towel din a jikinta a hankali. ..</p><p><br /></p><p> Tayi saurin amsa tana fadin ..Sorry MMA kawo na maki ...</p><p><br /></p><p> A hankali tace. ..barshi ma nayi. ...</p><p><br /></p><p> Sorry please ta fada tare da rike mata hannu ...</p><p><br /></p><p> Komawa tayi ta kwanta ....rigarta ta cire sae dae ta kasa kwance belt din dake kirjinta na aikin da aka mata ...</p><p><br /></p><p> Ma'aruf ta kira ya kwance sannan ya fita ya basu guri ...</p><p><br /></p><p> Sae da tayi sati daya a gidan tare da shamy ...kula yake bata sossae idan ya shigo ya ga tana kuka ...ya dinga tambayarta meke damunta sae dae tace ba komae ....</p><p><br /></p><p> Ranar da zasu koma ..ya shigo dauke da iv card na bikinsu ya mikawa Shamy ta gani ....</p><p><br /></p><p> Wani Tsalle ta buga ganin designing din da aka masu da ratsin gold ...ta makale Meenalle tana nuna mata ...</p><p><br /></p><p> murmushi tayi ta kallah tana karantawa </p><p><br /></p><p> *Conjugal Bless* 💖</p><p><br /></p><p> _MR MA'ARUF IBRAHIM_</p><p><br /></p><p> *weds*</p><p><br /></p><p> _SHAMSIYYA A MAMMAN_</p><p><br /></p><p>_on 21 July 2017_</p><p><br /></p><p><br /></p><p> sae decoration din da aka bishi dashi da gold ana rubuta meenatou ...idan ba sani kayi ba bara kace mae aka rubuta ba ...zaka dauka kwarewace gurin wanda ya buga IV din ...</p><p>Wow yayi kyau ...ta fada tana waro ido ...</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi ya wucesu ...sae uban murna Shamy take. ...sae da ya canzo kaya sannan ya fito rike da ticket guda uku ya mika masu ....</p><p><br /></p><p> Da nashi dana Meenalle Sae na amarya Shamsiyya ....</p><p><br /></p><p> Meenalle ta kalleshi ido a waje tace Mr Ma'aruf ..ni ba gobe zan tafi gida ba ...</p><p><br /></p><p> Gobe zaki tafi Fateema ..ya fada a hankali tare da bude coca cola ya zuba a cup ...</p><p><br /></p><p> Da Sauri ta tashi ta je ta dauke cup din da sauran lemun tana kallonshi ...doctor yace ka daena shan lemun dake da gas a ciki ...</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi sannan ya bude su yana mata wani irin fitinanne kallo ...</p><p><br /></p><p> Da sauri ta juya ta koma kusa da shamy ta zauna tare da daura kanta saman bayanta ....</p><p><br /></p><p> Zo nan Fateema ....ya fada tare da mika mata hannu ...</p><p><br /></p><p> Makale kafada tayi tana kallon shamy ...wacce ita hankalinta ma naga wayarta sae daukar photon IV din take tana turawa a social media ....</p><p><br /></p><p> Ido ya lumshe yace ...me zaki bani tunda kin dauke nawa ...</p><p><br /></p><p> Mikewa tayi ta je ta bude fridge ta dauko mashi lemun kankana da abarba da ta hada dazu ta tsiyaya mashi a cup ta mika mashi ...</p><p><br /></p><p> Hannunta da cup din duka ya hade ya rike yana kallonta ...</p><p><br /></p><p> Bata fuska tayi ya saketa da sauri tana yarfe hannu. ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI ........</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦Talented Writers Forum💦</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>65. to. 66</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tun da safe suka tafi Airport ...shi da Shamy suka zauna side daya sae Meenalle na gabansu ita da wata mata .....</p><p><br /></p><p> Ko da suka sauka Meenalle har ta kira su Alhaji Sadee tace sun iso ..don haka tare motocinsu Ma'aruf suka iso da wadanda aka zo sauka Meenalle dasu ....</p><p><br /></p><p> haka ta shige mota ba tare da ta kallesu ba ...har suka fice daga airport din ...sae lokacin ta sake kuka tare da fadawa jikin Mus'ab don tare suka zo ...</p><p><br /></p><p> Bawan Allah duk ya rude ..duk da yayi aure</p><p> har da yaro daya baya. tafiyarta ......</p><p> </p><p> Haka suka isa gida ...</p><p><br /></p><p> Sae da ta huta sannan Alhaji Abubakar da Sadee suka kirata Falo ..</p><p><br /></p><p> Alhaji. Abubakar yace ...da gaske Aminatu an maki aure ...</p><p><br /></p><p> Gabanta ya fadi don tama manta da wani aure a rayuwarta ...daga masu kai a hankali ...</p><p><br /></p><p> Alhaji Abubakar yace ...da yardarki aka maki auren ? ..</p><p><br /></p><p> Nan ne tace aa ...bata san anyi auren ba sae dae kawae musa ya zo ya dauketa ..</p><p><br /></p><p> Alhamdulillah ...Ya fada tare da tashi ya fita ...</p><p><br /></p><p> Sadee ne ya. bude mata komae a ranar har da ba shine ubanta na Asali ba sae da ya fada mata ...sannan ta fada mahaifinta na sonta don ba yarda zayayi ne shi yasa har ya barta hannu. mamanta ..</p><p><br /></p><p> Tabbas bata mu sa mahaifinta na sonta ba .don zaman da tayi tare dashi ya nuna mata so ..sae dae bashi da dalilin da zai banzatar da ita don Mahaifiyarshi ta umurceshi don Haka tace Ma Sadee ..yayi hakuri tacigaba da kallonshi a matsayin ubanta ..</p><p><br /></p><p> Nan ya nuna mata matsayin da uwa ke da shi ga yayanta tare da mata waazi sossae har jikinta yayi sanyi ta cire kalmar da take fada cewa bata daukeshi uba na kirki ba ..</p><p><br /></p><p> A Ranar ta dauke Abubakar a matsayin Ubanta amma ta kasa yarda da hajiyarshi a matsayin kakarta</p><p>Basu bar falon ba sae ga hajiyar ta shigo tana murna an fada mata Meenalle ta dawo </p><p><br /></p><p> ta janyota jikinta tana fadin ...yaushe kika dawo yata ..</p><p><br /></p><p> zare jikinta tayi ta fita daga falon ta barta zaune tana kallon Ikon Allah</p><p><br /></p><p> Sadee lafiyar Aminatu kuwa ? ..ko wani abu kukayi mata</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi yace ...babu abunda ya sameta Hajiya ...</p><p><br /></p><p> Anya kuwa Sadee ...ta fada tana taba hannu ..</p><p><br /></p><p> Me kika gani ne Hajiya ..ya fada yana murmushi ..</p><p><br /></p><p> Ahto ..naga yarda Meenalle ke nan nan dani amma yau ta nuna kamar bata sanni ba ...kasan Allah Sadee ..ina kaunar Aminatu ..da iyayenta zasu. bar man ita da ta zauna hannuna har na aurar da ita ..shin ni kau sadee baka san inda Rabi da diyarta suke ba ..idan nama abubakar maganar baya saurarena ..</p><p><br /></p><p> Hajiya kenan . yanzu kuma jikkar har mace kina so ..? </p><p><br /></p><p> jikinta yayi sanyi tace ..to tunda ita Allah Ya bani ba dole na rungumeta ba ? </p><p><br /></p><p> Hmm Aa Hajiya ki tsaya ki gani ko Allah dae zai baki namijin ....yana gama fadar haka. ya tashi ya shiga ya kira mata matarshi ta fito ...</p><p><br /></p><p> Sama Sama suka gaisa ta tashi ta tafi cike da tunani </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Feedohm💞*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI. ....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦Talented Writers Forum💦</p><p><br /></p><p> 🔝</p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>69. to. 70</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tun da safe Meenalle ta shirya tace wa Sadee zata je ta Gida gurin Mamanta ...</p><p><br /></p><p> Direba ya saka ya kaita har zarian sannan ya bata kudi masu yawa ...</p><p><br /></p><p> A Zaure ta tarad da Mamanta na waina ...ta rungumeta cike da murna ..suka shiga cikin gidan ...ta sake maman ta fada cinyar Kaka tana kuka ....</p><p><br /></p><p> Yaro ya shigo wae ana kiran Meenalle ....</p><p><br /></p><p> Kamar tace bata zuwa sae kuma taga kara taje kila drivern da ya kawota ne zaya juya ...dan haka ta dauki gyalenta ta fice ...</p><p><br /></p><p> Sae da ta daga kai ta kalli Benen gidansu Ma'aruf kafin ta fita ...</p><p><br /></p><p> Tsaye ta ganshi rike da robar swan yana waya ...sae murmushi yake da alama da shamy yake ...</p><p><br /></p><p> Ajiyar zuciya ta sake ba tare da ta fita ba ...sae aikawa tayi tace wanda ke kiranta ya shigo tana zaure ...</p><p><br /></p><p> Kamar mahaukaci ya shigo duk ya rame yayi baki ...sa sauri taja baya tana bata fuska ta nuna shi ...Kai ke nemana? ..</p><p><br /></p><p> Washe baki yayi yana fadin ...kece Meenalle ...Meenalle ke kika koma haka ...Allahu Akbar ...kin ganeni ...nine Musa ..</p><p><br /></p><p> Musa ta fada tana kallonshi sama da kasa ..sannan tace ...daga ina. ..</p><p><br /></p><p> Baki ya washe yace...Musa dae Mijinki har kin manta ni ..gaskia an cuceni ...</p><p><br /></p><p> Ido ta waro. ...oh wae Musa dan Sani na gidansu Luba? ..</p><p><br /></p><p> Shi ma Meenalle ....bara naje na fadawa Baba kin dawo sae a janye karar sae mu koma ko ? ..</p><p><br /></p><p> Dariya tayi tare da nuna shi da hannu. . ina jin har yanzu baka manta da ko wacece Meenalle ba ko .....</p><p><br /></p><p> Bata jira amsarshi ba ta koma gida ta barshi tsaye ...</p><p><br /></p><p> ••°°••</p><p><br /></p><p> Mamanta ta kalleta tace ...wa nene ya aiko kiranki ..</p><p><br /></p><p> Mama wae Musa ne ..ta fada a hankali...sannan ta kalli kaka. tana goge hawayen da suke neman zubo mata tace ..</p><p><br /></p><p> Kaka Maikamshi ya shigo ....</p><p><br /></p><p> Daga mata kai tayi tace ..yazo Meenalle ..Kullun sae ya tambayi shin kin dawo Meenalle ..ko dazu da safe ya shigo ya gaidamu ....jiya ya dawo ma ..</p><p><br /></p><p> </p><p> Lumshe ido tayi a hankali tana kallon wainar da suketa lodawa a Coler ..wannan fa ta mecece..</p><p><br /></p><p> Tsohuwar ta kaudar da kai tace ...gudunmuwa nakewa Maikamshi ta bikinshi ...aure zayayi ..jibi ake daura auren ma Meenalle ....</p><p><br /></p><p> Kaka ta goge hawayen da suka zubo mata tace ...naso Meenalle ...naso ki zama matar Ma'aruf ...amma aka cucemu ...Yana sonki sossae. .</p><p><br /></p><p> Tashi tayi tana fadin ...zan koma kaka.......</p><p><br /></p><p> Da sauri ta fice daga gidan ta shige mota tace su koma kawae .....haka driver ya jata suka koma gida ba tare da tayi kwanakin da ta zo yi ba. ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Tana shiga gidan ta tarad da Shamy tazo ....suka rungume juna suna ihu ...</p><p><br /></p><p> Shamy tace tazo daukarta ne ...ana ta hidimar biki amma babu ita ....sannan Mr Ma'aruf duk yabi ya damu baki zo ba ...gaskia ki shirya ..don ni na riga na tambayi dady da mommy ashe ba wanda kika fada mawa ...da banzo ba da bara ki zo ba kenan. ..</p><p><br /></p><p> Murmushi tayi tace ..Shamy ai kinsan dole nazo bikinki ..</p><p><br /></p><p> Harara ta sake mata tace ..Banga alama ...ni dae yanzu ki shirya muje ...</p><p><br /></p><p> Duk wani abunda zata bukata sae da ta dauka ...sannan ta shiga tayi wa Mom bankwana suka shiga mota da yake shamy tare da driver suka zo ...suka koma zaria ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ••°°•• </p><p><br /></p><p> Tun a mota Shamy ta kira Mr Ma'aruf tace tare suka taho da Fateema ...</p><p><br /></p><p> Yana tsaye ta bene ya kurawa gidan kaka ido ya waro ido yana murmushi ..yace da kun shigo gari ki kirani ..</p><p><br /></p><p> Ok hubby ..ta fada tare da kissing din wayar sannan ta kalli Meenalle tace ..</p><p><br /></p><p> Gaskia dole ki saki jikinki wannan bikin ..in ba so kike ki dagawa hubby hankali ba. .ni na rasa wane irin mutuncine tsakaninku ..karfa kiyi man snatching. ..</p><p><br /></p><p> Murmushi Meenalle tayi tace ...kisha kurumin Shamy sanin kanki ne banda niyar maki snatching karki manta kidney dina daya tana jikinshi ..kuma silar hakan ne na hadaku ..kinga kuwa fadin kalmar snatching kamar butulci ne kika mani .....</p><p><br /></p><p> Zatayi magana ta dakatar da ita .. please mu bar wannan maganar Shamy. ..</p><p><br /></p><p> Shamy ta kwantar da kanta a bayanta tare da fadin ...Am so sorry Meena. ..</p><p><br /></p><p> Lumshe ido meenalle tayi ..itama ta daura kanta saman cinyarta ..a haka har suka isa ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Suna shiga garin ta kira Ma'aruf ta fada mashi sun iso ..yace su jirashi bakin gari ..zaya zo yanzu ..</p><p><br /></p><p> </p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧 SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦Talanted Writers Forum💦</p><p> 🔝</p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>71. to 72</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ko 15 Mints basuyi ba ya iso tare da kwankwasa masu glass din motar ..da yake side din Meenalle yayi knocking sae ta sauke glass din ...</p><p><br /></p><p> Kamshinshi ya bugeta bata san lokacin da ta furta ..Maikamshina....</p><p><br /></p><p> Saurin kallon bakinta yayi tare da fadin Me kika fada fateema ..</p><p><br /></p><p> Lumshe ido tayi tare da bude kofar ta fito ..sannan tace ..Ango ina wuni ..</p><p>No ba haka kika fada ba ...abunda kika ce shi zaki maimata ..</p><p><br /></p><p> Dan hararanshi tayi tace ...Cewa nayi ..sae Kamshi kake ...</p><p><br /></p><p> A hankali ya lumshe ido tare da dubar Shamy yana fadin muje na kaiku ...shi ya tafi</p><p>Motarshi suka shiga ...Har gida ya kaisu ...Meenalle ta shiga ciki ta barsu a mota .....gidan ya cika da kawayensu ..har da soofy. ..sae murna suke ana labarai .....</p><p><br /></p><p> Da daddare kowa yayi bacci aka bar Meenalle sae juyi take ...Soofy ta farka ta dade tana lura da ita ...sannan ta gangaro kusa da ita ta kira sunanta a hankali ...</p><p><br /></p><p> Meenalle ta bude ido tana kallonta tace ...Bakiyi bacci ba ...</p><p><br /></p><p> Soofy ta mike tare da jan hannunta suka koma falo ...zama sukayi sannan ta kalli Meenalle tace ...Meena meke damunki ..</p><p><br /></p><p> Me kika gani Soofy ...ta fada tana kallonta ...</p><p><br /></p><p> Meena komae ma na gani ...Mr Ma'aruf shine Ma'aruf dinki ko? ..</p><p><br /></p><p> Da sauri ta rufe mata baki ...tace ...waya fada maki Soofy ..dan Allah ki bar wannan maganar ...bashi bane . </p><p><br /></p><p> am not kid ...Meena...me yasa zakiyi haka ...kuma ba Shamy ce ta bashi kidney ba kice Meena ...duk wannan sirrin na meye ....Shin baki sonshi ne yanzu ....Dole zan fada mashi gaskia gobe ..</p><p><br /></p><p> kuka ta sake tana fadin ..</p><p>aa Soofy. ..karki fada mashi dan Allah ...wallahi baya sona yanzu ...</p><p><br /></p><p> Karya kike Meena ..har yanzu akwae kaunarki ..duk da bai san ke bace Meenalle amma ki kalli idonshi kaunarki ce ke cike dashi ...kuma sae na fada mashi ...</p><p><br /></p><p> Cikin kuka ...wallahi Soofy baya kaunata naji yana fada ne ..ya tsaneni ..bansan me na mashi ba. ....</p><p><br /></p><p> Ke dae kika sani ..ni zan fada mashi idan kinso idan zai aureki sae ki ki aurenshi </p><p><br /></p><p> Soofy ni matar aurece ...ta fada a hankali</p><p><br /></p><p> A masifance ta juyo tana fadin karya ne wallahi ...</p><p>Hannunta ta ruko tana kuka ...ki yarda dani Soofy ina da aure ..da banda aure da babu abunda zai hani bude *SIRRIN ZUCI* ...sun aurar dani ga wani ...wani wawa Soofy Wawa irin Musa ...Tabbas ina son Ma'aruf ..amma katanga babba ke tsakanina dashi ...sun dasa mashi tsanata ta yarda har yake furtawa ....ya zanyi Soofy ....ta kara fashewa da kuka. .</p><p><br /></p><p> Tausayinta yayi balain kamata ...dukawa tayi tare da rungumeta a jikinta ...kiyi hakuri Meena...in sha Allahu dole musa ya sakeki ...kin sani mahaifina Justice ne ...zan mashi magana dole a bi maki hakkinki ...kiyi hakuri dan Allah</p><p><br /></p><p>°°••°°</p><p><br /></p><p> Karfe biyu dae dae aka daura Auren Ma'aruf da Shamy gaban dunbin mutane. ...Amarya baki yaki rufuwa haka ango ...Sae shirye shirye ake ..don bayan biki da kwana uku zasu bar kasar saboda karatunta da kuma aikinshi ...</p><p><br /></p><p> Wajen karfe 9 ne akace a fito da amarya zaa tafi dinner ..</p><p><br /></p><p> Amarya ta shigo hall tare da manyan kawayenta guda biyu ....</p><p><br /></p><p> Chanchadi Mazakwae ...uhmm abun baa magana ..idan kaji ana Carai ..to wannan amaryar ta wuce anan ...Sky blue din gown ne a jikinta ...fuskarta na rufe da wani golding din net daga samanshi ya fitar da wani shape kamar an daura crown ......</p><p><br /></p><p> Ango na zaune suka shigo ....lumshe ido yayi tare da jingina da kujeran da yake kai ..sannan ya bude su a hankali tare da sakin wani fitinannen kallo yana kallon right side din amarya ....</p><p><br /></p><p> Sae lokacin na kalli inda yake kallo ....</p><p><br /></p><p> Ido na waro sannan na lumshesu nima kamar yarda yayi ...Phone dina ta sulale ta fadi kasa ...duka glass din ya dargaje😒😥😥...bansan lokacin da nayi zaman dirshan ba ...ina kallo.. .sae da na lalubi wayar da niyar na fada maku me na gano ...sae lokacin na lura ashe ta dargaje 😒😒😒</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm*💞</p><p>💧💧 SIRRI ZUCI ....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦Talented Writers Forum💦</p><p> 🔝</p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p>================= Gidan Novels =====================</p><p><br /></p><p>73. to 74</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Meenalle nagani tsaye rightside din amarya ...sanye da gown itama amma Pinch colour ....sae head maroon ...ta gaji da haduwa ..fatar har wani kyalli take. ....</p><p><br /></p><p> Ma'aruf ya taso a hankali har ya iso kusa da amaryarsa ...hannnuta ya kama tare da matsawa kusa da Meenalle ...</p><p><br /></p><p> Natural beauty ...ya fada mata dae dae kunnenta ....phone dinta tayi kara ....</p><p><br /></p><p> Ta dan saci kallonsu ta dauke kai ..tare da ficewa daga hall din ....ta dauki sayar. ..</p><p><br /></p><p> Aminatu ...gamu a bakin gate amma kamar baku ciki ko ? ...aka fada daga dayan bangaren ...</p><p><br /></p><p> Muna ciki. mana ku shigo har zaa fara dinner ....</p><p><br /></p><p> ki fito. ki shiga damu please ...ko mun shigo bamu san inda zamuyi ba ...don gurin da alama yana da girma. ....</p><p><br /></p><p> Okey ..gani nan fitowa ta fada ...tare da juyawa ta kalli su Shamy ...Ma'aruf rike da hannunta ...wani abu ya tokare mata kirji ta fita da sauri ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Daga can side din ta hango wata bakar jeep ....ta fito da wayarta ta kira number. ..kuna ina ...</p><p><br /></p><p> Ki tsallako muna cikin jeep din dake tsaye gefe guda ....kafin tayi magana an kashe wayar ..</p><p><br /></p><p> Tabe baki tayi ta tsallaka tare da knocking din glass din motar na gaba ....</p><p><br /></p><p> Kofar baya aka bude ...wani kato ya fito ya toshe mata baki ya jata cikin motar suka hau titi da gudu ...</p><p><br /></p><p> Hannun ta cire daga bakinta tare da jan uban tsaki ta gyara zama cikin motar tana watsa masu wani uban kallo ..</p><p><br /></p><p> Da cewa kuka yi na fito kunzo sace ni ne da baku wahalar da kanku ba ....ta fada tana kallonsu ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Torch light din wayarta ta kunna ta haska su daya bayan daya. ..sannan ta maida hasken ga na kusa da ita ..</p><p><br /></p><p> Musa Sani ..ta fada tana kallonshi ....matsalata dakae wawa ne ...bakka ganewa ..dan zaka dauki yarinyar da kake tunanin matarka ce sae ka hado da wadannan jakunan ....? ..</p><p><br /></p><p> Ke.....wani ya daka mata tsawa ...tare da nunata da hannu. </p><p><br /></p><p> Hannun yaji an murde da karfi har sae da yayi kara alamun karewa .tare da angazashi baya ....daga lokacin bai kuma cewa komae ba ..</p><p><br /></p><p> Meenalle ba tsoro ...haka ta dinga wankesu ..har suka shiga wani tsohon daji ...sae lokacin ta lura sun bar titi ....</p><p><br /></p><p> Bata kuma cewa komae ba sae kallon ikon Allah da ta tsaya tana yi ....har suka isa wani dogon gini ..baraka iya cewa ga karshensa ba . ..</p><p><br /></p><p> Daya ya sauka ya bude masu gate din suka shigar da motar ciki. ...</p><p><br /></p><p> Ba wani babban gida bane ...duka kofarshi daya ta shiga ciki sae ta gate ..duka gidan arufe yake ...suka faka motar suka fito ...</p><p><br /></p><p> da yake akwae hasken wuta ...ta bisu da kallo ..kamar mahaukata haka suke ko wane bakikkirin dashi sae mazurai suke ...</p><p><br /></p><p> Ta hadiyi wahalallen miyau sai lokacin gabanta ke faduwa ....amma ta dake ta na hararansu ....</p><p>Mu shiga ciki Meenalleta ...Musa ya fada yana dariya ...</p><p><br /></p><p> Murmushin ta sake mai cike da takaici ...tace ..ai ko bakace ba Musa kasan zan shiga sannan na zauna daku har sae kun gaji dan kanku ku mayar dani kuma na kwanta idan kai dan iskane kayi gigin zuwa kusa dani ...</p><p><br /></p><p> Girgiza kai yayi yana wata dariya ..Meenalleta kenan ..kiyi hakuri ki soni muyi rayuwa a duniyata ..ki haifa man ya'ya kyawawa irinki ...</p><p><br /></p><p> Wace duniyace gareka Musa...duniyar karnuka ..Sannan ba Ya'ya zan haifa maka ba ...Uwaye zan haifa maka. ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gaba yayi yana dariya ta bi bayanshi ...sauran suka take masu baya. ..har wani karamin daki ya kaita mai dauke da karamin gado sae wasu akwatuna guda uku ...</p><p><br /></p><p> Meenalle ga lefenki nan ...wanda da ban baki ba ....akwae english wears a ciki kinsan ni mayan sune ....ya fada yana washe baki ..</p><p><br /></p><p> Dariya ya bata sossae har tana rike ciki ...sannan ta nufi gurin gadon ta cire pillow ta aje a kasa ta kwanta ..tunda dama tayi isha'i ..</p><p><br /></p><p> Tana kwance ya shigo tayi saurin tashi zaune tana kallonshi...kazar amaryace na kowa ..ya fada yana kallon kirjinta ...</p><p><br /></p><p> Babu tsoro taja ledar ...tana dubawa ....je ka dauko plate ..ta fada ba tare da ta kalleshi ba ...</p><p><br /></p><p> Da sauri ya mike yana fadin Meenalle har kin sauko zaki ci kazar amare ..kila dama dan ban nuna maki ita ba shi yasa kike zagina dazu ..</p><p><br /></p><p> Musa baka gane ...ko dae Mamansu luba hada maka da nonon awakai lokacin da take shayar da kai....ta fada tana murmushi </p><p><br /></p><p> Da kuwa ta cuceni yasin ...ya fada sannan ya fice daga dakin ...</p><p><br /></p><p> Da Sauri ta mike ta rufe dakin da keys din dake jikin kofar ta koma ta harde kafa ta fara cin kazarta ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦Talented Writers Forum💦</p><p> 🔝</p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>75. to 76</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Meenalle bude ga parantin ....ya fada yana buga kofar ...</p><p><br /></p><p> Musa Aje akwanta sae Allah ya hada mu gobe ....ta fada daga cikin dakin ..</p><p><br /></p><p> Haba Meenalle ke fa kikace na dauko ..ki bude dan Allah ...wallahi ni bama kazar zanci ba ..ke nake so...</p><p><br /></p><p> ashe ma kai sakaraine .....ta nannade ledar tare da gyara kwanciya ..</p><p> </p><p> Yayi lallashin duniyar nan ..amma taki ko kulashi ..daga karshe yace ...Meenalle ke yar iskace ko...kinsan ba tare zamu kwana ba kika cinye man kaza ko...to wallahi da safe sae na maki shegen duka ....ya bugi kofar da karfi ya wuce ....</p><p><br /></p><p> Tana kwance taji alamar mota ta fita daga gidan ...ta mike ta leka ta taga ...taga sun fice sae mutun daya zaune bakin kofar an barshi gadi .....</p><p><br /></p><p> Ta bude kofar ahankali tare da lekawa ...babu kowa sae falon dake gauraye da hasken wuta ...ta fito tana sanda ta rufe kofar shigowa ciki sannan ta shiga wani karamin daki mai shegen duhu. ...da wayarta ta haska taga duk kayan fadane aciki ..sae bindiga da bata wuce 5 ba kirar AK ....sae uwayen akwatuna da da buhu cike da kudade ....</p><p><br /></p><p> Sae lokacin ta tabbatar yan fashine .. ..dakin da aka bata ta koma da kwanta ..</p><p><br /></p><p> Su Musa suka dawo babu irin bugun duniyar da basuyi ba amma Meenalle bama ta sani ba tana baccinta ...</p><p><br /></p><p> Da Asuba ta farka ta iske missed call kusan 76 ...50% duk na Ma'aruf ne ...sae Soofy itama ta kirata ...sae Mamanta ....</p><p><br /></p><p> Mamanta ta kira ..tace fada mata duk abunda ke faruwa ...sannan tace mata ta kwantar da hankalinta ...ta dinga mata addu'a in Allah ya yarda zata dawo ....</p><p><br /></p><p> Sannan ta kira Soofy ..itama addu'arta ta roka ta kashe wayar ...</p><p><br /></p><p> Text ya shigo mata na Ma'aruf ne ... _Fateema ina kika shiga ne ? kina dae lafiya ko ,? ...._</p><p><br /></p><p> Reply ta mashi _Na koma gida fatan Alkhairi kai da amarya_</p><p><br /></p><p> Ta kashe wayar gaba daya ...cikin saa taga toilet acikin dakin ...ta shiga tayo alwala ..cikin akwatin da Musa ya nuna mata ta duba ko zata ga hijab ...amma babu ...sae Zanin atamfa ta dauko ta lulluba tayi sallah .....</p><p><br /></p><p> Sae da gari ya waye sannan ta fita daga dakinta ...lekensu tayi babu wanda ya farka ..kamar matattu ...tsaki tayi ta bude kofar ...</p><p><br /></p><p> Firgigi suka farka ...ko wane sae ya taso da zuciyarshi ...da sun hada ido da musa sae ya koma ya kalli kasa ...</p><p><br /></p><p> Musa kuwa duk bala'in da yayi niyar ya mata sae ya kasa ...ya matsa yana washe mata baki.....ba kuma wani abu ya hana ya mata ba .aa tunowa yake da lokacin da suna kauye ..idan zai bugeta azabar da take mashi ...</p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Tun kafin a shiga court Alhaji Abubakar ya sami Alkali ya mashi bayanin Musa ya sace Yarinyar ...Haka aka nemi Malan Sani shima bai zo kotun ba .....</p><p> </p><p> Alkali ya aika a daukoshi ...yana zaune bisa dankali aka daukoshi sae masifa yake</p><p><br /></p><p> </p><p>Aka zo dashi office din Alkali ...aka tambayeshi ina Musa ....kada kai yayi yace bai sani ba ..</p><p><br /></p><p> Juyin duniyar nan Amma Malan sani ya yace bai san inda musa yake ba ....</p><p><br /></p><p> Nan take Alkali ya raba auren tare da tsare Malan Sani har sae Musa ya dawo da Meenalle lafiya ..idan kuma wani abu ya sameta to hukunci mai tsanani zai hau kanshi ...</p><p><br /></p><p> Lokacin da labari ya isa gurin musa sae cewa yayi ...indae sae ya dawo da Meenalle zaa saki Malan sani sae dae ya mutu a daure ...</p><p><br /></p><p> Ran Malan sani yayi bala'in baci ...ranar ya tsinewa musa yafi a kirga. .sannan yayi nadamar abunda ya dinga yi akan musa gashi yanzu ance ya maido Yarinyar a kwanceshi yace sae dae ya mutu a daure .....</p><p><br /></p><p>••°°•• </p><p><br /></p><p> Ma'aruf da amarya aka koma india ...rayuwa suka bude mai kyau ...matsalar daya ce Shamy bata san yarda zata kula da mijinta ba ....illa iyaka ta dafa break ta ta fi school ...amma abincin rana dana dare sae dae ya sawo masu ...</p><p><br /></p><p> Lokacin suna gab da fara exam amma babu Meenalle ..hankalin Ma'aruf yayi bala'in tashi ..har rigima sukayi da Shamy lokacin ...wae sae ya fada mata dalilin da yasa ya damu ....</p><p><br /></p><p> Bai ce mata komae ba ...yaja har school din ya saki iyayen kudi sannan ya samu wata wadda ta riga ta gama school din aka sakata ta zaunawa Meenalle ...</p><p><br /></p><p> Shamy ta shiga dakin Ma'aruf rike da cup din coffee ...bai san ta shigo ba yana rike da photon Meenalle ....ji yayi an fuzge photon tare da fasashi kasa ...</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi ba tare da yace mata komae ba ya duka yana tattara photon ..</p><p>kafa ta saka tayi wurgi da wanda ya tattara ....</p><p><br /></p><p> Azuciye ya mike ya wanka mata mari ...tare da jan hannunta ya fitar da ita daga dakin ya saka key ...</p><p><br /></p><p> Bugun kofar ta dinga yi kamar mahaukaciya tana bala'i ....har sae da ta gaji sannan ta yi shiru ...sae da tayi Wata ba tazo shinfidarshi ba ...haka bata mashi magana ba ...</p><p><br /></p><p> Ma'aruf ba mai son hayaniya bane ganin abun nata bana karewa bane ya saka ya kirata da kanshi ya lallasheta ganin lokacin tana dauke da ciki .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ......</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦 Talented Writers Forum💦</p><p> 🔝</p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>77 to 78</p><p><br /></p><p><br /></p><p> An baza ko 'ina ana neman Meenalle amma ko labarinta baa samu ...an kirata a waya an tambayeta ina take amma sae dae tace wallahi bata sani ba ....</p><p><br /></p><p> Haka musa ma nemanshi ake ruwa jallo ..amma da yake munafukine ..suna da wani tsari indae ana neman su to basu taba haduwa da masu neman nasu ....</p><p><br /></p><p> Kuma bai fasa shigowa zaria ba ....duk lokacin da yaso zaya shigo kuma ya fita ba tare da wadanda ke neman nashi ba sun ganshi ...ko da kuwa zaya wuce ta gabansu to shi kadae zai gansu ....</p><p><br /></p><p> Meenalle kuwa tana can zaune ...duk tabi ta ishesu ....akwae ranar da suka bata girki ...Shinkafa da miya ...sae da ta juye masu quatern gishiri cikin miyar ....ranar Musa kamar yayi hauka don baya cin gishiri .....</p><p><br /></p><p> Sannan babu shegen da ya isa ya nuna mata hannu ....komae tayi masu kuwa ...Musa ma ya taba gigin dukanta ranar da suka dawo daga fashinsu sa daddare suka iske kofar bude ...sukayi ta murna don sun saba kwana a waje ...ga sauro ..ga kunamu ....Suka shiga falon babu wuta su duka sukayi mamaki don babu inda zaka tarad ba da wuta a gidan ...</p><p><br /></p><p> Gashi babu mai ko waya ...haka suka shiga cikin ...ko wane da ya shiga sae ya fito da gudu yana ihu rike da kafa ....</p><p><br /></p><p> Zuwa can wuta ta kawo ...sae lokacin suka lura da cewa kwalbace farfashe a kasan gurin ....kuma sun tabbata Meenalle ta sakata ....</p><p><br /></p><p> Musa ya shiga dakinta a fusace tana kwance ya fizgota tare da daura mata mari ....bai sauke hannu ba yaji kalan nata a fuskarshi. ..afusace ya cire belt ya zura mata...</p><p><br /></p><p> Zafi da azaba bata san lokacin da ta murde mashi abun fitsari ba tare da aza mashi cizo a idon dama .....</p><p><br /></p><p> A rude ya fito yana ihu rike da wando ....suka tareshi suna rikeshi ...wasu na Allah ya kara wasu na tausayinshi ....kafin safe ido ya kumbura ....</p><p><br /></p><p> Sae da yayi sati baya fita ...don daga karshe ma zazzabi ya rufeshi ...tunda lokacin bai kuma gigin dukanta ba ...</p><p><br /></p><p> kowa ta isheshi a gidan ...bayan ya warkene. ..yayi alkawarin ko zata mutu sae ya kwanta da ita ranar ..don haka suna gama fashinsu ya sawo mata kaza ...har wani karamin gidansu ya tsaya yayi wanka sannan suka taho ...</p><p><br /></p><p> Da yake generator dinsu ya lallace ...babu wani shamaki suka kutsa kai cikin falon ....</p><p><br /></p><p> Meenalle na tsaye bayan kaure rike da tabaryarta ...Musa ya kutso kai rike fa ledarshi .</p><p>.</p><p> ta daga tabaryarta iya karfinta ta buga mashi a goshi ...ya dafe gurin tare da sakin ledar ya koma baya da gudu ...</p><p><br /></p><p> Lafiya oga ...wani ya tambaya ...</p><p><br /></p><p> Saboda azaba da hannu ya nuna mashi cikin gidan ...ya daga labubalai ya shiga yana lafiya ....dukan da yajine ya bashi amsa ya yo baya dafe da goshi ga jini na zuba ...</p><p><br /></p><p> Cikinsu babu wanda bai yi kokarin shigowa ba haka babu wanda baiji ciwo ba ...da Meenalle ta tabbata kowa ya samu rabonshi ta dauke ledar ta shige dakinta da gudu ta saka makulli .</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Safe suna zaune kowane fuska a kumbure ta fito ta saka su gaba tana ta dariya ..</p><p>wani Sale cikinsu sae da yayi kuka ranar saboda takaici ...gashi sun san ita tayi masu wannan rashin kirkin amma babu halin magana ...</p><p><br /></p><p> Bayan sati daya ne suka dawo suka iske ta kona masu duk abunda aka tara a gidan ...</p><p> </p><p> Ranar sukayi Meeting musa baya nan suka sami Meenalle suka roketa tazo su fitar da ita cikin gari ...</p><p><br /></p><p> Cewa tayi bata so bara ta tafi ba ...don bata gaji da zaman ba ..</p><p><br /></p><p> Suka dinga hada ta da Allah ..Da kyar ta yarda ta shiga motar suka taho ....Har kofar gidan Kaka suka ajeta sannan suka juya da sauri ...</p><p><br /></p><p>*Feedohm*💞</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦Talented Writers Forum💦</p><p> 🔝</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>79. to 80</p><p><br /></p><p> Lokacin da musa ya dawo ya iskesu tsaye bakin gate ....ya taresu yana tambayar lafiya...sae suka ce masu police ne suka zo suka tafi da Meenalle basu nan ...</p><p><br /></p><p> Kamar mahaukaci ya juya ya tafi police station din rike da bindiga ...da yake shashasha ne yama manta da nemanshi ake soyayya ta rufe mashi ido ...</p><p><br /></p><p> Yana zuwa ya fara harbe harbe yana zage zage ...nan da nan suka kamashi suka daure ...</p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Ina Raliya ..</p><p><br /></p><p> Da Raliya ta tabbatar Mr Ma'aruf ya rigaya ya mata nisa ...don ko tana tsafi da bakar jaba bara ta sameshi ba ...har office dinshi taje messenger shi ke fada mata yayi aure ...sae ta tattara kayanta ta koma nigeria ...ta sayi gida ta bude wani bariki na yan lesbian ...da yake dama maza ba damunta sukayi ...ba ...dama Mr Ma'aruf ne take bala'in so kuma bata samu ba ...</p><p><br /></p><p> Haka ta lallashi partner ta Ruky da ta rude tana son Meenalle tun tana yarinya don tun lokacin da Meenalle ta shigo gidansu har ta dauketa bata kuma kara kula Raliya ba ...suka shirya suka koma kamar da ..</p><p><br /></p><p>°°••°°.</p><p> </p><p> Bayan an rufe musa ne aka sake Malan Sani ....Lokacin Ya koma yana so rabi ta koma gidanshi ...amma fur kaka tace bara ta koma ba ....</p><p>Sannanne kaka ta murje ido tace Malan Sani sae ya tashi daga gidan ...</p><p><br /></p><p> Malan sani ya tsorata ganin Kaka zata maidashi kotu ...gashi ya sayar da gida kuma ba kudi. ...yayi nadama sossae Rabi tace a kyaleshi amma ya saketa dan bara ta koma gidanshi ba ...</p><p><br /></p><p> Jiki na kyarma ya bata takardar saki ... .</p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Meenalle kuwa tana dawowa kaka ta mayar da ita gidan ubanta ...ko sati bata kara ba ta koma makaranta ...</p><p><br /></p><p> Ranar da ta isa kasar bata san wanda ya fadawa Ma'aruf ba sae ganin kiranshi tayi ..bata dauki kiran ba sae da suka hadu School da Shamy take mata tsegumi ..... .</p><p><br /></p><p> Duk yarda Shamy taso Meenalle taje gidanta amma taki yarda taje ...haka ta hakura ta kyaleta ...Shima Ma'aruf yayi kokarin su hadu ya ganta amma duk ta toshe hanyar da zasu hadun ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°•• </p><p> </p><p> da Hajiya ta ishi Abubakar maganar diyarshi ...sae ya dauko mata Sadee ..ya gaya mata gaskia ....</p><p><br /></p><p> Su hajiya har da kuka tana neman gafararsu. ..sannan tace akaita gurin Rabi ta roki gafara ...haka suka shirya suka tafi ....</p><p><br /></p><p> Lokacin da Abubakar yaji auren Rabi ya mutu ..ba karamin farinciki yayi ba. ...ya fadawa Hajiya yana so ya maido rabi ...da yake hajiyar tasha wahala gurin matar da ta sakq ya aura ..sae ta amince dan da nan ...</p><p><br /></p><p> ••°°••.</p><p><br /></p><p> Cikin wata hudu akayi komae aka gama ..rabi ta koma gidan tsohon Mijinta ...wancan matan kuwa tana jin zayayi aure tace bara ta zauna da kishiya ba ..ta tattara komatsunta ta yi tafiyarta ....</p><p><br /></p><p> Da Hajiya kuwa ta gyara halinta suka zauna lafiya da Rabi. ...da labari ya sami Meenalle har kukan murna sae da tayi ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦Talented Writers Forum💦</p><p> 🔝</p><p> </p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>81 to 82</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Nine Month*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tun da Safe Ma'aruf ya kira Meenalle ...yace tazo Shamy na kiranta bata lafiya ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Taxi ta hau ...kasan cewar tsakanin makarantar da gidansu Shamy din akwae nisa ...minti biyar tayi ta isa gidan ...</p><p><br /></p><p> Lokacin har an fito da Shamy din daga cikin gida zaa kaita asibiti ...</p><p><br /></p><p> Da Sauri ta isa gurin Ma'aruf tana tambayarshi lafiya ....</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi yace tana labour ne wallahi ...tun jiya ...</p><p><br /></p><p> Bayan sun je asibitin ne akace. ..sae an mata CS saboda haihuwar tazo amma kuma Mahaifar ta rufe. ...</p><p><br /></p><p> Canza mata asibiti yayi ya maidata asibitin da aka masu aiki ...yana tunanin ko zasu iya mata wani abu ...don baya kaunar CS ...Cikin Saa ya tarad da doctor din da ya mashi aikin Kidney ...</p><p><br /></p><p> Thesame nan ma cewa akayi sae anyi aikin don barata taba iyawa ba ...</p><p><br /></p><p> Haka aka shigar da ita dakin tiyata ...Meenalle duk ra rude. ..bayan minti 45 ..wata nurse ta fito da baby boy ...</p><p><br /></p><p> Ta nufi wani room dashi da sauri ...Meenalle ta bita tana tambayarta lafiya. ...</p><p><br /></p><p> bayan ta fito daga dakin ta zo tana masu bayanin ...boy dinne yasha ruwan mahaifa kuma akwae matsala. ...</p><p><br /></p><p> Abunka da ruwa ruwa nan da nan idon Meenalle ya ciko da kwalla ...don tasha jin inda yaro ya samu irin wannan matsalar da wuya ya tashi .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Minti Talatin da shigar nurse din ta fito ta fada masu cewa baby boy din ya koma ga Allah ....</p><p><br /></p><p> Meenalle ke ta hawaye ...amma Ma'aruf lumshe ido yayi kawae yana kallon dakin da Shamy ke ciki ....</p><p><br /></p><p> Zuwa can aka gangarota ....aka shigar da ita wani dakin ....lokacin idonta biyu tana kallonsu ...ta yafito Meenalle da Hannu ....</p><p><br /></p><p> Doctor din ya girgiza mata kai ...yace tana bukatar hutu ....</p><p><br /></p><p> Bayan an shiga da itane ..ta dinga rokan doctor din akan ya barta tayi magana da Meenalle minti 30 kawae ....daga farko cewa yayi tayi hakuri ...amma daya fahimce ta sossae sae yaga bai dace ya hanata ba ....</p><p><br /></p><p> Shi da kanshi ya kira Meenalle yace ta shiga patient din nason magana da ita ....</p><p><br /></p><p> ta shiga da gudunta ...Ma'aruf ya bita da kallo ....</p><p><br /></p><p> Shamy ta rike mata hannu suna kuka ...Ma'aruf dake kallonsu ta cikin glass ya kura masu ido ...ya rasa wace irin shakuwace tsakaninsu ..wadda har daga fitowarta da operation take son magana da ita bayan gashi ...</p><p><br /></p><p> Meena ...Shamy ta kira sunanta ahankali ...</p><p><br /></p><p> Meena ya maimata a ranshi tare da matsawa saitinsu yana kallonta ..</p><p><br /></p><p> Ki fadawa Ma'aruf gaskia...Dan Allah Meena ko bayan na mutu ki fada mashi ki gaya mashi bani na bashi kidney ba Meena. . ki fada mashi ke ki bashi ..kece masoyiyarshi ta gaskia bani Meena ..ki fada mashi kece Meenallen shi ....</p><p><br /></p><p> Girgiza mata kai tayi tana kuka ...aa Shamy zaki warke dan Allah ki bar wannan maganar ...zaki warke insha Allah ..</p><p><br /></p><p> Hannuta ta kawo ...bazan tashi ba Meenalle ..baby din na haifa ki rikeshi Meenalle ke na bawa amanarshi ..ki auri Ma'aruf dan Allah ...idanuwanta suka fara rufewa </p><p><br /></p><p> Kuka ta saki da karfi tare da ficewa da gudu ...a kofa ta bangaji mutun tsaye amma ta wuceshi ...ta fita tana kiran doctor ...</p><p><br /></p><p> Ma'aruf na tsaye idonshi a lumshe doctor yazo ya jashi yana fada mashi matarshi ta rasu ....</p><p><br /></p><p> Meenalle kuwa gurin ta suma ....ko bude ido Ma'aruf baiyi ba bare yaga yarda akayi da ita ...</p><p><br /></p><p> Bayan sun shiga office da doctor din ..Ma'aruf ya tambayeshi ...wacece cikin su ta bashi Kidney ...</p><p><br /></p><p> Ganin babu bukatar boyewa yanzu doctor din yace ...Meena Abubakar ....</p><p><br /></p><p> Idonshi ya lumshe hawayen dake makale suka gangaro ...</p><p><br /></p><p> Waya ya fito ya kira wani friend dinshi dake aiki airport yace yana son helicopter yanzu ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> bai kuma cewa komae ba ya nemi a bashi gawar Shamy ..</p><p><br /></p><p> Cikin wani box aka sakata sannan aka nufi airport da ita ...suka koma nigeria ......</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm*💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💧💧SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦Talented Writers Forum💦</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Godiya mai tarin yawa ga talented writer Allah ya hada kanku tare da hakuri da juna*</p><p><br /></p><p>_Islah tee_</p><p>_Zahra_</p><p>_Smart_</p><p>_Halieymerh_</p><p>_Mufeedah_</p><p>_da sauran mu gurin bara ya isa ba na rubutu ku duka💞_</p><p><br /></p><p>*Thank you so much for your well nd eniest wishes*</p><p><br /></p><p>*Mum twins*</p><p>*Aunty Sis*</p><p>*Khadija Candy*</p><p>*Bilkisu bilyaminu*</p><p>*Namesy Classic*</p><p>*Aunty Maijidda*</p><p>*Salamatun Inna*</p><p>*nd Ladies Novel world members*💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>83 to 84</p><p><br /></p><p><br /></p><p> A gidan Iyayenta aka mata sutura ...bayan sati biyu ...ya taka har gidan Kaka ...ya fada mata komae sannan ya nemi yaje gurin iyayen Meenalle ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kaka baki yaki rufuwa ...ita da kanta ta kaishi har gidan Alhaji Abubakar ..lokacin su Rabi an murje ..ni kaina kasa ganeta nayi ...</p><p><br /></p><p> Maganar da Ma'aruf ya gayawa kaka ita ya maimatawa Rabi da Alhaji Abubakar ....sannan ya nuna yana bukatar aurenta kafin ya koma ..</p><p><br /></p><p> Alhaji Abubakar yace sae an nemi Meenalle anji ta bakinta ....</p><p><br /></p><p> Haka aka kira Meenalle a waya aka tambayeta ...</p><p><br /></p><p> Kasa cewa komae tayi ..sae kaka ta ce ...ta yarda ...</p><p><br /></p><p> ••°°••</p><p><br /></p><p> Biki ake amma bada sanin amarya ba ...komae an mata cikin gata da aminci ....</p><p><br /></p><p> Kaka kuwa baki yaki rufuwa .....haka hajiyar Abubakar sae nan da nan ake da dangin rabi ...</p><p> </p><p> Kudi kawae Abubakar ya tura aka sayar mata komae acan.....aka hada mata komae na jin dadi ....</p><p><br /></p><p>°°••°°</p><p><br /></p><p> Ma'aruf kuwa sae da aka gama komae sannan yama iyayen Shamy bayanin duk abunda ya faru sannan ya taho ...</p><p><br /></p><p> Meenalle kuwa tunda Kaka ta kirata ta fada mata an daura mata aure gabanta keta faduwa ...haka Ma"aruf bai kirata ba ko sau daya ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Karfe 8 din dare Ma'aruf ya dawo ...direct makarantar su ya nufa ...Soofy ya kira yace ta kira mashi Meenalle din ...</p><p><br /></p><p> Yana cikin mota ta iso sanye da maroon din hijab mai hannu ...cikin sanyin murya ta mashi sallama ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ya amsa kasa kasa tare da dagowa ya kalleta ..wani abu ya tokare mashi kirji ....ya lumshe idonshi ....</p><p><br /></p><p> Shiga tayi ta zauna ...tana zama ya rufe kofar yaja motar .....</p><p><br /></p><p> bata ce mashi komae ba ..har suka isa wani katon gida ..ba wanda aka aje Shamy a ciki ba ....</p><p><br /></p><p> Ya fito ya yi gaba abinshi ...haka itama ta biyoshi cikin sanyi jiki har ta iskeshi falon tsaye ....</p><p><br /></p><p> Bayanshi ta tsaya kanta na kasa tana wasa da yatsunta da suka sha jan lalle ....</p><p><br /></p><p> Juyowa yayi idonshi a lumshe ya kira sunanta ...a hankali ...</p><p><br /></p><p> Bata dago ba ...amma ta amsa a hankali ...</p><p><br /></p><p> Na dawo dake rayuwata Meenatou ba wae don ina son haka ba.....</p><p><br /></p><p> Idonta ya ciko da kwallah ...bata yi tunanin gogesu ba ...</p><p><br /></p><p> Ya cigaba ....Meenatou duk da irin son da nake maki kina yarinya lokaci guda kin gogeshi ...zan maki adalcine saboda abunda kika man ...amma maganar so ..babu sam ...bazan so yarinyar da ta yada darajarta ba. .....</p><p><br /></p><p> Da sauri ta kalleshi ....tana nuna kanta da hannu .....daraja Ma'aruf ....</p><p><br /></p><p> Yes Meenatou ...ya fada idonshi na kanta ...</p><p><br /></p><p> Girgiza kai tayi ...tana fadin ...Nagode sossae ..Meenalle Maikamshi ...na fita fitina Allah ..ko ka manta</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Murmushi yayi kasa kasa yace ...Ta ya zan manta ....wucewa yayi ya shige wani daki ya barta tsaye ....bayanshi ta bi itama ta shiga ....</p><p><br /></p><p> Bai kalleta ba....ya cire suit din dake jikinshi ya fada toilet ...hijab dinta ta cire ...ta haye saman gado ta kwanta .....</p><p><br /></p><p> Tana kwance ya fito daure da towel ya tsaya gaban mirrow daga ya shafa wannan sae ya shafa wannan ...kamar mace ...nan da nan dakin ya dauki kamshi .....</p><p><br /></p><p> Da gefen ido ya kallota tana kwance ta rufe ido ....takowa yayi a hankali ya sauko pillow a kasa tare da shimfida bargo ...ya dawo ya sabeta ya dire ta saman shimfidar ya koma ya kwanta saman gado ....</p><p><br /></p><p> Wallahi Ma'aruf baran kwana a kasa ba duk abunka ..ta fada tana kallonshi ...</p><p><br /></p><p> Hararanta yayi yace ...idan bara ki kwanta anan ba ki koma dakinki ..</p><p><br /></p><p> Itama hararan ta sake mashi tana fadin ..haka kuma baran kwana ni kadae ba ...Na rantse maka da Allah baran kwana ko ina ba...</p><p><br /></p><p> Juya baya yayi ya kyaleta ...yana jin lokacin da tazo ta kwanta gabanshi ...don neman magana ma daura kanta tayi a hannunshi tayi pillow ...</p><p><br /></p><p> Baice mata komae har tayi bacci a haka ..gangarowa tayi ta shige kirjinshi ...ajiyar zuciya ya sake tare da gyara mata kwanciya ...sannan shima baccin ya daukeshi .....</p><p><br /></p><p> Ya rigata tashi da asuba ...yayi wanka tare da alwala ...ya dawo ya tadata yaga har ta tashi ...jallabiya ya saka ya tada sallah ...sae da yayi nafila sannan ya jirata ta fito ya ja masu jam'i ......</p><p><br /></p><p> Yana kwance wajen 9 ta fito cikin shirin makaranta ...tun daga sama har kasa ya bita da kallo ...sannan ya kau da kai. ...</p><p><br /></p><p> Ki sako Hijab ..sannan ...ya fada ahankali ...</p><p><br /></p><p> Bata ce komae ba ta sako hijab din ta fito tana tura baki ...mikewa yayi ya dauki keys yayi gaba ..Kamar kurame suke tafiya...</p><p><br /></p><p> Restaurant ya biya da ita sae tayi breakfast sannan ya wuce da ita makaranta ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ......</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p> 💦Talented Writers Forum💦</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>85 to 86</p><p><br /></p><p><br /></p><p>kasuwa ya wuce ya sawo masu duk abunda zasu bukata sannan ya dawo gida ya aje kayan ya wuce office ...</p><p><br /></p><p> lokacin da Meenalle ta dawo ...sannan ta samu damar zagaye gidan ...ba karamar dukiya aka kashe mata ba ...dakin da take tunanin nata ne ta shiga .....buda baki tayi tana kallon ikon Allah ....drawer ta bude akwatuna ta gani set Hudu masu shegen kyau ...da kyar ta saukosu duka ta zazzagesu kaf kasa tana dagawa ....</p><p><br /></p><p> Dae dae lokacin Ma'aruf ya shigo dakin ...jingina yayi da kofar ya kallonta ...sae da ta gama daga komae ...sannan ta dauko wata sarka da yan kunne ta aje gefe guda ....tana fadin ....Duk da bana magana da maikamshi bara ya dawo ya fada man yarda ya sawota ...</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi tare da barin dakin ba tare da ta sani ba ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> da kyar ta mayar da kayan cikin akwatunan ..amma ta kasa maida akwatunan inda suke .....</p><p><br /></p><p> Cikin lefen ta fito da Riga da siket na material milk colour ta aje bisa gado .....wanka tayi sannan ta saka kayan tare da sarkan da ta fito ....</p><p><br /></p><p> Yana kwance falo daga shi sae farar singlet da boxer ja idonshi a rufe ...... </p><p><br /></p><p> Ta dade tsaye tana kallonshi ....sannan ta matso kusa dashi ta dafa kujeran ...Uncle Ma'aruf ta fada a hankali...</p><p><br /></p><p> Banza yayi da ita kamar bacci yake. ...sajenshi ta shafa...shiru ya mata ...amma wani zafi yake ji a ranshi </p><p>..</p><p><br /></p><p> Ma'aruf dan Allah ka tashi kayi hakuri ...wallahi bansan me na maka ba ka yafe man ....ta fada kamar zatayi kuka ...</p><p><br /></p><p> shiru ya mata .....tasake cewa ...kaji to Dan Allah idan bara ka bude idon ba ka fada man nawa ka sayi wannan sarkan mai stone a ja ta cikin wadannan akwatinan ...</p><p><br /></p><p> Dariya sossae ta bashi ...amma ya danne ya bude idoshi ...ya murde hannun da ta shafi sajenshi dashi ...ta sake kara tana kokarin janyewa ....</p><p><br /></p><p> Tashi yayi zaune ...sannan ya sake mata hannun yana hararanta ....duk lokacin da kika kuma tabani sae na karya hannu ....yana gama fada ya shige daki ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Zama tayi gurin ta sake kuka tana rike da hannun....</p><p><br /></p><p> Jin kukan yake har cikin ranshi ...keys ya dauka ya fice daga gidan kwata kwata</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Lokacin da ya dawo da daddare har tayi bacci a inda ya barta ...wuceta yayi ya shige daki yayi wanka sannan yayi kwanciyarshi .....juyi kawae yake amma babu alamun bacci a idonshi ....ganin kwanciyar ba zata fishsheshi ba ya saka ya fito falon .....</p><p><br /></p><p> Kanta na bisa hannun kujera ...ya dauketa ya daura saman doguwar kujera ....</p><p><br /></p><p> Cikinta ya shafa yaji kamar bata ci komae ba ...ledan da ya shigo dashi ya dauko ...kazane da fresh milk sae dugheese ya zazzage cikin plate tare da knife ...</p><p><br /></p><p> Kumatunta ya dinga shafawa tare da hura mata iska ...tayi saurin mikewa tare da sakin sabon kuka ...</p><p><br /></p><p> Shiiiiiitttt ya daura hannunshi saman lebenta ...sannan ya tura mata plate din ....</p><p><br /></p><p> Mikewa yayi ya koma saman kujera ya kunna TV ...hararanshi kawae take ...suka hada ido ...jira take yace.. taci ..amma ya shareta ...</p><p><br /></p><p> Hawayen takaici suka gangaro mata ...ya dan saci kallonta ...ta bashi tausayi ...</p><p><br /></p><p> Kici mana Meenatou ....ya fada a hankali don ya gane abunda take so taji kenan ..</p><p><br /></p><p> Hawayen ta saka bayan hannu ta share tana fadin ...dama ko baka ce na ci ba yanzu nayi niyyar ci ....</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi kasa kasa ....baice mata komae ba ...</p><p><br /></p><p> Har ta koshi sannan ta dawo kusa dashi ta zauna kasan carpet .</p><p>..</p><p><br /></p><p> Plate din ta mika mashi ...tana kallonshi ..</p><p><br /></p><p> Harara ya banka mata ....tayi saurin dauke kai tana fadin ..</p><p>dan Allah kaci kaima ...</p><p><br /></p><p> Murmushi ya sake kasa kasa yace ..ba bukata ...</p><p><br /></p><p> Please ....ta fada ..</p><p><br /></p><p> Girgiza kai yayi yace ...A da Meenatouta tayi forcing dina naci irin haka .. yanzu ke ba tawa bace ...kuma baran ci ba ....ya mike ya shige daki ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ni din taka ce ...ta fada a hankali sannan ta mike ta shiga dakin </p><p><br /></p><p> Kayanta ta cire daga ita sae inners...sannan ta daura towel ta shige toilet ....akan idonshi tayi komae har ta fito ....duk abunda yake shafawa sae da ta shafa ....sannan ta leka fuskarshi taga idon a rufe ...murmushi ta sake tana murza hannu..</p><p><br /></p><p>..</p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>87 to 88</p><p><br /></p><p>Pillow ta sauke kasa tare da shinfida bargo ....sannan ta hawo gadon ta koma gabanshi ta dinga murginoshi kasa ....</p><p><br /></p><p> Yana jinta yayi banza da ita yasan dai barata iya daukarshi ta maidashi kasa ba. ..sae uban nishi take ...sae da ta gaji dan kanta taga bara ta iya maidashi kasa ba ....sannan ta janyo hannunshi ta daura kanta ....bata fi minti 10 ba ya gane bacci ya dauketa ta gangaro jikinshi ...ya saka hannun ya gyara mata kwanciyar sannan shima baccin ya daukeshi ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°•• </p><p><br /></p><p> Ganin bata fito ba har karfe 9 ya saka ya leka dakinta ....tana kwance saman gado ido a rufe ....</p><p><br /></p><p> Meenatou ...ya kirata a hankali ....</p><p><br /></p><p> Shiru ta masa ....Ki fito ina jiranki falo ....ya wuce abunsa ...</p><p><br /></p><p> Yayi minti 20 yana jiranta amma shiru bata fito ba ......</p><p><br /></p><p> Dan karamin tsaki ya sake lokacin da ya duba agogon dake makale a hannunshi ....</p><p><br /></p><p> Ya koma dakin a fusace ya tsaya bakin gadon tare da dago kanta ....</p><p><br /></p><p> Da sauri ya taro kan ...ganin ya koma da kanshi ....jijjiga yayi ...yana kiranta ....sae lokacin ya lura da ba lumfashi a jikinta .....</p><p><br /></p><p> Daukarta yayi ya sakata mota ya ja motar da gudu ...tun yana tafiya ya kira doctor </p><p><br /></p><p> Yana zuwa suka amsheta emergency ....kusan 1hours sannan aka samu numfashinta ya dawo normal shima da taimakon oxygen ...</p><p><br /></p><p> Ma'aruf na wajen dakin sae..kae da kawowa yake ...doctor na fitowa ya tareshi yana tambayar lafiya ...</p><p><br /></p><p> ce mashi yayi ..zafin masassara ne ke damunta ... da marece aka sallamesu suka koma gida ....</p><p><br /></p><p> A gate din gidan ta saka mashi kuka wae barata iya takawa ba ....jikinta ya taba yaji da zafi ...sannan ya dauketa suka shiga ...</p><p><br /></p><p> </p><p>Dakinshi ya direta ...ya shiga kitchen ya dafa mata ruwan zafi ..sannan ya dafa mata kwae guda biyu ya kawo mata ....Ya aje saman stool din dake gefen gadon ya fita ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sae da yayi kusan Awa daya sannan ya dawo ...yarda ya aje haka ya tarad da abunshi ...ya kalleta ta gefen ido ...ta maida hankalinta kan wani dan karamin littafi dake aje gefen gadonshi ...</p><p><br /></p><p> Bakya jin yunwa ne Meenatou ...ya fada tare da zama gefen gadon ...</p><p><br /></p><p> Bakya jin yunwa ne Meenatou ...ta maimaita abunda ya fada tare da sake mashi harara ..sannan tace ....ko wannan abun zaya shekara anan baran ci ba duk da ina jin yunwan ..tunda nima lokacin da baka lafiya idan naje gidanku ai a baki nake ba ...nima din sae ka rama man ..har dukana ake a makaranta idan na makara ..to wallahi sae ka rama man .. </p><p><br /></p><p> Murmushi yayi kаsa kasa tare da fadin ...Dama Halinki ne Meenatou ...gori ba ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sannan ya janyo flask din ya hada mata tea din tare da dauko sandwitch ya mika mata ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ka Wanko hannunka ta fada tana hararanshi ...</p><p><br /></p><p> Ni ai ban taba hamatar ko wane kato ba ...ya bata amsa ba tare da ya kalleta ...</p><p><br /></p><p> Nima da nake tabawa ai yanzu na daina ....</p><p><br /></p><p> Sae ta mata? ...ya tambayeta tare da kura mata ido ...</p><p> </p><p><br /></p><p> Bata ce komae ba ta koma ta kwanta tare da rufe idonta .....</p><p><br /></p><p> Ki tashi kici ....ina da aikin yi da yawa ...ya fada tare da kallonta ...</p><p><br /></p><p> Bata motsa ba tace ...Alhamdulillah ...</p><p><br /></p><p> Kafada ya dage tare da ficewa daga dakin .....</p><p><br /></p><p> Bai kuma dawowa ba sae bayan isha'i ....</p><p><br /></p><p> lokacin ta dan tashi tayi wanka tare da sallah sannan ta koma ta kwanta amma jikinta kamar wuta ga Uwar yunwar dake damunta. ..kuka take a hankali ...</p><p><br /></p><p> Ya shigo da sauri ya shige toilet yayo alwala tare da kabbara sallah .. ..</p><p><br /></p><p> Sannan ya janyo ledar daya shigo da ita ya fito da abunda ke ciki ...</p><p><br /></p><p> Ya zauna yaci ya koshi sannan ya yo wanka...sae lokacin ya leka fuskarta ...tare da duba duba abunda ya bar mata ...</p><p><br /></p><p> Da Sauri ya kira sunanta ....Meenatou ...</p><p><br /></p><p> Tana ji tayi banza dashi ...hannu ya sanya ya cire hannunta dake saman goshinta ...</p><p><br /></p><p> Zafi sossae yaji jikinta ...nan da nan ya rude ..ya janyo kayan da ya. shigo dasu ..ya fito da Fresh milk ya bata ...da yake yunwa take ji ..batayi gardama ba ta amsa. ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💧💧SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>89 to 90</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Towel ya jiko da ruwa sannan ya dawo zaya jika mata jiki ....</p><p><br /></p><p> Bargon data nannade jikinta dashi ya cire tare da tadata zaune zaya cire man shirt din dake jikinta ....</p><p><br /></p><p> Hannunshi ta rike ...duk da zafin masassaran dake damunta bai hana ta sake mashi harara ba tare da fadin. ...Meye zaka cire man riga ...</p><p><br /></p><p> Karamin tsoki yaja ..yace ...cire hannunki daga jikina Meenatou ...</p><p><br /></p><p> Allah Ma'aruf bara ka ga jikina ba ....ta fada kamar zatayi kuka ..</p><p><br /></p><p> Hararanta yayi tare da fadin..Meye a jikin naki da zan kalla Meenatou ...jikin da kowace kazama ta gama kallo ..mtsee ..</p><p><br /></p><p> Hannunta duka biyu ya hade ya rike da hannu guda tare da cire mata rigar ...ya barta daga ita dae bra .....haka ya zare Siket din ya bar mata Pant ...sae uban ihu take mashi amma ko kulata bai yi ba ....</p><p><br /></p><p> Har sae da zafin jikinta ya ragu sannan ya sake hannun sae lokacin ya lura da tayi bacci ....</p><p><br /></p><p> Har ya dauko rigar zaya maida mata ya tsaya tare da kurawa surarta ido ...tabbas Meenalle ta hadu ta ko ina ....</p><p><br /></p><p> Sauke ajiyar zuciya yayi tare da jefar da rigar gefe guda ...ya mike yayo wanka ya kashe haske sannan ya dawo ya kwanta ....janyota yayi ya rungume yana maida numfashi a hankali ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Da asuba ta rigashi tashi ....ta kwace kanta daga rikon da ya mata ...tare da sake ihu ganin yarda take ...lokacin jikinya ya koma lafiya lau ...</p><p><br /></p><p> Jikinshi ta haye tare da dukanshi da pillow tana fadin Allah ya isa ka gani Maikamshi ...ganin hakan bai mata ba ya saka ta daga jallabiyarshi ta zare hannuwan ta cireta ...ta barshi daga shi sae boxer dake jikinshi tare da sake mashi cizo a kumatu tana fadin ...Nima na rama ...kuma baran kara kwana da kai da mugu ....ta dauki rigarta ta fice daga dakin ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tana fita ya mike tare da girgiza kai ..don duk abunda take yana jinta shareta kawae yayi ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ••°°••</p><p> </p><p> Lokacin sun gama Exam ba makaranta ..da safe ta hada masu Break su zauna su ci tare sae dae babu magana sae harare harare ... </p><p><br /></p><p> Ranar da daddare taki zuwa dakinshi ...duk da take ...haka shima ya kwanta sae juyi yake ...kusan Karfe biyu yaji ta bude kofa a hankali tare da kwanciya kusa dashi .....bai yi motsi ba sae da ya tabbatar bacci ya dauketa sannan ya janyota jikinshi ...a haka bacci ya daukeshi ......</p><p><br /></p><p> tunda Asuba ta sulale ta koma dakinta a tunaninta bai sani ba ...</p><p><br /></p><p> Da Safe da ya fito ..kamar abun arziki ta tareshi tace ..</p><p><br /></p><p> Good Morning ...</p><p><br /></p><p> Ya dan kalleta kafin yace ....Morning ...sannan ya ja kujera ya zauna ...</p><p><br /></p><p> Ta hada mashi komae sannan ta tura mashi gabanshi tana fadin ...kasan me yasaka na gaidaka ?,..</p><p><br /></p><p> Girgiza mata kai yayi yana kallonta ...</p><p><br /></p><p> Ta washe baki tana fadin ...so nake bakin ciki ya dameka na kwana ni kadae ban mutu ba ...ta watsa mashi harara ...</p><p><br /></p><p> Dariya ya sake har da rike ciki .....</p><p><br /></p><p> Me kakewa dariya ..? ta tambayeshi tana hararanshi. ..</p><p><br /></p><p> Hararan ya maida mata ba tare da yace mata komae ...har ya gama breakfast dinshi ya mike ya tafi office ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Haka da daddare ranar yana jin lokacin da ta dawo jikinshi yayi murmushi ya janyota ya rungume ...da asuba yana jin tana kokarin kwace kanta amma yaki sakinta ....</p><p><br /></p><p> Tayi kwance sae Mazurai take ...ya bude ido tare da zuba mata harara ...</p><p><br /></p><p> Ta hadiyi yawu tare da zuba mashi harara itama sannan tace ....</p><p><br /></p><p> Daga zuwa tayar dakai Sallah sae ka rikeni ....</p><p><br /></p><p> Harara ya zuba mata yace ...ta ina kika shigo ...</p><p><br /></p><p> Ta kalli kofar tare da fadin ...ta kofa mana ...</p><p><br /></p><p> Keys din kofar ya fito daga kasan filon daya daura kanshi ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💧💧SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p>================= Gidan Novels =====================</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>91 to 92</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Turo baki tayi tare da fadin ...To Maikamshi na dawo din dakinka sae akayi me ..dadin abun ma ba cire maka kaya nayi ba nace zan gasa maka jiki don na kalleka ..kuma anan din ma zan dinga kwana kullun duk tsiyarka....tana gama fadar haka ta mike tare da fadawa toilet ..</p><p><br /></p><p> dariya ya dinga yi sossae yana jinjina baki irin na Meenalle ..gashi dae ya nuna mata ya san nan take kwana maimakon ta nuna taji kunya sae ma ta nuna ta fishi baki ....</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>°°••°°</p><p><br /></p><p> Zamansu haka ya fara damunta ..har lokacin bai fada mata asalin laifinta ba ..sae dae ya dinga jifarta da maganganu ......</p><p><br /></p><p> Soofy ta kira a waya ta fada mata matsalarta ....</p><p><br /></p><p> Shawarwari ta bata sossae tace ta dameshi ya fada mata laifin da tamashi ..sannan kar tayi zuciya baa banza yake mata haka ba ....</p><p><br /></p><p> yana zaune falo ...rike da wani novel .. tayi sallama ba tare da ya kalleta ba ya amsa mata ...</p><p><br /></p><p> Hannushi ta bude tashige jikinshi tare da maidawa ta rufe ....</p><p><br /></p><p> Ya dan Saci kallonta ...tana sanye da karamar riga pink sae three quater baki ....manyan kalaba ne akanta ....ya saki ajiyar zuciya tare da maida kallonshi ga littafin ....</p><p><br /></p><p> Ta rasa yarda zata mashi magana ...shimq ma ya gaji da zaman da take a jikinshi Allah kadae yasan me yake ji ....</p><p> Ya rufe littafin tare da zareta ya maidata saman kujera yana fadin .</p><p><br /></p><p>Menene Meenatou ..</p><p><br /></p><p> Bakomae ...Dama magana nake son muyi ...ta fada a hankali ...</p><p> </p><p> Ina saurarenki ....ya fada tare da lumshe ido..</p><p><br /></p><p> Dan Allah ina so ka fada man abunda na maka ....</p><p><br /></p><p> Banda lokacin wannan maganar Meenatou ...tashi ki fitar man daga falo indae wannan ya kawoki .</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kayi hakuri dan Allah .....Da Kana sona Ma'aruf ...amma yanzu me yasa kake man haka ...ta fada a hankali ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Saboda bana sonki yanzu ...ya fada kai tsaye ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kana sona mana ...ta fada tare da sakin kuka ..</p><p><br /></p><p> Idanuwanshi sukayi jawur ..cikin tsawa yace ..karya kike bana sonki Meenatou ...ya karashe maganar tare da fadawa saman kujera ya dafe kanshi</p><p><br /></p><p> Kai ta girgiza tare da fadawa dakinshi da gudu ...</p><p><br /></p><p> Drawer dinshi ta dinga janyowa tana kuka har ta fito da glass din da ribbon din da ta bashi yake ...sannan ta fito dakin ...</p><p><br /></p><p> Yana ganin ta fito ya mike da sauri tare da nunata yana fadin ...ki mayar dashi Meenatou .</p><p><br /></p><p> Cikin kuka tace.. idan baka sona me kake da wannan ...</p><p><br /></p><p> Ki maidashi nace Meenatou ..ya fada tare da nufota ...</p><p><br /></p><p> Kasa ta jefar dashi da karfi glass din ya fashe ...</p><p><br /></p><p> Daga hannu yayi da niyar marinta yayi saurin rufe ido ....ta cikin fasasshen glass din ta bi zata wuce ....</p><p><br /></p><p> Da sauri ya duka tare da saka hannunshi inda zata taka saman kwalaban ...</p><p><br /></p><p> Rufe ido tayi zata daura kafar a hannunshi Ta taka ta wuce ....amma ta kasa ...kuka ta sake da karfi tare da juyawa ta canza hanya da gudu .....</p><p><br /></p><p> Binta yayi da kallo ...hawayen dake makale a idonshi suka sauko ...ya dauke ribbon din ..sannan ya kwashe kwalbar ya koma daki ....</p><p><br /></p><p> °°••°°</p><p><br /></p><p> Kusan satinsi biyu a haka ...gurin bacci kawae ke hadasu </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Duk rintsi basu raba makwanci duk da ba wani abu ke shiga tsakaninsu ba ...sae dae ta daura kanta a hannunshi ...idan tayi bacci ya maidota jikinshi ...</p><p><br /></p><p> Soofy ta sake kira tagaya mata yarda sukayi ...</p><p><br /></p><p> Cewa tayi Meenalle kiyi hakuri ki sake jaraba tambayarsa karkiyi zuciya ...indae kinyi imani da soyayyar da yake maki tun ta yarinta to har yanzu akwaeta ....</p><p><br /></p><p> To kawae tace ...zata je amma wannan shine na karshe ...idan ya fada mata to ..idan kuma bai fada mata ba. ..sae dae su cigaba da zama haka ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ....</p><p><br /></p><p> </p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p> 93 to 94</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shigowa Meenalle tayi yana zaune yana kallo ....ta samu guri ta zauna ..tana kallonshi ...</p><p><br /></p><p> Mr Ma'aruf ....ta fada a hankali ....</p><p><br /></p><p> Ido ya dago a lumshe ...yace . Meenatou Wani abu kike bukata ....</p><p><br /></p><p> Girgiza kai tayi a hankali tana wasa da zoben dake hannunta. ...</p><p><br /></p><p> Ok. .ya fada tare da cigaba da kallonshi ...</p><p><br /></p><p> Ganin baida niyar kulata ya saka ta mike ta koma kusa da kujeran da yake zaune. ..</p><p><br /></p><p> Ta kwantar da murya tace ...Kayi hakuri Ma'aruf ...wallahi bansan laifin da na maka ba ...Dan Allah ka yafe man ...</p><p><br /></p><p> Ya danyi murmushi ciki ciki yace ...Meenatou kenan na rasa kalmar zan bi wajen fada maki ki daina zuwa inda nake amma kin kasa ....please ki fice daga falon nan ....</p><p><br /></p><p>Daga kai tayi tana kallonshi idonta cike da hawaye tace ..Dan Allah Ma'aruf ka fada man laifin da na maka ...wallahi bansan nayi maka shi ...tun ina karama muka rabu ..yaushe har mukayi haduwar da ka tsaneni kuma wane kalar laifi na maka ...</p><p>Kayi hakuri dan Allah nice fa Meenalle Ma'aruf ka tausaya man mana. ...</p><p><br /></p><p> sossae yaji tausayinta ...sae dae yana tunano pictures din da Raliya ta nuna mashi ...tsawon shekaru masu yawa da suka wuce ....lumshe ido yayi ...yace ...Idan har Meenatou zaki iya bawa wata wace jikinki shekaru da suka wuce tun kina yarinya to yanzu fa ....</p><p><br /></p><p> Kuka ta fashe dashi tace ...ban fahimceka ba Ma'aruf ...wallahi ban gane me kake nufi ba .....</p><p><br /></p><p>Mikewa yayi ya daga hannunta sama tare da janta har zuwa kofar falonshi...ya bude tare da turata waje. ...karki kuma zuwa falona ...</p><p><br /></p><p> Kuka ya kwace mata ta toshe bakinta ta juya da gudu ...sae ji tayi ya kamo hannuta tare da sakata a jikinshi ya rungumeta ....</p><p><br /></p><p> Daga kai tayi sossae tana kallonshi ...sannan ta maida kanta a kirjinshi ...tana jin lokacin da ya sake ajiyar zuciya ...a haka ya zauna saman kujera tana kirjinshi ...sun dade a haka sannan ya dago kanta yana kallonta ...</p><p><br /></p><p> Meenatou ...yaja sunan...</p><p><br /></p><p> Bata amsa ba sae da ta kalleshi ...kin san Raliya ...ya tambayeta ..</p><p><br /></p><p> Girgiza kai tayi a hankali tana share hawaye ......</p><p><br /></p><p> Mikar da ita yayi ya zaunar da ita sannan ya shiga dakinshi .</p><p>ya fito dauke da wata waya ya kunna tare da mika mata a hannu ...</p><p><br /></p><p> Da sauri ta yardar da wayar tare da sakin kuka ....take ta tuno da abunda ya faru lokacin da ta shiga gidan wadannan yan iskan ...</p><p><br /></p><p> Wallahi dole suka man Ma'aruf ...ta fada tare da buga kanta jikin hannun kujera ...</p><p><br /></p><p> Fuskarta ya kamo ya saka hannunsa cikin gashinta ...yana kallonta ...</p><p><br /></p><p> Kwantar da kanta yayi bisa kirjinsa ...Sorry Meenatou ...i trust you yanzu kinji ko ...kiyi hakuri ..na yarda baki aikata ba ...</p><p><br /></p><p> Kuka take sossae bata ga laifinshi ba abunda ya mata ...don ta tabbata kara karuwa mai bin maza da yar lesbian ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Cikin kuka take fadin wallahi banyi ba Ma'aruf ...me yasa ka yarda ...</p><p><br /></p><p> Lallashinta ya dinga yi har ya samu tayi shiru. ..shima yayi nadamar abunda ya dinga mata ...ashe bada hakkinta ba .....</p><p><br /></p><p> a haka bacci ya dauketa sae ajiyar zuciya take ....Allah kadae yasan iya kissing din da ya mata ...kafin ya dauketa ya kaita dakinshi ya kwantar da ita saman gado ya fita ....</p><p><br /></p><p> Cikin wayar ya duba ...number raliya ya gani ...yayi hamdala Allah yasa bai gogeta ba ...tunda dama tunda abun ya faru da ya dauki wayar bai kuma kunnata ba ....</p><p><br /></p><p> Ringing daya ta dauka ...ya tambayeta inda take ...da yake bata ganeshi ba tunda ba da numbershi ya kirata ba. . ta mashi kwatancen gidan da suke ...da yake ta dawo da taga nigerian ba harka</p><p><br /></p><p> Direct can ya nufa ....yana zuwa yacewa mai gadin ya kira mashi ita ....</p><p><br /></p><p> Ta fito rike da sandar guragu tana tafiya .....lumshe ido yayi lokacin da ta iso ...</p><p><br /></p><p> Mr Ma'aruf ...ta fada tana washe baki ...</p><p><br /></p><p> Alhamdulillah Raliya ...yaushe kika zama haka ....</p><p><br /></p><p> Tabe baki tayi tace ...accident muka samu wallahi ..amma dad yace zaa gyara man kafar ta koma kamar yarda take da ...idan aurena kazo karka damu da wannan ...</p><p><br /></p><p> Dariya ya sake ...yace ai ta riga ta zama haka Raliya ..wannan shine makomar munafiki...kin rabani da Meenatou kike tunani ...well da zuwa nayi ki fada man wace shegiyace tayi forcing din Meenatou ...amma yanzu yarda na ganshi ma naji dadi ..dan nasan soon itama waccen zata hadu da tata kalar masifar ....</p><p><br /></p><p> Yana gama fadar haka ya shige mota ya barta tsaye .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p>95. to. 96</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kwafa tayi ta shige cikin gidan tana dogara sandarta ....</p><p><br /></p><p> Yan matane birjit sunata shashansu ....kusa da wata taje ta zauna ...tana rada mata magana a kunne ...murmushi sukayi tare da tabawa ...</p><p><br /></p><p>••°°•• </p><p><br /></p><p> Zaune ya isketa tana cin Apple ...kusa da ita ya zauna yana murmushi ...</p><p><br /></p><p> Har kin tashi ....ya fada tare da kanne mata ido ...</p><p><br /></p><p> Da kai ta bashi amsa sannan ta mika mashi wanda ke hannunta ...</p><p><br /></p><p> Bai amsa ba sae dae ya bita da ido tare da janyota jikinshi ....</p><p><br /></p><p> Am sorry Meenatou ....ya fada a hankali ...</p><p><br /></p><p>Batace komae ba ta saka mashi apple din a baki tare da mikewa ta dauko mashi dinner ....</p><p><br /></p><p> A plate ta zuba mashi ta tura mashi gabanshi kamar yarda ta saba ...sannan taja nata ...</p><p><br /></p><p> Kujeran da take zaune ya dawo ya dagata sama ya zauna sannan ya daurata saman cinyarshi ....ya karbi plate din ya debi tare da bata a baki ....</p><p><br /></p><p> aa Maikamshi ....ta fada tare da kau da kai gefe guda ....</p><p><br /></p><p> Why Meenatou ....? .</p><p><br /></p><p> Ka manta abunda kace ...ta fada tare da kura mashi ido ...</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi tare da girgiza kai ...Me na fada Meenatou ...</p><p><br /></p><p> Hararanshi tayi tare da fadin ...ka manta kace bara ka taba bani abinci da hannunka ba ...</p><p><br /></p><p> Dafe kanshi yayi ...dama yasan zaa rina. yanzu komae ya mata baya yasan sae ta dinga tunawa tana fada mashi ...</p><p><br /></p><p> Cikin lallashi ya shafi wuyanta ....tare da langwabar da kai yace ...To ai lokacin Meenatou kin bata man raine ...</p><p><br /></p><p> Harara ta banka mashi tace ...yanzu fa. ...</p><p><br /></p><p> to yi hakuri na tuba kinji ko ...ya fada tare da mika mata abinci ..</p><p><br /></p><p> Karba tayi tare da kwafa ....</p><p><br /></p><p> Shi ya rigata fitowa daga wanka ...ya shinfida tarduma yana jiranta ....</p><p><br /></p><p> Sanye da kayan bacci ta fito daga toilet din....</p><p><br /></p><p> Sabon salo ...ya fada a ranshi ...bai san taji shi ba ...sae da ta banka mashi harara tare da hayewa gado abinta ..</p><p><br /></p><p> Meenatou ...ki sauko muyi sallah ko ...? .</p><p><br /></p><p> Nayi a toilet ...ta fada tare da gyara kwanciya ...</p><p><br /></p><p> Girgiza kai yayi ya tada sallah shi ya gama sannan ya hawo gadon tare da janyota ...</p><p><br /></p><p> Kin tuna?,...ya fada cikin kunnenta ..</p><p><br /></p><p> Girgiza kai tayi tana kallonshi...</p><p><br /></p><p> Lumshe ido yayi ..yace ...lokacin da kika ceman malamarku bata sallah ..yanzu ai kin gane dalilin rashin yinta ...</p><p><br /></p><p> Duka ta kai mashi a kirji tare da lafewa tana dariya ...</p><p><br /></p><p> Shima dariyar yayi yana fadin ...I love you Meenatou you're my everything ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Tana zaune taji Sallama ...ta mike tare da daukar hijab ..</p><p><br /></p><p> Tana bude kofar ta sake uban Tsalle tare da rungume kaka ...</p><p><br /></p><p> Imagine kakata ...ta fada tana dariya ...</p><p><br /></p><p> Hajiya tayi zuru tana kallonta ...sae da kaka ta buge mata hannu tana fadin ...baki ga hajiya bane ..</p><p><br /></p><p> Turo. baki tayi tace. ..na ganta ..ai bata sona ...</p><p><br /></p><p> naki kaniyarki Meenalle ..bata sonki ta hawo jirgi kamar zamu fado tazo inda kike ....</p><p><br /></p><p> Ma'aruf dake tsaye jingine da kofa tunda suka shigo ..sam bata lura dashi ba ...</p><p><br /></p><p> Ya ja hannu hajiya yana murmushi yace ...Taho hajiya rabu da ita zata neme mu ne da kanta ...</p><p><br /></p><p> Sae lokacin tasan tare suke ...ba kunya ta nufeshi tare da rungumeshi ta mashi kiss a kumatu ...</p><p><br /></p><p> Oyoyo ......</p><p><br /></p><p> Hancinta yaja a hankali har ta saki kara ...yace ...baran amsa ba ..</p><p><br /></p><p> Ta dan ja baya kadan tare da waro idanu tana kallonshi ...acikin shagwaba tace ...Why ..</p><p><br /></p><p> Hannu ya mika mata ta matso kusa dashi sannan ya kalli hajiya ya kalleta ...</p><p><br /></p><p> Murmushi tayi taje ta rungumi hajiyar tana mata sannu da zuwa ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>97 to 98</p><p><br /></p><p> </p><p> Bayan sun hutane Kaka ta kurawa Meenalle ido tace ..</p><p><br /></p><p> Meenalle banga alamar samun da ba da wuri ....</p><p><br /></p><p> Kaka a Ina ...ta tambayeta cikin rashin fahimta ..</p><p><br /></p><p> to ba hausa ina nufin banga ciki ya fito ba ...</p><p><br /></p><p> Ta sake dariya tare da kwalawa Ma'aruf kira ....yana tsaye yana shan ruwa gaban fridge ya iso yana tambayarta lafiya da ido ..</p><p><br /></p><p> Hannunshi ta janyo tare da zaunar dashi kusa da kaka tace ....Fadawa kaka me kace ..</p><p><br /></p><p> Me nace kuwa Meenatou ....ya tambayeta a hankali ..</p><p><br /></p><p> Harara ta sake mashi ...ya saurin dafe kai ...yasan Meenalle da naci ta yiyu wata magana ya mata shine bata hakura ba zata tada ta yanzu ...</p><p><br /></p><p> Lokacin da kace bana da ko. ...</p><p><br /></p><p> bata karasa ba ya tashi tare da jan hannuta da karfi ya shige da ita kitchen ...</p><p><br /></p><p> Am sorry Meenatou ...baran sake fadar komae ba ...</p><p><br /></p><p> Harara ta sake mashi tana fadar ...naji to ka sake man hannu ko ....</p><p><br /></p><p> Zan sake amma karki sake fadar komar kinji ko ...ki manta ...</p><p><br /></p><p> In manta me ..har cewa da kayi karuwa ta ...</p><p><br /></p><p> bakin ya murde ta sake kara ...ya daure fuska sossae ...yace ...</p><p><br /></p><p> Kar na kuma jin wannan kalmar a bakinki ....me kika hadawa su kaka .</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yanzu dae zaka tayani mu hada masu ..ta fada tare da kwantowa jikinshi ....</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi suka fara aikin tare sae da suka gama girkin suka gyara kitchen din tare </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kwanansu goma cif ...tun Meenalle bata sakin jiki da Hajiya har ta koma tana sakin jikinta kamar yarda take da kaka ...</p><p><br /></p><p> Ranar da suka tafi kuwa kuka ta yini mashi ...sae da kyar ya samu ya lallasheta tayi shiru ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Da yake rigima take ji ...ko abinci bata masu ba ...fita yayi ya sawo masu abinci ...inda yake sawo wa ya samu sun rufe ...sae ya sawo mata kaza da ice cream ya dawo ....</p><p><br /></p><p> Tana kwance bisa kujera ya dawo ko dan oyoyon da ta saba mashi batayi ba ...ya wuceta ya shiga kitchen ya dauko plate ya juye da knife sannan ya dawo falon ...</p><p><br /></p><p> Ya leka fuskarta tare da kiran sunanta a hankali ...Meenatou ...</p><p><br /></p><p> Zaune ta tashi tana sharar kwalla ...da sauri ya rungumota ..</p><p><br /></p><p> Ya Salam Meenatou ...kukan ne har yanzu ...Sorry yi shiru kinji ko ...Muna next month zamu je ....</p><p>Da sauri ta washe baki ...tana fadin da Gaske ...</p><p><br /></p><p> Daga mata kai yayi alamar eh ...tare da janyo plate din </p><p><br /></p><p> sauko kici ...</p><p> </p><p>Saukowa tayi tana cin abunta ba tare da ta sake cewa komae ba ...sae da ta koshi sannan ta kalleshi tana murmushi tace ...</p><p><br /></p><p> Kasan dama ina son kazar amare ..amma wadda na taba ci bata kai dadin ta nan ba ...</p><p><br /></p><p> Hararanta yayi yana fadin ..waya baki wata kazar amare ...</p><p><br /></p><p> Musa ya sawo man ita ...amma karamace bata isheni ba ...</p><p><br /></p><p> Baki ya tabe yace. ..Bata amaren bace shi yasa kika cinye...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Allah itace....kuma ban rage ko kadan ba ....</p><p><br /></p><p> Dawowa yayi kusa da ita tare da janyo hannunta yana murzawa ....</p><p><br /></p><p> Idan na sawo maki ta amaren zaki cinye ...ya fada dae dae kunnenta</p><p><br /></p><p> Harara ta sake mashi tana fadi ...dukanta kuwa .. .</p><p><br /></p><p> Girgiza kai yayi tare da jan hancinta .....</p><p><br /></p><p> Idan na sawo maki ta amaren ma Meenatou bara ki ci ba ....</p><p><br /></p><p> Giranta ta hade tana fadin Kana wasa da ni ...</p><p><br /></p><p> Ko ? .. ya tambayeta .....</p><p> </p><p> Eh .....</p><p><br /></p><p>Zakiyi bayani da kyau ...ya fada tare da mikewa tsaye ...</p><p><br /></p><p> Kaima din zakayi bayani .....ta fada tana hararanshi ...</p><p><br /></p><p> Hannunta ya janyo ta mike tsaye yana kokarin zura hannunshi cikin rigarta </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p>99 to 100</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Saurin rike hannunshi tayi ..Meye haka ...ta fada kamar zatayi kuka ...</p><p><br /></p><p> Bayanin nake so ki sakani nayi da kyau ...</p><p><br /></p><p> Bafa irinshi nake nufi ba ....ta fada tare da dukar da kanta kasa ....</p><p><br /></p><p> Hmm ....kawae yace ..ya saketa ya shige daki ...bayanshi ta bi ....tana murmushi ita kadae ...ya dan juyo ya kalleta tayi saurin juya baya itama ....murmushi ya sake sannan ya juya ....</p><p><br /></p><p>°°••°°</p><p><br /></p><p> Kayan Sport ya aza mata saman jiki ....</p><p><br /></p><p> Ta waro ido tare da kallonshi ..har ya sako nashi ...riga da wando sae hula tare da safar hannu da takalmi ...da yake kayan yellow ne ...sae sukayi bala'in mashi kyau ...abunka da fari ....</p><p> </p><p><br /></p><p> Ki tashi kin canza kayan ..ko sae na canza maki da kaina ...ya fada tare da kamo hannunta ....</p><p><br /></p><p> Harara ta sake mashi tare da cire siket din dake jikinta ta saka wandon ...sannan ta juya mashi baya </p><p><br /></p><p> Bude man zip din ...ta fada a hankali ....</p><p><br /></p><p> Zip din rigar ya zage mata ...ya kai hannu ya shafi wani digon baki dake tsakiyar bayanta ...sannan ya saka hannu ta baya ya karbi rigar daga hannunta ...</p><p><br /></p><p> Hannunta ta daga sama ya zura mata rigar ...sannan ya duka ya dago kafarta ya daura saman cinyarshi ya saka mata takalmin ...tare sa safar hannu sa hula ...ya ja hannunta ...</p><p><br /></p><p> Wani labule ya daga ...wanda ke facing din side dinta ....ta bishi da kallon mamaki ganin koface a gurin ...don duk zamanta bata san meye a gurin ba ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Wani abu ya danna a jikin kofar ...glass din ya bude suka wuce ....sae da suka wuce wani dan corridor sannan suka isa wani katon fili ....</p><p><br /></p><p> Ido ta bude tana kallon gurin ...kamar baa gidan ba ...</p><p> </p><p><br /></p><p> Gurin yayi masifar kyau ...har da filin football gefe guda an zagayeshi da net ...sannan swimming pool shima zagaye da net din...</p><p><br /></p><p> Sae gurin table tennis da volley ball hade ...</p><p>Gefe daya kuma flowers ne masu shege kyau ....ganin ta sake baki tana kalle kalle ya saka ya kwanto bayanta ...</p><p><br /></p><p> Me kike so muyi aciki ...</p><p><br /></p><p> Ido ta waro tare da nuna mashi Volley ball din ...</p><p><br /></p><p> Oya let start ....ya dauko kwallon tare da wullo mata ...</p><p><br /></p><p> Ka fara buguwa ...ta fada ban mata iya komae ba .....</p><p><br /></p><p> Sae ya bugo mata Ball biyar bata maido mashi ko daya ba ...amma da ta samu ta bugo mashi sae ta hau tsalle tana mashi gwalo ..</p><p><br /></p><p> Bata iya komae ba Sae masifar rintu ....har sae da aka fara kiran magrib sannan ya ce ta taho su koma ciki ...</p><p><br /></p><p> Zubewa tayi gurin ta mike kafa tana nishi ...</p><p><br /></p><p> Mene Meenatou ...kin gaji ko ...ya fada tare da dagata sama ...</p><p><br /></p><p> kafana baran iya tafiya ba ....ta fada kamar zatayi kuka ..</p><p>Da sauri ya duba kafar baiga abunda ya sameta ba ...</p><p><br /></p><p>haka ya sabeta a kafada ...ya direta gaban fanfon dake gurin sukayi alwala ..sannan ya sake daukarta ya kaita dakinshi ya shinfida mata darduma ...</p><p><br /></p><p> Ya fice masallaci ..</p><p>Ya saba dawowa da anga Sallah ...amma ranar sae da ya tsaya aka yi Isha'i sannan ...ya dawo ...</p><p><br /></p><p> Tana tsaye bakin kofa kamar zatayi kuka ...ya shigo ...da sauri ta juya mashi baya ...</p><p><br /></p><p> Rungumota ta baya yayi tare da daura kanshi saman wuyanta yana shakar kamshinta</p><p><br /></p><p> Nayi laifi ...tuba nake ....ya fada cikin kunnenta .....</p><p><br /></p><p> Make kafada tayi tana murza idonta ....</p><p><br /></p><p> am sorry Meenatou ...ya fada a hankali ..</p><p><br /></p><p> juyowa tayi tana kallonshi tace ..To ina ka tsaya ...</p><p><br /></p><p> juyota yayi tana facing dinshi yace ....Kazar amare naje sawo maki...sae da na nemo wadda zata maki wuyar cinyewa....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ..</p><p><br /></p><p>================= Gidan Novels =====================</p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p> Nagode sossae da sakonninku ...wanda ban bawa amsa ba dan Allah suyi hakuri wallahi yayi man wuya nabi kowa na bashi amsa ...Kuyi Hakuri🙏🏻</p><p><br /></p><p><br /></p><p>101 to 102</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gabanta yayi mummunar faduwa tayi tsuru tsuru tana kallon carpet ..</p><p><br /></p><p> Tsaf ya gama karantarta ....lebenta na kasa yaja ..tare da jan hannunta ...bai tsaya falo ba ...ya wuce bedroom dinshi da ita ...</p><p><br /></p><p> Tana zaune kamar mutun mutimi ya fito wanka ...sannan ya mika mata towel ...</p><p><br /></p><p> Sae da ta dauki kayan baccin da zata saka ta shiga toilet din dasu ...gudun kar ta fito yace ta saka gabanshi ....</p><p><br /></p><p> Yana zaune bisa abun sallah ta fito ..ya mika mata hijab ...</p><p><br /></p><p> Raka'a biyu sukayi ...ya dafa kanta ..ya dinga kwararo mata addu'a ....tana zaune kamar gawa ...sae binshi take da ido ....</p><p><br /></p><p> Ledar ya janyo ya juye cikin plate ..</p><p><br /></p><p> Gata nan kici Meenatou idan ma bata isheki ba akwae wata a leda don bana so kice nima na kawo maki karama bata isheki ba ...</p><p><br /></p><p> Harara ta banka mashi tare da fadin ...ni na koshi ...</p><p><br /></p><p> Dariya ya sake Kasa kasa yace ...da sauri haka Meenatou...ko dai na matso na baki da kaina ...</p><p><br /></p><p> Saurin ja da baya tayi ganin ya matsota .</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Dariya ma abun ya baci ...kamar ba Meenatou dake bala'in sae ta kwana kusa dashi ba ...amma yau tana gudunshi ...</p><p><br /></p><p> Yau naga abunda ya daure man kai ...Meenatou ni kike jiwa tsoro ...</p><p><br /></p><p> Bawae shi takewa tsoro ba ...aa abunda zaya mata shi takewa tsoro. ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sae da kyar ya samu ta karba sau daya ta kau da kai ...duk cika bakin Meenatou yau ga kazar amaren a gabanta amma ta kasa ci ...ko ta manta da Musa ya kawo mata ..ba sonshi take ba kuma tana da yakinin da bara ya mata komae ba shi yasa ta sake jiki ta cinye .... </p><p> </p><p> Amma Yau ta Ma'aruf mai dadin ma ta kasa ci ....</p><p><br /></p><p> Da kanshi yaja hannuta ya kaita toilet sukayi brush sannan suka fito ....</p><p><br /></p><p> Can karshen gado ta koma ta makure ....</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi ya fita ya rufo kofar falon sannan ya dawo ya hawo gadon tare da kashe fitila ...</p><p><br /></p><p> janyota yayi tayi saurin mikewa zaune tana fadin ...Yau zan iya kwana a dakina ni kadae ...</p><p><br /></p><p> Ko ..ya tambayeta yana kokarin rabata da rigarta ...</p><p><br /></p><p> Wallahi kuwa ...ko gidan musa na taba kwana ni kadae. ..ta bashi amsa da sauri ..</p><p><br /></p><p> Gidan Ma'aruf fa ...ya tambayeta ....</p><p><br /></p><p> Shima zan iya kwana ...please ka sakeni ...ta rike hannunshi ...</p><p><br /></p><p> Maidata yayi ya kwantar da ita tare da hade bakinsu guri daya ......</p><p>*</p><p>*</p><p>••°°••</p><p> </p><p> Ba karamar jarumta Meenalle tayi ba ...duk ihun da zakaji ana cewa amare nayi ko daya batayi ba ....sae dae hawayen da suka dinga fita daga idonta ..haka wani Allah ya isa da zakaji amare nayi duk batayi ba ...kuma hakan yayi bala'in kara mata value a gurinshi ...ba kamar shamy ba da yasha cizo da zagi a first night dinsu wanda ko kwatar matsewar Meenalle batayi bare ashe ta fita shan wuya</p><p><br /></p><p> Ma'aruf baiyi tunanin zai sameta virgin ba ..don duk tunaninshi Musa ya riga ya warga mashi farinciki ..amma sae ya sameta budurwa mai tarin Ni'ima ...albarka tashata kala kala ...don har cewa ya dinga yi ...</p><p><br /></p><p> Meenatou indae ni zan daga kafa ki shiga Aljannah ..to na daga maki ita ki wuce Meenatou ....</p><p><br /></p><p> Da asuba ya shiga toilet sae sauri yake ya fito ya taimaka mata . .</p><p>Dama already ya daura ruwan zafi ya zuba kanunfari aciki ...</p><p><br /></p><p> Yana fitowa ya ganta bakin kofa tana dafa bango zata fita ...</p><p><br /></p><p> Yayi saurin isa gurinta ya riketa yana tambayarta. ..</p><p><br /></p><p> Meenatou ina zaki ...</p><p><br /></p><p> Bata ce mashi komae ba sae hawayen da ke fito mata ....lips dinsa ya kai gurin idonta ...ya tsotse idon tas ...sannan ya dauketa ya shige da ira toilet ...</p><p><br /></p><p> Cikin zuwan zafin ya sakata ...bai saka detol ba sae kanunfarin da ya dafa ruwan dashi ...don ya riga yasan detol na bata gaban mace sossae saboda chemicals din daka hadashi dashi ...</p><p><br /></p><p> Kara ta sake tare da rikeshi gam..</p><p><br /></p><p> Sorry kawae yake ce mata ...don ya san tayi bala'in shan wahala ...</p><p><br /></p><p> Sae da ya tabbatar ta gasu sannan ya canza mata wani ruwan zafin da babu komae a ciki yace tayi wankan tsarki ya fita ....</p><p><br /></p><p> Suna azkar bacci ya dauketa ...ya kwantar da ita saman jikinshi sae da ya gama sannan ya maidata saman gado ya rungumeta kamar zaa kwace mashi ita. ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>103 to 104</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Shi da kanshi ya shiga kitchen ya soya masu bread da kwai da kifi ...sae ya dafa masu tea ....</p><p><br /></p><p> Kafin ya dawo har ta fito daga wanka tana sha mai ajikinta ...</p><p><br /></p><p> Da Sauri ya karba ya shafa mata sannan ya taimaka mata ta saka kaya ...riga da siket na atamfa ....</p><p><br /></p><p> Hannunta ya kamo yana kare mata kallo sannan yace ...</p><p><br /></p><p> Kinyi kyau Meenatou ..duk da ma ke din mai kyauce...ina matukar kaunarki kinji ko. ..Allah ya maki albarka ..ban san wace irin godiya zan maki ba ...kin adana man jikinki duk da kin auri wani kafin ni ...naji dadi sossae ...</p><p><br /></p><p> ••°°••</p><p><br /></p><p> Da Daddare kuka ta saka mashi bara ta kwana a dakin ba ...sae da ya mata alkwarin bara ya mata komae ba sannan ta yarda ta kwanta shima karshen gado ....sae da tayi bacci ya maidota jikinshi ...</p><p><br /></p><p> Tun daga ranar bai kuma neman wani abu ba ..ta koma ta saki jikinta dashi kamar da ...soyayya suke zubawa kamar ba gobe ...idan yana office waya ba makale a kunneshi ...idan kuma yana gida gwanin ban shaawa ...</p><p><br /></p><p> Yana kwance ya saka eyepiece a kunneshi yana sauraren wani waazi ..ta shigo falon ...sanye da kayan sport don yanzu ta kware sossae da wasanni ....</p><p><br /></p><p> Ta dade tsaye tana jiran ya tashi suje ...sae ya ware mata hannunshi ta shiga ciki tare da kwanciya saman kirjinshi ...ya maida hannun ya rufe.</p><p><br /></p><p> Eyepiece daya ya cire daga kunnenshi ya makala mata akunne ...suka cigaba da jin wa'azin tare ...wasan da baayi ba kenan ranar ....</p><p><br /></p><p> ••°°••</p><p><br /></p><p> Da daddare suna zaune ta kalleshi tana bata rai ...tace</p><p><br /></p><p> Ina kazata ta rannan ...ta tambayeshi tana hararanshi ...</p><p><br /></p><p> Wace ciki Meenatou .....</p><p><br /></p><p> Ka manta ...ba fa ta jiya ...bana sonta don bata kai ta ranan nan dadi ba ...wacce ka sayo man nace bana ci ...ka tunata ? to ita zaka biyani .....ta fito da ido waje ..</p><p><br /></p><p> Dariya ya sake yace ...Kazar amarya zaki ce man ...ita kike son kici yanzu ...</p><p><br /></p><p> Bata kawo komae ba tace ...eh Please ...</p><p><br /></p><p> Cak ya dauketa ya direta saman gado ..yana fadar bara yanzu zan baki ...</p><p><br /></p><p> Hadashi ta fara yi da Allah ganin abunda yake shirin yi mata ...amma ko saurarenta baiyi ...ba ..ranar ma tarihi ya maimaita kanshi ...tayi nadamar tambayar kazar da tayi ...</p><p><br /></p><p> Meenalle irin matannane wanda ko yaushe zaka jisu kamar ranar aka fara saninsu ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tun daga ranar bata kuma mashi maganar kaza ba ...ko kawo mata yayi ...sae an zauna anyi alkawarin bara ya mata komae ba ...sannan take yarda taci ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°••</p><p><br /></p><p> Safiyar wata litinin suka dira A nigeria ...gidanshi dake kaduna GRA Unguwar sarki suka sauka ...tun kafin su iso dama ya saka an gyara ko ina tsaf ...</p><p><br /></p><p> Kwanansu biyu suna hutawa sannan ta je gidansu ....</p><p><br /></p><p> Hajiya sae nan nan take da ita ...taga gata sossae ...kuma ta iske mamanta cikinshi ......</p><p><br /></p><p> daga can gidan Sadee ya kaita ...sae da tayi kwana biyu sannan ta dawo gida ...</p><p><br /></p><p> Da ta dawo Ko kulata baiyi ba ..don fushi yake da ita ...wae ta tafi ta barshi ...da ta fara rikitashi nan da nan ya huce yana dariya ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm*💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💧💧SIRRIN ZUCI...</p><p><br /></p><p> </p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p> </p><p> 105 to 106</p><p><br /></p><p> </p><p> Satin daya a garin suka je zaria ...a gidansu Ma'aruf din ta sauka ..sae dae ta kwana gidan kaka ....</p><p><br /></p><p> Suna zaune tace mashi tana so suje islamiyyarsu ta gaida malaman ...</p><p><br /></p><p> Ya harareta yace. . ki dai nemo gafara. ..</p><p><br /></p><p> Zagayo wa tayi bayan kujeran da yake ...ta sagalo hannunta bisa wuyanshi ....kanshi ya dago yana kallonta ...ta dauro fuskarta saman tashi ....suna fitar da numfashi tare ....</p><p><br /></p><p> Baka so Ustaz ya yafe man ..? ta fada dae dae bakinshi ....</p><p><br /></p><p> Nan da idanuwanshi suka canza ..ya zagayo da ita ya daura saman cinyarshi ....tare da kwantar da kanshi a kirjinta ........</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ••°°••</p><p><br /></p><p> Wani dan karamin gida ya fara biyawa da ita ...ya fito da key ya bude gidan tare da jan hannunta cikin ...</p><p><br /></p><p> Cherii ...ina ne nan ..ta fada tare da kallonshi ...</p><p><br /></p><p> Daki dayane cikin gidan babba ...yana bude kofar ...ya duka yana fadin ....Teeta ......</p><p><br /></p><p> Wata kare ta fito ta tsaya gabanshi tana sinsinanshi tare da haushi ...sannan ta duka gabanshi ...</p><p><br /></p><p> Ya kalli Meenalle ...yace ..kin tunata ? ..</p><p><br /></p><p> Girgiza kai tayi a hankali cike da mamaki</p><p><br /></p><p> Hannunta ya janyo ta duka kusa dashi ...sannan ya juya yana kallonta yace ....</p><p><br /></p><p> Kin tuna ranar da na fito gida na ganki kina kuka ...na tambayeki me aka maki ...sae kika ceman ...wae mamansu kausarce tace idan karensu ya haihu zasu baki guda ....Sae kikace kaka tace bara ta aje kare a gidanta ba ...saboda mala'ikun rahama basa shiga gidan .....Sae kika ce ko zan aje maki shi a gidanmu bakin gate ..idan mala'ikun sun zo sae su shigo ta katanga ...to shine na karbo maki anan....ya kara maganar tare da dago habarta ...</p><p><br /></p><p> Rungumeshi tayi tana murmushi ....</p><p><br /></p><p> Sannan suka tashi sukaje islamiyyar...</p><p><br /></p><p> Ustaz na ganinta ya ganeta ....Aminatu abubakar ..</p><p><br /></p><p> Ta amsa da fara 'a....duka malaman islamiyyar suka taso suka gaisa da Ma'aruf ...</p><p><br /></p><p> Ustaz ya kalli gefen fuskarshi ya shafi wani tabo yace ..Aminatu gaskia ba karamar cuta kika mani ba ...</p><p><br /></p><p> Tayi murmushi tace ...Ustaz sae dae a yafe dan Allah .....</p><p><br /></p><p> Yace ..ai an yafe Aminatu...</p><p><br /></p><p> Tace Ustaz ina wata shaddarka da ka taba zuwa da ita sabuwa ..daka koma gida kaga an yageta ta baya ....</p><p><br /></p><p> Da Sauri yace Kece ko aminatu .....</p><p><br /></p><p> Eh Ustaz sae dae a yafe ...Wallahi lokacin banda abun goge majina ..sae na Yaga da reza ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Basu bar gurin ba sae da Ma'aruf ya masu alkhairi mai yawa sannan suka tafi ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>°°••°°</p><p><br /></p><p> A gurin kaka take samun labarin Musa ya kara guduwa daga prison sannan har yau baa kara ganinshi ba .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>•°°••</p><p><br /></p><p> Ma'aruf bai san Meenalle na da ciki ba sae da yakai wata shidda sannan ya fito ....wata sabuwar soyayya da kulawa yake bata ....Ko karatu zayayi in yana gida sae dae ya zauna tana jikinshi ta karanta mashi ....</p><p><br /></p><p> Karyar Rashin lafiya kuwa ya sha yayita gurin aiki sae yayi sati bai je ba ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ranar wata litinin ta tashi da mugun ciwon mara ...Ma'aruf na kwance gefenta ...yana bacci ..ta mintsineshi da karfi ...</p><p><br /></p><p> Ya mike yana kallonta ....cikin kuka tace ...sae aja wa mutun ciwo sannan a kwanta ayi bacci ...</p><p><br /></p><p> Me ya faru kuma Meenatou .....</p><p><br /></p><p> Maimakon ta bashi amsa sae ta fashe da kuka .....da farko ya dauka rashin jin Meenalle ne ..</p><p>sae daga baya ya fahimci da gaske take ......</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Feedohm💞</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>107 to 108</p><p><br /></p><p> Da sukaje asibiti cewa akayi sae an mata CS itama ...</p><p><br /></p><p>Please doctor kuyi wani abu mana ...bana son CS dinnan wallahi ...ya fada tare da rike hannun doctor din ya rufe idonshi gam ....</p><p><br /></p><p> Calmdown mana ...in Allah ya yarda ba wata matsala Mr Ma'aruf ...</p><p><br /></p><p> taya zan kwantar da hankalina bayan Meenatouta tana can tana labour ...ni dae kawae ayi mata komae amma banda CS ....ya karashe maganar da karfi ....</p><p><br /></p><p> Nurse ta shigo tana fadin Sir zata iya haihuwa da kanta mahaifar ta bude da kanta ...</p><p><br /></p><p> Daga doctor din har Ma'aruf din rigen shiga ake dakin duk da mutane basu shiga amma haka suka kyaleshi ....</p><p><br /></p><p> Yana Zuwa ya zauna tare da tallabo kanta ya daura saman cinyarsa ....</p><p><br /></p><p> A wahale ta bude ido tare da rike hannunsa tana kallonshi da i</p><p>Cheri...ta fada tare da lumshe idanu ...</p><p><br /></p><p> Iska ya hura mata yana shafar kanta ganin yarda take zufa duk da sayin AC dake dakin ...</p><p><br /></p><p> Hannunta ya damke sossae tare da daura gudan hannun a goshinta</p><p>Sorry ..Meenatou ...ki daure please kinji ko ...ya fada dae dae kunnenta ..</p><p><br /></p><p> Girgiza mashi kai tayi ..aa Cheri mutuwa zanyi kamar yarda shamy tayi ..ka yafe man kaji ka sakawa babyn mu sunana ...</p><p><br /></p><p> Bazaki mutu ba Meenatou ki barni ...da rayuwarki nake rayuwa ..idan babu ke Meenatou Zan kasance kamar gawa da raice ..kin manta alkawarin da kika man ..kince Tare zamu rayu sannan mu mutu a tare ..ko kin karya alkwarin ne Meenatou?,......</p><p><br /></p><p> Zafin ciwo bai hanata girgiza mashi kai ba ....</p><p><br /></p><p> Yauwa Meenatou ...zaki daure ko?..ki daure ki haifa mana baby ki bashi tarbiyar ..Ina Matukar sonki da kaunar ko da can da kika ga na shareki Meenatou dan ba yarda zanyi ..amma soyayyarki tana cikin Zuci ...ta zama Sirrin Zuci ...zan iya rayuwa babu abinci Meenatou ..indae kina tare dani ...Dukiya da duk jin dadin duniya yana tare dake Meenatou ..kece hasken dake haskaka rayuwata ...idan babu ke zan dawwama cikin duhun da bazaya taba gushewa ba ...</p><p>Kin kasance wani bango Wanda akayi shi da azurfa a gareni ...ki daure Meenatou ...Ke din kamar Hurul 'ain ce wadda Allah ya sauko man domin cikar rayuwata ....</p><p><br /></p><p> Idonshi ya lumshe tare da daura lebenshi saman nata yana tsotsa ya mata katanga da faffadan kirjinsa ...yana jin lokacin da taja numfashi da karfi tare da kara rikeshi. ...hawayen dake zuba a idanunta. ...suke gangarowa saman lebenshi ....</p><p><br /></p><p> Doctor dake tsaye da baby a hannunshi ya dafa bayan Ma'aruf tare da daura babyn a bayanshi ...</p><p><br /></p><p> Ya dago da sauri yana kallon Dr din ...</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi mashi yana fadin ..Congrat Mr Love ..ya mika mashi baby din. .</p><p><br /></p><p> Yaron ya kallah dauke da murmushi a fuskarshi sannan ya kalli Meenalle wadda har lokacin Idonta a lumshe yake</p><p>Dukawa yayi Dae dae kunnenta ...ya kira sunanta a hankali ...</p><p><br /></p><p> Meenatou...</p><p><br /></p><p> Bude idonta tayi tare da kallonshi ...Deep kiss ya manna mata a goshi...sannan ya dago da idanuwanshi da suka rike zalla soyayya ya na kallonta ...</p><p><br /></p><p> Barata iya jure irin kallon ba ta juyar da kai gefe guda tana murmushi ....</p><p>Tsam ya mike tare da komawa inda ta juya ...zata sake juyar da kanta ..ya saka hannu daya ya rikota ...</p><p><br /></p><p> Me kike so a rayuwarki Meenatou ...fadan me nene gurin ..ko da lumfashina zaya kare zan cika maki shi ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Hannunshi ta rike tare da daurawa saman kirjinta ...Kai nake so Ma'aruf .kai kadaene gurina ...daga kai bana son komae ...</p><p><br /></p><p> Babyn ya daura mata a kirjinta ya duko da kanshi ya sumbaci lebenta ...kin Samu Meenatou dama can ni naki ne ...kin saka man farinciki mara misaltuwa a rayuwa. .dame zan saka maki ..?..</p><p><br /></p><p> Ka barshi a sirrin zuci ...ni kadae zan fahimci haka ...</p><p><br /></p><p> °°••°°</p><p> </p><p> Dama Already ya fadawa dangi tana labour ....tun da safe jirgin su Hajiya da kaka da mahaifiyar Maaruf ya dira ...farinciki kamar baa taba haihuwa ba a dangin ....</p><p><br /></p><p> Hajiya tace. zaa koma da Meenalle nigeria ...amma Ma'aruf yayi kememe yace ba inda matarshi zata tafi ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><p>💧💧SIRRIN ZUCI ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 💞</p><p><br /></p><p>Na Feedohm💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>109 to 110</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Juyin duniyar nan amma ya kiya ...da daddare ya samu Meenalle zaune daki ...yaron na hannu kaka zaa mashi wanka ...</p><p><br /></p><p> Hawa yayi saman gadon tare da kwanciya ya daura kanshii saman cinyarta ..yana kallonta ...</p><p><br /></p><p> Murmushi tayi tare da shafar sumarshi ...</p><p><br /></p><p> Bara ka bari a tafi dani ba Cheri....ta fada tare da juyar da kai ga barin kallonshi ...</p><p><br /></p><p> Kina so ki bisu ne. .? ..ya jeho mata tambayar..</p><p><br /></p><p> Tasan da biyu ya tambayeta tayi saurin kallonshi ..har ya janye kanshi daga jikinta ...</p><p><br /></p><p> Girgiza mashi kai tayi a hankali ...</p><p><br /></p><p> Idan kina son binsu Meenatou baran hanaki ba. .kinji ko ..ki shirya ku tafi ....</p><p><br /></p><p> Ya mike yana shirin sauka daga gadon ...hannunshi ta rike tare da kwantar dashi ...sannan ta kwanta jikinshi ...tana fadin ...</p><p><br /></p><p> Cheri idan har kai baka so nayi nisa dakai ...ni taya zanyi tunanin nesa dakai. ... *Muna Tare* </p><p><br /></p><p> Mirginata yayi tare da sake mata kiss ya mike yana murmushi jin motsin kaka na zuwa ..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>••°°•• </p><p><br /></p><p> Allah Cheri ka tashi ...ta fada tare da mintsininshi a kumatu ..</p><p> </p><p> Gyara kwanciya yayi yana mata dariya kasa kasa</p><p><br /></p><p> ...pillow ta dauko tana dukanshi ...amma yaki kulata. ..</p><p><br /></p><p> Kuka ta sake mashi ..tare da daukar Sudais dake faman mata kuka ta sauka daga gadon..ta nufi kofar fita ....</p><p><br /></p><p> Da sauri ya mike tare da rungumota ta baya yana dariya ...</p><p><br /></p><p> Ka sakeni ...ta fada tare da share kwallanta ..</p><p><br /></p><p> Am sorry ...ya rike kunnanshi ..sannab.ya saka hannu ya karbi Sudais ya daura saman baya ...ya juya mata ta saka mashi zani</p><p><br /></p><p> Dama abunda take so kenan ...ta sake mashi harara tare da daura mashi zanin a baya .....</p><p><br /></p><p> Sae da ya goyashi sannan ya dauketa cak ya maidata saman gadon ...ya fara jijjiga Sudais har ya koma bacci ...</p><p><br /></p><p> Ya maidashi saman gadonshi sannan ya dawo ya janyota jikinshi ....romancing dinta ya fara ....</p><p><br /></p><p> Hannunshi ta rike idonta na lumshe haka shima nashi ...</p><p><br /></p><p> Cikin kunnenshi tace ..Cheri ka tuna fa ..kace wae banda abunda zai ...</p><p><br /></p><p> Bakinta ya kulle da nashi ya hana sauran maganarta fitowa ...sannan ya dago yace .</p><p> Oh Meenatou nace na tuba Wallahi ..wannan magana bara ta kare ba haka nan ...dan Allah ki rufa man asiri ...na tuba wallahi ...</p><p><br /></p><p> Murmushi tayi tare da rungumoshi .....dariya yayi ...yana fadin Meenatou ta bara ki canza ba ...idan aka maki abu har mutun ya mutu kina tunawa ....</p><p><br /></p><p> bayanshi ta buga a hankali tare da zura halshenta a kunnenshi tana lasa ......</p><p><br /></p><p> Fatan Alkhairi Meenalle ....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Godiya mai tarin yawa ga masoyana ...Allah ubangiji ya bar mu tare. ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>يا يهل الذين ء ا مبو اتقو. الله ولتظزنفس ما قد مت لغد..... ..</p><p><br /></p><p>ALLAH YA YAFE MANA KURA KUREN MU .....MU HADU A SABON LITTAFINA ... *_AHLUL KITAB_*</p><p><br /></p><p> Ina kaunar masoyana baran iya lissafo ku ba ..dan page bara ya isa ba ..amma ku sani kuna raina ....</p><p> Namutu kanku ...😅😅</p><p><br /></p><p> 08066598868 </p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Feedohm💞*</p><div><br /></div>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-30196239530330216772022-02-12T05:07:00.000-08:002022-02-12T05:07:00.521-08:00MISBA COMPLETE HAUSA NOVEL<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEgtgoj1lO5V3L-WceLaJya5yFIvOOPWDMx7w_LTkTuQ7PlAoYngwdgoq1KWvmbHghOwKFQjFZNWThJEhWX1SqmNY1wGmq9FSttzNtjOIqyEdLgwGtLasoZPeuWgW8E-PXvt5OOCgnhV__H3cZXUS9UABLYAJ3W9nsou3YwmolXKUEL4e8PrqfIpcU7M=s2286" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="MISBA COMPLETE HAUSA NOVEL" border="0" data-original-height="1768" data-original-width="2286" height="309" src="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEgtgoj1lO5V3L-WceLaJya5yFIvOOPWDMx7w_LTkTuQ7PlAoYngwdgoq1KWvmbHghOwKFQjFZNWThJEhWX1SqmNY1wGmq9FSttzNtjOIqyEdLgwGtLasoZPeuWgW8E-PXvt5OOCgnhV__H3cZXUS9UABLYAJ3W9nsou3YwmolXKUEL4e8PrqfIpcU7M=w400-h309" title="MISBA COMPLETE HAUSA NOVEL" width="400" /></a></div><br /> 👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬<p></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI</p><p><br /></p><p><br /></p><p>=================== GIDAN NOVELS ====================================</p><p><br /></p><p><br /></p><p>BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM</p><p><br /></p><p>PART ONE </p><p><br /></p><p>01</p><p><br /></p><p>Yammaci ne mai cike da sanyi hade da ni'ima tare da kamshi irinna damina, dai dai wannan lokacin ta fito daga islamiiya iska na kada hijabinta tare da hura fuskarta yana ratsata.haka nan ta dinga jin soyayyarsa tana bin jikinta, tana ratsata,kewarsa taji tana shigarta.farida kenn matashiyar budurwa da bata wuce sha bakwai ba .<span></span></p><a name='more'></a><p></p><p> Daga kai tayi ta kalli gate din gidansu data zo wucewa ,haka nan zuciyarta ta bata ta shiga gidan wanda yake makwabtaka da gidansu, haka nan gidan tamkar nasu gidan ne .</p><p> Nan ta tura karamar kofar shiga gidan ta kutsa kai tana tafiya cikin nutsuwa ,zuciyarta na magana tana tunanin wacce dabara zatayai taga NURA ? Da wannan tunanin ta shiga falon gidan ,tayi sallama .</p><p> Mama ce ta amsa mata tana daria ,tace Farida ce ? Yan mata ,an taso daga islamiyya ?</p><p> Ta sunkuyar da kai tana dariya ,ita dai mama ranta nason farida ,yarinya me kunya da tarbiyya .</p><p> Nan ta zauna bisa carpet ta gaida mama ,ta amsa da fara'arta tare da tambayarta karatu na islamiyya dana boko, ta amsa da Alhmdllh .nan tayi mata addu'a tare da fatan alkhairi .</p><p> Tana nan baba ya shigo wanda hakan yasa mama mikewa dan daga tafia ya dawo.faridan ta gaisheshi tare da amsar kayan dake hannunshi tayi kitchen dashi, sannan tadawo ta gaisheshi tare da yimishi ya hanya, yana daria ya mika mata wata leda dake dauke da zannuwa guda biyu masu kyau da tsada , yace to kinga kin tarar da tsarabarki ,ki dauki daya ki bawa Aisha kanwarki daya .</p><p> Tayi murmushi tace ,"nagode baba, Allah ya kara arziki"</p><p>Nan ya haura sama ,mama ta bishi .</p><p> Wannan yabawa farida damar zuwa bangaren nura wanda suke kira da DEENI .</p><p>Nan ta kwankwasa kofar dakin shuru ,ta kwankwasa ya kai kamar sau uku shuru ba motsin kowa ,hakan yasa ta tura kofar dakin tare da yin salllama. Har yanzun shuru tamkar ba me rai a ciki,sai karar Ac da sanyinta ya ratsata tare da kamshin turaren deeni mai qamshi da dadin gaske .ta lumshe ido tana shaka ,tana jin sonsa a ranta..</p><p> A hankali ta dunga ratsa dakin tana ganin yadda ya tsara dakin ,ta kwantar da kai tana murmushi a ranta tace, "shiyasa nake sonka deeni,daga yanayin yadda ka tsara dakinka ya nuna halayyarka da personality dinka a zahiri ,,wannan yasa banajin akwai namiji irinka a duniya, kai daban ne,kai nawa ne ,kai mallakina ne"</p><p> Nan ta lumshe ido ,ta fada wata duniyar tunanin wadda daga ita se deeni a ciki ,wata rayuwa mafi dadi a cikin rayuwar duniya"</p><p>Ta jima a haka sannan ta ware idanu tana neman ina nuran yake ?tunaninta yabata ba ya dakin,, hakan na nufin baya gidan . Nan ta turo baki alamar bataji dadi ba .</p><p>Naso ganin deeni yau ,kuma sai ya fadi dalilin da yasa naji shuru kwana biyu ban sashi a idona ba ,sai ya biya pains din danaji a zuciyata na rashin ganinsa da tsada ""</p><p><br /></p><p> Har zata juya sai wani haske na daban ya dau hankalinta ,wannan ya tuno mata da study room dinshi dake manne da dakinshi ,nan ta nufi gurin da saurinta .nan ta hangoshi cikin tsakiyar takardu suna zube a gurin , yayin da ta hangoshi fuskarsa mai sauke mata duk wani jin dadi da nishadin a zuciyarta ....</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI</p><p><br /></p><p><br /></p><p>COPIED BY SUMAYYA SAAD(sumy luv❤)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>02</p><p><br /></p><p>Cikin nutsuwa yana karatu ya mai da hankalinsa sosai kan littafin, duk wanda yaganshi yasan yana karanta wani abu mai matukar mahimmanci da motsa kwakwalw da tunani.</p><p> Ta jima tana tsaye kansa amma ko alamarta be ji ba ,,sai data kalleshi iya san ranta sannan tayi mishi uzuri data tuno gagarumar jarrabawar da ke gabansa,,haka nan tasan naci ne kawai ba wai dan yansan karatun ba ne sai yayi dagaske yake iya fahimtar karatun, sabida wannan bashi ne ra'ayinsa ba ,ra'ayine na mahaifinsa ya bi don ya faranta masa rai..</p><p> A yadda tasan deeni mutum ne wanda baya son karatu me tsanani ko me zafi ,,deeni yanason abubuwa masu sauki haka rayuwarsa da tunaninsa duk masu sauki ne ,duk da tafito daga gida da yake cike da mutane masu zafi ,mutane ne masu matsayi,,rayuwarsu me tsada ce,tunaninsu mai girma ne,yayin da shi kadai ya bambanta..</p><p> Deeni masoyin abubuwa masu sauki ne ,farin cikinsa yanaga abubuwa masu sauki..</p><p> Deeni masoyin tsuntsayene ,dabbobi da duk wani abu da bai da bakin magana. Abu uku ke tsananin sanyashi farin ciki a rayuwa ,karance karance game da rayuwar wasu mutane daban da bai sani ba ,mutum ne me son karatu da bincike sai swimming pool wanda yana matukar sashi nishadi ,sai zama cikin tsuntsaye da dabbobi yana karantarsu,yana fahimtarsu tare da connecting kansa da su,sai kuma soyayyar farida data zame masa wani haske a rayuwar. Don haka a study room dinsa cime yake da takardu kala kala tun daga kan na larabci ,hausa dana turanci,na tarihi dana addini. Sai kuma takardunsa na makaranta da suka zame masa dole badan son ranshi ba sai don mahaifinsa.</p><p> Duk da farida tasanshi da son karance karance yadda hankalinsa ya tafi akan littafin har beji motsinta ba yabata mamaki,mutumin dake fahimtar tana guri tun kafin ta iso inda yake shine yau ta iso har gabanshi amma be san tana gun ba ,hakan yasa ta sunkuya dan taga wani irin littafi ne haka daya dauke mishi hankali har fiye da ita ?nan idanunta suka hango mata abu daya data tsani gani ,suna daya data rsani gani ba dan ta tsani me sunan ba sai dan yadda wannan marubucin ya ke dauke hankalin masoyinta akanta,,duk kuwa yawan son dayake mata..Tayi tsaki tarw da fisge littafin ,bai ankara ba ta galla masa harara tarw da turo baki ,cikin tsiwa ta ce "SAUYIN SHAUKI ko? The change of emotions) shi ne abinda zakaje ka rubuta a exams din ko ? Na tsani marubucin nan l just hate wannan writer din,saboda kai na tsani wannan MISBAH din "</p><p> Tayi wurgi da littafin ta fita tana mita ,ya mike da sauri ya bita hankalinsa tashe ya sosa ran farin cikin rayuwarsa.</p><p>"" haba farida na,,kinsan fa bani da kamarki a duniyar nan"</p><p> Nan ta dalla masa harara,"ai naga alama ,shiyasa har nashigo nagama tsayiwata a dakin baka san inayi ba ,naga yawan son da kake mun . Wannan banzan liffafin MISBAH din yafini muhimmanci" </p><p> "Oh oh !! Haba farida na ya kike hada kanki dawani writer daban,ai darajarki ya wuce haka a gurina ,ni fa i have nothing to do with MISBAH ,damuwata shi ne brains dinsa,da intelegent dinsa" hakan ya kara kular da ita tace "to ai sai kaje kayi soyayya da brains dinsa da labaransa ,kaje ka rayuwa da labaransa,dama new version na littafinsa ya fito shi yasa kwana biyu ban ganka ba ,na zata karatun exams kake ashe kaba nan kana wai abun daban ,to nafasa soyayyar ma "</p><p>"Haba farida na ,ai bazan iya rayuwa ba ke ba ,kema kin sani kece macen kadai da deeni zai iya rayuwa da ita,kece kadai macen da zata iya jan ragamar rayuwata ,in ba farida ai ba deeni"</p><p> Ta turo baki ,ni dai gaskia ban yarda ba farida ta fada"</p><p> Farida kalle ni mana "ya fada cikin murya me kashe jijiyar jiki ,ba shiri ta juyo tana kallonshi. </p><p> Ya harde hannu tare da zuba mata idanunshi masu rikira zuciya da kwakwalwarta,yana mata murmushi me kwantar da hankali da dauka bacin rai.</p><p>Yace tama ki yarda dani farid,trust me you re d most important person in my life,kece macen da tafi komai muhimmancin a rayuwata,my love ,my wife, my friend .</p><p> Tuni jikinta ya mutu,taji wani irin sonsa me karfi yana tsuma ta ,ta dinga jin tamkar ta rungume shi,ra zauna a jikinsa har abada.</p><p> Ta kwantar da kai tana masa kallon kauna tace ,," deeni kamin alkawari as long as ina rayuwarka bazaka sake karanta littafin MISBAH ba ,komai koyarwarsa ,komai ilimin dake cikinsa ,saboda littattafan MISBAH sun zama kishiyoyina ,shi ne abu na farko dana taba gani yana kokarin janye hankalinka a gare ni. Deeni bana son ganin abinda zai janye hankalinka daga kaina.... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied sumy luv ❤❤</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI</p><p><br /></p><p><br /></p><p>COPIED BY SUMAYYA SA'AD (sumy luv❤)</p><p><br /></p><p>03</p><p><br /></p><p>Kamar yadda kace baka da damuwa da MISBAH sai brains dinsa ,to nima bani da damuwa dashi,damuiwata shine deeni,in kuwa labaransa na dauke hankalin deeni a kai na ,to inada matsala da hakan ,don haka inada matsala da brain dinsa,da intellegent dinsa,i have a problem wit his stories"</p><p> Ta dan fadada murmushinsa tare da fadin "" anyi an gama ,daga yau bani ba karanta littafin MISBAH ;nayi alkawari""</p><p> Tayi daria har da tsallen farin ciki ta ce " shiyasa nake son deeni na ,he care for me yana jin maganata ya damu da farin ciki na ,,my deeni is d best""" </p><p> Dariya yake mata shina yace my farida is d best"ki tsaya a gabana in ta kallonki ina jin dadi . Haka kawai kin hanani jin dadi da sukuni ,kwana uku ban ganki ba ,meyasa kika ki zuwa ki ganni ? Kinsan baba kulle yakemun inmun fara jarrabawa ya hadani da wannan manya manyan takardun ina karantawa, bana ganewa,daga na bude littafin sai inga furkar farida tanamun murmushi,bana iya komai sai kallon fuskarki a littafin "tayi murmushi tace meyasa baka dirko ta window ba ? </p><p> Yace " so kike in karye a ce mijinki gurgu?</p><p>Tayi daria tace "to ina ruwansu ,inma gurgun ne ba mijina bane ? Deeni na ne ni daya " </p><p> Yace haka farida na ni daya ""</p><p> Farida ta dubeshi taxe deeni yaushe zamuyi aure ? Ya kalleta ya ce ko yau Abbanki ya shirya aura minke zan aure ki "</p><p>Ta masa hararar wasa ta ce ina zaka ajiyeni baka da gida baka da aiki ? Ya ce,shine damuwarki ? Kalli girman dakin nan bazai ishemu ba ? Ya jawota ,"zo kiga yawan abincin da mama take samun kullum so uku so hudu a rana ,ko ke rumbu ce zaki koshi. Awani lokaci mama nasamun abinci fiye da kala hudu a rana ,wani lokaci ma bana ci ake fita dashi .</p><p> Bari in fada miki ni mrs deeni NURADDEN dan gatan mama da baba ne auren gata zatamun dakina ya ishemu,abincina ya ishe mu ,balle ma inkin zo mama zata kara kara. Kayan sawa zan sai miki ko wanne ,inada kudi enough a account dina ,kullum baba samun yake bana kashesu . Zan iya kula da lafiyarki ,babban shine zan kula da farin cikin ki,kullum zan dunga saki daria ,har funny faces zan dunga miki in kina so .</p><p> Zan so ki sosai my farida ,ki rayu a dakina ,gado na,wardrop dina,toilet dina ,komai na baki . Ni zan rayu a jikin kj" yana magana yana lumshe ido.</p><p>Murmushi tayi ,kinya tasa ta sunkuyar da kai. </p><p>Ya kira sunanta yana mata murmushi,wannan tunanin da halayyar tasa yake kara haukata zuciyarta cikin soyayyarsa, itama murmshin take masa,ganun yana matsowa gareta yasa ta fara ja da baya ,tayi hanyar fita tana kallonsa,bataki tai ta kallon sa a haka ba. Sai dai ya zama dole tayi gidan dan an fara kiran sallar magriba,za'a nemeta a gida in anji shuru bata dawo ba . Haka tana tsoro kar mama ta leko su .</p><p> Bata ankara ba kuwa taji tayi karo da abu,da sauri ta juyo tare da daga kai. Yaya SHAMSU ne yayan deeni ,ya kalleta . </p><p> Haba farida yi a hankali maba,bakya gani ne?" </p><p> "Yi hakuri yaya ai duk laifin deeni ne " ya zaro ido ,sharri zakk mun ? Yaya laifinta ne" girgiza kai ya yi tare da murmushi ,ya ce "Deeni da Farida sai Allah ,ba'a gane muku kuma ba'a shiga tsakaninku . Ni kan nayi masallaci ,maza kaima kayi harama ,kema ki shige ciki ayi sallah,in yaso kuyi soyayyar daga baya "</p><p> Kunya tasa ta rufe fuska ,ta fita da gudu ko sallama da mama batayi ba, deeni yabita da kallo yana murmushi ,sonta na bin jikinsa . Ya Shamsu ya kalleshi yace wai wani irin so kake wa farida ne ?</p><p>"Yaya nima ban sani ba ,ni kaina na rasa wane irin so nake mata da yawansa "</p><p> Girgiza kai shamsu ya yi ya wuce ya barshi a wurin ...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cpied by sumy luv❤❤</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p>Wirtting by SA'ADATU WAZIRI</p><p><br /></p><p><br /></p><p>COPIED BY SUMAYYA SA'AD(sumy luv ❤)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>05 </p><p><br /></p><p>Gidansu farida cike yake da mata da maza da kuma matan aure uku,farida ta kasance yar amarya Alh Ahmad,wato mahaifinta,kuma ita kadai ce a gurin mahaifiyarta . Haka hankalin Haj A'i yafi zuwa dana mahaifiyar farida ,dan haka shkuwarsu da zumuncinsu yafi karfi da mahaifiyar farida Haj bilki akan sauran mata Alh Ahmad din. Haka nan burinta farida ta zamo surikarta saboda salihar yarinyace ,zata zamo mace ta gari kuwa uwa ta gari. Don haka sun dade suna tsara yadda zasu hada auren deeni da farida.</p><p>Duk wani dan yasan deeni to da farida ya sanshi,haka duk wanda yasan farida da deeni yasanta ,sun zana identity na juna . Ahalin yanzu deeni nada shekara ashirin da daya yayin da farida take shekara sha bakwai,tana aji shida na secondry, su kuma yan katsina ne. </p><p> Farida na shirin jarrabawar gama secondry ,,shi kuma deeni ya na shirin jarrabawar shiga aji biyu na jami'a. Haka wannan lokacin zuciyoyinsu nada burin auren juna a wannan shekarar,sabida aladar gidansu farida be aurar dasu suna gana secondry sch ba cigaba se a gidan miji. Wannan ya karawa deeni karfin gwiwar yin karatu da naci domin mahaifinshi ya cika masa burinsa. Dabi'ar deeni na son karatu yasa shi cin karo da littafin MISBAH, wanda shahararren marubuci ne na harshen hausa dama turancin duka,,idan yayi littafi da turanci yakan fassarashi ta harshen hausa,wannan ya nuna cikakken bahaushe ne,,sai dai bayaga sunan sa da email din sa bawani abu da ya nuna shi din waye ko dan ina ne"" bawani tarihinsa ko wani abu game dashi,banda sunan labari da email address dinsa sai sunan sa,,ba information akansa sai na email address din sa dayake bayyane a zahiri,,amma kuma ya boye kansa.</p><p> Yawancin labaransa ya kunshi irkicin da samari da yammata suke suntar kansu a lokacin tasowarsu da irin matsalolin da suke fuskanta ,sai kuma abinda suka shafi shauki emotions dinsa ,yadda kwakwalwa ke ban bamta da zuciya,,da yadda suke tafia tare kwarai.</p><p>Akwai ilimantarqa sosai a littatafansa ,daga rubutunsa zaka fahimci mutun ne me ilimi da sani,,da kuma bincike akan abinda yake rubutawa ,haka nan zaka san tubutu passion dinsa ne,wani abu ne dayake so kuma yake jin dadin rubutawa,hakan ya zama tamkar wani bangare na rayuwarsa,yana nuna hikima sosai a rubutunsa ,,ga bincike ta fuskar addini da boko, ga sanya irin matsalolin da mutane ke fuskanta . Hakan yakansa mutun yaki tamkar dashi yake,ko ya taba wata matsalarsa. </p><p> </p><p>Wannan yasa deeni yake ba karatunsa muhimmanci fiye da na sauran marubuta. </p><p><br /></p><p> Abinda yakara jan hankalin wannan karan shine yadda marubucin yake fada wasu halayyar da kwatance tamkar irin nasa,marubucin na rubutu tamkar ya sanshi,da tunani irin nasa,da hobbies dinsa, da kalar soyayyarsa,irin yadda yakeson rayuwarsa ta fati,,da irin matsalolin da yake fuskanta a halin yanzu ,,da irin rayuwar auren da yakeso yayi da farida.........wannan kenan </p><p><br /></p><p><br /></p><p>CIGABAN LABARI</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>writting by SA'ADATU WAZIRI </p><p><br /></p><p><br /></p><p>COPIED BY SUMAYYA SA'AD(sumy luv❤)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>04</p><p><br /></p><p> Nuradden da farida sun kasance makwabtan juna,gidajen su na kallan na juna ,haka nan akwai mutunci da zumunci me karfi a tsakanin gidajen,akwai abota a tsakanin iyayen deeni da na farida,,haka iyayensu mata wanda zaman unguwa daya ne kawai ya hada su,duk da yanayin rayuwarsu da dukiyarsu ya ban bamta,,wannan be hanasu abota da zumunci da juna ba.</p><p> </p><p> Mahaifin deeni mutum ne dan kasuwa ,mai dukiya. Rayuwar gidansa kuwa zamu iya cewa rayuwace ta yan bariki tsantsa,dayawa sukan masa lakabi da bakin bature ,saboda yanayin rayuwar sa .</p><p> Matar sa daya hajia A'i da yaransu maza uku rak. Shamsudden shine babba, sai Nuruddeni da kaninshi lukmanudden wadan nan sune yara hajia A'i .su biyar dinnan su ke rayuwa a gidansu,sai ma'aikatansu,sai dai lokaci lokaci yan uwa na kawo musu ziyara..</p><p> Alh Umar mahaifin deeni duk da turancinsa da bokon sa bashi da wani mugun hali, ko wani mugunta . Mutum ne me kirki da alkairi ga mutane,jamaar unguwa sunajin dadin zama dashi da mu'amalar sa da su . Shi dai kawai baya so a shigar masa rayuwa,ko wani shisshigi ta fannin gidansa ko iyalinsa. Haka mutum ne me yanke shawara akan abinda ya ma sa ta harkar gidansa ko iyalinsa,mutum ne ne ra'ayi da akidar tsiya.. bai shiga harkar rayuwar wasu haka nan beso a shiga nashi. Mutum ne da in ya yanke abu ba wanda ya isa ya canja mishi ra'ayi..</p><p> Duk wani abun jin dadin rayuwa ya mallakawa iyalinshi,,matarsa da yaransa,,haka sauran dangi da iyayensa ya wadata su da duk wani abu da zasu bukata. Sai dai fa yaransa da matarsa shi ne me yanke musu hukunci,duk wani abu dazasuyi kamar ta fannin karatunsu,me zasu karanta ,a ina zasuyi karatun ,da sauran su...</p><p><br /></p><p> Shamsu babban danshi yasa shi ya karanta fannin kasuwanci domin taimaka masa wurin business dinsa,yana da shekara ashirin da bakwai a duniya ya kammala masters dinsa,yana aiki tare da mahaifinsa a kamfaninsu.</p><p> Suna zaune cikin garin kaduna ,sai dai mutanen gombe ne ,,gaba dayan zuriarsu suna can gombe.</p><p> Shamsu yayi karatunsa a waje ,sai nurudden da mahaifinsa ya ce medicine zaiyi duk da kuwa baya so,sai dai bai masa musu ba saboda sanin hali irin na mahaifinsa.</p><p> Tun suna yan yara shine me yanke hukunci ,ko da abincin da zasuci ne ,hatta suturar da zasu sa shike yanke musu hukunci . Sai dai wannan shekararsa ta biyu ,amma abin ya gagara ,duk nacin sa ya kasa,har yanzu yana aji daya ,duk yan ajin su da suka fara tarw sun wuce sun barshi.</p><p> Mahaifinsa yaso turashi waje kamar yadda yayiwa shamsu ,sai dai ranshi nason deeni da yawa da bazai iya nisa dashi ba. Cikin yauansa yafi kaunarsa,ba mahaifinshi kadai ba duk wanda ya zauna dashi sai yaji ya shiga ransa,yana kaunar sa.haka nan Allah yamasa wannan baiwar. Halayyarsa da dabiunsa abin so ne da shaawa ga kowa,dan haka yasa duk tsananin Alh umar amma yana dagawa deeni kafa.. </p><p> Wannan karan deeni zai sake jarrabawa ta shiga aji biyu a ABU zaria,yayin da babanshi ya mishi alkawarin yi mishi duk abinda yakeso matukwar yaci jarrabawarsa. Haka nan deeni ya dage domin a zahiri ba abinda deeni yakeso kamar farida,,zai yi dukkan iyawarsa dan mahaifinshi ya bashi farida ,ya aura masa ita .</p><p> Soyayyar farida da deeni da shakuwarsu ya samo asali,tun suna yara ,tare suka tashi suna girma,saboda zumuncin da iyayensu mata sukeyi.... Deeni ya girmewa farida da shekara hudu ,tun suna wasan yara har takai ga suka fara girma da abota,har ta juye soyayya da shakuwa me tsanani,,wanda mutum bazai gane wayafi son wani ba a cikinsu. Iyaye da yan uwansu duka ba wanda beson maganar soyayyarsu ba . Mahaifiyar deeni na matukar son farida sabida kaunar da sukewa juna,da kuma irin tarbiyyarya da nutsuwarta . Ta fita daban da yan uwanta.</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI </p><p><br /></p><p><br /></p><p>COPIED BY SUMAYYA SA'AD(sumy luv❤)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>06 </p><p><br /></p><p>Tunda deeni yadawo daya masallaci bayan sallar isha ya zubawa wannan littafin na MISBAH ido,wanda faruda tayi wurgi dashi ,labarin ya taba zuciyar sa da tunaninsa,yanason sanin ya aka kare amma kuma alkwari yayi ,haka nan farida na gava da wannan labarin .</p><p> Yasa hannu ya dauki littafin yasa shaida a inda ya tsaya ,ya rufe yana kallon littafin har yasa shi cikin wata karamar drower ya rufe ,yana tunanin kalmar nan ta sauyin SHAUKI anya kuwa ?change of emotions gaskia hakan bai yiwuwa ba,gashi shi yakan gasgata duk wani labaran MISBAH ,yana da yakinin duk wani abinda ya fada yana iya faruwa,infact yana ma faruwa gana gani ,to amma wannan karon yana da ja ,sabida bai taba yadda shauki yana canjawa ba ,musamman ma shauki irin nasa,shauki na gaske ,shaukin da ya jima yana gina shi gini me karfi da tushe ,rushe shi abune da bazai taba yiwuwa ba balle a akai ga canji ..</p><p> Nan ya yi saurin canja tunani ya dakko littafin sa yana karantawa ,amma fa karatun babu abinda yake tunawa sai littafin . Tuni haushin kansa ya kama shi , ya ma zaayi ya bari haka ta faru dashi ,?</p><p> Zuciyarsh yaji tana zafi ,,deeni akwai dan banzan zuciya,tuni yaji tana hawa. Rufe ido yayi yana addua cikin zuciyarshi,sannan yayi saurin mikewa yabar study room din ,ya nufi cikin dakinsa ya dakko laptop dinsa yana kallon hotunan farida yana murmushi,,wasu hotunan nata tun tana jairirya,wasu kuwa tana yarinya ,,wasu kuwa suna tare tun suna yara har zuwa girmansu..</p><p> Waya ya dauko ya buga mata ta dauka tana murmushj tare da kashe murya tana mishi kalaman soyayyar da yake so,wanda suke kara haukata zuciyar sa da soyayyarta.</p><p> Lumshe ido kawai yayi yanajin kaunarta na bin jikinsa,yana ratsawa tare da hango su suna gudanar da wata aurw ne tattare da tsananin so da kauna,,tarw da farin ciki mara iyaka.</p><p> Bayan sun gama wayar ne ya tirawa MISBAH labarinsa kamar yadda ya saba ta email dinsa,yana yawan sharing feelings dinsa da kuma experience dinsa akan soyayyarsa da rayuwarsa ,da tarin tunaninsa da kuma hangensa, harma yayi challengn sabon labarin sa da ya rubutu na CHANGE OF EMOTIONS .</p><p><br /></p><p> Duk da MISBAH bai taba bashi amsar emails dinsa ba bai sa ya fasa rubuta masa ba ,,saboda yasan ba dole ne saya karanta ba,kuma in ya karanta din ma ba dole ne yabashi amsa ba. Irin su misbah dole za suyi jin kai da miskilanci,duk littattafansa yana nuna illar girman kai,,don kuwa Allah ke bada daukakar da mutum zai yi takama dashi,in yaga dana zai iya kwacewa darw daya,wanda a wannan lokacin muamalarshi da mutane zai iya taimakonsa,sai Allah sai dai yasan akwai mutane dayawa da suke da bambanci a rubutunsu.</p><p> Rashin amsar da misbah baya bashi be damshi ko ya bashi mamaki ba ,saboda dama ya zaci haka daga gareshi. Yasha masa tambayoyi amma shuru ,dan haka ma wannan karan yana gama tura masa email din ma ya rufe . Da da jyar yasamu karatun ya fara shiga yana fahimta kadan kadan har bacci ya dauke shi ..</p><p><br /></p><p>Deen matashin saurayi ne dogo ba baki,kyakkyawan gaske . Ba kyanshi zai sa kasoshi ba se halayyarshi ,yana da shiga zuciya . Matashi ne da yake da kula da addininsa sosai,ya yarda cewa Allah zai taimakeshi a rayuwa,zai cika masa burinsa na samun mace saliha,kamila ta gari...</p><p> </p><p>Bayan bautar ubangiji da biyayya ma iyaye deeni bashi da wani buri da wuce yayi aure ,rayuwar cikin aurw da yadda ya tsara zai yi shi,rayuwa ce me cike da soyayya da kuma ibada irin wadda annabin mu (SAW )ya yi da matansa,dan haka kullum adduarshi Allah ya cika masa wannan burin nasa tarw da farida.</p><p>Duk wani abu dayake fata da so da tunani a mace to farida na da shi,ga kuma soyayyar da sukewa juna mai tsanani wanda wannan shi zai taimaka su gina rayuwar auren da suke da buri. Saboda idan akwai so da kauna ana iya jure dukkan wani tsanani da jarrabawar rayuwa.</p><p> Duk da karancin shekaru irin na deeni shi da auren nan yakeso,bashi da wani dogon buri illa ya kara girma yayi dogon karatu da kudi,ya mallaki abin duniya kafin yayi aure,saboda a fadinsa rayuwar sa ba a hannunsa take ba ,bai so ta Allah ta kasance akansa batare da ya cika burinsa ba .</p><p>Haka nan ta bangaren farida ,tunda tayi wayo,ta girma tasan kanta ,to deeni shine abokinta ,kuma masoyinta ,bata sauraron wani namjij balle ta bashi fuskar soyayya. Asali ma dai tun kafin wani ya tunkareta labarin ta da shakuwar su da deeni zai riske shi.</p><p>Gata mace me kyau da tsari ,ga tarbiyya ,abin so da sha'awa ga kowanne namijj,sai di fa nan gani nan bari ,saboda ita jinta take tamtar matar deeni,bambancin ta da matar aure kadan ne a cewarta.saboda a tunaninta tsayawa da ma ta yi magana da wani namiji tamkar tayi cin amana ne ga deeni ...</p><p><br /></p><p>Wannan kenan🤔</p><p> </p><p> </p><p>Copied by sumayya sa'ad</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI </p><p><br /></p><p>COPIED BY SUMAYYA SA'AD(sumy luv❤)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>07</p><p><br /></p><p>Kwani tashi deeni ya tattara ya koma zaria,suka fara jarrabawa. Haka nan ra bangarwn farida ma suka fara jarrabawar kammala secondry,hakan yasa sukayi besa da juna . Haka nan yawan mu'amalar su ya ragu sabida karatu da kuma karancin lokaci,sai dai duk da haka rana bata fitowa ta fadi batarw da sunyi magana da juna ba na tsawon lokaci tare da mafarkin tsara rayuwarsu tare..</p><p> Deeni ya rigata gama jarrabawa dan haka ya tattaro ya dawo gida tare da shiri da tsare tsaren yadda aurensu zai kasance .yana karati sannan wani lokacin yana zuwa gidansu farida suna karatun tare ,,yana koya mata abinda bata gane ba . Haka nan yana matsawa mahaifiyarsa akan tafara yiwa mahaifinsa maganar auren sa da farida .</p><p> Takanyi murmushi tace karka damu mahaifinka zai yi kama komai ,,farin cikinka shine namu duka "</p><p> Hakan yasa hankalinsa kwanciya tare da alkawarin dagewa yayi duk abinda mahaifinsa yakeso,donya faranta masa ko da zaiyi abin da ransa bai so,don ya yadda farin cikin mahaifinsa shi ne samun nutsuwar sa da kwanciyar hanklainsa </p><p> </p><p>* * **************</p><p>Farida !farida!!farida !!! Taji muryar kaninta na kwala mata kira.</p><p> Hararsa tayi ,"meye ne ?</p><p> Tana kwance kan gado rungume da hoton deeni,yayin da take magana dashi ta waya,kuma ko minti goma basuyi cikakke da rabuwa ba . Ba abinda ta tsana irin tana magana dashi a katse ta .</p><p> Ganin harar datayi masa yasa kanin nata me suna yusuf shima ya turo baki . </p><p> "Meye kikke hararata ? Ai nima Abba ne ya aiko ni in kiraki ,in ba zaki zo ba sai inje in fada masa kina waya baki da lokacin amsa kiransa;""</p><p>A'a'a ,zo yusuf,tsaya,yi hakuri bazan sake harararka ba ,kace masa ina zuwa""</p><p>Harararta yayi yace kinci sa"a da kinga sharri :"</p><p> Nan ya fice ,ita kuma ta mike da sauri ,ta bangarwn deeni a waya kuma yanata tsokanarta.</p><p> "Kicewa Abba kina biyayya wa mijinki ne ,kina faranta masa rai ,kina masa hira me dadi ,yana jin miryarki me dadi yana ratsa masa jikinsa,kina samun lada,""</p><p>""Eh sosai zan fada masa,in yazo mun fada sai in tattaro har da kai ya hada-" </p><p>"Bakomai ya bata amsa"</p><p>"Ai dama dadi da wuya munyi alkawarin rabashi ni dake "</p><p> Tayk murmushi zan dauki wuyar ka dau dadin .</p><p>"A'a ni zan dauki wuyae ke ki dau dadin " ni dai a'a . Ta fada xikin muryar shagwaba .</p><p> Kin gankk ko ? Kin fara kashemun jiki da shagwabar kin nan ko ? Yanzu tunaninki sai ya fitine ni ya hanani sakat "</p><p>Tayi daria , ai haka nake so ,tunani na ni kadai ya fitini zuciyarka ""</p><p> Farida ! </p><p> Ta sake jin murtar mahaifiyarta ,da sauri ta katse wayar ta fita da gudu ,ta ce </p><p>Gani nan zuwa umma ,ina bayj ne ." To maza kiyi ki fito Abbanku nasan magana dake tun dazu " to umma " </p><p>Nan fa tayk falon nashi zuciyarta cike da tunanin kiran me yake mata haka?</p><p> Ganin sauran yayunta mata yasa gabanta faduwa ,dole akwai maganar da Abba zai mata .</p><p> Nan ta nemi guri ra zauna ta gaishe shi tare da fadin "Abba gani "</p><p> Ya kalleta yace naki ra yan uwanki nayi musu maganar aure ,kamar yadda kika san aladar gidan nan kuna gama sexondry nake auren ku . To Alhamdullilah ,lokaci yayj yan uwanki kowacce ta fada mun zabinta ,kuma nace su turo iyayensu ,sannan zanyi bincike in mun dai daita sai aure,don haka kema nakeso ki fadamun zabinki ,in baki dashi to sai ni in zabar miki ."</p><p> Kanta sunkuye zuciyarta taji tana harbawa ,ga Abba yasa mata ido alamar ita yake saurare . Bata dago kai ba ta ce ."Abba Deeni ne mukayi maganar aure dashi ""</p><p> Dama dai hakan ya zaci ji ,,sai dai saboda sanin su tare da kuma mahaifiyarta ta fada masa,sai dai yana son jin hakan daga bakinta . Ya gyara zama ya kalleta ya ce " deeni dan gidan makwabcin mu ko ?"</p><p> Ta amsa da eh "</p><p>"Yace to kamar yadda na fadawa yan uwanki ,kema ki fada masa ya turo mahaifinsa inhar aurwnki zai yi da gaske ,yaro ne da aka haifeshi a ido na nasan iyayensa,nasan halayyar sa,don haka bani da bukatar bincike akansa illa maganar aure. Ku tashi kuje dama maganar kenn""</p><p> Nan suma mike duka suka fita.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Farida ta tsinci kanta cikin wani yanayi dabata taba shiga ba ,,ta rasa wani irin abu takeji a zuciyarta da jikinta ? Fargaba ne ? Farin ciki ne ? Doki ne ko tunanin aurwn ne ? Ta rasa me takeji ,sai dai tabbas jikinta ya mutu murus.</p><p>Jiki ba kwari ta dau waya ta latsa sunan deeni ta sa a kunne, sai dai wayar tayi ringing har ta gaji ba amsa.</p><p><br /></p><p>A dai dai wannan lokacin deeni na zaune gaban mahaifinsa eansa bace yana masa fada saboda sake faduwa jarrabawar sa da yayi wannan karon . Ya jima baiga mahaifinshi cikin bacin rai haka ba,shi dai kansa sunkuye yana bashi hakuri,saboda shima baiji dadin hakan ba .</p><p> "" Baba kayo hakuri ,nayi iya kokarin iyakacin iyawata amma har yanzj Allah bai sa na kai ga masara ba "" </p><p>Wannan kake kira kokri " baban ya fada a fusace.</p><p> " ai mai kokari ba ya gazawa,kar ka dauka zamu shirya muddin kana wasa da karatu,in har baka min yadda nakeso ba kar ka zata zan taba maka yadda kake so ""</p><p> Nan ya mike ya fita ya barshi a wurn .</p><p>Hankalinsa ya tashi matuka ,haka ran sa ya mummunan baci ,yaji wanj irinzuciya da bacin rai na taso masa. Rufe ido yayi yana addu'a saboda samun saukin abinda yakeji. .</p><p>Wai har yaushe za su dunga samun rashin fahimta da mahaifinsa ? Sam ya kasa fahimtar sa ;ya kasa ganin kokarinsa. Ya makale a aji biyu ya kasa gaba ya kasa baya ,tabbas in ya sake faduwa korar sa za'ayi.</p><p>Zuciyar sa da kwakwalwarsa suka cushe da tunani iri iri ,ya rase meke masa dadi .</p><p>Mahaifiyarsa ce ta shigo tana bashi baki da lallashi tarw da kalamai masu kwantar da hankali har ya samu zuciyarsa tayi sanyi kadan ,,sannan ya mata godia ya samu ya mike ya shiga ciki . A nan yaci karo da tarin kiran farida a wayarshi,bai bata lokaci ba ya kirata ta dauka cikin muryar shagwaba tace "</p><p> " nayi fushi "</p><p>". Afuwan my dear ". Ya fada cikin mueyar lallashi.</p><p>"". Deeni meke damunka naji muryarka kana cikin damuwa?</p><p> "Akwai farida ,yau ma kamar kullum ban sami nasara a jarrabawata ba ,banji dadi ba ,haka na batawa baba rai , dukkan wani tsammani na yanaga jarrabawata""</p><p> Murya kasa kasa tacw nina banji dadi ba deeni ,,wannan karon naji ciwon abun diue da kai da Baba " </p><p>""Farida kalamanki sun razana ni ,yau ce rana ta farko danaga kin nuna damuwarki akan rashin nasarata , na zata kin fahimce ni ,kinsan matsala ta na rashin fahimtar karatun da nake amma duk da haka ina dagiya don ganin na cimma burin baba da kuma burin kasancewarmu tare da ke "" na sani deeni " ta bashi amsa .</p><p>Murya kasa kasa tace "kamun rashin fahimta nima,na nuna damuwata ne badan gazawarka ba ,sai dan son kasancewarmu tare ,tunda da bakin ka kace idan ka ci wannan jarrabawar babanku yayi alkwarin maka duk abinda ka nema ko kake bukata ,tabbas da ka samu nasara da yazo dai dai lokacin da muke da neman biyan bukata .......</p><p> </p><p> Bye </p><p> </p><p>Copied sumayya sa'ad❤</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRU GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p>COPIED BY SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>09</p><p><br /></p><p> Muryar deeni sukaji tsaye daga kofa.</p><p> Ya karaso cikin falon hankalinsa a tashe. In akwai abinda take dagawa deeni hankali be wuce ace zai rasa farida ba ,ya durkusa a gaban mahaifinsa idanunsa jawur ,hanakalinsa baya jikinsa,,ya ce ,</p><p>"Baba addini be hanani aure ba ,hasali ma ya halattamun yin aure a wannan lokacin. Baba addini bece dan bakaci jarabawar makarantar duniya ta boko karkayi aure ba ,,addini bece dole sai kanada gida da mota da abun duniya sannan kayi aure ba . Baba ka fadamun hujja da addini ba da abin duniya ba . </p><p> " ina zaka ajiye matar?</p><p>"Dame zaka ciyar da matar?:</p><p> Mahaifinsa ya jefa masa tambaya fuskarsa a daure,saboda koda wasa bai shirya yiwa deeni aure a yanzu ba .</p><p>Baba inada mahaifina wanda yake da arzikin da zai iya rikeni nida mata ta,har zuwa lokacin da zan gina kaina incigaba da rike kaina da matata har da iyayena da kuma sauran 'yan uwana. Baba ba zama zanyi kaita ciyar dani kana rike ni ba ,zan tashi in nema ,zanyi karatu,komai zanyi dan in kafa kaina . Baba ka taimaka mun matsayinka na mahaifina ka dafa mun .</p><p> Baba ni dan gatan ka ne ,na roke ka don Allah kayimun wannan gatan ka auramun farida, baba idan na rasa farida na rasa komai,baba farida macece ta gari,yarinya ce kamila ,ga nutsuwa da addini,macece danake yiwa yayana kwadayin samun uwa kamar ta.</p><p> Na jima ina gina soyayyata da rayuwata da zanyi da farida,baba banj da wata rayuwa in har ka rusa min wannan rayuwar na rasa ta............</p><p> Tausayinsa ya kama hajia don haka itama tasa baki tana taya deeni rokonsa. </p><p> Alhaji yaji ransa na baci ,,sai dai deeni yayi abinda zai yi ,amma bai isa yace zaiyi aure yanzu ba ,hasali ma ya dauki abin nasa a yarinta ,dan haka ya mike yabar musu falon ransa a bace batare da yace musu kala ba . Sai dai hakan ya tabbatar musu dacewa bai yiwa deeni abinda yakeso ba ,lokuta da dama daga yanayinsa suke gane eh ko a'a dinsa.</p><p>Hakan ya kara rikita deeni ,yabishi yana rokinsa.</p><p><br /></p><p> Ransa na matukar kaunar deeni ,,komai zai iya masa amma fa banda maganar aure yana dan karaminsa. Bashida wani dalilin da zai sa yaki aurawa deeni farida,sai don kawai ba yanzu bane lokacin da yakamata deeni yayi aure ba . Don haka ya dauka kai garesu yayi tafiarsa.</p><p> Bangarensa ya nufa batare da damuwa da halin da deeni yake ciki ba,dan yasan yarinta ce ke damunsa,rashin sanin ciwon kansa ne yasa yake cewa zaiyi aure yanzu.</p><p> Deeni yakasancwe cikin halin dimuwa da tashin hankali,lokaci guda yaji duniyar tana juye mishi sama da kasa ,rayuwa ba farida wani abune da bai taba tunani ba ,don haka da sake .</p><p>Ganinsa cikin tashin hankali yasa mama itama hamkalinta ya matukar tashi,ta hau lallashi da bashi baki cewa zata cigaba da lallaba mahaifinsa har ya amince. Da kyar tasamu ya saurareta ,sabida idonsa ya rufe ,bai san ma me yake fadi ba .</p><p>Yace ,, ba wanda ya isa ya hanani auren farida ,ko mahaifinsa bai yadda ba shi zai aureta a haka". </p><p><br /></p><p>A wannan dare deeni yayi kwanan tashin hankali da bakin ciki tare da tsoron rasa farida a rayuwar sa,a duk lokacin da yatuna zai iya rasa farida idan har nahaifinsa bai amince masa ba sai yaji ya tsinci kansa cikin gigita da dimauta. Haka ya kwana abin a ransa,ya kuma tashi dashi ,yayin da hajia ta kwana magana daya da mahaifinsa tana nuna masa tsakanin deeni da farida in an raba su ba karamin illata rayuwar su za'ayi ba.amma fir Alhaji ya kafe ba wanda ya isa ya canja mishi ra'ayi.</p><p> Washe gari a haka suka tashi gidan cikin rashin kwanciyar hankali ......</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv❤❤❤</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p>Writting by SAADATU WAZIRI GOMBE </p><p><br /></p><p>COPIED BY SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>08</p><p><br /></p><p>Deeni ,abba na yamana maganar aure yau,kariga da kasan hakain abba,muna gama secondry sch yake aurar damu,kuma kasan tsattsauran raayi irin nasa,ba mai canja masa,wannan akidar gidanmi ne ,ni ban isa incanja ba . Kuma deeni kasan kaine rayuwata,baza iya ko tunanin rayiwa da wani da namiji ba ,inba deeni ba . Abba yace katuro,in baba yaki fa ?</p><p> " bazai ki ba farida ,saboda baba naso na,kuma zan nuna masa idan bayason rasa kai na to ya auramun farida "</p><p> Tuni muryarshi ta canja ,"Farida kimun alkawari duk runtsi bazaki rabu dani ba ki auri wani ba. Farida bansan ya zan rayu bake ba ." </p><p> " Deeni nima ba zan iya rayuwa dawani ba in ba kai ba ,,nutsuwata da lafiata sai in ina tare da kai deeni" </p><p>Cikin muryar damuwa yace ,farida muna tare duk rintsi bazamu rabu ba ,zan fadawa abba zai zo nema mun aurenki gurin abbanki"</p><p> " kayimun alkawari deeni?? Nayi miki alkawari farida " ya bata amsa. </p><p><br /></p><p> Nan sukaita bawa juna kwarin gwiwa tare da kaunar juna,,sannan sukayi sallama.</p><p><br /></p><p> Wannnan tsoron dashi deeni yake kwana yake tashi ,wato tsoron rasa farida. Yana firgitashi sosai,sabida sanin halin mahaifinshi dana farida,dukkansu suna tafia ne akan ra'ayinsu da tsarinsu,ba wanda ya isa ya canja musu ,,sai dai yakan danji sanyi idan ya tuna irin soyayyar da mahaifinsa ke masa,zai iya aura masa farida don farin cikin sa.sannan a tunaninsa daga shi har farida basu da wani dogo buri,,dakinshi zai ishesu rayuwa kafin su kai ga inda zasu.</p><p><br /></p><p>Suna gama waya bai bata lokaci ba ya nufi dakin mahaifiyar sa,kai tsaye ya labarta mata abinda ake ciki. Kansa sunkuye gaban ta yana sauraron amsar ta,yayin da ita kuma tayi jugum tana juya maganar a ranta.</p><p><br /></p><p> Tabbas tasaan abu ne me wuyar gaske,sai dai kuma tasan irin tarin soyayyar farida da deenikarfin soyayyarsu ya wuce a rabasu,,ya wuce tsattsauran ra'ayi da akida irinta iyayensu ,dole ne daya zai sakko ko mahaifinsa ko nata,raba deeni da farida sai Allah .</p><p><br /></p><p> ""Mama""deeni ya katse mata tunani.</p><p>Ya kalketa,tunanin me kike ? Ko akwai matsala ne ? </p><p>Tayi masa murmushi tarw da girgiza Kai , ta ce .</p><p> """ Bawani matsala insha Allah ,anjima idan ya shigo zanyk masa maganar ,karka damu "</p><p> Ya sake kallonta cikin fuskar damuwa ya ce ;;</p><p>" mama ba ' a samj matsala ba ko ?</p><p> Tayi masa daria ,deeni kenan ,baza'a samu ba insha Allah ,komai zai tafi dai dai .ba kai kadai keson farida ba,nima ina sonta "</p><p> Murmushi yayi ya sunkuyar da kai,, ya fiya zuciyarahi cike da murna.</p><p> Tun fitarsa mama tashiga cikin damuwa da maganar zuci,tasan dole akwai rigima tsakanin deeni da mahaifinsa. Nan tacigaba da addua Allah ya kawo abun cikin sauki.</p><p> Daga deeni har mahaifiyarsa sun kasance cikin zulumi da tunanin me zai faru ? </p><p>Jin dawowar mahaifin nasa yasa yaji bugun zuciyar sa ya karu ,ya dunga safa da marwa a tsakar dakinsa. Baiyi yunkurin fita ba ,yana jira har sai an bukaci yaje.</p><p> Yadda deeni yake cikin tunani da fargaba haka farida ma ta kasance ,tana sauraron wayar deeni .</p><p> Bayan Ahj umar wato mahaifin deeni ya gama duk wani abu daya saba na al'adar sa in ya dawo,yana zaune a falonsa haj A'i ta same shi da maganar deeni . </p><p>"Alhaji magana zamuyi" ta fada tana kallon sa ,hakan yasa ya juyo ya maida kallonsa gare ta tare da tattaro hankalin sa akanta yace """ wace irin magana kuwa "? Ta gyara zama tacw ,,nu kabata sanin soyayyar deeni da farida kuwa,,''??</p><p>Ya kalleta ban gane ba ,deeni da farida?</p><p> "". Ta girgiza kai " kwarai......</p><p>Nan ta bashi labarin soyayyarsu,da shakuwarsu, takara da cewa .</p><p>"Yanzu lokaci yayi da mahaifin farida yakeson ya aurar da ita tarw da yan uwanta,kamar yadda kasani shi mahaifinsu yaranshi na gama secondry sch yake aurar dasu ,farida kuwa bata da wani saurayain da yawuce deeni ,,dan haka tayi masa magana ya fito,ya tura iyayensa a san da maganar neman aurenta ,shi ne ya min magana ya ce in fada maka""</p><p>Alhaji ya kallwra cike da mamaki ,ya ce .</p><p>Haba hajia ,ya kikemun irin wannan maganar kamar wata karanar yarinya ? Insu yara ne kema sai ki zama yarinyae ki biye musu ? Yaron da karatu ma ba inda yaje ? Yaron da baisan ciwon kanshi ba shine zaa nemar masa aure? Dan uwansa ma yaushe akayi maganar airen sa wanda ya girme da komai balle shi ? Da maganar shamsu ma kika min sai na saurareki amma DEENI ?ai ko ina da yarinya bazan aurawa kamar deeni ba ,yaron da yaki karatu,ya kasa nai da hankali akan rayuwar sa, yasan me yakeyi,ahekarun deeni nawa wai kike maganar auren sa? Shekarunsa ishirin da daya,yaro ne dabai san ciwon kansa ba balle har a dora masa na wata .</p><p>" baba addini ya hana dan shekara ishirin da daya aure ????</p><p>Muryar deeni sukaji tsaya daga kofa...................</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by sumy luv❤❤</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p>COPIED BY SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>10</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tunda sassafe farida ta bugawa deeni waya,daga jin muryarsa tasan ba lafia ba ,hankalinta yai mummunan tashi,kawai sai ta fashe mishi da kuka ,muryarta na rawa tace .</p><p> ""Deeni ya zamuyi ? Dama abinda nake tsoro kenn kullum ,kasan babanka ba zai yarda ba ,haka abbana ba mai canja masa ra'ayi,bazai taba bari na in zauna injiraka ba ,hada ni aure zaiyi da koma waye ""</p><p>" cikin muryar rauni da matujar tashin hanklai yace </p><p> ""Saurareni farida, baki da wani miji sai in Nsha Allah,Allah ne ya hadamu ba mai rabamu . Inma baba yaki nizanje in sami yayana babana,Bappah na zaj daura mana aure ,ba dai abbanki zai aura min ke ba ?</p><p> Abbanki zai aura min ke ,in har nabturo waliyyi na zai daura mana aure . Anjima kadan ,zan fita,zan wuce gombe ,zan je in sami bappah na ,kafin in wuce inason ganinki,ki fito kofar gida mu hadu"</p><p> Nan ra amsa masa da toh,ta ajiye wayar .</p><p> Bai bata lokaci ba yayi wanka ya kimtsa,ko breakfast bai tsaya yi ba ,ya cewa mama shi ya fita. Ko kallon mahaifinsa baiyi ba balle ya gaishe shi.</p><p>Tsawa ya daka masa tare da kiran sunansa.</p><p> Cak deenin ya tsaya ,sai dai ko juyowa bai yi ba balle ya yi niyyar zuwa inda yake.</p><p> Alhaji yace ,ban haifi dan da gari zai yawaye yana kallona ya wuce bai gaisheni ba,baka isa ba ." </p><p>Jin hakan yasa deeni ya juyo ya kalleshi fuska ba walwala ya ce .</p><p> " Ina kwana ? Da fatan ka wayi gari lafia ""?</p><p> Bai saurari amsar mahaifin nasa ba yasakai ya fita ,mahaifin nashi ya bishi da kallo. Baiyi mamakin hakan ba,sabida yasan halin deeni ,sai dai fa duk abinda zaiyi yi dan baazaiyi aure yanzu ba da bai san ciwon kansa ba ,yayi haukansa ya gama .</p><p> </p><p>""Ina kaunarka dana ,,shiyasa nake son yiwa rayuwarka gata kafin in kai ga maka aure,,sai na maidaka mutum sosai,,mace kowa zaka sani kowacce iri kakeso a rayuwa " </p><p> Mahaifiyar deeni ce ta shigo tare da matsowa inda yake , ta tsake masa tunanin da fadin "</p><p> Alhaji bazaka sake duva maganata ba kuwa ? </p><p> Ka auna irin soyayyar da rayan nan suke yiwa juna , karfa ka illata rayuwarsu sabida wani dalili naka na daban . Sannan yarinuar nan ya kakeso tayi ? Dukkna tsawon rayuwarta bata da wani wanda take saurara in ba deeni ba ,kanaso ace deeni ya yaudareta ya rabata dawasu mazan kuma shi be aure ta ba ? </p><p> Ya dago udo ya kalleta yace ,</p><p> In bazaki gaji da maganar nan ba ,to nima bazan gaji da fada miki a'a ba ,sabida bazan biye miki inbata rayuwar dana ba . Inshi bashi da hankali yakamata ace ke kina dashi .</p><p> " Alhaji a duba yarinyar nan,ita kuma meye laifinta a ciki don taso danmu,jininmu ,sai mu hukuntata akanshi ? So kake mahaifinta ya hadata da duk wanda ya samu ? Farida kamar diyarmu ce,bazamuso ta shiga gidan wani can da bata san halinsa ba ..""</p><p> " wannan ne damuwarki ?</p><p> ," duka"" ta amsa masa .</p><p>" Saboda deeni yanason yarinyar nan fiye da tunaninka ,haka ba jima da saka burin farida tazama surikata ,uwar jikoki na . Na tabbatar da zanyi alfahati da ita ,duk inda akeson mace ta gari ,yarinyar nan ta kai ""</p><p> "". To shikenn naji ,karki damu indai wannan ne damuwarki ""</p><p> Ta kalleshi cukin murna sa doki tace ,,kana nufin ka amince ? </p><p> " ki saurara ,ki sa ido kiga hukuncin da zanyj ,,ba zan bata rayuwar kowa ba "</p><p> Yana gama fadi ya mike ya nufi dining table ,ta bishi da kallo tana nazarin kalamansa.</p><p> Kawarai hakan ya mata dadi ,saboda akwai alamun nasara . Da murna ta mike ta bishi tana murmushi ba tare da takara ce mishi komai ba ,sai kokarin masa hidima . </p><p><br /></p><p> Denni na fita kai tsaye ya wuce gidansu farida ,a kofar gida suka hadu dukkansu hankalinsu a tashe ,,farida idanunta jawur tana ta zabgar kuka tamkar wadda akace iyayenta syn rasu. Hakan ya mummunan daga hankalin deeni ,soyayyarta ya dinga ji yana ratsa shi,yaji tankar ya jawota jikinsa ya rumgumeta ,sai dai bashi da ikon yin hakan ,don hakan sai yayi abinda yasan zai iya ya hau lallashinta tare da bata karfin gwiwa cewa ba gudu ba ja da baya yana tare da ita ,alkawarin da ya mata na aure ba fashi ,yana tare da ita.</p><p> Ta kalleshi idanu jawur sun kimbura ,ta ce </p><p> ""Deeni ina zan saka raina in na rasa ka ?</p><p> " ya zanyi rayuwar da batare da Deeni ba ?yaya zan soma rayuwa da wanj namiji a rayuwa matsayin miji ba Deeni ba ??</p><p> Nan yayi saurin rufe mata baki ,idanunsa suka kada,ya dinga jin wani irin zafi da radadi a zuciyarsa.</p><p> " karki kara furta haka farida ,karki sake ambatun rayuwa da wani namiji a rayuwarki. Kinajin zan iya numfashi in ganki kina rayuwa da wani ? Farida duk runtsi,duk wuya ,duk dadi ,munabtare da junan mu. Ni ne mijinki abokin rayuwarki,in Allah ya yarda zan mutu in na budi ido naga kin auri wani namiji """</p><p> Hawayene ya gangaro mishi na tausayin kansu duka .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv❤❤</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽</p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p>COPIED BY SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>11</p><p><br /></p><p>Deeni ,farida ,ku ne da sassafe haka? Lafia kike ta kuka inata magana tun dazu baku.ma san ina gurin ba ?</p><p><br /></p><p> A tare suka mai da kallonsu kansa,shamsu ne yayan deeni. Tuni deeni ya fada jikinsa yana kuka.</p><p> " ya shamsu kaji abin da Abba ya mun ko? Wai bazan auri farida ba ,ya shamsu kasan irin son da nakewa farida,ta yaya zan iya rayuwa babu ita ? </p><p> Itama faridan tayashi tayi tana kukan tace .</p><p> " ya shamsu ka taimakemu ,bazan iya auren wani namiji ba sai deeni,ya shamsu zan mutu inba deeni ,"</p><p> Kawai ta durkushe har kasa ta rushe musu da wani irin kuka deeni na tayata . Gaba daya suka zamewa shamsu hoto,ya bude baki yana kallonsu,yana mamaki duk da yasan irin soyayyar datake tsakaninsu ganin su cikin wannan tashin hankalin ya bashi mamaki tare da tausaya musu.</p><p> " yi hakuri farida " ya fada cikin muryar lallashi.</p><p> "" ba mai rabaki da deeni insha Allah ,zan taimaka muku , dake da deeni duk kanne na ne ,share hawayenki,mike muyi magaana." </p><p> Haya ya dunga sharewa deeni hawayenshi ,yana lallashinsu duka har suka dab fara samun nutsuwa ,anan ya tambayi deeni ya bashi labarin yadda sukayi da mahaifinsu,farida ma ta fada mishi yadda tayi da nata mahaifin ,ta kare zancen da kuka tana cewa "</p><p> Ya shamsu in deeni bai fito ba wlh Abba auramun duk wanda yakeso zaiyi,ni kuma ya shamsu deeni nake so " ta fashe da kuka .</p><p> " ya isa farida,naji "</p><p> Ya fada cikin muryar lallashi da tausayawa , a ransa yace ,"soyayya me zafi ta kama zuciyar yan yara."</p><p><br /></p><p> Ya tausaya musu kwarai,musamman a wannan shekarun irin na su da dukkansu ba mai tunani dai dai,,haka nan duk yadda zaa musu bazasu taba fahimta ba ,sabida sun haifi soyayyarsu tun suna yara suka tashi da ita ,sukayi ta rainonta ,don haka ravasu da juna ba karamin tashin hankali bane a gare su. Don haka ya kudiri aniyar taimaka musu,sabida a halin yanzu bazasu taba fahimta ba ,abu daya zasu fahimta a aura musu juna,kafin haka ya faru kuwa sai iyayensu sun canja ra'ayinsu ,ko dai baba ya hakura yayiwa deeni aure yanzu,ko kuwa Abban farida ya hakura tabar farida har deeni ya gama karatunshi. Sai dai fa wannan abin yafi komai wahala,don kuwa in duk duniya da abinda ke cikinta zasu taru basu isa su canjawa iyayensu ra'ayi ba.</p><p> A nan ya shamsudden suka yanke shawara da deeni da farida. Cewa zasuje can Gombe su sami Bappan su suyi mishi bayani ,haka zai nemi wani yayanta ya rakashi katsina itama su sami wani yayan mahaifinta wanda in abbanta yaki amincewa shi sai ya daura mata aure da deeni,shima deeni se kanin mahaifinshi ya masa waliyyi, in yaso wurin zama gida da komai zai dauki nauyinsu akansa. </p><p><br /></p><p>Nan take murna ta cika zuciyar deeni da farida,har ma suka haskowa juna murmushi,suna yiwa shamsuddenen godiya .</p><p> Kwarai yaji dadin ganinsu cikun farin ciki ,saboda shi dai daga deeni har farida kannen sa ne . </p><p> Bayan sun sami butsuwar ne ya tambayeta ko Abbanra ya tashi ? Don dana baba ne ya aikeshi ya ce ya fada masa yau da yamma inbaya komai yana so su hadu,akwai maganar da zasuyi .</p><p> Nab deeni da farida suka kalli juna jikinsu yayi sanyi,deeni ya ce " maganar rabamu zasuyi ko ?</p><p> Shamsu yace kwantar da hankalinka ,in ma magnar zasuyi ai mun samo mafita ko ? Kasan ko baba beji maganar bappa ba amma dai bappah zai saurare mu ,kuma ya daura maka aure ko ? </p><p> Farida ma tace ,Abban mu dai najin maganar Bappan mu,amma fa zai yi wuya ya canja masa ra'ayi , sai dai nima zai iya daura min aure "</p><p> Shamsu yace to kun gani ,karku damu,kuyi murmushi"</p><p> Nan suka masa murmushi duka,shima ya musu sannan ya shige ciki ya barsu a gurin a tsaye.</p><p> Deeni ya kalli farida yace, " Nsha Allah sai na mallake ki masoyiyata ,matsayin matata ta sunnah". </p><p>Allah ya tabbatar mana deeni,tafada tana kallon sa.</p><p> Yace , farida in yaya shamsu ya fito zamu wuce,inaso ki tuna ki sani ,duk wuya duk rintsi muna tare,farida ke tawa ce kimun alkawari."" </p><p> "" ni taka ce har abada ,ni amanarka ce""</p><p> ""Farida nima naki ne har abada ""</p><p> " Mu tafi " muryar shamsu sukaji ya fito. </p><p> Nan ya dinga zolayar farida yana cewa.</p><p> " mata zankadediyar zan masa a Gombe ,sai ku zama ku biyu ;" </p><p> Ai kuwa bai ankara ba ya ga tasa masa kuka ,ba shiri ya hau lallashi har ya samu tayi shuru. Yana jinjina soyayyar da suke yiwa juna . Nan ya shige ciki ya fadawa baba sakonsa ,sannan ya ciro motar sa suka kama hanyar Gombe ,farida na tsaye tana kallon su har suka bace .</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>12</p><p><br /></p><p>Dab da magriba Alh.Umar ,wato mahaifin deeni ya dawo daga office dinsa,kai tsaye ya wuce gudansu farida,ya samu mahaifinta a falon sa ,suka gaisa ,suka hau tattaunawa akan kasuwanci sannan matsalolin kasarmu da muke ciki na yau da kullum har aka kira magriba,sukayi alwala suka nufi masallaci tare.</p><p> Abinci da komai tare sukaci a gidan Alh. Ahmad,wato mahaifin farida. Suna nan tare har bayan isha'i,sukayi sallah suna hira har Alh. Umar ya yi masa maganar da ainihin ta kawoshi. Sun jima suna tattaunawa akan maganar wanda ya dauke su tsawon lokaci,har kusan karfe goma na dare ,sannan suka kai ga matsaya ,suka yanke hukunci, da alama kuwa dukkan su sun amnince da hukuncin da suka yanke.</p><p> Goma da rabj sukayi sallama ya nufi gida wanda ya yi dai dai da lokacin da su deeni suka dawo daga gombe.</p><p> Alhji yayi mamakin ganinsu a wannan lokacin. </p><p> " shamsu ,deeni, daga ina haka "? </p><p> Deeni bai saurareshi ba ya kama hanyar shiga cikin gida,ya daka masa tsaqa. </p><p> " Wai bada ku nake magana bane zaka kama hanya ka shiga ciki?</p><p> Bai saurare shi ba ya cigaba da tafiya,hakan yasa Alhaji shan gabansa ya ce,,,,</p><p> "" kai saurara ,gidana kake ,magana nake maka,wa zaka gwadawa danyen kai ? Me kake ji dashi ne ? Kana tsaye a gidan nawa.............""</p><p> Deeni ya katse shi ,ya ce, " ina tsaye a gidan mahaifina ne ,bandmga kuma wanda ya isa ya hanani shuga gidan nahaifina ba ,randa na shiga gidan mahaifinka sai ka kore ni ;;""</p><p> "" Deeni !!! Shamsu ya daka masa tsawa .</p><p> "" Bakada hankaki ne ? Baban kake yiwa wannan maganar? Ban fa sanka da rashin da' a da kadabi ba , meye ya haifae da wannan rashin da'ar ? </p><p> Mahaifin nasu ya kalle shi ,"dakata shamsu,kyale ni dashi ," ya kalle deeni ya yi murmushi tare da shafa kansa ya ce , </p><p>"" kayi gaskia dana ,nan gudan mahaifinka ne ,ba wanda ya isa ya hanaka shiga ko da kuwa mahaifin ne da kansa. Ina alfahari da hakan,da fatan kai ma zaka yi kokarin tsayawa kan kafafuwanka ka samu naka gidan na kanka ka ajiyeqa naka yaran yadda watarana zasuyi alfahari da cewa nan gidan ubansu ne ,don kuwa kai zan iya kyale k saboda kace nan gidan ubanka ne,kuma ba yadda na iya da kai tunda ni nakawo ka duniya. Amma kasani bazan bar dan ko yarka a gidana ba ,sabida kai ka kawosu duniya ,dan haka kayi kokarin nema musu muhalli kafin suzo,in ba haka ba karkayi kuka dani duj randa ba kori naka yaran a gidana na bar nawa dan,tunda gidan ubansa ne ..?</p><p> Nan deeni ya dinga jin zuciyarshi kamar wuta ,ransa bace ya shige ciki ba tare da ya sake tankawa ba . Ya fahimci sarai me mahaifin nasu ke nufi.</p><p> Alhajin ya bishi da ido yana masa daria ,zuciyarsa cike da tsananin kaunar sa. Sannan ya mai da hankalinsa kan shamsu,ya kalleshi yace .</p><p> " In shi yaro ne kai babba ne a kansa,ka dunga kula dashi kana bashi shawara me kyau,ka dai na biye masa. Karku manta ku ya'ya na ne ,ni mahaifinku ne "</p><p> Yana gama fadi ya juya ya yafi batare da ya saurari me zai ce ba ,nan shamsu ya wuce daki yana nazarin maganganun mahaifinsa tare da juya su a kwakwalwarsa.</p><p> Bayan fitar Alh. Umar daga daga gidansu farida bai jira sai da safe ba ya nufi bangaren su farida don yana da bukatar yin magana da ita a wannan daren. Ga mamakin sa kuwa ,da ya buga kofar bangarensu ita tazo ta bude masa kofa,ya lura tana cikin damuwa wanda shi ya hanata baccin ma.</p><p> Hannunta ya ja har zuwa falonshi ya zaunar da ita suna fuskantar juna ,idonta jawur ,fuskarta cike da tashin hankali. Tausayin 'yarsa da kaunarta ya shige shi,tana cikin rudani a lokacin da take da shekaru masu rauni.</p><p> " farida "" ya kira sunanta.</p><p> Ta dago kai ta kalle shi.</p><p> Menene damuwarki ?=</p><p> Menene matsalarki ? Ni mahaifinki ne ,zan miki duk wani abu da kikeso a rayuwa muddin ba cutarwa ne a gareki ba ""</p><p> Hawaye ne kawai ya fara zubo mata,don haka ya kyaleta da maganar tambaya,ya ce ,,,,</p><p> "" share hawayenki,ki kwantar da hankalinki,ki kuma sani duk wani abu da zan miki ,ko wani hukunci da zan yanke akanki ba cutarwa ba ne a gareki. </p><p> Dazu mahaifin deeni yazo gidan nan,wato Alh umar,"</p><p> Kanta a sunkuye ,sai a lokacin ta dago kai ta kalleshi ,ya ce;;;</p><p> " ya dafa mun duk abinda ke faruwa,kinsan irin mutuncin da dangantaka me karfi da ke tsakaninmu ,duk da bamu da wata dangantaka ta jini sai nakwabtaka . Sai dai fa mun dauki wannan makwabtakar da matukar muhimmancin gaske fiye da komai,ko dan uwana na jini bamu da kusanci da su kamar Alh umar . Mun daukaki juna ,kuma mun rike juna da mutunci da amanar makwavtaka. Don haka mun yanke hukuncin daura auren yaranmu ,dansa da ke 'yata ,ina fata ba zaki ban kunya ba ,za ki ban hadin kai ki min biyayya.............</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>13</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Wani irin farin ciki taji ya lullubeta ,bata san lokacin da tasaki dariya ba tana fadin.</p><p> " Nagode Abba "</p><p> Kafin ma yace wani abu tayi ciki da gudu tana tsananin murna.</p><p> Binta ya yu da kallo yana murmushi tare dabkadankai.</p><p> Tana shiga daki ,ta fada kan gado ta zari wayarta tana kiran deeni,amma layinsa yaki shiga ,ta kira har a gaji hakan ya tabbatar mata wayar sa na kashe. Amma duk da haka bata hakura ba ,haka ta dinga danna wayar har bacci ya dauke ta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Deeni kuwa a wannan dare kwana yayi yana safa da marwa,kansa ya dauki zafi,yana tunanin yadda bappansa zai kaya da babansa,in yaji zai daura masa aure. To amma duk da haka Bappansu ya tabbatar musu da in har baba yaki yarda shi zai shige masa gaba a al'amarin aurensa. Saboda Bappan sa mutum ne me addini da sanin ilimin sanin yakamata,duk zafin mahaifinsa ba zai hana shi fadar gaskia ba da yin abinda ya kamata.</p><p> " farida insha Allah sai na mallake ki matsayin mata,sai kin zama abokiyar rayuwata,uwar 'ya'yana ,soyayyar sa mukwyiwa juna ba zai tafi a banza ba ,burinmu da mafarkin mu bzai rushe ba "b</p><p> Da wannan tunanin a ransa da zuciyarsa har asuba .</p><p> Bayan dawowarsa daga masallaci ne ya dauko wayarsa , anan ya lura ashe ma tana kashe ne. Nan yayi saurin kunnata ,don yana son jin muryar farida kafin kowa,muryarta na bashi nutsuqa da duk wani gwarin gwiwa. Dan haka ya danna sunanta,shiga daya kuwa yaji ta dauka da sauri tana haki,tamkar wacce tayu gudu. </p><p> "" farida lafia kuwa ? Ya fada a firgice.</p><p> "" haba deeni "" </p><p>Ta fada cikin muryar haki da sauke ajiyar zuciya, ra cigaba.</p><p> ,"" me yasa ka boye min gaskia baka fada mun ba tsawon dare ,ka sa na kwana cikin tunani da dokin wayewar gari ?</p><p> Farida me kike fadi? Me na boye miki ?</p><p> Ban fahimta ba "</p><p> ' deeni ashe baba da Abba sun amince su daura mana aure ?"</p><p> "WHAT " ya fada da karfi .</p><p>" me kike nufi ? Wa ya fada miki ? Ina kikaji ? </p><p> A jere ya mata wadannan tambayoyin .</p><p> "Hey deeni relax,kana nufin baka sani ba ? </p><p> " Ni ban san komai ba ,ba wanda ya fadamun .</p><p> Farida tace ,to nida jiya da daddare abba ya kirani ya fadamun ,yace jiya babanku yazo sunyi magana,kuma sun yanke hukuncin daura mana aure " ALHAMDULILLAH " </p><p>Ya fada da karfi tare da ajiyar zuciya ,ya ce .</p><p> _" farida wannan albishir din naki wani irin tukuici kike so na baki ? Da yardar ubangiji farida zata zamo mallaki na,uwar 'ya'yana ?</p><p> Ban san ma wacce irin murna da farin cikin zan nunawa abba ba,ya gama min komai a duniya farida ina zuwa ........"</p><p> </p><p> Nan ya kashe wayar ya nufi falon babansa da gudun sa ,zuciyarsa cike da tsananin farin ciki da jin dadi mara misaltuwa. Ya same shi zaune a terrance na falon sa,hannunsa rike da jarida yana karantawa yana shan tea. Da Murnar sa ya iso yana daria tare da fadin .</p><p> ""Baba ina kwana ? Baba dama na san kana so na ,ba zaka so gani na cikin damuwa ba ,you re d best father in d world nagode baba ,Allah ya kara girma da daukaka. Baba na maka alkawari i"ll do my best to prove myself,,zan yi karatu ,in tsaya da kafafuna ,zanyi duk wani abinda kakeso ,daga yau bani da wani buri ko mafarki sai na faranta maka ya babana.</p><p> Na gode da wannan gata da ka min na aura min abinda nakeso ,ka tsareni daga fadawa sharri iri iri,kamin babban gata ,ka min abinda kowani uba mai hali zai yiwa dansa. Allah ya. Kara arziki ,Allah ya barni da kai ya babana,nagode".</p><p> Kawai sai ya rungumeshi ,abin da bai taba masa ba da girmansa.</p><p> Wani irin sanyi da farin ciku yaji a zuciyar sa,tabbas yana matukar kaunar dansa Deeni fiye da komai ,ganinsa haka a jikinsa tamkar yadda yake masa tun yana dan karaminsa yawanci da yake yaro in ya masa wani abu da yake so,irin wannan rungumar yake masa,yana nuna masa yaji dadi soaai da abinda ya masa.</p><p> Tuni shauki ya dibesa ,har yaji hawaye sun cika masa ido. Shima ya dada rungumar sa tare da sa hannu yana shafa bayansa,ya ce.</p><p> 'Naji dadin ganinka haka Deeni,wannan farin cikin da jin dadin da na jima inason ganinsa a fuskar ka ban ganshi ba sai yanzu ,nayi missing din wancan deenin nawa da wannan moment din a kokarina na gyara ka in sa ka a hanyar da naga ya dace da kai, kazama mutum mai daraja da kima anan muka samu sabani ,muka yi nesa da juna ,muka zama tamkae bakin juna,"" </p><p> Ya dada manna shi a jikinsa tare da fadin . </p><p> "" Bari inyi enjoying wnnan moment din don ban san yaushe zan sake samun wannnan kauna da kulawa daga gareka ba haka deeni """ </p><p> A zuciyar sa yake wannnan maganar ,sai dai a zahiri lumshe ido kawai ya yi yana jin kaunar dan nasa cikin farin ciki.</p><p> Muryar deeni ya jawo hankalin mama da ya shamsu da lukman zuwa inda suke ,suka tsaya suna kallon su. Mama ce ta ga abin ba na karewa bane tace . </p><p> " Deeni lafia ko ? </p><p> Nan ya saki baban da sauri ya nufe ta, " Mama "</p><p><br /></p><p> Ya kalli ya shamsu ,ya kamo hannunsa yace ,,</p><p> " kaji baba ya amince zai aura min farida ,mama ku tayani godia wurin baba,ban san irin godiar da zan masa ba sai addu'a"" </p><p> Dukkansu murna suke suna dariar ganinsa cikin farin ciki.</p><p> "" Deeni abinda zai sa ahi farin ciki ba wani abu ne wuya bane ,san shi bai dau duniyar da zafi ba,,,"" mama ta fada a ranta .</p><p>"" Dama nasan mahaifinka zai gane cewa abinda yake hanga maka da rayiwar da yake son maka ba shi ne a gabanka ba,farin cikinka yana ga abubuwa masu sauki,rayuwa mai sauki.Allah ya tabbatar da wannan farin cikin a rayuwarka ";;</p><p> Ya koma gaban mahaifin nasa tare da zama a daya kujerar dake gefen sa,ya jawo hannunsa ya hada da nasa ya manna,ya ce ,,</p><p> " Baba me kakeso in maka a rayuwa ??</p><p> Mahaifin ya kalle shi ya yi murmushi , ya ce.</p><p> ". Karatu nakeso kayi Deeni ,zaka iya barin kasar nan karatu,ba zaka dawo ba sai ka gama ????????????</p><p><br /></p><p> 🤔🤔ANYA BABU LAUJE CIKIN NAKI KUWA A WANNAN TAFIYAR</p><p><br /></p><p>SHIN A RA'AYI IRIN NA IYAYENSU DEENI ZASU IYA SAKKOWA CIKIN SAUKI HAKA DAMA ?? </p><p><br /></p><p>KUBIYO MU DANJIN ME AKE CIKI </p><p><br /></p><p>SUMY LUV😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wrirting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p> </p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤ </p><p><br /></p><p><br /></p><p>14</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Shuru yayi na tsawon lokaci,yana kallon sa ,sannan ya ce.</p><p> " Baba ban fahimta ba ""</p><p> Ya yi murmushi ya ce ," zan fahimtar da kai ,ba dai farida kakeso ba ?? </p><p>Ya girgiza masa kai da ,Ehh " </p><p>"" kanason farida ,inaso kayi karatu,tunda kuwa ba sama maka farida kai kuma zaka cika min burina na ganka a cikakken likita ko ? Ya girgiza masa kai alamar eh . Yace " to nayi magana da mahaifin farida ya amince zai bar farida ta jiraka,kaje kayi karatunka ka dawo tunda har nasa baki yasan da gaske nake. Sai dai duk da haka zabi biyu na bashi ; ko ya amince sai ka dawo ,ko kuma a daura auren karshen wata baka nan jar se kadawo ta tare,da kanshi ya yanke shawarar se ka dawo din,saboda ba yadda za'ayi ka tafi da ita wata kasa kana karatau ita kuma tana zaune haka a kasar da bata san kowa ba ,haka karatinka nason nutsuwa da mai da hankali,ba gadda za'ayi ka raba hankalinka ya zama baka bata lokaci ba,haka baka bawa karatun ka lokaci ba,kaga za'ayi biyu babu.</p><p> Don haka ya amince mana na tsawon shekara biyar din nan ,dan mutinci na da kuma zumuncin da ke tsakaninmu da kuma soyayyar da ke tsakaninka da faridan. Amma yace idan ya wuce ahekara biyar din nan bazai kara maka ko kwana daya akai ba ,don haka ya rage naka kayi kokari kagama karayunka na likita a cikin wadannan shekarun ka dawo ka aureta ,ko ka tsaya wasa kayi ta komawa baya wannan damar ta kubuce maka.."</p><p> Y kalli mahaifin nasa ya ce ,,"Abba na.maka alkawarin zan yi dukkan iya kokarina da iyawata ,ba zan yi wasa ba ,zan dage inyi karatuna in gama a cikin shekarun nan insha Allah . Ina fatan in cin ma manufata; in cika burinka da nawa ,ba zanyi wasa da damar da Abban farida da kai ku ka vanj ba ,da fatan zaku taya ni da addu'a kusa min albarka ,Allah ya taimake ni ""</p><p> "Zamuyi maka Deeni insha Allah ,Allah ya saka maka da mafificin alkhairi ,Allah ya baka abinda ya fi maka alkairi albarkacin wannan biyayya da kai min "" </p><p> ""Ameen baba ""</p><p> Ya amsa yana godiya ,sannan ya kalli mahaifiyarsa yace ,,,</p><p>"Mama ina bukatar addu'arki,ya shamsu kaima kasani a addua. Sannan mama na baku amanar farida ,da kula da ita kafin in dawo""</p><p> Tayi murmushi," zan maka addua deeni,,sannan farida "yata ce,zamu kula da ita insha Allah ""</p><p> Nagode mama</p><p> Ya fada yana murmushi,ya fita jikinsa a mace sabida tafiyar ya bar farida ba abu ne me sauki ba ,sai dai zai dage ya yi abinda zai sa ya samu farida ,ya mallaketa na har abada.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Wata guda da maganar Alh umar ya yi ta shige da fitar samawa deeni addmission gurbin karatun likita a America,ya taki sa'a suna daukan sabbin dalibai,dan haka ya shiga ya fita sai da yaga ya samawa deeni gurbin kaeatu a florida medical collage .</p><p> </p><p> A wannan lokacin kafin tafiar deeni kullum suna tare da farida,,baiyi wasa da wadannan kwanakin ba gurin kasancewa da farida,ko a gidansu ko a gidansu faridan,don kuwa haka suke shiga gidajen juna kai tsaya kamar nasu,haka irin so da kauna da tarairaya da mahaifiyar Deeni ke nunawa farida ko mahaifiyarta sai haka,son da mahaifiyae deeni kee masa ya shafi farida,haka mahaifan farida keji da Deeni sosai.</p><p> </p><p> Ranar da deeni zai tafi tun sassafe farida taje gidansu ta tayashi shirya kayan ssa,duk inda deeni yayi idanun farida na kansa,ya lura da hakan amma sai yai kokarin kau da kai saboda kar tayi kuka ,,amma daga karshe sai tayi abinda bai so din,ya matso gabanya yana mirmushi tare da ciro wayar sa ya ce ,,</p><p> "" saki fuska ki daina daure ahi in dauke ki hoto in dinga kallonki ina yuna ranar da na tafi na bar farida "" </p><p> Kara kumburo kumatu tayi saura dis tasa kuka,haka ya dunga daukarta hoto , ya ce .</p><p> "" To na kumburarrun fuska da kumatun sun ishe ni haka,ayi min murmushi kuma in gani. Ki tuna duk randa kika sake ganin deeni to ranar zai zama angonki ,me gidanki,,wannann kadai be isheki murmushi ba ;;? </p><p> Nan da nan tasaki murmushi ,bai bata lokacin daukar ta hoto ba . Ya yi saurin matsowa kusa da ita ya dauke su tare suna yiwa juna murmushi,wanda daga karshe mirmushin ya koma kuka.</p><p> Farida tasa kuka da karfinta,,"" yanzu deeni bazan sake ganinka ba se bayan shekara biyar? Ya zan rayu na tsawan wannan lokacin ? Deeni bazan iya jure rashinka na tsawon wannan lokacin ba ,,ni dai karka tafi ka barni,ka tsaya a daura mana aure ka tafi dani,"</p><p> Kuka take sosai wanda kukanta da yanayinta ya mugun karyawa Deeni zuciya,yaji kamarbya zubar mata da hawaye,tausayinta da tsananin soyayyarta ya dinga ratsa shi . Ranar ta farko kenan dayaji yason ya rumgumeta a jikinsa domin ya lallasheta. </p><p> Son ta mai karfi da wani irin shaukinta yaji yana fisgarsa,ya yi nufin rungumar ta din ,amma sai ya dinga jin zuciyar sa na bugawa da karfi,ta hana shi ,tsananin tsoron yin hakan ya shige shi,tsoron Allah ya shige shi. Shin in ya taba ta suka kai ga aikata abinda bai kamata ba fa ? </p><p><br /></p><p> "A'uzubillahi minasshaidanjrrajim " </p><p> Abinda ya dunga maimaitawa kenan.</p><p>Gaba daya ya rude ,ya rasa abin yi ,ga sonta ,ha tausayinta,ga tunanin tafia ya barta. Dabara ce ta fado masa,ya jawo hijabinta da take sake dashi,ya fisgeta har dakin mama,ya kaita gaban mama ya ce . To mama kinganta zata hana danki tafia ko ? Ta sani a gaba tamun kuka ,fada mata manyan 'yan mata da suka isa aure ba sa kuka kamar na 'yan yara"....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>15</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ai kuwa kamar ya ce ta kara kukan ta kara fashewa da kuka.</p><p> Ta ce " To wata baturiya ma zan samo can in aura"</p><p> Nan ta dalla masa harara hawaye na zuba ta ce ,,</p><p> Mama kin ganshi ko ?</p><p>Mama ta jayota jikinta,"Rabu da shi kinji,duk baturiyar da zai je ya samo bazata kai rabin farida ba ,zai yi ya gama ne ya dawo ya nemeki,duk randa ya dawo ki masa yanga son ranki,ki kyale shi ki sami wani mijin .</p><p> Duk da wasa mama take amma sai da yanayinsa ya canja,ya canja fuska duk da yana kokarin murmushi,juyawa yayi ya nufi ciki.</p><p> Farida tasan halin kayanta,don haka ta bi bayansa ta ce .</p><p> '" Ai duk duniya ba wanda ya kai deeni na a wurina,indai ba deeni ba sai dai in hakura da aure"</p><p> Jin hakan yasa ya tsaya tare da juyowa ya kalleta tare da sakar mata murmushi,yace.</p><p> " shi yasa nake sonki farida na,kin san yadda zaki kawo murmushi fuskata,kin san yadda zaki kula dani. Ina da yakinin in na aureki zan kasance ciikin farin ciki tarw da ke. Farida inasonki,ina kaunarki ke daya,ki kirw wannan a ranki gada ke ba wata."</p><p> Tayi masa murmushi itama,ta ce," Deeni na ka rike wannan a ranka ,daga kai bawani a zuciyar farida ,na ma alkawarin kaina da ajiyar kaina da zuciyata,zan tsarw maka amanar kaina."</p><p>Nan suka zubawa juna ido suna yiwa juna murmushi na tsawon lokaci,sannan deeeni ya yi ciki,ita kuma ta wuce gida da niyyar sai yazo tafia tazo su kaishi airport.</p><p><br /></p><p> Sai dai deeni bai bari hakan ya faru ba,wannan sallamar da sukayi shine ban kwanan da yayi mata,saboda yasan inta rakashi airport bazasu iya jure rabuwa da juna ba .</p><p> Jirgin deeni karfe biyu ne,amma sai yace mata karfe shida ne ,saboda baiso ta rakashi.</p><p> Lokacin tafiyar su ,har gidan su ya shiga ya yiwa iyayen farida sallama,sai dai basu san lokacin zai tafi ba . Nan suka masa addu'a tare da fatan alkhairi da kuma Allah ya kiyaye masa hanya. Lokacin nan farida na ciki tana ta kokarin faman neman kayan da zata sa ta yiwa deeni gayu ya yanga lokacin da zata rakashi,a wannan lokacin ma har deeni sun kama hanyar airport har da mahaifin faridan.</p><p><br /></p><p> Tunda suka dau hanya yake basu amanar farida,tare da kara jaddada musu irin son da yake mata,da kuma irin dagewar da zaiyi ya yi karatu. Nan mahaifinsa ya kara masa tuni da ko hutu bazai zo ba ,shi da nigeria sai ya gama karatu.</p><p> Ya kalli mahaifin nasa yace," nasanj baba,ba zan dawo ba sai na cimma manufata da burinka da yardar Allah.," </p><p> Mama da shamsudden tarw da kaninsa. Lukman da mahaifin farida suka masa rakiya wanda mahaifin sa kuma tare zasu tafi sai ya kaishi sannan ya dawo .</p><p> </p><p> Bayan sun isa zasu shiga jirgi kafin ya kalli mama yace,</p><p>" in farida taji na tafi zatayi kuka,ki lallasheta sosai kinji mama ?</p><p> " To deeni ,zan lallasheta,sai dai kai kuma wa zai lallashe ka?</p><p> Idanunsa suka kada sukayi ja ,ya yi saurin kai da kai ya ce,ba komai zan lallashi kaina"</p><p> Shamsuddeen yayi saurin rungumarsa yana lallashi har da lukman a masu bashi hakuri,dakyar ya iya danne zuciyarsa ya juya ya tafi. Har ya bar ganinsu yana kara maimaita musu ,mama,shamsu,lukman ku kula min da farida ,na baku amanar farida.Mama tayi karfin hali kamar zatayi kuka tace .</p><p> Mun rike amana deeni,Allah ya kai ka lafia,ya kare ka"</p><p> Ameen" ya amsa,sannan ya shige suka tafi. </p><p> Su mama basu bar filin jirgin ba har sai da suka ga tashin jirginsu sannan suka kama hanyar gida,dukkan su jikinsu a mace,zuciyar su cike da kewar deeni.</p><p><br /></p><p> Suna isowa kofar gida kuwa sukaci karo da farida ra hada kai da gwiwa tana ta zabga kuka,,tun daga wannan lokacin mama tasoma aikinta na lallashi. Ta ja hannunta suka shiga ciki,ta dinga lallashinta tarw da kalamai masu dadi da kwabtar da rai,ta nuna mata deeni ya yi haka ne saboda kada ya ganta ya karaya ya kasa tafiya.</p><p> "" farida kiyi masa addua tare da kara masa karfin gwiwa har ya samu nasarar yin abinda ya kai shi ya dawo lafiya kuyi aurenku kinji ko ?</p><p> Ta girgiza mata kai ,. Naji mama ,na gode,zan jure in Allah ya yarda.</p><p>Yawwa farida ,shiyasa nake sonki,akwai biyayya da jin maganar na gaba da ke. Allah ga miki albarka.</p><p> Ameen mama" . Ta fada murya a sanyaye. Ta mike tayiwa mama sallama ta nufi gida zuciyarta cike da tsananinson deeni,da kuma kewar sa. Ita dai bataki ta dawo gidan da zama ba tayi ta zama a dakin deeni tana kallon inda yake rayuwar sa tana jin dadi ,sai dai ba halin yin hakan sai dai ta dinga zuwa,ya zama dole tayi hakuri da rashin Deeni......</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sabo shi akewa kuka,inba so kuma baza'a yo ba ,,ma'anar so a zuciya ku rike amana ku kau da zan ba..... ...😍😍😍😍😍</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Byee </p><p><br /></p><p>Sumy luv😍❤😍❤😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting bySA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p>=================== GIDAN NOVELS ====================================</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>17</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Washegari bayan sun gama breakfast ,Alh. Umar tare da shamsu da likman duk sunyi shirin fita office yayin da lukman makaranta zai tafi.</p><p> Alhaji ya kalli shamsu dake shirin mikewa yace ,</p><p> " ka zauna ina da maganar da nakeso muyi da kai da mahaifiyarka ,kai kuma lukman kaje driver ya ajiyeka a makaranta"" </p><p> Nan ya mmike ya fita ,yayi da shamsu ya bar dining table din ya nufi tsakiyar falon kamar yadda yaga mahaifinsa yayi yana tunanin to wacce magana Alhaji zai yi da shi haka?</p><p> Mama ta iso cikin falon ta zauna a kujerar da ke kallon tashi , tace .</p><p> " *Alhaji muna sauraronka ,wace magana ce haka?</p><p> Ya gyara zama yace,inaso ku saurare ni da kyau da kunne basira,kwanakin baya kafin deeni ya tafi karatu munyi wani shirri ni da mahaifin farida. Maganar gaskia bamu shirya maganar auren deeni da farida ba ,sai shamsuddeen da farida ,haka kuwa bazai yiwu ba har sai deeni ya tafi karatu ya bar kasar nan,fatiyarsa kuwa abu ne mai wuya in ba har yaji za a aura masa farida ba.</p><p> Maganar gaskia mahaifin farida bai yarda da barin 'yarsa tayi jiran shekaru biyar ba,ni kuma ban yarda da aurawa deeni mace ba tare da ya gama karatu ya mallaki hankalin kansa,yasan ciwon kansa ba daga farida har deeni soyayyar yarinta ce ke damun su,dukkan su basu san ciwon kansu ba ,ba yadda za'ayi mu hadasu aure da deeni .</p><p><br /></p><p> Sai dai maganar ta mana amfani , na sami deeni ya nutsu yana karatu,kafin shekara biyar din nan zai shiga ruwan hankalinsa,ya nutsu ,zai mance farida idan yaji dan uwansa ya aureta ya fara sabuwar rayuwa. Itama kafin nan zata gane shamsu shi ne wabda ya dace da ita.</p><p> Babban dalilin kulla wannan aure shi ne ,na farko dacewar farida da shamsu,tana dai dai lokacin aurw shima haka. Sannan Nuraddeen ya bata mata lokaci ,tun tana karama bata bawa wani saurayi dama ba sai deeni,ba zan so yanzu da ta tashi aure ya zama tamkar deeni ya yaudar ta ba. Yanzu bata da wanj,haka bazan so kuma nahaifinta ya aurar da ita ga wani wanda bai dace da ita ba ,wanda bazai bata kulawar da jindadin da ya dace da ita ba . </p><p> Farida tamkar diyar cikina na dauke ta ,shiyasa zan damka amabarta ga dana wanda na yadda dashi ,na amince masa. Inada tabbacin shamsuddeen zai bata suk wata kulawa da kauna matsayin mijinta. Sannan burina da naki zai cika na ganin farida ta zama surukar mu,zamu hada jini da zuri'a dasu ,zata haifa mana yan jikoki. Da Shamsuddeen da Nuraddeen duk abu daya ne a wurin mu,don haka mun yanke hukunci a watan sha biyu za muyi auren su december ,sai ku soma shiri." </p><p> Yana gama fadi ya mike zai fita,,hajia tayi saurin mikewa cikin girgiza da firgitar jin maganganunsa hade da mamaki,yayin da shamsuddeen kansa na sunkuye,maganar mahaifinshi ta mugun kadashi da bashi tsoro. A kullum yana yiwa mahaifinshi abinda yake so,amma wannan karan zasuyi tsiya irin wadda basu taba yiba ,don kuwa ba zai taba aurwn macen da kaninsa,jininsa,dan uwansa ke ciwon so ba.</p><p> Hajiya ta sha gabansa,ta tsare shi da ido ,ta ce</p><p> " wacce irin magana kake ne me kama da ta yara? Ba na tsammanin deeni da farida yara ne ,sai dai kai da mahaifin farida ne tunaninku irin na yara. Kuna nufin kuce min kun yaudari yaran ku kenn? Kun yiqa yaranku karya kuna iyayensu ? Kana son fada mun zaku wargaza rayuwar yaranku da hannun ku ? </p><p> Na yarda na amince ina son farida matsayin sirika ,haka kuma babu bambanci tsakain shamsu da nuraddeen a wurinmu. Sai dai fa inaso kasani akwai bambanci tsakanin deeni da shamsudden a wajen farida . Zuciyarta da ruhinta gaba daya deeni suke so,deeni suke muradi.</p><p>Wannan maganar da ka kawo bata wasa bace,kanason haddasa gaba tsakanin yaranka ,ka dauki abinda daya take matukar so kabawa daya? Shamsu yace kamaka yanason farida ne ko ita faridan ta fada maka zata amincd ta auri shamsu ? Kasan ko yawan soyayyar da ke tsakanin farida da deeni?</p><p> Wannan ba damuwa ta bace " ya fada cikin daga murya d bacin rai,ya ce </p><p> " karki zara maganganunki zasu canja min niyyata da ra'ayi na,ba shawararki nake nema ba ,ina fada muku ne dake da danki ku soma shirye shiryen biki,banason sake jin wani raayi naki ko na wani musu akan maganar nan "" ya kalle shamsu da kansa yake sunkuye , ya kira sunansa. </p><p> " Kai shamsudden ,dago kai ka kalleni nan " yayi saurin dago kai cikun tashin hankali da kuma tsorata da yanayin mahaifin nasa, yace .</p><p>Na maka zabin mat matsayina na mahaifinka ,ina fata ba zaka bani kunya ba idan har na isa da kai,kuma na taba maka wani alfarma a duniya a matsayina na uban da ya kawo ka duniya,to ina so kayi biyayya ga maganata ka auri farida, ka rike ta hannu bibbiyu da amana . Ni nan mahaifinka nina baka amanar farida kanaji na ? In kuma kana ja to inji "</p><p> Ya sunkuyar da kai muryarsa na kyarma yace ,,naji baba ,na amince,na maka biyayya,bani da ja ,"</p><p> Mahaifin nasa yayi murmushi , ya ce naji dadi ,Allah ya maka albarka ,Allah yasa ka gama da duniya lafia,Allah yasa 'ya'yanka su maka biyayya kamar yadda ka mun ""</p><p> Ya kalli mama cikin bacin rai ,ya ce.</p><p> Saura wani yayi garajwn sanar da deeni abinda ke faruwa,ko ma waye ne zai fuskanci mummunan fushi daga gare ni""</p><p> Yana gama fada ya juya ya fita,ya bar mama da shamsu cikin balain tashin hankali.</p><p> Haka kai yayi da gwiwa tamkar wani karamin yaro yana kuka ,hankalinsa ya mummunan tashi . Dum yadda ya kai ga kin aurwn masoyiyyar dan uwansa bai isa ya ki bin umarnin mahaifinsa ba,bashi da karfin gwiwar kin yiwa mahaifinsa biyayya ,ya zama dole ya bi umarnin mahaifin sa kamar yadda ya ke masa tun yana dan kankaninsa. </p><p> Mama ta tsinci kanta cikin rashin hankali da kaduwar da itama tana bukatar mai lallashinta balle ta lallashi shamsu.</p><p> Sai dai shamsu ya kas jurewa har sai da ya matsa gabanta yana kuka yana fadin .</p><p> Mama ki taimake ni kiyiwa baba magana ,ya za ayi in auri farida yarinyar dana shaida soyayyarsu da kanina da nake matukar so ? Tun suna yara ni na san irin soyayyar sa sukewa juna ,mama ya za ayi in jefa kannena biyu cikin tashin hankali da bakin cikin rabuwa da juna? Ya za ayi in raba su ta hanyar auren farida ? Mama da wane ido zan kalli Deeni? </p><p> Kasa magana tayi saboda bata da abinda zata iya fada masa illa ta taya shi kuka ,hawaye taji yana gudu a fuskarta,tausayin yaran nata duka biyub ya kamata.shin mahaifin su bashi da zuciya ne da bai tausayinsu ? Ko baya hangk cewa zai hada gaba da fitina a tsakanin yaransa? </p><p> Da kyar ta iya budar baki tana lallashin sa tare da bashi hakuri cewa basu da yadda suka iya ,saboda mahaifinsu yafi karfin su duka .</p><p> " ka dage da addu'a in haka shi ne mafi alkhairi Allah ya tabbatar ,in kima ba alkairi Allah ya warwre shi.</p><p> Mama ina alkairi a auren cin amana ? Mama kin tuma har deeni ya shiga jirgi yana bani amanar farida ? Mama yaya deeni zai dauke ni in yaji na ci amana na auri macen da take rayuwar sa,farin ckin sa,koman sa ? </p><p> Tayi murmishin karfin hali tace, kar ka damu ,Allah na nan ,kayi kokarin mai da al'amarin ka gare shi,haka nan deeni ya san halin mahaifinku,zai fahimci ba kayi auren ne da niyyar cin amana ba .</p><p> Shamsu ,yana da kyau ka kwantar da hankalinka ,kasawa kanka aurwn farida ko baka so,ka tursasawa kanka da zuciyarka,saboda tun da mahaifinka ya lashi takobi sai ka auri farida to ba makawa si ka aureta ,sai wani ikon Allah,,""</p><p>Nan ta shige ciki ta barshi a wurin a durkushe ,abin duniya ya masa zafi. Daga karshe ya mike ya koma dakinsa,office din da bai fita ba kenn. Ranar mahaifinsa ya masa wannan uzurin ,don yasan halin da ya tsinci kansa . Ya bashi dama yaji da kansa da zuciyar sa.</p><p> Haka mama ta koma daki hankalinta tashe ,idonta rufe tana addu'a da fatan kar wanan abu ya zama sanadin wargaza kan 'ya'yanta ,yayin da tausayin farida da deeni ya cika mata zuciya . Tabbass zasu fuskanci tashin hankali,sai dai zata taya su da addu'a Allah ya basu juriya......</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>Shin farida zata amince da wannan sabon al'amarin ?? </p><p> </p><p>Yaya deeni zaiji idan ya riski wannan bakin labarin ??</p><p> </p><p> Ga masu binmu sai ku biyomu a wannan lambar 08029350366 dan jin ra'ayoyinku ,,kofarmu a bude take ... </p><p> </p><p>Cigaban labari kuma yanaga yawan ra'ayoyinku ,domin shine zai tabbatar da kuna binmu da gaske kamar yadda kuka fada..mun gode </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p> Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>16</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sati guda da tafiyar Deeni komai ya mike masa,ya gane yadda wurin yake. Gida guda mahaifinsa ya sama masa kusa da makaranta,bai samu wata matsala ba ya fuskanci abinda ya kawo shi,ya hau karatu gadan-gadan . Ganin ya mike yasa mahaifinsa ya yi sallama da shi ya dawo gida nigeria don fuskantar nasa ayyukan.</p><p> </p><p> Ya dawo hankalinsa kwance,bashi da wata matsala ganin deeni ya mike kuma da gaske yake,wannan ya matukar bashi kwanciyar hankali.</p><p><br /></p><p> Duk da Deeni yana matukar kewar farida,amma ya daure bai mata waya ba saboda gudun mai da hannun agogo baya,a duk lokacin da zai ji muryarta dukkan wani kokarinsa zai iya komawa baya,hankalinsa zai tashi yaji yanason komawa ya ganta. Don haka ya daure,ya hora zuciyarsa da rashinta na tsawon lokaci ,sannan ya kirata.</p><p> Da farko ta nuna masa fushinta na kyaleta da ya yi ba waya da kuma tafia ba yayi ba tare da ya bari ta masa rakiya ba . Sai da ya jira ta gama mitar sannan ya ja dogon numfashi ya ce.</p><p> "" farida na,farida matar Deeni . Kinsan deeni da irin son da yake miki ,trust me inada da dalilina na yin haka"" </p><p> " Na sanj Deeni "</p><p>Ta fada murya kasa kasa,ta kara da cewa.</p><p> " ina kewar ka ne kawai Deeni,kasan na saba da kai da soyyyarka ,Deeni ba dadi da baka nan "</p><p> Yi hakuri farida,zai zama tarihi"</p><p>Ya canja zancen ta hanyar zolayarta da cewa,</p><p> Nasan duk randa kikazo America kika ga dogon gini rudewa za kiyi ,saboda farida ta yar kauye ce "</p><p> "" Ta turo baki tamkar yana ganinta ,ta ce. </p><p> "" kai da bamu ga ka rude ba ,saboda kaima dan kauyen ne ai" </p><p><br /></p><p> Yace oho dai ,ni dai yanzu na zama dan birni na barki" </p><p> Dariya sukayi duka,sun jima suna hira suna bawa juna labarin yanayin da suka shiga da kuma halin da suke ciki. Ya bata labarin yadda yake matukar jin dadin karatun sa a yanzu,,yake kuma ganewa,saboda yadsa aka saukaka musu shi,sabanin yadda yake a nigeria. </p><p> Itama ta bashi labarin makarantar high islam da mahaifinta yasa ta koma,saboda yaki barinta tashiga university sai dai tana karuwa sosai ta fuskar addini a wannan makarantar ,tana kuma ganewa ,tana jin dadin karatun addini. </p><p> Sunyi sallama da juna ,suna yiwa juna addu'a da fatan alkairi,zuciyoyin su cike da jin dadi da farin cikin magana da juna </p><p><br /></p><p>Wasa gaske deeni ya mike da karatu har ya saba da rashin farida ,yana kiranta wani lokaci sau daya a wata ,saboda dagewa da yayi ya fuskanci karatun dake gabansa,soyayyar farida na kara masa karfin gwiwa. Haka itama farida kullum suka yi waya sai ta karfafa masa gwiwa da kara jaddada masa soyayyar da take masa . </p><p> Itama haka tayi sabo da ba sa waya da deeni sosai sai lokaci lokaci,kuma ta fahimci dalilin sa don haka tayi masa uzuri ta fuskanci nata karatun tare da musu addu'a. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> * * * * *</p><p><br /></p><p> Zaune yake a falo shi daya yana kallon labarun karfe tara ,Alh umar kenan ya mai da hankalinsa gaba daya kan jin abinda ke faruwa a kasar tamu, lokacin Alh Ahmad ya masa sallama ya shigo falon. </p><p> Ya mike da sauri yana dariya ya tare shi saboda muhimmancin da yake dashi a wurinsa,yana matukar girmama shi,da kuma dangantakar su ta makwabtaka. </p><p> Nan ya nuna masa wurin zama tare da sawa a kawo masa abin sha. Suka sake sabuwar gaisawa,suka dan taba hirarsu data shafi kasuwanci da kuma kasar gaba daya. Tare suma kalli labaran suna sharhi akai.</p><p> Bayan sun gama Alh Ahmad ya kalle shi ya ce . </p><p><br /></p><p> "" ya labarin deeni kuwa ? Duk da dai muna waya da shi amma mun kwana biyu bamuyi waya ba ,yana lafia ko ?</p><p> Alhaji yayi murmushi yace ,lafia kalau,ya maida hankali yana karatu yadda ya kamata. Ina kara maka godia bisa taimako da hadin kai da ka bani ""</p><p> Alh.Ahmad ya yi daria ya ce ,"Ai deeni ya dana ne,kamar yadda ku ka riki farida kamar 'yarku haka nima na riki deeni""</p><p> Ya kara kallon sa da kyau yace,,"yanzu ma maganar yaran nan ce ta kawo ni,kan maganar da mukayi kwanaki ,kaga tsahon wata tara kenab da tafiar deeni,komai ya mike masa ya soma fuskantar karatunsa da gaske,haka nutsuwa tana kara shigar sa,din haka inaga lokaci yayi da zamu fito mu bayyanawa yaran nan da iyayensu mata manufar mu da kuma dalilinmu ,kaga watan sha biyu nakeson auren yaran nan ,kuma har da farida ciki,kaga yanzun wata biyu ya saura ,gara mu sanar dasu su shiryawa maganar auren tun wuri;""</p><p> Alh. Umar ya sauke ajiyar zuciya ,yace. </p><p> " kayi gaskia tamkar ka shiga cikin zuciyata ne,inada shirin maka maganar sai ka rigani ,inaga yanzu abinda za'ayi ,ka kira farida da mahaifiyarta kayi musu bayani,haka nima nan zan kira nawa iyalin nayi musu magana. Abinda nakeso da kai shi ne,mu tabbatar musu da maganar da muke fada UMARNI ne muke basu ,maganar mu doka ce a gare su ,dole su bita ba wai ra'ayin su muke nema ba. In munyi haka zai zo mana da sauki,amma in muku nuna ra'ayinsu muke nema zai sa mu sami matsala ,zai zamana tamkar mun vasu damar kin bin abinda muke so ne "</p><p>Alh Ahmad yayi dariya,yace,,kayi gaskia ,maganarka abin dubawa ce. Inaga gobe in Allah y kaimu zan kirasu muyi maganar,zaka ji yadda mukayi da su"</p><p> Alh. Umar ya amsa da,nima in Allah ya yarda goben zanyi magana dasu,sai mu duba ranar da ta dace mu tsayar da ranar biki"</p><p> " To shikenn ,Allah ya kaimu goben " </p><p> Da wannan. Maganar suka yi sallama ,tare da yiwa juna sai da safe akan zasu hadu washe gari bayan tashi daga harkokin su da yamma za su hadu..........</p><p><br /></p><p><br /></p><p>SHIN IYAYEN SU SUN YARDA ZAA AURAWA DEENI FARIDA NE KAFIN YA DAWO ????</p><p><br /></p><p> WANI IRIN FARIN CIKI DEENI ZAI YI IDAN YA SAMU LABARIN AN DAURA AURENSHI DA FARIDA? </p><p> MUJE ZUWA 😜😜😜</p><p><br /></p><p>.</p><p>sumy luv😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p>Cpoied by SUMAYYA SA'AD❤❤ </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>18</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kamr yadda ta kasance da su shamsu haka ta faru tsakanin farida da mahaifinra da mahaifiyarta. Tunda ya fara musu bayanin manufar sa bai kai ga karasawa ba ma farida ta mike ta tare shi da fadin .</p><p> "Abba ba zan taba airen wani namiji a duniya ba inba deeni ba ,nayiwa deeni alkawarin kaona da zuciyata,zuciyata deeni take matukar so,don haka Abba kabar wannan maganar ta yaudara. So kike inci amanar deeni ? Kuma Abba bazan iya rayuwa da wani ba in ba deenni ba ,Abba ka taimakeni ,gara min mutiwa ta daa rasa deeni" </p><p> Mikewa yayi ya sharara mata mari sai data ga taurari.</p><p> " yarinyar banza mara kunya" ya fada yana huci. </p><p> ". Ke har kin isa kiyi jayayya dani ? Yaushe kika koyi rashin kunya ? Kin san me kike fada kuwa ? Har kina fadan mutuwa da iliminki da hankalinki ,kin san meye mutuwa da har kike ikirarin gara miki mutuwa ? Me aka miki me zafi a duniyar nan haka ? Kuma ko me ya miki zafi babban sabo ne kice kin gwammaci mutuwa . Miji dai nike da hakkin zaba miki shi ko ? Ba ke ba ,don haka na zaba miki shamsu ,inkin isa in na daira miki aure da shi ki ki zama a gidansa ,sai in san ke cikakkiyar mara kunya ce "</p><p> Ta durkusa har kasa tana kuka ,baba kayi hakuri don Allah kar ka rabani da masoyi na deeni,Abba deeni shi ne rayuwata ,ban taba tunanin wani a matsayin mijina in ba deeni ba,Abba ba zan iya biyayyar aure ga kowanne namiji ba sai Deeni "</p><p> Ki daina bata yawun bakin fa, shamsu dai kin aurwshi kin gama "</p><p> Ta miki , Abba bazan auri shamsu ba sai dai ka kashe ni "</p><p> Ya kalleta cikin bacin rai ,ya ce</p><p> Baki isa ba ,idan kinason zama a gidan nan matsayin diyata ,idan kinaso mahaifiyarki ya cigana da zaman aure a gidan nan kar ki sake musu dani akan maganar auren ki da shamsu""</p><p> Maganarshi ta karshe ya mugun girgizata ,tabbas bazataso auren uwarta ya kare akanta ba . Ya kalleta,kina da zabi ,ko naki auren ko na uwarki,ina saurarwnki"</p><p> Cikin tsananin kuka da bakin ciki tace ,Abba na amince ba don inaso ba ,sai don umma," </p><p> Ro banason sake jin komai ko wani musu akan maganar nan,munyi mun gama . Haka ko da wasa ban yarda idan kunyi waya da deeni ki sanar masa ba ,balle ya dawo ya daga mana hankali. Sai ki soma shirye shiryen biki" </p><p> Ya kalli mahaifiyarta da ta bude baki tana sauraron su cikin tsananin mamaki ,ta rasa abin fadi. Tabbas namiji halinshi sai shi . </p><p> Yace ,ki rubuto mun duk abinda ku ke bukata na bikin farida za'a siyo shi,cikin december za'ayi auren "</p><p> Yana gama fadi ya juya ya fita ba tarw da ya saurarwsu ba,haka farida ta zauna a wajen ta sa hannu akai tana ta rusar ihu tamkar wacce aka cirewa ido ko ta easa uwarta ko ubanta. </p><p> Mahaifiyarta dai bata da yadda zatayi sai lallashi da nasiha ,sai dai tabbas dole ta taya 'yar ta kukan rashin babban masoyinta . Sannan karin tashin hankalin ma wai ta auri dan uwansa? </p><p> Nan ta rungumo ta a jiki tana lallashi ,tana mata addu'a.</p><p> 'Farida Allah zabi mafi alkairi"" tana fadi tana hawaye ,basu ankara ba sukaga jama'ar gidan duk sun cika falon kowa na tambayar meya faru ? Duk wanda yaji abinda ya faru sai ya tausayawa farida gami da juyayin wannan alamari,saboda kowa yasan karfin soyayyar dake tsakanin Deeni da Farida. </p><p> Haka farida ta wuni kuka ,ba ci ba sha,bakin ciki da takaici ya cika mata zuciya,tsananin kewar deeni da kaunarsa taji yana ratsa ta. Hankalinta ya mummunan tashi ,taji kwakwalqarta na juyawa tabdinga jin kamar zata yi hauka saboda kwakwalwarta ta kasa amince mata da hukuncin da mahaifinta ua yanke akanta,ta dawo tamkar wata mai jinni. </p><p> Ta mike da gudu ko dan kwali babu akanta ta nufi gidansu deeni,kai tsaye ta wuce dakin shamsu tana kwala masa kira.</p><p> ". Ya shamsu"" ya shamsu ka taimake ni " </p><p> Ta sameshi ya kasa tsaye ya kasa zaune yanata zagaya dakin ,shima abin duniya ya masa zafi. Bai ankara ba ya ganta a dakinsa ba zata tamkar an jehota ,ta sunkuya ta kama kafafunsa. </p><p> </p><p> Ya shamsu ka taimake ni kace baka sona,kace ba zaka aure ni ba . Yaya shamsu kaima ka sani ko ? Kasan deeni nake so,kasan ba zan iya rayuwa da wani namiji ba in ba deeni ba . Ya shamsu ina son Deeni ,ka taimake ni ya shamsu ,bazan iya aurenka ba "" </p><p>Kaka take tana ta surutai kamar mahaukaciya ,sai da shamsu ya rikota suka fuskanci juna. Kiyi hakuri farida ,an fada miki ba dole akayi min ba ne kamar yadda aka miki ? Bani da yadda zanyi sai dai bin umarnin mahaifina,bani da yadda na iya,ya zame min dole zan ci amanar dan uwana . </p><p> Deeni ya bani amanr kula da ke kafin ya dawo,zai dawo ya samu naci amanarsa ,na auri macen da yake matukar so. Farida ba abu ne me sauki ba a gareni,duk kuka da rokona da zakiyi bani da ikon canja ra'ayin mahaifina ,yadda bazaki iya kin bin umarnin mahaifinki ba haka ba zan iya kin bin umarnin mahaifi na ba ;""</p><p> Ta fashe da kuka, to ya kakeso nayi? </p><p> Kasan dai deeni nakeso ,Deeni ne rayuwata,please ka taimake ni ya shamsu ka taimake ni.</p><p>Mama ce taji hayaniyarta ,ta fito ta zo ta janyeta, yayin da shamsu ya lumshe ido hawayen bacin rai na zuba masa,yana jin kukanta na ratsa kunnuwansa,yana kuntata masa zuciya </p><p>.....</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kuyi hakuri bacci yazo yasin 😀😀</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting bySA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Salam !!yan uwa ayi mun afuwa na rashin posting two days🙏🏼🙏🀊</p><p>uma sannan naga sakonninku,kuma naji dadi sosai Allah ya bar zumunci</p><p> Ameen ..</p><p> </p><p><br /></p><p>19</p><p><br /></p><p> A daki mama tayi ta lallashi amma inaaa!! Farida kuma take ,bata ji bata gani,bata saurare,daga karshe ta tashi ta tafi dakin deeni,ta hau bisa gadonsa tana shakar kamshinsa,tana kuka tana fada masa irin tsananin son da take masa.</p><p> Farida taba gushe ba a gurin har sai data shide ta suma a wajen,mama da shamsu sukayi asibiti da ita a rude. Da kyar likita ya samu ta karfado,,sai dai zazzabi mai zafi ya lullubeta,haka nan bata nar kukan da take ba har sai da akayi mata allurar bacci,bacci me nauyin gaske ya dauke ta . </p><p> Mama ta zuba mata ido tana kallonta,tana matukar tausaya mata tare da mata addu'a a ranta ,tana maganar zuci.</p><p> " Yarinya karama ta hadu da kaddarar da ta kasa jurewa,ta kasa tawakkali,haka nan mahaifanta sun kasa ganewa."" </p><p> Nan ta mike don zuwa tayiwa mahaifiyar farida waya ,,nan shamsu ya zauna ya zura mata ido,sai ya daina jin tausayin kansa se farida.. halin da ta shiga ya firgita shi,ya san suna matukar son juna da Deeni amma bai zaci farida na haukan son deeni haka ba. Shin taya zai rayu da macen da take matukar haukan son wani bata ji bata gani ? Taya zai iya rike amanar da mahaifinsa ya damka masa bayaan cin amanar dan uwansa da ya yi ? </p><p> Yana cikin wannan hali mahaifiyar farida da yan uwanta suka shigo,hakan yasa ya fita .</p><p> Kowa dai bashi da ikon mata wani abu sai addu'a har kusan magriba ,mahaifansu maza sukazo. Tabbas sun tausaya mata,amma hakan bai sa dayansu yaji yana da niyyar canja ra'ayi ba.</p><p> Har faridan ta farka tana kuka tana rokon mahaifinta,amma sai ya kau da kai gareta,yace,intaga bata auri shamsu ba to dayan su ba ya numfashi ne ko ita ko shi mahaifinta,ko kuma shi shamsu din . Yana gama fadi ya fice abinsa. </p><p> Daga nana farida tasawa kanta dangana,sai dai ita tasan tabbas mutuwa zatayi in tta auri wani da ba Deeni ba ,don haka ta soma shirin bankwana da duniya tana jiran ta Allah ta kasance akanta.</p><p><br /></p><p> * * * * * * * * * * *</p><p><br /></p><p> Tun lokaci da aka kulla maganar auren shamsu da farida duk iyayen su suka hau shirye shiryeb biki ,duk wanda yaji magnar aurwnsu sai yayi mamaki saboda kowa dai yasan farida da Deeni take soyayya ba da yayansa ba . </p><p> Tuni Alh umar ya siyawa shamsu da farida tsalelen gida na gani na fada,ba abinda bai sa musu ba na zamanj mai tsadar gaske.</p><p>Hatta kayam daki bai bukaci Alh Ahmad da yayi ba,b dakin da bai sa kaya a ciki ba ,duk wani kayan l</p><p>Kyalw kyale an sakwa farida da shamsu.</p><p> Ganin kara da kawaici da Alh umar ya masa yasa shima ya ce to ya bar wani maganar hada kayan aure ,haka nan shi ya dauki nauyin biya masa kudin sadaki. Alh umar baiki tayi sa ba ,saboda a fadinta shamsu dansa ne.</p><p> Ansa bikinsu a juma'ar farki na watan karshe.</p><p><br /></p><p> Ranar da Deeni ya bugowa mama waya gaba xaya rudewa tayi har ya so ya fahimci akwai matsala ,amma sai ta nuna masa ba komai,tana fama da hayaniya ne ana shirin auren yayun farida wani satin ,sannann shamsu ma zai yi aure.</p><p> Ihu yasa mata na murna da mamaki ,ya ce </p><p> Mama ya shamsu zaiyi aure ? Mama kinsan ban taba ganin ya shmsu da budurwa ba sai kace me tsoron mata,amma nayi mamaki . A ina matar da zai aura take ? Unguwar mu ? </p><p> Mama tayi masa dariar da bata kai zuci ba ,tace. </p><p> Deeni kenan ,wannan tambayoyi haka,ro koma dai yana nema ko baya nema ya samu ,yarinyar unguwarmu take ," </p><p> Ayya mama,ina farida? Tna zuwa kuwa ? Kinsan nayi ta neman wayar ta a kashe,haka layin ummanta ma baya shiga ,ina jin dai hidimar bikin suke mama,yanzu da ina nan da har dani za a hada da auren yayun ta da yaya shamsu ayi,amma ba komai mu namu mu biyu zaayi mana special one ....</p><p> Tuni mama taji t rude ,ganin shamsu ya shigo tayi saurin mika mishi wayar. </p><p> Ga dan uwanka nan kuyi magana ""</p><p> Jiki ba kwari shamsu ya karbi wayar yayi da mama ta koma gefe tana hawaye,tsananin taisayin danta ya ratsa ta ,tana tunanin ranar da deeni zai samu labarin auren farida shamsu da halin da zai shiga ,bacin rai da tashin hankalin da zai shiga ne babban fargabarta . Tasan halin Deeni da zuciyar sa,in ta kule shi ba me kyau bane ......</p><p> Oh Allah !!! Kayi mana maganin abinda ba zamu iya yiwa kanmu ba ""</p><p> Tunda shamsu ya karbi wayar Deeni ke ta masa surutu yana zolayar sa,yana masa tsiya amma yayi tsit kamae ruwa ya ci shi. Deeni na tambayar sa yarinya da zai aura yar wanj gida ce? Kuma meye sunanta? </p><p> Tuni yaji kansa ya sara,tambayar tayi masa kunci , y rasa inda zai sa kansa.ya hau masa kame kame,yayin da deeni ya dauka zafin kan aure ne ya debe shi,don hka ya kyale shi,nan ya kawo masa zancen da yafi kowanne kunci.</p><p> Ina amanata da na baka ,farida ? Ina fata kana kulamun da ita ,ya take ,a wane hali take ? Kullum sonta da shi nake kwana ina tashi ,bani da burin da ya wuce in gama karatu in dawo in auri farida............</p><p> Kafin ya kai ga ida maganar sa shamsu ya yi saurin katse wayar tare da kashewa ,saboda ba zai iya jurewa ba . Dum kunyar deeni ta ishe shi hauahin kansa da tsanar kansa ya kama shi , bai san yaushe ya sa kuka ba............. </p><p><br /></p><p>Nace wai dan ma ba ido da ido suke magana da deenj ba kenn🤔</p><p><br /></p><p><br /></p><p>ASUBA TA GARI YAN UWA</p><p><br /></p><p><br /></p><p>SUMY LUV😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>20</p><p><br /></p><p>Kwanci tashi ba wuya,bikin su farida ya matso,an gama shirin komai ,'yan uwa da abokan arziki sun gama cika gidagen duka biyu cike yake da jama'a. </p><p> Duk wanda ya kalli fuskar shamsu da farida yasan suna cikin dmuwa da tashin hankali,kowa kuwa yasan dalili ,don haka dai aka dinga binsu da fatan alkhairi.</p><p> Ana gobe daurin auren da safe mahaifin farida yayi kiranta falo,fuskarta a kode kuma a kumbure saboda kullum tana cikin kika. Nan ya sata a gaba yana mata nasiha.me ratsa jiki sosai tare da fada da kuma gargadi na taji tsoron Allah tayi biyayya ga mijinta,ta rungumi kaddarata hannu bibbiyu.</p><p> Tana kuka tayi masa godia ,tare da alkawarin zata yi masa biyayya,ya rungumi kaddara ,ta saduuda,Allah ya bata ikin jurewa.</p><p> Yaji dadi kalamanta sosai ,ya sa mata albarka sannan ya ce mata Deeni ya kira shi yana son magana da ita saboda duk wayar da zai saneta ya kora a rufe.</p><p> " Inaso in ya kiraki ki nutsu ki amsa,kar ki nuna masa komai . Sannan karki fada masa abin da bai sani ba ,kar kiyi yadda zai zargeki. Ki tuna taratu yake yi ,idan yaji wani abu yana iya barin karatun ya dawo,kuma ya samu an daura miki aure,yazo aita rigima dashi ,zhi ya rasa ki kuma zai rasa karatun ,kinga ya yi biyu babu kenn. Ni na tabbar in kina son deeni ba zaki so hka ya faru da shi ba ".</p><p> Nan ya mika mata wayar," zai iya kira a kowanne lokaci"". </p><p> Gabanta na tsnkewa ta karba tana tunanin me zata ce masa ? Ya zata yi ta fara magana da deni ? </p><p> Tana cikin wannnan tunanin kuwa ya bugo ,nan ta zurawa wayar ido da lambobin nasa tana kallo,idonta ya ciko da hawaye ,da kyar ta iya hadiye kukanta ta dauki wyar .</p><p> Murya kasa kasa tayi sallama,nan Abba ya mike ya bar falon,don ya basu wuri suyi magana.</p><p> Farida na!!!. Deeni ya fada cikin muryar shauki . </p><p> Farida I missed u so much,nayi rashinki sosai wayarki da ta umma sam ba a samu,na san dai hidimar biki ne ko ?</p><p>Lumshe ido tayi tna jin muryarsa hade da soyayyarsa mai karfi suna ratsa ta .</p><p> "Darida kinyi shuru ,kina jina kuwa ?</p><p> Ina jinka deeni,ina sauraron daddadar muryar da nayi matukar kewa ne. Deeni kunnuwa na sun jima suna son jin wannan muryar,kasan mun jima bamu yi waya ba ,wayarka ba a kira ,sai dai kai ka kira,in kuwa an kira ma za a ji baya shiga." </p><p> Jikinsa ne taji yayi sanyi,ya rasa dalili muryarta duk ya kashe masa jikj. </p><p> _" Farida kiyi hakuri ,ki kuma dada hakuri akan wanda kikeyi ,kinga yanzun mun gama jarrabawa har na samu nasarar shiga aji biyu ,kinga kuwa na fito da result me kyau irin wanda ban taba ba . Inasha Allah kamar yau ne zan gama in dawo "". </p><p> "Nayi murna matuka deeni,Allah ya baka saa ,Allah ya taimake ka. Ina nan ina maka addu'a.</p><p> " na gode farida,shi yasa nake sonki,nake kuma jin kamar duk duniya zai yi wuya a samu mace kamar ki. Ya shirin biki? Naji har da ya shamsu ma zai yi biki,ranar muna magana da shi su mama wayar ya yanke ,da na sake kira kuma bai shiga ba. Ya ce mun a unguwarmu rake ko ? Kin san wacce yarinya ce ?</p><p> Nan da nan ta rude ,ta dabarbar ce ,ta rasa inda zata sa kanta ,baki na bari ta ce.</p><p> Ban sani ba ".</p><p> Tayi saurin cewa ,baka tambayeni karatu na ba""</p><p> Haka ne fa faridana ,in na dawo zaki hada matsayi biyu ai ,mata da kuma malamata,don kuwa darasi zan dunga dauka a gurinki. Tabbas farida inna aureki nayi sa'ar mace ,'ya'yana sai sun min godia da sama musu uwa ta gari.</p><p> Kuka me karfi taji yazo mata,tayi karfin halin cewa ,</p><p>Deeni umma na kirana ,zan mata qani aikin,sai mun sake waya""</p><p> To farida na ,ya amsa .</p><p>Kullum kina tuna inasonki ,kullum sonki karuwa yake ,ina nan na rike miki amanar kaina kamar yadda kika rike mun amanar kanki".</p><p> Ba shiri ta kashe wayar ta kwanta a wurin tayi kukanta ta koshi,ta tuno gove inAllah ya kai mu war haka ta zama mallakin shamsu ,ta rasa deeni har abada.</p><p> Bayan ta fita ta mikawa Abba wayar sa ta nufi gidansu deeni ,kai tsaye ta wuce dakinsa domin yin bankwana da shi da memories dinsa. Haka ta dinga bi tana tsincs duk wani hotunanta,wasikunta da duk wani tarkacenta da zai tuno masa da ita. Duk wani gift data taba bashi sai da ta tattara . Sai dai tana da tabbacin ba za ta rasa wasu a wurin sa ba,yayin da ta dakko nata gaba daya da ya taba bata ta dawo da su. Duk randa ya dawo yaga haka yasan ehh sun rabu har abada,taci amanar kaunarsu da soyayyar da suje wa juna ,bata rike alkawari ba.</p><p> ""KAYI HAKURI DEENI "</p><p>Nan tayi kuka tayi kuka har ta gode Allah,yayin da take kallon dakin tamkar yana ciki,tana ganin duk wanj shiga da fita nasu da suka raba yi a dakin,fadan su,wasan su,dariyar su da kukansu . Ta tuno da zolaya tare da tsokana irin na Deeni ,sai da tay murmushi.</p><p> Ba shiri ta dinga tuno irin ran da ya dinga daukar ta hoto ranar da zai tafi. Bata da yadda ta iya sai hkuri da abinda ya fi kardinta.</p><p> Nan ta share hawayenta ta fita,t ja kofar.</p><p>Tuni taji zuciyarta ta bushe ,hawayen idanunta ma sun bushe ,bata da sauran abinda zai kara daga mata hnkli ko sa ta kuka ko daria ,ko wani farin ciki tunda ta riga ta rasa DEENI ........</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hmmmmmm.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Naji dadin yadda wasu suka fahimci cewa wani baya taba auren matar wani,haka nan wata bata taba haifar dan wata ,,yayinda wasu suke ganin anyiwa Deeni rashin adalci ,,tabbas dan jin dadi kam dole deeni bazai ji dadi ba amma ku duba exactly abinda ke faruwa mana ,wlh nawa ne suke shan soyayya kuma yazama na wadda akayi dashi ba dashi ake murarta ba ......</p><p> Gareki MARIAM HASHIM naji dadi yadda kika fi kowa fahimta😍😍i am really appreciated, tnks </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>21 </p><p><br /></p><p>Washe gari bayan an sauko daga masallacin juma'a aka daura auren Shamsuddeen da farida,dubban jama'a ne suka shaida ,kasancewar daurin auren dana yan uwanta yasa jama'a sukayi yawa,aka cika,manya da kananan ,talakawa da masu kudin duka wannan ranar unguwar ba masaka tsinke,cike take da jama'a 'yan daurin aure,'yan uwa da abokan arziki.</p><p><br /></p><p> Bayan daurin aure mahaifansu maza suka shirya gagarumar walima wanka aka gayyaci manya manyan malaman sunnah ,suka zo suka gabatar da wa'azi me tsoratarwa da kuma shiga jiki game da aure. Daga shamsu har farida sun sha jinin jikinsu ,wa'azin ya shige su,suka kara tabbatarwa da fa aure ibada ne ba son rai ko zuciya ba,haka nan aikin ibada zasuyi . In kuwa aka samu akasin haka za su iya fadawa ga halaka,ya zame musu dole su ji tsoron Allah ,suyi aikin auren don Allah don tsoron sa da kuma kwadayin samun rahamar sa. Anan dukkuansu suka kara sakankancewa,suka saduda,suka rungumi kaddara.</p><p> Da yamma lis aka tashi daga walimar ,jama'a suka watse ,wanda suke nesa kuwa suka koma cikin gidajen da suka zo,sai washegari su tafi ,saboda su Abba dai sunce ba wani sauran taro ko bidi'a ,wannan daurin aire da walima ya isa.</p><p><br /></p><p> Bayan sallar isha'i Abba da kansa ya raka sauran 'ya'yansa gidajensu,yayin da farida take karshe kasancewarta kusa,nan ya kira farida ta kara jan kunnenta da taji tsorob Allah,kada ta kuskura ra biyewa wani son zuciyarta tace zatayiwa mijinta wani eashun kunya ko saba masa,din kuwa aljannatar na karkashun kafar sa,don haka ta bi a hankali tayi masa biyayya ,ta manta baya. Ya kara sa mata albaek na biyayyar da tayi masa,tare da mata alkawarin cewa zai mata duk abinda take so a duniya muddin bai fi karfinsa ba . </p><p> Bayan angama iyauenta mata ma suka bita da tasu kalar nasihohin,sannan Abban da kansa ya rike hannunta tare da kishiyar mahaifiyarta suka kawo ta har gidansu deeni. </p><p> Falon baba sukayi da ita,inda mama da Baban tare da shamsu da kuma wasu 'yan uwan suke jiran zuwan su,nan kuwa suka mike suka tarbe su cikin murna da farin ciki,inda mama ta jawo hannun farida dake ta rusar kuka tace.</p><p> " Bari ni dai in amshi 'yata da ke ta rusa kuka,an rabaki da mama bayan kina tare da daya maman naki ,me zai dame ki?</p><p> Nan suka yi daria duka,amma ban da farida da shamsu. Nan dai akayi gaishe gaishe tare da barkwanci ,yayin da aka gabatar musi da abinci da sha ana hira. Sannan Abba ya bada amanar farida ga Alh umar da mama da kuma shamsu.</p><p> Sun karba hannu biyu tare da nishi alkawarin farida ba zata taba fuskantar wata matsala ko damuwa ba ,zasu riketa tamkae yar cikinsu . Haka shamsu ma yayi alkawarin riketa amana da kula da ita ,tare da yin hakuri da duk wani abu dazata masa.</p><p> Abba yaji dadin maganar sa kwarrai ,nan aka ta saka musu albarka ,yayin da suka hadu duka suka yi musu nasiha sannan suka kara jaddadawa juna yanzu zumunci ya kullu,an zama yan uwan juna . </p><p><br /></p><p> Bayan tafiarsu baba yasa shamsu a gaba yana gargadin sa da ya rike farida hannu bibbiyu ,ko da wasa kada ya musguba mata . Anan shamsu ya masa alkawarin rikera da gaskia .</p><p> Mama kuwa alfarma ta nema abarta tayi rikon farida na tsawon sati biyu a wurinta kafin su tafi gidansu da shamsu.</p><p> Baba yace wannan tsakaninki da ita da mijinta ,in sun amincen to,in kuwa ba su amince b babu dole,.."</p><p> Nan farida tayi saurin mannuwa a jikin mama tace ,"na amince" </p><p> Mama tayi murmushi tace ,"yawwa yar mama "</p><p> Shamsu ya kalle su yana daria ,ya ce </p><p> Nima na amince"</p><p> Baban shima ya kallesu yace ," To nima na amince ."</p><p> Nan suka sa daria duka,sun jima suna hira a wajen kafin suyi sallama. Shamsu ya nufi dakinsa na gidan ,baba ya yi bangarensa,mama ta ja farida suka yi nasu bangarwn. Ta sa mata ruwan zafi tayi wanka saboda tasan tana tattare da gajiya ,ta bata gashasshiyar kaza mai zafi tare da tea me zafi. Bata so haka ta sa ta ci sosai,sannan ta ce to maza ta haye gado ta shige bargo tayi bacci don ta samu hutu.</p><p> Bata musa mata ba saboda ita dai farida ko ummanta bata sakewa da ita kamar yadda take sakewa da mama tun tana kankanuwa.</p><p><br /></p><p> Washegari kuwa 'yan biki suka watse kowa ya kama gabansa,gida ya saura daga mama sai farida ,shamsu,lukman da masu aiki. A wannan lokacin mama ta samu damar yiwa farida gyara ba musammana wanda ta san mahaifiyarta bata samu damar mata wannan ba ,sboda wai kunya da kuma ba wani shakuwa tsakanin su. Dan haka mama ta daukarwa kanta nauyin farida da kula da ita.</p><p> </p><p> A hankalin ta dinga mata nasiha akan aure,da kuma tadda rayuwar aure take. Ra dinga fahimtar da ita abubuwa da yawa wanda bata sani ba ,ta wani bangaren tana shiga da ita kicin tana koya mata girke girke kala-kala saboda ita mama Allah ya bata baiwar iya girki. Ba anan tsaya ba,hatta kwalliya da iya dressing kamar ba dattijiwa ba ,,sai da ra koya mata tana nuna mata wani...... </p><p> </p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p>=================== GIDAN NOVELS ====================================</p><p><br /></p><p><br /></p><p>22</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Wani lokacin haka zata ta dinga mata fada da nasiha akan ta rungumi abinda Allah ya bata hannu bibbiyu ,idan ta nuna halayya na kin amincewa hakan ya nuna bata yarda da abinda Allah ya bata ba,don haka ta hore ta da tayi hakuri ,tayi juriya ta saka soyayyar shamsu a zuciyarta,saboda shine mijinta yanzu,don haka ba karamin zunubi bane ta mayar da tunanin wani namiji da sunan so balle har taji sha'awar sa. Ya zame mata dole ta danne son zuciyarta,ta fi karfin zuciyaeta ta rungumi abinda Allah ya bata hannu bibbiyu ,ta gode masa.</p><p> Nan ta girgiza kai tare da fadin , naji mama,nagode ,insha Allah zanyi duk yadda kika ce.."</p><p> Mama tace ,"Akwai wani aiki a gabanki ,nasan bakya son shaamsu,haka shima baya sonki,amma fa yanzu ya zame miki dole ki so shi,kuma dole ki ja hankalinsa ya so ki a matsayin ki na matarsa. Yana da kyau ki kama zuciyarsa,ki jefa soyayyar ki a zuciyar sa kafin ku kai ga fara zaman aure.</p><p> Sunkuyar da kai tayi kinyar mama ta kama ta ,hakan yasa mama ta mike tace. </p><p> To zan fita amma ga kaya nan ki ahirya kiyi kwalliya ki fito ,shamsu na falo yana jiranki ,na hada muku dinner zakuyi tare.</p><p> " To mama "</p><p> Ta amsa murya kasa-kasa .</p><p>Bayan fitar mama ta mike ta kalli kayan,,wani jan material ne mai kyau da tsadar gaske ,sai kamshi yake. Ta sa a jikinta,doguwae riga ce mai sharpe ,dinkin ya kamaa jikinta tamkar don ita akayi material din ,fatarta mai haske tayi matukar karbar kayan.</p><p>Nan ta tsaya tana kallon kanta a mudubi,ta tuno yadda take bata lokaci da tana kwalliya don ta burge Deeni,amma in ya zo sai dai ya yi ta mata daria da gwalo yana cewa bata yi kyau ba . Da kanshi yake tayata ta gyara yana koya mata yadda zata yj kwalliya,in yaga ya kalleta ya mata murmushi yacs,,</p><p> ". Kinyk kyau mrs Nuruddeen duk duniyar nan ba macen xa ta kai matata farida kyau a wurina_</p><p> Ta kanyi murmushi ta boye fuska ,amma yau da ikon Alkah tana kwalliya don ta burge wani ba deeni ba,wani namijin da bata taba noticing dinsa ba a matsayin namiji ,bata taba kula da shi ko ta bashi muhimmanci ba ,asali ma ita yaya shamsu tamkar bako ne a gareta ,shi ne yau ya zamo mijinta. Lallai Allah shi ya barwa kansa sanin abinda ya lullube .</p><p> Tana cikin wannan tunanin mama ta dawo ta ce.</p><p> "Har yanzu farida,ina ji dai sai na sa miki hannu . Farida sarkin tunani ,na ce miki ki rage tunani amma ba kya ji ko ?</p><p> Murmushi kawai tayi ta sunkuyar da kai. Ta ce ' kinyi kyau kuwa,kayan sun karbe ki. Bari in miki daurin tunda naga ke bakya son yi.."" </p><p> Nan kuwa ta ajiyeta ta mata daurin da ya kara fito da kyan fuskarta,ta taimaka mata wurin sa dan kunne da abin wuya da dai sauran kayan karau. Ta bata takalmin da ya dace da kayan ,sannan ta fesa mata turare mai kamshin da dadin gaske.</p><p> Ta ce ,yauwa ,yanzu 'yata ta fito a amarya sak,sai gun ango ko ?</p><p> Kanta sunkuye tayi saurin rufe fuska.</p><p> Mana tace to na rafi tunda kunyata akeji ,amma fa ina fita ki fita ,kinga tun dazu yana jiranki.."</p><p>" To mama " ta amsa murya a kasa.</p><p> Bayan ta fita itama ta bi bayanta ,tana tafiya cikin nutsuwa da hankali tamkar mai tsoron kasar ko taisayinta.</p><p> Tun kafin ta iso turarenta ya rigata isowa,hakan yasa ya dago kai a zatonsa ta iso falon. Hango ta yayi tana tahowa ,ta zuba kyau,tana wani taku tamkar wacce take filin gasar sarauniyar kyau. Yarintarta da cikarta ,budurcinta ya bayyana a zahiri,nan ya tsinci kansa da kallonta ya kasa kau da kai daga garera . Sai sheki take tana kamshi,bai ankara ba har ta iiso dab da shi. Nan yayi saurin kau da kai.</p><p> Ta ja kujerar dake kallon sa ta zauna itama ta kasa dago ido ta kalle shi,kanta a sunkuye ta ce . </p><p> Yaya shamsu ina wuni?</p><p> Muryarta me dadi da sanyi ta daki dodon kunnensa ,yaji ya taba zuciyarsa.</p><p> Ya amsa," lafia farida ,ya kike? Ya fada cikin kau da kai .</p><p> Ta amsa kai sunkuye ,"lafia "</p><p> Mama ta shigo tace ,To ko waye ake kawar wa da kai da sunkuyar da kai ban sani ba. Shamsu ,farida halal dinka ce fa,farida shamsu mijinki ne,kina da damar kallonsa ko mene abin sunkuyar da kai ban sanj ba . Ni zan wuce bangaren babanku,ki tashi ki zubawa mijinki abinci, kuma ina so ku saki jiki da juna kuyi hira," </p><p> To mama" suka amsa a tare.</p><p> Bayan fitar mama farida ta kasa daga kai,yayin da shamsu ya yi karfin halin dago kai yana kallonta kanta sunkuye tana wasa da yan yatsunta.</p><p> Nan y yi kokarin kawar da shirun ta hanyar cewa. </p><p> Tunda bazaki zuba min abincin ba bari ni in zuba miki,"</p><p> Nan ya bude kular abincin fried liver with potatos ne,ya zuba mata ta hade da juice ya mika mata . </p><p> Ta dan kau da kai ," Da ka barshi zan diba da kaina " </p><p> Ya yi murmushi yace,"Naki ba barshi".</p><p> Ya fada cikin muryar tsokana da kwaikqayonta ,hakan yasa t dago kai ta kalleshi. Gabanta ne yayi mummunan faduwa saboda yadda ya yi sai taga ya bala"in yi mata kama da Deeni,yadda yake murmushin sa da yadda yake zolayarta. Bata san yaushe ta saki murmushi ba ,murmushin da yasa shamsu yaji ya tsaaya masa a zuciya,ya tsinci kansa da kasa dage idanunsa daga gareta har sai da ya ga ta dago. </p><p> Ya yi saurin mikewa," Ni zan wuce naga dare yayi "</p><p> Cikin sanyin murya tace,ya shamsu kaci abincin mana,kar ka kwanta da yunwa"=</p><p> Ya tsinci kansa da kasa musa mata. </p><p> Sun ci abinci tare ,sai dai sunyi zaman kurame,dukkansu sun kasa sakeqa da juna yayin da suke kallon juna a sace,,har mama ta dawo ta same su a haka. Ita ta zauna a wurin ta kau da shirun tana kokarin jansu da hira tare da sa su yin magana da juna . Da Shamsu ya zo tafiya mama ta sa farida tayi masa rakiya har kofar dakinsa da ke gidan ,suka yiwa juna murmushi tare da fadin " sai da safe " ta juya.</p><p> Shamsu ya bita da kallo yana jinjina takunta da yaba halittar da bai taba mai da hankali ya lura ba,yayin da farida taji hankalinta ya tashi da ta hango kofar dakin Deeni wanda suka kallo juna da na shamsu . Ta sawa kofar dakin ido,hawaye suka zubo mata,soyayyar sa da kewar sa taji yana ratsa ta.</p><p> Shamsu ya tsinci kanshi da zuwa inda take,ya lura da yanayin da take ciki idonta lumshe hawaye na zuba ,bai san yaushe ya jawota jikinsa ba ya mannata da jikinsa gami da shafarta yana lallashi.</p><p> " kiyi hakuri farida ,nasan ba abu ne mai sauki ba ,sai dai tuna baya ba abinda zai baki sai bacin rai."</p><p> Nan ta fashe masa da kuka ,ya zanyi ya shamsu? Ya zanyi da soyayyar Deeni da ke cina yana azalzalar zuciyata? Ya shamsu ina son Deeni ,ina cikin tsananin kewar sa. Ina son kasan cewa da Deeni"</p><p> Nan ta dada kankame shi tana kuka,tun yana lallaahi har ya daina ,ahi kadai yansan me yakeji a jiki da zuciyarsa.</p><p> Tabbas abinda bai so ba abin da bai zata ko ya tsammani bane ya faru da shi,wato ya tsinci kansa da jin kishin dan uwansa,hakan yana nufin soyayyar farida ta shiga zuciyarsa kenn ? Ya ci amanar dan uwansa da tushe ,ya bari zuciyar sa ta kamu da son farida lokaci guda.</p><p> Addu'a ya dinga yi a zuciyarsa,tare da kokarin sharewa farida hawaye.ya ja hannunta ya kaita har kofar dakin mama tare da kara bata baki,har sai da ya ga ta saki ranta tayi murmushi tare da masa godiya.</p><p> Ta shige ciki ta samu mama suka dan yi hira kadan sannan tayi shirin bacci. Duk yawanci hirar tasu ta kare ne a nasiha da misalai da mama ke bata game da yanayin irin mata da t ahiga ne ..............</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>Gaskia yau nayi typing da yawa 😡😡se kuma ankwana biyu😜😜</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA"AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>24</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kwanci tashi ba wuya a gurin ubangiji,sai ga ciki ya bayyana jikin farida,iyaye da 'yan uwa kowa ya yi mirna musamman iyayensu maza da mta. Suna shan addua da albarka a kowanne kwanann duniya.</p><p> </p><p> Shamsu dai kamar zai cinye farida,da yanada iko da numfashi ma sai ya mata. Baya bari tayi komai , ya bata kulaqa ta musamman tare da kokarin ganin kullum tana xikin farin ciki . Kullum ana kan binciken lafiaeta data baby.</p><p><br /></p><p> Tun daga wannan lokacin mama ta kara tsinkewa da al'amarin auren farida da shamsu,ta kara tabbatarwa aurensu wani hukunci ne na ubangiji,rabon shamsu ne a jikin farida bana Deeni ba,wani baya haifar dan wani,haka wani baya auren matar wanj</p><p><br /></p><p> Nan ta kara dukufa da yiwa deeni addu'a. Allah ya bashi ikon hakuri da juriya,ya kuma kawo masa nasa rabon ta wani wurin.</p><p><br /></p><p> Farida ta haifo danta santalele namiji mai matukar kama da shamsu,tamkar an tsaga kara. Nan zuciya ta cika da murna ,iyayensu sunyi matukar murnar samun zuri'a da akayi tsakaninsu . Wannan ya kara karfin zumuncin su da kara tabbatarwa sun zama daya.</p><p><br /></p><p> Farida da baby sun sha kaya da gata kala-kala. Sun zama abin so a dangi,kowa son su yake da sha'awar su.</p><p><br /></p><p> Shamsu ya fadawa iyayensa cewa ya yiwa yaro huduba da sunan kaninsa deeni,wato NURADDEEN . Sun yi murna kwarai,musammaman mahaifin deeni da mama.</p><p> Tabbas deeni ya cancanci haka daga gare su,saboda dukkan su masoyan Deeni ne,daga shamsu har farida,haka nan shi masoyin su ne.</p><p><br /></p><p> Alh Umar ne ya bugawa deeni waya ya yi masa albishir da zuwan baby da kuma takwara da aka masa ,wato mai suna da shamsu ya masa.</p><p> Kwarai Deeni ya ji dadi yayi murna soaai har ya cewa babansa zai zo in sunyi hutu,sai dai mahaifin nasa ya taka masa birki,ya nuna masa zuwa gida zai mai da masa hannun agogo baya ,ya daure dai ya karasa,sauran sa shekara biyu ya gama ,in yaso zuwa ya sayo wa mai sunan sa duk irin abinda yakeso.</p><p>Ba don yaso ba haka ya hakura ,ta wani bangaren yana ganin gaskiyar mahaifinsa ne. Tabbas inya dawo gida yaga farida sake tafiya ya barta zai yi wuya,don haka hakurin dai shi yafi masa.</p><p> Haka rayuwa ta cigaba da tafiya musu,shamsu da farida da dansu Deeni karami,suna rayuwa tare da rainon dansu cikin so da kukawa da juna ,tare da kulawa da juna ,tare da mahaifansu,yayin da deeni ya dage ya ci gaba da karatun sa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>* * * * * * * * * *</p><p><br /></p><p>Tunda ya sauka kasar sa nigeria yake cike da farin ciki da wani irin dokin zuwa ya ga yan uwansa,lumshe ido yayi yana shakar iskar kasar sa mai albarka,kasar mama da baba,kasar masoyiyar sa farida.</p><p> Sanye yake da red t.shirt hade da blue jeans ,idanunsa boye cikin fararen glass ,ya yi wani irin haske da kyau ,saboda samun hutu da canjin yanayi da ya samu.fuskar sa kunshe da murmushi,kana ganinsa kaga wanda yake cike da farin ciki.</p><p> </p><p> Hayar taxi yayi a nan cikin airport din,ya sa kayansa a boot sai gida.</p><p> A cikin taxi din Deeni yana ta sake sake tare da tunanin shin wa zai fara zuwa ya gani?masoyiyarsa farida ko kuma iyayensa ko yaya shamsu da matar sa? Yaba son basu surprise ne shi yasa ko baba bai fadiwa yana zuwa ba ,yafi so sai dai su ganshi kawai,mahaifinsa ya zata sai wani watan zai gama ya dawo.</p><p> Ya yi murmushi,"Farida zata ganni bazata,zanga ni da ita wa zai fi farin ciki da ganin dan uwansa?</p><p> Yana wannan sake saken har suka iso cikin unguwarsu,a nan ya tsaya yana tunanin ina zai fara shiga gidnsu ko na su farida ,ko kuma gidan ya shamsu..............??</p><p><br /></p><p>To masu karatu ku bawa deeni shawarar inda zai fara shiga........</p><p> Sai munji shawararku wadda zan bawa deeni😜😜😜😜😜</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>23 </p><p><br /></p><p>A wannan sati biyu mama tayi dukkan iyawarta da dagewarta akan Shamsu da farida,taga sun saki jiki da juna ,da kokarin nuna musu su rungumi kaddara suyi ibadar aure,su manta komai. In sunyi haka tabbas basu yiwa Allah butulci ba ,kumansun yarda da kaddara kamar yadda ake so kowane musulmi na kwarai ya yi. In sun haka kuwa Allah zai sa albarka a rayuwar su,ya daga darajar su a duniya da lahira. </p><p> Da irin wannan maganganun na mama yasa suka saki zuciyar su,musamman ma dai farida ta riga ta saduda,ta daura damarar manta baya,ta kuma cusa soyayyar mijinta da Allah ya kaddara mata a zuciyar sa.</p><p> A satin biyin ta koyi abubuwa da yawa ,don haka tayiwa mama godiya sosai,dami da mata alkawarin zama mace ta gari,saliha ga Shamsu,zata yi kokarin kawo farin ciki da kwanciyar hankali tare da nutsuwa a rayuwar Shamsu ,ta riga da ta amince,ta karbe shi matsayin mijinta. </p><p> Wannan magaba tayiwa mama dadi matuka da zancen farida ,tayi ta saka mata albarka.</p><p> </p><p>Shamsu shima bai yi kasa agwiwa ba ya kara jaddadawa mama rikon da zai yiwa farida bisa gaskiya da amana da kuma soyayya.</p><p> Mama tayi ta sa musu albarka ,ta raka su har mota tare da hadawa farida guzuri iri-iri.</p><p><br /></p><p> Farida taji kewar mama sosai ,saboda shakuwa da sukayi a yan wadannan kwanakin da sukayi tare.</p><p> Kauna da soyayya tare da kulawa da shamsu ya dinga nunawa farida. Ya tabbatar mata da soyyayr ta na tare dashi ,don haka itama ta saki jikinta da shi,ta mika wuya gareshi. Da kanta ta kai kanta garw shi har dakinsa,mutuncin mama kadai da girmanta da take gani ya isa ya hnata cutar da shamsu.</p><p> Ta lura yana sonta da bukatarta ,amma ya kau da kai,bai taba nuna mata hakan ba ,don haka da kanta ta yanke shawarar mika kanta da rayuwarta gaba daya ga mijinta. Bazata iya raba kanta da son Deeni ba ,amma zata iya raba kanta da tunaninsa ta cusa na mijinta a zuciyarta.</p><p> Wanka tayi fes ta feshe jikinta da kamshi ,tare da saka sexy dress ,ita kanta ta yaba kanta,ta zurawa kanta ido a mudubi .</p><p> " Yau ce ranar da zan ci gaba da rayuwata,ranar da zan mallakawa wani kaina,zuciyata da gangar jikina,wani ba deeni ba. </p><p> Ina fata zaka yafe mun ,ka manta dani a rayuwarka Deeni,na yankewa kaina hukuncin rungumar aurena da mijina hannu bibbiyu don nemar yardar Allah.</p><p> Da wannan tunanin ta nufi dakinsa,tayi sallama ,yana zaune bisa gado sanye da kayan bacci,hannunsa rike da ipad yana danne dannen sa alamar wani aiki na office yake yi.</p><p> Sallamarta yasa shi daga kai yare da amsawa,ganinta a yanayin da bai zata ba yasa shi kasa karasa sallamar. Ya yi saurin kau da kai zuciyar sa na bugawa,tuni ya ji ya rude musamman da ya jita dab da shi.</p><p>Hannu tasa ta karbi ipad din ta ajiye a gefe ,ta dare bisa cinyarsa tare da jawo shi jikinta ta rungume shi . Nan ya bata hadin kai ,shima ya kara mannata a jikinshi sosai yana shakar kamshi tare sauke wani irin ajiyar zuciya yana jin tsananin son ta da sha'awarta suna shigar sa.</p><p> Cikin muryar rada idon sa a rufe yana manne a jikinta yace...</p><p> Farida kin amince dani,ba kya tunanin dee.....</p><p> "" shhhhhh" </p><p>Ta fadi gami da saurin rufe masa baki tace ,,</p><p> Karkace komai,na mika rayuwata da kaina ga mijina wanda shamsu shine mijina,gaskiyar rayuwata. Ni matarka ce,kanada hakki da damar yin duk abinda kake son yi dani,buri na a yanzun kawai in kyautata maka . Ina neman yardarka ,saboda Allah ya yarda dani.</p><p> Nan ya dunga sauke ajiyar zuciya ,shi kadai yasan me yakeji a zuciyar sa da jikinsa.</p><p> Bai bata lokaci ba ya dada cusuwa a jikinta ,tuni suka manta komai suka fada wata duniya. Farida ta mallakawa mijinta shamsu kanta ,, yayin da shimanya mallaka kansa da komai nasa ,yana mai sa.mata albarka gami da alfahari da ita .</p><p> Tuni suka rungumi auren su suka rike hannu bibbiyu,suna kula da juna tare da tarairayar juna,suka bude sabon shafi na rayuwar su,iyaye na sa musu albarka.</p><p>Ba wanda ya kai mama farin ciki da kuma fargaba ,a kullum Deeni ya yi waya sai shamsu da farida sun tsinci kansu cikin sabon tashin hankali . Sai dai a kwana a tashi har sun saba da hakan ,don kuwa mahaifin deeni ya hana ko da wasa a fada masa gaskia ..</p><p> Lokacin da karatu yayi wa deeni yawa ma yana dadewa bai yi wayar ba.mahaifinsa yana yawan ziyarar sa,yana ganin yadda ya cigaba sosai a karatunsa,ya yi nisa kuma tana kokari sosai ,ya kwantr da hankalinsa,,saboda ko da wasa bai san me ke faruwa ba. Kullum da burin auren farida yake kwana yake tashi........</p><p> Bye </p><p><br /></p><p>Mu kwan lahia jama'a</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv 😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>25</p><p><br /></p><p> Can dai deeni ya yanke hukuncin zuwa gidan dan uwansa ,ya cewa direba ya juya. Dama ya riga yasan gidan da mahaifinsu ya bawa shamsu,don haka ya yanke hukuncin wucewa gidan shamsu ya ga mai sunansa Deeni da dan uwansa,ya yi masa murnar aure,ya ga kalar matar da yayansa ya aura...😭</p><p><br /></p><p> Yana daria ya fito hannunsa dauke da akwati wanda cike yake da kayan sawa da kayan wasa na mai sunansa Deeni karami. Nan ya cewa mai taxi din ya jirashi zai shiga ciki ya amso masa kudinsa. Nan ya yi ciki ya bar sauran kayansa a motar.</p><p> Tura gate din gidan ya yi yana jan akwatin da ke hannunsa,yana ratsa tsakiyar gidan,yana kallin ginin da cikin gidan yana murmushi. A ransa yana fadin,kwannan shima zai mallaki nasa gidan tare da farida.</p><p> "Anya kuwa in na auri farida ina da wani sauran buri kuwa a rayuwa?</p><p> Yana cikin wannan tunanun yaci karo da security na gidan wanda dama ya shiga ciki kai wani sako ne ,ganin Deeni yasa shi washe baki yana dariya saboda dama tsohon mai gadinsu ne Alh ya bawa shamsu shi yana masu gadi.</p><p> Nan ya karbi akwatin tare d a bude masa kofar falo,anan ya ci karo da Deeni karami a tsakiyar falon ,an baza masa toys yana wasa .</p><p> Da sauri ya isa gare shi yana dariya,yasa hannu ya daga shi, Deeni kuwa kamar ya sanshi ya wangale baki yana dariya.</p><p> Deeni yana zura masa ido yana kallon irin kamar da yake yi da shamsu,son yaron da kaunar sa yaji ya shiga zuciyar sa,nan ya dinga masa wasa yana cilla sama shi kuma yana daria.</p><p> Nana ya bude akwatin ya ciro masa sabbin toys din da ya siyo masabya bashi,anan wurin deeni ya zauna yana ta wasa da Deeni. Shi dai megadi ya tafi ya barsu don Deeni ya hana ya musu magana ,ya ce suprise zai basu.</p><p><br /></p><p> Tsawon minti goma yana da Deeni har ya soma mamakin me yasa yaji tsit ba wanda ya fito duba Deeni karami shi daya? </p><p>Nan ya daga shi ya nufi falon ciki yana fadin...</p><p> " zanci tarar iyayenka ,sun barka kai kadai na tsawon lokaci ba wanda ya leko ka,kar ka damu ga uncle Deeni ta dawo ,zai dauke ka ya tafi da kai su kuma suyi ta zaman su a ciki...."""</p><p> Deenibdai sai dariya yake masa tare da fadin mommy ko daddy.</p><p> Ya ce "uncle zaka ce,uncle Deeni "</p><p> Nana ya yi kokarin kwaikwayon sa ya fada cikin maganar yara 'yan koyo. Shekararsa biyu amma ba baki sosai,sai girma da yayi kamar dan shekara uku.yaro ne lafiyayye mai ki da karfi. Da alama ya samj kyakkyawan raino da kula daga iyayensa.</p><p> " Salamu Alaikum ,mutanen gidan suna nan kuwa ko sai na tafi muku da yaro za ku fito?</p><p> Deeni ya fada yana kokarin kutsawa cikin daya falon tare da daga labule.</p><p> Wani abu idonsa ya gane masa me kama da mafarki ko almara,,wani abu da kwakwalwa ko hankalinsa ba zai iya dauka ba.</p><p> Farida ya hango kwance jikin shamsu ,shi kuma ya rungumota yana ta kokarin massaging kanta,yana matsa mata kai alamar yana mata ciwo ,tana ta zuba shagwaba.</p><p> " Daddy kaina zai tsage,daddyyn deeni inajin murda;;""</p><p> Yi hakuri mommyn Deeni,zai bari,kwanta ina ci gaba da matsa miki tunda kin sha magani zaki samu bacci yanzu,kiyi shiru kar ciwon kan ya karu"</p><p> " Daddy deeni fa ? Ta fada cikin shagwaba da kuma ciwo .</p><p> Yana can yana wasa ,ki samu bacci zan fita da shi in kaishi gun mama tunda ka kya jin dadi. Wannan babyn namu dai da yazo yanzu yana wahalar min da farida na,sai mun masa bulala in yazo.</p><p> Tayi murmshi ta ce , Ya shamsu macw zamu haifa mai sunan mama,kaga kuwa ba a yiwa mama bulala ba,in kuwa ka mata sai hannunka ya nade" </p><p> Dariya sukayi duka,sam basu kula da Deeni da ke tsaye a kansu ba,wabda tsananin firgita da kaduqa da abinda ya gani sai da ya saki deeni ya sha kasa ,bai ma san yayi hakan na. Gaba daya hankalin sa ya bar jikin sa,baya hayyacin sa.</p><p> Ihun deeni ya jawo hankalinsu ,shamsu ya mike a firgice gabansa ya mummunan faduwa,yayin da farida ta ji wani irin hajijiya ,sabon zazzabi ya lullubeta ,tsananin firgita da ganin Deeni bata san lokacin da taji mararta ta juya ba ,wani azabar ciwo taji ya kamata,tuni jini ya soma bin kafarta yna gudu ,alama ne na cewa cikin jikinta wanda bai wuce wata biyu ba ya bare saboda tsabar tsorota da tashin hankali data shiga. Haka nan shamsu duk kokarinsa ya kasa ko da motsi a wurin ,kansa sunkuye ya kasa hada ido da Deeni,ya kasa ko da motsawa balle yaje ya daga deeni dake ta kwala ihu a wurin </p><p> Farida dai dakyar ta samu ta zauna bisa kujerar da suke da sabida hajijiya da wani abu da taji yana yawo a tsakiyar kanta ,ki ciwon marar ma bata lura da shi ba sai dai tabbas tasan abu na bin kafarta wanda bat san menene ba.</p><p> Tsawon minti biyar suna cikin wannan halin,duk wani farin ciku da murnar da jin dadin da ya dawo da shi nigeria sai da ya neme shi ya rasa,kunci ,bakin ciki ,takaici, da bacin rai ya maye gurbin su.</p><p> Halin da ya gansu ya ganar da shi dukkan abinda yake faruw ,ya fahimci cin amana da. yaudarar da farida da shamsu suka masa.wani abu da bai taba zata ba balle tsammanj ,ko a mafarki ko. A tunaninsa bai taba giftawa ba.</p><p> Wani abu yaji ya tokare shi a zuciyarsa,haka ya dinga jin wani azabar radadi a kansa,wani irin azabar ciwo da bai taba jin makamancin sa ba . Amma duk da halin da yake ciki sai ya sa hannu ya dauki Deeni ya nufi gabansu ya mika musu shi,sai dai dukkansu ba wanda ya iua motsawa balle ya sa hannu ya karbe shi. Hakan yasa ya ajjye shi. Akan cinyar farida ya juya ya fita.</p><p> Yana shirin barin falon ya ci karo da su umma tare da baba ,da kuma Abba da umma ,wato mahaifiyar farida.</p><p> Ashe Alh Umar ya yi waya can America aka ce masa ai tun tuni Deeni ya taho nigeria,tun daga nan hankalin sa ya tashi ya aina tsawon lokacin da aka ce masa ya taho yasan tabbas ya iso,haaka nan tunda bai je gida ba ko gidansu farida ,to tabbas yasan gidan shamsu zai nufa. Ranar da suke gudun zuwanta ne dai ta zo.</p><p> Tunda mama ta sami labari hankalinta yai mummunan tashi,Alh ya tattaro su duka don su yiwa Deeni bayani,su fahimtar da shi ,wanda a zatonsu zai fahimta,(hmmmm atunaninsu akwai wani bayani da deeni zai fahimta ne🤔),to amma mama tasan dama za'a rina.....</p><p> Mama na ganinsa da yanayin da ya shiga hankalinta ya kara tashi,ta jawo shi ta rike gam tana fadin .</p><p>Deeni addu'a zaka yi kaji,ka dinga maimaita hasbunallahu wa niimal wakil,ko la'ilaha illah anta subhanaka inn kunti minazzalimin""</p><p> Gaba daya kansu suka yi kowa da irin abinda yake fada masa ,da irin bayanin da suke masa . Sai dai deeni ya dawo kamar zararre,tamkar mara hankali,kallon su kawai yake bakinsa na motsi amma baya ma jin me suke fadi balle ya gane.</p><p> Ya kalli mahaifiyarsa yace,,Mama kinada kudi ki bani in biya me mota lr da ya kawo ni ?</p><p> Deeni na biya shi,har mun sa ya sauke maka kaya ya sa a motar mu,zo mutafi gida""</p><p> Deeni ya kalleta,"Mama farida ,jini na zuba a jikinta ku kaita asibiti"</p><p> Sai a lokacin suka mai da hankalin su kanta,umma ce da mama sukayi kanta,suka dagota hankalinsu a tashe suna salati,sukai mota da ita. Tare da Abba suka tafi,yayin da baba ya tsaya tare da shamsu da deeni,ya jawo su duka.</p><p> Bayani ya fara da nasiha ,da kuma fadin ba laifin shamsu da farida bane ,su suka yi hadin nn saboda wani dalili nasu,su kuma suka musu biyayya.</p><p> Bana son ji Baba ,duk wani abu da zaka fadamin ko wani dalili bana son ji,ka rike dalilinka,duk abinda zaka fada ba zai cire min ciwon da nakeji yanzu a zuciyata ba. Kasan me nakeji Baba ? Da kasani da baka tsaya yi mun wani magana ba ...</p><p> Baba ka sama mun magani ,ciwon da nakeji a kwalkwata da zuciyata yanzu za su iya kashe ni,Baba yanzu ina jurewa amma anjima ba zan iya jurewa ba. Baba zai kashe ni ka kaini asibiti ko ka min addu"a ,kamin duk abinda zaka iya mun ko zan samu saukin ciwon da nakeji ..... </p><p> Kai Babana nw ,ME SONA ,me yanke dukkan wani hukunci na rayuwa saboda ka kawo ni duniya ,ka bani ci da sha, ka kula da lafiyata da karatuna ,ya zamar min dole in maka biyayya.</p><p> Nayi biyayya baba da abinda kayi ,sai dai baba ka taimake ni wannan abinda nakeji baba ban taba jn irinsa ba,baba bana ganinka sosai ,duhu na rufe mun ido,ina jin duniyar na zagawa dani ....</p><p> Kama kansa yayi da karfi,basu ankara ba sai ganinsa sukayi ya fadi ,ya zube kasa a sumeeee.............</p><p> </p><p> 😭😭😭😭😭😭😭😭</p><p><br /></p><p>Allah ya bamu alkairi jama'a ,,dan wlh nima hannu na rawa yake kar ayo biyu,,ga deeni a sumee nima wayata karta fadi......</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽</p><p><br /></p><p><br /></p><p>writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p>ASSALAMU ALAIKUM </p><p><br /></p><p>Yan uwa!! Mata ce ta cewa mijinta ya saketa,shi kuma yaki ,hakan yasa ta dakko wuya wai idan be saketa ba zata kashe kanta.</p><p> Shi kuma ganin haka yasashi sakinta. SHIN YAYA HUKUNCIN WANNAN SAKIN DA YAMATA ? TA SAKU KO BATA SAKU BA 🤔🤔?</p><p> Sai naji daga gareku....nagode</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>27</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wasa gaske al'amarin Deeni ya tsananta,wani lokaci ka ganshi lafiya wani lokaci ya haukace musu,gana daya baya hayyacinsa,bai san me yake yi ba,hankalin iyayensa da masoyansa ya kai kokuluwar tashi. Daga karshe Alh ya fita dashi kasar india ,anan aka ci gaba da duba lafiyar kwakwalwar sa,saboda abin yamatukar raba masa kwakwalwa,kwakwalwarsa ta kasa dauka da jurewa wannan damuwar.</p><p><br /></p><p> Ana duba lafiarsa a asibiti kuma ana masa rokon Allah,tare da sauke masa Alkur'ank ,da haka da taimakon ubangiji Deeni ua soma dawowa hayyacin sa. Sai ya zamana ya daina surutu tunda suka dawo gida,ba ya kula kowa ,baya cewa kowa komai. Kullum yana zaune a dakinsa,baya fita sai dai wani ya tafi masallaci ya dawo. In an kai masa abinci wani lokaci zai ci ,wani lokaci kuma haka abincin zai kwana wani ya tarar da wani.</p><p> </p><p> Lokaci guda rayuwar Deeni ta canja ,ya yi baki,ya rame ,kuma baya aikin komai sai kwanciya da zaman gida. Ya dawo rayuwar sa sam bata da wani manufa.</p><p><br /></p><p> A duk lokacin da Deeni zai kwanta bacci,to yakan rufo ido ya hango shi da farida,lokacin da hoton farida da shamsu zai bayyana a fuskar sa yakan yi saurin bude ido wanda a nan za su rine suyi ja,yaji kansa ya fara sarawa ,ya kama kai da kirji . Wani lokaci sai dai a shigo a same shi a sume. </p><p><br /></p><p> Halin da Deeni ya shiga ya daga hankalin kowa a zuri'ar su,musamman iyayensa da kuma shamsu da farida. Wani lokacin mahaifin sa sai ya zubar da hawaye saboda bakin cikin halin da dansa ya shiga. Rayuwarsa ta dawo useless bata sa wani amfani ,ya yi da na sani tare da jin bakin cikin abinda ya yi.</p><p> Kulum yana binciken asibiti ko masu maganin gida da za su dawo da shi dai dai,sai dai abu guda yake ji kullum,shi ne abin ya mugun taba masa kwakwalwa da zucya,wanda fitar sa a wannan hali sai a hankali . Sai dai dayawa masu magani ko likitoci na bashi shawarar cewa ya canja masu wuri,wato ko dai ba ya bar garin ko kasar ,ko dai wani wurin da zai nesanta deeni da rayuwar da yayi ta baya.</p><p><br /></p><p> Wannan yasa Alh Umar ya tattara nasa ya nasa da kasuwancinsa ya raba su biyu ya koma lagos ,ya yin da ya barwa Shamsu sauran kasuwancin sa a kaduna .</p><p><br /></p><p>Alh Umar ya tattara iyalinsa,wato hajia A'i da Deenj da lukman suka koma garin lagos ,ya bar Arewa gaba daya. Saboda ya san Deeni yana da sha'awar zama a garin ,sannan yana ga zai ji dadin tafiyar da kasuwancin sa. Haka Deeni zai samu kyakkyawan canjin yanayi ,yayin da ya bar Shamsu da Farida a kaduna. </p><p> </p><p> Tabbas Alh.Ahmad ya yi bakin cikin rabuwa da abokinsa,makwabcinsa,wanda yake kamar dan uwansa Alh. Umar . Ya daukar masa manar dansa da kuma hakkin kula da shi da kasuwancin da ya bar masa,da ya dinga kokarin sa ido inda yaga ya karkace ya yi masa gyara.</p><p> Farida da mama sun rabu cikin kuma tare da bakin cikin rabuwa da juna.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*** *** *** **** **</p><p><br /></p><p> ""ALHAJI ! ALHAJI !!</p><p>Haj. A'i ta shigo falonsa tana kwada masa kira .</p><p> Ya kalleta a firgice ," lafiya cikin daren nan ?</p><p>Ta mika masa wani farin takarda ,ya kalleta cike da mamaki.</p><p> "Menene wannan ?</p><p> Tace ,Address ne na samu,inda zamu kai Deeni,yanzu na kasa bacci na kunna tv kenan naga suna tallen wurin nan. Na lura masu matsala irinta Deeni sun samu waraka..""</p><p> Ya kalleta ransa bace ,ya ce,"Dana ba mahauci bane ,kuma ba dan shaye shaye bane da za a kaishi REHABILITATION CENTER </p><p> Cikin nuna damuwa Haji. A'i tace. Alhaji ka duba ka bincika ,wannan wurin ba mahaukata ko 'yan shaye-shaye bane,kafin in baka sai da nayi bincike naji komai akan su. Abinda yafi jan hankalina gare su ahi ne,sun hada da Addini da kuma magungunan musulunci . Deeni yana bukatar taimako na Addini da na asibiti duka,wanda duk sun hada.</p><p> Dakyar ta samu ta shawo kansa ya yarda zai binciko,in ya masa yadda hankalin sa zai dauka to zai yi tunanin tura Deeni wurin.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Gaya nan ayi breakfast😜😜😜</p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>=================== GIDAN NOVELS ====================================</p><p><br /></p><p><br /></p><p>26</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Alh Umar ya mugun rudewa ,rabon sa da ya zubar da hawaye har ya manta,amma a wannan lokacin sai da ya zubar da hawaye,hankalin sa ya mugun tashi.ya tsorata da lamarin Deeni,haka shamsu duk jikinsa ya mutu,ya rasa me ke masa dadi,ga halin da Deeni ke ciki ,ga na farida.</p><p> Tare suka nufi asibiti dashi,in da faridan take nan suka je,sai dai ita an dace an shawo kan alamarin ,sai dai tayi barin cikin har an mata wankin ciki tare da bata magunguna da allurai.</p><p> Tana kwance tana hawaye ,mama rungume da ita tana bata baki da nuna mata ta ci gaba da dauriya da cijewa kamar yadda tayi a baya,,zai wuce.</p><p> Umma rike da Deeni karami tana kallonsu,ta kasa fadin komai sai tsabar tausayin 'yarta da ya kamata,ta ahiga halin tsaka mai wuya.</p><p> Nan ta matsa itama tayi mata nata nasihar ,sannan ta ce zata wuce gida da Deeni,sannan zata shirya musu abinda za su ci ta aiko asibitin. Mama kuwa tacw zata zauna da ita.</p><p><br /></p><p> A nan ta samu damar kwaniciya a cinyar mama tayi kukanta sosai,mama bata hanata ba sai dai bata fasa lallashi da bata baki ba.</p><p> Suna cikin wanann halun shamsu ya iso yana rude ,mama ta kalle shi tace,,,,</p><p> Ka dauki abin nan a hankali,komai ta yi zafi magninsa Allah."</p><p> "Mama Deeni yana kwance a emergency tun dazu muna can likitoci a kansa sai yanzu muka samu ya farfado,"</p><p> Hawaye ne ya gangaro masa,ya ce,"Mama Deeni yana cikin wani hali wanda mu ne dalili." </p><p> Da sauri mama ta mike ba tare da ta karasa jin me yake fadi ba ta fita wurinsa,Shamsu ya matsa gaban farid yana fadin . "Ban baki kulawa ba lokacin da kike bukata,saboda Deeni yana bukatar kulawata fiye sa ke. Farida ban kaea sanin cewa bamu kyautawa Deenj ba sai yau da naga halin da yake ciki ,halin da ya shiga yana cikin tsanani da firgita tare da zafin zuciya da kwakwalwa""</p><p> Ta fashe da kuka ,"Ya shamsu ba abinda zai samu Deeni ko? Ya shamsu munci amana.."</p><p> Ta fada a lokaxin da ta kara fashewa da kuka .</p><p> 'Ya Shamsu ba zan iya fuskantar Deenj ba har abada,fatana Allah ya bashi lafia,yasa kuma ya manta sa ni da wannan cin amana da muka masa."</p><p> " Ba mao sauki banw farida ,tabbas bamu kyauta masa ba ,har ga Allah bamu kyautawa Deeni ba "</p><p> Nan suka lallashi juna ,daga karshe Shamsu ya kama ta suka nufi gurin Deeni a emergency.</p><p> Tana hango shj ko daga nesa ne,hango shi tayi yana kwance idonsa biyu sai dai ya kau da kai hawaye kawai ke zuba masa,ransa a mugun bace,hankalinsa a tashe.</p><p> Tausayinsa da tsohuwar soyayyar sa taji sun taso mata suna tsuma zuciyarta,tayi saurin dafe kirji tana hawaye,ta lura ya kara girma da haske hade da wani irin kyau duk da yana cikin tashin hankali.</p><p> Ta lumshw ido tana jin wani abu mai ciwo da radadi yna ratsata.</p><p> "Ka yafe min Deeni na ci amanar kauna ,sam ko kadan ban yi fighting wa soyayyar mu ba,nayi saurin mika wuya . Na cika makiyarka da nayi sanadin jefa ka a cikin wannan halin,nasa ka dandani wannan zafin zuciyar. Allah ya baka wacce ta fini,ni kam ban dace da kai da rayuwar ka ba da soyayyarka,tunda can ma kila shiyasa Allah ya rabaka danj. Na tabbatar Allah zai baka wacce tafi dacewa da kai,sai dai ka sani Deeni ba zan daina sonka ba ,hae abada soyayyar ka zata kasance a cikin karkashin zuciyata. Sai dai zan danne ta in ci gaba da rayuwa ta da mijina gami da faranta masa iyakar iyawa ta..""</p><p><br /></p><p> Muryar mama ce ta katse mata maganar zucin da take yi,ta mai da hankalinta kansu.</p><p> Mama ke masa magana cikin kwantar da murya,tana shafar kansa kamar karamin yaro tace,,"" Deeni kayi hakuri ,bani da abinda zan iya baka sai hakuri ,ba wani bayani ko kokarin kare kanmu da zan maka. Magana guda ce ,mun maka laifi duk da muna manya kai kana karami ,amma min maka laifi,mun zalunce ka,kayi hakuri ka yake mana,kar kayi fushi damu."</p><p> Deeni yayi murmishin kardin hali yace,"Fushi "" ? Da wa zanyi fushi ? Kima ni waye da zan yafe muku ? Ku iyayen mu ne,kuna da damar yin yadda ku ka so. Da mahaifin farida zanyi fushi don ya zabawa 'yarsa miji ? Ai bani da hujja.</p><p> Da farida zanyi fushi ,masoyiyata ,wacce ta min alkawarin soyayyarta da kanta ,wacce tun muna yan kanana muke wa juna son da bamu san irinsa ba ? Ko da yayana da na bawa amanar masoyiyata ,wanda yasan duk wani sirri da tarihin son da nake wa farida ? Ko da nahaifina da ya yaudare ni ya min karya? Ko da mutumin da na dauke shi tamkar mahaifina yace min ya mun alkawarin bani yarsa har inje in dawo ? Ko da mamana mahaifiyata da ta boye min gaskiyar magana? </p><p> Mama da wa zanyi fushi a cikinku ? Kuma meye riba ta in nayi fushi da ku ? Abinda ya faru zai canja ne ? </p><p> Ya mike cikin zabura da zafin zuciya ,ya ce.</p><p> "Damuwata shine yadda zan share wannan mummunan al'amarin daga kwakwalwata da zuciyata ..""</p><p> Ya kalli likita dake tsaye a kansa tare da mahaifansa ,ya ce</p><p> " Doctor ,kaga nima doctor ne ,likita ne cikakke,sai dai ban kware ba,ni ba professional bane,hala likiminka ya kai inda za'a iya yiwa mutum wankin kwakwalwa?ka bude mun kwakwalwata da zuciyata ka wanke mun su tas ,ina son manta dukkan mutanen nan a rayuwata,bana son tuna su balle in tuna abinda ya faru. Kaga wannan painful memories din abinda ya faru dani ,ina so ka bude ka wanke mun su duka saboda ba zan iya rayuwa da su ba,suna min ciwo sosai ,baza su barni in rayu ba ,ni kuma inaso in rayu. Please Doctor ka taimake ni..""</p><p> Tun yanayi a hankali har ya fara da tsawa,lokaci guda ya haukace musu,da kyar ak samu aka masa allurar bacci ya kwashe shi.</p><p> Ba mama ba har baba ya shiga cikin mummunan tashin hankali da Abba ,har suka yi nadamar abinda suka aikata masa.</p><p> Mama tana kuka tana tofa masa addu'a haka daga farida har shamsu kuka suke bamai lallashin wani..............</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hmmmmmmmmmm😭😭</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting buSAADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>28 </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ruwan sama ake tsugawa sosai ruwa irin na lagos,wanda idan ya fara sai anga tsawarsa. Iska ce me hade da feshin ruwa ya shigo ta windo ya wanke mata fuska,hakan yasa tayi saurin bude ido hade da addu'a. </p><p> Ta mike ta nufi jikin window din ta lumshe ido tana shakar daddadar iskar da ke dukan fuskarta tana jin yana ratsa ta ,yanayin da tfi so fiye da kowanne yanayi kenn.tuni taji zuciyarta tayi mata fari,ta tsinci kanta cikin wani nishadi.</p><p><br /></p><p> Karar door bell ne da aka danna ya ja hankalinta zuwa kofa,Doctor Bahijja kenan tayi saurin zarar hijabinta ta nufi kofar falon , a nan mai gadi ke fada mata suna da baki da ke son ganinsu,sunje cikin asibiti aka ce basu iso ba ,shi ne suka biyo su gida,sun ce wai yana da matukar muhimmanci suga likita.</p><p> Tayi mirmuahin da tasaba wanda kullm yana makale a fuskarta ,ta ce</p><p> " Kaisu falon baki,kace su jira ko ?</p><p> To madam</p><p>Ya amsa tare da juyawa ,duka cikin harshen turanci suke maganar..</p><p> Nan ta juya ta nufi dakin barcinsu,kai tsaye ta same shi har yanzu bacci yake duk da iska mai sanyi da ke ratsa dakin ,yana ratsa fuskar shi bai sa shi farkawa ba .</p><p> A hankali ta sa hannu tana jan bargon da yake lullube tana murmushi ,amma sai ta ga ya dunkule guri guda ya ci gaba da baccin sa tamkar wani baby.</p><p> Ta kalli kyaykkyawar fuskar sa me kunshe da annuri da lafiya ,tare da kwanciyar hankali . Soyayyar sa taji ya kara tasiri a zuciyarta ,cikin muryar shagwaba tace.</p><p> ""Please my dear" ka tashi mna,kana da baki "</p><p> Bai saurareta ba sai kokarin jawota jikinsa da yayi yana narke mata a jiki,ya cigaba da kwanciyarsa a jikin ta,yana jin sonta na karawa baccin nasa dadi.</p><p> Girgiza kai tayi tana murmushita kwace jikinta tare da sa hannu tana jan hancinsa,tana wasa da shi .</p><p> My dear please ka tashi ka duba time fa karfe sha daya na safe ,baccin ya isa haka. Ba don ruwan sama ba da fa ka fita tun karfe takwas."</p><p> Cikin muryar bacci ya ce,"shiyasa nake son damuna ,yana bani hutu ,ina samun nutsuwa da Bahijja na,amma ina!! Wannan likitar ba zata bar wannan likitan ya huta ba.</p><p> In barka ka huta daga baya kace me yasa ban tashe ka ba ? Ka fa tuna me kace mun "</p><p> ," Komai bacci me dadi da nake ki tashe ni ko da kamshin jikinki" </p><p> Rungumota ya sake yi ya cigaba da kwanciyar shi"</p><p> Bata kulashi ba ta mike ta nufi gadon Muhammad da taji alamar ya tashi yana ta ciccilla kafa yana wasa tare da surutai irin na yara. Yana ganinta kuwa ya wangale baki yana mata daria,yana sanye da body suit dinsa masu kyan gaske da ban sha'awa .(hmm, kaga dan likitoci ,😀)kaunar dan nata taji ya kara shiga zuciyarta ,dariyar da yake mata ya sa taji kaunar danta har cikin zuciyarta tare da godewa Allah da ya azurta ta da kyakkyawa kuma lafiyayyen da son kowa.( dama ahalin likita na cuta ne 😜😜ciwon ma tsoran gidan likita yake)</p><p> Tasa hannu ta daga shi,yaro ne da bai wuce wata shida ba ,ta rungumo shi a jikin ta ,ta ce. </p><p> Ni dai na kasa tashin Abbanka ,amma ni da kai zamu tashe shi tare.</p><p> Nan taje ta ajiye shi a kansa,nan da nan ya wangale baki har da tsalle saboda ya ga abokin wasansa. Nan ya hau sukuwa a kansa yana jansa tare da masa yaren su na yara ,dolensa ya bude ido yace.</p><p> " Ta nan mommyn ka ta bullo ko ? Ta hada ni dambe da kai,to bari in mike muyi.</p><p> Nana ya tashi ya biyeshi suna wasa yana cilla shi sama ,shi kuwa yana ta dariya,itama ta taya su. Sannan ta barsu ta nufi toilet don shirya masa bayi ,ya yi wanka . Tazo ta barki Muhammad ta kai shi gurin baba Andi,dattijuwa me kula da shi in bata nan. Sannan ta dawo ta taimaka masa ya yi wanka,ya shirya kusan komai ita ta masa,hatta turare ita ta fesa masa ,gyaran fuska da komai ,sannan ta kalleshi ta ce . </p><p> Perfect!!! Mijina is d best" Ya jawota jikinsa yace,"A'a mama ta is d best ,,ina sonki Bahijja na,ina son ki sosan gaske ,musamman in kina sakaltani ,ina jina kamar dab baby. Zan iya yin tiyata inyi allura in bada magani in duba mara lafia,amma ba zan iya kula da kaina ba,ko daurawa kaina tied bazan ita ba balle shafar mai ko sa kaya. Ko siyen sutura nawa ban iyawa saboda Bahijja na ta bata ni,ban iya komai nawa.</p><p> Allah ya bar mun ke Bahijja na,Allah ya miki albakrka ,Allah ya hadani da ke har a gidan aljannah"</p><p> " Ameen my dear""</p><p> Ta fada a lokacin da take kokari. Kwanciya a jikinshi,idon ta a lumshe ,ta ce.</p><p> Wa zan sakalta in bata in ba mijina ba ? Kai ne first baby na,babyna na farko kafin Muhammad,kaine zuciyata, kaine rayuwata,kaine mutumin da bazan taba gajiya da masa hidima ba har iya karshen tmrayuwata. You are my world nd my happiness duk wani abu a duniya bayan Addini na to komai ya biyo bayan kai da Muhammad ,bani da kamar ku.</p><p> Aure na da rayuwarsa gaba daya na daukeshi ibada ne,sai nayi dace da samun soyayya da kwanciyar hankali da duk wani abu da mace zata bukata a rayuwa . Na gide Mislihu ,Allah ya saka ma da gidan Aljanna. Duk wani abu da nake maka ban yi rabin wanda kake min ba ."</p><p> Yayi murmushi ,A duk lokacin da na kalle ki da Muhammad da kuma asibitina,yadda kike taimako na ,kika fahimce ni,yadda kika yi spporting dina sai naji tamkar Allah ya biya mun dukkan wani bukata ta na rayuwa,sai fatan Allah ya hadani da ke har a Aljannah. Ina alfahari da ke Bahijja."</p><p> Tayi murmushi ,Nima ina alfahari da kai Mislihu.."</p><p> Nan ta ja shi zuwa dining area kamar kullum kamar yadda suka saba,ta tabbatar ya ci ya sha abinda ya kamata ,sannan ta raka shi har kofar ya fita wurin bakin sa. Sun rabu cikin soyayya da kaunar juna kamar yadda suka saba.</p><p> Dr Mislihu ya samu bakinsa a falo Alh. Umar ne da amininsa Alh. Tahir suka zo da maganr Deeni . Nan ya nemi jin abinda ke damun sa ? Me ya faru dashi ? Dan yana son ganin medical report dinsa wanda ya tabbatar musu da sai in yaji case din irin wanda suke maganin matsalar sa ne ,to zai karbe shi. </p><p>Alh. Tahir ya masa bayanin komai sannan suka yi alkawarin kawo miahi medical report dinsa washegari. Da wannan suka rabu akan za su hadu washe gari a cikin asibiti......... . </p><p><br /></p><p><br /></p><p>To nan muka kawo karshen wannan kashi.....</p><p> Sai kuma ku tara a nan gaba ,wanda zamuci gaba ranar monday in Allah ya kaimu..domin gobe sunday ranar hutu nace 😎😎😎</p><p> </p><p>Nagode ,taku har kullum,,,</p><p>👩🏻🔬👩🏻🔬MISBAH👩🏻🔬👩🏻🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p>writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>=================== GIDAN NOVELS ====================================</p><p><br /></p><p><br /></p><p>30</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bahijja mace ce abarbso ga kowa balle mijinta. Macece da tasan hakkin mutane da basu hakkin su, tare da tsananin kulawa da nuna damuwa ga mijinta. Tasan yadda zata kula da kanta da kuma mijinta da duk wanda yake tare da ita ko yake karkashinta, don haka ma'aikatan su ke matukar jin dadin aiki da ita. </p><p> Komai tsananin abu ta iya mai dashi mai sauki, mace ce mai so da kuma kokarin aika gudunmawarta ga alumma, a duk lokacin da ta samu wata yar dama komai kankantar ta tana amfani da ita don tura sakonta ga al'umma a </p><p>fili ko a boye, a zahiri ko a badini. A duk lokacin da taso tura sakon da bata so a santa ko a san ita ce, to takan yi amfani da sunan MISBAH, wato ta hada sunanta da na mijinta, farkon sunanta da farkon sunansa. </p><p>Shikansa Dr Muslihu bai jima da gane wacece MISBAH ba. Saboda bata fada masa ba, a fadinta tace ba tayi dan a santa ba, sai dan bukatarta ta biya, ta tura sakon da takeso turawa kuma ya isa. Wanda ladanta gun Allah takeso ba mutum ba. </p><p>Wannan halaiyar tata shike karawa mijinta sonta, yake gani kamar ba irinta a duniya. Bahijja baice ta hada komai ba dan 'yar'adam take (She is not 100%) amma halayenta masu kyau da niyyarta sun maidata 100% da har ba'a kula da sauran illolin nata. </p><p>Bahijja (MISBAH), macecemai aiki da niyya, mace mai akida da ka'ida, mai yin abinda tace da abinda tayi niyya. Intai alkawari zata cika, in kuwa tayi magana gaskiya ce zata fito daga bakinta. Bayan aikint babu inda take samun matukar nishadi da jin dadi kamar ta tsinci kanta a gaban (computer) tana bincike ko ta fada duniyar rubutu, tana aika sakon zuciyart da iliminta da iya fahimtarta ga al'umma. </p><p>Tana kula da bangaren mata a asibitinsu, shi kuma bangaren maza. Suna kula da damuwar juna da farin cikin juna, suna bawa juna lokaci da kula, suna tsananin farin ciki a duniyarsu. </p><p>Lokacin da ta cika shekara goma da aure Allah ya azurtasu da haihuwar da namiji mai kama da Bahijja, yayin da ya biyo mahaifinsa ta hanyar halittarsa. Farin cikinsu ya karu, suka yiwa Allah godiya. </p><p>Bahijja ta rungumi danta da mijinta wanda suke sune duniyarta da farin cikinta gaba daya. </p><p>Bahijja ta sami dukkan abinda takeso, saidai ta inda tayi rashin sa'a ta bangaren dangin mijinta, wani lokaci uwar mijinta da 'yan'uwansa zasu zo har gida su zageta suci mutuncinta gaban ma'aikatanta. Suna tunanin ta mallake Muslihu, gata tsintacciyar mage bata da asali. Ba irin cin mutuncin da basa mata, amma bata taba nunawa Muslihu ba balle ta fada masa, har ya gane da kansa, saidai bai nuna mata ba tunda ya lura bata so ya sani balle har ya nemi fad da 'yan'uwansa akanta. Dan haka yai yadda takeso, bai musu maganar ba balle su sami rashin fahimta. </p><p><br /></p><p>Bayan son Bahijja yana mugun ganin girmanta da darajarta, wani lokacin yakan rasa mai zai mata dan ya nuna mata jin dadinsa da farin cikinsa da soyayyarsa gareta, kome yai mata sai yaga yayi kadan, dan haka yake ronkon Allah ya bata farin ciki da kwanciyar hankali duniya da lahira. Allah ya daukakaa, ya daukaka darajarta a duniya da lahira, Allah ya bata Aljanna.</p><p> A halin yanzu Bahijja na hutu tunda ta haihu ba ta koma aiki ba,saboda Mislihu ya hanata,ya ce sai ta huta nabtsawon shekara guda.</p><p> Bata musa ba tayi yadda yake so. Sai dai fa Bahijja Bahijja ce ,bata san zaman banza ba,don hka ta bawa jikinta hutu amma kwakwalwarta kullum tana cikn rubuce - rubuce ,daga na turanci har hausa,daga na addini har na zamani.</p><p> Wani lokaci (poem )take rubutawa daga na hausa har na turanci,wani lokaci kuma ta zauna tana koyon abinda bata iya ba matsayinta na mace,kamar girke girke ,iya kwalliya ,(dressing) da sauransu. Don Bahujja kam tana da mugun rauni a wurin, wani lokaci takan fi sati bata shafa ko (powder )a fuskarta ba ,balle jan baki da sauransu.a</p><p> Wani lokaci Mislihu ke zama yana mata kwalliyar,har gyaran gashi. Wani lokaci yakan tsokane ta,ya ce sai ya auro wacce ta iya kwalliya da gayu.</p><p> Ta kanyi murmushi tace,"Wa ya hana ka ? Ni duk abinda kake so ina maraba da shi." </p><p> Yakan jawota jikinsa ya tallafi kanta,ya ce.</p><p> Ga abinda nake so, wannan halayyar,wannan (personality ) din ba kwalliyar fyska ba . Ina miki fata da addu'ar ki zauna a yadda kike kar ki taba canjawa. Ina son wannan Bahijja kullum kwanan duniya ina da da sonta."</p><p> Takan rungume shi tace,"Ina sonka Mislihu na ,ka kasance dani har karshen rayuwata."</p><p> Yakan amsa mata da,"Insha Allah ."</p><p><br /></p><p> Asibitin su Bahijja Alh. Umar ya yanke hukuncin kawo Deeni,saboda yadda ya buncika yaga ingancin asibitin ,da tasirin da yayi sosai a cikin al'umma ,da kyakkyawan shaidar da suka samu.</p><p> Shi kanshi yadda ya ga tsarin asibitin da ayyukan su sai ya ji sun burge shi, har ma ya yiwa dansa Deeni sha'awar bude irinsa in Allah ya bashi lafiya.</p><p> </p><p> Kamar yadda sukayi alkawari,washegari Alh. Umar ya kawo wa Doctor Mislihu (report)din Deeni na duk wani asibiti da suka taba zuwa,daga gida Nigeria har na waje. A nan Doctor Mislihu ya bashi kwana uku cewa zai neme shi bayan ya karanta (report) dinsa.</p><p> Tunda ya karbi ( report din bai samu zama ya karanta ba ,saboda ayyuka da suka masa yawa,kuma gashi kwana ukun da ya basu saura kwana daya,don haka ya yanke hukuncin dawo da su gida ta duba ,duk da baya hada lokacin iyalin da na kowa don haka baya dauko aiki ya kawo shi gida,haka itama Misbah. Wannan dama ka'ida ne a gida basu da lokacin komai sai na kansu,sai dai ko in baya gida ita takan yi wasu ayyukan ,in ta gama da ayyukan gida . Lokaci na farko kenn da Doctor Mislihu ya taho da aiki gida........</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Pls ayi mun hakuri na rashin posting din jiya ,,,wlh gaba daya service dina ne ya dauke ......Nsha Allah yau sai kun gaji da karatu</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv 😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SAADATU WAZIRI GOMBE.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SAAD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>31</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya dawo gida a gajiye ,Misbah tayi masa abinda ya kamata,suka yi hirarsu irinta ma'aurata masu matukar son juna.</p><p> Can ta jiyo Muhammad yanata rigima a gurin baba Andi,hakan yasa ta fice wurinsu,lokacin Doctor Mislihu ya samu damar dauko (report ) din Deeni yana karantawa yana bin (history) na ciwon nasa da matsalar sa.</p><p> Ya yi nisa sosai wanda har Bahijja ta shigo kusan sau ukku amma baiji shiguwarya ba,ita kanta tayi mamaki,abinda bai taba yi ba. Yawanci ma in yana da aiki yakan je (office ) dinsa ya zauna koman dare,amma baya dawowa da shi.</p><p> Shigowar da ta sake yi na hudu ne ta samu bacci ya kwashe shi da takardun a gabansa. Murmushi tayi ganin yadda ya karya wuya kamar wani karamin yaro yana bacci.</p><p> Bayan ta kwantar da Muhammad a gadonsa ta zo ta gyara masa kwanciya tare da lullube shi,nan kuwa ta ga ya kara gyra kwanciya ya jawota jikinsa yana fadin,,,"Na gode Bahijja,Allah ya miki albarka.</p><p> Murmushi tayi ta kara manna shi a jikinta yadda zai ji dadin baccin ,har itama baccin ya fara daukarya. Nan ta farka ta zame jikina a hankali sannan ta tattara takarsun tare da canja kaya ta sa na bacci,har zata kwanta sai kuma wannan file din yaja hankalinta,wanne irin muhimmanci yake da shi haka yasa Doctor dawowa da shi gida ?</p><p> Nan ta bude ta fara bi a hankali tana karantawa ,kamar wasa gaske ta tsunduma cikin karatun ,tana kokarin fahimtar case dinsa. </p><p> Tuni taji zuciyarya ta karaya ,ta tausaya ,duk da ba ainihin tarihinsa taji ba amma (report ) dinsa ya nuna ya kamu daa ciwon (emotional disorder)tabbas yana bukatar taimako,yana bukatar (couseling )musamman ta fuskar Addini .sannan yana bukatar a nuna masa reality gaskiyar rayuwa ta canja masa,saboda tsawon shekarun da ya dauka a cikin wannan yanayi amma ba canjj,ya rayu cikin bakin ciki,bacin rai. Wanda wannan ba karamin ciwo bane kwarai.</p><p> Ta so tasa kanta cikin (case) din don jin me ya jawo masa wannan (emotional pains ) din ? Amma tayi shiru ta yarda da mijinta fiye da kowanne likita,fiye da ita kanta ,ta tabbatar zai taimaka masa . Nan ta tattara ta rufe ta ajiye file din gefe guda,yayin da ta kwanta da tunanin abin a ranta. </p><p><br /></p><p>Washe gari da safe bai fada mata ba,ita kuma bata tambayeshi ba,ta tabbatar in yana bukatar taimakobta zai fada mata.</p><p><br /></p><p>Kamar yadda suka yi alkawari a washegari ya nemi su ,wanda yayi dai dai da kwanakin da ya basu,anan doctor ya basu form su cike ,sannan wata takarda wadda take cike da sharudan asibitin kafin su karbi mutum,da kuma in sun karbe shi. Idan sun amince da sharudan su to su sa hannu su kawo shi,in kuma basu amince ba to kar ma su dawo.</p><p> Tun a wurin Alh. Umar ya karanta duk da halayyar da Doctor Mislihub ya nuna musu ya yi kama da gadara,amma ba yadda ya iya sai ya bi dokar don ya lura ba maganar alfarma wa kowa a bisa dokar su da akidarsu. Bashi da zabi saboda yanada bukatar taimakonsu,ya yarda da sahihancin su da gaskiyar su,hka akwai tsaro na sosai .dole ya amince da dokar su.</p><p> Doka mafi tsauri a cikin dokokinsu shi ne ba a dauke mara lafiya har sai in. Su suka sallame shi bayan ya warke,haka nn basu da wani sauran iko ko isa akan mara lafia da suka kawo,basu da ikon wani yanke hukunci akansa.</p><p><br /></p><p> Alh. Umar ya so yaja baya ,sai dai a lokacin da ya rufe ido ya tuno halin da Deeni yake ,sai yaji hankalinsa ya tashi,tsananin tausayinsa ya ratsa shi,soyayyar dansa da tausayinsa yasa shi zub da hawaye tare da dora laifin halin da dansa ya shiga akansa. Haka nan zuciyar ya amince da wannan asibitin, yana da tsammanin Deeni zai samu lafiya a wurin. Don haka wannan ya bashi karfin gwiwar sa hannu,ya yi cike - ciken da duk ya kamata tare da karbar (sliip) don biyan kudin jinyar Deeni. Sun rabu akan washegari zasu kawo shi...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SAADATU WAZIRI GOMBE </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SAAD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>32</p><p><br /></p><p> </p><p> A hankali ya turo kofar dakin nasa tankar mai jin tsoron kofar,zuciyarsa na tsinkewa saboda tunanin wane hali zai samu dan nasa ? Tsawon sati guda kenn bai leka shi ba,saboda gudun wani hali zai same shi.</p><p> Kamar kullum ya same shi makure a lungu guda tamkar mai jin tsoron kar azo a kama shi,fuskar sa daure tamau ba alamar fara'a tare dashi. In bai manta ba kayan da ya barshi da shi wancan satin har yanzu sune a jikinsa. Tuni idanunsa suka kada suka yi jawur.</p><p> Deeni da na sani da tsafta da son gayu komai fes-fes ba ma jikinsa ba,dakinsa ,kayansa komai fes-fes suke,kuma cikin tsari. Amma yau rayuwa ce ta mai da Deeni haka kuma ni ne sanadi"".</p><p> Ya yi haske amma ya fada,yayi wata irin rama mara kyau ,hasken da ya yima albarkacin zama wuri daya da take yi ne,da kuma yanayi irin na lagos. Tunda suka zo garin ko kofar gida bai fita ba ,yana nan a dakinsa da aka ware masa.</p><p> Mama bata fasa masa addu'a ba da nema masa sauki, da mafita a wurin ubangiji.</p><p> Deeni "" mahaifin nasa ya kira sunansa.</p><p>Juyowa ya yi suka yi ido biyu,tuni kuwa ya kara daure fuska tamau,idanunsa suka juye alamar bacin rai ya bayyana karara a fuskar sa ,ya yi saurin dauke kai.</p><p> Mahaifin nasa ya fahimci har yanzun yana cikin fushi dashi ,ya matso dashi.</p><p> Kayi hakuri Deeni,na maka laifi ,zan yi iya dukkan kokarina inga na gyara kuskuren da nayi,Deeni kar ka hukuntani ta hanyar tsanantawa kanka da bata rayuwarka a banza,Deeni wanne farin ciki ka tsinta a irin wannan ratuwar da kake ? </p><p> Deeni nasan ba zaka so ba kuma ba zaka yarda ba,dai dai zan fada maka ina son kaika inda raguwarka zata dai daita,wanda bayan nan na maka alkawarin ba zan sake maka shisshigi a rayuwarka ba,zan baka dama kayi rayuwar ka yadda kake so kuma yadda kaga dama. Ina so ka shirya mu tafi don Allah...""</p><p> Jin kalamansa da yayi na karshe ne ya juyo ya kalle shi,ya ce.</p><p> " Kai mahaifina ne ,ba sai ka rokeni ba zan maka biyayya . Ina kake so inje ? Zan je zan je amma karka taba zaton wai don kaina ne sai don kanka,kamar yadda ka dauko mana tun farko ka sabar mana ,bamu da zabi sai naka,to yanzu ma haka ne. Saboda ni kan yanzu a rayuwa ba abinda ya saura zaka min ,baka da abinda zaka iya sake min ko bani ya sani farin ciki,ba abinda zaka min ya goge min bakin cikin da bacin ran da ke cikin kwakwalwats da zuciyata .</p><p> Wanann abinda kuka hadu kuka mun va zai taba barina naji wani dadi ba a ratuwata ba,ba yadda za'ayi in samu wani farin ciki ko kankani bayan cin amana da rashin kauna da kuntata mini da yaudarar da iyayena da dan uwana da wacce... .........</p><p>Maganar ta sarke ,numfashinsa ya dinga fita sama sama,vai ankara ba sai ganinsa yayi ya fadi ya suma . Cikin tashin hankali da damuwa sukayi asibiti da shi,asibitin da bai shiga yana cikun hankalinsa ba sai a sume.</p><p> Dokar farko ta fara aiki akan su,wato su ajiye shi su tafi su barshi ,kuma ba zasu sake waiwayar sa ba sai bayan wata shida wanda in ya samu wannan wata shidan zasu iya zuwa bayan wata daddaya.</p><p> Haka haji. A'i da Alh. Umar suka tafi suka bar dansu cikin mawuyacin hali da ciwk ,mama tayi kuka har ta gode Allah ,yayin da Alh. Umar bai yi ba,sai dai abinda yake ji a zuciyar sa yafi kuka ciwo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Doctor Mislihu ne tsaye kan Deeni tare da sauran likitoci da ke aiki a karkashinsa,da sauran ma'aikatan asibitin suna iya dukkan kokarinsu don ganin ya farfado.sai dai fa abin ya ci tura,va irin dabarar da basuyi ba hakan yasa ya nemi taimakon gaggawa dafa sauran 'yan uwansa wadanda suke manyansa ne ta hanyar wayar sadarwa.</p><p> Tabbas duk kokarin ka da kwarewar ka wataran sai aikinka ya kunyata ka,kwarewa da dai dai sai Allah,Dr. Mislihu bai kasa va kuma bai yi kasa a gwiwa ba ya ci gaba da ba da himmar sa da kokarin sa,bai ji dar ko tsoro ba,sai dai abin ya matukar daure masa kai,saboda shi yasan ya sha fuskantar masu ciwo irin na Deeni.</p><p> Da taimakon Allah yana addu'a tare da yakini a zuciyar sa ya samu deeni ya farfado da wani bakon yanayi,yana cikin tsananin ciwo da rudani,idanunsa sunyi jawur ,hawaye kawai ke zubaa ba kakkautawa,haka nan ya rike kansa gam alamar yana jin azabar ciwo,abin har ya kaishi ga yana doka kansa jikin karfen gadon da yake kwance.</p><p> An masa allurar da ya kamata ayi masa ya samu nutsuwa kadan,da kyar suma samu bacci ya dauke shi. Baccin da yakamata yayi na wuni guda kafin ya farka,amma awa biyu zuwa uku kawai allurar take masa aiki ,haka magani ba ya aiki a jikinsa.</p><p><br /></p><p>A wannan dare Doctor Mislihu ya koma a gajiye tare da wannan damuwar a tare da shi. Bahijja na ganin sa tasan ba lafiya ba,ta riga da tasan yanayin aikin nasu ,akwai gajiyarwa ,sabida jikinka da kwakwalwarka da zuciyar ka duk sai sun jigata,sun wahala.</p><p> Ta shirya masa ruwa yayi wanka,bayan ya fito tayi kokarin sauke masa gaijyar sa da (tension ) dinsa ta hanyar masa matsa a gabban jikinsa da kansa,tana (massaging )cikin nutsuwa yadda zaiji dadinsa,kuma ya yi masa aiki.</p><p> Yaji dadin hakan kwarai,ya jawo hannu ta.</p><p> Na gode Bahijja ,naji dadi sosai, naji dadin wannan abinda kike min don ya bani nutsuwa tare da sauke min wani (tension)din . Tayi murmushi tare da shafa shi,ta ce ." Burina kenan inga na rage maka damuwa,naga yau kana cikin zafi ,bari in kawo maka abincinka daki.</p><p>Nan ta fita ta dawo hannunta dauke da babban (tray ) ta shirya masa duk wani abinda zai bukata. (Coffe) mai zafi ta fara bashi sannan ta zuba masa abincin wanda kadan ya ci shima don ta matsa masa ne,kafin ma ta ce wani abu aka masa waya ya nufi asibitin a rude..</p><p> Wannan al'amarin ya daurewa Bahijja kai,"" To shin meke faruwa ne ?</p><p> Nan ta buga waya asibitin don jin meke faruwa? A nan aka bata labarin sabon mara lafiya da aka kawo wanda ya ta da hankalin oga.</p><p> Haka ta dunga kawai da kawowa har ya dawo ,ta tare shi da tambayoyi amma bai amsa mata ba ya nuna ta kyale shi akwai binciken da zai yi ,in ya gama zai sanar da ita.</p><p> Wannan abu ya daure mata kai ,sam bata jin dadin ganinsa haka. Ya dawo kullum yana cikin karatu da bincike saboda matsalar Deeni ta zame masa sabo,ya zama kamar (challenge) ne a tare dashi..</p><p> Abokinsa Doctor yasir ya nemo wanda suka yi karatu tare ,kuma sunyi aiki tare a dashi lokacin da suke ( teaching hospital) wanda shi bayan bude asibitin su ne suka rabu. Sai dai dama lokaci lokaci sukan hada kai suyi karatu.</p><p> Dr. Yasir kamar aboki ne a gare shi,kuma abokin aikinsa,don haka ya roki alfarmar ya zo su binciki case din deeni tare.</p><p> Da farko ya so yasa Bahijja ciki,sai dai baya sob wahalar da ita,sannan tana cikin hutu ne,gara ta zauna ta bawa muhammad kyakkaywar kulawar da yake bukata. Kuna yasan Bahijja sarai da daukan zafi,tana iya watsar da komai ta tsunduma kanta ciki,don haka ya yanke shawarar ya yi aikinsa da kansa.</p><p><br /></p><p> Wata guda suna bawa Deeni(treatment) amma ba wani cigaba ,babbar damuwar sa yana cikin ciwo balle har a samu nutsuwar da za a sai ta hankalinsa da tunaninsa,balle har a san matsayin da kwakwalwarsa da zuciyarsa suke ciki. wannan abu ya mummunan daga hankalin Doctor Mislihu da sa shi cikin damuwa,duk maganin da ya bashi baya aiki dai dai a jikinsa yadda ya kamata yayi. </p><p> Gaba daya y rasa nutuwa da kwanciyar hankali,kullum bashi nan bashi can neman yadda za a samu waraka ,haka ya dauki (case)din deeni da zafi tamkar na wani dan uwansa na jini,ya ci alwashin sai inda karfinsa ya kare.</p><p> Ya dawo ba ya bawa kowanne mara lafiya kulawa kamar yadda yake bawa Deeni,tausayin sa da kaunar sa ya shiga ransa,musamman in yaga yadda wataran Deeni ke zura masa ido yana kallon sa tamtar mai kokarin fada masa wani abu,tamkar yana ce masa ka ""ka taimake ni,"" tamkar dukkan tsammaninsa na kansa. Haka wani lokaci hawaye zai yi ta zuba masa,lokaci guda kuma ya kuma rikecewa.</p><p> </p><p> Abin na Deeni gaba-gaba yake,don haka Doctor yasir ya bashi wata shawara akan abinda zasu masa,amma fa sam ya ki yarda ,yaki amincewa ,saboda yana ga akwai garaje ciki,sannan ciwon Deeni bai kao har hakan ba. Amma a hankali Doctor yasir ya dinga nuna masa dukkan wani (treatment) da zasu mada sun masa,amma baya (respondng) wannan shi ne option da ya rage dashi.</p><p> Ya tuna ya yiwa kansa alkawarin yin duk abinda zai yi don ya taimaki shi ,haka iyayen yaron na da dukkan wani tsammaninsu akan shi. Da kyar Dr. Yasir ya shawo kansa ya amince...........</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Barkanku da rana jama'a</p><p>Sai ayi wa deeni addu'a za'a yi masa theatre Allah yasa a dace 😭😭</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by. SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>33</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Nan ya hau shirye-shirye ,yasa lokaci da rana,ya gama amimcews kansa amma duk da hakan sai yaji zuciyarsa na fada masa ya nemi shawarar matarsa,ya sanar da ita,ko ba komai rana da ilimi akan cuwon Deeni sosai kamar yadda yake da shi. Da wannan tunanin ya dauki waya ya bugawa Bahijja.</p><p> "Bahijja"</p><p> "Yes my dear,kana hanya ne na jira ka shuru,hope dai lafia."</p><p> Ya yi mata murmushi tamkar tana kallinsa,ya ce </p><p> "Lafiya Bahijja ,wani aiki ne yasha kaina da na gama zan taho. Dama ra'ayinki nake son ji akan wani abu da zan yiwa patient dina."</p><p> Tayi masa daria tace ,"Zan yi farin ciki da baka shawara mai kyau ,na lura kana cikin damuwa akan wannan mara lafiyar ,kar ka damu nasan ko me zaka yi ( you re the best on it).</p><p> Yace,"Duk da haka dai ina neman kwarin gwiwar a wurin ki."</p><p> Ta ce,"To ina jinka,mene ne matsalar ka?</p><p> A hankali ya labarta mata case din Deeni da yadda yayi ta fama da shi.</p><p> Ta dan yi dogon shuru tana tunanin ai indai wanda ta karanta file dinsa ne case dinsa ba haka bane,abinda reporrt dinsa ya ce daban abinds kuma Doctor ya fada mata yanzu da irin treatment din da suke masa daban .</p><p> "Bahijja " </p><p> Muryarsa ta katse mata tunani.</p><p> Kina jina kuwa?</p><p> " Eh ina ji"</p><p> Ta fada cikin muryar damuwa,sannan ta ce.</p><p> To yanzu wane shawara ka yanke? Me kake ganin zaka masa?</p><p> "Shawarar da muka yanke yanzu ni da Doctor Yasir shine,zamu masa (E.C.T)</p><p> ""WHAT!!!!!!!!</p><p> Ta fada da karfi cikin zare ido tamkar yana ganinta,hankalinta ya tashi.</p><p> Ta ce please Doctor kar kuyi masa,kasan dangers na wannan therapy din" </p><p> "Bai kai stage din da za a masa haka ba.</p><p> " Da hankalinka,da tunaninka?</p><p> "Me kike nufi? Kina so kice bani da hankali ko ban san me nake yi ba ? Laifina ne ba naki ba da na fada miki ,dama na lura komai ke kina son nuna kin fi kowa sani."</p><p> Tayi kasa da murya ,Kayi hakuri my dear ba haka nake nufi ba,nasan kai fini ,kasan komai ,amma ina so ka fahimci danger din dake cikinsa ne,kar muyi wasa ko garaje da rayuwar wasu. Ka tuna amana da yarda yasa iyaye da 'yan uwa ke kawo mana marasa lafiya,kasan yadda (electro convulsive therapy )yake,idan ya yi (seizing ) kwakwalwar sa gaba daya fa?</p><p> A tunanina baya bukatar wannan,ina gain (right medication) da (couseling ) ya ishe shi ya dawo dai dai ,wato maganin da ya dace.</p><p> Maganganunta yasa shi kasala ,ya ce.</p><p> Na bugo ne ki bani kwarin gwiwa ba kisa na karaya ba,ni kike yiwa maganar (right medication)?Don baki ganshi a gabanki bane da irin kokarin da nayi akansa da ba zaki fara fada min haka ba. "</p><p> Doctor duty na ne in tsaida ka,please na rokeka kar kayi,ka sake tunani.</p><p> Kashe wayar yayi ya kyaleta cikin rudani tana ta buga wayar tana ihun kar yayi amma bai dauki wayar ba ma. Hankalinta ya matukar tashi,ba shiri ta dauki hijab ta nufi cikin asibitin da sauri.</p><p> Sai dai kafin ta zo Doctor yasir yayi nasara akansa na cewa.</p><p> Kasan halin mata da tsoro ,da gajeriyar kwakwalwa ."</p><p> Ya amince amma maganar Bahijja da dalilan da ta bashi na yawo akansa,don kuwa yasan matarsa Bahijja bata cikin mata masu tsoto ko gajeriyar kwakwalwa amma da yake ya riga da ya yanke hukuncin sai ya yi din . Don haka kafin Bahijja ma ta iso dun riga da sun yiwa Deeni abinda suka yi niyya.</p><p> Yana kwance a wurin kamar gawa,dukkan gabobin jikinsa sun amsa,duk jikinsa ya sassake ,bawan Allah shi kadai yasan wahalar da yasha. Gashi jikin Deeni jiki ne da bai saba da wahala ba,bai ma santa ba gaba daya don haka abin ya fi wahalar dashi fiye da yadda ya kamata. Tuni ya manta kansa da duniyar da yake ciki.</p><p> A lokacin da Doctor Bahijja ta shigo zama tayi ta kama kai tana kuka .</p><p> Doctor me yasa kayi haka ? WHY!!!!!!</p><p> Tuni ya harzuka ,"Me kike nufi da (why)? Ban san me nake yi bane ? Me kike so kiyi (proving) da kika shigo kina min tsawa gaban abokan aikina da ma'aikatana ? Me kike ji da shi ? Wa ya baki izinin fitowa ki zo ?</p><p> " Doctor (please )."</p><p> Ta fada cikin kwantar da kai .</p><p> ( This is not you)wannan ba kai bane,ba haka na sanka ba ,kai mutum ne me taka tsan tsan da rayuwan alumma. Wannan ciwon nasa da ya zamo maka sabo ba firgita ka ya kamata yayi ba,ko kuma wani abin cews sai naga ya warke ko ta halin kaka kar a ce na gaza .</p><p> Ka tuna asalin purpose dinmu shi ne mu taimaki mutane ba mu wahalar da su ba ,ba muyi wasa da rayukansu ba. Yaushe tunaninka ya kauce,ya canja ? Yau ina cikin bakin ciki da na kasa tsai da ka,na kasa hana ka yin abinda ba dai dai ba,sai addu'ar Allah ya tashi kafadar wannan bawan Allah.</p><p> Bai kulata ba sai sa kai da yayi ya fita cikin bacin rai,yayin da sauran suka rufa masa baya.............</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shin wai wani irin aiki doctor mislihu yayiwa deeni ,,wanda har ya sa shi hatsaniya da matarshi... 🤔🤔</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Writting by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bismillahirrahmanurrahim</p><p> RABBANAGFIRLI WAL-WALIDAYYA WALIL MU'UMININA YAUMA YAKUMUL HISAB............AMEEN YA ALLAH.😭😭Allah yasa mu dace duniya da laira..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>34</p><p><br /></p><p> Ta mai da hankalinta kan Deeni ,taje tayi dukkan iya kokarinta domin ta samu ya dawo hayyacinsa,ya farfado kafin ya yi nisa. Sai data dauki tsawon awa uku akansa kafin ta samu ya bude ido sannan ya sake rufewa,numfashinsa ya daidaita. Sannan ta dan samu kwanciyar hankali da nutsuwa kadan,ta koma gida hankalinta a tashe ,tayi ta fama da Doctor Mislihu .</p><p> </p><p> Fada yake mata ta inda ya shiga bata nan yake fita ba,ta lura yana cikin tsoro da tashin hankali ,sai dai yana kaucewa hakan da fada.</p><p> Bata ce masa kala ba sai rungumar sa da tayi sosai a jikinta,ta riga da ta fahimci (fears) dinsa da tashin hankalin daya shiga. </p><p> Kwantar da hankalinka ,insha Allah komai zai dai dai ta ,baa abinda zai faru (he will be fine) . Kuskure be kowa yana yi a rayuwa ,sai dai muyi kokarin kare faruwar haka a gaba. Bamu da damar yin wasa da rayuwa wasu.</p><p> "Bahijja ban san me ke faruwa ba,na kasa gane komai. Nasan cewa duk wani (treatment) da nake masa dai dai ne ,sai dai ban san me yasa ba ya (responding) ba,kuma ban yi niyyar wasa da rayuwar sa ba har zuci,ina son taikamakon sa ne. Ina ganun wahalar da yake sha,ina jinsa kamar dan uwana,sannan inason raikamakon mahaifinsa shi yasa duk abinda zanyi ya kare na dauki wannan (option )din. Ban yi tunanun komai ba ,sai dai nasan wanann a cikin (shock treatment ) wannan (is the most safest and effective).</p><p> Na sani my dear ,amma wannan ciwon sa(disorder) din da yake da shi ba na wannan treatment din ba ne. A ganina kun yiwa abin gaggawa ,kuma naga kamar baku yi shi dai dai ba,dole akwai wani kuskure a wani wurin ( something wrong somewhere ). Wa ya baka wannan ( idear ).?</p><p> " Doctor yasir ;;" ya fada kai tsaye .</p><p> Ta dafe kai cikin takaici ,ta ce. Haba doctor !!</p><p> " Har yaushe ka fara amfani da basirar wasu maimakon taka?</p><p> Kin san mutumin nan likita ne dan uwana ,meye a ciki in munyi (studying case ) na mara lafiya,munyi (sharing idea)?</p><p> " Baa laifi bane,amma abin akwai daure kai"</p><p> A wanann dare daga Dr. Mislihu har dr. Bahijja ba wanda ya runtsa ,suna tunani tare da juya al'amarin a cikin ransu wanda Dr. Muslihu ya kasa jurewa gari ya waye,a daren ya fita domin zuwa ya sake ganin Deeni.</p><p><br /></p><p> Ga mamakin sa yana kofar shiga dakin yaji muryar Doctor yasir da wasu ma'aikatansa guda hudu wanda amintattun ma'aikaransa ne,yaji dr. Yasir yana raba musu kudi na aikin da suka masa. Ba farko sunyi ta canja duk wani magani da allurai da ya ce su kawo a dinga bawa Deeni. Wanda wannan yasa jikin Deeni ya kara rikicewa maimakon samun sauki. Saboda yana so ya batawa dr. Misilhu suna don ya jima yana jin haushin cigaban da ya samu ya barshi. Abu na biyu shi ya so Alh. Umar ya damkawa Deeni a asibitin su saboda ya ci kudinsa sosai ,amma sai Alh. Umar ya ci mutuncinsa ya ki. Tun daga lokacin ya dau lwashin sai ya dau fansa,kuma ya batawa doctor mislihu suna. Don haka ya bawa ma'aikatansa cin hanci.</p><p> </p><p> Da farko kun ki,amma ganin yawan kudin da ya saye imaninsu suka manta amana da yarda dake tsakaninsu da mai asibitin. Ya ce kuma in aiki ya yi zai kara musu .</p><p><br /></p><p> Lokacin da Dr. Mislihu ya gama jin abinda suke fadi ya ciro wayar sa ya kira (police) sannan ya kira Bahijja yana fada mata. </p><p> "Doctor yasir ya ci amanata ,Bahijja gaskiyarki ne,akwai abinda ua faru wanda ban fahimata ba sai yanzu".</p><p>Yana cikin magana da ita ya jiyo motsin su zasu tafi,ya yi saitin banki kofar ,bai bata lokaci ba ya cakuno wuyan rigarsa tare da shakar masa wuya yana zaginsa.</p><p> "Yau sai na kashe ka ,maci amana. Ku kuma sai nasa an kulle ku,kun ci amanar yarda,kunyi wasa da rayuwar wani sabida abin duniya."</p><p> Ganin yadda ya haukace musu Dr. Yasir ya ce. </p><p> Yaa zama dole muyi maganinsa kafin ya fallasa mu"</p><p> Tuni suka hadu akansa,hayaniyar su ya ta da Deeni ,ya yin da yakr ganunsu hazo-hazo ,duk da baya magana da Dr.mislihu ya saba da shi da dawainiyar da yake masa. Sannan da ikon Allah da taimakon da misbah tayi masa ya masa amfani ,ya dawo hayyacinsa.</p><p> Gani yadda suka toshe bakin dr. Mislihu suna dukansa tare da kokarin toshe masa hanci yasa ya mike ya nufi inda wani bell yake wanda alama ne na danger in an danna,ya yi sauri domin dannawa ,anan daya ya hango shi,ya yi kansa suna ta kokawa,yayin da dr. Yasir ya dauko wani almakashi ya soma cakawa Dr. Mislihu tuni jini ta wanke wurin . Yana kokarin guduwa ya ceci kansa ko ta halin kaka,yasan in Dr .mislihu ya kubuta to asirinsu zai tonu.</p><p> Deeni bai san yaushe ya bude baki a firgice yana ihu bmtare da neman taimako ba,yana fadin .</p><p> "Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun!!!!</p><p> Nan sukayo saurin toshe masa baki da hanci har sukaga ya dai na nunfashi. Za su fita kenan sai ga 'yan sanda sun iso,kafin su gudu kuwa aka cafke su,yayin da akayi kokarin daukan doctor mislihu zuwa emergency tare da deeni......</p><p><br /></p><p> Lokacin Bahijja ta iso a rude tamkar mahaukaciya ,ganin mislihu cikin jini ya bala'in firgita ta da razanata. Tashin hankali ne wanda bata taba fuskantar irinsa ba,duk kuwa karfin hali da karfib zuciya irin nata a wannan rana sai da ta karaya ,hankalinta ya nemi barin jikinta.</p><p> Tayi kan dr. Mislihu jikinta na bari,ta rasa ma me zata mishi? Ta rude sai kiran sunansa take tana salati.</p><p> Tare akayi wani asibiti da su da wasu yan sanda dob basu taimakon gaggawa ,likitoci sunyi kokarin tsai da jinin dake zuba a jikinsa wanda a wuyansa suka caka masa da gefen ciki amma jinin bai tsaya ba,haka aka dinga masa kari wani ni fita wani na shiga. Suna iya dukkan kokarinsu akanshi.</p><p> Bahijja dai alwala tayi ta zo ta fara sallah,daga karshe ta hau addu'a saboda ta rasa nutsuwar yin sallar.</p><p> Wani likita ne ya zo ya kirata mijinta ya ce yana son ganinta. Jiki a sanyaye ta isa dakin tana kuka kamar ranta zai fita,ya kalleta cikin galabaita da kyar ya iya bude baki.</p><p> Kar kiyi kuka Bahijja ,ko yanzu ko bayan raina ,kituna yanzu nauyin asibiti da sauran al'umma da ke cikinsa na kanki,ki tuna mafarkin mu ne da burin mu wannan asibitin. Sai dai ki kula kar abinda ya faru dani ya faru da ke,mutum yana nan yana rayur sa bai damu da wani ba ashe makiya suna nan sun sa masa ido suna neman yadda za su cutar da shi.</p><p> K tuna nauyin asibiti da Muhammad na kanki,sannan in bani da rabon haduwa da mama in ta zo kun hadu kice ta yafe mun ""</p><p> Bahijja dai kuka take kamar zata hallaka ,ga tsoro da fargabar rasa mijinta ,ga maganar sa mai kama da bankwana,ga azabar ciwon da ta ganshi a ciki.</p><p> " Dole ne in maka kuka my dear,dole kuma in yiwa kaina kuka . Mutanen nan sun cuce mu,sun rusa mana 'yar karamar duniyar mu da muke farin ciki a cikinta .."</p><p> " Sun cuci kansu dai Bahijja ,ki tuna kece me lallashin wasu da ( couseling ) dinsu in sun shiga hali makamancin wannan ,yau rana tazo da zaki yiwa kanki wanann tatan.</p><p> Bahijja kada ki karaya kima fi yadda na sanki da,kiyi addu'a Allah na tare da ke ,kada ki taba jin ke kadai ce a duniya. Ki tuna duniya taki ce da mutanen arzikin da suke cikinta ,duk wani Musulmi dan uwanki ne .</p><p> Abu na karshe Bahijja,wannan. Bawan Allah da ya shiga rudanin rashin lafia da karin ruda masa jiki da kwakwalwa da ya samu ta sanadina ,ina fata zaki taimaka masa ya warke da iyakar iyawarki . Ina fata zaki gyara kuskuren da nayi."</p><p> Tayi karfin halin share hawayen da ke zuba mata tare da yi masa murmushi , tace,,</p><p>In sha Allah my dear zan taimaka masa har kaima ka samu lafiya mu taimaka masa tare,mu cigaba da kula da asibitin mu da Muhammad,a duniyarmu zamu sake ginata tare da kai insha Allah." </p><p> Duk da yana cikin ciwo sai da yayi mata murmushi alamar gamsuwa da maganarta. Nan ta kwantar da kai a gefen pillown dake jike da jini,tana rike da hannunsa,ita kadai tasan irin radadin da zuciyarta ke mata ,tana masa addu'ar fatan samun sauki da lafiya.hawaye na gudu a idonta ba kakkautawa,tana tunanin duniyarta ta zo karshe a duk lokacin da ta rasa doctor Mislihu .</p><p> ** Ya Allah nasan baka barin wani don wani,ya Allah ka bani karfin imani da karfin zuciyar daukan duk wani ikon ka da aiwatar akan mu"</p><p> Da irin wadannan addu'o'in a zuciyarta bacci ya debe ta bata sani ba ................</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hmmmmmmm.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Please kuyi hakuri na rashin jina jiya ,,bikn aminiyata ake shiyasa na mnta daku😎😎😎</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>35</p><p><br /></p><p> Da irin wadannan addu'o'in Bahijja a zuciyarta bacci ya debe ta bata sani ba,sai farkawa tayi taji hayaniya akanta. Sauran likitocin asibitin ne suke bata hakuri mijinta kam ta Allah ta kasance akansa,ya bar duniya. </p><p> Jin abin ta dinga yi ba zata,kamar mafarki. Wani jiri taji yana dibanta tana salati tana kallonsa tamkar mai bacci.</p><p> Wayyo duniya,duk wanda ya dauke ki da zafi tabbas yana cikin masu asara. Jiya tana yare da mijinta ,abokin rayuwarta,gatanta a duk duniya ,amma yau baya duniyar.</p><p> Hawaye na zuba ta ce,Allah ya jikanka Doctor ,Allah ya maka rahma,ya yafe maka kurakuranka,yasa ayyukanka na alkhairi su bika" .</p><p> Bahijja tayi kuka tayi kuka har taji ba dadi. Kafin a yiwa Doctor wanka da sutura 'yan uwansa suka iso daga kano ,mahaifiyarsa da danginta tare da dangin mahaifin sa tare dasu akai masa sutura aka kaishi gidansa na gaskiya,yayin da mahaifiyarsa ta yafe masa tare da binsa da addu'a.</p><p><br /></p><p>Gidan Bahijja suka dawo aka yi ta karbar gaisuwa ,yayin da maganar rasuwar ta baza ko ina,saboda Doctor mislihu yaui suna kwarai ,haka yana da jama'a . Ya yi suna ba don yana kudi ba sai dan kwarewarsa ta wurin aikinsa da sunan da yayi saboda asibitin su.</p><p><br /></p><p> Kwana uku aka yi ana karbar gaisuwa ,mahaifiyar sa tace su za su tattara su koma kano,don ita har yanzu ba wai tana son Bahijja ba ne ,asali ma ta dauka nauyin mutuwar danta akanta saboda ta ce ita ta sa shi zama a lagos yaki komawa can gida kano,ya guje su. Tunda tayi sanadin sa to zasu kwace danshi su tafi da shi ta dinga ganin jikanta. Kuma ta ce ko da wasa Bahijja kar tayi tunanin cewa zata zo ko da ganinsa balle daukar sa.</p><p> Anan fa ciwon yayiwa Bahijja bibbiyu,hankalinta ya mummunan tashi. Ta yaya za a rabata da Muhammad da bai fi wata takwas a duniya ba ??</p><p><br /></p><p>Ba irin rokon da bata yi musu ba har ta musu alkawarin kawo shi idan ta yaye shi,amma fur mahaifiyar mislihu ta ki. Haka ta tattara shi suka koma kano yana kuka Bahijja na kuka suka rabu.</p><p><br /></p><p> **** **** *****</p><p><br /></p><p>A wannan lokaci Bahijja tayi dan karamin hauka ,ko dai ta dinga jin muryar Doctor ,ko kukan Muhammad. Zuciyarta tayi rauni sosai,kullum tana cikin kuka,bata iya kulla komai. Daga karshe ita ke tashi ta share hawayenta,tayi karfin halin lallashin kanta.</p><p> Ta so ta bi iyayen Mislihu kano ,sai dai kuma ta tsai da kanta,ko me za su mata ba zata taba fada da su ko shari'a dasu ba albarkacin dansu da take so take ganin girma da darajarsa fiye da kowane namiji a duniya. Don haka ta sawa kanta hakuri,kamar yadda ta jure rashin mijinta shima dan nata zata jure rashin sa,in da rabon haduwarsu kuma da rai da lafiya to Allah zai hada su wata rana.</p><p><br /></p><p>Haka Bahijja ta hau takaba ,kullum kwana take tana zubar da hawaye tana yiwa mijitan da danta addu'a tare da fatan Allah ya kara mata hakuri da juriya. </p><p> Daga ita se Baba Andi a gidan wacce take mata rainon Muhammad,kasancewar kyautatawa da take mata ta dauketa kamar uwarta,yasa itama ta zauna tare da ita tana mata hidima tare da bata shawarwari da bata baki da lallashi. Tana matukar tausaya mata.</p><p><br /></p><p> Bahijja ta kasance bata da kawa ko wata 'yar uwa ko wata da suke da kussanci na sosai,saboda a RAYUWAR BAHIJJA ba (space) na kawaye ,wato ba fili ko lokacin yin kawance a rayiwarta,saboda ayyukanta da rabuce-rubucenta. Mijinta da danta sune kawayenta,sune rayuwarta.</p><p>Don haka yanzu rayuwa tayi mata wahalar gaske wanda daga rubutun har aikin sai da suka gagareta,damuwa da yawan tunani suka sako ta a gaba,ta rasa inda zata sa ranta taji dadi . Tuni ta kma ga Allah ,kullum tana cikin karatun Alkur'ani da addu'o'i tare da yawan istigfari don neman waraka daga halin da ta shiga..</p><p><br /></p><p> Wani lokacin takan rufe ido ta dinga tuno da kalaman Doctor wanda suke kara mata karfin gwiwa ,taji tana son mikewa tayi wani abu me amfani da rayuwarta bayan kuka da bacin rai.</p><p> Da haka a cikin wannan halin da yanayin ta gama takabar,sai dai duk da hakan ba tayi yunkurin fita fara wani aiki ba....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>36 </p><p><br /></p><p>Bayan rasuwar Mislihu Alh. Umay ya samu labari don haka ya zo ya dauki Deeni bayan ya farfado ya samu sauki na jiki amma fa kwakwalwarsa tamkar ya farka da sabon abu ,kullum yana cikin firgita da yin wasu abubuwa tamkar yana tsorace.</p><p> Haka mahaifinsa yasa ana yi masa addua su ma suna masa ,har ya dan samu sauki,amma kam har yanzu da matsala . Yayin da kotu ta yankewa Dr. Yasir da sauran ma'aikatan asibitin hukuncin daurin rai da rai. Allah ka tsare mu da son zuciya..</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Asibitin ya tsaya na dan wani lokaci saboda abunda ya faru da gidan da asibitin duk sun shia gado ,sai dai dama asibitin nasu ne su biyu da shi,sannan itama tana da gadonsa. A takaice dai wurin ya dawo nata da danta Muhammad ,wanda tayi alkawarin kula masa da shi ta damka masa kayansa wataran in tana da rai. Don haka ta shirya komai a rubuce saboda mutuwa ta kuma nemi lawyer na musulunci da Alkali suka zama shaida.</p><p><br /></p><p> Watanni shida da rasuwar Doctor Mislihu bayan gama takabarta ta hau shirye-shiryen yadda zata farfado da asibitin yafara aiki,ya dawo kamar da,a niyyarta ma har yafida,saboda tsaro da tantance ma'aikata sai yafi nada.</p><p> Bahijja kenan mace mai kamar maza,haka ta dage tana ta shige da fita ba zama ,tana neman taimako da yadda zaayi komai ya farfado ,wanda gudun tunani da bacin rai yasa ta dage da zama(busy) yau bata nan gobe bata can har sai da ta tabbatar komai ya dai daita mata kamar yadda takeso ,komai ya farfado ya soma aiki,sannan ta samu nutsuwa kadan.</p><p><br /></p><p>A kullum ta zauna maganar Deeni ke fado mata,da sakon da amanar taimakonsa da mijinta ya damka mata.</p><p> "Ya zama dole in nemo shi inji ya ya kare ? Sannan in sake duba (case) dinsa inga wane irin (treatment) ya kamata a masa."</p><p> Bata bata lokaci ba ta fara binciken file din Deeni wanda ta riga da dama tasan wannan case din,sai kari akan (wrong treatment ) din da aka yi ta masa.</p><p> Nan ta bincika address dinsa,sannan ta sake zuwa asibitin da aka kwantar dashi tare da Doctor ta sake bincike akan treatment dinsa ,sannan ta sake tabbatar da address dinsa. Daga nan ta daura damarar niyyar taimakon sa har sai inda karfinta ya kare,in ta tabbatar ya samu lafia zata samu kwanciyar hankali ,burinta da na mijinta ya cika,daga nan zata ci gaba da cika burin mijinta da nata har ta Allah ta kasan ce akanta,idan kuwa Muhammad ya girmata damka masa dukiyarsa,ta ci gaba da masa addu'a da shi da mahaifinsa. Wannan shi ne burin Doctor Bahijja da kuma kudurinta ,bayan shi ba komai a zuciyarta da tuaninta ,daga aikinta sai rubuce rubucenta.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Hmmmmm ,,Doctor MISBAH KENAN </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Please kuyi hakuri aiki ne yamun yawa 🙏🏼🙏🏼🙏🏼</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>SUMY LUV 😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by. SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by. SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 37</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haj. A'i na zaune a falo ita daya tayi nisa sosai a tunani,tana tuna yadda rayuwarsu take da da ta yanzu,lokaci guda rayuwarsu ta canja ,sun baro yankin su cikin 'yan uwa da abokan arziki,inda suka saba da rayuwarsu da komai ,sunyi nesa da dansu da 'yan jikokinta guda biyu da duk da suna zuwa lokaci-lokaci,ga rayuwar Deeni ta canja gaba daya . Duk kokarin da suke yi akan Deeni ba wani canji,yadda Deeni yake rayuwa yana matukar kona mata rai. Lukman ne take dan gani taji dama- dama,shima tunda ya kammmala katarunsa na jami'a kullum yana tare da mahaifinsa wurin harkar kasuwancin sa,rayuwar su na cike da kewa da wani walwala.</p><p> Mai musu aiki ce ta katse mata tunanin,'"Hajiya kna da bakuwa".</p><p> ""Wacece haka ? Daga ina take ?</p><p> Gata nan ." Ta bata amsa,sannan ta juya.</p><p> Bahijja tayi sallama tare da karasowa cikin falon, Hajiya ta amsa tana mata maraba tare da mta kallon rashin sani.</p><p>Bayan sun gaisa Bahijja ta kalleta,ta ce.</p><p>"Nasan zaki yi mamakin ganina,saboda baki sanni ba. Sunana Doctor Bahijja ,ni likita ce a asibitin da aka kai Deeni kwanakin baya,asibitin doctor Mislihu . Ni matarsa ce da muke aiki tare ,bayan rasuwarsa ni na ci gaba da kula da asibitin.</p><p> Kafin ya rasu burinsa ne ya ga ya taimaki Deeni,sai dai burin nasa bai kai ga cika ba ta Allah ta kasance akan sa. Ina fatan cika masa wannan burin don haka nake son taimakon Deeni da dukkan kokarina har dai naga ya samu lafiya.</p><p> Bama bukatar taimakon ki""""".</p><p> Sukaji muryar Alh. Kamar daga sama .</p><p> Dukkansu suka mai da kallon su kan Alhaji,ya ci gaba da fada.</p><p> "Yau ce rana ta karshe da zaki sake tako gidan nan ,kowa yasan irin yadda ku ka kara dagula rayuwar Deeni,ku ka yi wasa da lafiyar sa. Ku godewa Allah da banyi kararku ba.</p><p> Cikin sadda kai da girmamawa Bahijja ta ce.</p><p> "Alhaji dukkan mu ba wanda yaso abinda ya faru,kuma bamu yi haka da ganganba sai don wata kaddara da ta fada mana. Burin mu ne daga ni har marigayi maigidana mu ga muna taimakon mutane,haka taimakon danka yana daya daga cikin burin,don haka nake me rokon ka da ka kara bamu dama ,insha Allah zamu yi kokarin mu akan danka ya samu lafiya.</p><p> Alhaji dai ya dage Bahijja ma ta dage da kyar da kyar ta sha kansa ya yarda ,sai dai ta dinga zuwa duba shi har gida . Bata musa masa ba saboda tana son taimaka masa,don tasan an musu laifi ,sannan zata karasa abinda mijinta ya fara kamar yadda ya UMARCE ta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hajiya ce tayi mata jagora har zuwa bangaren Deeni,ta nuna mata kofar dakinsa. Nan ta cewa hajiya ta koma ita zata shiga. Hajiya bata musa mata ba ta juya,ita dai addu'ar ta Allah ya bawa danta lafiya.</p><p> Tura kofar dakin tayi wanda yake mamaye da duhu,duk da rana ce amma ya rife ko ina kif. Yanayin garin kuma dama inba a kunna wuta ko bude windo ba babu ta inda haske zai shigo. Hakan yasa ta kara bude kofar don taga haske,nan ma ta hango window din dakin.</p><p> Kai tsaye ta nufi window din ta sa hannu ta zuge labulen tare da bude (windows) din daki duka ,tuni haske da wani irin iska mai sanyi ya dinga ratso dakin,nan ta maida kallonta gare shi ,yana zaune tsakiyar gado kamar kullum ya hade kai da gwiwa yana kife wuri daya.</p><p> Cikin nutsuwa ta matso gare shi ta tsaya tana kallon sa tare da nazarin halin da yake ciki . Kamshin turarenta tare da iska mai sanyi ne suka soma ziyartar sa,wannan ya dawo da shi daga wata duniya da ya fada.</p><p><br /></p><p> Assalamu Alaikum Nuraddeen ". Ta fada cikin sassanyar murya.</p><p> Jin murya da bakon yanayi yasa shi dago kai suka hada ido,tayi masa murmushi ,shi dai kallonta yake. </p><p> Ta sake kiran sunansa,"Nuraddeen ,na maka sallama baka amsa ba,kasan kuwa shaidanun mutane ne kawai ba sa amsa sallama ? Kai kuma nasan ba ka daya daga cikin su,kai salihi ne,bawan Allah(you re a gentleman) nasan nan gaba in na shigo zaka amsa sallamata. Ni sunana Doctor Bahijja,amma zaka iya kirana da Bahijja . Ni sabuwar kawarka ce,abokiyar ka,naji baka da aboki haka kake rayuwa kai daya,nima bani da kawa don haka na cewa hajia me zai hana mu zama abokan juna ni da kai,? Ka fadamun damuwarka ,in fada maka nawa,mu bawa juna shawara. Ina fata zaka amshi abota ta ?</p><p> Kallonta yake fuskarsa daure,sannan da alamar mamakin ganinta duk da yana jinta amma bai kulata ba ,daga karshe ma ya kau da kai daga gareta saboda Allah Allah yake ta fita ta bashi wuri,saboda ba abinda yafi kauna irin ya zauna shi daya ya fada wata duniya daban wacce take da bambanci da wacce mutane ke rayuwa.</p><p> Ganin ya juya kai yasa ta sake zagayawa ta fuskance shi,ta ce.</p><p> " Hakan na nufin baka amince da abota ta ba? Duk da baka amince da ni ba ni dai ba zan fasa zama abokiyarka ba,saboda Niraddeen shj kadai ne abokin da nake so nayi a duniya,saboda daga ji da ganin Nuradden (is special) .</p><p> Zan fara aikina daga yanzu kafin ka amince,shawara ta farko ka dunfa barin ( freash air ) yana ratsowa cikin dakinka,zai baka (good company) kuma zai kara maka lafiya ( it will keep u healthy nd cheer you up).</p><p> Na biyu,ni bana abota da kazamai,wannan dakin da kake zaune cikin kura ga kayanka a zube (,toilet )dinka datti,kai baka gyara ba,sannan ka hana a gyara maka. To in kanaso mu zama abokai sai ka koyi tsabta,kasan mu likitoci bama shiri da kazamai,din haka ka tuna kai abokin likita ne." Tana maganar tana tattara dakin.</p><p> Ba shiri ya dazo kai yana kallonta,da ta ishe shi,yaji ranshi ya baci,ya mike a zuciye ya fisgi hijab dinta,yaja ta har kofar ya cillar ,fuska murtuk yace.</p><p> "" Waye abokin ki ? Bana son kowa,bana bukatar kowa arayuwata ,bana son kowa,ina so in rayu ni kadai,in kika sake zuwa nda nake zan kashe ki. </p><p> Bata yu mamaki ba ,dama ta zaci haka daga gare shi...</p><p> Murmushi ta masa,tace," Shi yasa nake son ka zama abokna,zan dawo gobe in Allah ya kaimu sai ka fada min damuwarka (and yes ) bana so in dawo in same ka da kazanta,ka tabbatar da kayi wanka."</p><p> Rufe kofar ya yi da kardi ,ta jima tana tsaye tana kallon kofar,yayin da kwakwalwarta ta shiga zarya tana tunanin ta hanyar da zata bullo masa har taja ra'ayinsa. </p><p> Alama ta farko ta nuna mata yana cikin fushi da zafi ,na biyu kuma kamar yana cikin wani fargaba. Na uku ,alama ya nuna ya yanke kauna daga dukkan wani farin ciki da rayuwar duniya. Wannan ya nuna rauninsa akan addini a zahiri.</p><p> Ta jima tana nazari kafin ta juya ta samu Hajiya tana kaiwa da kawowa alamar jiran fitowar ta kenn,tana ganinta kuwa ta nufi wurinta da sauri. " </p><p> ""Likita yaya kika ganshi :?</p><p> Bahijja tace,"kwantar da hankalinki Hajiya ,zauna zan miki bayani"".</p><p><br /></p><p> Ta ce,"Insha Allah Deeni zai samu lafiya,zai samu sauki. Sai dai sai na danyi fama da shi,saboda na lura mutum ne me zafin zuciya da zafin rai,sannan yana tattare da wani fishi da bacin rai a tare dashi...</p><p> Sannan akwai wani (memories)* a kwakwalwar sa da yake son shafe su,ya mance da su. Yana so ya shafe wani bangare na rayuwar sa a baya wanda suke masa ciwon gaske. A kokarinsa na wannan yasa kwakwalwarsa ta kamu da ciwo ,rashin lafiya. Ba wai hauka yayi ba,kamar yadda Kai, ko zuciya ,ko ciki suke yyiwa mutum ciwo a jikinsa, haka kwakwalwa ma tana ciwo wanda dole sai ya sha magani zai samu waraka da yardar Allah. Sannan kuma ya kaucewa wannan tunanin.</p><p> Na biyu ,matsayinsa na musulmi ya samu rauni,na uku, na lura yana da matsala da duk wata dangantaka a duniya wanda ya jawo yasa ya tsani kowacce irin dangantaka ,har yasa baya kaunar kulla dangantaka kowacce iri ce da kowa ,yafi so yayi ta rayuwa shi daya.</p><p> Don haka Hajiya deeni na bukatar taimako kwarai wanda zan yi iya kokarin nayi,sai dai ba mai sauki bane. Mutum ne mai taurin kai da zafin zuciya ,tankwara shi ko juya shi abu ne mai wahala. Ina son jin tarihin deeni kakaf da ainihin shigar sa wannan halin ,saboda in san ta ina zan soma bi in taimaka masa..</p><p> Hajiya ta ja dogon numfashi ta kalleta ido cike da tsammani ,tace.</p><p> "Zan fada miki komai,tabbas Deeni danmu ne amma bamu kyauta masa ba ,bamu masa adalci ba. Zan baki dukkan wani hadin kai da kike nema domin inga dana cikin walwala............</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Please nagaji wlh ,,kuyi hakuri se da safe............</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>38</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Deeni mutum ne wanda yake (full of life)kullum yana cikin dariya da zolaya gami da kyautatawa kowa,duk da yana fmda zafin rai yana da zuciya da fushi da kuma ra'ayi amma yana wuyar gaske ka fahimci haka,saboda kullum yana cikin wasa da dariya.</p><p> Duk wani abu da deeni yake so mu ba shi muke so masa ba,don haka muka sa shi yin abinda muke so musamman mahaifinsa ya danne abinda yake so yana yin abinda muke so saboda biyayya. Sun sha samun sabani da mahaifinsaakan abu da yawa ,amma daga karshe zai hakura yayi abinda mahaifinsa ke so.</p><p> Deeni bashi da rauni a addini,asali ma sanin addini yasa shi yi mana biyayya duk da mun fi ba da karfinmu ga neman ilimin duniya shi da kanss ya dage da neman lahira,don haka anan mu muke da rauni ba shi ba.</p><p> Ya yi amfani da iya ilimun da ya nemawa kansa na addini ,yana kokarin neman ilimin ne kuma muka raba masa hankali tare ds daga masa hankali akan karatun jami'a ,din haka ya qatsar ya koma bokon.</p><p> Raunin Deeni guda daya ne a rayuwa FARIDA."</p><p> Sai a lokacin Dr. Bahijja ta ce wani abu tunda ta fara magana ,ta ce.</p><p>"Farida ?""</p><p> Mama ta girgiza kai ,tacd ,"kwarai farida,in akwai abinda Deeni yake so a rayuwa da muradi a rayuwarsa to farida ce. Dukkan ZURI'AR mu ba wanda bai san da haka ba,tun yana yaro har ya girma ya mallaki hankalin kansa,abinda yake so daya ne Farida,ita ce rauninsa..........</p><p><br /></p><p> A hankali Hajiya ta labarta komai tun daga farko har karshen abinda ya faru.</p><p> Bahijja taji jikinta ya yi sanyi,ta matukar tausaya masa sosan gaske.</p><p> "Allah sarki bawan Allah." Ta fada tana kallon mama .</p><p> " Tabbas ba ku kyauta masa ba ,mahaifansa ,dan uwansa da masoyiyyarsa,tabbas wannan cin amana ne mai girma,dole ya ji dukkan wata dangantaka ta fita ransa.</p><p> Tabbas ya yi kokari ma da ya tsaya a haka,Deeni jarumi ne,na jinjna masa,kuma Nsha Allah zan taimaka masa ya fito daga cikin wannan kejin ya zo yayi rayuwar sa kamar kowa.</p><p> Kila da mutuwa farida tayi,zai iya daukar kaddara ya jure, da farida ce masa tayi Deeni bana sonka wani zan aura zai jure ya hakura,amma wannan abinda ku ka masa ya masa ciwo wanda ciwon da cin amanar shi yafi zama a zuciya da kwakwalwar sa fiye da Farida.</p><p> Yana jin cewa iyayensa basa son sa,ba sa kaunar sa,sun ci amanar sa. To in iyauenka za suki ka su ci amanarka zaka dinga jin to kai ina zaka shiga ? Ya zaka yi da rayuwarka ?</p><p> Abinda ciwo matuka,zaka iya jure tsana da kiyayyar kowa amma ban da mahaifanka,saboda mahaifanka ,'yan uwanka su ne kai,su ne rayuwarka.</p><p> Abinda Deeni yakeji, ciwon da ke cikin cikinsa da ni daku duk ba zamu iya sani ko fahimta ba sai shi sai Allahnsa. Ina fata Allah Ubangiji ya bashi lafiya,ya bani iko da taimakon iya taimaka masa,ya cire masa wannann ciwon da ke zuciyar sa."</p><p><br /></p><p> Ta mike ,'Ni zan wuce ,zan dawo gobe in Allah ya kaimu . Sannan zan ci gaba da bincike akansa daga gare ku,da fatan zaku bani hadin kaii""</p><p> Mama dake sharar kwalla ta ce,"insha Allah za muyi duk abinda ya kamata ,mun gode "</p><p> Nan sukayi sallama ta tafi.</p><p><br /></p><p> Alhaji dake tsaye yana jinsu hankalinsa ya matukar tashi,tsananinnadama ya kara shigarsa,tausayin dansa ya kama shi. Ya iso falon hankalinsa a tashe ,ya kalli hajiya.</p><p> " Ki yafe mun abinda na miki ,abinda na yiwa danmu ban kara fahimtar illar da na yiwa yara na ba sai yanzu.</p><p> Hajiya tsayawa tayi tana kallonsa,don kuwa a tsawon shekarun da sukayi na aure bai taba budar baki ya bata hakuri ba komai girman laifin da ya mata,haka bai taba nadama akan wani abu daya zartar don ra'ayinsa ba ....</p><p><br /></p><p> ***** ***** *****</p><p> </p><p> Washegari karfe sha daya ta nufo gidan,bayan ta gama zagaye marasa lafiya a asibiti.</p><p> Kamar yadda ta same shi jiya haka ta sake samun sa a yau,hannunta rike da tray.</p><p> " Asslamu Alaikum Nuraddin"</p><p> Dago kai yayi ya kallera ya watsar,ta kalle shi ta girgiza kai..</p><p> *Ka.manta me nafada maka jiya? Ka dinga bude (window) ,kaga yau ka kara min aiki,dole in dinga zuwa bude maka (window ) tunda ina son abokina ya shaki iskar duniya.""</p><p> Nan ta zage komai kamar jiya ,sannan ta zo ta hada (coffee) ta mika masa. Ko kallonta bai yi ba balle ya karba,ya dage kai...</p><p> Bata hakura ba ,"kayi kokarin sha (I'am a very good coffee marker ).oh na gane ,ko sai na sa maka a baki ne ?</p><p> Nan tayi kokarin kai cup din bakinsa,ya yi saurin doke hannunta sai da cup din ya fadi kan tiles ya kashe har ruwan coffee din ya dan kona ta.</p><p> ""Auchhhh!!! Tayi kara.</p><p> '"" In ba zaka sha ba meye na bigewa ? Kaga yanzu ka kona ni, ( u re such a bad friend ) ""</p><p> Har yanzu bai kulata ba,nan ta hau tattara glass di. Da ya fashe,bata ankara ba kuwa ya yanke ta. Ga mamakinta ta ga ya mike ya dauko (first aid box ) yayi dressing wurin ..</p><p> Ra jima tana kallonsa tana mamaki ,saboda bata zaci hakab ba.</p><p> Ya kalleta fuska a murtuke ," Wai me kike so ne gare ni ? Na ce miki bana son ganin kowa a inda nake,bana bukatar wata DANGANTAKA !!!!</p><p> ya fada cikin tsawa da huci..</p><p> Kinji ciwo saboda ni,ban so,don haka kar ki sake kuskuren zuwa inda nake.""</p><p> Da karfi ya fisgeta zai yi waje da ita ,sai yaji kansa yana wanj irin sarawa ,yana masa azabar ciwo . Nan ya saketa ya rike kai yana nishin azaba tamkar mai shirin barin duniyar....</p><p> Hankalinta ya tashi ,tayi saurin ciro wasu allurai guda uku a cikin jakarta tayi masa a hannu,ta taimaka masa zuwa gado ya kwanta,bacci mai karfin gaske ya dauke shi. Ta jima tana zaune tana kallon sa cikin damuwa da tausayawa,sannan ta mike ta karasa abinda take yi a dakin ,sannan ta fita.</p><p><br /></p><p> Haka Bahijja ta kasance kullum sai ta zo gidan du Deeni duk da baya son hakan,baya kulata,haka zata yi ta masa surutu tana masa hira,har ya soma sabawa da hakan.wataran cikin dabara zata dinga jefa masa magani cikin (juice) ko abinci.</p><p> Ganin har yanzu bata samu yadda take so ba tsawon qata uku amma Deeni ba shi da niyyar canjawa,don haka tayi niyyar sake canja salo,ta cewa hajiya tana son zuwa har kaduna gidansu Deeni inda ya zauna da inda ya yi rayuwa ,sannan tana son ganin farida don mata wasu tambayoyi akan deeni.</p><p> Hajiya tace,'Da zai yiwu da na rakaki,to amma ba inda zan iya rafita in bar Deeni,don haka zan yi waya in sanar da su Shamsu zuwanki,zan baki cikakken (address) ba zaki fuskanci matsala ba insha Allah ".</p><p> Ta mike ,"Na gode Hajiya da yarda da kuma hadin kai da kike bani."</p><p> Hajiya tayi murmushi tace ," Nice da godiya,ba abinda zan miki sai addua,Allah ya ska miki da lakhairi"".</p><p> Sn rabu akan zata yi kwana biyu kafin ta dawo...</p><p><br /></p><p> **** ***** ****</p><p><br /></p><p> Kwance yake yana ta juye-juye a gado ,ya rasa me ke masa dadi,tun dazu yake sauraron zuwanta amma shuru. Ya riga ya saba da tana zuwa kullum dai dai wannan lokacin,amma yau har yamma shuru..</p><p> Nan ya mike ya zuge labulen dakin kamar yadda ta saba masa,nan ya dinga kaiwa da komowa . Can ya bude kofar dakin ya fita abinda ya jima bai yi ba tunda ya dawo daga asibitin yana nan a cikin dakinsa.</p><p> Hajiya na tare da Alhaki a falon kawai sukaga Deeni bazata yana leke-leke ,a tare suka mike cikin mamaki ...</p><p> " DEENI" </p><p>Suka kira sunansa a tare.</p><p> Ya kalli Hajiya yace ,"Mama ba wadda ta zo gidan nan yau?"</p><p> Kallon sa take da mamaki ,ta jima sosai rabon da taji Deeni ya kirata balle.magana,kuka zatayi ko dariya? Ta rasa.</p><p> Bai bata amsa ba ya koma ciki ya tuea kofa ya kwanta,kwanciyar da yaji bata masa dadi ba ,ya mike ya nufi bakin window ya tsaya yana kallon motoci dake wucewa bisa titi..........</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Se anjima jama'a </p><p><br /></p><p>Taku har kullum...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv 😍😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SAADATU WAZIRI GOMBE </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>ASTAGHFIRULLAH WA'ATUBU ILAIK</p><p> Allah kayafe mana kura-kuranmu,,,,Ameen </p><p> </p><p> </p><p>39</p><p><br /></p><p> Zaune take a falo tana jiran isowar masu gidan,yayin da take kallon yadda aka tsara ginin gidan da yadda aka tsara falon.</p><p> Farida ta iso tare da 'yan yaranta guda biyu suna ta tsalle-tsalle Deeni karami da Aisha,ta tarbi Bahijja cikin fara'a ,itama ta amsa tana daria ,suka gaisa.</p><p> Deeni karami ne ya gaisheta,ta amsa tare da jawo su tana musu wasa da dariya ,tana tambayarsu makaranta suna bata amsa.</p><p> Farida ce tace,to maza a je ciki ayi wasa a barni zanyi magana da Aunty ko?</p><p> Nan sukayi ciki sannan ta maida kallon ta ga Bahijja tace,</p><p> "Hajiya tamun bayanin zaki zo,sai dai bata fada mana ko mene ne ba "</p><p> Bahujja tayi murmushi tace," Abu me muhimmanci ke tafe dani,sunana Doctor Bahijja,kamar yadda na fada miki ni likitar Deeni ce.</p><p> Jin sunan Deeni yasa fatida taji zuciyarta ta tsinke,hankalinta ya tashi. Nan da nan Bahijja tayi mata murmushi.</p><p> Keantar da hankalinki,ba wani abu me wahala yake tafe dani ba,illa iyaka inaso ki tainake ni in taimaki Deeni. Inaga wannan shi ne iya abinda zaki iya masa ki taimake shi shima yaci gaba da rayuwa kamar yadda kika ci gaba da naki rayuwar.."</p><p>Kanta sunkuye jiki ba kwari tace,"A shirye nake da in baki ko wani irin taimako ,zanyi farun ciki in har akwai taimakon da zan iya wa Deeni."</p><p> Bahijja tace ,"Naji dadin hakan ,ina so ne ki fada min komai akan Deeni ,ina nufin ,halayyarsa,me yake so ? Meye baya so ? Banda wanda nasani ,a ganina kece mutum mafi kusa da Deeni,wacce tasan kananan abubuwa akansa wanda wasu ba za su sani ba. Komai ina son sani,me yafi sashi farin ciki,? Ya yake rayuwar sa? Kamar ( hobbies ) dinsa ,wane abinci yafi so ? Wanne yanayi yafi so? Me yafi sa shi nishadi da farin ciki ?</p><p> Farida tayi shuru ta fada duniyar tunani ,rufe ido tayi tana tuno komai a game da shi,tana tuno wasu yanayi da suka yi tare a da.</p><p> Ta bude ido jikinta a sanyaye tace,tashi mu shiga ciki"</p><p> Nan ta ja ta sama zuwa bangaren da Deeni yake ,ta bude mata dakinsa,ta kunna wuta haske ya bayyana ,ta ce.</p><p> Ga dakin Deeni wanda ya shirya shi da hannunsa,ina ga ganin wannan ko ban fadi ba zai fahimtar dake ko wanene Deeni.</p><p> Bahijja tayi murmushi tace,"Kwarai ddakinsa ta bayyana shi a zahiri,daga (study room) dinsa na fahimci Deeni mutum ne me son karance-karance."</p><p> Farida tayi dariya,"Kwarai yana son karance-karance da binciken takardu tin daga kan na Addini har na boko.</p><p> Deeni ma'abocin ilimi ne ,ma'abocin soyayya. Yana samun farin ciki a kananan abubuwa,mutum ne me son zama cikin dabbobi,tsuntsaye da son kiwon su.</p><p> Deeni yana son (spat) yana son (swimming),yana matukar son MISBAH da labaransa"</p><p> Ras! Ras!! Ras!!! Bahijja taji gabanta ya fadi,ta maimata </p><p> **MISBAH**</p><p> Ta tambaya cikin mamaki.</p><p> Farida ta girgiza mata kai ,'Kwarai MISBAH (the author )wannan marubuci Deeni yana sonsa da labaransa. (Ideologies ) dinsa suna matukar burge Deeni,a kullum in munyi fada da Deeni to akan littafin MISHAB ne ,har na dauki littattafansa kishiyoyina saboda ba abinda ke dauke hankalinsa daga gareni sai takardun MISBAH.</p><p> Tana maganar tana bude mata wani drowar dake cike da takardun MISHAB,gaba daya ba wanda bashi da shi,daga na hausa har na turanci,daga na labari har na addini.</p><p> Shuru tayi tana jnjina soyayyar da yakewa takardunta,ko ita bata da wasu copies na takardunta sai dai original dake cikin computer dinta.....</p><p> Lafiya Doctor ??;</p><p> Farida ta katse mata tunani.</p><p> Ta girgiza kai,,"Ba komai""</p><p> Farida taci gaba ,"Deeni yana son rayuwa mai sauki,haka nan yana son ganin ya taimaki marasa karfi. Deeni bai dauki rayuwa da zafi ba""</p><p> Magode kwarai da wannan bayanai naki da hadin kai da kika bani."</p><p> Farida ta kalleta ,(please ) likita ki taimake shi""</p><p> Bahijja ta girgiza kai,"Nsha Allah.</p><p> Bahijja bata bar gidansu farida ba wanda ainihin cikin gidan su Deeni suka dawo tunda zuka koma lagos,sai da ta sa Bahijja taci abinci tayi wanda da sallah sannan suka rabu.</p><p> Bahijja ta gama abinda take a garin kaduna ,washegari ta hau jirgi ta koma lagos,tare da sake sabon shiri wa yadda zata tafiyar da Deeni.</p><p><br /></p><p> Asslamu Alaikum"</p><p> Ta fada lokacin da take kutsa kai cikin dakin .</p><p>Yana tsaye bakin window bai juyo ba,ta karasa dab da shi.</p><p> " Deeni sallama nake "</p><p> Nan ya juyo ya kalleta a yatsine ya watsar , sannan ya amsa ciki -ciki .</p><p> Tayi murmushi,yau ce rana ta farki da ya amsa sallamarra.</p><p> Tayi murmushi ,a ranta tace,"Wanann akwai son nunawa mutane isa."</p><p> Gado ya nufa ya kwanta,ya juya mata baya. Ta matsa kusa da gadon.</p><p> Deeni abokina ba gaisuwa ? Ko fishi kake dani ne ? Sorry "</p><p> Ta kama kunne,"Na tafi na bar abokina ,to ai ba laifina ba ne,in na zo baka kula ni,baka jinm maganata,ba ka taya ni aiki,shi yasa na dai na zuwa. Ina zaune yau a gida sai mind dina ya dinga fada mun Deeni abokina yana missing dina ,kuma gashi na zo ka juya mun baya..""</p><p> Duk surutun nab da takeyi bai ce mata kala bahar ta gaji ta kyale shi,can ta canja salo. </p><p> Naji labarin abokina ma'abocin son karance-karance ne,ko zaka iya fada min waye (favourite author ) dinka?</p><p> Har yanzun bai kulata ba,nan ta mike ta bar inda yake ta zauna kan kujerar dakr dakin,ta jawo jakar data zo da shi tafara ciro littattafan da ke ciki tans dubawa,har yanzun ya juya mata baya. Waya ta dauko tayi kamar tana magana.</p><p> '"Naga kun samin sabbin littattafai har wanda bana karantawa,wa ya ce kusa min littafin MISHAB? Ni bana son karanta labarinsa,yabi ya ishe mu da labaran rikicin rayuwa ,duk labaransa na bakin ciki shi kullum sai wahalar da mutane ,kullum yana hada mutane da matsaloli.</p><p>In soyayya ce ma yayi ta wahalar da su,mutm ba zai samu wanda yakeso ba." Tana maganar tana satar kallonsa.</p><p> Gani tayi ya juyo ya mai da hankalin sa kanta gaba daya,ganin ya mai da hankalinsa gareta tasa ta ajiye wayar ta juyo da sauri suka hada ido,ya yi saurin kau da kai.</p><p> Tayi dariya ta mike ta matso kusa da shi hannunta rike da littafin .</p><p> "Kasan labaran marubucin nan kuwa ?</p><p> Ya dago idanunsa ya tsareta dasu,"kar ki sake""</p><p> Ya fada yana kallonta har ta so ta rikice,akwai wani abu a muryar sa mai sa a saurare shi,kuma ayi yadda yake so. Zai iya controlling mutum da muryar sa kawai wanda za mu iya cewa baiwa ne da Allah ya yiwa Deeni.....</p><p> Tayi saurin cire idanunta cikin nasa,tace.</p><p> " Kar in dake me ? </p><p> *Zangin (best author ) dina MISHAB . Dazu kin tambayame ni waye beat writer na,to MISBAH NE"</p><p> Ta dan yi murmushi tace,"Ai ba zaginsa nayi ba,gaskia na fada"</p><p> Ba gaskiya bane,me kika sani akan rubutun MISBHA ?</p><p> "Fadamun ina son sani."</p><p> Haka nan yaji yana son biye mata,yace.</p><p> "Ba zan fadi ba sai dai in kina so mu zama abokai kamar yadda kika nema ki dauko sabon littafin da kika ce ya yi sabo ki karanta mun,saboda yanzu ina da ciwon kai ba zan iya karatun ba. Kinga kema in kin karanta za kiji wani darasi ne dabirin (logic )hikimar da ke cikin rubutun sa."</p><p> Tayi murmushi,"Me zai hana ? Zan karanta maka ,amma ba don mu zama abokai ba,,saboda na riga na zama abokiyarka tun tuni. Sharadin karanta maka labarin MISBAH shi ne,zaka dinga jin maganata,zaka dinga fada min damuwarka,sannan zaka yarda in dinga duba lafiyar ka"""</p><p> Lafiya ta ? Ya tambaya yana kallonta.</p><p> "Ban fada maka abokiyarka Bahijja likita bace? Kuma na lura abokina baya cikin koshin lafiya,kamar ciwon kanka,inka bani hadin kai cikin kankanin lokaci zamu yi maganin sa. Sannan kana fada min damuwarka in baka shawara ,kaga riba biyu ,yi sauri ka amince ,yi sauri ka yarda..."""</p><p> Kallonta yake yana mamakin ta,ita ko wace iri ce ? Bata fushi bata gajiya da magana,duk da baya kukata ba ta gajiya da duj halin da ya nuna mata,gashi har ta koya masa ya saba da ita da halayyarta.</p><p> Zura masa ido tayi tana kallon sa,'Ina sauraron amsar ka""</p><p> Bai bata masa ba sai jan pillow da tayi ya hadasu waje daya yayi matashi dasu,ya dago kansa tare da dora kafs daya kan daya. Ya kalleta yace.</p><p> "Ina jin ki"</p><p> Tayi murmushi,'inason (style ) dinka da (attitude ) dinka ""</p><p> Tayi saurin ciro wani card da biro a jakarta.</p><p> ". Samin hannu mana (autograph)in zama mutum ta farko saboda nan gaba in ka fita kana yiwa 'yan mata wannan halin zasu haukaxe akan ka,kasan "yan mata na son namiji mai aji (classic tall ,handsome) sannan ga (attitude);yana musu jun kai yana shan kamshi,maganaa ma tsada take masa,yanzu zan zo ince in suna son zuwa kusa da kai to su zo ta wajena,saboda ni abokiyarka ce,ta hannun damarka,har (Autograph )dinka ina dashi. A lokacin ni zan zaba maka irin matar da ta dace da (personality ) dinka ,wacce za ku dace,zata haifa maka (cute cute little angels)"</p><p> Tsayawa yayi yana kallonta kamar wata t.v,yana mamakin ra.</p><p> Cikin tsawa da daga murya yace ,"Zaki karanta ne ko a'a ? Na rasa wane irin tunani ne dake"</p><p> Ta harare shi,kai ,karfa kaga na ce ni abokiyarka ce ka nemi ka raina ni,ni yayarka ce,na girmeka (at least respect my age) ka daina min tsawa "" </p><p> Juya mata baya yayi ya kyaleta,dariya ma ta bashi,ya hau murmushi shi daya...........</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>RAF. RAF. RAF </p><p>👏🏼👏🏼👏🏼👏🏼👏🏼👏🏼👏🏼👏🏼👏🏼👏🏼</p><p>A tafawa MISBAHA ,tasa deeni murmushi wanda ya rasa shi tsawon shekaru har ya fidda tsammani da kuma yin sa...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv 😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>40</p><p><br /></p><p>Juya mata baya yayi ya kyaleta, dariyq ma ta bashi, ya hau murmushi shi daya. </p><p>Lekashi tayi tace, "laa ! murmushi nake gani a fuskarka ? Amma shan kamshin nan yafi maka kyau, gaskiya zaka daina murmushi kar ya bata maka kwatancen ka na (Mr. Attitude).</p><p>Karamin pillow dake gabansa ya dauka ya wurgeta dashi, tai saurin cafkewa tana dariya tace: "to tsokanar ya isa lokacin karatu yayi". Nan ta dauko wasu littattafanta ta fara karanta masa. Ya juyo ya kalleta, "sabon littafin MISBAH".</p><p>Nan tahau 'yan kame-kame tana zare ido, ka bari wannan sai gobe, bari in fara maka da wani. Ban so, ya fada kai tsaye sai kin fara wannan. Sai tace naji (Mr. attitude). </p><p>Nan ta dauko wani littafin da tayi BALLE ta karanta masa, don haka kawai ta juya masa baya ta fara kirkiro masa sabon labari a lokacin, saboda duk littafin da zata karanta masa nata ya sani, kuma ba yadda za'ayi ta karanta masa labarun wasu tace nata ne, don haka tai dabarar kirkira ta hada masa labari a lokacin. </p><p>A hankali yaji labarin na ratsa shi yana taba zuciyarsa, yaji yana sashi nishadi, baisan yaushe ya juyo ba ya samata ido, dukda ta bashi baya, ya lumshe ido yana sauraronta. Dr. bahijja na ta kokarin hada labari kiran Sallah ya katsesu, tayi godiya ga Allah ta juya ta kalleshi. Lokacin Sallah yayi. Ya bude ido kinyi alkawarin ci gaba ? Ta girgiza kai, amma bayan ka dawo daga masallaci. </p><p>Mikewa yayi ya fita daga dakin ya nufi masallaci, sabanin da da yake sallah a daki. </p><p>Fitar sa ya bata damar gyara gadon, da kade kurar da take gadon, ta tattara dakin sannan ta fita ciki tayibdakin am don yin sallah. </p><p> Mama tasa aka kai masa abincinsa dakinsa, yayin d suka zaunanda Bahijja sunanhira wanda duk ya kare akan rashin lafiyar Deeni ne da irin canjin da aka samu sosai a tare da shi. </p><p> Deeni ya dunga kaiwa da kawowa cik8n dakinyqnq jiran dawowar Bahijja a haka ta same shi. </p><p> " kaci abincin kuwa ? </p><p>"sai kin karasa mun'"</p><p>Ta nade hannu, sai ka ci abinci"</p><p> " Banzan ci ba.. "</p><p> "Nima bazan karasa ba " </p><p>Nan ta bude abincin ta zuba nasa ta mika masa, karba yayi da karfi yana ci. </p><p> "Bi a hankali, karka kware, bakasan cewa akwai (manners) na cin abinci ba ma ? " </p><p>"Ban sani ba mana na, sai kin fada mun".</p><p>Ta girgiza kai,"za dai ka iya kirana yayarka amma banda mamanka".</p><p> Murmushi yayi ya girgiza kai, ya kyaleta har ya gama cin abincin ya mika mata. </p><p> Tayi daria, (good boy) ,"Karbi magani kasha"</p><p> Bai musa mata ba saboda burinsa taci gaba masa da labarin da ya tsaya masa a rai, yayinda Bahijja ke tunanin ta ina zata fara karasa masa ? Haka dai ta zauna tana hado labarin tana jan ransa har bacci mai karfi ya fizge shi alamarmaganu da yasha ya fara aiki ,ta kimtsa dakin ta tattara jakarta (box) din maganunsa ta adana waje guda, tazo fita ta tsaya tana kallonsa. </p><p>"Ina tayaka murna da sabon canji da ka soma samu a rayuwarka, na fahimci kai mutum ne mai kirkin gaske da saukin kai duk da zafin zuciyarka".</p><p>Sau da dama Bahijja kan debewa kanta kewa ta hanyar hidimar Dini da asibiti wanda ta lura suna taimakon juna ne ta sami abuda ke debe mata kewa, ta mance damuwarta da kuncin da take tsintar kanta na dan wani lokaci, yayin da inta koma gida da dare ne komai ya zam a mata sabo, soyayyar mujinta da danta ya dawo mata sabo. </p><p>A haka kullum Bahijja ke yi da Dini, har timetable na karatu ta sa musu, in sukayi karatu na addini kamar Alqur'ani da sauran takardu, sai tai ta kokarin hada masa labarin da take kirkira, daga nan sai shawarawri ya biyo baya. Cikin dabara da hikima da kwarewa irin nata ta ringa masa (brain therapy), tana bashi addu'o'i da magani na asibiti da Islamic medicine kamar su habbtis sauda da zaitun da makamantan su, tana bashi shawarwari masu amfani da misali kalakala. </p><p>Haka nan cikin dabara ta dinga dangana labarin da take masa na kirkira da labarin rayuwar sa, a hankali ta dinga saita tunaninsa har ya soma manta damuwarsa da bacin ransa. Ya tsinci kansa da rungumara sabuwar rayuwar da ya tsinci kansa, wacce yake jin dadinta. Kana ganinsa za kaga alamar sauki atre dashi, saidai a duk lokacin da yaga mahaifinsa ko yaji sunan dan'uwansa Shamsu yakan tsinci kansa cikin bakin ciki da damuwa.</p><p><br /></p><p> Kamar kullum yau da ta shigo ta samu yayi kaca-kaca da jakar takardunta da suke karatu yana ta bincike..</p><p> " Meye haka Deeni? Me kake nema?</p><p> "Naji sauki ne nake neman littafin da kike karanta mun na MISBAH in karanta,meye sunan labarin ma ?</p><p> Ras !! Taji gabanta ya fadi.</p><p> Ya tsare ta da ido,"Ina littafin ?</p><p> Tayi saurin kau da kai ,xBan sani ba,don kawai kana neman littafu sai ka wargaza mun kaya? To sai ka tattara."</p><p> "Bazan tattara ba." Ya bata amsa kai tsaye. </p><p> Ba zan tattara ba ,kuma sai kin bani littafin nan."</p><p> In naki fa ?</p><p> 'In kinki yau bazaki fita a dakin nan ba".</p><p> Hannu yasa ya daddanna (password) din kofar.</p><p> "Ba zaki fita ba sai kin bani"</p><p> *Deeni ""Ta fada cikin zare ido.</p><p> "Baka da hankali ne ?</p><p>"Bani dashi "</p><p>"Please ka bude "</p><p>" In kina son tafiya ki bani.</p><p> Ya juyo ya kalleta ,"Kar ki damu ba abinda zan miki ,ni kanunki ne."</p><p> Nan ya dare gado ya hau ya juya mata baya tana ta masa masifa amma bai sairareta ba.</p><p>Nan tayi ta kokarin daddanna numbers din tana kokarin canka,yace.</p><p> In kika yi sau uku ba dai dai ba to ko ansa na dai dai din ma bazai bude ba,kinga zama daram ni dake (my sweet)yaya." Ya fada cikun zolaya.</p><p> Nan ta hau masa magiya har yamma ,tace masa ta tafi da littafin gida ta manta ,gibe zata kawo masa.</p><p> Nan ma bai kulata ba ,nan fa ta hau lallaba shi tana lallashi,duk wannan bai yi aiki ba.</p><p> Ta ce,"Deeni in na tafi fa ba zan sake zuwa ba,ka manta sharadin mu zaka dinga jin magana ta ??"</p><p> Ya juyo ya kalleta,"Maganar ki wanne ne banji ba ? Na sha magani,na ci abinci irin wanda kike so,na sa kaya irin wanda kike so,na saurari shawarwarinki ,kullum muna karatu tare sannan yanzu mu abokai ne ,surutun da banayi kinsa na fara magana ,tun banaso har na fara so,menene baki sani nayi ba Doctor Bahijja...........Oops Abokiyata Bahijja?</p><p> Ta daka masa harara ,"Akwai abinda ya saura baka yi ba,shi ne kunce abotar mu,daga yau na daina abotar ,kuma ta window zan fita kaje ka nemi wata abokiyar ta karanta maka labarun ,don ba zan baka littafin ba ,kuma ko ina zaka shiga ba zaka samu ba.""</p><p> "Me yasa?</p><p> Ya bata amsa,,"saboda ke ce MISBAH da zaki hana ni ko kuma zaki boye mun labarin. Sannan batun neman wata abokiyar bazan iya ba,saboda ko bakomai a tare da ke akwai muryar da take taba min zuciya in kina karanta min labarin, don kuwa ko shi MISBAH da ya rubuta labarin in yaji yadda kike karantata shi da dukkan (feelins) dinki da (emotions )dinki zai ji kamar ba shi ua rubuta ba.</p><p> Sannan batun fita ta window kuwa Bismillah,iyakaci kugunki da kafarki daya ta karye,iyaka ta in sai miki ayaba da lemo"".</p><p> Harara ta galla masa,ta kuwa nufi window gadan-gadan zata fita ,ya yi saurin fisgota fa rigarta.</p><p> Ta daure fuska ,"Ka kyale ni""</p><p> Zuwa yayi ya bide mata kofar ,"Fita,kin kira kanki da abokiyata amma ba zaki iya daukar wasa da nake miki ba.""</p><p> " Eh bana son irin wanan wasan. ""</p><p> Nan ta sa kai ta fice ,ya lura ranta ya baci,sam baiji dadi ba.</p><p><br /></p><p> Kwana uku Bahijja bata zo ba,Deenj ya rasa me ke masa dadi? Ya samu sabuwar rayuwa tare da ita da (company) dinta.</p><p> Hankalin sa ya matukar tashi da rashin ganin Bahijja ,ya kasa hakuri har sai da ya tamvayi mama ina ne gidansu ne ? A wanne asibiti take aiki ?</p><p> Mama ta kalle shi,Deeni kenan yanzu duk zuwan da Bahijja yake gidan nan baka taba tambayarta ita wacece ko daga ina take ba ?</p><p> "Mama ki ban amsa." </p><p>""Nima ban sani ba ,sai na bincika. Zan tambayi mahaifinka""</p><p> Ranshi ya baci,ya juya ya koma ciki. Wanan ya bata damar yowa Bahijja waya ta fada mata halin da yake ciku.</p><p> Bahijja tace,""Mama ina ga lokaci yayi da Deeni zai soma zuwa asibiti yana shiga cikin ajin da muke musu (lecture da ba da shawarwari,ya kamata ya fara shiga mutane. Munyi mai wuyar,kiris ya ragewa Deeni. Kafin ya samu waraka sai ya dai na kebe kansa a gefe......</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wannan kenan </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv ce dai har kullum😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Assalamu Alaikum </p><p> Gaskiya ina matukar jin dadin yadda jama'a da dama ke binmu da nuna jin dadin wannan labari,hade da qara min kwarin gwiwa,da addu'o'i da nake samu,duk da wasu sun san cewa bani na rubuta ainahin labarin ba..........👏🏼👏🏼👏🏼👏🏼</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>42</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bahijja tayi kokarin janye kanta daga gidansu Deenj saboda tana gani lokaci yayi da zata janye daga gareshi,yanzu ya sona dawowa hayyacin sa. Abu kalilan ne ya rage masa yawan nasiha da masa tuni akai-akai, don haka ta bada shawarar in yana zuwa daukan darasi a (couselin center ) dinsu zai mike.</p><p> </p><p> Mama ta same shi a daki ta mika masa (address)din su Bahijja,ta lura yana cikin damuwar rashin zuwanta,tabbas Bahijja tayi tasiri a rayuwar Deeni.</p><p> </p><p> Tunda ya karbi (address) din yake tunanin yaje ko a'a ? Haka zuciyar sa da kwakwalwarsa suka dunga tun zura shi da ya je.</p><p> Washegari ya shirya ya fita,tunda ya shiga wurin kwakwalwar sa ta dinga tunano masa da abunda ya faru. Hankalinsa yaji yana tashi, yaji kamar ya koma,ya tsaya shi dai bai shiga ba shi bai fita ba.</p><p> Wani ma'aikacin wurin ne ya masa magana.</p><p> "Malam wa kake nema ? Ba a tsayawa a nan,ko shiga ko fita"".</p><p> Deeni ya kalle shi ya mika masa hannu suka gaisa,sannan yace.</p><p> "Ina tambayar Doctor Bahijja ne ""</p><p> Mutumin ya kalle shi yace,"Madam tana can bangaren koyarwa ,tana cikin aiki amma ka jira in ta gama zan mata magana,in kuma kana sauri sai ka dawo gobe da wuri kafin ta fara aiki.</p><p> Deeni yace ,"In ba zaka damu ba ka raka ni zuwa inda take sai in jirata a can"".</p><p> Tare suka jera da mutumin zuwa ciki,suna fatiya yana kalle-kallen yadda wurin yake,da irin jama'ar da ke zarya a wurin.</p><p><br /></p><p> (Hall) ne dan madaidaici cike da majinyata kuma dalibai,Bahijja tsaye gaban su tana ta bayani,tana ilmantar da su tare da wayar musu da kai,su kuma suna mata tambayoyi tana basu amsa,yayin da ta dinga binsu daddaya tana tambayarsu matsalolinsu suna fada mata tare dsmusu misalai da mutane daban-daban. Wani lokaci takan koma tarihin Annabawa,Sahabbai da manyan bayin Allah da irin gwagwarmayar da suka sha a rayuwa. Don haka ba wani bakin ciki ko bacin rai da zai saka tsayawa da rayuwarka bayan kana da Allah da addini,kuma Allah ya baka yadda zakayi in ka koma ga Alkur'anj ,sannan zaka ga kai baka da matsala ma kan tasu ko na wasu.</p><p> Allah ya mana kyautar rai da lafiya ne don mu bauta masa,don samun rabo duniya da lahira,ba zamu samu wannan babban rabon ba sai mun kula da kanmu da lafiyarmu,sannan muji dadin kyautata idar mu.</p><p> Nan ta basu addu'o'in da za suyi na cikin Hisnul muslim,wanda yake cike da azkar din da Annabin mu yayi,kuma ya yi umarni da a yishi.</p><p><br /></p><p> Deeni ya harde hannu a kirji yana tsaye ya kwanyar da kai yana jin ta da saurarenta,maganganunta na ratsa shi. Hikimar ta na iya zance da iya fahimtar da mutane ya burge shi,iliminta da fahimtar ta yasa shi jin wani sauyi.</p><p> Ya zura mata ido yana kallonta yana murmushi,wai da wa wannan likitar ke masa kama ? Yanayinta,koyarwarta,hikimarta akwai inda ya sansu.</p><p> Kamar da wasa ta juyo sukayi ido biyu,ta hango shi tsaye gabanta. Nan ta dage kai kamar bata ganshi ba.</p><p> Murmushi yayi ya kutsa kai ajin ,ya wuce kai tsaye gabanta ya kama kunne.</p><p> "Sorry"</p><p> Bata kula shi ba,ya juya ya kalli ajin ,"Sannun ku 'yan uwana dalibai majinyata,wannan. Malamar ta ku kuma likitar ku nima malamata ce kuma likita ta,na mata laifi na zo bata hakuri kuma nima daga yau zan fara zuwa ajinku,ku tayi ni bawa malama hakuri na dawo dan uwanku kuma abokin ku."""</p><p> Nan suka hada baki suka ce,,'''muna maraba da sabon abokin mu..""</p><p> Suka kalleta ,"Malama kiyi hakuri.."</p><p> Nan suka sake hada baki suna ta bata hakuri har sai da ta amsa ta hakura,Deeni ya kafa mata ido yana mata dariyar zolaya. Bata kula shi ba har suka tashi ya bita har (office)a nan ya sata gaba yana ta mata naci tayi hakuri.</p><p> " Ba zan kyaleki ba kamarnyadda baki kyale ni ba kwanakin baya,kiji ya fitinar take ? Gara ma ki hakura mu shirya."</p><p> Ta kalle shi ba alamar wasa,ta ce.</p><p> "Mr . Deeni ,nan ba gida bane,wurin aikina ne inda ma'aikata na ke ganin girma na da girmamani ,don haka ban son wasa. In har zaka ginga zuwa daukan darasi to ba wasa,muna da (discipline)da dokokin da zaka kiyaye. Ba latti,ba fashi,kuma ba yin yadda kake so..""</p><p> Dauke kai yayi ya bata fuska,"Bana son (classes) din naki.""</p><p> Ganin yadda ya juya ya murtuke ,lokaci daya kamanninsa suka canja ya firgita ta,ta mike . </p><p> ""(Please )mana Deeni ,ka saurare ni"</p><p>Damuwa ta bayyana karara a fuskarta.</p><p> Nan kuwa ya kwashe mata da dariya yana tsokanar ta.</p><p> "Na firgita wata .""</p><p> "Deeniii """""</p><p>Ta fada tana zare ido.</p><p> " Kai ki,zan kama ka ne .</p><p> Dariya yayi yabfita yana fadin," Gobe karfe tara na safe (i will be here )ba latti ba karya doka,ba fashi.</p><p> Nan ta bishi da kallo taba dariya,har ya tafi ya dawo.</p><p> "Zan sami littafin nan ki sunan littafin ??""</p><p> Juyawa tayi bata kulashi ba ,ta rufe kofar office din. Don haka Deeni ya dage da zuwa kullum ba fashi,haka kullun yana mata nacin labarin nan ko sunan sa,amma bata saurare shi ba,va irin nacin da bai yi ba har ya hakura. Har (internet )ya shiga yana (searching)sabbin littafan MISBAH amma bai samu ba,tun na karshe da ya sani da ba sunan wani sabo a cikin list din littattafansa.</p><p> Abun yana matukar daure masa kai,duk nacinsa da kokarinsa ya kasa samun ko mutum daya da yace ya samu sabon littafinsa.</p><p> Haka Deeni ya samu sabuwar rayuwa tare da sabbin mutane da suke tare da Doctor Bahijja,killum takan musu darasi tayi musu tambayoyi,duk wanda ya ci takan fita da su yawo zaga gari,da zuwa ziyarar wuraren tarihi na ilimi. Duk wanda ya warke gaba daya a sallame shi </p><p> Anan Deeni ya dunga taimaka mata da wasu ayyukan kasancewarsa likita,duk da kwarewar sa da karatun da bai kai nata ba zama da ita yau da gobe yasa ya fara sabawa da koyon aiki sosai ,daga dalibi ya bige da (praticing)da (training).</p><p> Bahijja takan yi mamakin kokari da nuna kware na Deeni gashi da saurin fahimtar aiki,tabbas da ya jima yana aiki da karo karatu da ba karamin taimako zai yi ba ...</p><p><br /></p><p> A kwana a tashi Deeni ya ya warware ,shakuwa da sabo yana karuwa tsakanin sa da Bahijja ,zukan wuni tare a asibiti suna aiki tare.</p><p> Sai dai har yanzu Deeni bai taba fada mata damuwarsa ba wanda ke cinsa,abinda iyayensa da farida suka masa ya kasa mantaws da wannan cin amanar,haka kullum gudun haduwa da su yake,gudun maganarsu yake ko jin labarinsu. Wanda Bahijja kuma ta dage sai ya fuskanci abin ya wuce ya huya,sai dai duk kokarinta ya kauce....</p><p> </p><p> Bai taba tambayarta ta tarihinta ba ,haka bai taba fada mata nasa ba,a haka suke zaune ,haka nan har yanzu bai fasa binciko labarin MISBAHA ba......... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yaseen ya nagaji zan je hutun sati🤔🤔bayana ya rike😡😡</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA</p><p> SA'AD❤❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Assalamu Alaikum</p><p>Masha Allah!!! Bisa ga hutun zango da muka dauka ,yau Allah ya dawo damu...Nagode da kulawarku a gareni ,Allah ya kara zumunci. Masu cewa ko lafia aka jini shuru ,,,wlh lafia lau sai dai Dan Adam da baa rasa shi da wasu yan hidimomi nashi na daban ... </p><p> Sannan dan Allah ina fatan baza'a kuma samun miskila kamar yadda aka samu a baya ba ,,wannan abu nina sa kaina pls nd pls abarni murabu lafia da kowa kamar yadda aka fara tun farko....</p><p> </p><p> Ina godia ga big Aunty Allah ya barmun ke bisa ga jajircewarki wajen ganin nacigaba da wannan rubutu(Aunty zee )maman nawal❤❤❤❤love u wujiga wujiga😘😘😘😄😄</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>42</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wata safiya Bahijja da Deeni bayan sunyi aiki sun gama da marasa lafia,suna zaune a (free time )dinsu ,Bahijja ta kalleshi .</p><p> ''Deeni, me yasa ka ke gudun mahaifinka ? Me yasa baza fuskanci gaskia ba da abinda ya faru ? Abinda ya faru ya wuce,kayi hakuri ka yafewa dan uwanka,wannan kaddara ce,bashi da laifi . Farida taci gaba da rayuwa,tana rayuwarta da mijinta da yaranta,me yasa zaka yi ta kuntatawa kanka ? </p><p> Idanunsa ne suka kada sukayi jaa,ranshi ya mummunan baci,duk da haka bata fasa maganar ba. </p><p> Deeni (you have to let go of ur past )ba zai yiwu ka rike su a zuciyarka ba kana wahalar da kanka,please ka yafe musu....</p><p> Nan kuwa taga ya haukace mata yana zazzafa mata bala'i....</p><p> Bazan yafe ba,saboda me zan yafe ? In ma na yafe nusu kina nufin zan iya mantawa da abinda suka mun in zauna lafia da su ? Ko na yafe musu bani ba su,bana son jin maganar su a ratuwata,na tsane su,zan iya kisa idan na ganus gabana...</p><p> Ta kalleshi cikin fuskar damuwa ta tsiyaya masa ruwa mai sanyi a cup ta mika masa,tace..</p><p> Please Deeni zauna... Ya zauna amma bai karbi ruwan ba </p><p> Saurare ni Deeni,in har ka dauke wannan zafin a ranka ba zaka iya yafe musu ba ,ko tsana ne ko so je ka sake shi a ranka,ka fiddashi a zuciyarka akansu. Ganun su ko maganarsu dole ne ,dan uwanka ne uwa daya uba daya,zumunci dole kayi,Allah ne ya ce kayi.. Gaba ma ba zakayi da musulmi dan uwanka ba balle dan uwa na jini.</p><p> Farida kuwa akwai lokacin da kyakkyawar dangantaka ta hada ku,yamzu kuwa matar yayanka ce,dole ka yarda da wannan....</p><p> Mahaifinka kuwa in kayi fada da shi baka da riba ,duk kai zaka sha wuya kaita wahalar da kanka...</p><p> Kayi hakuri Deeni,Allah zai baka ladan hakurin da kayi,ya kuma baka sakamako mai kyau a duniya da lahira....</p><p> Tana maganar kamar zata zubar da hawaye....</p><p> ""kamar kani kake a gareni ,ba zan so ganin kanina cikin wannan halin ba... </p><p> Tsura mata ido yayi yana kallonta,maganarta na ratsa shi,haka nan ya dinga jin maganganunta na masa tasiri a zuciyar sa ,yaji zuciyar sa ta sauka ,tayi sanyi..</p><p> Ya dauki ruwan sanyin yasha ,ya kalleta ya mata murmushi tare da mika mata tissue.</p><p> "" Gashi ,share hawayen da ke shirin zubo miki,kar su zubo in miki tsiya nan gaba.......</p><p> Murmushi tayi ta amsa,"Deeni ba zaka canja ba,tashi yau kaine best student koyarwar da na maka ya shiga kwakwalwarka da zuciyarka,don haka yau da kai zamuje outing..</p><p> Yayi daria ,"yau ta ina rana ta fito Abokiyata DoctorBahijja zata fita dani yawo ?? </p><p> Murmushi tayi bata kulashi ba ,taje ta dauko mota ya shiga suka fita...</p><p> Kai tsaye suka wuce asibitin gwamnati na garin suka dinga bi tana nuna masa marasa lafiya,wasu gasu nan kwance cikin azabar ciwo ba lafiya wasu ga ciwo ba kudin magani,wasu na son yin ibada da sauran ayyuka ba lafiya. Abin tausayi kala-kala da ya fara sa jikin Deeni mutuwa,daga nan suka wuce sauran asibiti na masu kudi su kuma ga kudin ga komai amma lafiya da saukin Allah bai nufa ba...</p><p> Daga nan suka zarce gidan marayu,marasa galihu ,masu neman taimako basu da kowa bansu da komai sai Allah, sai abinda gwamnati taga dama ta san musu,suna watse basu da mai tallafa musu,ba uwa ,ba uba da zasu lallashe su,basubda wanda suka damu da su da rayuwarsu. Anan Deeni ya ga abun tausayi sai da ya zubar da kwalla...</p><p> A mota duk jikinsa yayi sanyi ,Bahijja ta kalle shi tace,</p><p> "" Yaya bakin cikinka da dacin ranka yake da na wadannan bayin Allah ? Baka ganin ni'imar da Allah ya maka,kana da lafita da karfinka da gatanka da iyayen da suka damu da kai...</p><p> Anta baka ganin matsayin iyaye ya kai suyi mana yadda suke so ko da bata mana rai ne suna da hakki?? Deeni rayuwar nan tayi kadan mutsaya muna bata lokacin mu akan wani bacin rai ko tsana,gaba ko wata kiyayya...</p><p> Ka godewa Allah da ni'imomin da ya maka,in ya jarrabe ka sai kayi kokarin ka ci jarrabawar . Ka yarda da kaddara,ka saki ranka kayi hakuri Allah yana tare da masu hakuri(innallaha ma'assabirin😭)...</p><p> Yayi murmushi idon shi jawur,hawaye ya gangaro masa,ya ce.</p><p> "Nagode Bahijja ,tabbas kin cika abokiya tagari,likitan da tasan hakkin patient dinta,sannan ke mutumiyar kirki ce,Allah ya miki sakayya da abinda kika mun. A yau kinsa naji wani kunci da nauyi ya bar zuciyata ,duk wani fushi da kiyayya da nake ji a raina ya tafi .......</p><p> Tabbas nayi nadamar bata lokacina da nayi,sai dai insha Allah zan gyara gaba ,daga yau,daga yanzun nan Deeni ya zama sabon mutum wanda ba ya rike da kowa a zuciyar sa,ba ya fushi da kowa. Ina jin zuciyata fara , zanyi kokarin gyara rayuwata da tsakanina da iyayena da 'yan uwa na...</p><p> </p><p>Yau ce rana ta farko da nakeji da son fuskantar yaya Shamsu da Farida ba tare da wani bacin rai ko tsanar su ba, na yarda na amince haka Allah ya hukunta mun. Na gode Bahijja ...</p><p> Lumshe ido tayi hawaye na gangara wanda bata san yaushe suka zo ba ,tana fadin..Alhamdulillah "".. A ranta..ya tsura mata ido yana kallonta,kamar wata bakuwa ko sabon halitta,kaunarta yaji ta shiga ransa,haka yana bata wani girma na musamman. Ta mike,"Yau ranar farin ciki ce garemu da ni da kai,sai godiyar Allah .yanzu saura guri guda zan kaika,ina fatan zaka ji dadin zuwa wurin ""</p><p> " Me zai hana ?" ya bata amsa ..</p><p> ""Musamman inda ke a wurin..</p><p> murmushi tayi ta girgiza masa kai suka tafi..</p><p> wani tafkeken farm house ta kaishi na (lagos state government )ba abinda babu ciki,kaji ne,dabbobi ne ,shuke-shuke ne,tsuntsaye ne,kala kala a wurin ..</p><p> Wani farin ciki da jin dadi ta gani ya bayyana a fuskarsa,ya dinga ratsa cikin gonar yana bin kan dabbobin dabtsutsayen yana shuke-shuken dake wurin sun matukar burge shi, bai san lokacin da ya fara dariya shi daya ba. Irin abin da yake so yaga ya yi,ya kafa a rayuwar sa. Ga bishiyoyi,ga shuke-shuken 'ya'yan itace kala daban -daban ...</p><p> lumshe ido yayi ya ware hannun yana shakar iskar wurin yana jin yana ratsa shi,yana jin wani irin tsananin dadi a ransa irin wanda ya jima bai ji ba.</p><p> Zuwa tayi gabansa ta harde hannu tana kallonsa tana murmushi,tana jin dadin yadda ta ga tayi sanadin kawo farin ciki a rayuwar sa. Nan ta dinga jin wani irin farin ciki a ranta ,wannan dama shi je burinta a rayuwa ta ga tana sanya dariya da farin ciki a rayuwar mutane ,anan take samun nata farin cikin da nutsuwa da jin karfin gwiwar cigaba da rayuwa....... </p><p><br /></p><p><br /></p><p>sry nasan zaku iya samun mistake ko typng erro ,,wlh typing din dare nayi kuma ban kuma bi nayi editing ba kawai nayi posting,,wlh nagaji ne kuma burina kawai nima inga yau nasaku farin cikii (kamar dr da patient dinta😛😛)</p><p> Tnks </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>43</p><p><br /></p><p>Kamshin turarenta yaji iska ta debo yana sauka kan fuskar sa yana shaka yana ratsa jiki da zuciyarsa,yana shiga yana ratsa shi. Soyayyar tace mai zafi da sanyi tare da dadin gaske yaji yana shiga yana kama zuciyarsa da dukkan ilahirin jikinsa yana ratsa shi tare da saukar masa ds wani irin farin ciki da ni'ima mai dadin gaske.....</p><p> "Alhamdullah",Allah na gode maka."</p><p> Ya bude ido yaci karo da fuskarta tana masa murmushi,shima ya hau mata murmushin Suka kyalkyale da daria duka,tace. "Wow! In kayi dariya kana cikin farin ciki (u rilly look great)"".</p><p> Ya kalleta,"(thanks to u )Bahijja."</p><p> Ta girgiza kai,"Mun godewa Allah,don haka Mr. Deeni daga yau kasan inda ka kama,kasan inda kasa gaba,(u belong here)...... Ta nuna masa gonar.</p><p> Ba gidan magani da allura ba,duk da likita kake amma kafi kyau da dacewa da nan gidan gonar,inda farin cikinka,jin dadinka da passion dinka yake,to me zaka jira? Ko ka nemi aiki anan ko kayi kokarin bude naka,duk wanda kakeso zaka iya""...</p><p> Yayi dariya," Na gode da shawararki ,tabbas a nan passion dina yake ,(thank u so much)Bahijja . Daga yau din nan na miki alkawarin bude sabon rayuwa ,kuma zan fara yin wani abu me ma'ana da rayuwata insha Allah.</p><p> Amma ina so ki min wani alkawari, ki zama abokiyata mai ban shawara ,yayata kuma mai guiding dina...""</p><p> Tayi murmushi ,"Insha Allah ,Allah ya yi mana jagora duka".</p><p> Ameen "Ya amsa tare da fadin .</p><p> ""Sannan zaki bani littafin nan na MISBAH ,kuma zaki zama ABOKIYAR RAYUWATA...""""</p><p> Ta dalla masa harara ,"Abokiyar rayuwarka kadai? Ka manta har ABOKIYAR MUTUWARKA ma zan zama .."</p><p> Ya yi dariya ,"yauwa my Bahijja'"..</p><p> Wucewa tayi ta fita ta wuce mota ,har ta saba da halinsa na zolaya. Ya bita har ya shiga suka tafi yana zolayarta.</p><p> Har gida ta kaishi ta ajiyeshi,ba yadda bai yi ba ta shiga ta ki,ta ce ya gaida hajiya. Anan ya karbi numbern wayarta sukayi sallama.</p><p><br /></p><p> Kai tsaya ya wuce falon mahaifinsa,anan ya same su duka har lukman kaninsa,yana dariya ya gaishe su. Kallo daya zaka masa kasan yana cike da tsantsar farin ciki.</p><p> Ya zauna kusa da mahaifinsa tare da kwantar da kansa a cinyarsa. </p><p> "Baba ka yafe mun"</p><p>Alhaji Umar ya dinga ji da ganin Deeni kamar a mafarki,sai da hawayen farin ciki ya zubo masa bayan shekara takwas zuwa tara Deeni ya fito daga kejin da ya shiga...</p><p> Mahaifinsa ya kalleshi,Deeni Alhamdulillah ,tsantsar farin cikin da nake ciki bnsan iyakarsa ba. Nima ka yafe mun.</p><p> Mama dai ta kasa jurewa sai da tayi kuka,farin ciki da jin dadin da suka tsinci kansu a ciki,sai godiyar Allah. A nan Deeni ya tabbatar musu da ba zai taba sake daga musu hankali ba.</p><p> "Zan yi biyayya a gare ku insha Allah"".</p><p> Alhaji ya kalleshi,ya ce,"Allah ya maka albarka Deeni,nima na muku alkawari dukkan ku 'ya'yana ba zan sake shiga rayuwarku ba,kowa yayi abinda yakeso duk da nasan nayi latti duk kun gama karatu..</p><p>""Baiyi latti ba Baba ."Deeni ya katsae shi.</p><p> Ko a yanzu zaka iya yin abinda nake so,ina fatan zaka taimake ni kasa mun albarka."</p><p> Insha Allah Deeni sai inda karfina ya kare..""</p><p> Yace,"Wannan yarinya likita Bahijja Allah ya mata albarka ..</p><p> Mama ta kalli Deeni ,"Zaka kaini jar gida insa mata albarka.</p><p> Yayi dariya ,"To mama ko yanzu ma in kin shirya".</p><p> Tayi dariya ,*ba yanzu ba sai gobe " </p><p> Alhaji yace,"Nma ba za a barni a baya ba""</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Washegari bayan sallar isha Deeni ya tuka su zuwa asibiti wanda anan gidan Bahijja yake,suka yi tambaya don kuwa Deeni bai taba zuwa gidanta ba.</p><p> Sun samu baba andi ta ce bari ta shiga ciki ta mata magana,anan Deeni ya mike yana zagaye falon nata dabyadda ta tsara shi yana murmushi yana jin sonta na kara tasiri a zuciyarsa,soyayyar Bahijja na shigarsa yare da saka masa wani irin tsananin farin ciki da jin dadi.</p><p> Yana tafiya yana zagaye wurin har ya hango gurin da ta kebe mai kama da (libry)anan ya hango hotunanta da mijinta da danta suna rumgume da juna,ya zurawa hoton ido yana tuno Dr. Mislihu . Sai a lokacin ya fahimci mijinta ne.</p><p> Wani dan madaidaicin (diary)ya gani da biro a hade alamar bata jima da yin rubutu ciki ba,haka zuciyarsa ta dinga azalzalarsa ya bude ,yana kwadayin sanin komai game da Bahijja. Nan ya yi karfin halin budewa duk da yasan hakan ba dai dai bane.</p><p> Abu na farko da ya fara gani yaji zuciyarsa tayi mummunan tsinkewa shi ne,(To my dearest wife MISBAH).</p><p> ""MISBAH ? Ya maimaita a ransa ..</p><p> Bai bata lokaci ba yaci gana da karantawa,sai lokacin ya lura da diary din da marigayi mijunta ya rubuta mata ne,yana fada mata irin muhimmancinta da soyayyar da yake mata gami da yabonta na ayyukan kwarai da take,yana mata addu'a gami da sa mata albarka.</p><p> Nan ya rufe ido yana kokarin tuno inda yake ganinta da diary din nan mai kama da littafi,da lokacin da take zuwa gidansu wurinsa,da kuma asibiti,in tana zaune bata da komai takan dauko littafin tana karantawa ...</p><p> Sannan wannan shine littafin da ta rike da sunan tana karanta masa sabon littafin MISBAH.</p><p> "Wato Bahijja ita ce MISBAH"". Ya maimata.</p><p> 'Author din da nake so tun ba yau ba ,Author din da na hada (special bond ) da ita tun lokacin da na fara karatun littafin ta a rayuwata,Bahijja abokiyata wacce take yanzu masoyiyata ita ce MISBAH na da na jima ina so ina kauna? Wow ! Bahijja na ita ce MISBAH na ..""</p><p> Kaunarta yaji yana dada tsuma shi,yana ratsa shi..</p><p> </p><p> **Ke din daban ce special ce tunda har kika iya min dabara ,ni kika mayar marar wayo ? Ni kika fooling,wato dama wannan labarin kirkirankika yi a lokacin shi yada na nemi lityafin nan sama da kasa na rasa,ashe dama yana boye ne a cikin kwakwalwarki. (I love ur smartness)ina sonki Bahijja 'yar Baiwa,MISBAH na . Sai yanzu na fahimci labarin rayuwata da kikela yi kokarin hada min naji yana shiga ta,naji labarin ya tsaya mun a rai . Na so inji karshen sa ko zan samu in warware nawa matsalat..""</p><p> Ya yi murmushi yana kallon hotonta ,""labarin da kika fara ni zan karasa miki,ba ni kika fooling ba ? Jiya kiga yadda zan fooling dinki...""</p><p> Nan ya yi ta ganin takardunta a wurin daban-daban da irin article din da tayi ta rubutawa.</p><p><br /></p><p> MISBAH na 'yar baiwa ce ,Nsha Allah zan zama ABOKIN RAYUWAR ki da MUTUWARKI kamar yadda kika fada,zaki ga yadda zan kawo farin ciki da canji a rayuwarki" </p><p> Ya yi murmushi ya ce,""Yayata Bahijja,Abokiyata,masoyiyata MISBAH .""</p><p> Nan yasa hannu ya dauki littattafan da yake so,sannan ya dawo gun su mama ya samu Baba Andi ta gabatar musu da abin motsa baki,yasa hannu ya dauki apple yana ci yana lumshe ido ,yana jin kamshin Bahijja ko ta ina a gidan .</p><p> Baba Andi tace,"kuyi hakuri na samu ta fara sallah ne .""</p><p> Mama tayi murmushi ,""Bakomai"</p><p> bata rufe baki ba kuwa Bahijja ta fito da fara'arta lullube da hijab,tunda ta shigo falon idonsa ke binta,ya zurawa fuskarta ido me cike da kamala da annuri ,murmushin dake kan fuskarta ya kara haska fuskarta ,yaga ta masa wani irin kyau da kwarjini......</p><p> Wani irin SO me karfi yaji yana shigar sa,Son da bai taba tsammanin akwai irinsa ba ,ashe da wasa yake ba so ba,MISBAH ita ce so,ita ce SHAUKI. kallonta na kara masa son rayuwa,yana kara masa tsammani ,yana sa shi wani irin farin ciki da nishadi............</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>he's inlove again 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🤔🤔🤔🤔amma anya kuwa Deeni baya zurfafawa dayawa a soyayya ?? </p><p> </p><p>Shin Bahijja zata karbi Deeni kaninta a matsayin masoyi ???</p><p><br /></p><p>wani hali Deeni zai kasance idan Bahijja taki amincewa a karo na biyu???</p><p><br /></p><p> sai munji ra'ayoyinku...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>taku har kullum......</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>SUMY LUV😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>=================== GIDAN NOVELS ====================================</p><p><br /></p><p><br /></p><p>44</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yadda Deeni yaga tana gaisawa da su Mama da Baba suna ta hira cikin kaunar juna da kulawa ya kara masa jin dadi da nutsuwa,haka yake burin ganin matarsa da iyayen..</p><p> Bahijja ta mai (a kallonta kansa,ta lura ya tafi wata duniya. Biron dake hannunta ta jefa masa tana dariya ,ta ce.</p><p> '"Abokina Deeni,wacce duniyar aka tafi??</p><p> Yayi mata murmushi,ya ce,"Duniyar abokiyata Bahijja,gidanki ya mun kyau ,ya birgeni ,musamman (libry)dinki,cike yake da irin littattafan da nake so""</p><p> Ta zaro ido tana kallon sa,"Kaji min yaro ,daga zuwa gidan mutane har kasan hanyar (libry)dinsu ?? </p><p> Ya yi mata muryar tsokana ,yace,"Ba gidan mutane bane ,gidan Abokiyata fa Bahijja ne. Sannan kin manta lokacin da kike zuwa nawa dakin kina mun yadda kike so ? Yanzu lokaci na ne."""</p><p> Tace,"" Gidanku gidanmu ne ,ko mama? </p><p> Mama ta girgiza kai,"kwarai """.</p><p> Ta kalli Deeni tana masa gwalo,ta ce.</p><p>"Gidana kuwa gidana ne ni daya,Baba Andi daga yau in yazo kar ki bude masa kofa ..""Baba Andi tayi dariya tace,"Ni na isa in shiga tsakanin yaya da kaninta ?? Deeeni yayi dariya,ya ce ,"Yawwa Baba Andi, daga yau kin zama babbar abokiyata,zan shigo inyi yadda nake so gidan yayata..""</p><p> Bahijja tace,"In kuwa kayiwa yayarka barna zaka sha bulala."</p><p> Dariya sukayi duka har da Alhaji,Mama ta kalleta tace.</p><p> " Allah ya miki albarka 'yar nan "</p><p> Ameen Maama."ta fada kanta sunkuye.</p><p> Tace,"kuyi ta mna addu'a mama,kuna sa mana albarka,insha Allahu Allah zai taimake mu..</p><p> Deeni ya kalleta yana dariyar tsokana,zuciyarsa cike da sonta ,yace.</p><p> "Allah ya miki Albarka 'yar nan ......</p><p> Ta hararebshi ,"Mama kinga yaron nan ya raina ni." </p><p> Alhaji ya kalleta yana murmushi ,ya ce .</p><p> Zan baki bulala ki dinga zane shi."</p><p> Suka yi dariya duka,tace,'Yauwa Baba,gara in fara zane shi don naga girman jikinsa na yaudararsa...</p><p> Deeni yace,"To wata ma tayi girman jijin mana </p><p> Mama tace,"Deeni naga alama nima zan fara maka bulalar.."</p><p> Nan suka yi ta dariya suna hira har wurin karfe tara sukayi niyyar tafiya,Bahijja ta raka su har mota. Ta lura da wani irin mayataccen kallo da Deeni yake mata,haka ta ganshi cikin tsananin farin ciki. Sai dai bata zurfafa tunani ba ta kau da abin a ranta amma ta rasa me yasa kallon yake yawan fado mata rai(💃🏻💃🏻💃🏻)...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>***** ***** ****</p><p><br /></p><p>Deeni da iyayensa suka ziyarci su Shamsu tare da sauran dangi,Shamsu da Farida kam sunsha mamakin ganin yadda Deeni ya ware har abinci ya zauna suka ci tare da shi da Faridan da yaransu ana wasa da dariya..</p><p> Tun Farida najin wani iri ,tana takura har ta ware tana kallonsa tana mamakin ganinsa haka. Ya kuma nuna mata shi dan duniya ne ,ya dinga janta da hira,"Aunty Farida kaza ,Aunty kaza akayi." Tun bata da niyyar sakewa har ta sake..</p><p> Deeni kuwa har cikin ransa ya gama da farida da tunaninta ko soyayyarta,a halin yanzu duniyarsa,farin cikinsa da shaukinsa yana ga Bahijja.</p><p> 'yan uwa da abokan arziki kowa ya yi murna da sabon canjin da aka samu daga Deeni. Farida ta masa murna sosai ,amma sai ta tsinci kanta a cikin wani bakon yanayi na rasa soyayyar Deeni da tayi,sai a lokacin ta kara fahimtar abinda yayi,addu'a tai tayi har ta samu saukin abin. Saboda ita har yanzu cikin kasan zuciyarta akwaii Deeni a binne ,sai dai zata ci gaba da jurewa da kuma rungumar rayuwarta da mijinta da 'ya'yanta ,ba zata taba tono shi ba.</p><p><br /></p><p> </p><p> A cikun wannan lokacin Deeni da mahaifinsa suka yi ta shiga da fita da buge bugen neman makeken fili a kusa da asibitin Bahijja don ann ya cewa mahaifinsa yake so ya yi gidan gonarshi. Shi dai bai tambayeshi dalili ba,ya biye masa don yanzu duk abinda Deeni ke so shi ake masa,da sauri ma kuwa. Shakuwa da soyayya ta musamman ta shiga tsakaninsa da mahaifinsa,gaba daya Deeni ya dawo sabon mutum..</p><p> </p><p> Abinka da masu gidan rana ,lokaci kankani aka gama ginawa Deeni gidan gonar sa,aka daukar masa ma'aikata masu taimaka masa da komai. Duk wani abinda yake bukata an sa masa ciki,a hankali wurin ya dinga habaka yana yiwa Deeni yadda yake so..</p><p><br /></p><p> Irin farin ciki da jin dadin da ya tsinci kansa a wannan lokaci ba a magana ,yayin da ya sako Bahijja gaba da nasa salon tsokanar wanda ya samo. Wata number ya samu yana tura mata text message.</p><p><br /></p><p> Tana zaune office dinta tana karance karance taji wayarta tayi kara alamar shigowar sako,ta dauka ta bude. Gabanta ne ya ba da rass!!</p><p> "MISBAH""</p><p>Shine abinda taga an rubuta.</p><p> Tayi bala'in rudewa saboda duk duniya mutum daya ne yasan ita ce MISBAH ,wanda yanzu baya duniyar.</p><p> Kafin ta gama fita daga wannan rikicin ta sake ganin an turo mata wani.</p><p> (I knw u re my MISBAH).</p><p>Mikewa tayi tana sake maimaita sakon a ranta,mamaki ya bayyana karara a duskarta,nan tayi saurin mai da amsa.</p><p> "Waye kai?(wrong number)</p><p> ya bata amsa da ,"In wrong number ne me yasa kika tambayeni ? </p><p> Nan tayi saurin kiran layin,amma sai taji a kashe ,tayi shuru tana tunanin duk wanda yayi abin nan yasan yadda take tunani,yasan zata kira ,to waye ne ? Ko da wasa bata taba kawo Deeni a zuciyarta ba,asali na ta kasa kawo kowa a ranta. Haka tayi aikin wurin da abin a ranta.</p><p> Tana sallama gidanta kuwa wani sakon ya shigo.</p><p> "Allah ya hice gajiyarki my MISBAH ""</p><p>Yanzun abin ya fara taba mata rai ,wa ce ko wane dan rainin wayon ne ? </p><p> Tayi tsaki ,zata wuce ciki taji muryarsa. </p><p>"Haba madam Bahijja ,wucewa haka ba kya duba gabanki ? Tun dazu nazo ina jiranki,awa na guda na samu Baba Andi itama har ta gaji ta tashi,amma ni ban gaji da jiranki ba. Haba abokiyata."</p><p> Bahijja ta harare shi,"Gama cin abincin ka sha ruwa maza kaje gida kayi wanka ka kwanta kayi bacci,kana da aiki gobe..""</p><p> Ya yi saurin mikewa ya sha gabanta ,"Wa kike cewa yaro ? Wai an fada miki shekara talatin wasa ne ? </p><p> " Matsa ni kaban wuri,talatin din har wata kayan gabas ce ? Akai na dai talatin dinka na komai bane.." </p><p> Har ta soma tafiya ya sake shan gabanta ya harde hannu tare da shan mur ,ya kafa mata idanunsa.</p><p> ' Waye yaro ? </p><p> Muryarsa da irin kallon da yake mata duk suka rikitata ,ta rasa me yasa take jin shakkar sa. Nan dai ta dake ,murya na rawa ta ce.</p><p> ""Way... ...waye kake zarewa ido ? Wa zaka bawa tsoro ? Ni da waye a wurin ? </p><p> cikin muryar rada mai kashe jiki yace,"Yayata Bahijja da abokiyata Bahijja ,ita nake bawa tsoro ,kuma naga ta tsorata...</p><p> Gaba daya ta rikice ,taji jikinta na bari,da kyar ta iya daga kafa tayi ciki da sauri . Ya bita da kallon kauna yana murmushi,can ya jiyo muryarta tana cewa.. </p><p> " Ka fita ka kira baba Andi ta rufe mana kofa,kuma karka sake zuwa mana gida da dare""</p><p> "" zan zo ko yaushe nakeso,kuma in kin isa ki fito ki fuskance ni ki hana ni.</p><p> nan ta leko da kai ta ce,"Na fuskance ka,sai me ? </p><p> " ki kalli cikin idona in kin isa" "Naki din "ta fada tare da rufe kofar da karfi tasa key.</p><p> ""Wannan yaro ya zame min damuwa gurin aiki da gida duk bai kyale ni ba,sai na hada shi da mama".</p><p> Tana cikin wanann mitar wani sako ya sake shigowa ....</p><p> " Ki tabbatar kin ci abunci kafin ki kwanta,karki kwana da yunwa MISBAH NA.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>SUMY LUV😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kuyi hakuri da abinda kuka samu,wlh nayi typing me yawa da safe ban san ya akayi ba akamun deletn....wlh saura kadan nayi kuka ,sabida yafi na koyaushe yawa..</p><p> </p><p><br /></p><p>45 </p><p> Tsaki Bahijja tayi ta kashe wayarta takwanta a wurin ko kayan jikinta bata cire ba ta kwanta a kasa zuciyarta cike da tunani kala kala musamman na wanann sakonni dake shigo mata.</p><p> Can ta kau da tunanin ta soma tunanin yadda Deeni ya saki jiki da ita sosai,tayi zaton in ya warke a yadda ta sanshi da attitude zai fita harkarta ne amma sai wani sabon shakuwa ma da kara kusanci da ita yayi,lokaci guda sun zame mata kamar 'yan uwa shi da mahaifansa da 'yan uwansa. Tabba da haka kowani mara lafiya yake mata da duk kusan rabin kasar nan sun zama yan uwanta. Shi dai Deeni daban yake,mutumin kirki ne,mutumin kwarai.</p><p> Dariya tayi da ta tuna halayyarsa da yadda yake yawan nasara akanta.</p><p> Deeni kanina ,ina son sweet nature dinsa.</p><p> Ta yiwa kanta murmushi ,sannan tasa hannu ta dakko hoton Doctor Mislihu da danta kana kallo tana jin tsananin kewarsu.</p><p> "Allah ya jikanka,ya maka rahama masoyina. Muhammad dana Allah ya maka albarka ,ya albarkaci rayuwarka. Allah ya kare min kai a duk inda kake..</p><p> Hawaye ne ta dinga gangaro mata,ta tsinci kanta cikin kewa kamar yadda ta saba kowani dare,da hakan bacci ya dauke ta.</p><p> </p><p> Haka Deeni yasa Bahijja a gaba da tura sako,ya hanata sakat. Wani lokacin sai ya zo gabanta sai ya tura mata,nan da nan zai ga ta rikice tayi wurgi da wayar har ya zamana tana shakkar kunna wayar,a dole take amfani da layin saboda shi ne layin da aka santa dashi ,ana iya nemanta.</p><p> Haushi ya kamata ,ga matsalar me matsa mata da text da bata san waye ba ,ga Deeni kusan sati guda bata ganshi ba ,ta masa waya bai dauka ba ,kuma bai kirata ba. Ta kira mama ta tabbatar mata lafiyar sa lau,aiki ne ya masa yawa.</p><p> Tsaki tayi ta kasa kulla komai,can ta yanke hukuncin leka shi a ma'aikarsa ,tunda ta shiga ta hango shi yana aiki bai zauna ba yana ta faman kaiwa da kawowa da ma'aikatansa,ya leka wannan fannin ya leka wancan . Can ra ga ya hau tractor yana zaga cikin farm din nasa,ta sa masa ido tana kallonsa tana murmushi..</p><p> Nan take ta rsinci kanta cikin nishadi,tana jin dadin ganinsa haka tana matukar sha'awar halinsa,wasa da dariya da maaikatansa gami da mutunta su,haka tsakaninsa da dabbobi,kaji da sauran tsuntsaye tamkar abokan sa.</p><p> Harde hannu tayi tana kallonsa kamar t.v. can ta ga wata yarinya matashiya ta zo tana kiran sa,ganinta yasa ya sauko daga kan tractor din ya zo yana kallonta yana daeiya suna magana,haka ya bata muhimmanci sosai. Haka kawai taji ranta ya baci,ta kasa ci gaba da jure kallonsu.</p><p> Har ta juya zata tafi sai taji muryarsa,''Har abokiyar tawa zata tafi bamu gaisa ba?</p><p> Ta kau da kai ,"Dole ne in gaisa da kai ?</p><p> Gaisuwa ba dole bace amma ganina dole ne "</p><p> Ta harare shi ,"Ta yaya ya zama dole?</p><p> Tabbas nasan tunda har kika zo gidan gonata ba kinzo yawan shan iska bame"</p><p> " Kwarai ". Ta bashi amsa.</p><p> "kaji nazo gani da dabbobi."</p><p> To ai baki gansu ba zaki tafi.</p><p> " Na fasa "</p><p> Ta fada a hasale tana kallon yarinyar alamar tana tsaye tana jiransa ne.</p><p> " kaje kaji da bakuwarka "</p><p> Ya yi murmushi ,kar ki damu da bakuwa ta,wannan special ce ba rabuwa za muyi yanzu ba,gara in gama da ke yanzu in koma.</p><p> "Yanzu ma ka gama dani,sai ka tafi.</p><p> "Bashi yiwuwa kizo ki tafi baki shiga office kinsha ruwa ba"</p><p> Ba shi nazo sha ba""ta bashi amsa.</p><p>"Na sani amma za kisha "</p><p> Dura mun zaka yi ?</p><p>"A'a da hannunki""</p><p>" wai me kakeji da shi? Ta fada a hasale. "Ban ji ds komai sai gidan gona ta da special bakuwata" </p><p> Hawaye ta ji ya ciko mata ido,jikinta yayisanyi tace,</p><p>Deeni sati guds ba waya ba ziyara? Na kira baka dauka ba ,ko special bakuwar ce ta hana ka ? </p><p> Yayi mata murmushin dake fadar mata da gaba ,yace</p><p> Ki yi hakuri aiki ne ya mun yawa da lokaci.</p><p> Deeni ba zaka iya samun lokaci komai kankantar sa ba mu gaisa?</p><p> Tana maganar saura kiris tayi kuka glhar ya lura da hakn yayi saurin kau da kai don ya bata damar zubar da hawayen.</p><p> Ya ce,MEYE DANGANTAKARMU? Bahijja kina naki duniyar ina tawa ,kina farin ciki da aikinki ina yi da nawa,idan halin haduwa ya zo sai mu hadu. Yanzu ba da bane,dukkan mu muna da abinyi,saboda me zamu dinga bata lokacin mu ?</p><p> " Haka me ".Ta fada murya kasa kasa .</p><p>Kayi hakuri,sai anjima.</p><p> Tajuya jiki ba kwari da kyar take iya daga kafarta .</p><p> "Bahijja"</p><p>Ya kirata amma bata juyo ba valle ta tsaya. Ya so ya bita amma sai ya fasa ,ya nemi wuri ya zauna ya fada wata duniyar tunaninta yana jin wani irin shauki mai karkin gaske game da ita yana ratsa shi,idonshi ya kada yayi ja yayin da gugiwar kaunarta ta dinga tashi a zuciyar sa...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sumy luv 😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤ </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>46</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bahijja ta koma office amma ta kasa zaune da tsayee,gaba daya ta kasa samun nutsuwar yin aiki,dole haka ta tattara ta koma goda. Nan ma tayi kokarin yin rubuce rubucen ta amma hakan ya gagara...</p><p> Duniyar internet ta shiga ko zata samu abin bincikawa shima ta kasa,nan ta dauko liyyafi amma karatun ya gagara,ranta yayi mummunan baci,ta rasa me ke mata fadi...</p><p> Wannan shi ne lokaci na farko da haka ya faru da ita a tarihin rayuwarta,damuwa da bacin rai komai yawan sa da karfinsa ba ya hanata sukuni har ta kasa yin komai,ta kasa jin dadin komai a rayuwarta. Haka ta kasance har yamma lis ita daya a gida,don baba andi ma bata nan taje gai da yan uwanta zata yi kwana biyu..</p><p> Kicin ya shiga amma ta rasa abinyi,ta fitofalon. Tana nn tsaye ta hango kanta tsaye a gaban tafkeken madubin dake manne a bangon falon.</p><p> A hankali ta matsa tana kallon kanta da yanayin ta,gaba daya ta canja,ta birkice,ba nutsiwa ko kadan a tare da ita.</p><p> " Meye haka Bahijja ?</p><p>Ta tambayi kanta.</p><p>"Me ke damunki ? Me ya hanaki sukuni? </p><p> Can karkashin zuciyarta tasan amsar ,amma sai ta ki amincewa wanda ita kanta tasan kin amincewa abinda kasan ba gaskia bane yana matukar wahalar da zuciya tare da ruhi da jikin mutum gaba daya.</p><p> Idanunta suka kada sukayi ja,tausayin kanta ya kamata. A hankali ta sa hannu ta zame gyalen da ta daure kanta dashi,ta baza gashin kanta tana shafa fuskarta da gashin ta,idanunta suka kada sukayi jajawur,ta tsinci kanta cikintsananin kewa . Sai a wannan lokacin ta tuna cewa eh ita mace ce fa mai rauni,abinda ta manta da shi duka yau ta tuna,tana bukatar a kula da ita ,tana bukatar soyayya ,tana bukatar wani ya sota,ya kuta da ita,ya kawo karshen wannan emptiness din a rayuwarta.</p><p> Bata ankara ba sai hawaye taji yana zubo mata da karfin gaske,har bakinta na bari. Ta sa hannu duka biyu ta rufe fuska tana kuka .</p><p> Ya sake kallon kanta ,"Bahijja ya kike ? Ya kamanninki kaye ? Ke kyakkyawa ce ko mummuna ?</p><p> "Ya kamannina yake ban taba sani ba,kullum dai mijina ya kan kalle ni ya yabani da kyauna,amma ni ban taba tsayawa na kula ba""</p><p> Shin me yasa nake son kula da kamannina na yau? Shin wa zai fada min ya nake? Ya kamannina suke? </p><p> ""Bahijja u re a beautiful woman,""""</p><p> Taji muryar Deeni tsaye a bayanta.</p><p> Ras !!!Gabanta ya fadi,tuni tayi wani mugun rudewa,tayi saurin jan gyalen ta lullubu,ta kasa ce masa komai.</p><p> ""Gidanki ne amma zan miki tayin gurin zama""</p><p> Ta rasa me yasa yake iya controlling dinta,bata iya musa mishi ko tayi niyya duk kuwa zafinta da jin ta isa.</p><p> Wuri ta nema a kujersr falon ta zauna,ta kau da kai.</p><p> Ya matsa gabanta ya kafa mata ido,"Bahijja meye damuwarki?</p><p> ""Me yasa zan fada maka damuwata? </p><p> "Hakan na nufin cewa akwai damuwar kenan ? Ina son sani...""</p><p> Sunkuyar da kai tayi ta kasa cewa komai.</p><p> "Bahijja ""ya sake kiran sunanta.</p><p> A duk lokacin da ya kira sunanta tana jin wani abu me sanyi da dadi yana ratsa ta har cikin zuciyarta da kwakwalwarta,yana kashe mata jiki.</p><p> Lumshe ido tayi tana jin wani abu me karfi game dashi..</p><p> Ya cigaba ,"Bahijja ninda ke duk muna cikin kuncin zuciya da shauki,bambanci shi ne kawai naki ya fito nawa kuma na boye shi a zuciyata,saboda bana son bayyana shi har sai na fahimci meye a zuciyarki.</p><p> Kuncin da kika shiga yanzu ni na shige shi na tsawon lokaci,ni kadai nasan ta yaya na rayu da wannan shaukin ..""</p><p> Wayar sa ya ciro ya daddanna a gabanta ,yayin da tana ji nata wayar yayi kara. Shi ya dauka ya mika mata,gaba daya jikinta ba kwari maganganunsa kawai ke mata yawo a jiki dabjijiyarta,da kyar ta iya karba ta bude sakon tana karantawa,ya sa mata ido yana karanta mata abinda sakon yace.</p><p> " I love you MISBAH"</p><p> Bugun zuciyarta taji ya tsananta ,ya sake maimaitawa yana kallon cikin idonta.</p><p> "Ina son ki MISBAH " </p><p> Nan tayi saurin sunkuyar da kai ,gaba daya taji ta rufe ,ta susuce,bakinta na bari,ta rasa abin fadi,ta kasa zaune da tsaye ,gashi ya tsareta da ido.</p><p> "" Na san abokiyata itace MISBAHna tun randa na fara zuwa gidan nan , na miki abinda kika koya mun ne na kirkirar sabon labarin MISBAH a lokacin,tunda kin kasa karasawa ni zan ci gaba ,sauran sai mu karasa tare. Ina fatan za ki bani hadin kai mu karasa tare .</p><p> Bahijja ina matukar sonki,so na hakika,zan kawo farin ciki ratuwarki,zan kula da ke,zan shagwabaki ,dukkan damuwarki zai zama nawa,zan dauki nauyin sa ki farin ciki a rayuwa...</p><p> Nasan nayi soyayya mai zafi a baya ,sai dai ina so ki sani dangantaka ta da kaunata da ke ya jima sosai,tun kafin in san ke wace . Na jima da kaunarki tun kafin in san ke mace ce ko namiji,ta hanyar rubutunki.</p><p> Bayan haduwa ta dake,kin taimake ni na manta da abin da ya faru a baya,wanda soyayyarki ce ta mantar dani. Yanayin rayuwarki abar so ce,abar koyi ne,sannan kin fahimtar dani abubuwa da yawa da baiwarki,wanda karo na biyu na sake fadawa sonki ba don komai ba sai wannan halayyar taki wanda ita na jima ina mafarki da burin gani a wurin mata ta (how u cope ur loneliness)ya birgeni ,ta kara min ganin ganin girmanki ,sannan lokaci guda na zo na fahimci MISBAH na ita ce Bahijja na ,sai abin ya min bibbiyu.</p><p> Halayyyar Misbah da Bahijja shi ya haukata zuciyata da sonta har na manta da na taba wata soyayya a rayuwata,duk abinda Misbah tayi yana burge ni,yana min dadi,musamman zuciyarta da boye kanta da tayi wa duniyata watsa iliminta da baiwarta ga alumma suna amfana.</p><p> Bayan nan Misbah kina da kyan da ya shiga zuciyata ya zauna,murmushinki,muryarki mai dadin sauraro,wannan bakin dake min mita da surutu kullum,wannan idanun masu kashe min jiki ko kirarki ,iya takunki ko nutsuwarki me hanani sukuni.</p><p> Bahijja ina sonki ,kina sona ?? </p><p> Gaba data ya gama tsuma da kalaman sa,ya kashe mata dukkan gabban jikinta ,sonshi ne mai tsananin gaske take jin yana huda dukkan ilahirin jikinta. Da kyar ta iya bude baki murya kasa kasa tace.</p><p> " Kasan me kake fadi kuwa ? Ni na ce maka ina sonka? </p><p> Ya karya kai yana kokarin su hada ido amma taki ,yace.</p><p> "Ba ke kika ce ba,ni naga haka,ni naji a jikina ,lokacin da hankalinki ya tashi da na daina zuwa wurinki na daina daukar wayarki,lokacin da hankalinki ya tashi da kika ganni da ma'aikaciyata. Wannan abin shi ne so Bahijja ,wannan feelings din da muke ji shi je so. Ko ki so ko ki qi mun riga da mun shirya duniyarmu nida ke tun tuni,mun tsara rayuwar mu ba tare da mun fahimci haka ba sai yanzu. Ina fada miki gaskiyar da kin kini sani ne ...""</p><p> Ta mike da sauri,"karka manta kai kanina ne,har yanzu ni yayarka ce,wacce na taba aure har ma na haifi yaro. Kai saurayi ne,dan gata ne,dan asali ne. Kar ka manta ni marainiya ce da bani da asali.</p><p> "" Martabarki da darajarki ya wuce haka,ke abar so ce Bahijja,ina son sani wanne ne daya kike magana akai,sona ne bakya yi ko kuma wannan bayanan zai hana ki aure na ? Uwa ta gari nake nemawa 'ya'yana na gani a tare da ke,mace saliha nake nema na gani a tare da ke ,don haks ki bar wannan zancen..</p><p> Ni ne me aurenki ba mutanen duniya ba,ni zan zauna da ke na miki alkawarin soyayyarki ba zata canja ba,haka zan cigaba da daraja ki da mutunta ki. Ke abu ce mai matukar muhimmanci da daraja a wuri na,kin wuce wasa""</p><p> Bata furta komai ba duk da alamar maganganunsansun ratsa ta,wucewa tayi library dinta hankalinta a tashe ta rasa inda zata sa kanta da soyayyar Deeni da ke azalzalar zuciya da ruhinta. Ta dauko wannan diary din da kullum ta rsinci kanta cikin kewa da rudani yake bata kwanciyar hankali in ta bide ta karanta,twyi ta kokarin budewa page by page amma ta kasa karanta komai,sai hawaye da ya cika mata idanu . Bata ganin komai haka ta dinga bide shi da sauri da sauri.</p><p> Ya biyota ya sa hannu ya karbi diary din.</p><p> ""Duk da abu ne mai muhimmanci a gareki Bahijja ni yana kona min zuciya ,ina kishi da shi,kishin gaske da ba na wasa ba nake yi da diary dinki.</p><p> Kiyi hakuri ina jin wani tashin hankali,Bahijja ina tare da tsoron rasa ki,duk da una da tabbacin kina sona,ina tsoran kar wannan diary din da dalilan da kika kirkiro dazu marasa tushe su sa na rasa ki..</p><p> Bahijja da can na yi hakuri amma yanzu ban san ta yaya zan fara wanann hakuri ba ,saboda abinda nakeji yanzu da can ban ji rabinsa ba . </p><p> Bahijja ni masoyinki me,me yasa zaki hana ruhinki abinda yake bege? Me yasa za ki cutar da mu ki kuntatawa zuciuar mu?</p><p> Muryarta na rawa tana kuka ,ta ce.</p><p> " Deeni saboda ina tsoro. Ina fargaba da tsoron son da nake maka,so ne mai yawan gaske ,son da yafi karfina,son da ya tilasta mini mika wuya ga soyayyarka,so mai radadi da ciwon gaske. Ina tsoro Deeni idan duniya ta raba ni da kai fa ? Ba zan iya wata rayuwar jin dadi ko sukuni ba tare da kai ba . Ina tsoron idan na bata makafa na ki aurenka saboda wasu dalilai da nake ganin zasu iya hana mu kasancewa tare ? Deeni shekaru uku na baka kai saurayi ne,ni bazawara ce,iyauenka ma ba zasu amince ba,nima in nayi haka ban maka adalci ba . Budurwa ya kamata ka nema ka aura ku more rayuwarku tare ""</p><p> ""Bana son budurwar,ke nake so. Bahijja ke nake so ,ko shekara nawa kika bani ke nake so ki zama abokiyar rayuwata. Iyayena ba ruwansu da aurena,wacce nake so ita zan aura,kuma zanyi alfahari da auren mace irinki."</p><p> " Deeni ina tsoro"</p><p> Ta fada cikin murya dishasshiya.</p><p> Ina tsoro Deeni,so na kake ko kuma ina cire maka keawar Farida ne ? Ina tsoron wataran kaji kana bukatar auren budurwa i dont want to rubish myself wato bam son wulakanta kaina,bana so ka aureni saboda ka rasa Farida ne ".. </p><p> "Ba haka bane Bahijja ,ke kika ja hannuna kika sa ni mancewa da Farida da soyayyarta"</p><p> "Wanann gaskia ne,amma soyayyar da nake miki na faara ta ne lokacun da soyayyar Farida ta kare a zuciyata,ki yarda dani ba Farisa a zuciyata ko kadan..</p><p> Farida matar wani ce,uwar wasu ce,na shafeta a babin rayuwata,SHAUKI NA YA SAUYA tun tuni,idan kika rabu dani akan haka ba ki min adalci ba,kuma zaki kuntata rayuwata,kyautar da kika mun na farin ciki a rayuwata za ki kwace shi. In kika yi haka za ki kuntata mana duka..</p><p> Ki tuna kece me fadakar da mutane akan wanann matsalar,yanzu kuma da yazo kanki sai ki nemi kauce masa ? Bahijja ina sonki,kina sona? </p><p> Girgiza masa kai tayi alamar eh hawaye na zuba,ta kwantar da kai tana kallonsa tana jin sonshi kamar zai hallaka ta,wani so da bata taba sanin akwai irinsa ba. ..</p><p> Ra ce,"Ina sonka Deeni so na sosai,ina kishinka,ba zan jure ba nan gaba in ka auro wata,saboda wani na kasu ko gazawa a tare da ni,Deeni bakin ciki zai kasheni a wannan ranar.."</p><p> Durkusawa yayi a gabanta yace ...</p><p> ""zan miki alkawari yau,ina kin yarda dani?</p><p> Ta girgiza masa kai.</p><p><br /></p><p> "Na baki kyautar kaina ke kadai,ba zan taba auren wata wai don saboda una bukatar budurwa ko don kina bazawara ba,idan na same ki MISBAH bana bukatar wata mace..""</p><p> Ya jawo diary din,"Gashi a rubuce ,ni Deeni mallakin Bahijja ne ita daya kawai👌🏼👌🏼👌🏼👌🏼👌🏼👌🏼..................</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Gaskia yau na rubutu,,sai bayan sati daya nida kuma yin posting😒😒😒ina jin wata ce tamun baki ,na dingi rubutu kamar an aiko ni wlh....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>SUMY LUV😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>47</p><p><br /></p><p>Kallon shi take tana jin wani nutsuwa a ranta,yadda dai Deeni ta amince masa tasan mutum ne da yake yin abinda yace,haka soyayyar sa ba karya ba yaudara,mutum ne mai gaskia da nagarta.</p><p> Tayi masa murmushi ,"Deeni ,ba sai ka rubuta ba,na yarda da kai,nima wanann halayyar taka ita taja hankalina gareka har na saki jiki da kai muka shaku. Sai dai nima zan rubuta maka na amince maka Deeni ka auri ko wacce irin mace a duniya in kana so,amma banda mutum daya FARIDA wacce nasan ka daina sonta,kuma matar aire ce. Amma ita ce mave daya da nake kishi a duniya,nake jin zafin kishinta a raina ,saboda nasan irin soyayyar da ka mata ba na wasa bane. Idan kuwa kaddara yasa ka aureta to duk hukuncin da na yanke zaka amince da shi.."</p><p> Ya yi murmushi,"Bahijja na haramtawa kai farida tun lokacin da ta zama matar wani,ba ciwon sonta na yiwa jinya ba sai ciwon Cin amanar da suka min. Amma duk da haka don ki samu kwanciyar hankali na amince.</p><p> Tayi masa murmushi me cike da kauna tana masa kallon so ,ta ce,</p><p> Deeni komai kake so matarka ta maka zan maka shi a rayuwa duk dadinsa ko wuyar sa ""</p><p> " Ina da yakini akan haka Bahijja,kuma nima zan miki duk wani abu da mijin kwarai ,uba na gari ga 'ya'yanki MISBAHna,Abokiyata,matata."</p><p> Dariya sukayi duka,sun jima suna hira sannan sukai sallama da kyar kamar ba zasu rabu ba.</p><p> </p><p> Soyayya mai tsafta da tsananin shakuwa ya kullu tsakanin Deeni da MISBAH,dukkan su suna son juna sosai so mai ban mamaki,dukkunsu kowa na aikin sa,sai dai wanann bai hana su bawa juna lokaci daga gidan gonar Deeni zuwa asibitin Misbah ba,nisan sa bai wuce tafiyar kafa ba.</p><p> Haka wata rana Deeni zai bat abinda yake ya je wurin Misbah yana kallonta daga nesa ko da bata sani ba baya gajiya da kallon ta,haka kullum sonta karuwa yake a ransa. Tana masa wani irin kwarjini,ya dinga jin sonta yana tsuma shi,yana godewa Allah da ya hada shi da MISBAH ,yana godiya da wannan shauki nata da yaje ji,fatansa da burinsa Allah ya bashi 'ya kamar MISBAH...... </p><p><br /></p><p> Ta bangaren Bahijja lokaci gida Deeni ya canja rayuwarta,ba ta taba zato ko tsammanizata tsinci kanta a wannan sabuwar rayuwar ba. Wani lokaci inta tuna irin soyayyar da take yiwa Deeni hankalinta na tashi saboda nata tsoron kar wani ya shiga tsakaninta da Deeni,don kuwa tasan tabbas bazata iya rayuwa ba Deeni ba. Don haka kullum tasa goshinta a kasa tayi sujjada sai ta roki Allah da ya mallaka mata Deeni matsayin abokin rayuwa ,ya mallaka mata deeni da zuciyar sa.</p><p><br /></p><p> Zaune take a office dinta idonta rufe ta tafi wani duniya tana hango rayuwar da za suyi da Deeni,tana jin son shi na tsuma ta. A lokacin ya shigo ya harde hannu a kirji yana kallonta yana murmushi,yana jin wani irin dadi a ransa.</p><p> Kamshin turaren sa mai karfi da dadin gaske ya dawo da ita hayyacinta,ta bude ido ta ci karo da fuskar sa yana mata wannan murmushin nasa da take so fiye da komai a rayuwa...</p><p> Itama murmushin ta masa ta zuba masa nata many manyan idanun ,ta ce...</p><p> "Har sakon zuciyar nawa ya isa gare ka ? </p><p>Ya fadada murmushinsa,yace ,"Wannan idanu suna kasheni da yawa ,suna tsumani ,suna gigita ni."</p><p> Nan ta sake lumshe masa su ta kuma bude su,sai da wani abu yaji ya tsirke shi har tsakar kanshi,yaji wani irin tsananin kaunarta da sha'awarta mai karfi yana shigarsa. Zai yi magana yaji muryarsa na shakewa,da kyar ya iya furta maganar...</p><p> Bahijja lokaci yayi da zamuci moriyar soyayyarmu,Bahijja ina bukatarki kusa dani,ba zan iya jure yin nesa da ke ba. Ina zaune yanzu fitinar sonki ya hana ni sakat ,na rasa sukuni ,na rasa inda zan sa kaina ..</p><p> Mayiwa baba. Waya nace masa Baba zan yi aure ,ya ce in kawo duk mayar da nakr so a duniya zai aura min ita,na ce masa na samu mata,na samu uwar 'ya'yana ,Doctor Bahijja,Abokiyata kuma likita ta. Ya taya ni murna ,ya min alkwarin mallaka myn abinda nake so ko menene shi indai bai fi karfinsa ba.</p><p> Na ce masa bana son komai sai Bahijja 'yarsa ce,shi babanta ne,'yarsa nake so ya aura min. Na masa alkawarin rike masa ita da amana,don haka yau mamanki da babanki zasu tambayeki wa kikeso? Ina fata zaki fito musu da gwaninki..</p><p> Kalamansa sun ratsata,kuma sun mata dadin gaske,wanda bata san yaishe ta fara hawaye ba. Tun tana 'yar karama take buri da sha'awar ta ga soyayyar uwa da uba,ta ga kauna da gata daga iyaye kamar kwacce yarinya ,amma ta san wannan burin nata ba zai taba cika ba. Muslihu ya so ya cika mata wannan burin ,sai dai hakan bai samu ba...</p><p> Bata san yaushe ta kifa kanta bisa hannayensa ba tana kuka..</p><p> "" Deeni ka gama min komai a rayuwa"""</p><p> ""Burina kenan Bahijja in faranta miki,inga na cika kowanne irin buri naki karami ko babba,duk da ke din ba mai buri bace."</p><p> ""Burina guda in mallaki Deeni da zuciyarsa "</p><p> Yayi mata murmushi,"Burinki ya cika my dear,ina jin dadin yadda kike sona Bahijja ,yadda kike nuna damuwarki da kulawarki a gareni.. Ina bukatar wannan har karshen rayuwarta..""</p><p> " kasamu Deeni,soyayyata da kulawata naka ne"</p><p> Yayi murmushi ,"Nagode ,anjima Mama zata zo ta tafi da diyarta gida don mata shirye-shiryen aure,saura kadan Abokiyata ta zama amaryata..""</p><p> Murmushi tayi tare da boye fuska saboda kinya ,musamman da ta ga irin kallon da yake mata.......</p><p><br /></p><p><br /></p><p> **** **** ****</p><p><br /></p><p> Da yamma Mama ta zo ta tafi da Bahijja tare da Baba Andi can gidansu Deeni,duk da tana jin wani iri da nauyin Mama amma ta daure sabodaDeeni..</p><p> Mama ta lura da haka,don haka tayi kokarin kawar mata da nauyin da take ji,ta ce.</p><p> "Bahijja ke diyata ce,soyayyar da kike wa Deeni shima yake miki ya sani sonki da kaunarki kamar 'yata. Ina godiya ga Allah da ya kawo ki rayuwar Deeni,don haka saki jikinki nan gidanku ne,zan miki duk wani abinda uwa zata yiwa diyarta ko shakar haka kar kiyi..""</p><p> Alhaji ya shigo yana jinsu ,shima ya matso ya ce.</p><p> Haka zan miki duk abinda amahifi zai yiwa 'yarsa Nsha Allah"" </p><p> "" Na gode Baba "</p><p> Ta fada kai sunkuye yayin da taji hawaye na kokarin ciko idonta,wani feelings ne da bata taba jin irinsa ba,wani irin farin ciki na daban taji yana ratsa ta.. </p><p> Allah abin godiya ,Allah mai kyauta da kari,ya bata miji da iyaye lokacin da bata zata ba balle tsammami....</p><p> Alhaji ya zauna gefen Mama ,ya ce,"Bahijja wane lokaci kika ga ya dace mu tsaida ranar aurenku?</p><p> Kanta sunkuye tace,"Baba ai ku iyayena ne,duk ranar da kuka ga ya dace ku ka tsayar dai dai ne.." Alhaji yace ,"To Allah ya miki albarka,ina so zan hada airen ku tare da lukman ,shima ya samu matar sa,sai mu hada muyi nan da sati biyu masu zuwa. In mun hada ku mun hutar da 'yan uwa masu zuwa daga nesa sau biyu,tunda mun shirya sai mu hada""</p><p> To Baba ,tafada kai sunkuye.</p><p> "To Allah ya miki albarka."</p><p> Nan ya mike ya fice,mama ta kalleta ta ce, </p><p> "To diyata zata zama amarya sai an bawa asibiti hutu ko saboda a bawa jiki hutu da nutsuwa""</p><p> Tsananin kunya yasa Bahijja kife kai,Mama na dariya ta ce.</p><p> "Na fada miki ni mahaifiyarki ce.."</p><p> Deeni dake tsaye yana kallon su ya tsinci kansa cikin wani irin tsananin farin ciki da jin dadi ,son mahaifan sa da kaunatsu yaji yana kara kardi a zuciyarsa.</p><p> ""Zan mallaki Misbah na nan da sati biyu Nsha Allah."</p><p><br /></p><p>A sati biyun nan mama tayi hayar masu gyaran amarya na musamman suka sa Bahijja gaba da gyara baji ba gani..</p><p> Mama ta fahimci nauyinta da Bahijja ke ji,wanann yasa ta damkata a hannun masu gyara da kuma aminiyarta Haj. Amina da tazo bikin da kanwarta...</p><p> Ya zame mata dole tayiwa matar Deeni gyara,Deeni gudan zuciyarta ne,zata iya komai don farin vikinsa,tunda Bahijja ce farin cikin Deeni ba zata yi wasa da ita ba...</p><p> Lokaci guda Bahijja ta canja,rayi wani irin kyau da haske me ban mamaki ,ta dawo tamkar wata Balarabita,duk inda ta wulga sai kaga tamkar anyi walkiya saboda tsabar haske da kyau da daukar ido da take ...</p><p> Deeni ya kasa daga ido akanta duk inda tabi yana binta da idanunsa,yana jin alfahari da samun mace irinta. Tabbas Bahijja ta ishe shi har iya karshen rayuwarsa,bashi da bukatar wata mace ......</p><p><br /></p><p> Ana saira kwana uku biki 'yan uwa da abokan arziki suka cika gidan wanda musamman Alhaji ya tura ticket na jirgi wa mutanen gombe da kaduna don zuwa bikin dan gatansa. </p><p> Daya bangaren na gidan aka warewa baki,yayin da bangaren su Hajiya sai aminiyarta da kanwarta tare da su farida da mahaifiuarta.</p><p> Dakin Deeni shi ua koma dakin Bahijja shi kuma ya koma gidansa na farm house sai dai kullum yana makale tsakanin idonsa kan Bahijja ,bai iya jure rashinta ko na kankanin lokaci...</p><p> Bahijja ta kasa gasgatawa kanta sabuwar duniyar da ta tsinci kanta,gata da kauna da take gani gun mahaifiyar Deeni da 'yan uwansa kadai ya isheta farin ciki,ballantaan kuma uwa uba Deeni..</p><p> </p><p> Bayan sallar juma'a jama'a da dama suka shaida daurin aurwn Deeni da Bahijja ,aure yayi albarka,dumbin jama'a ne suka cika a daurin auren. Bayan nasu aka daura na lukman da Amaryarsa Abida,duk a masallacin juma'ar unguwarsu aka daura...</p><p> Bayan daurin aure Mama ta shirya walima ta musamman ,abinci ba irin kalar da babu tun daga gargajiya har turawa. Wajen ya tsaru soaai,an gayyaci malamai mata masana da kuma 'yan uwa da kowa in ya ci abinci ya tofa albarkacin bakinsa.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ina kuke FANS din Dr Deeni Da Dr Bahijja 🗣🗣🗣🗣ranar da kuketa jira yau gata ta zo....... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>SUMY LUV😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Copied by SUMAYYA SA'AD❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>48</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka a wajen Alhaji ya shirya nasa da maza abokai da yan uwa a waje,kowa ya ga Deeni wannan rana yasan yana cikin tsananin farin ciki. Wannan ya kara kayatar da kyan fuskar sa.</p><p> </p><p> Cikin gida a daki Bahijja ta sha kwalliya da gayu sosai,duk da shiga mai sauki tayi,doguwar riga mai tsadar gaske ta sa wanda Mama tayi mata order daga Dubai. Blue ce ammata kwalliya mai sauki da fararen duwatsu,ya matukar karbar fatarta mai haske ,haka ya dad fito da kwalliya fuskarta. Ta tufke gashinta baki mai tsayi da sheki tare da lulluba gyalen rigar ,ta sa cover shoe masu tsadar gaske da ya yis shige da irin dressing dinta,ta sa bracelet mai saukin kwalliya tare da zobuna guda biyu wanda suka yi matukar kayatar da dogayen yatsunta.</p><p> Bahijja macece doguwa mai kyakkyawar kira,shigar da tayi tai matukar kyau da bata taba ganin tayi ba ,sai kamshi take.</p><p> Mama ta shigo ta ganta ita kanta tayi bala'in mata kyau,ta dinga ganin duk yawan taron nan ba kamar surukarta Bahijja ,tabbas ta amsa sunanta matar Deeni.</p><p> Tayi murmushi,"Tabbas diyata tayi kyau"</p><p> Tace,"Bari inje zan turo wacce zata zo ku tafi tare wurin walimar,duk an gama taruwa"" </p><p> Ita dai Bahijja kanta sunkuye har mama ta fita,shuru taji gidan yayi alamar duk an fits wurin walima. Tana nan zaune shiru zuciyarta cike da tunani kala kala taji motsin shogowa. Kamshin turarensa ya tabbatar mata da Deeni ne ya shigo dakin,nan tayi saurin daga kai suka yi ido biyu,yana mata wannan murmushin..</p><p> Ya zuba mata idanu,itama ta kasa dauke idonta a kansa,yayi mata kyau sosai. Sanye yake da blue shadda kalar nata kayan ya sha aiki,shigar ta matukar masa kyau. Hular da ya kafa a kansa ta kara fiddo da kyan fuskarsa,gashin kansa kwance irin na fulani sak,ga sajen da ya karawa fuskarsa kwarjini da annuri...</p><p> Ji tayi tamkar ta je ta fada kirjinsa ta kwanta,amma sai ta kasa saboda kunya duk da yana mijinta. Shi yasa hannu ya jawo hannunta yana wasa da 'yan yatsunta,tsigar jikinta taji tana tashi tana jin sonsa da shaukinsa yana ratsa jijiyoyinta,yana bin jikinta.</p><p> " Haba MISBAH na ,ya zaki kawar min da fuska,amaryata ki tuna fa ke halal dina ce yanzu,baki san irin jin dadi da tsananin farin ciki da fuskarki ke sauke mini bane da baki kawar da kai gare ni ba . A yau sai naji soyayyarki ta zama sabuwa ,ta zama danya sharaf a zuciyata. Toho gareni,please Bahijja ko zan samu nutsuwa.."</p><p> A hankali cikin nutsuwa ta matso gare shi ya jawota jikinsa tare da bata kyakkyawar runguma,tuni ta bace a cikin jikinsa,suna manne da juna tare da jin irin son juna da sha'awar juna..</p><p> Cikin muryar rada yake mata wasu irin kalaman soyayya masu ta da hankali da tsuma zuciya da ruhinta.</p><p> Nagode Bahijja da soyayyarki,wannan shi ne (the most beatiful moment of my life)..</p><p> Rufe ido tayi jin kalaman sa na ratsa ruhinta,tana shakar kamshin sonta tare da fadin.."Deeni ina sonka ,kai nawa ne ni daya,mallakina ni daya.."</p><p> Haka ne Bahijja ni naki ne ke daya kamar yadda kike ke tawa ce ni daya,bana taba hada ki da kowacce mace a duniya,haka ba zan taba hada soyayyarki da kowa ba""</p><p> Sun jima a cikin wannan halin na tsananin shauku da son juna..</p><p> </p><p> A hankali ta turo kofat tayi sallama amma shuru,hakan yasa ta kutsa kai,Farida kenn..</p><p> Gabanta yayi mummunan faduwa ,ya dinga bugawa da karfi ganin Deeni da Bahijja a hakan ya mummunan daga hankalinta.</p><p> Wani irin masifaffen kishi taji yana turniketa,masifaffen kyan da ta ga sunyi da Deeni da Bahijja ya razana ta tamkar dama an halicce su don juna ne. Tsohuwar soyayyar sa taji ta taso mata ta kasa gani da jure soyayyar da taga Deeni yana yiwa Bahijja wanda ita duk tsananin soyayyar da suka yi a baya ta dinga gani kamar wancan soyayyar wasa ce..</p><p> ''Ya za'ayi Deeni yaso wata mace a duniya fiye da ita? Ya za ayi Deeni ya ci amanar kauna? (Readers kuji fa karfin ) Na zata Deeni zai yi aure ne ba don soyayya ba sai don raya sunnah kamar yadda nayi,ya za'ayi Deeni yaso wata fiye da ni ? Har yau ban taba son wani fiye da shi ba ,duk da nayi aure na zama uwa amma soyayyarsa bai taba barin zuciyata ba ko na second daya. Ya zanyi in rayu da wannan bakun ciki da bacin ran da na gani yanzu. ???(To jama'a farida na tambaya)....</p><p> Nan ta sake daga kai ta kalle su,har yanzu suna wata duniyar . Ta kalli kanta ta kalli Bahijja sai taga ta mata nisa,ta mata fintinkau nesa ba kusa ba...</p><p> ""Shin ni ya akayi na kasa hada Deeni da kowanne irin namiji a duniya ? Tabbas saboda Allah bai taba hadani da namijin da ya kaishi bane,yayin da Allah ya hada Deeni da macen da ta fini."</p><p> Kau da kai tayi taji hawaye na zuba mata,tsananin kishi da son Deeni taji yana shigarta,ta macen da abinda ya kawota,ta mance da cewa ita matar wani ce,uwar wasu ce....</p><p> Karar wayarta ce ta dawo da su hayyacinsu duka,nan tayi saurin share hawayen yayin da Deeni da Bahijja suka ganta bazata a gabansu..</p><p> Ras !!! Bahijja taji gabanta ya fadi,ita ma din kishin farida taji ya shigeta,har yau in ta tuno irin soyayyar da Deeni da Farida sukayi sai taji hankalinta ya tashi...</p><p><br /></p><p> Deeni ganin Farida a gabansa bazata tana kallonsa tamkar ta hadiyeshi yasa ya ji ya shiga dan rudani,musamman da ya san yadda Bahijja take da kishin Farida a zuciyarta,duk da ya sha nuna mata cewa Farida ba ta gabansa yanzu,amma ta kasa fahimta. Sam ko kadan babu ita a ransa,amma ya rasa dalilin da yasa yaji ya wani irin rudewa a wannan lokacin...</p><p> Bahijja na kallon irin rudewar da yayi yasa taji ranta ya mummunan baci,hankalinta ya tashi .</p><p> Dukkan su idon su ya rufe da wani irin kishi,musamman irin kallon da Bahijja ta ga Farida na yiwa Deeni. Yayin da Farida ta dinga jin kishin irin kallon da Deeni ke yiwa Bahijja...</p><p> Nan faridan ta daure,tayi dariyar yake ,ta ce....</p><p> ""Ango da Amarya ,ina tayaku murna,Allah ya bada zaman lafiya.."</p><p> Bahijja bata iya ta amsa ba,sai Deeni ne ya amsa a takaicw,yasa kai ya fita..</p><p> Farida ta kalli Bahijja tace,"Amarya,Mama tace in fito da kee ana jiranki wurin walima""</p><p> Girgiza kai tayi dakyar ta cije tayi dariyar yake,ta fito suka jera tare..</p><p><br /></p><p> Tunda ta fito idon kowa ya koma kanta ta fito ta haska wajen gaba daya kowa sai albarkacin bakinsa yake fadi,Mama kanta ta kasa hakuri ,ta taso da fara'arta ta zo ta kama hannun Bahijja ta jata gun zamanta. Wannan ya kara bakanta ran Farida,har agun mama ma Bahijja ta ture gwamnatin ta ...</p><p> Wani hawayen bakin ciki taji yana zubo mata ,wurin walimar da bata zauna ba kenan,ta juya ta koma ciki,har aka tashi daga walimae bata dawo ba....</p><p><br /></p><p> Ranar lahadi jamaar biki kowa ya watse ,yayin da ranar lukman ya tare da amaryar sa a gidansa da mahaifin su ya bashi,yayin da Shamsuddeen ya koma saboda aikin da ya bari a kamfaninsu na kaduna. Farida kuwa da yake ana hutu da yaara za su zauna su yiwa mama hutu...</p><p> Mama ta shiryawa Bahijja da Deeni kayansu,siyayyar da ta musu na kayan sawa da sauran su ta sa a mota ta tura tare da baba andi taje ta shirya musu.... </p><p><br /></p><p> Gidan yayi tsit ba kowa daga Farida da yaranta,sai Deeni da Bahijja wanda suma suna shirin tafiya nasu gidan....</p><p><br /></p><p> Alhaji ne ya kira Deeni da Bahijja falo suka same shi yana zaune shi da mama ,nan suka nemi wuri suka zauna.</p><p> Alhaji yayi musu nasiha da fada sosai tarw da musu fatan alkhairi haka mama ta kara damka musu amanar juna tare da musu nasiha da cewa siyi hakuri da juna,zo mu zauna zo mu saba..</p><p> Alhaji ya mika masa key na gida.</p><p>ya yi murmushi ,"Nagode Baba,mallaka min Bahijja da kayi matsayin nata ta kadai ya ishe ni babbar kyauta. Ka mata waliyyanci,ka zama mahaifinta,yayin da Bappah ya min waliyyanci. Na gode da amanar yarka da ka bani Baba,ina da gidana nallakina na godan gona wanda ka taimaka min na kafa shi,haka Bahijja tana da gida,zamu zauna a duk wanda muke so. A halin yanzu rayuwar mu soyayyarmu ,ayyukanmu,gidajen mu da dukiyoyinmu suna hake ne. Baba,Mama,mun gode ,kuyi ta mana addu'a,muma zamuyi ta muku.."</p><p> Dariya sukayi yayin da yace,"Allah ya muku albarka Deeni"</p><p> ""'Ameen """.</p><p> Suka amsa a tare ,sannan sukayi sallama da su mama ta raka su har bakin mota ita da Bahijja kamar ba zasu rabu ba.</p><p> Wannan soyayya da shakuwa na Bahijja da Mama ba karamin dagawa Farida hankali yake ba,sai tana ji kamar ta zama ita bata da mihimmanci..</p><p> Tabbas daga Farida har Bahijja suna fama da kishin juna da ke tsananin cin su a zuciya..</p><p> Kai tsaye suka wuce gidan Deeni ,wanda ya ra tsara musu shi sosai,kana shiga gidan zaka fahimci gida ne na masu ilimi daga bokin har addini...</p><p> </p><p> Tun a mota Deeni ya lura da Bahijja bata magana,duk kokarin da yayi don ya takaleta amma bata kula shi ha,shima sai ya nuna mata halinsa,ya dage kai ya kyaleta..</p><p> Addu'a tayi sannan ta sa kafarta a gidan ,wani irin kamshi taji yana tashi mai kwantar da zuciya.. Ta lumshe ido tana shaka,nan take taji hankalinta na kwanciya ,fushin nan da take taji yana sauka. A hankali ta dinga bi tana zaga gidan ,Deeni ya bita danido zuciyarsa cike da sonta da sha'awar ta.</p><p> Ko ina ta gama zagawa yana biye da ita,ta dawo falo ta zauna,nan ya jawo kujera ya zauna a gabanta yana kokarin su hada ido amma taki. Ya yi murmushi ,yace..</p><p> Haka kawai Amarya taji bata son sakar min fuska a daren mu na farko a gidan mu ?</p><p> Zuba mata ido ya yi yaji kamar yanzu ma ya fara sonta..</p><p> Ina sonki Bahijja soyayyar da ban san irinta ba,komai kika yi a rayuwa sai inga ya miki kyau. Wannan kamshin da ake sha min ma sai naga ya miki kyau,kin kara burgeni"".</p><p> Nan ya sauko yasa kanshi bisa cinyoyinta ,ya jawo hannayenta kansa.</p><p> MISBAH na meye ya dame ki ?</p><p> Ta kwantar da kanta akan nasa suna manne da juna ,ta ce.</p><p> (My dear nice house)".</p><p> Ya yi murmushi ,yace. Na tabbatar u will be a good home maker?" </p><p> Nsha Allah"Ta amsa.</p><p> "Deeni ina sonka"</p><p> Ta fada tamkar meyin rada a kunnen sa,yana jin muryarta na ratsa shi,yana jin tsigar jikinsa na tashi ,tsantsar sha'awarta cike fal zuciyar sa.</p><p> ""Bahijja ki kasance dani har abada karki kyale ni,ki cika min gida da irinki da alnarkar ki,ki cika min gida da yaranki,zaki sani farin ciki sosan gaske""..</p><p> "" Komai kake so zan maka Deeni,,Allah ya bani yaran da zan cika masu. Nima ina addu'ar Allah ya bani irin Deeni,Allah ya bani ikon sanya ka farin ciki da kyautata maka,Allah ya bani juriya akan ka Deeni..</p><p> Ina maka wani so Deeni,gashi dai ka zama nawa amma zuciyata na cike da tsoro da fargaba." </p><p> "" Kar kiyi fargaba Bahijja,ni naki ne ""</p><p> Bai ankara ba sai jin hawaye na zuba masa yayi Saurin dago ta hankalinsa a tashe..</p><p> My deae mene ne ??</p><p> Idonta jawur ta kalle shi,"ko zaka iya fassara min rudewar da kayi lokacin da kaga Farida ??? Na mene ne ?? Don kaji tsoro masoyiyarka ta gannu a manne da juna ko kuma ka rude ne saboda ka ga tsohuwar masoyiyarka ???</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tofaa!!!! Ango kaka-kara kaka.........</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>SUMY LUV😍😍😍😍</p><p>👩🏽🔬👩🏽🔬MISBAH👩🏽🔬👩🏽🔬</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by SA'ADATU WAZIRI GOMBE</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>=================== GIDAN NOVELS ====================================</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Assalamu Alaikum</p><p> Yan uwa a wannan page din nake tunanin zan kammala littafin nan part 2 wato kashi na biyu insha Allah...</p><p>Wanda kuma a nan nake tunanin dakatawa zuwa bayan sallah in Allah ya kaimu.......</p><p> Idan da me korafi nasan dayawa sunada contact dina,,,so se yayi pinging dina.....tnks </p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>49</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zura mata ido yayi cike da mamaki,"Haba Bahijja,ban zaci haka daga gareki ba,wannan halin na zace shi ne daga halin wata me kasa da shekarunki, (me matured)" </p><p> Ranta taji ya mummunan baci,ta ce.</p><p> I will not be ,me kake nufi? Me yasa kake avoiding tambayata ? Ka fada min wane irin rudewa kayi don kaga Farida. ??</p><p> Ranshi yaji ya baci,amma sai ya daure ya ce.</p><p> Ke kinga ya dace mu zauna muna bata lokacinmu a irin wannan lokacin akan wannan maganar marabtushe ko kan gado ? Me ya kawo maganar Farida tsakanin mu a yanzu ? </p><p> "Akwai abinda ya kawo,ka ban amsa,me yasa mijina zai rude don yaga tsohiwar budurwarsa ?</p><p> For God sake!!Farida matar wani ce,uwar wasu ce,saboda mene ne zaki ta da min rigima yanzu ? Har sau nawa zan fada miki cewa bana son farida,na manta da farida. In ada baya can na so farida laifina ne da za ki dinga daga min hankali akan farida? Haba Bajijja ,a yau zamu fara sabuwar rayuwa,ya zaki bari wani dalili mara tushe ya nemi kawo mana matsala ?</p><p> To naji ya ishe ni haka, kiji kiyi tunanin duk yadda ki ka ga dama ,na ganta na rude sai yaya ?""</p><p> Cikin zafin rai da bacin rai yake maganar wanda ya kara tunzura Bahijja,ya kona mata zuciya. Ta fashe da kuka ta nufi daki ta rufe ....</p><p> Bai yi yunkurin binta ba don shima yana cikin zafi,ya zurawa abubuwan da ya shigo musu dashi na ci da sha ,duk ta daga musu hankali har ya ji bashi da sauran sha'awar cin wani abu.</p><p> Kukanta yaji yana matukar daga masa hankali,ga sonta dake kara ruruwa a cikin zuciyarsa,amma zafin zuciya ya hana ya bita dakin balle yayi lallashi. Haka ya dinga kaiwa da kawowa cikin dare,ya rasa me ke masa dadi,haka suka kwana baran-baran a darwnnsu na farki..</p><p> </p><p> Ankira sallar asuba yayi alwala ya murda kofar dakinta,ga mamakinsa bata sa key ba ya sameta zaune kan sallaya. Bai ce mata komai ba ya fice zuwa masallaci,ya dawo ya nufi nasa dakin ,duk da ya kwanta ba bacci kirki amma haka baccin ya gagare shi..</p><p> Karfe takwas na safe ya fito falo,anan suka yi kicibis sanye da hijabinta...</p><p> ""Ina kwana?"" Ta fafa tare da kau da kai </p><p> Bai amsa mata ba ya sha gabanta ,tayi saurin kaucewa ta kama hanyar fita..</p><p> "Ina zakije ? Ya fada cikin daga mirya.</p><p> Gidana zan tafi".ta bashi amsa a takaice.</p><p> Da izinin wa ? Da yardar wa ? Karki manta baki da gidan da ya wuce wannan,sannan fita a gidan nan ba da izinina ba,kar ki sake wanann kuskuren....</p><p> Ya fada cikin tsare gida ,fuskar sa ba alamar wasa,ya juya..</p><p> Wani iein bacin rai da takaici taji ya turnike ta,ta juya ta nufi kicin ranta bace ta dinga kaiwa da kawowa ,gata ba gwana ba wurin girki,da kyar ta samu ta hada masa patatos da source tare da yanka fruit da fresh juice da kuma ruwan tea a flask tare da sauran kayan tea ta jera kan dining table..</p><p><br /></p><p> Yayin da Deeni yake kaiwa da kawowa ,sam baiji dadin yadda ya mata ba,to amma yana da matukar muhimmanci tasan cewa shi mijinta ne,aure sukayi ,ba zata yi yadda take so ba. Haka nan zafin zuciya da jin kai ya hana shi zuwa ya lallasheta,don shi gani yake bai mata laifi ba..</p><p> Bahijja na shiga daki ta fashe da kuka,nan ta dauko diary din nan cikin jakarta ta rungume tana kuka...</p><p> Hankalinsa ya kasa kwanciya har sai da ya bita dakin ganunta rungume da diary din tana kuka sosai ya taba zuciyarsa. Abu biyu ne suka hadu masa,tsananun sonta da tausayinta da kuma wani zafin kishi,saboda yasan me ke cikin wannan diary din .</p><p> Nan ya daure ya isa gareta ya jawota jikinsa,nan ta hau kokawar kwace jikinta amma bata yi nasara ba. Ya rufeta ruf kan faffadan kirjinta,ga turarensa mai hade da kamshin sin sa da ke ratsa ta ,yana kashe mata jiki,kawai ta fashe masa da kuka..</p><p> ( I'm sorry my dear)nayi laifi kiyi hakuri..</p><p> Ya fada cikin murya mai taushi da lallashi. </p><p> Bahijja hawayenki da kukan ki yana daga min hankali fiye da komai,kin san yadda nake matukar jinki a raina ,kin san yadda jiki da euhina tare da zuciyata suke tsananin sonki ,please Bahijja kar ki daga mana hankali daga ni har ke.</p><p>Ba mai samun farin ciki a kan wannan halayya taki na kishi (I'm sorry l hurt you).</p><p> Bahijja da ina da ikon share baya da na share,amma bani da wannan ikon,abinda zan iya shi ne yanzu-yanzu kuwa da nan gaba duk kece.</p><p> Bahijja ina so kamar yadda kika taimaka min na manta baya na cigaba da rayuwata ina so ki taimaka ki bani hadin kai ,mu shirya rayuwarmu mai cike dab tsabtatacciyar soyayya da fahimta tare da kula da farin cikin juna...</p><p> Ina so ki sani kina da matukar muhimmanci a rayuwata,please dont make me hurt you again.."</p><p> Ta fashe da kuka,"Deeni na gaza ban san mw yasa na kasa jurewa ba,ban san me yasa nake jin tsananin kishin Farida ba ,duk da na sani matar aure ce,matar dan uwanka ne,uwace. Deeni ka taimake ni,zan iya jure komai anma banda wannan.."</p><p> Ta dago dara-daran idanuwanta wanda sukenrine,suka dawo ja,hawaye na zuba wanda yanayinta ba karamin tsuma shi yayi ba,ta ce ,</p><p> ""Deeni kasan ina sonka ko? Ina sinka sosai "" Ya girgiza mata kai yana jun tamkar ya hadiyeta don so ,ya ce.</p><p> Nima ina sonki Bahijja kin san haka kuma. Ina sonki"</p><p> Ta kankameshi ,"Nasani Deeni ,"please ka kula dani..</p><p> "Zan kula da ke Bahijja na,bari ma in fara daga yanzu."</p><p> Nan yasa baki yana lasar hawayenta tare da bin fuskarta,kan idanunta zuwa wuyanta yana sumbata. Haka ya dinga bin jikinta.</p><p> Wani irin abu taji yana zaga jikunta har zuwa tsakar kanta,yayin da ta dinga jin wannan kuncin yana barin zuciyarta,sai tsananin so da shaukinsa,taji zuciyarta ta wanke tas. Nan ta biye masa itama ta ramawa kura aniyarta..</p><p> Sun jima manne da juna sannan ta zame jikinta a hankali ta nufi bayi don shirya masa ruwan wanka,yayin da Deeni ke kwance idonsa jawur,hankalinsa tashe.. (Deeni dai ba wanka yakeda bukata ba🙈🙈🙈🙈🙈🙈sry anty zee karkice banda kunya)..</p><p><br /></p><p> Kwarai ya so kasancewa tare da ita yau,sai dai kasancewar Bahijja na farko ya zamana a wuri na daban lokaci na daban.......</p><p> Karfe goma mama ta turo musu da break fast kala-kala,sannan tayi waya suka gaisa ta kara da cewa su shirya jirgin su zuwa kasa mai tsarki,wato saudia. Karfe sha biyu ne wanda ta biya musu suje suyi Umra su kara yiwa Allah godia tare da yin addu'o'i,sannan daga nan in suna so su wuce duk kasar da suke so su zaga duniya har na wata guda ,sannan su dawo.</p><p><br /></p><p>***** ***** ***** </p><p><br /></p><p>A kasa mai tsarki Deeni da Bahijja suka san sirrin juna,suka zama abu guda,,suka barji gumin juna. Kwarai sun more rayuwar su yadda ya kamata ....</p><p> Bayan sun gabatar da idabar su ta Umrah tare da yin addu'o'in su,nan suka ci gaba da gudanar da ibadar su na aure ,sun manta duk wani damuwa da bacin rai da tashin hankali da suka taba fuskanta a rayuwa ,suka bude sabon rayuwa mai cike da farin ciki da kwanciyar hankali tare da yiwa juna alkawarin kula da juna farin cikin juna da kuma kasancewa da juna har abada Nsha Allah...</p><p> </p><p> Bahijja na da kyau na daukar hankali,kyau mai sa nutsuwa da kwanciyar hankali ga wanda ya mallake ta,yasan sirrin ta,ya dandani zumar ta. Don haka Deeni ya tabbar shi din mai sa'a ne da ya mallaki mace kamar ta...</p><p> Duk inda ake son mace Bahijja ta kai ta kawo,sai dai abinda yake kara jan hankalin sa gareta da kara masa sonta shi ne halayyar ta,hikimar ta da baiwarta. Yadda take kula da shi,take sarrafa shi da rayuwar sa,irin soyayyar da take masa,take kuma nuna masa,ga wata girmamawa ta musamman . Duk da kasancewar ta girme masa amma bata taba nuna masa raini ba,asali ma in ba an fadi ba babu mai cewa ta girme masa,saboda bala'in dacewa da sukayi da juna ...</p><p> Halayyar su ta zo daya,tunaninsu yazo daya,duk abinda daya keji dabshi daya naji da shi. Don haka suke yawan hakuri da juna ,in data ya hau daya na dannewa,sun zauna sun tsara yadda za su gabatar da rayuwarsu cikin soyayya da saukin rayuwa..</p><p> </p><p> Bayan sunyi sati biyu suka bar saudia zuwa Dubai,sun zaga kasashe uku zuwa hudu suna yawon shakatawa da more rayuwar su. Sunyi wani irin sabo da kara shakuwa da juna sosai sosai..</p><p> Sun kasance cikin farin ciki marar misaltuwa ,watansu guda suka tattaro suka dawo gida Nigeria..</p><p> A nan suka tarar da mummunan labari da kuma mummunan tashin hankali na rasuwar Shamsuddeen tare da mahaifin Farida...</p><p> Satin su biyu da tafiya hatsarin ya faru da su a cikin garin kaduna,mahaifin Farida ya je duba Shamsu a ma'aikatar su don ganin ya yake da yadda ayyukan suke tafiya,dama ya saba kai masa irin wannan ziyarar . Anan Shamsu ya bar motarsa a office ya biyo Alhaji Ahmad don dawowa gida tare ,a hamyar su ta dawowa tsautsayi da karar kwana suka hadu da doguwa ta taho ba birki ta hade motoci da yawa tayi barna wasu sunji rauni wasu sun rasa rayukansu ciki har da Shamsuddeen da Alhaji Ahmad wato mahaifin Farida.</p><p> Cikin tashin hankali da damuwa Deeni da Bahijja suka nufi kaduna inda ake zaman makoki....</p><p><br /></p><p> Muje ga littafi na uku...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>DANDANO DAGA LITTAFI NAGABA</p><p> </p><p> kanta sunkuye gaban su ya ce,"Mama ina jinki ""</p><p> Hajia ta kalli Bahijja ta ce,""Bahijja kin tabbar kin amince ina sonki kamar yadda nake son Deeni ko ? Kin dauke ni mahaifiyarki ?</p><p> Bahijja ta girgiza kai,ta ce,"Kwarai Mama,tsakanina da ku sai addu'a ,bani da iyaye amma kun maye gurbin su,tsakanina da ku sai addu'a"</p><p> Mama tayi murmushi ta ce,Alhmadulillah,kamar yadda na rike ki 'yata haka ba riki farida,ina neman alfarmarki bamu hadin kai mu hada auren Deeni da Farida.......🙆🏻♀🙆🏻♀🙆🏻♀</p><p><br /></p><p><br /></p><p>SHIN WANNAN MUTUWAR TA SHAMSU FARIDA AKAYIWA KO BAHIJJA ???????</p><p> SAI NA JIKU</p><p> TAKU HAR KULLUM </p><p><br /></p><p>=================== GIDAN NOVELS ====================================</p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-469701165744484222021-12-02T06:03:00.001-08:002021-12-02T06:03:23.836-08:00JASEENA COMPLETE HAUSA NOVEL<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEg-uweSlel_xbSfC1k53ex1hXdgg-SnU1VGJY3AdH_MJMR1oqupRVhM841wyH9e3d10jNiS06qTszGlueKUkDFKtSGGGxeGaj7pxqFsNRwXWrOI_c3w9kHTiuRrYUmggBerq1uCVAx7nJjnawaFLMuHjkKYku4KmGQ_6iHjfN39OVHjDg86P4S3Mirg=s2048" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="JASEENA COMPLETE HAUSA NOVEL" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="310" src="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEg-uweSlel_xbSfC1k53ex1hXdgg-SnU1VGJY3AdH_MJMR1oqupRVhM841wyH9e3d10jNiS06qTszGlueKUkDFKtSGGGxeGaj7pxqFsNRwXWrOI_c3w9kHTiuRrYUmggBerq1uCVAx7nJjnawaFLMuHjkKYku4KmGQ_6iHjfN39OVHjDg86P4S3Mirg=w400-h310" title="JASEENA COMPLETE HAUSA NOVEL" width="400" /></a></div><br /> [3/2, 5:44 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃 JASEENA🦃⚔ 2016<p></p><p>🐚Na Jeeddah jao🏵🐚</p><p> 1⃣⏯5⃣</p><p><br /></p><p> Gudu yake kan wani farin doki mai kyaun gaske da ka ganshi kasan a rude yake ,wata mata ce a bayanshi ta ‘kank’ame shi sai zare ido take yi yayinda shi kuma sai ‘kara gudu yake ,da an hau tudu ko tsauni sai matar ta sa ‘kara ta rike ciki da hannu daya, da ‘kyar ya samu wani kogon dutse ya shige ga dukkan alamu Matar na’kuda take yi domin dauke take da juna , ‘karar dawakai da yaji sun tukaro inda kogon yake yasa ya toshe wa Matar baki da hannun shi ganin tana kuka duk jikinta yana b’ari ,mutanen suka gama dube -duben da zasuyi sai wani daga ciki yace “sun yi nisa sosai!! Mu koma kawai ,a lab’en da suke babu wanda ya motsa har mutanen suka tafi sannan ya cire hannun shi daga bakin Matar da tuni na’kuda ya zo mata gadan-gadan, Allah cikin ikonsa ya jiyo ‘karan ruwa daga d’ayan ‘bangaren kogon ya mayafin ta ya nufi hanyar da gudu ,kafin ya dawo ma har ta haifu Yar cikin Jini Kwance a ‘kasa itama uwar haka ,ruwan da ke jikin tsumman ya d’an matsa a fuskar ta ta dan farfado ,shi da kanshi ya gyara yarinyar ya mik’a mata. Murmushi take yi tana hamdala amma hawaye ne zafafa ke bin kuncin ta ,ta sumbaci yarinyar sannan ta rufe idonta hannunta ta sa ta damk’e hannun mutumin wanda da ka ganshi kaga sadauki, tana salati rai yai halinsa.<span></span></p><a name='more'></a><p></p><p> 🦂wani ‘kara mutumin ya saka wanda duk kogon sai da ya d’auka, ya kifa kai a cikin matar yana ta rusa kuka mai ban tausayi ,idanuwan shi suka rine kamar garwashi ya mik’e tsaye ya d’aga jinjirar sama cikin murya mai firgitarwa yace” masarautar KALAHARI !!! Sai na mayar muku jin dad’i da walwala !! Na lashi takobi!! da ikon Allah sai JASEENA ta zamo ciwon ido ga azzalumi JALALUD-DEEN!!!!</p><p><br /></p><p> 🐚 🐚🦂🦂🦂🦂🦂🦂🦂🦂🐚🐚</p><p>Asalin labarin</p><p><br /></p><p> Masarautar Kalahari babbar masarauta ce wanda ake sakota a matsayi na farko cikin jerin masarautu, mai kuma cike da tarihi, mayak’a da kuma kayan ma’adanai na ‘kasa kamar su lu’ulu’u , gwala-gwalai da sauransu. Sarki Hameed shine ke mulkin Wannan masarauta, mutum ne jarumi ,mai tausayin talakawa gashi da kwarjini. Hameed shine d’a na biyu kuma na k’arshe gun mahaifin su ,ma’ana yana da wa mai suna JALALUD-DEEN ,wanda ya kasance baya son talakawa kuma shi duk abunda zai yi in dai don ya musguna ma talaka ne toh ya fi burgeshi, son zuciya gareshi , hakan ne yasa da aka tashi bada sarautar sai dattijawan gari suka zabi a bawa Yerima Hameed kasantuwar d’abiun sun daban ne kwata kwata JALALUD-DEEN bai chanchanta ya mulki Kalahari ba, a fuska JALALUD-DEEN ya nuna babu wani abu amma dai na ciki na ciki !!domin zuciyar sa tafarfasa takeyi kuma a nan ne ya k’udiri niyyar ganin bayan Hameed !!!</p><p><br /></p><p>Jeeddah jao🏵</p><p>[3/3, 7:07 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵 Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p> 6⃣⏭1⃣0⃣</p><p><br /></p><p>Bayan an na’da Yerima Hameed a matsayin sarkin Kalahari sai Jalalud-deen ya fuskanci cewa matar sarki Hameed Sarauniya JASEENA tana dauke da juna biyu hakan ya tunzirashi ya kasa zaune ya kasa tsaye ko baccin kirki bayayi tsabar Kishi domin gani yake yi in har Hameed ya samu magaji to tabbas babu makawa ko ‘kamshin sarautar ma zai daina ji…………</p><p><br /></p><p> 🏵cikin Sarauniya Jaseena yana wata tara ,haihuwa ko yau ko gobe ,tana zaune cikin dakinta mai cike da kayan ado da k’yal-k’yali sarki Hameed ya shigo ,mutum ne mai tsayin gaske ga haske kyakkyawa ne wanda ba sai na tsaya misalta shi ba haka ma Jaseena kasantuwar a kasar masar ya auro ta , zama yayi kusa da ita yana zolayan ta suna ta hira ,basu ankara ba sukaji ‘kara a waje ,a tare suka mik’e cikin firgici Jaseena ta rike Hameed ta ‘boye ta bayan shi jiki na rawa yayin da shi kuma ya zare takobin shi 🗡ya rik’e yana dube-dube don yaga ko waye zai shigo Kwatsam sukaji an banke k’ofa kamar daga sama mutanen suka yo kansu nan suka kaure da fad’a ,gashi mutanen fuskar su a rufe da kyar ya iya fisge mayafin d’aya daga cikin su ,abun da ya gani ya matuk’ar girgiza shi !!! Amintaccen shi na fada ne Zakar da wasu wanda ya tabbata fadawan shi ne ,da yaga sarkin yawa ya fi sarkin k’arfi kaway ya figo Jaseena suka fita yayinda mutanen suka bi bayansu ganin Jaseena ta gaza yasa ya kwantar ta bayan wani k’aton tukunya yace yana zuwa ,cikin sand’a yake tafiya har ya isa gurin da dawakai suke ,fito kawai yayi wani kyakkyawan ingarma ya nufoshi fari ne fes ,ya shafa kan Dokin sannan ya haura shima ya nufi inda ya bar Jaseena,ya sameta yanda ya barta cikin ciwon na’kuda ,take ya umarci dokin da ya kwanta ,hakan yayi ma Jaseena daidai yanda zata samu sauk’in daidaitawa a saman dokin ,kafin su ankara sukaji harbi kibiyar ta chaki Jaseena ta gefen ciki ganin sun kusa far musu yasa ya fita a d’ari da dokin suma suka hau dawakai suka bi bayan su har suka samu suka shiga Wannan kogon dutsen……..</p><p><br /></p><p>🦃🦃🦃🦃🦃 JASEENA. 🦃🦃🦃🦃🦃</p><p><br /></p><p> Hameed ya d’auki gawar Jaseena ya fito bakin kogon ya tsaya , kasantuwar bai taho da komai ba daga shi sai takobin shi haka ya dinga tono da Wannan takobi har rana ta fito yayi gumi ba na wasa ba hannuwan sa duk sun salube sun ya’yyanke har saida ya gama tono ya sallace ce sannan ya binne ya d’au takobin ya koma cikin kogon ya zauna ya k’urawa jaririyar ido ,tsananin tausayin ta ya kama shi kasantuwar ta zo duniya ne lokacin da uwarta take gangaren barin duniya ,gashi shi bashi da abincin da zai ciyar da ita gata kuma abar tausayi kasancewar ta bak’uwa a duniya ,ya d’aga hannayen sa biyu yace ” ya Allah ga baiwar ka ta zo duniya lokacin da zalunci ya mamaye al’umma Kowa burinshi yaga shine a gaba ,Allah na rok’eka ka raya ta kan tafarki madaidaiciya kuma ka bata ikon kare hak’k’kin duk wani wanda aka zalunta a gaban idon ta ,ya Allah ka kareta da ikon kariyar ka!!!</p><p> 🏵 Kukan Jaseena(sunan mahaifiyar ta ya maida mata) ne ya katse shi ya je da sauri ya dauketa ya rasa ta inda zai fara domin kuka take na fitar hankali ,kamar ance d’aga kanka sama kawai ya hango wani haske ya hasko cikin kogon kuma ba daga asalin k’ofar da ya shiga ba ne, ya mik’e ya nufi gurin dokin shi ma ya bishi kasantuwar kogon makeken gaske ne …..,</p><p><br /></p><p> Abunda idon shi ya gane mishi yasa ya zaro idanuwa ya d’aga hannu yana godiya ga Allah .,……..,🦃</p><p><br /></p><p>Jeeddah jao🏵</p><p>[3/3, 11:10 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔</p><p>🐚🏵Jeddah ja’o 1⃣1⃣⏭1⃣5⃣ Wata sabuwar duniya ce domin kogon nan zagaye yake da wani dutse wanda tsakiyar Wannan dutse ya kai girman rabin masarautar Kalahari gashi kuma jeji ne sosai mai yawan duhuwa ,kayan itatuwa kuwa babu kalar da babu ga ruwa yana gudana daga saman dutse tsuntsaye sai shawagi suke a gurin ,🕊🕊 , ‘kara da yaji ta wani 6angaren ya tabbatar masa akwai namun daji ciki kuma masu cike da had’ari🐅</p><p><br /></p><p> 🦃ya ja dokin sa har inda ruwan yake hannun shi d’aya kuma rik’e da Jaseena. Ruwa ne mai kyaun gaske ,yanda yake gudana ma abin kallo ne a nan ya dauraye jikin Jaseena dokin shi ma ya sha..nan ne fa Hameed ya fara sabuwar rayuwa daga shi sai dokin shi Zabil da kuma Jaseena wanda mahaifin ta ya maida ruwan kwakwa abincin ta, shi kuma yakan kama kifi ya busar don ya samu abin ci ,ko kuma y’ay’an itatuwa..haka suka yi ta rayuwa a jejin………..🦁</p><p> </p><p><br /></p><p> 🦂bayan shekaru goma sha shida(16 yrs ltr)🦂</p><p><br /></p><p> Zaune yake a fadar sa, su waziri sai zuba fadanci ake , wasu maza wad’anda da ka gansu kasan cewa magidanta ne sanye cikin kayan da basu fi a k’ira su da tsumma ba suka shigo fada gami da zube wa ‘kasa suna kwasar gaisuwa duk jikin su sai 6ari yake yi d’aya daga cikin su yace ” Allah ya baka nasara sarki !!! Mun kawo k’arar Yerima !! Ya takurawa y’ay’an mu ko diban ruwa basa iya fita saboda da ya gansu sai ya fasa tulun,shine muk………….kafin ya k’arasa yaji sauk’ar mari Tas!!!! Hakan yasa ya mik’e a firgice yaji an sake kwarfe shi ta k’afa take ya zube ‘kasa warwas !! Sarki ya ja tsaki Mtsew!! Yace ” ni zaku dubi tsabar idona Ku zo min da zancen banza Wai kun kawo karar Yerima? Toh baku isa bah !! Wato har an fara sa mishi ido kenan ? Ina so ku sani ,Rizwan Jini ne na sarauta yana da ikon taka duk wanda ya so kuma babu mai tanka masa ” ya dubi sarkin yak’i yace ” me kuke jira ne Amjad?!!! Aje a rufe min su a kurkuku da kuma horo mai tsananani!! Da sauri sarkin yak’i Amjad ya kama hannayen su ta baya ya tisa ‘keyar su suka bar fada yayinda Jalalud-deen ya koma kan kujerar sa yana maida numfashi kamar wani damisa 🐅</p><p><br /></p><p> Sarkin yak’i Amjad yana fita da su yayi hanyar kurkuku dasu ,murya ‘kasa- ‘kasa yace sai dai ku yi hakuri da irin Wannan zalunci da ake muku ni na tabbatar cewa akwai ranar da zata zo idon Jalalud-deen sai ya raina fata kuma sai ya zama wulak’antace a idon jama’a!! Yayi d’an murmushin takaici dai dai lokacin sun iso mashigar kurkukun ya wuce chan ciki da su ,sun dad’e suna tafiya kafin su iso d’akin da za’a sa su ,ganin masu gadin na kallon sa ya sa ya hakad’a su ciki a fusace ,gami da rufo k’ofar ya juya idonsa cike da k’walla ya fice Daga kurkukun…..</p><p><br /></p><p>🗡🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🗡</p><p><br /></p><p> Gudu take a kan dokin sanye da bak’in dogon wando mai fad’in gaske ta sama , ta ‘kasa kuma a tsuke,rigar jikinta na cikin dogon hannu ne da shi kuma sak’awa akayi da auduga na saman kuma da fata akayi shi bak’in mayafi ne rataye a kanta wanda har ya zagaye fuskar kamar wanda tasa nik’ab baka ganin komai sai girar ta ,idon ta da kuma saman zirin karan hancinta , takalmin k’afarta ma na fata ne ,ta rataya wata y’ar jaka a jikinta sai wani dan biri da ke zaune a kafad’ar ta yana ta fama da ayaba🐒…..</p><p><br /></p><p> ” Hyaaaa!!!” Ta fada gami da bugan dokin ta baya ,yayin da shi kuma ya kara gudu. Sun dad’e suna tafiya kafin su isa mashigar garin tana isa ta sauk’a daga saman dokin ta kama linzamin suka ci gaba da tafiya basu zame ko ina ba sai kasuwar garin nan ta wuce gun wani mai saida ganyeyaki na magani ta mik’a masa jakar , ya karba ya Ciro kad’an daga ciki ya shinshina sannan yayi murmushi ,yace ” yayi kyau Jaseena !! Wannan na’a na’a mai kyau ne !! Ya sa hannu cikin aljihun shi ya Ciro sulalla ya muk’a mata ta kar6a ta juya abunta ba tare da ta ce k’ala ba ……..</p><p><br /></p><p> Cikin kasuwar ta sake kutsa kai tana ganin yanda Kowa ke gudanar da alamuran sa cikin kwanciyar hankali ,kai tsaye ta nufi gun mai shinkafa ,ya auna mata ta kar6a kawai ta jiyo hayaniya bata ankara ba ta hango dawakai kusan biyar sun dumfaro inda suke ,da wasu matasa a kai sai 6arna suke ,guda daya daga cikin su ya sha ado da kaya irin na alfarma shi ya fi Kowa ma ta’adi a cikin su suna ta buge mutane ,suna zubar musu da kayayyaki ,ta gefen Jaseena suka wuce gami da banke wata mata mai juna ta fad’i ‘kasa kayan marmari da ta siyo ma duk suka zube ,a fusace Jaseena ta dubi mai shinkafan tace “Wannan kuma su waye haka kamar mahaukata ??!!! Mai shinkafa ya zaro ido yace ki rufa ma kanki asiri baiwar Allah!! Wannan shine Rizwan d’an sarki Jalalud-deen !! Ta juya ta sake kallon hanyar da suka wuce tana wani irin murmushi na k’eta ” a ranta tace lallai yau kakarta ta yanke sak’a!!! Mai shinkafa ya ce ” amma baiwar Allah kina garin nan kice baki san Yerima Rizwan ba? Murmushi kawai tayi ta d’auki shinkafan ta sa a Jakarta ta juya ba tare da ta kalle shi ba balle ma ta bashi amsa ,ta nufi gun matar da ta fad’i kasa wanda duk an zagaye ta ana kallo kuma babu wanda ya ma je kusa da ita don ya taimake ta…………….🦃</p><p><br /></p><p>Jeeddah ja’o🏵</p><p>[3/3, 10:16 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔</p><p>🐚🏵jeeddah ja’o🏵🐚</p><p> </p><p><br /></p><p> 1⃣6⃣⏭2⃣0⃣</p><p><br /></p><p> Kutsawa tayi cikin taron mutanen da k’arfin hali ta samu ta shige inda matar take ta d’aga ta tana yi mata Sannu yayinda sauran mutanen suka watse daga gurin Kowa ya fara tattare 6arnar da akayi masa amma da ka gansu kasan a tsorace suke duk da Jaseena ta fuskanci hakan bai sa ta ko girgiza ba ta d’aura matar kan dokin ta sannan ta ja akalar dokin suna tafiya matar na mata kwatance har ta kaita gidan ta, ta kuma taimaka mata har cikin gida ,wanda ba girma gareshi ba amma sai tsafta ,wani gadon kara ne gefe guda ta hango ta ja matar har gurin ta zaunar da ita sannan ta tashi ta nufi d’ayan 6angaren gidan don nema wa matar ruwa, akayi sa’a ta samu ta d’ebo mata….</p><p> Bayan ta tabbatar matar ta samu nutsuwa sai ta tashi zata fice ,hannun ta matar ta rik’e ta ce ” nagode baiwar Allah !! Amma yaya sunan ki ? Ta juyo da murmushi tace ” “Jaseena ” matar ta d’an jinjina kai ta ce ” amma ke bakya tsoro labari yaje kunnen Yerima Rizwan cewa kin taimaka wa wanda ya wulak’anta? Zai ce kin raina mar hankali ,sannan ya sa a miki horo mai tsanani ,kuma gashi ke yarinya ce bai kamata kina k’arama ki jefa kanki cikin had’ari ba !!! Murmushi kawai Jaseena ta sake yi tace ” Kar ki damu umma !! Ni ma ba kanwar lasa bace !!!in yana ji da sarauta nima ina ji da ita !!🗡 ke dai ki kula da kanki kuma ki daina fita ke kad’ai domin hakan ba k’aramin had’ari bane” tana kai Wannan ta juya ta fice gamida rufo k’ofar gidan ,matar ta bita da kallo ,a ranta tace ” yau naga mace mai kamar maza!! Yanzu har a masarautar Kalahari akwai macen da zata iya tsallake dokar Yerima ?? Ta girgiza kai ta koma ta kwanta.</p><p><br /></p><p> 🐚 kasuwar ta k’ara komawa ta gama saye-sayen da zatayi sannan ta juya ta bar garin , da la’asar ta isa kogon su ta shige ta nufi inda tasan kullum mahaifan ta yake motsa jiki da yamma ,wani d’an fili ne ya zagaye da itatuwa a nan ya ke koyawa Jaseena dabarun yak’i ,da gudu ta nufi inda yake ta zari wani sanda suka fara fad’a cikin raha har suka gaji suka bari.</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> 🔥wuta suka hura tana taya shi gasa kifi sai zuba take yi don duk abunda ya faru a Kalahari sai da ta zayyano masa shi dai bai ce ‘kala ba ya ci gaba da gasa kifin ,ganin ba sauraron maganar ta yake ba ta mik’e ta nufi wata duhuwa mai siriryar hanya ,gaba kad’an ruwa ne ke sauk’a ta saman dutse birin ta wanda take k’ira da suna Zainu yana nan kan kafad’ar ta yayinda take Kutsawa cikin duhuwar 🌳 kukan damisa ta jiyo hakan ya sa ta wata Yar siriryar dariya ta kama wata reshe kamar biri tana lek’o inda taji kukan ,domin takan ji kukan ne tun tana Yar yarinya amma bata tab’a yin gaba da Wannan gurin ba kasantuwar daga Wannan dutsen mai ruwa babu wani guri a gaba balle ta ce ko daga chan ta jiyo k’ara. yau de ba Jaseena bace zata fita ,mahaifin ta Hameed ne zai fita duk da ranta bai so ba amma tasan bata isa hana shi fitan ba ,kamar kullum ya debi ganyeyaki a jaka ya ja Zabil suka fice …..tana cikin wasa da zainu su kama Wannan reshen su saki wancan Kwatsam ta sake jin Wannan kuka na damisa ,ai kuwa nan ta k’udiri niyyar sai ta gano duk inda Wannan ‘kara ke fitowa !!! Diro wa tayi daga saman bishiyan tabi hanyar da ta jiyo karan kamar kullum de bakin dutse take riskar kanta amma yau tace bazata juya ba sai taga menene a bayan ruwan da yake zuba kuma zata nemo inda Wannan damisa take</p><p><br /></p><p>; Hawa tayi kan dutsen duk ruwa yana ta jik’a ta a hankali ta mika k’afan ta gaba taji dai ya zauna ai kuwa sai ta kutsa kai ,zainu kuwa tun da yaga ta shiga ruwa ya koma gefe yana kallon ta itama bata biya ta kanshi ba tai shigewarta………….</p><p><br /></p><p>Wata Yar siriryar hanya ce a ciki sai duhun tsiya amma don rigima ta shige sai tafiya take ,har tayi tsakiya ta juya tana kallon hanyar da ta baro ,sai kuma ta tabe baki ta ci gaba da lulawa……………</p><p><br /></p><p>Jeeddah jao</p><p>[3/4, 7:41 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>2⃣1⃣⏭2⃣5⃣</p><p><br /></p><p>Ta kai ak’alla minti talatin tana tafiya wani wajen ma sai ta sunkuya don ta wuce amma bata fasa ba har sai da takai wata Yar k’aramar k’ofa wanda aka toshe bakin da Yar ciyawa tasa hannu ta ture ciyawar dayake rana ta kusa faduwa Hasken wanda yay ja ya dalle mata ido sai kakkarewa take da hannun ta ,cikin dabara ta fito daga ramin dutsen ta tsaya ta jikin dutsen tana bawa idonta abinci domin banda dajin da yake gurin tana hango wani gini mai tsayin gaske ga kyau ,da gani kasan masarauta ce amma gaba yake da dajin shima ta hango shi ne don tana saman dutsen ne ta hango amma akwai wata siriryar hanya da ta bi gurin. Daji ne mai kyau don har yafi na inda suke kyau, da gudu ta juya tana dariya ta koma kogon bata yi wata wata ba sai gida Zainu na ganin ta yai tsalle ya koma kafad’ar ta yay zaman shi ita kuwa ganin yadda tayi datti yasa yasa ta nufi inda take wanka gefen Wannan ruwan tai ta wanke jikin ta tana wasa da ruwa ,k’iran da babanta yay mata ne yasa ta fita da sauri ta nufi inda taji Muryan shi ,fuska a turnuk’e yace “ina kika je?!!!” Nan ta fara kame kame ya juya ya barta gurin bai kuma cewa qala ba….</p><p><br /></p><p>Cikin sand’a ta nufi d’akin ta, gami da turo k’ofar shi kuwa Hameed sai da ya gama kaifa takobin shi sannan ya wuce d’aki. Cikin dare ya kasa bacci domin jikinshi na bashi akwai abunda zai faru ,duk zuciyar shi sai bugawa take ya rasa dalilin faruwar hakan ,ya d’auki takobin shi ya nufi d’akin Jaseena wanda itama ba baccin take ba ,tana ganin shi ta tashi ta zauna tace ” baba na mai ya sameka? Yaya na ganka cikin daren nan? Murmushi yayi sannan ya kama hannun ta ya d’aura takobin ta daga kai tana dubanshi bai daina murmushi ba har Lokacin yace ” Jaseena !! Ko ma me zai faru yau d’in nan ka……….. Kafin ya k’arasa yaji motsi a waje tuni ya ce Jaseena ta fita ta bayan d’akin amma ta ture Wai itama zata iya fad’a ai kuma bazata tafi ta bar shi ba ,ya gaura mata mari wanda tsabar ta rikice sai da taga wuta🔥 ya ce ” nace ki tafi !!! Cikin kuka ta zari jakar ta na fata ta rataya zainu na biye da ita ta fice ta kofar bayan shi kuma ya fita don ya duba me ke wakana. Sauk’ar itace yaji a kansa wanda hakan yasa shi k’ara da zubewa a ‘kasa sumamme , duk abun nan da ya faru a idon Jaseena ne domin la6e wa tayi tana ganin duk abunda ke faruwa duk mutanen ta ga fuskokin su kasancewar Hasken farin wata duk ya mamaye gurin suka jashi suka tafi da shi ,nan ta zube tana wassu zafafan hawaye na takaici, a ranta tace ” toh ya akayi suka gano inda baba ya 6oye? 🗡……,</p><p><br /></p><p>🐚🕸🕸🕸🕸🕸 🕸🕸🕸🕸🕸🐚</p><p><br /></p><p>Kafin kace wani abu har gari ya waye Jaseena na idar da sallah tana goge takobin da Hameed ya bata kawai taji takun mutane ,cikin sauri ta haye wata bishiya cikin duhuwa zainu ma ya bita , a hankali suke magana tana jin su ,”sarki yace a duba ko akwai Dan sa ko kuma d’iya domin da ciki a jikin matar sa ya baro Kalahari !! Jin haka yasa Jaseena ta diro ta yi hanyan Wannan kogon wanda ke bayan ruwa mai zuba ta shige Wannan ramin Wannan karon har da zainu a tare da ita tana dirowa ta d’auki Yar ciyawar ta maida shi gurbin da yake ta fara tafiya tana bin Wannan hanyar da ta gani sai kalle kalle take yi zainu kuwa an samu bishiyoyi ya hau wancan ya kama wancan. Har lokacin bata daina kuka ba ,don tsoro take yi Kar a kashe mahaifin ta.. Gurnani ta jiyo ta gefen hanyar kamar na zaki ai kuwa Kwatsam yayi tsalle ya tare gabanta 🦁 ta tsaya chak a gurin ta zubawa sarautar Allah ido , bata ankara ba taga wani kyakkyawan sadauki a gabanta ya tsugunna yana shafa kan zakin ,damtsen shi ma. Kad’ai abin kallo ne shi kanshi kamar zakin yake ga gashi har Ka fad’a wata Yar farmalam ce a jikin shi wanda gabanta a bud’e take ya rataya kwari da baka a bayanshi takalmin ‘kafar shi kuwa na fata ne , ya mik’e yana kallon Jaseena sannan ya k’arasa kusa da ita ,hawayen da ya gani a fuskar ta yasa ta bashi tausayi saidai ba tare da yace komai ba ya ciro k’ullin gurasa a jakar shi ya bata ,kamar yasan tana jin yunwa. Da sauri ta wafce ta nemi guri ta nad’e k’afa ta fara ci ,chan sai ta tuna da mahaifin ta, hawaye na zubo mata sai chusa gurasar take yi tsabar ta zuciya ,har ya shak’e ta ta fara tari kamar dama jira yake , matashin ya ciro wata Yar gora na fata ya mik’a mata ta kar6a sai bayan ta d’an nutsu sannan ta dubeshi tace ” nagode !!👏🏽 murmushi kawai yayi ya yi mata nuni da hannu ma’ana ta tashi su tafi , nan ne ta gane cewa baya magana kuma ba kurma bane yana ji sarai amma baya iya magana ,saidai akwai kyau kamar balarabe , ta tashi ta bi bayanshi suka ci gaba da tafiya har suka k’ure Wannan dajin ,abin da ya bata mamaki shine wani tafkeken kogi ne a gurin saidai daga bakin ruwan ma kafi ganin masarautar ,jirgin ruwa suka shiga mai tuk’in yan ta fama da tuk’in shi kuwa sai wasa da ruwan yake yi…..,…….🦃</p><p><br /></p><p>Jeeddah ja’o🏵</p><p>[3/17, 11:35 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>2⃣6⃣⏭3⃣0⃣</p><p><br /></p><p>Isarsu masarautar ,bai zame da su ko ina ba sai cikin hanyar fada ,yana gaba tana biye da shi cikin ranta tace ” yanzu har akwai masarautar da bawa zai dinga kutsa kai cikin fada ba tare da izini ba? ” bud’ewar wata k’atuwar k’ofa ne ya katse ta daga tunanin da take yi ,kai ya kutsa ba tare da fadawan sun Hane shi ba har ya k’arasa ya nemi guri ya zauna ……..🦃</p><p><br /></p><p>Zubewa tayi itama tana kwasar gaisuwa kamar yadda yayi sannan ta gyara zama. Wani bak’in mutum ne wanda fuskar shi ba wani almuru don ko murmushi da yake yi kamar dole aka sa shi yake yi . ” yarima har an dawo ne!!? ” tambayar da sarkin yay masa kenan ,yayin da shi kuma saurayin ya gyad’a masa kai ,nan yaci gaba da yi masa kwatance da hannu irin na kurame ita dai Jaseena ta zuba musu ido cike da mamaki da kuma tambaya dake cikin zuciyar ta ” me yasa Yerima guda babu ko hadimai balle shiga ta alfarma?! ” don ita da tayi zaton bawa ne😄 gashi kuma kyakkyawan gaske amma mahaifin sai bak’i da muni 😂 ,ta d’an jinjina kai tace ” hala mahaifiyarsa ya biyo”</p><p>Maganar sarkin ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta shiga ” Yaya sunan ki baiwar Allah? ” shine abunda yayi karo da kunnen ta. A d’an rusune tace “Jaseena”. Sarkin ya d’an yi murmushi yace ” daga yau na baki masauk’i cikin masarauta ta domin Yerima Haidar ya sanar da ni cewa 6ata kikayi ,toh nan ya zama miki gida kina da iko ki shiga duk inda kike buk’ata a masarautar nan ! Tai ma sarki godiya sannan Haidar ya ja ta suka fice daga fadar ya mik’e da ita har wani hanya daban wanda ta yi nisa sosai da fada ga k’ofofi kala kala masu kyau da kwalliya ga fitilu masu haske abin ba’a cewa komai …..</p><p>Wani d’aki ya nuna mata ta sa hannu ta bud’e ta shiga da murmushin ta zainu na biye da ita ,shima murmushi yayi sannan ya juya ya fice daga wajen yayinda ta bishi da kallo kamar Yar k’auye.</p><p><br /></p><p>🐚🐚🐚🏵 🏵🐚🐚🐚</p><p><br /></p><p>Yau kwanan Jaseena uku a Wannan gari wanda ko ita kanta bata san sunan garin ba ,Haidar kuwa kusan kullum da safe sai ya lek’o don ya duba lafiyar ta ,haka take wuni ita kad’ai sai zainu yana d’ebe mata kewa kasantuwar Haidar bai cika dawowa da wuri ba in ya dawo ma sai gari ya waye yake duba su….” Yau kam sai na fita na zaga gari!!” Cewar Jaseena kenan tana ta faman gyara zaman dogon rigar da ta saka ,sai duba kanta take ta madubi don bata saba saka irin kayan nan ba ,ita kanta ya mata kyau ,sannan ta dauki mayafin wanda da shi da kwalin tata duk d’aya ta yafa a kanta ta nannand’e ta fice zainu na binta a baya kamar yadda ya saba , tana tafiya tana faman tattare riga don yadda yake Jan ‘kasa a haka har ta bar fada ,tana ta kalle kalle ta tsaya can ,ta ta6a wancan , tana cikin haka har tayi nisa da masarautar a can nesa ta hango wasu mata guda uku kowacce da tulu sun sha ado sai ture -turen juna suke a kan hanya suna ta raha……</p><p>Cikin sauri Jaseena ta k’arasa inda suke ,tana iskesu ta sa hannu ta ta6a kafad’ar daya daga cikin su duk suka juyo suka k’urawa Jaseena ido sai kuma suka bushe da dariya suna nuna ta da yatsa 👉🏾 hakan yay matuk’ar bawa Jaseena haushi ta yamutsa fuska tace ” toh me nayi kuke min dariya !!😠. A tare suka tsare kamar da gaske sannan suka sake bushe wa da dariya ,wata Yar siririya sosai tace ” ke kuma Wacece haka !? Ko rigar ma bata iya sak’awa ba Yar k’auye kawai!! Suka juya suka ci gaba da tafiya yayinda ita kuma Jaseena ta tsaya Kallonsu har suka shige ta daina hango su ma……………🦃</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵</p><p>[3/18, 9:58 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>3⃣1⃣⏭3⃣5⃣</p><p><br /></p><p>Duk Wannan abun da ya faru Haidar na tsaye yana kallon ta ,shi ma kanshi ta bashi dariya kawai ya tsare ne,kwata – kwata rigar baibai ta saka shi bayan haka kuma gaba a baya ,duk da hakan da tayi yay matuk’ar yi mata kyau amma ba daidai bane shi yasa matan ke mata dariya….</p><p><br /></p><p>🎗Nan ta nemi k’ark’ashin wata y’ar bishiya ta zauna tana ta 6ata rai harda d’an hawayen ta ,tace ” ai yanzu da baba ne bazai min dariya ba cewa zai yi yayi min kyau !! Toh ma miye laifin kayan nan tunda dai ba tsiraici na bari a fili ba!!!Mtsew!!!” Take ta zabura ta mik’e tace” Baba!!!”</p><p><br /></p><p>🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸</p><p><br /></p><p>Kwance yake cikin wani matsatsen d’aki mai duhun gaske duk ruwan datti ta nan yake biyo wa ,ya tashi ya mik’e tsaye sai kai kawo yake a d’akin yana cizon le6e ,duk tunanin shi ya koma kan y’ar sa Jaseena addua kawai yake yi Allah ya sa Kar su gano ta ,Allah yasa basu kamata ba duk da yasan k’arfin damtse na y’arsa da kuma wayo irin nata. ” HAMEED!!! K’iran da waziri Zakar yayi masa kenan , hakan ya sa shi juyawa cikin sauri fuskar shi a d’aure. ” kamar yadda muka kamoka kamun wulak’anci haka zamu kamo d’iyar ka da kake tak’ama mai k’arfi ce mu wulak’anta ku a bainar jama’a !!! Hhahhah !!!!! ” Zakar kenan yayi Wannan magana ,bai ankara ba yaji an shak’e wuyan shi har saida idanuwan shi suka fito kwala kwala ,ya kasa magana. Hameed kenan !! Yana cikin kurkuku ma amma k’arfi na nan !!💪🏼. Wasu masu gadin gurin su biyu ne suka tunkari inda suke da ‘kyar suka cire waziri daga rik’on da Hameed yay masa sukayi waje da shi ,yayinda shi kuwa gogan ya koma ya zauna yana maida numfashi 😤………….</p><p>👑. 👑</p><p>A tsayen da take tana tuna halin da mahaifin ta zai shiga a Kalahari taji durowar abu ta bayanta tuni ta zari wata y’ar wuk’ar ta ta juya zata kai hari ,hannu ya sa ya tare ,wuk’ar ta yanke shi a hannu. Tana juyawa taga ashe Haidar ne 🙄ta zare ido,a rikice ta cire gyalen da ta rufe</p><p>kanta ta raba gida biyu ta d’aure masa yankan da tayi sai bashi hak’uri take yi ,ga dukkan alamu bai ji zafin ciwon ba sai murmushi yake mata ,jiki a sanyaye ta nemi guri gefen bishiyar ta raka6e tana y’ar hawaye….</p><p>Wata murya mai dad’in gaske da ratsa zuciyar duk wani mai sauraro taji yace ” Jaseena!! Ai barin kashi a ciki baya maganin yunwa ,inaga lokaci yayi da zaki sanar da ni matsalar ki wata’kila na nema miki mafita ko in taimaka miki!! Kinga dukkan mu nan ko wanne yanada matsalolin da yake neman mafita amma 6oye su bazai amfane my da komai ba har lokaci ya k’ure mana !! A firgice ta juya tana neman inda akayi maganar amma ta rasa domin ta lura babu Kowa a gurin sai Haidar da har Lokacin murmushi kawai yake yi rik’e da hannun shi yana kallon ta da kuma mamakin yadda ta rikice tana neman wanda yayi magana………</p><p><br /></p><p>Ta dawo gaban Haidar tana kallon cikin idon shi tace ” bakaji wani yayi magana ba ? Baka ga wanda yayi ba?” Murmushi ya sake yi sannan yace ” ni nayi miki magana Jaseena !!” Nan ta tabbatar tabbas shi ne yayi magana ,kafin ta ce komai ganin yadda ta saki baki kamar wawuya yasa ya fisge hannun ta yabi wata hanya da ita sai cikin wani daji dake gefe da gurin ,kan wani gungume ya nuna mata ta zauna ,yace ” eh nine nayi magana ! Kuma ke kad’ai ne kika san hakan ko sarki bai sani ba ,kuma ina so ki rik’e shi a zuciyar ki ,duk Lokacin da kike buk’ata muyi hira to kizo nan amma Kar ki kuskura wani yasan ina magana !” Kai kawai ta girgiza mishi cike da mamaki har lokacin ta kasa nutsuwa…,……….🦃</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵</p><p>[3/19, 12:16 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>3⃣6⃣⏭4⃣0⃣</p><p><br /></p><p>“Dama kana magana ne?” Shine tambayar da ta fara fita daga bakin Jaseena. Haidar yayi wata Kyakkyawar dariya yace ,ina magana amma banda iyayena babu wani mahalukin da yasan hakan ko sarki Hasheem da kika gani bai sani ba ,duk da shine silar dawowa ta hakan !! Duk Wannan maganganu da yake yi babu abunda Jaseena ta fahimta duk ya dagula mata tunani , Ta mik’e tace in na fahimce ka ,kana so ka ce min kai ba d’an Wannan sarkin bane ? Kuma akwai abunda kake 6oye masa a matsayin sa na wanda ya yi rainon ka?</p><p>Wata dariya ya saki mai ban mamaki yace ” Jaseena duniyar tamu zagaye take da azzalumai masu bak’ak’en zuciya da son abun duniya !! Zan baki labari na da kuma dalilin da yasa na zama haka ,amma kafin na baki labari ina so ki min alk’awari babu wanda zai san ina magana a cikin masarautar nan ko da wasa ne! ” Jaseena ta furzar da iska daga bakinta tace ” inshaa Allah bazan bari Kowa ya san da Wannan zancen ba !! Sirrin ka zan killace shi kuma na bashi mazauni na musamman a zuciya ta !!” Murmushi yayi yace na gode !! Amma yanzu muje in nuna miki gari ,gobe zan sanar da ke tarihi na in Allah ya yarda ” Jaseena ta d’an 6ata rai tace” me yasa bazaka fad’a min yau ba? ” murmushi kawai yayi yace ” muje ” ya tashi ya mik’e ita ma tabi bayan shi har ta sa k’afa zata tafi sai tace ” kai ka je !! Ni zan gyara riga na, ba tare da ya tanka ba yayi tafiyarshi ita kuma ta juya rigan ta gyara tsaf sannan ta fito daga duhuwar da take …</p><p>Tsaye ta same shi a gefen Wannan bishiyar yana jiranta ” na gama mu tafi” shine maganar da ta ratsa kunnen sa ,ya juyo ya k’ura mata ido kamar ya had’iye yace ” muje” ya fara tafiya ta bi bayanshi sai fama da doguwar rigar takeyi duk ta mata nauyi ta tattare rigar har guwiwa hakan yasa ta bata sauri sai ta d’an ruga ma take iske Haidar duk da ya ga yadda take fama da rigar wanda hakan ya bashi dariya matuk’a amma ya kafse kamar bai san ma tana yi ba .</p><p><br /></p><p>⚜kasuwar garin ya fara kai ta ,sai kalle kalle take yi ,Kwatsam ya bi da ita layin sayar da tsuntsaye ,su Jaseena an samu abun yi ,nan ta dinga bin keji keji tana ta dariya kamar pagal (mahaukaciya) shi dai haka yake a tsare sai tafiyar shi yake in taga yayi nisa sai ta sa gudu ta taro shi ,ga shegen surutu kamar aku ta sha gaban shi yana tafiya ita kuma tana tafiya da baya baya ,” kai nace ka d’an tsaya mana sai sauri kake yi ko baka ji na ne!! ? A garin ja da baya ta banke wata budurwa ta d’ebo kwai a kwando ta fad’i k’asa kwayayen suka fashe ,a gurin ta daskare ta kasa magana ,budurwar ta mik’e tana karkad’e jikinta yayinda Jaseena ta sunkuya tana kwashe mata wayanda basu fashe ba sai hak’uri take bata. Murmushi yarinyar tayi tace ” babu komai !! Ba kece wadda muka gani dazu zamuje deban ruwa ba?” Jaseena ta d’an d’aga kai alamar tunani tace “🤔 ” Eh nice !! Ina sauran guda biyun suke?” Yarinyar tayi murmushi tace suna can gida ni sunana Jauda , ke kuma fa?” Ni kuma Jaseena! Shine amsan da Jaseena ta bata .</p><p><br /></p><p>Ta juya sai dube dube take yi bata ga Haidar ba murya can k’asa tace “toh shi Wannan ina ya tafi ne?!” Murmushi Jauda tayi tace ” tun yaushe ya tafi!! Kizo mana mu tafi tare zamu nuna miki cikin gari ni da yan uwa na !” Da ‘kyar Jaseena ta yarda ta bi ta suka tafi………….</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵</p><p>[3/21, 9:24 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>4⃣1⃣⏭4⃣5⃣</p><p><br /></p><p>Suna tafiya tana mata hira har suka isa wani babban gida ,ginin mai tsayi ne sosai ga kyau kuma tare suka shiga kai tsaye hanyar d’akin girke -girke suka nufa yarinyar ta ajiye kwandon kwai din ,a d’ayan 6angaren kitchen din kuma wayannan yan matan nan ne da suka mata dariya tare da Jauda suna tsaye sun zuba musu ido ,d’ayar tace ” ke!! Benaxir fa ta dawo !!! Kika shigo da Wannan bakya tunanin zata iya 6ata miki rai in ta ganta ko??!” Murmushi Jauda tayi sannan tace ” babu komai Aisha ai zamu fita ta baya in Mun gama aiki !!” Aisha de bata sake tanka mata ba ,Jaseena tace ” Wacece Benaxir har kuke tsoron ta haka ? D’ayar da tun farko bata tanka mata ba tace ” Wannan bai shafe ki ba !!:roll:” a tare Jauda da Aisha suka daka mata tsawa gami da k’iran sunan ta Meenah!!! Wai ke me yasa bakya son mutane ne kin cika bak’in hali !!? ” Aisha ce ta k’arasa maganar……</p><p><br /></p><p>Jaseena tayi murmushi tace ” ni zan koma ,nagode da kyautata wa da kuka yi min ” Aisha tace don Allah ki tsaya mana yanzu zamu gama aiki mu tafi fada ,yau akwai tseren doki a fada kuma Kowa zai halarci gurin domin fidda gwani a wajen sarrafa doki ,kuma fa har akwai fad’a da zaki ,kowacce shekara yarima Haidar ke gaba a duk fannin.!! Kinsan yarima Haidar da son mutane ! Ai shine ma sadaukin Wannan masarauta Kowa yana karrama shi ,ba kamar mahaifin shi sarki Hasheem ba ,bai d’auke shi a kan komai ba ,Kinsan Haidar abokin mu ne tun muna k’anana tare muka taso har yanzun nan da kika gani ,ko lokacin da muka miki dariya a hanya ma ai shi ya hana mu in ba haka ba da abun ya fi haka ,ko wacce a cikin mu na da labari mai ban tausayi tun yarintar mu kuma labari mai ban tausayi amma da Sannu zaki san komai amma kafin nan ko zaki iya bamu labarin rayuwar ki da yadda akayi kika tsinci kanki cikin Wannan masarauta ta Ramali?? ”</p><p>Nan Jaseena ta kwashe duk labarin rayuwar ta ta fad’a musu har yadda akayi ta fito daga dutsen da had’uwar ta da shi Haidar ,duk sun tausaya mata matuk’a , Jauda ta mik’e tsaye tace ” toh ai duk labarin d’aya ne duk fa akan mulki aka k’ask’anta mu kawai don an fi k’arfin magabatan mu toh yanzu zama zamuyi a dinga cin kashi a kan mu ne??!! Aisha ta mik’e tace ” inaaaa!! A’a Sam bazai yiwu ba dole mu kwace hak’k’kin mu da kan mu mu tashi muyi yak’i mu k’watar ma kammu y’anci!!! ” Jauda ta sa hannu tace ” wa yake tare da ni??” Duk suka d’aura hannayen su a kan nata gami da cewa “ni!!” Duk suka maida dubansu ga Meenah da ko motsawa bata yi ba ,ganin duk sun sa mata ido itama ta d’aura nata hannun” Jaseena ta rasa Wannan wane irin hali ne Meenah take da shi kwata kwata batada fara’a a fuskar ta. A tare suka watsa hannayen sama kowannen su yana murmushi irin na masu k’arfi a jika 💪🏼</p><p><br /></p><p>💞🏵 Jaseena. 🏵💞</p><p><br /></p><p>Guri ne babba na gaske amma mutane duk sun cika gurin an zagaye makeken filin wanda Hasken farin wata ya cika shi fal! Gurin da mutanen suke hawa hawa ne ga fitilu nan ta ko ina sun haska benen dake sama sosai shine inda sarki Hasheem ke zaune shi da wata Kyakkyawar mata tasha ado na zinare ,gefe d’aya kuma sarakuna ne da matan su wayanda suka zo suma da y’an wasan su ma’ana sadaukai na k’asar su don suma su fafata a cikin gasar ,akwai gefen sarki Hasheem wanda duk cikin guraren ya fi ko ina k’ayatuwa ,wani sarki ne bashi da haske sosai amma da ka ganshi kasan ya dama ya shanye a sarauta ,gefen shi wani kyakkyawan saurayi ne ya sha ado gwanin sha’awa fuskar shi babu almuru ga dukkan alamu d’an sarkin ne ,ga kuma wani ta bayansu a tsaye da alama sarkin yak’in su ne don sanye yake cikin kayan yak’i saidai ya manyanta sosai don dattijo ne….</p><p><br /></p><p>Toh masu ku biyo ni a episode na gaba don jin wainar da zata toyu a Wannan fili na gasa ,ina godiya masu karatu love you all!!💞</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵</p><p>[3/23, 9:15 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>4⃣6⃣⏭5⃣0⃣</p><p><br /></p><p>Haidar ne a kan doki suna Jere shi da wasu ,yayan sarakuna ,Jaseena da ke zaune a bene na farko kuma na k’asa ita da su Jauda kawai ta mik’e ba shiri ,su Aisha ma suka mike suna tambayar ta ko meyasa ta zabura haka? Fuskar ta babu almuru tace ” tabbas na san wancan !! Shine Rizwan d’an sarki Jalalud-deen !!! Me kuma yake yi anan ? Duk yadda akayi sarki Jalalud-deen ma yana nan !!” Aisha tace ” kice ba mu muka je neman su ba su da kansu sun kawo ‘kafar su inda ya dace!!” Duk suka bushe da dariya ,chan kuma sai Jaseena tace ” toh amma ai in an gama gasar yau gobe zasu tafi ko ?” A tsare Meenah tace ” sati biyu ake yi ana wasannin lallai muna da dama ” duk suka jinjina kai ,yayin da Jaseena tayi murmushi cikin ranta tace ” lallai Wannan Meenah d’in y’ar ganin dama ne !!.</p><p><br /></p><p>Tun da aka fara tseren dawakai Haidar ne ke Jan ragamar Kwatsam sai dokin shi tayi wani irin ‘kara ta tik’a shi da k’asa ta yi gaba ,yarima Rizwan wa wuce shi yana masa wata muguwar dariya gami da cewa “Wannan karon kam baka isa ba!!! ” dokin Haidar da ya fita a guje ya zagayo ta inda su Jaseena ke zaune kawai se ta mik’e tayi tsalle ta fad’a kan dokin ” Hyaaaa!!! ” ta sa gudu ,ganin yadda ta kusa cimma Rizwan yasa sarki Jalalud-deen ya mik’e tsaye yana zare idanuwa.</p><p><br /></p><p>Gudu suke daf da daf da ita yayinda Rizwan ya kasa mai da hankalin shi kan tseren ,abunka da mayen mata ,ya tsura mata ido ita kuwa ta sakar masa da wata hadaddiyar murmushi wanda ya sa sai da ya kusa tsaya wa. Sai da ta tabbatar ya gama rud’ewa kawai taja linzamin dokin ta kara gudu har ta tsallake Jan layin da aka zana ,ta zo na d’aya ,bak’in ciki ya sa Rizwan ya gagara k’arasawa yayin da idon Jalalud-deen suka rine tsabar haushi ace duk shirin da suka yi na ganin sun ci amma hakan bai yiwu ba?</p><p><br /></p><p>Mutanen gari aka hau ihu ana Jaseena! Jaseena !! Jaseena!!! ,Wannan sunan da aka kira yasa sarki Jalalud-deen d’agowa cikin sauri yana kallon Jaseena !tabbas babu maraba tsakanin ta da mahaifiyar ta ,saidai a tunanin shi wata’kila idon shi ne ke mishi gizo sai yayi tsaki ya juya ya bar wajen ,yayinda Rizwan da sarkin yak’i Amjad suke taka mishi baya.</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵</p><p>[3/24, 7:40 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔</p><p>🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>5⃣1⃣⏭5⃣5⃣</p><p><br /></p><p>Haidar kuwa murmushi kawai yayi ya nufo inda take ,kanshi a k’asa yace ” nagode jarumar mata!!! ” Wannan sanyin Muryar tashi ta sa Jaseena lumshe idanuwa tana murmushi ba tare da ta tanka masa ba,shi ma yadda yayi maganar ba wanda zai gane magana yake yi ..</p><p>🐚. Gurin duk an watse Kowa ya koma gida, daga Aisha ,Jauda, Jaseena sai Meenah da Haidar, suna ta hirar su cikin nishad’i Meenah ce kad’ai kamar bata gurin. Jauda tace “Jaseena mu zamu tafi dare na yi sosai Kar Benaxir ta rufe k’ofa Kinsan ba mutunci gareta ba! Nan suka yi sallama suka bar ta da Haidar. Ganin sun share mintina babu wanda ya tanka wa wani yasa Jaseena ta mik’e tana kad’e rigar ta tace ” sai da safe yarima ,idon shi cikin nata yayi mata wani murmushi ba tare da ya tanka ba ,ganin shiru yasa ta juya zata tafi…….</p><p>Mahaifina sarki Mahmoud shine mai mulkin Wannan masarautar mutum ne wanda bai yadda ya ci ya sha ba tare da ya tabbatar jama’ar k’asar nan sun wadatu ba kullum burin shi yaga na gefen shi cikin walwala koda shi zai rasa ,hakan ne yasa ya fita daban da sauran yan uwan shi wanda kuma sun kasance ba uwa d’aya suke ba domin shi d’aya mahaifiyar shi ta Haifa kuma halin shi ma babu mai irin sa kasantuwar ,kakan mu mata biyu gareshi…..</p><p><br /></p><p>Da sauri Jaseena ta juyo ta dawo inda yake ta nemi guri ta zauna don ta jiye wa kunnen ta ……. Yerima Haidar yaci gaba da cewa ” duk mahaifina ne babba a ciki domin mahaifiyar sa itace ta fari daga baya ne zaliha (ta biyun ) ta haifi maza biyu Hasheem ,Hayatud-deen ,da kuma mace d’aya Saleemah. Duk cikin su ukun Saleemah kad’ai ke son baba na don sun shaqu sosai hakan ne yasa tun tana y’ar shekara goma ,mahaifiyar ta Zaliha ta bada ita aure a wani masarauta Wai shi Kalahari aka daura mata aure da d’an sarkin garin yarima Jalalud-deen , wanda hakan yasa bata ‘kara zuwa ko da ziyara nan masarautar ba,Domin shine hud’ubar da mahaifiyar tata tayi mata.</p><p><br /></p><p>Jin haka yasa Jaseena ta mik’e a razane ta ce ” Kalahari?? Jalalud-deen?!! ” shima Haidar ya mik’e yace “eh! Kin san su ne? Nan ta kwashe labarin rayuwar ta ta fada masa yayinda ya cika da mamaki ” haka Allah yake abin shi!! Shine abunda Haidar ya iya cewa kenan ,ya dubi Jaseena yace “Kin ga yanzu dare yayi ,ki je ki kwanta ki huta gobe in shaa Allah zan sanar da ke dukkan labari na. A nan suka rabu da alkawarin zai sanar da Jaseena komai game da shi washegari……………..</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵</p><p>[3/25, 12:20 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔</p><p>🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>5⃣6⃣⏭6⃣0⃣</p><p><br /></p><p>Tafiya take tana ta fama da y’ar doguwar rigar ta ,tazo wucewa ta gurin fada kenan taji kamar maganar mutane,ta d’an lek’a daya daga cikin tagogin fadar don taga su waye a fadar cikin Wannan dare. Tana lek’a wa idanuwan ta suka yi karo da sarki Jalalud-deen da kuma sarki Hasheem suna tsaye ,koda ta kasa kunne don tajiye wa kunnen ta abunda suke shiryawa……</p><p>” Ai Wannan ba komai bane ni a gurina domin a kan sarauta babu abunda bazan aikata ba !!! Ko yarima Haidar da ka gani ban barshi a Wannan masarautar ba saida na tabbatar cewa yana da nak’asa sannan kuma ban daukeshi a kan karon komai ba !!! Duk da ma de Y’ata Meenah bata k’auna ta Sam !! Amma Wannan karagar mulkin da ita ya dace ba Haidar ba!!!” Sarki Hasheem ne yayi Wannan maganar hannunshi rik’e da kofin zinare. Sarki Jalalud-deen ya mik’e yayi wata y’ar muguwar dariya yace ” lallai abokina baka da wayo !! Ai sai da wuta ake shan Zuma!!!domin dan hakin da ka raina shi zai tsone maka ido ,yaran yanzu da ka gani ,zamani ya chanja domin babu wata dabara da basu sani ba ,bar ganin shi da nakasa ,kaga fa yadda ya mamaye zukatan al’umma ! Abun yi kawai shi ne ka kawar da shi kwata kwata domin in baya nan tare da kai babu yadda za’ayi Meenah ta ‘ki kar6ar mulkin Ramali ,ka duba fa ka gani ,mace ce mai kwarjini ga jarumta bai kamaceta bama a ce Wai ta bar daular dake cikin wannan masarautar! Ni ina da shawara ,me zai hana a had’a su aure da d’an wajena Rizwan? Kaga zasu yi mulkin Ramali cikin kwanciyar hankali ,kasan ko d’ana Rizwan bashi da masaniya akan abubuwan da nayita tufkawa a masarautar Kalahari , don na lura yan da son gaskiya shi yasa na ci gaba da 6ata shi da sakalci don in har ya gano ni ba mai gaskiya bane ,Rizwan zai iya juya min baya kasan duk da ba Saleemah bace ta haife shi amma goyon ta ne shi yasa nayi duk yadda zan yi su daina ganawa da juna kullum!!” Duk suka bushe da dariya Hasheem yace ” baka da dama abokina!! Shikenan! Na amince da shawarar ka!! …..</p><p><br /></p><p>Jaseena ta toshe baki da hannayen ta ,ganin fitowa zasuyi yasa ta ruga a guje ,bata ankara ba taji an fizgo hannun ta cikin wani d’aki an rufe k’ofar ,zata yi magana yasa hannu ya toshe bakin ta yace , “ki nutsu” tana juyawa tayi ido hud’u da Rizwan:oops: tace ” kai!!! Sake min hannu na !!! ” ta fisge hannunta daga rik’on da yayi mata ,ta bud’e baki zata ‘kara wata maganar ya ce ” naji duk abubuwan da suke shiryawa !! Kamar yadda kema kika ji su ‘ da na zaci ni ne asalin wanda ya cancanci sarautar k’asar Kalahari ashe ba sarauta ta bace ta wani ne ! Duk rashin mutunci da cin amanar da nake wa mutane ashe de duk a banza ne , duk kuri da gadara da mulki ashe ba ta mahaifina bane !!! Kaicho na wlhy nayi nadamar samun irin wannan uban ,wanda kawai son zuciya ya saka a gaba ,kuma yanzu na tabbatar ba sona yake ba don yana turanine cikin halaka !! Wani hawaye ne ya biyo kumatun Jaseena tace ” hakane yaya Rizwan amma ai babu komai akwai Allah!! Tana kai wannan ta fice tana goge hawaye ,tabar Rizwan yana tunanin dalilin k’iran shi da tayi da yaya Rizwan ; cikin ranshi kuwa sai tambayar kan shi yake ,dama akwai ranar da zata zo har zai zubar da kwalla da kuma jin tsananin tsanar mahaifin shi?</p><p><br /></p><p>Da sassafe Jaseena ta shirya cikin irin shigar da ta saba ,ta fice don gari ko gama wayewa bai yi ba ,bata zame ko ina ba sai inda sukayi alk’awari zasu na had’uwa ita da Haidar ,amma abun da ya d’aure mata kai shine tun da taje tana masa magana ko kallon inda take bai yi ba ballantana ya amsa mata ,da gani kasan ranshi a 6ace ne. A fusace ya tashi zai bar gurin ta sha gabanshi da gudu tace ” Wai ni laifin me nai maka ne!?tun d’azu ina maka magana ka min shiru kamar da gunki nake magana alhali na tabbata kana ji na “! Bai saurareta ba ya bi ta gefenta zai wuce ta sake tare shi ,cikin tsawa yace ME KIKE YI JIYA A DAKIN RIZWAN!!! ” shiru tayi tana kallon shi ido da ido ta ce ” me kake nufi Haidar ? Me kuma zanyi a d’akin Rizwan ,chan ta juyo tace ,yaya Haidar !! Yaushe muka fara haka da kai? Me yasa bazaka fad’a min ba? Me yasa kake boye min ? ” Haidar yayi sauri ya tari bakin ta yace ” Jaseena ban fahimce ki ba ” tayi murmushi wanda yasa hawayen da ke idanuwan ta suka zubo ba shiri tace ” ka kasa fadamin kana sona ko” ka kasa kuma bawa zuciyar ka hak’uri har ta fara zuga ka,ka fara zargin abin da kake k’auna kuma sannan ka kasa daurewa! ” Haidar ya juyo yana kallon cikin idonta” yayinda ta juya zata bar gurin. Haidar yace ” na soki Jaseena kuma har abada zan soki ” ya durk’usa k’asa yace ” kiyi hak’uri ya ke Kyakkyawa ! Ki taimaka min da zuciyar ki domin tawa ta riga ta kufce min ! Ban kuma san yaushe zata dawo gareni ba don ta fita farautar abunda tafi mata komai soyuwa ne!”</p><p><br /></p><p>🏵 Jeeddah ja’o🏵</p><p>[3/25, 10:45 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>6⃣1⃣⏭6⃣5⃣</p><p><br /></p><p>Jaseena ta juyo idanuwan ta duk sun yi ja ,tace “Na baka !! Na baka ya Haidar!! Ka kula da ita domin taka ta riga ta iso inda zata tsaya da farautar kuma bani da tabbacin zata koma gareka !!” Haidar ya mik’e yace ” nagode kyakkyawa !! Jaseena tayi murmushi tace ” akwai maganar da nake son sanar da kai ne ” Haidar yace” ki fad’a mana ko ma menene. Ta kwashe duk abubuwan da ya faru a daren jiya ta sanar da shi har abunda yasa ta shiga d’akin Rizwan. Haidar ya sake bata hakuri ,sannan ta gyara zama ta ce ” baka k’arasa min labarin ka ba” ya d’an yi murmushi sannan ya ci gaba……..</p><p><br /></p><p>🕸🐚🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🐚🕸</p><p><br /></p><p>A lokacin ina da shekaru goma sha shida ne ,k’ anin babana wato Hasheem ya bi rud’in uwarsa na cewa Kar ya kuskura ya bar babana da rai don in har ya tsufa a kan karagar mulki nine zan gaje shi na zama sarki , don shi a cewar shi ni ba komai bane in ya kawar da mahaifina, da duk wani mai ji dani, kasantuwar kullum da safe muna fita daji ni da kakana yana nuna min nau’in ganyayyaki da amfanin su ,hakan yasa ya shirya mana gadar zare.</p><p>Mun yi Nisan kiwo nida kaka har bayan la’asar sannan muka iso gida ,muna shiga wasu mutane a kan dawakai su kuma suna fita ,ga gari duk ya turnuk’e da hayak’i ko da muka k’arasa cikin fada nan muka tarar da gawawwakin iyayena da kuma na k’annen k’ anin Hasheem Hayatud-deen , Hasheem ya kwanta a kansu sai kukan munafurci yake yi kamar da gaske ,a nan ne zuciyar kakana ya buga take rai yayi halinsa , bayan kwana uku da faruwar hakan ,kawu Hasheem ya na’da kanshi a matsayin sarkin Ramali ,duk dattijawan da basuyi Na’am da hukuncin da ya yanke ba sai ya sa aka kwashe su aka kai su masarautar Kalahari aka rufe ana basu horo mai tsanani ,daga cikin wadannan dattijawan sun had’a da mahaifan Aisha da kuma Jauda ,kamar yadda na fad’a miki Meenah itace d’iyar kawu Hasheem amma tun tana y’ar shekaru tara ne abun ya faru don duk sa’anni suke da Aisha da Jauda kinga kuma k’awaye ne hakan yasa ta baro fada ta zab’i zaman bauta a gidan Benaxir har ta girma ta kawo lokacin nan da kike gani….</p><p><br /></p><p>Ni kuwa tun lokacin da abun ya faru na daina magana da Kowa da na gano hakan kawu Hasheem ya ke so sai na nuna mishi ma kwata kwata bana magana na daina yi ko da da wasa ,a haka shi da mabiya bayansa suka zata na riga na zama miskini. Kin ji yadda rayuwa ta ta kasance kullum cikin k’ask’anci amma ko a jikina domin na san dole ne wata rana sai gaskiya tayi halinta!!” Amma tunda haka abun yake toh mu zamu fara wargaza mishi rayuwar sa” Jaseena ta goge d’an hawayen fuskar ta sannan tace ” lallai ka shiga k’uncin rayuwa Haidar !! A nan ne Jaseena ta kwashe labarin ta ta bashi ta kuma sanar da shi ko wanene sarki Jalalud-deen. Sun dad’e suna shan hirar su ,kafin nan suka nufi gidan Benaxir don yin magana da su Jauda……….</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵</p><p>[3/27, 11:25 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>6⃣6⃣⏭7⃣0⃣</p><p><br /></p><p>Sarkin yak’i Amjad ne zaune a gefen sarki Hameed hannun shi rik’e da na Hameed. Na ganta! Naga y’ar ka Jaseena ,tana cikin k’oshin lafiya ,kuma ga dukkan alamu tana cikin shiri,Hameed ya mik’e yana murmushi yace ” nasan ban haifi lalatacciya ba!! Kuma nasan dama tana nan tafe , amma ya maganan mayak’an da na ce ka tara ? Amjad yace ,komai an kammala shi kuma yanzu haka suna chan a kogon tare da y’an fursunan k’asar Ramali! Da sarki Hasheem ya sa Jalalud-deen ya d’aure shekaru kusan goma sha da suka wuce ” Hameed yayi murmushi yace ” da kyau sarkin yak’i!!! Aikin ka yana kyau ,Allah ya mana jagora!! Sarkin yak’i yace “Ameen”sannan ya mik’e ya fita………</p><p><br /></p><p>Yau tun da safen nan Jaseena take motsa jiki tun bayan sun dawo daga gurin su Jauda Zabil kuwa ya samu Haidar ba kasafai yake waiwayar inda Jaseena take bama don in zai fita daji tare suke tafiya. Saidai yau Haidar bai je ko ina ba yana tare da k’anwar sa Meenah a cikin makeken lambun dake wannan masarautar suna ta hirar su duk da ma dai itama maganar kurmancin yake mata amma ta saba don ko ubanta Hasheem bai iya magana dashi sosai ba. A nan ya sanar da ita cewa yana soyayya da Jaseena, murmushi kawai tayi. Haka sukayi ta hira har kusan azahar, sannan ya tafi domin gudanar da ibada yayinda itama Meenah ta juya tabar wajen ,zata koma gidan Benaxir.</p><p><br /></p><p>🏵🐚🏵🐚🏵🐚. Jaseena🐚🏵🐚🏵🐚🏵</p><p><br /></p><p>Yau kwana na uku kenan ana ta bidirin gasa, Sam Sam Rizwan abun ma bai dameshi ba balle ma ya shiga ,hasalima cewa yayi babanshi ya chanja wanda zai yi wasan shi bazai iya ba ,babu yadda aka iya haka aka chanja shi da wani k’ak’k’arfa daga cikin mayak’an Kalahari. Jaseena kuwa tun ranar farkon nan bata sake shiga filin ba kullum tana daga chan baya ita da su Aisha amma fa ta lura cewa sarki Jalalud-deen hankalin shi bai kwanta da ita ba. Washegari da safe ta shira cikin dogon bujen wandonta bak’i da wata riga fara sannan ta rataya takobin ta da y’ar jakar ta ta fice daga fada ,fuskarta a rufe ta bar idanuwan ta a waje kamar wanda ta saka niqab , tafiya take cikin sauri kamar zata tashi sama, duk saurin ta sarki Hasheem yana tsaye ta sama a d’akin shi daga tagar d’akin yana kallon duk abunda ke faruwa ,tana fita Rizwan ma ya bi bayanta, ganin haka ne yasa sarki Hasheem shima ya rufa wani k’aton mayafi don Kar Fadawa su ganshi su ce zasu rakashi ya fice daga fada suna tafiya yana binsu duk yana jin abunda suke fad’a har suka shiga Inda Haidar yace za suna had’uwa ,ya lab’e bayan wani dan ice yana sauraron duk abunda suke fad’a…..</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵 BACCI😴😴😜</p><p>[3/30, 9:17 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>7⃣1⃣⏭7⃣5⃣</p><p><br /></p><p>Haidar, Jaseena, Aisha, Jauda, Meenah, da Rizwan!!!! Duk na ji abubuwan da suke shiryawa !!! Don haka dole ne mu kawar da su tun kafin su cimma burinsu🙄. Sarki Jalalud-deen ya mik’e tsaye ya rasa me zai ce saboda ko kad’an baya son dansa ya shiga wannan alamari amma tunda ya nuna taurin kan shi a fili toh lallai ba makawa sai an hukunta shi.</p><p><br /></p><p>Haidar yana sane da cewa sarki Hasheem yana wannan gurin shi yasa ko ‘kala bai ce ba a gurin ,sannan kuma yasa Jauda tayi karya akan shirye shiryen da sukayi ,sun yi akan sai an gama gasa zasu far musu amma ashe shirin Sam ba haka yake ba !!! Cikin dare k’afa duk ya d’auke suka shirya duk irin yadda Jaseena take shiganta ,suka shigo fada ,Jaseena akwai ilimin duk wani abu da ya shafi yayan itatuwa da ganyayyaki saboda haka ta shiga d’akin da sarki Hasheem yake ta zauna bakin makeken gadonsa tana wani muguwar dariya 🤓ta fito da had’in maganin da tayi sannan ta debi kad’an ta watsa a fuskar shi a take ya farka gami da yin wani atishawa ya sulale ya koma kan filow ,nan ta d’aure shi ga igiya tam sannan tayi fito a hankali ,Haidar ya shigo shi da Rizwan suka ciccibeshi suka yi waje. Haka ne ya faru da sarki Jalalud-deen ma ,suna fita basu zame ko ina ba se cikin wani tangamemen daki mai kama da keji suka tura su ciki ba komai bane ke gadin wajen illa damisa guda uku manya manya 🐅</p><p><br /></p><p>Da dariya suka fito su Jauda suka d’aga Jaseena sama yayinda Haidar da Rizwan ke ta musu dariya, suka koma cikin gari ,kasantuwar inda suka je da nisa ,sai kusan asubah suka iso cikin Ramali ,wannan kurkukun kuma shine asalin kurkukun masarautar Ramali kafin sarki Hasheem ya hau mulki. Isarsu cikin gari basu zame ko ina ba sai fada ,Haidar yasa a tara masa duk jama’ar wannan masarautar su hallara a cikin fada ,kafin awa d’aya duk Kowa ya samu isowa ,Haidar yayi murmushi ya gyara murya sannan ya fara da cewa:</p><p>Al’ummar Ramali !!! Akwai wani d’an karamin labari da zan baku labari ne na mikiya kuma ina kyautata zaton daga jin wannan labarin zaku fahimci Inda na dosa!!” Cike da mamakin jin magana da sukaji yarima Haidar yayi suka amsa da ” muna sauraron ka yarima!”</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵</p><p>[4/3, 10:43 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>7⃣6⃣⏭8⃣0⃣</p><p><br /></p><p>Ita mikiya wata tsuntsuwa ce wadda zata iya rayuwa har tsawan shekaru saba’in, amma domin kaiwa wannan Shekarun ,dole sai ta d’auki tsatsauran matakai,domin lokacin da takai shekaru arba’in dogin faracinan ta zasu zama basu da karfin neman ko kuma chafke abunda zasu samu a matsayin abinci,wannan dogon bakin ta mai kaifin zai kwanta (lank’washe ) fukafukan zasu zama tsofaffi, masu kauri kuma ga nauyi , wannan fukafukan masu kauri da nauyi ,zasu zama kamar a k’irjin shi suke hakan zai basu wuya wajen tashi sararin samaniya daga nan ne mikiya zata zama bata da wani zabi wanda ya wuce guda biyu kachal ✌🏾 ko ta MUTU ko kuma ta rayu cikin salo mai wuya na neman SAUYI! Hakan yana bukatar mikiyar ta tashi ne sama ta hau kan tsauni ,ta zauna cikin gidanta (nest) sannan sai Yayita buga wannan tsohon bakin nashi jikin dutse har sai ya fincike shi , sannan wannan mikiyar zata bari har sai sabon ya fito sannan sai ta fincike tsofaffin faracinan ta da shi ,lokacin kuma da wadannan faracinan suka fito ,sai ta fara fiffige tsofaffin fukafukan nata da shi wannan shine chanji da yafi ciwo zafi!! Toh daga nan ne wannan mikiyar take sake daukan sabuwar rayuwa ta sake yin wasu shekaru talatin din a gaba! ME YASA AKE buk’atar CHANJI??? Saboda a rayu kuma ayi zamantakewa!! Muma dole mu bi hanyar SAUYI!!! Amma ba kamar mikiya ba ,Muma dole mu sauya munanan d’abiun mu zuwa kyawawa da kuma abubuwan da muka aikata marasa kyau zuwa masu kyau ,mu zama masu koyi da abunda addini ya zo mana da shi!!</p><p>Saboda haka domin daukar hanya zuwa wannan SAUYI sai ku watsar da wadancan d’abiun domin samun sababbi ,duniyar da fadi take amma mu bita a Sannu! Ku bude ajiyayyan k’wak’walwar ku don ku Adana wannan ko zaku tashi da sabuwar rayuwa irin ta mikiya!!!……..</p><p><br /></p><p>Kowa yayi shiru jiki a sanyaye ,fadar tayi dub kamar babu wata halitta a cikinta , wasu na hawaye amma hawaye ne na farin ciki cewa yau gaskiya ta dawo masarautar Ramali! Wani dattijo ya mik’e yace ” wannan haka yake yarima Haidar! Muna tare da kai ! Dattijawan gari suka na’da Haidar a matsayin sarkin Ramali , ganin yadda komai yazowa Haidar cikin sauk’i yasa Rizwan ya mak’ale mishi yace shi zai raka shi masarautar Kalahari don ya nemi gafarar mutane wata’kila in yasa baki za’a yafe masa shashanci da yayi ta aikata musu ba dare ba rana,nan suka sake sabon shiri dukan su tare da wasu mayak’a guda ashirin suka d’au hanyar Kalahari…………</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵</p><p>[4/7, 6:04 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>8⃣1⃣⏭8⃣5⃣</p><p><br /></p><p>Kasantuwar ba hanyar da su Jalalud-deen suke bi don shiga k’asar Ramali zasu bi ba ko dawakai basu d’auka ba cikin sauki suka bi ta inda Jaseena ta fito suka shiga wannan ramin ruwan har ta kaisu ga asalin cikin kogon ,bayan sun gama dirko wa daga wannan dutsen ne suka tsaya karkade jiki su Jauda se kalle kalle ake yi basu ankara ba suka ga sojojin yak’i sun zagaye su kowanne hannu rik’e da mashi ,gashi kuma abun da ya basu mamaki duk babu saurayi cikin su don duk sun manyanta da gani kasan sun yi zamani, Jauda ce ta fara jefar da jakar da ta rik’e tana motsar k’walla ” baba!!! Abunda ta iya furta wa kenan ta nufi gurin d’aya daga cikin wad’anda suka zagaye su ta rungume tana kuka Aisha ma ta nufi gurin wani da ke tsaye yana kallonta sai hawaye ,Jaseena da ke kallon su tuni itama ta fara k’wallar saboda ta tuna nata mahaifin da bata ma san wanne hali yake ciki ba , Muryar sarki Haidar ne ya dawo da ita daga duniyar tunani, tana juyawa taga gurin babu Kowa daga shi sai ita ta fara juye juye fuskar ta cike da alamar tambaya?? Kafin ta furta komai Haidar yace ” ya ke ma’abociyar kyau da farin hali, kada ki damu Mun basu dama ne su gana da iyayen su domin kuwa sun yi kewar juna ” Murmushi Jaseena tayi sannan ta fara share hawayen da ke gangaro wa daga idanuwan ta ,Haidar ya matso kusa da ita yace ” ya isa haka Kar ki sake yi min asarar hawaye ! Kuma baba yana cikin k’oshin lafiya” Jaseena ta d’ago manyan idanuwan ta tace ” don Allah muje in ga baba na ,don hankali na bazai kwanta ba in ban sa shi a ido ba tana fad’in hakan hannunta guda kuma ta chafke wuyar rigar shi ,inda ta shak’e ya kalla sannan yayi Yar murmushi cikin murya irin na zolaya yace ” irin wannan chafka haka ,duk kin yamutsa min riga! Lallai kina so na sa a kulle min ke a kurkuku yanzungaske.😜 ” Hakan yayi matuk’ar bata dariya yadda ya ta6e fuska kamar da gaske. Ya ce Haba!! Ko ke fa ? Amma matar sarki guda gashi kuma jarumar mata amma tana hawaye kamar raguwa?” Dariya ta bushe da shi tace ” Aa ba wani nan ! Cewa zakayi jarumar mata da maza 😝 ai mazan ma saidai in basu nemi in sambad’e su ba 💪🏼”. Dariya sosai ta bawa Sarki Haidar har ya shagala ya nemi gurin zama yana kallonta, ita ko sai fama take da y’ay’an innibi🍇 ,yana kallon yadda karamin bakinta ke motsawa cikin nutsuwa ta lumshe idanuwa sai faman tauna take, yayi murmushi ya mik’e ya d’auki wani dan karamin dutse ya wulla mata ya samu damtsen ta ,tuni hankalin ta ya dawo daga duniyar da ta lula tace ” ya dai?* ya had’e rai yace ” kin barni babu hira sai faman tauna kike yi !! Ni na fa gaji ma kuzo mu tafi inda zamu je kafin dare yayi mana” chan sai suka lura ko ina yayi shiru cikin kogon</p><p><br /></p><p>Cikin sand’a yake tafiya tana biye da shi ,haka suka gama dube duben su basuga Kowa ba a cikin kogon ,Jaseena tace ” toh ina suka tafi ne?” Haidar ya yi shiru na yan mintina sai yace” duk yadda akayi sun nufi Kalahari ne zo mu tafi!! ” ko da suka fito bakin kogon suka tsaya suna tunanin yadda za’a yi su tafi Kalahari babu doki kuma gashi da nisa suna so su tadda su Jauda. Har ta hak’ura ta jingina da jikin kogon kawai suka jiyo sautin doki ,tana juyowa ta hango zainu shi kad’ai ya dumfaro su ta juya ta dubi Haidar tace baba ne ya turo shi , na tabbata sun isa Kalahari!! ”</p><p><br /></p><p>🏵 Jeeddah ja’o🏵</p><p>[4/7, 9:36 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵Jeedah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>8⃣6⃣⏭9⃣0⃣</p><p><br /></p><p>Isarsu Kalahari basu zame ko ina ba sai cikin fada kamar wanda ake jiran isowar su mutane aka fara bude hanya don su samu su wuce ,Jaseena kam da ta hango baban ta taga yadda suke tafiya a hankali a saman dokin ,yasa ta dirko daga kan dokin ta ruga. Rungume mahaifin nata tayi tana kuka ,ya d’ago ta yana faman share mata hawaye ,zata yi magana kenan suka ji Hameed ya ja wani irin numfashi kamar an shak’e shi ,idon shi na hawaye ,tace ” baba!! Me ya sameka baba??” Kallo na biyu da zata masa ne ta ga abunda ya matuk’ar tada mata hankali ,mashi ne a wuyan shi ga kuma Jini yana malala kamar ruwa ,a take ta kurma ihu ta zube a k’asa jiki na b’ari ,da gudu Haidar ya iso inda suke ya rike Hameed yana hawaye , abunda ya iya furtawa shine ” ga Y’ata nan Amana ,Kar ku cutar da ita marainiya ce don Allah!! ” ya dan saki wani ‘kara gami da Kalmar shahada take ya mace a gurin ,wani irin ihu Jaseena tayi ta sulale daga zaunen da take ta fad’i sumammiya Haidar ya dubi su Jauda da ke faman zubar da k’walla yace ” ku kai Jaseena ciki ku tabbatar ta samu kulawa don Allah ! Suka yi kamar yadda ya umarce su.</p><p><br /></p><p>Haidar yace sojojin yak’i su shiga su nemo koma waye yayi wannan Harbin a kawo masa shi. Ana cikin wannan alamari ne wani soja ya zo da gudu wujiga wujiga duk jikinshi yanka ,sai haki yake yana kiran sarki Haidar. Fadawa suka tare gurin shigowar amma ya umarce su da su barshi ya karaso domin daga ganin shi kasan akwai wata matsalar da ke tafe da shi. Kafin mutumin ya fara magana ,Haidar ya juya ya dubi su Rizwan yace ” a shirya gawar baba mu sallace shi Mu kaishi makwancin shi na gaskiya,” sannan ya juyo ya dubi mutumin yace ” bawan Allah me ya faru da kai haka? Wa ya aikata maka wannan taaddancin kuma daga ina kake?</p><p>Cikin rawar jiki mutumin yace ” Allah ya baka nasara daga Ramali nake ….” Ko da Haidar yaji an ambaci Ramali yasan tabbas babu lafiya gashi sarki Hameed ya rasu ,ga Jaseena Kwance babu maraba da matacciya dole su Jauda su kasance tare da ita , toh me ma yake faruwa ne haka?” Tambayar da yayi wa kanshi kenan gaba daya ya kasa tunanin abu daya, ya tura wasu Fadawa tare da mutumin su bashi taimakon gaggawa kuma a kula da shi”…….</p><p><br /></p><p>Ana shirin sallatar Hameed ne Jaseena ta farka ,bata bi ta kan su Jauda ba ta furma a guje ko mayafi babu duk gashi a barbaje gashi duk ta zabga gumi gashin ya mammanne mata a fuska bata zame ko ina ba sai gaban gawar mahaifin ta cikin yanayi na tausayi ,bakinta karkarwa kamar mai jin sanyi , ta d’aga hannun ta mai karkarwa kamar zata yaye masa fuska sai kuma ta fasa ta dunkule hannun cikin kuka tace ” baba !! Ka tashi don Allah kar ka tafi !!! Abunda ta yi ta maimaita wa kenan hakan ya sake tada wa Haidar hankali don a tunanin su ta zauce ne ,yadda take yi din abin tsoro da kuma tausayi. ” Meenah ku koma da ita ciki don Allah ” shima yana kokarin danne kukan da ya so kufce mishi.</p><p><br /></p><p>Bayan sun dawo daga janaiza Haidar bai zame ko ina ba sai cikin fada don ya nemi dakin da Jaseena ke Kwance ,ko da ya iso gurin shi da Rizwan basuga Kowa a d’akin ba ,babu Jauda ,Jaseena Aisha da kuma Meenah. Haidar ya fito a fusace ya dubi bafaden da ke bakin k’ofar yace ” ina suka tafi kuma ?” Bafaden yace ranka shi dad’e sun fita su hud’u amma fa naji kamar suna maganar Ramali ban sani ba ko Chan suka nufa……. Bai ma saurari k’arshen zancen ba ya juya suka nufi hanyar fita……………….🦃</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵</p><p>[4/8, 8:19 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>9⃣1⃣⏭9⃣5⃣</p><p><br /></p><p>Gudu suke kamar zasu tashi sama ,Jaseena ce kan gaba sai faman k’walla take yi zuciyar ta na ta tafarfasa har suka isa masarautar Ramali ,shigan su ke da wuya suka ji ana ta rufe kofofin gurin wasu sojoji suka zagaye su kamar masu kama barayi ,babu wanda ya motsa a cikin su tabbas Jaseena ta lura cewa duk sojojin da ke zagaye da su kibiyar da ke kwari da bakan su iri d’aya ne da wanda aka harbi mahaifin ta ,ta tabbatar cewa wannan aikin Jalalud-deen ne ba Kowa ba ,abunda ya sake kulle musu kai shine yaya akayi suka fito daga wannan kurkukun? Jauda ma abunda take ta sak’a wa kenan………</p><p><br /></p><p>Ko da Haidar ya fito waje ,yasa an tara mishi jama’ar garin manya da k’anana da kuma gagga gaggan sojojin yak’i wadanda ake ji da su suma sun hallara nan ne Yerima Rizwan ya rok’eksu yafiya kuma ya sanar da su cewa zai yi koyi ne da irin halin kawun shi marigayi sarki Hameed ya kuma yi rantsuwa da hakan ,Kowa ya ji dad’in wannan alamari saboda haka dattawan garin basuyi wata wata ba suka na’da shi sarkin Kalahari ,bai hau kan karagar mulki ba yace har sai yaje an yak’i azzaluman da suka kashe sarki Hameed kuma in har bai dawo da rai ba ,toh ya bawa Meenah wannan gadon mulkin domin ita tafi chanchanta ,amma idan har komai ya tafi daidai toh za’a hada masarautar Ramali da Kalahari su zama masarauta d’aya a k’ark’ashin mulkin sarakuna biyu wato sarki Haidar na Ramali da kuma sarki Rizwan na Kalahari ⚔</p><p><br /></p><p>Jaseena bata wani tsaya 6ata lokaci ba ta zare takobin ta ta diro kasa suka fara fada su Jauda ma suka biye mata gurin ya kaure bakajin ‘karar komai sai na had’uwar karafuna kafin kace wani abu sun gama da sojojin suka tsaya a gurin sai haki kamar zakanya Jaseena ke yi ta mayar da takobin cikin rigar shi ,d’aga kanta da zata yi kawai ta hango munafukan guda biyu ,sarki Jalalud-deen rik’e da kan d’aya daga cikin damusar da ke gadin kurkukun ya d’aga sama yana kyalkyata dariya daga chan saman benen da yake yace ” me ya farune GIMBIYA JASEENA!? Ina fata ba karaya kika yi ba don in hakane wasan Sam bazai yi dadi ba ! In kin isa yadda na saka tsaro dinnan ki karaso kiga me zai faru! Amma ko da yake ina so inyi magana da ke ,kuma ke kadai don haka ke kadai nake so ki zo ki sameni babu makami kuma !!! Ya sake burgewa da wata muguwar dariyar. Jaseena da idanuwan ta sun kad’a sun yi jajir ta kau da kanta daga duban da take masa tace KAI !!!! MATSORACI!!! KAI NE KAKE TUNANIN TAKOBI KO BAKA SHINE ASALIN MAKAMI ,AMMA ASALIN MAKAMI A ZUCIYA YAKE!!!!” Ta zubar da makaman zata tafi su Jauda suka sha gabanta Aisha tace ” Jaseena ba zamu barki ki shiga ke kadai gurin wad’annan azzaluman ba gaskiya” Jaseena tayi murmushi tace Haba Aisha ,ai koda kashe ni zasuyi inshaa Allah zan shiga kuma zan d’auki fansa!!:evil: ta wafce hannun ta tayi ciki duk fadawan suka bita da kallo 🙄</p><p><br /></p><p>Shiganta kenan su Haidar suka iso gurin ,garin ma shiru kamar babu Kowa , a nan ya iske su Jauda cikin matsananciyar damuwa , suka sanar dashi duk abunda ke faruwa hankalinshi ya tashi Rizwan yace ” yanzu meye abun yi ??¿</p><p>Jaseena kuwa da ta shiga kai tsaye fada ta nufa shiganta kenan taji an rufe k’ofa ta juya da sauri don taga wanene daga cikin su, Muryar shi ne ya fara ratsa kunnuwan ta tabbas sarkin yak’i Amjad ne:oops: ta waro ido waje tace ” kai ! Dama Kaine?!! Me kake yi a nan kuma?!!” Ya matso kusa da ita ya makureta a bango kamar me neman kasheta ,sai taji yana mik’a mata abu a hannun ta ,tayi amfani da tunanin ta taji ashe karamar wuk’a ce tayi wata k’aramar dariya yace ” godiya nake” shi kuma ya hankad’a ta gefe ta zube a ‘kasa su Jalalud-deen kuma basu san wainar da suka toya ba sai wani dariyar keta sukeyi. Jalalud-deen ya karaso inda take rik’e da irin kibiyar da aka harbi Hameed yace ” ban sani ba Jaseena ! Ko tayaya zan fara gamawa da ke ! Ko in sambad’e ki da wannan takobin ne kokuma wannan kibiyar wadda itace silar barin ubanki da uwarki duniya?? Ko kuma………… Kafin ya karasa ta buga masa wannan y’ar wuk’ar a daidai mak’ogoro kamar me bud’e madarar peak 😜 tuni ya durkusa kan gwiwar shi ,Jini na malala kamar ruwa, ta zare wuk’ar tace ,ba sai ka za6a ba🙄 take ya fadi ‘kasa ya gama shure shuren sa har ya margaya (Hmmmm duniya kenan budurwar wawa akan son abin duniya har ka kai kanka ga halaka!!) Ta juya ta dubi sarkin yak’i tace” ina Hasheem? ” ya nuna mata k’ofar fita yace ” ya fice tun tuni! Mu bishi!!!!! Jaseena tayi wata muguwar dariya tace Kar ka damu ,yayi gudun gara ne ya tadda zago don nasan yanzu haka jikina yana bani ZAKI NAH!(Haidar) ya riga ya iso 👣</p><p><br /></p><p>Suka dunguma sukayi waje suma, ko da suka fita basu tarar da Hasheem a raye ba amma kuma kamar mutuwar kasko sukayi da Jauda😭 da gudu Jaseena ta yo kan Jauda da ke Kwance a gurin matacciya ta rungume ta ,kuka takeyi duk ta susuce su Meenah ma na durk’ushe a gaban su suna kukan. Haka ranar Jaseena ta kwana tana kukan zuci wanda yafi kuka ciwo😭……………</p><p><br /></p><p>🏵Jeeddah ja’o🏵</p><p>[4/8, 10:20 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016</p><p>🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚</p><p><br /></p><p>9⃣6⃣⏭1⃣0⃣0⃣</p><p><br /></p><p>BAYAN SHEKARA D’AYA</p><p><br /></p><p>Zaune yake kan kujerar mulkin sa yana magana da waziri Jabeer ,sarki Haidar ne cikin kaya na alfarma na sarauta sai hira sukeyi wanda har masu gadin ma suna saka baki , ana ta raha, chan waziri yace ” Allah ya baka nasara zan iya yafiya yanzu?” Haidar yayi murmushi yace me zai hana ? Ko so kake kayi tafiyar dare baka ga yamma ta kawo kai ba ? Waziri Jabeer yayi murmushi ya mik’e ya nufi hanyar fita.</p><p><br /></p><p>Dank’o ne a hannun ta irin na Harbin tsuntsaye ta saita shi a kan kujerar ta sake masa daya a hannun shi ,ko girgiza bai yi ba ya basar ,har tayi sau uku ,sannan ya juya don ganin me aikata masa hakan. Had’a idon da zasuyi kuwa ta zaro manya manyan idanuwanta da suka sha ado da kwalli:oops: sannan ta tattare doguwar rigarta ta ruga a guje ta fice zuwa lambu , murmushi kawai yayi ya mik’e ya kwashi duwatsun da ta jefo mar ya fice ,bai ma san inda ta nufa ba shidai kawai yana ta kallon yadda mutane Kowa ke gudanar da alamuran shi cikin lumana wasu yara kyawawa sun kai biyar suka rugo da gudu suka rungume shi suna dariya ,sai d’aga su sama yake yi yana musu wasa wata tazo wucewa dauke da kwando cike mak’il da kayan marmari ya tsayar da ita ta kawo ma yaran ,sai tace ” Allah shi taimake ka Sarauniya JASEENA ke da buk’atar su ” murmushi yayi yace ” ki basu sai a kai mata wasu , tana ina ne itan?” Matar tace tana cikin lambu ” gami da mik’a masa kwandon ta wuce. Shi kuwa ya durk’usa gaban yaran ya ajiye musu kwandon yace ” bismillah! ” kowannen su ya d’eba shima suna ta Saka mishi a baki sai da yaga sai loda mar suke ya mik’e da sauri yace ” Yauwa maza ku cinye kafin na dawo ya wuce ya barsu suna ta fama ,ba ma mutane ba har dabbobi ma sun san akwai y’anci a Ramali:).</p><p><br /></p><p>Lek’o ta yayi suna had’a ido ta ruga da gudu ya bi bayan ta sai fama take da doguwar riga hakan yasa ya cimmata ,ya d’aga dutsen data wurga masa kamar zai rama sai yaji daga waje wani mayak’i yace ” Allah ya baka nasara sarkin Kalahari Rizwan ne tafe da Sarauniya Meenah!!!! Jin hakan yasa ya sauk’e hannun shi yace ,a shirya tarbar su ,kuma a sanar da sarkin gida ” mayak’in yace toh ranka shi dad’e! ” sarki Haidar ya maida dubanshi ga Jaseena yace ,kin taki sa’a yau da sai na rama jifan da kika min!!” Ta rungume shi tana ta dariya tace ” kai dai kace kaji tsoro Kar na fille maka kai yanzun nan 😝 ” ya bushe da wata irin dariya yace ” ni din ? Toh ko za’a gwada karfi ne?” Ai ko bamu gwada ba kasan na fika k’arfi 💪🏼” ya sake bushewa da dariya yace ” karfin cin tuwo ba! Yanzu ma naga an taho da k’aton kwando cike mak’il da kayan marmari Wai naki ne 😜 ” Tuni ta had’e rai tace ” toh ai kasan ba ni kadai bace shi yasa 😒 ” ” Ohhhhh na gane !!! Kar kiyi ma d’ana sharri ,ke kad’ai kike cin kayanki ☺” ta bugi kirjin shi da hannun ta tace ” zan rama ai!!!” Ya kama hannunta suka fita suna tafe yana tsokanan ta………..</p><p><br /></p><p>Haka dai rayuwar su ta kasance cikin farin ciki da kaunar juna ,ga gaskiya da rikon Amana ,sukan ziyarci junansu daga su har su Rizwan ,Aisha ta auri abokin Rizwan ne majeed aka kuma suka zauna a gidan Benaxir don yanzu kam bata nan dama ba gidan ta bane mallakin su Aisha ne ,majeed kuwa likita ne don babu wani magani da bai san amfanin shi da kuma yadda ake hadawa ba!! Saboda haka wannan babban gida ake kiranshi da gidan majeed likita!</p><p><br /></p><p>Akwana a tashi yaran Jaseena biyu ,na farkon sunan mahaifin ta ne wato HAMEED na biyun kuma mace ce mai sunan JAUDA yara ne kyawawan gaske son Kowa !</p><p>Bangaren Meenah kuwa danta daya mai sunan mahaifin Haidar wato MAHMOUD! Aisha kuwa mace ta Haifa sunan ta Sameerah sunan kanwar majeed da ita ,gaba daya suna cikin farin ciki ,nutsuwa da kwanciyar hankali ,zalunci ya kau!!!!</p><p><br /></p><p>🙏🏽ALHAMDULILLAH🙏🏽</p><p><br /></p><p>Godiya ta tabbata ga ubangiji Allah mai Kowa mai komai wanda ya kawo ni har izuwa wannan ranar da na kammala wannan takardan nawa mai suna JASEENA !!</p><p><br /></p><p>Dama ance in kaki sharar masallaci zakayi ta kasuwa ,kuma abunda kashuka shi zaka girbe , masu iya magana sunce RABON KWAD’O BAYA HAWA SAMA!!!</p><p>Duk abunda Allah ya kaddara zaka samu tabbas babu makawa sai ka same shi ,amma in kasa son zuciya toh lallai zai zamto sanadiyyar zubar ruwan idanuwa a gareka 😭 Allah kasa mu dace AMEEN</p><p><br /></p><p>ALL CREDITS GOES TO</p><p>MY BESTIES</p><p>– Rukayya Abdullahi Kakumi (Rukey kaxs)</p><p>– Aishat Muhammad (maman abd Shakur)</p><p>– Sufeeyah abdoul</p><p>– mah Nancy trbl</p><p>-my ‘kawas Zeetu and Zainab Ahmad…..</p><p>And Ameener esmael( maman Ilham)</p><p>GODIYA TA MUSAMMAN</p><p>AJAJIGEEE GROUP</p><p>ZINARE BOOKS</p><p>SADAU GROUP OF WRITERS !!!</p><p>AND OTHER MEMBERS OF JEEDDAH JAO 📚NOVELSTOPIA🏵</p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-86276321600783160932021-12-02T05:54:00.000-08:002021-12-02T05:54:56.377-08:00FATU A BIRNI COMPLETE HAUSA NOVEL<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEjVMH1qlJg0cyNnAwpKDpp2id0RpOWP18EGpv4sBUZGtPHz3X3eAXsSswXZg741dcSjxmHxnCf3snOl8zyGSZ9FDDwe8OtTRd31utSihI6h7qhwgAQv7iRNMHjeMR66nGCYIneoyEAJlgMoh_hCxzvWK1-K66uAC8mvodU20x6AS-wGhBVVFH0TFcLk=s2048" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="FATU A BIRNI COMPLETE HAUSA NOVEL" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="310" src="https://blogger.googleusercontent.com/img/a/AVvXsEjVMH1qlJg0cyNnAwpKDpp2id0RpOWP18EGpv4sBUZGtPHz3X3eAXsSswXZg741dcSjxmHxnCf3snOl8zyGSZ9FDDwe8OtTRd31utSihI6h7qhwgAQv7iRNMHjeMR66nGCYIneoyEAJlgMoh_hCxzvWK1-K66uAC8mvodU20x6AS-wGhBVVFH0TFcLk=w400-h310" title="FATU A BIRNI COMPLETE HAUSA NOVEL" width="400" /></a></div><br /> [1:58PM, 5/4/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<p></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">CIKIN TASHA:<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Mutanen dake fitowa daga cikin bus din ne
na hango wata matashiyar budurwa, wacce inka lura da yadda take waige waige
tana zare idanu zaka tabbatar yaune farkon shigowanta garin Gombe,
"Gombawa diban fari, ba'a kwana daku ba an tashi daku"😜 Itama
FATU haka ya ksance da ita don ynxu misalin karfe 7:20 na safe. Matsawa gefe
tayi ta tsaya inda bbu mutane sosai ta cigaba da dube dubenta. Can nesa ta
hango wata mai sayar da kosai da dankali a cikin tashan. Nufanta tayi da sauri
cikinta na bada wani sauti qululululu don rabon da taci abinci tun jiya da rana
sai fura kadan da kakanta ya bata da dare. Sauri take yi har ta isa, sallama
tayiwa mata mai sayar da kosai, matar ta amsa, fatu tace a bata kosai da
dankali na dari, matar ta sa mata a leda ta miqa mata, kudi ta ciro 500 daga
cikin jakarta ta miqawa matar, aka bata canji, gurin wasu yara masu sayarda
pure water taje gefe kadan da mai sayar da kosan. Ta sayi guda biu. Anan ta
fara tunanin a ina zata zauna taci, don
har masu shaguna sun fara budewa. Bakin wani shago taje inda bbu mutane ta
zauna, juya baya tayi yanda baxa a ganta ba ta fara cin kosan tana korawa da
pure water. Sauri sauri har ta gama. Alhamdulillah ta furta, sannan ta wanke
hannunta ta goge bakinta da zumbulelen hijabinta. Minti biyu da haka ta miqe
hade da karkade jikinta ta dauki jakanta ta rataya ta cikin hijabi. Wajen
tashar ta fito tana tunani barkatai a cikin zuciyarta. Kuuuuuuuuuuu sai timm.
Innalillahi abunta matar dake cikin motar ta fada cikin kidimewa. Kafin ta fito
har an fara taruwa akan fatu, tana fitowa tayi kan yarinyar da saurinta tana su
taimaka mata su saka ta cikin motar ta. Wasu mata yan sharan titi ne suka
taimaka mata suka sata a mota yayin da matar ta shiga driver seat ta cilla kan
titi sai hospital.<span></span></span></p><a name='more'></a><o:p></o:p><p></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[2:25PM, 5/4/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Hospital:<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tana isa asibiti ta shiga sai gata ta fito
da nurses biu hade da gadon tura mara lafiya. Suka ciccibi fatu suka daura akan
gadon sukayi ciki da ita cikin sauri. Emergency aka shigar da ita, bayan 15
minutes wata doctor ta fito da sauri matar ta tare ta, tace "ya patient
din? Doc tace "da sauqi don bata buge sosai ba, tsoritan da tayi ne yasa
ta suma, sai kurjewa da tayi a kafa. Ynxu za'a kaita dakin hutawa zata farka
nan da 4-5 hours. Don tana bukatar hutu. Tana gama fadan hka tayi gaba abinta
yyinta wata nurse da gangaro fatu a kan gadon marasa lfyn ta kaita dakin hutu
matar ba biye da ita. Ta kai minti biu tsaye a kanta sannan ta juya ta koma
mota, yaronta dan kimanin 7 yrs yace 'mum ina wanda kika bugen? Sai a sannan ta
tuna ashe tare suke, school zata kaishi da yake yau monday tana sauri kar y
makara, shine hatsarin ya faru. Shafa kanshi tayi tace 'farouq tana ciki an
bata gado, muje in kaika school.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Acan school tayiwa teachers bayanin abunda
ya faru don yara sun dde da shiga class. Komawa gida tayi wanda a lokacin 9 da
yan mintuna. Ta samu dija mai aiki tana goge a palour, 'sannu da dawowa hajia'
hajia ta amsa tace 'kiyi abinci da mutum 1 za'a kai asibiti, na buge wata
yarinya a hanya. Bata farfado ba balle in san gidansu, na duba jakanta banga
tana da phone ba ko ID card. Cikin jimami dija tace "to hajia Allah ya
kiyaye na gaba, taji ciwo sosai ne? Hajia ta mata bayanin da Doc ta mata sannan
ta haura sama tana tunanin yarinyar game da tambayoyi cike a kanta wanda bbu
wanda zai bata amsan sai yarinyar. Don daga ganin shigar da tayi zaka gane yar
kauye ce, amma cikin jakarta kudi dari biyar biyar sabbi wanda yawansu zai kai
25k, kuma jakan nata irin na yara masu zuwa makaranta ne, sai kaya kala uku. Ni
kaina mmn Fa'iz sai da zare😳. Duk answers na gurin fatu wacce har ynxu
tana gadon asibiti bata san duniyar da take cikiba.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku Maman Fa'iz👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[11:44AM, 5/5/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu bata farka sai 12:23. A hankali take
bude idonta har ta fara gani rass. Juyo da kanta tayi gefe inda taji muryan
mace na mata sannu, kyakkyawar mata ce mai dan jiki kadan wanda da alama ta
danbmanyanta, "Ya jiki ta qara cewa
da fatu, a hankali ta furta da sauqi.
Sannan ta fara qoqarin tashi, matar tayi hanxarin taimaka mata ta zauna.
Tace "ki dan huta sai kici abinci. Bari in hada miki tea. Tea ta hada mata
mai kauri tasha kadan tayi hamdala. Sannan matar tace meye sunanki, kuma a ina
iyayenki suke? "Suna na fateema ana cemin fatu, dangina suna kauye mai
suna Garin Modibbo dake karkashin qaramar hukumar Akko. Matar tace "sunana
hajia kulsum, nice na buge ki da mota ina sauri zan kai dana makaranta. Kiyi
hakuri. Hope yanxu bakya jin ciwo? Daga kai fatu tayi, hajia kulsum tace
"gurin wa kika zo nan garin? Ina son in kaiki in bada hakuri. Saurin
girgiza kai tayi kanta na qasa tace "a'a hajia hakama ya isa, ba sai kinje
ba, nagode. Hajia kulsum ta tashi ta
deba mata abinci da kyar fatu taci rabin plate tace ta koshi tasha ruwa. Hajia
na lura da yanayinta, yarinyar tana cikin damuwa. "Hajia ina son zuwa
bandaki" hajia kulsum ta taimaka mata taje bandaki, kama ruwa tayi sannan
tayi alwala ta fito. Zama ta qara yi a
kan gadon, shiru sukayi na dan lokaci sannan aka fara kiraye kirayen sallah.
Sukayi sallah, sannan Doc ta shigo ta duba fatu, ta mata questions game da
yadda take ji. Doc ta juya gurin hajia kulsum tace "zaku iya tafiya gida,
shes gud now" ta fita. Hajia ta fita taje ta biya kudi ta dawo tace mu tafi.
Sun fito harabar hospital dinne fatu tace "hajia ko kun tsinci
jakata" hajia tace "eehh, yana gidana manta wa nayi ban dauko miki
ba. Amma muje sai ki karba. Mota suka
shiga suka tafi. Unguwar GRA suka shiga, ita dai fatu in banda kalle kalle bbu
abunda takeyi, wani layi suka shiga wanda yafi ko ina haduwa don gidaje 20 suna
kallon juna sai titi a shimfide a tsakiyarsu. Gaskiya fadin tsaruwar houses din
ma bata lokaci ne. Nidai mmn fa'iz nace kamar a turai. Fatu kuma tace Aljannar
duniya. A cikin jerin gidajen wata mota hadaddiya ta fito ta hau kan titi,
hakan yyi daidai da juyowar fatu wacce take kalle kalle tun shigar ta unguwar
mutumin da ta gani a cikin motar shiya sata daskarewa, bakinta a bude tana nuna
shi da yatsa, har yazo ya wuce baima san tanayi ba don waya ma yakeyi yana
murmushi. Horn hajia tayi a bakin gate din gidanta wanda yake kallon gidan da
mutumin ya fito. Aka wangale gate ta kusa hancin motar har ta samu parking
space tayi. Sai a sannan ta lura da fatu wacce idanunta na tsiyayar hawaye tana
nuna glass da yatsa, fatu" ta kira sunanta amma bata amsa ba, dafa
kafadarta tayi ta juyo a firgice sannan ta fashe da matsanancin kuka wanda yasa
hajia cikin wasi wasi. Anya yarinyar nan ba aljanu gareta ba? Ace yarinya da
ita ta fito daga garinsu ba kowa tare da ita, kuma ba'a mata komai ba tana kuka
tana nuna glass. Whats wrong with her? Kodai auren dole za'a mata ta gudu? Ko
ko ko? <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'iz👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:05PM, 5/7/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fitowa hajia tayi daga motar ta zagayo inda
fatu take, bude murfin kofan tayi ta kamo hannun fatu suka shigo cikin gida ta
zaunar sa ita kan kujera a palour. Fatu ta cigaba da kukanta. "Dija
dija" dija ta fito dga kitchen ta ce "gani hajia" hajia tace
"taimaka min da ruwa pls" komawa kitchen tayi ta fito da tray an
daura swan water da cup. Ta ajiye ta koma tana tunanin wace yarinya ce haka
hajia ta samu? Daga kafada tayi tace hala yar aiki ce. Hajia ta tsiyayi ruwa ta
miqa ma fatu wacce kukanta ya tsaya sai sheshsheka takeyi tace "kisha
ruwa" ba musu ta karba ta sha, tayi ajiyar zuciya. Hajia ta numfasa ta
fara magana "fatu a yanda na lura da yanayinki kina cikin matsala, kuma
kinyi yarinya a barki ki fito daga kauyenku ke kadai ba tare da wani dan uwanki
ba. Tambaya nake son miki, ki fadi tsakaninki da Allah, gurin waye kika zo anan
garin? Fatu da tunda hajia ta fara magana kanta na qasa tace "gurin
dan'uwa na nazo" " a ina yake? Fatu tace "na manta sunan unguwan amma
yana cikin jakata. "Farouq farouq hajia ta kira shi yana room dinshi yana
buga game, tun 12:30 y dawo daga skul. "Gani mummy" "jeka room
dina ka dauko min wani skul bag akan bedside drower. Yace "to, amm mummy
wannan ba itace ta mutu dazu ba? A cikin motarki. Hajia tayi daria tace a'a
suma tayi not mutuwa, now get d bag. Ya juya da gudu ya dauko ya miqawa hajia
ita kuma ta miqawa fatu, gurin fatu yaje da take kallonsa tun farkon
shigowarsa. Yace daxu mum ta bugeki, kinji ciwone? Tace "a'a tana
murmushi, amma kin suma ko? Tace ehh. Zai qara wata tambayar hajia ta katse shi
tace " farouq jeka fara shirin islamiyya. In ka dawo she wll answer all ur
questions. Ya haura sama da gudu yana cewa to mummy kar ta tafi, ta jirani fa. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Aljihun gefe na skul bag din fatu ta bude
ta ciro wani pic hade da guntun paper ta miqawa hajia kulsum. Mamakine ya
bayyana qarara a fuskar hajia data kalli pic din, paper ta bude ta qara gaskata
abunda ta gani. Ba komai ta gani ba illa pic din sultan gefenshi kuma fatu ce,
a kauye aka dauki pic din,don ga irin bukkan rumbun nan da ake ajiye amfanin
gona. A cikin paper kuma adress na gidansu sultan ne, wato gida mai kallon gidanta. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Hajia ta dubi fatu tace "wannan
dan'uwanki ne? Fatu tace ehhh, "ya dangantakar ku take? Fatu ta numfasa
tace hajia zan fada miki ko zaki taimaka min in shiga cikin gidan, don naga
kamar sai da mota ake shiga irin gidajenku. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">ASALIN LABARIN<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[4:57PM, 5/8/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">ASALIN LABARIN<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">
Kamar yadda na fada miki sunana fatima. Dangin mahaifina yan asalin
garin modibbo ne, fulanine usul. Dangin mahaifiya ta kuma yan dukku ne, suma
fulani. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Kaka na mallam Aminu malami ne sosae wanda yake
koyarda almajirai da manya, yana da matarsa binta wacce tun auren saurayi da
budurwa suke tare, auren dangi aka hadasu. Yayansu biyar amma biyu ba rai, uku
ne suka rayu har girma, goggo innani itace babba, sai sama'ila da kaninshi
jamilu sune suka rasu, sai babana mamuda da kaninshi muntari. Tun kafin a haifi
muntari goggo innani tayi aure. Tun tasowan babana Allah y yishi mai kokari ta
fannin karatu da neman na kanshi, baiyi boko ba amma yyi arabi sosae. Tun yana
saurayi ya fara kasuwanci, inda yake bin kasuwannin kauyuka yana sayar da
busheshen kubewa. In damina tazo kuma ya taya bbanshi noma. A yawonsa na bin
kauyuka ya hadu da mamata a Dukku, tazo siyan kubewa ya ganta yace yana so,
itama ta nuna ra'ayin hakan, bai bata lokaci ba ya samu babanta ya masa bayanin
inda ya fito da sana'ar sa kuma yaga diyarsa yana so. Babanta yayi murna da jin
haka, don akoyaushe addu'arsa bai wuce Rahmatu ta samu miji tayi aure ba, don
tun tana karama mahaifiyarta ta rasu anan zamanta ya dawo gurin kishiyar
mamanta, ba irin duka zagi da wahala rahmatu bata dandana ba, babanta kuma
bashi da bakin magana kamar an asirce shi. Bukatarsa kullum ta samu miji tayi
aure ko zata huta. Ya sami yayansa da maganan inda yaqi amincewa, wai tunda
gida bai koshi ba baza a bawa bare ba. Kuma ai zatayi nisa da gida. Shi a sonsa
a hada ta aure da dansa wanda duk garin bbu wanda baisan yana dauke dauke ba,
bashi da takamaimen sana'a. Babanta ya nuna rashin amincewarsa shima, a haka
suka tashi ba tare da tsayayyem magana ba. Babana kuma yana komawa gida ya
sanar da iyayenshi inda sukayi murna da fatan alkhairi.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sati daya da maganan babana ya koma dukku
don jin amsarsa, Inda ya tafi da kakana wato malam Aminu. mallam sirajo (baban
mamana) ya musu iso yasa aka shimfida musu tabarma a zaure, fura da nono aka
kawo musu hade da ruwa suka sha sukayi hamdala, sannan aka fara magana. Yayan
babana na aka kira yazo, koda aka koro masa bayani yace shi sam bai san zancen
ba, fada yakeyi sosai ta inda yake shiga ba tanan yake fitaba, wai sai da baki
suka zo sannan za'a kirashi, kuma sai da sirajo ya amince? To me zaice? Ai yarsa ce yayi abunda yaga dama. Don
anga danshi bashida abun hannu amma da mai kudi yazo shine xa'a bata? Karshe ma
cewa yayi bbu ruwansa akanta yayi tafiyarsa. Zuciyar fulani ta tashi na mallam
sirajo ya cewa mallam Aminu a yau za'a daura auren, karshen iko kenan. A ranar
aka daura auren a masallacin garin bayan an idar da sallahn azahar. Sai shigowa
da akayi da goro da cingam cikin gida yara na cewa an daura auren rahmatu da
mamuda. Da farko ta aza wasane sai da taga inna haule (kishiyar mamanta) na
watso mata kayanta waje tana cewa ta hada ta kulle yau zata tafi gidan mijinta.
Tana hawaye tana hada kayanta inna haule bata daina masifa ba da yake bakinta
daya da su yayan mallam sirajo da matarsa. Wasu na cewa bakin cikinsu ne ya
kashe maman rahmatun. Babanta ya mata nasiha ya miqa amanarta gurin kakana.
Tana kuka yana hawaye suka rabu. Basu dawo ba sai bayan isha. Kakata tana jiran
isowansu sai kawai taga har da amaryan aka taho. Bayan sun huta sunci abinci
mallam Amenu yake sanar da ita komai. Ta jinjina lamarin inda ta tausayawa
mamata. Dakin babana aka gyara musu inda ya siyo mata duk kayan daki da ake
sayawa amarya na wannan lokacin. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Hajia kulsum ta numfasa tace fatu ki tsaya
anan. Lokacin sallar la'asar yayi. Dakin hajia suka shiga anan ta nuna mata
yanda zatayi amfani da toilet din taa barta a ciki ta sauko kasa tana kiran
farouq yazo driver ya kaishi islamiyah time yayi. Bayan ta shigo daki ne ta
samu fatu har tayi alwala ta fito, sallaya ta miqa mata ta nuna alkiblah sannan
ta shiga toilet din don gabatar da alwala. Fatu sake baki tayi tana kallon
duniya tun a toilet din take kauyanci taba nan taba can da kyar ta yi alwalan
ta fito, a dakin ma sai da taga kamar hajia zata fito ne ta tada kabbara.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[12:26PM, 5/10/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sunyi sallah inda fatu taci gaba da
labarinta..<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">
Zaman lafiya akeyi tsakanin mamata da surkunanta, abu daya ya ke damun
mahaifiyata rashin haihuwa. Duk lokacin da goggo innani tazo sai ta samu bakar
magana ta yaba mata, nan ma kakata na mata fada. Ta shekara biyu ne ta shirya
zuwa ganin gida. Tana isa ta tarar babanta ba lafiya sosai sai dai a kwantar a
tayar, tayi kukan halin da yake ciki shi kuma yayi murnar ganinta, don tayi
kyau tayi kiba. Ta bawa kowa tsarabar sa bbu wanda ta manta, bayan kwana biu
tace a kaishi asibiti, mallam jauro (yayan babanta) yace ba za'a kaishi ba, ai rubutu
da maganin gargajiyan da ta raina shi ya kawo shi har yau, yayi ta mita. Satin
ta uku tana jinyarsa Allah ya amshi abunsa. Tayi kuka sosai bbu wanda bai
tausaya mata ba. Bayan sadakan arba'insa akace azo ayi rabiyan gado, aka raba
da yake ita mace ce bata tashi da komai ba sai budurwar akuya. Tun suna bata
abinci har rannan mallam jauro yace shi ya gaji da ciyar da ita, hala wani
mugun abun tayi acan mijin ya korota shine zata zo tace wai tazo ganin gida, ai
wata biun ya cika mijin baizo ba, tana kuka tana bashi hakuri amma ko a
jikinsa, hasalima inna haule da matarsa ce suke zugashi, a cewarsu zata cinyesu
in suna bata abinci, Akuyarta ta sayar take cin abinci. Ranar sai ga babana ya
zo inda ya tarar da rasuwan surikinsa, ya musu ta'aziyya yace zai dauki matarsa
su tafi. Budan bakin mallam jauro cewa yayi kar rahmatu ta sake zuwa garin don
wanda ya hada ya raba, (kuji rashin tunani da imani) in kuma tazo ta nemi inda
zata sauka badai gidansa ba. Mamata tayi kuka kamar ranta zai fita haka babana
ya jata suka tafi. Anan yake tambayanta yan'uwan mahaifiyarta. Tace fulani masu
yawo ne, sunzo dukku babanta mallam
sirajo ya ga mahaifiyar ta wacce ta taba
aure a cikin yan'uwansu amma zaman baiyi dadi ba, 'yarsu daya suka rabu da
mijin, aka daura musu aure, bayan wata 2 sauran kuma suka kara gaba. Daga nan
basu kara yowa ta dukku ba. Sun dawo gida ta samu muntari yayi amarya. Shekararsu 9 Allah bai basu haihuwa ba, inda
amarya asabe ta haifi 'yaya 4, goggo innani ta hada kai da asaben muntari suna
kuntata wa mamata kakata na tsawatar musu. Ana haka har ta samu cikina sunyi
murna sosai amma cikin yazo da laulayi ta wahala sosai inda tana haihuwata tace
ga garinku. Babana yayi kukan rashin matarsa mai hakuri da juriya ga sanin
dattako. Ran suna naci sunan kakata (mamar babana) wato Fatima inda ake ce mini
fatu. Na taso cikin kulawan mutum uku, kakannina da babana. Don yanzu kawu
muntari ya fara bin hudubar su goggo innani wai an fi sona akan yayansu. Na yi
primary anan kauyen mu. Inda duk garinmu bbu wanda ya kaini kokari, sannan na
shiga secondry ina jss 2 babana ya hadu da accident akan hanyarshi ta zuwa
kasuwanci. Bamu da labari sai gawarsa da aka kawo. Fadin irin tashin hankalin
da muka shiga ma bata lokaci ne. Nayi kuka har na rasa inda zan tsoma raina.
Anan nake tunanin kodai gaskiansu goggo asabe cewa dangin mu akwai mayu masu
cinye duk wanda suka rabe su. Kakata kuma tun daga lokacin ta fara kananun
rashin lafiya. Na cigaba da karatuna inda kakana ya jajirce sai na gama
secondry skul, duk sa'annina sunyi aure daga mai 'ya'ya biu sai mai uku. Na
kuma faranta masa nayi candy daga nan kuma samari suka min caaa! Don duk wanda
yazo gurina kakana kance mishi sai na gama karatu. A cikinsu kuwa harda dan
kawu muntari da dan goggo innani. Ni kuma wallahi duk cikinsu bbu wanda nake
so. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Rannan ina bacci da dare naji ana shafani,
bude idon da zanyi naga babangida dan kawu muntari ne. Zan yi ihu ya toshe
bakina, na takarkare na dankara mushi cizo sannan nayi ihu. Mutanen gida suka
fito ana haskawa. Fitowa nayi da gudu cikin gida ina haki, kaka yace "mene
fatu me ya sameki? Nace "babangida ne ya shiga dakina kuma yana
tabani" na fada ina matsar kwalla wanda har lokacin jikina bai daina rawa
ba. Inna asabe ta cabe "munafuka, sharri zaki yiwa yayan naki? Me zaiyi da
ke jiki kamar na aljanu" kaka ya dakatar da ita yace "ina babangidan?
Ya ce gani nan, "kaji abunda fatu
tace? Yace "wallahi karya take min, na fito zaga bayan gida ne naji
kamar nishin mutum a daki, nayi zaton batada lafiya ne da na haskata sai naga
mafarki takeyi tana wannan nishin. Shine na bugi hannunta tana tashi tasa ihu.
Salallamai goggo asabe tasa wai nayiwa danta sharri. Shi kuma ya fita zaure
inda dakinsu yake yana mita wai dama ba'a sonsu a gidan. Ni kuma sai rantse
rantse nake, kakanina da kawu muntari sun yarda don zai aikata. Kakatace ta
jawoni dakinta na karasa kwana anan. Daga ranan na dawo dakinta kwana. Sati da
faruwar lamarin kakata ta tashi da matsanancin ciwon kai da zazzabi ga jiri da
yake dibanta, anyi magani na gida har asibiti aka je inda suka ce jininta ne
yahau sosai.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[12:42PM, 5/10/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Inda sukace jininta ne ya hau sosai, bata
jima a asibitin ba ta koma ga mahaliccinta. Damuwa goma da ashirin. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Anan fatu ta fara hawaye, hajia kulsum
cikin tausayawa ta miqa mata tissue paper ta goge fuskarta sannan taci gaba.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na shaku da kakata sosai, a matsayin
mahaifiya na dauke ta. Bana jin rasuwar mahaifiyata kamar nata. Bayan rasuwan kakatace
zamana ya dawo gurin goggo asabe, nine wankinta dana 'yayanta da yake duk maza
ne sai autar ta zainab yar shekara 4. Shara, wanke wanke da girki ya zama daily
work dina, duka zagi da tsangwama kuma har na saba dasu. Duk abunda yake faruwa
kakana bai sani ba, da yake baya zaman gida yana can masallaci tare da tsofi
irinsa suna karatu. Idan ya ganni ina kuka sai yayita lallashina da inyi hakuri
komai zai wuce inyi ta musu addu'a, Tunaninshi mutuwar iyayena yake damuna, bai
san harda wahalan da nakesha yanxu bane. Kwatsam ranar wata friday bayan an
dawo daga sallahn juma'a goggo ta sameni da duka wai ban gama abincin rana da
wuri ba, na tsaya wasa, tace "shegiyar yarinya da ido kamar na mujiya ki
gama abincin sannan kixo kiyi wanki, kuma wallahi kika kai la'asar sai naci
uwarki. Ta aza mini rankwashi a kaina wanda ya sani sakin wani wahalallen qara,
"kina jina ina miki magana kina daga min kai kamar wata kadangaruwa don
ubanki" da sauri nace "goggo kiyi hakuri" na cigaba da sheshshekar
kuka, na tashi da sauri na fada kitchen. Kakana ne ya shigo da sallamarsa ta
amsa tana muzurai, Allah yasa baiji abunda tayiwa fatu ba, don batayi
tsammaninsa yanzu ba, baya dawowa a wannan lokacin. Ya shige dakinsa ya jima
sannan ya kwala min kira, ina sauri zanje ta yafuto ni, naje, murde min kunne
tayi tace "saura ki fada masa wani abu sai na ballaki, bulaliya
kawai" ta sake ni hade hankada ni har ina cin tuntube na shiga dakin
kakana. Cewa yayi inje inyi wanka zan rakashi unguwa. Na fito na fada mata ta
harareni tayi kitchen. Da sauri na watsa ruwa na fito, kaya nasa da hijabi na
cewa kakana na shirya muka fita. Maimakon naga mun shiga gari sai naga munyi
hanyar gona. A cikin gonarshi a karkashin wata bishiyar dorawa muka zauna. Yace
"fatu me asabe take miki a gida? Don yau naji wasu maganganu sabanin
hankalina" ban yi jayayyaba na fada mishi komai. Idonshi yayi jawur yace
" mahaifiyarki rahmatu amanace a gurina haka kema amanace, bazan bari ta
maida ke baiwa ba insha Allah zan nema miki mijin aure kwanan nan inda zaki sami
yancinki. Nayi farin ciki da haka sosai. Yayita bani baki hade da nasiha sai
yamma liss muka koma gida. Muna zuwa yace in shimfida mishi tabarma a kofar
dakinshi ya zauna. Daga ranar ya dawo wuni a gida yana waje tare da mutane, zai
aika a kirani sau goma shi ma zai shiga gida sau goma. Abun yana damun goggo
asabe sai dai bbu yanda ta iya. Na murmure na fara samun kwanciyan hankali,
kaka ya sama min miji dan ladanin garinmu. Hafizu yarone mai hankali da
nutsuwa, ga karatun addini baiyi boko ba amma yana da sana'arsa ta dinki, Yana
samu ba laifi. Kaka yace "ga zabina wato hafizu dan ladan, idan kin amince
inje in sami babansa muyi magana" gaskia bana jin sonshi a raina amma
hankali da nitsuwarshi sun kwanta min. Nace "kaka duk wanda ka zaba shine
zabina, fatana Allah yasa in samu zaman lafiya da kwanciyar hankali" kaka
yaji dadin furucina yace "Allah ya miki albarka uwargidana" daria
nayi nace "Ameen tsoho na" carbinsa ya dauka da niyyan min dukan wasa
nayi saurin shigewa gida ina daria shima yana daria. Daga kan da zaiyi ya hango
wata mota tana tahowa ta layin unguwanmu ga yara rudududu suna binta da gudu,
parking tayi a jikin katangar gidanmu. Samari biyu ne suka fito suka nufo
kakana da har yanzu yake zaune a kofar gida bai motsa ba. Kallo ya dawo kansu aka
manta da mota. Sun fi kama da turawa ko aljanu.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku a kullum<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman fa'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:27AM, 5/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">8</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sallama sukayi ya amsa, kana ya dubi yaran
da sukayi dandazo suna kallon samarin yace su tafi wasan su, kan kace me kowa
ya watse don basu da rashin kunya. daya daga cikin samarin yace<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">"Don Allah baba nan ne gidan mallam
mahmudu? Duk'ar da kai kaka yayi sannan yace "ehh" still wanda yayi
tambaya na farkon yace "gurinshi muka zo shi da matarshi, daga gombe
muke" kaka yayi dan jimm sannan yace "Allah ya musu rasuwa
dukansu" "sun rasu" saurayi na biyu ya fada cikin firgici,
sannan ya nemi guri ya tsuguna yana "innalillahi wa inna ilaihir rajiun.
Allah ya jikanku".<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Saurayi na farkon ya dubi kaka da tarin
damuwa a fuskarsa yace "Allah ya jikansu yasa sun huta" "Amin
Amin" kaka ya furta yana goge hawayen da ya zubo mishi ba shiri. Saurayi
na tsugunne yace "jameel mu tafi" ya miqe jikinshi a sanyaye ya nufi
mota. Kaka ne yace "zaku tafi baku sanar dani alakar ku ba" jameel
yace "wancan abokina nane, sunanshi sultan, matar mallam mamudu wato aunty
rahmatu qanwar mamanshi ce, uwarsu daya. "Allahu Akbar Alhamdulillah"
kaka ya fada cikin tsananin mamaki don baiyi tsammanin za'a ga dangin
mahaifiyar rahmatu ba cikin ruwan sanyi haka. "ai akwai rabo tsakaninsu
sun sami 'ya mace fatu, tana nan, ni mahaifin mahmudu ne" farinciki ne
kwance a fuskar kaka yana murmushi. Jameel ne ya kwalawa sultan kira ya fito daga
mota still jikinshi a sanyaye, jameel yace "akwai cousin dinka fatu, 'yar
aunty rahmatun ce" cikin doki yace "ina take? Yana kallon zauren
gidan. Kaka yace "tana ciki, amma in bazaku damu ba ina son magana daku. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tabarma kaka ya shimfida musu a zaure suka
zauna, shiga gida yayi ya sameni tsakar
gida ina karanta wani littafi, yace
"uwargida ki samin ruwa a kofi nayi baki" nace "to". Miqa
mishi kofin nayi ya karba ya wuce cikin zauren. Bayan sun qara gaisawa ne kaka
ya fara basu labarin mamata har zuwa kaina, bai rage komai ba harda wahalan da
nake sha gurin asabe idan taga kaka baya nan. Kaka ya qarasa magananshi da cewa
"idan baza ka damu ba kai sultanu ka auri qanwarka zata fi jin dadi cikin
ku, nasan dana fadi na mutu fatu bata da gata sai Allah, don wadannan ba riqeta
da gaskia zasuyi ba" kaka ya cigaba da maganarsa duk akan sultan ya aureni
ya taimaka min. Kan sultan ne yadau zafi yayi dana sanin nemo su, gaskia bazata
sabu ba. Shiru yayi kansa a qasa ko motsi mai kyau bayayi, ya bude baki zaiyi
magana kenan Jameel yayi caraf yace "hakan yayi kyau, Allah ya tabbatar da
alheri" Amin. Kallon mamaki sultan yake bin jameel dashi don ya wargaza
mishi plan, wata dabara ce tazo mishi in akayi sa'a zai fita.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Yace "mallam zamu koma gida sai daga
baya inshaAllah magabata su zo. Kaka yace "mutum bai san ranar mutuwanshi
ba, watakila bazan kai zuwa gobe ba har zuwa lokacin da zaka turo magabatanka,
kamar yadda na fada maka nine ke riqe da fatu, ayau nabar dunia zasu iya aura
mata wanda ransu yake so, inda zata cigaba da shan wahala. Nafi aminta dakai
shiyasa nake so ayau a daura muku aure, "Shikenan" abunda sultan ya
iya fadi kenan don tsohon ya cika kwarjini bazai iya mishi musu ba.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">An daura aurena da sultan a masallaci bayan
an idar da sallah. Inda kaka ya zame min waliyyi liman kuma waliyyin sultan.
(Tarihi ya maimaita kansa). Gida suka dawo inda kaka yace ya tafi dani, amma
sultan yace zai tafi wani course na wata biyu inya dawo zaizo ya daukeni, kaka
bai kawo komai ransa ba ya yarda. Shiga cikin gida yayi ya barsu a zaure inda
ya aika in kai musu abinci don ranar ni nayi girki. Har lokacin banida labari
don kawu muntari yayi tafiya, asabe kuma taje ganin gida. 'yayansu kuma ba zuwa
masallaci suke ba. Na fita na kai musu, durkusawa har kasa nayi na gaishesu mutum
daya ne ya amsa yana min murmushi, amma dayan ko dago kai baiyi ba. Mai
murmushin yace "me sunanki" nace "fatu" yace "masha
Allah abokina yayi sa'ar mata" fita nayi ina mamakin maganarsa, to a ina
hafizu ya sami abokai yan birni haka. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Shiga na keda wuya kaka ya kirani dakinsa,
da farko nasiha ya fara min kan ya bani labarin abunda ya faru. Babu abinda na
iyacewa illah hawaye da ya dinga bin fuskata, na rasa hawayen menene, ta wani
gurin ina farincikin samun dangin mamata, while ta wani gurin ina tausayawa
kaina don wanda aka aura min ko kallona bai yi ba. Na dade a dakin kaka sanna
ya fita dubo bakinshi ko sun gama cin abinci. Ya fita ya samu jameel yaci amma
sultan ko ruwa bai sha ba, jameel ne yake cewa wai sultan din azumi yakeyi. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Kaka ya musu iso cikin gida aka shimfida
musu tabarma ta bayan dakunan mu gurin akwai bishiiya gefenta kuma rumbun ajiye
abinci ne. Kaka ya wuce yana cewa bari ya kira fatun. Gefen su kadan na zauna
akan wani dutse na sunkuyar dakai ina wasa da yatsuna. Mijin nawa dai har yanzu
kansa na kasa bazaka game yanayin da yake ciki ba. Jameel ne ya fara magana.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:28AM, 5/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">9</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Jameel ne ya fara magana "Amaryanmu kina
lafiya" nace "lafiya kalau" ya kara cewa "sai kika ji an
daura aure babu wani taro babu al'adu irinsu zance, bayarwa, kayan aure da
sauransu. "Uhmm" na iya cewa. "Komai da kika gani muqaddari ne
daga Allah, wannan aure naku insha Allah baza kuyi dana sani ba. Ya cigaba da
maganan shi inda yake nuna mana mu riqe junan mu cikin amana duk da ba auren
soyayya bane, ya karasa magananshi cikin nasiha. Duk abunda yake cewa sultan
bai ce uffan ba, don wayarsa ya dauka yana dannawa. Mikewa yayi sannan yace "bari
in barku kuyi magana, kar in takuraku da yawa" ya fada cikin tsokana. Mun
fi minti biyar b wanda yayi magana can yace "kinyi makaranta? Nace
"ehh" "ina kika tsaya" "secondry" yace
"shekarunki nawa? Nace "17" sai lokacin ya dago kai ya kalleni 4
d first time nayi saurin sunkuyar da kaina. Can ya kara cewa "kin taba
shiga birni" nace "Aa'aa" yace cikin bata rai "kin min
yarinta da yawa, kuma karatunki baiyi zurfi ba, bana jin zan iya rayuwa da
irinki" dai dai nan jameel ya dawo yace "times up, kar muyi yamma a
hanya" hope kun daidata? Ya fada yana murmushi. Babu wanda ya kula shi don
ni ina kokarin mayar da hawayen da yake son zubo min ne, jameel ne yace in
matso kusa da sultan zai daukemu hoto. Shiru nayi sai da ya kara maimaitawa na
taso na tsaya nesa dashi, turo sultan yayi gurina wanda yake aika masa harara
ta ko'ina, baya yayi yace mu dago fuskokin mu, still kowa kansa na qasa, yace
to bari in kira kaka, may be zaku fi jin
magiyarsa. Saurin dago da kanmu mukayi yace "smile" sannan ya
daukemu a hoto. Abun mamaki yana daukan hoton wani abu ya fito daga cikin
camera, ya kara daukan mu abun ya qara fitowa. Miqa min na farkon yayi na karba
ban duba ba. Sultan har ya fita waje, ciro kati yayi daga aljihunshi ya bani,
yace "wannan shine address na gidansu sultan, abokina yana da wuyar
sha'ani amma in kika yi hakuri komai zaiyi karshe, ki ajiye address din don
bamusan gaba me zata haifar ba" ya karashe maganarsa cikin tausayawa. Nace
"Nagode Allah ya kiyaye hanya" shima fitan yayi inda ya iske kaka da
sultan suna hira kamar bashi ne yake bata rai dazu ba. Tafiya sukayi kaka ya
shigo cikin gida yana mai farincikin fatu tayi sa'ar miji. Ni kuma tun tafiyan
jameel na nade tabarman na shige dakina ina kuka mai tsuma zuciya, daa kaka
yasan wa ya aura min da bazaiyi farin ciki ba. Kiran da kaka yake min yasa nayi
saurin goge fuskata na fita ina murmushi yace in sameshi a dakinsa. A dakinsa
na samu guri na zauna ya miqo min kudi yace "sadakin ki ne dubu
ashirin" nace ya dauka ni bana so, yace ai hakkina ne maza in karba. Na
karba na wuce dakina na cigaba da kukana har bacci ya daukeni. Bugun kafa na
naji anayi na tashi ya firgice goggo asabe na gani tsaye a kaina fuskar nan a
tamke, tace "wani jita-jita nake ji a gari wai an daura miki aure hka ne?
Nace "ehh" nan ta fara masifa ai dama dangin mu haka suke sai sunga
mai kudi suke aura, ga babangida yana sona amma kaka ya hana shi. Allah yasa
mijin nawa ma dan yankan kai ne, kallonta nayi ido cikin ido nace "ba
kudin shi muka bi ba, sultan dan'uwana ne, mahaifiyarsa addar mamata ce"
cikin mamaki tace 'eeeyeee' nace
"kwarai" fita tayi daga dakin tana jin bakin cikin auren, don
yadda aka fada musu mijin nawa dan birni ne kuma ga kudi akace da mota irin ta
sarkin Kumo yazo. Sadakina na boye don nasan ko ita ki 'yayanta wani zai biyo
dare. An koma baya don goggo asabe tana ganin kaka ya fita zata fara cin
zalina, girki kuma da shara wanke wanke nice keyi da kaka yayi maganan a rage
min koda daya ne cewa tayi horar dani
takeyi, gidan wani zanje don haka ya kamata in saba da aiki, kaka kuwa ya yarda
da magananta. Bayan wata da daurin aure
na wani mutum yazo da envelope ya bani yace aikoshi akayi daga gombe. Na aza
wasika ce amma sai naga kudi ne 30k. Kakana na kaiwa yayi godia yana cewa sultan
bai mance dani ba tunda har yana kokarin sauke wasu hakkina. Bayan wata daya
muna tsammaninshi sai muka ga dan aikan rannan. Yace sultan yace a fada mana
zai qara yin wata uku. Kowanne karshen wata sai dan aiken yazo da envelope
kudine a ciki wataran 50k watarana 30k. Koyaushe aka kawo zanyi tsammanin akwai
wasiqar sultan a ciki amma babu. Har wata 3 ya wuce babu labarinsa daga nan su
goggo asabe suka fara habaici "ai nasan za'a rina, hala kakaba mishi ita
akayi, yoo dama me zaiyi da kucakar yarinyar nan; shi dan birni. A haka zakiyi
ta zama har ki tsufe, dama kudi kuke so to ai gashi ana turo muku" idan ta
fara maganganun nan nakan shiga daki inyi ta kuka ina kallon hoton da jameel ya
dauke mu.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:09AM, 5/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Idan na gaji inyi alwala inyi sallah in kai
kukana gurin Allah. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sati daya daya wuce na cika shekara daya da
aure, a cikin shekaran kuma dan aika yana kan zuwa kowanne month. Idan muka
tambayeshi labarin sultan sai yace bai dawo bane. Hankalin kaka ya fara tashi
ya fara dana sanin daura auren, akwai lokacin da ya kirani ya ke cemin ko
zamuje kotu a raba auren? Nace mishi a'a, don nasan gwanda zamana da igiyar
sultan akaina akan in zama bazawara hankalin kaka zai fi tashi. A ranar da zan
cika shekara da aure muke tsammanin zuwan dan aika, a ranar na shirya plan dina
don sanin matsayina. Yawanci bayan azahar dan aika yake kawo kudi, kaka na samu
a kofar gida karfe 12:30 nace zan shiga jeji debo ganyen lalle, yace in aika yara
mana, nace ina son zuwa da kaina ne, bai kawo komai a ransa ba ya mini izini.
Already na gama shiri na fito, hanya kawai na yanka na shiga jeji inda nan ne
hanyar shigowa cikin gari. Sai da na debo ganyen lallen na fito bakin hanya na
tsaya a gindin bishiya ina jiran dan aika.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Nafi minti 30 na hangoshi yana tahowa kamar
kullum a kan machine dinshi. Fitowa nayi ina tafiya nayi kamar ban ganshi ba,
yazo dab dani na juya ya ganni ya ce ahh fatu me kikeyi anan? Yana kokarin
tsayar da machine din, nace laa nazo tsinkar ganyen lalle ne yanxuma gida na
nufa. Yace in hau ya isar dani, nace a'a nagode. Yace to ga aikan tunda na hadu
dake a hanya, ki gaishe min da mallam Ameenu. Na karba nayi godia ya juya ya
koma. Sai dana tabbatar yayi nisa sannan na bude envelope din, yau ma kamar
kullum kudine babu wasiqa. Na fito da yar takarda daga cikin ledan da tun
fitowana daga gida yana cikin hijabi na, hade da dan kunu a farar leda takardan
na tura cikin envelope din na shapa kunu na liqe kamar ba'a budeba nayi hanyar
gida ina mai farin cikin hukuncin dana yanke. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Jama'a menene fatu ta rubuta? 😳😳😳😳<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Ina mai bawa masoya hakuri na rashin jina
kwana biyu, phone dina ne ya samu matsala. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Luv u ol<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku a kullum <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[1:33PM, 5/19/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Dawowa na gida na iske kaka na yana
masallaci, don haka kai tsaye dakina na fada na ajiye kayan na fito nayi alwala
nayi sallah. Ina idar wa naji kakana ya dawo, goggo asabe ta kirani in kai
mishi abinci, naje na karba, har zan juya ta kirani na jiyo, "amm fatu yau
ba'a kawo miki saqo bane, wallahi rance nake so ki bani na dubu uku,
masifaffiyar goggon kin nan innani na ara a gurinta, don tsiya jiya har da aiko
sadiqa tayi tamin rashin mutunci" nan ta fara matsar kwalla, kar ki manta
hajia duk randa aka aiko kudi rabashi akeyi duk abunda aka bani ita ke amshe wa
da wayo, wani tace zata biya bashi wani kuma tace zata karbo min maganin bakin
mutane, Wani kashin na abincin gida, don wani abincin da muke ci ba'a cinsa a
gidan maigari, kinga kamar taliya da dan waken fulawa, wallahi wataran harda
macaro muke ci (inji jawaheer😂😂).
Hajia tace "Macaroni kike nufi? Fatu tace "ehh, sauran a ajiye saboda
bukatun yau da kullum. Nace "an kawo in kaka ya bani zan kawo miki"
na fita a zuciyana ina cewa anji kanku. Dakina na fara bi na dauko envelope din
na wuce dakin kaka. A daki na iske shi yana kishingide, na masa sallama ya
amsa, ajiye abincin na miqa mishi saqon nace a hanya na hadu dashi ya bani. Ya
karba jikinshi a sanyaye yace zai kirani anjima. Ina fita naga goggo asabe a
kofar dakinta tana jirana, sai da na isa tace ina kudin? Nace " sai yaci
abinci sannan zai bani. Shiga dakinta tayi bata kulani ba ni kuma nayi shigewata
daki ina jiran kiran kaka don karanta wasiqa. Bayan Minti sha biyar lamido dan
goggo asabe ya zo ya kirani hijabi nasa na fita. Shiga nayi na samu guri na
zauna nace "kaka gani" yace "takarda na gani a cikin kudin Allah
yasa ba abunda nake zato bane, ya fada yana mai girgixa kai cikin damuwa. Nace
"ba komai kaka Allah ya zaba mana mafi alkairi. Yace "ameen"
hade da mikomin paper. "Hajia kinsan abunda na rubuta? Hajia tace
"a'aa" fatu tacigaba "rubuta ban hakuri nayi na jimawan da
sultan yayi bai zo ba, hakan ya samu asali ne ga riqeshin da akayi a kasar
wajen, kuma kaka ya bari inzo gombe gidansu yana so yayi wa mamarsa
suprise"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:17PM, 5/19/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tunda na fara kaka murmushi yakeyi cikin
jindadi, har bansan lokacin da hawaye ya zubo min ba, na share ba tareda ya
gani ba. Sai dana gama yace " fatu Allah ya amsa addu'a na, kullum burina
mijinki yazo ya dauke ki, ayau Allah ya nuna min ranar" kwalla taff a idon
kaka na farinciki. Hajia nayi dana sanin rubuta wannan wasiqar don bawai inason
zuwa gurin sultan don ya karbe ni a matsayin matarsa bane, a'a don ya sauwaqe
min ne nima in samu dai dai ni in aura. Kuma hakan zaisa kaka ya samu kwanciyar
hankali. To amma tsananin farincikin dana hango shimfide fuskarsa sai
tausayinsa ya kamani, ban kyauta masa ba. Kaka yace in shirya gobe in tafi.
Kuka na fara Nace a'a sai shi sultan din yazo, zanyi ta zama da igiyarsa a
kaina har ranar da Allah ya kawo shi. Ban taba yiwa kaka musu ba sai ranar. Bai
ce min komai ba har na tashi na tafi dakina na cigaba da kukana, ina tausayin
kaina da kaka. Da kawu muntari ya dawo aka fada masa abunda mijina ya rubuta
shima ya bada goyon baya in tafi, goggo asabe kuwa hankalinta ne ya tashi don
bata son taga abu mai kyau ya rabe ni. Ana gobe zan taho na fara shirin tafiya gombe don inje ayita ta
qare, na kasance koyaushe ina tunani da addu'ar Allah yasa zuwana ya kasance
alkhairi. Hajia har abinci nake kasa ci, ace an daura mini aure yau shekara
amma mijin bai ko waiwayeni ba. Abunda kaka ya fada min ne ya girgiza ni, wai
da kawu muntari zanyi tafiyan!!! Tirkashi😳😳<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Nace masa ai a wasiqar sultan yace inzo ni
daya, na nuna masa tunda nayi karatun boko ai bazan bata ba koda a kano ne😜,
Kaka ya amince. Da dare kasa cin abinci nayi don ina da tabbacin in naje sultan
zai sake ni kamar yadda zan bukata. Da kyar kaka yasa na sha fura da daddare a
dakinsa, mun kusan kai karfe goma yana min nasiha gameda inda zan koma wato
gidan mijina, jinshi kawai nake yi ina mai tausaya mana. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tun da asuba na gama shiri kaka yana dawowa
daga masallaci naje na gaishe shi, ya miqo min 15k wai in riqe zai min amfani a
can din. 5 din saman na dauka nace zai ishe ni, ya qara min nasiha ya bani
addu'o'I. A lokacin gari ya fara haske, machine din abokin baba ne mukaji yana
diri a kofar gida. Har daki na sami goggo asabe na Mata sallama, duk 'yan gida
aka fito domin ganin tafiyana. Ban dauki komai ba sai 'yar jakana na skull da
kudin sadakina 20k sai kayana kala 3 don nasan ba jimawa zanyi ba. Kudin kuma
bashi kayanshi zanyi. Na haye machine din ina hawaye haka muka kama hanya suna
daga min hannu. 6:22 muka iso kumo, direct tasha muka isa ya sakani a motar
gombe, shi ya biyamin kudin motan ma, yayi tafiyarsa don anan kumon yake aiki.
Bakwai saura motar mu ta tashi mune bamu shigo garin gombe ba sai 7:30. Anan na
sauka na sayi abinci, fitowana kuwa tsautsayi ya afka dani. Wannan shine
takaitaccen tarihina. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Shiru sukayi kowa da abunda yake sakawa a
ransa, farouq ne ya dawo yana mummy oyoyo, hajia ta shafa kanshi tace "Ka
dawo" yace "ehh, yauwa mummy kika ce dama baza ta tafi ba, to yanzu
in mata questions din? Hajia tace "gata a gabanka ai" zuwa gurin fatu
yayi yace "dama tambaya daya ya rage, ina ne gidanku? Kai tsaye fatu tace
"a kauyen kumo, ka taba zuwa kumo? Yace "aa'aa" tace "kana
kama min da wani sunan shi jameel" yayi caraf yace " ya jameel yayi
aure rannan ya tafi da matarsa south africa wai yana aiki, amma naji dady na
cewa ya kusa dawowa" kafin ya qara bude baki hajia ta katse shi tace
"aje a canja kaya ayi shirin zuwa sallah magrib" ba musu ya haura
sama da gudu. Hajia ta juyo ta kalli fatu da kanta na qasa tace " jameel
dana ne yana da kanne 4, mahmud ne mai binsa sai khadija da Aisha da autana umar
farouq. Mahmud yana karatu a cyprus lawyer ne, insha Allah nan da 4 months zai
kammala ya dawo gida. Khadija da Aisha sunyi aure inda khadija ke Abuja Aisha
ke kano. Jameel abokin sultan ne tun suna yara, daa ba'a unguwan nan muke ba,
muna jeka da fari ne, Allah cikin ikonsa ya budawa mahaifansu inda suka sayi
fili anan GRA, In kin lura yanayin ginin gidajen iri daya ne amma kowanne da
design dinshi. Skul daya sukayi tun daga primary har sec, inda a university
kowa da zabinsa, don sultan fita waje yayi ya karanci Business ad, while jameel
yana gwags karantan likita. Alhamdulillah sun kammala with flying colors.
8months da suka wuce jameel yayi aure ya tafi da matarsa south africa akan
karatunsa. Mahaifiyar sultan qawatace sosai, hakama dads dinsu suke abokai. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Kiran sallah da aka fara ya tsayar da
hajia, sai da aka idar tacewa fatu ta isa daki tayi sallah, ita kuma hajia ta
nufi kitchen don duba me aka girka.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> Nima
na fita daga gidan don inje in daura nawa sanwar kar oga ya dawo babu abinci,
kunsan bature yace "Hungry man is an Angry man"🏃🏽🏃🏽🏃🏽🏃🏽🏃🏽
<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku a kullum<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[12:32PM, 5/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sun idar da sallah suka ci abinci, dija mai
aiki ta tattare gurin fatu ta taya ta suka kai kitchen ta fito palour, farouq
sai zuba surutu yakeyi fatu tana biye mishi har aka kira sallan isha ya tafi
mosque suma suka tashi don yin sallah. Bayan sun idar da sallah ne suka dawo
palour hajia ke tambayar fatu "sultan din bai baku number wayarshi ba?
Fatu tace "hajia ai address din ma ya jameel ne ya bani bashi ba"
kuma ni ban taba yin waya bama, to da waye zanyi? Ta karasa tana daria.
"Babangida da kawu muntari ne kadai masu waya a gidanmu sai goggo asabe da
ta taba siya tayi wata hudu ba'a kirata ba shine ta sayar😂😂.
Murmushi hajia tayi tace "to yanxu fatu ya za'ayi ki tunkari sultan har
kice ya sauwaqe miki? Fatu tayi dan jimm sannan tace "hajia tunda innar
tawa qawarki ce sai ki fada mata ita tayi mishi magana" hajia tace
"ke bakya dokin ganin innar taki ce"? Fatu tace "hajia inaga
abunda sultan ya mini itama shi zata min, mahaifiyata suka zo nema bani ba,
kinga ko baza su damu dani ba, nima kuma bazan tura kaina cikinsu ba"
Haajia tace "fatu mahaifiyar sultan zata so ki sosai, don tun muna jeka da
fari ta je dukku gurin mamanta wato kakarki, sunje aka ce musu ta rasu, 'yarta
rahmatu kuma tayi aure a wani gari. Hajia sadiya (maman sultan) ba yanda ba
tayi su fada mata sunan garin ba amma suka ce sun manta, zuwanta na biyu bana
mantawa bamu dade da dawowa nan gidan ba ta qara zuwa, wannan karon Cewa sukayi karta qara zuwa gurinsu, don basu
hada dangi da ita ba, wacce suka hadan ma sun yafe ta. Duk maganganun nan daga
bakin yayan kakan ki yake fitowa, wai sunan shi mal jauro, ina mamakin yanda
akayi sultan ya nemo ku". Fatu tayi shiru tana tunanin ya auntyn ta hajia
sadiya zata karbeta, taji dadin jin ance tana son su. Hajia ta cigaba da cewa
"ni a nawa shawaran ki zauna anan har lokacin da kike tunanin zaki iya
samunshi ki masa magana, batun hajia sadiya kuma baza ta taba yarda sultan ya
sake ki ba, don haka ki zauna anan ki fara makaranta har zuwa lokacin da naga
ya dace ki tunkareshi. Fatu tayi shiru tana tunanin maganan hajia, hala in taje
gurinshi yanzu yace bazai saketa ba ya korata kauye, amma in ta zama 'YAR BIRNI
bazai wulakanta ta ba zai bata abunda take nema cikin salama tunda yasan tana
da ilimi.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[12:43PM, 5/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US">
<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Da wannan tunanin tace "hajia na
amince in har zaki yarda ki dauke ni, wanke wanke da shara ko girki zan dinga
yi? Hajia tace "ban gane ba" fatu tace "kince zan zauna anan
inyi karatu to kuma banida kudi kuma ai bazan zauna hakanan ba tareda ina muku
aiki ba" murmushi hajia tayi sannan tace "ni babu abunda zaki min,
kudin makaranta kuma nice zan biya, dake dasu jameel duk daya na dauke ku"
fatu harda hawayen farinciki tana kwararawa hajia kulsum addu'a sai da ta
dakatar da ita. Fatu tace "hajia to kakana fa? Don yace in sanar dasu in
na isa" hajia tace "karki damu nasan abunyi" farouq ne ya shigo
da sallaman shi ya nemi guri kusa da fatu ya zauna hajia tace " farouq a
ina ka zauna tun tafiyanka sallah isha? Yanzu gashi har 8:42" yace
"mummy gurin baba mai gadi na tsaya, yana bani labarin sojoji ne, kinsan
ina son zama soja" hajia tace "kai kam da son soja, shima mal amadu
da yake biye maka kana sa shi surutu" daria sukayi dukansu, farouq yaje ya
dauko home work dinshi ya kaiwa fatu wai ta tayashi. Yanda take nuna mai komai
dalla dallah yasa hajia cikin mamaki, don ta english take masa bayanin wanda in
bai gane ba sai ta masa da hausa, sun gama ya dauki bag dinshi ya musu sai da
safe ya wuce dakinshi. Hajia ta dubi fatu wacce tafiyan farouq bai mata dadi
ba, don har ta fara takura kana tace "fatu kince a kauyenku kikayi
primary, to sec fa? Fatu tace " a garin kumo nayi scndry skul dina, abokin
babana ne wanda ya kawo ni tasha yake zuwa da sassafe ya kaini, in an tashi ni
kuma in hau acaba ya mayar dani kauye, anan na fara tun daga jss1 har nayi waec
da neco, na samu kyautuka da dama ranar speech and prize giving day din mu.
After months result ya fito na samu both waec and neco, sai dai banyi jamb a
shekarar ba. Bayan aure na ne nayi jamb ina tunanin in sultan ya yarda sai inyi
university dina. To da yake bai zo ba sai abun ya mulmulce" hajia tace
"kinci jamb dinne? Fatu tace "eeh naci, ina da 220 points" hajia
tace "ahh lalle kinyi kokari, last year ne kikayi ko this year? Fatu tace
"nayi last year kuma nayi this year" hajia tace "ashe bazamu sha
wahalan sama miki admission ba, yanzu dare yayi muje ki kwanta ki huta, gobe in
Allah ya kaimu zamu qarasa magana" kashe komai na wuta sukayi suka haura
sama hajia ta kaita wani daki kusa da na farouq, daki ne madaidaici da toilet
dinshi a ciki, komai na dakin pink nd white ne, gadon Mai dan girma, sai
wardrobe dinshi da mirrow duka pink, can gefe kuma gurin karatu ne desk da
chair white, labulayen pink nd white sai paint na dakin sky blue mai oily sai
sheqi yakeyi. Sana'ar dai fatu ta sake yi wato sake baki, hajia tace "nan
dakin aisha ne yanzu kuma ya dawo naki" fatu tace "hajia duka wannan,
nikam ko da mai aikin ki zan dinga kwana" hajia tace "a'a anan zaki
zauna na fada miki bana son kina banbanta kanki dasu farouq, duk daya kuke, ki
saki jikinki tamkar nan ne gidanku, abunda nake bukata daga gareki kenan in har
zan samu" fatu tayi saurin riqo hannun hajia tace "kinfi karfin
bukatar abu a gurina sai dai ki bani umarni, insha Allah zaki sameni mai miki
biyayya, wallahi ban taba tsammanin akwai masu kudi da son jama'a irinku ba
hajia. Nagode Allah ya biyaki da Aljannah ya kuma raya miki 'yayanki"
"Ameen Ameen" hajia ta fada sannan ta mata sai da safe ta wuce
dakinta, rufe kofar fatu tayi ta ajiye jakanta a gado, ta hau kan gadon tana
daddannawa, can ta miqe ta shiga toilet din sai da ta gama qare masa kallo tana
daria sannan ta fito ta cire hijabinta ta bude jakanta ta dauko soso da sabulu
hade da brush da tootpaste ta ajiye a gefe. Cire kayanta tayi ta dauki Wani
extra zani da alama na wankanta ne tasa ta shiga wanka, bata dade ba ta fito ta
sane jikinta ta shafa mai, tazo daukan wani kaya ne taga wasu night wears riga
da wando orange colour masu laushi akan gadon, taga kuma an saka bedsheet an
lailaye gadon wahoho fatu tace "Alhamdulillah" tasa kayan ta jera
kayanta kala uku a cikin wadrobe din jakan ma tasa shi a ciki wanda akwai
kudinta a ciki. Ta kashe wuta ta haye kan gadon tayi addua ta rufe idonta tana
tunani har bacci ya dauketa.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku a kullum <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:15PM, 5/27/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Bangaren hajia kuwa wautan fatu take gani,
ace miji kamar sultan kaso rabuwa dashi? Ita dai bazata bari hakan ta faru ba
shiyasa take son fatun tayi karatu ta kuma waye yanda shi sultan bazai so koda
kuda ya gifta tsakaninsu ba. Duk da sultan bai kyauta ba amma ba taga laifin
shi sosai ba don rayuwar turai yayi, ya saba ganin mata masu class da wayewa
zai so matar sa ta kasance kamar su. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Don haka hajia tayiwa kanta alkawarin kai
fatu gidan sultan cikin so da kaunar junansu. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tun asuba fatu ta tashi tayi sallah ta dan
jima tana addu'o'inta sannan ta shafa. Ta kusan minti 30 a zaune tana tunanin
ko ta fita ne ta taya mutanen gidan aiki ko ta zauna ne oho. A haka har gari ya
fara haske Knocking kofarta taji anayi da sauri ta tashi ta bude. Hajia ta gani
ta durkusa har kasa ta gaisheta, hajia ta amsa tana murmushi tace "ya
kwanan baqunta" fatu tace "Alhamdulillah" hajia ta miqo mata
wata doguwar riga tace "idan kinyi wanka ki saka, sai ki sauqo kasa
breakfast ni zan je in shirya farouq zuwa skul" fatu ta karba tayi godia
ta ajiye kan gado Sannan tayi hanyar fita daga dakin hajia tace "ina zaki
je" fatu tace "zanje in shirya farouq dinne" bata jira me hajia
zata ce ba ta fita ta shiga dakin farouq don kusa da nata yake, tattausan
murmushi hajia tayi sannan itama ta fice zuwa dakinta. Fatu tana shiga dakin ta
samu shi baccinshi ma yakeyi, a hankali da wayo ta tashe shi ya shiga wanka
bayan ta hada mishi ruwan wankan. Da ya fito ta tsane mishi jikinshi ta shafa
mishi mai hade da sanya mishi uniform dinshi, gurin sa neck tie ne suka kai
ruwa rana, don daga ita har farouq din babu wanda ya iya. Daria yake ta mata
yace "mummy ta iya, muje ta saka min" daukan skul bag dinshi tayi
suka sauqo zuwa palour anan suka sami hajia tana rufe lunch box din farouq.
Tace "iyee har kun gama ne?" Cikin daria farouq yake bata labarin
yanda fatu ta rinqa kokawa da neck tie wai bata iya ba, hajia ta dara kadan ta
kirashi tana saka masa duk fatu tana gani. Dinning hajia ta kaishi aka hada
mishi tea ga hadedden indomie dinshi a gefe, cikin nitsuwa ya cinye ba tareda
ya bata kayansa ba, kana ya tashi yace "mum yau ma kece zaki kaini
skul" hajia tace "noo, driver zai kaika, jiya ma don yayi asubancin
tafiya garinsu ne" Farouq ya hade rai hajia na lallashinshi don kar ya
makara. Fatu ce ta jawo shi jikinta ta rada masa magana a kunne, duk iya gulma na banji me ta fada masa ba,
kawai naga suna daria ta riqo hannunshi tace "muje in raka ka mota"
hajia da ta tsaya kallonsu tace "ohh wariya za'a min kenan? Farouq yayi
saurin hugging dinta tace "a'a mummy kema zan fada miki in na dawo,
bye" har mota fatu ta rakashi ya shiga suna dagawa juna hannu, baba
maigadi ne ya bude gate suka fita, yana kokarin rufe gate din fatu ta kalleshi
da kyau. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">O M G 😳 mai kawo mata aika ne. Da
gudu ta koma palour shi bai ma ganta ba.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku a kullum<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fai'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:26AM, 5/28/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A guje fatu ta shigo palour, hajia dake
qoqarin haurawa sama ta dakata tace "lafiya fatu? Fatu tace "mummy
wallahi mal usman na gani, mai kawo min saqo din nan, yana tura gate"
hajia tace "mal usman ne yake kai miki saqo dama? No wonder kowanne month
yakance zaije kumo kai saqo, kuma ban taba tambayarshi ba, da yake shi dan
garin kumon ne" fatu dai bata ce komai ba sai zare eyes da take yi. Hajia
tace "karki damu, nasan abun yi, kije ki shirya ki sauqo muyi
breakfast" fatu tace "to" kana ta miqe ta haura zuwa dakinta. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Hajia kuma hijabinta ta saka ta nufi bakin
gate gurin mal usman. Yana ganinta ya taso da sauri har yana duqawa ya gaishe
ta, ta amsa masa cikin fara'a kana tace "mal usman saqo da kake kaiwa kumo
gurin waye kake kaiwa" mal usman yace "gurin wata yarinya da kakanta
ne, shekara kenan ina kaiwa, inaga na taimako ne ko kuma yar uwarsu yallabai
sultanun ne" harda abunda ba'a tambayeshi ba ya fada. Hajia ta nisa tace
"Yarinyar tana nan gidana amma shi sultan bai sani ba, idan ya baka saqon
next month ka kai can garin modibbon, idan kakan ya tambayeka labarin fatu kace
tana nan lafiya kalau, kar ka nuna masa ba'a gidan su sultan din take ba, zaka
min wannan alfarmar? Kai tsaye mal usman yace "hajia duk yanda kika ce
haka za'ayi" hajia tace "nagode kuma shima sultan din kar ka nuna
mishi komai" hajia ta fada sannan ta shige cikin gida. Shi kuma ya koma
bakin aikinsa don ta daure masa kai, amma dai yasan duk rintsi hajia baza ta
taba cutan wani ba, kuma in ba kwanan nan ba basu san cewa Iyalai biyun ba
dangin juna bane.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sake curtain din window fatu tayi bayan
taga hajia ta koma palour tayi ajiyar zuciya ta fada toilet tana mai addu'an
Allah yasa mal usman ya bada hadin kai.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:44AM, 5/28/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Wankanta ta tsala ta fito ta shafa mai da
dan pop powder dinta na 100, sai kwallinta data sawa idonta, ta lakuti vaseline
ta shafawa lips dinta. Doguwar rigan da hajia ta bata ta saka black ne mai adon
sky blue a gaban rigan, kana ta dauki gyalensa shima sky blue ta yane kanta
Wahoho jama'a sai yau na qarewa fatu kallo. Fara ce amma ba tass ba, tana da
matsakaicin tsayi, figure 8 ce don rigan anyi shaping dinta, idanunta ba manya
bane kuma ba kanana ba, tana da dogon hanci ba laifi, bakinta dan tsurut kamar
bakin bottle, tana da gashin gira dai dai, fuskarta mai yawan murmushi. Itama
kallon kanta ta tsaya yi a jikin mirrow tana smilling, sannan ta nufi kofa ta
fita. Tun daga kan steps hajia ta ganta a ranta tace "masha Allah"
don sultan yayi sa'ar mata, ga kyau ga ilimi both arabi da boko ga nutsuwa ga
kuma ladabi da biyayya. Fatu ta iso ta dan duqa tace "mummy sannu da
aiki" har ranta hajia taji dadin yanda fatu ta saki jikinta tana kiranta
da mummy. Dinning suka nufa fatu tayi serving dinsu indomie da dankali da kwai
sai tea. Suna ci suna hira duk akan yanda skul din fatu zai kasance. Bayan sun
gama ne hajia tace zata yi bacci kadan kana ta haura sama. Fatu ta tattare
gurin ta kai kitchen ta samu dija na wanke wanke,;ta tayata suka qarisa cikin
tadi da raha, suka gyara kitchen din. Anan ne dija take tambayar fatu
dangantakarta da hajia fatu tace "zan fada miki amma ba yanzu ba"
dija tayi daria tace "to Allah ya kaimu ranar" fatu tace ameen ta
haura sama itama ko zata runtsa.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku a kullum<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[12:16PM, 5/28/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">8</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Shigan fatu daki ta kwanta a gado tana
tunanin rayuwarta, ita kanta mamakin yanda ta sake a gidan takeyi, amma da ta
tuna da yanda hajia ta karramata sai take ganin ko me hajia tace tayi zatayi in
dai bai kauce shari'a ba. Duba agogo
tayi 8:34, kakanta ne ya fado mata a rai, yanzu haka yana can yana kewanta,
Allah sarki, hawaye ne ya fara sintiri a beautifull face dinta idonta a rufe, a
haka har bacci ya dauketa.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">11:00 ta farka, bandaki ta shiga ta kama ruwa
sannan ta sauqo palour, babu kowa sai kamshin girki da yake tashi a kitchen, ta
shiga kitchen din ta samu dija tana girka abincin rana, fatu ta mata sannu da
aiki ta kama sunayi tare. Fatu tace "maman isya (dija) mummy bata fito
bane? Dija tace "ta fito dazu ta fadi abinda za'a girka" Fried rice
wanda yaji hanta da kayan lambu sukayi sai coslow, fatu tace "akwai zobo
ne?" Dija ta kawo mata, tace "mman isya a ina zan samu bawon abarba?
Dija tace "sai dai a aika habu driver ya karbo, akwai masu sayar da fruits
a bakin hanya" dija ta fita ta bawa habu driver aika, minti goma ya dawo
da bawon abarba mai yawa, fatu ta karba ta daura akan wuta tasa ginger,
kanunfari da zobon, suka ci gaba da hiransu suna gyara inda suka bata har zobon
yayi, ta sauke dija ta tace shi a wani bokitin roba ya dan huce suka sa sugar
sukayi blending cucumber suka saka. Dija ne ta fara tabawa tace "zuwaiiitt
kenan, hajia zata ji dadin wannan zobo dama bata cika son na kwalin nan
ba" fatu tayi murmushi itama ta taba tabbas yayi dadi don bata taba yi ba,
time din da take secondary tayi food and nutrition to anan ta dan iya wasu
girke girken sai dai ba kowanne ta gwada saboda yanayin gidansu. Freezer suka
kai don yayi sanyi da wuri, barin dija tayi a kitchen Din ta fito palour, hakan
yayi dai dai da shigowan farouq 12:40 da sauri ta rungumeshi tana masa oyoyo,
peck ya mata a kumatu tayi murmushi itama ta masa duk suka sa daria, wa yaga
FATU A BIRNI har an fara wayewa😜. Duk abunda sukeyi hajia na kallonsu
tana jindadin shakuwarsu na kwana 1. Da gudu yaje gurin hajia itama ya mata
peck ta masa oyoyo.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:56PM, 6/3/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">9</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Hajia tace yaje yayi wanka ya sauqo yin
lunch, fatu ta riqe hannunsa suka tafi dakinsa tana tambayarshi labarin skul.
Yayi wanka fatu ta wuce dakinta don gabatar da sallah, shima farouq wucewa
mosque yayi. Bayan ya dawo ne suka hallara a dinning don cin abinci, suna kan
ci fatu ta dauko musu zobo, ta tsiyayawa kowa kana ta zauna. Farouq ne ya fara
tabawa yace "mummy wannan Ribena ne? Mummy tace " kamar zobo ne lemme
taste it" hajia ta dan kurba tace "natural" kana ta kira dija
tazo "haba dija, dama kin iya irin wannan zobon amma baki taba mana ba?
Dija tace "hajia bani bane fa, fatu ce tayi" nan hajia ta maida
dubanta ga fatu wacce cin abincinta take hankali kwance, tace "fateema a
ina kika koyi wannan zobon? Fatu tace "mummy a skul ne, nayi food nd nut
ai" fatu ta fada mata yanda sukayi. hajia tayi smile tace "zaki koya
min nima, gashi babu wani flavour ko color, komai natural sai qarin lafiya ba
abun cutarwa" duk sukayi daria, in banyi qarya ba kowa yasha zobo cup 5😜.
<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Kwanci tashi ba wuya a gurin Allah, yau
fatu ta cika 3 weeks a gidan, tayi fresh tayi kyau abunta, hajia tana nuna mata
gata ba qarya, don kaya kala kala naga fatu na sawa ita da tazo da kala 3,
shoes and bags ma gasu nan kamar na wata yar gwamna, make up kuwa takanas hajia
ta kaita PRETTY AYSHA PALOUR ta koya mata kwalliya na zamani. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sanye take cikin wani swiss lace mai pink
nd blue, tayi simple make up amma tayi matuqar kyau, kayan sun amshe ta kamar
ka sace ka gudu, gyalenta ta dauka ta yafa a kafada ta fito palour ta samu
hajia na kallo manara tv. "Sannu da hutawa mummy" hajia ta juyo tace
"yauwa yar mummy, gurin mal usman zaki je kice kafin ya wuce kumo ina son
ganinsa" fatu tace "to mummy" ta fita daga palourn ta nufi bakin
gate. Turuss ta tsaya ganin sultan na magana da mal usman din. Rabon da ta
ganshi tun ranar shigowanta gombe. Zuciyarta ne yake dukan uku uku, kar fa ya
ganeta ya korata kauye ko kuma yaci mutuncinta, wayyo Allah! A zuciyarta tana
ina ma bata fito yanzu ba. Yana gama maganansa ya miqa wa mal usman envelope
yana cewa "bari in gaisa da mummy" juyowan da zaiyi yayi arba da ita,
dumm gabansa ya fadi, "tsarki ya tabbata ga Allah da ya tsara wannan
halitta" sultan ya fada a zuciyarsa yana mai qarewa fatu kallo ita ma din
shi take kallo, sunfi 1 min a haka, fatu ce tayi qarfin halin fara tafiya ta
nufi gurinsa.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku a kullum<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:27PM, 6/4/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tafiya take yi a hankali zuwa gurinsa don
ita duk a tunaninta ya ganeta, tazo dab dashi ya aika mata da murmushi yace
"sannu yan mata" tsayawa tayi cakk, a ranta tace ashe bai ganeta ba,
don haka ta fuske tace "sannunka" kana ta cigaba da tafiyanta zuwa
gurin mal usman. Ta gaishe shi tace "mummy tace tana son ganinka kafin ka
tafi" yace "to" kana yayi qasa da muryansa yace "fatu
yallabai ya ganeki kuwa? (Mal usman gulma😂) shiru tayi tana kallon
gefe, sannan tace "ka manta abunda hajia tace ne? Duqawa yayi kamar me
neman gafara yace cikin karamin murya "ahh yi hakuri, wallahi mantawa nayi
fateema, bakin nawa ne ba sakata" murmushi tayi tace "ba komai"
wuce wa tazo ta sake yi ta gaban sultan wanda tun tafiyanta gurin mal usman ya
tsaya ya zuba musu ido, sai dai bai san me suke cewa ba. Tana shiga palour ta
isar wa hajia saqonta tayi saurin haurawa sama, hakan yayi dai dai da shigowan
sultan ya zuba ma bayanta ido, sai yake ganin duk duniya babu wanda hawan step
ya masa kyau irin wannan babe din. Sai da ta shige ya juyo da kallonsa palourn
ganin idon👀 mummy qurrr a kansa yasa yaji kunya. Daya daga cikin
kujeran ya samu ya zauna yace "sannu mummy" tace "kaima
sannunka" dariya yayi don duk a tsarge yake kamashi da mummy tayi yana
kalla mata baquwa. Suka gaisa, mummy ke jajensa tace "wato don jameel baya
nan shine ko kafanka ba'a gani ko" murmushi yayi yana sosa qeya yace
"wallahi mummy ban zauna bane, last wik ma dawowana daga china, kuma nazo
farouq yace kina bacci" hajia tace "ba komai in abokin naka ya dawo
ai zamu na ganinka, Kaga shikam yayi iyali, kai kuma naga alama so kake azumin
nan a fara kada maka gangan tuzuru" daria yayi sosai yace "mummy ki
shirya bayan sallah zakuyi bikina, na samu mata sai dai bamu daidaita ba"
Mummy ta kallesa tace "a ina" sultan yace "kin santa ma mummy,
ki tayani addu'a kawai" da jin haka mummy ta gane fateeman ta yake nufi,
sai ta fuske tace "nidai ban gane wacece ba, Allah ya baka sa'a"
ganin bai samu fuska ba yasa ya maida kallonshi kan tv, yafi kusan 30 mins
xaune da hajia suna hira sai dai ko kadan bata kawo masa tadin baquwarta ba,
fatu kuwa qin fitowa tayi. Ya gaji da jiran fitowan ta yayiwa hajia sallama ya
fita.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku a kullum<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:36PM, 6/5/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sultan na fita ya hadu da farouq ya dawo
daga skul, tafawa sukayi yace "big boy, ka dawo? Ya skul" yace
"lafiya kalau, yau muka yi games, mukayi gudu muna waqan soldiers"
sultan yace "Ai ana ganinka anga sojaa, give me five" suka qara
tafawa, kana sultan yace "amm sojaa, nikam wacece baquwar mummyn nan?
Farouq yace "anty fateema ce, tazo karatu ne" da yake hajia ta
gargade shi kan duk wanda ya tambayeshi fateema ya fadi haka nan. Yace "ok
good boy, maza in ka shiga gida kace ina gaisheta" yace to.
"Fateema" sunan ta mai dadi, murmushi yyi ya shafi face dinsa kana ya
dan bugi kirjinsa saitin heart dinsa, (ko me hakan ke nufi oho😜) fita
yayi daga gidan, a bakin gate ya hango mal ahmadu yazo karban mal usman guard
tunda zaije aika. Suka gaisa ya wuce gidansu. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Dawowan farouq yasa fatu sauqowa kasa ta
masa oyoyo, yace "bro sultan yace yana gaisheki" kallon mummy tayi
taga hankalinta na kan tv don haka tace "yaushe" yace "yanzu na
hadu dashi a bakin gate, kin ganeshi? Shine wanda nake baki labarin ya kawo min
tsaraba zuwansa china, muje in qara nuna miki tsaraban" fatu tace
"awww yanzu na tuna, kaje kayi wanka kayi sallah sai muci abinci, akwai
labarin da zan baka" ya tafi dakinsa. Mal usman ne ya shigo ya gaishe da
hajia ya tsaya a bakin kofa, hajia tace "sultan ya baka aika ne? Yace "ehh"
tace "ka bawa fateema ta dubamin, miqa ma fatu yayi ta bude kudi ne dai
har yanzu, har zata rufe taga wata karamar paper da dauka ta miqa wa hajia.
Hajia tace "a'a letter dinki ne" rufe envelope din tayi ta bawa mal
usman yasa a aljihu. Hajia tace wa fatu shikenan kije dakinki. Ta wuce. Hajia
tace "mal usman kamar yadda na fada maka fateema tana nan amma kakanta bai
sani ba, haka sultan, inaso a dauka a gidansu sultan take, kakanta kan iya
tambayarka fatu, kace masa tana lafiya, kuma a baka takardun karatun ta duka,
sultan zai saka ta a makaranta" da saurinsa yace "hajia an gama"
kudi ta bashi ya karba yana godia kana ya fita.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu kuwa tana shiga dakinta ta fada kan
gado tana tariyo yanda sultan ya mata murmushi, karo na biyu kenan da taga
smillin dinshi. Ya qara mata kyau da kwarjini, dazu tayi matuqar yin qoqarin
ganin bata kwapsa ba balle ya ganota. Papern tayi saurin budewa, ta fara
karantawa<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Hii<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">""Ki cewa mal Ameenu na gaishe
shi, ki kuma bashi hakurin rashin ganina, may be bayan sallah zanzo""<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Samun kanta tayi tana nanata wasiqar, duk
da ba ita akayiwa ba amma taji dadin sa. Murmushi naga ya subuce a fuskarta can
kuma ta fara hawaye, tana tausayin kanta, yanzu zata rabu da mijinta, duk da ba
sonshi takeyi ba amma zata so ta zauna da dan'uwanta. Kuma taga yana mata murmushi.
Wata zuciya tace fateema yake yiwa ba fatu ba. Kar ma kisa shi a ranki, a duk
lokacin da ya gano kece fatu bazai qara kulaki ba. Wasu zafafan hawaye ne suka
qara gangaro mata tayi saurin gogewa, farouq ne ya shigo dakinta wai ta sauko
yin lunch, goge fuskarta tayi suka fita tare da yake tana fashin sallah. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Acan garin modibbo kuwa mal usman ya kai
saqo kamar kullum. Mal aminu ke tambayarsa? Ina uwargidan nawa, da fatan tana
lafiya? Mal usman yace "tana lafiya kalau, tace a gaisheka ma. Kuma a bata
takardun makarantar ta zata cigaba da karatu. Cikin jin dadi kaka ya dauko
komai da komai ya bashi, da yake duk takardun nata a gurin kaka yake.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Bayan mal usman ya dawo ya bawa hajia, nan
da nan tasa a nema wa fatu admission a GSU cikin qanqanin lokaci aka sama mata,
aka gama komai ta fara zuwa lectures.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Anan zamu tsaya a FATU A BIRNI insha Allah
bayan sallah zamu cigaba.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Kuyi hakuri na rashin post da wuri hakan ya
samo asaline na rashin charge.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">FATU NA MUKU HAPPY RAMADAN🍉🍏🍎🍐🍊🍉<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Allah ya bamu ladan dake cikin wannan wata
ta Ramadan. Ameeen<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[3:15PM, 7/11/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Kwanaki sun shude yau watan fatu biyar da
barin garinsu tayi nisa a karatunta kuma tana fahimta, qawarta daya sunanta
itama ma fatima. Qawancen su ya samu asali ne ranan wata monday fatu tayi latti
sosai gashi har an shiga lecture kuma
lecturer baya barin a shiga, fatu sai safa da marwa takeyi a bakin hall din,
fatima da take ciki ta hango ta sai ta bata tausayi, don tana lura da fatu,
irin dodging lecture da students sukeyi ita sam bata yi ga kokari kamar me!
Tana cikin tunaninta taji an jefe ta da abu; dumm gabanta ya fadi don tasan
lalle yau zai korata waje, maimakon taji ance yi waje sai taji yace "Me
kike kallo a waje? Bata san lokacin da tace "qawata ce" "u can
join her" abunda ya fada kenan. Zare ido ta fara yi tace "sir bata da
lafiya ne, ko dazu she called me tace bazata samu zuwa ba, so ganinta da nayi
ne ya ban mamaki" sai da yayi dan jimm sannan ya mawa fatu hannu da take
waje ta sake baki tana kallon ikon Allah. (Sana'ar ta ne dama sake baki😂).
Sai da ta shigo yace "get well dear" tana in ina tace "thank you
sir" guri ta samu ta zauna aka cigaba da lecture. Bayan ya fita ne ta samu
fatima ta miqa mata hannu hade da sallama ta amsa hade da shaking hannunta.
Fatu tace "amma kin taimakeni nagode sosai, gashi ya bamu light akan
abunda zai fito a exams. Fatima tayi murmushi tace "ai kuwa, me sunanki?
Fatu ta amsa "Fateema Mahmud" tayi carab tace "sunan mu daya
amma ana kira na xahra levels" fatu tace "I like it" xahra tace
"tnks namesey"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Haka qawancen su ya cigaba cikin aminci.
Suna ziyaran junansu lokaci lokaci, hajia ta yaba da hankalin xahra shiyasa
take barin fatu tana ziyartar ta. Bangaren sultan kuma soyayyar fateema ta gama
narkewa a zuciyansa, sukan gaisa amma daga nan yake tsayawa, dan gaisuwan da
yake yawan shigowan ma ya rage, don akwai ranar da yazo fatu tana ganinshi ta
haura sama, yazo ya zauna suka gaisa da mummy, hajia tace "nikam sai kora
min 'ya kakeyi, da ta ganka sai ta tafi" yayi murmushi yace "afuwa
mummy" Haka suka cigaba da hiransu har yake tambayanta daddy tace yana
Abuja, don shi bai cika zama a gida ba, lokacin zuwan fatu ma baya gida, da ya
dawo hajia ta bashi labarin ta bai yi comment akai ba, illa cewa da yayi Allah
ya taimaka. Yasa hajia ta kira masa ita ya mata questions akan rayuwarta ta
bashi amsa, kana ya mata nasiha yace ta
dauki gidan kamar gidansu, kuma ta maida hankali akan karatu.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Yau shirye shirye akeyi a gidan don tarban
manyan baki, mahmud ne zai dawo daga cyprus sai jameel da matarsa suma zasu
dawo daga south Africa. Hajia ta kasa zaune ko tsaye haka fatu, duk wani shiri
da girke girke an kammala sai isowan su kadai ake jira, karfe 2 na rana sukayi
waya sun sauqo, nan da nan hajia ta aika driver a dauko su, farouq yaso a je
tarbansu hajia tace nooo. Bayan tafiyan driver fatu tace wa hajia zata je tayi
wanka kafin su dawo, hajia tace to. Fatu ansha aiki, tana shiga daki tace bari
ta dan miqe a gado kadan, bata san lokacin da bacci ya kwashe ta ba.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Jameel sun dawo cikin dokin ganin gida,
hajia tayi murnan ganinsu harda kwallanta, farouq murna kamar ranar ne sallah.
Bayan an gama gaishe gaishe aka nufi dinning cin abinci, amaryan jameel, lubna mai
dauke da qaramin ciki tafi kowa kwasan girki, sai santi take zubawa, mahmud da
yake qanin mijinta yana ta tsokananta kota kulashi, mummy dai dadi ya hanata
magana. Can hajia tace "mahmud kai kuma maimakon kana gama karatunka kayo
gida shine ka biya can south africa ko, wato ko missin din gida baka yi? Riqe hannunta yayi yace "wlh mummy
jameel ne ya dameni wai in biya can tunda suma sun kusa dawowa wa, mummy 3 wiks
kawai nayi a can din fa" ya qarasa maganarsa cikin shagwaba, daria sukayi
lubna tace "ji shi kamar wani yaro" "yaro nake tunda ban kusa
ajiye baby ba" mahmud ya bata amsan da ya saka ta kunya, don haka tayi
shiru. Murmushi Jameel yace "mummy nafi son mu dawo rana daya ne thats why
nace ya biya can, nd he enjoyed staying there" hajia tace "Alhamdulillah
tunda kun dawo lafiya all, sai shirye shirye walima da party na taya murna, in
da next 1 week" murmushin jindadi mahmud yayi yace "thanks mum, Allah
ya biyaku dawainiyan da kukeyi akan mu" dukansu suka amsa da Ameen.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Bayan kammala cin abinci kowa ya nufi part
dinshi, jameel ya dauki matarsa suka tafi gidansu da yake basu da nisa da gidan
iyayen nashi.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[3:19PM, 7/11/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu bata farka ba sai bayan la'asar,
kallon agogo tayi ta saka salati ta shige bathroom. Wanka tayo da alwala ta
bada farali kana tasa kaya hade da light make up. Palour ta fito taji shiru
tace ba dai har sun kammala ba. Kitchen ta shiga ta samu dija na aikin girkin
dare ta tsaya tambayanta hajia dasu jameel, dija tace "ai tun dazu su
lubna suka tafi, mahmud kuma inaga ya shiga cikin gari. Fatu tace "mmn
isya yanda kika san an mini duka haka nake jin jikina dazu, ina shiga daki
kawai na kwanta in huta ashe bacci ya kwashe ni" Dija tace "kinyi
kokari ai" fita daga kitchen din tayi dakin hajia, sai da ta knockin tayi
sallama aka amsa ta shiga. Hajia ta samu zaune a bakin gado tana waya da aunty
sadiya (maman sultan). Kujera na dressin mirrow taja ta zauna Sai da hajia tayi
hangin fatu tace "mummy ya gajiyan yau? Hajia tayi mrmshi tace "ai ke
za'a cewa ya gajiyan yau, kikayi ta bacci abunki" daria fatu tayi tace
"Allah mummy nima bansan tym din da bacci ya debe ni ba, kuma farouq ma ko
yazo ya tasheni" mummy tace "ni nace ya barki ki huta. Ki dauki
wancan jakan ki kaiwa hajia sadia tsaraban su ne, naki kuma sai kin dawo ki
gani" fatu tace "tooo" daukan jakan tayi ta fito, room dinta ta
shiga ta dauko hijabi iya gwuiwa tasa ta fito. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A palour ta tarar da qanwarsa Amrah tana
danne danne a waya, zata kai 13 yrs, "anty fateema oyoyo" amrah tace
da fatu yayinda take zuwa gurinta ta karbi ledan hannunta suka zauna, fatu tace
"washhh, Ina mammi" amrah tace "tana dakinta, bari in
kirata" bata jima da shiga ba suka fito tare, hajia sadia na cewa
"amrah bi kitchen ki daukowa fateema ruwa" zama tayi akan kujera
fuskarta dauke da murmushi tace "sannunki da zuwa fateeman mummy"
murmushin fatu ma takeyi amma fuskarta a qasa, ta zamo daga kan kujeran ta
gaisheta kana ta koma ta zauna. "Mummy ne tace in kawo muku
tsarabanku" ta fada yayin da take miqawa hajia ledan. Amrah ta kawo wa
fatu ruwa ta tsiyaya mata ta koma kusa da hajia sadia ta zauna tana cewa
"mammi ina nawa" hajia sadia tace "gashi nan, kinga na kowa Anyi
wrapping dinshi da suna" ta karba tace "anty fateema kice nagode
sosai" fatu tace "to amrah" amrah ta wuce dakinta don ganin
tsarabanta. Fatu ta miqe tace "mammi sai anjima" hajia sadia tace
"daga zuwa? Ko ruwa baki sha ba" fatu tace "mammi na sha"
sultan ne ya shigo a dai dai inda hajia sadia ke cewa "ki gaishe min da
mummyn naki" sultan yace "muje in raka ki" saurin dago da kanta
tayi ganin ita yake kallo yasa ta fara tafiya tana cewa "to mammi"
hajia sadia kuma ta koma ciki tana jindadi, don tun ba yau ba take son sultan
da fateema, don yarinyar ta mata, ga nitsuwa da hankali, har cikin ranta take
son fatu. A bakin gate ya cim mata, wani sauri takeyi bata son wani abu ya hada
su, gudun kar ta kopsa ya ganeta. Sultan yace "madam ba haka tafiyanki
yake ba" dolenta ta fara tafiya yanda ta saba, hakan ya bashi daman jerawa
da ita. "Ina wuni" fatu tace dashi, yace "lafiya kalau fateey,
kina lafiya" a gajarce tace "lafiya" dai dai nan suka iso bakin
gate ta shige abunta, shi kuma ya juya ya fara tafiya, tana shiga taga bai
biyota ba, sai taga sam bata kyauta ba, ko godia babu, leqawa tayi tace
"hey" ya juyo ta sakar masa murmushin da ya saka shi jin sansanyar
iska na bin jinin jikinshi. Yace "yess" tace "thanks" bata
jira amsar sa ba ta shige. Samun kansa yayi da tsayawa a gurin yana doka uban
murmushi da yasa hakoransa shan iska yana kallon kofar, yafi 5mins a gurin
wucewar wata mota ce ta sa shi dawowa hayyacinsa ya koma gidansu. Ita kuma tana
shiga a farfajiyan gidan ta hadu da mahmud zaune a irin kujerun shan iska nan
yana karanta newspaper tazo ta gurinshi tace "sannu da hutawa" ya
sauqe jaridan yace "yauwa" tayi wucewarta. A ranshi yace wacece
wannan? May be dangin su sultan ce don tana kama dasu, amma dai ta hadu ba
laifi, tashi yayi ya shiga cikin gidan shima, mummy ne ta fara ganinshi tace
"mahmud har ka dawo? Yace "ehh" ya nemi guri ya zauna. Fatu tace
"mummy shine ya mahmud? Mummy tace "shine" fatu ta gaishe shi ta
masa sannu da dawowa ya amsa. Tace "na hadu dashi a waje ban zata shi bane
ai" mummy tace "ayya, kina bacci suka dawo shiyasa" mahmud yace
"mummy banganeta ba" mummy tace "yar uwarku ce daga bauchi tazo
karatu ne" tana fadan haka ta tashi ta shige kitchen. Kallon fatu yayi
yace "a gidan wa kike a bauchin, don ban taba ganinki ba duk zuwa na"
shiru tayi ta rasa me zata ce can ta qakalo murmushi ta ce "ko na fada ma
baza ka gane ba" zai qara magana mummy ta fito da basket a hannun ta tace
"fateema ko zaki kai abincin gidan jameel? Ta nan sai ki musu sannu da
dawowa" da dokin ta tace "ai kuwa mummy" "amma ki jira
yanzu farouq zai dawo daga islamiyya sai ku tafi tare driver ya kai ku"
yamma liss farouq ya dawo driver ya kaisu gidan jameel da amarya lubna.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Afuwan fans, sai yau Allah yayi na turo
FATU A BIRNI. Ba jan ranku nayi ba, lokaci ne ban samu ba. Barka Da Sallah. Allah
ya maimaita mana. Ameen<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku a kullum<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:14PM, 7/13/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Gefen sultan kuma yana komawa gida ya wuce
dakinsa ya kwanta yana tunanin fateema, wayarshi ce ta katse masa tunaninsa,
ganin number jameel yasa shi miqewa tare da amsa wayar "ka shigo
ne?........ ok bari in fito. A haraban gidan ya ga jameel bayan sun gaisa ne
kai tsaye suka shige cikin palourn gidan, mammi ce kadai zaune tana rubutu a
wani memo, sallaman da sukayi yasa ta cire tabarau idonta "lale marhabin
da mutanen S Africa" zama sukayi, bayan sun gaisa da mammi ne suka fito
haraban gidan, sultan yace "dude yau ma tazo gidan nan wallahi, har rakata
bakin gidanku nayi" ya fada yana shafa sajensa daya kwanta luff a fuskar
sa, jameel dai kallon mamaki yake binshi dashi, tunda suke sultan bai taba cewa
yana son wata ba, shi har ya fara tunanin ko yana da matsala ne, mata sunsha
warce kansu a gurinshi amma ko kallonsu baya yi, amma akan wata wai fateema ya
gama rudewa. Koyaushe sukayi waya sai sultan yayi maganar ta, jameel yana so
yaga wacece fateeyn nan da take qoqarin
zautar masa aboki. "Wai dama haka love din yake? Da ita nake bacci da ita
nake tashi, jameel na rasa yadda zanyi" Jameel da ya tsaya kallonshi sai
yanzu ya samu bakin magana "why not ka tunkareta? Ajiyar zuciya mai qarfi
sultan ya sauke yace "I cant! Tana min kwarjini da yawa, to me zan ce mata
ma? Kuma I asked farouq bata riqe waya nd tura wasiqa ka gane yayi yawa"
Jameel yace "amma ka taba sanin tana da saurayi? Sultan yace "ko a
skul bata kula kowa qawarta ma daya ce, a gida ma babu wanda yake zuwa mata,
all I know shine ita TAWA CE! "Bravo alaika" jameel ya fada yana tafa
masa, "ka iya yanda zakayi ka samu details akanta amma baka san yanda
zakayi ka mata magana ba" sultan yace "kai dai ka taimakeni"
"yanzu dai muje gidana ma qarasa maganar acan" shiga cars dinsu
sukayi suka fita.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Gidan jameel ya hadu shima ba laifi, dai
dai zaman mace daya. Driver na ajiyesu farouq ya fito da gudu ya shige cikin
gidan, fatu ma ta fito tacewa mal habu ya jirasu yanzu zasu fito. Tana shiga
motocin su jameel suka shigo. Bayan sun fito ne jameel yake tambayan mal habu
ko aika ne ya kawo, yace masa ya kawo farouq da fateema ne, sultan dake gefe
yayiwa jameel ido, jameel yace "ok kaje zan dawo dasu anjima" ba musu
habu ya tafi. Su kuma suka tsaya anan suka cigaba da maganansu. Farouq a daki
ya tarar da lubna tana gyara cikin wardrobe dinta, tace "farouq yaushe
kazo" yace "yanzun nan, ni da anty fateema ne" tace waye kuma
anty fateema" yayinda ta riqo hannunshi suka fito palour inda fatu tayi wa
kanta masauqi a daya daga cikin kujerun da suka qawata palour.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sannu da zuwa lubna tayi wa fatu tace bari
in dauko miki ruwa, fatu tace "a'a nagode, ban jima da sha ba" suka
gaisa anan lubna tace "sai dai ban ganeki ba" farouq yace "nace
miki sunanta anty fateema kuma tazo karatu ne gurin mummy" daria sukayi
lubna tace "to uban yan surutu, kai na tambaya? Bai kulata ba don ya danno
tashan cartoon. Maida hankalinta tayi kan fatu tace "ke yar uwarsu ce
kenan, kamar na taba ganinki, daga bauchi kike ko? Fatu tace "ehh, mummy
tace a kawo muku abinci, kun dawo lafiya? "Lafiya kalau" lubna ta
bata amsa. Fatu ta kalli farouq tace "my sojaa lets go" ba musu ya
miqe yace "bye anty lubna, kuma sai na fadawa mummy kince nine uban yan
surutu" zaro ido lubna tayi tace "kaji dashi" fita yayi zuwa
inda sukayi parking amma wayam ba mota, sai motoci biu da ya gani, zai juya ya koma
ya hango sultan da jameel da bayan cars din. Gurinsu ya nufa dai dai nan su
fatu suka fito suma. Fatu tana ganin ba motan su tace "ba dai mal habu
tafiya yayi ya barmu ba? Sai dana ce ya jiramu fa" ta karisa maganan kamar
zatayi kuka. "DJ" lubna ta kwalawa jameel kira suka taho dukansu
sultan n Nna cewa "oyoyo uwargida, don yanzu kin tsufa wata sabuwa zamu
kawo" lubna ta harareshi na wasa tace "hurul ain kenan? Suna can suna
jiransa insha Allah" gaisawa sukayi tsakaninsu fatu na gefe riqe da hannun
farouq tana wasa dashi, can tace "ya jameel sannu da dawowa" yace
"yauwa, fateema ko? Tace "ehh" gaisawa sukayi tace sai anjiman
ku. Da sauri sultan yace "ina zaki je" bata kalle shi ba taja hannun
farouq tace "gida" jameel yace "ni nacewa mal habu ya tafi zan
maida ku in munyi sallah" ba yanda ta iya dole ta koma, su kuma suka wuce
masallaci da farouq. Lubna taja fatu dakinta sukayi sallah, sai tadi sukeyi
kamar sun jima da sanin juna, anan ta tayata qarisa gyaran wardrobe din, suka
share dakin duk da kafin su dawo an share da gyara ko ina na gidan. Su sultan
basu dawo ba sai bayan sunyi sallah isha. A palour suka tarar da su lubna da
fatu suna ta tadinsu, sallama sukayi suka shigo, Lubna tace "ba dai har
anyi sallah isha ba? Jameel ya zauna kusa da ita yace "ina zaki sani tunda
kin samu abokiar hira" lubna ne ta canja tasha zuwa cartoon wa farouq
tace "fateema ki shiga daki kiyi
sallah, bari inyi serving dinsu abinci" shigan fatu keda wuya suma suka
wuce kan dinning jameel yace "mutumina ka tafi da yawa fa, irin wannan
kallon haka" cike da tsokana ya karasa maganar. Lubna tace "ba dai
fateema yake kallo ba? Sultan yace "dadina dake yawan tambaya, ni kawai ki
tayani campaign" Jameel yace "ni dai kaman na taba ganinta a bauchi,
amma inaga mahmud zai fi saninta don ya fini shiga ziyara, ko hutu yazo sai
yaje bauchi ya zaga dangi" nan dai sukayi ta tattaunawa har suka samu
solution, fitowan fatu yasa sukayi shiru, ganin haka ta gane maganarta sukeyi
kawai ta wayance ta zauna kusa da farouq. Bata dade da zama ba suka kammala
jameel yace "muje ko fateey" sun fito haraban gidan jameel yace
"ohh ashee ba mai da yawa a mota na, pls sultan ka sauqesu mana" sai
da yayi dan jimm kana yace "ok" jameel ya tura farouq baya, lubna
kuma ta budewa fatu gaba tace "ki zauna a gaba ke" ba musu ta shiga,
lubna ta miqo mata leda tace "ga tsaraba ba yawa" godia fatu tayi
sultan yaja su suka tafi.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Taku a kullum <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'iz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:40PM, 7/16/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tun shiganta motan kamshin jikinsu ya
gauraya ya bada wani ni'imantaccen scent mai kwantar da hankali, ga a'c ya
sanyaya ko ina. Ba sultan kadai ba har fatu taso inama suyi ta zama haka har
abada *what? Fatu ar u in love?* tsohuwar cool music na celin dion mai taken
_TITANIC_ ya saka musu (in d nyt in my dreams I see u, I feel u....) yana bi a
hankali, fatu da ta gama narkewa ta juya kanta gurin window tana jin kalaman
waqar har cikin zuciyarta yana ratsa ta. Maimakon taga anyi hanyar gida sai ya
biya wani guri, basu tsaya a ko"ina ba sai katafaren gurin sayar da
phones. Ya juya zaiyiwa farouq magana yaga yayi bacci. Fatu ta juyo tace
"baka ce zaka yi branching ba, srry mun takuraka" yace "no
wahala, abu zan saya kuma gashi farouq yayi bacci banida dan rakiya, muje ki
rakani" tace "no, in kai alone ne zaka fi sauri" Yace "noo,
to ki biyani rakiyan dana miki dazu" yanda yyi maganar kamar yaro yasa
fatu daria tace "muje to". Suka shiga tana binshi a baya, yace "pls ki tayani zabe, amrah nake son
sayawa waya" tasan dai amrah nada waya koda yake abunka da masu shi, tara
wayoyi a hannu qaramin aikinsu ne. Iphone latest ta nuna tace "wannan
yayi" Yace "irin nawa" tace "sai kuyi anko" yace
"hakan za'ayi" Qaramin Nokia ya qara dauka ya biya kudinsu, anan ya
qara sayan sim cards 2 dfffrnt layi suka fita. Har komawansu mota farouq na
baccinsa, basu zame ko ina ba sai *eman* ya saya musu ice cream da snacks, daga
nan suka yoo gida wajen tara saura. Har cikin gidan ya shiga yayi parking suka
fito daga motan, fatu na qoqarin daukan farouq yace "lemme help" ba
musu ta matsa masa ya dauke sa suka shige gidan, a palour ya kwantar dashi
mummy kuma da alama tana dakinta, Fatu tace "thanks" yace kinyi
mantuwa a mota, tace "ni? Ok tsaraban da anty lubna ta bani" fita
sukayi ya bude motar ya dauko ledojin da sukayi shoppin ya miqa mata, tace
"wannan ne nawa" ta karba yace "dan tsaya pls" tayi juyi
irin ta gajin nan, yace "srry" bude ledan wayoyin yayi ya saka musu
layi duk tana tsaye ya kunna ya miqa mata, yace "bari in gwada kira"
ita duk bata dauka wani abu ba ta karba, wayarshi ya ciro sak irin na hannunta
ya kira sai ga numbern shi ya bayyana a screen din, miqa mishi tayi tace
"yayi" yace "kip it, naki ne" cikin zaro ido tace
"what? Noo kayi hakuri.... kafin ta qara magana ya rufe motarsa yayi
reverse tana tsaye har aka wangale masa gate ya fita, ta jima kana ta koma gida
jiki a sanyaye, a palour ta tarar har mummy ta shigar da farouq dakinsa, tana
sauqowa qasa, fatu tace "mummy mun dawo" hajia tace "sai yanzu kenan?
Jameel din ne yadawo daku? Fatu tace "a'a amm.... yayan amrah ne"
sarai hajia tasan sultan ne ya dawo dasu don tana ganin shigowarsu duka, tace
"bari in duba kullin masan nan, gobe da safe dadynku zai sauqo yace shi
yake sha'awa" har hajia ta dubo ta fito fatu na tsaye a gun, hajia tace
"auu baki haura bane? Kaman zatayi kuka tace "mummy wayoyi ya bani
fa" da fara'a hajia tace "a ina" fatu ta labarta mata komai,
hajia taga wayoyin tace "amma sunyi kyau Allah ya amfana" fatu da
mamaki ya gama lullubeta tace "mummy gobe zan mayar masa dai ko? bata
fuska hajia tayi tace "maganar gaskia fateema ki nemi soyayyar mijinki,
abunda zan iya fada miki kenan, kibi komai a hankali da nutsuwa" har zata
juya fatu tace "mummy ga tsaraba anty lubna ta bani" mummy ta gani
tayi Allah ya amfana tayi upstairs. Zama jugum fatu tayi tana aukin tunani, ita
ta rasa a wani yanayi take, shin tana son mijinta ne ko bata sonshi? Kodai
kawai son yan'uwantaka ne? Amma deep inside her heart tana jin bazata iya
rayuwa babu shi ba. Da taga tunani bazai fishhe ta ba tace "Allah ka shige
min gaba" tashi tayi ta dauki roban ice cream daya da snack iya wanda zata
ci sauran tasa a fridge, kashe wuta tayi ta kulle kofa tayi dakinta, bayan ta
gama ci ne tayi wanka ta fito taga leda akan mirrow nata, murmushi tayi tace
tsaraban mummy ne. Ta duba takalma ne yan ubansu guda uku kowanne da jakansa,
na lubna kuma turaruka ne da cosmetics, adana su tayi ta kwanta. Qarar wayanta
ne yasa ta tashi zaune a tsorice (sabon shiga😂🤓) a hankali tasa
hannu ta dauka, number ta gani wanda tasan na sultan ne tace "hello"
can gefe akace "hii" shiru ya biyo baya, can a gefe yace "sultan
ne ya gajia? Tace "lafiya, nagode fa Allah ya saka" har cikin ranshi
yaji dadin addu'anta yace "ameen, sai da safe, karki shanye ice cream din
ki ragewa farouq nashi" daria dukansu sukayi kana sukayi hanging, daga ita
har shi da murmushi a fuskarsu bacci ya dauke su. Hmm _lovebirds_😍<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fa'izz👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[7:41PM, 7/17/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Yau kimanin wata biu da sati biu kenan da
haduwan sultan da fatu a a gidan jameel, shakuwa mai tsanani ya shiga
tsakaninsu, wanda yawanci in sultan na qasar shi yake kaita school, waya kuma
kowanne dare sai sunyi b4 bacci, no love jst qanwa da yaya. Chattin babu wanda
fatu batayi da taimakon qawarta xahra levels. fatu har sunyi exams na second
semester suna hutu. Yau saturday sunyi da levels zasu je saloon, Karfe 11 na
safe tana gidansu levels daga nan suka rankaya gurin saloon din da yake ba nisa
tsakaninsu.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A gidan jameel naga sultan da abokin nashi
a palour suna magana, jameel yace "its time ka furtawa fateema cewa kana
sonta, don kun saba wanda nasan lokacin da kuka dauka kuna tare itama ta fara
sonka" sosa kai sultan yayi yace "kana ganin ta fara sona?
"Kwarai insha Allah" Jameel ya bashi amsa. Sunkuyar da kai sultan
yayi kana ya dago yana kallon gefe. Muryan jameel yaji yace "FATU FA?? Da
sauri sultan ya juyo da kanshi gurin jameel zuciyarsa na dukan uku uku, don shi
ya manta ma da wata fatu, yau kimanin wata uku kenan ko aika da yake mata ya
daina, fateema ta mantar dashi cewa yana da mata ajiyayya. Jameel ya qura masa
ido yana jiran yaji mai zai ce, shi dai fatu ta masa tun ranan har yanxu kuma
yana tausaya mata a matsayinta na marainiya abar tausayi, "baka yi magana
ba" jameel yace dashi, sultan da har yanzu bai gama saita kanshi ba yace
"ni fateema nake so, bani da ra'ayin zama da mata biu kuma. Inaga its time
itama da zan furta mata abunda ya dace da ita" jameel zaiyi magana sultan
yace "jameel u knw yanda aka hada auren, sam babu yarda ta. I cnt live
with her" Shiru jameel yayi, sultan sai da ji hankalinshi ya dawo jikinshi
ya dauki wayarsa yayi dialing numbern fatu.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Bayan an gama musu suka rankayo gida. Fatu ne
da xahra ke hira kan sultan levels na cewa "wallahi qawa har yanzu ina
mamakin wai sultan mijinki ne amma kuma bai ganeki ba, kuma wai he's in love
with new fateema" murmushin daya fi kuka ciwo fatu tayi tace "labarin
rayuwata kamar a movie, bansan nan gaba ya zaya kasance ba, zan rabu dashi ne
ko zamu kasance a inuwa daya a matsayin mata da miji, levels ki tayani addu'a
kawai. Allah ne kadai abun dogaro na" siririn hawaye ta goge hakan yayi
dai dai da ringing din da wayarta ya fara "dan halal, yaqi ambato"
cewar fatu yayin da murmushi ya bayyana a fuskarta, xahra ta bita da kallon
tausayi. "Assalam alaika yayan fateey" "wa'alaiku mussalam
qanwata, ya kike? Tace "lafiya lau, ya aiki? Yace "da godia, jiya
kince zaki je saloon kinje ne? Tace "ehh, yanzu muka dawo ina gidansu
levels ne" Yace "ok, in baza ki damuba anjima da yamma inason
ganinki" tace "ok yayana, zaka zo gidane? Yace "noo, mu hadu a
gidan jameel" sukayi sallama sukayi hanging. Fatu ta kalli levels tace
"I gotta go, zanyi wa mummy kunun aya nd sultan yana son ganina"
levels kada kai tayi kawai ta rakata haraban gidansu tasa drivernsu ya maida
fatu gida.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sultan na ajiye waya yace "jameel
insha Allah nan da 1 week zamu je Garin Modibbo gurin FATU"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:44PM, 7/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Jameel yace "I am sorry to say bazan
iya raka ka ba, I cnt face da dattijo" yana gama fadan haka ya fice daga
palourn, sultan ya bi bayansa amma yana fita jameel already yaja motarsa ya bar
gidan, shima ya fita.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Lubna dake kitchen ta fito jiki a sanyaye
da alama taji duk hiransu, jameel ya bata labarin fatu tun ba yau ba, haka
kawai itama take kaunar sultan da fatu, ko ba komai 'yar uwarsa ce, marainiya
mai neman taimako, kuma a yanda taji jameel ya fada fatun tayi karatu har zuwa
secondary, so why not ya maida ta skul in educated wife din yake so, tunani
barkatai lubna tayi akan fatu, tana tausayawa yarinyar. Tashi tayi ta shige
dakin jameel ta bude drawer da yake ajiye pictures, da kyar ta samo pic din
sultan da matarsa fatu. *WHAT*? naji ta furta da karfi hade da miqewa tsaye
harta manta cikin 6months da yake jikinta.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu na isa gida tayiwa mummy kunun aya
tasa mata a fridge, fitowanta daga kitchen din yayi dai dai da shigowan mummy
gidan, fatu tace "sannu da dawowa mummy" tace "yauwa
fateema" fatu tace "farouq daya dawo daga skul yace zai biki gidan
mammi, yaje ne" hajia tace "dan rigima yaje, ynxuma na barsu zasu je
unguwa da amrah ne" fatu tace "ayya, nima inason zuwa gidan anty
lubna anjima" mummy tace "Allah ya kaimu" fatu tace "Ameen,
na gama kunun ayan, yana fridge" da murmushi a fuskar hajia tace
"nagode 'yata Allah ya miki albarka" "Ameen mummy" fatu
tace ta bar mummy a palour ta shige dakinta don tadan huta zuwa yamma, ko
meyasa sultan yake nemanta oho. Wayarta ta dauka don tayi chattin amma sai taga
missed calls din lubna 4, da sauri ta kirata don ita ta dauka ma ba lafiya ne.
Ringing daya biyu ta dauka tace "Hello fateema kina gidana ne? Tace
"ina gida, naga missed calls dinki ne, lafiya kam? Lubna tace "sai
alkhairi, don Allah ina son ganinki yanzu yanzu" fatu tace "ai anjima
ina zuwa da yamma" lubna tace "a'a its urgent pls ko minti biyar
karki qara" fatu tace "to pls bari inyi wanka" "ohhh
fateema kiyi hakuri ki dauko kayan da zakisa in kinzo kiyi anan" fatu tace
"to gani nan zuwa" kashe wayan tayi zuciyarta na dukan uku uku. Anya
ba ganeta sultan da jameel sukayi ba? Saisaita kanta tayi ta dauki abubuwan da
take bukata taje dakin mummy tace "mummy bari inje yanxu anty lubna ta
kirani" mummy tace "to shykenan Allah ya kiyaye hanya, ki dauka mata
kunun ayan nan naga itama tana so" murmushi fatu tayi tace "to
mummy" bayan ta dauka ne ta fita mal habu ya drivin dinta sai gidan
jameel.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:45PM, 7/19/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">8</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sultan na fita gidansu ya nufa, kai tsaye
room dinsa ya nufa ya zauna akan daya daga cikin kujerun da suke room din. Shi
gabadaya jin haushin fatu yakeyi, ta bata mishi plan din rayuwarsa, gashi
akanta har sun sami matsala da abokinshi wanda tun suna yara rabon da hakan ya
faru, shi fa bazai iya ba, never!! Zai saketa ya kawota gurin mammi ya kuma
gargadeta tayi kipp da bakinta. Laifinshi ne ma daya qarfafa bincike wajen nemo
innar tashi. Tunani ya fara shekara biyu da suka wuce yana tare da mammin shi a
dakinta suna hira lokaci daya tayi shiru yace "mammi lafiya" tace
"tunanin 'yar uwata nakeyi, ko ya take? A ina take? ita kadai ce 'yar
uwata da muke uwa daya, sai kannena da muke uba daya, shekarana 6 a lokacin
aurensu ya mutu, ba yanda ba'ayiba a maida auren abun ya faskara, a haka aka
barsu amma kuma ana tare don rabuwansu bai raba zumuncin dake tsakanin babanta
da babanshi wanda suke yan uwan juna ba. Ina shekara 7 muka je dukku anan wani
da ake cewa mal sirajo ya ganta yace yana so, a lokacin yana da mata da
'yayansa 4, da kyar aka bashi aurenta don ma tace itama tana sonshi ne, saboda
bakin cikin hakan dangin mu suka tattara suka bar garin a cewarsu ta zabi bare
akan dan'uwanta, duk da shi din ma bafulatanin ne, amma wai su fulanin yawo ne.
Na sha kuka dana rabu da ita, bamu wuce ko ina ba sai yola dama can ne asalin
garin mu, anan muka zauna har babana ya fara shiga birni yana kasuwanci anan
yaga yara na zuwa skul ya saka ni, har Allah ya buda masa sosai yayi aure,
kamar yanda ka sani kannena biu, rufa'I da musa. Mahaifinka shima auren dangi
aka hada ni dashi, a can na haifeku duka muka dawo nan gombe lokacin ina goyon
amrah. Na tashi cikin dangi amma ina kewar mahaifiyata Muna dawowa gombe na je
dukku ganin mahaifiyata amma aka ce ta rasu, kanwata kuma tayi aure, nayi nayi
su fada min inda tayi auren amma suka ce sun manta, sultan ina kaunar naga wani
tsatso daga mahaifiyata" kwallan daya taru a idonta ne ya saurin zubowa ta
share. Tun daga wannan lokacin sultan ya qudura aniyar nemowa mahaifiyarsa 'yar
uwarta, yaje sau daya shima suka fada masa haka, zuwansa na biyu shigan dare
yayi da wasu soldiers da yayi hayansu, tsoro sosai suka bawa mal jauro wanda ya
fadi inda take aure har da sunan mijin nata. Yanzu a dalilin haka ya jawo wa
kanshi damuwa.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[11:06PM, 7/20/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">9</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu na isa gidan jameel ta shiga gabanta
na dukan uku uku, a palour ta tarar da lubna na zaune "kin iso? Tace da
ita, sai da ta zauna tukun tace "ehh, Allah yasa lafiya" hoton ta
ajiye akan cinyar fatu wanda lokaci qanqane dan walwalar da yake fuskarta ya
bace ya koma matsanancin damuwa, ido ta kurawa hoton kamar yau taba kallon
irinsa, lubna da ta kafe ta da ido tana nazarinta tace "explain
please" hawaye naga yana zarya a kumatun fatu tana girgiza kai tace
"its over, d charade" lubna ta matso kusa da ita ta dafa kafadunta
tace "its not over yet, yanxu aka fara, trust me" tiryan tiryan fatu
ta fara bata labarin har zuwanta gombe da yanda hajia ta taimaketa ta sakata a
skul ta maida ita *FATUN BIRNI* ta kuma dauketa tamkar 'yar cikinta da ta
haifa. Ajiyar zuciya lubna tayi tace "one last question, do u love
sultan" dago idonta tayi da sukayi dan jaa don kuka tace "anty
lubna......a life without sultan, even an immortal life would be empty, I wish
to stay on earth with him" murmushi mai bayyana 32 lubna tayi tace
"kamar yanda na fada miki its not over, to hakan ne" magana suka fara
wanda nayi nayi inji amma fateey na ta dameni da kuka, naga dai lubna na
zazzago magana yayinda fatu ke ta maida hankali 100% tana ji, can naji tace
"he'll love her too" fatu da ta kasa boye farincikinta ta ruqunqume
lubna tana daria kamar ance yau za'a kaita gidan sultan. Sai da suka natsa tace
"anty lubna tnx alot Allah ya bar mini ke" "Ameen" ta bata
amsa tana murmushi. Kiran sallah la'asar yasa suka farga dat its time. Lubna ta
shiga bandakinta ta hadawa fatu ruwa a bathtub turarukan wanka naga ta diga a
ciki, tayi alwala ta fito, ta bawa fatu towel ta shiga bathroom din yayinda ita
kuma ta fara sallah. 15mins ta dauka tana dirja jikinta kamar yau aka haifeta😉
kana tayi alwala ta fito, zani da hijab lubna ta bata tasa tayi sallah, daga
nan ta feshe jikinta da body spray ta shafa humra da kulacca duk na lubna, nan
da nan dakin ya dau asirtaccen kamshin da komin gulmanka bazaka gane me da me
aka hada ba. Wani swiss lace red nd black naga lubna ta dauko ta bawa fatu ta
saka, fatu tace "na taho da kayana fa" "ban taba saka shiba, ko
DJ bai san da zaman shiba, jst ki saka" ba musu ta karba ta saka, kamar a
jikinta aka dinka, figure 8 dinta ya fito tarr, zaunar da ita lubna tayi akan
kujera ta fara tsara mata make up, dauri ta kafa mata wanda yasa gashinta ya
fito ta tsakiya ya kwanta a bayanta, Qara feshe ta tayi da wani turare mai
sanyin kamshi, tace "done! Kallon kanta tayi a mirrow, ita kanta tasan
tayi kyau bana wasa ba, kamar wata amaryan da za'aje dinner, qaran phone dinta
ya katse kallon qurilla da take yiwa kanta, sultan nagani a screen din, dauka
tayi ta kashe murya tace "Hello" sultan da yake kusa da motarsa yayin
saurin dafawa don yanda muryan ya kashe masa jijiyoyin jikinsa, "hey"
ya fada a sanyaye, ya cigaba "gani zan fito yanzu, kina gida ne in biya mu
tafi tare? Sai data ja aji tace "nop, ina gidan yanzu haka" yace
"ok gani zuwa" ya kashe wayan. Tsayawa nayi na qare masa kallo yau,
dogo ne amma ba can ba, kuma da alama yana motsa jiki, fuskarsa irin na fulani
sak, dogon fuska, manyan idanuwa, dogon hanci da bakinsa dan daidai, ga saje
daya zagaye fuskar da quarter million suka qara qawata shi, gashin kansa kamar
na fulani Aww ashe fulanin ne, black ga santsi a kwance. Fatar jikinsa Brownie
ne kuma ba chocolate ba, daka ganshi kasan hutu da kudi sun zauna hade da
kwanciyar hankali. Half jumfa ne a jikinsa na dakakkiyar shadda mai launin
blue, takalmin shi da agogon shi black, ya hadu ne iya haduwa Dan Fulanin.
Motarsa ya shige sai gidan jameel.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:38PM, 7/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu ta kalli lubna tace "he's on his
way" jinjina kai lubna tayi ta fara magana "ki kula kiyi duk abunda
ya dace, zan fita in nemo mijina nima" daria suka sanya dukansu, hijabi ta
sanya ta fice a gidan a yar qaramar motarta, a waje ta hadu da sultan sukayi
gaisuwan light ta harba titi shi kuma ya shige gidan maigadi ya rufe gate. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Da sallamansa ya shigo falon fatu data
bashi keya ta juyo a kasalance ta amsa sallaman, daskarewa yayi a gurin yayinda
ita kuma take jefanshi da malalacin murmushi tace "ka shigo mana"
samun kanshi yayi da bin umarninta, a 1sitter ya zauna yayinda ita kuma take
2sitter suna fuskantar juna, bai taba ganinta haka ba gyale ko hijab ba sai
yau, manyan idanunshi sexy ya zuba mata
kamar yau ya taba kallonta, kunya ce ta rufe ta ta dago ido tace "kai
yayana wannan kallon" bai sani ba bakinshi ya furta "u luk
gorgeous" "tnx" ta furta mishi. Tashi tayi tace "mutanen
gidan basa nan bari in dauko maka ruwa" a hankali take tafiya wanda ya
bawa sultan daman kare ma bayanta kallo, tana shigewa kitchen ya jijjiga kanshi
yace "control sultan, control" saisaita kanshi yayi ya gyara zama
yana tunanin ta ina zai fara mata magana, bai gama shawara ba ta fito da tire a
hannunta ruwa ne da cups sai juice, nan dinma kura mata ido yayi har ta iso ta
jawo centre table kusa dashi ta ajiye kana ta sunkuyo yanda dole ya shaqi
kamshin jikinta, tace "wanne za'a zuba maka? Sultan da ya lula shaqar
kamshinta ya kuma shagala da kallon kirjinta yace "na'am" sarai tasan
abunda yake kallo amma ta nuna bata ganeba cikin ranta kuma tace ka kalla
halalinka ne. Miqewa tayi tsaye ta qara maimaita masa tambayar da sauri yace
"juice" don yasan dole ta tsaya shaking dinsa kafin ta zuba masa
hakan kuma na nufin shaking din abunda yake son kallo Murmushi tayi ta dauki
juice din ta shaking dinsa daga tsaye ta sunkuya tana saka masa a cup, tana
gama sawa ta koma gurin zamanta shi kuma ji yayi inama tayita tsiyaya masa har
gobe, kodai yace ta saka mishi ruwa ne? "Control sultan" ya fada a
sanyaye ya dauki kofin yasha kadan ya ajiye. "As u said kana son
ganina" fatu tace dashi yayinda take harde
kafuwanta, yace "ehh" tace "gani to".<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:38PM, 7/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sunanta ya kira "Fateema" tsikar
jikinta ne ya tashi tace "na'am" yace "magana ce tafe dani very
important" yayi shiru tace "ehen i'm ol ears" yace "fateey
tun ranar da na fara ganinki nake jinki cikin raina _love at first sight_ da
tunaninki nake kwana dashi nake tashi, nayi amfani da lokacin da muka dauka tare
don mu shaqu nd to knw more about each other" fatu da tun daya fara magana
kanta na qasa naga murmushi ya subuce a fuskarta, "fateey" ya kira
sunanta a hnkali, dago idanunta tayi suka sarqe cikin nashi "I'm really
madly deeply in love with you fateema" Da sauri ta sauqe kwayar idonta
yayinda wani siririn hawaye ya biyo kuncinta, na rasa gane na farinciki ne ko
ko! Shiru tayi, zufa ne ya fara keto masa ba dai tana da wanda take so ba!
"Fateema ko kinada wanda kike so ne? Ya fada cikin tashin hankali. Kada
mishi kai tayi alamar a'a. "Bakya so na ne? Talk to me fateema, idan bakya
sona zan iya jiran har lokacin da kikaji kin fara sona, shirunki kan iya sa
jinina ya hau pls talk to me" ya qarasa maganar yana dafe kanshi da yaji
yana barazanar tsagewa. Lura da yanayinsa yasa tace "Ina buqatar time nayi
tunani" yace "zuwa yaushe? Tace "ko nan da 2 weeks" yaqe
yyi 'wanda masu iya magana suka ce mugun kuka' yace "kiyi hakuri na baki 5
hours, zan kiraki anjima in d nyt" zatayi magana ya tari numfashinta yace
"kiji tausayina please" ya langabar da kai kaman qaramin yaro dolenta
yasa tace "to Allah ya kaimu" yace "Ameen matata" daria
tayi tace "tun kafin inyi tunanin? Kana gaggawa" shima darian yayi ya
mance ciwon kan daya fara damunshi dazu yace "I knw tunaninki zai kasance
positively" daga nan suka bige da hira yana sako maganan soyayyarshi tana
basarwa. Kiran sallan da aka fara ne yayi daidai da shigowan lubna da jameel
sai darawa sukeyi, ganin fatu ta sultan yasa sukayi kasaqe suna kallonsu,
sultan tadi yayi tadi ya dawo 2sitter inda fatu take sai hiransu suke. Gyaran
muryan jameel yasa suka farga yace "sannunku" fatu tayi saurin daukan
gyalenta ta yane jikinta sultan kuma ya miqe yace "ai sai muje sallah ko,
tunda kaji ana kira" bai kula darian da jameel ke mishi ba ya fita daga
falon shima jameel ya bishi suka wuce masallaci yana tsokanarshi wai akan
yarinya ya dawo parrot.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Suna fita lubna tace "mutumiyata ya
akayi" labarin yanda akayi fatu ta bata duka. Kallon sama lubna tayi tana
murmushi tace "sai nan da 4 days zamuyi move din mu na biyu" fatu
tace "na fara tsoro anty lubna, anya bazai..... "noo insha Allah babu
abunda zai faru sai alkhairi, mu hada da addu'a" Daga nan suka shiga daki
sukayi sallah suka girka simple abinci mara nauyi, ana kiran isha sukayi sallah
bayan sun idar ne su sultan suka dawo. Lubna tasa fatu ta qara gyara fuskarta
sai dai wannan karon da gyalenta suka fito falo, abinci suka fara ci wanda fatu
duk a takure take yayinda lubna, Jameel da sultan ko a jikinsu, suna qare cin
abincin Jameel da lubna suka rako su bakin mota, inka gansu sai sun burge ka, a
gaba ta zauna suka tafi.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Suna isowa gida tana kokarin budewa ya sa
lock tayi tayi ta bude ta kasa, kallonshi tayi ya zuba mata sexy eyes dinshi
yana murmushi, anan ta gane shi yasa
lock, da shagwaba tace "amma ka wahalar dani, Allah na dauka yaqi buduwa
ne" kwaikwayanta yayi yace "ai ban gaji da kallonki bane" daria
tayi tace "kai ko? Bude mata yayi yace "sai na kiraki, kar kiyi
bacci" "ok" tace yayinda ta fita ta maida marfin motar, daga
mishi hannu tayi alamar bye amma bawan Allah yaqi tafiya, har cikin zuciyarta
take jinjina irin son da sultan ke yiwa fateema. "Allah ka barmin
mijina" ta furta a hankali ta shige cikin gida, shima sai daya ga
kulewarta yayi ajiyan zuciya yace "Allah ka taimakeni" kana ya wuce
gidansu.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[4:05PM, 7/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu na shiga gida ta samu farouq na kallo
ya mata oyoyo tace "har yanzu bakayi bacci ba? Yace "yau
saturday, remember? Ba skul gobe"
tace "yess hakane, ina mummy? Yace "tana falon daddy" tace
"ok, bari in shiga in watsa ruwa".<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Wanka tayi ta sa sleeping dress ta dora
hijab kana ta fito palour, ganin mahmud a zaune kusa da farouq wanda har yayi
bacci yasa kirjinta dukan uku uku! Tun dawowan shi yake tsare ta da tambayoyi
yana so yasan daga cikin wani gida take a familyn nasu, answers da take bashi
basa gamsar dashi kuma akwai alamun rashin gaskia a tattare a ita, _real
lawyer_ 😄. Rufin asirinta daya shine after walima na gama karatunshi ya
fara aiki a abuja, ba kowanne weekend yake dawowa ba, duk randa ya dawo kuma
bata bari su zauna su kadai, in kuma suka zauna zai fara tambayoyi, in mummy na
kusa sai tace "mamuda nan fa ba kotu bane da zaka dame yarinya da
questions, distant relative ce baza ka ganeta ba" To yau kam qaryanta ya
qare tunda ba mummy mai rufe bakinsa. Murmushi ta qaqalo tace "ahh mutan
abuja sauqar yaushe" murmushin shima yayi yace "dazu da yamma, kina
fita na shigo, naje gidan jameel din ma na samu kuna maganarku ke da matarsa,
so bana son katse muku sai na tsaya, da naji bamai qarewa bane yasa na
tafi" cikinta ne ya bada sautin qulululu... kirjinta na bugawa da sauri da
sauri tace "m..me..me.. kaji? Murmushin cin nasara yayi ya qara narkewa a
cikin kujeran yace "abunda kuka gama magana akai" Shiru tayi fuskarta
na qasa tace "can u kip a secret?" bai motsa daga kwanciyar ba yace
"yess, amma ina son details" briefly ta fada masa abunda ya dace, ta
qarisa maganar da cewa "promise me babu wanda zaka fada wa" daria
yayi yace "ni banida gulma, bincike na iya" daria sukayi dukansu hkan
yayi daidai da shigowan mummy tana cewa "oya farouq kallon ya isa haka
kaje ka kwanta" ganin su fatu yasa ta yin shiru Tace "fateema kin
dawo? Fatu tace "eeh mummy, anty lubna tace a gaisheki kuma tana godia da
kunun aya" da murmushi a fuskar hajia tace "madallah, mahmud dauki
farouq ka kaishi dakinsa" Mahmud na haurawa tace "fateema akwai
matsala ne? Naga mahmuda yana damunki da tambayoyi" murmushi fatu tayi
tace "babu komai mummy, munyi magana dashi" hakan yayi daidai da
dawowan mahmud mummy tace "to asuba ta gari, fateema ki locking kofa ki
kashe wuta, na tafi" suka mata sai da safe ta wuce side din daddy.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">5mins ya qara shima ya mata sai da safe,
kopa ta kulle ta kashe wuta ta wuce dakinta. Tana hawa gado ta lalubo wayarta
ta kira xahra "badai kinyi bacci ba? Fatu tace da ita xahra wacce da alama
tayi nisa da baccinta tace "8:30 ma ina kan gado" fatu tace "ok
dama labari zan baki amma tunda kin fara bacci sai da safe" da sauri xahra
ta miqe zaune harda kunne bedside lamp tace "bani in sha, wallahi na
tashi" daria sosai fatu tayi tace "shegen son labari"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:37PM, 7/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Labarta mata yanda akayi duka tayi. Shiruu
xahra tayi can tace "anya wannan plan din babu hatsari a ciki, kar garin
neman gira a rasa ido fa" itama fatun shiru tayi xahra ce tace "are
you there? "Yess" fatu ta bata amsa ta cigaba da cewa "insha
Allah ba matsala, ki tayani da addu'a, Allah ya zaba mana mafi alkhairi"
"Ameen" xahra tace suka cigaba da tattaunawa daga baya sukayi
hanging.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Missed calls din sultan ta gani kusan goma
a screen din wayarta tace yaushe ya kirani? (Har yanzu dai sabin shiga ne) Wani
kiran ne ya qara shigowa ta dauka tace "hello" bai amsa ba ya watso
mata tambaya "da waye kike waya? Ina kiranki ana cewa call waiting"
murmushi tayi kaman yana kusa da ita tace "levels ne fa, ka koma lafiya?
Shima murmushin yayi yace "lafiya lau, ya maganar mu? Tace "wacce
kenan? Shiru yayi kaman bazaiyi magana ba, a kalla babes sun kai goma shima
yana musu irin tambayan nan cikin jin kai, amma reshe ya juye da mujiya yau shi
ake yiwa! "Answer na dazu, u said zakiyi tunani" fatu tace "ok,
na tuna" yace "ina jinki" shiru tayi yayinda shi kuma ya qagu
yaji matsayinsa a gurinta, gani yakeyi in ya rasa fateema duk matar da ya aura
baza ta samu soyayyar da yake yiwa fateema ba. Sunanta ya kira "fateey,
kinyi shiru" sai da ta dauki 5seconds kana tace "yess, Allah ya zaba
mana mafi alkhairi" farinciki fal a fuskarsa yace "u mean kin amince?
Tace "yeah". Hira suka yi cikin wayewa da natsuwa, sai da sukayi
30mins yace "ya kamata in barki haka kiyi bacci, amma ban gaji da jin
sweet voice naki ba" qanqame wayar tayi a kunnenta tana lumshe ido ta qara
qasa da murya tace "okay, gud nyt" yace "nyt dear, karki manta
kiyi addu'an bacci" tace "ok tnx" sallama sukayi. Suna kashe
wayan fatu ta tashi ta dauko pic dinsu tare da kudin sadakinta ta qura musu
ido, kuka ne ya kwace mata tayi mai isarta har bacci ya dauketa. Sultan kuma
yana ajiye wayan yace "saura fatu" murmushi yayi ya fara danne dannen
laptop akan business dinshi. Yau kimanin 4days da fara soyayyarsu, in kaga
yanda suke love sai ka aza sun shekara, wani zazzafan soyayya sultan yake
nunawa fatu, yayinda itama take nuna masa bata da kowa like him. Haka da yamma
zaizo ya dauketa suje yawon shaqatawa su sha hiransu ya dawo da ita, ga
shopping niki niki. Wata rana kuma a gidan jameel zasu yi hiran, sai dare ya
dawo da ita, nan ma sai an qara bata time kafin ta shiga gida. *love kenan*
Mummy ta lura da hakan ta kira fatu tace "meke faruwa tsakaninki da
sultan? Cikin jin kunya tace "wai mummy sona yakeyi" murmushi mummy
tayi tace "kefa? Kina sonshi? Rufe fuska fatu tayi hakan yasa mummy ta
gano answer dinta, "Alhamdulillah" mummy ta furta a hankali, tace
"kin fada mishi matsayinki a gurinshi? Da sauri fatu tace "a'a mummy
ba yanzu ba, kuma zan fada mishi da kaina in lokaci yayi" mummy taso ta
gane wani abu amma ta basar a cewarta tunda suna son junansu shykenan. Ranar da
suka cika 5 days suka hadu a gidan jameel. Hiransu sukeyi gwanin ban sha'awa,
lubna ne ta fito da pics ta rarraba musu suna kallo, na daria suyi daria, na a
bada labari a labarta, caraf a cikin pics din dake hannun fatu taga hotonsu
itada sultan, turo baki tayi tace "honey wacece kusa da kai haka? Ta wani
manne maka! Ta qarisa maganan tana miqawa lubna pic din, lubna na karba tace
"laa fatu ce, uwargidan sultan" sultan da tunda fatu ta fara magana
notinan kanshi ya sunce, ji yakeyi kaman ya rusa ihu, shikam fatu ta cuce shi,
a 'yan kwanakin da yayi da fateema ya lura tana da kishi, yanzu in tasan fatu
matarsa ce ya zaiyi. "Innalillahi" yayinda fatu ta miqe tsaye tana
dafe kirji "lubna matarsa fa kika ce".......<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:51AM, 7/31/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu ta juyo da kallonta gurin sultan tace
"matarka? Pls kace wasa ne" bai dago ya kalleta ba zuciyarsa na
tafarfasa, ya dafe kanshi yayi shiru, lubna ta miqe tayi daki dama jameel yana
gurin aiki. "alama ya nuna gaskia ne kenan, ya Allah" juyi tayi ta
cigaba "ashe yaudarata kakeyi? Na dauka kai mutumin kirki ne ashe ba haka
ba ne, why me sultan? Jin muryanta kaman tana kuka yasa ya dago da kanshi,
hawaye ne ke sintiri a fuskarta, ji yyi bazai iya ganin su suna zuba ba, kamo
hannunta yyi ya zaunar da ita a 2sitter shima ya zauna, still hannun su na
cikin na juna, yace "aure aka min amma bada son raina ba, ke kanki kinsan
ke kadai nake so, ki fahimceni" juya masa baya tayi tana share hawaye tace
"na fahimta amma ka sani ni bazan zauna da kishiya ba, kaje ka zauna da
matarka, Allah ya baku zaman lafiya" cikin kidimewa ya juyo da fuskarta
yace "what? Yanzu fateema zaki iya rabuwa dani? Wallahi bana sonta ko
kadan kuma nakusa zuwa in bata takardar ta, nima bazan iya zama da villager
irinta ba" wasu zafafan hawayene suka sauqo wa fatu yayinda wani baqin
ciki ya turnuqe ta, wato itace villagern!!!
daukan hoton tayi ta yayyaga kuci kuci, ta zubar a palourn tace
"maza duk halinku daya, jiki da kwalliyan mace kuke bi, baku damu da
kamala ba, karka qara taka inda nake" ficewa tayi a gidan ta barshi zaune
a gun yana jin radadin maganarta. Shi a iya saninshi mace bata taba hararansa
balle ta gaya masa magana. Me take nufi da kalamanta? Tattara pieces na pic din
yyi yasa a small dustbin din da yake falon, shima ya fita daga gidan. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu kuma tana fita ta tari keke napep ya
kaita gida, tana shigowa palour Allah yaso ba kowa ta haura upstairs zuwa dakin
ta, zaman yan bori tayi a tsakiyar room din tacigaba da kukanta. Meyasa mazan
ynzu basu damu da addinin mace da kamun kanta ba? Sunfi son wayayya yar boko wacce
ta dace ta zauna a gaban mota kuma ta nunawa duniya? Meyasa taimako da tausayi
yayi qaranci wanda har ana raba zumunci don son zuciya da kyale kyalen duniya?
Tayi alqawari muddin ya saki fatu to bashi ba ita har abada, kallon kanta tayi
a mirrow, me ya qaru a jikinta kuma me ya ragu? Gayu da gogewan da tayi yake so
ba ba ita ba. "Villager" ta furta ta qara rushewa da kuka, ita tayi
setting din draman amma ya dawo mata real life, a tunaninta zai so matarsa fatu
ita kuma ta fada masa gaskian wacece ita! But sai hakan bai faru ba, miqewa
tayi kaman wanda aka tsikara tace "yanzu inya sakeni ya zanyi? Ni fatu ya
zanyi" zuciyar ta taji na mata quna, hakan yasa ta kwanciya akan gado tana
aukin zubar da hawaye har bacci yayi gaba da ita.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:54AM, 7/31/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sultan gidansu ya nufa kai tsaye yayi
hanyar garden a can ya zauna. Maganar gaskia yana son fateema amma wani gefe
guda kuma yana jin bazai iya sakin fatu ba, don da zai iya da tuntuni ya aikata
hakan tun bayan aurensu da 1month, a lokacin ya fara mata aika mata kudi, yaso
ya rubuta amma zuciyarsa ta haneshi da aikata hakan, a baki kawai yake fada
amma shi kanshi yasan ko yaya zaiyi bazai iya ba. "Shes quit nd
innocent" daukan wayarsa yayi ya turawa fateema text....<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">_ban yaudareki ba kuma bana fatan hakan ya
taba faruwa, duk da bana sonta 'yar uwata ce kuma marainiya, I dunno what to
do, bana jin zan iya sakinta, amma please ki daina batun rabuwa dani, I cnt
take it fateema_<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tsawon minti goma da turawa ba'a masa reply
ba, hakan yasa yace "bata huce ba har yanzu, ya kamata na bata
lokaci"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu na tashi daga bacci kusan bayan
la'asar tayi wanka da sallah, yanzu kam ta daina jin qunar da zuciyarta yake
mata, wayoyinta ta dauko ta fito palour, ba kowa kamar mummy ta fita unguwa
farouq kuma yana islamiyya, a kitchen ta tarar da dija na yankan kayan miya
suka gaisa dija tace "ya na ganki kamar bakida lafiya? Fatu tace
"kaina ke ciwo, ina mummy? Tace "tana gidan hajia sadia, a zubo miki
abinci ne? Fatu tace "a'a kiyi
aikinki zan zuba" daukan plate tayi ta zuba tuwon shinkafa ne miyar ugwu
yasha kifi da nama sai kamshi yakeyi, spoon ta dauka ta fito daga kitchen din,
a dinning ta zauna tafara cin abicinta, wayarta ta dauka sai a sannan taga text
din sultan, fuskarta ba yabo ba fallasa ta ajiye, tana gama cin abinci takai
kitchen ta dawo falo ta kunna data wayarta, mssgs na sultan ta gani duk na ban
hakuri, ta karancesu tsaf ta kashe data ta kunna kallo amma hankalinta baya kai
sai tunani, a haka mummy ta shigo tayi sallama bata jita ba, sai da ta taba ta
sannan ta juyo a dan tsorice, ganin mummy ne ya sata fara'a tace "sannu da
dawowa mummy" Mummy ta kalle ta fuskarta da damuwa, zama tayi tace
"fateema lafiyanki kuwa? Idan akwai abunda ke damunki ki fada min, karki
boyemin komai I'm ur mum" kanta ta kwantar akan kafadan mummy yayinda
hawaye masu dumi suka biyo fuskarta tace "mummy nayi missing din gida ne,
tunda nazo banje ba haka kuma banji daga garesu ba" shafa kanta mummy tayi
tace "karki damu, in kin kusa komawa skul zakije musu, saboda akwai abunda
nake so in aiwatar kafin kije" <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[12:04PM, 7/31/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Yau saturday ya kama ranar da sultan zaije
garin modibbo, da kyar da lallami yasa jameel ya shirya ya rakashi, wayarsa ya
dauka ya turawa fatu text,<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">_yau zan tafi garin modibbo, pray for me_<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sai daya tura kuma yaji haushin kansa, yau
kusan kwana uku bata daukan wayarshi bata amsa text dinshi, ko yazo ya aika ta
fito bata zuwa, rabon daya ganta tun ranar da lubna ta kopsa masa, amma hala
kawai ko abinci zaici sai ya mata text, zuwa unguwa da sauransu, amma bata kula
shi. Shiga mota yayi ya zauna yana jiran jameel ya fito daga gidansa. Fitowa
jameel yyi tare da lubna sai wani mannewa juna sukeyi suna I miss u, I miss u,
haushi ne ya cika sultan ya danna horn da karfi wanda yasa suka dawo cikin
hayyacinsu, tsaki jameel yaja yace "mallam zaka kashe min kunnen
yaro" ko kulashi baiyiba, yanashiga yaja motar suka fara tafiya.
Tittitititi alamar shigowan saqo da sauri sultan yaja birki wanda yasa jameel
tsorita shi ya aza ma sun buge wani ne, da sauri Ya dauki wayan ya duba saqone
daga fatu<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">_ka gaisheta_<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> Shine abunda ya gani, wato duk mssgs dinshi
tana gani wannan ne kawai taji zata amsa? Jameel wanda har yanzu zuciyarsa bai
daina bugu ba yace "amma kai dan iska ne sultan, wannan wani irin ganganci
ne zaka tsayar da mota cikin sauri haka? Kuma akan wata kake qoqarin kashe mu
duka? Da mamakin shi sultan murmushi yake yi yace "srry dude, na
love" jameel bai iya qara cewa komai ba don tsananin mamaki, shi ko ada da
yake cewa in soyayya ya kama sultan zaisha wahala to bai taba zaton abun zai
kai haka ba. "This is madness" sultan ya kunna motar yace
"indeed". A haka suka kama hanyan kumo, jefi jefi sultan na bude
saqon yana dubawa, da jameel yaga abun yayi yawa yasa ya karbi driving din,
sultan yayi ta gwada calling fatu ko zata dauka amma taqi dauka, daya gaji ya
hakura. Fatu kuma yau levels ta kawo mata ziyara, a daki na gansu suna zaune
akan gado, fatu tayi wani _silent_ kamar marainiya xahra na bata baki "bai
kamata kisa damuwa a ranki, duk da nasan its hardly ace baki damun ba amma
gaskia ki sassautawa zuciyanki, addu'a zaki cigaba dayi, ki barwa Allah komai,
kinji kam? Fatu da alama bata jin abunda xahra k fadi don wayarta take dannawa
a hankali, kwace wayar xahra tayi pics din sultan take kallo, ido xahra ta bita
dashi yayinda fatu ta gyara kwanciyarta ta bawa xahra baya, "ehh lallai
babyn nan wato ni na zauna ina baki shawara kin maida ni bi ta can ko? Kinata
kallon mijinki" tashi xahra tayi ta dauko laptop din fatu da sultan ya
saya mata wai na karatu tace "me ma pasaword din? Sarai tasani amma ta
tambaya _"SULTAN"_ fatu ta
bata amsa, daria xahra tayi tace "soyayya ko wahala" ta cigaba da
danne dannen ta har ta samu film din da take so ta fara kallo. Fatu kuma tunani
ne fall a ranta na abunda zai faru in sultan ya isa ya tarar fatu ta fita
nemansa months back!!!<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[12:06PM, 8/1/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Basu sha wahalan gane gidan ba duk da dan
sauyin da aka samu kusan shekara da rabi, yau ma a kofar gida suka samu mal
Ameenu yana zaune da wani mutum suna magana. Tun dosowar motar mal Ameenu yake
kallonta duk da bashi sultan ya taba zuwa da ita ba amma yana kyautata zaton
yau fatu tazo da mijinta. Nesa dasu kadan suka parking yayinda suka fito kowa
da dan murmushi a fuskarsa, ganinsu yasa mal Ameenu fadada fara'arsa kaman an
mishi bushara, yana leqen bayansu yaga ta inda zaiga *FATUN BIRNI* Kawu muntari
da yake gefen mal Aminu yace "baba, ko dai maigidan fatu ne yazo? Gyada
masa kai yayi saboda sun iso, sallama sukayi aka amsa musu suka sami guri akan
babban tabarman suka zauna, kaka yace "muntari shiga gida ka samo musu
ruwa" kawu muntari ya tashi da sauri ya shiga gida. Gaggaisawa sukayi
cikin mutunci kaka bakinshi yaqi rufuwa sai hamdala yakeyi yace "ai na aza
da ita zaku zo, ashe ku kadai ne" Jameel yace "na'am baba" don
bai fahimci maganar ba sultan ma haka. Kaka ya cigaba da cewa "bbu abunda
zance maka sultanu sai Allah ya maka albarka, yasa ka gama da duniya lafiya,
wato naji dadin wasiqarka, shekara da auranku baka zo ba, nayi tsammanin ko
baka son hadin da aka maka ne, har na fara maganan raba auren ganin yanda aka
fara surutu a kauyen nan, mutane sunyi gaskia da suka ce 'mai hakuri shi kan
dafa dutse har yasha romonsa' nan din ma hakan ya faru, ranar da kayi aika ta
hadu da mal usman a hanya ya bata saqon kamar kullum" kallonsu kaka yayi
da fara'ar da har ynzu bata bar fuskarsa ba, daga jameel har sultan sun zuba
mishi ido, ya cigaba "wasiqan da na gani a ciki yasa na dauka ko ka
sauwaqe mata ne, data karanta muka gane" daria kaka yayi amma babu wanda
ya tayashi don gabadaya kansu ya daure, sun rasa inda maganarshi ya dosa,
fitowan muntari yasa jameel cewa "me ya rubuta" muntari yace "rubutawa
sultanun yayi cewa fatu ta bishi gombe zai yiwa mamarsa bazata, ko ba haka kace
min ba baba? Kaka ya amshe "ehh" muntari yace "ai naso inje aga
gurin da kuke din saboda ziyara, amma fatun tace ita kadai kace taje" tari
ne ya sarqe sultan yanayi ba kakkautawa ruwa aka miqa mishi yasha sannan ya
tsaya idonshi har yayi jaa, Jameel ne yayi qarfin halin qaqaro murmushi yace
"haka fa, abun zai kai wata nawa ma? Daga kanshi yayi kamar mai son tunowa
muntari yayi caraf yace "wata takwas ai ko" kiran sallah azahar da
aka fara yasa sukayi shiru kowa da abunda yake saqawa a ransa, sai da aka idar
mal Ameenu yace bari a kawo muku buta kuyi alwala, shiga gidan kaka yayi da
kawu muntari aka barsu su kadai, a sannan ne sultan ya dubi jameel da tsananin
damuwa a fuskarsa don a yanzu sun gane komai daya faru yace "ina cikin
duhu jameel" girgiza kai jameel yayi yace "ita ta rubuta wasiqa kace
taje, tun wata takwas da suka wuce kuma da alama har yau bata dawo ba, sultan,
fatu ta bata" shiru sukayi sultan ji yakeyi kamar ya kurma ihu ko zaiji
sassauci a zuciyarsa, _FATU TA BATA! IDAN MAL AMEENU YA GANE BATA TARE DASHI YA
ZAIYI? IDAN MAHAIFIYARSHI TAJI ABUNDA YA AIKATA HAR HAKAN YA JANYO BACEWAR YAR
QANWARTA YA ZAIYI? SHIN FATU TANA RAYE? IDAN TANA RAYE TA INA ZAI FARA NEMANTA?
TA INA?_ Tambayoyin da suka cika brain
din sultan wanda babu wanda zai iya amsa
mishi, ji yayi zuciyarshi na zafi yana ganin duhu duhu, hakan yayi daidai da
fitowan kaka da muntari suka ajiye buta miqewan da sultan zaiyi yaji kanshi
yayi nauyi ya zube a qasa.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[6:48PM, 8/1/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">8</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">"Innalillahi wa inna ilaihir
rajiun" abunda kowannensu yake furtawa kenan sukayo kanshi, jameel ne ya
shiga jijjiga shi yana "sultan, sultan ka tashi" yama manta cewa shi
doctor ne, ruwan buta yasa aka miqo masa ya yayyafa masa, ajiyar zuciya mai
qarfi ya sauqe kafin ya bude idonshi a hankali yace "ina fatu? Ganin zai
qara magana yasa jameel saurin cewa "mu daga shi mu kaishi mota, dole sai
an kaishi asibiti" mal Ameenu da yake da salallamai a gefe yace
"muntari tayashi ku dauke shi, maza maza" hannayensa suka saka a
kafadunsu suka kaishi mota kaka na "ashsha Allah ya bashi lafiya" yana
girgiza kai. Suna sakashi a mota yana cewa "ina fatu? Ina fatu? Jameel
yayi saurin shiga driver sit ya kunna motar, yana tunanin yanda zasu fara nemo
fatu, tunawa da yayi cewa fateema ta yaga pic din fatu da suke dashi yasa yayi
saurin fitowa daga motar ya samu kaka fuskar shi gwanin tausayi muntari na cewa
"baba, sai cewa yakeyi ina fatu fa" alamar akwai matsala kenan, kaka
na ganin jameel bai ko saurari muntari ba yace "jikin ne? Ko dai a qira
madam nasi (nurse daya da suke dashi a qauyen) ta dubashi? Jameel yace
"a'a nima doctor ne, fatu yake son gani, in akwai hotonta a bani"
kaka cikin jimami yace "kayya wannan wani irin cuta ce? Fatu bata daukan
hoto sai hoton ta daya da aka dauketa tana shekaru uku" da azama jameel
yace "a bamu" kaka yayi saurin shiga gida muntari ya mara masa baya,
shi kuma jameel ya koma gurin sultan a mota. Yana isa ya samu sultan ya fara
dawowa hayyacinsa yace "yarinyar nan tana son kashe ni, tana jawomin
matsala a rayuwata ta koyaushe, ina take? Bubbuga bayanshi jameel yakeyi yana
cewa "be strong, be strong dude, zamu nemota insha Allah, I'm with u"
jameel kaman ya fadawa kaka batan fatu amma yana hango tsananin tashin hankalin
da zasu shiga in suka ji labari shiyasa ya shirya qaryan cewa sultan nason
ganin hoton ta ne, fitowa kaka yayi muntari na binshi a baya kamar jela, da
sauri jameel ya isa gurinsu ya karbi hoton tare da cewa "mungode, amma
dole sai mun dangana da asibiti" muntari yace "to wani irin cuta ce
wannan da zaisa mutum suma ya tashi da son kallon matarsa? Kaka ne ya harare shi
kana ya maida kallonshi kan jameel yace "ai ya kamata ku hanzarta tafiya
kafin wata matsala ta kunno" sallama sukayi jameel ya koma mota, ya samu
sultan ya dafe kanshi yace "ka rage tunani sultan don kar ka jawowa kanka
matsala, zamu nemota duk inda take" motar yaja suka tafi suka bar kaka
cikin daurewan kai, meke faruwa ne?<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu na kwance kamar wacce aka tsikara ta
tashi tace "xahra akwai matsala" xahra tasa pause ta juyo tace
"a ina? "Yanzu idan suka je suka fadawa kaka bana tare dasu wallahi
hankalinshi zai mugun tashi dama gashi da hawan jini, yanzu ya zanyi? Ido xahra
ta qura mata tana tuna maganar fatu da take cewa rayuwarta kamar a film, wannan
shine asalin film. Kafin xahra ta bude baki fatu ta sauqo daga kan gado ta
dauki gyalen dogon rigan da yake jikinta ta yafa kawai tace "tashi muje
gidan lubna, kaina ya daure, ban san me zanyi ba, zata fini sanin ya
za'ayi" daukan gyalenta xahra ma tayi suka fito a palour suka tarar da
mummy sukace zasu je gidan lubna, tace Allah ya kiyaye a gaisheta.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Suna fita daga garin sultan yace "taya
zamu nemota bayan bamu san inda ta nufa ba, kuma ko hotonta bamu dashi"
Jameel ya miqa mishi pic din da kaka ya bashi ya qurawa hoton ido kaman tana
kama mishi da wata daya sani, tunawa da cewa ya taba ganin fatun yasa yabar tunanin,
yace "wannan fa tana yarinya ce, ina wanda ka dauke mu? Jameel bai masa
magana ba, tunowa da cewa fateema ta yaga yasa yayi zugum yana kallon dajin
Allah. Suna shigowa gombe yace "jameel muyi gidanka" haka suka iso
kowa da tunanin da yakeyi, ko gama parking jameel baiyi ba sultan ya bude ya
fita da sauri jameel ya qarisa parking din ya biyo bayanshi "whats wrong
sultan? Ina!! Already ya shige. Ko tsayawa kallon wadanda suke palourn baiyiba
ya wuce gurin da dustbin yake ya juye a qasa.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:28PM, 8/3/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">9</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Ba fatu kadai ba har lubna da xahra
mamakine a fuskarsu, tsintan pieces na
pic din sultan ya fara yana ajiyewa a gefe, jameel ne ya shigo ya tsaya a
kanshi yayinda su fatu ma suka matso suna ganin ikon Allah. Sai daya gama
tarawa ya kwashe, yazo zai wuce ta kusa da fatu, tsayawa yayi yana kallonta
itama ta tsura masa ido, har ta fara tausaya masa ganin a yini daya har ya fara
susucewa, kawar da kanta tayi shima ya wuce bai ce mata komai ba, zama yayi a
kujera ya jawo centre table ya baza pieces din ya fara jerawa, jameel ne ya
zauna kusa dashi ya dafa kafadarshi yace "sultan" bai kalleshi ba
yaci gaba da jerawa amma ko kadan basu jeru ba don kuci kuci suke, gumin da
yake hadawa ya diga akan wani piece yayi saurin gogewa hakan yasa abunda yayi
qoqarin hadawa kusan minti 10 ya wargaje, watsa nakan table din yayi a qasa ya
dafe kanshi, ya kwantar da kanshi akan kujera, jameel da yake gefenshi yace
"kayi addu'a sultan" addu'o'I ya fara idonshi a rufe yana dafe da
kanshi. Jameel ne ya fara basu labarin abunda ya faru tun zuwansu, yana
qarisawa sultan ya tashi zai fita, jameel ya tareshi yace "ina zaka je? Ka
huta tukun" girgiza kanshi yayi yace "zanje gida ne, ka kai hoton
gidan tv a fara cikiyanta don Allah, da gidan radio please" yana gama
maganarshi ya fice, jameel yabi bayanshi. Lubna ta juyo da dubanta gurin fatu
wacce take danna wayarta alamar bata da matsala tace "fateey ya kamata ki
fada mishi kece, kiga fa yanda yake qoqarin zaucewa" tsayawa tayi da danne
dannen tace "dadina daya da basu bayyana wa kakana ba" xahra tace
"u have to talk to him" tashi tayi ta tsaya tace "a'a ba yanzu
ba" murmushi tayi tacigaba "na zauna tsawon shekara daya cikin
zullumin inda mijina yake, nayi kuka, nayi addu'a, duk inda nabi mutane magana
sukeyi anacewa ga bazar bazar, wato mace mai aure amma ba miji, kaka ya hana ni
fita, haka na zama tamkar mujiya, cikin gidan ma ba'a barni ba, goggo asabe
cikin gaya min baqaqen maganganu take" juyo da dubanta tayi kan su xahra
tacigaba "duk akan waye na sha wannan bakin ciki? Akan sultan, dalilin
cewa ni baqauyiya ce, wacce bata waye ba, ban dace dashi ba" lubna tayi
ajiyar xuciya tace "bawai na raina halin dakika shiga bane, a'a kinaji
yanda DJ ya fadi abunda ya faru, har suma fa yayi" murmushi fatu tayi tace
"babu abunda zai sameshi, xahra mu tafi" sallama sukayi wa lubna suka
wuce gida, ita lubna har ta fara tausayawa sultan, fatun ma ta tausaya mishi
amma tayi alqawarin saiya horu tukun, tana son nuna mushi dan adam ba abun
wulakantawa bane, kuma cewa "kare ma yanada rana, balle mutum dan adam mai
tunani da hankali"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[4:13PM, 8/5/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fitansu suka wuce gidan tv bayar da
cikiyan, ba qaramin daru sultan ya tayar musu ba kan sunce bazasu karbi hoton a
matsayin wanda zasuyi cikiyar ba, A cewarsu suna buqatan hoton ta na yanzu,
yanda jama'a zasu ganeta, da kyar suka karba ganin yana neman daga musu
hankali, suka ce zasu saka amma ba dole bane jama'a su gane ba. A gidan radio
ma hakan ya faru sun buqaci a fada musu kamanninta da shekarunta, kamannin
Jameel ne yayi guessing ya fada shekaru kuma sultan yace "17 noo 18"
kallon mamaki ma'aikatan suke binsu dashi, ace yazo a masa cikiya amma
bashida cikekken details. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A hanyansu ta dawowa sultan yayi shiru yana
tunanin abunda zai faru gaba, don shi gani yakeyi fatu ta mutu ko kuma an sace
ta, gani yakeyi baza a taba ganinta badon wata takwas ba wasa ba, yanzu me zai
cewa mammin sa, yanda take muradin ganin qanwarta da zuriyarta, akan son kai
irin nashi ya saka mafarkin mahaifiyarshi bazai taba zama gaskia ba. Hawaye
naga ya gangaro a fuskar sa, yayi saurin gogewa don kar jameel ya gani, Yace
"jameel nayi kuskure kuma nayi nadama, daa na yarda da qaddaran auren
yarinyar nan daa haka sam bai faru ba, nayi wa mammi alqawarin nemo mata
qanwarta, amma sai gashi ta dalilina da selfish mind dina nayi sanadiyyar
bacewar the one nd only blood din aunty na. Ban san a wani hali yarinyar take
ciki ba, ko tana raye ko ta fada hannu mara kyau I dunno, jameel Allah zai
kamani akan hakkin fatu, tana matsayin matata shekara da wata takwas ban
waiwayeta ba" muryan shi ya fara rawa hawayen da yake qoqarin boyewa ne ya
silalo, jameel ya kalleshi ya girgiza kai cikin tausayawa, sultan ya cigaba da
magana bayan ya share hawayen "jameel da na dauki shawararka tun bayan
auren da ban shiga matsala yanzu ba, yarinya ce fa, she's just 17 a lokacin,
tana kuka ina fada mata maganganu marasa dadi, kamar qanwata take fa, qanwata
ce kuma matata" gyara zamanshi yayi idonshi na hawaye yacigaba "ban
san wani hali kakanta da mummy zasu shiga ba in har ba'a samu yarinyar nan ba,
ban san da wani ido zan kalle su in musu bayani ba" Zai qara magana jameel
ya dafa kafadarshi yace "its ok, ka rage damuwa sultan, za'a sameta da
yardar Allah"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:17PM, 8/5/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sun shigo unguwan jameel yace "mu wuce
gidana muci abinci ne? Sultan yace "ka kaini gida kawai, nikam na
koshi" gidan su sultan ya nufa, a haraban gidan yayi parking ya fito amma
sultan yaqi fitowa, gani yake yana shiga mammi zata karanci abunda ya faru!
Jameel ya bude masa kofa ya jawo hannunshi ya fito dashi kamar mara lafiya, a
palour gidan ya zaunar dashi ya fara kwalawa amrah kira, amrah da take dakinta
ta amsa ta fito ta gaishe shi ta dubi sultan da ya wani sanyi dashi kamar
maraya tace "ya sultan bashida lafiya ne? "Ehh, ki kawo mishi
abinci" tace "too" ta wuce kitchen, dai dai nan mammi ta fito
daga dakinta tana waya, ganin sultan cikin wani yanayi da bata saba ganinshi
ciki ba yasa tace da wanda take wayan "zan kiraki anjima" ta kashe,
jameel ya gaisheta hankalinta na kan sultan da yake binta da ido kamar yau ya
taba kallonta (yayi laifi yana tsoron duka😆) Tace "meya sameka
_manga_? Runtse idonshi yayi, ji yakeyi kamar ya fada mata laifin daya aikata
na wasa da rayuwar abunda take muradin gani. Jameel ya ari bakinshi yace
"kanshi ke ciwo mammi kuma bai ci abinciba, a bashi paracetamol in
yaci" amrah ta fito da tray a hannunta ta ajiye a qasa tace "inyi
serving ne? Mammi tayi saurin cewa "ehh" jameel ya musu sallama ya
tafi gidanshi cike da tausayin halin da abokinshi yake ciki, Amrah ta zuba masa
a plate jalof na spaghetti da irish potato yaji kifi, da kyar ya yadda yaci don
sai da mammi ta bata rai tukun, magani ta ballo masa ta bashi dolenshi yasha ba
don zai yaye mishi matsalan da yake ciki ba. Yana gamawa mammi tace ya tafi
dakinshi ya kwanta ko na 30mins ne. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Su fatu na isa gida suka wuce dakinta,
tunanin fatu daya yanzu kuma, kar magana ta fito mummy taga laifinta, shiru
tayi tana tunano halin da tabar mijin nata ciki, xahra ta buge ta tace
"kinyi abu yana damunki, ko a yanzu sultan ya jijjiga, abeg karki sashi
kwanciyar asibiti, kinsan ajeebo ne bai saba da damuwa ba" harara fatu ta
watsa mata tace "eeyee tunda ni kuma ajeebako ce na saba da damuwa sai in
tausaya mishi ba? Levels tace "ba haka bane qawas, lamarin duniyan nan in
kowa yace zai rama abunda aka masa fa baza'a zauna lafiya ba, kuma hakuri yana
da kyau, ko yanzu ya gane kuskurenshi kuma yayi nadama, shawara nake baki"
tana gama fada ta shige toilet. Kogin tunani fatu ta fada 'tana son mijinta sosai, tana son kasancewa
tare dashi, amma yini daya yayi kadan a cikin horon laifin daya aikata' ajiyar
zuciya ta sauqe ta rafka uban tagumi, alamar an bude kofa yasa tayi saurin
sauqe tagumin, xahra na fitow tace "ni zan tafi gida" rakata tayi mal
habu ya maida ita, fatu ta dawo gida cikin damuwa, kitchen ta nufa tana taya
dija aiki don rage yawan tunani.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:14PM, 8/7/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sultan a room dinshi ya kasa samun sukuni,
ya kai gauro yakai mari, tunaninshi ina fatu zata iya zuwa a nan garin, tuno
maganar jameel yayi ranar da aka daura musu aure suna hanyan dawowa.... jameel
ya miqa mishi pic yace "ga pic dinka" ko kallonshi baiyi ba yace
"don Allah mallam ka barni, duk kai ka jawo min, ka wani saurin amsawa
kamar kai za'a aurawa ita, gaskia ni baka min dai dai ba" girgiza kai
jameel yayi yace "yarinyar nan tana da nutsuwa ga hankali, baka san
alkhairin da ke tattare da auren nan ba, nine kai daukanta zanyi ta zauna a
matsayin matata har lokacin da naji na fara sonta, koda ban sota ba zan zauna
da ita saboda yar'uwata ce kuma zan iya qara aure nan gaba, ni dai na bata
address na gidanku idan baka zo ka dauketa ba zata biyoka" yana tunawa a
lokacin haurawa sukayi sosai akan wai jameel yana masa katsalandan a rayuwa
"don meyasa zaka bata address dina? Baka taba bata min rai irin haka ba
jameel" dawowa daga tunanin yayi yace "may be tazo nan" da sauri
ya fita gurin maigadi yana kwala masa kira Iliya ya fito daga bandaki da gudu
yace "yallabai gani" yace "wata takwas da suka wuce wata mace
tazo nan gidan tana nemana? Daga kai
iliya yayi yace "babu wacce tazo nemanka sai wannan yarinyar sharipa da
kace kar in kuskura in barta ta shigo, ita ce take zuwa lokaci lokaci nemanka,
wallahi yalla.... sultan ya katse shi yace "ba ita na tambayeka ba, babu
wacce tazo kamar yar kauye kauye haka? Iliya yace "a'a yallabai, sai dai
yar aiki da hajiyayya ta kawo kwanaki, naji ita ke share maka daki. Juyawa
sultan yayi da sauri cikin gida, a palour ya tarar da mammi da amrah na hira,
lokacin yamma yayi liss, mammi ta kalleshi tace "sultan ya kaji jikin?
Yace "da sauki" don shi har ya fara tunanin ko larai mai gyara masa
daki itace fatu, yace "mammi ina larai mai gyara mini daki? Mammi tace
"amrah kira min ita" da sauri amrah ta tafi kiranta. Mammi ta dawo da
dubanta gurin sultan tace "manga wani abu ta maka? Girgiza kai yayi yace
"a'a tambaya zan mata" mammi tace "to" nan amrah ta shigo
larai na binta a baya a tsorice Allah yasa ba laifi tayi ba, kallonta yayi,
yayinda ita kuma ta durkusa a gabansa jiki na bari tace "gani ranka shi
dade" alama ya mata data miqe, da sauri ta miqe amma kanta na kasa,
kallonta yayi yana tuno kamannin fatu, fatu fara ce wannan kum baqa, fatu
kyakkyawa ce wannan kuma masha Allah😁, fatu yarinya ce wannan kuma da
alama ta haihu 7, sai dai rashin jiki da tsayi wanda in baka ganta da kyau ba
zaka ce yarinya ce. Tsaki yaja yace "jeki kawai" zama yayi a kujera
yayi shiru Mammi da take kallon show din tun daga farko tace "sultan
lafita kuwa? Ka kira mata kuma baka ce mata komai ba, me yake damunka ne yau
din nan? Kallon amrah yayi yace "kije dakinki zanyi magana da mammi"
ba musu ta wuce dakinta. Zamowa yayi ya zauna a kasa kusa da kafafun mammi yace
"mammi ki yafe mini, na miki laifi"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[7:30PM, 8/8/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Kallonshi mammi tayi cikin rashin gane me
yake nufi, tace "me ka mini sultan? Ina jinka" qara sunkuyar da kansa
yayi ya fara bata labarin tun daga farko har karshe, anan yace "ki gafarce
ni mammi wallahi son zuciya ne ya kaini da aikata haka, nasan nine silan
bacewarta, zan nemo miki ita a duk inda take mammi" ya qarisa maganan
yayinda yake riqe da kafafuwanta, shock mammi ta shiga, Kasa magana tayi don
ranta yayi mugun baci, hawaye ne ya gangaro daga idonta, 'wannan wani irin
rashin hankali sultan yayi? tashi tayi zata tafi, sultan da yake riqe da
kafanta ya dago ya kalleta, hawayen daya gani a fuskarta yasa hankalinshi qara
tashi, magiya ya fara yana kuka yana bawa mammi hakuri, kwatar kafanta tayi
bata ce dashi komai ba ta shige dakinta, shirun mammi yayi yawa, shi da dukansa
tayi ko ta masa fada amma shirunta na nufin abubuwa da yawa har da 'kar in qara
kallon fuskar ka' tashi yayi ya fita yana share hawayen da baisan lokacin da
suke ambaliyan fitowa ba, in ka ganshi sai kace yayi sati a kwance, duniyar gaba
daya yaji ya fita a kansa, idan yau akace an samu fatu to duk soyayyar duniyan
nan zai dora a kanta, "where are you fatu" ya furta yayinda ya fice
daga gidan zuwa masallaci sallan maghrib. Yana idar da sallah ya shige motarshi
ya dinga bin unguwa unguwa ko Allah zaisa yaga fatu, a wata unguwa yayi sallahn
isha, ya samu limamin mosque din yace a tayashi da addu'a matar shi ta bata,
Limamin ya mishi alqawarin tayashi addu'a, yawo ya cigaba dayi, idan yaga masu
neman taimako sai ya taimaka misu, bai dawo gida ba sai kusan 11, abunda bai
taba yi ba. Yana shigowa yaga kiran abbanshi ya dauka yayi sallama aka amsa
mishi, abba yace "kazo palour na ina son ganinka" cikin girmamawa
yace "too abba, gani nan". Da sallama ya shiga ya samu mammi ce da
abba zaune, kallon mammi yayi ta dauke kai, daka ganta zaka san tana cikin
bacin rai. Gaishe su yayi mammi taqi ta amsa, abba ne ya fara magana
"Mahaifiyarka ta sameni da magana wanda banji dadinsa ba ko kadan, hakan
da kayi ka nuna cewa kayi girman da mu iyayenka babu ruwanmu da sha'anin
rayuwarka, abunda kayi niyya shi zakayi, kusan shekara biyu da aura maka mata
amma mu iyayenka bamu da masaniya, baka kyauta ba ko kadan" sultan da
kanshi ke qasa tun da abba ya fara magana ya samu bakin cewa "nayi kuskure
abba, kasa baki mammi ta yafemin"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:09PM, 8/8/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Nasiha sosai abba ya mishi kana ya kalli
mammi yace "hajia sadia kinsan sha'anin yara da rashin hankali, kiyi
hakuri yayi nadama" kasa furta komai tayi, alama abba ya mata da ido yasa
tace "naji, wani mataki ka kai na nemo ta? Sultan da yaji sanyi a ranshi
yace "na bayar da cikiyanta a gidan Tv da radio, insha Allah za'a
sameta" jinjina kai mammi tayi tace "Allah yasa" tambayoyi abba
ya mishi ya bashi amsa sannan yace "kaje ka kwanta, zan nemeka gobe akwai
abunda za'ayi" da farinciki sultan ya musu sai da safe ya fita. Abba ne ya
fara bawa mammi baki sai daya tabbatar ta rage damuwa sannan suka kwanta. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sultan na shiga dakinshi ya shiga wanka,
bayan ya fito ne ya saka kayan bacci daukan wayanshi yayi, ya lalumi aljihun
rigan daya cire ya fito da pic din fatu tana 3yrs, inka ganta kaman baby doll,
taci kaya masu ado an mata jagira ga jan farce an mata diqo dashi a goshi,
tasha kwalli rambadadau, bakinta ne da alama ba'a mishi kwalliya ba don pink
ne, zura mata ido yayi yace "sweet matata yar rigima, kina bani
wahala" nan take ya tuno da fateema yace "sai na samu fatu zan dawo
kanki" daukan pic din yayi a hoto ya postin a facebook, twitter, da duk
wani chat da yakeyi yace "duk wanda ya ga mai kama da ita yar 18yrs ya
fada masa, akwai kyauta ga duk wanda ya sameta" <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu tana gama Taya dija aiki ta wuce
dakinta, tama rasa me zatayi, gashi ba makaranta balle karatu ya debe mata
kewa, chattin ta fara tana karanta novels anan taci karo da sabuwar littafin
BEBEELO 'HANNE 💣' daria takeyi tace 'lallae hanne kin cika bomb' kiran
sallahn maghrib yasa ta tsaya da chattin ta wuce tayi sallah, farouq ya shigo
dakinta yace "anty fateema ki bani laptop dinki inyi game" ya
rausayar da kanshi, linke sallaya da hijabin tayi ta ajiye akan bedside drawer
ta kamo hannunshi suka zauna akan gado tace "baka ce please ba" kama
kunnenshi yayi yace "ok please kinji? Murmushi tayi tace "zan baka
amma sai munci abinci tukun" washe baki yayi yace "nagode" taja
hancinsa tace "u ar wlcm" hira suka yi har aka kira sallah isha,
farouq ya tafi mosque ita kuma ta kabbara nata, bayan ta idar ta sauko palour
ta tarar da mummy a palour da alama itama bata jima da fitowa ba, fatu ta mata
sannu mummy tace "Yau kuma kin zama matar daki" murmushi tayi tace
"na fito dazu kina daki ne" sallama farouq da mahmud sukayi suka
shigo, fatu ta fadada fara'ar tace "oyoyo mutan abuja" daria yayi
yace "inda wata bata taba zuwa ba" fushin wasa fatu tayi tace
"anji, nima watarana zanje" mummy tace "kyale shi, kuje kuci
abinci, dadynku ya dawo daga mosque ne? Ta tambayi mahmud, yace "nidai
tahowan mu mun barshi da abban amrah a haraban masallacin" "ok"
mummy tace ta tashi ta wuce side din daddy. Fatu suka wuce dinnin tayi serving
dinsu sai wasa da daria sukeyi ita da mahmud, yana ce mata yar qauye. Bayan sun
gama ne ta tattara takai kitchen ta dawo palour suka qara bude babin wani
hiran, farouq ya tuna mata alqawarinta tace yaje ya dauko laptop din a daki,
bayan ya dauko ta cire masa password din ya fara game suka cigaba da hiransu.
Kusan 10 mummy ta shigo tace "farouq kaje ka kwanta" dama ya fara
gyangyadi, ya tashi ya tafi dakinsa, su fatu suka mata saida safe ta wuce side
din daddy. Sabon hira suka bude anan fatu tace "yau baka ga sultan ba?
Yace "na ganshi, ana idar da sallah ya fice a motarsa, kamar ma bashida
lafiya" daria fatu tace "yaje garin modibbo ne ya samu bana can shine
ya shiga tashin hankali harda suma" zaro ido mahmud yayi yace
"yaushe? Murmushi qarfin hali tayi tace "yau" gyara zama yayi
yace "kin sanar dashi ne? Girgiza kai tayi alamar a'a. Mahmud yace
"karki dau alhakinsa fa madam" tace "bazai kai har can ba"
dauko wani zancen sukayi na case din da ya gama abun daria abun haushi yana
bata labari, su ne basu tashi ba sai 11, bayan ya fita ta kulle kofa ta haura
upstairs zuwa dakinta, wanka tayi tasa kayan bacci ta dauki wayarta ta bude
data mssgs suka shigo, updates din sultan ne ya bata daria da tausayi, tace ya
kamata in masa jaje, typing ta fara masa.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:14AM, 8/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">
_Allah ya yasa a ganta cikin sauqi, ya kuma kare na gaba._<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Abunda ta tura mishi kenan, yana cikin
ganin comments din mutane yaga na Fateemah Mahmud da sauri ya karanta, yaji
dadin jajen da ta masa, a zuciyarsa yace she loves me.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">
_Thanks alot baby_<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Murmushi tayi tace duk randa ka gane nice
fatunka akwai drama.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Kashe data tayi ta kwanta amma ta kasa
bacci, tunanin mijinta kawai takeyi ko a wane hali yake ciki sai Allah, rungume
pillow tayi tana aukin tunanin sultan dinta har bacci barawo ya saceta.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sultan yaga bata qara masa reply ba a
ranshi yace da sauran aiki kenan, ganin dare ya tsala yasa ya shiga toilet ya
daura alwala ya fara nafilfili, Allah yasa a ga matarshi fatu.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Washe gari haka ya tashi duk jikinshi na
mishi ciwo saboda rashin bacci da bai samu ba jiya, hatta idonshi sai da suka
kumbura. Misalin 8:12am ya shiga palourn abban nashi, samu yayi mummy na jera
abinci akan dinning table duk jikinta a sanyaye, ganin yanayin danta yasa ta
tausaya mishi, gaisheta yayi ta amsa ba yabo ba fallasa, tace "sultan kayi
bacci kuwa jiya? Shiru yayi tace "magana nake maka" ya dago da kanshi
yayi yaqe yace "nayi mammi" bata yarda ba don daga ganinshi bashida
kwanciyar hankali. A daidai nan abba ya fito yana daura agogo a hannunsa, mammi
ta isa ta tayashi, sultan ya gaishesa, abba yace "kaci abinci kuwa?
"A'a, na koshi ne" ya bashi amsa, "kaji mini shiririta, rashin
cin abincinka zai warware maka matsala ne, zo nan ka zauna kaci abinci, hajia
zuba masa" Zama sukayi duka akan dinning table din mammi ta zuba masa
dankali da kwai ne sai ferfesun zabuwa wadda yaji kayan hadi, ga ruwan lipton a
gefe, mammi ta tashi zata tafi abba yace "kefa? Tace "ba yanzu zanci
ba" dukansu suka bita da ido yayinda ta fice daga falon, sultan kamar yayi
kuka, abba ya girgiza kai ya fara cin nasa amma sultan sai jujjuya fork din yakeyi
cikin abincin, ganin haka yasa abba yace "idan kaci akwai good news"
sultan ya kalli abban nashi, shi kuma ya masa murmushi, cin abincin ya fara don
yasan good news a yanzu bai wuce ace an fara tracing inda fatu take ba, yaci
abinci sosai. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Suna gama karyawa abba da sultan suka fice
daga gidan, driver ne yayi driving dinsu a motar abban nashi, a hanya abba yake
fada masa zasu je gidan commissioner ne a watsa masu nemo fatu saqo saqo na
gombe a binciko inda take, hatta local govs sai an bincika, dadi ne ya cika
sultan, don yana mai fatan Allah ya karbi addu'arshi ya takaita mishi wahalan
nemo fatu, gidan suka je aka musu iso nan da nan don abban nashi sananne ne,
kuma commssnr abokin shi ne. Bayan sun gama gaishe gaishe abba ya masa bayanin
abunda ke tafe dasu, cmmssnr yace "alhaji za'a sa a nemota, kuma ya kamata
a fadawa su iyayen yarinyar don watakila ta gurinsu a samu wani haske"
abba yace "tashin hankalin da zasu shiga muke tunani, basu da kowa anan
garin da zata iya zuwa can" magana suka cigaba dayi ta yanda za'a bullowa
al'amarin. Basu tashi ba sai da suka gama tsara yanda za'ayi komai, Sukayi
sallama driver ya ajiye abba a office, sultan kuma ya koma gida. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu ta tashi washegari wasai abunta, bayan
sun karya ne farouq ya fita wasanshi a cikin gida, suka zauna a palour da mummy
suna kallon wani indian series jefi jefi suna hira. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:21AM, 8/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> Sultan na dawowa gida ya tarar da mummy a
dakinta ta zuba uban tagumi yayi sallama ta amsa, yace "mammi...."
daga mishi hannu tayi tace "bana son jin komai daga gareka sultan, idan
kana son kaga farinciki na ka kawo min fatu, ban taba tunanin bakada tausayi
irin haka ba, yar uwarka ta jini ka barta cikin wahala da uquba don kawai an
aura maka ita? Ka tashi ka bar mini daki" tashi yayi ya fita yana share
hawaye ashe mammi ba yafe masa tayiba? <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Gefen mammi tana tausayin danta amma
kowanne second ta tuno bacewar fatu wanda ta dalilin sultan ne sai taji bakin
ciki mara misaltuwa, share siririn hawayen daya zubo mata tayi tace "Allah
ka bayyana fatu a duk inda take" <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Yana fita kai tsaye ya shiga motarshi
maigadi ya bude masa gate ya fita, motar jameel ya hango ta nufo shi parking
yayi a bakin hanya jameel ya qara gaba kadan shima yayi, tare suka fito jameel
ya nufo shi yayinda sultan ya jingina da motarshi, gaisawa sukayi jameel yana
lura da shi yace "sultan yaya dai" yace "na fadawa mammi
komai" Da sauri jameel ya kalleshi cikin tashin hankali yace "why?
Meyasa baka bari har sai mun nemo fatu ba? Baka tunanin mammi zata shiga wani
yanayi? Yanzu mebya faru? Sultan ya fada masa yanda akayi jameel ya girgiza kai
yace "daa ka nemi shawarata tun farko bazaka fara fada mata ba, yanzu abun
ya zame maka biyu, ga neman fatu ga tunanin halinda mammi take ciki"
sultan yace "gani nakeyi kowanne daqiqa laifina qaruwa yakeyi, gani nakeyi
rashin fada mata da wuri zaisa ta tsaneni, gani nak......." "its
ok" jameel ya tareshi yana bubbuga kafadunshi Qoqarin shiga motarshi ya
fara jameel yace "ina zaka je? Shiga yayi ya kunna motar yace gidan tv and
radio" jameel yace "kace min abba yayi magana da cmmsnr" yace
"ehh, bamusan ta ina za'a ganta ba, yafi a bawa ko'ina muhimmanci"
jameel yace "ka jirani in ajiye motata a gidanku in fito" kallonshi
sultan yayi yace "jameel kar in daura maka wahala" yace
"damuwarka tawa ce, what are frnds for? Shigar da motarsa yayi gidansu
sultan kana suka tafi. Sunje amma babu alaman nasara haka suka dawo gida jiki a
sanyaye nan ma jameel na kwantar masa da hankali, hannayensa ya dora akan
steering yace "ka fadawa mammi zan nemo mata fatu, zan zo tare da fatunta,
da daina fushi dani" jameel da bai gane nufinshi ba ya fita daga motan
yana qoqarin zagayawa ya budewa sultan, kafin ya ankara har sultan yayi reverse
ya fice a gidan da gudu. Yayi Saurin shiga motarsa yabi bayanshi amma ko
alamarsa bai gani ba, ya nema sa duk inda yake zaton zai samesa amma babu
labarinsa, hankalinshi yayi mugun tashi don za'a yi biyu babu yanda ya fita da
gudun nan komai kan iya faruwa dashi, naushin steering yayi ya furzar da iska,
ji yakeyi kaman shima yayi kukan, da sauri ya lalubo wayarshi ya dialing number
sultan amma 'switch off' sauran numbers din ya gwada suma duk a kashe, cikin
tashin hankali ya nufi gidansu sultan.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Ayi hakuri da rashin jin FATU kwana biu,
qanwata aka yiwa aiki a tayamu addu'a Allah ya bata lafiya da duk marasa lafiya
Ameen. Masu jaje ta group, ta private har masu kira a waya nagode muku da nuna
kulawa, Allah ya saka da Alkhairi👏🏽👏🏽. Luv u
all😘😘<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[8:48PM, 8/19/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Da sauri jameel ya shiga gidan kai tsaye ya
shiga falo, a zaune ya samu mammi ta qurawa tv ido wanda daga gani hankalinta
baya kan kallon. Sallama yayi ta amsa da guntun murmushin ta, ganin yanayin
fuskar sa yasa tasha jinin jikinta tace "jameel lafiya? Sai da ya zauna ya
gaisheta a gurguje ta amsa tace "ya na ganka haka? Baka jin dadi ne?
Girgiza kai yayi yace "mammi sultan ya fita cikin wani yanayi, na kira
layukanshi duk a kashe, kin tsananta fushi a gareshi, ina gudun kar ayi biyu
babu mammi" tashi tayi tsaye tana "innalillahi wa inna ilaihir rajiun"
ta dauki wayarta da yake kan kujera a gefenta ta dialing number abba, sanar
dashi tayi ta qarisa maganan tana hawaye Abba bai ce komai ba ya katse wayar,
gwada layukan sultan yayi duk a kashe, baiyi wata wata ya dawo gida, a palour
ya tarar da jameel zaune ya zuba uban tagumi, mammi kuma sai safa da marwa
takeyi tana ta kiran sultan a waya amma baya shiga,<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tana ganinshi tayi saurin zuwa gurinshi
gaba daya hankalinta a tashe, tace "ka sameshi? Bai mata magana ba ya
maida dubansa gurin jameel daya cire tagumin yana gaishe sa, abba ya amsa shima
fuskarsa cike da damuwa yace "jameel me yake faruwa ne? Jameel ya kalli
mammi tukun abba yace "fada min komai ba matsala" jameel ya kwashe
duk yanda akayi har abunda mammi ta yiwa sultan da safe ya fada masa,
"kinga irinta ko? Yanzu kam kinji dadi ai, meyasa ku mata bakwa tunani
kafin ku aikata abu?" Abba ya fadawa mammi yayinda takaici ya gama rufesa,
ganin haka yasa jameel ya musu sallama ya dauki motarsa ya fice a gidan ya
shiga gidansu.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">"Sadia na miki magana akan yaron nan,
kina ganin halinda yake ciki amma kika qara masa akan hakan! Na samu ya fara
walwala, dazu gidan commissioner muka je don a nemo matar tashi, mun gama tsara
komai, lokaci daya kin bata komai, sai ki fada min waye za'a fara nema"
mummy da ta fara hawaye tun dazu tace "kayi hakuri, wallahi naso danne
zuciyata amma laifin da sultan ya mini yayi nauyin da bazan iya boye fushi na
ba" abba yace "idan wani abu ya samu sultan....." nan wayarshi
ta fara ringin ya dauka.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:37PM, 8/20/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">8</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Gaisawa sukayi da wanda yayi masa wayan,
mutumin yace "don Allah da ahaji rufa'I nake magana? Abba yace "ehh,
shine" gefe daya akace "idan kanada spare key na motar danka kazo nan
ebele road its an emergency" abba bai tsaya tambayan meya faruba yace
"gamu nan zuwa" don yasan bai wuce ace sultan yayi hatsari kuma motar
taqi buduwa ba, ya dubi mammi ta cikinta ya gama kullewa tana kallonshi a tsorice
tace "alhaji lafiya? Qin fada mata yayi yace "ana nemana a office
ne" bai saurari me zata ce ba yayi fita. Zama tayi a kan kujera gabadaya
hawayen ma ta nemesu ta rasa, idan wani abu ya samu tilon danta sultan ya
zatayi? Sultan da amrah kadai suka rage mata cikin 'yayanta duk sauran daga
tayi miscarriage ko kuma suna jarirai su rasu, gashi Allah ya saka mata son
'yaya, shi yasa take neman zuriyar mahaifiyarta itama tace ga nasu sun tara
'yaya masu yawa. Zufa ne yaketa keto mata ta ko'ina, tana son tashi tabi bayan
abba amma ji takeyi kafafunta bazasu dauketa ba, anan ta samu hawaye ya fara
zuba, a haka amrah tazo ta sameta tace "mammi, mammi meya sameki? Share
hawayen mammi tayi tace "babu komai amrah, kaina ke ciwo" a sanyaye
ta tashi ta shige dakinta, amrah tayi zugum tana tunanin me yake faruwa ne a
gidan daga jiya zuwa yau, don daga mammi har sultan yanayinsu ya sauya sosai,
akwai abunda yake faruwa amma kowa yaqi ya fada mata. (Kai fatu, kinsa mutane
da yawa a cikin damuwa) Mammi na shiga daki ta kira layin abba amma bai dauka
ba, tayita kiransa shiru, hakuri tayi ta zauna kawai tana addu'a Allah ya dawo
mata da danta lafiya. Abba na fita ya wuce dakinsa ya dauko key din, bai ko
saurari driver ba yayi driving da kansa zuwa ebele road, kiran layin mutumin
yayi ya masa kwatancen inda suke, nan da nan ya isa gurin amma baiga alaman
anyi hatsari ba, asalima motar a parkee take a gefen hanya ga mutane sun
zagayeta, da sauri abba ya isa gurin zuciyarsa na fada masa ciwo yayiwa sultan
yawa ya mutu, duk dauriyansa sai da zuciyarsa ta karye ganin danshi sultan
cikin mota kanshi akan steering babu alaman numfashi a tattare dashi bai kula
mutanen da suke masa magana ba ya bude motan gaba daya jikinshi a mace, ya jayo
sultan, taimaka mishi wani mutum yayi suka maida shi baya yayinda abba ya shiga
driver sit ya kalli mutumin daya tayashi yace "kaine ka min waya? Mutumin
yace "ehh nine alhaji" abba yace "shiga muje" suka wuce
asibiti dama already ya locking motarsa daya taho da ita.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Jameel na shiga gida ya samu ba kowa a
falo, ya zauna jagabb a kujera Fatu ce take sauqowa daga steps tana waya, taci
makeup ga kayan jikinta sun amshe ta, da qaramin jakanta yayi matching da
takalminta tana cewa "ke dallah yanzu ma haka ina qoqarin shiga mota
ne" tana sauqowa suka gaisa da jameel a ranshi yace 'bakisan halinda
masoyinki yake ciki ba' yace "ina mummy? Tace "ta fita unguwa
dazu" Yace "kefa" tayi murmushi tace "wollah zanje birthday
party na qawata ne xahra levels" yace "hala bakida labarin am nemi
sultan an rasa ko" miqewa yayi zai tafi fatu da ta zama statue ta yi
saurin qarisa gurinshi kamar zata shige jikinshi tace "yaa jameel meya
samu sultan dina? Ina yake? Tana maganar ne yayinda hawaye ke sintiri a
fuskarta kamar famfo, jikinta har rawa yake gaba daya ta fita a hayyacinta kowanne
pore na gashin jikinta gumi yake fitarwa "kamin magana yaa jameel"
ganin bashida niyyan magana yasa ta fita da gudu, ya kwala mata kira yayi
saurin bin bayanta.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[1:04PM, 8/21/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">9</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A haraban gidan ya sameta tana kokawa da
kuban gate, (ta manta akwai qaramar kofan fita), yayi saurin qarasawa gurinta
yana kiran sunanta "fateema, fateema! Ta juyo tana kallonshi amma bata
fasa kokawar ba, yace "ki nitsu, idan har kina son jin inda yake.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Abba na isa asibiti aka gangara sultan
emergency, likitoci uku ne a kansa suna faman nemo numfashinsa, abba ya zauna
akan chair yayi tagumi, bakinsa na motsi a hankali alama addu'a yakeyi, wayarshi
ce ta qara ringing bai duba ba don yasan mammi ce, bai san me zaice mata ba.
mutumin da abba yazo dashi yace "alhaji ayita addu'a insha Allah babu
abunda zai sameshi, zai fito lafiya" abba yace "Ameen, Ameen"
mutumin yace "ai muna zaune a shagon bakin hanya muka ganshi yazo da gudu
lokaci daya kuma yaja birki ya tsaya, shiru shiru bai fito kusan awa daya,
ganin haka yasa na tashi in duba ko lafiya, don na shaida motar, ai nima ta
unguwar taku nake amma a pantami, da naje na duba sai na kwankwasa glass din
motar, shiru shiru bai dago ba har yan majalisan mu suka taso suma suka zo,
anan dai suka tabbatar da cewa ba bacci yake yi ba, Shine na kira masinjanka
makwabcina ne, ya turo min numbern ka. Abba yace "nagode kwarai mal
dahiru" doctors minti 30 suka dauka akan sultan kafin suka samu
daidaituwar numfashin sa, dakin hutu aka kaishi don sunce yana bukatan hutu
sosai don jininsa ya hau, zai iya farkawa in da next 48hrs. Abba ya dade tsaye
a kansa yana tofa masa addu'a, kana ya fito bayan ya shaidawa family doctor
nasu ya kula mishi da danshi sultan sosai, mal dahiru yabi bayanshi yana cewa
"alhaji ya mai jikin? Yace "da sauqi Alhamdulillah" a haraban
hospital din abba yacewa mal dahiru ya shigo motarsa ya ajiyeshi a shago amma
yaqi, yace "alhaji zan hau mashin wallahi, iyalinka na jiranka a
gida" abba yace "to shykenan" ya dauko kudi mai dan tsoka
yabashi, mal dahiru sai godiya yakeyi har abba ya shiga mota ya fita daga
hospital din. Sai da jameel ya tabbatar ta nutsu kafin ya fada mata yanda ake
ciki, durkushewa tayi a gurin tana kuka mai tsuma zuciya, "duk ni na jawo,
nine na jawo" tashi tayi tana kuka make up din zuwa party ya cabe, ta fita
daga gidan, jameel ya dauka akan sabanin da suka samu tsakaninta da sultan ne,
jikinta ba kwari ta nufi hanyar fita, jameel ya tsayar da ita yace "bazaki
fita a cikin state din nan ba" komawa gida tayi ta zauna tana rabzan kuka,
ta rasa me zatayi? Tukunna ma ina sultan dinta??? Tashi tayi ta leqa falo ganin
jameel yasa ta tsaya, shi kuma qin tafiya yayi don kar a kuma baro wani aikin,
ba'aga fatu ba, ba'a san inda sultan yake ba, to in fateema ma ta fita wayasan
inda zata je? Layukan sultan ya qara kira amma shiru, ya kira na abba shi kuma
bai dauka ba, (Allah sarki, abba bai ma duba ba don ya dauka mammi ke kiransa)
yana son fita nemo abokinshi amma yana tsoron barin fateema ita kadai. Ya kusan
1hr kafin wayarsa ta fara ringin ya dauka.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Abba na dawowa ya gida kai tsaye dakin
mammi ya nufa don yasan hankalinta a tashe yake tana ganinsa kuwa ta taso yayi
saurin zaunar da ita yace "ki kwantar da hankakinki, an samu danki"
mammi wacce muryanta ya dashe don kuka tace "ya rasu ko alhaji? Abba yace
"yana nan da ranshi sai dai tension da ya masa yawa yasa jininsa ya hau,
yanxu yana asibiti zai farka nan da awa 48, tace "Alhamdulillahi, Allah
nagode maka, alhaji muje in ganshi" abba yace "a'a kiyi sallah azahar
tukun zai muje" ba yanda ta iya tace "to" abba ya fita daga
dakin zuwa side dinsa, sai a sannan ya dauko wayarsa ya duba missed calls ciki
harda na cmmssnr da jameel, a ranshi yace 'Allah sarki duk inda yake
hankalinshi shima a tashe yake, kiran jameel din abba yayi, yace "jameel
an samu sultan, yanzu haka yana asibiti" jameel ya miqe tsaye yace
"abba a ina aka sameshi, ya aka sameshi? Abba ya fada masa jameel yace
"Alhamdulillah, gani nan zuwa nima" fatu da take labe tana jiran
jameel ya fita itama ta fita neman mijinta tayi saurin sauqowa qasa har tana
tuntube tace "an same shi? Jameel wanda murna ya sakashi murmushi yace
"an sameshi, Allah abun godia" itama murmushin tayi idanunta cike
taff da hawayen murna ta sharce tace "muje in ganshi" jameel yace
"too"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:05PM, 8/21/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Motar jameel suka shiga, ya kunna suka fita
daga gidan zuwa gidansu sultan don abba ya fada mishi cewa sai sunyi sallah
azahar suma zasu je. A haraban gidan suka sami abba na magana da driver yace
"ka hau achaba na bar motana a ebele road gurin *FA'IZ PLAZA*" Abba
ya miqa mishi key din driver ya karba ya fita, har qasa fatu ta tsugunna ta
gaishe da abba, ita kunyan hada ido dashi takeyi don a dalilinta danshi ya
shiga wani hali, shiga cikin gida tayi tabar abba da jameel zasu je masallaci.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tana shiga falo babu kowa, zama tayi
kirjinta na dukan uku uku, tana son ta bayyanawa mammi cewa itace fatu amma
tana tsoron abunda zai biyo baya, don yanda mammi take son sultan baza taji
dadin abunda fatun ta musu ba, kusan minti biyar tana zaune gashi har an kira
sallah, amrah ta fito daga dakinta zata shiga dakin mammi, nan taga fatu zaune
a falo da uban tagumi, amrah ta kira sunan ta amma inaa! Hankalinta ya gama
tafiya, sai da ta matso sannan fatu ta juyo a tsorice, ganin amrah ne yasa ta
kwaqulo murmushi wanda iyakacin shi fatar baki tace "amrah" tace
"anty fateema lafiya" tace "lafiya lau" amrah tace
"mammi tasan kinzo kuwa? girgiza kai fatu tayi tace "a'a, nima ban
jima da shigowa ba" amrah tace "ki shiga dakinta mana" fatu tace
"a'a, kaini dakinki inyi sallah" amrah tace "to muje" a
dakin amrah tayi sallah tayi addu'a Allah ya tashi kafadun mijinta, tana gamawa
ta share hawaye a fuskarta ta koma falo, bata dade da zama ba mammi ta fito
tare da amrah kowa da shirin zuwa asibiti, fatu ta sunkuyar da kanta qasa ta
tsugunna ta gaishe da mammi, mammi tace "sai kika ji abunda ya faru ko?
Kasa cewa komai fatu tayi mammi tacigaba da magana "qaddara baya wuce
ranar sa, sai addu'a zamuyi Allah ya tashi kafadunshi" kuka fatu ta fara
har da sheksheqa, takaicinta daya, meyasa taqi bayyana kanta tun ranar da
sultan yaje ya samu bata nan? Gashi yanzu a dalilin ramuwarta mijinta da take
matuqar so yana kan gadon asibiti, muryanta a sarqe tace "ban kyauta
ba" mammi tausayin fatu ya gama cikata, tana son yarinyar sosai tana son
sultan ya aureta ko da an samu fatu, daga mammi har amrah bbu wanda ya gane
abunda ta fada, mammi ta isa gurinta ta dago ta daga tsugunon da tayi, ta kama
hannunta suka fito haraban gidan suka shiga mota, jameel yana driving yayinda
abba na gefenshi, mammi da fatu na baya amrah a tsakiyarsu. Fatu Hawayen dai
bai daina zuba ba, ta juya kanta gurin window tana cewa a ranta 'a yau kowa zai
san wacece ni! yau zan dawo fatu! Share hawayen tayi tana mai fatan ganin
mijinta ta bayyana masa kanta!!!<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:25PM, 8/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Suna isowa asibitin suka fito suka shiga
ciki har kofar dakin da sultan yake, anan suka tsatstsaya suna lekanshi ta
window don ance ba'a son a shiga, fatu ta leqa ta ganshi kwance ga drip an
daura mishi, ya wani haske ya rame, kuka ne yazo mata tayi saurin toshe bakinta
ta fita da gudu, mammi ta bi bayanta tana kiranta, abba ya girgiza kai ya nufi
office din dr, jameel da amrah kuma suka samu guri suka zauna cikin jimamin
abunda yake faruwa. A haraban hospital din mammi ta samu fatu akan bench a
karkashin wata bishiya tana zaune tana kuka, mammi ta zauna kusa da ita ta jawo
ta jikinta tana jijjiga ta, fatu tace "mammi kiyi hakuri na miki laifi,
nice na jawo halinda sultan yake ciki" ta qara fashewa da kuka, mammi ta
dagata tace "kul! Kar kice haka, bakida laifi ko kadan, nice mai laifi
fateema" fatu ta zamo daga kan bench din tayi knelling hannayenta nakan
cinyan mammi tace "mammi" mammi ta tace "na'am fateema, ki tashi
ki zauna, bana son ganin kina kukan nan, ki tashi" fatu ta girgiza kai
tace "mammi kinsan inda fatu 'yar qanwar ki take? Tuno da fatu yasa mammi
hawaye ta share tace "a'a fateema, kema kinsan abunda ya faru ko? Muna kan
nemanta" Fatu ta kama hannun mammi tace "nice fatu mammi, nice yar
qanwar ki rahmatu wacce kike nema mammi, gani gabanki ki mini duk hukuncin daya
dace dani" shock mammi ta shiga ta miqe tsaye tana nuna fatu da yatsa,
tace "kece fatu? Fatima yar qanwata? Yar mahmud da rahmatu? Fatu dake
still a durqushe ta daga kanta alamar ehh hawaye shabe shabe a fuskarta tace
"nice mammi, nice wallahi" tsayawa mammi tayi cikin tsananin mamaki
tana kallon fatu, wacce sai yanzu take ganin kamanninta dasu sultan da amrah,
"ashe ke dama jinina ce, shiyasa nake jinki har cikin raina, nake ganinki
tamkar yar dana haifa, Alhamdulillah" mammi ta fada yayinda take hawayen
farinciki, lokaci daya kuma ta canja, fuskarta ba alamar annuri tace
"meyasa kika kasa sanar dani tun baya??? Dago da kai fatu tayi ganin
fuskar mammi yasa ta firgita bakinta na rawa tace "m...mam...mi
walla..hi..." mummy ne ta qaraso ita da lubna cikin sauri don tun dazu
jameel ya kirasu ya fada musu, ganin yanayin fatu da mammi ya tabbatar musu an
bayyana wacece FATU A BIRNI....<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[11:22AM, 8/23/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Mummy na qarisowa ta daga fatu ta dora
kanta akan kafadar mummy tana hawaye abun tausayi mummy tace "its ok
daughter, its ok, ki daina kukan nan haka kar ya jawo miki matsala" mammi
da take kallonsu cikin mamaki kanta ya kulle, yaya akayi fatu tazo gidan hajia
kulsum? tace "hajia how comes fatu ta kasance a gidanki? Please ku cireni
a duhu, anya itace fatuna? Mummy tace "itace fatunki hajia, kar kiga
laifinta na qin sanar dake da tayi, lubna ku shiga ciki keda fateema zanyi
magana da hajia sadia" lubna taja hannun fatu suka shiga cikin hospital
din, mammi da mummy suka zauna akan bench din mummy tace "fateema bata da
laifi ko kadan mammin amrah, in har hakan laifi ne to nice da laifi, hasalima
hakan da nayi shi ya kawo kusancin da yake tsakaninta da sultan, wanda adaa
babu wanda yake son dan'uwansa" Mammi tace "naso in fahimceki hajia,
ni ba don halinda sultan yake ciki bane, a'a Ina matsayin mahaifiyarta tana
kusa dani amma ta kasa fada min? Nifa uwace, kuma nasan kin fada mata yanda
nake son ganinsu, sultan kuma shi ya jawowa kanshi, banga laifinta ba, ai ya
fada min yanda aka yi har aka daura mishi aure da ita" anan mummy ta fada
mata yanda akayi ta kadeta da mota ta kawota gidanta har yau da take bata
labari, mummy ta qarasa da cewa "ban san sultan yaje neman ta ba, da nazo
na warware komai, fateeman ma inaga bata da labarin cewa yaje can garin
midibbon" Murmushi mammi tayi ta daga hannu sama tace "Allah na gode
maka, Alhamdulillah, Allah ka bawa sultan lafiya ya tashi yaga fatun shi"
"Ameen Ameen" mummy amsa itama tana murmushin jindadin yau ta kusan
cika burinta, saura haduwan FATU DA SULTAN. Suna zaune a gurin abba yazo zai
wuce commssnr yana nemansa ya kallesu yace "hajia zan wuce gidan cmmsnr
yana nemana, inaga akan matar sultan ne" da mamakinshi sai yaga dukansu
suna murmushi a ransa yace 'mata dai akwai matsala' yasha mur da yake suna wasa
da mummy yace "kun tasa ni a gaba kamar qaramin yaro kuna min daria, hala
kun shaqi laughing gas ne" ya qarisa maganar da dan murmushin sa. Mummy
tace "gashi kaima ka shaqa ai, hajia bari in shiga ciki ki mishi
albishir" tana gama fadan haka ta shige cikin hospital din, abba na ganin
ta qule yazo ya zauna yana mamakin wani albishir za'a masa, shi dai yasan ba
akan sultan bane don yanzu ya baroshi kwance, to kodai an samu matar sultan ne?
Noo bazai yiwu ba don basuda link da inda za'a ji labarinta. to menene haka?
Kallon mammi yayi yace "bazaki fada min bane sai kinja raina?<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[7:16PM, 8/23/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Hararanshi mammi tayi cikin wasa tace
"bribe me" tsananin sonjin menene yasa yadauki wayarshi ya bata,
mammi tace "a'a riqe kayanka, an sami matar sultan, fatu 'yar qanwata
rahmatu, tana tare damu kusan shekara amma bamu ganeta ba" abba yace
"tana ina kenan" mammi ta bashi labarin komai. Abba cikin mamaki yace
"ikon Allah, ranar dana fara ganinta a gida na dauka 'yan uwa ne daga
yola, ku dai mata sai a hankali, ai sai ku sanar damu, hakan da kukayi kun nuna
bazaku umurci 'yayanku akan abunda kuke so ba, sai dai ku biyo musu ta yanda
suke so, munada iko akansu tunda mu muka haifesu, Allah ya kyauta, ni zan tafi
gidan commissioner in sanar dashi an samu yarinyar" mammi dai tana shiru
har ya dasa aya tace "Ameen, a dawo lafiya" murmushi ya mata yace
"ameen, na tayaki murnan ganinta" tace "nagode, sannunka da
wahala kaima" bai bata amsa ba yace "sai na dawo" ya tafi gurin
ajiye motoci. Mammi ta tashi ta shiga cikin asibitin.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Su fatu na shiga lubna tace "kin fada
mata ne? Fatu ta goge hawayen fuskarta tace "na fada mata, yanzu ji nakeyi
kamar an dauke min wani nauyi a kaina, saura sultan shima da kaina zan fada
masa insha Allah, amma lubna ina tsoron kar mammi taqi yafemin don na sanya
danta kwanciya a gadon asibity" lubna ta dafa kafadarta tace "karki
damu, mammi ta riga da ta yafe miki na sani, ke dai sultan ne ya rage, shima
baza'a samu matsala dashi ba" anan suka iso gurinsu jameel lubna tace
"DJ ya labarin matar sultan? Yace "kayya, madugu uban tafiyan ma ya
kasa controlling kanshi kin gamshi a kwance, yanzu inaga gurin abba zanje muyi
proceeding kafin sultan ya farfado" murmushi lubna tayi tace "u dnt
have to" cikin rashin gane inda maganarta ya dosa yace "ban fahimceki
ba! Tace "ga fatun nan da kuke nema" ya kalli fatu yayi yaqe yace
"lubby u must be joking, ke a wannan halinda muke ciki har kinada lokacin wasa"
ya gama maganarshi cikin bata fuska. Amrah da tunda suka fara magana tana binsu
da ido cikin rashin fahimtan akan su waye ake magana tace "waye ya bata?
Wane sultan? Kallonta sukayi dukansu sukayi shiru, fatu ta isa gurinta tace
"ni cousin sis dinki ne, da mammi da mamana mahaifiyarsu daya" Ta
cigaba "yayanki yaje nema na aka aura masa ni, to ni yar kauye ce ba
ajinsa bane yasa ya tafi ya barni 4 a year bai qara waiwayana ba, ganin haka
yasa na fito nemanshi, anan mummyn farouq ta kadeni a bakin tashan nan garin,
lokacin da na bata story na tace I should stay with her har randa mai bayyana
ta bayyana" fatu ta kalli lubna alamar labarinta yayi daidai yanda za'a
fadawa amrah? Lubna ta mata 👍 yayi dai dai, fatu ta maida dubanta ga
amrah wacce ta sake baki tana mamakin wannan labari, tace "to meyasa
yayana ya kwanta rashin lafiya? Lubna ta karba tace "ya fara sonta, da
yaje can garinsu sai ya tarar bata can, shine hankalinshi ya tashi yazo ya
fadawa mammi, mammi kuma ranta ya baci, so kinsan yanda sultan baya son bacin
ran mammi, dats why he end up here" amrah ta fara tunani tana kada kai, no
wonder jiya sultan da yamma yace ta tafi dakinta zasuyi magana da mammi, kuma
taga mammi cikin damuwa don ita kanta tasan yanda mammi take son ganin auntyn
nasu, ehh lallai biri yayi kama da mutum. Jameel ya miqe ranshi a bace yace
"lubna for how long kika san cewa fateema fatu ce? Lubna ta fara inda inda
yace "tell me" tace "tun ranarda suka hadu suka fara hira"
cikin bacin rai yace "kin kyauta, yanzu idan mutuwa yayi ma babu ruwanki,
a dalilin ki tayata ramawa kika qi fada min ina? Weldone, banga laifin fateema
ba sai naki don ita sultan ya mata laifi nima shaida ne" yana gama fadan
haka yayi ficewarsa, a bakin kofa ya taradda mummy na shigowa yace ina abba?
Tace "yana tare da mammi" lubna ta iso gurinsu cikin sauri sau haki
takeyi jameel na ganinta yace "mammi bari in dan fita, zan dawo
yanzu" ya fice lubna tayiwa mummy yaqe ta bi bayan mijinta, har suka wuce
su mammi basu ankara dasu ba, keke napep ya tara a bakin asibitin ya shiga
itama ta shiga tana bashi hakuri. Kamar na bisu nace 'kai labarin fatu nake bi
ba nasu ba"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu kuma tun fitansu kirjinta yake dukan
uku uku, to wannan reaction din jameel ne, yaa na sultan kuma zai kasance a
kanta? Zufa ya keto mata tace "kar fa yace bazaiyi accepting dina ba tunda
ban tausaya mishi ba" amrah da take gefenta tace "me kika ce anty
fateema? Yaqe fatu tayi tace "babu komai amrah, maganar zuci ne" dai
dai nan mummy ta qaraso ta fara bawa fatu baki kan ta kwantar da hankalinta, batada
matsala da mammi, fatu dai kada mata kai kawai takeyi amma tunaninta nakan irin
draman da za'ayi in sultan ya farfado.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[8:55PM, 8/25/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Suna cikin haka mammi ta shigo itama, fatu
sai sunkuyar da kai takeyi bata son hada ido da ita, ganin haka yasa mammi ta
isa gurinta ta kamo hannunta suka zauna tace "karki damu kanki, laifinki
daya fateema na qin sanar dani wacece ke, mummy ta fada min dalilinki, have no
worry dear, uwa bata fushi da danta" rungume fatu mammi tayi tana jin
tsantsar sonta cikin ranta, taso ace mahaifiyar fatu tana da rai itama taga
wannan rana, hawayen farin ciki ne ya gangarowa mammi ta share ta dago fatu
wacce itama fuskarta ya cabe da hawayen, mammi ta ciro hanky a dan qaramin bag
din da ta taho dashi tana gogewa fatu fuska, abun ya bawa mummy daria tace
"hajia surkuwa ce fa"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Mammi ta dago fuskar fatu tana mata
murmushi yayinda fatun ma murmushi takeyi amma idanunta na qasa tace
"wannan ba suruka bace, 'yata ce hajia kulsum" mummy ta kada kai tace
"hakane hajia sadia"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Amrah tace "nice show👍" <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A mosque din hospital din sukayi sallah
Daga nan suka dawo suka duba jikin sultan, yana nan kwance kamar yanda suka
barshi, abba ya shigo yace "ya kamata ku tafi gida tunda ance zaiyi 48hrs
b4 ya farka, zan zauna dashi" mammi bata so ba haka ma fatu, dolensu suka
fita. Mummy tayi drivin dinsu a motarta da suka zo ita da lubna a ciki, cikin
gidan mammi suka fara sauqa suna maida zance fatu ta kule dakin amrah, basu
jima ba mummy tace "hajia zan tafi gida, sai gobe insha Allah zamuje mu
duba shi, ina fateema taxo mu tafi" mammi tace "to ba komai Allah ya
kaimu, hajia baza ki barmini yar taki bane? Ta fada cikin barkwanci, mummy tace
"na bar miki yanzu amma zanzo in dauki diyata" mammi ta kira fatu
tace "mummynki tace ki dan zauna a nan, me kike buqata a kawo miki daga
gida? Fatu tace "mummy kayan sakawa na" sukayi sallama ta tafi. Anan fatu
taji ta wani iri, tafi sabawa da mummy kuma ita kunyan maman sultan din take,
komawa tayi dakin amrah ta zuba tagumi tana tunanin mijinta koyaushe zai farka?
Sa'I sa'I amrah na mata magana tana bata amsa. Bayan sallah isha farouq yayi
sallama ya shigo da dan madaidaicin travelling bag ya kawowa fatu, ta karba
yace "mummy tace a gaisheki" ta shafa kanshi tace "ina
amsawa" bai jima ba ya koma don dare ne, yana komawa gida ya turnuqe fuska
yace "mummy ni a dawo min da anty fateema na, kar ta kwana a gidansu sis
amrah" mummy tace "to farouq, gobe zata dawo" <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Bayan fitan farouq fatu ta musu saida safe
ta shiga daki, mammi na lura da fatu tana cikin damuwa, wanda itama daurewa
kawai takeyi don hakan bai taba faruwa da danta sultan ba, mammi ta kalli amrah
tace "ki bar mata dakinki, ki kwana a nawa, ni zanje side din
abbanku" amrah tace "to" kana mammi ta tafi.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[11:01AM, 8/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu na shiga daki ta bude jakan, phones
dinta ne a sama sai kayan sawanta kala biyu da night gown, brush da undies sai
dan abunda baza'a rasa ba. Wanka ta shiga ta fito, tana tunawa jiya sultan
lafiyanshi kalau amma yau a gadon asibity zai kwana, 'mutum ba'a bakin komai
yake ba'<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Hakan ta ayyana a ranta, tasa kayanta,
bayan ta gama ne amrah ta shigo ta dauki kayan baccinta ta mata saida safe,
fatu ta lockin kofar ta zauna a gado ta dauki wayarta ta bude, sai yanzu ta
tuno jefar dasu da tayi dazu a falo, daidai nan calling din xahra ya shigo fatu
ta dauka a sanyaye tayi sallama xahra tace "fateema kin daga min hankali
wallahi, kina lafiya kam? Fatu tace "lafiya" xahra tace "na
dauka wani abu ya faru dake, u said yanzu zaki shiga mota, after 15mins inda
yaci kin iso sai na jiki shiru, I clld ba'a dauka ba, me ya faru ne? Fatu sai
lokacin abun ya dawo mata sabo ta fara hawaye tace "xahra sultan na gadon
asibity, zuciyarsa saura kadan ta buga bcos of me" "innalillahi wa
inna ilaihir rajiun, garin yaya? Xahra ta tambaya cikin tashin hankali. Fatu ta
fada mata yanda akayi, xahra ta mata jaje sukayi sallama akan itama gobe zataje
dubashi.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Budo pics din sultan tayi tana kallo a
hankali hawaye kuma na wanke mata fuska, wani pic dinshi ne ta tsurawa ido,
inda daga gani ba'a nan qasar ya dauka ba, yana sanye ne da suite dark blue
tayi matuqar karbanshi, fuskar nan tashi kaman na baralabe don tsaban walwali
da kwarjini, murmushi yakeyi wanda har hakan ya sanya idanun shi kyalli da
haske, ta cigaba da kallonshi tana shafa fuskar shi ta screen din wayarta, tana
ayyana irin farin cikin da zatayi in yau akace sultan dinta ya tashi. A haka
bacci barawo ya saceta, karfe 1:30 ta farka dalilin alarm da ta saka ta tashi
tayi alwala ta fara sallah tana mai roqon Allah ya bawa mijinta lafiya.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Washe gari tun asuba ta gama shirinta ta
zauna tana duba agogo lokaci lokaci, qarfe 6 amrah ta shigo ta gaisheta ta
dauki uniform dinta, zata fita ne fatu tace "amrah mammi ta fada miki
yaushe ne zuwa asibitin? Amrah tace "ehh, wai sai kun karya" fatu
tace "ok" Tana nan zaune har amrah ta gama shirin school ta tafi,
karfe 7 mammi ta shigo dakin, fatu ta durqusa ta gaisheta mammi ta amsa cikin
sakewar fuska, tace "ki fito mu karya sai mu tafi" fatu tace
"ina azumi mammi" tace "wani irin azumi keda ko sahur bakiyi ba!
Fatu tace "nasha ruwa da asuba" mammi tace "wannan azumin naki
fatu baiyi ba, jiya ma haka baki ci abinci da dare ba" shiru fatu tayi
kanta na qasa tana wasa da yatsunta, ganin haka yasa mammi tace "to
shykenan, bari inna gama zan kiraki, ko zaki fito falo ki zauna? fatu ta kada
kai alamar a'a, mammi tasa kai ta fita. Itama mammin kasa cin abincin tayi ta
zuba masa ido, tunanin abba takeyi wanda shima a tsatstsaye yayi breakfast ya
fita tun da sassafe ya tafi hospital, jiya ma bai dawo ba sai 11 na dare.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Ganin tana bata lokaci yasa tacewa dija
tazo ta kwashe gurin, mammi kuma ta saka hijabinta ta kira fatu suka tafi
hospital.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[12:54PM, 8/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Suna isa suka tarar abba na cikin dakin da
sultan yake shi da doctor suna magana, mammi suka zauna a chairs din kofar
dakin suna jiran su abba. Doc dinne ya fara fita kana abba shima ya fito, fatu
ta gaishe shi, ya amsa da sakewar fuska, ya dubi mammi yace "zaku iya
shiga ku ganshi, amma ba'a son yawan surutu" mammi tace "ya jikin
nashi? Abba yace "to da sauqi dai, likita yace jinin shi ya sauka yanzu,
zai iya farkawa any moment from now" Mammi tayi hamdala abba yace
"zan leqa office akwai meeting da muke dashi" mammi tace "Allah
ya kiyaye" yace "Ameen" ya fita. Shiga dakin sukayi kowannensu
jiki a sanyaye, fatu tsayawa tayi a bakin kofa tana kallonshi cikin tausayawa,
mammi kuma ta isa gurin shi ta masa addu'a kana ta fita daga dakin, aka bar
fatu da sultan su kadai.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A hankali ta isa gurinshi, ta jawo kujera
ta zauna daidai fuskar shi, hannunshi ta riqo ta kawo dai dai bakinta tayi
kissing dinshi hawayen da ya taru a idonta ya samu damar gangarowa a fuskarta
har kan hannun sultan, rungume hannun tayi tana kallon fuskarshi, a hankali ta
fara shafa kwantaccen gashin kanshi fuskarta bai daina zubar hawayen ba, magana
ta fara a hankali kamar mai rada tace "ka tashi gani nan kusa dakai JANNAH
nah, ka tashi ga fatunka da kake nema, ka tashi baby nah, kaji? Wake up"
kuka ne ya kwace mata tayi mai isar ta tana kallon sultan wanda har yanzu yana
nan kwance bai motsa ba, dora kanta tayi a gefen gadon kusa da kirjinsa,
hannunshi na cikin nata ta riqe gamm! Jefi jefi tana daga kai tana kallonshi ko
ya farka. A haka su mummy suka zo suka sameta, ta gaishe da mummy tace
"fateema ya mai jiki? Fatu tace "da sauqi mummy" tace
"Allah ya qara sauqi" bayan fitan mummy ne jameel da lubna suka shigo
wanda da alama sun shirya, suma suka mata ya mai jiki suka fita, dangi da
abokan arziki sai zuwa dubiya sukeyi amma ganin ana yawan shiga da fice yasa
likita yace a daina shiga, mai son ganinshi ya leqa window, kowa ya leqa sai
yaga fatu zaune kusa dashi, suna mamakin wacece ita, marasa hakuri sukanyi
tambaya sai mammi tace 'yar uwace, ba daman yawan tambaye tambaye haka suke
tafiya da dunbin questions a kansu. Dai dai azahar likita ya shigo yace
"bai farfado ba? Fatu tace "ehh" ya qarasa shigowa ya duba shi
ya <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Bude idon sultan ya rufe yace "ya
kamata ya farka yanzu" ya dubi fatu yace "ke qanwarshi ce? Fatu tace
"ehh" yace "make sure kun kirani idan ya farka, kin gane? Tace
"yeah ok" ya fita, Tana nan zaune abba ya shigo ya duba shi yace
"ki fito ku tafi, anjima da yamma sai ku dawo" fatu na jin haka tasa
kuka harda sheshsheka, abba yace "ki zauna to, shykenan? Ta daga kai ya
fice yana murmushi. Daukan su mammi yayi suka koma gida akan sai yamma zasu
dawo, aka bar fatu ita kadai. Bayan da idar da sallah ne ta daga hannunta sama
tana addu'a, sultan ya fara motsa yatsun shi, a hankali a hankali komai yake
dawo mishi kamar a flash yayinda yake qoqarin bude idonshi, haske ya gani yayi
saurin rufewa, ya qara budewa ya rufe, a haka har ya saba da hasken, a hankali
ya juya kanshi gefen da yake jin motsi, wata ya gani zaune akan sallaya tana addu'a,
fuskarta hawaye na bin wasu, ganinta yayi kamar fateema amma lokaci daya yaga
kamanninta kamar na wata.....kamar a flash ya tuno kamannin fatu, da sauri ya runtse idonshi idonshi ya
fara recalling........ "Kinyi makaranta? Tace "ehh" yace "a
ina kika tsaya? Tace "secondary" yace "shekarunki nawa? Tace
"17" yana tunawa dai dai nan ya kalleta 4 d first time, kallon na kan
sallayan yayi yaga ta shafa addu'an kanta na qasa tana kuka a hankali, ya tuno
fatu wacce ita ma a lokaci kuka take son hadiyewa, yayi saurin kai kallonshi
kanta yana tuna fatu tanada wani jijiya a tsakiyar goshinta, wannan din ma
hakane tana dashi, kallonta ya cigaba dayi yana ganin fuskar fatu, fuskar
fateema a fuskar wacce take kan sallayan nan!! Wacece ita??? Dago hannunshi
yayi wanda aka saka mashi drip hakan yasa qarfen da aka dora drip din yayi
qara, fatu da take kuka ta dago kanta da sauri, lokaci daya kuma ta miqe kamar
wacce aka tsikara, nan da nan fuskarta ta washe da murmushi yayinda idanunta na
tsiyayan hawayen farin ciki, ta nufo gurinshi ta kamo hannunshi yace
*"FATUUUUUHHH"*<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[8:28AM, 8/27/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">"Shhh" tace dashi, "ba inda
yake maka ciwo? Ido ya tsura mata, tuno da cewa doctor yace a kirasa yasa ta
fita da sauri, shi tsoro ma ta bashi, wacece ita? Shin an samu fatu? To ina su
mammi? Tukunna ma waya kawoshi nan?? Qoqarin tashi ya farayi daidai nan aka
bude kofa, fatu ne da doctor sai nurse tana riqe da kayan aiki, fatu tazo
gefenshi ta tsaya doc ya mishi gwaje gwaje yace "can u talk? Sultan yaqi
ya kulashi, ya qara cewa "me kake ji a jikinka? Nan ma shiru yayi, Fatu
tace "baby kayi magana kaji? Sai yanzu ya qare mata kallo ya gane
muryanta, ya fara qoqarin tashi da sauri ta taimaka mishi ya tashi zaune,
kallonta yayi yace "fateema what ar u doing here? Tace "ka amsa
tambayar likita tukun" ya maida dubansa kan doctor yace "just
headache sai jikina da yake ciwo" doc yayi 'yan rubuce rubuce yace "ki
bashi abinci in yaci a bashi magungunan shi, nurse ki basu sai ki fada musu
yanda zai sha" tace "ok doctor" ya fita, nurse ta gwadawa fatu
yanda zata bashi itama ta fita. Fatu tace ka sauqo kaje kayi brush sai kaci
abinci, yace "baki bani amsa ba" tayi murmushi ta cire hijabinta ta
ninke, dogon rigan atamfa ne a jikinta wanda daga sama ya kamata, ta qasa kuma
ya dan budu, babu make up ko kadan a fuskarta, ta isa gurinshi da murmushinta
ta jawo kafafunshi tace "nazo jinyar ka ne, ka sauqo in raka ka bandaki"
ba musu ya sauqo yana mamakin meyasa su mammi suka bari fateema na jinyarsa
alhali sun san cewa ba muharraman sa bane. Ya shiga bandaki ta tsaya daga kofa
yace "ki shigo mana" da sauri ta juya shi kuma yayi murmushi ya rufe
kofar, yayi wanka yayi brush ya leqo yace "akwai kaya ne? Tace ehh ta miqo
masa t-shirt white da dogon jeans baqi, ya karba ya saka sannan ya fito, jiri
jiri yake ji hakan yasa ya nufi gado da sauri ya zauna. Fatu da take nazarinsa
tace "jiri kake ji ko? Yace "ehh" tace "rashin qarfin jiki
ne gashi kuma akwai yunwa tattare dakai" kada mata kai yayi ta miqe tana
zuba mishi abinci, gwaten dankali wanda yaji kayan lambu da kifi, sai kunun
gyadan cous cous mai madara ta tsiyaya masa a cup, ta nufo gurinshi, gaba daya
shi tunani yakeyi tana isowa yace "kinada waya a hanunki" tace
"ehh, akwai" yace "dan bani inyi kira" ta miqa mishi,
numbern abba yayi dialing ya dauka yace "Assalamu alaikum abba, sultan
ne" abba yana zaune ya miqe tsaye
yace "sultan ka tashi? Baka jin komai ko? Ya jikin naka? Yace "da
sauqi Alhamdulillah, an samu fatu abba? "An samu fatu ka kwantar da
hankalinka, amm fateema bata fada maka bane? Sultan da mamaki ya kamashi kan a
ina abba ya san fateema, kuma me hadinta da fatu? Yace "abba me zata fada
min? Nan fatu ta mai alama daya miqa mata wayan, yayi kamar ya hanata amma sai
ya miqa mata yaga iya gudun ruwanta, sallama tayi tace "abba yanzu ya
farka, yanzu zai ci abinci yasha magani" abba yace "to ki saka yaci
abinci kinji, yanzu muna zuwa" tace "to abba, Allah ya kawoku lafiya"
sukayi sallama. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sultan da yake binta da kallo yace
"fateema Can you tell me whats going on here?<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[8:43AM, 8/27/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">8</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tashi yayi yana cewa "zan tafi
gida...." jiri ne ya debeshi kanshi na juyawa da sauri fatu ta zaunar
dashi akan gadon fuskarta dauke da damuwa tace "pls kaci abinci kasha
magani, nd I promise zan fada maka duk abunda kake buqata"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Shiru yayi can yace "ok, qarfe nawa
yanzu? Ta duba phone dinta tace "2:01pm" yace " Ya kamata inyi
sallahn azahar" fatu tayi daria tace "dear salloli da yawa akanka,
azahar, asr, maghrib, isha, asuba, azahar" yace "ban gane ba"
kallonshi tayi ta debo abinci a spoon ta kawo dai dai bakinshi tace "tun
jiya kake kwance baby" bude bakinshi yayi ta saka mishi, a haka yaci
abincin sosai tana masa hiran barkwanci, tuni ya manta damuwarsa harda daria,
yasha kunun sosai da yake yana son kunu, bayan ya gama cin abuncinne yasha
magani ya tashi tsaye, yaji baya jin
ciwon kan, gashi jiri jirin ma babu, kallon fatu yayi wacce take saka
magungunan cikin leda, yaji kaman ya jawota jikinshi (ehhh lallai ka qoshi🤔)
yana nan tsaye har ta gama ta dauki used plate da cup din ta saka a basket, ta
dauki hijabinta ta saka, juyowan da zatayi ta ganshi tsaye, tace "har ka
fito? Murmushi yayi yace "ban ma shiga ba" tace "kana jin jirin
ne har yanzu? Yace "a'a" dai dai nan abba, mammi da jameel suka
shigo, ganin dansu tsaye yana murmushi kamar ba wanda ya tashi daga gadon
rashin lafiyaba ya saka su farin ciki, mammi harda dan guntun hawayenta, jameel
ya isa gurin sultan ya rungume shi yace "wellcome back dude, fatu ta
wahalar mun da kai, amma naga alama she's taking good care of you" sultan
yace "ban gane ba" abba yazo ya dafa kafadan shi yace "ya kake
jin jikin naka? Yace "da sauqi abba" mammi tace "baka jin komai
ko? Kaci abinci? Yace "bana jin komai, naci abinci" abba yace
"bari inyi magana da doctor" ya fita daga room din, jameel da mammi
suka samu guri suka zauna sultan ya shige bandaki, fatu kuma ta fara kimtsa
musu kayansu, sultan ya dade a bandakin yana tunanin maganan abba da sultan
...abba "an samu fatu... fateema bata fada maka bane? .....jameel "fatu ta wahalar mun da kai,
amma naga alama shes taking good care of you" ya dafa kan sink din
bandakin maganansu na mishi yawo akai, to Yaushe fatu tazo har tayi jinyar shi?
Ganin yana bata lokaci yasa yayi alwala ya fito a ranshi yana cewa tunda dai an
sameta shykenan, wani farin ciki ne ya lullube shi<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">daya tuno da fatun shi yana ayyana irin
kyakkyawan qaunar da zai gwada mata. Ganin ba mammi da abba a room din yasa
sultan yace "jameel abban bai dawo bane? Jameel da yake danne danne da
waya yace "sun tafi gida, zamu tarad dasu a can, an sallameka" sultan
ya maida dubanshi kan fatu wacce ta dale kan gadon nashi itama tana danne
dannen phone dinta, yace "fateema ina sallaya? Ta shimfida mishi ya fara
rama sallolin da ake binshi fatu da jameel na jiranshi ya gama su tafi gida.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[11:02AM, 8/30/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">9</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Yana gama sallolin aka kira asr, jameel
yace "mu tafi mosque mubi jam'I" hakan kuwa akayi, sultan a hanyar
fitansu yaga fateema sai masa magana takeyi a ranshi yace 'kodai na bata
tausayi ne yasa ta ajiye kishinta a gefe? A mota suka barta suka shige mosque
din asibitin, a lokacin fatu ta fara tunanin ya zata fara fadawa sultan cewa
itace fatu!! Duk irin abubuwan da takeyi daurewa kawai takeyi don zuciyarta har
yanzu yana bugawa da sauri idan ta tuno kalan draman da zasu kwashe ita da
sultan, ta rafka tagumi, wayarta ya fara qara, xahra ce "sai yanzu zaki
kirani? Cewar fatu, xahra tace "tunda safe naso inzo, kakana ne ba lafiya
muka kaishi hospital shima, kuna wani ward ne? Fatu tace "ayyah Allah ya
bashi lafiya, ai an sallame mu" xahra tace "what? Gani nan fa cikin
asibitin! Fatu tace "don Allah? Kizo parkin space 'B' ina gurin a motar ya
jameel, bamu tafi ba, sun shiga sallah ne" xahra ta iso a motarta fatu ta
fito sukayi huggin juna, xahra tace "ya? Kin fada mishi komai? Fatu tace
"not yet, ban samu chance ba" xahra tace "ki fada mishi da kanki
don zaifi jin zafi in wani ne ya fada mishi" Fatu tace "hakane, bazan
bari wani ya fara fada masa ba" dai dai nan sultan da jameel suka iso
fuskar sultan kamar wanda aka aikowa saqon mutuwa, ya hade giran sama da qasa,
fuskar sa sai da tayi wani jaa, ya shiga mota next to driver, ganin yanayinsa
yasa fatu da xahra suka sha jinin jikinsu, tabbas jameel ya labarta masa, fatu
ma tayi sauri ta shiga baya jikinta har rawa yakeyi, xahra da jameel suka
gaisa, ta leqo ta window tace wa sultan "ya jiki" yayi yaqe yace
"da sauqi, nagode" itama ta nufi motar ta bayan tayi wa fatu kallon
tausayi. A hanya babu wanda yayi magana, sautin qira'ar da jameel ya sanya
kawai ke tashi a motar, jameel yace "daa baka kulashi ba wallahi, irinsu
ne masu tayar da hatsaniya" ya cigaba da cewa "fateema angonki akwai
zuciya, an idar da sallah ana fita sultan ya dan bugi wani saurayi bai sani ba,
shine saurayin ya hayayyaqo mishi harda barazanan wai zai kulle sultan, to
shine gogan naki yaso ya nuna qarfinsa mutane suka shiga tsakanin su"
sultan yayi tsaki yace "to fadi ba'a tambayeka ba, parrot, jameel ka koyi
surutu wallahi" jameel yayi murmushi ya shafa kanshi yace "zama da
madaukin kanwa......" anan suka iso gida, fatu ta sultan suka fito jameel
yace "ka huta gajiya, zan zo anjima da dare" ya kalli fatu yace
"amarya a kula min da abokina" maigadi ya bude masa gate ya fita. Qaramin
basket din hannun fatu wanda suka dawo dashi daga asibiti sultan ya karba yace
"kawo in tayaki" ya fara tafiya, tace "ina son magana da
kai" ya tsaya yace "mu shiga gida to" tace "noo, anan nake
so muyi" ya kalleta a diririce yace "fateema hope ba'a kan matata
fatu bane, please ki janye wancan maganan" ta kalle shi da idanunta da
suka fara tara hawaye tace "ba shi bane" yace "ina jinki ki fada
min" shi ya qagu ya shiga gida ya tarar da fatunshi, ya tambayi jameel ya
fada mishi inda aka samu fatunshi da yanda aka sameta amma jameel yaqi sanar
dashi, wai fateema ce zata fada mishi, whats so special in fateema ta fada
mishi? Anyway tunda ance fatun shi lafiyanta kalau, nd babu abunda ya sameta he
can wait fateema ta gama maganarta. Kallonta yayi yace "ina jinki"
shiru tayi kanta na qasa, yayinda hawaye ke bin kuncinta tace "NICE
FATU"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:05PM, 8/30/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Kallonta yayi yace "fateema please
banda joke a wannan time din" Ta dago idanta tace "ba joke bane,
gaskia nake fada maka" sultan ya gyara tsayuwarshi yace "ina fatun?
Tace "I said nice fatu, nice matarka, na fito nemanka mummy na hadu da mummy"
kan sultan ya dau zafi yana kallonta kamar wacce take masa tatsuniya, wani
lokacin tana masa dan kama da fatu especially in tana kuka. yace "ban gane
ba, ban fahimceki ba, shin rikida kikeyi from fatu to fateema ko me kike so ki
fada min? What do you mean? Fatu tace "please muje garden, not here"
yace "noo, nan din ma is ok" tace "please" yace "ok
muje" a garden suka zauna akan kujerun da suka qawata gurin, ya dafa table
din dake tsakaninsu yace "ina sauraronki" Fatu tace "ka min alqawari
duk abunda na fada maka baza ka yi fushi ba" sultan daya qagu yaji maganan
yace "ba komai, ina jinki" Fatu ta fara bashi labari tun daga
zuwanshi garin modibbo har yau, tashi yayi tsaye yana nunata da yatsa jikinshi
har rawa yake yi yace "a hakan ne kike sona? Ko kunyar fada bakya yi?
Kinada tausayi kuwa? Ya harde hannayensa a qirjinsa yana tsaye a kanta, ranshi
a bace, fatu ta miqe tsaye itama ta share hawayen fuskarta ta turo baki tace
"ai bani kadai bace mara tausayin, kuma naga abunda kamini na rama"
ta murguda baki ita ala dole ta masa masifa. Taci gaba da magana wanda ita a
ganinta masifa takeyi, shi dai ya tsaya yana kallonta bacin ran da yake ji
zuciyarsa yana raguwa a hankali, Yanda take maganan tana juya idanu ya mishi
kyau har baisan lokacin da ya saki murmushi ba, ita kuma kallon gefe tayi ta
riqe qugu tana wani girgiza, sauke hannayensa yayi tareda yin nannauyan ajiyar
zuciya yace "naji na miki laifi amma bai kamata kimin horo da wannan
hanyar ba, kina gani fa yanda na rikice amma ko a jikinki" ta kalleshi
taga yana murmushi, a ranta tace 'bari muja ajii' ta qara hade fuska tace
"kaima haka kamin, bayan an sanar da kai halinda nake ciki amma hakan bai
sa ka tausaya min ba" ta qara murguda baki, ya ciji lips dinsa Yace
"wa kike murgudawa baki? Kallonshi
tayi taga ita yake kallo ta kawar da kanta tace "ni ba da kai nakeyi
ba" ta qara murguda baki, qoqarin zagayawa gurinta ya fara yi, ita kuma
ganin haka yasa ta matsa, Suka fara zagaye table din, shi burinshi ya kamata ko
rankwashi ya mata na wahalar dashi da tayi, ita kuma taqi hakan ya faru, ganin
yana qoqarin kamata yasa ta kwasa da gudu cikin gida, tsayawa yayi yana kallon
yanda take gudun kamar wata small girl, murmushi yayi ya kalli gabas yayi SUJUD
SHUKR yayiwa Allah godia da ya bayyana masa fatu ta inda baya tsammani, a
hankali ya furta "Allahu Akbar, Alhamdulillah" Ya dauki basket din
yayi cikin gida.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[2:02PM, 9/2/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu sai data saisaita kanta kafin ta shiga
falo, mammi ne kadai zaune tana jiran isowarsu, fatu ta mata sannu mammi tace
"ina sultan din? Fatu tace "yana shigowa" tana rufe baki ya
shigo yayinda ita kuma ta shige room din amrah,
zama yayi kusa da mammi ya riqe hannunta yace "mammina kin yafe min
abunda na miki? Ta kalleshi cike da qauna tana murmushi tace "na yafe maka
manga na" shima murmushin yayi yace "nagode, duk dana saba alqawari
ayau burina ya cika, na samo miki fatu" tace "Alhamdulillah komai
yazo da sauqi, yanzu kaje ka huta zamuyi magana anjima da dare" yace
"to" mammi ta tashi ta shiga dakinta, sultan na ganin haka yayi sanda
ya shiga dakin da fatu take, da alama ta shiga wanka, don ga kayanta data cire,
kwafa yayi yace 'Allah ya taimakeki, zamu hadu ne' sosa kai yayi yana murmushi,
wani irin farinciki yakeji mara misaltuwa, wai fateema da yake so itace fatun
shi da yake nema!! Yayi tunanin ya rama wahalar dashi da tayi amma wata zuciyar
ta haneshi da aikata hakan, don a dalilin rama abunda ya mata ya kwanta a
asibiti. Ya fita daga room din zuwa part dinshi. Da dare bayan isha anci abinci
abba ya tara familyn gaba daya a palour nshi, yace "Alhamdulillah ala
kulli halin, komai ya faru ga dan adam muqaddari ne daga Allah, anan nake so
naja hankalinku dukan ku cewa kar a bawa kowanne shashe laifi kan abunda ya
faru, abunda ya faru ya wuce, kuma ina mai qara jawo hankalinku kan cewa ku
kasance masu jin maganan iyayenku, sannan ku daina wulakanta mutum duk inda
kuka ganshi, kowanne bawa da baiwar da Allah ya masa, and lastly kuji tsoron
Allah, ku kiyaye hakkokin junan ku, duk wani abun da akace hakki ne rataye a
wuyanku kuyi iya qoqarin ku wajen sauqe shi don saboda gujewa fushin Allah, ba
tone tone ba, kai sultan tun farko daka dauki aurenka a matsayin qaddara ka
kuma yi imanin cewa 'matar mutum kabarinsa' da duk wani tashin hankali bai faru
ba, zaka iya cewa ai shima qaddara ne, yess qaddara ne amma anbi don zuciya,
wanda son zuciya kan kai mutum ga ga halaka, Allah ya kare" a hankali kowa yace "ameen" jikin
kowannensu yayi sanyi da alama nasihar abba na shiga dai dai "sai ke
fateema, duk da bakida laifi amma nasan kinyi hakan ne don ki hora shi kan
abunda ya miki, shi hakuri maganin zaman
duniya ne, kar ku rama sharri da sharri, ku kasance masu aikata alkhairi ga
kowanne mahaluqi, hakan zaisa ku sami babban rabo a gurin Allah, ku kasance
masu yafiya wa junanku don gudun nadama nan gaba, Allah ya shige mana gaba a
duk al'amuran mu" "ameen" suka qara amsawa. Anan sultan ya kalli
fatu wacce kanta na qasa tun shigowanta taqi su hada ido a zuciyarshi yace
'she's now fatu' karaf idanunsu suka hadu, murmushi ya sakar mata yayinda itama
ta mayar mishi da murmushin ta sunkuyar da kanta, sosai abba yayi nasiha har
amrah an tabo ita kuma akan karatunta, gyaran murya abba yayi yace "sultan
yaushe zaka dauki matarka?? Dumm gaban fatu ya buga, don ita duk lissafinta
bata taba zaton za'ayi maganar tarewanta nan kusa ba, da sauri ta dago ta kalli
sultan shima ita din yake kallo, wannan karon murmushin mugunta ya mata ya
kanne mata ido daya yace ".......<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[2:04PM, 9/2/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Yace "abba nan da sati daya"
kallonshi fatu tayi kamar zatayi kuka ya qara narka mata murmushi har
hakoranshi na bayyana, abba yace "to sultan bakayi gaggawa ba? Mammi ta
amshe "ehh gaskia sati daya yayi kadan, ina laifin wata daya? Sultan ya
kalli mammi a natse yace "mammi har wata daya? An daure auren fa, kawai ku
dauketa ku kaita shine zai dau wata daya? Haba mammi" daria abba yayi yace
"kuyi shawara to, amm fateema kefa wanne kike so? Sati daya ko wata daya?
Fatu ta kasa magana, ta daga ido ta kalli sultan murtuqe fuska yayi alaman ki
zabi nawa, mammi kuma tace "fateema kiyi magana babu mai takura miki"
fatu ta nisa tace "abba yanda mammi ta fada yafi" murmushi abba yayi
sultan kuma ya bata rai, shi gaskia ba'a masa adalci ba, wata daya ai yayi
yawa, mammi ko tausayin shi batayi. Abba yace "sultan sati daya yayi kadan
a gama shirye shirye duk da an daura aure kasan mata akwai su da son biki, da
sati da wata dayan duk daya ne, hajia sadia ku fada min duk abunda kuke buqata
na hidiman da za'ayi, komai da komai" mammi tace "to Alhaji mun
gode" sultan dai yana shiru don shi a ganinshi sam ba'a kyauta mishi ba,
shi farko ma da cewa zaiyi a bashi matarsa su tafi yanzu tunda yana da gurin
zama, amma sai yayi kulaku yace sati daya, kenan sati dayan ma a gurinsu yayi
kadan, "wata daya, ina zaman jira?" ya furta a zuciyarsa amma baisan
har ya fito fili ba, amrah da take kusa dashi ta tuntsire da daria harda riqe
ciki, mammi tace "amrah lafiyanki kuwa? Sultan yana mata ido amma ina bata
ma ganshi ba tace "wai cewa yayi 'wata daya, yana zaman jira" duka ya
kai mata a baya wanda yasa ta saki kuka mammi tace "kiyi hakuri, kije ki
kwanta" tashi tayi tana kukanta ta fita, mammi ta maida dubanta kan sultan
wanda yanzu kam kowa yaga yanda ya hade rai tace "to sannunka da cin zali,
in kayi wasa sai in qara wata biyu akan dayan, sati daya kamar auren yar tsana
za'ayi? Wannan ne karo na farko da zan aurar, kuma 'yaya biyu, haka kawai in
sungumi 'yata in baka ba wani biki? Kamar zaiyi magana sai ya fasa ya tashi
yace "sai da safenku abba" abba yace "mu kwana lafiya, ka
tabbata kasha maganinka kafin ka kwanta" yace "to" yasa kai ya
fita. Fatu da tunda aka fara draman nan kanta na qasa ta dago tabi bayanshi da
kallo, mammi tace "fateema kema kije ki kwanta, ki huta gajiyanki, Allah
ya miki albarka" "ameen" fatu ta amsa ta musu sai da safe ta
fita. A hankali take tafiya tana waige waige don bata son haduwa da sultan,<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tazo daidai bakin main falo zata shiga taji
ance "fatu" waigowan da zatayi taji an fincikota tayi masauqi a
kirjin mutum, tana daga ido ta kalli fuskar sultan wanda yake mata murmushi
wanda daga gani murmushin mugunta ne, rufe mata baki yayi da hannunsa ya fara
janta zuwa side dinsa.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:40AM, 9/3/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tirjewa tafara tana qoqarin cire hannunsa
daga bakinta amma hakan bai samu ba don wani irin kyakkyawan riqo daya mata,
ganin zata bata masa lokaci yasa ya dagata cidok har dakinsa, bai direta a
ko'ina ba sai kan kujera, ya juya fatu ta bishi tana magiya yana tattareta yayi
locking kofar, key din ya cilla sama ya cafe ya kashe mata ido yace "baby
nah, yaya dai? Ji dan rainin hankali ta fada a ranta a fili kuma tace "don
Allah ya sultan ka bude mini kofa, don Allah kar kamini komai" tsayawa
yayi da karkada key din da yake yi yace "oohh kin dauka wani abu zan miki?
Okey wato har kinsan abunda ake yi? Ya qarisa yana daga mata gira, sunkuyar da
kai tayi cikin jin kunya ta fara wasa da yatsunta, kallonta yakeyi kamar zai
cinyeta, yace "don mugunta ina kika bi shawaran mammi? Shiru tayi yace
"answer me" tace "nifa ba haka bane" yace "to mene?
Tace "dama ina son zuwa garin modibbo ne" yace "okey, don kina
son zuwa garin modibbo shine zai sa ki qi tarewa a gidan mijinki? Shin nace
miki baza kije bane ko mene? Shiru tayi yace "da alama yau zaki kwana anan,
da nayi niyyan barinki amma shirunki zai sa ki kwana mini" ta dago da kai
tace "don Allah...a'a.... to kayi hakuri" matsowa yayi kusa da ita,
taja baya, kyakkyawan runguma ya mata sannan ya ajiye nannauyan ajiyan zuciya,
batayi qoqarin kwatar kanta ba saboda yanda jijiyoyin jikinta suka mutu
lakasss! Sai da suka kusan minti uku a haka sannan ya saketa ya bata key yace
"sai da safe" ba musu karba ta bude kofan jiki a sanyaye ta fita ta
mayar da kofan ta rufe, wani irin sanyi ne ya bugeta wanda har tsikar jikinta
sai da suka tashi, ta kankame jikinta ta fara tafiya, a ranta tace 'anya bazan
koma ba? Irin wannan sanyi' murmushi tayi tunowa da cewa ko giyan wake tasha
bazata kai kafarta gurinshi ba. A haka ta iso part dinsu ta rufe kofa bayan ta
shiga, ta wuce dakin da take kwana.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sultan kuma da kyar ya saita kanshi ya samu
salama, amma tunanin fateema kawai yakeyi, da kyar bacci ya debe shi cike da
dreaming dinta.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Shirye shirye aka fara tun<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">washe garin ranar, events 5 mammi ta
lissafawa abba wanda za'ayi yace ta rage bidi'an yayi yawa, daga baya aka maida
shi 3. Bayan kwana 4 sultan, fateema da mammi suka je garin modibbo, kaka ya
rasa inda zaisa kanshi don dadi, koda aka ce masa ga fatu da farko kasa
gaskatawa yayi, fatu harda guntun hawayenta ta rungumi kakanta, su goggo asabe
suka zubar da makamai don ganin fatu ta musu nisa, dolenta ta dawo ta nan nan
dasu, ganin haka yayiwa fatu dadi ta godewa Allah, kawu muntari ma yayi murna
inda ya aika aka siyo musu fura da nono mai dadin gaske aka kuma yanka kaji biyu
aka musu miya, bayan azahar naga mammi da kaka zaune a cikin zaure, mammi ta
kwashe duk abunda ya faru ta sanar dashi tace "daa nace ko baza a sanar
daku ba sai abban sultan yace lallai a fada muku kar ranku ya baci kuma kusa
shakku a zuciyanku idan magana ta fito waje, nasan 'dana yayi kuskure amma yayi
nadama, ina mai baka hakuri a matsayina na mahaifiyarsa" kaka yayi shiru a
cikin ranshi baiji dadin abunda ya faru ba, ashe shiyasa ranar da sukazo sultan
ya rikice don sanin bata tare dasu? Biri yayi kama da mutum, tun ranar
zuciyarsa take raya mishi abubuwa daban daban, in bai manta ba yau sati kenan
da faruwan al'amarin. Yace "babu komai hajia, yanzu kam ya zama
tarihi" mammi taji dadin yanda bai tsawaita maganan ba ta sako musu hiran
bikin fatu da take shirin yi, nan da nan fuskar kaka ta washe yana murmushi
yace "diyar ku ce, sai yanda kukayi, fatanmu Allah ya hada kansu ya basu
zaman lafiya" sultan da fatu sun tafi gona inda yake ganin yanda ake shuka
domin damina ta fara, Basu jima ba suka dawo dalilin kiran da mammi ta musu kan
su dawo su tafi gida, tsaraba sosai kaka ya tara musu, goggo asabe ma harda
garin kuka, daddawa da man shanu, mammi bata barsu ba sai da ta cikawa kowa
aljihunsa ta kuma roqi alfarman cewa idan lokacin biki yayi suzo, kaka yace
insha Allah za'a zo. Fatu bata so tafiya ba amma haka suka tafi tana mai kewan
su kaka, a wajen fita daga gari ne suka hadu da hafizu dan ladan da alama daga
gona yake, fatu tace "ga hafizu" qasa qasa yanda sultan zaiji, yace
"waye shi? Tayi murmushi tace "kaka bai baka labarinshi bane? Sai a
sannan sultan ya tuno ya murtuqe fuska yace "shine kike kallonshi kina
murmushi ko? Tayi tsit, don yanzu tana tankawa qari zai zama kababa. A yanda ta
lura dashi yana da kishi sosai Murmushi tayi tace "sorry" daga nan
kuma ta dauko musu wani hiran, mammi dai tana baya ko ta kula su, hasalima waya
takeyi da wata qawarta yar borno wacce zata hadawa fatu humra, kulacca dasu
turaren wuta. Woo mammi🤓. A haka har suka iso gida.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[11:56AM, 9/3/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu ta koma gidan mummy da zama, mammi ta
lura da yanda sultan ya takura mata, hakan ba qaramin dadi yayiwa fatu ba domin
in har ta bari suka zauna su kadai to sai yasan yanda zaiyi ya sata kuka da
irin abunda yake mata. Shi kuma baiji dadi ba amma ya nuna musu ko a jikinshi,
qarshe ma tafiya yayi dubai kan cewa shi zai hado kayan lefe da kayan daki,
mummy ta mammi suka rubuta masa duk abunda suke buqata. A ranar da zai tafi ya
shigo gidan mummy, a falo ya tarar da mummy tana zaune, ya gaisheta tace
"sai tafiya ko? Yace "ehh" tace "fateema tana kitchen, ka
shiga kuyi sallama" kamar bazai shiga ba amma yayi missing dinta, a
kitchen ya sameta ita da dija suna aiki, dija ta gaishe shi ta fice daga
kitchen din, fatu ta gaishe shi tace "ya na ganka haka? Yace "kamar
ya? Tace "kamar bakada lafiya" ya shafa sajensa yace "lafiyana
kalau, zanyi tafiya ne" zare ido tayi ta matso kusa dashi tace
"yaushe? Ina zaka je? Murmushi yayi ganin reaction dinta alaman bata so
ba, yace "yau, dubai daga nan in wuce china, sai ana saura kwana biyu biki
zan dawo" fatu da idanunta suka fara tara kwalla tace "don na dawo
nan shiyasa zakayi nesa dani ko? To zan koma gidan mammi, kaji? "A,a kiyi
zamanki, dama kema bakya son ganina, kuma ina takura miki, so kinga inna tafi
zaki fi sakewa ayi shagalin biki dake" girgiza kai tayi tace "ni baka
takura min ba, don Allah ka zauna, kayi hakuri, bazan iya jure rashin ganinka
ba har tsawon kwanakin nan, ban saba da rashinka ba" tausayi ta bashi
sosai, amma shima abun tausayawan ne, kuka ta fara ya jawota jikinshi ya
rungume ta yana bubbuga bayanta "its ok dear, nima ba'a son raina zan tafi
ba, 10 days zanyi kawai in dawo, u happy? Girgiza kai tayi tace "shima
yayi yawa" ya dago da kanta ya share mata hawaye yace "kamar yau ne
zakiga 10dys din yayi" wayarshi ce ta fara qara ya dauka jameel yace
"ina jiranka a waje, kar kayi missin flight naka" yace "ok ganin
nan fitowa" jin haka yasa fatu tara wani kwallan ya kalleta yace "in
tafi? Tayi shiru, peck ya bata a kumatu yayi ficewarsa don shima daurewa kawai
yakeyi, mahmud ya samu a palour, mummy kuma da alama ta shige dakinta, ya tsaya
suka gaisa, mahmud ya hango fatu a bakin kitchen tana kuka yace "dukanta
kayi ne sultan" sultan ya juyo ya kalleta yace "wai don zanyi tafiya
ne, dadi ne ya mata yawa" mahmud ya kwashe da daria yace "dan tsaya
don Allah" .....'ashe sabo yana da dadi, amma in za'ai rabo da zafi'.....
waqan 'sai wata rana' ya saka musu, sultan yaja tsaki ya fita daga falon, fatu
kuma ta fito tayi hanyar dakinta tana matsar kwalla, mahmud sai kwasar daria
yakeyi, dai dai nan mummy ta fito tace "me haka mahmud? Ya tsagaita
darianshi yace "sultan zaiyi tafiya shine 'yar kauyen nan take ta
kuka" mummy ta bata fuska tace "kai kuma qaton banza shine kake mata
daria? A haka wai kai yayanta ne? Shiru yayi fatu kuma tasa daria mummy tace
"sannu mai kuka da daria" fatu ta haura sama tana murmushi. Sultan ya
sauqa lafiya, kai tsaye ya wuce hotel din da yake zama, fatu ya fara kira yace
mata ya iso, ta mishi barka da hanya. Yana wanka ya fita zuwa gidan wani
abokinshi Ahmad, balarabe ne amma yayi zaman naija, sosai yake jin hausa,
matarsa Nihal ta kawo wa sultan abinci ya zauna yaci anan yake bashi labarin
aurenshi. Ahmad ya masa murna, sultan yace "ina gayyatarku kaida madam ku
tayani sayayya" ahmad yace "karka damu, a shirye muke" daga nan
suka dunguma zuwa kasuwan deirah dubai, matar ahmad nihal ita tayita zaban
kayan lefe su sultan na tayata, gurin kayan bacci sultan yace "ni zan zabi
wannan kam" daria suka mishi ya fara kwasa, a gajiye likis suka dawo gida,
shi kuma ya wuce hotel din daya kama.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[1:18PM, 9/7/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Washe garima haka suka fita, sukayi ta
siyayya, sultan na duba list din su mammi, a ranar suka gama hada lefe,
akwatuna 12, kowanne shaqe da kaya na gani na fada, Wani set din sarqa, dan
kunne, rings da bracelet na gold ya siya mata, wanda fadin tsadarsa ma bata
lokaci ne, Shoes nd bags designers, kayan cosmetics gasu nan birjik, undies,
dogayen riguna kala kala, kai zan muku video kawai kowa ya gani😜. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Kwanan shi uku a Dubai ya gama siyayyar da
zaiyi har da furnitures da kayan kitchen, a rana ta hudu ne ya tura kayan
nigeria shi kuma ya wuce china business trip dinshi. Yau saura sati biyu a fara
shagalin biki, amarya fatu ta fara shan gyara, takanas qawar mammi yar borno ta
aiko matar da zata yiwa fatu dilka da turaren jiki, mummy ta hado
"SINADARAI"😉 ingantattu marasa illah. Sultan kuma waya kan
waya suke da fatu, don wani irin qaunarta da yake fisgar sa har yakan ji kamar
wani zai kwace masa ita. Ita din ma hakan ne, wani zazzafan sonshi take ji a
zuciyarta, gashi tayi missing dinshi sosai. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Dangi yan uwa na kusa har sun fara zuwa,
mammi ta fadawa dangi an samu fatu, wato dangin mahaifiyarta, murna a gurinsu
ba'a cewa komai, kowa yana marmarin yazo yaga fateema nan da mammi take nema.
Akwai wata qanwar kakar fatu wacce take kaman uwa a gurin mammi, don itama
tasha neman addarta wato maman rahmatu mahaifiyar fatu, ana kiranta inna
habiba, tana ganin fatu ta fashe da kuka wai taga yayarta zainabu, kowa ya
ganta sai yayi mamaki don kamanni da takeyi da kakarta sosai, duk da basu san
rahmatu ba sunyi kewarta a matsayinta na
yar uwarsu, fatu taga dangi, tayi murna ta kuma godewa Allah da ya nuna mata
dangin mahaifiyarta masu sonta. Ranar sunday ana saura sati biki, ana yiwa fatu
dilka tana wani tutturo baki wai ta gaji da murje murjen nan, salma cousin din sultan tayi daria tace "murje
murje ko? Wannan kadan kika gani" xahra da bizzy (itama cousin din su
sultan ne, duk sa'anni suke da fatu) suka fashe da daria, fatu da bata san inda
maganan su ya dosa ba tace "ohh nan gaba murjewan zaifi haka? Bizzy tace
"sosai ma, kuma wanda za'a miki nan gaba in bakida dauria har kuka
zakiyi" suka qara fashewa da daria, fatu tayi shiru tana kallonsu one by
one, jikinta yayi matuqar sanyi tace
"baku da kunya" falmata matar da take yiwa fatu dilke wacce bazata
wuce 28yrs ba tace "rabu dasu fateema, suma suna hanya ai, ba'a yiwa motar
gawa daria" murmushi fatu tayi kawai su salma kuma suka ci gaba da yiwa
fatu tsiya falmata na kare ta. Maman dota ne ta shigo dakin tace "wai har
yanzu baku gama ba? Kusan azahar, xahra ba kunce zaku je rabon Iv ba? Xahra da
take shafe shafe da mirrow a hannunta tace "zamuje, amma sai anjima da
yamma" maman dota tace "to shykenan bari a kawo muku abincin ku"
tasa kai ta fita, salma tace "haba bizzy ki shafa a hankali mana, zaki sa
mu rasa ai, irin wannan makkalawan da kikeyi" bizzy kota kulata ta cigaba
da shafawa, salma ta kwace robar dilkan taje bakin kofa ta tsaya, itama tana
shafawa, bizzy tace "ai wallahi baki isa ba, ban shafa a wuyana ba
fa" zagaye dakin suka fara su xahra na musu daria, da yake dakin babba ne,
takanas mammi tasa aka gyara wai wajen gyaran amarya, carpet ne shimfide a
dakin sai katifa guda daya da kujeru one one sitter biyu, sai da suka gaji suka
zauna suna shafawa tsakani da Allah.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Bayan dilkan ya bushe falmata ta shiga
bathroom din dakin don hadawa fatu ruwan wanka wanda shima yasha hadin
turarukan wanka masu dadin qamshi, anan fatu tace kallesu tace "nifa banga
amfanin shafe shafenkun nan ba, ni kunga mijina nake yiwa, kufa? Harara suka
watsa mata, bizzy da aka fi jin muryanta saboda surutu baya mata wahala tace
"aikin banza, idan yazo yabon kwalliyan naki mummurje ki zaiyi" suka
kwashe da daria da yake sun san bata son kalman "murjewa' Itama daria tayi
alamar ko a jikinta tace "wa yaga taliyar hausa ta murji" anan
falmata ta fito tace "fateema ki shiga wanka, bari in je in debo garwashin
yin turare" ta fita, fatu ta shige bathroom tana kada musu duwawu, salma
tace "hhh yarinya zaki gane" bayan ta fito tayi sallah aka mata turaren
jiki, Ta saka wani maroon doguwar riga
cotton mai guntun hannu, fatarta ta qara haske, santsi da taushi, jikinta na
fitar da wani daddadan qamshi mai sanyi, tayi wani fresh da ita, cream dinta
mai hade da kulacca ta shafa a jikinta,
ta murza farar powder ta saka lip balm, da yake ance ta daina kwalliya
mai yawa, abinci suka fara ci suna hiransu duk akan yanda bikin zai kasance,
suna tsakar ci wayar fatu ta fara ringing ta dauka, sunan sultan ne akan screen
din, ta daga ta kashe murya tace "Jannah" gyara zamanshi yayi a kan
kujeran da yake yana murmushi yace "Habibteey ya kike" ta rausayar da
ido kaman yana gabanta tace "lafiya lau" su salma suka sa ihu har
bizzy na kwarewa, yace "su waye haka? Ta kalli su xahra da suke dukan
bayan bizzy wacce ta kware suna dura mata ruwa, tace "yara ne suke
wasa" hararan da suke watsa mata ne yasa ta juya musu baya taci gaba da
wayanta, sultan yace "please kije dakina akan gado zakiga wasu papers a
cikin envelope ki bawa mammi" tace "dakin naka a bude ne? Yace
"ehh a bude ne" tace "ok" ya kashe wayan ta miqe ta dauki
gyalen rigar ta fita zuwa shashen sultan.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:02PM, 9/7/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A hankali ta murda handle din dakin ta
shiga da sallamanta duk da tasan babu kowa a ciki, qaramin palourn nashi tsaf
tsaf kamar baiyi tafiya ba, ta bude kofar dakin ma tayi sallama tareda kutsa
kai ciki, ganin duhu a dakin yasa ta fara lalube gashi bata san inda switch din
yake ba, kafarta ne ya bugi gado, ta daga kafar ta riqe tana wayyo Allah na.
Tuno da cewa tana da waya hannunta yasa ta kunna light din wayar ta duba
qafarta gurin har yayi jaa, ta shafa gurin ta ajiye kafar ta haska dakin, dummm
gabanta ya fadi ganin mutum kwance a kan gadon yana kallon ceiling, tare
fuskarsa yayi yace 'kina haska min ido" fatu ta kasa motsi don tayi
matuqar razana lallai yau tayi gamo da aljani a dakin sultan. Ganin ya tashi
yana qoqarin zuwa gurinta ne yasa ta fasa ihu tace "wayyo mammi....na
shiga uku" tayi hanyar qofa da gudu har tana jefar da wayarta, nan da nan
hasken dakin ya mutu sakamakon mutuwar wayarta da yasha qasa, addu'a takeyi
tana kokawa da kofar yayinda kuma tana juyawa tana ganin inda aljanin yake, ji
tayi an tuntsire da daria hade da kunna hasken dakin, Balloons pink nd white ta
gani ko ina, an qawata dakin dasu, can kuma gefe cake ne madaidaici an rubuta
'fateema is 19' ta dawo da kallonta kan sultan wanda ta tabbatar ba aljani bane
tace "jannah" qarisowa yayi gurinta yana murmushi ya kamo hannunta
har gurin cake din, kallon mamaki take binshi dashi yayinda tana gani ya dauko
lighter ya kunna 3 candles din da suke kan cake din ya juyo gurinta yace
"bismillah" a raina nace Karfa ta kashe candle din da ruwa😂,
itama murmushine a fuskarta tace "with u dear" Rage tsayi sukayi a
tare suka ce one...two....huuuuuhhh suka hure candle din wutan ya mutu, Yana
clapping itama tanayi harda guntun tsallenta, a tare suka yanka cake din yana
"happy birthday to you, happy birthday to you" ya bata a baki itama
ta bashi, sai a sannan suka zauna a bakin gado yace "washhh na gaji"
ta juyo tana kallonshi tana cin cake tace "amma guy din nan ka tsorita ni
wallahi, tukunna ma yaushe ka dawo? Ba sanarwa haka" Kallonta yakeyi yaga
ta qara masa kyau tayi wani bul bul da ita, yace "kinyi kyau" ajiye
sauran cake din hannunta tayi murmushi tace "nagode, nd thanks for
everything" Murmushin shima yayi yace "u ar welcome dear, now
selfie" ai kuwa ta turo baki suka dauka, na biyun kuma tayi murmushi, a
haka suka yita daukan pics kala kala, sai da suka tsagaita ya dauko wani
qaramin akwatin ring daga aljihunsa yace "ga gift dinki" ya bude wani
hadedden zobe ne wanda daga gani na pure azurfa ne, ya saka mata a yatsanta,
fatu ta murna yasa ta kasa rufe baki tace "thank u so so so much, Allah ya
bar mini kai" daria yayi yace "ke daya? Tace "yesss ofcos"
yace "towww" tace "amma kasan na manta cewa yaune birthday na,
ya akayi ka tuna ne? Yace "dama ina tune kuma nasa reminder a phone dina,
jiya a china na ga remindern, so already na gama abunda nakeyi kawai nayi
bookin flight na dawo, tun safe nake gida amma abba ne kawai ya sani" Fatu
da take kallonshi tana qare masa kallo don shima yayi dan haske ya mata kyau
bata san sanda bakinta ya furta "kayi kyau" ya shafa sajensa yace
"godia nake, amma na rame ko? Ta dan hararashi tace "me zai ramar da
kai? Yace "rashinki kusa dani" kafin tayi magana ya jawo ta suka fada
gado ya kashe light din dakin yace "muyi bacci"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Bayan su xahra sun gama cin abinci sukayi
wanka, sukayi shirin fita rabon iv, anan suka shiga cikin gida sukayi yiwa
mammi sallama tace "da fatan ba da fateema zaku tafi ba? Salma tace
"mammi ai ta shigo cikin gida ma" mammi ta kada kai, su kuma suka
fita a motar xahra bixxy na driving. Can bayan la'asar sakaliya suka dawo, a
bakin gate suka hango dandazon yan biki kowa hankali a tashe wai ba'aga amarya
ba!! Mammi tafi kowa rudewa sai kiran numbern fatun akeyi yaqi shiga, ta kira
abba shi kuma bai dauka ba da alama yana gurin meeting, dawowansu xahra yasa
aka fara tambayansu inda fatu take, anan suka ce rabonsu da ita tun suna cin
abinci sultan ya kirata a waya, amma basu san meya fada mata ba ta tashi ta
fita a dakin, da sauri mammi ta kira numbern sultan na china, 'is switch off'
aka fada mata, ta kara kiran numbern abba shiru, anan ta kira jameel ya dauka
yana gaisheta bata saurareshi ba tace "jameel ba'a ga fateema ba, ka kira
sultan in kana da numbern hotel din da yake" jameel da mamaki ya kamashi
yace "mammi ai sultan yana gida, yau da safe karfe 9 naje na daukoshi a
airport" kafin ya karisa maganar mammi ta kashe wayan tayi hanyar part din
sultan ranta a bace, ganin haka yasa kowa binta cikin kidimewa kan me yake
faruwa????<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Yanzu labari ya fara😜<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[2:07PM, 9/8/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A bakin falon mammi ta tsaya tana knocking,
shiru shiru ba'a bude ba yasa ta bude door din ta shiga, a ranta tana ayyana
irin bacin ranta da zata nunawa sultan, ganin ba kowa a falon yasa ta tabbatar
lalle suna daki, kasa motsi tayi ga jama'a a can a bakin kofa, ga sultan nason
sakata kunya, knockin din dakin tayi shiru ba'a bude ba, ta dauki wayarta ta
kira sultan din da number nasa na Nigeria.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A bacci fatu take jin kamar ana bugun kofa,
ta bude idonta tare da zare jikinta daga na sultan wanda baccinsa yakeyi
hankali kwance, barin jikinshi da tayi yasa shi farkawa yana mutsike ido, da
muryansa ta masu bacci yace "fateey yadai? Fatu data kasa bude kofan don
yanda zuciyarta ke bugawa, kuma bata ji an qara knocking ba tace "ana
knockin ne" ya tashi a hankali ya bude kofan, wayamm ba kowa, ya leqa
falon nan ma ba kowa ya juyo yace "babu kowa fateema" ya qarisa bakin
gado ya dauki wayarsa its 4:02pm, yace "lokacin sallah yayi, ki shiga kiyi
alwala muyi sallah" tace "a'a nikam zan tafi, wallahi mammi zata neme
ni" ya tsaya ya riqe qugu yace "ki shiga kiyi alwala nace"
kallonshi tayi ganin ba wasa a fuskarsa yasa ta shiga bathroom din ranta bai so
ba, tana fitowa shima ya shiga yayi alwala, kafin ya fito har ta gyara masa
shimfidin gadonsa ta kimtsa gurin, sallaya ya dauko musu ta karba ta shimfida,
sai a sannan ta tuno bata da hijab, ta kalleshi tace "banida hijab
fa" ya bude wardrobe dinshi ya ciro wani pink hijab wanda daga gani ta
gane nata ne, zata yi magana yayi kabbara ta saka hijabin ta bishi, bayan sun
idar da sallahn sukayi addu'a ta ninke sallayun ta adana, anan ya mata umurnin
su fita, daukan cake dinta tayi suka fito, zatayi cikin gida ya jawo hijabinta
yace "um um, yau tare dani zaki wuni, muje garden" kallonshi tayi
tana murmushi tace "jannah, mammi fa!! Yace "idan kina son mu shirya
ki daina kira mini mammi, gutsureki zanyi ne? Ko ni ba mijinki bane? A hankali
yayi maganan amma da alama ranshi a bace ne, tace "srry, muje to" qin
tafiya yayi, ta jawo hannunshi da kyar ya bita suka tafi. Hira sukeyi cikin
kwanciyar hankali har yamma sakaliya. Anan wayarshi ta fara ringing ya dauka
yace "Hello mammi" tace "ina fateema? yace "gata nan"
tace "ka bude kofan ka bani 'yata" yace "wani kofa? tace
"tambaya na kakeyi? Yace "mammi mufa muna garden tun dazu"
hamdala tayi zuciyarta yayi fess, ta fito daga dakin tana murmushi ganin haka
yasa aka fara tambayan ina fatun?? Tace "suna lambu" su bizzy da
salma ne akan gaba harda gudu gudu, suna isa kuwa salma ta hango cake din kan
table bata bi ta kansu ba ta qarisa zata dauka sultan ya aza mata rankwashi,
"wayyo innata" ta furta a wahale, dai dai nan su mammi suka iso, tana
cewa "ka kyauta, kaji? nace ka kyauta" murmushi yayi yace "ina
wuni mammi" tace "lafiya, yaushe ka dawo? Yace "dazu ne da
safe" tace "shine baka sanar mana ba? Shiru yayi yana kallon bizzy da
take qoqarin daukan cake din itama don taga mammi na kusa, ya make hannunta da
qarfi, ta cire da sauri tana yarfe hannun don ta bugu, anan ya fara gaisawa da
sauran 'yan uwa suna tsokanarsa, sai da kowa ya watse ya rage daga su salma sai
mammi, mammi ta cewa fatu "ki shiga gida fateema" ta tashi ta dauki
cake dinta su salma suka rufa mata baya (kwadayi😜) Guri ya rage daga
mammi sai sultan tace "manga" yace "na'am" tayi shiru can
cikin tsigar rarrashi tace "kaga yanzu ka dawo ko? Kuma saura sati a gama
biki, to please kar inji wata magana ta taso kaji?" Daria yayi yace
"to" da sauri tabar gurin tana cewa "anjima after isha ka sameni
a falon abbanku"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:12PM, 9/19/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">8</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tun daga ranar bai qara kiran fatu gurinshi
ba, hasalima qaura yayi zuwa sabon gidansu da zasu tare, anyi fenti an saka
furnitures da komai an gyara ko'ina das das, gida yayi ready yana jiran amarya.
Ranar wednesday aka yiwa fatu lalle jaa da baqi ya amshi fatarta, Anan ta fito
amarya sak, ga yanda jikinta yasha dilke tana kyalli, Kitso kanana falmata ta
yarfa mata wanda suka zubo bayanta suka qara haska ta, mammi bakinta ya kasa
rufuwa don farinciki, qawayen amarya su xahra, bizzy, salma, sai shiga da fita
sukeyi. Su kaka sunzo tare da jagorancin kawu muntari, da inna asabe da goggo
innani, ba yanda mammi batayi ba kaka ya kwana yace inaa!!! Zasu ga gida daga
baya, a ranar suka koma shida kawu
muntari bayan mammi ta cika su da abun biki, aka bar su inna asabe suna santin
gida da daular da fatu take ciki.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Ranar thursday akayi KAMU inda amarya da
ango suka fito kamar taurari, gashi suna kama, anyi pictures kala kala, abun ya
qayatar ba laifi, ranar fariday akayi WALIMA Inda amarya tasha laffaya fara sol
mai adon golden, ansha wa'azi sosai kuma anyi rabon kaya irinsu hijabs, paper
bags masu hoton amarya da ango, atamfofi,
da sauran kayan da ake rabawa a bikin 'yayan manya. Washe gari saturday
aka shirya dinner qarfe takwas na dare no african time, saboda ba'ayi daurin
aure ba yasa dinner ya zama big event, abokanan abba, frnds din sultan, abokan
kasuwanci duk za'a hallara. Jameel babban abokin ango shi ya shirya komai,
babban hall makeke aka kama inda aka qawata shi da ado masu kyau da ban
sha'awa, a can step din sama na hall din Royal kujeru biu ne na amarya da ango,
a qasa kuma tables ne kowanne da kujeru 4, gurin yasha decoration ba laifi.
8:08 kowa ya hallara amarya da ango kadai ake jira, ko ina ka duba mutane ne
kowa yayi shiga ta alfarma, manyan yan kasuwa da qososin gwamnati da sauran
jama'a, abba na hango cikin frnds dinsa ana raha hatta daddyn jameel wanda bai
cika zaman qasan ba ya hallara. Mammi da mummy ma ba'a barsu a baya ba, sunyi shiga ta mutunci suna zaune cikin
qawayensu ana jiran shigowan amarya da ango, su inna asabe ma sunje. Anan
abokin su jameel Naseer ya tashi da mike a hannunsa yadan bubbuga yace
"hello" aka ce "hiiii" ya gabatar da shigowan couple, kowa
ya qura ido yana jira, a hankali aka saka kida mai sanyin sauti, farouq da wata
yarinya ce wacce zasuyi sa'anni suka fara shigowa, yana sanye da coat brown ita
kuma gown pink an gyara mata gashinta ya zubo bayanta, farouq na riqe da
hannunta sunyi kyau, anan sultan da fatu suka shigo suma hannunsu a hade sai
doka murmushi sukeyi, tafi aka fara raff! rafff! raffff! Sanye take cikin riga
sa siket na hadedden code lace milk color, sai head da shoe dinta red, veil
dinta mai walwali da kyau shima red ta saka a kafadanta daya ya zagayo ta
qugunta an riqe shi, sultan kuma jamfa da gare ne milk color sai hularsa zanna
brown, takalminsa da agogonsa brown, tafiya suke yi da murmushi a fuskar su,
sunyi kyau iya kyau, hasken flashes din camera na masu daukan hoto da kuma
phones din mutane ya qarawa gurin haske da walwali, bayansu kuma qawayen amarya
sanye da ankon pink gown da head milk, abokan ango suna sanye da brown jamfas,
har suka iso gurin zaman su suka zauna suma qawaye da abokai suka zauna a inda
aka tanadar musu. Aka bude taro da addu'a, aka fara shagali, jameel ya bada
tarihin ango, xahra kuma ta bayar dana amarya, kowa cikin harshen turanci,
Mammi, abba da ango suma sun fito sun miqa godiarsu ga baqin da suka halarci
wannan taro, sultan da fatu suka yanka cake, ya yanko qarami ya bata a baki ita
kuma ta yanko dan babba ta bashi aka saka tafi, An kira amarya da ango su fito
yin rawa, abokanan abba suka fita ana musu barin kudi, bayan sun gama qawayen
su mammi ma suka fito suka yi nasu liqin, komai ya tafi yanda ake buqata ba
hayaniya da cunkusowa, karfe 9:14pm abokan abba suka fice bayan sun cika couple
da gifts, su mammi da qawayenta ma suka rufa musu baya, guri ya rage daga
abokan ango sai qawayen amarya, sunyi shagalinsu son ransu amma sultan ya hana
fatu rawa wai bbu wanda zai gane mishi jikin matarshi na karkaduwa. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">An kusan tashi ya jawo hannunta ya rada
mata a hankali "daga nan gidanmu zamu tafi ko? Ta harareshi qasa qasa tace
"a'a nikam, ka maida ni gurin mammi na" murmushi yayi yace "kina
wasa yarinya" qarfe 10:10 suma suka tashi, mahmud sai lilliqewa salma yake
yi tana basarwa, da za'a koma gida ma shi ya daukesu dasu bizzy, jameel ya
tattari matarsa da qaton cikinta shima.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sultan ke drivin yayinda fatu ke gefenshi
tayi miqa tace "waashhh, na gaji wallahi" kallonta yayi ta gefen ido
yace "dats y nace mu tafi gidanmu zaki fi watstsakewa" da sauri ta
girgiza kanta tace "um um nikam, gida zan tafi" yanda tayi magana ya
bashi daria yace "nayi hakurin 1 month kinga zan iya yin na kwana daya,
inace gobe za'a kawoki? Daga gobe shykenan"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:12PM, 9/20/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">9</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Jikinta yayi sanyi tayi shiru, bai qara
cewa komai ba har suka iso gida, ta bude kofa ta fita a hankali yana kallonta
ta juyi tace "good night" yace "Ahaa" ta rufe motar, jin
shiru bai kirata ba har ta kusa shiga gida yasa ta juyo ta tsaya a gurin window
dinshi tace "na bata maka rai ne? Ya girgiza kai yace "a'a me kika
gani? Tayi shiru kanta na qasa yace "ki shiga gida dare nayi, kinga mune
last din shigowa" a sanyaye tayi hanyar gida tana jin jikinta ba dadi, sai
data kusan shiga gida yace "heyyy" ta juyo yace "kinyi
kyau" murmushine ya subuce a fuskarta tana kallonshi har ya fice daga
gidan. Washe gari hka ta tashi jikinta kamar wacce aka yiwa duka, haka dai ta
lallaba har bayan isha, tayi wanka aka bata kaya fitted gown na lace green, aka
kafa mata dauri tasha make up, jikinta da kayanta sai qamshi yakeyi. Wani abu a
gora kamar madara falmata ta miqa mata tace "gashi kisha inji mummy"
fatu ta bata fuska tace "nikam abubuwan nan bazasu qare bane? Lubna da take
gefenta ta dafa kafadarta tace "kisha fa" fatu ta karba ta kafa kai
ta shanye tass ta ajiye goran tace 'Alhamdulillah" daria su salma suka
saka. Anan mammi ta shigo da wani babban mayafi white mai adon stones kala kala
ta daurawa fatu a kanta tace "muje gurin abbanku" ta riqo hannunta
har palourn abba, sukayi sallama suka shigo, mammi ta zauna a kujera fatu kuma
ta zauna a qasa gurin kafafuwanta. Fatu ta gaishe da abba, ya amsa yana mai
fara'a dai dai nan sultan ya shigo shima sanye yake da green shadda jamfa da
hularsa itama green, sai zuba qamshi yakeyi ya samu guri kusa da abba shima ya
zauna yana satar kallon fatu wacce ta sunkuyar da kanta qasa sosai har baka
kallon fuskarta. Abba ne yayi gyaran murya ya fara musu nasiha dukansu, sosai
nasihar sa ya ratsa zuqatansu bayan ya gama sultan ne yayi magana yace
"abba mun gode" anan mammi ma ta fara nata, a lokacin fatu ta fara
kuka harda shesheka, idon sultan na kanta. Sai da mammi ta gama nata nasihar ta
kalli sultan tace "ga amanar fateema, marainiyace gaba da baya, qanwarka
ce yar uwa, kuma mata a gareka, don Allah idan tayi laifi a gyara mata ta hanya
mai kyau, Allah ya baku zaman lafiya" fatu bata samu damar magana ba don
irin kukan daya kwace mata tunowa da iyayenta da tayi, anan ta bawa kowa
tausayi, abba yayi addu'a aka shafa. mammi ta dauketa zuwa gurinsu inna asabe,
suma nasihan dai suka maimaita aka shigar da fatu mota mummy a gefenta da goggo
innani, har aka iso gidanta dake New GRA bata bar kuka ba. Gida ne madaidaici
hawa daya, zagaye yake da flowers masu ban sha'awa ciki da waje, ana shigowa
zaka iske parkin space wanda a kalla zai dau motoci 5 zuwa 6, sai ta bayan
gidan lambu ne shima madaidaici, babban palour ne a qasa mai dauke da set din
kujeru da tangamemen tv sai sauran kayan kallo, an qawata falon ba laifi, a
palon akwai kitchen sai wasu dakuna biyu, dayan kusa da kitchen daya kuma kusa
da toilet in palour, still a palourn akwai wata kofa wacce ba'a bude take ba.
Upstairs aka haura da ita, nan ma zaka iske wani qaramin palour ne shima da
kayan kallonsa,sai dakuna hudu, A cikin dakunan aka bude daya aka shigar da
fatu, har kan qaron royal bed dinta mummy ta zaunar da ita tareda dan daga
lullubin kan fatun tace "fateema kukan nan ya isa haka, ki share
hawayenki" anan ta ciro hanky daga jakarta ta sharewa fatu fuska ta gyara
mata shi, tace "karki qara bata fuskan ki kinji? Fatu ta daga kai tana
ajiyar zuciya, lokacin qarfe 8:43pm mummy sukayi haraman tafiya fatu ta riqe
gyalenta tace "mummy zan biku"
murmushi mummy tayi tace "kiyi hakuri ki zauna gidan mijinki fateema, ai
gasu xahra zasu kwana miki" jin haka yasa fatu murmushi tace "to
shykenan mummy" su goggo innani suka mata sallama kan gobe zasu koma kumo,
ta musu sallama tace su gaishe mata da kaka" gida ya rage daga amarya sai
qawayenta, salma da bizzy na waya da alama da samarinsu ne yayinda lubna da
xahra da fatu kuma suke hira, fatu tsakaninta da Allah ta yarda zasu kwana bata
san wayo mummy ta mata ba. Goma saura wayar lubna ya fara qara ta dauka ganin
sunan mijinta, yace ta sauko su tafi. Bayan ta kashe ne ta kalli su bizzy ta
musu ido, nan da nan suka fahimta. Xahra ce ta fara tashi tace "nifa banga
gidan nan da kyau ba, bizzy kuzo muje mu gani" aiko nan suka miqe suka
fita, lubna da take murmushi ta juyo tace "kinsan nikam bazan kwana ba,
bari in tafi DJ yazo" fatu ta marairaice fuska tace "shi yaya jameel
dan kwana daya bazai bar mana ke ba? Lubna tayi daria yayinda take yafa
gyalenta tace "nima bazan iya ba, sai da safenki amarya" fatu ta
tashi zata rakata lubna tace "a'a yi zamanki, ba komai, bari in kira miki
su bizzy" Tana fita fatu ta koma ta zauna harda cire mayafi, tana zaune
shiru har kusan 15mins kuma bata ji motsin su ba, tsoro ne ya shige ta a take
tace badai tafiya sukayi ba. Da sauri ta fito daga dakin, ganin basa palourn
sama yasa ta sauko qasa nan ma basa nan, cikinta ne ya fara bada stars tabbas
guduwa sukayi, a'a ta haura sama da gudu tana bubbude dakunan tana leqawa,
kowanne ta bude basa ciki, room din qarshen ne taga hatta door din daban ne,
nan ta murda handle din ta shiga dai dai lokacin da sultan ya fito daga wanka
da jallabiya fara sol a jikinshi yana taje gashin kansa, jin an bude kofa yasa
ya juyo yana kallonta yana mata murmushi, akan mirrow ya ajiye comb din ya
dauki wani remote ya danna saitin kofa, nan take kofar ta rufe, fatu ta juya
tana qoqarin budewa da taga bazai budu ba ta juyo fuskarta kamar wacce zatayi
kuka tace "inasu xahra? Sultan daya harde hannu yana kallonta sama da qasa
yace "jameel ya maida su gida" Ido ta zaro ya gyada mata kai hade da
kashe mata ido ya nufo gurinta yana cewa "WELCOME HOME HONEY"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[2:13PM, 9/21/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">0</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Tsayawa yayi daff da ita har suna shaqan
qamshin jikin juna yace "me zaki yiwa su xahran? Ta dake tace "mummy
tace zasu kwana ai" yayi daria yace "wayo ta miki, babu wanda zai
kwana miki sai ni kadai" ta turo baki kamar zatayi kuka tace "nifa...
nifa..gaskia ka kiramin su xahrah" murmushi yayi ya juya ya dauki remote din
ya danna kofar ta bude yace "kije kiyi alwala ki dawo yanzu" tace
"nayi salla fa" yace "I know, ko zakiyi anan? Tace
"a'a" tare da ficewa daga dakin. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Bata jima ba ta dawo da alama tayi alwala,
sai data shigo ta manta bata dauko hijab ba ta juya zata koma, ya tsayar da ita
yace "ina zakije? Tace "zan dauko hijab ne" yace "me zakiyi
da hijab din? Tace "zan saka muyi sallah mana" yace "sallahn me?
Tayi shiru murmushi yayi irin na😎 yace "oohh wato kinsan ana
sallah kenan, ashe ba sai nasha wahalan koyar dake komai ba" bata kulashi
ba ta qara niyyar juyawa yace "wait" yaje gaban makeken wardrobe
dinshi ya bude ya dauko mata wani white hijab ya bata. Mamakine a fuskarta don
this is the second time da yake bata hijabi daga wardrobe dinshi kuma duk nata
ne. Tace "a ina ka samu? daga kafada yayi yace "nima ganinsu nakeyi a
gurina" tace "serious dai" yace "a gurin shanya kaya nake
gani sai in dauka" daria tayi tace "to a dalilin me? Me kakeyi dasu?
Yace "ohoo, yanzu ba gashi sun miki amfani ba? Lets pray" Ba musu ta
bishi yaja su raka'a biyu suka sallame. Ya juyo ya dafa kanta tare da kwararo
addu'o'I da musulunci ya tanadar domin samun zaman lafiya da zuria dayyiba.
bayan ya gama, ya qara wasu addu'o'in suka shafa. Ya miqe tareda da fita daga
dakin, a hankali ta tashi ta linke darduman sallah tareda hijab dinta ta adana
su, ta rasa me zatayi gashi gabanta sai dukan uku uku yakeyi, bata qara 2mins
ba ya shigo da ledoji a hannunshi, ya ajiye a lallausan carpet din dake
tsakiyar dakin ya zauna yace "kizo" ba musu tazo itama ta zauna dan
nesa dashi. Murmushi yayi ya kada kai ya ciro kazar dake cikin ledan ya daura
ta a kan plate din da ya shigo dashi, fresh milk ya saka a glass cup ya miqa
mata, ta girgiza kai yace "what? Tace "na qoshi" bai ajiye hannunsa
ba yace "gashi" ta karba, ya qara tsiyaya wani a cup, hankali ya
yanko tsokar kazar tare da kaiwa bakinta ta juya fuska, murmushi yayi ya gyara
zama yace "kinsan me? Ta juyo tace "a'a" yace "ranar dinner
saura kadan in shaqe, cake din da kika bani ya mini qato" daria tayi tace
"sorry dear" yace "noo, naqi hakurin" wasa wasa ya rinqa
janta da hira har ya miqa mata kazar ta karba ta fara ci tana korawa da fresh
milk din, da na hannunta ya qare da kanta ta qara yanko wata tsokar, shima a
haka yana ci sai da sukayi nakk! Ya cire hannunshi yace "Alhamdulillah,
anaso ana kaiwa kasuwa, gashi ke kadai kin yiwa kazar illah" ta sunkuyar
da kanta kasa tana juya empty glass cup din dake hannunta tace "ba wayo ka
mini ba, kana ta jaana da surutu" yace "ba wani dama jira
kikeyi" ya fada yana murmushi, itama murmushin tayi ta fara tattara gurin
ta kai kitchen. Dakinta ta wuce ta cire kayan jikinta ta fada wanka, bata jima
ba ta fito ta shafa humran ta mai dadin qamshi saqo saqo na jikinta, ta shafa
cream dinta mai kulacca, tana tsaye a bakin wardrobe ta rasa wani night wear
zata saka don gaba dayansu basuda M😉. Tana tsaye taji mutum a bayanta
ya rungumota a hankali ya daura habarshi a shoulder dinta ya zagayo hannunsa ta
kan tummy nata yace "in tayaki zaba?<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">saboda irin yanda jikinta ya mutu yasa ta
kasa koda kwakkwaran numfashi, ya daga ido ya kalleta yaga yanda tayi kasa da
kanta dan mitsitsin bakinta a bude tana numfashi, saketa yayi ya shiga duba
kayan, ya dauko daya ya manna a jikinta ya dan dubeta, tana nan tsaye kamar
statue da dan qaramin towel dinta, ya ajiyeshi ya dauko wani purple dan guntu
silky one, gaban rigan anyi ado da pink flowers, hannun rigan irin na bra, ya
manna a jikinta yace "wannan zai miki kyau" ta dago ido ta kalli
rigan tace "nifa ba irinsu nake sakawa a gida ba" murmushi yayi ya
cire rigan daga hanger ya bata yace "banbancin gida da gidan miji kenan,
idan kin gama ki sameni a dakina akwai abunda zan nuna miki" ya shafa
sajenshi ya fita daga dakin, binshi tayi da ido yana fita ta murguda baki hakan
yayi dai dai da juyowanshi yace "ni kika murgudawa baki? Ehhh lallai zaki
gane" ya fita. Murmushi tayi ta dauki rigan tana kallo, ganin ba sarki sai
Allah yasa ta saka, ba qaramin kyau rigan ya mata ba, ta zamo kamar wata baby
doll, kallon kanta tayi a madubi, ta juya ta qara juyawa, qarar wayanta ne yasa
ta tsaya da juye-juyen kafin ta dauka ya zama missed call, body spray ta fesa
ta saka dogon hijabinta ta kashe light din dakin ta fita tareda rufe kofan. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[7:10PM, 9/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">1</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A hankali ta murda handle din kofar sultan
ta kutsa kai tareda sallama a bakinta, yana zaune a bakin gado yana danne-danne
da laptop dinshi, dago da kai yayi ya amsa mata, tsayawa tayi a bakin kofar
tace "kace zaka nuna min abu" yace "yeah, zo ki gani"
yayinda ya mai da kanshi kan laptop din yana dannawa. Dan nesa dashi kadan ta
tsaya tace "gani" hannunsa ya miqa mata alamar ta taho, kamar bazata
je ba amma ta miqa nata hannun, jawota yayi jikinshi tareda cire hijab din
jikinta, hakan yayi daidai da mutuwar laptop din, ya rufe ya ajiye a bedside
yace "labari zan baki, amma first ki saki jikinki kuma karki tsorita!!!<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Washe gari misalin 8:45am yaji ana buga
kofa, bude idonshi yayi a hankali ya sauqe akan kyakkyawar fuskar matarshi
fatu, wacce baccinta takeyi hani'an, murmushine ya subuce a fuskarsa, lokaci
daya kuma tausayinta ya mamaye zuciyarsa tuno da irin wahalan da tasha jiya,
"she's special" ya furta qasa-qasa yayi kissing goshinta tareda zare
jikinshi a hankali daga jikinta. Jallabiyarsa ya zura tareda fita daga dakin
zuwa palourn qasa inda ake bugu har yanzu. Salma da bizzy ya gani bayan ya bude
qofar kowacce bakinta a washe da food warmers a hannunsu, bizzy tace
"sannu ya sultan" salma tace "ina kwana, an tashi lafiya? Bizzy
tace "ya gajiya? Kallonsu yakeyi ya zura musu ido kuma bai amsa duk
gaisuwan da suke masa ba. Ganin haka yasa suka rage fara'a salma tace
"mammi ce tace mu kawo muku breakfast" Tokare qofar yayi yace
"da sanyin safiyar nan? Kallon juna sukayi salma ta zaro ido tace "ya
sultan yanzu fa karfe 9, ai ko na goye yasan rana ta fito" ya harde
hannayensa yace "magana zaki fada min ne? Salma tace "wane ni? Sorry.
To bari mu shiga mana" ta fara qoqarin yin step gaba. Ya sauqe hannayensa
yace "ba matsala, kawo abincin, mungode" Baki suka sake yayinda ya
karbi na hannun bizzy ya ajiye a falon, ya qara karban na hannun salma shima ya
ajiye yace "ku huta gajiya" Ruff ya rufe kofar ya barsu tsaye a
gurin, mahmud da yake cikin mota don shi ya kawo su ya tuntsire da daria harda
riqe ciki, ganin sun juyo yasa ya masge ya fuske. Jiki a sanyaye suka qaraso
gurin motar salma kamar ta nitse don kunya don mahmud da take yiwa big time
yaga an mata ajii down. Babu wanda yayi magana har suka shiga motar, maigadi ya
bude musu gate suka fita bizzy tace "ohhh yanzu karfi da yaji ya hanamu
shiga? Daria ne ya subucewa mahmud, yanayi a hankali salma ta harareshi ganin
haka yasa bizzy itama tayi daria tace "ba laifinshi bane" anan abun
ya zama na tsokana suka dinga darawa har suka iso gida.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> Sultan na komawa daki yaga ba fatu akan gadon,
dakinta ya nufa anan ya samu ta shiga bathroom. Komawa dakinshi yayi yana sosa
kai shi daya yana murmushi.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Ruwan zafi ta qara hadawa ta shiga tayi
sitbath duk da cewa jiya sultan ya gasata, tafi 15 mins a ciki sannan tayi
wanka da ruwan dumi tayi brush ta fito, ba laifi ta daina jin ciwon da jikinta
yake mata sai abunda ba'a rasa ba. Cream dinta ta shafa tayi light make up,
riga da siket na wani super wax mai yellow nd blue ta saka, dinkin ya amshe ta
kamar a jikinta aka dinka, dauri ta kafa kamar mai shirin zuwa liyafa, bin
jikinta tayi da turare ta ko'ina. Tana ajiye kwalban turaren sultan ya shigo
shima da alama yayi wanka don ya canja kaya, brown three quarter ne a jikinshi
da black t-shirt an rubuta _special you_ a jiki, sai zuba qamshi yake yi
sajenshi da gashin kanshi ya kwanta luff luff yana kyalli. Sunkuyar da kanta
tayi don irin kallon da yake aiko mata ta mirrow bazata iya juraba. A hankali
ya qaraso gurinta ya rungumeta ta baya tace "ina kwana" yace
"lafiya lau, kin tashi lafiya? Tace "lafiya" yace "ya jikin
kuma? Shiru tayi ya juyo da ita suna fuskantan juna fuskarsa so serious yace
"har yanzu kina jin zafi, sorry habebteey. Ok dauko gyalen ki mu tafi
hospital" Ta marairaice fuska tare da dago fararen idanunta tace
"nifa lafiyata kalau, bari in sauka in mana breakfast"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Ya kama hannunta yana kallon cikin kwayar
idonta yace "are sure bakijin komai? Ta daga kai yace "um um fa"
tace "Allah naji sauqi" murmushi yayi yace "ok Allah ya qara
lafiya, kinyi kyau dear" murmushi tayi tace "thanks" yace
"shi kadai kika ji? Baki amsa addu'an da na miki ba" kwace hannunta
tayi a hankali ta fara tafiya tace "zan hada mana break fast" binta
yayi yana cewa "mammi ta aiko mana" a dinnin ta tarar da food flasks
din zata wuce kitchen ta dauko plates da cups ya tsayar da ita yace "ki
huta, don naga baki dawo normal ba" ya zaunar da ita kan daya daga cikin
chairs din dinning table din shi kuma ya wuce kitchen. Bai jima ba ya fito riqe
da plates da cups a hannunsa ya ajiyesu akan table din ya fara servin dinsu,
ferfesun kifi ne sai masa da miyan ganye wacce tasha tsokokin nama, kunun gyada
ya saka musu a cups din ya turawa fatu gabanta, anan ya kalleta yaga ta zuba
masa ido tun shigowansa take kallonsa tana jin wani irin sonshi na fisgarta,
dan fulani kyakkyawa wai mijinta ne ita dayanta, gaskia na taki sa'a.... iskan
daya hura mata ne yasa ta farka daga kogin tunanin da ta fada, murmushi ne a
fuskar sa yace "what are u thinking? Ko na miki kyau ne? Murmushi tayi ta
kalli abincin gabanta tace "nagode" A hankali suke cin abincin suna
hira jefi-jefi har suka kammala, ya dauki used plates din ya kai kitchen fatu
ta bishi da cups din, anan suka wanke hannu, zatayi<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> wanke-wanke
yace "noo, ki bari akwai masu aiki, zasu zo suyi" zatayi magana ya
daura yatsansa a kan lips dinsa yace "shhhh, muje muyi bacci"<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">*AFTER 3yrs*<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:12AM, 9/23/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">2</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">*AFTER 3YRS*<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Gurin cike yake da mutane, ko'ina ka duba
group group ne na family sunzo taya 'yan uwansu murnan gama university. A cikin
su na hango familyn su fatu, mammi, mummy, lubna da jameel da 'yarsu yar
shekara 2 da rabi, mai sunan mummy ce wato kulsum amma ana kiranta khairy,
amrah ce a gefe ta zama budurwa tana bawa al'ameen ruwa a baki, yarone dan
shekara da wani abu, yana gama shan ruwan ya wuce gurin mamanshi salma matar
mahmud yana cewa "ummii give me cake" dan gaba dasu naga fatu tareda
sultan suna zaune abinci take zuba masa a plate yayinda yake qoqarin bude Qaton
cooler da sukayi guxurin drinks a ciki, coke ya dauko ya balla marfin ya fara
sha, tana gama saka masa ta miqa mishi ya karba ya koma gurin su jameel da
mahmud wanda suma abincin ne a gabansu. Anan suke labarin yanda graduation din
ya qayatar, fatu ta fito da flying colors wanda hakan ba qaramin dadi kowa yaji
ba, mammi harda hawaye. Bayan an gama shagali suka kama hanyar gida. Kai tsaye
kowa ya wuce gidansa don irin gajiyar da suka kwaso, tun safe suke cikin GSU
sai yanzu bayan la'asar suka koma gida. A falo fatu ta yada zango ta dafe kanta
tana tunani. Shigowan sultan yasa tayi saurin sauqe tagumin ta qaqaro murmushi,
fuskarsa da damuwa yazo ya zauna kusa da ita yace "what again, nikam bakya
tausaya min ne? Ya kike so inyi ne? Tace "babu komai fa, kawai gajiya na
debo ga ciwon kai da yake damuna" Hugging dinta yayi tsam a jikinshi yana
buga bayanta, a hankali wasu siraran hawaye suka gangaro daga idanunta, da wayo
ta gogesu don kar sultan ya gani. Mintuna kadan suka yi upstairs. Dakinta ta
shiga shima ya wuce nashi, ta kwabe kayan jikinta ta shiga wanka. Ruwan mai
dumi ta hada a bathtub din ta diga turaren wankanta wanda bata rabuwa dashi tun
aurenta yau shekara uku. Shiga ciki tayi ta zauna tareda sauke nannauyan ajiyar
zuciya. A haka ta fara tunani..... tun bayan aurensu suke dokin samun haihuwa
amma har yau Allah bai basu ba, shekara da aurensu mammi ta kira fatu gida take
tambayanta "fateema kinyi planning ne? kina school may be kina tsoron
wahala, ga karatu ga yaro ko? Don Allah Ki bari ki haihu in yaso ni zan karbi
babyn" fatu tace "mammi wallahi babu abunda nayi, har asibity naje a
dubani ko inada matsala ne suka ce a'a, mammi ban san ya zanyi ba" ta
qarisa maganan tana hawaye. Anan kuma mammin ta shiga lallashinta tana bata
baki, tace "ki kwantar da hankali, Allah zai baki a lokacin da ya dace,
kinga mahaifiyarki ma sai data shekara 9 kafin ta haifeki a labarin da naji, ni
kuma kinga daga nayi miscarriage sai su rasu suna jarirai, mu kuma haka Allah
yaso ya ganmu. Muyi tawakkali" fatu ta jinjina kai tana share hawayen
fuskarta. Daga ranan mammi bata qara mata magana akai ba sai qoqarin ganin ta
kwantar mata da hankali takeyi. Shima sultan ya taba mata kwatankwacin haka
still shekaransu biyu da aure lokacin mahmud da salma sunyi aure, salma ta
haihu ana gobe suna, sun fita shopping din kayan suna yaga wani feeding bottle
dan qarami mai kyau, ya dauka yana juyawa a hannunsa, anan ta dauko wani riga
na jarirai tana nuna masa amma hankalinshi nakan feedern, tabashi tayi ya juyo
da dan murmushi a fuskarsa yace "wannan ya miki kyau" itama murmushin
tayi tace "yayi kyau" yace "zan ajiyewa babyn mu da zamu haifa"
daga kanshi yayi kamar mai tunani can yace "yau 2yrs da aurenmu harda wata
uku, anya fateema banida matsala kuwa? Ya sauqe Idanunshi a kanta yaga har ta
fara kuka, kafin yayi magana ta fita daga gurin, ranshi a dagule yaje ya biya
abubuwan da suka siya ya kai mota, a motar ya sameta tana kuka ya ajiye ledojin
shopping din a backsit ya zagayo zuwa mazauninsa, yana shiga ya jawota jikinshi
yace "na bata miki rai ne? Ta girgiza kai yace "to meyasa kike kuka?
Tayi shiru yace "fateema talk to me" share hawayen fuskarta tayi tace
"babu komai" yace "don kawai nace ko inada matsala? Last year
mammi ta mini magana akan ko munyi planning nace mata a'a, amma ta tambayeki
may be kinyi ban sani ba, wanda kuma nasan hakan zaiyi wuya, bayan ta kiraki ne
take sanar dani cewa babu abunda kikayi lokaci ne kawai baiyi ba, ta fada min
cewa kinje asibity wanda a sanina baki fada min zaki je test ba, amma sanin
irin halinda kike ciki yasa kwata kwaata banji raina ya baci ba kuma na nunawa
mammi cewa da sanina kikaje" ya dago fuskarta yace "damuwarki daya: mammi
tana son jikoki nd ni kadai ne danta kina tunanin ko hakan zaisa in qara aure!
Ni mata biyu nake da niyyan yi kuma already na auresu" a firgice ta miqe
daga jikinshi lokaci daya kuma tace "aure?? Mata????<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:00PM, 9/24/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">3</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Ya gyada mata kai yace "dayar fateema
mahmud dayar kuma fatu mamuda" ya qarisa yana daria, duka ta kai mishi a
kirji kana ta juya mishi baya tana kallon window, share hawayenta takeyi tana
murmushi, Allah ne kadai yasan yanda zuciyarta tayi pounding jin cewa sultan
dinta yayi aure, ya jayota tana qoqarin kwacewa ita ala dole tayi fushi,
matseta yayi sosai ya juyo da fuskarta har suna shaqan numfashin juna yace
"u ar d only one I need, kece fateema kece fatu so ke kadai kin
isheni" ya dan sassauta riqon daya mata yacigaba "amma saidai bamusan
abunda Allah ya tanadar mana gaba, amma in dai nine u ar d one nd only"
murmushi ya subuce a fuskarta tace "abunda yasa kaga nayi haka bawai
tsantsan kishi ba ne, nooop tunanina cewa kayi aure baka sanar mini ba wanda
hakan ya nuna rashin matsayina kenan a gurinka, babu macen da zata ji dadin
cewa mijinta<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Yayi aure ba tare da saninta ba. Naji dadin
maganarka na cewa I am d one nd only kuma daga baya ka fada min gaskia cewa
bamusan abunda Allah ya tanadar ba, yana daya daga cikin abunda yasa nake qara
sonka fadin gaskiarka, Ban taba addu'an zama ni daya ba don nasan kai *mijin
mace hudu* ne littafin eeshmal. Sai dai koyaushe addu'ana Allah ya kawo
abokiyar zama tagari" shafa kanta yayi yana murmushi yace "Ameen, in
kuma ni mijin mace daya ce Allah ya qara mana zaman lafiya da zuria masu
albarka" tace "Ameen Jannah"...... kwankwasa kofan bandakin da
akeyi yasa ta dawo daga tunanin da takeyi. Tayi gyaran murya, bude bandakin
yayi yace "lemme join u" ta karkada mishi kai alamar a'a, bata fuska
yayi yace "please" Tace "ok" wankansu sukayi suka shirya
cikin qananan kaya, zama sukayi a palour suna kallo suna hira, wayar sultan ne
ya fara ringing ya dauka yace "hello" magana aka fada mishi, ya dan
kalli fatu kamar mara gaskia yace "zan kira anjima please, bye" fatu
bata ma jishi ba don kallonta take yi. Washe gari da asuba bayan sunyi sallah
sunyi karatu dama wannan qa'ida ce har sai rana ta fito, fatu tayi addu'a ta
shafa ta miqe ta niyyar kwanciya a gado ya tareta yace "sai ina? Tace
"bacci jannah" yace "noop ba yanzu ba, muje in tayaki shirya
kaya, tafiya zamuyi" Tace "ok" wankansu sukayi suka shirya cikin
qananan kaya, zama sukayi a palour suna kallo suna hira, wayar sultan ne ya
fara ringing ya dauka yace "hello" magana aka fada mishi, ya dan
kalli fatu kamar mara gaskia yace "zan kira anjima please, bye" fatu
bata ma jishi ba don kallonta take yi. Washe gari da asuba bayan sunyi sallah
sunyi karatu dama wannan qa'ida ce har sai rana ta fito, fatu tayi addu'a ta
shafa ta miqe da niyyar kwanciya a gado ya tareta yace "sai ina? Tace
"bacci jannah" yace "noop ba yanzu ba, muje in tayaki shirya
kaya, tafiya zamuyi" Ta ware eyes tace "ina? Yace "around da
world" aiko da gudu ta dane kanshi tana daria shima tayata yayi. Dama ya
mata alqawarin in ta gama skul zasu fita yawon bude ido.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> Saai
da suka nitsu tace "thanks jannah, Allah ya saka da alkhairi" yace
"Ameen, oyaa dauki abunda kike buqata don qarfe 9 jirginmu zai tashi"
a qaramin akwati ta hada abubuwan da take buqata don ya hanata daukan kayan
sawa wai zasu sayi new ones, dan sinadaranta, undies da turarukanta sai dan
abunda zata buqata, kafin 8 sun gama shirinsu tsaff, suka rufe ko'ina suka
fito, doguwar riga ce a jikinta indian design mai purple nd pink, sai baby
hijab dinta black, takalmi da jakanta ma black, tayi dan make up tayi kyau
abunta kamar sweet 16 kai kace bata yi shekara 22 ba. Shi kuma jeans da
riganshi t-shirt ya saka yana riqe da jakan laptop dinshi sai dan qaramin
trolley dinshi yana ja, a palourn qasa suka hadu yace "kinyi kyau
habeebtey" tace "thanks jannah, kaima kayi kyau kamar wani dan
saurayi" daria yayi yace "me banbancina da saurayi? Itama ta dara ta
nuna kanta da yatsa tace "gani kuwa, idan aka ganmu tare ansan lallai ka
ajiye iyali" Kayansu suka saka a bayan mota tayi driving dinsu zuwa gidan
mammi suka mata sallama ta bisu da addu'a, tana jin dadin irin yanda suke zaman
lafiya, dadi fall a ranta ta koma gida yayinda drivern abba yayi drivin dinsu
zuwa gidan mummy. Itama suka mata sallama farouq yake cewa "da ana hutun
school dana biku" fatu tace "next time da kai zamu tafi". <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A airport driver ya ajiyesu su kuma sukayi
proceeding jirginsu ya daga zuwa abuja, daga nan suka qara shiga wani zuwa
Mauritius, daki suka kama a wani 5star hotel, sun zaga cikin gari sun bude ido,
kwanansu 5 suka daga zuwa india, shima basu jima ba suka wuce london, paris,
china, daga nan suka wuce saudi arabia sukayi umrah, satinsu biyu a qasa mai
tsarki sannan suka wuto dubai, anan sukayi masauqi a wani apartment da sultan
ya siya, da yake fatu tana zuwa dubai in anyi hutu, kuma harkan business dinsa
yafi yawa anan dubai din. Fatu ta cika tayi bul bul abunta ga wani haske data qara.
Satinsu biyu sukayo haramar dawowa gida, tsaraba kam sun kwaso shi, da safe
jirginsu ya tashi zuwa Abuja Nigeria, daga nan suka hau na gombe, kusan la'asar
suka sauqa airport, driver ne yazo ya dauke su ya kaisu gidansu. Kamar koyaushe
an gyara musu gida an share ko'ina kamar dama masu gidan suna ciki, bayan sunyi
wanka sun shirya suka fito palourn qasa, Amrah suka tarar a xaune da food
flasks a gefenta. Ta tashi da dan tsallenta ta rungumesu tana cewa "I miss
u guys" sai da suka gaggaisa amrah tace "kai anty fateey wallahi kin
qara kyau, ya sultan kaima kayi kyau" fatu tayi murmushi tace "amma
cikinmu wa yafi kyau? Na fishi ko? Tafada tana winking din amrah. Daria sultan
yayi yace "aiko makaho ya laluma yasan na fiki" buga kofan da aka
fara yasa amrah ta miqe tare da budewa, khairy yar jameel ce ta shigo da gudu
amrah ta dagata suna daria tace "ina mom dinki? Sallama jameel da lubna
sukayi aka amsa musu fatu ta tashi ta tari lubna cikin dokin ganin juna, lubna
ta ajiye basket din hannunta sukayi hugging juna, jameel ya zauna kusa da
sultan ya bugi kafadanshi yace "ka gansu kamar basa waya koyaushe"
daria sultan yayi sukayi hand shake yace "zaka fara ko?<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[9:09PM, 9/25/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">4</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Hiran yaushe gamo sukeyi har aka kira
sallarn<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maghrib, bayan sunyi sallah suka hadu a
dinning table, tuwon shinkafa miyar egusin da amrah ta kawo sukayi serving,
snacks da kunun aya lubna ta kawo. Sultan sai kallon fatu yakeyi, in sun hada
ido sai yayi murmushi, jameel ne ya bugi kafadarshi a hankali yace "ya?
Sultan shima yayi qasa da murya yace "I am confused! To ta yaya
zan...." wayar amrah ce data fara ringing ne yasa ya dakata da maganan da
yakeyi, har wayan ta katse bata dauka ba, sultan yace "bakiji ana kiranki
bane? Ta bata fuska tace "yaya ka bari kawai" bai qara cewa komai ba
har suka gama cin abincin ita kuma tasa wayar a silent. 8:19pm su lubna sukayi
haraman tafiya, fatu ta kwaso musu tsarabansu ta basu, amrah ma aka bata nata,
suna tafiya amrah tace "nima fa zan tafi, bari in kira driver" sultan
yayi saurin katseta yace "ki barshi kawai, kizo in kaiki" fatu ta
kawo tsaraban su mammi da abba tace a kai musu. Suna isa gida suka sami mammi a
falon abba, sultan ya gaishe su, sunyi murnan ganinshi, mammi tace "manga
kun dade kam gaskia, har na fara zaton ko kun koma can da zama ne" ya sosa
kai yana murmushi yace " a'a mammi" tace "ina fateeman? Tana
lafiya? Yace "lafiyanta kalau, tace a gaisheku, gobe itama zata zo"
mammi taji dadi tace "to Allah ya kaimu, in banda ita ai da ta huta
tukunna" sultan yace "ita ta matsu mu dawo, wai tayi kewan gida"
mammi tace "ayya fateema na" bai jima ba ya musu sallama mammi ta fito
ta rakashi har gurin motanshi suna hiran tsakanin d'a da uwa, yace "mammi
akwai maganan da zamuyi" ya fada wani sunkuyar da kai, tace "wani
abune manga? Magana naga yake fada mata tayi shiru tana sauraronsa can tace
"amma kunyi bincike ne? Yace "a'a zamuyi dai, amma kar a fadawa abba.
Ba yanzu ba" mammi tayi murmushi tace "ai abun farin ciki ne, ya
kamata ya sani tun wuri" sultan yace "a'a mammi, to ki bari ni zan
fada masa da kaina" daria mammi tayi tace "kai kadai dinka, Allah ya
tabbatar da alkhairi" yace "Ameen" shima yana daria, tace "mara
kunya, mun gode da tsaraba" ya shige motarsa yana daria. Kafin ya isa gida
sai da ya biya ya sayawa fatu chocolates da ice cream sannan ya koma. A dakinta
ya tarar da ita ta fito daga wanka tana shafa mai, ya lallaba zai dan tsorita
ta sai kuma ya fasa, yayi sallama ta amsa ya shigo tace "ya ka sami su
mammin? Yace "lafiyansu sunce ma a gaisheki" tace "ina amsawa,
na qagu ai gobe tayi inje inga mammi na" ta qarisa magana tana murmushi.
Fita daga dakin yayi yana zolayarta wai goben ma bazata je ba, tana gama shiri
cikin kayan baccinta ta mulka humranta ta fito, a falon sama ta hango leda akan
kujera ta bude, ice cream ne da chocolates ai da murnanta ta hau sha, kafin
sultan ya fito ta cinye tasss, Ya fito shima da kayan baccinsa ya ganta yace
"ina nawa" ta ware ido tace "dama baka ci bane? Ya harde
hannayensa yace "tukunna ma wayace naki ne? Shiru tayi tana mai murmushi
can tace "sorry" yace "zanga wazai siyo miki gobe" ta
marairaice fuska ta turo baki tace "bana baka hakuri ba? Yace "its
ok, ai bakya laifi, muje mu kwanta" Washe gari fatu ta shirya tun 11
sultan ya sauqeta a gidan mammi shi kuma ya wuce, mammi ba qaramin dadi taji ba
ganin fatunta tayi kyau tayi fresh, tana azahar ta wuce gidan mummy itama taji
dadin ganinta, ta basu tsarabansu duk na farouq
yafi yawa, anan ta hadu da khadija qanwar jameel tazo da yaranta biyu,
khadija ke cewa " Madam ya kamata yanzu kam muga baby" fatu tayi
shiru kaman ruwa ya cinyeta, khadija ta qara cewa "kinyi shiru ko har
yanzu baku gama amarcin bane? Fatu ta dago kai fuskarta ba yabo ba fallasa tace
"kinsan komai sai lokacinsa yayi, kuma mutum bashi yake bawa kansa ba,
Allah ne zai kawo a lokacinda ya dace" tana gama fadan haka ta tashi tace
"bari in dauko abu a kitchen".<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A kitchen khadija ta sameta ta dauki ice
cream tana neman qaramin spoon, tace "fateema kiyi hakuri da abunda na
miki, I was a victim too, lokacinda nayi aure kafin na haihu sai da nayi 2yrs,
irin haka in dangin mijina na qauye sukaje hutu gurinmu sukan fada min irin
maganganun nan and bana jin dadinsu, duk abunda baka so a maka kar ka yiwa dan
uwanka, kiyi hakuri don Allah" fatu ta dafa kafadarta tana murmushi tace
"ni baki bata mini rai ba maman sabeer, don a raina na dauka hakan yana
faruwa ga irina, so kinga in nace zan dinga bata rai zan hadu da matsala,
haihuwa na Allah ne da kudi ko matsayi basa bawa mutum" Khadija tace
"hakane kiyi hakuri" fatu tayi daria tace "c'mon ki daina bani
hakuri, nifa ban dauka da wani manufa ba" khadija tayi murmushi tace
"nagode" a haka sukayi ta tadi har bayan la'asar sakaliya ta koma
gidan mammi. Ana isha sultan yazo suka wuce gida. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">*Bayan Sati daya*<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu ne zaune a palourn lubna tana shan
kankana yayinda lubna ke kitchen tana aiki take cewa "kayan nan suna ta
tafiya fateema, hajia nazifa ta kirani tana son swiss guda 24, dozen biyu
kenan" fatu zatayi magana taji muryan jameel a waje yana cewa "kana
nufin har yanzu baka fada mata ba? Sultan yake cewa "ka santa da sa abu a
rai, kuma ma me zance mata? Dai dai nan suka shigo fatu tayi saurin amsawa lubna
maganarta da cewa "idan na koma gida zan aiko miki sai ki tura mata"
amma can qasan ranta ta fara tunanin akwai wani abu da yake tafiya, 'something
is fishy' kwanan nan ta lura da wani extra care da sultan yake bata haka ma
mammi koyaushe saita kirata tana wani lallabata. A ranta tace she has to find
out. Zama sukayi suna hira sai bayan isha suka koma gida. Qarfe 9:55pm agogon
wayan fatu ya nuna, fitowanta daga wanka kenan tasa kayan baccinta ta feshe
jikinta da turare ta nufi palourn qasa inda sultan ke aiki da laptop dinshi
lokaci daya kuma yana waya. A gefenshi ta zauna ta canja tasha zuwa zee world,
kallonta yakeyi kamar ya cinyeta don wani irin kyau da take qara masa koyaushe,
a daddafe ya qarisa abunda yakeyi ya jayota jikinshi yana shinshina wuyanta
yace "kin hanani aiki" tayi murmushi tace "dama already ka
gaji" ganin abubuwan da yake mata yana yawa yasa ta dan zare jikinta tace
"can we talk? Gyara zamansa yayi lazily yace "why now? Meyasa yanzu?
Tace "sorry jannah" yace "ina jinki" tace "me yake
faruwa ne? Naji dazu kuna magana da ya jameel" ta kalleshi tana son
karantan yanayinshi. Fuskarsa ba yabo ba fallasa yace "a ina? Tace
"dazu bayan maghrib da kuka shigo gida" murmushi yayi yace "me
kika ji? Juya idanunta tayi irin questions din sunyi yawa tace "yana tambayanka
dalilin da yasa baka fada min wani abu ba" ta gyara zama ta fuskanceshi
sosai tace "mene kake boye min? Yau kam ka fada min, kafin mu tafi
mauritius naga kayi waya wanda magananka baiyi tsawo ba kace zaka kira, kamar
baka son yin wayar a gabana, ina lura da kai. Ko abokiya zaka kawo min ne? Ta
qarisa maganan yayinda wani irin abu ya tokare mata maqoshinta yana qoqarin
sata kuka. A hankali sultan yake kallonta da dan murmushi a fuskarsa yace
"tunda kinyi smelling ya kamata in sanar dake" ya kamo hannunta duka
biyu yana murzasu a hankali yace "fatuhhh....."<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:24PM, 9/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">5</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Yace "fatuhhh" tayi shiru ta qura
masa ido kirjinta na bugawa da sauri da sauri, yace "fateema" tace
"na'am ina jinka" don ta qagu taji menene don zuciyarta na gab da
tarwatsewa. Ya cigaba da murza hannunta yana cewa "ranar da jones nake
magana don shi ya mana visa, so bana son kiji a lokacin ne" Tace
"uhum" yace "fateey wai u ar pregnant" ya qura mata ido
yana kallonta. Ta girgiza kai tace "wai? Kuma... oh god!! Don Allah ka
fada min abunda yake faruwa, nasan ba
maganar ba kenan" wani siririn hawaye ya gangaro fuskarta ta share. Yayi
ajiyan zuciya yace "wallahi maganan kenan, ranar da muka dawo su lubna ai
sunzo, so anan jameel daya ganki yaga alamun masu ciki tare dake, so mun fita
sallah yake gaya min, in kin lura muna cin abinci inata kallonki amma banga
alamun komai ba" da sauri fatu ta shafa cikinta tana lalumawa kamar mai
neman abu, tana cewa "da gaske inada ciki? To tayaya zan gane? ganin hakan
bazai nuna mata komai ba ta kwaye rigarta tana dubawa, sultan ya zuba mata ido
yayi tagumi, yace "kinga dalilin da yasa naqi fada miki kenan, don kar kizo
ki sa rai alhali ba cikin gareki ba ki qara tada hankalinki" Ta dago ido
tace "muje chemist mu siyo PT strip" yace "me kenan? Tace
"abun gwada ciki ne" tashi muje" Ta miqe ta haura sama da gudu
harda harhada steps, tana kulewa sultan ya dafe kanshi yace "ya Allah ka
taimakeni, Yanzu in ba ciki bane sai tayi wata daya mood dinta bai dawo dai dai
ba" fitowanta yasa ya juya yana kallonta, tasa zani da hijab, ta iso
gurinshi tana wani dafe ciki tace "muje to" Ba musu ya dauki key din motarsa
da yake kan kujeran suka fita. Da yake dare yayi wasu chemist din har sun
rufe, A.A Aliyu chemist suka samu a
bude, ya barta a mota ya shiga, yace "ina son PT strip, abun gwada
ciki" mutumin yace "guda nawa? Sultan yace "da guda nawa akeyi?
Yace "da guda daya akeyi alhaji" Sultan yace "ok, a bani 5"
aka bashi ya ciro kudi ya bayar ya koma mota. Fatu tana can tana jiranshi sai
addu'a takeyi a zuciyarta Allah yasa ciki take dashi, sai a sannan ta tuno
rabonta da tayi period tun tafiyansu mauritius, kuma cikinta ya dan tashi, amma
ta danganta hakan da irin ciye ciye da cin abincin da takeyi kwanan nan, kuma
dama tayi dan qiba.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Ya miqa mata ledan suka koma gida, kafin ya
fito daga mota har ta shige gida, tayi fitsari a wani dan qaramin roba ta saka
strips din duka tana ajiyewa, anan ya shigo bandakin yace "fateema ki
nitsu fa" ta matso gurinshi tana kallon agogon hannunshi tace "nan da
minti 5 zamu ga result" Zaiyi magana tace "shhh, muyi addu'a jannah,
zuciyata tana ta bugawa, kaji" ta daura hannunsa akan kirjinta tace
"kaji? Yace "ehh" fatu ta bata fuska tace "kamar kai baka
damu ba" yace "ya zanyi? Kin kasa fahimta ta, banso fada miki ba, to
yanzu tunda na fada miki dole in biye miki" kallon agogon hannunshi tayi
tace "saura 3mins" shiru shiru har 5miins din suka cika. Ta kalleshi
tace "ina tsoro, kaje ka duba" yayi ajiyar zuciya ya fara tafiya zuwa
gurin ta riqo shi idonta taff da hawaye data kasa tantance na menene tace
"zanje" ya matsa mata taje ta dauka bakinta sai addu'a take
kwararowa, ta rufe ido ta bude a hankali... "P...popp...POSITIVE"
wani irin tsalle ta daka sai akan sultan yace "what? Menene? Gabadaya ya
kidime, kukan farincikine ya hanata magana, ya sauketa yaje ya duba, dukansu
sun nuna lines biyu red, ya dauki pack din strip din ya karanta, "Alhamdulillah"
ya dinga maimaitawa har ya iso gurin fatu wacce take daria ga hawaye shabe
shabe a fuskarta yace "its true fateema, kinada ciki, Masha Allah,
Alhamdulillah" Gaba dayansu sun kasa controlling farincikin da suka tsinci
kansu ciki. (Shekara uku ba wasa ba, d'a kuma da dadi, Allah ka bawa wanda
basuda shi Ameen) A bakin gado suka zauna kowa da murmushi a fuskarsa tace
"jannah har yanzu na kasa gaskatawa, gani nake kamar mafarki nakeyi"
yace "ba mafarki kikeyi ba, yau Allah ya nufe mu da samun abunda muka dade
muna addu'an samu" sultan ya kira jameel a cikin daren ya fada mishi, fatu
tana hanashi akan ya bari sai gobe amma yaqi don d'oki, har zai kira mammi ma
fatu tayita roqonsa sannan ya bari, bude cikin yayi yana ta shafawa can kuma
sai ya daura kansa wai zaiji heart beat din babynshi, da kyar ranar sukayi
bacci don fatu gani takeyi ma sultan ya fita farincikin samun cikin.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[10:39PM, 9/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">6</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Washe gari qarfe 10 suna gidan mammi wai
daga nan zasu wuce hospital don fara anti natal, a palour suka samu amrah tana
breakfast, da murnanta ta gaishesu, sultan yace "ina mammi? Tace
"tana dakinta" yace "dear mu shiga" fatu ta noqe kafada
tace "a'a nikam ina jin kunya" murmushi yayi ya shiga dakin mammi,
bai jima ba suka fito tare da mammi, fuskarta annuri kamar wacce akayiwa
bushara, fatu tayi sauri sauqowa daga kan kujera zata gaisheta, dagota mammi
tayi ta zaunar da ita a kujeran tace "a'a fateema, ki daina aikin wahala,
Allah ya miki albarka 'yan nan yasa ki sauka lafiya" amrah tace
"mammi tafiya zatayi? Mammi tace "amrah abun farinciki ne ya samemu,
fateema zata kawo mana d'a" amrah tayo gurin fatu da gudu zata rungumeta
mammi tace "ke amrah me haka? Zaki bugeta ai, bana son irin haka"
sultan da yake gefe yana kallon show din a ranshi yace 'an gamu da mammi yanzu
kam' a fili kuma yace "fateema tashi mu tafi asibityn. Mammi tace
"A'a ka barta ta huta, zuwa anjima zan kaita da kaina, tukunna ma wani
asibity? Wani asibity ne suka fi bada kulawa? Da kyar sultan ya bari mammi ta
hakura yakai fatu don yasan fatun bazata sake tare da mammin ba. Private
hospital mai kyau ya kaita, doc ya mata tambayoyi ta bashi amsa yace za'a mata
scanning. A gurin scanning dinne likitan ya kasa gane 'ya'ya nawa ne a cikinta,
don clearly biyu ya gani amma ta gefensu yaga wani kaman babyn, yace "a
bisa scanning da mukayi cikinta wata uku ne da sati daya da kwana 3, kuma 'yan
biyu ne a cikin nata amma zata fara zuwa anti natal daga jibi thats kowanne
wednesday don duba lafiyanta da abunda ke cikinta" sultan da fatu da suka
kasa magana don tsananin mamaki don basu tsammaci cewa zasu sami 'yan biyu ba.
Suna komawa gida aka fadawa mammi Again murna tayi kamar me, anan ta kira mummy
ta sanar mata, ko minti biyar ba'a qara ba mummy ta shigo tana barka barka.
Dangi aka kira ana fada musu fatu har abun ya fara bata kunya kamar a kanta aka
fara haihuwa. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">*4months 2weeks later*<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">2:12am na dare, sultan ne zaune ya qurawa
fatu wacce ke kan gado ido da goran faro babba cike da madaran shanu a
hannunshi yana dan jijjigawa don saboda ya dan huce, a hankali fatu take
motsawa, idonta ta bude ta shafo rusheshen cikinta wanda girmanshi har abun
kallo ne. Da sauri sultan ya isa gurinta ya taimaka mata ta zauna, ruwa ya fara
bata ta kukure bakinta ta zuba a wani container da ya kawo daidai bakinta,
straw ya saka a cikin goran kana ya bata tana zuqa a hankali har ta shanye
tass,😳 nace kaii!!! Ta dago ido ta kalleshi ya mata murmushi tace
"nagode" yace "nine da godia, don yarana suna wahalar min dake,
ga ci kamar me" daria tayi tace "lafiya kenan" sai daya tabbatar
tayi 30 mins sannan ya gyara mata kwanciya yace "kiyi bacci" shafa
gashin kanta ya fara tana lumshe ido ko minti biyu bata qara ba kuwa ta soma
bacci. A hankali ya tashi ya koma dayan side din yana tunano irin wahalan da
suke sha aka cikin nan, fatansu dai Allah ya sauqeta lafiya....... tun daga
ranar da suka fara zuwa anti natal ake mata scanning koyaushe ana cewa 'yan
biyu, da cikinta ya cika wata shida aka turasu wani hospital a mata scanning
don doc din da yake dubata he's confused yana ganin kamar babies uku ne, thats
why ya tura su wani asibitin. A can da aka mata cewa sukayi 'yan uku ne kuma
kosassu lafiyansu kalau, wani abun mamaki shine fatu batayi laulayi ba sai na
ciye ciye, abinci kam tana ganin damarsa, kuma bata jimawa zata nemi wani. Da
mammi taji haka tace to scanning din ya isa, Allah shi yasan komai. Fatu bata
wasa da maganin da ake rubuta mata a wurin awo, sam bata skipping, sultan har
tausaya mata yakeyi in yaga ta ajiye abinci a gabanta tana ci, watarana haka
zata bude mishi tumbin yana ganin yanda babies din suke naushinta har abun
mamaki. Da cikin ya cika wata 7 kuwa tashin dare ta fara wai yunwa takeji, haka
zai tashi ya hada mata tea tasha amma baza'a jima ba zata qara tashi tace
Yunwa, ana haka rannan kaka ya ziyarceta ya kawo mata maganin shawara da ake
bawa masu ciki, anan ya kawo musu madaran shanu mai yawa a gallon jarka, a
ranar da dare fatu ta tashi tace a bata madaran, sultan ya kawo mata, da yake
an saka shi a fridge yayi sanyi tace a dumama mata, dolenshi ya sauka ya duma
mata ya juye a gora ya bata, to a ranar bata qara tashi neman abinci ba, daga
ranar yake aika mata nonon shanun daga kumo. Marking din lokacin tashinta yayi,
kafin ta tashi zaije ya dumama ya dawo ya zauna yana jiranta har ta farka ya
bata tasha. Mammi tayi tayi ya dawo da fatu gida amma sai yayita mata
kwana-kwana. Yau dai EDD din fatu saura kwana 8, yayi niyyar maida ita gida gobe
don kar abu ya tashi baya gida. Dauke wutan da akayi ne yasa ya dawo daga
tunanin da yakeyi, da sauri ya dauki handa fan ya fara mata fifita don bata son
zafi ko kadan, ba'a yi minti 3 ba maigadi ya kunna generator, anan sultan ya
ajiye handfan din ya shige toilet ya dauro alwala, ya gyara mata pillow yayi
kissing goshinta kana ya fara nafilfili Allah ya sauqeta lafiya.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[7:39PM, 9/29/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Washe gari da safe Tana zaune akan gado
tana shan Apple shikuma yana hada mata kayanta da zata buqata. Kallonshi takeyi
cike da tausayi don ba qaramin qoqari yake yiba, tunda cikinta ya girma ya
hanata girki duk da ma sunada mai wanke wanke da shara, Haka kuma koda zai
bukaceta ya dinga tambayarta kenan cewa "bazan takuraki ba? A'a "are
u in d mood? Da ire irensu, tana mugun respecting dinshi akan hakan. Sultan
mutum ne wanda take alfaharin samun shi a matsayin miji, yana tausaya mata kuma
bashida saurin fushi. Gashi baya gajiya da mata hidima, takanas ya fita waje ya
musu siyayyan haihuwa wanda kwanan shi uku ya dawo wai tunaninta ya hanashi
zama. Laluma plate apple dinta takeyi taji wayam, wato har ta shanye apples 8,
dai dai nan ya juyo yana kallonta da murmushi a fuskarsa yace "a yanko
miki wani ne? Ta girgiza kai tace "a'a, na koshi" yace "to ki
tashi in miki wanka mu tafi" tace "to" A hankali ta miqe yayinda
shi kuma ya dauko mata towel ya tayata cire kaya yana daura mata towel din. Tace
"jannah" ya dago ido yace "maman uku yadai? Murmushi tayi tace
"thank u" bai ce komai ba ya jata zuwa bathroom. Don ya saba da irin
hakan, koyaushe tana cikin nuna jindadin ta ga yanda yake nuna mata kulawa,
hakan shi kuma kan qara masa qwarin guiwa wajen kyautata mata. Wanka sukayi
amma fatu na lura da sultan akwai abunda yake damunshi. Bayan sun fito ne take
tambayarshi lafiya yace ba komai. Bata fuska tayi tace "ka fada min don
Allah" zaunar da ita yayi a bakin gado yace "can u help me? Anan ta
gano bakin zaren, don yau kusan 3wiks
rabon daya nemeta wanda tasan duk a dalilin tausaya mata da yakeyi ne, lallai
tana da sonkai, tasan yanayinshi ba mai juriya bane amma ta mance dashi tana
enjoying sangartata da yakeyi. Murmushi tayi tace "I am sorry jannah, nayi
sonkai da yawa...." bata qarasa
magana ba taji an rufe mata baki da lips nasa........<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Sai da yaji he's okey ya tashi ya shiga
bandaki. Bayan ya fito ya kwaye bargon data lulluba dashi yace "taso
kinji, sorry dear" da kyar ta miqe don wani irin ciwo da bayanta ya fara
tun dazun. Zai bita bathroom din tace "ba komai zan iya" ganin yanda
take cize baki tana riqe da bayanta yace "ko dai nayi hurting dinki ne?
Tace "a'a" tare da shigewa bandakin. Da kyar ta samu tayi wanka don irin
ciwon da mararta kuma ya fara. Tana fitowa ta samu ya gama shiri har yasa kaya
ya ganta wani iri yace "na sani na ji miki ciwo, I am so sorry, ya
Allah" ya dafe goshi, tausayinshi taji don haka tadan fuske duk da irin
ciwon da takeji tace "kadan ne fa, kuma ya fara tafiya ma" bai
saurareta ba don yanda yaga take hada gumi yasan tana jin jiki, daguwar riga ya zura mata yace "mu tafi
hospital" Magiya ta fara mishi wai ita bazata je hospital kar suce haihuwa
ne, tana tsoron haihuwa balle ita da aka ce yan uku ne. Kafin ma su isa asibiti
abu ya qara jiqa, don yarfe hannu takeyi tana dafe mararta. A gaggauce nurses
suka karbeta aka shiga da ita labour room, doctor da take dubata ya kira a waya
ya fada mata ya kawo fatu asibity, ko minti biyar bata yi ba ta iso bakin
labour room din don dama tana cikin asibitin. Safa da marwa ta samu sultan
yakeyi yana kiran sunan Allah sai kace shine mai labourn. Da dan murmushi ta
gaisheshi ko amsawa bai yiba yace " ki shiga ki dubata, inaga ba haihuwa
bane doctor, coz nine na jawo" da dan mamaki a fuskarta tace "kamar
ya? Kamar bazai fada mata amma yaga no need da boye boye shi dai fatanshi a
Magance halinda fatu take ciki don haka yace "I...I have.. I have se* with
her" doc tace "ba matsala ai hakan, kar ka damu" da hanzarinta
ta shiga labour room din yayinda sultan ya cigaba da safa da marwa, anan ya
kira mammi ya shaida mata suna asibiti. Minti goma doc ta fito tace
"haihuwa ce coz har ta kai 5cm" cikin rashin fahimta yace "me
5cm? yanzu haihuwa zatayi? Zan iya
shiga? Ganin yanda ya rude yasa doc din ta fara kwantar masa da hankali, sai
anan ya tuno cewa ai EDD dinta bai cika ba, yace "doc edd dinta next week
ne" tace "wasu suna rage kwanaki wasu kuma suna qarawa. So yau Allah
yayi zata haihu" Anan mammi ta shigo itama daka ganta zaka san hankalinta
a tashe yake.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[12:56PM, 10/1/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">8</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Gaishe da mammi yayi ta amsa tace "ba
dai tun jiya abun ya fara mata ba? Yace "a'a yau da safe har mun shirya
zan kawota gida" harara mammi ta watsa masa kana ta dubi doc din ta bata
wani ruwa bottle din Faro tace "ga wannan ruwan addu'a ne a bata
tasha" da sauri sultan ya karba yace "doc zan iya shiga? Tace "ehh
zaka iya" mammi da mamaki ya gama rufeta tace "ya zaka shiga gurin
haihuwa? Kafin ma ta qarisa sun qule shida doc. A kan gado suka samu fatu tana
jijjiga kai tana yarfe hannu, ganin sultan ba qaramin qwarin guiwa tajiba, ya
isa gurinta ya kamo hannunta yace "INA TARE DA KE, ki dinga addu'a kinji?
So sorry dear" Gyada mishi kai tayi cikin baqar wahalan da take ji, ruwan
ya bata, ta girgiza kai yace "na addu'a ne mammi ta kawo miki, kisha kinji? Jin ance na addu'a ne ta karba
tare da bismillah ta shanye. Shiru shiru kusan 20mins. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Ganin fatu har ta fara nishi nishi doc tace
a gwada mata cm nawa take. Daya daga cikin nurse dinne tazo gwada fatu sultan
ya tareta yace "what are you doing? Me haka? Da kyar doc ta fahimtar dashi
sannan ya yadda. Fatu ko ta kansu bata bi. Nurse din tana gwadawa ta fadawa
doc, tace "ina kayan haihuwa? Don mun muku list din abunda muke
buqata" sultan yace "yana mota" da sauri yaje ya dauko ya kawo
mammi na kallonshi yazo ya qara shigewa. 30mins da haka ta haiho babies dinta
hudu duk maza, fatu ta wahala sosai. Murna gurinsu ba'a cewa komai. Su da akace
musu uku sai ga hudu. Mammi kam ta rasa inda zata sa kanta don murna, dukansu
sai hamdala sukeyi tayi (wani jinkirin ma Alkhairi ne) Awa hudu da haka aka
sallamesu bayan an tabbatar da lafiyan maijego da babies. Kafin suna 'yan uwa
da abokan arziki sunzo barka. Yara tubarkalla kyawawa dasu tula tula, kama
sukeyi da babansu sosai. A ranar suna suka ci sunan Abu-bakr, Aliyu, Usman da
Umar. Anyi shagalin suna na gani na fada, mai jego da babies sunyi kyau cikin shiga
ta alfarma. Mutanen garin modibbo suma sunzo suna.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">[11:09AM, 10/2/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻 <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na Mrs Aslam Haidar</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">✍</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">7</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US">9</span><span lang="ZH-CN" style="font-family: SimSun; mso-ascii-font-family: "Times New Roman"; mso-hansi-font-family: "Times New Roman";">⃣</span><span lang="EN-US"><o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Su xahra amarya, bizzy mai ciki, (suma sunyi
aure) lubna da salma qawayen mai jego sun entertaining baqi sam barka,'YAN
MUMBARI tare da MUM FATEEY FANS suma sun halarci wannan bikin suna. Da yamma
akayi walima inda Malama Asma'u (maman Al'ameen) ta gabatar da wa'azi kan
tarbiyatan da yara bisa yanda addinin musulunci ya tanadar. An ci, ansha anyi
guzuri, su Mrs umar, Autar hajia, ummi Aisha, Jabo, da jegal sunfi kowa kwasar
abun suna. An raba soveniers kamar ba gobe, taro yayi ansha pictures kala-kala.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> *11
years later*<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Fatu na gani da dan jaririn cikinta wanda
bazai wuce 5 months ba, a kan cinyanta plate ne cike da gyada dafaffe tana
barewa tana ci. Gefenta kadan sultan ne shima zaune suna kallon wani indian
film mai suna "SULTAN" inda SALMAN KHAN ya fito a wrestler. Da alama
dukansu hankalinsu ya tafi ga kallon don fatu ko kallon gyadar batayi take
barewa tana turawa a baki. Sai ta bare goma tasa a baki, kana ta baro daya ta
bawa sultan. Gama film din yayi daidai da Qarewan gyadan fatu ta laluma taji
wayam sai bawon gyada kawai. Sultan ya juyo yace "film dinnan ya
hadu...." ganin plate ba komai yasa ya waro ido yace "ba dai kin
cinye ba? Ta turo baki tace "mun cinye dai" ya lalumi bakinshi da
harshen shi yace "kin cinye dai, don nikam banji alaman gyada a bakina ba,
matar nan zanyi maganinki, daga yau na siyo abu sai na ci nawa a hanya before
na kawo Gida, ko samarin gidan nan baki ragewa ba" daria tayi sosai tace
"in kana kiransu samari abun har daria yake bani" tashi yayi ya nufi
door inda ake bugawa yace "naga haka kike kiran waleedah (mai sunan mammi,
shekaranta 8, mammi ta dauketa tun da amrah tayi aure) fatu tace "waye ne?
murmushi yayi yace "inaga sun dawo" a hankali ya bude ya leqa, wasu
kyawawan yara yan kimanin 11yrs su hudu na gani bayansu karamar yarinya da
bazata wuce 4yrs ba tana matsar kwalla,
sultan yace "kun dauko ta ko? Tare da basu hanya suka wuce, daukan ta yayi
ya saba a kafada yace "Ameera munyi missin dinki" ta turo baki
Abu-bakr yace "bata jin magana sam, boarding school zamu kaita, da kyar
muka banbareta a jikin Al'ameen din aunty salma shima yaje gidan granny"
fatu ta tashi tace "wa za'a kai boarding school? Katti daku ba'a kaiku ba
sai yar yarinyar nan? To akul dinku naji kun takurata mata, yarinya yar qarama
da ita kunbi kun sa mata ido....." karban 'yar tayi taja hannunta suka
shige daki tana fadanta. Sultan dai baice komai ba ya samu guri a kan kujeran
ya zauna kana ya dubi zaratan samarinsa wanda inka gansu zaka dauka sun kai 13
ko 14, Aliyu wanda duk cikinsu yafi zafi yace "mommah tana sangarta
Ameera" Usman yayi murmushi yace "mai sunan mamanta ne ai" zama
sukayi dukansu a kan kujera sultan yana binsu da ido cikin tsantsar qauna yace
"ba sangartata take yi ba, shekarunta 4 ne, wanda komai a yanzu cikin
lallami da wayo za'a nuna mata ba by force ba, kuma haka mommah dinku ta raine
ku har girman ku. And gashi kun tashi a
nitse da ilimi both Arabi da boko. Sons I am proud of your mom and i trust
yanda take tarbiyantar da yara" Jinjina kai sukayi cikin amincewa anan
suka fara maida zance. Gurin driver taje tace ya kaita gidan granny inji momma,
shi kuma without bincike ya dauketa ya kaita. Dawowanshi yayi dai dai da
dawowan sultan yake tambayrsa inda yaje, driver ya fada mishi, anan sultan ya
mishi warning kar a qara daukanta in ba babba yayi magana ba. Shiganshi gida
yasamu samarinshi suna taya mamansu hira, ya fada musu suka tafi dauko ta don
washegari monday akwai skul. Shine suma suka yi zamansu sai yanzu suka dawo.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">A hankali fatu ta sauqe ameera akan gadonta
wacce take bacci. Ta lullube ta tare da mata addu'a ta kashe wutan dakin kana
ta fita. A falon qasa ta tarar da samarin suna kallo, tace "Umar, Usman,
Abu-bakr, Aliyu ku tashi kallon haka ya isa, gobe kunada skul, hope kun gama
all assignments dinku? Usman yace "yess mommah" Umar yace "dama
ni na fara jin bacci" ya miqe tareda kashe socket din. Daya bayan daya
suka mata peck suna cewa "gudnight mommah" Suka shige dakinsu dake
falon yayinda na Ameera yake sama. Zata juya taji mutum a bayanta yace
"good morning mommah, yau tilldawn zamuyi, don sai kin biyani gyada
na" Daria sukayi suka haura sama zuwa dakinsu. <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">AND THEY LIVE HAPPILY EVER AFTER.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">ALHAMDULILLAH<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">GODOYA<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Godia ya tabbata ga Allah daya bani ikon
gama wannan littafi. Abunda na rubuta dai dai Allah ya bani ladansa kuma ya
amfane mu gaba dayanmu, wanda nayi na
kuskure Allah ya yafe.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Godia Ga dukkan Groups da suka so fatu.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">M Jabo mumbari da Duniyar novels<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Mum Fateey Fan's<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Mrs Umar hausa novels <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Hausa novels (na maman safwan)<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Mace Mai Aji<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Be his star<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Matan Aljanna da <o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Matar So<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Hausa novels (na maman safwan) da duk
sauran groups da bansa sunansu ba. I really appreciate ur love nd support.😘😘<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">JINJINA<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Jinjina ga sauran 'yan uwana writes. Allah
ya saka muku da mafificin alkhairi Allah ya qara basira.<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Gareku masoyana, nagode da dunbin qaunar da
kuka nuna mini tare da FATU A BIRNI. Mum fateey tana sonku sosai nd I Respect u
all. Allah ya bar zumunci ya hada kanmu a Aljannatul Firdous. Ameen<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">KUNA RAINA<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Salmatun inna, xaynoobiey, sara2 wsg, ummi
b, xahrah levels, miss rukeey, stew, wasilatBMI, Ayeesh naner, bizzy, mrs
al'ameen, umm marwa, maman zahra, falmata abubakar, ummy naseer jibia, maman
dota, maman jawaheer, maman Al'ameen, shatoo, Aysha (ummu abdul) khairie India,
Maman Dr, da duk wadanda bansa sunanku ba, kuna raina bil hakki.😘😘<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Kinfi kowa qaunar FATU, Aunty Zainab (maman
hauwa) Allah ya sauqeki lafiya muje cin shinkafa. Rengemm👯👯😅<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">SADAUKARWA<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Na sadaukar da wannan littafi ga
mahaifiyata Hajia Aishatu Baffa Aliyu<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Allah ya qara tsawon rai mai albarka Allah
ya bar mana ke Hajiata ya raya miki 'yayanki. Ameen. Luv u mommah.😘😘<o:p></o:p></span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US"> </span></p>
<p class="MsoNormal"><span lang="EN-US">Maman Fateey👯👯<o:p></o:p></span></p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-82517158283735121302021-06-12T14:05:00.002-07:002021-06-12T14:31:12.308-07:00NA-CUCE-TA COMPLETE HAUSA NOVEL<p> </p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-w2IhL600HCQ/YMUgIjodjHI/AAAAAAAAJqI/Jt4vtK7p1xIm9Y5NQDd9QdYVAnDKPxQSACLcBGAsYHQ/s2048/NA-CUCE-TA.jpg" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" src="https://1.bp.blogspot.com/-w2IhL600HCQ/YMUgIjodjHI/AAAAAAAAJqI/Jt4vtK7p1xIm9Y5NQDd9QdYVAnDKPxQSACLcBGAsYHQ/s320/NA-CUCE-TA.jpg" width="320" /></a></div><p></p><p>COMPILED BY ESHATT SMILER HOM OF HAUSA NOVLS DOCUMNTS</p><p>馃挌馃挏鉂ゐ煐ゐ煉欚煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挌馃挋馃挏馃枻馃挍鉂�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> 庐zuwairat( ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>1鈨�</p><p> _Alhamdulillah, Allah praise be to almighty Allah_ </p><p> _Am back again_</p><p>Cikin wani gidan Wanda ke ginin kasa mai dauke da daguna biyu wata yarinya ce wacce bazata wuce shekara shabiyu zuwa sha uku ba ke daka sai tim Tim Kawai kakeji saboda yanda take dakan garin furan dake cikin trumi, daga dayan gefen Kuma wata matace ke hura wuta sai kafawa murhun bakin take tana hura wutan, duk idanuwanta sun chanza kala saboda yanda hayake ke shiga idonta, wata yar yarinya na gani ta taho da gudu da wata faifai<span></span></p><a name='more'></a><p></p><p>"Ammi ki hura da wannan...." Yarinyan ta fada mata, matar dake durkushe gaban murhun dagowa tayi ta sakarwa yarinyan murmushi tare dacewa</p><p>"Yauwa...nagode binto..." Matar ta fada tana amsan faifan daga hannun yarinyan.</p><p>Da ganin Matan da yanayin gidan kasan gidan kasan masu karfin haline sosai don komai NA gidan is low to the last core, yarinya dake dakan goge zufan goshinta tayi ta kalli matar da aka kira da ammi tace</p><p>"Gaskiya ammi gobe mu kai injin...NA gaji da daka Wallahi hannuna duk ya kumbura.. Nidai NA gaji..." Tafada tana turo baki tare da kallon tafin hannunta ya kumbura saboda yawan daka</p><p> Ammi kallon ta tayi Sannan ta maida dubanta ga muhur </p><p>"In banda abinki dije AI kin San da wannan dakan muke samun abinda zaa bawa awakan nan ...in an kai inji ba su bamu dusa..." Ammi ra fada tana hura wutan, dija Kara turo baki tayi</p><p>"Wai ammi dole ne mu bar wayan nan awakan?... A saida su mana Kawai..." Tafada in I don't care manner, ammi kallon ta tayi ta tabe baki</p><p>"Ai babu abinda kika Sani..maza ki kara kar su saude su bar ki yau ma..." Ammi ta fada mata bayan ta gama hura wutan. Dija kara turo baki tayi</p><p>"Nidai NA gaji....binto..." Ta kwalawa kanwarta kira, </p><p>"Naam...." Yarinya ta amsa mata</p><p>"Zo ki tayani...." Tafada tana barin tabaryar cikin turmin, ammi kallon ta tayi </p><p>"Wai ke wace irin banzar yarinya ce?...yanzu binto zaki barwa dakan furan?.... Dalla ki maida hankali kar lokaci ya kure...sakara Kawai.." Ammi ta fada tana debo taliyan kadi daga kan igiya tana zubawa cikin kwarya dake hannun ta. </p><p>Dija tana turo baki ta dake furan ammi tayi molding dinshi ta zuba mata cikin roban da take zuwa talla da ita Sannan tayi mata gammo, </p><p>"In kin saida ki sayo magi da hamsin... Fulawa quarter..sai ki sayo sabulu guda daya Dan hamsin da biyar..." Ammi ta fada mata tana Dora mata gammon bisa kanta, dija dai Bata ce kala ba don in da zaa kashe ta ya fiye mata wannan tallan da take amma Kuma Bata Iya kin zuwa saboda ta nan suke samun mostly abinda suke amfani dashi da yau da kullum, furan ammi ta dauki ra aza mata bisa gammon har lokacin Bata bar kumbure2 ba</p><p>"Wai ke meke damunki?..." Ammi ta tambayeta, kara turo baki tayi</p><p>"Ni wallahi ammi banason talla... In munje garejin daura duk yawancin mazan yan iska ne...." Baki ammi ta bude tana kallon ta, dija ta cigaba dacewa</p><p>"Sai suce sai sun taba mutum Sannan su sayi furan sa...." Idanuwa ammi ta zaro tana mamakin abinda yarta take fada mata, kallon yarinyan tayi ta kalli kirjinta dake dauke da boobs yan kanana da basu gama developing ba, </p><p>"Wallahi ammi jiya wani cemin yayi in zauna kan kafanshi ya sayi dukkan furan..." Ta fada tana fashewa da kuka, da Sauri ammi ta sauke furan daga kanta tana cewa</p><p>"Wai da gaske kike?..." </p><p>"Wallahi ammi... Da ...gaske...nake....kullum haka suke mana...wasu sun girmi kawu nanu amma duk yan iska me...ni wallahi ammi banason talla..." Ta karasa maganar ta cikin matsanacin kuka, ahankali ammi ta zauna kan Dan kujeran dake gaban ta tayi tagumi Kawai sai ta fara hawaye, </p><p>"Ya Allah.. Gamu gareka...ga yar marainiyarka gareka...ya rabbi kar ka bari a cutar da yar marainiyarka...." Tafada cikin kuka, kallon dija dake hawaye tayi Sannan tace</p><p>"Dija...inda nasan yanda zanyi da ko kadan bazakiyi tallaba...amma ke kanki kinsan halin da muke ciki... Kin koshi da taliyan da kika CI?..." Ammi ta tambayeta, cikin kuka ta gyada mata kai alaman AA,</p><p>"To kin gani...dukda tallan da kike ba koshi muke ba...kiyi hakuri ...wata rana sai labari..." Ammi ta fada cikin kuka, dija Dan turo baki ta kara tana cewa</p><p>"To ammi ki yiwa inna ladio magana mana ko zata samo min gidan aiki a birni kaman yanda Ladidi takeyi...." Idanuwa ammi ta zaro,</p><p>"Allah ya sauwake...ban yarda kije aikatau....ke Kawai Allah ya rufa mana asiri..Kuma kar ki yarda wani ya taba koda akaifanki ne balle jikin ki...kina jina?..." Ahankali ta gyada mata kai ta Kara cewa.</p><p>"Nidai ammi..nafison..." Sallama wasu age mate dinta yasa tayi shuru Bata karasa maganar da tayi niyyan fada ba, yan fura2 ne kusan su takwas suka shigo Dan karamin gidan</p><p>"Kam yau anci saa kin shirya baki tsaya bata mana lokaci ba..." Inji daya daga cikin yanmatan, hararanta dija tayi </p><p>"To uwar iyayi..." Inji dija, ammi Dora mata furan tayi tana cewa</p><p>"Kar ki manta abinda NA fada maki..kinji?.." </p><p>"To ammi..." Tafada Sannan suka fita daga gidan, daman da akwai wani mai motan dake daukan su daga kauyansu zuwan cikin garin daura dake jihar katsina. Ammi daki ta shiga, nima binta dakin nayi, ina ganin yanayin rayuwarsu nace alhamdulillah Allah dai yasa babu wayanda ke zaune a irin wannan gidan a zahirin rayuwa don their life is low beyond words, tagumi ammi tayi tana tunanin yaushe wahalan su zai kare don kullum gani take kaman is getting worse, gashi yaranta hudu Kuma dija ce babban cikin su, </p><p>"Hmmm..ya rabbi ka tausaya mana..." Tafada tana Dan mikewa kan tabarman dake kasan dakin da ko cement babu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A chan wani bangare NA Kano kam wani gida ne cike ana ta bude akwatuna da alaman lefe aka kawo, duk wacce ka gani kasan yan Hutu ne don every body around is glowing kaman babu wahala cikin duniya. </p><p>"Amma wannan kayan sun hadu da yawa..kayan kaman na mata biyu?.." Inji wata mata, Dariya Matan wurin suka saki Sannan daya daga cikin su tace</p><p>"Ai yanda mutum yake hakan komai nace yake...baku ganin yanda diyar tawa take kaman ita tayi kanta?..." Inji wata mata, guda daya daga cikin su ta saki don murna,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A daya daga cikin dakunan gidan kam wata beautiful lady ce zaune kanta babu headtie sai yanmata biyu zaune kusa daita sai hira suke, da alaman lefen ta aka kawo,</p><p>"Kinsan wallahi sai kin bani wannan swiss lace din...tunda an kawo maki uban kaya..." Inji daya daga cikin yanmatan dakin, wacce akayiwa magana Dariya ta saki Wanda yasa hakorin Makkah dake bakinta ya bayyana,</p><p>"Dan wannan babu case..." Shuru tayi ta kalli wayanta daya fara ringing, murmushi ta saki tana dauka wayan, yanmatan kallon juna sukayi suna cewa</p><p>"Halan angon ne?..." </p><p>"Yes...babyna ne..." Tafada tana picking wayan, </p><p>"Baby..." Ta fada cikin sexy voice, daga Chan bangaren aka saki murmushi, wani saurayi ne zaune a office, yana Dan buga pen dake hannun shi ahankali kan desk dake gabanshi, yana jin muryan Mufida ya ajiye pen din tare da yin mika Sannan yace</p><p>"My angel ya kike?..."</p><p>"Lafiya lau...ya kake ya rayuwa?.." </p><p>"Alhamdulillah... An kawo kaya ko?.." Ya tambayeta in a low voice</p><p>"Yes baby....is so beautiful..." Tafada cikin whisper, Dariya yayi yana biting lip dinshi ahankali Sannan yace</p><p>"Not as beautiful as you...ai in ma shigo Kano sai NA kara kai personal shopping.. Kayanda babu idanuwan da zai gani sai ni kadai..." Murmushi mufida tayi tana sauraron yazid cikin so da kauna, </p><p>"Is that necessary?.." Ta tambayeshi ahankali,</p><p>"Yes mana...ai wannan da kika gani choice din Hajiya karama ne...ni zanyi nawa bayan sun gama nasu..." Yarinyan da bazata wuce shekara 22 ba ta saki murmushi Sannan tace</p><p>"Baby yaushe zaka dawo?..." Ta tambaya ahankali, </p><p>"In biki sauran sati biyu..." </p><p>"Haba mai baby...ina missing dinka...ko baka missing dina?...." Ta tambayeshi cikin sanyin murya, Dariya yayi ahankali Sannan yace</p><p>"Ina missing dinki mana...in nazo kusa dake inajin kaman in cinyeki shiyasa ban San in zo sai nan da sati biyu..." Kukan karya ta farayi tana cewa</p><p>"Yanzu nan da abuja shine bazaka zoba?... Don Allah kazo wannan weekend din...pls..." </p><p>"No...sai in the next two weeks... By then wedding din sauran sati biyu.. Kinji babyna..." Ya karasa maganar cikin whisper, </p><p>"Hmm shikenan...kana ina?.." </p><p>"Office..." </p><p>"Kaci abinci?..." </p><p>No..ko zaki zo ki bani?.." Shuru tayi Bata amsa mashi ba, hiran sukayi for almost an hour Sannan sukayi sallama, mufida wulla kanta kan gado tayi saboda murna, shi kuna ya kashe wayan ya Dora kafa daya kan daya tare da relaxing, karewa gayen kallo nayi sai naga kaman yafi mufidan kyau don ya hadu sosai, he's every ladies dream guy, bai ankaraba yaji an ture mashi kafa daga kan desk dinshi bude idanuwa yayi ya saki murmushi </p><p>"Wai ka baka sallama ne?...kullum always boosting into people's office..." Inji yazid dake gyara zamanshi, Dariya gayen da ya shigo yayi Sannan yace</p><p>"Ka koya min sallama</p><p> Mana...ustazz..." Gayen ya fada yana zama kan kujeran dake gabanshi, murmushi Kawai yazid yayi yana cewa</p><p>"Ai kasan ban yi karya ba..." </p><p>"Muje muci abinci..." Gayen ya fada mashi, agogon dake kwance hannun shi ya kalla yaga har 3pm,</p><p>"Muje..." Yazid ya fada yana mikewa, laptop dinshi ya maida cikin bag tare da wasu files, kara kallon gayen nayi nace hmm am definitely dropping dead don yazid is killing me, tsayawa nayi INA kallon yanda yake abu very slow, komai nashi a nutse babu alaman Sauri ko.hanzari tare dashi, yafi minti goma yana parking abubuwa shi Kuma dayan gayen yana zaune yana kallon shi, sai da ya gama Sannan yace</p><p>"Mu tafi..." Yafada yana rataya bag din a shoulder dinshi, gayen kallon shi yayi</p><p>"Are sure ka gama don NA san halin ka da delay kaman mace..." Yazid tabe baki yayi yabi ta gefen shi ahankali ya wuce, yanda yake tafiya sai ka rantse bashi da bone ko daya a jikinshi don tafiya shi so sluggish. Gayen mikewa yayi yana cewa </p><p>"Allah ya huci ran ango..."ya fada ya tarda yazid dake tafiya a hankali, banza yayi dashi </p><p>" wai sauran kwana nawa bikinka?.." Gayen ya tambayeshi,</p><p>"Four weeks exactly..." </p><p>"Wow...zan je Kano..I can't wait.. Allah ya hadani da mata yar Kano..." Inji gayen</p><p>"Ameen sultan..." Sultan kallon shi yayi yace</p><p>"Amma nasan kana da younger sisters.. Ka hadani da daya daga cikin su mana..." Sultan ya fada mashi, </p><p>"Ni ba hadani akayi da my mufi ba...kaima ka nemo naka..." Ya amsa mashi atakaice yana danna lifter, kofan ya bude suka shiga ya jingina da jikin lifter yana cewa</p><p>"Am so tired.. NA gagara in fara Hutu wallahi..." </p><p>"Ai kai kullum a gajiye kake..lazy guy..." Sultan ya fada mashi.</p><p>"Ai am not a racer balle in ce anason inyi gudu,...I believe in easy way ..." </p><p>"Yeah...you believe in easy tunda you are lazy...kasan muje gym wannan weekend din kaga yanda guys ke motsa jiki...." Dariya yazid yayi Wanda ta bayyana well set of teeth dinshi mai dauke da madaidaishin wushirya daga tsakiya </p><p>"Hmm mufida you are one lucky gal....," NA fadawa kaina, </p><p>"Workout kaman wani Dan danbe?... Kai am OK the way I am...Kawai I love my self...I don't need to workout.." Ya fada suna fita daga cikin lifter, hallway suka nufa suna gaisawa da wasu Colleagues nasu na CBN abuja har suka isa parking lot Kowanne su ya dauki elegant car dinshi mai tsadan gaske sukabi bayan juna zuwa wata expensive restaurant inda suka saba cin abinci.</p><p>[3:11PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 鉂ゐ煉涴煉氿煐ゐ煉滒煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挋馃挌馃挏馃枻鉂ゐ煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat( ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>2鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Suna cin abinci yanmatan wajen NA Dan flirting dasu daman sun saba da behavior dinsu, yazid kam ko daga kai baiyi balle ya kallesu shiya sa suke ce mashi oga ustaz, kullum in suka zo wajen bai daga kai balle ya kalli mutum daya cikin tsalatsalan yanmatan dake sayar da abinci shi kam sultan sunayi yanayi har wani lokacin ya batawa yazid rai, </p><p>"Hot Bomboy...." Wata yarinya dake sanye da mini skirt ja da white shirt da aka rubuta eleganza gabanshi ta fada tana tsaye kusa da sultan amma yazid dake zuba salad kan abincin shi Kawai take kallo. Cikin dariya sultan yace</p><p>"Yes sweet baby...how far..." Yafada yana cin abincin shi don in da sabo ya saba shi ko kadan bashi da kyaliya while shi yazid ko kallo basu isheshi ba,</p><p>"Oga ustqz...how is work today..." Budurwan ta tambayi yazid, banza yayi daita yacigaba da cin abincin shi,</p><p>"I will come to CBN quarter this weekend... Can I visit?..." Yarinyan ta tambayi sultan, sultan kallon hot legs dinta dake salki yayi zuwa boobs dinta dake cike dam da kirjinta Sannan yace</p><p>"No thank you...I don't want to do anything stupid..." Yafada yana maida kanshi wurin abincin shi, yarinyan dafa shoulder shi tayi Wanda yasa yazid Sauri daga kanshi ya kalleta tare da watsa mata wani irin irritating look Sannan yace</p><p>"Do you want to loose us as your customer?..." Ya tambayeta babu alaman wasa cikin muryan shi, da Sauri yarinyan ta dauke hannun ta tana kallon inda madam mai wurin ke zaune don kar taji don tasan hakan NA Iya zama matsala, sultan kam sai dariya yake yana cin abinci, </p><p>"No sir..." Yarinyan ta amsa mashi,</p><p>"Then stop all this...we're not here for gals...we are here to eat...so if you don't want to loose us then stop it..." Yafada yana bugun table din da karfi Wanda hakan ya jawo hankalin wasu costumers garesu, yana kaiwa nan ya mike, da Sauri madame ta yo wurin shi amma bai tsaya ba ya nufi kofan fita, da Sauri babban matar ta tardoshi tana cewa</p><p>"Sorry... What's the problem?..." Ta tambayeshi ahankali, afusace ya juyo yana cewa</p><p>"Tell your gals to stop disturbing us...we only come here for food... Nothing else..." Yafada Sannan ya fita, kai Kawai sultan ya girgiza ya tashi tabi bayanshi, ita Kuma madame ta balbale yarinyan tana cewa</p><p>"Daga yau kar ki kara zuwa wajen wannan Hausa boys ...kinji ko?.." Ta fada mata cikin yarensu na Igbo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yazid kam motanshi ya shiga shima sultan yashiga nashi ya bi bayanshi yana cewa</p><p>"Ko rabi abinci NA banci ba...mtwsss...".</p><p><br /></p><p>Gaban wani medium restaurant yazid yayi parking shima sultan parking yayi, fitowa yazid yayi ya kalli sultan daya nufoshi, </p><p>" why did you follow me?.. Ai kai kana jin dadin abinda suke maka...you shouldn't have followed me..." Yafada fuskan shi daure, tsoki sultan yaja,</p><p>"Wallahi kana da matsala... Kaga we are all Muslim amma kai you are always taking things to high... Gaskiya wannan abun da kake bai dace ba..." Sultan ya fada mashi ranshi bace, kallon up and down yazid yayi mashi</p><p>"Wato kam abinda nake bai dace ba...kana barin yarinyar da ba matarka ba tana taba ka....well is your life..." Yafada yana nufan hanyan restaurant din bayanshi sultan yabi da harara,</p><p>"Kai dai Kawai you are sadist... In ba haka ba don yarinya ta tabani sai ya zama iskanci nayi daita?..."</p><p>"Ai daga yanzu ban Kara zuwa wannan restaurant din..kai dake jin dadin abinda suke maka sai ka cigaba da zuwa wurin..." Ya fada nashi ataikace, dariya sultan dake biyedashi kaman bindi yana cewa</p><p>"Am really laughing in Swahili...kai dai Kawai kace 8k per plate of food is too expensive for you shiyasa kakeson chanza wuri..." Wani irin bazwaran dariya yazid yayi yana cewa</p><p>"Kaima kasan ba haka bane don ko ban aiki a CBN common 8k a plate na abinci bazai gagareni ba....amma don't worry Allah ya kawoka Kano lafiya zakasan ba da CBN nake takama ba...." Dariya sultan yayi Yana cewa</p><p>"Oho dai...kai zaka biya kudin duk abinda naci..." Inji sultan</p><p>"Wannan ba case bane..." Yazid ya fada adaidai lokacin da aka bude mashi kofan restaurant din suka shiga tare.</p><p><br /></p><p>Wannan shine kaidan yazid, baya dauka lack of moral character, ko gidan su ansan da hakan, din duk yanda kannanshi ke jin dadin rayuwa da yazo gida komai nasu yake tsayawa don dole su dawo gidan by 8pm ko su kwana waje, alhaji wato babanshi yana sonshi saboda wannan halin nashi, haka Hajiya babba wato mahaifiyarshi hakama Hajiya karama kishiyar mamansu, amma yaran gidan especially shahid da Sharif basuson zuwan shi don yana slowing rayuwan su kaman yanda suke cewa, amma yan Matan gidan irin su Zainab da yusra tare da Maryam NA sonshi kaman lollipop, likewise yan yaran gidan marzuq, mimata, ihsan da Ameera suma basu wasa da shi they love him so much don gani suke duk sun fi sonshi fiye da kowa,. Yazid ne babba a gidansu, sai da akayi shekara takwas da haihuwanshi Hajiya Bata kara haihuwa ba sai alh ya kara aure wanda month din da alh ya kara aure Hajiya babba ta samu cikin shahid itama amarya ta samu cikin Sharif wanda hakan yasan ake kiransu da twins from different mothers, saboda kamaninsu daya da alh, Kuma komai masu iri da har tsawon Sannan behavior dinshi NA rashin ji is the same, don ko da wasa Hajiya babba Bata isa ta siyawa shahid abu bata siyawa Sharif ba,</p><p> Bayan shahid Hajiya Bata kara samun haihuwa ba saida Hajiya karama ta haifi yusra da Maryam Sannan Hajiya babba ta samu cikin Zainab, atakaice dai yaran Hajiya babba 4 yazid, shahid, Zainab sai auta marzuq ita Kuma Hajiya karama nada 6, Sharif, yusra, Maryam, mimata ihsan sai auta Ameera. Zaman su is very lovable saboda ko kadan alh bai basu room din kishi ko wani abu makamancin wannan ba, he make all of them feel special don duk lokacin da yake tare da daya yana mantar da ita wata kishiya, zai nuna maki babu kaman ki so kowacce gani take yafison ta alhalin ba haka bane yana sonsu daidai amma fa bai wasa da Hajiya babba saboda karamcinta. </p><p><br /></p><p>Yau suna zaune falo Hajiya babba tare da Hajiya karama kowacce taci ado cikin expensive swiss lace little brats of the house NA wasa cikin tsakiyan falo kaman yanda su Sharif ke kiran marzuq ihsan da Ameera kenan, </p><p>Hajiya babba kam tamkar carbon copy NA yazid don komai nasu iri daya har red lips dinta. Wata matace dauke da yar paper da pen hannun ta da alaman list take, Hajiya babba kallon Hajiya karama tayi</p><p>"Ni iyakan abinda nakeson ayi kenan... Ki fada naki..." Tayi directing maganan ta to Hajiya karama, </p><p>"Ni dai ayi dinner.. Ko Kuma party till dawn..." Tafada tana girgiza kirjinta, da ganinta irin civilised women din nan ce, itama ta hadu ba kadan ba, dariya Hajiya babba tayi</p><p>"Kinsan Dan naki..Yana iya cewa bai attending..." Inji Hajiya babba,</p><p>"Kam har ya isa?.. AI bai isa ba...first wedding da zaayi a family din isa bala should be the talk of the nation..." Hajiya karama ta fada, kallon Matan dake zaune tsakiyan su tayi Sannan tace</p><p>"Hajiya wedding planner...kiyi adding party till dawn...." Shuru tayi ta kalli kofan da aka bude, shahid ne ya shigo ya zauna gefen Hajiya karama don mostly sunfi yi daita saboda Bata fiya hanasu duk rashin jin da zasuyi ba, baki ta bude zatayi magana shima Sharif ya shigo ya zauna dayan side din Hajiya karama, Hajiya babba kallon su tayi ta saki murmushi tare da girgiza kai, Hajiya karama tacigaba dacewa</p><p>"As I was saying before my angels interrupt me...kiyi planning big till dawn party..." Wannan irin shewa Sharif da shahid sukayi tare da manna mata kiss a both cheek dinta </p><p>"That's why I love you little mom..." Inji shahid don haka suke kiranta da little mom, dariya tayi tana lumshe idanuwa don jindadi, </p><p>"Wallahi haka ya kamata ayi Kawai..." Inji Sharif, Hajiya babba dariya tayi tana cewa</p><p>"Ai kunsan da Kyar Zai yarda...kun San halin yayan naku..." Daure fuska sukayi shahid yace</p><p>"Big mom..Kawai ki fada mashi yayi zaman shi Chan abuja in yaso in an gama bikin sai ni da Sharif mu saka matar a mota mu kai mashi..." Yafada babu wasa, </p><p>"Ai hakan Kawai zaayi...zuwan shi ma bai da amfani..." Inji Sharif, </p><p>"Kunci gidanku... First son dina kuke cewa hakan?... Zanci ubanku wallahi kunsan halina sarai..." Hajiya karama ta daka masu tsawa, shuru sukayi din sun San tana Iya birkice masu yanzu, Hajiya babba dai kallon su Kawai take with adoration, tana tunanin lokacin da akace zaayi mata kishiya komai nata tsayawa yayi saboda bakin ciki amma yanzu kam kullum cikin hamdala take da Allah ya hadata Dana gari, </p><p>"Kuma ki hada mana get together NA mothers Kawai..." Inji Hajiya karama, matar da aka kira da Hajiya wedding planner sai rubuce2 kawai take, duk abinda aka fada sai ta rubuta, sai da aka gama fada mata komai da zaa bukata sannan tace </p><p>"To zanyi listing komai Sannan in aiko maku da bill..." Inji Matan</p><p>"Wannan babu case..." Inji Hajiya karama dake magana tamkar danta zaayiwa biki, matar mikewa tayi Hajiya babba da Hajiya karama suka bi bayanta, har bakin motan Matan suka rakatq Sannan suka komo cikin part din Hajiya babba don most of the time nan suke zama suci susha, har yan yaran ma basu zama a dakin wasansu sunfi son su kwaso kayan wasansu su dawo part dinta Kuma bata hanasu tunda da akwai masu aiki da zasu gyara waje ko sun Bata.</p><p> Falo suka dawo suka zauna suna listing wayanda zasu gayyata din kar lokacin ya kara matsowa su rikice, Hajiya babba NA fadan sunayen mutanen itakuma Hajiya karama NA rubutawa cikin iPad dake hannun. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sai daf da sallan ishai su dija suka dawo daga tallan daman kusan kullum haka suke dawowa saboda sai bayan sallan asar suke tafiya, agajiye ta shigo gidan ba ko sallama ta shiga dakin ta tarda ammi zaune su binto suna bacci kan tabarma, ajiye ruban tallan tayi da karfi ta zauna kasa gaban ammi</p><p>"Sannu da dawowa..."</p><p> Ammi ta fada mata tana cire gammo daga kanta,</p><p>"Yauwa..." Ta fada tana kallon su binto dake bacci,</p><p>"Har sunyi bacci?.." Ta fada har lokacin Bata bar kallon su ba, </p><p>"Yan rigima sunyi bacci...ya kasuwa?..." </p><p>"Lafiya lau..." Ta amsa mata tana kwanciya kasan inda take,</p><p>"Madalla..." </p><p>"Ga kayan da kikace in sayo nan cikin roban,...." Ta fada tana nuna Roban data ajiye</p><p>"Yauwa yar albarka..." Ammi ta fada tana jawo roban gabanta tana kallon abubuwan da dija ta sayo, dija gyara kwanciya ta tayi yanda zata Iya dauko kudin dake daure a haban zaninta, daga kwance ta fara kunce daurin ta dauko kudin </p><p>"Ga sauran...dari biyar ne da ashirin.. NA sayi awara ta talatin cikin kudin..." Ta fada tana mikawa ammi kudin</p><p>"To dijata...nagode kinji...dafatan babu Wanda yayi maki zancen banza yau?..." Daga kwance ta girgizawa ammi kai</p><p>"Yau ban shiga garejin ba...cikin garin dauran na shiga kuma na saida duka...."</p><p>"To alhamdulillah...." Ammi ta fada tana jin dadi, ammi mikewa tayi ta dauki roban ta ajiye shi gefe </p><p>"Ammi gobe Dan Allah a kai gero injin... Wallahi marata ke ciwo...." Tafada tana Dan dafa maranta, ammi ajiye roban tayi ta dawo ta zauna </p><p>"To sai a kai injin din..amma ki kokarta muyi surfe mu wanke don mu bawa awaki su sha..." Dija turo baki tayi tana cewa</p><p>"Ammi ni marata ke ciwo...irin ciwon da yayi min wancan lokacin yake yi min..." </p><p>"To kilan bakon watanne zai zo..." Sai lokacin dija ta tuna da watan da ya gabata ta fara ganin jini Wanda ammi ta shaida mata cewa alaman girma ne. </p><p>"Wai ammi duk wata sai nayi wannan abun?..ni wallahi banason shi...." Tafada hannun ta biyu kan maranta, </p><p>"Ai lalura ne Kuma Allah ne ya dorawa mata Kuma ba din bayason mu ba...wasu ma sai sun nema amma basuyi...don haka ki bar cewa bakison shi...." </p><p>"To ammi..." </p><p>"Tunda bai kaiga zuwa ba kije kiyi sallan ishai...." Dija ta fi minti biyar kwance Sannan ta mike ta fita ta dauki buga ta shiga kewayen su da aka zagaye da buhu. Few minutes later ta Fito tana cewa</p><p>"Ammi yazo..." Tafada da karfi, ammi murmushi Kawai tayi Bata amsa mata ba.</p><p>[3:12PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挏馃挍鉂ゐ煐ゐ煉欚煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>鉂ゐ煉滒煉涴煐ゐ煉氿煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat(ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>3鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da Sauri ta dawo cikin dakin tana cewa</p><p>"Ammi NA ganshi..." Tafada cikin jindadi</p><p>"Naji...wai in tambayeki...murnan me kike?...." Ammi ta tambayeta tana kallon ta, </p><p>"Babu komai..." Ta fada ahankali, </p><p>"Hmmm NA gane Kawai don bakison yin sallah ne...to kiji tsoron Allah... Maza ki tashi ki tafi makaranta....nasan an zauna tunda anyi sallan ishai...." Ammi ta fada mata, nan ta kara Bata rai tana cewa</p><p>"Ammi NA gaji..." Bata idaba ammi tayi mata dakuwa</p><p>"Kinci mai garinku...maza ki tashi ki tafi..." Ammi ta umarceta, bata fuska tayi kaman zatayi kuka ta fara cewa.</p><p>"Ammi gasu binto basu je ba?...ni ki bari sai gobe.. " ta fada kaman zatayi kuka, baki ammi ta bude tana kallon ikon Allah, tana mamakin yanda komai sai dija ta hada kanta da kanwarta, komai Bata yarda itace babba sai tace su binto kasa da kasa</p><p>"Wai ke in tambayeki... Ke da binto waye babba?..." Ammi ta tambayeta tana kallon yanda idanuwanta suka chanza kaman zatayi kuka</p><p>"Ni..." Ta amsa mata ahankali,</p><p>"To meyasa komai sai kin hada kanki da binto?... Baki San kome kika shi su ma Zasuyi ba?... Ke ce babba son haka ki dinga daukan girma..." Ammi ta fada mata cikin lallashin, </p><p>"To ammi..." Ta fada rana turo baki don ko kadan Bata gamsu da maganar ammi ba, kullum komai ita, shiyasa kullum tana aduan Allah yasa a dauketa, har wani lokacin adua take tana cewa</p><p>"Allah kasa a saceni a kaini katon gida ko shara da wanke2 in dingayi..." Take fada duk lokacin da take tallan fura ba kaman in ta zama frustrated.</p><p>"Maza tashi kar a fara ba dake ba..." Ammi ta fada mata, </p><p>"To..ammi amma ki bani ashirin din in kashe in naje chan..."</p><p>"Ban baki ashirin... Amma ga goma..." Ammi ta fada mata tana bata naira goma daga cikin kudin data kawo, amsan kudin tayi Ta bude wata old Ghana must go ta dauko wata old and faded pant tare da kyalle ta cire pant dake jikinta ta saka Wanda ta dauko tare da tura kyallen data dauko, ta gyara daurin dankwalinta tana fita daga gidan babu hijab, tana tafiya tana kallon yara dake wasa cikin hasken wata har ta kai kusa da wani mai nama, karasawa tayi kusa da inda mutum yake</p><p>"Danmusa inayini..." Ta gaida shi tana kallon naman dake maiko a gabanshi</p><p>"Khadija ya kike?..." Inji saurayin Wanda bazai wuce shekara 18 to 20 ba</p><p>"Lafiya lau..." Ta amsa mashi ko blinking batayi saboda yanda take kallon naman, murmushi yayi</p><p>"Har kun dawo kenan?..." </p><p>"Eh..." Ta amsa mashi atakaice, har lokacin tana kallon naman tana aduan Allah yasa ya yanmata kaman yanda ya saba, </p><p>"Makaranta zaki je?.." Ya tambayeta</p><p>"Eh...", dariya saurayin yayi yana kallon yanda take lashe baki, yanka uku ya debo ya zuba cikin takarda ya mika mata, kaman zakin daya shekara bai ci abinci ba ta miko hannu zata amsa sai saurayin ya maida hannun shi yana kallon ta Sannan yace</p><p>" yaushe zaki bani amsa ta?..." Ya tambayeta ahankali, Dan turo baki tayi tana cewa</p><p>"Gobe..." Dariya saurayin yayi</p><p>Hmm dija sarkin wayau..kullum sai kice min gobe...to yaushe goben zai iso?..." Da Sauri tace</p><p>"Allah gobe zan baka amsa..." </p><p>"Allah ya kaimu goben... Amma in baki bani amsa ba bazan kara baki nama ba...kin amince?.." Da Sauri ta gyada mashi kai tana cewa</p><p>"NA amince..." Sai lokacin ya mika mata naman, tana amsa ta bar wajen da Sauri tana bude takarda naman, tana tafiya tana yaga kadan2 wai don kar ya kare. Haka tana zaune makaranta tana cin namanta ahankali daman she's use to it.Har aka tashi karfe goma dija bata gama cinye naman ba saboda yanda take yagan daman ahankali. Ana tashi ta tafi gida tana hamma, daman Tasan kafin ta iso duk sunyi bacci don haka tana shiga gidan taja kaurensu da baida sakata taje ta kwanta tana tunanin yanda gobe zai kasance mata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yazid bai shiga apartment dinshi ba sai bayan sallan ishai daman mostly sai bayan sallan ishai yake shiga gida don quarters din is very lonely Kuma shi bayason hayaniya most especially Kuma ba yanayin halinsu daya da sauran guys din ba don mostly su da yan mata suke wining time dinsu shikuma da calling iyayenshi ko Kuma karatun alquran sai kuma kiran mufida Wanda wani lokacin da wayan yake kwantawa a kunnenshi saboda ita.</p><p><br /></p><p>Yana shiga apartment dinshi Wanda ta hadu daga company don komai is made abroad, ko zama baiyi falo ba ya shiga daya daga cikin four bedrooms din ya cire kayan jikinshi yayi folding dinsu tamkar mace ya ajiye su cikin closet ya shiga wanka ta fito bai wani shafa mai ba ya saka jallabiya Sannan ya dauki wayanshi yayi dailing number Hajiya babba</p><p> Alokacin duk suna babban falon alhaji suna fira yara suna wasa sai sai yanmatan na chatting da wayansu ga katon naman akuya roasted suna ci ana hira, Hajiya dauka wayan tayi yan yara suka taho wurin ta da gudu don sun san shine cos mostly lokacin yake kiran su, sallama Hajiya babba tayi ya amsa yana cewa</p><p>"My mommy good evening..."</p><p>"Evening sweetie... Ya aiki?..."</p><p>"Alhamdulillah... Ya gida da yara?..." Ya tambayeta a nutse, da Sauri yaran sukace</p><p>"Yaya ga mu...." Suka fada a chorus, Dariya yayi, Hajiya babba ta ajiye masu wayan bayan ta sashi hands free, nan suka fara labari ko wa NA bashi labarin abubuwa kala saida suka gama Sannan Hajiya babba ta dauki wayan suka fara hira tana cewa</p><p>"Son ga junior mom tana hada maka party till dawn..." Dariya yayi yace </p><p>"Small mom...nasan kina jina...banason party till dawn..." Ya fada yana Dariya,</p><p> Itama dariya tayi Sannan tace</p><p>"Kayi kadan..." Tafada cikin high voice, yanda zai jita da kyau, dariya ya karayi yana cewa</p><p>"Nidai ko kun hada ban zuwa...sai dai kuyi abunku Ku kadai..." Yafada cikin raha yana jiran amsan small mom don yasan ta da tirjewa kan abu, </p><p>"Ai kayi kadan yaro...party kam an hada an gama..." Ta fada again da karfi, alhaji kam ko kallon su baiyi sai cin naman yake yana korawa da juice while suma yan yaran suna ci suna wasa. </p><p>"Wai yaushe zaka dawo?..." Hajiya babba ta tambayeshi,</p><p>"Sai nan da sati biyu..." Ya amsa mata</p><p>"Kai yaro maza ka dawo...nan da sati biyu is too far..." Inji Hajiya karama,</p><p>"Sai lokacin hutuna zai fara..." </p><p>"Nidai ka dawo nan da sati daya..." Hajiya karama ta umarceshi,</p><p>"To momcy..." Ya amsa mata in a funny way.</p><p>"Ina twins?..." Ya tambaya, don haka yake kiran Sharif da shahid,</p><p>"Basu dawo ba..." Hajiya babba ta amsa mashi</p><p>"Aikensu akayi ko yawon ne Mara amfani?..." Ya sake tambaya, dariya Hajiya karama tayi tana cewa</p><p>"Suna waje suna shan iska...." </p><p>"Ai ba zafi ke da akwai cikin gidan ba...bari in kira su..." Ya fada Sannan sukayi sallama, kashe wayan yayi Sannan yayi dailing number shahid, alokacin Sharif na tukin mota shi Kuma shahid na zaune, yana chatting, yana ganin kiran yazid ya kalli Sharif yace</p><p>"Guy ga vigilanty NA kira..." Yafada yana dariya, shima Sharif dariya yayi</p><p>"Kar kayi picking.. Kilan ya kira gida an fada mashi muna waje.." Kin picking sukayi har wayan ya gama ringing, yazid dai girgiza kanshi yayi yana murmushi</p><p>"Sheggu..." Ya fada yana dailing number mufida. Sai da suka kusa hour biyu suna waya Sannan sukayi sallama ya kwanta yana imagining nan da sati four yana da aure.</p><p><br /></p><p>The following day ya shirya as usual ya tafi office daman a chan ake kawo mashi breakfast.</p><p><br /></p><p>Dija kam sai data gama surfe geron ta wanke ta shanya Sannan ta shiga wanka, acikin karamin toilet din Wanda babu cement ta tsaya tana kallon tsaraicin ta, daman tunda alamun girma suka fara fito jikinta ta maida kanta tamkar madubi ba kaman in ta shiga kewaye, yau ma haka ta tsaya tan kallon white skin dinta dake fari tas compared to her face don jikinta ya fi fuskan ta haske nesa ba kusa ba, kallon yan boobs dinta tayi ta kurawa dark nipple dinta ido tana mamakin yanda akayi Bata lura da sanda suka fara fitowa ba don ita kaman farat daya ta fara ganin su,Dan juya baya tayi tana kokarin kallon ass dinta amma Bata gani kaman yanda ta bukata, tafi minti talatin tana kallon kanta don ko kadan Bata gajiya da kallon kanta</p><p>"Wai ubanme kike in kika shiga kewaye?..." Ammi ta fada da karfi, da Sauri tace</p><p>"Ammi kashi nake..." </p><p>"Ke kullum sai in kin shiga wanka kike kashi?... Dalla maza ki fito kafin in sameki..." Ammi ta daka mata tsawa</p><p>"To.." Ta amsa mata Sannan ta fara wanka. Ko.minti biyar batayi ba ta fito da daurin kirji ta shiga daki ta shafa Vaseline ta saka wata faded but neat atamfa Sannan ta fito lokacin ammi NA jifan Dan wake cikin tukunya</p><p>"Ke dauki yaji ki daka.." Ammi ta fada mata, turo baki ta karayi don one thing about khadija ko kadan batason aiki ko sai goma zaa aiketa sai ta nuna bacin ranta dukda zatayi amma ba don ta soba</p><p> Haka ta daka yaji tana turo baki har ta gama, bayan kaman minti arbain aka sauke danwake sukaci Sannan ta tafi injin din. Da wuri ammi ta gama mulmula mata furan amma still sai bayan sallan asar suka tafi tallan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hajiya karama ce zaune kusa da Hajiya babba a falon Hajiya babba tana cewa</p><p>"Gaskiya yaya nidai NA gaji da halin wannan yarinyan... Kokadan Bata daukan darasi...ka barnatar da kaya..gaskiya wata yar aiki zan sake..." Inji Hajiya karama, Hajiya babba shuru tayi for a while kaman mai tunani Sannan tace</p><p>"To me zai hana a karo maki wata batare da ki kori ita zulan ba?.." Hajiya babba ta fada mata, da Sauri Hajiya karama ta girgiza kai</p><p>"Gaskiya ni ko kadan banason zama da wannan yarinyan yanzu..Kawai wata zansa antyn katsina ta samo min..." Dariya Hajiya babba tayi tana cewa</p><p>"Har katsina Neman yar aiki?..."</p><p>"Yo yaya ya zanyi ?.. Ai gara katsina tunda yawancin yan Matan birnin nan sun fiya wayewa...amma in aka samu cikin kauyen kayayau basu daukan abu for granted,..." Inji Hajiya karama</p><p>"To shikenan amma Dan Allah karki sallami zulai...kinsan babu kyau hana mutum hanyan samun abinci.. Kawai a nemo maki wata ki hada su biyu..." Inji Hajiya babba, </p><p>"To shikenan...amma yarinyan nan taci arzikinki wallahi.. Don da nayi niyyan da an kawo min sabuwa zan sallami shegiya ta je Chan gidansu ta bar na tar masu da abinci kaman yanda take nan..." Yanda tayi maganar yasa Hajiya babba dariya </p><p>"Wallahi kin Iya bada dariya..." Inji Hajiya babba, itama Hajiya karama dariya tayi</p><p>"Ai yarinyan ce da ban dariya...sai ta kusa karar da dettol daya wajen wankin toilet...jiya daga nace ta hadawa Ameera tayi tayi fulling jug da tea ta mika mata..." Hajiya dariya ta karayi,</p><p>"Funny Wallahi.. Sakarcinta is written all over her..." Inji Hajiya babba, </p><p>"Aikam am feed up with her wallahi... Amma bari insa a samo min wata kilan tayi learning daga gareta don NA lura su ma yaran suna son sakarcinta especially Ameera..." </p><p>"Yo daman yara haka suke...sunfi son naughty people..." Inji Hajiya babba, Hajiya karama Bata kara cewa komai ba ta dauki wayanta tana cewa</p><p>"Bari in kira yayan katsina muji ko zan samu mai aikin...." Ta fada tana dailing number elder sis dinta dake aure a katsina</p><p>馃挌馃挋馃挏馃枻鉂ゐ煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>鉂ゐ煉欚煉涴煐ゐ煉滒煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat(ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>4鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Three days later_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dija ce dauke da roban furan ta tana yawo tana shiga manyan gidaje don ita gani take yan kananan gidan basu da kudin siyan fura</p><p>"Duk daya muke daku..." Take fada duk sanda taga yar karamar gida. Tana cikin tafiya ta shiga cikin wani beautiful house, daga tsakar gidan ta hangi wata mata zaune kan carpet tana waya, daman ta taba shiga gidan Kuma an saye dukan furanta, hakan yasa ta tsaya Bata tafiba ta tsaya tana sauraron abinda matar ke cewa</p><p>"Eh wallahi Hajiya ce tace kanwata na son yar aiki Kuma duk Wanda NA samu sai suce Kano yayi masu nisa..." Ta fada ahankali tana sauraron abinda ake fada mata, bayan few seconds ta kara da cewa</p><p>"Ni ma ko kadan banason ace wasu su kai mata yar aikin ba muba saboda cewa tayi yayarta matar isa bala ce..kinga da akwai samu...." Ta fada Sannan shuru ya kara biyo baya tana sauraron abinda ake fada mata, </p><p>"To shikenan.. Dan Allah ki bincika.. Nima zan cigaba da nema amma fa ance wacce zata Iya aikin komai..." Matar ta fada, dija kam duk tana jin abinda matar ke cewa, shuru tayi tana tunanin inama a dauketa, bayan kaman minti biyu matar ta kashe wayan ta Sannan ta daga kanta ta kalli dija, da Sauri dija tace</p><p>"Kuna sayen fura?..." Ta fada ahankali, matar murmushi tayi Sannan tace </p><p>"Ki kawo in gani..." Ta fada mata fuskan Hajiyan dauke da murmushi da ganinta kasan irin yan duniyan nan ce don da gani tana shan taba, ahankali dija ta karasa ta sauke furan gaban Matan ta yaye ledan furan don matar ta samu daman ganin furan da kyau, </p><p>"Kece kika kawo min fura kwana kin baya?..." $ matar ta tambayeta, da Sauri dija ta gyada mata kai tare dacewa</p><p>"Eh nice..." Ta fada har lokacin Bata daina tunanin abinda taji matar NA cewa ba,</p><p>"To ki bani NA dari biyu in saka a fridge...don naji dadin furan kwanakin baya..." Da Sauri dija ta dauko Leda daga gefen roban ta ta fara zuba furan cikin natsuwa kaman ba ita ba, sai da ta gama ta ta dauko biyu ta kalli matar tana cewa.</p><p>"Ga gyara..." Ta fadawa matar, murmushi matar tayi Sannan tace</p><p>"Nagode..." Ta fada tana daukan purse dinta, budewa tayi ta dauko dariya biyu ta Bata, dija ta amsa tare dacewa</p><p>"Nagode..." Rufe furan tayi da ledan Sannan ta mike tana son yiwa matar magana amma ta kasa, daukan furan tayi har ta kai bakin gate ta juyo ta kalli Matan dake latse2 wayanta, tsayawa tayi bakin gate din Wanda yasa matar kallon ta, </p><p>"Lafiya dai ko?..." Matar ta tambayeta, da Sauri tace</p><p>"Eh...daman...." Sai tayi shuru, matar tsaya kallon ta tayi don sauraron abinda zatace, jin tayi shuru Kuma Bata tafi ba yasa ta cewa</p><p>"Daman me?..." Inji matar cikin natsuwa, dija kasa cewa komai tayi Kawai tayi tsaya kikam dauke da robanta akanta, </p><p>"Dawo inji..." Matar ta fada mata, ahankali dija ta dawo , gefen ta matar ta nuna mata</p><p>"Sit..." Matar ta fada mata, dukda dija batajin turanci ta gane abinda matar ta fada mata, ahankali ta sauke roban kanta ta zauna gefen Matan. </p><p>"Ki fada min...me kike son fada min..." Matar ta tambayeta, dija dai shuru tayi tana wasa da yatsunta,</p><p>"Ke nake sauraro..." Matar ta sake fada mata, ahankali ta fara cewa</p><p>"Daman....naji...kina...cewa....kinason... Mai..aiki...shine..." Sai tayi shuru saboda yanda gabanta ke faduwa, Matar ta gane inda ta dosa dukda muryanta NA cracking</p><p> "Ina jinki..." inji matar, </p><p>"Nace..in..babu...damuwa....zan....yi..." ta kai.karshen maganar da kyar, murmushi matar tayi tana cewa</p><p>"Da kaman bazaki ida maganar ba...kina Iya aikin ne?..." Da Sauri dija ta gyada mata kai tana cewa</p><p>"Eh.." Yanda tayi maganan yasa matar dariya tana cewa</p><p>"In iyayenki basu yarda ba fa?..." Da Sauri tace</p><p>"Babanmu ya rasu..nasan ammi zata yarda...in kin je ..kin fada mata ..." Ta fada muryanta na cracking, matar kura mata ido tayi tana kallon beautiful and innocent face dinta Kuma tana tunanin wane irin dalili ne zaisa yarinya ta so zuwa gidan aiki Kuma da kanta ba wai forcing dinta akayi ba, amma tana kallon how faded her hijab and wear looks sai ta gane she will definitely needs some income Kuma Tasan ta cancanci irin gidan da ake magana.</p><p>"In Bata amince ba fa?.." ta sake tambayan ta, muryan NA rawa tace</p><p>"Nasan zata yarda..." Ta Bata assurance dukda tana ganin da kyar hakan zai yiwu don Tasan stand din ammi kan barin ta tafi wani wuri aiki amma gaskiya ta gaji da wannan wahalan tallan Kuma tayi deciding zatayi anything necessary don ammi ta amince NA wannan zancen</p><p>"Wane wuri kike?..." Ta tambayeta, nan dija ta fada mata sunan kauyensu, baki matar ta bude</p><p>"Yanzu daga Chan kuke zuwa nan cikin garin?.." Kai dija ta gyada mata</p><p>"Lallai kam..amma ina ganin da nisa Kuma aikin ba a garin katsina zaayi ta..Kano ake bukatan mai aiki..." Da Sauri dija ta katseta dacewa</p><p>"Ai ba komai... Tunda baa kasa zanje ba..." Dariya matar tayi </p><p>"To..yanzu tunda an fadamin ana bukatan mai aikin da wuri bari in kaiki garin naku sai muyi magana da amminki..." Wani irin dadi dija taji amma sai cewa tayi</p><p>"Ai ban gama saida furan ba..." Dariya matar tayi tana cewa</p><p>"Ki kirge min sauran..." da Sauri dija tayi counting sauran cikin Leda ta mika mata</p><p>"NA nawane?..." Matar ta tambayeta</p><p>" sauran na dari uku da sabain..." Dari biyar matar ta dauko ta Bata, </p><p>"Ki jirani nan..." Inji matar Sannan ta shiga cikin falonta, Bata yi wasting time ba ta fito da gyale tare da car keys dinta, sai adua take Allah yasa a amince don Tasan ba karamin samu bane in kayi hulda da family isa bala, dija sai mar mar da idanuwa Kawai take, mota matar ta fidda daga parking lot dija ta shiga ciki duka kama hanyan garinsu. </p><p><br /></p><p>Karfe biyar da minti ashirin suka iso kofar gidansu dija, da Sauri dija ta fita ta shiga gida matar ta fito tana kallon kauyen tana mamakin</p><p> Ya akayi suke rayuwa a irin wannan wuri don tamkar bayan duniya suke saboda karanta kauyen, dukda ba cikin gari take ba amma Sam batasan daura yayi extending zuwa haka ba. Dija na shiga gidan ta fara kwala ammi kira</p><p>"Ammi!!...ammi!!!..." Ta dinga fada tun.zaure, ammi dake kada miyan kuka ta mike da Sauri saboda yanda gabanta ya fadi don kiran dija har cikin zuciyanta saboda yanda take kwala mata kira on top of her voice, da Sauri ta ta taro dija dake shigowa, kallon ta tsaya yi hannun ta dafe da kirjinta, </p><p>"Dija lafiya?..." Ta tambayeta cikin tashin hankali, dija kallon ta tayi da gwala2 idanuwanta tana murmushi</p><p>"Ke lafiya?..." Ammi ta sake tambayeta tana kallon ta from head to toe, </p><p>"Lafiya lau..wata Hajiya ce ta zo wurin ki..." Ta amsa mata tana ajiye roban furan ta, kallon mamaki ammi tayi mata, </p><p>"Wacce Hajiya?..." Ta tambayeta, </p><p>"Gata nan..." Dija ta fada tana nuna matar data shigo cikin gidan da sallama, da Sauri ammi ta amsa tana kallon ta, </p><p>"Barka da zuwa...shigo mana..." Ammi ta fada jikinta NA rawa don batasan abinda dija tayi ba da aka biyota, da Sauri ammi ta shiga cikin dakin matar ta bi bayanta tare da daga labulensu da ya kasu kusa kashi takwas saboda yanda ya yage, ta kasan wusiya matar ta dinga kallon dakin tana mamakin how living creature can sleep in such an awful place, ammi kakkabe tabarma dake kasa tayi jikinta sai rawa yake Kuma zuciyanta tamkar ya fito ta bakinta saboda fargaba. Dija kam gefe daya ta tsaya tana aduan Allah yasa a samu nasara, Da Sauri ammi ta debo ruwa cikin randa ta mika wa matar tana cewa</p><p>"Maraba..maraba..." Cikin faraa matar ta amshi ruwan amma tasan ko da wasa bazatyi gigin kai kofin bakinta ba, rike cup din tayi tana kallon dija dake ragube jikin bango tana kallon su, murmushi ta sakar mata itama dija tayi karfin halin maida mata martani, ammi durkusawa tayi kasa kneels dinta biyu kasa sai tafin hannun ta biyu suma kasa </p><p>"Ina yininmu..." Ammi ta gaidata, cikin faraa matar ta amsa da </p><p>"Lafiya lau..ya gida ya yara?...."</p><p>"Lafiya kalau suke...." Ammi ta fada Sannan tayi shuru tana sauraron abinda ke tafe da matar, ahankali matar ta ajiye cup din Sannan ta fara cewa</p><p>"Sunana Hajiya Aisha...ina zaune a cikin garin daura...ina Sana'a kala2 cikin su har da kai yara gidan gidan manyan mutane don suyi masu aiki don gyara rayuwan yaran..." Ta Dan yi shuru ita Kuma ammi dai tana nan durkushe tana sauraron ta, Hajiya Aisha ta cigaba dacewa</p><p>"To da akwai wata kanwar aminiyata dake son mai aiki karama daidai kaman yarki dija...shine ta shaidamin..." Da Sauri dija ta dan buga kafa kasa wai ita mai wayau don kar ta fadi ita tace tana son aikin, Kuma Hajiya ta gane sai tayi shuru ta chanza maganan zuwa</p><p>" shine naga yarki nace bari in biyo in tambaya ko zaki amince in kaita..." Ammi da kanta ke kasa sai ta fara girgiza kai alaman AA, dija dake tsaye tana kallon su nan take taji kwaiwanta yayi sanyi don Kawai so take ta je.</p><p>"Gaskiya Hajiya kiyi hakuri... Yarana marayune...nice uwarsu nice ubansu tunda yawancin yan uwan ubansu basu damu da suna raye ko suna mace ba...nasan muna cikin hali amma gaskiya nafison in wayi gari in gan dukkan yarana kusa dani...ko kadan banason abinda zai taba masu mutuncinsu saboda nasan yanda ake wulakanta marasa karfi cikin birni..." ta fada ahankali cikin natsuwa da sanyin murya Kuma har lokacin bata mike daga inda take ba, ahankali matar ta daga kai ta kalli dija da idanuwanta suka ciko da kwallan bakin ciki, murmushi Hajiya ta saki Sannan tace</p><p>"Babu komai...amma yar uwa inason in shaida maki cewa babu inda mutuncin ya mace ke saurin zubewa kaman talla saboda yanda duniya ta lalace... Da akwai maza azzalumai Wanda suke gurin lalata rayuwan yaran mata mussanman wayanda ke yawo kan titi...." Ahankali ammi tace</p><p>"Allah NA tsarewa ai...ni kaina don babu yanda zanyi ne amma ko kadan yata Bata talla" Ta fada cikin sanyin murya, ahankali Hajiya Aisha tace</p><p>"ga dama nan...NA daya yarki Bata zuwa koina tana cikin gida..Kawai ta kula da bangaren uwar dakinta Kuma ba ita kadai bace...Sannan duk wata zaa aiko da albashinta Wanda INA tabbatar maki yafi talla saboda ita Bata wahala ba ke baki wahala ba....Kuma wannan gidan da nake fada maki suna kuka da masu aikinsu tamkar yaran da suka Haifa don har boko da islamiyya suke saka su sai na karshe ina tabbatar maki dacewa zaa kare maki mutunci yarki...don haka ina baki shawaran da zan bawa kaina...ki gwada ki gani in hakan baiyi maki ba kina iya bukatan a maido maki ita...." Hajiya Aisha ta karasa maganar ta tana kallon dija dake hawaye, ammi dai shuru tayi har saida Hajiya ta kai aya Sannan tace</p><p>"Ni gaskiya nafison in tashi in ga yarana kusa dani...Sam hankali na bazai kwanta ba duk lokacin Dana tuna yata tana wani wajen Kuma basan irin halin da take ciki ba..." Ta fada kanta kasa, da Sauri dija ta fita daga dakin tayi waje ta fara kuka sosai kaman an doketa</p><p>"To shikenan... Allah ya shige mana gaba..amma zan dawo gobe koda kin chanza shawara.. Ba don komai yasa na fadi hakan ba sai don dija ta shiga raina...haka nan naji ina sonta tamkar nawa..." Itadai ammi shuru tayi Bata kara cewa komai ba, Ahankali Hajiya ta mike tare da dauka handbag dinta, itama ammi mikewa tayi tana cewa</p><p>"Don Allah ki tsaya kici turo..." Dariya Hajiya Aisha tayi</p><p>"Aa ..nagode kwarai..." Itama ammi Dariya tayi tana cewa </p><p>"Ai Baku Iya cin irin abincin mu dake lami..."</p><p>"Sam ba haka bane...Kawai na koshi ne..." Ta fada tana fitowa waje ammi na biye daita har waje, ta wutsiyar ido ta kalli kukan dake tafasa tsanwa shar babu alaman kayan miya ciki. Kallon yaran ukun dake zaune tayi ta bude bag dinta ta Ciro Dari biyar ta mikawa babban cikin su wato binto, durkusawa tayi ta amsa tana cewa</p><p>"Mun gode..." </p><p>"Haba Hajiya...har da wata hidima...mun gode kwarai Allah ya saka da alkhairi..." Tafada tana raka ta zaure, </p><p>"Babu komai... NA gode nima...sai goben..." Hajiya tafada tana fita waje, sai ihun dija ke tashi duk ammi najinta amma tayi banza daita dukda Tasan halin yarta da kwallafa amma saidai ta mutu. Hajiya kallon dija data Dora hannu bisa kai tayi tana Dariya</p><p>"Haba dija...ki bar wannan kukan mana...in Bata amince ba to Allah bai kaddara zaki ba..kiyi shuru kinji..." Ta fada tana kallon yanda take Bata baki tana kuka kaman anyi mata mutuwa, kara volume din kukanta tayi dataga Hajiya ta shiga cikin motanta. Da gudu ta shiga cikin gida ta kwanta kasa tana cewa</p><p>"Wallahi... Ban kara zuwa talla..."</p><p>[3:12PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 鉂ゐ煉滒煉涴煐ゐ煉氿煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挏馃挍馃挌馃枻馃挋鉂�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat( ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>5鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tafada cikin matsanacin kuka tare da kwantawa kasa tana rolling kaman wacce akayi wa albishir da mutuwa, babu Wanda ya tanka mata su binto tsayawa sukayi kanta suna kallon yanda take birgima kasa, ko kallon ta ammi batayi ba har tagama zuba wa su binto miya kan tuwon dake cikin kwano Sannan ta shiga ciki, har lokacin dija NA kwance kasa yaran neighbors sai lekota suke don ba karamin ihu take ba tana cewa </p><p>"Ban kara zuwa talla...ban kara zuwa talla...saidai yunwa ta kashe mu gidan nan...." Ta fada cikin kuka, ammi na shiga cikin dakin ta nufi inda take ajiyan bulala ta yo waje, dija dake kwance na ganin ammi da bulala ta tashi tayi waje da gudu tana kuka, </p><p>"Shegiya da kin tsaya yar banza...." Ammi ta fada tana maida bulalan. Har bayan sallan magrib dija Bata dawo gida ba tana nan labe gefe daya tana kuka gashi har lokacin Bata bar fargaban abinda ammi zatayi mata ba.</p><p><br /></p><p>Ammi na ganin Bata dawo ba tasa binto ta nemota, sanin inda take zama in tana kuka yasa binto bata sha wahalan gano ta ba, </p><p>"Kizo inji ammi..." Ta fada mata, hararanta dija tayi da red eyes dinta tana cewa</p><p>"Ki wuce ki bani wuri..." </p><p>"Ammi tace kizo ..." Binto.ta sake fada mata, aikam sai ta rarumi takalminta binto NA ganin hakan ta bar wajen da gudu taje ta fadawa ammi yanda sukayi daita,</p><p>"Ta shigo Dan kanta..." Ammi ta fada tana shiga cikin daki, har bayan sallan ishai dija da zaune inda take tana kukan bakin ciki, gani take gwara Kawai ta amince tana son dan Musa suyi aure kamar yanda yake yawan fada mata dukda batasan burouban da akeyi cikin aure ba amma ko kadan batason ta kara talla, tana nan zaune Bata ankaraba taji an damketa da Sauri ta daga kai taga ammi, baki ta bude zatayi kuka ammi ta dora yatsanta daya kan bakinta tana cewa</p><p>"Wallahi kika sake naji bakinki sai NA lahira ya fiki jin dadi...maza tashi ki shige min gaba..." Amma ta fada tana rike daita don tasan dija da kafan gudu kaman taci kare, da Sauri dija ta mike ra shiga gaban ammi suka taho gida sai shessheka Kawai take saboda yanda tayi kuka, daki ra shiga ta rabe jikin bango tana sauraron abinda ammi zatayi mata, ammi ce ta shigo rike da kwanon tuwo ta ajiye gaban dija</p><p>"Maza ki zauna ki cinye kafin ki ci ubanki...." Ammi ta umarceta, babu musu ra zauna ko hannu Bata wanke ba ta fara cin tuwon, ko kai Bata dagaba har saida ra cinye tas saboda sanin halin ammi, tana kamawa ta daga kai ta kalli ammi dake kallon ta, ahankali ammi ta fara cewa</p><p>"Yanzu dija kin fi son gidan wasu kan gidan mu?... Kinfi son zama da wasu kan zama damu?..." Ta tambayeta cikin natsuwa, dija shuru tayi batace kala ba, ammi ta cigaba dacewa</p><p>"Yanzu kinfison inda zakije a maidaki kaman baiwa?...baki da gatan komai sai yanda akayi dake?... Dija njasan bani da ko sisi amma ban barin wani ko wata ta wulankanta Mani Ku....yanzu tambaya daya nakeson yi maki...kin fison zama dxa wasu kanmu?...." Da Sauri dija ta girgiza mata kai,</p><p>"To wane dalili ne yasa kike kuka don NA hanaki zuwa aikatau?..." Ammi ta sake tambayan ta, tana shessheka ta fara cewa</p><p>"Ammi....Kawai inason mu dinga samu kaman yanda su hase ke samu..." </p><p>"Kinsan halin da take ciki?..." Bata idaba dija ta katseta dacewa</p><p>"Ammi babu halin da take ciki..kalli yanda ta koma ranar da ta dawo...Kuma tace min har boko take zuwa...nidai ammi ki bari in je...in babu dadi zan dawo..." Tafada da gaske, ammi.zama tayi tana kallon ta cike da mamakin yanda take magana babu alaman tsoro, kara fashewa tayi da kuka tana cewa</p><p>"Dan Allah ammi ki bari inje...in da akwai matsala zan dawo...Kuma ni wallahi inason boko..." Ta fada cikin kuka,</p><p> Ammi tsaya kallon ta kawai tayi saida tayi kukan mai isanta Sannan ammi tace</p><p>"Amma kinsan cewa ba ni kadai ke da iko da Ku ba ko?.... Dukda yan uwan ubanku basu damu da Ku ba nasan da zaran wani abu ya faru zasu samu bakin magana..." Da Sauri dija tace</p><p>"Ai duk suna birni...kawu nanu Kawai ne nan...ammi muje mu fada mashi...." Ta fada har jikinta NA rawa, </p><p>"Badai yanzu kike nufi bako?..." Ammi ta tambayeta, sadda kanta kasa tayi Sannan tace</p><p>"yanzu.." Tafada tana murmushi,</p><p>"Jaira... Babu inda zamu yanzu ..saidai gobe..in bai yarda ba sai ki hakura..." Inji ammi, </p><p>"Nasan zai yarda...ai ba damuwa yayi da rayuwata ba...." Tafada cikin jindadi, hararanta ammi tayi Sannan tace</p><p>"Je kiyi salla...nasan rabonki da salla tun NA zuhr..." Bata idaba dija tace</p><p>"Ai har yanzu ban gama ba..."</p><p>"Amma kaman kinyi salla da zuhr</p><p>" aa NA duba naga har lokacin bai tsaya ba balle inyi wanka..."$ ta amsa mata kaman ba ita bace ke kwance kasa tana kuka kaman wata yar karama yarinya. </p><p>"Je ki kara dubawa..." ammi ta fada mata, da Sauri ta mike ta fita.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yazid NA zaune kan gado babu kaya jikinshi kafafunshi cikin blanket waya ne hannun shi yana magana kaman mai jin bacci idanuwanshi lumshe, </p><p>"Baby I can't wait..." Ya fada cikin whisper, daga Chan bangaren mufi dake kwance sanye da kayan bacci ta danyi Dariya tare dacewa</p><p>"Can't wait for what?.." Ta tambayeshi, shima murmushi yayi yana kallon erection dinshi yace</p><p>"Nothing.. Kawai am eager to be with you.... Gani nake kaman 24 days din nan tamkar 24 months or year..." Idanuwa itama mufi ta lumshe saboda maganar shi ke yawo straight into her system, mika tayi Sannan tace</p><p>"Nikam kaman gobe nake ganin 24 days..." Yazid Dan kwantawa yayi yana cewa</p><p>"Don baki damu dani kaman yanda NA damu da ke ba...amma ni I feel rike in tariyo time din..." </p><p>"Don't worry... Kaman gobe ne..." Ta fada mashi cikin sanyin murya, </p><p>"Hmmm alright... I have been patient for a while.. So 24 days won't matter..." Ya fada ahankali, </p><p>"That's my love... Shiyasa nake kara sonka....$" Dariya yayi</p><p>"Da gaske? Tell me why..." Yafada cikin whisper, </p><p>"Cos you are gentle..." Dariyan kasan makoshi yayi</p><p>"Hmmm baby am not that gentle... I don't want to disappoint you... On our first night..." Ya fada kasa2 yanda ki NA kusa dashi bazaiji abinda yake cewa, kuka karya mufi ta farayi tana cewa</p><p>"Ka bar fadan hakan...kana tadamin hankali..." Dariya yayi</p><p>"Name...Kawai am telling you kar ki daukine gentle don I might be bad ass..."</p><p>"I know you are not..." </p><p>"To shikenan...I will try to be gentle as I look..." Yayi assuring dinta, hira suka cigaba dayi for sometime Sannan sukayi sallama, Ahankali ya ajiye wayan, ana kallon joystick dinshi, tunani yake wai haka maza ke ji in suna magana da mata ko matsala gareshi din mostly in har zasuyi waya yana jin muryanta cikin kunnenshi sai ya samu erection, shidai gurinshi yayi aure ko ya huta da wannan matsalan.</p><p>Ahankali ya mike ya shiga bathroom ya sakar wa kanshi ruwa Sannan ya dawo ya shiga blanket ya rufe kanshi from head to toe.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>The following day tun da wuri dija ta addabi ammi suka kama hanyan gidan kanin marigayin babanta wato kawo nanu</p><p> Sallama sukayi ita da ammi suka shiga ba tare da an wani amsa masu ba don ana ganin kaman roko ya kawo su kaman yanda suke zuwa wasu lokuttan in abubuwa suka kakare masu, mutumin dake zaune yana wanke bakinshi da asuwaki ya kallesu</p><p>"lafiya tun dugudugu?..." Mutumin ya tambayesu, dija data nufi wurin shi tace</p><p>"lafiya lau...INA kwana..." Ta gaidashi tana durkusawa,</p><p>"Lafiya..." Ya amsa mata atakaice, ita ammi dakunan Matan gidan ta shiga tana gaidasu suna amsa mata atakaice wata ma Bata amsa ba Sannan ta nufi inda dija ke tsaye gefen kawunta, itama durkusawa tayi ta gaida nanu dake yi mata kallon wulakanci Kuma ba komai ya haddasa hakan ba illa yaso ya aureta bayan mutuwan babansu dija amma taki sai ya tsaneta </p><p>"Lafiya...wai me akayi ne?.." Ya tambayeta yana goge hakoranshi, ahankali ammi ta fara fadamashi abinda ke tafe dasu, sai da ta kai karshe Sannan ya kalli dija dake tsaye tana sauraron su</p><p>"Ke haka ne?..." Ya tambayeta</p><p>"Eh kawu..." Ta amsa mashi cikin sanyin murya</p><p>"To shikenan.. Allah ya bada saa..." Ya fadawa dija don ko kadan bayason magana da ammi,</p><p>"Yauwa kawu Ameen...mun gode.,.." Ta fada cikin murna sosai Wanda ko kadan Bata Iya boyewa,</p><p>"Ammi mu tafi..." Ta fada tana barin wurin da Sauri, itama ammi ta bi bayanta tana tafiya ahankali kawu nanu ya bi bayanta da kallo yana cewa</p><p>"Ga mace har mace amma ta bar dukiyanta suna wulakanta babu mai kula dasu...yanzu da ina nan ina morewa amma ta yi min bakin ciki..." Ya fada tare da Jan tsoki, ammi fita tayi Bata kar bin ta kan Matan gidan ba don su har yanzu kishi sukeji suna ganin kaman tana iya amincewa mijin su ya aureta don ta fisu komai da komai,</p><p> Dija NA tsaye waje tana jiran fitowan ammi tana fitowa dija tayi saurin cewa.</p><p>"Ammi ki bani kudin abun hawa in tafi daura in fada mata kun amince..." Hararanta ammi tayi ta wuceta Bata tanka mata ba, har suka kai.gida dija Bata bar fada mata ta Bata kudi ta tafi daura ba, saida ammi taga zata sha mata kai Sannan ta fada mata Hajiya Aisha zata dawo anjuma, sai lokacin dija ta sake ta fita ta fara gayawa kawayenta zata birni, da sun tambayeta katsina zata? Sai tace</p><p>"Kambu ni na wuce katsina.. Kano zani..." Duk saida tabi kusan dukkan gidajen kauyen su ta fada masu zata birni</p><p> Ammi kam tunanin yanda dija Bata damu dasu ba Kawai take don ko kadan ta nuna bazatyi missing dinsu ba, sai kuma ta tuna da yarinta ke damunta. Dija wanke faded clothes dinta tayi ta shanya su ko abinci bataci ba, ammi kallonta tayi </p><p>"Ke baki ma tunanin halin da zamu shiga in kin tafi...kinsan bamu da komai gidan nan..Kuma da tallan nan muke ci, gashi zaki tafi..." Dija Dan Bata rai tayi Sannan tace</p><p>"ammi ki bawa binto ta saida mana..." Hararanta ammi tayi</p><p>"Amma baki da hankali... Wannan yarinyan zan bawa tallan fura?..." </p><p>"Yo ammi ni ai ban kai ta ba NA fara tallan awara..to ki yi mata awara ta dinga kaiwa tasha...." Ta fada in I don't care manner, ji take kaman ta kira Hajiyan ta zo ta dauketa. </p><p>Sai bayan sallan asar Hajiya Aisha tazo, alokacin kam dija har ta fidda ranta zatazo ita Kuma ammi tana ta aduan Allah yasa kar tazo sai gata da sallama ta shiga cikin gidan da gudu dija ta rungume ta tana cewa</p><p>"Sun yarda..sun yarda..." Ta dinga fada tana rike da Matan, itama Hajiyan riketa tayi tana cewa</p><p>"Da gaske?..." Kai akwai dija ke ta daga mata cikin jindadi, Hajiya kam tamkar Tasan halin da suke ciki, kallon ammi dake zaune tana murmushi tana aduan Allah yasa aso yarta tamkar yanda Hajiya Aisha ke son dija. </p><p>"Kisa yara su biyoni..." Ta fada mata tana fita, da Sauri su dija da sauran yan gidan suka bi bayanta, bayan motanta ta bude sai ga shinkafa da mai da magi sai su taliya katon da macaroni. Ihu su dija suka fara Sannan suka fara shigowa da kayan da Sauri ammi ta mike tsaye tana kallon su. Nan ta zube kasa tana godewa Hajiya Aisha.</p><p>Bayan sun zauna ammi take shaida mata sun yarda ta tafi da dija</p><p>"don Allah kisa a kula daita...Dan Allah kisa su dauketa tamkar su suka haifeta..." Inji ammi dake hawaye, kafadarta Hajiya ta dafa Sannan tace</p><p>" ki kwantar da hankalin ki...yaran da na kai gidan aikatau sunfi su ashirin Kuma baa taba samu matsala ba...kullum iyayensu cikin gode min suke saboda yanda rayuwan yaransu ya chanza...don haka ki kwantar da hankalin ki..." Kai ammi ta gyada mata. Sannan suka tashi tafiya dija ta dauko old Ghana most go dinta, Dariya Hajiya tayi tana cewa</p><p>"Ki bude wannan bag din in gani..." Dan dija ta baje kayanta, banda Dariya babu abinda Hajiya takeyi, </p><p>"Kawai ki bar wayan nan..in munje daura sai in Dan samo maki.kaya kafin in kaiki..." Tsalle Kawai tayi ta fita ta tsaya jikin motan tana kallon yan kauyen su da suka taru jikin motan suna kallon ta, Hajiya fitowa tayi ta bude motan dija ta shiga Sannan suka tafi.</p><p>[3:14PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 鉂ゐ煉氿煉滒煐ゐ煉欚煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挏馃挋馃挍馃枻馃挌鉂�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat(ummu Maryam</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>6鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dija ko kallon mutanen batayiba balle ta daga masu hannu kaman yanda suke daga mata hannu, ammi dake kuka Kawai take kallo tana tausaya mata amma in ta tuna yanzu basu da matsalan abinci sai ta samu nutsuwa, har suka iso cikin garin daura Bata ce uffan ba, Hajiya kallon ta tayi taga yanda tayi sanyi farat daya ta saki murmushi tare dacewa</p><p>"Lafiya dai ko?..." Ta tambayeta cikin muryan dake kwantar da hankalin mai sauraro, dija daga idanuwa tayi ta kalleta</p><p>"Babu komai..." Ta fada muryan ta NA rawa, tunanin yanda komai zai kasance Kawai take, tunda take Bata taba kwana wani wajen ba sai in sun je kauyen ammi.dake bauchi shima tare suke zuwa Kuma su dawo tare, Kawai sai taji Kuma batason tafiyan. Ana kiran magrib suka shiga gidan Hajiya tayi parking motanta suka fito daidai lokacin da wasu yanmata biyu suka fito daga falonta, daya babba ce sai daya kaman dija, dukkan su sanye da kaya ta alfarma, dija kallon su tayi ta fara tunanin ya akayi ita bata tura yaranta aikatau ba sai ta tuna Ashe su masu kudi ne Kuma ita talakace, gaidasu tayi suka shiga cikin falon. Jikinta sai rawa yake don she feels so out of place, yanmatan sai kallon ta kawai suke, Hajiya zama tayi ta dauki wayanta ta kira number yayan Hajiya karama ta shaida mata ta samu yar aikin da suke bukata Kuma ta fada mata zata shigo mata daita gobe.</p><p>"To shikenan.. Allah ya kaimu.." Inji yayar Hajiya karama. Sallama sukayi Sannan Hajiya Aisha ta kalli yarta dake zaune kusa daita tana kallon dija </p><p>"BaBy zaki aramin kayanki biyu...zuba uku..." Yarinya Bata rai tayi</p><p>"Mom me zakiyi da kayana Kuma?..." </p><p>"Zan Bata ne....I promise zan saya maki replacement..." Sai alokacin yarinya ta saki fuskarta, kallon dija data sadda kai kasa tayi Sannan ta kwalawa nata mai aikin kira, nan wata babban budurwa ta fito, dija kallon ta tayi </p><p>"Tabdin...wallahi bai kaiwa kaman wannan, ina yar aiki..." Ta fada cikin ranta, y</p><p>Mai aikin durkusawa tayi ta gaida Hajiya ta amsa Sannan Hajiya tace</p><p>"Ki kaita dakinki..ki Bata abinci taci ta koshi Sannan Dan Allah ki duba kanta in yana bukanta gyara ki wanke mata kisata ta wanke bakinta ta wanke koina NA jikinta zan kawo kaya yanzu....." Hajiya ta fadawa mai aikinta, </p><p>"To ..." Kawai yarinya tace Sannan tayiwa dija alaman tazo, da Sauri ta mike ta nufi wajen yarinyan sukayi dakinta, dija bude bakinta tayi tana kallon dakin mai aikin, </p><p>"Kam Allah kasa nima a bani kaman quartan wannan dakin Dana haye..." Ta fada cikin ranta. </p><p>"Ki zauna..." Yarinyan ta fada mata tare da nuna mata katifan dake kasa, da Sauri dija ta zauna ita Kuma ta fita daga dakin, few minutes later ta dawo da jelof din taliya dayasha kayan miya, </p><p>"Wow dadi...Allah yasa inda zaa kaini su dinga cin irin wannan..." Ta saki fada cikin ranta tana aman abun daga hannun ta, nan dija ta apkawa abincin ta cinye tas ta tside kwano Sannan ta ajiye, yarinyan dauke kwanon tayi ta kai kitchen Sannan ta dawo,</p><p>"Bude kanki in gani..." Yarinyan ta fadawa dija, da Sauri dija ta bude kanta, kitson kanta yafi wata daya dayi Sannan kanta dilindilin, </p><p>"Kambu..da akwai aiki..." Inji mai aikin Hajiya Aisha,</p><p>Da Sauri ta fita daga dakin ta fadawa Hajiya Aisha status din kan dija, </p><p>"Kina da sauran relaxer?..." Hajiya ta tambayeta, </p><p>"Eh ..." </p><p>"To ki shafa mata kan..don gaskiya bazan kaita a haka ba tunda manyan mutane ne..." Ta fada, nan mai aikin ta koma ta bawa dija tsinke ta shigar daita bathroom dinta </p><p>"Ki tsaya nan ki kwance kanki..in kin gama kiyi min magana..." Ta fada mata Sannan ta fita ta barta nan tsaye, dija kam tsaya kallon bathroom din tayi tana gani ya ninka dakin su kyau sau goma, dukda babu wasu kayan wanka cikin bathroom din amma tiles din wurin Kawai ya isheta kallo, da Sauri ta kwance kanta dake gari bisa jikinta daman Zane ne guda six amma ki tsaganta baka ganin saboda tsufa. Lekawa tayi ta kalli mai aikin</p><p>"NA gama..." Ta fada mata, budurwa mikewa tayi ta dauki sauran relaxer ta shiga bathroom din, nan ta umarceta data durkusa Sannan ta fara shafa mata, tana shafa wa tana mamakin irin gashin dija, don Bata San dunkule yake ba saida ta fara shafa man, tafi minti talatin tana shafa mata, </p><p>"Lallai.. Kina da tsawon gashi..." Ta fada, dija dake neman kuka saboda zafin relaxer tace</p><p>"Yanke min ammi take saboda tsawo..." Ta amsa mata muryan ta na rawa, few minutes da gamawa dija ta fara yarfe hannuwanta tana cewa</p><p>"Ki cireshi haka nan...wallahi zafi nake ji..." Yanda tayi maganan yasa ta Dariya, nan ta wanke mata kai tas taga yanda kanta ke silky saboda baki da tsawo,.</p><p>"Hmm daman mu yan kauye munfi yan birni komai.. Amma wahala bai sa a gane hakan..." Yar aikin Hajiya Aisha ta fada cikin ranta, saida ta gama ta hada mata ruwan wanka mai dumi, dija kam jinta take kaman princess, </p><p>"Ni ake hadawa ruwan wanka mai dumi..." gari su kam duk sanyi sai dai kayi wank da ruwan sanyi din baka samun ruwan.</p><p>"Ki wanke jkinki sau biyar kafin ki fito...kinji?..." Da Sauri dija ta gyada mata kai. Tana fita dija ta cire wet clothes dinta ta fara dirje jikinta kaman mai dilka da sabulu mai kamshi don ita dadin sabulun Kawai take ji, sai adua take Allah yasa da akwai irin wannan hutun inda zaa kaita. Wanke jikinta tayi sosai har in ta saka ruwa jikinta bai zama saboda yanda ta wanke kanta. tsayawa tayi tana kallon kanta kaman yanda ta saba, tafi hour tsaye har saida taji an Dan buga kofan bathroom din Sannan tayi saurin cewa </p><p>" na gama....kayanane suka jike..." Ta fada da karfi,</p><p>"Ki daura wannan tawul ki fito..." Ta fada mata, dija tsaya kalle2 tayi tana mamakin meye tawul, jin shuru yasa mai aikin cewa</p><p>"Wannan farun kyallen zaki daura...." Sai lokacin dija ta gane ta dauko towel ta daura amma sai ta kasa fitowa saboda yanda bai da tsawo, </p><p>"Na daura...." Ta fada, kanta kasa sai gasjinta baje kan shoulder ta, budewa mai aikin tayi ta shigo ta zuba mata makilin a brush ta bata ta nuna mata yanda zatayi dashi.</p><p>Atakaice nan take dija ta fito kal kaman ba itaba, Hajiya ta shigo mata da wata doguwar Riga yarta ta Bata, ita kanta hajiya sai da ta tsaya tana kallon gashin dija don ba karamin mamaki tayi ba.</p><p> Kallon mai aikinta tayi Sannan tace</p><p>"Dan Allah ki Bata shawaran da kike bawa sauran in an kawosu kafin In akaisu gidan aikin su..." Inji Hajiya Aisha,</p><p>"to..." Ta amsa mata, fita Hajiya tayi dija ta zumbula rigan da aka bata, nan mai aikin Hajiya Aisha ta fara cewa</p><p>"Kina jina?..." da Sauri dija ta gyada mata kai, </p><p>"NA farko inda zaa kaiki ba gidan Ku bane...gidan aikinki ne...ki tabbatar kina girmama koda akuyan gidan..." Da Sauri dija ta kalleta, itama kallon ta tayi</p><p>"Eh din...dole ki girmama su...babu ruwan ki da abinda baa saki ba...duk abinda akace kiyi kiyi...in ance ki bari ki Bari...banda kwadayi...banda zuwa inda baa ce kije ba...banda shisshigi...banda yayata sirrin uwar dakinki ko na wata...babu ruwanki...banda sata..." Again dija kara kallon ta tayi</p><p>"Yo kina mamaki ne?.... To da akwai wata yarinya da Hajiya ta kai saida aka maidota wai tana dauk2....don haka ko kudin su zai dinga yawo kasa babu ruwanki don wani lokacin gwadaki suke...kar kiga babu mai kallonki kiyi abinda baace kiyiba...kiji tsoron Allah a duk inda kike...Kuma kar zaman birni yayi maki dadi ki mance inda kika fito...kinji ko?..." Da Sauri dija ta daga mata kai,</p><p>"Sannan babu mai son yar aiki kazama...kiyi wankan ki kafin ki fara aikin gida....don haka ki tabbatar kina mikewa da wuri...ki kula da kanki...Kuma in kina da wata matsala ki fadawa uwar dakinki... Mussanman irin matsalan mu na mata...da fatan kinji abinda nake fada maki...." Da Sauri dija ta kara daga mata kai</p><p>"Ke ki bar daga kai.kaman wata kadangaruwa...ki dinga amsawa..."</p><p>"To ..." Dija ta fada, wasu advice ta Kara Bata sosai kan yanda zata zauna da su batare data samu wata matsala ba, dija taji dadi sosai don sai gata tana cewa</p><p>"Nagode..." Labari suka cigaba dayi har bacci ya dauki yar aikin Hajiya Aisha ita kam dija yanda ta ga rana haka ta ga dare. Tun da asuba mai aikin Aisha ta tashi tayi wanka itama dija tayi wanka ta maida kayan ta bi bayanta suka fara aiki tana nuna mata abubuwan daya kamata mutum yayi, </p><p>"Ai Kwara wannan da dakan fura..." Ta fada cikin ranta,. Kafin bakwai da rabi sun gama komai har mai aikin Aisha ta kusa ida breakfast. Sai karfe takwas Hajiya ta fito ta sha tea da bread su Kuma yaranta sukaci abincin, mai aikinta ta debo abinci ta kai dakinta sukaci da dija Sannan Hajiya Aisha ta kirata ta fito, wata karamar jaka ta bata </p><p>"Gashi da akwai kaya kala uku cikin shi...ki kula dasu kafin su kara maki wasu..." Da Sauri dija ta amsa Sannan suka kama hanyan katsina. Gidan yayar Hajiya karama suka isa, nan ma dija baki ta bude don kyau da girman gidan, matar dake kaman daya da Hajiya karama ta kallesu fuskan ta dauke da murmushi tana cewa</p><p>"Wannan yarinyan tana da kyau.. Ina kika sameta?..." Ta tambayi Hajiya Aisha, Dariya Hajiya Aisha tayi ta labarta mata yanda akayi ta samu dija,</p><p>"To alhamdulillah... Yanzu bari in baki address dinsu dukda gidansu ba boyayye bane a garin Kano..." Nan ta rubuta mata address, ta mika mata, Sannan tace</p><p>"Bari in dauko maki NA mai..." ta fada tana hayewa upstairs, dija dai kanta kasa gabanta ne Kawai ke faduwa saboda tsoro, few minutes later ta sauko da bandir din Dari biyu ta Bata,</p><p>"Wannan ai yayi yawa..." Inji Aisha, Dariya tayi</p><p>"Inafa...ai kinyi kokari...ki gaida manasu dukda muna da biki nan gidan..." </p><p>"Kanwar taki ce zata aurar?.." Kai ta girgiza mata</p><p>"Dan abokiyar zamanta ne zaiyi aure ...." Ta fada mata</p><p>"To Allah yasa ayi a saa... Bari mu tafi tunda muna da tafiya gaban mu..." Ta fada tana jefa kudin cikin bag dinta tare da mikewa. Nan sukayi sallama Sannan suka kama hanyan Kano</p><p>[3:14PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挋馃挌馃挍馃枻鉂ゐ煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挋馃挌馃挍馃枻馃挏鉂�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat(ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>7鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ko uffan dija batace ba har suka iso garin Kano,Hajiya kallon ta tayi ta fara Bata new advice har suka iso kofar wata katuwar gate, gaban dija kara faduwa yayi ta Dan leko da kanta tana kallon gate din da Hajiya ke horn a bakinta, wani ne ya leko ya kalli motan yaga mace ce da wata yarinya ya koma ciki Sannan ya bude gate din don ba kowa ake bari ya shiga gidan ba saboda tsaro, ahankali Hajiya shiga gidan itama tana mamakin girman gidan, </p><p>"Hmm gaba da gabanta..." Ta fada cikin ranta, ahankali tayi parking motanta a available space dake wurin ta fito tana kalle2, fadin girma da haduwan gidan is a waste of time amma ko motocin gidan Kawai are enough, Manyan gidaje six ke da akwai wurin, hakan yasa Hajiya Aisha ta rasa inda zata shiga, dija kam boyewa tayi bayan Hajiya tana kallon gidan, mai gadi me ya nufota da murmushi fuskan shi, gaidata yayi ta amsa sannan Hajiya tace</p><p>"Dan Allah bangaren Matan gidan zakanuna min..." </p><p>"Wacce daga cikin su?.." Mutumin ya tambayeta</p><p>"Karama matar..." Ta amsa mashi, nuna mata gidan dake middle yayi yace</p><p>"Nan ne..." Ya fada mata Sannan ya kokma duty post dinshi su Hajiya suka nufi inda aka nuna mata, ita kanta Hajiya Tasan tunda take kai yara gidan aiki Bata taba zuwa gidan da yayi Rabin wannan ba wajen girma da kyau, dija kam tafiya take amma tamkar an rike mata kafa, ahankali ta dinga takawa tana kare kanta da Hajiya Aisha dake gabanta, bakin kofan ta Hajiya ta tsaya ta danna wata bell, few minutes later wata budurwa ta bude ta gaidasu, amsawa Hajiya tayi Sannan tace</p><p>"Hajiya tana ciki?..."</p><p>"Eh...Ku shigo..." Yarinyan ta fada masu tana komawa gefe, cikin falon suka shiga sanyin ac ya bugi dija nan take taji kaman tana fever, tafiya ta dingayi a hankali don kar tiles ya kwaceta, Hajiya zama tayi dija ta zauna kasa kanta kasa heartbeat dinta NA kara highing by the minutes, Hajiya kam baki ta bude tana kallon ikon Allah tana mamakin yanda aka tara abun duniya waje daya, budurwan data bude kofan ce ta kawo drink da wasu elegant cups biyu ta ajiye Sannan tace</p><p>"Bari in kirawo ta...." Ta fada tana barin wurin, Hajiya kallon dija tayi </p><p>"Dija kinyi saa... Ban taba kai yarinya irin wannan gidan ba...sai kiyi ladabi ki bi doka ki ci arziki...." Ta fada mata kasa2 tana tsoron kar CCTV ya dauki maganar ta don tasan baa rasa sawa cikin irin wannan gidan. Bayan minti kaman biyar Yarinyan ta dawo tace</p><p>"Gatanan zuwa..." Ta fada masu Sannan ta bar falon. Sunfi minti goma shabiyar zaune Sannan Hajiya karama ta fito da faraa fuskan ta, gaisawa sukayi Sannan Hajiya karama tace</p><p>"Kece Hajiya Aisha?.." Ta tambaya</p><p>"Eh nice...Kuma wannan itace Yarinyan da kikace a samo maki...." Ta fada tana nuna dija dake lankwashe kasa, sai lokacin dija ta gaidata muryanta na rawa</p><p> Hajiya karama kura mata ido tayi tana kallon ta Kuma tana mamakin kyauwunta, </p><p>"Lafiya lau..Wallahi I thought she's your daughter... Ah ina kika samo wannan beauty..." Tafada cikin raha kaman sun Dade da sanin juna da Hajiya Aisha, Dariya kawai tayi , Hajiya karama kallon yanda dija ke nonnokewa Kawai tayi ta saki Dariya</p><p>"Ya sunanki?..." Ta tambayi dija</p><p>"Kha...fi...ja..." Ta fada kanta kasa don ko sau daya Bata daga kai ba, </p><p>"Ah...ah...ah....sunan hajiyar mu gareki Ashe...kice NA samu sabuwar uwa...." Tafada cikin Dariya, itama Hajiya Aisha Dariya tayi hankalin ta kwance da Hajiya karama Bata nuna batason dija ba, </p><p>"Asabe!... " ta kwala kira, sai ga yarinya data bude masu kofa ta dawo ta durkusa gaban Hajiya karama, </p><p>"Ga sabuwar mai taimaka maki an kawo...ki.tafi da ita dakinki..." Ta umarceta, Dariya jin dadi budurwa da bazata wuce shekara sha takwas ba tayi tana nuna jin dadinta karara da samun mai rage mata aiki, </p><p>"Taso..." Ta fadawa dija, ahankali dija ta mike jikinta na rawa, sai lokacin ta daga kai ta kalli Hajiya Aisha Kawai sai ta fara hawaye, don Kawai sai taji gidansu take so, </p><p>"Ah...ki bar kuka...nan ma gidanku ne kinji?.." Hajiya karama ta fadawa dija, da Sauri dija ta hadiye kukan ta fara takawa ahankali tana bin bayan asabe, Hajiya karama kallon ta kawai take don kallon yar gidan manya kawai take mata don ko kadan Bata kama da yar talakawa, saida suka bar falon Hajiya karama ta kalli Hajiya Aisha</p><p>"Amma wannan yarinyan zata Iya aiki kuwa?... Naga she's a little bit dull..." Dariya Hajiya Aisha tayi Sannan tace</p><p>"Sosai kam Hajiya...Kawai yanzu kunya take ji..amma ina tabbatar maki.babu abinda bazata iyaba..." </p><p>"To shikenan.. Nawa ake biyan yaran da kike kaiwa gidan aiki?..." Hajiya karama ta tambaya, murmushi Hajiya Aisha tayi tace</p><p>"Ai duk yanda kika bada daidai ne..." </p><p>"To shikenan...masu aikin mu dubu talatin ake basu duk wata ga baki dayansu don haka zaa din biyanta...." Wani irin dadi Hajiya Aisha taji don tunda take kai yara gidan aiki babu inda ake biyan dubu ashirin balle talatin</p><p>"To shikenan... Hakan yayi sosai...." Inji Hajiya Aisha,</p><p>"To sai ki bada account number in bada a bawa manager kar a manta da albashinta..." Da Sauri Hajiya Aisha ta dauko Biro da paper ta rubuta ta mikawa Hajiya karama Sannan tace</p><p>"Ina yaran ne?.." Ta tambayeta</p><p>"Suna chan bangaren babban mominsu....bari in sa a hada maki wani abu naci...." Inji Hajiya karama,</p><p>"Na gode kwarai... Tafiya zanyi don inason in shiga kasuwa kafin in koma katsina...." </p><p>"Haba da wuri haka?... Haba ki bari sau gobe mana..." Injin Hajiya karama,</p><p>" sai in NA sake dawowa in Allah ya yarda..." Ta fada tana mikewa,</p><p>"Ina zuwa..." Hajiya karama ta fada mata Sannan ta bar falon bayan yan mintuna goma tadawo da wata katuwar Leda dauke da manyan atampa guda uku sai perfumes, sai kudi cikin envelope </p><p>"Gashi a rabAwa yan gida..." Hajiya karama ta fada tana mika mata ledan</p><p> "Har da wata hidima?... Gaskiya NA gode...Allah ya aka da alkhairi... Allah ya kara girma...nagode kwarai..." Ta fada cikin jindadi, </p><p>"Babu komai... Bari muje in kaiki gurin uwargidata Ku gaisa kafin ki wuce..." Hajiya karama ta fada tana shige mata gaba, bayanta Hajiya Aisha tabi har falon da yaran gidan ke wasa ita Kuma Hajiya babba zaune kan kujerana alfarma tana kallo zee aflam, da sallama suka shiga Hajiya karama ta shaidamata an kawo mai aikin. NaN suna gaisa Sannan Hajiya Aisha ta tafi bayan itama Hajiya babba ta Bata atampa da turare. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dija baki ta bude tana tafiya ahankali tana waige2 har asabe ta bude dakinta suka shiga, dija tsayawa tayi tana kallon ikon rabbi don dakinta katuwa ne Sannan ga katon gadon da ko amaryan garinsu Bata isa ta mallakesu ba, </p><p>"Ki zauna mana..." Asabe ta fada mata amma dija bataji ba saboda yanda take kallon ceiling din dakin, kallon katon madubin dake jikin bango tayi ta tsaya tana kallon kanta, sai yanzu ta gan kanta sosai yanda take so, kallon kayan shafan dake kan mirror tayi ta dauke kanta ta kalli wata katuwar bag dake dakin</p><p>"Ki zauna mana.." Asabe ta fada tana Dariya,sai lokacin dija ra dawo hayyacinta ta kalli asabe dake dariya, sauke kanta kasa tayi tana murmushi,</p><p>"Ya sunanki?..." Ta tambayeta sounding friendly.</p><p>"Di...ja...." Ta amsa mata, </p><p>"Ni sunana asabe...sannunki da zuwa yaruwa...daga wane gari kike?..." Ta tambayeta, </p><p>"Baude...." Dariya asabe tayi </p><p>"Inane Baude?...." Dija dai shuru tayi don batasan abinda zata fada mata ba</p><p>"Ni yar dala ce...shekaranki nawa?..." Asabe ta sake tambayanta, shuru dija tayi kaman mai tunani Sannan tace</p><p>"Sha uku ko hudu..." Idanauwa asabe ta zaro </p><p>"Shine kike da tsawo haka?...wallahi nayi tunanin shekarunmu daya...Ashe ke yarinya ce...bari in dauko maki abinci...." Ta fada Sannan ta mike, fita tayi daga dakin dija ta kara mikewa ta nufi wajen split air conditioner, sai kallon abun take hannun ta ta kai wajen taji wani irin sanyi NA ratsa hannun ta, da Sauri ta dauke hannun ta takoma ta zauna har lokacin bata bar kalle2 ba. Rice and stew cike da kifi asabe ta shigo dashi ta ajiyewa dija sai ta bude Dan karamin fridge dake dakin ta dauko ruwa ta ajiye mata</p><p>"Bisimillah...." Asabe ta fada mata, da Sauri dija ta sauko kasa ta zauna ta fara cin abincin tana kara godewa Allah, daman dija Bata wasa da cikinta sai gata ta cinye abincin tas Sannan ta sha ruwa, asabe sai kallon ta tana murmushi don haka nan taji tana son dija. Sai da dija ta gama cin abincin Sannan asabe ta fara fada mata ayyukan da zasu dinga yi, itadai dija sauraron ta kawai take tana lumshe idanuwa saboda sanyin dake ratsata daman batayi bacci ba jiya</p><p> "Ko zakiyi bacci ne?.." asabe ta tambayeta da Sauri ta girgiza mata kai, Dariya asabe tayi </p><p>"In zakiyi bacci ki kwanta kafin..." Bata idaba wayanta ya fara ringing da Sauri tayi picking, shuru tayi tana sauraron abinda Hajiya karama ke fada mata</p><p>"To..." Ta amsa Sannan ta ajiye wayan ta kalli dija,</p><p>"Hajiya ta ce in kawoki bangaren Hajiya babba,..." Ta fada mata, da Sauri dija ta mike itama asabe ta mike suka fito zuwa part din Hajiya babba, sallama sukayi suka shiga kan dija kasa hannun ta rike da junansu duk yan yaran dake wasa Tare da yanmatan dake kallo kura mata ido sukayi. Durkusawa tayi ta gaidasu har da yanmatan, kallon juna sukayi suka tuntsure da Dariya suna kallonta with adorations, itama Hajiya Dariya take, rarrafawa tayi wajensu Hajiya ta kara gaidasu suka amsa suna Dariya</p><p>"Amma wannan yarinyan da abun Dariya take..." Inji Hajiya babba dake dariya, har lokacin dija na nan durkushe kasa itama asabe Dariya take, marzuq da Ameera ne suka ce</p><p>"Small mom wannan mai aikice?..." Ihsan ce ta buge masu baki, sukayi shuru don yana daga cikin tarbiyan yaran gidan basu raina maaikatansu, </p><p>"Ku koma..." Hajiya karama ta fada masu, sai lokacin dija ta mike suka koma part din Hajiya karama marzuq da Ameera NA biye dasu suna kallon dija kaman madubi don duk a masu aikin gidansu babu mai kyauwun ta, kitchen suka shiga tare dija ta bude baki, su Ameera NA biye dasu har cikin kitchen sai cewa tayi</p><p>"Tea zan sha...." Inji Ameera,Dariya asabe tayi tana cewa</p><p>"Sarauniyar shan tea..." Ta fadawa Ameera dake yar shekara 8 amma tana abu kaman yar shekara uku saboda sangarta, cup asabe ta dauko zata hada mata tea sai cewa tayi</p><p>"Bake zaki hadamin ba...ki bari ita ta hada min..." Ta fada tana nuna dija, </p><p>"To kinji da ke take..." Asabe ta fadawa dija, Dan matsawa dija tayi kusa da asabe Sannan tace</p><p>"Meye hakan?..." Ta fada cikin whisper, cup asabe ta mika mata, ta kaita ta zuba ruwa Sannan ta bude mata katon tin NA milk da Ovaltine, ta dauki spoon ta mikawa dija Sannan ta umarceta data hadasu cikin cup, yaran sai kallon su suke suna Dariya tana gamawa ta mikawa Ameera ta amsa Sannan suka bar kitchen din.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hajiya Aisha NA fita ta duba envelope din da Hajiya karama ta Bata taga mint na Dari biyar, dadi taji tana cewa</p><p>"This is what am taking about..." Tafada cikin jindadi. Kasuwa ta shiga tayi sayayya tare da siyan wasu atampa yan 3k guda uku don ta kaiwa ammi</p><p>[3:15PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挏鉂ゐ煉氿煐ゐ煉涴煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挍馃挋馃挌馃枻馃挏鉂�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat( ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>8鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Daga kitchen dinning area asabe ta kai ta Sannan dakin daukan baki sai dakin su Ameera don dakinta Kawai take gyarawa sauran yaran suke gyara wurin su da Kansu, </p><p>"Ba wani aiki ke da akwai da yawa ba...Kawai dai baa sin gani kazanta ko kadan ..." Asabe ta fada mata suna komawa dakinsu, dija dai sauraron ta kawai take don gurin ta dare yayi ta kwanta,</p><p>"Kiyi wanka mana kafin lokacin sallan magrib.. Bamu da girki yau don haka babu aikin da zamuyi saidai in Hajiya ta bukaci muyi mata wani abu..." Inji asabe, </p><p>"Ina zanyi wankan?..." Dija ra tambayi asabe cikin sanyin murya. Mikewa asabe tayi ta bude kofan dake cikin dakin tace</p><p>"Taso ki shiga...." Ta fada mata, ahankali dija ta mike ta shiga bathroom din tana kallon ikon Allah don babu abinda ta Iya amfani dashi a wurin tsaya kallon bathroom din, asabe jawo kofan ta farayi dija tayi Sauri rikewa </p><p>"Ban...Iya...ba..." Tafada muryan ta na rawa. Dariya asabe tayi Sannan ta shiga cikin bathroom din ta fara nuna mata amfanin shower da heater tare da bathtub, dija kura mata ido tayi Bata ko kaftawa har asabe ta gama Sannan tace</p><p>"Yanzu ki nuna min abubuwa dana koya maki..." Fada mata, nan itama dija ta fada exactly abubuwan da ta fada mata, mamaki ne ya kama asabe cos she explained everything perfectly. Nan asabe ta fita ta barta tayi wankan sai lumshe idanuwa take saboda yanda take jin dadin kamshin sabulun wankan. Atakaice cikin kwana uku dija ta gane kan bangaren Hajiya karama, har da sunayen yan gidan gaba daya kaman yanda asabe ta fada mata Kuma ba karamin dadi take ji gidan ba don within that three days ta chanza cos ko fita batayi Kuma gashi da sun gama aiki kwanciya suke suyi bacci, yanzu kam dija ta bar tsayawa bathroom ta kalli kanta sai dai a gaban mirror dake dakin su amma sai in asabe Bata dakin sai ta tsaya ta kunshe towel dinta ta kalli jikinta da kanta tana kashewa kanta ido tana Dariya , yauma tana tsaye gaban katon mirror tana kallon kanta asabe ta shigo da plate din abinci, da Sauri dija ta gyara towel din tana kallon asabe, itama asabe kallon mamaki tayi mata, </p><p>"Me kikeyi haka?..." Asabe ta tambayeta cikin surprise, da Sauri dija tace</p><p>"Babu komai..." </p><p>"Kaman ya babu komai..." </p><p>"Aa... Kawai wanka NA fito....shine nake shafa mai...." Tafada ahankali, asabe dai Bata kara cewa komai ba ra ajiye abincin suka fara ci,.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yazed ne kwance yana bacci, alarm ne ya tadashi ya mike da Sauri tare da godiya ga Allah ya shiga bathroom yayi wanka Sannan ya fito daure da alwallah. Kaya ya saka yayi salla nan cikin dakin Sannan ya cire jallabiya dake jikinshi ya shirya cikin suit ya fashe kanshi da perfumes ya fito looking handsome than ever, kallon agogon hannun shi yayi yaga 6:15am </p><p>"I still have some time..." Yafadawa kanshi tare da fiddo wayanshi daga cikin aljihunshi, number Hajiya yayi dailing suka fara hira </p><p>"Son ka dawo haka nan mana...wai nan da abuja kake wannan abun kaman Wanda ke abroad?..." Dariya yayi</p><p>"Ai mom wahalan tuki nakeji...Kuma sauran sati daya hutuna..." </p><p>"To shikenan... An turo maka pic din gidan ?..." </p><p>"Yes mommy... It's beautiful... Amma nan abuja zaa kawota....".</p><p> Yafada yana naughty laugh</p><p>"Kaci gidanku...nan Kano zaa ajiyeta..." Turo baki yayi kaman yana gaban ta Sannan yace</p><p>"Mom NA....aikin fa?..."</p><p>"Ka dinga zuwa every weekend..." Idanuwa ya zaro, yayi shuru Kawai baice komai ba don kar Hajiya tace yana mata rashin kunya, haka suka gama hiran ya fita daga quarters din zuwa office.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau Hajiya Aisha ta koma gidansu dija din kai mata kayan data sayo mata, da sallama ta shiga cikin gidan, da Sauri ammi dake zaune ta rafka ban tagumi ta mike</p><p>"Ah..ah..Sannu da zuwa..." Inji ammi Tafada cikin murmushin karfin hali, </p><p>"Yauwa..." Sannan suka fara gaisawa, ledan Hajiya ta mikawa ammi</p><p>"Gashi inji uwar dakinki dija...." Ahankali ammi ta bude ledan Bata wani yi murna kan kayan ba,</p><p>"Ya dija take... Ina Iya zuwa ganinta?.." Ammi ta fada har jikinta NA rawa, murmushi Hajiya Aisha tayi</p><p>"Ki kwantar da hankalin ki..diyarki tana gidan Hutu...Kuma albashinta dubu ashirin..." Da Sauri ammi ta kalleta, </p><p>"Wane irin aikine zatayi da zaa Bata dubu ashirin cikin kwana talatin?.." Ammi ta fada cike da mamaki.</p><p>"Ai NA fada maki yarki tana gidan manyan mutane... Yanzu karshen watan nan zan sayo maki waya sai ki dinga waya da yarki..." Inji Hajiya Aisha, dadi ammi taji har cikin ranta.</p><p><br /></p><p> _A week later_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau yazid zai dawo sai shirya kayan dadi ake kala2 kaman sarki zaizo gidan mussanman Hajiya karama duk wata in yazid zai zo gida weekend haka zata dinga hidima ko kadan Bata gajiya don tana ji dashi tamkar ita ta haifeshi shima bai wasa daita. </p><p><br /></p><p>Dija NA tsaye gefen asabe dake yankawa mai dafa abinci cabbage cos ba su ke dafa abinci ba, </p><p>"Wai me akeyi naga anata dafa abinci kala2?.." Dija ta tambayi asabe cikin kunnenta, </p><p>"Babban Dan gidan ne zaizo..." Ta amsa mata, kai Kawai dija ta karkata, haka suka yi aiki har suka gaba aka cika dinning da abinci dija kam sai mamakin yawan kayan take don gani take ko mutane goma abincin yayi masu yawa</p><p>"Kilan ci gareshi..." Ta fada cikin ranta. Sai wajen 12 suka gama komai suka koma dakinsu. Kwanciya tayi tana tunanin ammi da kannenta don she missing them beyond words, da tana tunanin it won't matter amma she's so wrong she miss them so much, at times in suna cin abinci da asabe sai tace</p><p>"Inama su ammi suna nan..." Take fada cikin ranta. </p><p><br /></p><p>Around two yazid ya shigo gidan cikin wata beautiful and expensive car, da gudu yaran gidan sukaje bakin gate, shima da Sauri ya fito ko parking baiyiba ya dauki Ameera hannun daya ya dauki marzuq da hannun daya, nishi ya farayi</p><p>"Wai ...me kukeci....duk kunyi adding weight..." Tafada yana nishi kaman Wanda ya dauki buhun cement. Sauke su yayi suna Dariya, hannun shi cikin nasu suka shiga part din Hajiya babba</p><p> Da gudu mimata da Zainab dake zaune falo suka nufoshi, bude masu hannuwanshi yayi yana murmushi, rungume su yayi</p><p>"Nayi missing dinku...." Ta fada masu</p><p>"Yaya bakayi missing dinmu ba...jiya dakayi waya da big mommy baka nememu ba..." Inji Zainab dake turo baki, Dariya yayi Wanda ya kara bayyana handsomeness dinshi </p><p>"To in ni ban nemeku ba Ku bazaku kirani ba?..."</p><p>"Ai bamu dakudi..." Inji mimata, kai ya girgiza yana cewa.</p><p>"Baku da kudi amma kullum kuna online..." Yafada tare da kama hanyan mini falon dake wurin, nan ya hangi Hajiya babba da Hajiya karama zaune fuskan su dauke da murmushi, da Sauri ya karasa wurin su ya durkusa Sannan ya gaida su, </p><p>"Ji yanda ka wani koma...duk ka rame saboda rashin abincin kwarai..." Inji Hajiya karama, Dariya Kawai yayi Hajiya babba kam murmushi Kawai take tana kallon danta cikin so da kauna</p><p>"Ai gani yanzu sai ki bani mai dadi inci in yi adding weight kafin in koma...." Hararanshi Hajiya karama tayi tana cewa</p><p>"Kana zuwa kana maganar komawa...." Tafada kaman tana fushi, zama yayi kan hannun kujeran da take ya rungumota, </p><p>"Da wasa nake mommy...." Yafada yana manna mata kiss a cheek dinta, mikewa Hajiya karama tayi ta kama mashi hannu,</p><p>"Muje kaci abinci..." Tafada tana janshi, Dariya yayi yabi bayanta don in da sabo ya saba, </p><p>"Yaya ina sarabanmu?..." Marzuq ya tambayeshi,</p><p>"Ban sayo komai ba..Ku bari da yamma sai in kaiku eleganza,..." Tsalle yaran suka fara, suka fita Hajiya karama NA rike dashi kaman wani karamin yaro, gate aka bude motan shahid ya shigo, tun daga nesa ya hangi yazid da Hajiya karama, Dan karamin tsoki yaja yana cewa</p><p>"The fun killer is back..." Yafadawa kanshi yana parking motanshi, Fitowa yayi ya nufosu sanye da three quarters dake low waist a kugunshi, yazid tsayawa yayi yana kallon shi</p><p>"Yaya sannu da zuwa..." Ya fada mashi kanshi kasa, yazid bai amsa ba ya tsaya kallon dressing dinshi, </p><p>"Ki daga ina kake?..." </p><p>"Daga factory...". Kallon up and down yayi mashi</p><p>" ina Sharif?...." Ya sake tambayan shi, hannun shi Hajiya karama ta kara rikewa</p><p>"Ka rabu dashi ..muje kaci abinci.. Don't waste your precious time on those silly boys...." Ta fada mashi, kai kawai ya girgiza ya bi ta, shi Kuma shahid ya tabe baki ya nufi part dinshi da Sharif yana tafiya irin NA niggas wandonshi sai Neman kwalewa yake. Saida suka isa dinning Sannan ta saki hannun shi, zama yayi yana kallon jerin abincin</p><p>"Small mom ya zanyi da wannan abincin?..." </p><p>"Kaidai kaci Iya cinka ka bar sauran..." Ta fada tana dauko mashi ruwa daga cikin fridge dake wurin, ajiye mashi tayi Sannan ta bar wurin ta koma bangaren Hajiya babba.</p><p><br /></p><p>Yazid zama yayi yana kallon abincin sai yaji ya koshi don ya rasa abinda zaici Kuma ko kadan baison bata mata rai, Ahankali ya bude warmer daya yacikaro da white rice ya diba kadan Sannan ya bude next warmer ya zuba thick stew dake ciki ya fara ci bayana ya debi dambun nama ya zuba akai, saida yaci ya koshi ya sha ruwa yayi relaxing nan yana waya da mufida. Kawai kaman daga sama sai yaga dija ta bude kofa ta fito asabe NA biye daita, Dan tsaya kallon ta yayi har saida muryan mufida ya dawo dashi hayyacinshi, itama daga idanuwanta tayi ta kalleshi tayi Sauri durkusawa</p><p>"Ina kwana?..." Ta fada da Sauri, sai kuma tace</p><p> "Aa.. Ina yini..." Ta fada muryanta NA rawa, Dariya asabe tayi yazid kam zaro idanuwa tayi yana kallon ta har lokacin waya NA kunnenshi, hade rai yayi ya daga mata hannu, da Sauri ta mike ta koma ciki, itama asabe gaidashi tayi itama ya daga mata hannu ya cigaba da wayanshi</p><p> Saida ya gama ya zauna nan yana tunanin wacece wacce ta fito daga dakin masu aiki, zama yayi nan ko zata Kara fitowa. Dija kam da Sauri ta zauna kan gado kanta kasa,</p><p>"Wai ya akayi kika rude?...ko baki taba ganin mutum mai kyauwunshi ba?..." Asabe ta tambayeta, dija dai kasa magana tayi saboda abinda ya makale mata a wuya, </p><p>"Ko kin taba ganin shi?.." Ta sake tambayanta, da Sauri ta girgiza mata kai, </p><p>"Kinyi shuru..." </p><p>"Ba..bu...komai..." Ta amsa mata tana Dan kwantawa, </p><p>"Bazaki sha ruwan ba?... Tunda NA manta ba sa ruwa a fridge ba..." asabe ta fada mata don diban ruwa suje amma ganin yazid yasa ta dawo don wani irin faduwan gaba taji data ganshi Sannan ko daidaida minti daya Bata fatan kara haduwa dashi don yayi mata kwarjini da yawa</p><p>"Anjuma zansha...." Tafada tana kara lafewa kan gadon, </p><p>"Kije ki debo mana...ko so kike in debo maki?..." Da Sauri dija ta girgiza mata kai</p><p>"To ki tashi ki debo ruwan..." tafada tana bude fridge ta dauko roban da take zuba ruwa ciki ta ajiye ta mika mata, ahankali dija ta amsa ta mike tana tafiya ahankali ta nufi kofan ta bude gabanta na faduwa, tana budewa ya kara daga manyan idanunshi suka kara hada ido, da Sauri dija ta kara komawa ciki ta maida kofan ta rufe.</p><p>[3:16PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挋馃挏馃挌馃枻馃挍鉂�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挋馃挏馃挌馃枻馃挍鉂�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat( ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>9鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da Sauri asabe ta mike </p><p>"Lafiya?..." Ta tambayi dija da ta komo ciki kaman ta ga ghost, </p><p>"Ya...na... Nan....nidai tsoron shi nakeji...." Kallon mamaki tayi mata,</p><p>"Tsoro Kuma?... In kina haka kina Iya rasa aikinki...ya zaki dinga haka kaman kinga gawa?...shine fa babban gidan nan...in Hajiya taji tana iya koranki don Bata hadashi da kowa ba...yanzu kije ki debo ruwa kaman babu abinda ya faru kar ya fadawa Hajiya...." Asabe ta fada mata cikin fada, da Sauri tace</p><p>"To...." Tafada tana kara komawa bakin kofan, yazid kam zama yayi yana kallon ikon rabbi, </p><p>"What such of insanity is this?.." Ta tambayi kanshi, mamakin yanda take gwalo dukkan manyan idanuwanta in sun hada ido Kawai yake,</p><p>"Did she know me from somewhere?..." Ya sake tambayan kanshi, jin an kara bude kofan yasa ya kara maida hankalin shi ga kofan, dija ce ta fito wannan Karin Bata daga kai ba, Allah ya taimaketa da akwai distance tsakanin inda yake zaune da inda take, tunawa tayi da ya yana Iya fadawa Hajiya abinda tayi kaman yanda asabe ta fada mata, ahankali ta fara takawa kanta kasa, yazid kam kara balancing yayi yana kallon each and every step dinta yana mamakin yanda take tafiya kaman an somata cikin ruwa, kafanta sai rawa yake, Kawai sai ya tsinci kanshi da kallon waist dinta, dukda tana sanye da doguwar Riga yana ganin hip bone dinta, da Sauri ya kauda kanshi gefe har lokacin bai bar tunanin ina small mom ta samo wannan unique gal ba, dija NA jinta cikin kitchen ta saki ajiyan zuciya tare da dafa saitin heart dinta dake beating a very high rate, saida tayi rike sink din da zata debo ruwa for like ten minutes Sannan ta dawo normal, da Sauri yazid ya mike daya tuna baiyi sallan zuhr ba, barin falon yayi amma to his surprise he found himself turning back to look at the kitchen kafin ya bar falon. Direct ya wuce part dinshi NA gidan Wanda shi kadai ne gurin. Alwallah ya dauro ya fitoyayi salla ya zauna nan kan praying mat. Ko tunanin me yake oho. Yafi minti talatin zaune Sannan ya chanza kayan jikinshi zuwa English wear ya fita. Part din Hajiya babba ya tafi ya samesu nan ya shaida masu zaije factory wajen Abba sukayi mashi adawo lafiya , at that moment Kawai sai yaso ya tambayi Hajiya karama inda ya samo yarinya amma sai ya tuna da halin ta da saurin zargi da Kuma tambaya. Haka ya fita ya shiga motanshi ya nufi daya daga cikin factory din babanshi.</p><p> Dija na Gama deban ruwan ta fito ahankali tana aduan Allah yasa ya bar gurin Kuma luckily Bata tardashi ba, da Sauri ta shiga dakinsu ta maida kofa ta rufe, asabe kallon yanda tayi tsuru2 Kawai take, ajiye ruwan tayi cikin fridge Sannan ta koma ta zauna har ta tagumi,</p><p>"Wai meke damunki?.." Asabe ta tambayeta cikin kulawa, girgiza kai Kawai tayi alaman nothing,</p><p>"Ya zaayi ki ce babu komai alhalin cikin minti daya kika chanza...ki fadamin.. Kinga tamkar yaya nake a wajenki..." Tafada mata ahankali, </p><p>"Ni banason... wannan mutumin..." Ta fada cikin sanyin murya, maganar ta Dariya ya bawa asabe,</p><p>"Me yayi maki.daga ganinshi zakice bakison shi?..." Da Sauri dija tace</p><p>"Babu komai... Nidai...banason shi..." Tafada muryan ta na rawa, rike kunne asabe tayi</p><p>"Kinsan wallahi kar ki bari aji wannan maganan daga bakinki...haka nan zakice bakison shi... " dija dai shuru tayi tana tunanin how she feels about him the first instant, Kuma ita kanta Bata iya defining feeling dinta amma she's just calling it hate, </p><p>"Amma wayan nan biyun sunfi shi kirki..." Dariya Asabe tayi tana cewa</p><p>"Lallai bakisan kan abun ba...kina nufin shahid da Sharif sunfi shi kirki?... Kambu...to wallahi karkiyi fatan lambanki ya fito wajensu don har wanki mota sai su sakaki...Kuma suyi zaune suna kallon ka suna dariya....shi kam babu ruwan shi da kowa..mussanman mu maaikatansu..." Baki dija ta bude dataji ance wanki mota</p><p>"Kuma gabansu Hajiya suke kasaku wanki mota?..." Kai.asabe ta girgiza mata</p><p>"Aa.. In sun ga su Hajiya sun fita sai suce ni da haya... Muyi masu car wash....kaman yanda suke fada..." </p><p>"To meye maanan ka...was..." Dija ta tambayeta, </p><p>"Oho masu..." Dan Bata rai dija tayi Sannan tace</p><p>"Kilan yan iska ne..." Tafada Ahankali, da Sauri asabe ta kalleta, </p><p>"Ki bar furtan irin wannan maganar..babu kyau.." Kai dija ta gyada mata, </p><p>"Ki je kisha ruwan..ki kwantar da hankalin ki bashi da matsala Kawai kin tsorata ne da kyawunshi...kar ki kara nuna alaman tsoro in kin ganshi ..kinji ko?..." Ahankali ta kara gyada mata kai don tamkar babbar yaya ta maida asabe yanda Bata yiwa kawo gardama to itama batayi mata gardama.</p><p><br /></p><p>Yazid na barin factory ya nufi gidan su mufida, daman Tasan da zuwan shi don haka ba karamin haduwa tayi ba don tasha shadda skirt da riga ta gyara kanta sai ta daura dankwali yanda gaban goshinta zai bayyana, har cikin gidansu yayi parking ya fito yayi sallama bakin falinsu, cikin wata irin sexy voice da ya kusa sa shi shivering ta amsa mashi, ahankali ya shigo falon, ita kadaice hakimce kan kujera kaman wata princess, yana ganinta Kawai AI yaji kaman he's should strip her naked an go down with her, dukda yana practicing ustaz yasan over manliness na damunshi cos he easy turns on, wani irin kasaitaccen murmushi suka sakarwa juna,</p><p>"Sannu da zuwa baby...nayi missing dinka..." Ta fada mashi in a very low voice kaman tana flirting dashi, </p><p>"I miss you too..." Yafada yana zama Dan nesa daita, da Sauri ta mike ta shiga kitchen, sai bin bayanta Kawai yake da kallo yana imagining all this will be his in the next two weeks, mufida irin Matan ne masu kissa don ko bakasonta maganar bakinta Kawai is enough to draw your attention, Sannan she have the perfect body size, medium sized hips same with her boobs ga Iya tafiyan kasaita, tana daga cikin reasons din da yazid bai fiyason zuwa Kano ba cos she always turn him in and yanda ta Iya magana da komai she might not be hard to get most especially yasan no woman can resist him amma alhamdulillah he's not into women, yana cikin tunani ta dawo ta ajiye drink gabanshi</p><p> Tana Dana durkushe gabanshi ta daga pure white eyeball dinta ta kalleshi,</p><p>"Should I pour the drink?..." Ta tambayeshi cikin whisper, murmushi ya kara sakar mata</p><p>"Na hutar dake..." Ya fada mata, ahankali ta mike ta koma ta zauna kan kujera tana tafiya mai dauke hankalin mai kallo, mufida is a gal raised by only female parent after the demise of her multimillionaire father Kuma her mom nada all kinds of friends irin yan duniya nan so the most important thing she learnt was that kana Iya manipulating namiji with kissa and what are view, so hakan yasan she an expert when it comes to handling man's feeling Kuma tana succeeding don her cool and colourful attitude yana daga cikin reasons din dayayi tighting yazid to her</p><p>"Ina momcy take..." Ya tambayeta yana bude drink </p><p>"Tana upstairs..." Tafada tana Dora kafa daya kan daya,</p><p>Tare da zama kan ass dinta daya, tana karkada kafa Ahankali, kara kallonta yayi ta sakar mashi murmushi tana cewa</p><p>"Baby yau naga mai kama dai..." Tafada in a low voice, Dariya yayi</p><p>"A ina?..." </p><p>"A cikin peace TV...." </p><p>"Hala majed Mahmoud?..." Yafada yana zuba drink cikin cup, da Sauri tace</p><p>"Eh Wallahi.. Baby resemblance dinku is remarkable.. Kaman yan biyu...." Dariya ya karayi yana lumshe idanuwa</p><p>"Haka small mom take cewa duk sanda taga program dinshi...ni Kuma ko kadan bana ganin kamanninmu..." Mufida kallon Dan juice da yayi siyaya cikin cup yayi tace</p><p>"Yanzu baby Iya Wanda zaka sha kenan?..."</p><p>"Yes baby Kawai don kar kayi fushi dani amma small mom ta cika min ciki.. " Bata rai tayi</p><p>"Ba dai kana nufin bazakaci abinci a nan ba..." Dariya yayi</p><p>"Am sorry.. Gobe nan zanyi dinner..." Bai idaba ta rufe face dinta da left hand dinta ta fara kukan kissa, </p><p>"Baby are you crying?.." Ya tambayeta surprisingly,</p><p>"Yo sai kace...baka cin ..abinci NA...." Ta fada ciki kuka, </p><p>"Ok zan CI...stop crying..." Ya fada mata yana mamakin yanda ta Iya kuka Mara dalili don ko waya suke ba wuya ta fara kuka</p><p>"I can't wait inga kina mai dalili..." Yafada cikin ranshi, dauke hannun ta tayi daga face dinta yaga babu hawaye ko daya</p><p>"Ko kaifa...." Tafada tana mikewa, Dariya yayi shima ya mike</p><p>"Baby babu hawaye fa face dinki...Ashe haka kike yi min ko?... To yau NA ganoki..." Yafada yana biye daita har dinning table,</p><p>"Ai don kana nan ne banyi hawaye ba don banason in tada maka hankali..." Tafada tana jawo mashi kujera daya cikin kujerun dinning, zama yayi yana kallon glowing face dinta, abinci ta bude tayi serving dinshi itama tayi serving kanta</p><p>"Daman kai nake jira muci abincin..." Tafada mashi. Haka sukaci sukasha sai gyasa yazid yake saboda yanda yayi fulling cikin shi da abinci, sai da yayi sallan magrib a masjid din unguwan su Sannan.</p><p>"Sun gano gidan ko?..." Ya tambayeta, </p><p>"Eh..sun gano..." </p><p>"Yayi maki? Ko da akwai wani abinda kikeso a kara...." </p><p>"Ai ni banje ba..amma sunce its perfect..." Tsaya kallon ta yayi for a while Sannan yace</p><p>"Yaushe zan kaiki shopping?...." Dan turo baki tayi</p><p>"Ni ka bari tukunna... Kasan mami bazata bari in fita dakai yanzu..." Gira daya ya daga yana murmushi</p><p>" sai mu bari in mun je abuja mu tsaya...so ni zan tafi..sai gobe ..." Idanuwa tq zaro</p><p>"Kana nufin bazamuyi wayaba?.."</p><p>"Zamuyi mana..I mean zan dawo gobe....pls ki gaidamin momcy..." </p><p>" zataji...." Suna hira ta raka shi bakin motanshi ya shiga tayi blowing kiss</p><p> Shima yayi the same Sannan ya bar gidan. Ana kiran sallan ishai ya shiga estate dinsu, da alwallah magrib yayi Sannan ya shiga part din dad inda ya tarda almost dukkan yan gidan a falon dad amma banda Sharif da shahid, gaban mom dinshi ya zauna ta dauko cup dake kusa daita ta mika mashi amsa yayi ya bude yaga pure white kunun gyada ya saki murmushi tare dacewa</p><p>"Thanks...." Nan aka baje dina sai jira yake ko zaiga wannan yarinyan daya gani dazun amma bai ganta ba sai mai aikin mom dinshi. Sai wajen 8:30 su Sharif suka dawo gida yana tsaye bakin gate kaman shine maigadi, saida ya balbalesu Sannan yare da warning Sannan ya barsu suka shiga. </p><p>The following day yana kwance kan doguwar kujera sanye da blue shadda dayasha aikin hannu sai hira suke da Hajiya karama inda yake shaida mata baison zuwa party datasa akayi planning ita Kuma tana he must attend, hira suke amma he wants to see that gal again, Kuma gashi bai iya tambayan small mom. Yana nan zaune har zuhr amma bai ganta ba sai asabe data fito daga dakin sau daya. </p><p><br /></p><p>Daman tunda dija tazo gidan da sun gama aikinsu to tana dakinsu hardly ta fito sai kuma yanzu abun ya karu data ga yazid ko kadan batason ta Kara fita.</p><p><br /></p><p>Three days later yazid bai kara ganin dija ba Kawai sai yayi tunanin kilan ta bar gidan amma still one part of his heart really wants to see her. </p><p><br /></p><p>Yau suna zaune falon Hajiya babba su duka banda Maryam da yusra dake university suna daukan lecture sai Shari da shahid dake factory, yazid NA zaune gefen Hajiya karama yana latsa wayanshi,</p><p>"Gaskiya ANTY banason kayanda aka kawowa yaran nan...why not muje kasuwa muyi selecting wasu?.." Inji Hajiya karama, da Sauri su Ameera suka fara cewa suna zuwa, </p><p>"Me zai hana a kawo masu wasu?... Ni ban fiya son shiga kasuwa ba...kinsani..." Inji Hajiya babba,</p><p>"Nidai da mun shiga kasuwa wajen Dubai market nasan zamu samu wasu latest design NA kayan yara..." Tana fadin haka mimata tace</p><p>"Eh wallahi.. Big mom mshiga kasuwa yau ..ni bani da matching shoes..." Bata idaba Zainab ta katseta dacewa</p><p>"Nima bani da bag..pls big mom mu shiga kasuwa...." Suka fara magiya </p><p>"Amma saidai mu ajiye su marzuq gida tunda yazid yana nan..." inji Hajiya, Bata idaba marzuq da Ameera suka fara kuka</p><p>"Muma muna zuwa..." Suka fada in chorus, </p><p>"Shikenan kin jamana..." Hajiya babba ta fada tana mikewa, itama Hajiya karama mikewa tayi Ameera ta bi bayanta. Part dinta ta shiga ta umarci asabe ta shirya Ameera, ta Kuma fada mata ta shirya su shiga kasuwa don ta tayata rike Ameera, da Sauri asabe ta gama shirya Ameera itama ta koma dakinsu ta fara shiryawa, dija kallon ta tayi</p><p>"Ina zaki?..." Ta tambayeta, </p><p>"Kasuwa zan raka su Hajiya..." Bata rai dija tayi</p><p>"Yanzu ni kadai zan zauna kafin ki dawo?..." Ta fada kaman zatayi kuka, Dariya asabe tayi tana Sauri tasa kayanta don kar Hajiya ta kirata, fita tayi dija ta biyo bayanta suna fitowa Hajiya da Ameera NA fitowa</p><p>"Dija ki kula da gida..dukkan mu kasuwa zamu..." Hajiya ta fada mata,</p><p>"To..Ku dawo..lafiya...." Ta fada kanta kasa,</p><p>"Allah yasa..." Hajiya ta amsa suka fita. Dija NA ganin sun fita ta zauna nan falota kurawa TV dake aikin kallo.</p><p> Suna fitowa Hajiya babba ma ta fito dasu marzuq, yazid ne ya fito daga bayan mom dinshi yace</p><p>"Ko in kaiku?..."</p><p>"Just relax..." Inji Hajiya karama, rakasu yayi har suka shiga wata katuwar motan da suke fita da ita in general outing ne driver ya jasu suka tafi. Yazid komawa yayi part din mom dinshi yayi relaxing yana danna wayan hannun shi. Few minutes later kiran sultan ya shigo yayi picking suka fara hira.</p><p><br /></p><p>Dija kam kurawa TV ido tayi tana kallon tashen Bollywood, kura Katrina kaif ido, tana kallon yanda take da jkinta tana rawa, itadai abun ya burgeta ba kadan ba duk Wanda zai ganta sai yayi Dariya saboda yanda ta gwalo idanuwa abunka da mai manyan idanuwa tamkar zasu fado, </p><p>"Hmmm kallo da dadi wallahi..." Ta fadawa kanta, don tunda tazo gidan Bata taba kallo ba, kullum suna daki in sun gama aiki, so yau she decided to use the house to her advantage. Kara relaxing tayi tana kallon film din Bata ko blinking. </p><p>After like 30 minutes ta nan zaune tana kallo, yanda ake wanka cikin bathtub ne ta tsaya kallo. Komai burgeta Kawai yake. Da Sauri ta mike ta shiga dakinsu, direct ta shiga ta cika bathtub da ruwa, kayan jikinta ta cire ta shiga ciki, relax tayi ciki tana shafa leg dinta kan juna kaman yanda taga anayi.</p><p><br /></p><p>Yazid na nan zaune har bacci ya fara daukan shi, ahankali ya mike ya fita har yayi hanyan part dinshi ya tuna da ita, ahankali ya juya ya koma part din Hajiya karama, falo ya shiga yaga babu kowa. Dija na gajiya da ruwa tafito daure da Dan karamin towel jikinta gashin ta jike da ruwa, tsayawa tayi gaban mirror tana jujjuya gashin kanta kaman yanda taga anayi cikin film, </p><p>"Nima inada doguwar gashin..." Tafada tana kar basa gashinta kan shoulder dinta, yazid na ganin babu kowa falo yayi hanyan dakin dayaga ta fito kwanakin baya, ahankali ya bude kofan, yarinyan ya gani tsare da towel Wanda bai kai cinyanta ba, gashin kanta ya kalla, da Sauri ya maida kanshi baya, kara lekowa yayi da kanshi adaidai lokacin da dija ta yaye towel dake jikinta tana kallon jikinta ta as usual, da Sauri yazid ya koma baya ya jingina jin bangon idanuwanshi so wide open in a surprise way, tunda yake bai taba ganin tsaraicin mace ba ko a social media bai kallon bad things, Kawai sai taji yana samun erection, da Sauri ya dafe joystick dinshi ya fara komawa falo , dija kam batasan yanayi ba don a iya saninta she alone in the whole house don Hajiya ta fada mata ta kula da gidan, that means babu kowa gidan anata tunanin. Yarda towel din tayi ta juyawa mirror baya tana kallon small bombom dinta, Dariya ta kama yiwa kanta don sai yau ta ga bayanta mostly gabanta Kawai take gani. </p><p>Yazid tafiya yake duk ilahirin jikinshi sai rawa yake hannun shi biyu dafe da joystick dinshi din tunda yake samun urge na yau ya banbanta da sauran. Har ya sa hannu kan kofan zai bude ya tsaya</p><p>"Just one sin won't take me to hell...Allah knows am obedient... This is beyond me...I can't handle this...." Yafadawa kanshi Kawai sai ya juya ya kama hanyan dakin</p><p>[3:17PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挏馃挋鉂ゐ煐ゐ煉氿煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挍馃挋鉂ゐ煐ゐ煉滒煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat( ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>1鈨�0鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da Sauri ya kai bakin kofan amma sai ya tsaya</p><p>"Don't....do this..." wata zuciya ta fada mashi, kara rike joystick dinshi yayi yana cije lip dinshi,</p><p>"Oh Allah.. I can't... Am being human...." Ahankali ya sa hannun shi ya rike mabudin kofan, ahankali ya Kara budewa,this time yawunshi ne ya kafe cos she's totally nude, sai kara baza gashinta Kawai take wai ita dole baindiya, yazid kam tsaya kallon pure white skin dinta yayi from her dark hair to her tiny toes, jikinshi sai rawa yake, kaman babu kashi cikin jikinshi ya fara takawa zuwa inda take kallon kanta cikin mirror, Kawai sai ta ga kaman mutum bayanta, da Sauri ta juyo, nan taga yazid da idanuwanshi suka koma kaman garwashi, dukkan idanuwanta ta zaro tayi Sauri zata dauki towel dinta amma before ta kai har yazid ya kai gareta ya rike skin dinta dake sanyi saboda wasan ruwan datayi, idanuwa ta kara zarowa, wai ita dija ce yau tsaye gaban namiji babu komai jikinta, ita da ko hannun ta babu namijin da ya taba tabawa, yazid kallon cikin idanuwanta Kawai yake, kokarin kwacewa Kawai take, amma ya riketa sai kallon black nipple dake kan fair boobs Kawai yake, yasan basu gama girma ba amma its OK for him, baki dija ta bude zata kwala ihu ya Dora yatsanshi kan bakin shi, da Sauri ta rufe bakin. Har lokacin yana rike da naked waist dinta to himself, dija ji tayi wani abu na tokare mata ciki,</p><p>"Am....sor....ry..." Yafada cikin wani irin murya da baisan yana daita ba, kara matsa ta yayi ga jikinshi dija ta kara gwalowa, ko kadan batasan abinda ke zuciyanshi ba amma tasan is not something good, sakinta yayi ta fara baya2 duk step data dauka sai shima ya dauka ya kara zuwa kusa daita, kallon gabanshi tayi tana imagining abinda nan wuri dukda Tasan maza NA da abun fitsari but she haven't see anything like this, har lokacin one side of yazid heart bai bar fada mashi kar yayi wannan mistake ba amma he's make up his mind to make just one mistake, after all no body will know about it, dija NA ja da baya hannun ta daya kan kirjinta dayan Kuma kan gabanta, tana Jan bayan yazid na kara matsawa kusa daita, ya lura she's so young, he is so woken by her,tana kara matsawa baya har ta kai bakin gado, da Sauri ta hau ya bita, hannuwanta ta fara yarfawa, tana Jan baya har ta kaiga bango, idanuwanta duk waje amma babu alaman hawaye ko daya idonta don gani take sai in abu is not serious kake ganin hawaye. Farat daya ya jawota jikinshi </p><p>"Wayyo..." Ta fada da karfi, kwantar daita yayi yana kara kurawa jikinta ido Kuma har lokacin good side of him bai bar warning dinshi against abinda yaje niyyan aikatawaba amma the more ee looks at her the more he wants to dive into her,idanuwa ta kara zarowa jikinta ya fara rawa kaman mazari,</p><p> Idanuwanta ya kurawa ido yana kallon how scared she looks amma still bai da niyyan tsayawa, bayanta ya dinga shafawa Ahankali sai ture mashi hannu take amma bai bar shafa soft skin dinta, </p><p>"Wayyo., ka....ba....ri...." Tafada tana ture hannun shi, bayan wuyanta ya rike yana shafa long silk hair dinta dake kyalli as a result of relaxer da Hajiya Aisha tasa aka shafa mata, wani kallonj big gal yake mata saboda yanayin jikinta, she looks so matured to him, bakinshi ya kawo saitin nata tayi Sauri kauda kanta gefe kara juyo da kanta ta kara kauda kanta gefe, jikinta na kara rawa by each second, bai nuna wani hanzari ba cos yasan yan gidansu basu da Sauri when it comes to shopping Sannan yasan distance dake tsakanin estate dinsu da kasuwa, baki yasa ya fara kissing wuyanta tureshi ta farayi bakinta NA rawa saboda yanda bakinshi ke sending electric shock into her whole body, musurniya Kawai take duk sanda bakinshi ya taba naked skin dinta, </p><p>"Am...sor...ry...ba...halina....bane...." Yafada mata cikin kunnenta cikin wata irin murya, har lokacin dija bqtq San abinda yake niyyan aikatawa gareta ba ta daisan iskanci ne don ko taba hannun Mace is labeled iskanci balle wannan, tasan zaman ta gidan ya kare don kilan rayuwan yan gidan ne haka Kuma bazata so wani ya kara ganinta haka don gani take duk sun gan asabe ahaka amma ita ko kwana bazata kara cikin gidan ba balle wani ya kara yimata irin wannan abun. Bata ji kanta cikin tashin hankali ba sai da taji finger dinshi na kokarin shiga in between her, sai nan ta fara bugun shi tana cewa</p><p>"Ka..kyaleni....banaso... Ni..ba...yar...." Bata idaba ya rufe bakinta da nashi. Idanuwa ta zaro don dazun da take kallo film taga na miji ya sawa mace baki Kuma taga hakan a matsayin kazantan da bazata taba yi ba har ta mutu amma gashi itama wai ana samata baki</p><p> Broad shoulders dinshi ta fara turewa da two hands dinta amma ko gizau, duk abinda ake mata babu hawaye ko digo daya a eyes dinta Kawai shock ma ya isheta, barin shoulder dinshi tayi ta koma ta rike hannun shi dake in and out a gabanta amma still bai daina ba, bakinta take son zarewa amma ya kama bakin gam kaman lolly pop har zafi suke mata saboda yanda yake sucking dinsu, jin ya cire hannun shi yasa ta fara kokarin tureshi Kawai sai taji kaman snake na wurin cinyanta Kuma it's going upward, still tayi tana sauraron ko meye Kawai sai taji same thing na Neman shiga gabanta, wani irin jizo ta zabga mashi ga baki yayi Sauri bude closed eyes dinshi tare da zare bakinshi, amma still he's still looking for way, </p><p>"Wayyo... Wani...abu... Wayyo gabana..." ta fada cikin tashin hankali adaidai lokacin da yayi forcing kanshi ya shiga kadan, da Sauri ta fara girgiza kanta bakinta na rawa likewise duk ilahirin jikinta, kallon shi tayi tana cewa</p><p>"Wayyo nashiga uku...wani abu kasana...ka daina...mutuwa zanyi...." Tafada wannan Karin kaman zatayi kuka, shikam gani yake in duk duniya zasu taru a kanshi he can't stop now, her warmth was something he wants to last for ever, bai tabajin abinda yake ji at that moment ba Kuma gani yake ba zai kara jin anything like this ba, idanuwanshi lumshe, dija dai batasan abinda yake sa mata ba amma Tasan ba abun arziki bane cos it hurts like hell, gani still cikin ya kara shiga ta kara sakin ihun wahala Wanda yasa ya rufe mata bakinta da hannu daya ya rike waist dinta da hannu daya ya kara thrust this time making sure there is nothing left of him, dija kuka ta farayi idanuwanta duka waje, tsayawa yayi Kawai sai yace</p><p>"Am a monster...am a monster...am a molester...I am a disgrace to my family...." Yafada muryan shi na cracking kaman zaiyi kuka, hawaye ne suka dinga gangarowa daga idanuwa dija, jin ruwa a hannun shi dake kan bakinta yasa ya cire hannun shi ahankali, bakinta sai rawa yake zatayi magana amma ta kasa, kara thrusting yayi ta rike shi gam tana girgiza kanta at the same time tana hawaye, </p><p>"Dan Allah.... Ka..bari...." </p><p>"Kiyi..hakuri...." Da Sauri ta gyada mashi kai alaman OK don ko.dodo bata tsoro kaman yanda take tsoron shi, thrusting ya dingayi dija ta fara kira ammi tana kuka tana rokonshi ya bari amma he turned deaf ears har saida ya gama yayi extracting kanshi daga cikinta ya kwanta kanta yana hawaye, shi kanshi baisan he can be this dangerous ba sai yau, </p><p>"I have know the true colour of myself... " Yafada cikin kunnen dija dake sauke ajiyan zuciya don yana cirewa ta lumshe idanuwa wasu new tears na rolling, ita ba kukan lalata mata rayuwa dayayi take ba don batasan taka maiman abinda yayi mata ba Kawai kukan azaban da takeji take, har lokacin yana kwance kanta yanajin yanda heart dinta ke harbawa kaman zai fito, daga kanshi dake kan shoulder ta yayi ya tallabo face dinta cikin palm dinshi ya tsaya kallon ta for almost a minute yana kallon yanda take goge duk hawayen dake fitowa, hannun ta ta sa zata kara goge wasu dake fito ya rike mata hannu tare da girgiza mata kai, ajiye hannun tayi ya Dora goshinshi kan nata yana hawaye tana hawaye, pointed nose dinsu kan juna, bude idanuwanta tayi taga yanda yake hawaye har nashi sunfi nata zubowa</p><p>"Ko kukan me wannan mugun yakeyi?..." Ta tambayi kanta cikin ranshi, sunfi minti goma a haka yana hawaye, ko tsoron wani ya riskesu bai ji, Ahankali ya saki face dinta ya mike ya maida wandonshi dake wajen knees dinshi, da Sauri dija ta saka hannu gabanta taji wani ruwa dago hannun ta tayi taga wani farin abu hade da jini sai ta kara fashewa da kuka yana tsaye yana kallon ta, shi baima San abinda zai fada ba ya shiga bathroom din ya cika bathtub da ruwa ya dawo har lokacin tana zaune kan gado tana hawaye, kneeling yayi gaban gadon tayi saurin ja da baya,</p><p>"Ki yafemin... Bansan dalilin dayasa irin wannan kaddara ya faru tsakanina dake ba...amma I will marry you... I don't have to know who you are or where you came from but I will marry you.... Ki yafemin...." Ya karasa maganar cikin kuka, da Sauri dija ta gyada kai alaman ta yafe mashi amma sai kuka</p><p>"Dan Allah kar ki fadawa kowa abinda ya faru..." Da Sauri ta kara girgiza mashi kai Kuma duk abinda takeyi cikin tsoro take yinshi, </p><p>"Pls this should be our secret... Nobody should know the reason I want to marry you..." Yafada thinking tana jin abinda take fada,</p><p> Ita Kawai sai daga mashi kai take, </p><p>"Pls ki bar hawaye..." Da Sauri ta goge face dinta kaman bata taba kuka ba,</p><p>"Shekaranki nawa?..." </p><p>"Sha...uku..." Tafada bakinta NA rawa, kara dafa kanshi yayi yana kuka yana cewa</p><p>"Am 18 years older than you..." Yafada cikin kuka, </p><p>"Dan Allah kiyi hakuri... Its not my way of life..Allah kadai yasan dalilin faruwan hakan amma NA CUCE ki...you are to young for what I just put you through... You are not even matured...I don't know what came over me...am sorry..." Yafada cikin matsanacin kuka, itadai tunda yace ta bar hawaye bata karaba sai kallon shi Kawai take Kawai so take ya fita ta San inda dare yayi mata don ko second daya batason karawa cikin gidan, sai yanzu ta gane gidanku duk yanda yake yafi maka gidan mutane don ta tabbatar da a gidansu take da babu Wanda ya isa yayi mata irin wannan abun. Ahankali ya mike bata ankaraba taji ya dauketa nan ta saki sabon kuka don she was thinking he's coming for more, bathroom ya shiga daita ya direta cikin bathtub ta saki ihu Kuma sai tayi saurin rufe bakinta da hannun ta saboda tsoron shi, tsaya kallon ta yayi ya jingina da bango yana kallon yanda ta rumtse idanuwa tana yarfa hannuwanta. Fita yayi ya duba gadon yaga babu inda ya bace Sannan ya dawo</p><p>"Kiyi wanka...." Ya fada mata ya fita don a tunanin shi bata balaga ba balle yace tayi wankan tsarki. Fita yayi ya nufi part dinshi, maigadi dake zaune ya gane da akwai abinda ke damunshi don daga nesa face dinshi yayi red.</p><p><br /></p><p>Yana fita dija tayi saurin fita daga ruwan ta fito, da Sauri ta saka doguwar rigan datazo gidan dashi ta dauko pant dinta ta saka dukda zafin da takeji, da Sauri ta yafa Vail din kayan, ta fito falo tana cewa</p><p>"Gwara a kashe ni cikin gari da in kara zama gidan nan</p><p>[3:17PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挏馃挌馃挋馃枻馃挍鉂�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挍馃挋馃挋馃枻鉂ゐ煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat(ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>1鈨�1鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tafada tana kalle2 kar ashe yana nan falon, ganin ba kowa yasa ta Dan saki ajiyan zuciya tare da shesshekan kuka data sha, Ahankali ta bude kofa ta fito compound din gidan, yanda take tafiya says it all don duk kokarin da take wajen daidaita tafiyanta sai ansan something is wrong. Bakin gate tazo mai gadi NA zaune ya kura mata ido yana imagining abinda ke faruwa, yanzu yaga yazid ya fito daga bangaren da red face, sai kuma ga yar yarinya ta fito tana tafiya ba daidai ba, kura mata ido yayi yana tunanin </p><p>"Allah yasa ba abinda nake tunani bane...kai haba alhaji yazid bazai yi irin wannan shaidancin ba..." YaYi assuring kanshi dukda deep inside yasan something fishy is happening, bakin gate ta karaso ta bude karamin kofan ta fita, daman basu da ikon hana fita sai dai shiga ne ba a yarda dashi anyhow ba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yazid NA shiga part dinshi ya hada kai da bango ya dinga kuka yana dukan bangon kaman shi yasa shi aikata abinda yayi, ganin lokacin zuhr ya gabato yasa yayi niyyan wanka sai ya tuna ya kamata ya bata maganin tasha kafin ya dawo ya, pain reliever ya dauko daga cikin first aid box dake bedroom dinshi ya fito yana Sauri ya shiga part din Hajiya karama, still mai gadi NA zaune yana kallon shi, straight dakin daya barta ya shiga direct to the bathroom saiya ga wayam, fitowa yayi ya tsaya kalle2 dakindai ba lungu da sako ke da akwai ba so yasan something is wrong, falo ya fito yana son kwala mata kira amma baisan sunanta ba balle ya kirata amma babu alaman ta koina, da Sauri ya fita ya nufi maigadi dake kallonshi, da Sauri mai gadin ya mike, </p><p>"Wata ta fita yanzu?.." Shine tambayan dayayi mashi with rage, </p><p>"Eh..." Maigadi bai idaba ba ya saki Maganin kasa yana cewa</p><p>"What have I gotten myself into?..." Yafada tare da fita daga gate din da Sauri, shima maigadi da Sauri ya biyo bayanshi, afusace yazid ya juyo</p><p>"Go and mind the gate...." Ya daka mashi tsawa, dukda bai gane abinda yake nufi ba yasan he's not welcome komawa ciki yayi, yazid tsayawa yayi bakin gate din ya kalli haggunshi yaga babu kowa, juyawa yayi ya kalli right dinshi ya hangeta daga dan nesa tana tafiya a hankali, da gudu yabi bayanta Allah ya taimakeshi babu kowa wurin, saida yazo daf daita Sannan yayi slowing down, daman dija NA fita daga gidan ta kama kuka tana kiran ammi tana cewa</p><p>"Wallahi ammi ban kara yi maki gardama...danasani ban zo ba...." Take ta maimaitawa tana kuka, tana jin kaman kafan mutum bayanta tayi Sauri juyawa ta gan the dodo behind her </p><p>Idanuwa ta zaro zata kwalla ihu ya Dora mata yatsa kan bakinta, da Sauri taja numfashi</p><p>"Ina zaki?.." Ya tambayeta yana maida numfashi saboda gurin dayayi,</p><p>"Gida..." Tafada bakinta na rawa, tsayawa yayi yana kallon yanda hawaye ke bin junansu, </p><p>"Kiyi hakuri.. Kar ki tafi...zan maidaki da kaina....kinji ko?..." Da Sauri ta gyada mashi,</p><p>"To ki bar kuka..." Da saurinta kara goge face dinta, </p><p>"mu tafi gida to..." Ya fada mata in a calming tune, kallonshi tayi da idanuwanta da suka danj chanza kala saboda kuka tace</p><p>"Kar ...ka...kara...Dan...Allah...." Tafada cikin tsoro, kai ya gyada mata,</p><p>"Bazan Kara ba...even if you are my wife...I won't until you are matured..." Yafada mata cikin sanyin murya, dija tsayawa tayi </p><p>"Muje pls..." Yafada mata, da Sauri ta shige mashi gaba tana tafiya tana dingishi, </p><p>"Ki Dan gyara tafiyanki..ko kinason asan abinda ya faru tsakanin mu?.." Ya tambayeta cikin nutsuwa, da Sauri ta girgiza mashi kai ta gyara tafiyanta tana Dan cije labe, ahaka suka iso gida mai gadi ya miko mashi Maganin daya yarda ya amsa suka shiga part din Hajiya karama, mai gadi rike baki yayi yana cewa</p><p>"Wai meyasa yaran zamani basu da tabbas?... Yanzu yanda wannan yaron ke kama da mutumin arziki Kawai don yaga babu kowa gidan sai ya yage masu ya?...kai Allah wadaran..." Yafadawa kanshi ya kara dacewa</p><p>"Allah ya taimaka sauran masu gadin basu nan...da sun samu abun magana...nikam baa jin mutuwan sarki a baki na...".</p><p>Suna shiga ciki ya riketa mata hannu har bakin gadonsu Sannan ya fita, kitchen ya shiga ya hada mata tea mai kauri ya kawo mata, ta amsa kanta kasa </p><p>" ki.shaye in baki magani..." Da Sauri ta kafa kai ta shanye kasancewan ba mai zafi bane. Magani.ya balla mata ta amsa ta dauko ruwa ta shanye</p><p>"To ki kwanta...kar ki sake ki Kara kokarin fita kinji?..." Da Sauri ta gyada kai</p><p>"Good..." Yafada ya ja mata blanket Sannan ya fita, part dinshi ya koma ya yayi tagumi yana mamakin shi da yanmata ke kawowa hari yaki shine yau yayi wa yar yarinya fyade, har yanzu adua yake Allah yasa he's dreaming cos he couldn't believe what he did, he's such a decent and gentle amma wai yayi zani barely ten days to his wedding, mikewa yayi ya shiga bathroom ya tsaya gaban mirror yana kallon face dinshi da lips dinshi NA kasa da yayi ja saboda cizonta, har yanzu bai tambayi sunanta, kanshi ya buga da bango yana cewa</p><p>"Why...why me....why..." Ya dinga fada yana buga goshinshi da bango ji kake tim, har gaban goshinshi yayi ja amma bai bari ba, sai ihu yake yana Marin kanshi</p><p>"Ya Allah take me and give me the punishment I deserve... Ya Allah why me?..." Yafada yana sulalewa kasa, yafi minti talatin a haka Sannan yayi wanka gaban kanshi kumbure, face dinshi yayi ja sosai kaman ba shiba, ga wani azabtaccen ciwon kai dayake, kullum yana alfahari da kanshi da zani ta zama ruwan dare amma bai taba aikatawa ba har ya kai 31 amma sai gashi duk fadan da yakewa su Sharif, shahid and most especially friends dinshi sai nashi yafi nasu worst don he knows basu molesting yara, Ahankali ya fito daure da towel, ya saka jallabiya har zai tafi masjid Kawai sai cewa</p><p>"Am not worthy of entering the house of Allah..." Kawai dawowa yayi ya shimfida praying mat yayi salla nan bedroom dinshi ya kwanta nan kasa yana tunanin yanda zsai bullowa wannan alamarin,</p><p> Shi baisan Wanda zai fadawa wannan maganar ba don he's so ashame of himself, kullum cikin yiwa friends da co workers dinshi yake baisan mummunar kaddara awaits him ba</p><p>"Its really true kaddara ta Riga fata..." Yafada Ahankali yana juya kwanciya shi, </p><p>"I need an advice... But who can I confide in...." Ya tambayi kanshi hawaye NA gangaro mashi, </p><p>"Who can I tell NA lalatawa yar shekara sha uku rayuwa?... Wa zan fadawa I molest a juvenile?... Inna lillahi waina ilaihi rajuun... Oh Allah why me?..." Ya fada cikin matsanacin kuka, nan take sanyi ya rufeshi Kuma jikinshi zafi rau amma sai rawan sanyi Kawai yake Kuma yaki ya tashi daga kasan inda yake, gani yake yau is the darkest day of his life.</p><p>Bayan minti kaman goma da fitanshi bacci yayi gaba da dija, bata minti biyar bata firgita ba saboda irin mafarkin da take Mara dadi da ban tsoro. Before asar fever ya rufe yazid ita Kuma dija data farka bataji komai ba sanadiyan Maganin daya bata tasha. </p><p>Sai wajen karfe 4:15 su Hajiya suka dawo da kaya niki2 kaman Kasuwan duka suka dauko, direct part Hajiya babba aka shiga da dukkan kayan, asabe da mai aikin Hajiya babba suka shiga da kayan cikin falon suka ajiye, juyawa tayi zata tafi Hajiya karama ta kirata tare dacewa</p><p>"Ki tafi da wannan ledan, ke ki dauki biyu dija ta dauki hudu..." Hajiya ta fada mata, da Sauri ta durkusa</p><p>"Mun gode..." Tafada tana daukan ledan da ta nuna mata, da Sauri ta fita daga falon ta nufi part din Hajiya karama, tana bude kofan bedroom dinsu dija dake zaune bakin gadon tayi saurin mikewa, ganin asabe ne yasa ta fashe da matsanacin kuka, da Sauri asabe ta saki ledan kasa ta karaso wajenta da sauri ta rike hannun dija dake komawa zaune tana cewa</p><p>"Lafiya?..." Ta tambayeta tana kallon yanda ta susuce kaman baita data barta dazunba, dija baki ta bude zatayi magana sai ta tuna yace mata kar ta fadawa kowa abinda ya faru tsakanin su sai tayi shuru ta cigaba da kuka sosai, nan take hankalin asabe yayi mugun tashi ta rike hannun ta tana kallon jikinta ko zata gano abinda ke damunta, amma bata gano komai ba sai kukan dija ke kara tashi,</p><p>"Inna lillahi... Wai me ke damunki?... Meyasameki?... Dan Allah ki fadamin?..." Ta tambayeta kaman itama zatayi kuka, dija kama hannun ta tayi tana cewa</p><p>"Gida...gida nake...so...gida zani..." Tafada cikin kuka, kallon mamaki asabe tayi mata don the last time she checked dija NA son gidan sosai</p><p>"Bangane ba..wani.abun akayi maki?... " da Sauri dija ta girgiza mata kai</p><p>"Inason ganin ammi... Gida nakeso..Dan Allah... Ki...fada masu..." Tafada cikin kuka mai ratsa zuciyan mai sauraro,</p><p>"Dan Allah ki fadamin in wani abun akayi maki...nasan haka nan bazaki ce kin fasa zama nan gidan ba...Dan Allah me akayi maki?.." Asabe ta tambayeta hawaye NA turawa idanuwanta saboda yanda dija ke kuka, ara girgiza mata kai dija tayi</p><p>"Babu...abinda... Akayi...Mani...gida...nakeso..." Ta fadi.maganar bakinta NA rawa,asabe kuka ta farayi tana girgiza mata kai</p><p>"Dan Allah karkiyi haka...kinga har mun fara sabawa..don Allah kiyi hakuri..." Da Sauri dija ta kara fashewa da wani kukan tana girgiza kai</p><p>"Ni gida nakeso..." Tafada da karfi, da Sauri asabe ta mike ta dauko ledan dake kasa ta warware kayan dake ciki kasa, </p><p>"Kalli... Duk Hajiya ta sayo mana..tace ke ki dauki hudu ni in dauki biyu...." Tafada tana warware mata gowns masu kyau kala2 duk yanda dija keson abu mai kyau bubbuga kafanta tayi da kasa tana cewa</p><p>"Ni banaso... Gida nakeso..." Tafada ko kallon kayan batayi ba, afusace asabe ta mike ta goge hawayen face dinta</p><p>"Sai kije ki fada mata da kanki..." Ta fada tana barin dakin, da Sauri dija ta biyo bayanta har lokacin bata daina jin zafin gabanta ba, </p><p>"Dan Allah ki tsaya...ki fada mata Dan Allah..." Dija ta fada wa asabe dake shiga falon, juyowa tayi ta kalli dija sai taji ta tausaya mata dukda batasan the real reason behind her sudden attitude ba, </p><p>"zo kiji..." Asabe ta fada mata cikin sanyin murya, Ahankali dija ta fara takowa tsaya kallon tafiyanta asabe tayi tana mamakin why her step changed, </p><p>"Lafiya kike tafiya haka?.." Ta tambayeta sounding very serious, da Sauri dija ta tsaya ta girgiza kanta tana hawaye tace</p><p>"Babu komai.. Dan Allah ki.fada masu su maidani gida..Dan Allah NA rokeki...gida..nakeso..." Jin an bude kofa yasa suka kalli kofan</p><p>[3:18PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挋馃挏馃挌馃枻鉂ゐ煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挌鉂ゐ煉涴煐ゐ煉滒煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat(ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>1鈨�2鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hajiya karama ce ta shigo dija tayi saurin goge face dinta kanta kasa, mai aikin Hajiya babba ce ta biyo bayanta da kaya cike da wata katuwar Leda, Hajiya kallon dija tayi tana duk ta koma kaman ba itaba, dukda kanta kasa ta gano something is wrong with her, </p><p>"Dija..." Ta kirata, da Sauri dija ta daga kanta tare da durkusawa, kura mata ido Hajiya tayi for a moment Sannan tace</p><p>"Meke damunki?.." Ta tambayeta, baki ta bude zatayi magana asabe tayi saurin cewa</p><p>"Wai kanta ke ciwo...." Ta fadawa hajiya, dija batasan sanda new tears suka fara rolling ba, kara kallonta Hajiya tayi</p><p>"Don kanki na ciwo sai ki kama kuka?..." Ta fadawa dija Sannan ta kalli asabe, </p><p>"Ki biyoni in baki magani ki bata..." Ta fadawa asabe Sannan tayi hanyar dakinta asabe da mai aikin Hajiya babba suka bi bayanta. Ahankali dija ta mike ta koma dakinsu ko kallon kayan dake kasa batayi ba ta koma ta zauna bakin gado tana kuka, few minutes later asabe ta shigo rike da magani, da saurinta karaso wajenta, har lokacin bata mamakin how comes take tafiya haka ba, </p><p>"Dan Allah ki.fadamin.. Me ya sameki bayan fitan mu?..." Ta tambayi dija, shuru tayi tana hawaye,</p><p>"Dan Allah ki gayamin...wani ya shigo nan?.." Ta tambayeta cos tana suspecting wani abu, kai dija ta girgiza mata, still not believing her ta sake cewa</p><p>"Ko su Sharif sun dawo bayan fitan mu...? don ita tasan with them anything is possible, kai dija ta kara girgiza mata</p><p>" to me ya sameki..." Ta tambayeta wannan Karin is a soothing tune, </p><p>"Babu komai... Gida zanje...Dan Allah.. Ki fadawa hajiya...ko basu bani...ko sisi ba...zan..tafi...." Tafada cikin kuka, asabe zamatayi bakin gadon tana kallon ta, Tasan something is really wrong, </p><p>"Ki tashi mu shiga kitchen..Hajiya tace mu hada tea musha kafin a gama abinci..." Asabe ta fada mata, da Sauri ta girgiza kai,</p><p>"Bansha...gida nakeso..." </p><p>"Waike me akayi maki?... Duk kin birkice min...Allah zan fadawa Hajiya inyaso ta tambayeki da kanta..." asabe ta fada mata cikin fada,, kafa dija ta fara bubbugawa a kasa kaman yanda ta saba yi a gida tana cewa</p><p>"Nidai gida zani..." Tafada cikin kuka sosai, tana tunanin abinda ke faruwa, tana tunanin kilan ko Sharif ki shahid wani daga cikinsu yayi mata wani abu don tana ganin babu abinda basu Iya aikatawa mussanman yanda dija tafi Sauri yan aikin gidan kyau don su ma basu tsira ba don at times in Hajiya sun fita sukan kirata da mai aikin Hajiya babba suce suzo su gyara masu part dinsu daga nan su dinga tattaba su amma da sun nuna masu zasu fadawa Hajiya sai su koresu har da zagi, </p><p>"Hmmm to kilan fyade sukayi mata...." Ta fadawa kanta kasa2, ita dai dija kukanta ma ya isheta </p><p>"Kwantawa sukayi dake?..." Asabe ta tambayeta Ahankali, dija kara fashewa tayi da kuka ta girgiza kai,</p><p>"Babu abinda...akayi min...Kawai..gida...zani..." Tafada mata atakaice. </p><p>"Ke kika Sani...in ma wani abun akayi maki baki fada ba ke kika Sani..." Tafada tana mikewa deep inside tana aduan Allah yasa kar ace anyi mata wani abu don she's too young for that,.</p><p> Fita tayi daga dakin ta shiga kitchen ta hado tea cup biyu ta dawo dakin ta mikawa dija daya amma kememe taki amsa sai kuka take wai ita gida zata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yazid kam da kyar yayi sallan asr Sannan ya kwanta Kawai sai ya tsinci kanshi da murmushi Kuma sai ya fashe da kukan guilty yana ji yan gidan suka dawo amma bai Iya tashi saboda yanda duk joint dinshi ke ciwo, duk system dinshi felt empty ko Dan abinda bai tabayi bane oho, wayanshi ne ya fara ringing bai dauki wayanba balle yasan mai kira, shidai Kawai how he will find he's way out of this, tunanin mufida yayi sai yace.</p><p>"It won't be the case since am the man..." Ya fadawa kanshi, sai yayi tunanin abinda zai fadawa su Hajiya da alhaji for he's sudden decision, blanket ya rufe kanshi dashi yana jin yanda fever din ke hawa amma har lokacin bai sha magani ba, goshinshi ya Dan taba yajita very swollen, wayanshi ne ya fara ringing ya ziro hannu ya dauketa ya maida ta cikin blanket tare da kafa ta a kunnenshi, muryan mufida yaji, hiran was very brief don ya fada mata zai kirata later. </p><p>Har magrib su Hajiya basu ganshi ba, hakan yasan Hajiya babba ta kirashi don jin ko fita yayi nan ya shaida mata yana nan</p><p>"To kazo muci abinci..." Ta fada mashi,</p><p>"Nakoshi..." Ya fada mata Ahankali, Hajiya dake zaune kusa da Hajiya karama dake zuba abinci a plate dinta tace</p><p>"Koshi Kuma?...be kaci zakace ka koshi?..." Ta tambayeshi, </p><p>"Na ci abinci dazun are eleganza..." Yayi mata karya,</p><p>"Ok.." Ta amsa mashi Sannan ta kashe wayanta.</p><p><br /></p><p>Itama dija har lokacin bata bar kuka ba ita Kawai gida tun asabe NA rarrashin ta har ta gaji ta kyaleta don kanta haka lokacin cin abinci kiri2 dija taki cin abincin nan hankali asabe ya kara tashi taga ya zama dole ta fadawa Hajiya kar a samu matsala,</p><p>"Kizo kici abinci..in Hajiya ta dawo daga bangaren Hajiya babba zan fada mata..." Kai dija ta mata</p><p>"Banci ..." Haka asabe taci kadan ita kadai saboda yanda dija ta tada mata hankali. </p><p> </p><p>Har bayan sallan ishai dija bata bar kuka ba don gani take in bata bar gidan ba gani take zai dawo ya kara aikata the same thing don haka Tasha alwashin bazata ko ruwan gidan bazata shaba har ta bar gidan. Sau wajen karfe 8pm bacci mai nauyi ya dauketa asabe zama tayi bakin gadon tana kallon yanda take sauke ajiyan zuciya. </p><p><br /></p><p>Shima yazid yana Chan kwance har bayan sallan ishai bai fita ba duk a dakin yayi prayers dinshi, duk family sun hallara a falon dad kaman yanda suka saba duk dare amma bandashi nan ma kiranshi Hajiya babba ta karayi ya shaida mata bayajin dadi ne. Hajiya fadawa su dad abinda ya fada tayi</p><p>Da Sauri Hajiya karama ta mike itama Hajiya babba ta mike nan take dukkan yan falon suka mike banda dad, part din yazid suka nufa ga baki dayan su kaman zasu yaki, sallama Hajiya karama tayi a falon shi babu amsa da gudu marzuq yashiga bedroom din da yake ya ganshi kwance rufe da blanket</p><p>"Ku zo nan gashi kwance..." Ya fadawa su Hajiya, nan suka shigo yazid ya yaye blanket daga kanshi,</p><p>"Subhanallahi... Meya sameka?..." Hajiya karama ta tambayeshi tana kallon yanda for head dinshi yayi ja,</p><p>"Babu komai.. Kaina ne ke ciwo..." Ya fada Ahankali,hannu mom ta Dora a goshinshi taji zafi sosai, bata ce komai ba ta kalli mimata </p><p>"Kije ki fadawa dad dinku jikinshi is serious a kirawo doc..." Bata idaba ya katseta dacewa</p><p>"No mom..am okay...Kawai ciwon kai ne...nasan zuwa morning zan samu sauki..." Yafada muryan shi NA rawa saboda yana tunanin don basu San abinda ya aikata ba don da sun Sani yasan halin family dinsu. </p><p>"No let them call the doc...." Inji Hajiya karama, </p><p>"Ga wacce take bukatan doc chan on attended..." Yafada cikin ranshi, </p><p>"No..am OK...bana bukatan doc..." Banza mom tayi dashi,</p><p>"Baki jina ne?.." Ta dakawa mimata tsawa da Sauri ta fita ta nufi part din dad ta sanar dashi abinda mom tace, nan ya kira doc Sannan shima ya tafi Chan part din, duk sunyi tsaye sai Hajiya karama Kawai ke zaune gefen shi, dad ma na shigowa yagan for head dinshi same question yayi mashi same answer ya bashi</p><p>"Don't tell me nothing.. Baka ganin your for head is swollen?... I said what happened?..." Dad ya daka mashi tsawa, Ahankali ya Dora hannun shi kan goshinshi Sannan yace</p><p>"I mistakenly hit my head..." Yayi mashi karya,</p><p>"Kai ka Sani..." Dad ya fada Sannan ya bar dakin.</p><p> Yazid kam juya kwanciyan shi yayi yana tunanin halin da yasa yar mutane ciki, Kawai he wish he can see her before she goes to bed amma hakan is not possible, Kawai shi ji yake kaman yace su tafi su barshi da abinda ya dameshi especially Hajiya karama da bata full minti biyar bata dafa goshinshi ba. </p><p>"In kawo maka abinci?..." Hajiya karama ta tambayeshi, kai Kawai ya girgiza mata yana lumshe swollen eyes dinshi. Sai wajen karfe tara NA dare doc yazo yayi yan dube2 shi ya rubuta mashi magani bai fadi exactly abinda ke damunshi don shima baisan abinda ke damunshi ba. Sai wajen karfe 11 suka bar dakin sai lokacin yaji sakat ya kara fadawa duniyar tunani har lokacin bai bar searching Wanda zai fadawa ba, </p><p>"I have to tell someone... In ba haka ba this will hunt me for the rest of my life..." Yafada Ahankali, Kawai ji yake inama yana iya gano halunda yar mutane ke ciki.</p><p><br /></p><p>Abangaren asabe kam jiran Hajiya tayi har karfe goma jin shuru bata dawoba yasa ta je ta kwanta gefen dija dake bacci amma tana firgita saboda nightmares . </p><p>The following day dija ta tashi da fever saboda still da kuka ta tashi idanuwanta sun kumbura kaman ba ita ba, lokacin zuwa gaida Hajiya yazo suka tafi da asabe, nan ma Hajiya saida ta tambayeta abinda ke damunta wannan lokacin asabe taso yin magana dija tayi Sauri cewa</p><p>"Gida...nakeso..." Tafada tana fashewa da kuka, tsaya kallon ta Hajiya tayi for a moment Sannan tace</p><p>"To wani abun akayi maki?..." Da Sauri ta girgiza kai</p><p>"To me akayi all of a sudden kikeson zuwa gida?... Ko kina missing family dinki?..." Ta sake tambayan ta, dija bata ji abinda tace ba don haka bata ce komai ba kanta kasa sai hawaye take.</p><p>"Da fatan dai ba wani abun ni nayi maki ba da Sani na ba?..." da Sauri dija ta kara girgiza mata kai,</p><p>"To shikenan... Zan kira wacce ta kawoki tazo ta maidaki..." Wani irin dadi taji cikin ranta batasan lokacin data saki murmushi ba, itama Hajiya murmushi tayi</p><p>"Ai ba kuka zakiyi ba...in kina wurin mutum kina da bukatan ayi maki wani Abu sai ki fada ..." Tafada tana mikewa,falon ta bari ta fita zuwa ganin yazid. Da Sauri itama dija ta mike ta shiga dakinsu tana murna ita Kuma asabe ji tayi duk babu dadi. A falo ta tarda yazid ya fito sanye da English wears looking so decent, gaidata yayi ta amsa ta tambayi ya jikinshi ya amsa da sauki</p><p>"Me zakaci for breakfast?..." Ta tambayeshi, Dan murmushin karfin hali yayi yace</p><p>"Ai yanzu part dinki zanzo..Zan fada ma asabe ta hada min tea..." </p><p>"Ok then..."ta fada Sannan ta tafi part din Hajiya babba ta shaida mata abinda dija ta fada, Hajiya babba batayi mamakin hakan ba inda tace</p><p>" kinsan ba dukkan yara suka saba da rabuwa da families dinsu ba...so maybe she's missing home.. Kawai ki kira a maidata a samo maki wata..." Ta fada mata, itadai Hajiya karama bataji dadi ba amma a haka ta kira Hajiya Aisha ta shaida mata abinda ke faruwa inda Hajiya Aisha batayi gardama ba ta fada mata zata taho gobe.</p><p><br /></p><p>Shi kam yazid part din hajiya karama ya tafi yayi relaxing yana jira yaga dija don yaga how she's feeling amma bai ganta ba har ya kai kusan hour daya zaune, asabe ce tazo wucewa ya kirata </p><p>"Ki hadamin tea..." Ya fada mata yana Neman hanyan da zaibi ya koreta don ya samu ganin dija. Few minutes later ta kawo mai tea, har ta fara tafiya ya kirata</p><p>" dauko hijab dinki.." Ya fada mata, babu musu ta shiga ciki ta dauko hijab ta fito bata fadawa dija dake zaune kala ba din haushin ta take ji wai don zata tafi. Hannun yasa cikin aljihunshi yaga babu komai,</p><p>"Ki biyoni..." Ya fada mata yana ajiye tea din, ya mike. Bayanshi tabi har part dinshi ya dauko 5k ya bata,</p><p>"Gashi ki sayomin wannan drugs din..." Ya fada yana mika mata prescription slip da kayi bashi, </p><p>"Kiyi Sauri..." Ya shaida mata. Da Sauri ta amsa ta bar gidan inda shi Kuma ya tafi part din, bai tsaya wasting time ba ya shiga bedroom dinsu dija dake zaune ta kurawa waje daya ido bata daga kaiba thinking asabe ce Kawai sai taji kamshin perfume dinshi da Sauri ta daga kai tare da mikewa tana yarfe hannuwa, tsaya kallon yanda idanuwanta suka kumbura yayi, da Sauri ya karaso ya riketa jikinta sai rawa yake</p><p>"Ya jikinki?..." </p><p>"LA....fi...ya...." Ta amsa mashi jikinta NA rawa, </p><p>"Dukda NA fada maki karkiyi kuka shine kikayi har idanuwanki suka kumbura ko?... Yanzu fadamin me kike so in baki ki bar kuka?..." Yafada yana lallashinta, kai ta girgiza mashi, handsome smile dinshi yayi ya juya yadan kalli kofan Sannan yace</p><p>"Da gaske nake..ki fadamin abinda zan baki ki bar kuka....ko in saya maki jirgi?..." Ya fada in a funny way, dija hade rai tayi tare da girgiza kanta,</p><p>"To in saya maki mota?.." Kai ta kara girgiza mashi,</p><p>"To bari in je in dauko maki kudi...in NA kara ganinki kina kuka zan amshe abuna..." Yafada yana barin dakin. Da sauri ya tafi part dinshi ya dauko bundle na 500 guda biyu making 100k ya saka a aljihunshi ya ya dawo sai Sauri yake kar a kama shi, har lokacin dija tana tsaye a inda ya barta, hannu yasa cikin aljihunshi ya dauko kudin idanuwa dija ta zaro tare da rufe bakinta da palm dinta, </p><p>"Gashi ki boyesu...NA sayi kukanki.da wannan... Kika kara kuka zan amshe kayana..." Yafada yana mika mata kudin, kin amsa tayi ta tsaya tana kallon shi, da Sauri ya kama hannun ta ya damka mata kudin yana cewa</p><p>"In har kika bar nuna damuwa ..in NA kaiki gidanku zan baki wannan da yawa...." Ya shaida mata, tsaye tayi tana kallon kudin da take jinsu kaman mountains. </p><p>"Ki boyesu mana ko kinason wata ta gansu?.." Da Sauri ta girgiza kai,</p><p>"To maza boyesu, .." Ya sake fada mata, gabanta na faduwa ta ajiye kudin karkashin bag dinta ya tsaya yana kallon ta, sai da ya tabbatar tayi hiding dinsu Sannan yace</p><p>"Kinci abinci?..." Kai ta daga mashi,</p><p>"Kin koshi?..." Kai ta kara daga mashi,</p><p>"To sannu kinji...hope babu inda keyi maki ciwo...." Nodding ta karayi </p><p>"To shikenan..." Yafada Sannan ya fita daga dakin, ko kallon tea dake zaune baiyi ba ya wuce part dinshi. Aranar dija ta samu relief sosai ba don komai ba sai don Hajiya ta shaida mata ta kwantar da hankalin ta gobe zata gida. </p><p>Yazid kam shidai tunani kawai yake yanda zai bullowa alamarin don he has made up he's mind to take her as a second wife amma baisan ta ina zai fara ba gashi yanzu wedding dinshi sauran 8 days</p><p> "Maybe I should wait after the wedding..." Yafadawa kanshi a hankali. The following day Hajiya Aisha tazo gidan around karfe 12 na rana, gefe ta kira dija ta dinga NATA hakuri kan ta zauna gidan amma kememe dija taki, haka Hajiya ta sata gaba bayan Hajiya karama da Hajiya babba sunyi mata abubuwan arziki , don dubu goma Hajiya karama ta bata bayan ga atampa uku da perfumes kaman wata babba sai kayan data sayo mata shekaranjiya dija kam yanzu ta barjin zafin gurin hakan yasa tafiyan ta normal, motan suka shiga bayan Hajiya Aisha ta shaidawa hajiya karama zata samo masu wata yarinya. Suna fita yazid ya shigo gidan daga gidansu mufida don tunda yasamu mistake da dija bai je ba sai yau don a chan yayi breakfast. Koda yazo part dinshi ya shiga ya dauro alwallah ya tafi masjid, bai dawo ba sai 1:30 Kuma direct falon Hajiya karama ya shiga inda ya tarda asabe zaune ita kadai kaman tana tunani</p><p>"Bani ruwa..." Ya fada mata, da Sauri ta dauko mashi ruwa, zama yayi yana Neman yanda zaiyi yaga dija kasancewan duk ranar bai ganta ba Kuma the most surprising thing is that seeing her also makes his day baisan why ba amma kilan because yayi adding dinta to his life. Don wani special connection yake ji duk sanda ya ganta Kuma each moment da yake spending da ita really matters, Kawai he can't wait to have her close to him though tayi kadan amma seeing her alone zai zamo mashi among things that makes him happy. Kallon asabe dake tafiya kaman kwai ya fashe mata yayi </p><p>"Come and return the cup..." Ya fada mata yana kallon how moody she is, </p><p>"Meke damunki ne?..." da Sauri tace</p><p>" babu komai.." Ta amsa mashi tana amsan cup din daga hannun shi.</p><p><br /></p><p>Zamanshi yasha amma bai ganta ba Kuma ya rasa yanda zaiyi ya tura asabe daga dakin. Dole ya mike ya bar falon ya koma part din mom dinshi inda almost all the family ke zaune ana labari.</p><p>"Small mommy ba sai an kawo maki wata ba..Kawai a bar asabe Kawai..." Inji yusra, yazid sauraron hiransu yayi amma bai saka baki ba, </p><p>"Kai sai na samu wata..few days da wannan yarinyan tayi spending naga change...ai tace zata samomin wata..." Tayi responding to abinda yusra tace. Yazid tunani yayi yana cewa</p><p>"What are they talking about?..." </p><p>"Daman ni ban iya barin gida for long time... Gaskiya suna kokari.. Tafi sauran yan aikin gidan nan sanin darajan family.. Ba kaman suba da ko maganan gida basuyi .." Inji Maryam, gaban yazid ne ya fara faduwa yana tunanin Allah yasa is not what he's thinking</p><p> "Ni ban ma San sunan ta ba har ta tafi..." Zainab ta fada, sai nan yazid ya gano she's gone, da Sauri ya mike har mom dinshi na tambayan shi ina zashi ya amsa mata da part dinshi, </p><p>"Inna lillahi waina ilaihi rajuun..." Ya dinga maimaitawa yana tafiya yana hawaye, har ya isa part dinshi baisan inda yake takawa ba, Kawai yana jin kafanshi is moving, wulla kanshi yayi kasa ya fara kuka sosai, </p><p>"Yanzu I have ruined her for another man?..." Ya tambayi kanshi, da Sauri yace </p><p>"No!!!... I won't let that happen.... No..never..." Ya fada da Sauri, mikewa yayi ya goge face dinsu ya fita yaje part din Hajiya karama, asabe ya kira ta taho da Sauri, </p><p>"Ya sunan yarinyan nan?..." Ya tambayeta kai tsaye don caring if she understands what is going on, da Sauri asabe tace</p><p>"Wace yarinya?.鈥�" don ko kadan bata gano he's talking about dija ba, </p><p>"Yarinya nawa kuke aiki tare?..." Da Sauri tace</p><p>"Khadeeja..." </p><p>"Tana ina?..." </p><p>"An maidata gida?..." Kara daure fuska yayi</p><p>"Inane gidansu..."</p><p>"Nima ban Sani ba...." Ta amsa mashi wondering why all the questions </p><p>"To kinsan garinsu?..." Ya sake tambayan ta,</p><p>"Aa.. Amma tace katsina...." Fita Kawai yayi bai kara cewa komai ba, asabe sai mamaki Kawai take dukda har lokacin batayi suspecting anything happened between them ba don ita tafi zargin su Sharif.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koma part dinshi yayi ya hada kai da gwaiwa yana tunanin, wayanshi ya dauka yayi dailing number wani childhood friend dinshi.</p><p>[3:19PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 鉂ゐ煉涴煉氿煐ゐ煉滒煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>鉂ゐ煉涴煉氿煐ゐ煉滒煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat(ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>1鈨�3鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana zaune nan kasa jingine da kujera wayanshi a kunnenshi yana sauraron wakan dake tashi cikin as caller tune sai bayan second biyar akayi da </p><p>"Da ustaz.. Da Malam...da arramma...da ango mai jiran gado...." Yazid hararan wayan saboda irin kirarin da best friend dinshi keyi mashi before da yayi mashi irin wannan kirarin dadi yake ji amma yau ko kadan bayason jin hakan, yazid goge hawayen shi yayi</p><p>"Hello..ya akayi ne...." Gayen ya tambayeshi daga Chan bangaren,</p><p>"Kana ina?..." Yazid ya tambayeshi Ahankali, nan take gayen ya gane something is wrong,</p><p>"Wai what's wrong with you?... You sounds bad..." Inji gayen, dukda yanda yazid ke kokarin boye damuwanshi kasawa yayi Kawai sai ya fashe da kuka, da Sauri gayen ya kashe wayan.</p><p>Yazid na nan zaune ya hada kai da gwaiwa gayen yazo bayan kaman minti talatin.</p><p>Direct part din yazid handsome guy din ya shiga ya tarda shi zaune yana kuka kaman wani karamin yaro,da Sauri gayen ya rike should dinshi yana zama kan kujeran da yazid ya jingina,</p><p>"Lafiya?..." Ya tambayeshi sounding very tensed, yazid shuru yayi yana hawaye at the same time yana tunanin ayya yana Iya fada mashi damuwanshi don yasan shi da shakiyanshi har na rabarwa, </p><p>"Wai what is the problem???..." Ya sake tambayan shi, Ahankali yazid ya goge face dinshi da hannun shi ya daga red eyes dinshi ya kalleshi, </p><p>"Pls...can...I confide in you...." Yazid ya tambayeshi, da Sauri gayen ya daga mashi kai har lokacin yana dafe da shoulder dinshi</p><p>"Why not...I always confide in you... Besides what are friend for?..." Inji handsome gayen, yazid kara goge wasu tears dinshi yayi yana kallon gayen da duk hankalin shi ya tashi saboda yanda yazid ke hawaye,</p><p>"Pls don't discriminate me...Dan Allah don't judge me on what am about to tell you..." Ya fada cikin kuka, kara shafa shoulder dinshi gayen yayi </p><p>"Kasan wannan Kuma halinka ne...ni you know me well... Pls tell me...." Gayen ya fada mashi in a comforting tune,</p><p>"I...I...." Yazid ya fada Kawai sai ya kara fashewa da kuka, cikin tashin hankali gayen yace</p><p>"Did you kill any one?..." Da Sauri yazid ya girgiza mashi kai kaman wani karamin yaro, </p><p>"Then what?...I know that is the worst..." Inji gayen, da Sauri yazid yace</p><p>"Abinda nayi is worst... Could you believe me...." Ya nuna kanshi yacigaba dacewa</p><p>"Me yazid ..wai ni nayi ra...." Sai yayi shuru yana kuka, gayen gira daya ya daga in a surprising way, Ahankali yace</p><p>"Did you rape any gal?..." ya tambayeshi, da Sauri yazid ya daga mashi kai don shi bai Iya furta wannan word din, </p><p>"Subhanallahi... You?...how?.. When?....how comes?.." Gayen ya fada sounding speechless, da Sauri yazid ya fara cewa</p><p>" da akwai wata yarinya... I liked her tun first time Dana fara ganinta so...shekaranjiya... Su Hajiya sun fita....I decided to see her..when I went into the room...she was nude...I tried to control myself... Amma na kasa...did you know the worst part?..." Yazid ya fada kaman Wanda aka turke don duk Wanda ya ganshi yaga tashin hankali, Ahankali gayen ya girgiza mashi kai yana kallon yanda veins din gaban goshinshi suka tashi, yazid ya cigaba dacewa</p><p>"She begged...cried... Scream... Amma the devil deaf my ears...did you know another thing?.." Ya sake tambayan gayen cikin kuka, cikin sanyin jiki gayen ya jara girgiza mashi kai</p><p>"Salem...the gal in question is only 13..." ya karasa maganar cikin matsanacin kuka, shima gayen hawaye ne suka fara taruwa idanuwanshi,</p><p>"Inna lillahi waina ilaihi rajuun...." Salem ya fada yana kokarin maida hawayen eyes dinshi, </p><p>"What have I done wrong to act so stupid..." Yazid ya fada, shidai salem dafa shoulder dinshi yayi yana rarrashin shi saboda yanda yake kuka</p><p> "Ba laifinka bane... Haka Allah ya tsara...ko babu komai ni ina shaidanka...I know how guilty conscience is... Amma take it easy.. Ka dauki kaddara..." Salem ya fada mashi ahankali, yazid shuru yayi yacigaba dacewa</p><p>"Wane irin kaddara ne wannan... Kullum ina cikin yiwa su Sharif fada Ashe am worst than them... I wish Allah zai dauke raina...I hate my life....." </p><p>"Shush...stop crying... Hope su Hajiya basu gane ba..." Ahankali yazid ya girgiza mashi kai</p><p>"She so strong and brave..." Yafada Ahankali, </p><p>"Ni har yanzu I can't believe it.. To ina yarinya take?..." Da Sauri yazid yace</p><p>"Nan kizo ke tsaka..she's gone..." </p><p>"Bangane she's gone ba?.." Salem ya tambayeshi,</p><p>"Ta tafi gidansu... Kuma I think I love her..I want to marry her..." Ya fada cikin kuka, hararanshi Salem yayi</p><p>"Bangane you want to marry her ba?..ko you want to continue the act of molestation?..." Da Sauri yazid ya girgiza kai</p><p>"No..ba haka bane...NA CUCE TA..and I have to marry her..." Hararanshi Salem ya karayi</p><p>"Kama ajiye wannan zancen gefe daya...remember she's just 13..Kuma if possible ka aureta ba kyaleta zakayi ba.. Kawai ka kyaleta tunda ka kusa auren..." Daure fuska yazid yayi</p><p>"Kana nufin in lalata mata rayuwa in kyaleta?...no..impossible..." I will marry her..." Ya fada babu wasa, kallon mamaki Salem yayi mashi</p><p>"I no how you feel.. Kawai you are feeling guilty.. Amma it happens every day... Yara nawa ake ma haka?..Kawai ka ajiye wannan maganan... Just ask for her forgiveness.. Then you can better her life don ka nuna mata how remorse you feel..amma gaskiya ban baka wannan shawaran auren ba don hakan zai tona asirinka..." </p><p>"I don't bloody care!..." Yazid ya fada a tsawace,</p><p>"Banji tsoron yiwa Allah laifiba sai mutum?...I have made up my mind..sai NA aureta..remember I told you inasonta..." Shima Salem cewa</p><p>Yayi</p><p>"What about mufida?.." Yazid katseshi yayi dacewa</p><p>"Don ita kadai aka yoni?...if she can't stay she leave..." Kallon mamaki Salem yayi mashi yana imagining yanda yake son mufida yau yake cewa suna Iya rabuwa saboda wata, dariyan gefen baki Salem yayi.</p><p>"I know what your problem is.." </p><p>"What?..." Yazid ya tambayeshi kaman ba shike ke hawaye few minutes back ba, shuumin murmushi yayi Sannan yace</p><p>"Because she's your first.. Shiyasa you feel attached to her..amma am sure if you taste..." Hannu ya daga mashi cos yasan inda ya dosa, </p><p>"Stop it..." Kallon banza Salem yayi mashi</p><p>"Dalla rufe min baki..you can't even resist 13 years old gal..balle big full babe kaman mufida..." Yazid hawaye ya farayi yana cewa</p><p>"Yanzu don NA fada maka secret dina shine har zaka fara zagina dashi..." Yafada kaman wani Dan karamin yaro, Dariya Salem yayi</p><p>"Am sorry... Don't worry sai muje gidansu.. Hope kana Da address dinta?.." Kai yazid ya girgiza mashi</p><p>"No I don't know... Amma ance yar katsina ce..."</p><p>"Wannan ba case bane...tunda muna da relatives a katsina... Daman baka yarda ka rakani katsina gashi yanzu dole kaje...yanzu ka samo address dinta daga wajen small mom sai muje..."</p><p>"I don't think small mom tana da address dinta.."</p><p>"Why b sister dinta bace?...." Salem ya tambayeshi cike da surprise, </p><p>"No..yar aikin ta ce...." Idanuwa Salem ya zaro amma ya kasa magana saboda kar yazid ya hau shi da fada, </p><p>"Hmm..yanzu ganota is a case..cos bamu Iya tambayan ta ta nemo mamu address dinta..amma I suggest mu bar komai har sai bayan wedding dinka..." Salem ya fada mashi yana aduan Allah yasa ya bar wannan maganan</p><p> Donshi ko kadan bai gani wani abun burgewa a auren yar yarinya da bata San ciwon kanta ba. Ahankali yazid ya koma kan kujera ya zauna yana tunanin dija Kuma yana mamakin yanda akayi ta shiga ranshi farat daya ko dai maganar Salem gaskiya ce don ko mufidan daya Sani kusan shekara daya da rabi bai jinta cikin system dinshi kaman yanda yake jin dija</p><p>"Zan shiga wurin big mommy in kwaso gaisuwa..." Salem ya fada yana mikewa, yazid yaji shi amma bai tanka mashi ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dija kam tamkar tayi tsuntsu ta isa gida take ji don gani take Hajiya Aisha bata Sauri dukda uban gudun da take, sai wajen 3:30 suka iso garinsu dija amma haka nan sai taji gabanta na faduwa don gani take kaman ammi zatasan abinda wannan mutumin yayi mata, shuru tayi tana kallon small village dinsu as Hajiya tana tuki zuwa kofar gidansu. Ita har lokacin bata Iya cewa ga exactly abinda yayi mata amma har yanzu bata bar jin zafin gabanta completely ba amma ba kaman wannan lokacin ba, Kuma abu guda shine wani lokacin ta kan ji kaman ana tsira mata abu a gabanta. Parking motan yasa ta dawo hankalin ta, Hajiya Aisha data lura da dija kaman da akwai abinda ke damunta ta riketa yayin da take niyyan fita daga cikin motan. Da Sauri ta daga kanta ta kalli Hajiya,</p><p>"Wai dija naga kaman kina tunanin wani abu, da akwai abinda ke damunki ne?..." Ta tambayeta, da Sauri dija ta girgiza mata kai</p><p>"Ba..bu...abinda ke damuna..." Ta amsa mata muryanta na rawa,</p><p>"To shikenan..." Hajiya ta fada Sannan ta fita daga cikin motan ita ma fita tayi amma not as fast as she should, Ahankali take tafiya kaman wacce kwai ya fashewa a ciki hannun ta rike da bag dinta dake dauke da duk kayan da aka bata tare da kudin da yazid ya bata. Ita har yanzu bata San abinda zata fadawa ammi kan wannan Kudin ba. Tana biye da bayan Hajiya har cikin gidansu, sai boyewa take bayan Hajiya kaman ba gidansu ba. Sallama Hajiya tayi ammi dake alwallah ta amsa mata tare da cewa</p><p>"Ah..ah..yau kece tafe Kuma?...maraba da zuwa..." Tafada ko kadan bata gan dija dake labe bayan Hajiya ba, amsawa Hajiya tayi, sai lokacin dija ta leko da kanta sukayi ido hudu da ammi, sai lokacin ta taho kanta kasa don tamkar gaban ammi akayi mata wannan abun haka take ji, da Sauri ammi tace</p><p>"Wa nake gani kaman dija..." Tafada with surprise, jin an kira dija yasa binto da sauran siblings dinta dake daki suka fito da gudu, </p><p>"Aikam dija ce...tace a maido ta gida..." Inji Hajiya Aisha, baki ammi ta bude saboda mamaki yanda dija ta dinga hauka saboda an hanata zuwa Kuma ko wata batayi ba har ta gaji ta dawo, Kuma ta lura data susuce kaman ba itaba, rungume ta su binto sukayi suna kallon kayan jikinta, "ki shigo ki zauna..." Ammi ta fadawa Hajiya Aisha,</p><p>"Ah ah...wucewa zanyi...rabona da gidan tun safe...daman gidan aikin ne suka kirani wai dija tace gida taje so..shine NA daukota na maido maki amanar da kika bani..." Inji Hajiya Aisha, ba karamin dadi ammi taji ba,</p><p>"To madalla..nagode kwarai Allah ya saka da alkhairi.. Gaskiya samun mutane irin ki sai an tona...mun gode da irin dawainiyan da kikayi damu..Allah ya biya..." Ammi ta fada tana durkusawa, </p><p>"Babu komai.. Allah ya shige mana gaba..ni zan wuce..." Hajiya Aisha ta fcada Sannan ta kalli dija</p><p>"To khadija sai kin shigo daura ki zo mu gaisa ko?.." Da sauri dija ta gyada mata kai. Fita tayi ammi tabi bayanta sai sanya mata albarka take har Hajiya ta shiga motarta ta tafi Sannan ta dawo cikin gidan, har lokacin dija na tsaye inda ta barta rike da bag dinta sun binto sun zagayeta kaman basu taba ganinta ba Ammi dawowa tayi ta dinga kallon ta daga sama har kasa</p><p>"Har kin gaji da bautawa mutane?..." Shine tambayan da ammi tayi mata, da Sauri dija ta gyada mata kai kaman wata sakara, </p><p>"Ya akayi kika dawo?.."ammi ta tambayeta don ta lura da akwai abinda ke damunta don Tasan halin yarta da kiriniya,</p><p>" ko.wani laifi kikayi masu?..." Da Sauri dija ta girgiza kanta,. </p><p>"Babu komai.. Kawai..nafison.. Gida..." Ta amsa mata gabanta faduwa, still kallon ta Kawai ammi.ta dingayi Wanda yasa yan cikin dija tsinkewa, </p><p>"Meye nan ciki?.." Ammi ta tambayeta tana nuna bag dake hannun ta, da Sauri dija ta ajiye bag din kasa ta durkusa nan ta bude bag din ta fara fiddo kayan ciki tana cewa</p><p>"Kinga kayan da suka bani...da kudi..." Tafada muryanta na rawa dukda ta fara samun kwanciyan hankali saboda ammi bata yi mata tambayan me akayi mata ba, sai fiddo kayan, ammi baki ta bude saboda new gowns data gani sabbi kal cikin ledan su, mutuwan tsaye tayi da dija ta fiddo kudin da yazid ya bata, da Sauri ta ja hannun ta zuwa daki</p><p>"Ina kika samo wannan kudin?.." Ammi ta tambayeta cikin tashin hankali har lokacin tana kallon 100k dake hannun dija, bakinta NA rawa tafara cewa</p><p>"Su...su..ka..bani..." Tafada muryanta na rawa don gani take yanzu asirinta ya tonu, </p><p>"Wane irin aiki kikayi masu da zasu baki irin wannan makudan kudin..dija?..." ammi ta tambayeta kaman zatayi ihu, </p><p>Da Sauri dija tace</p><p>"Sune...suka...bani...dazan taho..." Tafada mata deep inside tana son fadawa ammi.gaskiya alamarin amma gani take zai gane ya biyota nan in ta fada,</p><p>"Dija ki fada min gaskiya.. Daukar masu kudi kikayi?..." Ammi ta tambayeta kaman zatayi kuka, da Sauri dija tace</p><p>"Ammi Wallahi tallahi ban daukar masu ko sisi ba...su suka bani..masu kudi ne...sosai...." Tafada, tsayawa ammi tayi tana kallon kudin dake hannun ta fari kal kaman babu Wanda ya taba touching dinsu,</p><p>"Cewa sukayi...in ..bar talla...wai muyi Sana'a...." Tafada da Sauri,</p><p>"Ya akayi suka San kina talla?.." Ammi ta tambayeta, da Sauri tace</p><p>"Fada masu nayi...sai sukace..babu kyau..talla...shine suka bani in baki..." Tafada kaman gaske, ahankali ammi ta amshi kudin jikinta sai rawa yake, don tunda take bata taba rike kudi masu yawan wannan ba. Kallon sama tayi</p><p>"Ya Allah nagode maka..." Yafada Sannan ta kara mikewa dija kudin</p><p>"Ki rike inyi salla sai mu irga..." Da Sauri ita amshi kudin Kuma she felt so relieved da baa gane abinda akayi mata ba. </p><p><br /></p><p>Salla ammi tayi itama tayi salla don jin kanta take kaman an bata award saboda she feels so happy don gani take no any harms will ever comes to her again.</p><p><br /></p><p>Suna idar da salla suka zauna sukayi counting kudin inda duka ga dubu Dari da shabiyar kasancewan Hajiya babba ta bata 5k ita Kuma Hajiya karama ta bata 10k. Ammi dai har lokacin bata bar mamaki ba. </p><p>"Yanzu me zamuyi da wannan kudin?.." Ammi ta tambayeta, </p><p>"Nima ban Sani ba..." Tafada feeling relaxed, </p><p>"Wannan kudin Nada yawa sosai...ko mu dinga saida aja?."" Ammi ta tambayi dija</p><p>"To amma bazamuyi talla ba ko?..." Ta tambayeta, Dariya ammi tayi</p><p>"Basai kinyi tallaba... Sai mu dinga bazawa nan kofar gida..." Ammi Tafada mata, ba karamin dadi dija taji ba don yanzu babu abinda take bukata kaman security don ita yanzu tsoron maza takeji fiye da tunanin mai karatu.</p><p><br /></p><p>Cikin dare kam dija da bacci kawai sai taga kaman yazid ya taho sai ta fara kuka tana</p><p>"Kayi hakuri...kace...bazaka...karaba...kayi hakuri...." Amma duk rokon da takeyi mashi bai hanashi abinda yayi niyya ba ganin zai kara raping dinta yasa ta kwalawa ammi kira tare da farkawa daga nightmare din da take Itama ammi da Sauri ta mike ta kunna hasken touch taga dija zaune sai zufa take tana kuka, da Sauri ta rarrafa ta koma gaban ammi tana kalle2 cikin dakin don tabbatar babu kowa dakin don tamkar yana wajen take ji. </p><p>"Meke damunki?.." Ammi ta tambayeta tana haskwa face dinta fitila, kara matsawa daf da ammi tayi tace</p><p>"Tsoro nakeji..." Tafada tana waige2,</p><p>" tsoron me?.." Ammi ta tambayeta tana kallon yanda take sweating, </p><p>"Wani ne..." Tafada har lokacin bata bar waige2 ba Kuma tana kara shigewa jikin ammi,</p><p>"Me zaiyi maki?..." </p><p>"Nima ban Sani ba...ammi tsoro nakeji..." Tafada tare da rungume ammi Kawai sai ta fara kuka tana kama ammi gam, </p><p>"AI kece baki adua kafin ki kwanta..." Ammi ta fada tana kokarin kwanciya amma yanda dija ta riketa ya hanata kwanciya, da kyar ta samu tayi loosening grip din dija a jikinta ta kwanta dija ta kara riketa gam.</p><p><br /></p><p>Shima yazid yana chan cikin dare sai mafarkin dija yake yana bata hakuri yana kuka nadama amma Sam bata bashi fuska ba balle yaga alaman ta yafe mashi, yana nan durkushe yana bata hakuri ta juya baya zata tafi yayi saurin tare gabanta</p><p>"Ki yafemin.. Ban karawa.. Dan Allah..." Ya dinga maimaitawa har ya farka daga Bacci, zama yayi kan gado tare da hada kai da gwaiwa don mafarkin looks so real.</p><p><br /></p><p>Dija kwana tayi manne da ammi which was very surprising to ammi don abinda bai taba faruwa ba kenan. Da safe bayan sallan fajr saida ammi ta tambayi dija mafarkin datayi amma sai taki fadin gaskiya tayi mata karya kan actual dream don't. Bayan kalaci ammi ta shirya sai cikin garin katsina inda ta shiga kasuwar yar kutungu kasancewan suna zuwa time to time tayi sarin kayan haja irin su turaren irin nasu na yan kauye, da atampopin roba da su powder da sauran kayan gayu irin na yan kauye sai su magi, gishiri da sauran kayan miya sai su klin da omo da sabulun wanki, har da kayan dinki da su zip, zare da sauransu atakaice da ammi ta dawo gida bayan sallan asr saida kusan dukkan mutanen kauyen suka fito don kallon kayan da aka kawota dashi cike da katuwar buhu sai wata karama buhu duk cike dam, data shiga gida mutane biyosu sukayi suna kallon kayan Kuma suna mamakin ina ta samu jalli har haka don duk kauyen babu mai shagon dake dauke da kayan mai yawan wannan daman shago biyu duk garin Kuma kayan su biyu basu kai yawan kayan da ammi ta sayo ba.</p><p><br /></p><p>A wannan daran ma sai da dija ta samu same nightmare Kuma still ammi ta tambayeta amma same karya tayi mata. Wace gari suka baza kaya waje kan buhu nan kasuwa ta barke dija da siblings dinta ke zaune suna sayarwa amma sai tayi kusan minti talatin tana tunanin abinda yazid yayi mata. Yanzu abun biyu ya zamar mata saboda jiya danmusa mai nama ya sake zuwa inda ya fada mata shi yanason aurenta. .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abangaren gidansu yazid kam an fara wedding events inda already gidansu yayi tatul da family and friends amma shi kanshi angon kullum karewa yake kaman kudin guzuri saboda yawan tunani Kuma the more days go by the more he keeps falling for her, gani yake if something is not done soon he will loose his mind. Salem kam yayi comforting dinshi har ya gaji amma nothing changes</p><p> Ita kam amarya tasan something is wrong don tun ranar da dija ta bar gidansu yazid, yazid bai kara fita ba balle yaje gidansu mufida Kuma in suna yawa he makes the conversation brief, sai yau da suka hadu a wajen till dawn party da Hajiya karama tada aka hada baki ta bude tana kallon yanda yazid ya koma kaman ba shiba, shima sultan coworker dinshi da suke aiki a CBN tare amma Dan plature wato jos yayi mamakin yanda ya koma don saida ya kirashi gefe yana tambayan shi what's wrong amma murmushin karfin hali Kawai yayi ya amsa mashi da wedding stress, itadai mufida kallonshi Kawai take amma ta zama short of words, saida suka zauna ta Dan matsa kusa dashi ya kalleta ya sakar mata killer smile dinshi itama murmushin tayi</p><p>"Baby what's wrong with you?.." Ta tambayeshi Ahankali, kurawa glowing face dinta ido yayi </p><p>"Me kika gani?.." Ya tambayeta tare da boye damuwanshi, </p><p>"You look pale..is it me?..." Ta tambayeshi, Ahankali ya daga hannun shi ya kama hannun ta abinda bai taba yiba kenan</p><p>"No is not...Kawai abubuwan ne is too much for me...don't worry am OK..." Yayi assuring dinta. Ahaka akayi party ko karfe tara baiyi ba ya sa a maida mufida gida shi Kuma ya wuce gidan. Su kam sun San something is wrong with him don irin takuran da yake masu in ya dawo gida yanzu baiyi don in zasu kai shabiyun dare basu dawo gida ba bai tanka masu Hajiya babba kam ba damu sosai ba dukda bai fiya cin abinci ba amma Hajiya karama that is in charge na abincin shi tq damu Kuma ta tambayeshi har ta gaji sai ya amsa mata da stress ne. </p><p><br /></p><p>Yau Saturday ne zaa daura auren yazid, yana kwance cikin blanket sai rawan sanyi yake dakin cike da big boys duk Wanda ka gani kasan yana ji da kanshi, kusan guys goma ne tsaye inda yazid ke kwance cikin blanket, </p><p>"Let's call a doc.." Daya daga cikin guys din ya fada, Ahankali yazid yace</p><p>"No...yanzu...zanyi.. Wanka..." Yafada murya shi na rawa, Salem NA zaune kan kujera yayi tagumi yana kallon yazid shi tunda yake bai taba ganin inda guilty conscience yayi weighing mutum down kaman yanda yayi weighing yazid down ba, Ahankali yazid ya yaye blanket dinshi daga shi sai boxer ya ajiye pure white legs dinshi kasa yana tafiya Ahankali ya shiga bathroom, kallon madubi yayi Kawai sai ya fashe da kuka, yana hawaye yana wanka don ji yake kaman heart dinshi zai lalace saboda yanda yake ji. Sai da yayi kuka ya isheshi Sannan ya watsa ruwa ya fito, kayan da aka tanada saboda shi ya dauko ya saka pure white shadda babba riga ya saka looking so breathtakingly handsome. Gayu sai hailing dinshi suke amma ko daga kai baiyi ba balle ya amsa masu. </p><p><br /></p><p>Around 12 aka daura auren su Sannan suka sake shiri don zuwa reception. Ba karamin kudi aka kashe wajen ba don manyan mutane sun hallara amma ango kan looks disturbed and it's written all over him, around six suka koma gida inda aka wuce da amarya gidansu. </p><p>Wajen karfe tara akazo kai daukan ango don kaishi dakin amarya.</p><p>[3:20PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挍鉂ゐ煉滒煐ゐ煉欚煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挏鉂ゐ煉氿煐ゐ煉涴煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat( ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>1鈨�4鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana zaune yayi relaxing idanuwanshi lumshe, Ahankali ya balla button din suit dinshi</p><p>"Wai me kake haka?...ana shirin tafiya da kai ka gidanka Kuma kana cire kaya..." Salem ya fada mashi, murmushin karfin hali yazid yayi ya kalli Salem </p><p>"Sai kace dole?... Ku tafi I will find my way..." Yafada idanuwanshi lumshe. </p><p>"Pls guy mutafi lokaci na tafiya Kuma kasan da akwai tafiya..." Salem ya fada yana fita daga dakin wasu guys hudu suka bi bayanshi suka bar yazid zaune nan falon. Cire suit din yayi ya wullar Ya mike ya shiga bedroom ya ida cire kayanshi ya dauko wasu English wears masu kyau ya saka Sannan ya fita sai kamshi yake part din mom dinshi ya shiga ta kalleshi, ahankali ya karaso wajenta ya zauna kusa daita tare da dan fadawa jikinta,</p><p>"Yanzu damuwa ya kare..sai ka maida jikinka...don ka rame da yawa..." Mom ta fada mashi tana shafa kanshi, lumshe idanuwa yayi</p><p>"I wish..." Ya fada cikin ranshi. Ahankali mom ta dinga bashi advice kan Wanda suka bashi a baya sauraron ta Kawai yake amma he's absent minded, Kawai tunanin yanda one mistake ke Neman ruining perfect life dinshi yayi, daman hakan yake da sauran mutane ko nashi is different, Hajiya karama ce ta shigo da manyan basket dauke da manyan food warmers, ta ajiye gabanshi</p><p>"Ga abincin da zaka tafi dashi...don nasan duk baku ci abinci ba,..." Tafada mashi,daga eyes dinshi yayi ya kalleta tare dacewa</p><p>"Thank you..." Itama zama tayi daya gefen shi ta bashi nata advice din Sannan ya fita zuwa su Sharif suka bishi da abincin. Wurin Abba ya tafi shima Abba ya saka mashi albarka Sannan suka tafi, yana zaune bayan motan yana aduan Allah yasa kar yayi ruining perfect moment dinsu da suka dade suna planning. Sai almost 11 suka isa gidan, </p><p>"Kawai Ku wuce tunda is late..." Ya fada ma Salem, hararanshi Salem yayi</p><p>"Wannan is your problem..." Yazid bai kara cewa komai ba yafita aka fiddo mashi basket din ya dauka sai zolayan shi suke amma ki uffan. Kofan falo ya bude ya shiga wani irin elegant kamshi yayi welcoming dinshi, ajiyan zuciya ya sauke ya tsaya yana yiwa kanshi fada kan kar ya bari abinda tq shiga tsakanin shi da khadeeja yayi ruining happiness din matarshi, ya fi minti goma tsaye Sannan ya kama hanyan part din da aka kai mufida. Falonta ya shiga still kamshin perfumes na Arabian Kawai yake ji, sai lumshe idanuwa yake har ya isa bakin daya daga cikin doors dake part dinta, Ahankali ya bude ya shiga da sallama, mufida dake zaune kan royal bed mai shegen kyau da tsada ta daga kanta dake cikin net ta amsa sallaman sai yaji voice dinta NA cracking, murmushi yayi ya ajiye basket din kan dinning din mutum biyu dake gefe daya Sannan ya taka Ahankali zuwa bakin gadon, tsayawa yayi yana jin kukanta, </p><p>"You are not the only scared one...I am too..." Yafada cikin ranshi, zama yayi kan gadon ya matsa kusa daita kamshin turaren ta is unbearable, hannu yasa ya cire net din fuskanta beautiful wet face dinta ya bayyana. Kura mata ido yayi yana mamakin how could he have astonishing beauty but still longs for another, murmushi yayi mata</p><p>"Kukan me kike...amarya?..." Yafada in a whisper, daga big eyes dinta dayasha thick lashes tayi ta harareshi, ya kara saki murmushi.</p><p>"Ko baki Sona yanzu?..." Ya sake tambayan ta, shuru tayi bata amsa mashi ba, </p><p>"To bari in sayi bakin sai kiyi min magana...." Yafada yana saka hannu cikin aljihunshi</p><p>: Wrap din 500 guda biyu ya dauko daga cikin aljihunshi ya mika mata, Kawai sai dija ta fado mashi a rai, ya tuna lokacin daya bata kudi irin wannan he remember the look on her face, wani irin kallon tsoro tayiwa kudin kaman taga dodo, Ahankali mufida ta daga kanta ta kalleshi gani tayi ga kudi yana miko mata amma hankalin shi bai wurin, Dan taba hannun shi tayi ya dawo hayyacinshi tare da saki murmushi,.</p><p>"Ki amsa mana...na sayi bakinki... Da Kuma kukanki..." Yafada Ahankali, kara hararan shi tayi, ya kama hannun ta ya Dora kudin sama </p><p>"Kizo inyi feeding dinki...." Yafada mata yana mikewa, mufida sai binshi take da ido, kara juyowa yayi yaga bata da niyyan tashi, dawowa yayi ya dauketa ya direta kan kujeran dinning, abincin ya bude ya zuba a plate dake cikin basket din. Sai da ya cika plate da abinci da chicken salad Sannan ya debo ya kai bakinta, Ahankali ta bude ya zuba mata, kura mata ido yayi yana kallon how beautiful she is amma still his heart is not taken completely by her, inda dija wata babba ce da yace ta hada da asiri. Ahankali ya kara debo abinci zai kai bakinta ta kauda kanta</p><p>"Kai kaci mana..." Ta fada cikin sanyin murya, murmushi yayi</p><p>"Hmmm naji muryan matata...ni na koshi..." Yafada mata Ahankali, bata rai tayi kaman zatayi kuka, </p><p>"Nima na koshi..." </p><p>"Zaki fara kukanki mai tadamin hankali ko?.. Zakiyi mai dalili..." Ya fada yana kashe mata ido daya, da Sauri ta saki ranta, amsan spoon tayi daga hannun shi ta debo abinci ta kai bakinshi ya bude ta zuba mashi. Yana ci yana kallon idanuwanta, Kawai sai yaga kaman yana kallon dija, ahaka ya ciyar da ita shi 3 spoons Kawai ya ci. Tana zaune ya tattara plate ya kai kitchen ya bar food warmer nan ya shiga bathroom ya dauro alwallah, wurin ta ya dawo ya tsaya bayan kujeran da take zaune ya duka yayi mata kiss a wuya</p><p>"Baby je kiyi alwallah..." Yafada yana shafa hancin shi a wuyanta. Da Sauri ta mike har ya saki murmushi saboda yanda jikinta ke rawa, few minutes later ta fito. Tana tafiya Ahankali tabude bag da akayi mata arranging kayan da zata bukata urgently ta dauko long hijab, tsaya kallon ta yayi kaman he's seeing her for the first time.</p><p><br /></p><p>Bayan sun idar da salla nafila ya juyo ya kalleta tare da rike hannun ta, kurawa fingers dinta datayi fixing yayi </p><p>"Meye wannan?..." Ya tambayeta yana shafa nails dinta, shuru tayi kanta kasa, kurawa nails dinta ido yayi yana kara tabbatar dacewa ba nata bane</p><p>"Fixing dinsu kikayi?..." Ya tambayeta, Ahankali ta gyada mashi kai</p><p>"Ya zaayi ruwa ya shiga hannun ki in zakiyi ablution?..." Ya tambayeta, at that moment sai yaji kaman yayi shuru don shima yana da dirty character amma sai ya tuna she's now his wife.</p><p>"Gobe ki ciresu...." Yafada mata Ahankali yana shafa hannun ta, babu musu ta gyada mashi kai don ita ko kadan ba zatayi mashi gardama ba don she knows she's lucky to him don mata da yawa can do anything just to with such person.</p><p>"Bari in hada maki ruwa kiyi wanka..." Yafada cikin sanyin murya yana mikewa, bathroom ya shiga ya hada mata warm water Sannan ya dawo</p><p>"baby your water is ready..." Yafada mata yana zama bakin gado. Ahankali ta mike ta dauki small bag din, tsaya kallon ta Kawai yayi ta shiga. Dan relaxing yayi tare da sakin ajiyan zuciya don yasan he's trying very hard da bai bari situation fin da yake ciki yasa ya ruguje mata happiness ba. Yafi hour bata fito ba alhalin ta gama ta saka wasu sexy nighty amma kunya ya hanata fitowa, bakin kofan yaje ya kirata tare da shaida mata zai shiga ciki, Ahankali ya bude kofan ya ganta tsaye sai wasa take da yatsunta, Dariya yayi</p><p>"Masha Allah... Wannan haduwa sai NA bada tukuici..now come let's make this night memorable...." Ya fada mata yana daukanta, kan gado ya direta. Nan ya fara exploring each and every part of her body especially boobs dinta, even at that moment dija rana yi mashi yawo cikin kai. Saida yayi aduan saduwa da iyali Sannan ya sadu daita, Sam bai sha wahala wurin shiganta ba saboda ta sha wahala wajen shiganta ba cos ta sha magunguna kala2 which makes her wet and welcoming, ba karamin sumbatu ya sha ba har da kiran sunan khadija amma kasancewan mufida batasan inda hankalin ta yakeba bataji ba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Around 1:30am dija dake bacci ta kwalla ihu tana </p><p>"Kayi hakuri...kar ka kara...na..hakuri...nashiga uku..ammi..ki...hanashi...." Take fada da karfi Wanda</p><p> Wanda yasa ammi ta tashi da Sauri tare da kunna touch tana kallon dija dake danna gabanta tana shure2 da kafanta kaman da akwai mutum kanta,</p><p>"Wayyo marata....ciwo...ka..daina....zafi...nakeji..." Tafada da karfi Wanda yasa ammi zaro idanuwa tana kallon yanda take yi kaman ana kwanciya daita Kuma bataso, wani irin duka ammi tayi mata dija dake zufa ta firgita tare da mikewa zaune idanuwanta waje tana kalle2, da Sauri ta rarrafa ta rike kafan ammi tana shigewa jikinta, zama ammi tayi tana kallon yanda take yi,</p><p>"Dija..meke damunki?..." Ammi ta tambayeta, da Sauri tace</p><p>"Mafarki...nayi..." Shuru ammi tayi tana tunanin wannan matsalan ya fara damunta don tunda ta dawo bata tsallake rana batare datayi irin wannan mafarkin ba</p><p>"Wai me Wanda kike gani yake maki?.." Ammi ta tambayeta,</p><p>"Nima ban Sani ba..." Tafada tana fashewa da kuka, tureta ammi tayi</p><p>"Ban gane baki Sani ba..ba ke kike ganin abinda yake maki ba..fadamin abinda yake maki...." Ammi ta fada babu wasa, shuru dija tayi tana kuka, </p><p>"Ko wani abun akayi maki chan birni da kika je?.." Da Sauri dija ta girgiza kai</p><p>"To meye sanadiyan wannan mafarkin haka kullum tunda kika dawo sai kin tadani da dare?... Gaskiya gobe muje muga Malam..." Tafada tana komawa wajen kwanciyan ta, da Sauri dija ta je gabanta ta kwanta tare da riketa gam kaman yanda ta saba yi . </p><p><br /></p><p>Da asuba yazid ya hadawa mufida ruwan wanka Sannan ya tadata daga bacci, idanuwanta kumbure saboda kukan datayi don ko kadan baiyi slowing down ba</p><p>"Rise and shine...baby na... Thank you for yesterday..ki fadi abinda kikeso inyi maki..." Yafada yana shafa hancinshi a wuyanta at the same time yana kissing dinta, hararan kanshi tayi don wani irin haushin shi takeji don her looks gentle amma mean in bed, Ahankali ta dan ture kanshi ta sauko tare da tahowa da blanket din, da Sauri ya janye ta tsaya naked tana kare kanta da hannun ta, ganinta haka yasa yaje ya rungume ta yana kissing dinta ganin zai kara kwantar daita yasa ta fara kuka amma abanza sai da ya gama ya dinga bata hakuri, ya kaita bathroom tayi wanka tare da zama a ruwan dumi Sannan ta fito tana tafiya Ahankali, shima wankan yayi ya jasu salla Sannan suka koma sai kara shigewa jikinta Kawai yake, </p><p>"Dan Allah.. Kaje part dinka ka kwanta....bacci nakeji..." Tafada kaman zatayi kuka, Dariya yayi</p><p>"Yanzu baby ni kike kora?... Me nayi maki kike korata?... Gaskiya nan jikin ki zan kwanta..." Yafada kaman wani karamin yaro, haushi ta karaji ta fara dirza kafa kan gadon tana cewa</p><p>"Dan Allah ka tafi...Pls..." Tafada hawaye na taruwa eyeball dinta, </p><p>"Ki kwanta..babu abinda zanyi maki..." Ya shaida mata, sai lokacin ta yarda ta kwanta ya kwanta bayan ta amma sai kara shigewa jikinta yake kuka ta farayi datagan kaman zai maimaita, gani kuka take kaman ranta zai fita yasa ya bar dakin ya koma daya daga cikin rooms din part dinta ya kwanta tare da fadawa duniyar tunani</p><p> "Now my missions begins...." Ya fadawa kanshi, shuru yayi hawaye na taruwa idanuwanshi,</p><p>"I wonder how many times she have cried... Ki yafe min</p><p>... I know I hurt you.. Pls am sorry..." Ya dinga maimaitawa kaman dija tana gabanshi. Yana nan zaune sanye da jallabiya har karfe 11, har an kawo abinci daga gida ya jera kan dinning amma mufida bata fito ba, dakin ya koma ya ganta kwance sai baccin ta take. Kan gadon ya nufa ya zauna, ko minti daya baiyi da zama ba ta bude ido, murmushi ya sakar mata ta kauda kanta, hannun ta ya rike tare dayi mata kiss a forehead</p><p>"Did I wake you?..." Ya fada mata cikin whisper, kai ta girgiza mashi. Hannun ta ya kai bakinshi yayi kissing dinsu tare dacewa</p><p>"Baby baki fadi abinda kike bukata inyi maki ba...kin San kin shayar dani dadi...I need to compensate you for that...so tell me what do you want..." Ya tambayeta Ahankali, shuru tayi tana kallon yanda yake caressing hannun ta, harshe yasa yana licking fingers dinta Ahankali yana cewa</p><p>"Pls tell me..ban San abinda zan baki ba...so I want you to tell me...don't be shy..." Yafada cikin wata irin murya, ita dai mufida ban da faduwan gaba babu abinda take don gani take he will ask for more, Ahankali tace</p><p>"Banason komai.. I just want to be alone with you for the rest of my life..." Tafada Ahankali, daga kai yayi ya kalleta don ya gane inda ta dosa, bakinshi ya kai wuyanta yana kissing dinta Ahankali, </p><p>"Kaman ya alone?..." Ya tambayeta word din na sauka a wuyanta,</p><p>"Daga ni sai kai...sai yaranmu...promise me bazaka hadani da wata ba..." Tafada mashi Ahankali tana lumshe idanuwa saboda yanda yake kissing wuyanta, deep down tana mamakin yanda duk kunyan nan tashi yanzu babu don tunda yake zuwa gidansu bai taba kama mata hannu ba, Dariya yayi yana licking kunnenta yana cewa</p><p>"Baby in banda abinki...mata nawa aka hallata mana?..." Ya rada mata cikin kunne, Ahankali tace</p><p>"Hu...du...." Tongue dinshi ya cigaba da turawa cikin kunnenta yana cewa</p><p>"Ni ba hudu zanyi NA...daya Kawai zan kara bayanke...." Ya fada yana nishi Ahankali, </p><p>"Yanzu..zaka...kara...wani...auren...in future?..." Ta tambayeshi muryanta na rawa,</p><p>"Baby ba...in..future ba...very soon...." Yafada mata aikam tureshi tayi ta fara kuka </p><p>"First day na a gidanka kake fadamin zaka kara aure this days...daman you don't love me?... Daman you were two timing me?..." Ta fada tana kuka, da Sauri ya so rungume ta amma ta kara tureshi tana kuka, </p><p>"Baby ke kika kawo wannan maganan.... Kuma banason karya a zamantakewan mu...I want us to live a truthful life...banason yi maki alkawarin karya...you know I love you...." Yafada yana kokarin kaman hannun ta amma tana dojewa, </p><p>" ba wani kana Sona....duk wahalan danasha hannun ka babu abinda zaka sakamin sai wannan maganan... Ni ban Iya sharing dinka da kowa..." Tafada cikin matsanacin kuka kaman yanzu zaayi mata kishiyan</p><p>"Am sorry for hurting you... Now let's close this chapter... Fadamin abinda kikeso..." Ya tambayeta yana hawa kan gadon tare da jawota jikinshi, sai kuka take har da shessheka, dora kanta kan shoulder dinshi yayi yana shafata Ahankali</p><p>"Baby am sorry... Pls let's forget about what I said..." Yafada yana rarrashin ta, cikin kuka tace</p><p>"To bazakayi min kishiya ba?...wallahi mutuwa zanyi..." Tafada cikin kuka, Dariya yazid yayi yana cewa</p><p>"Don't worry.. When we get to that bridge we will cross..." Yafada yana shafa bayanta, kara fashewa tayi da kuka</p><p>"Yanzu bani kadai ce cikin ranka ba?..." Dariya ya karayi yana cewa</p><p>"Hmmm bakison kishiya amma dazun korata kikayi daga dakinki..."</p><p>"To na daina..." Ta fada cikin kuka,</p><p>"To in baki son kishiya..." Yafada yana daga jallabiya shi ya fiddo joystick dinshi, mufida tayi saurin rumtse idanuwanta,</p><p>"Zo ki zauna nan..." Yafada yana nuna mata joystick dinshi. Knowing bazata iyaba, boye face dinta tayi </p><p>"Zo ki zauna in baki son kishiya..." Yafada yana dariya</p><p>"Ai na gaji...." Ta fada Ahankali</p><p>"To kin gani...baki da karfi...dole in samu mai taimaka maki...." Zatayi magana ya jawota </p><p>"Taso kici abinci..." Yafada bai bata daman magana ba ya dauketa, daga ita sai kayan bacci ya bata abinci shi Kuma yasha kunun gyada.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gari na wayewa sukayi kalaci dija taso fita da kayan saidawansu ta jera su waje kaman yanda suka saba amma ammi ta hanata kan sai sunje gidan Malam Baude sun dawo Sannan a fidda kayan, mutane sai zuwa Neman kaya suke amma ammi tasata ta shirya cikin daya daga ciki kayan da aka saya mata masu kyau itama ammi ta shirya suka kama hanyan neighboring village. Sunfi hour suna tafiya Sannan suka isa wata karama thatch house, shiga sukayi da sallama aka amsa masu, gaban dija sai faduwa yake don gani take zaa gane abinda da yafaru Kuma mutumin da ya yayi mata abun na Iya biyota don ya fada mata kar ta fadawa kowa, zama sukayi gaban Wanda suke gani is the eyes of all Kuma yana ganin abinda ke boye, Malam Baude babba malami ne Wanda ansan shi a many small rural areas Kuma ana respecting dinshi sosai. Gaidashi ammi tayi ya amsa tare dacewa</p><p>"Me ya kawoku?.." Ya tambayesu, Ahankali ammi ta fara cewa</p><p>"Daman yata ce tunda ta dawo daga birni take mafarke2 duk dare ihu take tana cewa wani na tahowa...shine mugazo ka duba mana...Kuma ka fada mana mafita...." Yafada kanta kasa, </p><p>"Ammi zanyi....fitsari..." Dija ta fada kaman an fixgi maganar daga bakinta, </p><p>"Je kiyi..." Ammi ta fada mata not paying attention to the tension in her voice, dxa Sauri ta mike ta bar dakin. Mutumin kasa ya zuba kasa ya fara bincike kaman yanda ya saba, ya zana ya goge, yayi yafi sau biyar, dija tana tsaye bayan wurin tana jinsu,</p><p>"Bakin aljani ne ya shigeta...zaa rubuta mata rubutu ..." Idanuwa dija ta zaro, </p><p>"Ashe babu abinda ya Sani ..." Dija ta fada cikin ranta tana Dariya, komawa ciki tayi ta zauna kanta kasa cikin ranta tana zagin malamin Kuma tana tausayawa wayanda suka yarda da abinda yake masu. Kallon yanda yake rubutu kan allo tayi mashi hararan kasan ido. </p><p>Bayan ya gama ya wanke ya juye a kwarya ya bata, gefen zaninta ta kwance ta fiddo dari biyu ta ajiye kasa ta mike dija tabi bayanta.</p><p>Suna zuwa gida ta zuba mata tasha Sannan suka fidda kayan Sana'a su.</p><p><br /></p><p>Wajen karfe shabiyu tana zaune tayi tagumi kaman wata babba ko tunanin me take oho, wasu age mate dinta uku ne sukazo </p><p>"Ke kin huta da wahalan talla..." Daya daga Cikin su ta fada, dija dai shuru tayi don abinda ya isheta daban. Zama sukayi kusa daita suka fara labari dija na dan sa bakinta time to time, kaman ta tuna sai tace</p><p>"Wai Dan Musa yace zai aureni..." Ta fada masu, idanuwa suka zaro</p><p>"Kinci nama..." Inji daya daga cikin su</p><p> Tafada tana dariya, </p><p>"Daman gata mayyar nama..." Wata tayi adding, dija hararan su tayi batace kala ba, daya daga cikin su kam cewa tayi</p><p>"Ni bazan yi aureba..." Da Sauri suka kalleta </p><p>"Meyasa?.." Dija ta tambayeta, </p><p>"Hmm ai tunda naje gidan salaha nace banyi aure..." Yarinyan ta fada, dukkan su kallon ta sukayi Sannan daya daga cikin su tace</p><p>"Me akayiwa salaha?..." Ta tambayeta, </p><p>"Bazan fada ba..." Inji yarinyan, da Sauri dija tace</p><p>"Dan Allah ki fada mana..." Hararan ta Yarinyan tayi</p><p>"Salon kuje Ku fada mata ko?..." Da Sauri dija tace</p><p>"Ai ni tunda akayi bikinta banje gidanta ba..."</p><p>"Ai kina birni akayi bikin..." Wata tayi adding, dija dafa shoulder wacce tace batayin aure tayi</p><p>"Dan Allah ki fada mana...bamu fada mata...ko zaku fada mata?..." Ta tambayi sauran, da Sauri suka girgiza kai, yarinyan kalle2 tayi Sannan tayi kasa da bakinta su dija suka sauko da kunnensu da kin gansu kinsan gulma suke, cikin whisper Yarinyan ta fara cewa</p><p>"Cemin tayi...kullum.. Sai ya saka mata abun fitsarinshi...cikin..abun fitsarinta..." Dukkan su idanuwa suka kwalo tare da sakin salati, dija kam tunani ta farayi, tana tuna lokacin da yazid ya tura mata wani abu a gabanta, she remember how it pieced through her body with pain and agony, </p><p>"Kuma tace da zafi sosai..wai har da rana sai ya saka mata abun...." Yarinyan tayi adding, </p><p>"Kambu..ashe lamido Dan iska ne?..." Inji daya daga cikin su,</p><p>"Kedai bari...shiyasa nace banyin aure...don da kyar salaha take tafiya..." Tafada, </p><p>"Kilan nima shiyasamin...." Dija ta fada cikin ranta,</p><p>"To meye amfani haka?..." Daya ta tambayi yarinyan dake basu labari, </p><p>"Wai ce mata yayi ta nan zata samu ciki ta haihu...wai haka iyayenmu sukayi..." Da Sauri daya daga cikin su tace</p><p>"Kambu karya yake... Saidai in iyayenshi ne ke yin hakan...." Dija dai batajin abinda suke cewa don tunanin yanda yazid ya dinga tura abun cikinta Kawai take nan taje tsigan jikinta ya tashi,</p><p>"Indai haka ne nima ba zanyi aure ba..." Dija ta fada a zahiri don ko a lahira bazata so jin irin wannan azaban ba,</p><p>"Ya zakiyi da danmusa..." Wata ta tambayeta,</p><p>"Oho...nima ban Sani ba...amma har in mutu ba zanyi aure ba..." Ta fada masu atakaice, haka suka dinga labari amma dija tayi jugum tana tunanin ya zaayi mutum ya saka abinda ake fitsari dashi gaban mace, </p><p>"Allah yaisa wallahi.. Ban taba yafe maka....." Tafada cikin ranta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> *One week later*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yazid ya chanza sosai don ba karamin kulawa mufida ke bashi ba, duk abinda yake so takeyi don duk yanda zaiyi mata bata complain haka duk abinda tace tayi mashi wurin kwanciya yi take, babu irin dirty and rough style da basuyi ko tana jin zafi haka zata dake , hakan yasa ya Dan rage tunanin dija dukda she still lock around in his heart, ko.kadan mufida bata bashi breathing space wai don kar yayi zancen aure, daga gida sai masjid, yau suna zaune bayan sallan ishai kallo suke amma hankalin yazid bai wurin, Kawai tunanin yanda zaiyi yaga dija Kawai yake yasan duk yanda mufida zatayi mashi he's not complete without her, yanzu hutunshi sauran sati biyu and yayi deciding yasan abinyi kafin ya koma abuja</p><p> Mufida da kanta ke bisa cinyanshi ta daga ido ta kalleshi taga wani wuri yake kallo, Dan taba shi tayi ya maido hankalin shi gareta tare da sakar mata murmushi, Dan turo baki tayi</p><p>"baby tunanin me kake?.." Ta fada cikin shagwaba, Ahankali ya tale baki kaman zaiyi kuka, duk yayi squeezing fuskan kaman karamin yaro, </p><p>"Love meke damunka?..." Ta tambayeshi, yana shafa bayan hannun shi a gefen fuskan shi kaman yanda yara keyi in suna kuka yace</p><p>"Wannan nakeso...." Yafada yana nuna boob dinta, har lokacin bai sakin fuskan ba, mufida Dariya tayi saboda how funny his face looks,</p><p>"Dan wannan.. Ai is all yours..." Tafada mashi tana shafa face dinshi, </p><p>"Yeyyyy...thank you mommy... To ki bani..." Yafada cikin shagwaba, daman ta saba cos kusan da boobs dinta yake kwana, Ahankali ta mike tana kallon yanda ya saki baki kaman he's about to see her boobs for the first time, yanda yake mata yasa ko.kadan batason ko a mafarki ta hadashi da wata, Ahankali ta fara daga riganta,</p><p>"Are you ready?..." Ta tambayeshi, da Sauri ya gyada mata kai, Ahankali ta zare rigan daga jikinta ta tsaya babu riga ajikinta, kurawa glowing skin dinta ido yana lashe baki kaman wani maye,</p><p>"Baby...pls ki bani in sha..." Yafada kaman yana baran abinci, Ahankali ta taka ta zauna kan kafanshi </p><p>"Baby take anyone you want..." Ta fada mashi ahankali, kallon su yayi yana lumshe idanuwa</p><p>"Let me start with the right one..." Yafada yana kallon eyeball dinta tare da kafa lips dinshi kan right hand side boob dinta, idanuwa ta lumshe saboda yanda tsigan jikinta ya tashi saboda warm lips dinshi,</p><p>"Love it?..." Ya tambayeta yana sucking nipple dinta, groaning ta farayi tana cewa</p><p>"Yes...I love it.. Pls more..." Tafada muryanta na rawa,</p><p>"Right away ma'am...' Ya fada yana wasa da second boob dinta, nan dai wasa ya chanza tsakanin su, it was as pleasant as always.</p><p><br /></p><p>An hour later tana kwance kanshi sai nishi suke kaman wayanda sukayi race</p><p>" baby I can't get enough of you..." Ya rada mata cikin kunne,</p><p>"I don't want you to get enough of me...I want you to long for me for ever..." Dariya yayi</p><p>"Ai dole...." Yafada yana kokarin mikewa,kara danneshi tayi da boobs dinta, </p><p>"Wai babu yaushe zamu koma abuja?..." </p><p>"Nan da sati biyu..." </p><p>"Baby why not mu koma da wuri so that muyi shopping din da ka fada?.." Ta fada mashi cikin kunnenshi,</p><p>"To amma sai nan da kwana goma...don I have something important to attend to..." Yafada yana shafa bayanta,</p><p>"Kaman me?..." Ta tambayeshi, shuru yayi ya fara kokarin mikewa don baison yi mata karya kuma yasan fadin abinda ke cikin ranshi will ruin this perfect moment</p><p>"Baby muje muyi wanka..." Yafada kaman baiji tambayan datayi mashi ba, itama basarwa tayi ta mike daga kanshi don yana daga cikin abinda aka fada mata kan she should not priy in the affairs that he didn't ask her to.</p><p>[3:22PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挍馃挋鉂ゐ煐ゐ煉滒煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挍馃挏馃挌馃枻鉂ゐ煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat( ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>1鈨�5鈨�</p><p><br /></p><p> Sannan tasan shisshigi yana kawo matsala tsakanin maaurata, amma she don't want him to have anything important to attend to apart from her, shima mikewa yayi ya dauketa sai bathroom dinshi kasancewan a part dinshi suke.</p><p><br /></p><p>The following day bayan an kawo masu breakfast sunci ya fara shiryawa cikin wasu native wear, mufida zama tayi bakin gado tana kallon yanda yake shirya kanshi sai perfumes kala2 yake fesawa, Kawai sai ta fara tunanin wurin budurwa zashi, yana kallon yanda take kallon shi ta mirror, saida ya gama yazo inda take zaune</p><p>"Baby zanje family house in dawo..." Yafada mata yana shafa kanta da bai gama drying ba, marairace fuska tayi</p><p>"Baby ina zuwa..." Da Sauri yazid yace</p><p>"No..ki.kwanta ki huta bazan Dade ba..." Yafada mata babu wasa don kar ta jajirce kan zata bishi, da Sauri mufida tace</p><p>"Pls baby banason kwantawa...I want to follow you...banason zaman gidan ni. Kadai...it's lonely..." Tafada kaman zatayi kuka, daure fuska yayi</p><p>"Wai in banda abinki...kin taba ganin inda amarya taje gidan in-laws dinta just one week after wedding?..." Da Sauri tace</p><p>"Ai ba wani abun bane...pls baby kaje dani...I don't want to stay with out you...pls...." Tafada tana kokarin kuka, komawa gaban mirror yayi yana gyara hulan kanshi yana cewa</p><p>"You better start learning don in nayi resuming office ai ba dake zan dinga zuwa ba...." Da Sauri ta mike ta kama bashi waist ta baya</p><p>"Dan Allah kaje dani..." Tafada tana fashewa da kuka at the same time tana kokarin squeezing kayan jikin shi ya gane manufar ta, she wants to turn him on don ya fasa,</p><p>"Stop it!!!..." Ya daka mata tsawa, da Sauri mufida ta firgita ta koma baya tana kara fashewa da kuka,</p><p>"Yanzu baby don nace zan bika shine kakeyi min shouting?..." Ta fada cike da mamaki don bata taba jin shi so tensed ba, kara daure fuska yayi</p><p>"Kar ki kara ce min ina shouting... Ni mahaukaci ne da zaki ce min am shouting?..." Da Sauri ta girgiza kai tare dacewa</p><p>"Am sorry..." Yacigaba dacewa</p><p>"Fadawa babba he's shouting is an insult..and I won't tolerate that..." Yafada mata still yana fada , yana hakan ne don ta fasa cewa zata bishi don har cikin ranshi yanason zuwa daita amma ba gidan zai fara zuwa ba.</p><p>"Nace am sorry..." Ta sake fada mashi amma deep down tana tunanin why is he shouting at her Sannan tana mamakin shi cos batasan he can be like this in just a minute ba. Rungume ta yayi tare da yimata kiss, </p><p>"Am sorry too...ki kwanta kinji...bazan dade ba.. In case an kawo lunch ban dawo ba just eat with out me..." Ya fada mata yana goge tears dinta. Kaman tace har zai kai lokacin lunch waje? Amma sai tayi shuru tayi nodding Kawai. Ko rakashi batayi ba ta koma part dinta cikin ranta baki wulik cos tana tunanin wurin budurwa zashi, in ta tuna how breath taking he was looking before he lives the house sai ta fashe da kuka, bakin window taje ta tsaya tana kallon shi yana waya sai ta koma ta kwanta tana hawaye. </p><p>Yazid NA fita ya kira Salem don jin inda zai sameshi Sannan ya shiga motanshi ya fita daga gidan.</p><p><br /></p><p>Abangaren dija kam night mare dinta ya fara raguwa don cikin wannan satin sau uku Kawai tayi inda ammi take tunanin Maganin Malam Baude ne yake aiki not knowing it's a coincidence. Yanzu ta fara manta abinda yayi mata don yanzu sai ta kwana daya bata abun bai fado mata ba sabanin da da take tunawa every now and then</p><p>Har lokacin kuma babu Wanda ta fadawa abinda ya faru, at times in age mate dinta sun zo wurin mega business dinsu takan ji kaman ta fada masu abinda ya faru amma sai ta tuna yace kar ta fadawa kowa sai tayi shuru, one thing ammi ta lura daita tunda ta dawo daga birni shine attitude dinta ya chanza don yanzu bata halin yarinta kaman yanda ta saba kuma yanzu tana wanka kullum sabanin da da sai ammi ta dinga maimaitawa kafin tayi. And one more thing about her da babu wanda yasani shine she's a good artist, ta Iya Zane sosai don yanzu in ta tuna abinda yayi mata sai taga face dinshi yana yi mata yawo so sai ta dauki small stick tana zana face dinshi cikin kasa tana gogewa, sai ta zana shi kusan sau goma arana in tana zaune wurin kayan saidawan su. Shi kan danmusa har yanzu yana nan kan zai aureta amma the most funny thing shine in yazo sai ta kurawa gabanshi ido tana kallo ko kadan bata blinking don tanason ta tabbatar shine wannan mutumin ya tura cikin ta, amma sabanin abinda ta ga gaban wancan bata ganshi gaban Dan Musa ba hakan yasa tayi labelling danmusa not as dangerous as yazid her dodo don ita bata San sunan shi ba dukda asabe ta taba fada mata sunan shi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana zuwa office din Salem ya fada mashi plan dinshi da kuma taimakon da yakeson yayi mashi, kallon mamaki Salem yayi mashi</p><p>"Wai har yanzu baka mance da wannan maganan ba?... Haba pls forget about her...Kawai haka Allah ya kaddara.." Yazid bata rai yayi</p><p>"Ka dai San you are not my only friend.. The fact that nayi choosing dinka should not let you talk to me anyhow... In bakason taimaka min no problem..." Yafada cikin sanyin murya, Salem kura mashi ido yayi yana mamaki halin yazid da kafewa,</p><p>"Bawai banason taimaka maka bane...what will people think the whole you getting married to an underaged gal..." Bai idaba yazid ya katse shi dacewa</p><p>"I don't care...can't you understand?... I love her..." Yafada da karfi sosai, yacigaba dacewa</p><p>"Wannan yan kwanakin mufida have really tried that ina Iya mantawa da kowacce ya Mace apart from her amma Wallahi Yarinyan nan tana cikin raina..." Yafada kaman zaiyi kuka, shuru yayi for a while sannan yacigaba dacewa</p><p>"I even think I might love her more than mufida...don duk abubuwan da mufida keyi mun bai hanani tunanin ta ba...am.sorry if I disappoint you amma I don't tell my heart whom to love..." Ya karasa maganar yana dora kanshi kan desk din gabanshi, shidai Salem kallon shi Kawai yake, jin yazid ya fashe da kuka yasa shi mikewa, inda yake zaune yana kuka yaje ya dafa shoulder dinshi</p><p>"Wallahi har yanzu wannan abun yana bani mamaki...kodai Yarinyan ta fadawa iyayenta abinda kayi mata kuma sun daure soul dinka?..." Salem Yafada cike da mamakin wai ga yazid zaune yana kukan small gal alhalin yana da big gal agida at is disposal, yazid daga kanshi yayi yana hawaye ya galla mashi harara</p><p>"Soul din ubanka aka daure..." Yazid ya fada mashi Sannan ya maida kanshi kan desk ya cigaba da kuka, Salem Dariya yayi yana cewa</p><p>"Ai maganar gaskiya..kasan yan kauye da voodoo...ni ina tsoron abinda zai biyo baya in sun Hajiya sun gane abinda ya faru tsakanin Ku..."</p><p>"I don't care...Kawai I want to see her..." Yafada Ahankali, Salem kura mashi ido yayi for a while Sannan ya koma kan desk dinshi ya tattare kayan aikin shi waje daya. Ya dauki wayanshi ya saka cikin aljihunshi </p><p>"Muje..." Ya fada mashi, Ahankali yazid ya daga kanshi tare da kara hararanshi ya mike ya shiga bathroom dake office din, salem na kallon shi yana cewa</p><p>"Cikin sati biyu kayi disvirgining yan mata biyu ba dole ka shiga irin wannan halin ba,...hege Kawai..." Yafada in a funny way...." Yazid banza yayi dashi ya shiga ya wanke face dinshi sannan ya fito suka kama hanyan family house din yazid</p><p>wajen 12 suka isa bakin gate dinsu , da motan yazid Kawai sukazo, </p><p>"Ga Dan akuyan...." Wannan maigadi dake zargin shi ya fada cikin ranshi yayin da yake bude masu gate. Ko gaidashi baiyi ba kaman yanda ya saba suka shiga ciki, ko parking kirki basuyi ba suka fito. Yasan dad dinshi bai gida a wannan lokacin so direct part din Hajiya babba suka shiga inda suka tarda almost kowa a nan harda Hajiya karama, Hajiya karama na ganin shi ta saki guda tana cewa</p><p>"Dana ya fara maida jikin shi.. Kai alhamdulillah.." Tafada, yazid kam Dariya yayi kanshi kasa, Hajiya babba kam kallon carbon copy dinta Kawai take tana jin dadi cikin ranta don gani take ta fi sonshi kan duk yaranta, durkusawa sukayi suka gaidasu suka amsa, duk yaran suna school don haka babu wata hayaniya falon. Zama sukayi mai aiki tayi serving dinsu da abun sha, yazid kam bai amsa ba ya zauna yana jiran Salem ya fara magana. </p><p>"Wai ina ka barta?..." Hajiya karama ta tambayeshi, Ahankali ya fara cewa</p><p>"Tana gida..."</p><p>"Why baka zo daita ba?..." </p><p>"Ai Salem ne yace in rakoshi yanason ganin ki..." Hajiya karama kallon Salem tayi </p><p>"You mean ni?.." Ta tambayeshi, Ahankali Salem ya gyada mata kai kaman gaske, gyara zama tayi</p><p>"Hope dai lafiya..." </p><p>"Eh Hajiya...wata alfarma ce nakeson kiyi min..." Salem ya fada kanshi kasa, shidai yazid ba haka yaso ba, Salem zai fara magana yazid yayi saurin cewa</p><p>"Bari inyi excusing dinku..." Yafada yana mikewa, gaban Mom dinshi yaje, ya kama mata hannu,</p><p>"Momcy muje muyi wata hira..." Ya fada mata, Ahankali ta mike kasancewan tana da Dan jiki, bedroom dinta suka shiga ya juyo ya kalli Salem yayi mashi sign din pls don't fuck up.</p><p>Suna tafiya Salem ya kalli Hajiya karama Sannan ya fara cewa </p><p>"Daman Hajiya...last three weeks Dana zonan....naga wata yarinya...to so nayi tambaya aka fadamin yar aikin kice..." Baki Hajiya ta bude tana kallon shi don Sam bata gane inda ya dosa ba, Salem yacigaba dacewa</p><p>"To sai na tambaya akace min ta tafi..." Da Sauri Hajiya tace</p><p>"Pls I don't understand what you are talking about... Me kake nufi?..." Ta tambayeshi impatiently, </p><p>"I am talking about khadija..." Sai lokacin Hajiya ta gane</p><p>"Ohhh..." Tayi exclaiming, Salem yacigaba dacewa</p><p>"Dan Allah address dinta nake nema ko Allah yasa kin Sani..." Ya karasa maganar yanajin kaman an cire mashi wani irin mountain daga kanshi saboda irin aikin da yazid ya saka shi, gashi yana son Maryam yar Hajiya karama amma gashi yazid ya tisa shi gaba kan yayi wannan karyan, Hajiya kam kallon shi Kawai take tana mamakin me yake nufi,</p><p>"Hmmm Ashe Kaine sanadiyan korarmin yar aiki... I know you confronted her shiyasa ta kasa zama cos kayi scaring dinta...in banda abinka me zakayi da yar yarinyan da bata wuce 15 years ba?... I think zan baka shawaran ka nemi class dinka kaman yanda bestie dinka yayi and stop wasting your time on little kids..." Ta fada calmly,</p><p>"What a disgrace... Yazid ka gama dani..." Ya fada cikin ranshi, Hajiya tacigaba dacewa</p><p>"And about her address gaskiya bani dashi don jiya2 nan NA goge number matar data kawo min ita... Pls don't feel as if na hanaka address dinta...am sorry I can't help.." Ta fada mashi Ahankali, da Sauri Salem da kunyan duniya ta isheshi yayi Sauri cewa</p><p>"Ba komai... Nagode..."</p><p> Yafada kanshi kasa Allah Allah yake yazid ya fito su tafi yaci uban shi, sunfi minti talatin zaune yazid bai fitoba suna cikin bedroom din mom dinshi suna labari daman mom dinshi tana mugun son samun time dashi kadai.sai hira suke amma yana aduan Allah yasa Salem ya samu address dinta. </p><p>Ganin flashing din Salem yasa shi mikewa itama mom dinshi mikewa tayi suka fito tare, ganin yanda Salem ya sadda kai kasa yasa shi giving up, yana fitowa Salem yayi ma su mom bankwana shima yazid ya fada masu zai koma gida Sannan suka fito tun basu kai wurin mota ba Salem ya fara cewa</p><p>"Wallahi ban taba jin kunya kaman yau ba..." Yafada sounding so furious</p><p>"Am so ashamed... Yanzu kallon mutumin banza su Hajiya zasu dinga yi min..." Yazid dai tafiya yake kanshi kasa gabanshi na faduwa don bai San halinda zai fada muddin bai samu address din dija ba,</p><p>"Pls me ta fada maka?..." Ya tambayeshi muryan shi na cracking tun kafin yaji result amma for sure yasan babu nasara.</p><p>"Tace tayi deleting number wacce ta kawo mata khadija... Could you believe tace in nemi mata kaman naka in aura in bar wasting time dina?..." Salem ya fada cikin takaici, yazid kam bai kara cewa komai ba tunda yaji Salem yace ta goge number yaji komai nashi ya tsaya, jingina yayi jikin mota sai hawaye Salem kam shiga yayi cikin motan yana jiran shigan shu su tafi amma yazid ya tsaya wurin sai kuka yake,</p><p>"Yanzu shikenan?..." Ya tambayi kanshi, </p><p>"Yanzu NA lalata mata rayuwa haka nan kenan?..." Yafada cikin kuka, Salem bude motan yayi ya sake fitowa ya kalli yanda yake kuka</p><p>"Haba yazid...kaman bakasan kaddara ba?...you know if she's destined to be with you Allah zai kara hadaku...ps let's go...try and forget about what happened... Many people have done worst..." Da Sauri yazid yace</p><p>"Am not many people... I am me...kan yanda mu yan north muke..in har ta auri wani kallon karuwa zaa dinga yi mata..." Hannu Salem ya daga mashi</p><p>"Pls is OK....after all the gal is just 13...kilan kafin tayi aure wurin zai koma normal..." Da Sauri yazid ya girgiza kai</p><p>"Not after what I did to her... NA shiga uku...ya Allah why me..." Yafada yana kuka not minding in wani Dan gidansu zai ganshi yana hawayen. Dariya Salem yayi</p><p>"Wato kayi mata dalla dalla kenan.. Well brother take heart...just go and ask for Allah's forgiveness... Kawai shawaran da zan baka kenan..." Cikin kuka yazid yace</p><p>"What about her own forgiveness?... What about the love I have for her?..." Yafada cikin matsanacin kuka,</p><p>"Take that as the punishment of what you did to an innocent gal...and remember hausawa sunci in so cuta ne hakuri ne Maganin shi...so kayi hakuri nasan tunda kana da aure nan gaba kadan zaka manta ta..." Salem ya fada mashi in a comforting tune, zagayawa yayi ya bude driver seat ya shiga tare da zare keys daga hannu yazid. Ahankali yazid ya zagaya ya zaune amma har lokacin bai bar kuka ba. Har suka yi sallan zuhr yazid yana hawaye yana fadawa Allah damuwanshi dukda he's feeling he's not worthy Allah ya amshi aduan shi.</p><p> Kafin su kai gidan yazid was around 3 kuma by then idanuwanshi sunyi mugun kumburi da ja abinka da farin mutum. Salem na parking ya kalli yanda yake shessheka kaman wani Dan karamin yaro,</p><p>"Ni mamaki kake bani...kilan the gal in question ta mance da abinda ya faru amma kai kana nan zaka kashe kanka...." Da Sauri yazid yace</p><p>"Ina tausayawa kaina ne...sannan ina tausayawa khadija cos she will never forget she was molested for the rest of her life...and nasan duk lokacin data tuna sai ta tsine min...Salem ina zani da wannan alhakin?..." Ya tambayi Salem yana kara fashewa da kuka, duk jikin Salem mutuwa yayi don yanda yazid ya hada kai da gaban motan yana kuka, Kawai jw wish they is something he can do, he wish he van make him stop amma shima baisan abun yiba,</p><p>"Da kana da pic dinta da sai in tura katsina a nemota..." </p><p>"Bani dashi...." Yafada cikin kuka. Yafi additional minti talatin yana kuka Salem na rarrashin shi amma baiyi shuru ba sai saida yaji kanshi na wani sarawa Sannan ya fita tare da fadawa Salem ya tafi da motan daga baya ya kawo mashi tunda babu inda yake zuwa.</p><p><br /></p><p>Tsayawa yayi ya goge face dinshi bayan ya shiga compound dinshi don kar mufida ta gane yayi kuka.</p><p>Itama mufida tunda ya fita take kuka don gani take yana chan suna soyewa da budurwan shi, har karfe daya tana kuka, kwantawa tayi bacci yayi gaba daita, sai karfe 2:30 ta farka taga har lokacin bai dawo ba, kuka ta farayi, itama idanuwanta sun kumbura saboda kuka. Sai da tayi mai isanta Sannan ta shiga bathroom tayi wanka tare da alwallah Sannan ta fito tayi salla. Ko mai bata shafa ba ta shirya cikin wasu material mai kyau da tsada. Falo ta dawo ta zauna, tana zama da minti biyar aka kawo lunch daga gidansu yazid, amsa tayi ta ajiye kan dinning tana tunanin yanzu duk abinda takeyi mashi bai wadatar ba kenan tunda har yana zuwa wurin wata, Kawai sai taji wani irin haushin shi, kuma still sonshi ya rinjayi tsanan da take mashi. Ahankali ta mike ta koma bedroom dinta ta kwanta tana tunanin abinyi don ko.a mafarki batason kishiya don she's so afraid taga yazid dinta in the arms of another woman. </p><p><br /></p><p>Hankali yazid ya shiga main falo yaga babu kowa. Direct part dinshi ya shiga ya sakarwa kanshi ruwa yana aduan Allah yasa jar ta gane don yasan har ga Allah mufida tana kokari don haka ko kadan bai son ya dameta da matsalan shi. Fitowa yayi daure da towel har lokacin bai barjin ciwon kan ba. Shorts ya dauko ya saka Sannan ya ya dauko very light jallabiya ya saka don ko kadan baisan abu mai nauyi. Part dinta ya shiga yaga babu ita a falon, direct daya daga cikin bedroom dinta ya shiga yana ganta zaune kan gado looking depressed, Ahankali ya taka ya shiga da sallama muryan shi na rawa, da Sauri ta daga swollen eyes dinta ta kalleshi tare da mikewa, kallon yanda idanuwanta duka kumbura yayi, itama kallon nashi idanuwa take, hannuwanshi ya bude mata ta fada ciki tare da fashewa da kuka, </p><p>"Am sorry I made you cry..." Yafada yana shafa kanta, Kawai sai shima ya fashe da kuka</p><p> Mufida saurarawa tayi don jin is he really crying, daman idanuwanshi suna yi mata kama dana Wanda yayi kuka sai kuma tace kilan wani abun ya fada mashi cikin ido cos batasan abinda zaisa grown up man kaman shi kuka ba, sai taji yana kuka ya rungume ta gam, Ahankali ta daga kanta daga kan shoulder dinshi tana kallon, Ahankali ya sulale kasa tare da hada kai da gwaiwa yana kuka, mufida kwalo idanuwa tayi tan kalle2 cikin dakin, ban da Kukanshi babu abinda ke tashi, ahankali mufida ta durkusa kasa gabanshi tana kallon shi, hannu ta Dora kanshi tana cewa</p><p>"Baby what happened?..." Ta tambayeshi cikin sanyin murya, bai amsa ba ya ciigaba da kuka, itama fashewa tayi da kuka din ba karamin tashi hankalin ta yayi ba</p><p>"Baby is it me?...wani abun nayi maka?..." Ta tambayeshi tana kuka , da Sauri ya daga kanshi yana girgiza kanshi, sai lokacin mufida ta lura da how swollen his eyes look, </p><p>"No..it's not you...it's me...I have made a very.... Bad mistake... And it will hunt me...for the rest of my life..." Yafada cikin matsanacin kuka, mufida Bata so jin mistake din da yayi ba cos kukan shima ya isheta tashin hankali, da Sauri ta rungume shi tana shafa bayanshi, shima riketa Gam yayi yana cewa</p><p>"Am sorry.. Babu ask Allah to forgive me?..." Yafada cikin kuka, mufida dai shafa bayanshi kawai take tana tunanin what could it be, ko two timing dinta dayayi ya ga baiyi daidai ba yazo yana kuka, tunani kala2 ta dingayi tana shafa bayanshi don ita data cika tana jin haushin shi dai ta koma rana tausaya mashi,sai wata zuciya ya dinga raya mata kilan budurwan ce tayi mashi wulakanci. Dan daina kukan yayi ya kalleta</p><p>"Baby kin ci abinci?..." Ya tambayeta ahankali, itama cikin sanyin jiki ta girgiza mashi, </p><p>"To muje inyi feeding dinki..." Yafada wet face dinshi dauke da murmushin karfin hali, da Sauri ta girgiza kai</p><p>"I don't have appetite..." Tafada tana zama nan kasan tiles, ahankali ya mike, tare da kama mata hannu</p><p>"Stand..." Yayi commanding dinta, ahankali ta mike, yana rike da hannun ta har kan dinning, mufida kam har yanzu bata bar mamakin abinda ke faruwa ba. Kan dinning ya zaunar daita ya fara Bata abinci tana amsa amma duk yanda tayi yaci kinci yayi daga baya itama tace bataci, dole yayi forcing dinta taci har to koshi Sannan ya shiga bathroom ya dauro alwallah, falo ya dawo ya tarda ta zaune tayi tagumi tana tunanin ganin ya fito zashi masjid yasa tace</p><p>"Baby..your face showed you are sad...pls kar kaje masjid kar ya zama kaman we are having some marital problems..." Ta fada mashi cike da so da kauna, murmushi yayi yana gyara hannun jallabiya daya nade kafin yayi alwallah,</p><p>"Don't worry.. I will be OK..." Ya fada mata tare dayi mata kiss a goshinta Sannan ya tafi. </p><p><br /></p><p>A wannan ranar yazid bai ci ko sha ba har dare, ba karamin tashi hankali mufida ta shiga ba, ha yanda kanshi ke sarawa Sannan ga fever daya rufeshi amma Kiri kiri yaki shan drugs, rufe kanshi yayi da blanket yana rawan sanyi. Aranar sai ya kasance a very bad day for him don gani yake its over for him. The following day ya koma family house ya sanar da iyayenshi zai koma abuja, data alkhairi sukayi mashi Sannan ya fadawa mufida ta shirya zasu koma abuja the following day. Nan hankalin mufida ya kwanta don har lokacin gani take rabuwa sukayi da budurwan da yake ce mata zai aura. Amma kuma abinda ke Bata haushi shine ta tabbatar yanason wannan budurwan don komai nashi yayi tsaye chak</p><p>[3:23PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挌馃挋鉂ゐ煐ゐ煉滒煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挋鉂ゐ煉涴煐ゐ煉滒煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat(ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>1鈨�6鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>One, two, three, four, five months have gone by da faruwan abun, duk Wanda yasan yazid the last months in ka ganshi yanzu sai ka rantse ba shi bane, don ya rame sosai daman ba kiban gareshi ba amma raman shi na yanzu is far worst, sau uku suka je Kano da mufida, duk zuwa sai dad dinshi dasu Hajiya sun tisashi gaba kan ya fadi abinda ke damunshi amma sai yace masu babu komai, sau biyu yana amsan sick leave daga wajen aikin, shi dai gani yake kilan Allah is really punishing him for devouring an Allah's property, he Kawai ji yake ya mutu ya huta, mufida kam ga Hutu ga komai amma tunda tana murna kilan rabuwa sukayi da budurwan shi har ta fara tunanin is better ta dawo suyi aure don kar ta rasa mijinta, dukda yazid na kokari sosai don kar ya shiga hakkinta amma ganin shi zaune a falo duk dare yana kuka is so unbelievable for her that she wishes he do what ever makes him happy, sau biyu Salem NA zuwa katsina yana Neman masu kaiwa mutane yan aiki yana tambayan su khadija amma sai suce basu Santa ba, ba komai yasa yake hakan ba is done kar ya rasa abokinshi cos duk inda yake tunani yazid yafi haka. A office kam sultan abokin aikin shi and bestie dinshi a abuja yayi mashi tambaya har ya gaji ya sa mashi ido, din countless times hakan ganshi zaune a office yana hawaye. </p><p><br /></p><p>Yau ma yana zaune a office ya hada kai da desk ba kuka yake ba amma he's so lost in his thoughts, shi gani yake kilan khadija is not human, Kawai Allah ya turo ta don ta nuna mashi ishara kan yanda komai abokanshi sukayi sai ya kushe, don gani yake ko matanda ka aura Allah yayi mata rasuwa within five months ya kamata ka fara healing amma nashi kullum heart dinshi is going bad saboda ita</p><p> Kullum ji yake kaman ya mutu ko Allah yasa ya huta cos its so unbelievable,</p><p>"Ya Allah pls just take me..." Yafada ahankali,</p><p>"Am tired... My heart hurts so bad....am tired....so tired...." Ya sake fada muryan shi na rawa amma bai yi kuka ba, da Sauri ya daga kanshi</p><p>"No I won't cry..." Ya fadawa kanshi da sauri</p><p>"Crying won't solve a thing...." Yafada sounding strong and firm, yana nan zaune sultan ya shigo da wasu files, har ya bude kofan bai San ya shigo ba har saida ya Dan bugi desk kaman yanda ya saba Sannan ya daga kanshi ya kalleshi. Zama yayi tare da ajiye file din,</p><p>"Pls na rokeka da Allah ka fadamin abinda ke damunka?... In kuma baka fadamin ba yanzu I promise bazan kara tambayan ka ba in har baka fadamin abinda ke damunka ba yanzu...." Ya fada a hausanshi irin na yan jos, yazid zama yayi idanuwanshi lumshe yana Dan juyawa cikin kujeran da yake, ko kadan bai da niyyan samun third party a wannan maganan so haka yasa yace</p><p>"Am OK....amma I think zanyi resign...." Da Sauri sultan yace.</p><p>"What?...hope you don't mean what you are saying?.." </p><p>"I mean it...I haven't been doing my job properly this days... So I think zanyi resigning...." Kai sultan ya dinga girgiza mashi,</p><p>"Don't do this...you are about to start a family... Kar ka zama daya daga cikin masu dogaro da dukiyan iyayensu...." Inji sultan, yazid dai NA zaune har lokacin bai bude idanuwanshi ba, yasan maganar sultan is right, amma tunda mufida is not yet pregnant yasan maybe kafin ta samu ciki ta haihu everything will be alright, kuma yasan yana da enough a account dinshi</p><p>"Pls don't do this...don't let what ever situations you are in take you down...bansan abinda ke damunka ba amma your depression is too much... Haba..." Yafada mashi, yazid murmushi Kawai yayi yana jin how he wish he can control what his feeling</p><p>"Nagode..." Kawai ya fada mashi har lokacin bai bude idanuwa ba. </p><p><br /></p><p>Bayan yayi closing daga office ya cire suit dinshi ya rage dagashi sai long sleeve shirt, mota ya shiga ya tafi gida yana tunanin maganan sultan da yayi niyyan ya ajiye aikin yaji da abinda ke damunshi, parking lot ya ajiye motan ya shiga lifter don zuwa apartment dinshi don har lokacin yana CBN quarter, bakin kofan su ya tsaya ya daidaita kanshi as usual Sannan ya danna doorbell, mufida ce sanye da long gown ta bude kofan, hannuwa ya bude mata yana murmushi ya sakar mata, ahankali ta fada jikinshi Sannan ta gaidashi tare da tambayan shi aiki, ya amsa mata kaman lafiya lau.</p><p>"My baby me kika dafa?..." Ya tambayeta yana shiga cikin falon Sannan yana rungume daita, hararanshi tayi</p><p>"Sai kace ci kake..." Ta fada kaman zatayi kuka, </p><p>"Ina ci mana...yanzu zokiyi feeding dina...." Yafada ahankali yana janta wajen dinning data jera abinci, Zama yayi ya ya jata kan cinyanshi,</p><p>"Nasan baki ciba... Bari in fara feeding dinki..." Ya fada mata, da Sauri ta mike </p><p>"No...haka kake cewa kullum amma daga baya haba CI kake ba...ni am tired... In ni ce bakaso I will go...am tired...." Tafada tana fashewa da kuka, yazid zama yayi yana kallon ta don yasan in har ya rasa mufida mutuwa zaiyi saboda ba karamin comforting dinshi take, mufida matace ta gari, samun mace mai hakurinta a wannan zamanin sai an tona, Sannan ga Iya tattalin miji ga juriya da hakuri</p><p>"In ni bakasona na hakura...Allah zai bani mai sona...tunda kafi sin khadija fiye dani..." Idanuwa yazaro yana yi mata kallon mamaki, </p><p>"Who is khadija?..." Ya tambayeta kaman baisan abinda take nufi ba, wani irin harara tayi mashi</p><p>"Ohh...bakasan wacece khadija ba?..." </p><p>I will kill Salem for this..." Yafada cikin ranshi thinking shi ya fada mata,</p><p>"How many times kake kiran sunan khadija while sleeping?... How many times kake kiran khadija while we are making love...is it because am not saying anything?... That is because my mother told me that marriage is all about patient... Am nagaji.." Tafada cikin matsanacin kuka, nan take jikin shi yayi sanyi, da Sauri ya mike zai rike ta, da Sauri itama ta ja da baya</p><p>"No...stop...it..." Ta daka mashi tsawa, tsayawa yayi</p><p>"Kasan inda NA fito...am sure bazakace saboda abun hannun ka nake sonka ko bearing duk abubuwan dake faruwa ba...and am sure no woman will take this..so I have made up my mind...."</p><p> Tafada tana juyawa, hanyan bedroom ta nufa don da tana ganin what ever zatayi bearing amma yanzu she us feed up, bai cin abinci, bai baccin kirki da dare kuma the most annoying part shine duk family sai su tambayeta meke damun mijinki, tana shiga ta dauko wata katuwar bag, da Sauri shima yazid ya shiga dakin yaga da gaske parking take, ahankali ya isa bayanta yayi kneeling tare da riko waist dinta yana kuka</p><p>"Baby don't leave me...in kin tafi mutuwa zanyi...you are the nicest thing that happened to me this past few months... Am sorry.. Wallahi I love you... Than Allah kiyi hakuri.." Yafada yana kuka, mufida shuru tayi tana hawaye tana sauraron shi, </p><p>"I made a mistake and it's killing me..." Yafada cikin kuka, da Sauri ta juyo</p><p>"Wane mistake ne Wanda ni bazaka fadamin ba....wane mistake ne bai kamata kayi sharing dani ba...I thought marriage is for better for worst according to my mother... Remember you once told me you want a truthful relationship... Pls tell me..." Tafada tana rike da hannun shi dake rike da waist dinta, da Sauri ya girgiza kai</p><p>" I can't tell you... You will hate me..." Ya fada cikin kuka, itama girgiza kai tayi</p><p>"No I won't...I promise..." </p><p>"Pls don't make me say it...I know you will dispise me...pls am sorry..don't go..." Yafada cikin matsanacin kuka har lokacin yana rungume da waist dinta, itama cikin kuka tace</p><p>"I promise I won't judge you...Dan Allah kayi sharing dani...the burden is to much for you alone.... Trust me ko.mutum ka kashe I won't tell a soul..." Tafada tana shafa wet face dinshi</p><p>Kura mata ido yayi yana kallon ta, bayason abinda zaisa ta tsaneshi cos she's a one in a million, </p><p>"Am sorry... I raped a gal...." Maganar tayi escaping daga bakinshi, kura mashi ido tayi don tabbatar he's not joking</p><p>"I raped a 13 years old gal..." Ya sake fada cikin matsanacin kuka, ahankali mufida ta fara baya2 har saida ta zauna kan gado Sannan ta fashe da wani matsanacin kuka, da rarrafe ya isa inda take zaune, knees dinta ya dafa tare da Dora kanshi kan kafan ta yana kuka</p><p>"What haven't I done to make you happy?...why do you have to do that?... I even suck you even though I hate it..." Tafada cikin kuka, da Sauri yace </p><p>"It was before our marriage..." Yafada don ya nuna mata ba bayan auren su hakan ya faru ba. Cikin kuka ya fada mata komai, tana hawaye tana jin haushi da kishi amma she promise not to judge him,</p><p>"NA rasa sukuni tun lokacin..." Yafada mata kanshi kan kafanta don kunyan hada ido da ita Kawai yake ji, amma it's better yaji na duniya dayaji NA lahira, mufida shuru tayi abubuwa da dama na running through her head, kullum tana alfaharin ita ta cire mijinta cikin Leda dukda lalacewan zamani Ashe she's wrong, wata yar 13 ta rigata saninshi, Sannan he has been attached to her,</p><p>" kilan ma she's better than me in bed.." Ta fadawa kanta cikin ranta, ita ba zanin da molesting yar mutane da yayi ke matsalan ta ba, Kawai she thinks khadija is better than her in bed, kara kallon shi tayi,</p><p>"So ta fi ni yi maka Zuma kenan..." Ta fada mashi, da Sauri ta daga kanshi ya kalleta, don bai gane abinda take nufi ba,</p><p>"Yes mana...kafi jin dadin ta that's why you always want more..." Tafada tana mikewa daga inda take, Kawai sai dariya ya kufce mashi for about 2 to 3 seconds Sannan yace</p><p>"Is that all you could say?..." Yafada amma deep down yasan she's not far from the truth, don the way he tear her in a gentle way still lingers in his brain, it will be among his best moment though it was sinful.</p><p>"Yes mana...in ba haka ba why will you still be crying?..." Ta tambayeshi not caring about the sin and atrocities.</p><p>"Haba baby..am being human... Nayi molesting yarinya..and all you could say Was about the sweetness?..." Ya tambayeta sounding surprised</p><p>"To in ba haka ba why all the trouble?.. Wasu sai suyi hakan su dubu amma nobody knows..."</p><p>"Haba baby am not anybody.. Ina da conscience...and remember kinyi min alkawarin bazakiyi judging dina ba...."</p><p>"Am not judging you Kawai am jealous da wata ta rigani sanin ka..and I know how men like small children..." Dariya yazid yayi da wet face dinshi</p><p>"baby you are incredibly funny..." Yafada yana crawling zuwa inda take tsaye hannuwanta harde kan chest dinta, riketa yayi ta tureshi, kara riketa yayi</p><p>"Baby in fada maki gaskiya?.." Ya tambayeta, banza tayi dashi tana kokarin kwace kanta daga rikon shi, </p><p>"Baby you are the juiciest, sweetest, hottest...again juiciest lady on earth.. Nobody can beat you to that...kar kiso kiji yanda kike wa brain dina..." Yafada yana kiss laps dinta dake cikin kaya, mufida kauda kanta gefe tayi ta Dan saki murmushi dukda she don't believe him amma Hus statement matter a lot to her, </p><p>"If am as you said...why this days sai kaga ina bukatan ka kake nemana?..." </p><p>"banason takura maki ne...amma I promise yau ni zanyi komai... Basai kinyi komai ba..let me do all the working..." Yafada yana kissing din kafanta, shidai har yanzu bai bar mamakin attitude dinta ba, </p><p>"Yanzu baby Kawai ki tayinida adua Allah yasa in ganta..." Kallon haushi da takaici tayi mashi </p><p>"Kayi mata me?..." Ta tambayeshi atakaice</p><p>"In nemi yafiyanta don kar ayiwa yaranmu abinda nayi mata...." Yafada cikin sanyin murya, </p><p>"Sorry kaji...nidai bana nan lokacin da kaji dadin ka so I will pretend baka fadamin komai ba..." Tafada tana kokarin barin dakin, mikewa yayi ya rikota,</p><p>"Haba the juiciest one ina zaki....zo ki fadamin how am I in bed..."Yafada yana wullata kan gado</p><p> Da Sauri ta mike, tana hararanshi tana cewa</p><p>"Ni ka kyaleni..." Tafada tana sauka daga kan gadon, </p><p>"I want you..." Yafada yana Kara turata kan gado, kara mikewa</p><p>"Ka fara cin abinci..." Tafada cikin haushi, </p><p>"Ni ke nake bukata..." Yafada kaman zaiyi kuka, baki ta tabe, ta mike abinta, bin ta yayi da kallo ta juyo ta watsa mashi disgusting look Sannan ta fita daga bedroom din.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abangaren dija kam duk Wanda ya Santa last five months bazai yarda itace ba don abubuwa da dama sun chanza dangane daita, yanzu ta kara girma farat daya boobs dinta sun ciko Sannan ta kara haske sosai, duk Wanda zai ganta zai szan tana da ciki amma dayake ba aure gareta ba so ake tunanin kilan don yanzu ta bar talla shiyasa take chanzawa, babu Wanda ya sani har ammi Kawai dai tana mamakin yanda take cin abinci don in ta zauna wajen kayansu ta dinga kashe kudin ke nan wajen kayan zaki, sau biyu ammi na dukanta kan haka amma she can't help, duk fadan da ammi zatayi mata ba ta dainawa sai in dai Bata ga mai tallan awara ko su sweet ba. Yanzu kam ko tuna abinda ya faru tsakanin ta da yazid batayi she's over it. Duk dare da fever take kwana amma da gari ta waye sai ta koma normal, cikin ta bai fito ba sai cibiyanta daya Dan fito da kasan maranta da ya Dan kumburo, duk dare sai Dan Musa ya kawo mata nama kasancewan ta yarda zata aureshi, yauma bayan sun kai kaya waje tana zaune gaban kayan kaman yanda ta saba taga mai zogala, kwada mashi kira tayi Wanda yasa ammi dake cikin gida taji, da Sauri ammi ta leko</p><p>"Dija me zakiyi?.." Ammi ta tambayeta, da Sauri tace </p><p>"Babu komai..." </p><p>"Ba ke kika kira mai zogale ba?..." Da Sauri ta sake cewa</p><p>"Ammi ba ni bace..." Ta fada tana kallon mai zogalan data taho,</p><p>"To ki saurareni da kyau...ki ka kuskura kika sayi abun kwandala so naci uban daya haifeki...kina jina?..." Ammi taja mata kunne, </p><p>"To ammi..." Tafada kaman zatayi kuka, mai zogalan ta iso gurinta</p><p>"Gashi..." Yarinya ta fada, kallon ammi dake tsaye bakin kofan tayi Sannan tace</p><p>"Ba kiranki nayi ba..." Mai zogala tafiya tayi ita kuma ammi ta koma cikin gida, tana ganin ammi ta shige ta mike da gudu ta nufi mai zolaya tana kiranta cikin low voice, gudun da take yi yasa taji wani abu ya tokare mata gaba, da Sauri ta tsaya don kasa moving tayi, Kawai sai taji kaman wani abu NA motsi cikin cikinta, da Sauri ta daga maranta, tafi min biyar tsaye maranta bai saketa ba. Tana kallo mai zolayan ta tafi Bata saya ba, ahankali ta koma ta zauna ko kadan Bata kawo komai cikin ranta ba. Haka nan sai take tunanin ta Dade bata yi wannan jinin sa take duk wata ba. Binto ta kwalawa kira ta fito daga cikin gida rike da cupin kokonta, </p><p>"Ki zauna nan in dawo..." Ta fada mata Sannan ta mike ta shiga gida, ammi dake wanke2 Ta kalla Sannan tace</p><p>"Ammi wannan abun ya bar zuwa..." Tafada da karfi, ammi Bata dago ba tace</p><p>"Me kenan?..." Da Sauri dija tace</p><p> "Wannan jinin dake zuwa ..." Tafada tana babu wani kunya, abinka da Dan fari, sai lokacin ammi ta daga kai ta kalleta, itama shuru tayi tana tunanin yaushe rabo da dija tayi fashin salla dukda janaba na jikinta don tunda yazid ya kwanta daita batayi wanka ba don batasan anayi ba. Ammi dai kura mata ido tayi tana kallon yanda idanuwanta sukayi kal Sannan yanda gashin gaban goshinta ke kwance kaman wata baturiya, idanuwanta ta sauke zuwa kirjinta tana mamakin girman boobs dinta don yafi girman NA yar shekara 14, amma in ta tuna kanwarta dake jos sai tace gado dija tayi wajenta don itama tana dasu sosai.</p><p>"Tun yaushe ke baki gani ba..." Ta tambayeta tana maida hankalin ta kan wanke2 da take don ko kadan Bata saka wani abu cikin ranta ba</p><p>"Na manta...yanzu ammi ina iya daina salla tunda ya bar zuwa?...." Ta tambayeta sounding serious, hararanta ammi tayi tare da Jan tsoki tacigaba da abinda take yi, ita kuma dija ta koma waje tacigaba da minding kayan da suke saidawa, suna ciniki sosai don kasuwan sai kara bunkasa yake din sau hudu ammi NA zuwa karo kaya da kudin cinikinsu. </p><p><br /></p><p>Wajen karfe 4 na maraice dija ta shiga gidan don yin wanka don yanzu duk yamma take wanka ta saka kaya mai kyau saboda zuwan danmusa. Har daya daga cikin perfumes da suke saidawa ammi ta Bata don ta dinga fesawa kafin taje wajen danmusa, a kauyen kam dija tana daga cikin yanmatan da ake gani are classy don yanda take saka kayan da tazo dasu daga birni. Bayan ta gama wanka ta shiga dakin ta zauna ta bawa kofan baya tana shafa mai, daga ita sai inner skirt. Ammi dake kai kawo tsakar gida kallon bayanta tayi sai taga kaman gefen cikinta yayi Dan fadi, tsayawa tayi tana kallon ta sosai </p><p>"Dija..." Ta kirata tana shiga dakin, da Sauri dija ta juyo, idanuwa ammi ta gwalo tana ajiye broom dake hannun ta tana shiga dakin, dija zama tayi tana kallon yanda ammi ke kallon ta, </p><p>"Tashi tsaye..." Ammi ta fada mata, daga sai skirt ta mike tsaye, ammi kurawa maranta ido tayi Sannan tana kallon yanda cibiyanta ya fito,</p><p>"Ammi meye..." Dija Ta tambayeta, ammi Bata amsaba ta karaso wajenta duk idanuwanta waje tanason ta tantance abinda take gani, kallon up and down take mata Wanda yasa itama dijan kallon kanta. Yatsa ammi tasa ta tura maranta taji tauri uta kuma dija ta Dan saki kara saboda zafi, hannu ammi ta Dora ga kai tare da sakin ihu</p><p>"Di...ja...wayayi...maki...ciki?..." Tafada kaman mai asthma saboda yanda numfashin ta ke up and down, dija kara kallon kanta tayi tace</p><p>"Ciki?..." Ta tambaya sounding very surprised, da gudu ammi ta fita waje, kaman mai.Neman wani abu kuma ta dawo dakin batare data dauki wanin abun ba, dija dai tsaye take tana kara cewa</p><p>"Ciki????..." Sai kallon kanta Kawai take tana maimaita same word NA ciki</p><p>"Wa yayi maki ciki?..." Ammi ta fada kaman wata sabuwar cigan mahaukaciya, dija Sam batasan abinda ammi ke nufi ba don a iya saninta tana da ciki mana so batasan cikin haihuwa ammi ke magana ba, jin wani irin mari yasa ta dafe cheek dinta</p><p>"Wa yayi maki ciki!!!!..." Ammi ta tambayeta wannan Karin tana fita waje still da gudu, itacen dake cikin murhun dake ci da wuta ta dauko ta shiga dakin, sai lokacin dija Tasan this is something serious,</p><p> tsalle ta farayi tana kuka</p><p>"Nace wa yayi maki ciki.. Ashe ke yar iska ce ban saniba..." Ammi ta fada tana kwalla mata itacen dake cida wuta, wani irin ihu dija ta saki tana cewa</p><p>"Nima ban Sani ba..." Amma jin ammi ta kirata da yar iska yasa ta fara tuna yazid kuma tana tuna abinda yayi mata, bare back dinta ammi ta kara kwalawa firewood dinta dija ta kara sakin ihu, sai tsosta jikinta take saboda garwashin wutan dake sauka a jikinta,</p><p>"Bazaki fadi ba kafin in kashe ki?..." Ammi ta fada tana harbe cikin ta, nan take dija ta durkusa kasa tana kuka tana dafe da cikin ta</p><p>"Wayyo Allah... Cikina....cikina..." Ta dinga maimaitawa da karfi, </p><p>"Baki fadi?..." Ammi ta fada tana dukanta kaman an aikota, dija sai rusa ihu take Tana kiran cikinta don ammi na harbe mata ciki taji kaman wani abu ya gitta cikin cikinta, ammi na dukanta tana kuka tana cewa</p><p>"Wa yayi maki ciki?..."</p><p> Tafada cikin wata irin murya mai kama dana macen zaki dake jin yunwa, dija dake dafe da cikinta duk idanuwanta waje ta kalli ammi da idanuwanta tana cewa</p><p>"Dan...Allah... Ammi....kar...ki...kashe...ban San...yanda..akeyin...ciki ba..." Tafada kaman mai asthma saboda yanda numfashin ta ke fita da kyar, kan itacen da har lokacin yake hayaki ammi ta kara buga mata, da Sauri ta fara scratching wurin wannan Karin batayi ihu ba saboda azaban da takeji a jikinta yafi karfin ihu,</p><p>"Da wa kike iskanci..." Ammi ta tambayeta, dija rana girgiza kai tana ja baya ko pant babu a jikinta, tana ja baya taga inda ta bari da jini kasa, kara dafe cikinta tayi </p><p>"Wayyo cikina... Mutuwa.. Zanyi...wani...ne...ya...saka..min..wani..abu...." Tafada da kyar, ammi ko kallon jinin kasan batayi ba ta ajiye itacen ta Dora hannu kan, </p><p>"Wani!!!!???...." Ta fada tana tsalle tana kuka, da Sauri dija dake cije lips dinta saboda azaba ta gyada mata kai, </p><p>"A ina?..." Ammi ta sake tambayan ta cikin tashin hankalin da tunda dija take Bata taba ganinta haka ba,</p><p>"A..chan...birni...." Tafada har lokacin Bata bar ja da baya ba Sannan har lokacin hannun ta biyu rike da maranta gam, </p><p>"Daman karuwanci aka kaiki?..." Ammi ta fada tana kara fashewa da wani matsanacin kuka,</p><p>"Karuwanci kika yarda aka kaiki?... Shi yasa aka baki wannan makudan kudin?..." Ammi ta fada tana sulalewa kasa sai kuka Kawai take, dija sai kara ja da baya take saboda yanda ta razana da ammi, sai da ammi tayi kuka ta koshi Sannan ta kalli dija da ta lumshe idanuwa hawaye na zuba, </p><p>"Nace ya bari..banso..." Tafada cikin kuka, ammi kallon tsana kawai take mata, ji Kawai take kaman ta shaketa ta mutu don bakin ciki. Tana maneji da yan marayunta dija ta rasa abinda zata kwaso mata sai ciki,</p><p>"Da bakiso kin fadamin abinda akayi maki?..." Ammi ta tambayeta wasu new tears na rolling, da Sauri dija ta girgiza mata kai Kara dafe cikinta tayi</p><p>"Wayyo cikina... Zafi nakeji..." Tafada cikin kuka, don dukan da ammi tayi mata baiyi mata zafi kaman yanda cikin takeyi mata zafi ba. Jin abu NA zuba daga kasanta yasan ta kara dagawa da kyar daga inda take zaune ta rarrafa ta koma gefe guda. </p><p>"Maza ki tashi ki tattara kayanki ki tafi gidan Matan da ta kaiki karuwaci...." Ammi ta fada babu wasa, sabon kuka ta farayi tana girgiza kanta</p><p>"Ammi...."</p><p>"Ki tashi nace!!!..." Ammi ta daka mata tsawa, da Sauri ta kama bango zata tashi amma ta kasa saboda yanda cikinta ya kara murdawa,</p><p>"Cikina...ammi...ban..Iya ...tafiya...." Tafada tana komawa zaune,itacen ammi ta kara dauka Wanda yasa dija tayi saurin mikewa da kyar, kallon yanda jikinta yayi jajir saboda duka da wuta. Sai jini ke bin kafanta, tana dafa bango ta je wajen bag dinta, dukawa tasoyi don ta saka kayanta amma hakan ya gagara, bango ta kama ta zauna Sannan ta bude bag din da Hajiya aisha ta</p><p> Saya mata ta dauko daya daga cikin kayan da ta taho dasu daga birni ta saka, kallon ammi tayi ta kalli yanda kafanta ya jike da jini, ko kadan babu alaman tausayi tattare da ammi, daga inda take zaune ta dauko pant ta saka da kyar Sannan ta dauki rag Wanda take amfani dashi wajen period dinta ta tura cikin pant din. Ahankali ta mike </p><p>"Ki dauki jikanki..." Ammi ta shaida mata, </p><p>"Ammi ...INA...zani?..." Ta tambayeta tana kuka</p><p>"Ki tafi chan inda aka koya maki karuwanci..." Ammi Tafada in I don't care tune</p><p>"Dan..Allah.. Ammi...kiyi. Hakuri..." Ta fada cikin matsanacin kuka, itace ammi ta kara dauka, da Sauri ta mike tana kara dafe cikinta, tana kuka tana bawa ammi hakuri amma a banza, ammi daukan kudin kayan da tayi niyyan zuwa kasuwa dashi tayi ta watsa mata</p><p>"Ga kudin karuwanciki..." Tafada tana watsa mata kudin, dija Bata kalli kudin ba ta fara tafiya duk kafanta jini, tana kuka ta juyo ta kalli ammi,</p><p>"Kiyi hakuri.. Dan...Allah... Bansan...inda...zanje ba..." Ta fada tana kuka kaman ranta zai fita, </p><p>"Inyi hakuri ki haifamin shege acikin gidan nan?...hakan ba zai taba yuwuwa ba..ki tafi Chan... Ko bani da da ko.daya ban zama da ke...balle inada saura...ban barinki ki Bata masu tarbiyan su...maza ki tafi..." Ammi ta fada mata tana nuna ta da itacen dake hannun ta,</p><p>"Kuma ki.kwace dukkan kudin nan da kayanki...banason in kara ganin ki...ban yafe maki ba...maza ki fitar min daga gida kafin in kasheki...." Ammi ta fada da karfi, sai lokacin su binto dake tsaye bakin kofan suka fara kuka, ko kadan ammi bata kalli karanta dija ba, da Sauri dija ta duka ta fara kwace kudin da hannun ta daya tana kuka, dukan su ta kwace ta zuba cikin bag tayi zipping Sannan ta dauki bag din da hannu daya, dayan hannun ta kan cikin ta, haka ta fita daga gidan tana tafiya ahankali ta kuka, Kawai karfin hali Kawai take tana tafiya amma ji take kaman wani abu zai fado daga gabanta. Tana tafiya ana tambayan ta inda zata amma ko kai Bata Iya dagawa balle tayi magana.</p><p>[3:24PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挌馃挏鉂ゐ煐ゐ煉欚煉�</p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挍鉂ゐ煉滒煐ゐ煉氿煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat(ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>1鈨�7鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kafin ta kai bakin titi har maraice tayi saboda ahankali take tafiya ga ciwon Mara ga duk jikinta zafi ga jinin bai bar zuba ba don ji take kaman rag din data saka yayi wet. Nan bakin titi ta ajiye bag dinta ta zauna sama tana kuka</p><p>"Wallahi sai naje kin fada mashi ya cire min cikin..." Tafada cikin kuka</p><p>"Ke kika kaini gidan...." Take fadawa kanta, tafi minti talatin nan zaune kafin ta samu motan zuwa cikin daura, wayanda ke cikin motan kallon yanda yar karamar yarinya ke kuka Kawai suke sai tambayan ta suke amma Bata cewa komai. Lokacin data isa kofar gidan Hajiya Hajiya Aisha ko gani batayi sosai don har lokacin jinin bai tsaya ba, tana Dan bugawa ta tsaya, jin shuru yasa ta kara turawa sai taji bude yake, cikin gida ta shiga tana kuka, tana shiga Hajiya Aisha tana dawowa daga unguwa, kallon dija dake faman kuka tayi from head to toe ta kwalo idanuwa tana kallon kafan dija dake jini, da Sauri ta karaso wajenta</p><p>"Dija lafiya?..." Ta tambayeta tana kallon bag dinta dake kasa, cikin shessheka dija tace</p><p>"Ki maidani chan gidan ya cire min...." Tafada cikin kuka, kallon mamaki Hajiya tayi mata don Bata gane abinda take nufi ba, Hajiya Bata damu da abinda take cewa ba sai Kara cewa tayi</p><p>"Dija me akayi maki !!..." Ta tambayeta cikin tashin hankali tana daga doguwar rigan dake jikinta tana kara kallon jinin dake kafanta, tana cewa</p><p>"Inna lillahi..." Don anata tunanin raping dinta akayi, dija Bata amsa mata ba tacigaba dacewa</p><p>"Ki maidani..." Bata idaba Hajiya ta ce</p><p>"Wai meke damunki..." Ta daka mata tsawa da karfi, da Sauri ta fara cewa </p><p>"Ammi tace ciki gareni....shine tace inzo ki maidani...a cire min..." Ta fada cikin kuka, idanuwa Hajiya ta kara zarowa</p><p>"Ban gane ciki ba...." Hajiya Aisha ta tambayeta cikin tashin hankali don abinda bai taba faruwa da sauran yaran da take kaiwa gidan aiki bane</p><p>"Wai ina da ciki ammi tace...." Inji dija,</p><p>"Wannan jinin fa?..." Hajiya ta fada tana nuna legs dinta </p><p>"Nima ban Sani ba...." Ta amsa mata,</p><p>"To wa ya fadawa amminki kina da ciki?..." Hajiya ta sake tambayan ta, </p><p>"Nima ban saniba....cewa tayi ina da ciki wai in tafi da jikkata kuma wai Bata yafemin ba...tace kar in kara dawowa..." Hajiya Aisha dai tsayawa tayi tana kallon dija don ko kadan babu alaman ciki tattare daita, </p><p>"Village mentality... In ma cikin gareki sai ta koreki?...to bari ijn tambayeki...kin raba kwanciya da wani?...." Ta tambayeta, da Sauri dija ta girgiza mata kai Sannan tace</p><p>"Wani ne ya saka min wani abu a gabana..." Da Sauri Hajiya tace</p><p>"Waye?..." Cikin kuka dija tace</p><p>"Chan gidan da kika kaini...." Baki Hajiya ta bude tana mamakin abinda ke faruwa, dija kara dafe cikinta tayi, ta fara yarfe hannuwa tana cewa</p><p>"Wayyo cikina..." </p><p>"Me ya sami cikinki...." Hajiya ta tambayeta</p><p>"Ammi ta harbe min ciki..." ta fada cikin kuka, mai aikinta Hajiya ta kwalawa kira, sai tataho da gudu saboda yanda Hajiya ta kirata on top of her voice, kallon dija tayi ta tsorata, umarni Hajiya tayi mata da ta dauki bag din dija su shiga dakinta ta gyara mata jiki zata kaita hospital. Nan suka shiga dakin dija ta shiga wanka sai kuka take dukda muryanta bai fitowa saboda kuka. Hajiya kuma zama tayi falo ta rafka uban tagumi, tana aduan Allah yasa ba hakan bane don batasan abinda zai biyo Bata ba muddin hakan ya zamo gaskiya.</p><p> Mai aikin Hajiya Aisha tambayan ta tayi abinda ke faruwa, dija fada mata komai tayi, fashewa tayi da kuka saboda tausayi don itama taga cikin sanda dija ke saka wasu kayan bayan ta fito daga bathroom, duk pant da rag da dija ta saka ya cike, pad mai aikin Hajiya ta Bata ta nuna mata yanda zatayi amfani dashi. Few minutes later Hajiya ta shigo ta umarceta data biyota, nan suka kama hanyan hospital, inda doctor ya shaida mata da gaske dija na dauke da cikin wata biyar kuma ya Kara dacewa tana bukanta bed rest, don kar cikin ya yamu matsala, hannu Hajiya ta dafa ga kai tana kuka, don gani take dija tayi karanta da sanin namiji balle ciki, kiran dija waje tayi, saida suka kebe Sannan tace</p><p>"Dija tsakanin ki da Allah wa yayi maki ciki?..." Ta tambayeta cikin sanyin murya, sabon kuka dija ta fara tana cewa</p><p>"Nima ban San yanda ake ciki ba..." Hajiya goge hawayen face dinta tayi</p><p>"Wa ya saba saka maki abun fitsarinshi...." Hajiya Aisha ta tambayeta, da Sauri dija tace</p><p>"Wannan mutumin dake gidan da kika kaini ne ya saka min wani abu... Ban San ko meye ba..." Hajiya kara fashewa tayi da kuka tana tuna lokacin da dija ta susuce kan dole sai an maido ta gida Ashe wannan ne dalilin, </p><p>"Nashiga uku..." Hajiya ta fada cikin kuka,</p><p>"Waye daga cikin yan gidan?..." </p><p>"Wannan babban...Wanda akace zaayiwa biki..." Ta fada cikin kuka, itadai Hajiya shuru tayi tana tunanin abinyi don da Bata kaita ba da bazaayi mata ciki ba, dakin doctor suka koma Hajiya ta zauna Sannan tacewa doctor</p><p>"Dan Allah a cire cikin... Yarinyan tayi karanta...Sannan ba aure gareta ba.." </p><p>"Inna lillahi waina ilaihi rajuun..." Doc ya fada Sannan yacigaba dacewa</p><p>"Gaskiya Hajiya bamu irin wannan danyen aikin nan wurin.. Sannan INA baki shawaran bai kamata ayi kisan kai ba don Allah ya kaddara hakan zai faru...sins din zasu yi yawa...Kawai ni shawara ta shine ki kaita gidan da akayi mata ciki, in da hali kilan ya aureta..." Doc Wanda ba bahaushe bane ya fada mata, cikin kuka Hajiya tace</p><p>"Ai mu bamu irin wannan abun..."</p><p>"To Baku irin wannan abun amma anayiwa yara raping?... This is an act of molestation... Kawai ni shawara ce na baki..." Yafada Sannan ya mike, bayan ya rubuta mata drugs da zaa sayawa dija</p><p> Hajiya kasa tafiya tayi don duk ta rasa abinyi, banda faduwan gaba babu abinda ke damunta, kallon dija dake tsaye gefen ta hannun ta dafe da cikin ta tayi </p><p>"Ya akayi kika yarda...bakisan babu kyau kwanciya da namijin da ba aurenki yayi ba?...gashi yanzu yayi maki cikin shege..." Hajiya ta fada, dija kara fashewa tayi da kuka don tanajin yanda ake magana kan cikin shege cikin tatsunniya kuma babu Wanda ya tabayi a garinsu sai ita,</p><p>"Ki kaini ya cire min..." Ta fada,Hajiya tsoki taja saboda haushi babu kaman yanda dija ke nuna Bata San komai dangane da abinda ke faruwa ba,</p><p>"Wa zai cire maki?.." Hajiya ta tambayeta tqnq hararanta,</p><p>"Shi Wanda ya saka min..." Tafada tana kuka. Wani irin dogon tsoki Hajiya ta kara ja,</p><p>"Sakarcinki yayi yawa..shiyasa kikaje kika gwale kafa...to ni babu ruwana...gidanku zaki koma...daga taimako bazaki batamin suna ba...ba a kanki NA fara kai yara aikatau ba..." Tafada tana mikewa, fita tayi dija ta bi bayanta suka shiga mota suka bar hospital. Chemist tabi ta sayi Maganin da aka rubuta ma dija. Sannan suka koma gida. Da kyar mai aikin Hajiya tasata taci abinci Sannan tasha Maganin kafin ta kwanta. </p><p><br /></p><p>The following day cikinta ya bar ciwo kuma jinin ya tsaya. Bayan breakfast Hajiya ta umarceta data dauko bag dinta, cikin sanyin jiki ta je ta dauko bag dinta suka shiga mota, hanyan garinsu dija Hajiya Aisha tayi, dija fashewa tayi da kuka tana cewa</p><p>"Dan Allah ki maidani...ammi tace kar in kara zuwa gida...tace batason kara ganina...Dan Allah ki maidani ya fara cire min kafin in koma gida.. Dan Allah.. " Tafada cikin matsanacin kuka,</p><p>"Dalla rufe min Baki...." Hajiya ta daka mata tsawa, da Sauri ta kama bakinta tana hawaye don yanzu baya ga yazid babu wacce take tsoro kaman ammi cos taga real colour dinta</p><p>"In ba don kina munafuka ba in namiji yayi maki wani abu bazaki fadawa amminki ba...amma sai kika boye mata...ko kin fada mata?..." Ta fada cikin fada, dxa Sauri dija ta girgiza mata kai,</p><p>"Har tambayan ki na dingayi kan abinda ke damunki amma kikace babu komai..." </p><p>"Shi yace kar in fadawa kowa..." Ta fada cikin kuka</p><p> Tsoki Hajiya ta Kara ja</p><p>"Amma baki da wayau Wallahi..." Tafada Sannan sukayi driving in silence har garinsu dija. Fitowa Hajiya tayi, dija kam da kyar ta samu courage din fita tana tafiya ahankali, sallama Hajiya tayi ta shiga tsakar gida yaran ne suka amsa banda ammi dake kwance lullube da wata tsohuwar bargo. Hajiya shiga dakin tayi ta kara sallama, da Sauri ammi ta mike zaune, nuna hajiya tayi da yatsa sannan ta fara cewa</p><p>"Allah yaisa tsakanina dake...yanda kikasa aka lalata min rayuwar ya Allah yasa ayiwa naki haka...don ina talaka Mara miji kikasa aka lalata marainiya rayuwa...." Kuka ne ya CI karfinta tayi shuru, </p><p>"Kin nunamin ke mutuniyyra kirki ce Ashe haka kike?... Sai Allah ya sakamin...kuma ko kadan banason in kara ganinki...ko...dija..." Ki fitar min daga gida..." Ta fada tana mikewa tsaye, daman dija Bata shigo ba, tana tsaye zaure tanajin duk abinda ammi ke cewa, kuka tacigaba dayi, Hajiya Aisha kam kaman stone haka ta koma saboda irin kalamun ammi, daman ance mai hakuri bai Iya fushi ba, don ammi kaman mahaukaciya ta koma duk idanuwanta sun kumbura, Hajiya kasa magana tayi tana Dana sanin daukan dija daga gidansu, zata bude baki tayi magana ammi ta kara cewa</p><p>"Ki fitar min daga gida..." Ta daka mata tsawa har Hajiya Aisha tq firgita saboda yanda muryanta ya fita kaman ba wannan Matan mai sanyin murya ba, </p><p>"Dan Allah..." Ammi Bata tsaya ta saurareta ba ta fita waje ta nufi inda take ajiye firewood dinta ta dauko daya, sai lokacin tq lura da dija dake tsaye zaure tana kuka,</p><p>"Wato sai da kika dawo ko?... " Tafada tana nufan inda take tsaye, da gudu dija tayi waje da gudu, ammi tabi bayanta,</p><p>"Kika sake taka min gidan da kafanki sai nasa an jefeki..." Ammi ta fada mata Sannan tayi daki da itacen hannun ta, dagawa tayi zata bugawa Hajiya , da gudu Hajiya ta bar dakin . Bata tsaya koina ba sai bakin motanta</p><p> Cikin tashin hankali ta bude kofan motan ta shiga ammi ta biyota tana cewa</p><p>"Allah ya shiga tsakanina dake muguwa Kawai.. " Tafada Sannan ta koma gida, itama dija shiga motan tayi tana kuka</p><p>"Na shiga uku..." Hajiya Aisha ta fadawa kanta, ko kadan batasan abinyi ba kuma har ga Allah she don't want an innocent blood on her hands, tana tuki ta kalli dija dake kuka</p><p>"Kuna da wasu dangin?..." Ta tambayeta, cikin kuka dija tace</p><p>"Eh..." </p><p>"A ina suke..." Hajiya ta sake tambayan ta,</p><p>"Jos...." Tafada cikin kuka,</p><p>"Kina Iya gane inda suke in da sakaki a mota?..." Cikin kuka dija ta gyada mata kai, Bata kara cewa kala ba har suka isa daura. hajiya ta kira wata kawarta kan ta sameta gida. Bayan kaman hour daya tazo, nan Hajiya ta sanar daita abinda ke faruwa, </p><p>"hmmm ni a nawa tunanin Kawai ki kyaleta ta tafi duk inda ta gandama ...kinsan yan kauyen nan yan iska ne...gashi saga taimako uwar yarinya ta bar baki ita..." Kawar Hajiya ta fada mata, Hajiya data rafka uban tagumi ta kalleta</p><p>"Gaskiya I can't... Yarinyan tayi karanta..." Hajiya ta fada cikin sanyin murya, hararanta KAWARTA tayi</p><p>"Lallai.. Kin taba ganin karamar yarinya da ciki?...haka nan zaki saka kanki tsaka mai wuya?...ki koreta ko kuma ki kaita gidan da akayi mata fyaden...I think it will be better... Amma Gaskiya ban baki shawaran a haifi shege cikin gidan ki ba...." Tafada in I don't care manner, </p><p>"Sis kina ganin in na maida yarinya inda akayi mata fyade zasu yarda?... Kinsan halin manyan mutane... You don't they don't want to be dragged into the mud...koda kuwa they are at fault..." Hajiya ta fada</p><p>"Ni dai ki kaita chan... In basu yarda ba then just abandoned her there..." </p><p>"Ni ina jin kunyan in je gidan da wannan maganan..." Hajiya ta fada cikin sanyin murya, baki kawarta ta tabe</p><p>"Muje tare..kinsan wannan is a small thing a wajena..." </p><p><br /></p><p>Wace gari tunda wuri suka kama hanyan katsina bayan Hajiya ta sa dija ta dauki bag dinta don tayi deciding ko basu yarda ba zata saka ta a motan jos. Gidan yayar Hajiya karama suka fara zuwa inda suka shaida mata abinda ke faruwa, baki ta rike ko kadan she's not surprised don tana zuwa Kano kuma tana ganin irin rayuwan dasu Sharif keyi don anata tunanin sune. Yayar Hajiya karama shiryawa tayi tabisu ko kiran sis dinta batayi ba balle ta shaida masu suna hanya.</p><p><br /></p><p>Yazid kam wayan cin ubanshi ya tsaya wajen mufida don tunda ya fada mata abinda ya faru tsakanin shi da dija ta tsaneshi, ko kadan Bata shiga harkanshi, sai hakuri yake Bata amma sai tace ko ya kyaleta ko kuma ta tona mashi asiri, yau ma bayan yayi shirin office yazo bakin kofan da take kwana yanzu yayi knocking don banyi wahalan budewa ba cos yasan it is lock, </p><p>"Baby zan tafi office..." Yafada ahankali, tana kwance tana sauraron shi amma ko kallon kofan batayi ba balle ta amsa mashi</p><p>"Baby pls yau ki.dafa min abinci...am missing you and your food... Pls" ya fada yana Dora forehead dinshi kan kofan, still no response, </p><p>"Baby pls ki fito ki rakani lifter..." Yafada mata cikin sanyin murya, banza tayi dashi, har ya juya jin Bata amsa ba, ahankali ya taka ya kai bakin kofan falo sai ya tsaya. Ajiye brief case dake hannun shi yayi ya koma bakin kofan ta</p><p>"baby you promise not to judge me....you promise not to discriminate me...you promise to stand by me...why are you doing this to me?...the last time I checked ba ke nayi wa laifi ba...ban aureki San da abun ya faruba...then why all this..." Yafada cikin sanyin murya, </p><p>"Is that all you could say?..." Mufida ta fada batare data bude kofan ba,</p><p>"Wato bakayi min laifi ba....molestation abune mai kyau ?..." Ta tambayeshi, </p><p>"No...amma da farko you don't care...pls in wata ke baki advice..." Bai idaba ta katseshi dacewa</p><p>"Babu Wanda ke bani shawara.. Kawai abun ne ke bani mamaki....I can't still believe you are a molester..." Da Sauri.yazid ya bugi kofan da karfi</p><p>"Don't call me that..." Bai idaba tq bude kofan,</p><p>"I will call you that cos that's who you are...you are nothing but a pathetic...molester... Liar..child abuser....." Bata idaba ba taji sauka mari,</p><p>"Kina hauka!!!..." Ya daka mata tsawa, mufida dafe cheek dinta tayi idanuwanta waje,</p><p>"How dare you call me such...am I your mate?... Ko don NA fada maki secret dina kike Neman maidani mate dinki...." Mufida nuna kanta tayi Sannan tace</p><p>"You slapped me cos am telling you the truth?..." Tafada kaman zatayi kuka.</p><p> "Fuck you and the truth... Banyi maki laifi ba...kuma if you dare insult me again wallahi I will do worst..." Yafada babu wasa, </p><p>"Ban zama da kai..." Shine abinda ta fada tana bangajeshi,</p><p>"Fine...I don't care...if you will go fine....that's your business...." Yafada kaman bai damuba, mufida Bata kara cewa komai ba, ta shiga inda wardrobe dinta yake ta saka doguwar Riga, daman wannan bag datayi fixing tun ranar da yazid ya fada mata abinda ke faruwa na nan Bata cire kayan cikiba, daman this is what she wants don ko kadan batason ganin shi at first tana jin kishi yanzu kuma haushin shi Kawai take ji, yazid kam falo ya koma ya tsaya yana rike da waist dinshi don abubuwan sun yi mashi yawa, it was khadija and now mufida, Kawai shima he wants to be alone in sonsu zai kashe shi ya kasheshi ya huta, </p><p>"Wane irin punishment ne wannan?...wane irin kaddara ne wannan?..." Ya tambayi kanshi, </p><p>"What happened to my perfect life?..." Ya sake tambayan kanshi, yana nan zaune mufida ta fito dauke da karamin bag, daga kanshi yayi ya kalleta, itama kallon shi tayi tare da watsa mashi wani irin kallon tsana da haushi, tsoki taja Sannan tayi heading for the door, </p><p>"Ki tsaya in kaiki..." Ya fada mata atakaice, ko juyowa batayi ba ta fita daga falon , da Sauri ya kwanta tare da unbottoning din button fin wuyan riganshi.</p><p> Idanuwanshi ya lumshe yana tunanin abinyi, yasan yanzu kilan kowa zasu San abinda ya faru tsakanin shi da dija don yasan dole mufida zata fadi dalilin matsalan su kuma he don't care anymore.</p><p>"I don't care!!!..." Ya fada da karfi kaman yana fadawa duniya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Around karfe 12 su dija suka isa Kano, har suka isa Bata bar kuka ba, horn driver din yayar Hajiya karama yayi aka bude masu kofa, parking lot yayi parking suka fito. Direct part din Hajiya babba suka nufa suna biye da yayar Hajiya karama har falon. Nan suka tarda Hajiya karama da Hajiya babba, da Sauri Hajiyas suka mike tare da runguma, yayarsu don ta girmi Hajiya babba kuma suna mutunci sosai, dija kasa shiga tayi ta labe bayan manyan curtains dake kofan falo, sai hawaye Kawai take at the same time gabanta na faduwa don gani take yana Iya kamata yayi mata wani mugun abun savida tafadawa mutane abinda ya faru.</p><p>Gaisawa suka shiga yi, nan da nan aka kawo masu abin sha. Hajiya Aisha juyawa tayi bataga dija ba, </p><p>"Dija!..." Ta kirata, sai lokacin ta fito ahankali tana goge hawayen ta, Hajiya karama kallon Hajiya babba tayi Sannan ta maida kanta wajen dija tana kallon ta from head to toe</p><p> "Aa.. Ashe tare da dija kuke..." Hajiya karama Tafada tana kallon dija datayi mata girma don ko kadan Bata gane itace ba. Ahankali ta durkusa ta gaidasu kanta kasa, amsawa sukayi cikin faraa as usual amma suna mamakin abinda ke faruwa har suka taho dukan su, yayar Hajiya karama ce ta ajiye drink din hannun ta ta fara cewa,</p><p>"Ni Ku saurareni in fadi abinda ke tafe damu don inason Zan koma katsina yau..." Tafada in a serious tune, murmushi Hajiya babba tayi Sannan tace.</p><p>"Hmm ke kullum kaman visitor a gidan nan...daman nasan ba haka nan kika zo ba...muna sauraron ki..." Tafada cikin raha, </p><p>"Ai dai kunsan wannan Yarinyan ko?..." Yayar Hajiya karama ta fada tana nuna dija,</p><p>"Sosai ma...ai itace tayi min aiki for just few weeks ko?.." Hajiya karama tayi responding, itadai hajiya Aisha shuru tayi tana godewa Allah dayasa yayar Hajiya karama ta biyosu don gani take ita da kawarta bazasu Iya fuskanta wannan maganar ba, </p><p>"To tana da ciki.. Kuma yaran gidan nan suka yi mata..." Tafada babu alaman wasa ko wani abu, da Sauri Hajiya karama ta kalli Hajiya babba sukayi four eyes, Hajiya karama daure fuska tayi,</p><p>"Yaya ban gane wannan magana ba?.." Ta tambayeta atakaice,</p><p>"Me baki.gane ba?..." Itama ta amsa mata atakaice,</p><p>"Haba yaya...ya zaayi ki biye wa irin wannan maganar... Kinsan gold digger will do anything to gate to fame..." Hajiya karama ta fada cikin baccin rai, itakam Hajiya babba mutuwan zaune tayi don komai.nata tsayawa yayi tana tunanin abubuwa da dama at the same time,</p><p>"Haka Kawai suna son dragging sunan mu into.mud Sai ki biye masu...." Hajiya karama ta fadawa yayarta Sannan ta juyo ga Hajiya Aisha,</p><p>"In wannan plan ne don ayi black mailing dinmu to tirrr...don it won't work... " yanda take magana shows she is so angry, yayarta baki ta bude tana kallon,</p><p>"Daman ke haka kike...baki.bincike.. Sannan baki ganin laifin yaranki...." Hajiya karama Kara daure fuska tayi</p><p>"Yo yaya haka nan Sai in fara ganin laifin innocent children?... Tun yau nake zaune da masu aiki?...sai wannan zaayi wa ciki?...ni Gaskiya su bar min gida kafin inyi rashin mutunci..." Tafada sounding very bitter, ahankali Hajiya babba ta rike mata hannun alaman cool down, itakam Hajiya Aisha kunyan duniya ne ya kamata farat daya, KAWARTA ma rasa bakin magana tayi, yayar Hajiya karama ce tace</p><p>"To kina nufin karya akayiwa yaran nan kenan?..." </p><p>"Sosai ma kuwa...I can't believe zaki yarda with such allegations against yaran nan ba..." Tafada tana watsawa Hajiya Aisha harara don gani take it was all her plan. Hajiya babba ce ta saki ajiyan zuciya Sannan tace</p><p>"Dija..." Ta kirata cikin sanyin murya don dama Hajiya babba Bata da hayaniyan Hajiya karama, ahankali dija ta daga wet face dinta ta kalleta batare data amsa ba cos ko kadan Bata Iya magana, don ita duk.maganar da akeyi bashi ne damuwanta ba Kawai kar yazo ya sameta, don tana shiga gidan wannan tsoron ya dawo mata kaman bha ita ke cewa a kawita ya cire mata ba.</p><p>"Waye ya kusanceki cikin yan gidan nan?..." Shine tambayan da Hajiya babba tayi mata , ba karamin haushi Hajiya karama taji ba</p><p>"Haba anty... Why are you asking such question?...badai ki yarda da wannan mutanen ke cewa ba?..." ta fada cikin fushi, hannun ta Hajiya babba tabkara kamawa, dija.shuru tayi ta kasa amsa mata, maimaita tambayan Hajiya babba tayi, Sannan dija dake kuka tace</p><p>"Wannan.. Ne...dayazazo daga...tafiya...da zaayiwa biki...." Tafada cikin matsanacin kuka, </p><p>"Hope she don't mean yazid?..." Hajiya karama ta fada kaman ta shake dija, Hajiya babba kam nan take ta fadawa kanta karya ne wannan zancen Kawai anason Bata mata sunan yaro ne,</p><p> "Me sunan shi..." Hajiya babba ta tambayeta trying to calm her self, </p><p>"NA...mance...." Dija ta masa mata cikin kuka,</p><p>"Sharif?..." Hajiya ta tambayeta, da Sauri ta girgiza mata kai,</p><p>"Shahid?..." Ta sake tambayan ta, Hajiya karama kam ta cika tayi fam,</p><p>"Ki fada kar ji tsoron kowa....." Yayar Hajiya karama ta fadawa dija, Kawai Sai Hajiya karama ta wulla mata harara kaman ba yayar ta ba</p><p>"Daman kin Dade kina nuna tsananki kan yaran nan..kome sukayi maki?... Oho..." Hajiya karama ta fadawa sis dinta, Hajiya Aisha da KAWARTA dai yan kallo Kawai suka koma don she can't wait wannan discussion yayi over cos yana damunta don ji take kaman ta bude kasa ta shiga, </p><p>"Yanzu ni kike cewa NA tsani yaranki?..." Yayarta ta fada tana nuna kanta,</p><p>"Yo ko baki fada ba ai kin nunamin baki sonsu cos babu mai son mutum da zaiyi conniving da wasu don su Bata maka suna...." Inji Hajiya karama dake cika tana batsewa, </p><p>"Dan Allah kiyi hakuri..." Hajiya babba Tafadawa yayar Hajiya karama, Sannan ta maida duban ta ga dija</p><p>"To waye cikin su..ko yazid ne?..." Sai lokacin dija t tuna sunan shi, da Sauri ta daga mata kai, wani irin tsalle Hajiya karama ta daka tare dacewa</p><p>"Ayyiiirrrrr...kin dai gan abinda nake fada maki ko?... Wai set up din ma bai tsaya kan yan yaran ba sai kan yazid... To before in rufe idona in bude...Ku bar min gida...now..." Tafada da karfi, Hajiya babba kam murmushin takaici tayi don gani take kowa na duniya na it aikata irin wannan abun amma banda yazid don ta sanshi in and out, anata tunanin, Hajiya karama NA ihu dija ta mike da Sauri ta fita daga falon tana kuka, karaf Sai wannan mai gadin ya ganta don ko.kadan bai lura da ita lokacin data shiga ba,</p><p>"Hmmm result din abinda kukayi ya fito...amma da gani kece zaki wahala...." Yafadawa kanshi cikin ranshi yana. Kallon dija dake kuka, Hajiya Aisha da KAWARTA ma mikewa sukayi itama yayar Hajiya karama ta mike tabi bayansu, da Sauri Hajiya babba ta rike yayar Hajiya karama kan kar ta tafi amma taki saboda bacin ran abinda kanwarta tayi mata. Bag din dija suka dauka daga cikin motan yayar Hajiya karama,. Koda ta tambayesu ina zasu kaita Hajiya Aisha tq amsa mata da jos zata kaita,. Nan suka fita daga gate a kafa ita kuma ta shiga driver dinta ya kama hanya KT daita. Dija NA tafiya tana kuka don batasan takamemen sunan ainahin garinsu ammi ba amma Tasan daga jos take. </p><p>"Allah na gani ban dauko ki don in wulakanta maki rayuwa ba....ki yafemin..." Hajiya Aisha ta fada tana fashewa da kuka,</p><p>"Kin dai tabbatar kin San garinku ko?..." Ta sake tambayan ta, kai Kawai dija ta daga mata don ita Kawai so take kilan a hanyan zuwa jos kilan tayi accident ta mutu Kawai da bakin ciki da take . keke suka tsaida ya kaisu har bus stop, kawar Hajiya Aisha Sai tsoki kawai take. Suna zuwa tasha dija ta shigaitan jos, Hajiya Aisha ta biya kudin mota Sannan ta Bata 10k. Number wayanta ta rubutawa dija, ta bude bag dinta ta saka kudin da number. Hajiya Aisha na tsaye har motansu ya tashi Sannan su suka hau motan KT.</p><p>[3:24PM, 3/20/2018] 鈥�+234 806 125 0020鈥�: 馃挍馃挌馃挏馃枻馃挋鉂� </p><p>NA CUCE TA</p><p>馃挍馃挌鉂ゐ煐ゐ煉滒煉�</p><p><br /></p><p><br /></p><p>庐zuwairat(ummu Maryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>1鈨�8鈨�</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan Hajiya babba ta koma falo zama tayi tare da rafka uban tagumi tana tunanin abinda ke faruwa, confirm Tasan something is wrong amma ba ta hanyan yazid ba kilan wasu yaran gidan</p><p>"Wai menene anty?..." Hajiya karama ta tambayeta tana kallon how lost in thought she is, ajiyan zuciya Hajiya babba ta saki</p><p>"Kawai ina tunani ne...ni ina ganin yaranj gidan nan are involved..." Bata idaba Hajiya karama ta katse ta dacewa</p><p>"Haba anty... Why will you think such...yanzu kina ganin yazid will do such thing?..." Itama Hajiya babba girgiza kai tayi</p><p>"No...amma what about your naughty children... Kinsan sarai suna iya aikata..." Baki Hajiya karama ta turo kaman wata karamar yarinya Sannan tace</p><p>"Gaskiya anty yarana ba zasu yi hakan ba...gasu asabe basuyi masu komai ba Sai ita da ko wata batayi a gidan nan ba?...Gaskiya anty ki bar irin wannan maganar kar suyi succeeding...." Tafada tana cika tana batsewa daman tafi Hajiya babba zafi da fada. </p><p>"Ni abinda nake tunawa shine yanda Yarinyan ta bar gidan nan...in baki mantaba har kuka kika cemin tanayi don ta koma gidansu...kilan.at that time da akwai abinda sukayi mata that made her change her mind at once..." Hajiya babba ta fada cikin sanyin murya, itama Hajiya karama shuru tayi tana tunanin maganan Hajiya babba don itama Sai lokacin ta tuna yanda dija ta koma kafin a kaita gida, she remember ko abincin kirki bataci, itama ajiyan zuciya ta saki</p><p>"It can't be...." Tafada cikin ranta tare da kallon hajiya babba da ta Dora kafa daya kan daya tana girgiza su ahankali, Sai kuma Salem ya fada mata a rai,</p><p>"Maybe Salem ne..." Hajiya karama tafada da Sauri tana kallon Hajiya babba, Hajiya babba daga kai tayi ta kalleta,</p><p>"Yes it may be him...kinsan NA fada maki ya tambayeni address dinta...kilan shine sanadiyan cikin...." Hajiya karama ta fada da Sauri, ahankali Hajiya babba ta gyara zamanta </p><p>"To in shine Sai ta kira sunan yazid?... Ai Sai tace Salem..." Da Sauri Hajiya karama ta kara katseta dacewa</p><p>"Ai kinsan Yarinyan bata da wayau...Sannan bata gane yan gidan ba sosai...kuma kinsan Salem da yazid suna yanayi..." Ta fada mata, Hajiya babba dai baki ta saki tana kallon ta, itama tayi tunanin hakan,</p><p>"Kina gani Salem zai iya aikata hakan?..." Hajiya babba ta tambayeta, da Sauri Hajiya karama tace</p><p>"Ai mutum bai gane halin yaran zamani ba..." Dariya Hajiya babba tayi</p><p>"Ashe kin San baa rantsewa yaran zamani amma kika rufe idanuwa kan yaran nan bazasu Iya aikata hakan ba..." Hajiya babba ta fada cikin dariya, iatam Hajiya karama dariya tayi</p><p>"Ai dole...wa zai yarda a goga ma nashi ...every mother will do all they can to protect their offspring..." Inji Hajiya karama</p><p>"Even if they are wrong?..." Hajiya babba ta tambayeta,</p><p>"Hmm am sure basu da laifi...yanzu meye abinyi?... Don duk fadan nan da kika ga inayi...deep down inajin tausayin wannan Yarinyan..." Hajiya karama ta fada,</p><p>"Ni ai duk jikina yayi sanyi..am just imagining how it will as a mother yar ka ta zo da cikin shege while the person responsible yana chan yana hutawa.." Hajiya babba ta fada kaman zatayi kuka, </p><p>"Allah dai ya kare mana zuria..." Hajiya karama tq fada Sannan tace</p><p>"Yanzu meye abinyi don we can't just fold our arms ...kuma Wallahi in nan gidan Salem yayi wani abu daita Sai naci ubanshi Wallahi..." Tafada sounding very serious,</p><p>"Ko dai mu kirashi nan mu tambayeshi?...." Hajiya karama ta tambayi Hajiya babba,</p><p>"Gaskiya I can't have such a shameful discussion da shi...Kawai ki kira yazid ki tambayeshi in ya San da akwai wani abu daya shiga tsakanin dija dashi don mostly basu boyewa junansu secret..." Inji Hajiya babba,</p><p>"To hakan zaayi...." Hajiya karama ta amsa mata</p><p> "In ya shaida maki da akwai Sai ki fada mashi Yarinyan tana da ciki....daga nan Sai mu San abinyi...." Inji Hajiya babba, </p><p>"To shikenan... Bari in kirashi...." Tafada tana da juyawa don daukan wayanta Sai tga bai nan wajen</p><p>"Ashe duk zaman da nayi a nan babu waya kusa dani..." Inji Hajiya karama</p><p>"Daman kin saba ...nasan yanzu miss calls na chan rututu..." Hajiya babba tq fada mata, dariya tayi Sannan ta mike, daman by then an farq kiran sallan zuhr.</p><p><br /></p><p>Tunda dija ta shiga mota take shessheka amma babu hawaye har wata mata dake zaune kusa daita ta tambayeta matsalan ta amsa mata da babu komai</p><p>"To ki bar damun mu da hayaniya...." Matar ta fadawa dija, dija hada kai da kujeran gabanta tayi tana tunanin sunan kauyen su ammi, tafi minti biyar tana tunani Sannan sunan wurin ya fado mata, Sai ta tuna tunda amminta da kanta ta gujeta Tasan koina ma gudunta zaa dingayi, </p><p>"Allah kasa in mutu..." Tafada cikin ranta wasu new tears suna fitowa daga tired eyes dinta,</p><p>"Allah kasa inyi hadari in mutu...banason duniya...." Ta sake fadawa kanta wannan Karin tana fashewa da kuka sosai, </p><p>"Wai ke lafiya kike mamu kuka cikin mota?..." Wanda ke zaune gabanta ya tambayeta, da Sauri dija ta share hawayen ta amma deep is side she's boiling,</p><p>"Allah yaisa....ban zan yafe ba...mugu....kasa ammi ta koreni..." Tafada cikin ranta wasu hawayen na zubowa, ita ba cikin jikinta ke concern dinta ba, koranta da ammi tayi, Tasan ana cikin haihuwa don tasha ganin Matan kauyen su da manya ciki daga baya ashe sun haihu, to anata tunanin ba irin wannan cikin gareta ba don ita cikinta bai da girma, batasan nan da four months da ko yarinya zata keto ta jikinta ba, </p><p>"Wallahi garzali bai da mutunci..." Taji daya daga cikin Matan dake zaune layin da take tana fadi,</p><p>"Inafa yaganshi...yarinya da ciki amma ya saketa... Ko tausayinta bai jiba... Yaran yanzsu sun maida aure tamkar wasa...." Wata ta saka baki, dija kasake tayi tana sauraron su, daman bata manta hiran da sukayi da kawarta ba inda take fada masu anasamun ciki in namiji ya sakawa mace abun fitsarinshi, tasan saki don tana jin ana cewa aure ya ruguje tsakanin wasu, shuru tayi tana tunanin abinda zata dinga fadawa mutane in an ganta, don gani take kowa na ganin tana da ciki kuma zaa dinga tambayan ta , </p><p>"Nima sakina yayi...." Tafada thinking that cikin ranta ta fadi hakan, da Sauri Matan dake gefen ta suka kalleta,</p><p>"Inna lillahi... Kinga irin abun ko?... Yanzsu wannan yar Yarinyan har ta isa a aureta balle saki?... Gaskiya muna da matsala..." Matar ta fada kaman zatayi kuka tana kallon dija, Dan ajiyan zuciya dija tayi don gani take ana tausayin ta</p><p> Ta samu tudun dafawa kenan tunda ta samu an tausaya mata, </p><p>"Allah ya saka maki..." Daya daga cikin Matan ta fada, </p><p>"Ameen..." Tafada ahankali. Har suka isa jos dija bata bar hawaye ba, Kawai tunanin halin da zata fada in har mutuwa bai dauke ta bha Kawai take, bus stop dake cikin garin jos motan ya paka mutane suka fara fitowa, dija zaune tayi tana kallon mutane dake kai kawo Sannan tana tuna lokacin da suke zuwa da ammi, bata manta irin murnan da suke muddin akace zasu zo jos amma yau gata cikin jos tana jira mutuwan ta.</p><p>"Ki fito mana...." Taji wani yana cewa, Sai lokacin ta dawo hayyacinta, bag dinta dake kan cinyanta ta dauko ta fito daga cikin motan ta shiga cikin park dake dauke da mutane kala2 kowa ta kanshi Kawai yake, gefe daya ta samu ta zauna, duk Wanda yaga yar beautiful yarinya zaune dauke da bag kan kafanta Sai ya juyo ya kalleta Sannan su wuce. Irin tambayan da ake yi mata yasa ta mike ta dauki bag dinta tana zagaya park din rike da bag dinta, mutane Sai tambayan ta suke ko zata hau mota amma ki daga kai batayi balle ta amsa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Har karfe biyu yazid na kwance inda mufida ta barshi, da kyar ya samu yayi sallan zuhr, tunanin rayuwan duniya Kawai yake, ahankali ya dauki wayansyayi dailing number mufida don yaji in ta isa gida amma ringing Kawai yake babu response, ajiye wayan yayi, baifi minti biyar da ajiye wayan ba ta fara ringing, ahankali ya mika hannu daga inda yake kwance ya dauki wayan, gani yayi small mom, Kawai tunanin sun samu labarin zuwan mufida yayi. Picking yayi tare da sallama cikin sanyin murya,</p><p>"Me ke damunka?..." Ta tambayeshi batare data amsa sallaman ba, shuru yayi don ya lura har yanzsu bata San abinda ke faruwa ba , </p><p>"Son am asking you?..." Ta sake fada mashi,</p><p>"Am OK..." Ya amsa mata cikin sanyin murya</p><p>"Ok..ina.. Mufida?.." Ta tambayeshi, </p><p>"Tana bacci..." Yayi mata karya don ko kadan baison magana kuma yasan in ya fada mata gaskiyan inda take to maganar ba karamin tsawo zaiyi ba, </p><p>'Daman wata tambaya zan yi maka..." Tafada ahankali,</p><p>"To small mom..." Ya amsa mata not thinking about what ever she has to say,</p><p>"Pls inason ka fada min...Salem ya taba fada maka da akwai abinda ya shiga tsakanin shi da wannan Yarinyan dayazo Neman address dinta?..." Da Sauri yazid ya mike zaune, tare dacewa</p><p>"Wace yarinya?..." Ya tambayeta muryan shi na rawa,</p><p>"Khadija..." Jin sunan khadija yasa yayi Sauri mikewa tsaye,</p><p>"Me ya sameta!!!!..." Ya tambayeta tension na rising cikin muryan shi Wanda yasa Hajiya karama kallon wayan daga inda take zaune a bakin gadonta. </p><p>"Ina tambayan ka...kana tambaya ta...I said ya fada maka wani abu ya shiga tsakanin su?..." Ta sake tambayan shi,</p><p>"Small mom...ki.fadamin mana...wani abu kaman me?..." Ya tambayeta cikin tashin hankali,</p><p>"Kai..why do you sound so tensed?..." Hajiya ta tambayeshi, </p><p>"Ki fadamin mana..." Ya fada in high tune kaman wata age mate dinshi, da Sauri ya sake cewa</p><p>"Sorrry small mom...pls ban gane abinda kike nufi ba..." Ya fada yana calming kanshi, Hajiya karama shuru tayi tana tunanin abinda ke faruwa don the tension in his voice says it all,</p><p>"Small mom ..pls...tell..." Yafada in a cracking voice, da kyar Hajiya ta samu courage din cewa</p><p>"An kawo ta dazun...wai she's pregnant...." Jin pregnant yasa yazid sakin wayan hannun shi, </p><p>"Inna lillahi... Waina ilaihi.... Rajuun..." Ya dinga maimaitawa yana fashewa da kuka</p><p>"Na shiga uku...na shiga uku...NA...shiga...uku..." Yafada cikin matsanacin kuka, hajiya karama na sauraron duk abinda yake cewa, itama da Sauri ta mike zaune tana fada kirjinta</p><p>"Hallo..." Ta dinga fada ko ta samu yayi magana amma Sai kukanshi kawai ke tashi.</p><p>Yazid zama kasa yayi yana kuka don a nashi tunanin wayan ta tsinke not knowing it still connected, da Sauri ya goge hawayen face dinshi ya dauki wayan don sake kiran Hajiya karama saiga yana counting, yasan babu zancen wani boye2 don karya ya kare,</p><p>"Pls...small.. Mommy... Ku...riketa... Am...coming..." Yafada cikin kuka, </p><p>"What is happening?.." Shine tambayan da Hajiya karama tayi mashi amma ko kadan bai Iya magana, katse wayan yayi Kawai , ya maida buttons din riganshi ya fito daga ciki part din shi, da Sauri ya kara komawa ya dauko car keys tare da kulle part din Sannan ya hau lifter zuwa parking lot da suke ajiye cars dinsu. Sai Sauri yake kaman zai tashi sama.</p><p> Cikin mota ya shiga yayi reverse ya fita daga gate dinsu, wayanshi ne ya fara ringing, dauka yayi yaga still Hajiya karama ce, kasa picking Sai hawaye yake yana tuki, yau zai zama ranar kunya a gareshi, yau su Sharif da shahid da yake yiwa fada kan rashin jinsu zasuji yayiwa mai aikinsu jiki</p><p>"How?...was she matured?..." Shine tambaya da yayiwa kanshi yana hawaye at the same time yana tuki at high speed. Abangaren Hajiya karama kam kasa tsayawa tayi ta koma ta zauna ahankali,</p><p>"How could this be possible?... How?..." Shine tambayan da Hajiya karama take wa kanta at the same time wayanta kunnenta tana sauraron ringing dayake tana aduan Allah yasa yayi picking, </p><p>"Daman wannan yaron haka yake?..." Ta sake of tambayan kanta. Ajiye wayan tayi ahankali ta maida kafanta kan gado tare da harde hands dinta kan kirjinta. Kawai Sai hawaye suka taro idanuwanta, tana nan tana kareshi amma she's wrong, nobody is above mistakes, </p><p>"Subhanallahi!!!...." Tafada ahankali, </p><p>"I wish I know... Inama na Sani... Yaya am sorry</p><p>.." Tafdaa tana fashewa da kuka, </p><p>"Dija am sorry... Am so sorry... I trusted my sons so much..." Tafada cikin kuka tamkar danta ne ya aikata wannan abun kunyan, daman haka take, she loves yazid more than her own blood children, ba don komai ba amma because of his respect da addini, he loves her too don duk abinda ta nuna tana so to bai tsallakewa har Sai yayi mata. Tunanin Hajiya babba tayi</p><p>"This will ruin my sister..." Ta fada cikin kuka tana tunanin halin da hajiya babba zata shiga in ta samu labarin abinda ke faruwa Don Tasan hakan zai jefa Hajiya babba cikin matsanacin tashin hankali don she's a peace loving person, ko kadan bata kaunar tashin hankali amma gashi yanzu babban matsalan zaiyi knocking on her door step, hawaye Hajiya karama ta share </p><p>"I wish am dreaming ...I wish I can make this go away..." Tafada tana kara fashewa da kuka, wayanta ne ya dau ringing, ahankali ta daga wayan kasancewan ringing din Hajiya babba daban, daidaita voice dinta tayi Sannan tace</p><p>"Anty ya dai?..." Tafada tana kokarin boye damuwa dake cikin ranta, </p><p>"Baki shigo ba..." Ta fada cikin sanyin murya don sun saba always together, </p><p>"Salla nayi..." Ta fada mata ahankali,</p><p>"To kin kira yazid din?..." Ta tambayeta, shuru Hajiya karama tayi not knowing what to say,</p><p>"Hello..ko baki kira shiba?.." Ta sake tambayan ta, da Sauri Hajiya karama tace</p><p>"Na.. Kirashi...amma the network is bad...zan sake kiranshi..." Tayi mata karya, ta kara dacewa</p><p>"Zan Dan kwanta kadan..." </p><p>"Ok...to daman ke na zauna jira...bari in kwanta nima...but pls call him don ko.kadan banason yin wannan discussion dashi..." Tafada ahankali,</p><p>"To shikenan..." Ta amsa mata Sannan ta katse wayan ta Dan jingina da pillow tana tunanin abinyi.</p><p><br /></p><p>Yazid kam yana tuki yana kuka kafin ya iso garin Kano har idanuwanshi sun kumbura sunyi jajir, haka face dinshi ma tayi ja sosai. Daf da sallan magrib yayi horn a bakin gate dinsu, har lokacin Hajiya karama bata kara fitowa ba, tana kwance tana sauraron zuwan shi, tana jin horn a bakin gate tayi saurin mikewa, lekawa tayi ta window taga motan yazid dake shigowa, da Sauri ta fito tana daure kanta da dankwali, tana fita yazid na fitowa daga cikin mota, kallon yanda ya koma tayi Sai ya kara fashewa da kuka, kasa magana tayi, jin hayaniyan yaran gidan ya maidato hankalin ta, da Sauri ta kama mashi hannu</p><p>"Ku koma...yaya yana zuwa..." Tafada tana rike da hannun shi har part dinta. Suna shiga falo ta sakar mashi hannun ta dawo gabanshi</p><p>"What is happening?..." Shine tambayan da tayi mashi, yazid shuru yayi yana kuka don baisan ta yanda zai fara fada mata abinda yayi ba, </p><p>"Tell me...meke faruwa?... Na tambayeka in Salem ne yayiwa khadija ciki amma instead Sai kukan ka Kawai naji...meke faruwa?...." Ta tambayeshi hawaye na taruwa idanuwanta, cikin kuka yazid yayi kneeling gabanta tare da rike legs dinta</p><p>"Am...sorry....I...ra....ped...her...." Yafada cikin matsanacin kuka, babu alaman surprise a fuskan Hajiya karama don already she's ready for this,</p><p>"Yazid how could you?... Me ya jamaka aikata irin wannan mummunar aikin?..." Tafada tana kuka, yana girgiza kai yana cewa</p><p>"Wallahi banisan ba...ko kadan ba halina bane...I don't know what came offer me...am sorry.. I disappointed all of you...Ku yafemin..." Ya karasa maganar cikin kuka.asabe dake tsaye cikin kitchen baki tarike, batasan ainahin abinda yake magana akai ba amma tasan it is not something good</p><p> "Dan Allah Ku yafemin.. Am sorry... Ku fada mata ta yafemin..." Yafada cikin shessheka, har lokacin asabe na sauraron su, itama Hajiya karama kuka Kawai take saboda yanda yazid ke kuka, dafa kanshi tayi</p><p>"Enough... Ka bar kukan haka nan...the damage have been done,..tashi..." Tafada tana goge hawayenta, kin tashi yayi ya kara cewa</p><p>"Pls Ku fadawa khadija ta yafemin... Na cuci rayuwanta...na zalunceta...am sorry... Sharrin shaidan ne..." Ya cigaba dacewa, sai lokacin asabe ta gano inda matsalan yake, ko kadan batayi tunanin dija is pregnant ba, Kawai tana tunanin yana confessing kan abinda yayi mata ne. Hajiya karama rike shi tayi ya mike ta saka hannu tana goge mashi tears din face dinshi wasu suna zubowa, duk a lokacin yana tunanin dija tana gidan. Hajiya karama kam tausayin yazid Kawai take don yanda ya chanza shows he's really sorry, kama hannun shi tayi sukayi hanyan bedroom dinta, Dan tirjewa yayi </p><p>"Small mom...I need to see khadija..." Yafada cikin low voice, </p><p>"An tafi daita..." Tafada mashi ahankali, kuka ya kara fashewa dashi, </p><p>"We don't know any of you could be responsible... Tace Kaine amma we thought it was a plan to blackmail us..." Ta fada mashi, ahankali yazid ya zauna kasa tare da dafe kanshi yana kuka. Hajiya babba kam tana cikin bacci taji hayaniyan yara suna kiran yaya yazid, da Sauri ta mike don tunda Hajiya karama ta shaida mata bata dawowa itama ta kwanta. Autanta ne ya shigo dakin yana cewa</p><p>"Big mom yaya ya dawo..." Kallon surprise tayi mashi, </p><p>"Yana ina?..." Shine tambayan data yi mashi don tabbatar he's not lying, </p><p>"Yana bangaren small mom...tace bashi da lafiya..." Yafada with exergration, surprise look ne kwance kan fuskanta, </p><p>"Bai da lafiya?..." Ta tambayi kanta ahankali, yaron dai komawa yayi itama ta sauka daga kan gado ta fito falo. Zama tayi tana jiran shigowa shi har kusan minti ashirin baizoba nan take ta mike tayi hanyan part din Hajiya karama, tuna shiga falon ta fara jin sautin kukan shi, </p><p>"Ni dai Ku fadamin inda take in tafi..." Taji yana cewa, da Sauri ta dafe kirjinta saboda yanda gabanta yayi mugun faduwa, </p><p>"I need to be on my way...." Yafada cikin kuka, nan take Hajiya babba ta yanke jiki ta fada kasa tim, Wanda yasa Hajiya karama da yazid kallon wurin suka ga Hajiya kwance kasa kumfa na fitowa daga bakinta.</p><p><br /></p><p>Har magrib dija na yawo wajen park da bag dinta, Allah ya taimaka mata bag dinta ba babba bane, babu wasu kaya ciki Sai gowns data dawo dasu daga Kano, duk inda ta ga mata nan take zuwa ta Dan raba da sun watse sai ta nemi wani wajen,har lokacin bata CI komai ba sai kalacin dataci gidan Hajiya Aisha, tana zaune kan wani benci kusa da wasu yara dake saida abinci kala na talakawa, tunanin inda zata zauna Kawai take, ji tayi wani abu NA juyawa cikin cikinta ga amai na tukanta,kusa da daya daga cikin masu saida abinci taje ta fada mata ta bata abinci na hamsin, yarinyan kallon ta tayi daga am a zuwa kasa Sannan ta maida kallonta ga abinda take saidawa, daya daga cikin robanta ta dauko ta zuba mata shinkafa babban spoon daya ta saka mata yaji da mai ta mika mata dija ta amsa ta bata hamsin cikin kudin dake cikin bag dinta Wanda ammi ta wurga mata. Gefe daya ta koma tana ci wasu da suka dan maida hankalin su kanta suna kallon ta while wasu basu damu daita ba. Tana gamaci taji abincin bai isheta ba ta kara komawa ta sai na hamsin. Atakaice saida taci kusan na Dari biyu Sannan ta koshi. Tana nan zaune har karfe goma, sai da mai saida abinci na karshe ta mike Sannan itama ta mike tana kallon titin daya fara komawa lonely, tana tafiya tana kuka tana kiran ammi, wani waje ta tsaya katon gate taga cars suna shiga suna fita itama ta kusa kai ta shiga wurin dake kama da gari guda, Ashe hospital ne, yawo Kawai take tana ganin mata da maza suna shiga suna fita, Chan nesa daita ta hangi wasu mata zazzaune da saurinta ta karasa wajen babu wacce ta maida hankalin ta kanta, ahankali tq zauna kan daya daga cikin kujerun, batafi minti biyar ba taji anacewa</p><p>"Ina masu Maryam isa?..." Da sauri mata biyu suka mike, dija tsaya kallon su tayi sai taji anacewa</p><p>"Ta haihu..an samu namiji..." Sai lokacin ta gane inda ake haihuwa ne. </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Around 8:30 a falon su dad dakin yazid, dad ne zaune sai Hajiya babba data fita hayyacinta kaman ba itaba duk idanuwanta sunyi mugun kumburi hannuwanta bisa kanta sai hawaye Kawai take, opposite dinta Hajiya karama ce zaune sai yazid dake zaune kasan carpet kanshi kasa duk ya chanza, dad kura mashi ido yayi ya rasa abun cewa don sunfi hour zaune wurin nan amma ko word biyar dad bai fita ba don he's beyond confused, banda kukan Hajiya babba babu abinda ke tashi don shi yazid a yanzu ko muryanshi bai fita sosai, saboda kuka, </p><p>"Am very disappointed in you..." Shine maganar da dad ya kara fada </p><p>"Very ...very...disappointed in you....kullum kaman ustaz amma Ashe deceiving dinmu kake....gashi yanzu halin ka ya fito fili...amma Allah yaisa tsakanina dakai...ka lalata min suna....." Dad ya fada cikin wata irin murya, yazid sai hawaye Kawai yake don he's expecting more, </p><p>"Allah NA ganin ba irin tarbiyan danayi maka bane....I tried my best..." Ya sake fada Sannan yayi shuru saboda yanda ranshi tayi mugun baci, Hajiya karama dake hawaye tace</p><p>"Kayi hakuri...nasan kaddara ya Riga fata....am sure bai taba irin wannan abun ba...regrets is written all over him...." </p><p>"Shut up!!!!" Dad ya daka mata tsawa, </p><p>"Daman kece ke goya masu baya suyi duk abinda suke zo..." Yafada mata Hajiya karama kara fashewa tayi da kujadon maganar ba karamin bata mata brain yayi ba</p><p>"And you..ka fita kaje chan Ku karasa...babu abinda ya dameni...." Dad ya fada yana kokarin mikewa, da Sauri Hajiya babba ta tashi ta je inda yake ta rikeshi Hannu daya tasa ta goge face dinta, ahankali yazid ya daga kanshi ya kalleta yaji wani irin haushin kanshi da tausayin mom dinshi. </p><p>"Pls don't forsake him...abinda yayi is bad...very bad..amma yanzu me zamuyi?... Abinda ya faru ya riga ya faru...let's find solutions to this...." Tafada cikin kuka, dad tsayawa yayi yana kallon ta gwanin ban tausayi don har cikin ranshi yake jinta, hannun ta dake rike dashi ya kama, </p><p>"Wane irin solutions?... Right now am confuse..." Tafada yana shafa hannun ta,</p><p>"We should find the girl...ya aureta ko yana so ko bai so..." Tafada tana hararan yazid, </p><p>"What about the pregnancy?.." Dad ya tambayeta,</p><p>"We find her first... Maybe ina Iya kaita wajen grandma har ta haihu...kar abar iyayenta da wannan abun kunyan cos our sons mistake will ruin them..." Tafada tana kuka, </p><p>"You are the best mom in the world..." Yazid ya fada cikin ranshi, hannu dad yasa ya goge mata face dinta</p><p>"In haka kike so babu komai... Hakan zaayi..." Yafada ahankali, kallon yazid dad yayi</p><p>"Kai kuma I will surely find away to deal with you...." Ya fada mashi cikin bacin rai Sannan ya bar falon, Hajiya babba barin falon tayi tana hawaye, itama Hajiya karama mikewa tayi ta kama hannun yazid sukayi part dinta. Hajiya babba nashiga part dinta ta tarda miss call din Maman mufida rututu, nan ta zauna ta daidaita kanta Sannan ta kirata, bayan sun gaisa take fada mata ga mufida ta dawo sai kuka take kuma ta tambayeta abinda ke damunta taki ta fada mata, Hajiya shuru tayi tana tunanin kilan maganar cikin taji shiyasa tayi yaji, </p><p>"Dan Allah Ku tambayi yazid ko ya fada maku abinda ya faru tsakanin su donni nayi har na gaji..." Inji mamn mufida,</p><p>"To shikenan..." Hajiya ta amsa mata Sannan sukayi sallama, tana kashe wayan ta kira yazid, yana kwance falon Hajiya karama yana counting hours before dawn yaji ringing din wayanshi, yana ganin mom dinshi yayi saurin picking,</p><p>"In bakason ranka yayi mugun baci kaje ka bawa mufida hakuri... In ba haka ba Wallahi ko.gaidani karkayi...." Tana kaiwa nan ta kashe wayan ta. Kallon agogo yayi yaga 9:00 yasan yanzu babu holdup don haka zuwa gidansu mufida won't be difficult. Mikewa yayi ya fita ya hau mota ya kama hanyan gidansu mufida, duk ranar baici abinci ba kuma ko kadan baijin yunwa, duk Wanda ya ganshi yasan Sam baya Cikin kwanciya hankali. Cikin minti 43 ya isa kofar gidansu, bai shiga da mota ba yayi parking nan waje ya fito ya buga kofan mai gadi ya bude mashi, shiga yayi har falo yaga babu kowa, nan ya tsaya yana kwalla sallama mom din mufida ta fito suka gaisa Sam babu alaman damuwa tattare daita, tambayan mufida yayi ta nuna mashi hanyan dakinta. Mikewa yayi yabi inda ta fada mashi har bedroom dinta, ahankali ya bude kofan ya hangeta kwance tayi rub da ciki, idanuwanta bude amma ta bawa kofa baya taji an bude kofa amma batayi tunanin yazid ba, ahankali ya Kara bakin gado ya zauna tare da dafe bayanta, sai lokacin taji kamshi perfumes dinshi, da sauri ta juyo ta kalleshi, mikewa tayi zaune</p><p>"Me ya kawoka?... Ko Marin kazo ka karamin...ka fitar min daga daki...." Ahankali ya mike daga kan gado yayi kneeling bakin gadon</p><p>"Baby am so sorry... I will never hit you again... Pls forgive me..." Yafada ahankali, kura mashi ido tayi tana kallon shi, sai lokacin ta lura da irin kumvurin fuskanshi don tunda suke bata taba ganin fuskanshi haka ba, ahankali ta sauka daga kan gado ta tallabo face dinshi, </p><p>"Baby me ya sameka?..." Shine tambayan datayi mashi, tana kallon shi at the same time tanajintanajin sonshi na ratsa zuciyanta, murmushin karfin hali yayi</p><p>"Kece kika barni..." Yafada ahankali, kai ta girgiza mashi,</p><p>"pls tell me...some is wrong again.. Did you rape another gal?..." Dariya ya karayi don ba karamin dariya ta bashi ba</p><p>"Yanzu baby kin maidani irin mazan nan da basu Iya ajiye joystick dinsu waje daya?..." </p><p>"Kaga laifina ne?...AI with you anything is possible... " ta fada ahankali, </p><p>"Now tell me...kin yafe min?...." Ya tambayeta yana kama waist dinta, hararanshi tayi tare da turo baki</p><p>"Ka bari saina huce..." </p><p>"Pls baby ki huce...mom tace in baki dawo ba kar in kara yi mata magana...so pls ijn har kinason fiddani daga fushin mom ki ki tashi ki shirya mu tafi...." </p><p>"You mean now?..." </p><p>"Yes...now...pls...", da kyar ya shawo kanta ta yarda tabishi. Mom din mufida kam mamaki Kawai take yanda batasan abinda ya hadasu ba kuma har sun shirya, around 10:30 suka kama hanyan gidansu yazid.</p><p><br /></p><p>part 19</p><p>38 17 5</p><p>by ummumaryam29</p><p>💙💚❤🖤💛💜</p><p>NA CUCE TA</p><p>💙💚💜🖤💛❤</p><p>®zuwairat( ummu Maryam)</p><p>1⃣9⃣</p><p>Yana tuki suna hira kaman babu abinda ya taba hadasu, yazid kam ban da tunani babu abinda yake, Wai shi yazid ne zaiyi fathering da out of wedlock, har yanzu tamkar mafarki yake don he can't believe it, sai yanzu ya yarda don't take yourself to be perfect, don't feel too perfect cos in har baka bar duniya ba to baka wuce jarabawa ba,</p><p>"Ganawa kaddara...." Tafada kasan makoshinshi Wanda yasa mufida dake lumshe swollen eyes dinta kaman zatayi bacci ta kalleshi, shima kallon ta yayi ya sakar murmushin karfin hali,</p><p>"Am sorry I hit you..." Yafada kaman shine main problem dinshi,</p><p>"Nace ya wuce..." Tafada tana rike hannun shi dake kan staring, duniyar tunani ya kara fadawa, yanzu ya yarda cewa not all that glitter is gold, don before gani yake most of his friends are corrupt with dirty different characters amma duk cikin su babu mai shege sai shi, tuna how young khadija is yayi, shi har yanzu gani yake kaman dream don a nashi tunanin she can't get pregnant. Yasan yanzu duk zaa tsaneta gidansu, yasan she will be stigmatized, he can't wait for tomorrow, tamkar ya jawo gobe yake ji, yanzu baiji kunyan kowa kan wannan maganar, haka Allah ya kaddara mashi kuma he will take it in good faith. Sai around after 11 sukaiso gidansu, part dinshi suka shiga ta ajiye bag dinta Sannan ya kama hannun ta sukayi bangaren Hajiya babba, yasan its late amma yasan for sure mom dinshi bazatayi bacci ba. Kofan falo ya bude suka shiga yana rike da hannun mufida, bakin kofan bedroom dinta sukaje ya radawa mufida tayi sallama, tanayi mom ta amsa mata, sakin hannun ta yayi ya koma baya don har yanzu basu kebe da mom ba tunda aka fara wannan magana Sannan he's so ashamed of himself da bazai Iya hada ido daita ba. Falo ya koma ya zauna ya dafe kai yana counting seconds to dawn.</p><p>Mufida NA shiga mom ta daga kai ta kalleta da idanuwanta da suka chanza tamkar ba nata ba, tana ganin mufida tayi saurin goge face dinta don ko kadan bata dau muryanta ba.</p><p>"Daughter kece da wannan Daren?..." Ta tambayeta ahankali, kan mufida kasa tace</p><p>"Eh..." Sannan ta durkusa ta gaida ta, amsawa tayi</p><p>: Cikin sanyin murya tana nuna mata wurin zsama kusa daita, ahankali ta zaune gefen ta, itadai mufida tunanin abinda ke damun Hajiya tayi sai kuma ta tuna kilan sai yanzu suka San abinda yazid ya aikata not knowing they is more to it. Cikin rawar murya Hajiya tace</p><p>"Kiyi hakuri kinji?... Komai mukaddari ne...haka Allah ya kaddara... Ki rike mijinki hannu bibbiyu..." Tafada tana fashewa da kuka, itama mufida fashewa tayi da kuka, ahankali Hajiya ta jawota jikinta suka bude sabon babin kuka kaman anyi mutuwa.</p><p>"Bansan irin wannan kaddara ba...ko sau daya ban taba kama yazid da wata karamin laifiba sai Kawai Ace yayi wa yar karamar yarinya ciki...." Hajiya ta fada cikin matsanacin kuka, gaban mufida yayi mugun faduwa dajin ciki, ahankali ta daga kanta daga shoulder Hajiya ta kalleta, cikin kuka Hajiya ta kalleta, surprise look dake face dinta ya tabbatar mata batasan wannan zancen ba kuma bataso ace ita ta fara sanar mata ba.</p><p>"Mom ciki gareta?..." Ta fada cikin kuka, Hajiya dafe kai tayi tana kuka,</p><p>"NA shiga uku...Hajiya gidanmu zani...ban iya zama dashi....." Ta dinga fada kaman wata zautatta, dafa ta Hajiya tayi tana girgiza mata kai,</p><p>"Don't say that....hannun ka bai rubewa ka yarda...mijinki ne kuma bazaki kishi saboda jarabawan Allah ba...kiyi hakuri wata rana zakiji kaman ba a taba hakan ba..." Tafada tana shafa bayanta, mufida kukan bakin ciki da kishi Kawai take, watanta biyar da yazid ko batan wata bata tabayiba, kullum tana fadawa mom dinta rashin batan watanta amma sai mom dinta ta fada mata its nothing wai itama saida tayi shekara uku Sannan ta samu cikin mufida, amma yanzu shine wata zata rigata haifawa yazid da ko ya</p><p>"Shege ne..." Ta fada cikin ranta, hakan yasa ta Dan saka ranta a inuwa amma still bata bar kuka ba. Tana cikin kuka bacci ya dauketa nan kan gadon Hajiya. Yazid kam yanda ya ga dare haka yaga rana. Haka Hajiya babba da Hajiya karama ma duk basuyi bacci ba.</p><p>Abangaren dija kam nan asibiti ta kwana inda yan waiting ke tsayawa, Allah ya taimaketa babu Wanda ya damu daita, kowa ta kanshi yake duk suna jiran yan uwansu su haihu lafiya kuma har garin Allah ya waye baa rasa mutane wajen ba, dija batayi wani baccin kirki ba saboda kuka da cizon sauro, tana fara ganin hasken gari mike ta dauki bag dinta, banda fitsari babu abinda ke damunta, kusa da wata mata dake zaune taje</p><p>"Dan...Allah... Ina.. Ake...fitsari?..." Ta tambayeta matar daga kanta tayi ta kalleta from head to toe tana mamakin me yasa zaa zo da irin wannan karamar yarinyan wajen haihuwa, wata kofa ta nuna mata batare data ce mata uffan ba. Da Sauri dija ta shiga cikin wurin rike da bag dinta don rike taje da bag dinta tamkar her life depends on it. Wurin babu laifi its neat, durkusawa tayi ahankali saboda yanda wani abu ke tokare mata maranta, tana fitsari tana wash, saboda yanda fitsari bai zuwa da yawa sai zafi da take ji ba don komai ba sai don tun jiya take jin fitsarin amma batayi ba sai yanzu</p><p>Tafi minti goma nan durkushe, for the very first time sai taji motsin abunda ke cikinta, dafe cikinta tayi don kara tabbatar da abinda taji amma sai komai yayi still. Kallon tap dake running tayi sai tayi tunanin why not tayi wanka tunda batasan kowa ba balle ta samu inda zatayi wanka later in the day, ajiye bag dinta tayi ta leka waje don tabbatar babu mai jira Sannan ta koma ciki ta kulle kofan, rataya bag dinta tayi Sannan ta cire kayan cikinta, tsayawa tayi tana kallon cikinta. Jikinta ta kalla da tsawun dukan ammi dake kwance bisa skin dinta. Kuka ts farayi. Tana kuka har ta gama wanka amma bada sabulu ba. Kayan data cire ta maida, bude bag dinta tayi ta koma gefe ta fiddo kudin da ammi ta watsa mata da yawa amma babu kudin kirki cikin su, duk yan biyar, goma, ashirin ne babban kudin dake ciki shine Dari biyu, ta kusa hour tana counting dinsu. Sun kai kusan dubu sha biyar, arranging dinsu tayi according to girmansu daman abinda ta sabayi kenan tun a gida. Saida ta gama ta fito tana tafiya ahankali. Bakin asabitin da akwai masu saida kayanci kala2 irin su taliya, kosai, koko da sauran su, wurin wata mkata dake soya kosai da koko ta nufa ta ajiye bag dinta ta zauna sama Sannan tace a bata koko da kosai, daman jos ba kaman sauran garuruwa yake ba, babu Wanda ya damu da ita. Nan ta zauna taci ta koshi Sannan ta koma gefe tana kallon masu harkokinsu.</p><p>Tagumi tayi tana tunanin abinda zai biyo baya, ammi ta fado mata ga rai,</p><p>"Yanzu ammi ta yafeni kenan?... Yanzu ammi bata Sona kenan?... Yanzsu ammi ta cire ni cikin yaranta kenan?..." Ta dinga tambayan kanta cikin ranta, Dan take baki tayi hawaye suka fara gangaro mata, da Sauri ta da hannu ta goge face dinta.</p><p>💙💚💛🖤💜❤</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙🖤💚💛❤</p><p>®zuwairat(ummumaryam)</p><p>2⃣0⃣</p><p>Don't forget to follow and vote me on wattpad @ *ummumaryam29*</p><p>_Thanks sweetie, novel am feeling your love and affection_</p><p>Ahankali ya amsa ya ajiye gefe daya sannan ya dafa chest dinshi saboda ba karamin zafi yake ji ba, gani yake kaman romon naman zai hau mashi brain dinshi, idanuwanshi su kara ja, Hajiya karama hannu tasa ta dinga shafa bayanshi ahankali Har ya samu sauki.</p><p>"Pls kasha tea..." Tafada mashi ahankali, ba musu ya dauka ya sha zuwa rabi amma da gudu ya mike ya kama hanyan bedroom yana kakarin amai,</p><p>"NA shiga uku...wannan yaron nason saka kanshi cikin matsala...." Inji Hajiya karama, kafin ya shiga bathroom ya saki amai kasa yellow kaman mai rashin lafiya. Saida ya amai da Dan tea din daya sha ya mike ya shiga bathroom ya wanke bakinshi sannan ya taka ahankali ya dawo bedroom ya kwanta. Hajiya karama ce tasa asabe taje ta goge inda ya bata, yana kwance yana kallon ta tana aikin ta, asabe kam cikin tsoro Kawai take don yanda take ganin kaman zai kamata ya danneta.</p><p>Jikinta na rawa ta gama goge wurin Har zata bar wajen ya kirata, jikinta na rawa ta juyo ta kalleshi, ahankali ya daga manyan idanuwanshi ya kalleta sannan yace</p><p>"Pls..kinga....khadija sanda tazo nan gidan?..." Yafada ahankali, surprise look ne kwance kan fuskar asabe,</p><p>"Ko baki ganta ba?.." Ya sake tambayan ta, da Sauri tace</p><p>"Tunda ta tafi..ba kara ganinta ba...." Ta amsa mashi muryanta na rawa,</p><p>"Ok..you can go..." Yafada idanuwanshi lumshe. Bayan kaman minti biyar ya mike ya fito tsakar gidansu masu gadi sai gaidashi suke amma banda wannan tsohon guda daya dake da masaniya kan abinda ke faruwa. Ko kallon su baiyi ba ya shiga part din mom dinshi, lokacin an shirya su marzuq da zasu school. Mom dinshi na tsaye rike da lunch box dinshi tana gyara mashi button din Riga, yana gani yazid ya tafi da gudu ya fada mashi, bayanshi Kawai yazid ya shafa bai daukeshi kaman yanda ya saba daukan shi ba cos da kyar yake daukan kanshi. Mom juya baya tayi yayi saurin durkusawa gabanta</p><p>"Mom...pls....forgive me...." Yafada hawaye na taruwa idanuwanshi, kokarin wucewa tayi amma ya rike mata kafa,</p><p>"Pls ki yafemin..." Yafada yana fashewa da kuka dukda muryanshi bai fita sosai . marzuq tsayawa yayi yana kallon su, horn din motan da akayi yasa marzuq barin su cike da tambaya cikin ranshi abinka da inquisitive child. Mom kwace kafanta tayi</p><p>"Laifin me kayi min...its your life.. And you have decided to live it the way you want... So ni babu ruwana...." Tafada tana kokari barin wurin, da rarrafe ya tare gabanta,</p><p>"Wallahi..mom ba halina bane...kaddara ne ya fadamin....ban taba kama hannun mace ba..."</p><p>"Amma Har ka Iya raping yar yarinya ..." Mom ta katseshi, yana girgiza kai yana cewa</p><p>"Mom sharrin shaidan ne...am sorry.. Pls...." Yafada cikin matsanacin kuka, mom goge hawayen face dinta tayi ta fixge kafanta daga hannun shi ta bar wajen, ahankali ya koma ya zauna kasa yacigaba da kuka, kofa aka bude ya daga kai ya ga mufida ce tsaye itama Sam fuskanta babu walwala, amma ganin yanda yazid ke kuka yasa ta saki ranta, ahankali ta karaso wajenshi itama ta zauna nan kasa, kura mashi ido Kawai tayi tana mamakin irin wannan kaddara.</p><p>"Baby am sorry... Khadija is pregnant..." Yafada mata cikin kuka, dukda zuciyanta na tafasa hakan bai hanata tallabo face dinshi ba,</p><p>"Stop crying... Haka Allah ya kaddara..."</p><p>"Baby NA CUCE TA...NA zalunceta...she's too young for this...." Yafada cikin kuka, baki mufida ta tabe</p><p>"But she's not young for you to sleep with... Yanzu dai zaa Haifa maka shege kafin ka samu na halal..." Tafada sounding very angry,</p><p>"Ba laifina bane...laifin kaddara ne...." Dan guntun tsoki taja,</p><p>"Da wannan kaddara yasa kaje kayi sata an harbeka dayafi maka gaskiya..." Ta fada atakaice ta mike ta barshi nan zaune, yana nan zaune yana tunanin halin mufida, one second she nice the other second she's mean. Ahankali ya mike ya shiga dakin da mom dinshi ta shiga, tana zaune bakin gado tana kuka, ya karasa gabanta</p><p>"Mom am sorry... Pls..." Banza tayi dashi ta cigaba da hawaye abinta</p><p>"Mom zan tafi....zanje Neman ta...." Yafada ahankali yana hawaye, mom dai batace uffan ba. Yana nan durkushe gabanta yana kuka tana kuka Har Salem yazo suka bar gidan. Yanayin shi ba karamin tadawa Salem hankali yayi ba don gani yake kaman wani mugun abu na Iya faruwa da best friend dinshi.</p><p>Yana tuki ya juyo ya kalli yazid daya rumtse idanuwanshi yana Allah Allah su isa katsina yace</p><p>"Guy wai ka manta kaddara ne?... Duk kabi ka damu kanka saboda wannan abun...we can't stop destiny... What will be will always be...ka sassautawa kanka pls...." Inji Salem, yazid dai baice kala ba Kuma bai bude idanuwanshi ba. Kusan a haka suka isa garin katsina around 10:30, amsan address din yayar Hajiya karama yayi yaga goruba road da number gidan, baisan goruba road ba don wurin grandparents dinshi Kawai yake zuwa</p><p>"Bari muje family house dinmu don mu nemi wani cousins dina su rakamu...." Salem ya fadawa yazid, ahankali yazid ya girgiza mashi kai,</p><p>"No pls...zaa bata mana lokaci...Kawai Bari in kira small mom ta fadawa sister dinta muna wajen round mai kwarya don ta aiko driver dinta yayi directing dinmu...." Yafada ahankali Sannan ya fiddo wayan shi yayi dailing number Hajiya karama ya sanar daita.</p><p><br /></p><p>❤💛🧡🖤💜💙💚</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙💚🖤💛🧡❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>®Zuwairat (ummumaryam)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>2⃣1⃣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Don't forget to follow and vote me on wattpad *@ummumaryam29*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Salem na tuki yayi dailing number Hajiya babba few seconds later Hajiya dake zaune kan gado tayi picking tare da sallama, gaidata yayi sannan ya fara cewa</p><p>"Mom...yazid yaki tahowa...." Ya fada ahankali, Hajiya shuru tayi for a while sannan tace</p><p>"Wannan matsalan shine...if he wants he can remain they for ever...." Ta fada atakaice sannan ta katse wayanta, Hajiya Aisha dake jin abunda Hajiya ta fada shuru tayi amma she feels pity for yaxid, Salem ajiye wayan yayi cikin sanyin jiki ya cigaba da tuki. Yana isowa kofar gidan Hajiya Aisha yayi parking ta fito yayi mata godiya har zata shiga gida ya tsaida ta tare dacewa</p><p>"Pls Hajiya da akwai wani babban supermarket nan?..." Ya tambayeta</p><p>"Yes...if you reverse... Kayi taking left turn then drive for like 8 minutes zaka </p><p> ga wata babba supermarket, ..." Hajiya Aisha ta fada Mashi, godiya ya sake yi mata sannan ya barwajen, directions dinta yabi har gaban wata medium size supermarket, parking yayi har zai fito sai a dauki waya ya kira dad din yazid, bayan yayi picking ya gaidashi yake fada Mashi exactly abinda ya fadawa mom, ko uffan baice ba ya kashe wayanshi. Salem girgiza kai yayi yana cewa</p><p>"Ko so suke su kashe shi sabida just one mistake.... Ko tuna halin yazid basuyi,...mtwww..." Yafada yana dailing number Hajiya karama. Bayan sun gaisa har zaiyi magana Hajiya tace</p><p>"Ina yazid...." Cikin sanyin murya Salem yace</p><p>"Small mom yaki tahowa..."</p><p>"Ban gane yaki tahowa ba..."</p><p>"Mungano gidansu khadija...Ashe motan jos wannan hajjyan ta sakata saboda amminta ta koreta....to shine mukaje har wajen amminta amma taki bamu address din ta....shi kuma yazid yace in bata bashi ba bai dawowa...." </p><p>"What sort of thing is this?....yanzu yana chan gidansu khadija kenan?..."</p><p>"Yes mom...." </p><p>"Kai kana INA?..." </p><p>"Na maido hajiyan data rakamu gidane...amma zan koma chan....kuma I think uwar khadijan needs a medical attention..." Inji Salem,</p><p>"To ya zaayi kenan...ko zaka nemi wani doctor ka tafi dashi ya dubata?...I will repay....." Inji Hajiya karama</p><p>"Wannan ba matsala bane..Allah yasa in samu...don wurin is a little bit low ne...amma I will search...." </p><p>"Yauwa thanks.... Bari in kira shi yazid...." Ta fada Mashi sannan ta katse wayata. Salem shiga cikin supermarket din yayi </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Daga chna gidan su dija, yazid daya gaji da jingina da bango sai ya dan kwanta tare da yin pillow da hands dinshi. Idanuwanshi lumshe amma ba bacci yake ba don yana jin duk tarin da ammi dake kwance takeyi. Bai Dade da kwanciya ba wayanshi ta dau kara, bai bude idanuwa ba ya saka hannu cikin aljihunshi ya fiddo wayan yayi picking. </p><p>"Yazid... " yaji muryan Hajiya karama ta kirashi</p><p>"Yes mom..." Ya fada in a very low voice da sai mutum ya Kasa kunne zaiji abinda yake cewa</p><p>"Wai me nakeji?..."</p><p>"Babu....komai...pls..." Bai idaba ta katseshi dacewa</p><p>"To in bakason ranka ya baci... Ku taho da Salem...." Ta fada Mashi atakaice, daga kwance ya girgiza kai</p><p>"Mom...am...sorry... Ban dawowa...sai an fadamin inda khadija take..."</p><p>"Ina fada maka ka dawo kana arguing dani?...."</p><p>"Mom ba haka bane....I can't leave thinking I have made an innocent gal an outcast... Pls mom kuzo Ku bata hakuri ko zata ga girman ku ...pls..." Yafada hawaye na gangarowa daga closed eyes dinshi, </p><p>"Dalla rufemin baki....ba ance tana wajen families din amminta ba?...." Ta daka Mashi tsawa,</p><p>"Mom...in suma sun koreta fa?.... Amminta ta koreta ballesu?...pls kuzo...." Ya fada yana kuka ahankali</p><p> Ajiyan zuciya Hajiya karama ta sauke sannan tace</p><p>"Haba dear...in ka zauna wurin zai nuna kaman you are proving stubborn... So ka dawo sai Ku koma bayan few days...." Yazid kai ya dinga girgiza kaman tana tsaye tana kallon shi </p><p>"I can't mom...I will stay...." Bai idaba Hajiya karama ta katse dacewa</p><p>"Wato gardama kake dai yimin ko?.... Kanason in cire hannuna cikin cases dinka?...".</p><p>" no..Mom... "</p><p>"Then come back home..." Yana shesseka yace </p><p>"Am sorry... Pls am sorry...I can't leave...." Ya fada ahankali sannan ya katse wayan tare da kashewa completely, sulalar da wayan yayi nan kasa yana goge face dinshi daga inda yake kwance.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abangren dija yawo ta dingayi nan cikin gari kuma duk in taga hankali mutane zai zo kanta barin wurin take ta koma wani wajen, kuma duk inda taga mata most especially age mate dinta masu tallah da sauransu take zuwa. Har zuhr bata karacin komai ba sai da cikinta ya fara motsi sosai sannan ta samu wurin masu saida abinci ta zauna ta saya taci</p><p> Tana ci tana hawaye sai kuma tayi saurin gogewa don kar ganta, tana gamawa ta mika kwano ta mike daga wurin tare da rataya bag dinta. Duk yawon da take bata nesa da hospital don tamkar resident dinta ta dauki. Har asr tana cikin yawo amma saitaji her legs is getting cold hakan yasa ta nufi cikin hospital, abunka d general hospital babu Wanda ya damu da harkan wani balle a gane she's not a patient, har zatayi hanyan Inda ta kwana sai ta tuna kar a ganeta, haka yasa ta fara searching inda zata zauna ta dan huta, tana tafiya ta hangi wata katuwar hall mai dauke da many sits wasu da akwai mutane amma most of them are vacant, ahankali ta biya ta wurin tana tafiya a hankali hannunta rike da bag dinta dake kan shoulder dinta kaman her life depends on it. Daga bayan sit ta koma ta zauna the last row don gani ko zaa koreta amma har kusan minti goma da zamanta babu mai kallon ta haka ya bata kwarin gwaiwan kwanciya tare dayin pillow da bag dinta, batafi minti biyar da kwanciya ba bacci ya dauketa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Salem baiyi wasting time ba ya shiga cikin Supermarket din ya sayi yoghurt drink da snacks kala2 sannan ya fito har zai shiga cikin mota ya hangi wata babba chemist, ajiye ledan hannunshi yayi sannan ya nufi chemist din, wani matured man ya gani rike da news paper sai medical specks a face dinshi. Sallama Salem yayi Mashi mutum ya amsa gaisawa sukayi sannan Salem ya fada Mashi abinda yake bukata. Nan mutum ya shaida Mashi hes a medical doctor kuma zai bishi amma wai he will not go alone saboda tsaro, dariya kawai Salem yayi. mutum kiran wani saurayi yayi yasa ya rufe chemist din sannan suka shiga mota su uku suka kama hanyan gidansu dija</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A gidansu dija around 5:30 suka dawo daga makarantan allo, nan suka ga mutum kwance tsakar gidansu, kasa motsi sukayi dukkansu, especially binto,</p><p>"Ammi!!...Ammi!!..." Ta dinga kwalawa kira tana Jan baya, ihunta ya sa yazid bude ido ahankali, same ihun yasa Ammi dake kwance daki mikewa zaune don batasan d mutum wurin ba</p><p>"Ammi... Zo ki gani...wani ne cikin gidan mu!...." binto ta fada da karfi, ahankali yazid yaso mikewa zaune aikam sukayi waje da gudu daman bakin zaure suke, dukda halin da yake ciki saida yayi murmushi don da bai cikin matsala da dariya zaiyi har ya koshi cos ba karamin dariya suka bashi ba, ahankali Ammi ta rike bango ta fito tana takawa ahankali kaman mai tausayin kasa, tana fitowa tayi tozali da yazid</p><p>"Me...kake....anan?..." Shine tambayan datayi Mashi tana magana da kyar, ahankali yazid yayi kneeling</p><p>"Dan Allah....kiyi min rai....kiyi hakuri..." Yafada kanshi kasa, hanyan waje ta nuna Mashi </p><p>"Ka...fita...ka barmin....gida....ka.fita kafin...in tara maka...mutane...." Ta fada tana dafe da chest dinta. Yazid kam ko gizau don ya rantse bai barin gidan sai da address din dija.</p><p>"Ka...tashi... Nace...." Ammi ta fada this time tana fashewa da sabon kuka,</p><p>"Kiyi hakuri ki yafemin....kukanki kawai is a enough to get me burning in hell...the cry of an innocent widow will definitely take me to hell...." Ya fada kaman tanajin abinda yake cewa, ammi kam tari ya sha kanta don haka ko kallon shi batayi ba at each minutes tarinta na increasing, ahankali yazid yayi crawling zuwa inda take tsaye tana tari, ammi bata ankaraba taji an rike mata kafa, tsoro taji tayi saurin ja da baya, tana Jan baya ya kara rike mata kafa</p><p>"Ki yafe ni...kiyi hakuri... Ki fadamin inda khadija take.... Dan Allah...." Yafada dan guntun hawaye da fitowa daga swollen eyes dinshi</p><p> Ammi tsayawa tayi tana kallon shi, kura Mashi ido tayi tana ganin nadama koina na fuskanshi, amma dayake tana da dakakken zuciya sai ta kara janye kafanta don gani take abinda ya aikatawa yarta ba abu bane wanda zaa yafe, gani take he deserves to die for what he did to her dija, </p><p>"Ka barmin...gida...." Shuru tayi tana kallon zaure da ake sallama, bata amsa ba haka shima yazid, daman Salem bai expecting a amsa don haka shigowa kawai yayi tare da mutane dake bayanshi, ammi kallon haushi da takaici tayi masu,</p><p>"Wai nace...Ku bar min...gida....wallahi.. Zan tara maku mutane...." Tafada tana tari, this time vomiting ta farayi sosai tana saukowa kan knees dinta, da sauri yazid ya mike d sauran strength dinshi shima Salem tahowa yyi da sauri ya rike shoulder dinta, ammi sai a man jini kawai take, amma sai ture hannun Salem dake shoulder dinta kawai take. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Su binto kam ko da suka fita suna ihu basu tsaya koina ba sai gidan kawu nanu,</p><p>"Kawu....kawu....wayyo Allah kawu wani mutum ne gidan mu.....kuma bamu ga amminmiu ba...dan Allah ka taho...." Binto dake haki kaman wacce ta kubuto daga bakin kura ta fadawa kawu nanu dake alwallah, kallon banza ya watsa mata,</p><p>"Wai Ku ba a koya maku gaida manya ba?..." Ya fada bbu wasa, binto dafa chest dinta tayi saboda yanda yake beating very fast, </p><p>"Kawu..amminmu...." Karamin cikinsu ya fada yana fashewa da kuka sai lokacin ya gano da akwai matsala,</p><p>"Me ya samu amminku?..." Ya tambayesu, nan binto ta kara fada Mashi abinda ta gani, kaman kar yaje don shima tsoro yakeji</p><p> Amma yayi ta maza ta mike ya shige masu gaba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dija tana nan kwance ta har daf da magrib, jitayi ana taba mata kafa, da sauri ta mike data tuna da inda take bacci, wata babbar mace ta gani tsaye tare da wata yarinya wacce bazata wuce 16 to 17 ba, dija hannu tasa ta goge bakinta tare da sadda kanta kasa,</p><p>"Ya akayi kike nan wajen har magrib?...ko baki samu ganin doctor bane?...." Shine tambayan datayi mata, dija ajiyan zuciya ta saki don gani take dukanta zatayi, da sauri ta gyada mata kai,</p><p>"Ke kadai kika zo ganin doctor?..." Hajiya ta kara tambayan ta, kara daga mata kai, matar tsayawa tayi ta kura mata ido for a while kaman xatace wani abu sai kuma tayi shuru tace</p><p>"To ki tashi ki tafi... Baa ganin doctor yanzu...sai in emergency ne...." Da sauri dija ta mike jikinta har rawa yake, budurwan dake tare d matar kura mata ido tayi tana kallon ta, same ita ma Hajiyan sai kallon dija dake sauri kawai take, </p><p>"Mom ni tausayinta nakeji...." Yarinya ta fada tana rike hannun mom dinta sannan ta tale baki kaman zatayi kuka, ni kuma kurawa yarinya ido nayi sai naga remarkable resemblance dinta da sultan coworker don yazid, </p><p>"Me akayi na tausayi yanzu da kike Neman kuka?..." Matar ta tambayeta suna takawa ahankali xuwa wajen wata black jeep dake tsaye, </p><p>"Mom kilan bata da mommy... Nasan inda mommy tana da uwa tare zasuzo ganin doctor...." Ta fada tana kankame hannun mom dinta, matar batace kala ba suka kusa zuwa wurin motan wani ya fito ya bude kofa amma yarinya ta tsaya</p><p>"Mom dan Allah ki sa wani doctor ya duba ta....mom daga gani ba daga nan garin ta ke ba....." Yarinya ta fada tana buga kafa kasa,</p><p>"Zaki fara rigiman ko?... To ki shiga hankalinki ko kuma you will never set foot in this hospital again...." Ta daka mata tsawa, kuka ta fara yi tana</p><p>"Sorry mom...." Ta fada ahankali tana shiga motan, </p><p>"Shahida kiyi hakuri, da akwai mutane da yawa irun wannan... In kace zaka fara kiran doctor suna dubasu daga baya bakinka zaa gani a dinga cewa sabod you are ahead of them shine kake yi masu haka...." Ta fada tana gogewa daughter ta face dinta, </p><p>"Kin San halin mutane...." Ta karasa maganar tana jawo yar ta jikinta</p><p> Bata kara cewa komai ba driver ya jasu suka bi hanyan gate amma sai waige2 take chan ta kara ganin dija dake tafiya zata tsallaka titi tana rungume da bag dinta. </p><p><br /></p><p>Dija na tsallakawa ta koma wajen yan matan dake saida abinci ta zauna nan kusa dasu, wani irin fitsari take ji don maranta yayi fam, zama tayi tana matse legs, da kyar ta iya bude baki ta tambayi wata inda zatayi fitsari, kallon ta yarinyan data tambaya tayi sannan tace</p><p>"Wai ke baki da gida ne?.... Jiya ma na ganki?..." Ta tambayi dija ahankali, dija shuru tayi bata ce komai ba. Ganin bazata bata amsa ba yasa itama ta daure fuska sannan tace</p><p>"Ga wani gida chan...kiyi sallama killan su barki kiyi fitsarin....", da sauri ta mike tayi gidan da aka nuna mata, cikin Saa aka barta tayi fitsari wannan Karin ma fitsari bai fitowa sosai, tafi minti goma nan durkushe sannan taji saka ta mike ta dawo wurin yarinya mai saida abinci ta saya yanda zai isheta.</p><p>Ammi tafi minti biyar tana wanna amai duk hankalin yazid da Salem ya mugun tashi, mutum da salem ya zodashi ya fara cewa</p><p>" gaskiya sai dai a kira ambulance a tafi daita hospital wannan yafi karfin home medicine.... " yafada Mashi atakaice, yazid dai kasa magana yayi. </p><p>"Waye nan cikin gidan?!..." Aka fada da karfi daga zauren gida Dukkansu maida hankalinsu, ammi ta kara ture hannun Salem dake shoulder dinta, da sauri yazid ya taka ahankali xuwa zaure, yana ganin babban mutum yayi kneeling cos he knows mutum family ne kuma a nashi tunanin yasan abinda ke faruwa,</p><p>"Dan Allah kuyi hakuri....Ku yafemin Ku fadamin inda khadija take...." Ya fada palm dinshi biyu harde wuri daya,</p><p>"Kai waye?...." Shine tambayan da kawu nanu ya yiwa yazid, yazid sadda kai kasa yayi sannan yace </p><p>"Ni....ni...nine....nayi...." Tari ammi ta dingayi da karfi don kar ya fada amma ko waigowa baiyi ba don shi bai gane manufar ta ba</p><p>"Ni...ne..nayi...mata...ciki...."</p><p><br /></p><p>[6/22, 4:29 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: Na cuceta 22</p><p>by Ummu Maryam</p><p>❤🧡💛🖤💜💙💚</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙💚🖤💛🧡❤</p><p>®Zuwairat (ummumaryam)</p><p>2⃣2⃣</p><p>Wattpad: ummumaryam29</p><p>Or</p><p>Visit www.ummumaryam.com for more</p><p>_Love you beautiful people_</p><p>Kawu nanu bude baki yayi don bai gane inda yazid ya nufa ba,</p><p>“Dan Allah kuyu hakuri….” Yazid ya kara cewa</p><p>“Wai ni ban gane ba….wa kayiwa ciki?….” Kawu nanu ya tambayeshi full of surprise, sadda kai kasa yazid yayi don sai yanzu ya San bai San da maganar ba, ammi sai kuka take tana</p><p>” Allah yaisa…. ”</p><p>“Ku fadamin mana…wa akayiwa ciki?….”</p><p>“Dija….” Yaji binto ta amsa mashi</p><p>Baki kawu nanu ya bude ita kuma ammi ta kara tsananta kukanta,</p><p>“Wai wace dija?…” Ya tambaya cikin tashin hankali, dukkan su shuru sukayi</p><p>“Ashe dija ciki gareta!!!!…Ashe karuwanci kika kaita?….amma ke gwadayinki ya jawowa zuriyan dan uwana abun kunya…..” Ya fada cikin fada,</p><p>“Babu…laifinta….laifinane….kuyi hakuri dan Allah….” Yazid ya fada yana hawaye. Likitan da yazid ya zo dashi kallon agogon hannunshi yayi</p><p>“Ya muke ciki….za taho da ita cikin birni ko yaya?….” Ya tambayi Salem, Salem kallon ammi yayi</p><p>“Dan Allah ki taso a kaiki asabiti….kina bukatan likita….” Salem ya fadata mata in a soft tune, ko kallon shi ammi batayi ba ta dafa bango ta mike</p><p>“Duk garin nan sai sun San abinda ki kayi…. Sai na fadawa mutanen garin nan yanda kika wulakanta rayuwa dija saboda kudi….” Kawu nanu ya fada tare da Jan tsoki sannan ya fita daga cikin gidan, da sauri yazid ya mike daga inda yake durkushe yabi bayan kawu nanu dake ruwan balai sai magana yake da karfi,</p><p>“Dan Allah ka saurareni….in ka fada min inda khadija take… zan baka kujeran Makkah….” Kawu nanu dake sauri yayi slowing down dajin kujeran Makkah, ganin yanda ya dan saurara yasa yazid kara cewa</p><p>“Zan saya maka mota….dan Allah ka fadamin inda khadija take… .” tsayawa yayi ya juyo tare dacewa</p><p>“Ai ban San inda take ba….” Ganin zai shawo kanshi yasa yazid cewa</p><p>“Ance tana Jos…wurin dangin amminta….” Yazid ya bashi clues, shuru yayi ya dan sauke murya sannan yace</p><p>“Da gaske kake zaka bani kujeran Makkah da mota in har na baka adireshinta?….” Ya fada yana waige2 kaman Mara gaskiya,</p><p>“Bana karya….da gaske nake… Ka bani address dinta nikuma na tabbatar da kai zaa sauke farali wannan shekaran….” Yazid ya kara tabbatar Mashi, wani irin murmushi ya saki sabida jin dadi sannan yace</p><p>“Matso kusa kaji….” Yafadawa yazid, da sauri yazid ya matso da kunnenshi saitin bakin shi, kaman mai munarfirci ya fara fada Mashi tiryantiryan yanda zaije gidansu ammi, wani irin ajiyan zuciya Yazid ya saki tare dacewa</p><p>“Nagode… Nagode… Nagode…. Kar shirya zakaji daga gareni….” Ya fada sannan ya juya ya koma gidan.</p><p>Ammi na shiga ciki ta tattara yan rags dinta dana sauran yaranta ta kwalawa binto kira, da sauri binto ta shiga ciki, kayan data daure da tsumma ta Dora mata bisa kai don tasan in har ta zauna kawu nanu ya sanar da mutanen gari ba karamin wulakanci zata fuskanta ba, hakan yasa ta yanke hukuncin tafi kafin mutane su San abinda ake ciki, yazid dai tsaye yayi shi kuma Salem na tunanin kilan ammi shirin zuwa hospital take.</p><p>Suna tsaye binto ta fito da kaya kanta, itama ammi fitowa tayi ta jawo kofan ta rufe sannan ta tisa sauran yaran biyu gaba suka bar gidan, yazid kallon Salem yayi baice komai ba illah haushin kanshi dake cike da zuciyanshi don gani yake Allah bazai taba yafe Mashi ba. Salem ne yayi karfin halin bin baya ammin dake tafiya da kyar</p><p>“Yanzu ina zaku?….” Ya tambayeta cikin sanyin murya, ammi shuru tayi bata amsa ba,</p><p>“Kindai San anayiwa Allah laifi kuma ya yafe mana…dan Allah kiyi hakuri…ki tsaya mu rage maki hanya…kinga dare yayi…dan Allah….” Yafada mata in a caring tune,</p><p>“Kinga dai bani nayi maki laaifi ba…ki daukeni a matsayin dan uwa dan Allah ki tsaya mu rage maki hanya…kin ga dare ya farayi kuma ga yara…dan Allah ki bari in rage maki hanya.” Ya sake fada mata in a cool tune, Ammi bata CE komai ba amma ta tsaya, yazid na tsaye bakin kofar gidan yana kallon su dukda baijin abinda suke cewa amma kullum gidewa Allah yake daya bashi amini kaman Salem, Salem na ganin ammi ta tsaya yayi baya da sauri don shaidawa yazid da doc su fito, bakin kofar gidan ya tarda yazid,</p><p>“Thanks…” Yazid yace Mashi ahankali, kallon haushi Salem yayi Mashi</p><p>“For?….” Ya tambayeshi bai tsaya sauraron amsanshi ba ya shiga ya kira doc don lokacin garin ya fara duhu sosai. Fitowa sukayi, duk suka shiga mota,su uku a gaba sai yaron doc a baya. Inda ammi ke tsaye ya kai mota sannan ya fito ya bude masu kofar motan suka shiga sannan suka kama hanyan cikin garin daura.</p><p>Ana kiran sallan ishai suka isa daura, ajiye doc Salem yayi ya bashi kudi amma yace a barshi, dukkan su babu mai cewa komai sai sound din tarin ammi dake tashi time to time,</p><p>“Dan Allah in kaiki hospital?…” Salem ya tambayeta, ahankali ammi ta girgiza kai tare dacewa</p><p>“Aa….”</p><p>“Dan Allah fa nace…ki bari ni in kaiki hospital…”</p><p>“Aa…in naje gida zansha magani….” Ammi ta amsa Mashi ahankali,</p><p>“Yanzu wane gida zaki?…” Salem ya kara tambayanta cikin sanyayyan lafazi,</p><p>“Jos….dan Allah da munje katsina… Ka ajiyeni a inda ake hawan mota….” Ammi ta fada Mashi, shidai yazid shuru yayi yana sauraronsu sannan yana mamakin how comes ammi take amsawa Salem?,</p><p>“Ai da kyar ki samu motan yanzu… Kawai in kaiku gidan kakana Ku kwana …gobe sai in kaiku….”</p><p>“Aa…haka ma mun gode….” Ammi ta amsa Mashi ahankali, Salem dai bai kara cewa komai ba, ledan kayan daya saya dake gabanshi ya bude ya fidda juice daya ya ajiyewa yazid kan kafanshi shi ya dauki daya sannan ya mika sauran bayan motan, da sauri autan ammi ya ashe daga hannunshi. Ko daya shiga cikin garin katsina bai saurari korafin ammi na ya kaita park ba, saida yaje kofar family house din parents dinshi sannan ya tsaya, da kyar ammi ta yrda t fito ta shiga gidan inda grandparents din Salem suka amshesu with happiness, yazid kam yana nan zaune cikin mota bai fito ba, Salem ne ya fito daga cikin gidan ya sameshi, bude motan yayi</p><p>“Kafito ka rama salat da ake binka….” Salem ya fada yana kallon juice dake kan kafan yazid untouched, yazid rumtse idanuwa yayi</p><p>“Wai kai so kake ka kashe kanka?….through out muna tare banga kaci komai ba…pls drink this…” Ya fada ya bude juice ya mika Mashi,</p><p>“I can’t….” Yazid ya fada Mashi muryan shi na cracking,</p><p>“I can’t…” Salem yayi mimicking dinshi sannan yacigaba dacewa</p><p>“That’s why baason mutum ya nuna his over perfection… Kai kullum what ever you did is right… Kai kullum mu yan iskane…kullum gani kake we are sinners…amma yau wa gari ta waya?…. Nobody is perfect… Nobody is above mistakes… No body is above destiny….am sure this is a good lesson ga mutane irin Ku that always think they are the best….gashi kaje kayi screwing small gal abun ya dameka…mtwssss…” Ya fada sannan ya mika Mashi hannu, ahankali yazid ya dora hannunshi kan palm din Salem, janyoshi Salem yayi daga cikin mota ya rufe motan sannan suka nufa inda suke sauka in sun zo KT, wanka yazid yayi sannan ya rama salats da ake binshi, jingina yayi da bango</p><p>“An fadamin inda khadija take….” Ya sanar da Salem,</p><p>“Waya fada maka?…”.</p><p>” wannan mutum dayazo…” Surprise look salem yayiwa yazid</p><p>“Wannan mutumin deke fada?… How comes ya fada maka?…” Ya fada yana gyara zamanshi tare da bude foodwarmer dake gabanshi, dan murmushi yazid ya saki</p><p>” I bribed him….” Dariya Salem yayi</p><p>“Kai ka fara mugun abubuwa da yawa…kasan bribes is haram…dame kayi bribing dinshi?….”</p><p>“None of you business….” Yazid ya fada yana daukan wayanshi,</p><p>Cikin kasala ya bude waya yana aduan Allah yasa ya samu ko one word SMS ne daga wajen mufida don tun safe basuyi waya ba, yana gama kunna wayan ya ajiye ko message zai shigo amma babu sai freaking annoying Mtn messages, daukan wayan yayi, number mufida yayi dailing, ringing kawai wayan take amma babu response,</p><p>saida ya jira mata upto five miss calls amma bata daga ba, kallon Salem dake kwasan loman tuwo da miyan dry okro yayi</p><p>“Wai me yasa mata basu da tausayi ne?…” Inji yazid, daga kai Salem yayi</p><p>“Gaskiya in baka ci wannan tuwon ba kayi missing…” Salem ya fada off point yana lumshe eyes, dan guntun tsoki yazid yaja yana ajiye wayan</p><p>“Wai bakaji abinda nace bane?…” Yq fada ahankali Wanda in mutum bai kasa kunneba bazaiji abinda yace ba</p><p>“Me mata sukayi da basu da tausayi?…”</p><p>“Wai ina ta kiran mufida…she’s not picking up…” Baki Salem ya tabe sannan yace</p><p>“Wallahi you are annoying…. Ai you are Lucky to have mufida…am sure in wasu Matan ne the relationship would have gone down the drainage… ”</p><p>“Amma kasan it’s not my fault…” Yazid ya fada yana kwantawa nan kasan carpet dayayi sallah dashi, murmushi takaici Salem yayi</p><p>“Ai its my fault tunda da joystick dina kayi raping khadija… Or better still laifin mufida ne cos ita ta wangale maka kafan khadija… You have got some nerves wallahi….” Yafada yana wanke hands dinshi, yazid lumshe idanuwa yayi har yanzu yana kallon the look of terror a idanuwan dija sanda yake devouring dinta, bai kara cewa komai ba don he don’t have enough strength, Salem tura tuwon yayi gabanshi</p><p>“Kaci kar ka mutu kafin a haifi bastard dinka….” Ya fada yana dariya, yazid daga big but tired eyes dinshi yayi ya kalli Salem</p><p>“That is not funny!!!….” Ya fada da karfi</p><p>“To sorry… Kaci kar ka mutu kafin a haifi dan sunnah ka….” Salem yafada this time laughing very loud,</p><p>“Its not funny either… Just stop it pls….” Yafada yana begging dinshi,</p><p>“OK naji…amma pls I beg you in the mane of Allah… Kaci abinci…you look terrible… Pls eat ko kadan ne….”</p><p>“I can’t eat solid food…amma in da ruwan zafi just help me with a cup of tea….” Ya fada ahankali, Salem bai kara cewa komai ba ya mike, dakin ya bari, few minutes later ya dawo da mug of tea ya mika Mashi.</p><p>Dija dai kaman jiya tana nan bakin titi har saida mutane suka fara watsewa sannan ta koma cikin hospital, luckily enough yau ma da akwai mutane so security din wurin bai wani maida hankali kanta ba, nan kan kujeran waje ta kwanta, duk cizon sauron bai hanata bacci ba.</p><p>Tana bacci tana scratching legs dinta da sauro ke sucking.</p><p>The following day ko breakfast ammi batayi ba suka kama hanyan wai zasu park, Allah ya taimaka da su salem bazasu San sun tafi ba, amma luckily suna fita shima yazid na fitowa, baida courage da zaiyi mata magana da sauri ya koma ya sanar sa salem.</p><p>Da kyar ammi ta yarda kan salem ya ajiyesu, ko wanka basuyi ba suka kama hanyan jos. Karfe bakwai saura suka bar katsina kuma tafiyan 490 km ne, so it takes them almost eight hours su isa cikin garin jos, daman da GPS salem yayi amfani cos baison damun ammi da tambaya amma daga garin jos zuwa village din su ammi ita ta dinga bashi direction, ana kiran sallan asar suka iso kofar wani karamin gidan which is not bad looking as gidan ammi na daura. Yazid dai ji yayi gabanshi na faduwa which he don’t know why, ammi fita tayi tare dayiwa salem godiya sosai, sannan suka shiga cikin gidan, yazid dan dafe chest dinshi yayi sannan yace</p><p>“My heart is beating very fast… Why is my heart beating like this…?” Ya fada yana kallon Salem,</p><p>“Kilan don zaka ga the mother of your bas…..” Irin kallon da Yazd yayi Mashi yasa shi shuru, fitowa sukayi suka bi bayan ammi, sallama sukayi a kofar gidan aka amsa masu, cikin gigantic compound din suka shiga, ammi ce zaune bakin wata kofa tana kuka dukkan mutane gidan sun taru kanta suna tambayanta, yazid kan tsayawa bayan salem yayi kaman wani shield</p><p>“Su waye wannan?….” Wani tsoho ya tambayi ammi, bata ce komai ba salem yace</p><p>“Wurin khadija mukazo?…” Ya fada kanshi kasa,</p><p>“To tana Ina?….” Shine tambayan da wata daga cikin tsafi dake tsaye kan ammi tayiwa salem, ammi dan tsagaita kukanta tayi ta daga kanta ta kalli Matan,</p><p>“Dija…bata…zo ba?….” Ta tambayi yan gidan?</p><p>“Zo ina wai?… Ba tare kuke daita ba?… Ko ta rigaku tahowa?…” Wata daga cikin Matan ta tambayi ammi, yazid ji yayi kafanshi bai daukanshi, daga nan inda yake tsaye ya durkusa kasa yana</p><p>“Na shiga uku… Na shiga uku…what have I put myself into….” Yafada kasan makoshin shi Wanda salem kawai yaji hakan, ammi ji tayi jikinta yayi sanyi</p><p>“Wai kuna nufin dija batazo ba?..” Ammi ta tambaaya cikin sanyin murya,</p><p>“Batazo ba….” Aka amsa mata, dafe kai ammi tayi ta rushe da sabon kuka, kunsan tsakanin da da mahaifi sai Allah, deep down she wanted to set her eyes on dija, she’s missing her like crazy duk da her pride and temper won’t let her show it, kukan da yazid keyi ya maida hankali yan gidan kanshi, da sauri salem ya kamashi ya mike yana</p><p>“Na shiga uku…maybe she’s dead…” Ya fada cikin kuka, mutanen gidan dai tambayan abinda ke faruwa suke amma babu mai amsawa, waje sukayi salem na rike da yazid dake kuka kaman ranshi zai fita, har bakin mota ya kaishi sannan ya sakeshi don bude Mashi mota amma yazid ya kara zama nan kasa</p><p>“Na shiga uku…kaicona…ya Rabbi I have learnt my lessons…ya Rabbi take me away…ya Rabbi take my life away… Na shiga uku….” Salem ne ya tsaya yana kallon shi, for the very first time da shima tears ya taru a eyes dinshi, yazid sai dirza kafa yake yana bugun saitin heart dinshi da hannunshi da sauran karfinshi,</p><p>“Pls stop it….stop it…you are hurting yourself….” Salem ya fada yana hawaye</p><p>“No…I don’t want to live anymore… Nafidon in mutu….I know I will surely die don ba zan Iya rayu da wannan bakin cikin ba…I raped her.. Get her pregnant… And now she’s nowhere tobe found…” Yafada cikin marsanacin kuka, dafa shoulder dinshi salem yayi</p><p>“Kwantar da hankalinka…zamu ganta…we will find her…”</p><p>“In bamu ganta ba fa?…”</p><p>“Then haka Allah yaso….now taso mu shiga cikin gari mu samu muyi sallah, yafada yana dagashi tsaye, da kyar ya mikar dashi tsaye tare da turashi cikin mota sannan shima ya shiga mota suka bar wajen.</p><p>[6/22, 4:31 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: NA CUCETA 23</p><p>by Ummu Maryam</p><p>❤💚💜🖤💙💛🧡 NA CUCE TA 💚💜💙🖤💛❤🧡</p><p>®Zuwairat( ummumaryam)</p><p>🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣ni yanzu kome zai kara daga min hankali a social media🤔🤔🤔 gaskiya babu cos we have seen and heard a lot so no shaking…yanzu we are as thick as the tortoise shell,💁♀💁♀💁♀路♀路♀路♀</p><p>_Sweethearts muje zuwa_ 😘😘</p><p>Suna zuwa cikin gari Salem yayi parking kusa da wata masjid, kallon yazid dake sauke ajiyan zuciya yayi sannan yace “Yanzu muyi sallah…sai mu nemi hotel da zamu kwana …gobe sai mu koma Kano…..” Ahankali yazid ya fara girgiza kai yana cewa “No…pls..muje police stations… Ko morgue… Kilan da akwai yan accidents victims….” Bai idaba Salem ya katse shi dacewa “Have a positive mind…zamu ganta…kilan bata zo nan ba…or better still kilan tana Kano….” Kai yazid ya kara girgiza Mashi “I doubt that…. Gaskiya ina jin ajikina something is wrong….” “Nothing is wrong….kawai let’s pray first….” Salem ya fada yana fita daga cikin motan, ahankali shima yazid ya fito yana dafa kanshi saboda yanda yake sarawa, sannan sai double kawai yake gani a daddafe yasamu yayi salla shima Salem yayi sallah,</p><p>Dija kam same thing yau ma sai da ta samu ta wanke jikinta sannan ta fito tayi breakfast kaman yanda tayi jiya sannan ta koma gefe ta rafka tagumi tana kallon mutane dake kai kawo, sai yanzu take kara jin zafi inda ammi ta bugeta da itacen wuta don wurin yayi bororo kuma bata da daman ta cire kaya ta sha iska, around five tana zaune bakin titi kusa da wani mai saida abinci daka ganta kasan she’s lost in thought don ko kadan hankalinta bai jikinta, opposite da inda take zaune ne su yazid suke sallah although da akwai dan distance amma clean clear zaka hangi Wanda ke fitowa daga cikin masjid din. Ta kurawa titi ido tana kallon motocin dake wucewa kaman ance ta daga ido sai ta hangi yazid dake safe da kanshi ya fito dga cikin masjid, kaman bashi ba amma how could she ever forget the person that put her into this predicament, jikinta ne ya fara rawa ta fara komawa da baya tare da kare kanta da wani dake sayan abinci, shi kam bai Sani ba, suna fitowa daga cikin masjid Salem ya bude Mashi mota ya jefa kanshi ciki Salem ya shiga ya ja motan suka bar wurin Dija kam jikinta rawa ya dingayi dukda mutane wurin basu lura ba, tana ganin motan ya fara tafiya tayi saurin barin wurin saboda tsaro don ita gani take duk duniya bata da abin tsoro kaman shi.</p><p>Suna cikin tafiya yazid daya kwantar da seat din motan ya kwanta yace “Pls…mu wuce..Kano..pls…” Ya fadawa Salem, “Gaskiya we need to rest….kawai mu sami hotel mu samu abinci muci, muyi freshening up mu huta then first thing in the morning sai mu kama hanyan kano. ” pls banson kwanciya kan gadon hotel….” Yazid ya fada idanuwanshi lumshe, murmushi Salem yayi “Ai sai ka kwanta kasa…amma gaskiya ban Iya tuki for another 3 to four hours…in kuma zaka tuka motan you are welcome… Sai na iso….” Ya amsa Mashi atakaice, yazid dai bai kara cewa komai ba, kawai yana tunani yanda duniya ta chanza Mashi farat daya ya koma bai da kowa sai Salem then Hajiya karama itama tunda ya kashe wayanshi bata kara kiran shi ba yasan fushi take cos he knows how upset she can easily be. “Khadija….</p><p>Where are you?….” Ya fada ahankali. Salem dai bai kalleshi ba har ya hangi wata babba hotel ya juya yayi wurin, parking yayi a parking lot bayan an bude masu gate, fita yayi ya shiga, reception ya nufa yayi booking daki for a night aka nuna Mashi dakin duk yazid na kwance cikin mota. Sai da ya shiga dakin ya watsa ruwa sannan ya fito ya sauka downstairs. Wurin yazid yaje yaga kaman ya fara bacci, tapping dinshi yayi yabude ido ahankali, “Muje…” Ya fada Mashi, hannu yazid ya mika Mashi Salem ya amshi hannun tare da jawoshi waje, jingina yayi da mota Salem ya kulle mota ya rike Mashi hannu suka koma ciki “Duk ka maida kanka kaman wani patient… You better be easy on yourself before you die for nothing….” Salem Ya fada yana hada Mashi ruwan wanka.</p><p>Dija kam tunda ta ga yazid abun da yayi mata ya dawo mata saboda, tana tafia tana goge hawaye, “Allah yaisa….da yanzu ammai bata koreni ba…” Tafada tana tunanin ba don abinda yayi mata ba da tana a small but happy and sweet home da siblings dinta, kara goge face dinta tayi amma hawaye bai daina fitowa ba, a wannan ranar ko low diet dinner data sabaci bata ci ba saboda bakin ciki da Kuma ciwon jikin don duk ilahirin jikinta hurts like hell, yau data koma labour room waiting area sai taga babu komai, it felt so lonely and scary, mai gadin wajen ne kawai zaune, bata je wurin ba ta koma baya, cikin hospital ta dinga yawo tana ganin mutane jefi2 inada ta kwanta jiya da rana taje taga babu kowa amma da akwai florescent light wajen, babu kowa wurin amma hasken wurin makes it a little less scary, wajen ta nufa ta ajiye bag dinta a jikin bango ta kwanta yanda ko mutum ya zo wurin bazai ganta ba, tana kuka tana kiran ammi har Bacci yayi gaba daita.</p><p>The following day around 12 a compound din gidansu yazid shareef zaune kusa da shahid kan mota, inda suke zaune yana kallon bakin gate, wayan hannun shahid ya nunawa shareef,”Ka gane wannan yarinya?….” Shahid ya tambayi Sharif,”Yes…kam hanan ko?…””Yes itace…kasan I have special plans for her….saboda abinda tayimin jiya a school in har na kamata sai na bata banana that will last her for eternity….” Shahid Ya fada sounding very mean, dariya shareef yayi”Ina zaka kamata?…” Sharif ya tambayi shahid, dariyan mugunta yayi”A wurin convocation party da zaayi zan bata ecstasy pills…” Bai idaba Asabe ta fito daga part din Hajiya karama zata part din Hajiya babba, dariya sukayi tare sannan Sharif yace”Ni kuma am so Hungry for this gal…</p><p>I wish I will have her for just a night…” Ya fada yana kallon Asabe dake tafiya waist dinta na shaking ahankali, dariya suka karayi sannan Shahid yace”Ka mance the last time da muka samu wannan yarinya ta dinga yi mana ihu….Allah ya taimaka grandma bata gida data…..” Bai idaba akayi horn a bakin gateShuru sukayi tare da maida hankalinsu ga gate don ganin Wanda ke tahowa, maigadine ya bude gate motan Salem ya shigo,”Abokin ustaz ne….” Inji Sharif, basu ga yazid ba kasancewan yana kwance, saida Salem yayi parking sannan ya fito ya zagaya ya bude kofa tare da tada yazid da yanzu yanayinshi is becoming scary, ahankali yazid ya fidda kafa daya zai fito amma duk ilahirin jikinshi sai rawa yake kaman irin people da old age, Salem kamashi yayi ya fito ya tallaboshi suka fara tafiya ahankali, Sharif kallon shahid yayi”Wai shi da waye wancan?…” Ya fada don ko kadan basu kawo wa Kansu yazid ne ba, ganin yanda Salem kadai bai Iya tafiya dashi don almost dukkan jikinshi ya sakar Mashi, Salem kallon su Sharif yayi”Pls you guys should give me a hand….” Ya nemi taimakonsu, sai lokacin suka diro daga bayan motan suna wondering who it could be, suna karasowa suka ga yazid ne, da sauri suka kwaceshi daga hannun Salem”What’s wrong with him!!!…” Sharif ya fada da karfi, Salem baice komai ba”Yaya!…meya sameka?…”</p><p>Shine questions da suke jera Mashi while suna rike dashi from both sides, ba karamin tashi hankalunsu yayi ba cos basu taba ganin dan uwansu haka ba,”Pls somebody should say something!…” Sharif ya fada sounding very tensed amma babu Wanda yace komai, kofan part dinshi Salem ya bude suka shiga ciki, kan three seater suka kwantar dashi kowannensu ya fito da gudu, Sharif part din dad yayi da gudu while shahid yayi part din Hajiya babba shima aguje, da ihu shahid ke kiran big mom da small mom, da sauri small mom ta mike ta tari shahid,”Moms…Ku taho…yaya isa critically sick… Yanzu nan yaya Salem ya shigo dashi….” Ya fada yana haki, dan dakatawa yayi yana kallon mom dinsu that looks so emaciated, sai lokacin ya lura da yanda ta koma, sannan yana kallon I don’t care looks on her face dayayi maganar yazid,”Mom bakuji bane?…. Yaya baida….” Bai idaba yaga big mom ta mike ta kama hanyan bedroom dinta”Mommy!!!…” Ya kwala mata kira amma ko juyowa batayi ba ta shige abinta, kallon small mom data sadda kai kasa yayi”Small mom…what’s happening?…” Shine tambayan dayayi mata yana shafa kanshi back and fro,”Ina yazid din?…”</p><p>Small mom ta tambayeshi, bai amsa ba yace”Small mom I know something is wrong… Nasan big mom bata wasa da yaya… So pls Ku fadamin abinda ke faruwa,…” Hajiya karama bata saurareshi ba ta fita zuwa part din yazid, shima sharef na zuwa part din dad ya tarda shi zaune yana karatu, shima cikin tashin hankali ya sanar da dad abinda ke tafe dashi, ko kallon shi dad baiyi ba,”Dad…am talking to you… Yaya…””Ka bar min wuri kafin ranka ya baci….” Dad ya daga kai tare da daka Mashi tsawa, surprise look ne kwance kan fuskan Sharif,”Dad am talking about yaya yazid fa…””Wai baka wucewa!…” Dad ya kara daga Mashi tsawa, aikam gefe daya ya koma yana buga kafa a kasa yana cewa”Dad ka taho mu tafi…hes in critical conditions… Pls dad…in ma da laifin da yayi maka kayi hakuri….” Bai idaba yaga dad ya Ciro palm sandal dake kafanshi ya biyoshi da gudu, shima aguje ya bar wurin yana mamakin abinda ke faruwa.</p><p>Hajiya karama zama tayi bakin kujeran da yazid ke zaune”Yanzu son kashe kanka zakayi?…you want to kill yourself?….so we are all worthless to you… Bamu da amfani wajenkako?…” Ta fada hannunta dafe da forehead dinshi dake harbawa, shahid dai yana tsaye yana jin abinda take cewa amma baisan manufarta ba”Gaskiya he needs a doc,…tun shekaranjiya da muka bar nan baici komai ba…” Inji Salem, Hajiya karama daga wayanta tayi tare da dailing number doctor, aguje Sharif ya kara shigowa yana kallon yazid dake kwance sai nishi yake, kallon shahid yayi”Ina big mom?…” Ya tambayeshi”She’s not coming….”</p><p>“So…is dad…what’s happening?….” Inji shahid, ahankali yazid ya Dora hannunshi kan hannun small dake magana da doc, daga idanuwa tayi sai ya girgiza mata kai alaman she should not call the doc. Hararanshi tayi ta cigaba da magana sai da ta gama sannan ta godewa Salem tare da ordering Sharif yahada Mashi ruwan wanka. Salem sallama yayi masu yatafi kan zan dawo da yamma, bayan yazid ya fito daga bathroom ya kwanta har lokacin su Sharif da Hajiya karama suna tare dashi, doctor na zuwa ya duba shi ya nemi jin abinda ke damunshi amma babu mai cewa komai.”Wai where exactly ke yi maka ciwo?…” Doc ya tambayi yazid,”Ba….bu….” Ya amsa Mashi ahankali,”Dan Allah yaya ka fada Mashi…you look terrible….” Inji Sharif ,”Am…OK….” Yazid yyi insisting,”Kayi Mashi Karin ruwa…he has not been eating….” Inji small mom, yazid dai jinsu kawai yake. Doc rubuta abubuwan da zai bukata yayi su Sharif suka tafi sayowa daga pharmacy dake nan kusa dasu, kan hanya kam sai tambayan juna abinda ke faruwa suke amma babu reasonable answer.+Two hours later yazid ne kwance ana yi Mashi Karin ruwa na biyu dakin cike da siblings dinshi amma babu matarshi da mom da dad,</p><p>Pls manage……see you late</p><p>[6/22, 4:33 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: NA CUCETA 24</p><p>by Ummu Maryam</p><p>❤💚💜🖤💙💛🧡 NA CUCE TA 💚💜💙🖤💛❤🧡</p><p>®Zuwairat( ummumaryam)</p><p>24</p><p>My dearest barrister Hajiya Hannatu, I love you so much, thanks for the care and the gifts, you are one in a trillion. Love you wujiga wujiga 💋💋💋💋</p><p>Sai da Karin ruwa ya kare sannan ya farka daga bacci, kallon siblings dinshi yayi sai ya tuna in har suka gano abinda yayi they will all be disgust, “Pls Ku tafi….am OK now….” Yafada yana kirkiran murmushi karfin hali, kallon juna sukayi amma basu da intention din barin wurin, “Kunji pls kuje….” Bai idaba Hajiya karama ta shiga da plate a hannunta “Tqshi kaci abinci….”</p><p>Ta fada Mashi atakaice fuskanta daure don kar yayi mata gardama, amma kauda kai yayi gefe baice komai ba, “Yaya pls eat….” Inji marzuk dake zaune gefenshi kan gado, shi tunanin mufida yake, ko batasan ya dawo ba, “Small mom…ina…mufida….” Ya tambayeta, “Tana nan….” Ta amsa Mashi atakaice sannan ta ajiye abincin kan bedside locker ta fita tana cewa. “You are on your own…” Yasan manufarta wato she won’t care about him anymore, su Sharif dake jingine da bango sai hissing suke ko me ke damunsu oho, “Yaya in hada maka tea?…” Maryam ta tambayeshi, ahankali ya girgiza mata kai “Haba yaya…what’s wrong?….are you on hunger strike?… Komai bakaci….” Sharif ya fada kaman hes the boss, yazid murmushi kawai yayi ya kauda kai gefe yana tunanin in har sun San abinda ya aikata they will all hate him, afusace shahid ya bar wajen Sharif yabi bayan shi. Yazid daga wayanshi yayi yakira number mufida amma batayi picking ba, mikewa yayi ya zauna da cannula dake hannun shi, “Yaya ina zaka?…” Maryam ta tambayeshi, “Wurin mufida….” Ya amsa mata yana kokarin sauke legs dinshi kasa, “No yaya relax…let me call her….” Ta fada tana maida Mashi legs dinshi kan gado, lumshe eyes yayi yana tunanin khadija, shi da ya aika mugun abu is here under ac amma the innocent gal is somewhere without parent or loved ones, yasan the street is a dangerous place especially for gals, he knows a gal like khadija will never go scot free for as long as she’s out there looking for food and shelter “She will be molested again…. Even with the pregnancy….” Yafda ahankali sai ya fashe da kuka forgetting the presence of his siblings, jin an rike Mashi hannu yasa yayi saurin hadiye kukan tare da goge hawayenshi.</p><p>Maryam na shiga part dinsu ta shiga dakin da mufida take, da sallama ta shiga ciki, mufida CE kwance itama yanayinta was bad don idanuwanta sun chanza kala saboda kuka, “Anty yaya yace kije…” maryam ta fada mata, ahankali ta daga kanta sannan tace “Banjin dadi ne….” Ta amsa mata sannan ta juya kwanciyanta, Maryam fita tayi taga Sharif da shahid sun fito daga bedroom din mom dinsu, “Wai ina mom take ne?….” Suka tambayi Maryam, “Nima ban Sani ba…kilan tana part din dad..nima yaya yace inkira Anty mufida kuma tace she’s not feeling too well.”</p><p>Ta amsa masu, kara daure fuska sukayi, “Wait….” Sharif ya fada sannan ya kama hanyan dakin mufida, yana isa ya dan bugi kofan tare da sallama, amsawa tayi tana mikewa zaune, shiga yayi yana kallon matar wansa da he’s older than, “Sis yaya yace kizo….” Ya fada atakaice not looking so bright, mufida gyara wuyan dan karamin hijjab dake kanta tayi “To ina zuwa….” Ta amsa Mashi amma kara gyara tsayuwanshi yayi yana cewa “Ai he’s said kafata kafanki….” Yafada yana kara murtuke fuska don yasan in ba don girman yayanshi ba ko kallon banza bata isa tayi Mashi ba, mufida bata kara cewa komai ba ta saka vine flat shoes dake bakin gadon ta mike, kofa ya bude mata ta fita ya bi bayanta tare da maida kofan ya rufe.</p><p>Maryam bata kara komawa part din yazid ba tayi zamanta falo, su kuma Sharif da shahid sukayi hanyan part din dad sai huce suke kaman wasu yan tasha.</p><p>Itadai mufida har ga Allah batason gani yazid for any reason in the world don yanzu tasan yana da someone that he loves and adores more than her Bedroom da yazid ke kwance tayi sallama, da sauri ya kalli kofan, ganinta makes him happy amma how she looks Scare’s him, siblings dinshi da suka rage wurin shi suna ganin mufida ta shigo suka mike suka bar masu dakin, tana tsaye a gefe daya har suka bar dakin, daga kanta tayi ta kalleshi shima mikewa zaune yayi yana kallon ta, ahankali ya mika mata hannu yayi mata alaman tazo, tsayawa tayi tana kallon how emaciated he is, “Baby pls come….” Ya fada mata ahankali yana mika mata hannu, ahankali ta taka zuwa bakin gadon ta zauna, “Princess.. I miss you….” Yafada yana matsawa kusa daita “Stop it….” Ta fada tana matsawa baya, “Am sorry… So sorry….” Ya fada mata yana rike wrist dinta, ahankali ta zare hannunta tana cewa “Stop it… I can’t pretend anymore…. Ban Iya zama da wannan bakin cikin….” Fashewa tayi da kuka tacigaba da cewa “Pls ka sallameni in tafi….” Da sauri yazid ya Dora yatsanshi kan wet lips dinta “Shushhh….” Ya fada yana in a whisper yana goge mata face, “Pls don’t say that…am sorry….mai rabamu sai Allah….” Yafada yana goge mata face dinta, kai ta girgiza Mashi, “No…you heart lies with her….baka damu dani ba….” Ta fada cikin matsanacin kuka, kai shima ya girgiza mata “My heart does not lie with anyone but you….kawai tausayi ne da guiltiness ke weighing dina down….I love you and you know it…….” “No you don’t love me…pls ka sakeni…” Bata karasa ba ya kara Dora yatsa kan lips dinta “Pls stop saying that……” “You know I love you…” “That was then….if kanasona why duk ka damu haka?… Just take a look at yourself… All because of another… Ko abinci bakaci…nidai gaskiya zan tafi.. when everything settles down sai in dawo…ganinka haka breaks my heart….” Tafada tana kara volume din kukanta, rike mata two hands yayi “Baby its not because of her….” Which hes lying of course “Zunubin is too much for me….babu inda baa nemeta ba amma she’s nowhere tobe found… Kilan she’s dead all because of me….</p><p>baby forgive me for being human…. This whole thing is killing me….the only thought that makes me strong is you…in kin barni ban san yanda zanyi da raina ba.. Pls baby don’t go….” Yafada yana Dora kanshi kan shoulder dinta, mufida shuru tayi deep down tanajin tausayinshi at the same time the thought of khadija irritates her, ahankali ta shafa bayanshi tana cewa “If you find her aurenta zakayi ko?…” Ta tambayeshi thinking about yanda zata Iya coping da sharing sweet, lovable romantic yazid dinta da wata, “Baby I don’t know yet…let’s find her first….” Yayi mata karya don yasan if he mistakenly says yes mikewa zatayi and hes enjoying her comfort, “Baby pls sleep by my side tonight….” Ya fada yana kara shige mata jiki, hararan bayanshi tayi “Only on one condition….” Ahankali yace “Anything for you…” “Promise me zaka bar nuna damuwa…promise me zaka koma normal life dinka as if nothing happened….” Shuru yayi baice komai ba don yasan that is absolutely impossible at the moment “I will try…” “Good.. Now bari inyi feeding dinka.. .” ta fada tana kokarin mikewa, kara riketa yayi da jikinshi, “Baby am not hungry…” Tureshi ta farayi “Then no deal….” Tafada tana tureshi, “OK…</p><p>Sorry…ki bani tea…zansha …” Ya fada don kar ya bata mata rai kuma Mikewa tazoyi ya Kara riketa, “Baby ki bari sai later…I miss you a lot….” Yafada ba don in zata bukaceshi zai Iya komai ba amma don ya nuna mata how much he cares, hannu ta Dora kan tummy dinshi that is so flat “Kalli yanda cikinka ya hade da bayanka….pls ni dai bari in hado maka tea din….” Bai kara cewa komai ba ya saketa ta mike shi kuma ya koma ya kwanta.</p><p>Direct Sharif da shahid suka shiga part din dad dinsu ba ko sallama, sai wani cika suke suna basarwa, big mom ce zaune tana magana da dad while Hajiya karama tana sauron su. Mom shuru tayi tana kallon su, kowannensu tsayawa yayi suma sun zuba masu idanu “Wai kuna haukane zaku shigo babu sallama sannan kunyi ma mutane tsaye?…” Hajiya karama ta fada cikin fada, “Munzo jin abinda ke faruwa ne….” Sharif ya fada yana daga gira daya, dad dinsu kam ya cika yayi fam “Kambu…amma wallahi zanyi maganinku yanzu nan in har Baku bar wajen nan yanzu ba…” Hajiya karama ta fada kaman zata tashi sama “Ai in mun bar wajen nan to kun gaya mana abinda ke faruwa… Dalilin dayasa yaya bai da lafiya amma duk baku damu dashi ba….ai muma yan gidan nan ne kuma we are no more kids….” Shahid ya fada atakaice sannan ya kalli Sharif yace “Ko ba haka bane?…” Ya tambayeshi da sauri Sharif yace “Haka ne …” Hajiya karama ji tayi kaman ta mike taci ubansu amma dad ya daga mata hannu alaman ta kyalesu, mom kam ko kallon su batayi ba balle su bata mata rai, dad daukan wayan dake gefenshi yayi sannan yayi dailing wata number, few seconds later ya fara cewa “Yauwa inspector… Ka taimaka ta turomin 4 police…” Sharif kallon shahid yayi shima shahid ya kalli Sharif suka yiwa junansu magana da ido suka juya, dad dinsu dakatawa yayi da wayan “Ku tsaya mana manya…you have some nerves…idiots…” Ya fada sannan ya ajiy wayan, daman he wasn’t making any Call Suna fita suka tsaya “Meye abunyi…nifa am disturbed… I really what to know abinda ke faruwa…dukda wannan ustaz yana hanamu walawa amma he’s our brother….” Inji shahid, ajiyan zuciya Sharif ya sauke “Nima I really want to know… Amma since it seems secret mu kyalle…in yayi tsami munji…” Ya fada given up “No gaskiya… We need to know… Duk sun raina mana hankali …har yanzu kallon yara suke mana.. They don’t think we are matured balle suyi sharing family problems damu…and were are the second born of this family…” Inji shahid, “Then me xamuyi?…” Sharif ya tambayeshi, shuru yayi for a while sannan yace “I know what to do…muje wajen grand ma….am sure mun San yanda zamuyi tormenting dinta har fada mana….” Yfada yana murmushin keta “Yes ni ban ma tuna ta ba…she’s our only hope… amma wait what if bata San abinda ke faruwa ba…” “Sai mu tisata gaba tazo ta tambayar mana…” Dariya shahid yayi yana cewa “Yau ana yinta kenan…” Kenan.</p><p>Abangaren dija kam ji tayi ana taba mata kafa tayi saurin mikewa, wata cleaner ta gani da kayan aiki, “Ke lafiya kike kwance nan?… Ko duk salon saurin zuwan ne?…” Matar ta fada, ita dai dija bata ce komai bai sai saurin take ta mike, ji tayi kanta yayi mata dummm, jikinta rau da zafi, bag dinta ta dauka ta fara tafiya ita kuma matar ta tsaya tana kallon ta. Dija ji tayi duk ilahirin jikinta babu abinda yake mata sai ciwo, ankles dinta kaman an takasu, kawai sai ta fara breakfast da kuka, tana tafiya tana kira ammi cikin ranta, ji tayi she still want to lay down, tana tafiya tana kallon ko da akwai inda zata dan zauna for a while. Wani wuri ta gani still cikin hospital din, wurin ta nufa ta zauna tare da hada kanta da gwaiwa, sabon babin kuka tabude, babu abinda take kira sai ammi kaman yau ta bar gida tajeji, tana kuka tana taba jikinta tqnq imagining what sort of hotness is this? Cikinta ne yayi motsi tayi sauri dakata da kuka tana saurraron motsin, still wani motsin ta karaji, ahankali ta Dora hannu kan cikin ta,</p><p>for the very first time dataji abu yayi portraying a cikinta, goge face dinta tayi ta rike cikinta da two hands dinta, kalle2 ta danyi don tabbatar da babu mai kallon ta, hannu tasa cikin riganta tana shafa cikin ta, still abunda ke cikinta sai motsi yake, ko a lokacin dija batayi tunanin dane cikin cikinta ba, sai da cikinta ya motsa for almost 8 times sannan yayi still. Sai lokacin ta cire hannunta ta cigaba da kukanta “Gida nakeso….” Kawai take cewa. Kafin karfe seven na Safiya fever ya rufeta sosai don babu abinda take sai rawan sanyi, gashi rabonta da abinci tun kafin taga yazid. Ganin masu wucewa da yawa suna kallon ta yasa tayi karfin halin mikewa ta bar wajen tana tafiya kaman Kazan da ruwan sama ya doka sai rawa jikinta yake, sai da ta kai bakin titi ta tsaya tana kalle2 wani chemist ta tsaya kallon mai wurin yana budewa tana ganin ya gama budewa ta taka ahankali ta shiga wajen har lokacin bata bar kuka ba, mai wajen dake dusting wurin zaman shi ya daga kai yana kallon ta, ganin batace komai ba sai kuka yasashi cewa “Lafiya baiwar Allah?…” Ya tambayeta yana zama, bakin dija na rawa ta fara cewa “Ma…ga…ni…zaa…bani….” Ta fada tana kokarin daidaita kukanta, saurayin tsaya kallon face dinta yayi sannan yana kallon how swollen her lips is, “Maganin me?…” Ya tambayeta, shuru tayi tana tuna yanda ammi ke aikenta siyan maganin musassara, “Na…musassara….” Ta amsa Mashi, still tsaya kallon beautiful but sad face dinta yayi “Wa ya aikoki?…” Ya sake tambayanta, kai kawai ta girgiza Mashi alaman babu Wanda ya aikota “Me ke damunki?…” “Jikina…ke…ciwo….” Ta fada tana kuka, “Ina mamanki?…” “Tana….gida….” Tayi Mashi karya “Kinci abinci?….” Kai ta girgiza Mashi, “To…zan baki magani….amma ki tabbatar kinci abinci kafin kisha…kinji ko?…” Da sauri ta gyada Mashi kai, mikewa yayi ya tattara mata drugs. Nuna mata yanda zatasha yayi sannan ya mika mata. “Nawa?…” Ta tambayeshu gwanin ban tausayi, kura mata ido yayi for a moment sannan yace “Ki barshi…yi sauri ki koma gida kici abinci sai kisha maganin ki kwanta…kinjiko?….” Ya fada mata sounding very caring, ahankali ta gyada Mashi kai. “Na….go…de….” Ta fada sannan ta juya ta bar wajen.</p><p>[6/22, 4:34 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: NA CUCETA 25</p><p>by Ibraheem</p><p>💙💛💚🖤💜❤🧡 NA CUCE TA ❤💙💜🖤🧡💛💚</p><p>®Zuwairat ( ummumaryam)</p><p>2⃣5⃣</p><p>Tafiya tayi for about 5 minutes taji legs dinta sun gaji, bakin wani closed shop ta zaune ahankali sai shessheka take, ji take kaman ta hau titi ko mota yabi ta kanta ta huta, bayan kaman mintu goma ta kara mikewa this time wani shop ta nufa ta sayi small bread da ruwa, ahankali ta koma gefe daya ta bude fara ci, nan take ta fara vomiting kaman babu gobe, sabon kuka ta fara tana rike cikinta “Wayyo cikina….ammi…cikina…”</p><p>Ta dinga maimaitawa while tana amai, tana gamawa ta zame ta kwanta nan wajen batare data sha maganin ba. At that same time itama ammi tana chan tana kuka, already mutane gidan sun San abinda ya sami dija, kuma ba karamin fada da tsinuwa tasha wajen danginta ba don cewa sukayi tafi dija laifi, tunda tazo take kuka don gani take dija is no more,</p><p>she hates herself so much that she wish death should take her away, babu mai kallon ta balle ya rarrasheta cos duk haushinta sukeji, at that moment da dija ke kwance kaman zata mutu itama ammi na kwance tana kuka tana kiran sunan dija, “Dija ki yafemin…” Kawai take maimaitawa, “Allah ka karemin dija in dai tana da rai…..Allah ka tsaremin dija indai bata mutu ….”</p><p>Ta fada tana kuka, “Wai baki yiwa mutane shuru?…bake kika koreta tabi duniya ba?… Kukan me zakiyi kuma?… Kawai ki zuba ruwa kasa kisha….” Inji wata tsohuwa mai kama da ammi,cikin kuka ammi ta dinga cewa “Yau ina jin dija cikin jikina….ina ji kaman wani abu ya sameta….” Tafada cikin matsanacin kuka, baki tsohuwar ta tabe “Ba sai ki ji dadi ba….ai sai ki zuba ruwa kasa kisha….</p><p>In ba keba wacece zata yanka hannunta ta yar koda kuwa hannun ya rube…..amma ke kika Iya korar marainiyar Allah bayan zaluncin data fuskanta….da akwai hisabi tsakanin ki da ita…kawai ki jira ki gani……” Tsohuwar ta fada sannan ta bar mata creepy and disgusting room wanda babu kamshin abinda ke tashi sai na tsamin furan daya kwana. “Ni dai…Ku taimaka Ku nemomin dija….wallahi nayi kuskure…</p><p>” Ta fada tana kuka “Ina jin da akwai abinda ke samun dija…ina ji a jikina….” Ta dinga maimaitawa.</p><p>Itama dija dukda tana kwance nan kasa idanuwanta rufe amma bata bar kiran ammi ba, hawaye da fita daga closed eyes dinta. Sai nishi kawai take tana haki kaman wacce tayi gudu while two hands dinta rike da tummy dinta</p><p>Wajen karfe biyar na maraice su Sharif suka iso gidan grandma dinsu dake hotoro Sukaje, kusa da bakin kofan falo sukayi parking motarsu instead of parking lot, ba komai yasa sukayi hakan ba sai don plan din da sukayi saboda abunda ke tafe dasu.</p><p>Falon old woman din suka shiga suka tardata ta kurawa arewa 24 ido da medical specks a face dinta. Daga kai tayi tana cewa “Wane arnene ya shigo babu sallama?…” Ta fada cikin tsiwa dukda tasan sune amma dayake itama ba daga bayaba. “Arnayen jikokinki ne?…”</p><p>Suka amsa mata suna zama both side dinta, tsoki taja “Wai Ku yaushe zakuyi hankali…?” Ta fada tana juyowa tana kallon faces dinsu one after the other, “Lokacin da jakkuna sukayi kaho…” Sharif ya amsa mata as usual, “Murja!!!!….” Shahid ya kwalawa wata kira, Wanda saida tsohuwar ta Dade kunnenta sabida kara cos sun San ko kadan bata kaunar hayaniya. Da sauri yarinyan da aka kira da Murja ta fito da gudu har jikinta na rawa don tasan ko suwaye, “Ki kawo mana abunsh…” Shahid ya fada mata, da sauri ta juya, su kuma suka kalli juna tare da fashewa da dariya, ko na meye oho.</p><p>Ko da yarinyan ta kawo masu kunun aya dariya suka sake yi duk sun takurawa baiwar Allah dake zaune tsakiyansu, saida sukasha sannan Sharif yayiwa shahid alama da ido, ahankali shahid ya dauke wayan grandma dake kusa dashi ya saka cikin aljihunshi sannan Sharif ya fara cewa, “Inna…munzo ne dan Allah ki fada mana abind ke faruwa chan gidnmu…” Ya fada mata sounding very stubborn, tsohuwar gyara zaman specks dinta tayi sannan tace “Ban ganeba….meke faruwa?… ” ta tambayesu tana kallon faces dinsu “Oho…muma bamu Sani ba…inda mun sani ai baki ganinmu nan…” Inii Sharif, dakuwa ta sakar Mashi a fuska tana cewa “Kaci uban daya haifeka….ni kake cewa oho?….ni Saar ubanka ne?…</p><p>Ku tashi Ku tafi kafin in kira ubanku….” Ta fada tana dungurin Sharif a goshi, shikam shahid rike baki yayi yana dariya, saida ta gama balbaleshi sannan shahid yace “Inna baki gane ba…yaya yazid ne bai da lafiya…Kuma duk yan gidan basu damu dashi ba,…ko zuwa inda yake basuyi ba…shine mukace muzo mu tambayeki ko zaki fada mana abinda ke faruwa….” Kallon banza ta watsa Mashi “To ban Sani ba…Ku tashi Ku bani wuri….” Kallon juna su kayi, Dukkansu mikewa sukayi, “Wallahi sai kin fada mana…ko kuma mu saka waka….” Inji Sharif, “Kun Dade Baku saka wakan ba…” Ta fada tana gyara zamanta, remote dinta suka dauka suka chanza zuwa tashan boom TV, suka saka waka sannan suka saka a highest volume, tsohuwa zaro idanuwa tayi tare da dafe kanta, da sauri ta mike ta kashe kallon tana neman wayanta don kiran dad dinsu amma bata ganshiba, gefe daya suka koma tare da folding hands dinsu a chest sukayi tsaye suna kallon tsohuwa tana birkita inda ta zauna, daga kai tayi ta kallesu “Dangin firauna ina kuka kaimin waya?…” Ta fada tana gyara daurin zaninta, “Ai inna ki fada mana kawai sai mu baki wayanki tare da bar maki gida….” Shahid ya fada atakaice, tsohuwar zama tayi bata ko kallesu ba Ganin Sharif ya nufi wajen kayan kallon zai kara kunnawa yasa ta mike “Kana kunnawa sai da tsinewa ubanka…. ” ta fada kaman zata sauce,</p><p>“Ai danki ne…in kin tsine Mashi matsalan ki…” Inji shahid dake jingine da bango yana dariya, Sharif kara kunnanawa yayi ya kara kura volume, ta bishi ya gudu ta koma kashe suka kara komawa, babu irin zagin da basu sha ba amma kememe suka ki rabuwa da ita har saida ta gaji da kashe kayan kallon ta zauna tana haki kaman wacce tayi race, “Wallahi ban san abinda ya fara ba…uban Ku bai fada min ba…” Ta rasa maganar da zagi, rage volume sukayi sannan shahid yace “An ma rainaki wallahi… Yanzu bari in dauko maki hijjab mu kaiki har gida ki jiyo abinda ke faruwa….” “To Ku fara bani wayata….” Ta fada masu, kallon juna sukayi suka tuntsure da dariya</p><p>“This old woman wants to use sense on us….” Sharif ya fada yana dariya “Ai inna in kin ga na baki wannan wayan to mun isa chan Gidan….” Inji shahid, daman tacika tayi fam kuma tana bukatar gaya danta yayi mata iyaka da su, Murja ta kira ta dauko mata hijab, few seconds later ta fito da hijab, fixgan hijabin tayi daga hannun Murja ta Dora a shoulder dinta ta tashi kaman zata tashi sama tayi waje, kallon murja dake tattare cups sukayi Sharif yace “Babe ya ranar nan?…” Ya tambayeta yana daga mata gira, batace kala ba sai dariya suke da sauri ta kwace cups, “Babe kilan mu dawo da mun ajiye Hajiya…</p><p>Me kike so…” Inji shahid, har ta shiga kitchen ta leko ta watsa masu disgusting look sannan ta shige, kara dariya sukayi sannan shahid yace “Kin harari uwarki da ubanki…” “Don’t mind her ta samu fresh boys sai yanga take…remember she wasn’t a virgin….” Inji Sharif, cikin dariya shahid yace. “Kilan she’s jealous of the gal we brought here last….” Bai idaba Hajiya ta dankara Masu ashar Wanda yasasu barin wurin. Suna kaiwa gida sukayi parking sannan suka bata wayan ta, tana fitowa ta fara kwallawa dad kira tundaga waje “Isa!… Isah!!!….” Kawai take fada da karfi, yaran gidan dake wasa a falon Hajiya babba fitowa sukayi da gudu “Inna lafiya?….” Daya daga cikin su ta tambayeta, “Kin ci ubanki….ina ubanku yake….” Tafada tana tafiya irin na old people sannan har lokacin hijjab dinta na kan shoulder dinta, dad ne ya fito, yaga mom dinshi sai zazzaga balai take, tana ganin shi ta fara “Wallahi kayi min iyaka dukkan yaranka…kar shegen daya kara takamin gidan….kar ka kuskura su kara zuwa gidana…” Ta fada tana wuceshi zuwa part dinshi, dad dai tsaye yayi ya rasa inda ta dosa, bin bayanta yayi “Wani abu akayi maki?…” Ya tambayeta in a soft tune, “Ni dai kayi min iyaka da yaranka kawai…mussaman wayan nan masu kama da shaidanun….” Tafada tana shigewa falonshi, shima shiga yayi.</p><p>Su mom ma zuwa sukayi suka gaidata amma ko amsawa batayi ba sai balai kawai take tana ya rabata da yaranshi, sai datayi mai isanta sannan tace “Ina yazidu?…” “Yana bangarenshi…” Hajiya karama ta amsa mata, “To ubanme yayi maku kuka ki kula dashi bayan ance baida lafiya?….” Ta tambayesu atakaice, dukkan su shuru sukayi sai dad yayi karfin halin cewa “Wa ya kai maki wannan maganar?…” Dakuwa tayi Mashi “Wato dai gaskia ne baida lafiya kuma Baku kulawa dashi…to Ku fadamin abinda yayi maku….” Ta kara tambayansu, dad zama yayi yana Neman hukuncin daya dace da dasu Sharif don yasan its their hands doing.</p><p>“To tunda bani da darajan sanin abinda ke faruwa bari in tashi in tafi….” Ta fada tana kokarin mikewa, da sauri dad yace “Kiyi hakuri inna….abinda ya aikata bakina bazai Iya furtawaba….amma muje ya fada maki da bakinshi….” Inji dad, harara ta watsa Mashi tare dasu mom sannan ta mike su dad sukabi bayanta. Part din yazid tayi suna biye daita kaman wasu guards. Daman su Sharif na boye cikin mota don sun San ba karamin haushinsu dad zaiji ba, suna ganin sunshiga part din yazid sukayi saurin fitowa tare da komawa bayan window dake direct to his bedroom, in dai zaayi magana da karfi zakaji, kasa kunne sukayi kaman dole Inna na shiga ta tarda yazid rungume da mufida suna bacci don data bashi tea ya dan sha kwantawa sukayi tare “Yaran zamani babu kunya babu tsoron Allah….gidan surukai take kwance jikin miji da rana tsaka….” Tafada tana karasawa bakin gadon, dad dasu mom tsayawa sukayi bakin kofa, hannu ta daga ta lukawa mufida duka a baya Wanda yasa ta farka a gigice Shima yazid farkawa yayi, mufida bude ido tayi ta kalli tsohuwar dake tsaye kanta tayi sauri zare jikinta daga na yazid, bata ji kunya ba saida ta hangi dad dasu mom tsaye kaman ta nutse kasa, shima yazid shafa face dinshi yana kallon inna tare da lekawa ta gefe yana kallon iyayenshi, fuskan mom ya kalla yaga ta watsa Mashi irritating look, sauke kanshi kasa yayi don bai Iya kallon dad, duk iyayen nashi sunyi mamakin ganin yanda ya koma don mom tamkar ta fashe da kuka takeji amma her face is saying something different, da sauri mufida ta fita daga cikin blanket tare da sauka daga kan gado, jikinta sai rawa yake, Allah ya taimaka she’s decent, yazid ne kawai dake sanye da boxers da singlet , inna bayan mufida da ke barin dakin tabi da harara sannan ta maida hankalinta kan yazid da Duk ya susuce,</p><p>“Kai wannan dan cutan zamani ya debo?….” Tayi directing question dinta to dad daya harde hands a chest dinshi fuskanshi babu walwala shima yana kallon yanda ya chanza kaman bashi ba, “Wai badaku nake ba?… Sida ya kwaso?…” Inna ta sake tambayansu, yazid daure fuska yayi baice komai ba, jin shuru yayi yawa yasa inna kallon yazid “Kai ubanme ke damunka?….” Inna ta tambayeshi, baice Kala ba kanshi kasa yana gyara blanket dake jikinshi, “Wai bakajine!!!…” Dad ya daka Mashi tsawa “Babu…komai….” Ya fada kanshi kasa, bski inna ta bude “Lallaima…wato baka fadamin ko?…” Imna ta fada tana nuna kanta, “Kana fadi kafin rainka ya ya baci?…” Mom ta daka Mashi tsawa, “To a kyaleshi mana…haba….” Inji Hajiya karama, nunata inna tayi da yatsa “Kiyi min shuru…badake nake ba….</p><p>Mtwsss” Ta dakawa Hajiya karama tsawa, turo baki tayi ta kauda kanta gefe, “Ni babu abinda ke damuna…” Inji yazid, “So kake sai ranka ya baci kenan…” Inji dad a fusace, juyawa yayi ya kalli inna sannan ya fara cewa “Wannan shegen yaron mugun mayaudari ne…yaudareni…na aminta dashi…na fifitashi kan sauran yaran gidan nan…Ashe dan iska ne ban saniba… Yar yarinya data bata fi shekara sha 14 da haihuwa ba yayiiwa….fyade….” Su Sharif bude baki sukayi, “Yanzu yanrinya tana chan da ciki babu Wanda yasan labarinta….shine yake wannan munafurcin…wai yana nadama….” Dad ya fada, yanda magana ke fita daga bakin shi kasan ranshi bace yake, inna mutuwan tsaye tayi tare da rike baki, mom kam kara fashewa tayi da kuka ta bar dakin, yazid Kuma sunkuyar da kai kasa yayi, inna data gama bude baki sai cewa tayi “To yanzu meye dalilin wannan ramar?…” Shine tambayan datayiwa dad, kallon mamaki dad yayi mata, “Ka tsaya kana kallo na….nace ya akayi ya rame haka?…” Ta sake tambayanshi, “Wai inna bakiji abinda nace bane?….” “Naji mana….ai dan fyade ko ciki ba yau aka fara ba!…ko wayan nan banzaye kananan yaran sunayi balleshi?….” Baki dad ya rike haka suma sharif, “Ban gane ba…” Dad ya fada with a shock on his face, “Sharifu da shahidu mana…mai gadina sai dayayi min kashedi Kansu…wai in na fita suna kawo yanmata…balleshi yazidu?….” Baki suka kama daga inda suke sauraron abinda inna ke cewa, “Muje…muje…muje….” Sharif yayiwa shahid whispering yana turashi daga inda yake tsaye. Da gudu suka shige suka bar gidan</p><p>Shima yazid kurawa inna ido yayi yana kallon ta don ya tabbatar da abinda take cewa don at that moment ya mance da matsalanshi, afusace dad ya bar wajen, inna kallon yazid tayi sannan tace “Kai kuma shege ba ance ana amfani da wani abu mai hana mace ciki ba?….”tafada sounding very serious, daga kai yayi ya harareta.</p><p>💚❤🧡🧡💜💚💛💙</p><p>Wai kaman ni ummumaryam in bude wattpad account, amma getting to three weeks har yanzu banda upto 1k followers🤔. Gaskiya nayi fushi tunda kuma Baku voting Baku following dina. Nima zantafi Hutu har sai kunyi following dina tare da voting.🤒🤒🤒😝😝😝 da gaske nake💁♀</p><p>[6/22, 5:50 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: ❤🧡💜💛💚💙</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💛💜💚💙❤</p><p><br /></p><p>®Zuwairat (ummumaryam)</p><p><br /></p><p>2⃣6⃣</p><p><br /></p><p> _Sweetheart thanks for the prayers, am getting better_ </p><p><br /></p><p> </p><p> _Babyna, sweetheart dina, habibtyna, I wish you happy birthday in advance, I wish ina iya kara typing cos of you tomorrow amma I can't, age in grace, may Allah grant you all you desired, you_ *know my love for you is.....🤦🏽♀ ban San yanda zanyi describing dinshi ba amma know that you are special to me. Happy birthday sweet* *Sawwama* .🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂</p><p><br /></p><p> _Dedicated to you, and you alone_ </p><p><br /></p><p>Hajiya karama dake tsaye bakin kofa tsoki taja ta bar dakin saboda takaicin abinda inna ke cewa, cikin matsifa inna ta juyo ta kalli bayan Hajiya karama</p><p>"Kinyiwa uwarki tsoki...banza fitsararra..." Inji inna, yazid dai gyara blanket dake jikinshi yayi yana harara inna</p><p>"Nace kai baka amfani da kayan zamani?... Kanenka basuyiwa kowa ciki ba sai kai banza soko...gaskiya kaji kunya...." </p><p>"Inna dan Allah ki rabu dani inji da abinda ya dameni...." Yafada yana daga mata hannu</p><p>"Kaci ubanda ya haifeka....ni kake yiwa matsifar dan uwarka...." Tafda cike da fada, yazid dai bai kara cewa komai ba, haka ta zazzaga Mashi fada Kuma ba kan meyasa yayi raping poor innocent gal take mashi ba sai kan me baiyi amfani da CD ba, takaici da haushi duk sun cika yazid, daman yasan wannan Karami daga aikinta kenan, hada kai da gwaiwa yayi yana tuna abinda inna tace game dasu Sharif </p><p>"Allah yasa is part of her cork and bull story...ya fadawa kanshi yana daukan wayanshi domin kiran mufida.</p><p><br /></p><p>Shahid na tuki Sharif dake zaune kusa dashi sai saukar Mashi ruwan balai kawai yake</p><p>" I told you mu rabu dasu since its a secret amma ka nace sai mu gano abinda ke faruwa...gashi garin binciko na wani an binciko namu...." Inji Sharif dake huci, tsoki Shahid yaja</p><p>"Wallahi kana kara cewa its my fault zanyi parking motan nan muci uban juna yanzu...." Bai idaba sharif ya katse shi dacewa</p><p>"Anje an fada...laifin uban waye in ba naka ba?... Its all your fault... Kasan halin dad...we don't know irin action da zai dauka kanmu ba...." Ya fada cike da tsoro, shahid baice komai ba yayi parking motan gefen street dinsu don daman basuyi nisa ba, Dora kai yayi kan staring yana tunani, shi kuma Sharif relaxing yayi jikin kujeran motan yana breathing kaman Wanda yayi race, ahankali shahid yace</p><p>"Just relax...dad ba zai hukunta mu kan maganar wannan lunatic old woman ba..." Yafada in a comforting tune don duk da ac dake cikin motan Sharif sai hada zufa yake saboda fargaba, daga kai yayi ya watsa ma Shahid harara</p><p>"You are talking kaman bakasan halin dad ba....yana wasa da maganar wannan tsohuwar ne?....kasan what ever she says is final...ni dai am scared... Allah yasa kar dad yayi cutting allowance dinmu...." Inji sharif, shuru ya dan biyo baya for a moment sannan Sharif ya saki wani dan iskan murmushi tare da cewa</p><p>"Wai is it true yaya yayiwa wata ciki?.... I still can believe this...." Yafada with amusement, shima shahid dariya yayi yana cewa</p><p>"Amma yaya is a disappointment... Ji yanda ya rame kaman kanshi farau....mtwsss...." </p><p>"Novice ne...don da gani he's regretting it...." Dariya sukayi duka, wayan shahid ne ya fara ringing,</p><p>"The boss is calling..." Ya fada yana nunawa sharif screen din wayan,</p><p>"Wallahi wannan tsohuwar najadun ta ja mana...." Inji sharif yana kallon screen din wayan da aka rubuta my hero, which means their dad, yana picking yayi saurin saka a loud speaker,</p><p>"H...." Bai karasa ba dad dinsu yace</p><p>"Ku sameni now!!!..." Yana kaiwa nan ya katse wayan. Kallon juna sukayi sharif ya hadiyi wani abu sabida tsoro, shahid hannu ya Dora bisa kai, few seconds later yace.</p><p>"See we have to be bold... We shouldn't look suspicious...." Inji shahid dake juya kan mota zuwa gida.</p><p><br /></p><p>Dija na nan kwance har karfe 10, wani irin bacci mai nauyi ya kara daukata amma ba mai dadi ba, taba bacci tana firgita, kudundune kanta tayi sabida sanyin da takeji amma rana da fara dukan jikinta ta fara jin dadi amma fever da takeji kara rising yake don inda zaa aunata da thermometer sai ta bawa 48 baya, abunka da jos babu mai maida hankali kanta, kowa ta kanshi yake amma wasu sukan tsaya su kalleta for just few seconds sai su wuce while wasu ko inda take basu kallo, ahankali ta bude idanuwanta da sukayi mata nauyi, ganin mutane na wucewa da yawa yasa tayi karfin halin mikewa zaune, kokarin mikewa tayi amma she couldn't, da crawling ta koma jikin wani bango dake gefe daya ta Jingina, duk abinda ke faruwa tana rike da bag dinta tare da drugs and sauran bread data saya, she never needs her mother the way she needs her now, she don't want anything, kawai abinda takeso is someone she can hold on to, somebody that will hold her back, </p><p>"Ammi...." Tafada ahankali tana nishi, maganin da aka bata ta dauko, ahankali ta daga kai ta yiwa mai saida ruwa alaman yazo da hannunta, da sauri yaron ya kawo ruwa ta mika Mashi goma ya bata ruwa daya batare datace uffanba, maganin ta balla ta saka a baki sannan tasha ruwa, bread tayi kokarin ci saboda yanda cikinta ke crumbling amma ta kasa, kara daga kai tayi tana kallon masu wucewa ko Allah yasa taga abinda zatayi shaawanci Allah so kind sai ta hangi mai saida gurasa, sai taji she can eat it despite her lost of appepite, kiranshi tayi ya zo ta sayi na hamsin, ko rabi bataciba ta ajiye sauran gefe daya, inda ta jingina babu rana so she was so cold, hawaye ne ya kara gangaro mata.</p><p> Ahankali ta daga hannunta ta goge, tana gogewa wasu na fitowa, yanzu takejin rashin uwar tattare daita, she's missing her family like crazy, adua take ko Allah yasa taga mutum daya Wanda tasani, she really needs a comforter, she's so lonely, she is wondering how cruel and wicked the world is, gata yar yarinya in pain and agony amma no body cares, gani take inda zata mutu nan babu bai bin ta kan gawanta,</p><p>"Mutuwa...kazo...dan Allah....." Ta fada sounding so feed up. Tana nan zaune har karfe sha biyu inda taji wannan fever ya sauka, amma she still feels weak, ganin babu mai damunta kan ta tashi inda take zaune yasa ta kara relaxing, bag dinta ta ajiye kayi tayi pillow dashi, few minutes later bacci ya kara dauketa.</p><p><br /></p><p> Bata farka ba sai bayan asr, mikewa tayi taji jikinta da sauki sosai, tanason dan yawo kaman yanda ta saba amma gani take zata hadu da yazid, har yanzu sunanshi bai zauna mata sosai ba, at times she recall Yasir wani lokacin Kuma ta tuna hes yazid not Yasir,</p><p>"Allah yasa kar in ganshi...." Ta fada tana tashi tsaye daga inda take zaune. </p><p><br /></p><p>Bayan sallan magrib dad ne zaune ya hada tagumi sai Hajiya karama da Hajiya babba da suke zaune both side dinshi, then inna dake zaune kan kujera da plate hannunta tana cin tuwo shinkafa sai fada take wai bai yi taushi ba</p><p>"Wai tuwon shinkafan sai gris...gris...yake...mata babu abinda suka Iya.....ko danko tuwon baiyi ba.. Ko saurin uban mu kuke oho...."tafada tana kai loma Kuma from all indication tana jin dadin abincin amma she cant stop complaining, Hajiya babba bata daga kai ba don abinda ya dameta daban, ita Kuma Hajiya karama kallon ta tayi ta watsa mata annoying look batare data bari ta ganiba, sallama akayi Hajiya karama ta daga kai ta amsama su sharif dake sanye da jallabiya kaman wasu ustazai, don suna dawowa suka tarda dad zai fita masjid, suma da sauri suka karasa tare da watsa ruwa suka tafi masjid, kowanne da tunanin dayake, direct daga masjid part din dad sukayi. Itadai Hajiya karama tasan abinda ke nan amma Hajiya babba bata Sani ba cos bata nan lokacin da inna ta fasa wannan kai, inna na ganin su shigo dakin ta daga kai ta watsawa each and everyone dinsu harara tare dacewa</p><p>" shegu Ashe kuna sallama...dayake ni kun raina ni...." Tafada masu, basu kalli inda take ba suka samu gefe daya suka rakube, sunfi minti biyar da zama sannan dad ya daga kai idanuwanshi kaman garwashi ya fara cewa</p><p>"Ba....." Da sauri inna ta daga Mashi hannu,</p><p>"Me zakayi?...." </p><p>"Magana zanyi masu... " </p><p>"Ina yazidu?... Ai shine babba... Don haka...kome zaayi dole a kirashi...." Inna ta fada atakaice, dad dai baiso hakan ba amma bai yiwa inna gardama don haka ya umarci shahid ya kirawo yazid, Shahid na zama shima ya shigo da sallama ya samu wuri ya zauna tare da mike legs dinshi sannan ya soka hands dinshi cikin cinyanshi, kanshi kasa, daman yana shigowa dad ya kara hade rai, saida kowa yayi settling sannan dad ya fara cewa</p><p>"The reason Dana kirawo Ku nan is not for anything sai don Ku biyu...." Ya fada yana nuna sharif da shahid, gabansu ne ya kara faduwa, matsawa shahid yayi kusa da Sharif ya Dora hannunshi kan hannun sharif dake kasan tiles,</p><p>"Na Baku nan da sati biyu kowannen Ku ya fiddo matar aure!!....." A razane su shahid suka daga kai suna kallon dad, surprise look ne kwance kan face din Hajiya babba, Hajiya karama tayi saurin cewa</p><p>"For what?...." Bata idaba inna ta katseta dacewa</p><p>"For meye?....basu isa auren bane?....ko da akwai abinda shegun yaran nan basu Sani ba?...." Shi kam yazid eyes dinshi lumshe Kuma tunda ya shigo falon bai daga kai ba, </p><p>"Gaskiya ni ban son aure...." Sharif ya fada</p><p>"Nima wallahi am not ready for marriage...." Inji shahid, </p><p>"Kai!!!...." Dad dinsu ya daka masu tsawa,</p><p>"Ina wasa daku?...." Da sauri suka girgiza kai, </p><p>"Then kowanne ya fiddo wacce yake so ko Kuma ni in zabar maku...." Dad ya fada atakaice, </p><p>"Ni wallahi bani da wacce nake so...." Shahid ya fada kaman zaiyi kuka at the same time yana harara inna dake lashe hannunta kaman babu gobe, </p><p>"To ai an gama...isa ka bari ni zan zaba masu mata cikin dangi....." Inji inna dake ajiye empty plate dake hannunta kasa, da sauri suka mike,</p><p>"Wallahi bamu son aure...yanzu ...." Suka fada in chorus, </p><p>"Sit now!!...." Dad ya daka masu tsawa, da sauri suka koma suka zaune, yazid dai ko uffan baice ba cos hes absent minded,</p><p>"Bakuson aure kuke bin Matan banza?..." Inji inna, da sauri suka daga kai suka kalleta</p><p>"Mu!!!!!" Suka fada tare kaman basu San abinda take cewa ba, itama Hajiya babba daga kai tayi tana kallon inna cikin tashin hankali</p><p>"Inna matan banza Kuma?..."</p><p>"Eh sharri zanyi masu?...to aure babu fashi... Sai anyi ko kuna so ko baku so...." Tayi directing maganar ta to su Hajiya, Da sauri hajia babba ta mike tana cewa </p><p>"Nifa ban gane abinda ke faruwa nan ba...." Itama inna mikewa tayi</p><p>"To dukana zakiyi ne....naga kin tashi tsaye,..." Kallonta dad yayi ta koma ta zauna</p><p>"Mu wallahi babu ruwanmu....sharri take mana...." Inji shahid, hannu innata Dora bisa kai, </p><p>"Ni kuke kira da makaryaciya?.....inna lillahi.....isa kana ganin yaranka suna kirana da makaryaciya?...." Inna ta fada kaman zatayi kuka, hararanta Hajiya karama tayi,</p><p>"To gaskiya baa yiwa wayan nan yaran da basu mallaki hankalinsu ba aure....how old are they?....ni dai ...." </p><p>"Keep quite!!...." Dad ya daka mata tsawa sannan ya maida hankali shi kan su shahid</p><p>"Both of you are getting married in the next two months... That's final..." Inji dad</p><p> Hannu suka Dora bisa kai</p><p>"Dad dan Allah kayi hakuri.. Babu abinda mukayi....wannan innan karya take...."</p><p>"Quite.. Inna ke karya?..." Inji dad, yazid ko nude eyes baiyiba balle ya daga kai har yace kala, </p><p>"You can go..tunda baku da wacce kukeso....sai inna ta nema maku mata...." Inji dad, da sauri shahid yace</p><p>"Ina da wacce nake so...." Wani irin disgusting look Hajiya karama ta watsa Mashi,</p><p>"Wai da gaske kake ne?..." Ta tambayi dad,</p><p>"Do I look like am joking?..." Ya amsa mata atakaice</p><p>"Haba alhaji...pls let's do some investigation.... It might not be true..." Inji Hajiya karama, Hajiya babba kam confusion bai barta tayi magana ba, ita ba aure ne damuwanta ba, kawai matar banza da inna ta ambata, daga kai tayi ta kalli yazid dake zaune wuri daya ko daga kai baiyi balle motsi, she feels for him har cikin ranta, </p><p>"Yauwa dan albarka...wacece kakeso?..." Inji inna ta tambayi shahid, bai amsa ba ya watsa mata harara</p><p>"Ba da kai akeba?..." Inji dad, da sauri shahid yace</p><p>"Asabe...." Ya fada yana tunanin his feelings towards her, kallon shi Sharif yayi </p><p>"Wacece ASABE?...." Dad ya tambayeshi,</p><p>"Mai aikin small mom...." Yafada kanshi kasa at that moment sai yaji ko yanzu aka daura aure its OK, wani irin tsoki small mom taja</p><p>Good....kai kuma fa?..." Dad ya tambayi sharif,</p><p>"Ai dad ni wayanda nakeso suna da yawa..." Ya fada yana turo baki,</p><p>"Made up your mind...." Inji dad, hajia babba mikewa tayi itama Hajiya karama tabi bayanta inna tabisu da harara. </p><p>"To mutum biyu nakeso...." Ya amsa wa dad,</p><p>"Zan aura maka daya kai kuma in kana da hali ka auri daya da kanka...." Inji dad</p><p> "Ai dad ban iya auran daya in bar daya...sai dai kayiwa shahid kadai in na fara aiki in hada su biyu in aura...." Ya fada babu kunya,, yazid baisan sanda murmushi ya bayyana kan face dinshi ba</p><p>"Wallahi dad karya yake....in baa yi Mashi yanzu nima kar ayi min...." Inji shahid, hararanshi sharif yayi</p><p>"Ai kai kana da wacce kakeso....kawai kayi ni nayi nan gaba ...." Shahid zai magana dad ya daka masu tsawa don ya lura abin zai zama wasa inna kuma tagumi tayi ta cika tayi fam.</p><p>"You are all dismissed.. Kuje Ku fara shiri...your wedding is in two weeks time...." Dad ya fada atakaice, da sauri suka mike </p><p>"Ku tsaya dan waje Ku maidani dan ubanku..." Inji inna, basu CE komai ba suka fice, inna mikewa tayi tabi bayan su shahid, ahankali shima yazid ya mike ya koma part din shi. </p><p><br /></p><p>Inna ba karamin jijjiga tasha a motansu shahid on their way back ba, sai tsine masu take amma basu juyawa balle su tanka mata, har bump suke tsallakawa da gudu.</p><p><br /></p><p> _Two months later_</p><p><br /></p><p>Atakaice cikin wata biyu saida yazid ya je jos sau uku duk don neman dija amma all to no avail, duk zuwan dayake bai fadawa mufida the exact place da zashi sai dai yace office things, amma duk zuwan zan in har ya dawo sai yasha drip sabida rashin cin abinci. </p><p><br /></p><p>Abu kaman wasa anata preparation din auren sharif da shahid, babu irin magiyan da su Mom basuyi ba amma babu abinda dad ke cewa sai ban barin yaran nan sukani cikin hallaka so better in fita hakkinsu. </p><p>Su kam yanzu basu damuwa don sun San dadin mace so suna tunanin they don't have to screw and be afraid anymore, they are free to do what so ever da matansu, kuma sun San money won't be the matsala cos dad yayi masu starting elaborate business kowa da nashi, wani lokacin sai sharif ya rafka uban tagumi da shahid ya tambayeshi matsalan sai yace </p><p>"Yanzu @ 25 zamu samu yara kenan?..." Sai shahid yace</p><p>"Haven't you had of family planning?..." </p><p>"Amma ance it's dangerous.... I love asiya( ASABE)...." </p><p>"Then get ready tobe a dad...nidai am not ready... Abinda nakeso is non stop sex...har inji na bar shaawa...." Inji shahid dake mika. </p><p>"Hmmm..." </p><p>"Ni one thing is that zan kara mata ko zuwa next year ne..." Shahid Yafada not planning at all.</p><p><br /></p><p>Ita kam ASABE tunda sharif yace ita zai aura dad yasa aka maidata gidansu without reason, gidansu fada suka dinga mata kan ta watsar da damanta tunda tayi laifi an maidota, duk explanations da take masu kan batayi komai ba is not accepted by her guidance har sai bayan sati daya da dad da wasu friends dinsu sukaje Neman auren asabe ga shahid. Da gudu suka amince amma ita da kanta bataso.</p><p><br /></p><p>Su Mom basuki zabin shahid ba don sun San da talaka da maikudi are all from Allah, and what will be will always be nor matter the obstacles. Lefensu irin daya akayi duk expensive and elegant kaya aka zuba. Tunda ake maganar wedding din yazid bai taba magana ko sau one ba, shidai nashi ido don according to him his problems are enough for him.</p><p><br /></p><p>Abangaren dija kam taga rayuwa cos tayi spending two whole months on the street of jos, yanzu her pregnancy is 7 months, in ka San dija last three months to yanzu bazakayi identifying dinta ba don tayi baki tayi dirty kafanta yayi developing cracks she looks so tired and pale, yanzu ko hijjab bata yawo dashi kanta kaman na mad person, she looks older than her age, people around sun Riga sun San she's homeless hakan yasa wasu ke dan bata abinci kyauta, tayi kukan rashin kowa har ta hakura ta barwa Allah komai. Amma one thing shine babu Wanda ya kara molesting dinta don kafin a farga da she's aloner har cikinta ya fito. At time in Tana zaune gefe daya kafin ta kwanta sai ta rungume cikinta da kanta don yanzu tasan da akwai da cikin cikinta, the moment tayi hugging cikin sai taji all loneliness is gone, wani lokacin sai ta dinga yiwa cikinta magana in short kaman wata insane person ta koma.</p><p><br /></p><p>Sweetheart kar wacce tayi min kuka cos of dija, remember its just a fiction nothing real.💁🏽♀</p><p><br /></p><p>Once again thanks for the prayers.</p><p>[6/22, 5:51 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: ❤💙💜💛💚🧡</p><p>NA CUCE TA</p><p>🧡💚❤💙💜💛</p><p><br /></p><p>®Zuwairat (ummumaryam)</p><p><br /></p><p>2⃣7⃣</p><p><br /></p><p>Yau anyi ruwa sosai a jos hakan yasa garin yafi da sanyi, dija da rakube gefe daya a inda take kwanciya wato inda masu ganin doc ke zama, ji tayi sanyin yayi yawa, ga jikinta nayi mata itching don har ta mance rabon da tayi wanka, she can smell her body, amma hakan bai hanata jin sanyin ba, bodyguard dintane ya motsa don tana ganin cikinta amatsayin abinda ke tsaronta don duk yanda take da jin tsoro data tuna da akwai wani cikin jikinta sai ta rage jin tsoro, duk yanda take cikin damuwa data tuna abin cikinta sai ta saki murmushi, kawai sai ta zauna tana picturing face din abin dake cikinta, </p><p>"Da sanyi ko?...." Ta fada ahankali bakinta na rawa, </p><p>"Kaima kana jin sanyin?..." Ta sake fada tana kallon cikinta, kuma Allah so kind in tanawa cikin magana bai dadewa sai yayi motsi kaman yana replying ba karamin dadi hakan ke saka dija ba, </p><p>"Banji ba...da sanyi?..." Ta sake tambayan silent tummy dinta, shuru tayi tana sauraron movement as usual amma nothing, shafa cikin tayi,</p><p>"Babu motsin yau?.... Kayi motsi....kaga yau babu wuta ....tsoro nakeji ...kuma ga sanyi...." Ta fada tana shafa cikin ta, still shuru babu response, sikam daga hannunta tayi ta laftawa cikin duka, Wanda sai da ta dan saki kara saboda zafi. Nan take abinda ke cikinta ya fara juyawa kaman yanda take bukata, murmushi ta saki </p><p>"Nace kana jin sanyi?...." Ta tambayi cikin, motsi ya danyi</p><p>"To bari in rufeka...karkaji sanyi...." Ta fada ta bude bag dinta daya kara tsufa yayi dirty saboda yanda take pillow dashi always</p><p> Daya daga cikin kayanta da sukayi dirty ta dauko ta rufe cikinta,</p><p>"Sanyin ya dainako...." Ta tambayi cikin tana shafa shi tro and fro, dan biting lips dinta tayi sabida yanda sanyi ke rasta legs dinta, Riga daya ta kara daukowa ta rufe legs dinta sannan ta samu sauki. Dan juya kanta tayi gefe daya kawai sai yazid ya fado mata arai, sai take tunanin da batayiwa ammi gardama ba da yanzu tana zaune lafiya da family dinta, she's young and innocent amma yanzu tasan yiwa babba gardama is bad don ta koyi darasi a rayuwa, tasan duk abinda babba ya fada is always right don she promise herself never to disobey an elder again. Tana tuna sanda ammi ke kukan kan kar ta tafi ta barsu amma she wanted a better life for herself and her family, bata yi zaton such an awful destiny awaits her ba, </p><p>"Mutane basu da mutunci...in nayi kudi zan dinga taimako....in naga yar karamar yarinya zan taimaka mata....dukkan mutane basu iya taimaka min...." Tafada tana fashewa da kuka at the same time tana scratching jikinta, bata iya good ten minutes batayi scratching private part dinta ba saboda yanda take ji, cikin kuka tafara cewa</p><p>"Na gaji...nagaji.. Allah nagaji...Malam yace aljanna da dadi...ka kasheni ka sakani a aljanna...ni dai nagaji...." Ta fada tana dukan kasa same time abun cikinta ya kara motsi, dan saurarawa tayi sannan tace </p><p>"Da gaske nagaji...kawai mu mutu ko mun huta...ko mun samu wurin bacci mai kyau</p><p>..ko mun dinga samun abinci kan lokaci...." Tafada tana goge face dinta sannan tana tuna ta kusa gama kashe kudinta, despite tana managing sosai. At times tanajin kaman ta tafi kauyen su ammi amma kuma the feeling of rejection sai ya hanata. </p><p><br /></p><p> Yau wedding dinsu shahid sauran 3 days, mufida na tsaye bakin wardrobe tana packing kaya cikin bag, yazid na kwance yana kallon ta, kawai sai tunanin Allah yasa ya shawo kanta kawai yake don yayi deciding ba zaije wedding din ba, instead zai kara komawa jos during the weekend ko Allah yasa yaga dija, dan juyowa tayi ta kalleshi shima ya kalleta tare da sakar mata murmushi, itama maida Mashi martani tayi sannan tace</p><p>"Baby na gama packing nawa....it's your turn...." Ta fada zipping bag din</p><p> Dan murmushi karfin hali yayi yana lumshe eyes kaman mai jin bacci </p><p>"Baby...I think ba zan je ba...." Ya fada ahankali, mufida dakata zipping tayi ta tsaya tana kallon shi for a moment sannan tace</p><p>"Why dear?...." Ta tambaya tana komawa kan gado kusa dashi, jawota yayi </p><p>"Cos I look horrible... Banason a dinga tambayan what's wrong with me...akwai kije...zan zo daukanki next week...." Yafada yana shafa gashin kanta, </p><p>"Haba dear...how is that possible... Ace two of your siblings zasuyi aure kuma your are absent... Gaskiya muje kawai...ko wedding fatiha kayi attending...." Ahankali ya girgiza mata kai</p><p>"No baby...kawai kije...after all we have a lot at the office... Kinga few days back da banyi aiki ba yasa aikin sun zama Lodi....." Kai kawai mufida ta dinga girgizawa, </p><p>"Baby yau Thursday.... Mu tafi gobe Friday...sai ka zauna gidanmu...amma gaskiya I don't want to travel with out you..." Tafada tana lafewa jikinshi, kissing kanta yayi</p><p>"Sorry sweetheart... Just this once...go with out me...", mikewa tayi daga jikinshi</p><p>" if you are not going.. Am not... Kai da abunka kace baka zuwa... Ina amfanin zuwa na ni?..." Tafada tana mikewa daga kan gado, wurin bag datayi packing ta nufa ta duka zatayi unzipping, da Sauri ya mike</p><p>"Baby mommies zasuyi fushi in baki je ba...." Yafda yana rike mata hannu kar tayi zipping bag din,</p><p>"What about you?.. Bazasuyi fushi in baka je ba?..." Tafada kaman zatayi kuka, tallabo face dinta yayi</p><p>"Bazasuyi ba...you know they don't care about me any more..." Yafada cikin sanyin murya</p><p>"They care mana...muje ko kuma in fasa zuwa...." </p><p>"No dear ki zakije....go first thing tomorrow morning... Ni kuma zan zo jibi...." Yayi mata karya, turo baki tayi</p><p>"I don't believe you...." Dariya yayi </p><p>"My word is my bond....just go and enjoy yourself...." Hararanshi tayi</p><p>"Wane irin enjoyment zanyi babu kai?...." Tafada sounding naughty, dariya yayi</p><p>"To muje muyi wanka sai in baki na sati daya...." Yafada yana daukanta.</p><p> Dariya itama tayi</p><p>"Na sati daya na zalunci kenan...." </p><p>"Ai kinsan am always gentle...." </p><p>"This days ko...amma before you are rude in bed...." Tafada tana tuna yanda yake handling dinta kafin pregnancy case din nan ya fito,</p><p>"Yanzu baby am rude?... Duk sauki na?...to yau sai na kwada maki rudeness... Yau my name is rudeboy...." Yafada yana tura kofan bathroom da kaanshi, dasauri ta diro daga hannunshi,</p><p>"Gaskiya banson rudeboy...just be gentle...." Tafada tsoro na kwance kan face dinta,</p><p>"Ai so nake yau in bar maki tabo yanda da kinje kano dadin na nan jikinki..." Hararanshi ta karayi tare da komawa gefe</p><p>"Banson... Na hakura...." Dariya yayi</p><p>"Just joking...kinsan I can't do anything like that..." Yafada yana cika bathtub da ruwa at the same time yana tunanin how well he's trying don ji yake kaman ya Dora hannunshi kai ya dinga ihu in ya tuna cewa his seven months baby na Chan wani waje cikin wahala</p><p>"That's if she make it...." Yafada under his breath</p><p> Mufida kura Mashi ido tayi son in da sabo ta saba several time zai dinga yiwa kanshi magana at times taji wani lokacin kuma batajin abina yake cewa amma she knows it's all about khadija. </p><p><br /></p><p>The following day suka shirya bayan breakfast wanda ba wani cin kirki yake ba don in don sonshine ya samu liquid abu ya sha ba kawai cos in sau goma zai kai abu cikin bakinshi sai ya tuna da dija ko ta ci ko bata ci ba hakan yasa ko kadan baison cin abinci amma yasan rashi hakan zai batawa mufida rai so dole yake forcing kanshi yana cin abinci. </p><p>Trolley bag dake shake da kayan sawan mufida ya dauka ita kuma mufida ta tsaya kashe electronic dake falon. Bakin kofan falon ya tsaya yana jiranta sai da ta gama ta taka cikin kasaita ta karasa inda yake tsaye, hannuwa ya bude mata ta fada jikinshi</p><p>"I will miss you..." Ya rada mata cikin kunne, </p><p>"For just a day ko....tunda kace zakazo gobe...." Tafada tana kara lafewa jikinshi, </p><p>"Amma kaman shekara nakeji...cos am gonna be lonely...." Ya ce mata, kissing dinta yayi for a moment sannan ya bude kofa</p><p>"Ladies first..." Ya fada yana nuna mata kofa ahankali ta wuce tana murmushi bayanta yabi tare da locking door dinsu sannan ya kama hannunta suka sauka zauwa parking lot. </p><p><br /></p><p>Da Sauri ya ajiyeta park don cewa tayi bata iya driving from abj to Kn wai zai bata wahala, empty golf ya amsar mata ya biya ta shiga sannan ya kama hanyan office. </p><p><br /></p><p>Around noon yana zaune a office yana tunanin rayuwa, yanzu yasan sauran two months dija ta haihu kuma baisan irin halin da zai shigaba muddin har lokacin yayi bai ga dija ba hakan yasa yayi niyyan in ya tafi jos wannan Karin zai je TV and radio stations ya bada description dinta don a tayashi cigiyan ta don ya tambayi pics dinta ammi bata dashi. </p><p>"Kai..." Yaji an fada ana dukan desk din gabanshi, hakan ya maidoshi hayyacinshi, gyara speck din face dinshi yayi yana murmushi</p><p>"Kai yanzu baka da abunyi sai tunanin..." Inji sultan dake zama kan leather seat dake facing yazid</p><p>"Ba tunani nake ba...kawai am just absent minded ne...." Ya amsa Mashi,</p><p>"Kai ustaz ne amma sai shegen karya....akamaka red handed amma kace ba haka ba...in ba tunani kake na did you know sanda na shigo ciki?..." Sultan ya tambayeshi, murmushi kawai yayi bai kara cewa komai ba, sultan zai bude baki yayi magana wyanshi ya fara ringing, murmushi yayi yana cewa</p><p>"My mommy..." Yafada yana picking wayan, yazid dai kura Mashi ido yayi don yanzu ya mance rabonda mom ta kirashi sannan in ya kirata discussion dinsu very brief ba kaman da da suke hours suna hira a kan waya ba.</p><p>"Mommy I promised zanzo ai....tare zamu cinye wannan weekend...." Yazid yaji sultan na fadawa mom dinshi</p><p> Murmushi kawai yazid yake saboda yanda sultan ke labartawa da mom dinshi, sunfi minti ashirin suna waya sannan sukayi bankwana, dariya sultan yayi yana cewa</p><p>"Wallahi zullumin tuki daga nan zuwa jos kawai nake..." Surprise look yazid yayi Mashi tare da dafa goshinshi</p><p>"Kasan na mance you are from jos?.... It escape my mind wallahi...." Dariya sultan ya karayi</p><p>"Da gaske kake?..." </p><p>"Wallahi kam...ai for the last two months sau uku baje jos....kuma a hotel nake kwana kafin in dawo...." </p><p>"Kam....amma baka kyau ta ba....ga gidajen mu chan har da guest house...." Inji sultan</p><p>"Ai I tell you na mance...ko gobe ma zan goma jos....." Yafada not sounding happy kaman da farko, </p><p>"To me kakeyi a jos?..." Sultan ya tambayeshi, shuru yazid yayi yana Dana sanin fada Mashi yana zuwa jos don ya mance zai tambayeshi dalilin. </p><p>"Ina zuwa wajen families ne..." Yazid yayi Mashi karya, girgiza kai sultan yayi</p><p>"Ban yarda ba ...kodai mata zaka kara...amma zuwa jos don ganin family har sau uku a cikin wata biyu is not accepted...." Dariya yazid yayi</p><p>"Ai ba mugun abu bane...kawai na fada maka gaskiya...." </p><p>"Hmmm ai ku ustazai ne...baku karya...saidai Ku fadi ba daidai ba....." Inji sultan, yazid dan daure fuska yayi don yasan he's no saint,</p><p>"Gobe sai mu tafi tare kawai..." Inji sultan, </p><p>"Ai ni ba cikin gari zani ba....sai dai zan kwana gidan Ku ne...." </p><p>"Ai wannan ba matsala bane ...kawai muje tare ..zanyi escorting dinka zuwa inda zaka...." Da Sauri yazid ya girgiza Mashi kai </p><p>"No.... "</p><p>"OK...muje sai kayi amfani da motan gidanmu kaje inda zaka ...." Sultan ya fada mashi,</p><p>"OK then....daman banson kwana a hotel wallahi...." Haka suka cigaba da hira sannan sultan ya koma office dinshi, the following day which was Saturday suka kama hanyan jos run da sassafe, da motan sultan sukayi amfani.</p><p>[6/22, 5:52 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: ❤💜💛💙💚🧡</p><p>NA CUCE TA</p><p>💚🧡❤💙💜💛</p><p><br /></p><p>®Zuwairat (ummumaryam)</p><p><br /></p><p>2⃣8⃣</p><p><br /></p><p> *Wattpad @ummumaryam29* </p><p><br /></p><p> _Www.ummumaryam.com_ </p><p><br /></p><p> *Email me @ Zuwairat.nuhu@gmail.com* </p><p><br /></p><p> *Don't forget to vote and comments. Thanks*</p><p><br /></p><p> *This page is for all my wattpad follower, voters and readers, thanks for the love* </p><p><br /></p><p>Sultan na tuki yazid yayi relaxing with his eyes closed, tunanin rayuwa, kawai adua kawai yake Allah yasa yaga dija wannan Karin don yasan sauran two months dija ta haihu, in har bai gantaba before then baisan yanda zaiyi da ranshi ba. Sunfi hour suna tafiya amma ko uffan baice ba, saidai sultan ya dan jashi da hira kuma he chooses the short word to reply him don kar hiran ya Dau lokaci. </p><p>"Wai pls what is wrong with you?....ba haka kake ba...." Inji sultan, cikin kasala yazid ya kalleshi </p><p>"Babu komai...kawai dai na gaji ne....amma am OK?..." Sultan kallon shi yayi for just few seconds sannan ya maida hankalinshi kan titi</p><p>"Kasan wallahi ina iya sharing problems dina da kai...though we are just co workers amma you have a special place in my heart...amma kai ba haka ba... Ga damuwa karara a face dinka amma baka iya fadamin abinda ke damunka...." Sultan ya fada yana tuki, dan murmushi yazid yayi yana gyara zamanshi</p><p>"Kasan ba Komai mutum ke iya fadi ba...wani abun sai hakuri...." Yafada cikin sanyin murya</p><p>"Amma ance problem shared is problem solved....taya zaka samu maganin matsalan ka in baka fadi ba?.....ni wallahi ina ganin kana daga cikin mutanen da zan iya sharing komai dashi....you are nice... Religiou...." Bai idaba yazid ya dan daga mashi hannu </p><p>"Am not all you have mentioned.... Am a monster... Am bad and dangerous... In short am dangerous than I gave myself credit for...." Yafada muryan shi na cracking kaman zaiyi kuka, ajiyan zuciya sultan ya saki</p><p>"Just let it out....zakaji sauki sosai...." Kai yazid ya girgiza Mashi,</p><p>"Something are better left unsaid.... Am not proud of abinda nayi....saying it ruins my happiness... Kawai kasani am not who you think I am....." Yafada yana murmushi wanda yafi kuka ciwo,</p><p>"OK....amma take it easy on yourself...." Inji sultan.</p><p> "I wish...." Inji yazid, haka sultan ya dinga driving har suka isa gidansu, kafin su iso babu abinda yazid keyi sai kalle2 yake har sultan ya gane maybe he's looking for something, </p><p>"Kana Neman wani abune?..." Sultan ya tambayeshi, kai ya girgiza</p><p>"No...kawai ina kallon garinku ne..." Ya amsa mashi, har cikin ranshi yanason fadawa sultan amma how would it sound ace shi yazid yayi impregnating yarinya. Shuru kawai yayi.</p><p><br /></p><p>Sultan bai gama parking ba lil sis dinshi da bazata wuce 17 ba ta fito a guje, sauran kadan data kadashi kasa sabida yanda ta diro Mashi kaman wata karamar yarinya, yarensu suka farayi daga inda suke, dan kauda kai yazid yayi tare da yin dariya for 0ne to two seconds saboda how funny it sounds</p><p>"Baki gaida friend dina ba..." Ya fadawa sis dinshi, da sauri tayi juya ga yazid dake wearing murmushin karfin hali ta gaidashi amsawa yayi yana cewa</p><p>"What a remarkable resemblance...." Don daka gansu kasan blood daya ke running through their vain. Sultan na rungume da sis dinshi ya juya ga yazid</p><p>"Ustaz...you are welcome to my home...." Murmushi yayi yana tunanin he wish zai ya fada mashi ya bar kiranshi da wannan sunan amma yasan ko ya fadi a banza,</p><p>"Gidanku dai...ka wani CE my home kaman naka kai kadai?...kaida baka da mata?..." Yazid ya fada mashi cikin zolaya. Haka suka shiga cikin katafaren falon, da sauri mom dinshi ta taresu cikin murna da jin dadi</p><p>"Mom wannan shine yazid isa bala?...wand...." Bai idaba mom dinshi tace</p><p>"Ohhh...you mean isa bala dai?..." </p><p>"Yes mom...shine mukayi wedding dinshi last few months...." Dariya mom tayi farin ciki karara a face dinta, </p><p>"Yanzu kuje kuyi wanka kuyi freshening up sai Ku fito kuci abinci...." Inji mom din sultan, sultan bin wata hanya yayi bayan ya umarci yazid daya biyoshi. </p><p><br /></p><p>Nan suka shiga wani part mai dauke da falo da dakunan bacci biyu. </p><p>"Uztaz kayi amfani da wannan dakin.. " ya nuna mashi left hand side room, </p><p>"OK..thanks... Amma yanzu zanje inda na fada maka.... In na dawo da yamma zanci sbuncin...pls help me explain it to mom kar tayi fushi...." Tsaya kallon shi sultan yayi</p><p>"Amma why not ka watsa ruwa nima in watsa ruwa sai muje tare?.." Da sauri yazid ya girgiza Mashi kai kaman Mara gaskiya,</p><p>"No...I will find my way back...." Amsa mashi</p><p>"Hmmm you are just unbelievable.... To bari driver ya kaika tunda ba garin kasani ba sosai..." </p><p>"OK.. " yazid ya amsa mashi amma ba don ya so ba</p><p> Sultan fita yayi ya fadawa mom dinshi yanda sukayi da yazid, Sam bataji dadi ba amma daya fada mata nan gidan zai kwana sai ta saki ranta. Wurin driver yaje ya sanar dashi ya shirya zai fita da abokinshi.</p><p><br /></p><p>Part din shi ya koma ya tarda yazid daya rafka tagumj, nan ya fada mashi motar is ready da sauri ya mike kaman wanda ke zaune kan allura. Bayanshi sultan yabi da kallo yana mamakin how boring yazid have become. Yazid na fita ya tarda driver dake zaune cikin motan yana jiranshi da sauri ya jefa kanshi gaban motan yanda zai samu view din gari da kyau,</p><p>"Ka kaini supermarket..." Ya fadawa driver don sayawa su ammi foodstuffs kaman yanda ya saba saye duk sanda zaije kauyensu. Daya daga cikin supermarket driver ya kaishi. Fita yayi ya shiga yana kalle2. Bayan kaman minti ashirin aka biyoshi da kayan abinci kala2. Daga nan suka kama hanyan kauyensu ammi.</p><p><br /></p><p>Ita kuma dija data tashi yau taji duk jikinta babu dadi, haka nan take samun weird feelings, kawai cewa cikinta tayi batajin dadi, ta fita tana yawonta amma she walking tana bude legs sabida yanda batajin dadin tafiyan. She feels so uncomfortable. Inda take cin abinci Safiya taje ta gaida matar</p><p>"Dija an tashi?..." Matar ta tambayeta,</p><p>"Eh...." Ta fada tana zama dan nesa daita don tana ganin the look on people's face duk sanda ta zauna kusa dasu hakan yasa take zama dan nesa dasu. Tafi minti goma zaune bata ce kala ba, juyowa mai kosan tayi</p><p>"Yau dija baki sayen kosai ne?... Ko sai ta kare?...." Matar ta tambayeta, </p><p>"Zan saya...." Ta amsa mata cikin sanyin murya, shuru ya an biyo baya sannan tace</p><p>"Dan Allah....inyi wanka.....gidanki?...." Ta tambayi matar muryan ta na rawa, </p><p>"Eh...babu matsala...amma ki jira in gama sai muje tare tunda da nisa kadan..." Matar ta amsa mata, wani irin dadi taji don tunda aka gano she's on the street bata kara samun wurin wanka ba, da tana wasta ruwa cikin bathroom din hospital amma yanzu angano she's not a patient aka hanata wanka wurin. Yanzu ta manta rabonda ta sakawa jikinta ruwa. Kosai ta saya na hamsin ta zauna nan ta ci tana jiran matar ta gama su tafi.</p><p><br /></p><p>Sai wajen 10:30 matar ta gama ta tattara kayanta dija tabi bayan ta suka tafi gidanta</p><p> Suna isa ta nuna mata kewayenta</p><p>"Bissimillah...." Matar ta fada mata,</p><p>"To...na...gode..." Dija ta fada ta nufi tiny toilet din, tana shiga taga empty bucket, daukowa tayi,</p><p>"Ina...ruwa...da sabulu?..." Ta tambayi matar da ke kaikaye gidanta saboda yanda yara suka hargitsa mata gida.</p><p>"Ga ruwa cikin wannan drum..." Ta fada tana nuna mata drum dake tsaye</p><p>"Sannan da akwai sabulu bakin window..." Ta nuna mata inda soap yake, jiki na rawa ta debo ruwa, bata diba da yawa ba ta dauka ta kai toilet sannan ta dawo ta dauki sabulun. </p><p><br /></p><p>Tana rufe kofa ta fara rage maranta sannan ta cire kayan jikinta, tana yi tana dan cije labe ko ina ke mata zafi oho, tana gama cirewa ta ratayesu, tsayawa tana shafa cikin ta,</p><p>"Yau zamuyi wanka...." Ta fada cikin whisper, hannunta biyu rike da tummy dinta ta jingina da bango, sai tayi saurin dagowa tare da Dan sakin kara, hannu ta dan zagaya bayanta tana tabo inda keyi mata zafi, still inda ammi ta doketa da itacene, tana tabawa taji kaman wajen na ruwa. Kurawa cikinta ido tayi kaman baa gobe, tana shafawa tana murmushi,</p><p>"Ko ta ina zaka fito?...." Ta tambayi cikin, ahankali ta duka ta fara watsawa jikinta ruwa sannan ta dauki soap da soso dake rataye ta fara wanke jikinta kaman wacce bata taba wanka ba, the more tana wanke jikinta the more tana jin relief especially her private part, wani irin sakayau taji, bag dinta dake gefe daya ta bude ta dauki wata riga amma ba neat one ba, saka kayan tayi ta maida wanda ta cire sannan ta fito. Adua take Allah yasa matar tace ta zauna ko da na minti ashirin ne, </p><p>"Na...gama...." Ta fadawa matar, juyowa matar tayi da murmushi fuskanta </p><p>"To dija...." Ta amsa mata</p><p>"Nagode...." Dija ta fada mata ahankali,</p><p>"Babu damuwa...." Ta amsa mata. Ahankali dija ta juya ta bar gidan.</p><p> Wankan datayi yasa taji kaman ta samu wuri ta kwanta, still tana jin yunwa cos kosan bai isheta ba, tana tafiya cikinta na crumbling,</p><p>"Yi hakuri....kudin mu ya kusa karewa....dole muyi maleji...." Ta fadawa cikinta tana tafiya. </p><p><br /></p><p>Wani waje Mara yawan mutane ta samu ta zauna nan kasa tare da mike legs dinta ta harde hands dinta kan cikinta ta zauna tana kallon masu wucewa.</p><p><br /></p><p>A kano kam ba karamin shagali ake ba, family house dinsu yazid ya cika tatul da mutane. Da mufida tazo ranar Friday tambayan yazid hajuya karama tayi ta sanar da ita zai zo yau asabar, mom dinshi kam haushi da takaici ya cikata da bata ga yazid ba, amma data tambayi Hajiya karama ko tayi waya da yazid sai ta shaida mata mufida tace zai zo yau. Hakan yasa ta dan kwantar da hankalinta.</p><p>Yau tun ten suke saka ido don ganin yazid amma babu shi, number shi mufida ta kira taji switch off. Mom dinshi fada ta dinga yi dataga har karfe 1 babu yazid kuma karfe biyu ake daurin auren. Itama kira tayi taji kashe</p><p>"Wannan yaron na naiman raina ni ko?... Zai ci ubanshi ne..." Inji mom dinshi dake tsaye kusa da Hajiya karama cikin wata karamar daki wanda babu kowa,</p><p>"It's not late...kilan ya iso kafin daurin auren..." </p><p>"I doubt that... Gashi wayanshi bai zuwa?... Wallahi in bai zo ba to he better remain in abuja... Don ranshi zaiyi mugun baci in har ya taka Gidan nan...."</p><p>Inji Hajiya babba dake huci</p><p>"Kiyi hakuri anty..kinsan yazid ya chanza...nidai Allah yasa yaga dija ko hankalin kowa ya kwanta...." Inji hajia karama in a calming tune. Hajiya babba bata kara cewa komai ba ta fice daga wurin, Hajiya karama daukan wayanta tayi ta sake trying number yazid amma shuru.</p><p><br /></p><p>Yazid dai nan zuwa gidansu ammi driver ya fito ya fara shiga da kayan da yazid ya sayo. Ammi ta koma rai da kashi don babu sauran flesh jikinta, duk wanda ya ganta sai yayi tunanin bazata kai hour daya da rai ba, yazid yayi sallama ya shiga bayan an gama shiga da kayan, an gidan ya fara gaidawa suna amsa mashi, da suna fushi dashi kan abinda yayiwa jikansu amma yanzu sun gane haka Allah ya kaddara, ji yayi binto nacewa</p><p>"Har yanzu bamu ga adda ba...." Ta fada mashi don tasan saboda ita yake zuwa. Nan take yazid yaji legs dinshi sunyi sanyi, amma daman he wasn't expecting su ganta. Inda ammi ke kwance ya nufa, gabanta ya durkusa ya gaidata, ko bude ido batayi ba balle ta amsa mashi, sai nishi kawai take</p><p>"Dan Allah ki bari in kaiki asabiti....dan Allah ki rufamin asiri kar hakkinku yayi min yawa...." Inji yazid dake magana kaman zaiyi kuka, still ammi bata ce kala ba, yafi minti goma nan durkushe amma ko eyes bata bude ba balle ta tanka mashi, ahankali ya mike ya je wajen tsohon gidan. Request ya nema kan a fadawa ammi ko zata yarda ya kai ta hospital, tsohon mikewa yayi ya tarda ammi inda take kwance ya dinga sauke mata zafafan words wanda yasa ammi fashewa da kuka</p><p>"Zanje...." Naji ta fadawa tsohon,</p><p>"Maza tashi ki shirya...in banda abinki ai wannan yaron nada tsoron Allah...ji yanda yake wahalan zuwa nan....INA tabbatar maki in wasu ne ko tunawa basuyi....maza tashi ..." Ya daka mata tsawa, ahankali ta mike jikinta sai rawa kawai yake Kaman 100 years old woman. Da taimakon binto ta shirya, yazid na waje yana jiran fitowanta, few minutes later ta fito binto rike da hannunta, sai wata mata dake biye dasu. Da sauri yazid ya bude mata bayan motan ta shiga da binto sai yaruwan ammi.</p><p><br /></p><p>Shima yazid shiga yayi,</p><p>"Ka kaimu asiti...." Yazid ya fada ma driver,</p><p>"Wanne?..." Driver ya tambayi yazid,</p><p>"Nima ban sani ba....amma ka kaimu mai kyau..." Yazid ya amsa mashi, tada motan driver yayi yana cewa</p><p>"Ko in kaiku general hospital?..." Da sauri yazid yace</p><p>"Aa...nasan da akwai cikowa..."</p><p>"Zanyi masu bayani tunda momin abokinka babbace a asibitin... Na tabbatar basu bata maka lokaci..." Inji driver, </p><p>"In ka tabbatar da hakan mujeto..." Ya fada ba don yaso ba don shi anything general ba so yake ba.</p><p><br /></p><p>Around three suka kama hanyan cikin gari, ammi ta jingina idanuwanta lumshe,binto sai kalle2 kawai take, adaidai lokacin da suka kusa isa gate da zai sadasu da hospital ita kuma dija ta taho zata cin abinci rana don tun wannan kosai bata kara cin komai ba duk don tayi manejin yan kudinta da baifi 1k ba, binto ta fara ganinta daga nesa amma bata yarda cewa itace ba, shima yazid ya ganta kuma kallo daya yayi mata ya kauda kanshi gefe, da sauri ya kara maida kanshi yana kallon ta while motan na shiga hospital, da sauri binto tace</p><p>"Laaaaa....wannan kaman.. Adda dija...." Tafada da sauri, da sauri ammi ta bude ido, yazid ji yayi gabanshi yayi mugun faduwa, </p><p>"Stop the car!!!!!....." Ya fada cikin muryan da shi kanshi baisan yana dashi ba, </p><p>"Adda!!!!...." Binto ta kwalawa dija dake wucewa gefensu, dija daga kai tayi sukayi ido hudu da binto, tsayawa tayi tana kallon binto then ammi data fashe da kuka ganin yanda dijarta ta koma kaman almajira ga kuma ciki, yazid dai mutuwar zaune yayi yana kallon dija at the same time hawaye na bin juna, dija na tabbatar amminta da binto ta gani ta saki bag dinta ta fara bin motan nake Neman wajen parking da gudu tana kira ammi on top of her voice, motan na tsayawa ta karasa wajen tarufe Marfin motan ta bude, nan take ta fada jikin ammi tana kuka, babu abinda take cewa sai </p><p>"Ammi....ammi...kiyi hakuri....ban...karawa....ammi waje nake...kwana.....ammi kalli cikina....ammi Dane cikin cikina...ammi yana motsi..ammi...ki maidani gida....ammi kar ki barni nan...ammi ban kara yi maki gardama....ammi dan Allah ki maidani gida in barjin sanyi daddare....." Yanda take magana sai ka rantse Mara hankali ce, babu abinda yazid yake sai kuka, yana hawaye hannunshi biyu kan bakinshi. Dija kara rike ammi tayi tana kuka tana magana, binto kuka likewise sis din ammi, shima driver dake zaune kusa da yazid juyawa yayi yana kallon yar yarinyan dake irin wannan maganar shima saida hawaye ya tarar mashi, ammi tallabo face dinta tayi </p><p>"Dijata...." Tafada cikin kuka, dija na kuka jikinta na rawa ta kama hannun ammi</p><p>"Ammi ki taba kiji....yana motsi...." Ta fada cikin matsanacin kuka, tun yazid na hawaye kawai sai kukan taci karfinshi, jin kukan mutum yasa dija daka kai ta dan leka gaba, nan suka hada ido da red and tearful eyes din yazid, da sauri ta mike tana</p><p>"Ammi shine....ammi wallahi shine...." Tana maganar tana ja da baya, ganin mota ya taho ita kuna na ja da baya2 yasa yazid saurin fita daga cikin motan, aikam tana ganin ya fito kuma su ammi basu hanashiba yasa ta juya da gudu wanda yayi daidai da zuwan motan. Before driver Motan ya taka break it was late, wani irin karo dija tayi da motan yayi sama daita. </p><p><br /></p><p>Hannu yazid ya dafa ga kai tare da saki wani irin razanannen ihu.</p><p>[6/22, 5:52 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: 🧡💜💙💚💛❤</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙💚💛❤🧡</p><p><br /></p><p>®Zuwairat (ummumaryam)</p><p><br /></p><p>2⃣9⃣</p><p><br /></p><p> _Follow me on:_ </p><p><br /></p><p> *Wattpad @ummumaryam29* </p><p><br /></p><p> *Email:Zuwairat.nuhu@gmail.com* </p><p><br /></p><p> *IG: zuwairatummumaryam* </p><p><br /></p><p> *Website:Www.ummumaryam.com* </p><p><br /></p><p> *And also join my new Facebook group: Zuwairat ummumaryam and Zuwairat ummumaryam page.* </p><p><br /></p><p> *Snapchat: ummumaryan29*</p><p><br /></p><p> Ammin data dade batayi tafiyan kirkiba sai gata ta fito daga cikin mota da gudu, haka zalika su binto da driver dake cikin mota, yazid bai San sanda ya karasa inda dija ke wance ba, shima doc daya bugeta fitowa yayi cikin tashin hankali,</p><p>"Khadija!!!....." Yazid ya dinga kiranta yana rike daita nan kasa, hannu ammi ta dora bisa kai tana kuka,</p><p>"Khadija dan...Allah... Wake up...." Yafada yana girgiza ta da karfi amma ko motsi batayi, mutane taruwa sukayi suna kallon su, doc daya bugeta ya rike yazid don ya samu daman duba dija amma wani naushi yazid ya kai Mashi Wanda ya tsorata shi yayi saurin ja da baya, </p><p>"Khadija... Pls....don't do this to me....I will be miserable for the rest of my life...." Yafada yana dorata kan kafanshi at the same time yana kuka kaman ranshi zai fita, duk mutanen dake tsaye babu Wanda yayi kokarin taimakawa, doc daya bugeta nason taimakawa amma yana tsoro kar yazid ya kara naushinshi, yazid tsaya kallon yanda cikinta ke motsi yayi ya daga kai yana kallon faces din mutane yana cewa</p><p>"Dan Allah Ku taimaka min....pls help....." Da sauri doc din nan ya zo ya rike wrist dinta for a while sannan yace</p><p>"Ka dauketa muje...." Inji doc cikin sauri, da sauri yazid ya mike ya dauketa, ammi da dasu binto babu abinda suke sai kuka, bin bayan yazid sukayi shi kuma yazid na biye da doc, sai sauri yake amma ko gabanshi bai kallo sai dija, yana tunanin yanda ta koma kaman baitaba</p><p>"Me zanyi maki in biyaki for all this pain...." Yafada yan kuka, kallon yanda cikinta ke ta motsi kawai yake, bai ankaraba yaji zaa amsheta daga hannunshi, sai lokacin yaga nurses da gadon da ake tura mutum, baisan ya akayi sukazo ba, babu musu ya dorata kan gadon aka fara turata amma yana rike da hannunta, goshinta daya kumbura ya kalla.</p><p>Motsin dan cikinta looks so visible da ko daga nesa kana Iya hangen yanda cikin ke motsi kaman zai fito</p><p> </p><p>Doc kallon ta yayi for ya moment sannan yace</p><p>"Take her to the labour room..." Hankalin yazid ne ka Kara tashi, baisan lokacin dayace</p><p>"Its just seven months....", doc dai baice komai ba amma deep down yana tunanin wanne relationship ke tsakaninshi da ita don they look so different, babu alaman dangantaka tsakaninsu don duk Wanda yagansu yasan they are from two different part of class and level amma yanda yake nuna damuwanshi is questionable to him</p><p> Inda dija ta kwana for some days aka shiga daita only she was unconscious, tsaye yazid yayi aka shiga ciki daita, ammi dai kuka yaki tsayawa, yazid goge face dinshi yayi ya fiddo wayanshi dake cikin aljihunshi Wanda ya kashe tun 12am na jiya kuma bai kara kunnawa ba saboda kar mufida ta tisashi gaba. Kunnata yayi sannan yayi dailing number Salem, after like ringing biyu zuwa uku yayi picking yana cewa</p><p>"Wai me yayi zafi da zaayi bikin lil brothers dinka amma baka zo ba?.... Gaskiya baka kyauta ba... Dazun saida dad dinku yayi min magana bayan daurin auren... Karya nayi Mashi nace kuna port...." Duk maganar da yake yana fada cikin annoyance ne amma gurin yazid shine ya kai aya sannan ya fada Mashi abinda yake son cewa, yana jin shuru yafara cewa</p><p>"Na ganta!..." Ya fada in one word,</p><p>"Wa?..." </p><p>"Khadija..." Ya amsa Mashi cikin sanyin murya , dasauri Salem ya saki ajiyan zuciya tare dacewa</p><p>"Ina?..."</p><p>"A jos...."</p><p>"Da akwai cikin?..." Ya tambayeshi full of excitement, </p><p>"Yes....amma she have an accident while running away from me...." Yazid ya fada muryanshi na rawa,</p><p>"Subhanallah!!....how is she?..." </p><p>"Yanzu anshiga daita ciki....salem... Na cuceta....you need to see her....ta koma kaman baitaba....I don't know what made me do it...." Yafada yana kokarin sake kuka saboda yanda heart dinshi keyi Mashi zafi,</p><p>"Rabo...kaddara...destiny...." Salem ya amsa Mashi in a calmly manner</p><p>"Yanzu me doc yace?... Hope it's not serious?..." </p><p>"Bata motsi....amma naga cikin na motsi...ka tayani adua...I don't want to loose anyone of them.... Inason in biya Khadija for the pain and agony I caused her....kuma inason abinda zata Haifa....nasan ana iya stigmatizing dan ko yan...amma ba laifin shi ko ita bane....it's all my fault... The child deserve to live...." Yafada in a regretting manner at the same time hawaye na gagarowa daga idonshi,</p><p>"Insha Allah the child will live...babu abinda zai samu both of them.... Ka kusa zama dad ko..." Salem ya karasa maganar da zolaya, yazid zai bude baki yayi magana yaji call ya shiga, dubawa yyi yaga small mom, </p><p>"Bari zan sake kira...mom is calling..."</p><p>"OK..pls give me updates about her..." Inji Salem</p><p>"OK..." Kawai ya fada yayi picking call dinta, itama balbaleshi ta farayi kan meyasa baizo daurin auren su Sharif ba, saida ta kai aya sannan ya fada mata ya gan dija</p><p>"Kai alhamdulillah...." Ta fada with excitement kaman baita ke fada few seconds ago ba, dan murmushi yayi sannan ya fada mata halin da ake ciki, </p><p>"Inna lillahi waina ilaihi rajuun!....hope it's not bad?..." Fada mata komai yayi</p><p>"OK...ka kula daita...zan yiwa anty magana don she's so angry..." Ta fada Mashi,</p><p>"OK nagode...." Ya fada yana juyawa don gani Wanda ke tahowa, ganin doctor ne yasa yayi saurin katse wayan tare da nufanshi</p><p>"Doctor... Ta tashi?..." Ya tambayeshi,</p><p>"Yes...pls waye mijinta?..." Shine tambayan da doctor yayiwa yazid Wanda har su ammi sunji Sadda kai ammi da family dinta sukayi while yazid ya kasa replying question din doc, </p><p>"Pls ya jikinta..hope its not bad?....." Ya sake tambayanshi,,</p><p>"Not that bad...few injuries ne...." Ya amsa Mashi sannan ya sake cewa</p><p>"Waye mijinta?..." </p><p>"Ni....." Ya amsa Mashi kanshi kasa, kallon up and down doc yyi mashi, yafi minti biyu yana kallon shi inda shi kuma yazid bai yarda suka hada ido na,sai da ya gama kallon sannan yace</p><p>"Follow me..." Ya fada Mashi atakaice tare da juyawa, jiki ba kwari yazid ya bi bayanshi, wani office dake kusa da labour room doc ya shiga inda wata babbar mace ke zaune, yazid na daf da shiga yaji kaman dija na cewa</p><p>"Wayyo ammi cikina...wayyo mutuwa zanyi...." Da sauri yazid ya shiga cikin office din yana cewa</p><p>"Kaman kukanta nakeji....pls what's happening?..." Ya fada cikin tashin hankali, </p><p>"Sit...." Matar dake cikin office ta fada Mashi tare da nuna Mashi seat dake opposite to Wanda ya banke dija.</p><p>"As a result of event daya faru..ta shiga labor...." Aikam sai ya dafa kai </p><p>"Labor doc...its seven months... Anya babyn zai rayu?...." Ya fada kaman zaiyi kuka, kallon juna sukayi don basu yarda He's responsible for the pregnancy ba...kawai suna ganin He's lying, </p><p>"Ai seven months na da...baka taba jin an haifi bakwaini ba?... Kawai saidai maganar incidents daya faru...amma da pregnancy is OK..." Inji matar, yazid shuru yayi ya rasa abun cewa, </p><p>"So zaa sayo kayan haihuwa...although bamu amsan irin wannan haihuwan but due to the circumstances we will help...." Matar ta sake fada Mashi, yazid dake zufa dag red eyes dinshi yayi ya kallesu </p><p>"Pls...Ku cire abinda ke cikinta....I don't think tana da strength da zata haihu...." Ya fada voice dinshi na cracking, kai matar ta girgiza,</p><p>"Its a government hospital.. We don't work that way..." Ta fada Mashi,</p><p>"Then zan kaita private hospital..." Ya fada yana mikewa, da sauri doc yace</p><p>"Ina da private hospital... In that case mu kaita chan..." Ya fada yana mikewa, daman already yazid tsaye yake, fita yayi ya sanar da ammi yanda sukace, fadawa doc din yayi suyi gaba yana biye dasu. </p><p>"Who will pay the bills..." Doc ya tambayeshi,</p><p>"Money is not the problem..." Inji yazid, cikin mota gidan su Salem ya shiga ya zauna baya, gudun kar dija ta kara ganinshi ta rude, few minutes later aka fito daita zaune kan wheelchair, sai kuka taka tana cikinta, tana ganin ammi ta mika mata hannu, da sauri ammi ta mike taje inda ake turota ta rike mata hannu, duk ta manta da aladansu, babu abinda ke cikin ranta sai tausayin dija, </p><p>"Ammi cikina....cikina...marata..." Kawai dija ta take fadi, yazid na kallon ta daga inda yake zaune cikin mota, cikin mota doc aka sakata su ammi suka shiga suka bar wurin, yazid ya umarci driver yabi bayansu.</p><p><br /></p><p>Kawai adua kawai yake kar wani abu ya sami dija he can bear loosing the child amma banda dija. Shi gani yake the child won't make it amma yana da hope cewa he will have any number of kids he want in the future</p><p>"Pls make it...." Ya fada under his breath, kiran mufidane ya shigo wayan, da sauri yayi picking yana cewa</p><p>"Baby am so sorry I lied... Kiyi hakuri....pls don't be offended..." Ya fada mata in a whisper don kwantar mata da hankali,</p><p>"What can I say...kawai kullum sai...." Bata idaba ya katseta dacewa</p><p>"Baby ki yafemin....pls don't say anything OK..." Ya fada mata cikin sanyin muryan dayasan she can't resist,</p><p>"OK...yanzu kana ina?...." Ta tambayeshi, shuru yayi for a while sannan ya fada mata exactly abinda ke faruwa, cikin karfi hali tace</p><p>"To Allah ya bada saa...." Zai bude baki yayi magana yaji ta katse wayan. Murmushi kawai yayi.</p><p><br /></p><p>Achan family house duk cikan dayayi sabida yan taro bai hana Hajiya karama kebewa da Hajiya babba ba, bayan sun Shiga inda babu kowa, sai Hajiya karama ta fadawa Hajiya babba exactly abinda yazid ya fada mata, shuru tayi hawaye na taruwa idonta, </p><p>"Allah yasa kar dan yazo da rai....in yaso sai ya aureta batare da ansan exact abinda ya faru tsakaninsu ba...." Inji Hajiya babba, idanuwa Hajiya karama ta zaro </p><p>"Aa wallahi...Allah yasa yazo da rai...yo haka Allah ya kaddara....besides ni fa ban ga wani aibun abinda ya faru ba...ai duk Muslim na kwarai yasan kaddara...yazid dai ba dan iska bane balle ashe daman ya saba....kuma duk Wanda yaga yanda ya damu yasan ba halinshi bane...don haka ni dai wallahi yazo da rai koni da raineshi...." Ta fada in I don't care manner kuma she's serious,</p><p>"Wai ke ko kadan baki tunanin abinda mutane zasu ce?...." Inji Hajiya babba, shoulder ta daga </p><p>"Who cares....kowa na da nashi cockroach in thea cupboard...so kowa yaji da abinda ya dameshi...." Ta fada sannan ta dafa shoulder Hajiya babba da Duk ta susuce </p><p>"Anty ki kwantar da hankalinki.... In mace CE ba sai taje waje aure ba balle ayi mata surutu...cikin dangi zaayi mata miji...in kuma na mijine babu case don for as long as he's rich no body cares...." Yanda take magana yasa Hajiya babba dariya, dan hararanta tayi</p><p>"Wato ke har kin gama plan din komai...." Ta fada in a funny way,</p><p>"Yo me yafi raina..." Ta fada tana dariya.</p><p><br /></p><p> Bayan kaman minti ashirin suka isa hospital, hospital din is not that big but it is unique and beautiful, da sauri nurses din wurin suka amsheta deyeka doc ya sanar dasu, fita yayi daga cikin motan yq nufi motan da yazid ke ciki, shima yazid fitowa yayi ya nufoshi, </p><p>"Zaa bada deposite of 80k...in an gama kafin a sallameta zaa bada balance of 70k,...150k muke cs anan..." Inji doc, yana kiran 80k yazid ya fiddo wayanshi, few seconds later ya daga kai yana yace</p><p>"Pls I don't have cash on me...kuna amsan transfer?..." </p><p>"Yes...no problem..."</p><p>"OK...pls account number..." Inji yazid, nan take ya karanto Mashi ya saka</p><p>"Bank name pls..." Inji yazid, fada Mashi yayi, ko minti biyu baiyi ba yayi receiving alert na 170K, kallon shi doc yayi zaiyi magana yazid ya katseshi dacewa</p><p>"20k din na wanda nakeson ka duba min ne....that woman...." Ya fada yana ammi data rafka tagumi, </p><p>"OK..." Doc ya fada ya juya da sauri. Ciki ya shiga, kafin ya shiga har an shanzawa dija dake ihu kaya, nan take aka hau aiki.</p><p><br /></p><p>A waje kam ammi mikewa tayi don tasan bai kamata ace tana zaune nan dija ta haihu ba, magana tayi da yar uwarta kan su tsaya da dija. Ahankali ta zo ta wuce inda yazid ke tsaye, </p><p>"Ina zaki kuma?..." Ya bi bayanya yana tambayan ta,</p><p>"Gida...." Ta amsa Mashi atakaice, </p><p>"Dan Allah ki tsaya a dubaki..." Ya fada mata cikin sanyin murya, kai kawai ta girgiza sannan tace</p><p>"Aa...." </p><p>"To bari ya maidaki..." Ya fada yana juyawa, fadawa driver yayi a kaita inda ya dauko ta. </p><p><br /></p><p>Driver zuwa yayi da mota inda take tsaye ta bude ta shiga. Yazid kallon agogon hannunshi yayi yaga kusan 5:30, sai lokacin ya tuna baiyi sallan asr ba. Dan shiga cikin yayi yaga har lokacin doc bai fito ba, fita ya karayi yana tafiya yana tunani, har yaje bakin titi bai Sani ba saida wani mai mashin ya kusa bugeshi sannan ya dawo sense dinshi. </p><p><br /></p><p>Bayan thirty minutes ya dawo direct ciki ya shiga ya nufi reception, nan wacce ke nan ta nuna Mashi office din doc, jikinshi na rawa ya shiga ciki, kallon face din doc yayi ko zai iya understanding halin da ake ciki, murmushi ya sakarwa yazid tare dacewa</p><p>"Congratulations... It's a boy..."</p><p><br /></p><p>💜💙💚💛❤🧡</p><p><br /></p><p>Sweethearts kuyi hakuri am soooooo busy ne shiyasa kuke jina shuru. Sorry for waiting too long and pls don't forget to vote and comments.</p><p>[6/22, 5:53 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: 🧡💜💙💚💛❤</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙💚💛❤🧡</p><p><br /></p><p>®Zuwairat (ummumpls am)</p><p><br /></p><p>3⃣0⃣</p><p><br /></p><p> _Follow me on:_ </p><p><br /></p><p> *Wattpad @ummumaryam29* </p><p><br /></p><p> *Email:Zuwairat.nuhu@gmail.com* </p><p><br /></p><p> *IG: zuwairatummumaryam* </p><p><br /></p><p> *Website:Www.ummumaryam.com* </p><p><br /></p><p> *And also join my new Facebook group: Zuwairat ummumaryam and Zuwairat ummumaryam page.* </p><p><br /></p><p> *Snapchat: ummumaryan29*</p><p><br /></p><p>Baki yazid ya bude yana sucking maganar doc into his brain, ganin shuru yayi yawa yasa doc cewa</p><p>"Yes...its a boy..." Yafada yana kallon how still yazid is, ahankali yazid ya daga kai ya kalli doc</p><p>"Babyn lafiya lau?...I mean...lafiya dan yake?..." Yafada sounding out of word, </p><p>"Yes....he's alright..."</p><p>"Khadija fa?.." Ya tambayeshi still not believing his ears,</p><p>"Itama tana lafiya....sai dai..." Da sauri yazid ya zaro eyes dayaji saidai </p><p>"I want to ask you...pls ka fadamin gaskiya..." Inji doc,</p><p>"Ina son sanin relationship dake tsakaninka da wannan yarinyan..." Doc ya tambayeshi</p><p>"She's... My...wife....pls can I see the boy now?..." Ya fada don kar doc ya sake yi Mashi wannan tambayan,</p><p>"Eh ana cleaning dinshi ...babu kayan yaro amma daman muna ajiye wasu in case if emergency..."</p><p>",OK...." Yazid ya fada yana mikewa jikinshi har rawa yake.</p><p>"Pls sit...." Doc ya kara umartanshi, da sauri ya koma ya zauna kaman wani Mara wayau </p><p> "Pls wane dalili yasa ka bar pregnant gal haka?.... Indai kai mijinta ne as you proclaim... Don ni har yanzu bani da assurance da gaske kake...." Inji doc, yazid shuru yayi yana tunanin abinda zai fadawa doc don ko kadan bai iya fada Mashi gaskiyar alamarin,</p><p>"Guduwa tayi daga gida as a result of aljannu da suka shafeta....yau na ganta...." Yayi Mashi karya which is written all over his face don bai iya karya ba,</p><p>"OK..amma she will need a medical care..." </p><p>"OK...pls can she fly out of the country?..." Ya tambayeshi cikin ranshi yana aduan yace yes</p><p>"No bazata iya ba yanzu... Amma don't worry.... Wannan hospital is among the best in town...zamu bata dukkan kulawan da ya kamata...." </p><p>"OK...do...pls....can I see the baby now?..." Ya sake tambayanshi, mikewa doc yayi shima yazid ya mike, har doc ya kusa shiga dakin da jaririn yake sai yazid yace</p><p>"Pls tana nan dakin?..." Ya tambayeshi gabanshi na faduwa,</p><p>"No...tana postnatal... " doctor ya fada yana bude kofan dakin. Nurses biyu ne zaune sai gadajen newborn kaman ten, babu newborn sai na Yazid, doc na gaba har wajen gadon yaron, da sauri yazid ya tsaya gaban gadon yana kallon yaron ko kiftawa baiyi,</p><p>"Doc. He's tiny... Are you sure he's alright?..." Ya tambayeshi yana taba small cheek din yaron,</p><p>"Ai bakwaini ne...kuma from all indication the mother have not been feeding well.... Amma in yana samun kulawan daya kamata...he will group in no time...." Doc ya fada Mashi</p><p> Still yazid bai gamsu da maganar doc ba, dan daga white towel dake jikinshi yayi yana karewa tiny boy din kallo,</p><p>"Pls doc a kara dubashi....he don't look fit...banga ya motsa ba...." Ya fada yana shafa hair din yaron, cikin ranshi kam yana tunanin rabon wannan yaron ne yasa ya aikata abinda bai taba aikatawa ba</p><p>"Am assuring you...lafiyan yaron lau....kawai ka bashi few months ka gani..." Inji doc, ganin irin kallon da yazid ke wa yaron yasa shi daukan yaron</p><p>"Will you like to hold him?..." Inji doctor, ahankali yazid ya gyada Mashi kai tare da mika Mashi hannu, ahankali doc ta dora Mashi yaron dake motsi, yazid ji yayi kaman he's dreaming, wai yanzu wannan danshi ne. Kallon tiny legs din yaron yayi with excitement. </p><p>"Yanzu me dame suke bukata?...am new to the whole system..." Inji yazid, murmushi doc yayi</p><p>"First zaka kwantar da yaron....then kayo shopping baby wears...sai kayan shayi da matarka zatasha...sai ka fadawa masu kula dasu suzo...." Inji doc dake amsan yaron daga hannun yazid don dagani bai Iya rika yaro ba,</p><p>"Pls doc zan Iya samun nurse da zai dinga kula da both of them kafin su bar hospital?.... Zan biya..."_ya fada don ko kadan baison yan kauyensu ammi suce zasu kula da dija ko new boy dinshi.</p><p>" OK..." Zan nemo maka daya cikin nurses dina..." Inji doc daya mayar da yaron kan gado,</p><p> Bayan doc ya tabbatar yaron yayi balance ya juya yazid yabi bayanshi yana waigawa yana kallon yaron, har tuntube ya kusa yi saboda yanda yake waigawa, </p><p>"Doc why ba zaa kaishi inda take ba?../"</p><p>"Because tana bacci..." Doc ya amsa Mashi, ji yayi he needs this opportunity ya ganta koda na minti biyar ne don bazaiyi gangancin shiga dakin in idonta biyu ba.</p><p>"Can I see her?..." Ya tambayi doc,</p><p>"Yes....tana wancan dakin.." Ya nuna Mashi wani right handside door da aka rubuta mother resting, wucewa doc yayi office din shi shi Kuma yazid yaje bakin kofan. Da kyar ya samu courage din bude kofan, hangota yayi kwance, an rufeta da sky blue kyalle kaman yanda akewa yan operation, hands dinta biyu kan cikinta, ahankali ya shiga dakin bayan ya maida kofan ya rufe, bakin gadon ya isa yana kallon ta from head to toe, kallon how dirty her hair and feet is kawai yake, hmmm nace don ma tayi wanka yau kenan, face dinta ya kurawa ido yana tunanin how she survived for almost two months on the street with pregnancy. </p><p>"Am sorry... Daga yau baki kara shan wahalan rayuwa....I promise you that...." Ya fada in a whisper, kallon yanda kirjinta ya kara cika yayi as a result of ciki, gira daya ya daga ya juya ya bar dakin, yana fita yaga binto da yar uwar ammi, nan ya sanardasu ta haihu na miji kasancewan doc bai CE masu komai ba. Tsalle binto ta dingayi while ita matar bata nuna wata alaman murna ba, yazid ya ga the look on her face</p><p>"Ku kwantar da hankalinku...I won't let her face any of your stigmatizations...." Ya fada cikin ranshi yana dailing number Hajiya karama don ita kadai yake Iya fara fadawa. Bayan tayi picking ya sanar da ita, har da guda tayi saboda murna,</p><p>"Yanzu wake kula da ita?..." Shine tambayan da Hajiya karama tayi Mashi,</p><p>"Babu...amma nayiwa doc maganan ya samo min masu kula da ita kafin a sallameta insan abunyi...." Yazid ya amsa mata,</p><p>"Wane irin masu kula alhalin ga wayanda keyi mana nursing yara?... Zan turo daya gobe...." Inji Hajiya karama, </p><p>"Ai mom kafin goben dole a kula dasu....Kuma kinsan ba lallai bane dad ya amince da hakan...Kuma banason a sani da yawa...." Tsoki Hajiya karama taja,</p><p>"Naji a kawo mai kula dasu just for to night... First thing in the morning zan turo doc fatima,...sannan don't worry ba dole bane sai sun sani abinda ya faru...iyaka tayi aiki a biyata...." Ta amsa Mashi sharply, </p><p>"I love you mom...." Ya fadawa Hajiya karama saboda yanda take nuna damu a duk alamuranshi,</p><p>"Keep quite..." Tace Mashi, dariya yayi sannan yace</p><p>"Mom...pls banason khadija ta shayar dashi.. I possible ya sha baby formulars..."</p><p>"Why?..." Ta tambayeshi, shuru yayi for a while sannan yace</p><p>"Cos hakan zai zame mata more stress... I don't want her to waste any more time...I want her to go to school..." Ya fada yana jinginawa da wata bushiyar umbrella dake compound din hospital din.</p><p>"Hmmm kana ganin hakan ya kamata?... Kasan breastfeeding yana saka more shakuwa tsakanin da da uwa...." </p><p>"I know mom...amma I don't want her to go through that right now...she's too young for all this...." Yafada idanuwanshi lumshe,</p><p>"OK if you say so....sai a fara bashi ko sma gold 1 ne kafin ayi Mashi ordering na almarai nuralac...." Hajiya karama ta fada mashi, zai bude baki yayi magana tayi saurin katseshi dacewa</p><p>"Kai kyaleni inje in bada good news...." Tana kaiwa nan ta katse wayan. Murmushi kawai yayi sannan yayi dailing number Salem, same story ya bashi, shima ba karamin dadi yaji ba, he feels so excited har da cewa</p><p>"The latest dad in the world...." Inji Salem cikin zolaya</p><p>"Hmmm ka manta he's out of wedlock?..." Inji yazid cikin sanyin murya,</p><p>"Mudai wannan bai hanamu shashewa next week Saturday...." Inji Salem, hira suka dan taba sannan yazid ya je inda yayi sallan asar yayi na magrib,, bakin gate din hospital ya koma ya zauna yana jiran dawowan. Bayan kaman minti ashirin da zamanshi ya dawo da wasu mata guda biyu da alaman still family din dija ne, bayan ya ajiyesu shikuma ya shiga mota sukayi gaba. Gaban katuwar plaza suka tsaya da taimakon driver, dukda darene amma wurin kaman rana, bangaren baby wears suka hau bayan ya tambayi wani ya nuna masu wurin. Jugum yayi yana kallon kayan wurin ya rasa mai zai saya, kallon wasu mata dake siyayyan kaya yayi, </p><p>"Dan Allah Ku tayani zabar abubuwan da jariri zai bukata..." Ya fadawa Matan bayan yayi masu sallama sun amsa. Nan suka fara zaba Mashi kayan sawa Dana amfanin, har dasu bombom baby perfumes kala2. Gefe daya ya tsaya saida suka gama sannan ya kwace kayan da taimakon yan aikin wurin zuwa inda aka duba kayan. </p><p><br /></p><p>Komawa yayi inda ake sayarda kayan sawa nan ya dinga kwasan gowns not minding the amount da zaiyi costing, daga nan ya je bangaren, shoes ya dauki simple but expensive slippers guda biyar sai, yana tura kayan yaje inda mayuka suke, ya rasa Wanda zai saya mata amma yasan da makari mufida ke amfani and yayi mata kyau, hakan yasa shima ya dauki makari da sabulunta ya zuba cikin trolley da yake turawa, daga wannan sai perfumes da hair shampoo don har yanzu bai manta how silky and shiny kanta yake ranar da yayi molesting dinta ba. Yana turawa ya je wajen beverages da kayan malaki, katuwar nido da Ovaltine ya dauka gida bibbiyu sannan ya dinga sayan su juice da kayan dadi kaman ba gobe, sai wajen 9pm ya gama before then sultan ya kirashi don jin why basu dawo ba har yanzu sai yayi Mashi karya da hira yakesha inda yaje amma ya kusa dawowa.</p><p><br /></p><p>Bayan ya bada credit card dinshi aka zari kudin masu yawa sannan suka saka Mashi kayan a bayan booth suka koma hospital. Saida yaje wajen doc ya fada Mashi ya taimaka Mashi yayi jagora a kai kayan Kuma ya fada mata in ta farka dole tayi amfani da kayan, doc bai nemi jin dalilin hakan ba yasa masu gadi suka shigar da kayan har inda dija ke kwance su Kuma Matan da binto na zaune suna jiran farkawanta. Ajiye kayan akayi Matan suka bude baki suna kallon ikon rabbi.</p><p><br /></p><p>Doc komawa yayi ya shaidawa yazid an kai kayan, sai bayan nan yazid ya kara tambayanashi kan wacce zata kula dasu, sai doc ya shaida Mashi an samu daya daga cikin nurses dinshi da zatayi wannan aikin. Dadi sosai yaji ya kara shaida Mashi kan dan Allah kar a bari a jagwalgwala yaron doc ya bashi assurance kan hakan bazai faru ba. Hannu yazid ya mika Mashi sukayi sallama sannan ya mike ya fita cikin ranshi yana cewa</p><p>"Am taking responsibilities for my actions..."</p><p>Da sauri ya Kuma dawowa daya tuna maganar shayar da danshi. Nan ya fadawa doc abund yakeso ko gardama baiyi Mashi ba y amince da yayi hakan, sai lokacin ya fita har cikin ranshi yana son kara ganin face dinta amma haka ya hakura likewise yana son ganin danshi amma shi ko kadan baison ganin yanda yake dan Karami. Haka ya hakura ya fita daga cikin hospital din feeling so relaxed, ya mance rabon da yaji irin wannan farin cikin, ji yake kaman an dauke Mashi wani katon stone dake weighing dinshi down. Jefa kanshi yayi bayan mota yana murmushi with his eyes closed. Kafin su kai gidan was around ten, wanka yayi yaci abinci sosai sannan yayi salla ya kwanta bayan sunyi brief hira da sultan.</p><p><br /></p><p>Dija bata farka ba sai wajen 10pm lokacin matan na zaune, sai nurse da zata kula daita dake kicingide kan kujera ita kuma binto tana kwance nan kasa, lokacin doc na shirin tafiya gida. Tana bude ido taji cikinta empty da Sauri ta fara shafa cikinta don ta manta events daya faru, ganin Matan dake zaune sai ta tuna taga amminta, then...yazid....da Sauri ta widening idanuwanta data tuna taga yazid tare da amminta da binto, sai ta tuna mota ya bugeta, daga nan ta tuna ta farka in do much pain,</p><p> Then an saka ta a mota an taho daita, she remember she was screaming saboda azaba then an shiga daita wani daki da wasu mutane daga nan bata kara tuna komai ba, kara shafa cikinta tayi taji kaman bandage sannan ga zafe, idanuwa ta zaro</p><p>"Ina cikina!..." Ta fada kaman Mara hankali wanda ya maida hankalin mutanen wurin kanta, da sauri nurse din ta mike likewise yan uwan ammi duk sukayi kanta</p><p>"Ina cikina?....." Ta fada sounding more tensed sannan tana shirin kuka, d saurin nurse din tace</p><p>"An fidda maki....kin samu namiji...." Ta yi mata dalla2</p><p>"Na...mi...ji?...." Tafada tana zaro idanuwa,</p><p>"Eh namiji...." Ta amsa mata, su kam Matan tsaye sukayi suna kallon su,</p><p>"To yana ina?...." Ta tambayeta, </p><p>" zaa kawo maki shi...." Tafada sannan ta fita daga dakin, office din doc dake tartare kayanshi ta Shiga ta sanar dashi halin da ake ciki, da saurinshi ya fita zuwa dakin.</p><p><br /></p><p>"Ina...ammi...." Ta tambayi sisters din ammi,</p><p>"Tana gida...." Daya daga cikin su ta amsa mata, bude kofa akayi nurse da doc suka shiga, </p><p>"Da akwai inda ke maki ciwo?...." Ya tambayeta, ahankali ta girgiza kai tare dacewa</p><p>"Cikina ne kawai...ina dan?..." Ta tambayeshi, murmushi yayi</p><p>"Yanzu zaa kawo maki shi...kinji ko?..." Kai ta gyada Mashi, alama doc yayiwa nurse kan a dauko dan, nan ta fita few seconds later ta dawo rike da Dan, tana shigowa dakin dija tayi saurin mika Mata hannuwanta, Dora mata yaron tayi, saida ta kalleshi for almost two minutes sannan tace</p><p>"Wannan shine ke yawo a cikina?...."</p><p>[6/22, 5:53 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: 🧡💜💙💚💛❤</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙💚💛❤🧡</p><p><br /></p><p>®Zuwairat (ummumpls am)</p><p><br /></p><p>3⃣1⃣</p><p><br /></p><p> _Follow me on:_ </p><p><br /></p><p> *Wattpad @ummumaryam29* </p><p><br /></p><p> *Email:Zuwairat.nuhu@gmail.com* </p><p><br /></p><p> *IG: zuwairatummumaryam* </p><p><br /></p><p> *Website:Www.ummumaryam.com* </p><p><br /></p><p> *And also join my new Facebook group: Zuwairat ummumaryam and Zuwairat ummumaryam page.* </p><p><br /></p><p> *Snapchat: ummumaryan29*</p><p><br /></p><p> _Don't forget to vote oooo_</p><p><br /></p><p>Murmushi doc ya karayi tare da daga mata kai, kura mata ido yayi yaga yarinyace ta gidan karshe, mamakin ya akayi yazid ya Iya auren dija yayi sai Kuma yaga she so gorgeous, dan nurse ta amshi yaron zata kara fita dashi da sauri dija tace</p><p>"Ina zaki kaishi?..." Ta fada babu wasa,</p><p>"Kwantar dashi zaa..." Ya fada dukda ba haka yaso ba, da tunanin shi in ta farka sai a kai mata dan ta fara shayar dashi. Dan baki dija ta turo</p><p>"Baa barinshi nan?...." Ta tambayeshi, </p><p>"Kar ki damu zaa kula dashi...." Ya fada mata sannan ya fita. Nurse ce ta shigo ta dauki cup da warm water data tanada saboda ita ta hada mata very thick tea ta sha tana lumshe eyes saboda yanda take jin dadi tea din. Sai da ta gama ta bata drugs tasha sannan ta saka towel cikin warm water to goge mata jikinta duka dija sai kokarin rufe nakedness dinta kawai take, su kam yan uwan ammi jira suke first thing in the morning su koma gida don ko jaririn baa basu suka gani ba. Dija komawa tayi ta kwanta ko minti goma batayi ba bacci yayi gaba daita</p><p> For the very first time in two months datayi bacci like a baby, she feels so save and secure.</p><p><br /></p><p>A gidan su yazid kam bayan Hajiya karama ta fadawa Hajiya babba dija ta haihu, zama tayi bakina gado tare da yin tagumi, </p><p>"Abu kaman wasa ya zama gaskiya...har kullum ina fatan I should wake up from this dreadful dream...amma gaske ne...." Hajiya babba ta fada cikin sanyin murya, zama Hajiya karama tayi kusa daita</p><p>"Pls ki kwantar da hankalinki...abinda zai faru ya riga ya faru.....so kawai muyi planning ahead..." Hajiya karama tayi comforting dinta, </p><p>"Yanzu meye abunyi....nidai am confused...." Inji Hajiya babba, itama Hajiya karama shuru tayi kaman mai tunanin wani for almost 3 minutes</p><p> "Me zai hana yanzu tunda ta haihu alhaji yaje ya nema mashi aurenta....I think hakan zaifi sauki...." Inji Hajiya karama, </p><p>"Nima haka nakeso amma ai kin San halinshi....yana Iya cewa bai zuwa ko kuma yace anemo wani yaje shi bai zuwa...." Inji Hajiya babba,</p><p>"Ko dai mu gawa inna?..." Hajiya karama ta tambayeta, shuru Hajiya babba tayi for a moment sannan tace.</p><p>"Me zai hana a fara fada Mashi...in bai yarda ba sai mu fadawa Hajiya inna...." Mom ta fada mata, haka dan taba hira kadan sannan suka fita daga inda suke hiran.</p><p><br /></p><p>Itakam mufida wani empty daki ta koma ta kwanta kasa tana rolling tana kukan bkin ciki, run lokacin da sukayi waya da yazid take kuka, babu Wanda yasan halin da take ciki cos babu Wanda ya ganta sannan babu Wanda ya nemeta saboda yawan mutanen dake gidan. Tana nan kwance bacci y dauketa bayan taci kuka ta koshi, bat farka ba sai wajen karfe bakwai, ji tayi jikinta zafi rau sannan kanta zafi. Da kyar ta mike ta shiga bathroom ta dauko alwallah, tana salla tana hawaye, sai da ta Ida ta kara komawa sai rawan sanyi take kuma batason ta fita don da an ganta zaa gane something is wrong with her, tana nan kwance bacci ya kara daukanta. </p><p><br /></p><p>Sai wajen ten ta farka feeling worst than earlier, mikewa tayi ta taka ahankali zuwa bakin kofan ta bude taji babu hayaniya sosai da alaman mutane sun koma sai yan kadan, Vail dake kanta ta yafa har kusa face dinta don kar a gan how swollen face dinta yake. I ana fita tana takawa ahankali kaman Kazan da aka tsoma a ruwa had ta kusa shiga falo yayi daidai da fita Hajiya babba da Hajiya karama daga inda suka gama hiran su, kallon ta sukayi ita kuma ta sadda kai kasa </p><p>"Daughter daga ina kike?..." Hajiya karama ta tambayeta</p><p>"Ba...." Ji tayi zatayi kuka sai tayi shuru, da sauri Hajiya karama ta zo kusa da ita ta daga jaw dinta, nan swollen and red eyes dinta ya bayyana,</p><p>"Subhanallah!!..." Suka fada atare while mufida ta kara fashewa da kuka dukda voice dinta bai fita</p><p>"Haba daughter.... Haba daughter.... Meye matsalanki da bazaki fada mana ba?.... In yazid ne ai bai fi karfin mu ba....ji yanda yanda jikinki ke zafi...." Inji Hajiya karama dake rike da wrist dinta, </p><p>"Kiyi hakuri kinji....(komai yayi farko dole zaiyi karshe....nasan it's a trial time for this family amma ya muka Iya da ikon Rabbi... Dan Allah kiyi hakuri kinji...nasan duk mahakurci mawadaci ne...." Inji mom yazid, kai mufida ta dinga gyada mata duk sai tausayinta ya kamasu,</p><p>"Muje insa a hada maki ruwan wanka sai kici abinci kisha magani...." Inji Hajiya karama dake rike da hannunta. Babu gardama tabita part dinta.</p><p><br /></p><p>.abangaren grooms kam bakaramin party sukasha ba, duk sai murna kawai suke au zasu kwana manne da mace babu kaman Sharif da sai shan maganin man power kawai yake. Wajen nine friends dinsu suka raba Kansu gida biyu don raka angwaye gidanjensu.</p><p><br /></p><p>Ba karamin rashin m Sharif yayi wa yar amini dad dinshi ba don har da suma ta dingayi saboda azaban da takesha hannun sharif. Wanda yasa ta rantse babu abinda zai sata kara kwana wannan gidan.</p><p><br /></p><p>Shi kuma shahid was so nice and gentle da asiya(Asabe), ko kadan baison ganin hawayen ta cos ji yake this is the happiest moment of his life.</p><p><br /></p><p>The following day da wuri nurse ta hada warm water tayi wa yaro wanka ta shirya shi cikin expensive clothes da ubansa ya saya sannan ta bashi milk yasha ya koshi sannan ta kwantar dashi. Kayan sawan dija ta fiddo daya ta zuba Mashi perfumes sannan ta shiga bathroom ta hada ruwan wanka, har lokacin dija bata farka ba, saida ta gama fixing komai sannan ta tadata.</p><p><br /></p><p>Bayan ta fito daga wanka nurse ta shafa mata mai, ita dai dija bata gane abinda ke faruwa ba amma taga kulawan is too much, kuma ga gayan yan gayu tana gani kala2 cikin dakin. Bata musa mata ba ta amshi kayan ta saka, kanta nurse tayi combing sannan ta daura mata. Dija dai ko uffan batace ba amma she's enjoying the moment, saidata ta gama shiryata sannan ta hada mata tea ta amsa tasha ta bata magani tasha doc ya shigo around 8 ya bata injection sannan ta koma ta kwanta, ko tambayan dan batayi ba saboda dadi</p><p> Tana lumshe idanuwa sai ta tuna d binto da yan uwan ammi, </p><p>"Dan...Allah... Ina..su inna suke?..." Ta tambayi Matan sounding very cool,</p><p>"Sunje gida... Amma sunce zasu dawo...." Ta amsa mata, kwantawa tayi bata kara cewa komai ba, cikin ranta tana ganin Allah ne ya amshi aduan ta don kullm cewa take Allah ya kawo mai taimaka mata.</p><p><br /></p><p>Shima yazid daya kwanta ana trying number mufida bai samu ba baisan sanda bacci yayi gaba dashiba , he slept like a baby don wani irin nutsuwa yake ji tattare dashi. Bayan sallan asuba bai farka ba sai karfe 8: 20 shima ba don baccin ya isheshi ba sai don yayi deciding ya je Kano yau sannan ya wuce abuja, don jiya bayan ya kwanta yayi trying number mufida amma bata dagawa</p><p> Ganin 8:20 yasa yayi aurin mikewa tare da shiga bathroom, wanka yayi ya maida kayan daya cire don da kaya daya kawai yazo. Bayan ya shirya ya fito falon sultan, nan ya tarda shi yana calling yana lumshe eyes da gani da mace yake waya, yana ganin yazid ya neme excuse yayi hanging off sannan ya kalli yazid,</p><p>"Ya ustaz you are looking very bright... Meye sirrin ne...ko dai mata kake zuwa nema garin mu?..." Inji sultan cikin zolaya, murmushi kawai yazid yayi ya muka Mashi hannu suka gaisa sannan yace</p><p>"Ina son wucewa Kano ...kafin in koma abuja da yamma in Allah ya yarda..." Yazid ya fada Mashi, dan bata rai sultan yayi</p><p>"Baka bari mu koma abuja da yamma?..." </p><p>"No gaskiya...kasan jiya akayi wedding din siblings dina biyu....so I have to be there.. Duk da nayi missing daurin auren..." Yafada yana saka hands dinshi cikin aljihunshi, </p><p>"OK...amma muje kayi breakfast if not my mom will be mad...." Ya fada yana mikewa, yazid baice komai ba yabi bayanshi fuskanshi dauke da murmushi, kan dining suka zauna aka kawo masu ruwan tea da intestine pepper soup, nan yazid ya cika cikinshi sannan yayi masu sallama ya mike </p><p>"Ka tafi da mota daya mana..." Inji sultan dake biye dashi</p><p>"No don't worry... In naje kano zan dauki daya daga na gida..." </p><p>"OK let d driver drop you at the park...." Sultan yayi insisting, yazid bai kara cewa komai ba driver ya bude Mashi mota ya Shiga yayi waving sultan good bye yana cewa</p><p>"Allah ya sake kaddara haduwan mu...." </p><p>"Ameen ustaz..." Sultan ya fada da karfi yayin da motan ke driving out of the house.</p><p><br /></p><p>Hospital ya umarci driver yaje, babu musu yayi hanyan hospital. Around 9:30 su ka isa hospital. Direct office doc ya Shiga suka gaisa ya tambayi ya masu jiki doc ya amsa masu da suna na samun sauki, danshi ya bukata a kawo Mashi doc yasa akawo yaron. Nan yazid yayi Mashi huduba ya rada Mashi suna Mahmud sannan ya maida masu suka mayar dashi wajen kwamciyan shi. Mikewa yayi y mikawa doc hannu sukayi ban kwana kan zai dawo next weekend. Fita yayi har zai fita amma he needs to see her, komawa yayi bakin kofan inda take kwance, da kyar ya samu courage din bude kofan luckily tana bacci sai nurse dake zaune kan kujera, shiga yayi yana sniking kaman Mara gaskiya, nurse zata gaidashi ya daga mata hannu sannan ya nufi bakin gadon, kallon kayan jikinta yayi da kuma how peaceful she looks,</p><p>"Hmmm alhamdulillah...." Ya fada yana lumshe idanuwa, juyawa yayi ya kallo nurse din</p><p>"Pls sister take very good care of her...feed her very well...zan biyaki in na dawo next weekend...." Ya fada ahankali don kar ya tada ta daga bacci</p><p>"No problem sir...." Ta amsa Mashi . fita yayi ya shiga mota sai park, yana zuwa ya tarda golf sauran mutum uku ya cika, biya yayi suka kama hanyan Kano.</p><p><br /></p><p>Karfe biyu da yan mintina ya isa kofar gidansu. Direcct part din mom dinshi ya shiga ya tarda mom dinshi da Hajiya karama, sai wasu sisters din mom da dad, durkuswa yayi ya gaidasu suka amsa har da mom dinshi don kar ta nuna masu da akwai matsala. </p><p>"Wai ya akayi baka zo ba tun jiya?...." Inji wata yar dad</p><p>"Aikine....ya rikeni...." Yayi mata karya. Mikewa yayi ya shiga inda yasan zai tarda mufida, hangota yayi kwance tayi rubda ciki, ahankali ya maida kofan ya kulle sannan ya taka ahankali ya haye gadon, wuyanta ya fara kissing kaman mayuwanci nan ta firgita ta farka taga yazid, wani irin disgusting look ta watsa Mashi, murmushi yayi ya tallabo face dinta yana kallon yanda face dinta ya kumbura ga eyes dinta sun chanza kala,</p><p>"Babyna am sorry if I made you cry...ki yafemin...." Ya fada yana shafa hancinshi kan nata, fashewa tayi da kuka tana cewa</p><p>"I want my own baby...nima inason in haihu....pls made me pregnant... " ta fada cikin matsanacin kuka..." Lips dinshi ya Dora kan nata yana murmushi,</p><p>"Muje part dina...yau in Allah ya yarda zakiyi ciki...." Yafada sounding very naughty, kuka kawai take saboda bakin cikin how excited he looks, duk Wanda ya Gandhi yasan he's happy saboda dan shegen da aka Haifa mashi. In yau itace ta haihu Allah kadai yasan irin gatan da zata samu, kallon yanda yaje shishige mata jiki kawai take,</p><p>"Babyna....muje part dina.....muje ki bani wajen da ni kuma in ajiye maki ciki...." Yafada kaman ba shi ba, wani irin haushi ta kara ji</p><p>"Wai wajen da...." Tafada cikin ranta, tureshi ta farayi</p><p>"Stop it...." Kai ya girgiza mata yana unzipping wandonshi</p><p>"Baby zan baki....just open up..." Yafada jikinshi na rawa, ganin da gaske yake yasa ta turashi ta mike ta shige bathroom tare da kulle kofan. Yafi minti goma nan kwance sannan ya mike yaje bakin kofan</p><p>"Baby ki kawomin abinci part na...." Yafada mata yana Dora kai kan kofan, shuru yaji</p><p>"Kinji babu am seriously starving.... Ki kawomin kinji.. Am waiting...." Ya fada sannan ya gyara kayan jikinshi ya bude kofan ya fita ya koma part dinshi ya mike kan gado yana jiran zuwan mufida.</p><p> 💜🧡💙💚💚💛</p><p>Thanks for the love, pls don't to vote don it will make so happy.</p><p> </p><p><br /></p><p>Ina baran aduanku Allah ya yiwa wani kaninmu rasu, pls pray for him.</p><p><br /></p><p>Sannan ga masu shaawan shiga group dina, ga number wata sis dita duk mai so tayi mata magana zatayi adding dinku. Don har ga Allah abubuwan suna iyimin yawa ban Iya adding mutane da kaina</p><p><br /></p><p>09034060521.</p><p><br /></p><p>.kuma masu complaint kan rashin post da wuri ko rashin yawan page wallahi am a very busy person kawai writing is my person not because am jobless, pls Ku cigaba da hakuri da managing Wanda kuke samu. Thanks💋</p><p>[6/22, 5:54 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: 🧡💜💙💚💛❤</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙💚💛❤🧡</p><p>®Zuwairat (ummumaryam)</p><p>3⃣3⃣</p><p>_Follow me on:_</p><p>*Wattpad @ummumaryam29*</p><p>*Email:Zuwairat.nuhu@gmail.com*</p><p>*IG: zuwairatummumaryam*</p><p>*Website:Www.ummumaryam.com*</p><p>*And also join my new Facebook group: Zuwairat ummumaryam and Zuwairat ummumaryam page.*</p><p>*Snapchat: ummumaryan29*</p><p>*Pls ina bukatan aduan Ku, don Allah duk sanda kukayi ibada Ku tuna dani da dukkan alumman Muslim, ina da abinda nakeso pls Ku rokan min Allah. Don't forget me plsssss*</p><p>Salem na zaune gaba kusa da driver while su dad suna baya. Salem daukan wayanshi yayi, ji yake kaman ya kira yazid ya fada Mashi amma he can't saboda su dad. Text yayi Mashi kaman</p><p>" _Ango!.... Ango!!!..... Ango!!!...."_ ya tura Mashi, alokacin yazid dake zaune office yasha suit looking more breathtaking than ever, bai Dade da gama waya da mufida ba, sai yaji karan shigan message, da kaman yayi ignoring sai kuma ya dauki wayan ya bude message din, dariya ya farayi tana cewa</p><p>"Sarkin zolaya..." Ya fada tana dailing number Salem, ringing ya farayi daga chna bangaren Salem ya kashe bai dauka ba, ya kara yi Mashi text kaman</p><p>" _Ango kasha kamshi...angon mufida...da khadija...."_ ya tura Mashi, yazid dayaji bai dauka ba ya ajiye wayan sai kuma karan text, kara daukan wayanshi yayi yaga another message daga Salem</p><p>"Wai what is this guy up to ne?..." Ya tambayi kanshi yana dariya at the same time yana kara dailing number Salem, still bai dauka ba few seconds sai ga another message daga Salem yana cewa</p><p>"The latest ango in town..." Wannan Karin bai kirashi ba sai shima yayi Mashi text kaman haka</p><p>" _Wai yau meke yi maka dadi ne haka?...."_ yazid ya tura Mashi. Sai ga reply kaman haka</p><p>" _In nayi maka albishir mai dadi me zakayi min?..."_ dariya yazid yayi yana shafa well groomed beard dinshi</p><p>" _Me kake so?..."_ya tura Mashi</p><p>" _Kayi min alkawarin zaka shiga gaba wajen jawo hankalin Maryam gareni...."_Salem ya turo Mashi, dariya ya kara yi Wanda ya bayyana open teeth dinshi,</p><p>"Kasan kome nace zatayi...amma it depends on</p><p>[6/22, 5:55 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: 🧡💜💙💚💛❤</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙💚💛❤🧡</p><p><br /></p><p>®Zuwairat (ummumaryam)</p><p><br /></p><p>CONTINUE TO 33</p><p><br /></p><p>Sai karfe uku da rabi su dad suka isa kano. Gidan alhaji Yunusa suka bi suka ajiyeshi sannan suka wuce gidansu yazid dad ya shiga sannan driver ya wuce da Salem gidansu bayan dad ya gode Mashi. Bayan yayi freshen up su mom suna falo suna jiran ya gama cin abinci don they are earger to hear what he will say. Saida ya gama sannan ya dawo falo. Ya fara cewa</p><p>" alhamdulillah our visit was a success... Iyayen yarinyan are welcoming... Beside an daura masu aure...." Bai idaba Hajiya karama ta Dau</p><p>"Ayyirrrrrrrrr!!!!!..." Har saida dad ya dafa kunnenshi, Hajiya babba murmushin jin dadi tayi da abun yazo a saukake.</p><p>"Naji dadi wallahi....yanzu biki kawai ya rage?..." Hajiya babba ta fada.</p><p>"Yes...kawunta yace zai kirani in sun gama maganar ranar that is suitable to them...." Ya fada yana jinginawa ga kujrera,</p><p>"Kai yara maza sunyi wallahi...cikin few months mun samu surukai har hudu..." Inji Hajiya karama tana dariya, murmushi Hajiya babba tayi shi kuma dad kura mata ido yayi yana imagining yanda akayi bata sanin ta girma, don wani lokacin in tayi abu kaman yar yarinya,</p><p>"Yanzu dai mu fara hada lafe...." Hajiya karama tayi adding,</p><p>"No...shi zaiyi da kanshi...." Inji dad,</p><p>"Ya zaayi yayi da kanshi...ai wannan rashin adalci ne....." Tafada tana turo baki kaman yarinya,</p><p>"Meye na rashin adalci?... Ba anyi Mashi na farko ba?.... Anyway ai kina da kudi...kiyi Mashi mana..." Dad ya fada mata cikin harshness, zata bude baki tayi magana Hajiya babba tayi mata alaman tayi shuru da ido.</p><p>Saida suka fita Hajiya karama ta fara cewa</p><p>"Anty gaskiya a zama dole mu taimaka Mashi...sabida nasan shi zaiyi kayan daki da komai tunda parent din yarinya are not buoyant..." Tafada lokacin da suke shiga part din Hajiya babba,</p><p>"To shikenan...sai mu kira a hada mana exactly irin wanda aka hadawa su Sharif...in yaso in yana da interest din kara wani abu sai a kara..." Inji Hajiya babba, dariya Hajiya karama tayi tana cewa</p><p>"Thank you antyna...." Itama dariya tayi sannan tace</p><p>"Babu wani thank you...ai 50 50 zamuyi wajen biyan kudin tunda yace bai badawa...." Inji mom</p><p>"Wannan babu case...." Hajiya karama ta fada tana zama kan kujera, kallon ta Hajiya babba tayi tana tunanin Allah ya bawa Matan kishiya irin Nata don tana jin dadin yanda take nunawa yaran tamkar ita ta haifesu mussaman yazid.</p><p>Da sauri hajia karama ta dauki wayanta ta kira Wanda ya hada lefensu shahid ta shaida Mashi suna bukatan exactly irin wannan.</p><p>Har yazid ya tashi yana expecting call din dad sannan yana tunanin abinda zai fadawa mufida. Gani yayi karfe biyar dad baice Mashi komai ba, kiran Salem yayi ya kara tabbatar da abinda ya fada Mashi. Sannan ya kira dad. Bayan sun gama gaisawa yace</p><p>"Dad...yau kaje factory ko?..how is it going?..." Ya tambayeshi, dad murmushi yayi</p><p>"This boy think he's smart...am your father..." Ya fada cikin ranshi saboda yasan already Salem ya fada Mashi abinda akayi</p><p>"Very fine..." Dad ya amsa Mashi,</p><p>"OK...bye... "</p><p>"Alright..." Dad ya fada sannan ya katse wayan shi.</p><p>Yazid zama yayi ya rasa abinda ke yi Mashi dadi don he wants to hear the word from dad don yaje Kano for the house preparation don yasan basu da halin yi mata komai kuma baison asan shi yayi komai mussaman mufida. Kuma ko suna da halin yi mata vaison wahalar dasu don he wants to show them.he really appreciate., bayan sallan ishai dad bai CE Mashi kala ba, kawai sai yayi deciding gobe zaije Kano amma bai barin su San yana Kano sannan ko mufida bata Sani yana Kano cos yau taje family house dinsu don haka zai sauka a gidanshi yasa ayi furnishing part din da dija zata zauna.</p><p>A chan Jos bayan kawu nanu yaci yasha bai fadawa kowa abinda ke tafe dashi ba sai bayan sallan ishai. Kiran ammi yayi da sauran manyan gidan. Sannan ya fiddo dubu darin da aka bashi na sadakin dija ya ajiye, dukkansu kallon juna suka farayi</p><p>"Na meye wannan?..." Wani dan uwan ammi ya tambayeshi,</p><p>"Wannan sadakin dija ne..." Da sauri ammi ta kalleshi,</p><p>"Ban ganeba..." Ammi ta tambayeshi</p><p>"Eh wannan mutumin dayayi mata ciki.. Iyayensa sukazo da maganar dansu zai aureta...ni kuma na basu don nasan hakan yafi daidai....kuma nan take aka daura masu aure....ko banyi daidaiba?.." Yafada yana mazurai, ajiyan zuciya ammi ta saki amma bata bari kowa yaji ba,</p><p>"Nace ko banyi daidai ba...." Ya fada yana kallon faces dinsu domin ganin reactions dinsu,</p><p>"Haba kai kam kayi daidai...daman in bashi din ba was zai aureta?... Kayi daidai wallahi...Allah ya saka maka da alkhairi..." Inii dan uwan ammi, ita kuma ammi tace</p><p>"Mun gode...."</p><p>"Meye na godiya?... Ba yata bace?... " yafada cike da haushin ammi don tunda taki amince Mashi ya tsaneta.</p><p>"Yanzu Sunce mu yanke hukuncin yaushe zaayi shagalin bikin?..." Inji kawu nanu, cikin nutsuwa ammi tace</p><p>"Ni in a tunanina ne ba sai anyi wani bikiba..kawai in an sallameta daga asibiti a wuce daita gidanta...ko ya kuka gani?..." Tafada kanta kasa,</p><p>"Daman su suka fadamin an fidda namiji daga cikin ta..." Inji kawu nanu,</p><p>"Gaskiya hakan ma yafi...Don in akace zaayi biki tamkar wani bacin sunanne don ga jariri ga biki...gwara kawai daga chan asibiti a wuce daita kawai...tayi abun kunya sai taje chan taji da shi...." Inji danuwan ammi, abban ammi nodding kawai yayi with acceptance</p><p>"Hakan yayi daidai..." Kawu nanu ya fada, complimentary card da dad ya bashi ya fiddo yana cewa</p><p>"To Ku bari in kira uban yaron gabanku don na fada Mashi zan shaida Mashi duk yanda akayi yafada yana saka daya daga cikin digits din dad dake jikin card din. Bayan ya gama sakawa cikin the oldest phone on earth yayi dailing number ya kanga da kunnenshi. Lokacin dad na zaune tsakiyan matanshi, Hajiya karama na rike da plate of watermelon yana dauka daga cikin plate, kiran wayan ya katse silent dake dakin, picking yayi tare da sallama, daga chan bangaren kawu nanu ya amsa tare da tuna Mashi ko shi waye sannan ya fara cewa</p><p>"Alhaji na isa Jos kuma na fada masu komai har da maganar bikin... Amma sunce kawai zasu so a dauketa daga asibiti a kaita dakinta...amma ban San ko hakan zaiyi maku ba.. " inji kawu nanu, dariya dad yayi</p><p>"Ai babu matsala....hakan ma yayi...." Yafada sounding excited,</p><p>"To alhamdulillah tunda hakan yayi maku...." Kawu nanu ya fada Mashi. Sannan ya katse wayan.</p><p>💙💚💛❤💙💜🖤💜💙💚❤💙💜💜Bayan dad ya gama waya ya fadawa su mom yanda sukace, mom ji tayi jikimta yayi sanyi''</p><p>"Wato abandoning dinta zasuyi kenan...basu damu ayi bikinta ko su San wa zata aura ba...kome ya sameta they don't care where she goes..." Mom ta fada cikin sanyin murya,</p><p>"Ai duk danku ne ya ja mata... " inji dad,</p><p>"Wahalanta will be over soon...duk Sai sunce inama yarsu akayiwa fyaden...yan iska kawai..." Tsoki dad yaja saboda maganar Hajiya karama.</p><p>Around 9:30pm yazid na kwance cikin blanket yana waya da mufida dajin muryanshi his moody Sai yaji kaman ana kiranshi, yana dubawa yaga dad da sauri yayi excusing mufida yayi picking, nan dad ya fada Mashi ya zo Kano gobe, da sauri ya amsa da OK, zai bude baki yayi magana dad ya katse wayan.</p><p>Tsalle ya farayi kan gadon saboda farin ciki, he can't still believe sweet khadija is his personal property, yana tuna mufida Sai jikinshi yayi sanyi, ahankali ya koma ya zauna tare da sake dailing number ta, bayan tayi picking tace.</p><p>"Baby har kun gama?..."</p><p>"Yes..." Ya fada cikin sanyin murya</p><p>"Baby ya akayi naji voice dinka yq Chan za... What's wrong..." Ta tambayeshi muryanta na rawa kaman zatayi kuka.</p><p>"Nima ban Sani ba baby.....kawai dad yace in zo Kano gobe..." Yafada kaman baisan abinda ke faruwa,</p><p>"Inna lillahi....to me ya faru?... Hope it's not something bad?../" ta tambayeshi cikin tashin hankali, murmushi yayi yana biting bottom lip dinshi sannan yace</p><p>"Baby bai fada min ba...pls baby muyi salla Allah yasa it's not something bad... Pls...." Yafada muryanshi na rawa</p><p>"OK baby...ka tadani da karfe daya...let's pray...insha Allah ko meye zai zama alkhairi..."</p><p>"OK sweetheart... I love you more than milk and honey...."</p><p>"Love you too..." Hira suka danyi amma yazid was sounding so worrying kaman baisan abinda ke wakana ba. Suna gama waya ya mike ya shiga bathroom ya dauro alwalla ya saka jallabiya ya fara salla yana godewa Allah daya bashi dija sannan yana rokan Allah yayi cooling zuciyan mufida kan abinda zai fada mata gobe.</p><p>The following day run six ya kama hanyan Kano bayan ya fadawa ogansu yana da emergency a gidansu. Karfe 9 saura ya isa Kano, first wannan dan uwan nasu mai saida furnitures ya kira kan su hadu a wearhouse dinshi. Karfe 10 saura suka hadu inda gayen ya fara gwada Mashi different design na kayan daki da pics na modern parlours tare da prices dinsu. Nan yazid ya zabi kayan falo da na bedrooms Wanda nan take ya kashe millions har 3.</p><p>"Yanzu tunda da akwai su kasa ana Iya fara sawa yau?...." Yazid ya tambayeshi Sai zufa yake,</p><p>"Why not...yanzu muje ka nunamin gidan sannan ka bani keys to the apartment..." Inji gayen,</p><p>"To zuwa yaushe zaa Iya gamawa?..."</p><p>"Gobe zuwa da rana komai ya kammala...tunda babu abinda zaa jira duk da akwai abubuwan da nake bukata..."</p><p>"OK then...yanzu muje dad na jirana..." Yazid ya fada yana fita daga wearhouse din. Mota ya shiga shima mutumin ya shiga nashi suka kama hanyan gidanshi.</p><p>Abangaren dija wace gari wajen karfe 9 bayan tayi wanka an bata abinci taci ta saka long Arabian gown tana zaune tana jin wani irin dadi cikin system dinta taji an bude kofa, ammi ta gani, da sauri tazo mikewa nurse ta dakatar daita. Bayan ammi taga kawu nanu, sunkuyar da kanta kasa tayi. Bakin gadon da take zaune ammi ta zauna tare da rike mata hannu, gaida kawu nanu tayi ya amsa kaman batayi laifi ba. Bayan yan magana da kawu nanu yayi wanda bata San inda ya dosa ba Sai gani tayi ya saka hannu cikin aljihunshi ya fiddo kudi</p><p>"Gashi sadakin ki ne..." Ya fada yana mika mata kudin, kallon ammi tayi ta kalli kawu nanu</p><p>"Ki amsa mana..." Ya daka mata tsawa, da sauri ta amshi kudin,</p><p>"To dija Allah ya kaddara saduwan mu...nidai nayi Iya nawa...inkinje ki bi mijinki sau da kafa...ban da gardama..." Ya fada mata, baki ta bude tana kallon shi cos she trying to take in abind yake cewa, tasan sadaki Nada alaka da aure, suna nufin tayi aure ne ko yaya,</p><p>"Ni na tafi...." Taji kawu nanu yafada, n</p><p>The next thing he's out of the room. Ahankali ta daga kai ta kalli ammi</p><p>"Ammi wannan kudin na waye..." Ta tambayeta cikin sanyin murya</p><p>"Naki ne dija...kawunki ya aurar dake..." Dan squeezing fuska tayi</p><p>"Ai ammi baayi biki ba..." Tafada cike da yarinta, murmushi karfin hali ammi tayi</p><p>"Ai ba Sai anyi ba...nidai dija hakuri zan baki...bani da halin yi maki komai....kuma in nace a saka bikin zuwa wani lokacin bakin mutane ma isanki zaiyi...hakan yasa nace da an sallameki a wuce dake dakinki..." Ammi ta fada cikin sanyin murya, hawaye ne ya taru a idanuwanta,</p><p>"Ammi dan Allah kar a tafi dani wani wajen...wurinki nakeson zama...ammi dan Allah kiyi hakuri... Dan Allah ammi ki barni wajenki..." Ta fada tana fashewa da kuka, itama ammi hawaye ta farayi tana cewa</p><p>"Kiyi hakuri dija...duk abinda nake saboda ban son ana sangwamanki.. Kije chan in Allah ya yarda bazakiyi Dana Sani ba don na lura yana sonki...." Cikin kuka dija tace</p><p>"Waye?.." Ammi bata amsa mata ba ta mike,</p><p>"Tafiya zanyi dija.. Dan Allah kibi mijinki...duk abinda yace kiyi kiyi...in yace ki bari ki bari...Allah yayi maki albarka...nasan haka Allah ya kaddara maki..." Da sauri dija ta mike ta kama hnnun ammi</p><p>"Dan Allah ammi kar ki barni...to ammi ki amshi kudin...banason su...ki tafi dasu...ammi dan Allah ki tsaya" Tafada cikin matsanacin kuka, cikin kuka ammi ta zame hannunta, ammi na tafiya dija na biye daita tana kuka tana kiranta, nurse CE ta riketa tare da mayar daita kan gado, dija kwantawa tayi tana kuka, few seconds later tayi shuru tana tuna hiran da sukayi da wasu friends dinta kan in mace tayi aure namiji na saka mata joystick, kara fashewa tayi da kuka tare da dora hannu bisa kai, har lokacin ko kadan batayi tunanin yazid ne ba, kawai gani take an badata sadaka saboda abinda ta aikata.</p><p>[6/22, 5:56 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: 🧡💜💙💚💛❤</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙💚💛❤🧡</p><p><br /></p><p>®Zuwairat (ummumpls am)</p><p><br /></p><p>3⃣4⃣</p><p><br /></p><p> _Follow me on:_ </p><p><br /></p><p> *Wattpad @ummumaryam29* </p><p><br /></p><p> *Email:Zuwairat.nuhu@gmail.com* </p><p><br /></p><p> *IG: zuwairatummumaryam* </p><p><br /></p><p> *Website:Www.ummumaryam.com* </p><p><br /></p><p> *And also join my new Facebook group: Zuwairat ummumaryam and Zuwairat ummumaryam page.* </p><p><br /></p><p> *Snapchat: ummumaryan29*</p><p><br /></p><p> _Sweethearts ina me yi maku happy Ramadan in advance, Allah ya amshi duk ibadun da zamuyi._ </p><p><br /></p><p> *In har my novels make you happy and keeps you entertained then pls repay me with your prayers, dan Allah kar Ku manta dani😥* </p><p><br /></p><p> *Don't forget to vote and comments*</p><p><br /></p><p>Kuka kawai take tana tunanin irin rayuwan da zatayi inda zaa kaita, kullum adua take ta koma gida don ta dinga yiwa ammi dukkan house chores don da tana yi mata gardama in ta sata aiki kaman wanke2 da sauransu amma yanzu she wants to do everything for her amma gashi bata kara samun daman ba. Kara volume din kukan ta tayi nurse dake zaune tana kallon ta sannan tana wondering abinda ke faruwa ta mike tazo inda dija ke zaune bakin gadon ta maida legs dinta kan gado tana cewa</p><p>"Ki bar kukan haka nan...kin San baki da lafiya...yi shuru kinji?...." Ta fada mata, dija kara fashewa tayi da kuka tana cewa</p><p>"Dan Allah ki kirawo ammi ta tafi dani gida....banason aure....." Tafada cikin matsanacin kuka, shoulder dinta nurse ta dafa still confused tace</p><p>"Kiyi hakuri kinji...baayiwa iyaye gardama...ki dauki kaddara...goge hawayenki..." Ta fada mata, ahankali dija ta sa bayan hannunta tagoge face dinta tana kallon kudin dake hannunta,</p><p>"To dan Allah ki karata ta amshi kudin...wallahi banason kudin...." Tafada new tears na rolling, still rarrashinta nurse ta dingayi har bacci ya dauketa.</p><p> Tana bacci tana sauke ajiyan zuciya.</p><p><br /></p><p>Abangaren yazid kam sai karfe 12 ya iso gidansu bayan ya bawa danuwansu keys to part din dija. Yana parking ya nufi part din dad dinshi, sai sauri yake don yasan he's around.</p><p><br /></p><p>Da sallama ya shiga dad ya amsa Mashi, zama yayi gefe daya ya gaida dad ya amsa in a Normal tune, bayan kamn minti biyu dad ya fara cewa</p><p>"Daman abinda yasa na kiraka shine sabida wannan yarinyan....munje gidansu da taimakon abokinka Salem....kuma alhamdulillah kawunta ya baka inda ya nemi a daura maku aure..." Idanuwa yazid ya lumshe hearing it from his dad makes it official</p><p>"So an daura maku aure..." Dad ya fada yana gyara zamanshi</p><p>"Kuma kawunta ya shaida min zai fada min lokacin daya kamata ayi bikin in yaje jos...jiya da dare ya kirani ya fadamin sun yanke hukuncin ba sai an yi wata shagalin biki ba...kawai sunce in an sallameta daga hospital an daukota...kaji yanda mukayi..." Yazid da kanshi ke kasa yana sauke ajiyan zuciya ahankali ya sake lumshe eyes dayaji ance from hospital a wuce da dija gidanshi, he never sees that coming, </p><p>"Thanks dad...." Yafada cikin sanyin murya,</p><p>"Don't thank me..." Dad ya katse shi sannan yacigaba dacewa</p><p>"Yazid!..." Dad ya kirashi, </p><p>"Naam..." Ya amsa Mashi tare da daga kanshi ya kalleshi for just few seconds ya kara sadda kanshi kasa,</p><p>"Mata biyu is not a joke....ka zama mai adalci...kar ka shiga hakkin kowa for any reason in the world...ka rike gidanka da adua...make them each others friend not enemies... Don't make them jealous... Make each and every one of them feel like and angel...banda son kai... Kar kace tunda wannan is not educated ko tunda yar kauyece ka shiga hakkinta wallahi the unjust shall never go unpunished.... Kana jina?..." Dad ya tambayeshi sounding very serious than ever, ahankali yazid yayi nodding, </p><p>"Remember all I have said and you shall have a peaceful home...ai kana ganin tunda kake baka taba ganin ko jin hayaniyyan iyayenka mata ba...to that's the secret... Nasan at times zakaji daya tafi kwanta maka ka daya amma never try to show it in public... Kawai ka nuna mata how much you love her when you are alone... Kadaiji ko?..." Dad yafada yana rike kunneshi don ya shaidawa yazid he's damn serious</p><p>"Yes dad...nagode... I will try any human in yi adalci a tsakaninsu..." Yafada kanshi kasa,</p><p>"That's very good...yanzu yaushe zaa daukota?..." </p><p>"I think Saturday..." </p><p>"OK...about the boy...inason a raineshi gidan inna...ko kanason Ku zauna tare?...." Dad ya tambayeshi, da Sauri yazid ya girgiza kai yana mai jin dadin abun.</p><p>"Good...jiya mommies dinka sunce doc Zara zata dinga kula da yaron har ya fita daga neonate stage..." </p><p>"Mahmud... Sunanshi Mahmud..." Yafada cikin sanyin murya.</p><p>"That's good...nice name...sai ka dauki rago biyu daga gona a yanka ranar asabar...." </p><p>"OK dad...nagode...." Yafada sounding very happy. Mikewa yayi ya fita daga wurin dad ya bi bayanshi da kallo yana murmushi. Part din mom dinshi ya nufa wayanshi ya fara ringing, jin ringing din yasa shi sanin cewa mufidace, murmushi yayi tare da picking call sannan ya sanyanya voice dinshi tare dacewa.</p><p>"My baby..." </p><p>"Yes babyna...baka iso bane?..." </p><p>"Na iso...yanzu na baro wajen dad..." Ya fada cikin sanyin murya</p><p>"Shine ko ka Karina ka fadamin kazo..." </p><p>"Sorry my love.... I wanted to surprise you ne..." Yafada muryan shi bai fita sosai,</p><p>"Baby wani abu?... muryanka kaman kayi kuka..." Murmushi yayi ya kara kashe murya</p><p>"Am OK...bari in wanka sai inzo in daukoki..." Yafada sounding very dull.</p><p>"Pls baby kana tada min hankali... Me dad ya fada maka?..." Tafada kaman zatyi kuka,</p><p>"Ki kwantar da hankalinki...in na daukoki ko me ke nan zakiji..." Ya shaida Mata, </p><p>"Me zan ajiye maka?...</p><p>" don't worry babyna....sai nazo... " tafada ahankali sannan ya katse wayan. Dariya yayi yana cewa</p><p>"At least bazaki ga laifina sosai ba..." Fada yana bude kofan part din mom dinshi.</p><p><br /></p><p>Da Sauri Hajiya karama ta mike tana cewa</p><p>"Ga ango...ango...ayirrr...ka kagi ubanka...." Tafada sounding so excited, mom dinshi dariya tayi tare da girgiza kai shi kuma yazid rufe face yayi kaman mace wai kunya yakeji, su Maryam baki suka bude </p><p>"Wai me akayi?..." Yusra ta tambayi small mom</p><p>"Yayan Ku aure ya karayi..." </p><p>"Aure!!!!...." Suka fada in chorus, tsalle su marzuq da ameera suka farayi while Maryam tace</p><p>"Gaskiya ni banso akayiwa Anty mufida kishiya ba..." Dakuwa Hajiya karama tayi mata tana cewa</p><p>"Kinci ubanki....Ku tashi Ku bamu waje dan ubanku...."</p><p> Ta daka masu tsawa, da Sauri duk suka mike har dasu ameera suka bar wajen. Kama hannun yazid tayi ta zaunar dashi tana cewa</p><p>Munafiki...ko kunyar me yakeji?..." Tafada tana dariya, durkusawa yayi ya gaidasu suka amsa mom dinshi sai murmushi kawai take.</p><p>"Mun hada maka lefe..." Hajjiya karama ta shaida Mashi, da Sauri ya kara durkusawa yana gode masu, </p><p>"Dalla koma ka zauna...sai wani abu kake kaman matsiyaci..." Dariya yayi ya koma ya zauna. </p><p>"Mun yanke hukunci zaa kai masu lefen don su San yarsu ba gidan matsiyata zata ba...sannan daga nan zaa taho da yaron...." Inji Hajiya karama, murmushi yayi tare da cewa</p><p>"Nagode mom...." "Taso ka gan kayan..." Ta fada Mashi, mikewa yayi ya kama mata hannu suka shiga inda kayan suke, dukawa yazid yayi ya fara budewa face dinshi dauke da annashuwa,</p><p>"Mom thank you...kawai damuwata shine mufida..." Ya fada cikin sanyin murya, daure fuska tayi </p><p>"What about her?..."</p><p>"Mom bansan yanda zan fda mata ba...." Tsoki hajjya karama taja </p><p>"Tsoronta kake jine?.... Nifa banson wacce zata tada maka hankali....in har she can't sai ka sallameta...ai ba hqrqmun bane mata biyu...kuma ba kanta farau ba...." Turo baki yazid yayi</p><p>"Mom I love her...kawai zan rarrashet until she comes to term...." Yafada sounding very dull,</p><p>"Your problem..." Tafda sannan ta barshi nan zaune yana duba two sets of bag wayanda ke cike da kayan kala2.</p><p><br /></p><p>Bayan ya gama ya koma falo yaci abinci sannan yaje part dinshi ya watsa ruwa yayi sallah sannan ya shirya ya kama hanyan gidansu mufida, yana tafiya yana waya da doc din dake kula da dija. </p><p><br /></p><p>Yana isa kofar gidansu mufida yayi wearing worried face ya shiga da sallama , da gudu ta fada jikinshi, cos mum dinta bata falo, face dinta ya tallabo ya kura mata ido while itama tana inspecting face dinshi,</p><p>"Baby...." Bata idaba ya kama bakinta ya fara sucking kaman he's life depends on it, saida yaga she's becoming breathless sannan ya saki bakinta yana cewa </p><p>"Baby I love you so much..." Yafda in a whisper, itadai ji take babu dadi</p><p>"Baby I can feel something is wrong...pls ka fadamin..." Tafada hands dinta kan cheek dinshi sai kallon face dinshi take kamam yau ta fara ganin shi, murmushi yayi kaman baiso</p><p>"Baby ina mumcy...." Ya tambayeta</p><p>"Bata nan...pls baby ka fadamin abinda ke faruwa...." Ta fada kaman zatayi kuka,</p><p>"Baby ki shirya mu tafi gida...zan fada maki komai...." </p><p>"Mom bata nan....kajira tazo sai mu tafi...." Tafada tana hugging dinshi,</p><p>"Baby pls mu tafi...in yaso ina Iya maidoki later da yamma in kina so...I really need to talk to you..." Yafada yana zamewa daga jikinta.</p><p>"OK then...bari in chanza kaya..." Tafada tana juyawa, da Sauri ya rike mata hannu</p><p>"No....just kiyi covering kanki ki taho mu tafi...." </p><p>"OK..." Kawai ta fada tayi hanyan upstairs, few minutes later ta sauko da Dan karamin Vail, rike mata hannu yayi suka is a baki mota ya bude Mata ta shiga sannan ya rufe shima ya shiga yana tunanin yanda mutane ke cewa kayan fadin kishiya . Baisan abinda zai saya mata ba.</p><p><br /></p><p>In silence suka driving zuwa gidansu</p><p>"Wai baby why bazamu je gidan mu ba?...nifa kunyan gidan nan nakeji...remember abinda inna tayi?..."</p><p>"Kinsan gidan nan is closer to your house...kuma kinsan hold up .." Ya fada Yana parking, fitowa tayi ta shiga part dinsu Hajiya babba ta gaidasu, kallon ta mom tayi tana imagining yanda zataji don she remembered perfectly yanda ta kusa hauka lokacin da dad zaiyi mata kishiya. Zama tayi har saida yazid ya kira ta a waya sannan ta tashi ta koma part dinshi, tana zuwa ya dauketa sai bedroom, satisfying dinsu yayi don yana tunanin in har ya fada mata halin da ake ciki sai sun kwana biyu bata bashi hadin kai ba, bayan sun gama ta fito daga bathroom daure da towel, ya mika mata hannu ta fada jikinshi, yana kissing wuyanta yana cewa</p><p>"Baby kin dai San cewa I live you ko?...." Yafada cikin whisper, ahankali ta gyada Mashi kai tare da daga kanta tayi Mashi kiss a baki</p><p>"Kuma kin San babu abinda zai cire position dinki a zuciyata..." Ya sake rada mata cikin kunne,</p><p>"Yes baby...what is the problem?..." Ta tambayeshi tana kallon eye balls dinshi, </p><p>"Baby I want you to know komai rubuce yake....we can't stop destiny...." </p><p>"Dan Allah ka fadamin abinda ke faruwa.. " tafada tana gyara daurin towel dinta, ajiyan zuciya ya saki ya rike palms dinta cikin nashi yana massaging sannan ya fara fada mata exactly abinda ya faru amma banda nuna farin cikin shi, aikam kura Mashi ido tayi sai hawaye sharrrr, </p><p>"Na shiga uku...." Tafada tana Dora hannunta kanta, da Sauri yazid ya rike mata hannu</p><p>"Pls baby stop it...." Yafada yana kokarin jawota jikinshi, tureshi tayi ta kara fashewa da sabon kuka,</p><p>"Wayyo ni mufida....ban kaunar kishiya....ban Iya zama da kishiya...wallahi banason sharing dinka da kowa....I love you..." Tafada cikin matsanacin kuka tana kokarin mikewa daga kan gadon, riketa yayi ya marairace fuska</p><p>"Baby pls stop saying such....kinsan ban iyawa su dad gardama..." Da Sauri ta katse shi dacewa</p><p>"Kai fuska biyu gareka....you are pretending kaman bakaso...alhalin nasan you are so happy... Nidai kawai ka sake...." Bai bari ta idaba ya kwantar daita kan kirjinshi, yana shafa kanta yana cewa</p><p>"Pls don't say such word....you are the best thing that ever happened to.me...kuma khadija is just a small gal...she will follow our training... Ki kwantar da hankalinki pls...." Yafada yana shafa kanta, amma the more he talks the more she cries, </p><p>"Baby pls ka sakeni...kishiya bata karama...." Tafada cikin kuka sosai, kawai sai dariya ta kufce Mashi don sai ya tuna maganar Malam Kabir gombe, wai kishiya bata karama</p><p>"Baby ki bari ki gani...naki sister karama CE...mu zamuyi training dinta...kawai pls just try and take her like the sister you never had....pls kiyi min wannan indai kinasona da gaske...." Yfada yana share mata hawaye, </p><p>",ni tsoro nakeji... Kar a rabani dakai...yan kauye suna da asiri...." Tafada gwanin ban tausayi</p><p>"No dear... Kawai just have faith.. Pls baby kiyi hakuri..</p><p> " lafewa tayi jikinshi tana kuka sosai, sai share duk hawayen daya zubo yake, hannunta biyu ta zagaye waist dinshi ta rike shi gam </p><p>"Dan Allah baby ki bar kuka haka nan....I promise zamanku zaiyi dadi....I will never do anything to hurt you...." Tafada ahankali, daga kanta tayi tana kallon shi da red eyes dinta</p><p>"Baby banason Sharing dinka da kowa....I love You so much that seeing entering another woman's part will hurt me badly.... Pls ." kuka yaci karfinta, kara danne kanta da naked chest dinshi yayi yana mata maganar cikin kunne,</p><p>"Baby ki kwantar da hankalinki... Kinga I won't make such mistake again... Babu abinda zai shiga tsakanina daita for years to come...." Daga kai tayi ta watsa Mashi harara</p><p>"Lie..." </p><p>"No baby am serious.... Ki tsaya ki ganta...zakaisan kawai shaidan ne ya rude na sadu daita.. Amma not because ta girma...so pls ki kwantar da hankalinki... Just feel like zaa kawo maki younger sister.... Basan bari ta rainaki ba....sannan ke kuma ki rike girmanki...she's 14... Kinga you are 8 years older than her... Don haka ki kwantar da hankalinki don Allah... Am assuring you bazakiyi regretting hakan ba....." Ya rada mata cikin kunne. Dan saurarawa tayi sai ajiyan zuciya kawai take, wai 14, she hates him so much, ko shekara basuyi da aure ba amma har yayi mata kishiya, yanzu she wish bata aureshi ba, tanada masu sonta da yawa amma ta nace sai shi, now ga irin shi nan, </p><p>"Yanzu nasan you don't love me as much as I loved you...inda kanasona baxakaji shaawan wata ba balle ka aikata wani abu daita....wallahi saboda kai bana ganin kowa as namiji sai kai...." Tafada tana kara fashewa da sabon kuka sosai, patting bayanta ya dingayi yana cewa</p><p>"Wallahi ba sonki ne bayi ba...kawai bazaki gane bane....It was beyond me....." Mufida banza tayi dashi ta cigaba da kukanta har saida jikinta ya Dau zafi, </p><p>"Baby tell me abinda kikeso...zanyi maki...." Yafada mata cikin kunne, mufida dake shessheka tace</p><p>"Kawai ka bari in tafi gidanmu....in kun gama amarcin sai in dawo....."</p><p>"No dear...ita nan Kano zan barta...." Yayi assuring dinta.</p><p> "Ni banson ka barta nan Kano.. Kar kajamin...kawai Ku tafi...bayan wata uku sai ka dauko ni..pls am begging you...." Tafada cikin sanyin murya, murmushi yazid yayi yana cewa</p><p>"Kashe ni kikesonyi kenan...ai wata uku with out you will be unbearable...." </p><p>"Ba wani..." Ta amsa Mashi. </p><p>"Kawai ki fadi abinda kikeso inyi maki...." </p><p>"Ai na fada maka...." </p><p>"Wannan bazai yuwu ba..make another request...ko in sake maki mota?..." Da Sauri tace </p><p>"Banso..." </p><p>"To in kaiki umrah..."</p><p>"Banaso...." Tafada tana hararanshi</p><p>"To in baki 1m ki fara home business...." </p><p>"Banso...." Tafada har da murguda Mashi baki, shuru yayi kaman mai tunani, daria ya farayi </p><p>"To me kikeso...." </p><p>"Ai I told you.. Kawai ka barni gida for 3 months....ko kuma ni ka Barni nan Kano ka tafi daita...." </p><p>"Hmmm no way...."</p><p>"Ai ina kishi in ganka kana magana da wata..."</p><p>"Babyna just wait and see..." Yafada. Haka ya dinga rarrashinta yana kwanta mata da hankali har bacci ya dauketa amma still koda ta tashi tambayanshi tayi if an daura Mashi aure ya amsa mata da yes nan ta fara sabon kuka kuma kafin dare fever ya rufeta amma ko ruwa batasha balle tasha ci abinci tasha magani, haka yazid yayi tagumi ya zauna gabanta yana kallon ta tana kuka har ta kara komawa bacci sai firgita kawai take.</p><p><br /></p><p>Itama dija ban da kuka babu abinda takeyi har ta fara dafa kasan maranta inda akayi mata aiki don tana kuka tana coughing, lokacin doc bai nan saida nurse taga abun da gaskene don kuka take sosai hannunta rike da cikinta ta kira doc ta sanar dashi. Bayan kaman minti talatin yaso yaga dija sai kuka take, komawa gefe yayi dailing number yazid, lokacin ya dawo daga masjid, ganin doc ke kiranshi yasa ya koma gefe sannan yayi picking, nan doc ya shaida Mashi Halinda dija ke ciki, </p><p>"Pls doc do something... Kar dinkin ya kunce...." </p><p>"Wani abu akayi mata?..." Doc ya tambayeshi, yazid shuru yayi yana tunanin kilan an fada mata she's married to him ne, </p><p>"Ai kune kusa daita...nidai just do something... Ko alluran bacci ne kayi mata...in ta farka in bata daina kukan ba ka kara mata...I don't want anything to happen to her pls..." Yafada cikin tashin hankali, daria doc yayi yana cewa</p><p>"We don't work that way...amma it will be better in zakayi mata magana...kiln ka kwantar mata da hankali..." Inii doc, idanuwa yazid ya zaro wishing inama yana Iya rada mata sweet words cikin kunne ta amma yasan it won't help, </p><p>"Doc ai tunda aljanu suka shafeta bata son ganina balle jin muryata...kawai take care of her.. " yafada agajiye don today is among the longest day of his life, kashe wayan yayi ya dan jingina da bango yana tunanin Ashe haka yake da wahala hada nauyin mutum biyu bisa kanka, </p><p>"Hmmm masu mata uku suna kokari...." Yafada ya kama hanya part dinshi.</p><p> Part dinshi ya koma ya tarda abinci kan dining while mufida na bacci sai ajiyan zuciya take saukewa. Komawa yayi falo ya cika cikin shi da abinci sannan ya zuba cikin plate ya rufe y kai bedroom ya ajiye kan side locker. Yafi hours zaune yana jiran mufidata tashi taci amma bata farka ba, daya gaji da zama ya kwanta.</p><p><br /></p><p>Har garin Allah ya waye mufida bata ci komai ba sai kuka, farat daya yanayinta ya Chanza, duk ta susuce. Tea ya hada ya bata ta ki amsa yayi Iya kokarinshi amma bata amsa ba. </p><p>"Pls baby in har you love me....ka bari in tafi gidanmu...ranar da zamu koma abuja sai kazo ka daukeni...pls I beg you. .." Tafada cikin dishessen murya..</p><p>"OK..." Kiyi wanka in kaiki...ranar Saturday zanzo maidaki gidanmu cos kinsan ke zaa bawa khadija... Sannan ranar Sunday zamu wuce abuja...I will give you the space you need ....alright?... " yafada yana rike da hannunta, kai kawai ta daga Mashi, mikewa yayi ya hada mata ruwan wanka ta shiga tayi ta fito sai tafiya take kaman iska na kadata. Bayan ta fito shimaya shiga ya watsa ruwa ya shirya, part din mom dinshi suka shiga tayi masu sallama, nan Hajiya karama ta zaunar daita tana bata shawara.</p><p><br /></p><p>Bayan ya ajiye mufida ya kira mai decorating gida ya shaida Mashi suna gidan suna aiki. Nan ya kama hanyan gidan don ganin how it's going.</p><p>Around 11am ya dawo gidansu inda ana ta shirye2 kai kayan lefen jos. Godiya ya kariya wa Salem cos still shi zai rakasu. Already doc Zara da nanny da akayi hiring don kula da Mahmud suna hanya </p><p><br /></p><p>Dija dai idanuwa sin kumbura sosai sabida kuka, yau ma data tashi bata bar kuka ba, tana zaune around 2pm aka shigo da yaron, ko daga kai batayi ba don banda tunani babu abinda takeyi, nan aka shaida Mata zaa tafi da yaron kaman yanda doc ya bukata,</p><p>"Ina zaa kaishi?..." Shine tambayan datayi masu,</p><p>"Inda zaa raineshi zaa kaishi..." Shine amsan da doc ya bata. Bata kara cewa komai ba aka fita da yaron.</p><p><br /></p><p>Mufida na shiga ta fada jikin mom dinta tana kuka, cikin tashi hankali ta fara tambayanta abinda ke faruwa nan ta fada mata abinda ke wakana,</p><p>"Don kishiya kike wannan kukan?... Har ya rainaki?..amma am so disappointed in you ..." Inji mom dinta</p><p>"Mom I love him ai...." Tafada cikin kuka sosai</p><p>"Mtwsss...amma iliminki baida amfani... Kinsan dai yazid yana sonki...so kawai kija hankalinshi...you know mu bamu bin boka ko Malam amma namiji yayi kadan ya wulakanta mu...don haka ki dauki kishiya as zero behind a decimal point... Kinji ko?..." </p><p>"Yes mommy... Yace nan zai barta"</p><p>"Kar ki yarda....ya tafi daku tare...karki yarda ya gama dake sannan ya dawo kanta...kowacce halinta ya ficeta....kuma zan kira Hajiya hannatu ta kawo maki sabon kayan harka...kawai ki kwantar da hankalinki kiji ko?..." </p><p>"Yes mommy..." Ta fada tana lafewa jikin uwarta.</p><p><br /></p><p>Shima yazid shaidawa su mom da dad yayi kan zai bar dija Kano suma sukace Sam basu yarda ba ya tafi dasu.</p><p><br /></p><p>Akauyen kam da aka kawo lefe ba karamin surprise sukayi ba don tunda suke basu taba ganin abu Irin wannan ba, duk garin taruwa sukayi suna kallon lefen nan fa maganar Hajiya karama ya zama gaskiya don ji suke ina yarsu ta samu irin wannan abun arzikin. Wasu ma cewa suke da ansa biki don ko bakomai zasu ci shinkafa. </p><p><br /></p><p>Ada suna son a kai dija gidan mijinta straight from the hospital amma yanzu an sake shawara kan a maidota gida ta shirya sai a kaita dakinta. Wani kawunta aka aika ya tambayo yaushe zaa sallameta nan aka shaida masu ranar asabar da safe.</p><p><br /></p><p> ~Saturday~ </p><p><br /></p><p>Da wuri doc ya sallami dija inda wasu sis din amminta suna jiran a sallameta, sunajin doc ya ce ya sallameta suka fara shirya kayanta. Bayan sun gama suka tsaida taxi suka shiga da dija da kayanta, sanyi dija taji don gani take kilan an fasa auren cos ammi ta fada mata daga hospital zaa wuce daita amma gashi an kama hanyan gidansu ammi. Ba karamin dadi takeji ba zata kara ganin amminta. Suna isa ta fito tana tafiya ahankali sannan tana daga gaban riganta don kar ya gogi inda akayi mata aiki. Tana shiga cikin gidan duk suka rungumeta wai suna murnan ganinta, baki ta washe don ta mance rabon da taji irin wannan farin cikin. Inda ammi ke zaune taje ta zauna gefenta. Gani ayi ai gidan ciki da mutane har wayanda ba cikin gidan suke zaune ba. Kowacce sai kallon ta suke, sadda kanta kasa tayi don she was thinking saboda cikin da akayi mata ne yasa duk aka zuba mata ido. Baban ammi ya kira ta ta tashi tana biting bottom lip dinta saboda zafin inda aka yi mata aiki. Tana shiga yasa ta zauna nan ya fara bata advice kan rayuwa.</p><p><br /></p><p>.abangarensu yazid komai is ready, part din dija kaman ba yar gidan talakawa ba don few things mufida zata nuna mata,komai looks wonderful and beautiful. Karfe biyu motoci hudu suka kama hanyan gidansu ammi, cikin motan Salem wata matace mai kyalliya dauke da kit guda biyu, daya na kayan aikinta sai dayan na kayan da hajjya karama ta saya a sakawa dija.</p><p> Yazid rike Salem yayi yace </p><p>"I promised babu mai hanaka auren Maryam sai Allah..." Yayi assuring dinshi sounding very firm. Dariya kawai yayi ya shiga mota suka bar gidan tare da sauran wayanda zasu dauko amarya.</p><p><br /></p><p>Yazid kira doc yayi ya umarceshi daya rubuta Mashi drugs din dija zai saya anan haka akayi. Daga pharmacy ya wuce gidansu mufida don daukarta. Yana shiga falon gidansu gabanshi na faduwa amma to his surprise da gudu mufida ta fado jikinta, </p><p>"My baby..." Yafada yana. Kallon yanda babu sauran damuwa tattare daita</p><p>"Yes sugar...." </p><p>"Am happy you are OK?..." </p><p>"Yes sugar... Nayi tunani kuma naga babu komai cikin dunyia....after all who are we to question the will of Allah..." Bata idaba ya kama bakinta ya fara kissing dinta forgetting ba gidansu bane. Sai da suka zama both breathless sannan ya saki bakinta</p><p>"I love you..." </p><p>"Love you too..." </p><p>"Now baby kije ki shirya muje gidanmu muyi like 3 rounds kafin a kawo sister dinki...." Yafada sounding very naughty, fari tayi da idanuwa sannan tace</p><p>"Yes baby...anything for you..." Tafada tana juyawa tare da gada Mashi kugu, dariya yazid yayi yana cewa</p><p>"Nasan yau kasheni zakiyi...." </p><p><br /></p><p>Karfe biyu da rabi su Salem suka is a kofar gidansu ammi, da gudu yara suka shiga cikin gidan suna</p><p>"Sunzo da motoci da yawa....sunzo da manyan motoci...." Nan gida ya hargitse, gaban dija faduwa yayi ta fashe da kuka, ba komai take tsoro ba illa abinda yazid yayi mata, ba wai tasan shi aka aura mata ba amma kawai tasan ko ma waye yau sai yayi mata irin abinda yazid yayi mata. Kara fashewa tayi da kuka suka hada ido da ammi, harara ammi ta watsa mata nan take ta hadiye kukan, daman ta sakata dogiwar Riga. Sallama matar dake kwalliya tayi aka amsa mata, daman already matan gidan sun fara shirin raka amarya da suka ga luxury cars.</p><p><br /></p><p>Matar Neman amaryan tayi aka nuna mata, nan ta baje kayan aikinta ta fara tsara mata kwalliya within few minutes dija ta Chan za from dijan kuaye to khadija yazid, ( remember no body is ugly... Inji psquare😉) baki duk yan gidan suka bude suna kallon yanda ake transforming dija zuwa wata. Bayan an gama makeup aka saka matadoguwr Arabian gown mai dauke da hijjab.</p><p>[6/22, 5:56 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: 🧡💜💙💚💛❤</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙💚💛❤🧡</p><p><br /></p><p>®Zuwairat (ummummaryam)</p><p><br /></p><p>3⃣5⃣</p><p><br /></p><p> _Follow me on:_ </p><p><br /></p><p> *Wattpad @ummumaryam29* </p><p><br /></p><p> *Email:Zuwairat.nuhu@gmail.com* </p><p><br /></p><p> *IG: zuwairatummumaryam* </p><p><br /></p><p> *Website:Www.ummumaryam.com* </p><p><br /></p><p> *And also join my new Facebook group: Zuwairat ummumaryam and Zuwairat ummumaryam page.* </p><p><br /></p><p> *Snapchat: ummumaryan29*</p><p><br /></p><p>Bayan an gama aka saka mata shoes da suka hau da sky blue Arabian gown dake jikinta. Perfumes matar ta fesa mata sannan ta tattara kayanta cikin bag tace</p><p>"Amarya kinyi kyau...." Tafada tana fiddo waya daga cikin pause dinta, pics tayi mata sannan ta fita daga dakin, ita ai dija sai feeling so weird don gani take kaman an damkar mata buhun cement a face dinta don nauyi taji fuskanta yayi mata.</p><p>"To ki tashi mu tafi...." Wata yar uwan ammi ta fada mata, jiki ba kwari ta mike idanuwanta cike da kwalla amma basu zubo ba, wurin grandparent dinta aka kaita suka karayi mata adua sai wajen amminta nan dija ta dinga kuka kaman ranta zai fita, tana kuka tana dafa maranta. Saida ammi ta daka mata tsawa sannan tayi shuru</p><p>"Kuma wallahi kar ki bari inji ance kiyiwa mijinki laifi...duk abinda yace kiyi kiyi kina jina?"..." Da Sauri ta daga mata kai</p><p>"Allah ya kaddara saduwanmu...tashi ki tafi Allah ya yi maki albarka ya yafe maki kurakurenki...." Jiki na rawa dija ta mike mata na biye daita, suna fita waje mata na tsaye cike da waje wasu sunyi ready zasu bi ta don kashe qarkwatan idanuwansu. Bayan an nunawa dija motan Salem ta shiga baya sai kuka take, sai yau Salem yaga dija, duk da kanta na kasa jikinta ya nuna karamar yarinya ce, murmushi yayi ya kauda kanshi gefe cikin ranshi yana cewa</p><p>"Shege yazid...." Salem lekawa yayi a mirror yaga yanda mata ke rige2 shiga mota</p><p>"Allah yasa kar su lalata masu mota. Bai Ankara ba wasu mata kusan su uku suna kikarin shiga gidan gaban motanshi, sai ture juna suke kaman wasu awakai, kaman yayi magana sai kuma yayi shuru</p><p> "Ki bari ni na kamata in bita ba ke ba..." Inji daya daga cikin su, </p><p>"Lallai ma..." Daya ta fada, matar datayiwa dija makeup dake zaune baya kusa da dija ta tabe baki sannan tace</p><p>"Haba kubi ahankali mana...ko so kuke Ku lalata masu mota..." Tafada cikin tsiwa da Sauri suka ja baya daya ta shiga. Salem ya fixgi motan suka bar wajen, duk sauran cars na dauke a mutane 8 biyar baya sai biyu gaba da driver. Salem kam yayi deciding bai maidosu saidai ya samo bus da zai maidosu, babu abind ke tashi cikin motan sai sheshekan dija.</p><p><br /></p><p>Bayan sun gama sukayi wanka tare mufida ta zauna gaban mirror yazid ya goge mata gashi da karami towel sannan ya shafa mai hair cream tare da combing kan, kawai yanayi yana kallon ta tacikin mirror yana aduan Allah yasa this is not a trap don ko kadan babu wata damuwa tattare daita hes wondering how comes don lokacin daya shaidawa mufida halinda ake ciki tamkar zaa kwantar daita hospital, hannunta data dora kan hannunshi ya maidoshi hayyacinshi, murmushi ya sakar mata yana cewa</p><p>"Baby I love you... Kinsan wannan shine abinda kikayimin daya fi komai burgeni...thank you.. " murmushi tayi dukda maganar shi ta bata mata rai wato duk kokarin da take wajen biya Mashi bukatan shi bata burgeshi kaman wannan ba, amma ko kadan bata nuna Mashi hakan ba saboda advice da mom dinta ta bata.</p><p>"Baby na zauna nayi tunanin babu komai duniya...sannan banason rabonda ke tsakaninka daita ya aikadani lahira...so kawai Allah ya bamu zaman lafiya...kuma pls promise me you will love and cherished me all the days of my life...." Tafada Mashi cikin natsuwa, hannuwanshi yayi rounding waist dinta daga inda take zaune yayi hugging bayanta, </p><p>"Baby I will love you for ever...I wish dukkan mata zasuyi yadda kikayi...su San cewa what will be will always be nor matter what...." Yafada yana kissing bayan wuyanta</p><p>"Baby I love you too..." Tafada tana shafa face dinshi dake bayanta.</p><p>"Yanzu baby tell me abinda kikeso inyi maki...." Shuru tayi kaman tana tunani for a while sannan tace</p><p>"Why not mu bari muje umrah tare...." Dadi yazid ya karaji ya kara rungume yana jin wani irin sonta da kaunarta har cikin system dinshi.</p><p>"That sounds perfect my Queen... Yanzu yaushe su Aisha zasuzo?..." </p><p>"Zuwa later..." </p><p>"OK muyi sallah...kafin ki shirya kafin su zo...and pls my Queen kar ki biyewa duk abinda zasuce....I know them too well...." Murmushi mufida tayi tace</p><p>"Baby don't worry... I won't let anyone lead me astray..." Tayi assuring dinshi</p><p> Murmushin jin dadi yayi bude closet ya saka jallabiya ya fita sallan asr. Itama doguwar riga tasa tayi sallah.</p><p><br /></p><p>Bayan sun ci abinci tace</p><p>"Baby kasan au bazan Iya girkin tarban baki ba...ko zakayi mana order na abinci?.. Tunda am sure basu komawa yau..." </p><p>"OK...banason kiyi wahalan shiga kitchen after all I have put you through yau..." Yafada yana dariya, hararanshi tayi tana murmushi</p><p>"Kawai zan sa akawo abinci daga one of the restaurant around..." </p><p>"Yauwa.. Thanks... " tafada tana sauraron doorbell da ke kara,</p><p>"I think friends dinki sunzo...." Yafada yana mikewa, bedroom ya shiga while ita kuma taje bude kofa. Wasu age mate dinta biyu ne tsaye daya na rike da beautiful baby gal,</p><p>"Ya akayi na ganki haka?...." Daya ta tambayeta tana shiga cikin falon, murmushi mufida tayi </p><p>"Ya kikeson ki ganni?...Aisha..." Hararanta Aisha tyi while sitting,</p><p>"Lallai ma...yazid dinkine yayi aure amma Sam banga alaman damuwa tattare dake ba...kodai karyane...." Dariya mufida tayi tana cewa</p><p>"Yo kashe kaina zanyi?... Ai Allah ya kaddara...kuma j know my hubby loves me...kawai ban bari wata ta tadamin hankali..." Tafada tana zama kusa dasu, Aisha da Zainab kallon juna sukayi suka kwashe da dariya</p><p>"Amma ke baki San meye kishiya ba..." Inji Zainab,</p><p>"Dalla rabu daita....kilan ma karya take baayi mata kishiya ba cos nasan halinki...." </p><p>"Ai kawai na kwantar da hankalina ne...".</p><p>" nidai har yanzu ban yarda anyi mata kishiya ba...." Zainab ta fadawa aisha,</p><p>"To Ku tsaya Ku gani mana..." Tafada tana mikewa, </p><p>"Me zan dan dafa maku kafin ayi ordering abinci... Don bani da komai kasa..." Tafada sounding very free. Aisha da Zainab kallon juna sukayi basuce komai ba don her attitude kaman ba mufida ba.</p><p> "Nace me zakuci kun tsaya kallon juna...." Iniji mufida, </p><p>"Ke mu mun koshi...." Aisha ta fada mata tana hraranta. Haka suka dinga zolayanta na kan karya take baayi mata kishiya ba ita kuma tana cewa su jira su gani.</p><p><br /></p><p>Around 5:30 yazid ya kira Salem donjin inda suke nan Salem ya fada Mashi, kallon agogon hannunshi yayi yagan in the next 30 to 40 minutes zasu iso. Bathroom ya kara shiga ya watsa ruwa har yanzu bai yarda dija zata kwana nan gidan yau as his wife ba. Yana fitowa ya saka shadda pure white da black senator cap ya fito falo inda mufida da su aisha ke zaune, </p><p>"Ango ango...." Mufida ta fada cikin zolaya, murmushi yayi ya mika mata Hannu, da Sauri ta mike ta fada jikinshi, Aisha da Zainab kallon juna sukayi, </p><p>"Ango sai kamshi kake...ni har na fara kishi...." Tafada tana marairace face. </p><p>"Baby har zolayata kike?..." Yafada yana kallon eyes dinta, dariya tayi, </p><p>"Zan je ordering abinci... Zuwa 6 to 6:30 zasu iso..." Yafada mata</p><p>"OK..." Tafada tana gyara zaman hulan kanshi,</p><p>"Me da me zaa kawo?..." </p><p>"Tunda daga rural area suke akawo rice and stew sai drinks..." </p><p>"Kaman plate nawa?..." </p><p>"Hmmm akawo dai da yawa...dayayi kadan it's better yayi yawa..." </p><p>"OK love... Ke me zakici?..." Ya tambayeta cikin so da kauna, murmushi tayi don tasan ko ruwa bazata Iya kara sha ba muddin Khadija ta shigo gidan nan</p><p>"Baby zanci duk abinda zasuci...." Tafada ahankali, Aisha dake sauraronsu Kara kallon Zainab tayi tare da tabe baki,</p><p>"Baby are you sure...nasan baki fiya son rice ba...."</p><p>"No baby zanci...." </p><p>"OK ...I love you..." Ya fada tare da yi mata kiss a forehead dinta sannan ya fita ko kallon inda su Aisha ke zaune baiyiba. Tsaye tayi wurin bata juya ba, </p><p>"Kinsan wallahi saida yayi mata asiri sannan yayi mata kishiya..." Zainab ta radawa Aisha cikin kunne,</p><p>"Maganar ki haka ne....don nasan ko kadan mufida bazata yarda da zancen kishiya ba...." Itama Aisha a fadawa Zainab cikin whisper, cikin sanyin jiki mufida ta shiga bedroom dinta, ta kwanta kan gado tayi ruf da ciki sai ta fashe da kuka saboda yanda zuciyanta ke zafi da kuna</p><p> Bayanta su Aisha sukabi suka tardata kwance tana kuka, ahankali suka zauna tare da dafa mata shoulder,</p><p>"Kiyi hakuri...sai yanzu na yarda da gaske kike..." Inji Aisha, cikin kuka mufida ta data kai tana cewa</p><p>"Ya zanyi...nashiga uku...my heart is busting..." </p><p>"Kiyi hakuri...amma ba dole ki zauna daita...you can...." Zainah bata idaba mufida ta girgiza mata kai</p><p>"No...bazan Iya aikata mugun abu ba...in nayi hakan I will loose him for ever.. Amma in nayi hakuri nasan zanci riban hakan... Mom tace I should pretend kowa tashi ta fissheshi....amma kaman zan mutu nakeji...." Tafada cikin matsanacin kuka while tana Dora kanta kan shoulder Aisha, patting dinta suka dingayi from both side</p><p>"Naji kina cewa from rural area...yar akuyece?..." Zainab ta tambayeta, cikin kuka ta gyada mata kai</p><p>"She's just 14..." mufida ta amsa mata</p><p>"Mtwsss...ko ina ya ganta?... Maza da kwace...."inji Aisha,</p><p>" wayan nan yan kauyen da kwace miji...kawai just be strong and be prayerful... Kinsan irin yazid is not someone da zaayi sakaci dashi...kawai kisan yanda zakiyi ki dauke all his attention... " zainaba tayi comforting dinta. Mufida tafi minti talatin tana kuka, </p><p>"Kinga in har kika shigaba da wanna kukan har sukazo raina ki zatayi sannan in yazid ya shigo yanzu zaice you are pretending.. So pls stop crying inyi miki fixing ruwan wanka kiyi wanka ki shirya kafin su zo..." Inji Aisha data mike, bathroom tashiga ta hada mata ruwan wanka suka jata tashiga. Tana wanka tana kuka haka ta gama t fito kanta na sarawa</p><p>"Duk wanda ya ganki yasan kinyi kuka..." Zainab ta fada mata. Ahankali ta bude wall to wall bedroom dinta ta dauki wani beautiful and expensive lace ta saka, gaban mirror ta zauna ta dan shafa mai sama2 sai wet lips, nan suka koma falo ta kwanta kan doguwar kujera, bayan kaman minti goma yazid ya shigo da sallama ta amsa tana mikewa zaune. Mai gadi ne ya fara shigowa da drinks cartons sai abinci aka ajiyesu gefe daya. Zamayayi kusa da mufida ya kura mata ido sai murmushin karfin hali take Mashi, yana ganinta yasan tayi kuka, hannunta ya kama suka goma daya daga cikin bedroom dinta ya zaunar daita </p><p>"Baby kuka kikayi ko?..." Ya tambayeta yana zama gefenta, murmushi tayi tana girgiza Mashi kai at the same time new tears suna taruwa eyes dinta. Rungumeta yayi yana shafa kanta yana cewa</p><p>"Baby you are trying... Pls keep on trying.. Kinji...." </p><p>"OK...." Tafada tana gyada Mashi kai. Da Sauri ta aga kai tana kallon yazid lokacin data ji karan horn kofar gidan su. Da Sauri ta mike ta shiga bathroom ta wanke face dinta ta fita falo.</p><p><br /></p><p>Dija bude ido tayi tana kallon gidan da zaa shiga. Mai gadi na bude gate ta koma zaune daga jinginen da take tana kallon compound din da suka shiga, gabanta ne ya fara dukan uku2, fashewa tayi da kuka cikin muryanta da bai fita sosai, parking lot sukayi parking. Nan kauyawa suka fara fitowa bakinsu bude suna kallon gidan. Yazid dake tsaye bakin window rike baki yayi yana dariya saboda yanda mata ke fitowa daga cikin motan daya na ture daya sannan yana kallon irin kallon da sujewa gidan. Kare kanshi da curtains yayi yana kallon su, gurinshi kawai yaga dija. Dija kyar dija ta fito bayan kowa ya fito, sai kuka take idanuwanta sun kumbura, daga inda yake yana kallon swollen eyes dinta dukda gari ya fara duhu. Tsaye sukayi suka rasa inda zasu shiga, wacce tayiwa dija kwalliya tayi masu jagora zuwa part din mufida, dayake an fada mata. Bayanta sukabi har falon, daga bakin kofa suka fara zama don basu da courage din shiga ciki, su Aisha dariya suka farayi suna cewa.</p><p>"Ku shigo ciki mana..." Sai lokacin suka shiga falon sai juye2 suke Suna kallon ikon Allah, wasumsu suna tunanin inama a daukesu as mai aikin a wannan gidan, still kasa suka zauna mufida datakurawa dija ido tace</p><p>"Pls Ku zauna kan kujeru...haba ai an zama daya..." Bata idaba suka koma kan kujera, babba cikinsu ta fara cewa</p><p>"Sannunku..." Tafada sounding out of words, mufida dake wearing murmushin karfin hali tace</p><p>"Yauwa.. Da fatan kun iso lafiya?..." </p><p>"Lafiya lau..." Suka amsa in chorus, daman koda akace su koma kan kujera dija bata koma ba, tana nan kasa kanta kasa sai hawaye ke diga, mufida kura mata ido tayi tana kallon how young she is, </p><p>"Hmmm maza basu da imani..." Ta fada cikin ranta data tuna yazid yayi raping dinta, sai taji ta tsaneshi, </p><p>"How could he do it..." Shine tambayan da takewa kanta cikin ranta, don a da tana tunanin yarinya CE mai katuwar jiki amma yaga Sam ba haka bane, </p><p>"Hmm kodai fuskanta ya rudeshi?..." Ta sake fadawa kanta, don ta lura yarinya Nada kyau,</p><p>"Ga amana da muka kawo maki... Don allah ki dauketa tamkar yaruwarki...in tayi maki laifi ki hukunta ta tsakaninki da Allah...marainiyace..." Wata mata ta fadawa Matan dake zaune not knowing wacece matar gidan,</p><p>"Ai wannan ba wani abu bane..in har ta dauketa a matsayin yaya itama zata dauketa amatsayin kanwa..." Aisha ta fada masu,</p><p>"Ai wannan ba komai bane...dija bazatayi mata ba daidai ba...in Allah ya yarda</p><p>..." Matar ta kara fada mata, </p><p>"Allah ya bamu zzaman lafiya...." Mufida ta fada da murmushi fuskanta, wanda yasa suka gane itace uwar gidan. Mikewa tayi ta daga dija data hada kai ta gwaiwa tana kuka</p><p>"Ki bar kuka...." Tafada mata cikin sanyin murya Da Sauri dija ta gyada mata kai tare da wiping face dinta da bayan hannunta. Sai ta bawa mufida tausayi don she's too young for all this. Wacce tayiwa dija kwalliya ta mike ta umarcesu su bita tare da rikewa dija hannu. Nan suka bita har part din dija. Har bedroom dinta ta kaita duk a bisa umarnin Hajiya karama nan tace</p><p>"To amarya ga bangarenki...Allah ya bada zaman lafiya...." Ta fada sannan ta fita ta bar family din dija baki bude, kasa dija ta zauna ta saka kai cikin cinya sai ajiyan zuciya take ga ciwon cikin da take amma basu bi ta kanta ba sai kallon gidan kawai suke, su shiga nan su bulla chan. Ta back door yazid ya fita bayan yayi alwallah. Daman ya kira salem ya gaya mashi ya jirashi cikin mota. Yana fita yazid ya watsa Mashi kallon haushi da takaici</p><p>"Wallahi tunda aka haifeni ban taba wahala irin wannan ba...am so tired...gaskiya ka nemo masu maidasu don ni na gama nawa...." Inji Salem</p><p>"Nagode kwarai...Allah ya kara dankon aminci a tsakanin mu...am so greatful..." </p><p>"Ni dai ka bar wannan gaisuwan...kawai remember what you promised..." Dariya yazid yayi</p><p>"Ai kasan bana karanta...in komai ya lafa zanyiwa dad maganar..." </p><p>"OK...ni zan wuce...asha kamshi lafiya...." Salem ya fada Mashi. Dariya yayi ya nufi masjid shi kuma Salem ya wuce. </p><p><br /></p><p>Aisha da Zainab suka shiga part din dija kai masu abinci, baki suka bude don basu expecting suga komai amma sai ka well decorated parlour, suma zagaye wurin sukayi sannan suka kaiwa mufida rahoto, </p><p>"Kam kinga irin kayan dake part dinta?... Indai yazid yayi mata su to baida adalci.... Don am sure ko dukkan families na yarinya zaa saida basu sayan cushions dake falon..." Aisha ta fada ciki da bakin ciki, mufida ai bata CE komai ba, Zainab tace</p><p>"Kinsan ni ina tunanin wannan yarinya babu ruwanta...sai dai kawaye su lalata ta..and am advising you kar ki bari tayi friends... Ki zama kawarta...ta hakan zaki san sirrinta don da ganin ta bata da wayau...." Zainab tayi adding. Mufida dai shuru tayi tana sauraronsu don ko kadan bazasu gane halin da take ciki ba. </p><p><br /></p><p>Haka suka gama surutunsu sukayi mata bankwana. Ahankali ta mike ta shiga bedroom ta kwanta bayan tayi sallan ishai. Part din dija kam cinye abinci sukayi tas basu tuna da dija ba kasancewan kwantawa tayi kasa daga nan bacci ya dauketa, yazid kam yana masjid har yayi sallan isha sannan ya dawo gidan, bedroom din mufida ya shiga ya ganta kwance. Car keys dinshi ya dauka ya fita daga gidan. After like hour daya ya dawo da manyan Leda's guda biyu, zama yayi cikin mota yana tunanin yanda zaiyi yagan dija sannan ya tabbatar taci abinci tasha drugs dinta kafin ta kwanta. Kallon agogon hannishi yayi yaga few minutes pass nine. Leda daya ya dauka sai drugs din da doc yayiwa dija prescribing daya sayo. Fita yayi ya nufi part din dija gabanshi sai faduwa kawai yake.</p><p>❤💛🧡💙💜💚</p><p><br /></p><p>Ina maku fatan alkairi, allah ya kaimu bayan sallah lafiya, pls still ina rokon aduanku.</p><p>[6/22, 5:58 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: 🧡💜💙💚💛❤</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙💚💛❤🧡</p><p>®Zuwairat (ummummaryam)</p><p><br /></p><p>3⃣6⃣</p><p><br /></p><p>*Wishing all my beautiful people happy sallah, Allah yasa dukkan ibadun mu* *karbabbune, Ameen*</p><p><br /></p><p>Ahankali ya bude kofan yana aduan Allah yasa Matan da suka rakota sunyi bacci, yana shiga falon luckily mata biyar ya gani kwance kasan tiles suna bacci, kaman barawo ya taka yana aduan Allah yasa tana inda she's suppose to be, yana bude kofan bedroom daya fi dukkan sauran haduwa ya ganta kwance kasa sannan babu kowa, da Sauri ya shiga kaman Mara gaskiya ya maida kofan ya rufe, ya yazo ya zauna gabanta bata san ya shiga ba, zama yayi yana kallon yanda take sauke ajiyan zuciya kaman wacce tayi 360 race.</p><p>Kawai sai ya saki murmushi yana lumshe eyes kaman Wanda aka yiwa albishir da aljanna. Kallon yanda take shessheka kawai yake don ya san ba karamin kuka tasha ba, kallon hannunta dake kan maranta yayi., ahankali ya mike bayan ya ajiye drugs da abinci daya shigo dasu. Cikin saddo ya bude kofa ya fita yana tafiya ahankali har ya isa kitchen, kara kallon kitchen din yayi yana tunanin ya gan dija tana amfani da kayan kitchen din don ko shi da kanshi bai san amfanin wasu kayan ba don he's not use to kitchen. Wani cup ya. Dauka cikin kayan da aka jera ya kai sink ya wanke sannan ya dauki plate shima ya wanke sannan ya fito. Kara shiga dakin still tana kwance yanda take. Zama yayi ya cika cup da milk sannan ya fiddo ragolis water ya ajiye gefen milk din, plate ya dauka ya zuba roasted meat, hannu ya daga kaman ya tadata amma baisan abinda zai tada mata hankali, yafi minti biyar yana daga hannu amma yana rasa courage, amma ganin wankin hula zai kaishi dare yasa yayi karfin halin dan taba kafanta, aikam a firgice ta farka tana mazurai, kallon Wanda ya tadata tayi da kyau ta tabbatar yazid ne, nan take ta fara ja da baya tana yarfe hannunta at the same time tana fashewa da kuka</p><p>Cikin kuka ta fara cewa</p><p>"Wayyo Allah na....wayyo ammi na shiga uku..." Tafda sounding very tired and fed up, sai ka take da baya while shikuma yayi kuri ya kura mata ido babu abinda yake sai kallon ta. Dija najin ta kai bango ta kara volume din kukanta. Yazid ji yayi kaman ya rikota amma yasan it will only make it worst. Gyara zamanshi yayi tare dayin ganmo da legs dinshi duk eyes dinshi kan ta,</p><p>" tashi ki shiga bathroom ki wanko bakinki..." Ya fada sounding formal, da sauri ta girgiza kai batare datace Kala ba, kuka tacigaba dayi</p><p>"Nace ki shiga bathroom ki wanko bakinki..." Yafada da karfi, aikam da sauri ta mike tashiga bathroom, tana shiga ya fara dariya yana girgiza kai, ya gano one of her weakness, which is tsoro, yasan tamkar monster yake wajenta and he's going to use it to his advantage, dija na shiga ta dafa bathtub tana kuka, tana mamakin duniya bayan duk abinda yayi mata amma sun hadata aure dashi, cikin kuka ta fara cewa</p><p>"Don sunga bani d baba....don Abba ya mutu...shiyasa sukayi min haka..." Tafada cikin kuka, ji tayi muryan yazid nacewa</p><p>"Ina jiranki...." Da sauri ta dubi toothpaste rack and dispenser ta dauki brush ta zaro toothpaste ta zuba jikinta sai rawa kawai yake, cikin sauri ta wanke bakin ta fito face dinta sharkaf da hawaye, daga kai yayi babu faraa sosai kuma fuskanshi ba daure yake ba, tsaye tayi bata da niyyan zama</p><p>"Ki zauna mana...." Yafada mata, da sauri ta saki jikinta ta zauna sai kuma ta rike maranta, mikewa yayi ya dauki milk da plate ya ajiye gabanta.</p><p>"Bissimillah....." Yafada mata tare da nuna abubuwan dake gabanta, da sauri ta girgiza kai tana kuka,</p><p>"Kinason ranki ya baci?..." Ya tambayeta, da sauri ta sake girgiza kai,</p><p>"To ki cinye yanzu nan...." Bai idaba ta fara cin naman tana kuka, duk cin da zatayi sai tears dinta ya diga, har ta koshi amma tana tsoro daina ci, gani yayi tana Neman cinye kaza daya kuma da alaman ta koshi amma bata Iya dainawa</p><p>Kallon yanda take tauna nama kaman paper yayi, kauda kai gefe yayi ya saki murmushi cos he's enjoying the moment don yasan Yana daga cikin abinda zai dinga zolayanta dashi in future, dauke plate din naman yayi ya maidata gefe sannan ya dauki cup of milk ya ajiye gabanta,</p><p>"Bissimillah..." Ya sake fada mata, tana shesssheka ta dauki cup din tana sha tana kuka at the same time tana tunanin halin d zata fada yau don tasan bazai fasa yi mata abinda yayi mata da ba, har yanzu bata bar tunanin dalilim dayasa ammi ta yarda aka hadata da irin wannan mutum ba, ajiye empty cup din tayi tare da goge bakinta da bayan hannunta, yazid daukan ledan drugs din yayi ya bude ya ballo wayanda zatasha ya mika mata, ganin yayi bata amsa ba, hannu yasa ya kama right hand dinta Wanda yasa dija kara volume din kukanta, murmushi ya kara saki enjoying the tenderness and warmth of her skin, ajiye drugs din yayi cikin hannunta ya dauko ruwa daga cikin ledan daya shigo daita ya bude ya mika mata, jikinta na rawa ta amsa ta juye dukkan Maganin cikin bakinta ta zuba ruwa ta rumtse ido ta hadiye, mikewa yazid yayi ya shiga bathroom ya hada mata ruwan wanka ya fito,</p><p>"Ki tashi kije kiyi wanka...." Ya fada sounding so commanding, da sauri ta mike kaman Kazan</p><p>Da aka tsoma cikin ruwa ta shiga bathroom, tana kuka tana cire kayan jikinta, kallon kofan tayi don gani take kaman zai shigo, bathtub ta shiga don already tasan amfani shi tun sanda tayi aiki gidansu yazid. Jikinta na rawa ta gama ta fito ko goge jikinta batayiba ta maida kayanta ta fito kanta kasa sai hawaye ke diga,</p><p>"Ko pump albarka...." Yazid ya fada yana kallon yanda tears ke fita daga eyes dinta. Yazid mikewa yayi daga inda yake zaune ya je bakin gadon ya yaye duvet dake rufe da gadon sai wata bedsheets ya bayyana daga kasa</p><p>"Zo ki kwanta...." Ya umarceta, nan jikinta ya fara shaking to the extent yana ganin yanda duk jikinta ke rawa, yasan he has ruin her life and he promise himself to make things right again, he will do anything to make her trust and rely on him, duk tafiyan da zatayi sai jikinta yayi rawa, ajiye duvet din yayi ya nufeta, bata ankaraba ya dauketa, wani irin kuka ya kufceta mata</p><p>"Wayyo na shiga uku....ammi...." Tafada cikin matsanacin kuka, kasa tafiya yayi ya tsaya rike data kaman babu komai hannunshi, kurawa swollen and tired eyes dinta ido yayi yana kallon yanda tears ke rolling,</p><p>"Dan Allah..... Ciwona....ciwo gareni....kayi hakuri....." Tafada sounding so tired and afraid, idanuwanshi ne suka ciko da tears, ahankali ya fara girgiza mata kai,</p><p>"Khadija.... Kiyi hakuri...." Bai idaba tayi saurin daga Mashi kai tana kuka</p><p>"Abinda ya faru tsakanina dake kaddara ne....dan Allah ki yafe min....nayi maki alkawarin bazan cutar dake ba....bazan karayi maki abinda baki raayiba....duk abinda kikeso zanyi maki...." Duk maganar dayake babu abinda take sai daga Mashi kai cike da tsoronshi with her eyes closed, ahankali ya taka zuwa bakin gadon ya kwantar daita, bargon ya dauko ya rufa mata, zama yayi bakin gadon yana yana kallon ta, bayan kaman minti five ya mike yayi pecking goshinta sannan rage wutan dakin ya fita feeling so happy, cikin motanshi ya koma ya dauko dayan ledan ya kulle motan ya nufi part din mufida.</p><p><br /></p><p>Ita kam mufida tana kwance amma ko kadan bacci baiyi gigin dauknta ba, kawai she's thinking ya akayi yazid ya Iya sex da khadija don ita yanzu wani irin haushin shi kawai take ji,</p><p>"Hmmm kawai kaga mutum..." Ta fada tana chanza position na kwanciya ta, tana jin stories na molestation na yara amma she can believe she's married to a child abuser, sallaman shi ya maidota mind dinta, dan daga kai tayi ta watsa Mashi wani irin kallon that tells the disgusting being is here tayi Mashi sannan ta amsa sallaman ciki2, murmushi kawai ya saki batare dayaji zafin kallon datayi Mashi ba. Ajiye leden yayi kan small dining sannan ya nufi bakin gadon yana balla buttons din riganshi, yana zama mufida ta kauda kanta gefe daya tare da bashi baya, hannunshi ya Dora kan bayanta tayi saurin bige Mashi hannu with all her strength,</p><p>"Baby nayi laifine?...." Ya tambayeta yana shafa inda ta bigeshi,</p><p>"Mtwssss....monster in disguise..." Ta fada under her breath, daure fuska yayi while taking in what she just said, yafi minti biyu bai ce komai ba, saida ya tabbatar temper dinshi ya dan sauka sannan yace</p><p>"Baby why this harsh words.... I thought kin bani hadin kai...ko wani laifi nayi kuma?..." Yafada kaman ranshi ba bace yake ba,</p><p>"Mtwssss.....sounding like angle...." Ta sake fada tana kara matsawa daga inda yake,</p><p>"Baby pls kibar yi min tsoki....it's a sign of immorality and disrespect....." Bai idaba ta mike zaune tana yi Mashi kallon haushi da takaici</p><p>"Look WHO is talking about immorality.... Wallahi you are a disgrace to all your kind....am ashamed to call myself your wife.... Child abuser kawai...." Yafada on top of her voice, face din yazid ya yi ja, he's feeling so hurt and angry inside amma yasan she's not far from the truth,</p><p>"What brought all this now?...." Yafada kaman bashi ba,</p><p>"Everything... Ganinta dazun makes me shed tears....kai mugu ne....I hope nemesis caught up with you...if you can upen such gals leg and sex then babu irin mugun abun da baka iyawa....dan iska....." Wani irin saukar mari ya dauke mata wuta,</p><p>"Don't you ever....ever....ever...in You entire life call me that again...." Ya fada sounding super furious, mufida na kuka hannunta kan cheek dinta tana cewa</p><p>"Naje na fada....dan iska...dan iska...dan iska...that's your real name...not yazid...." Ta fada cikin matsanacin kuka, banza yayi daita ya fita daga dakin while ita kuma ta zame kasa tana kuka hating him like never before.</p><p>Direct part dinshi ya wuce ko falo bai tsaya ba ya shiga bathroom, bai cire kayan jikinshi ba ya sakarwa kanshi shower wearing clothes, with in few seconds ya jike sharkaf, tsaida numfashin shi yayi for like 20 seconds sannan yayi breathing out loud tare da sakin kuka, he hate his life, only if mufida tasan how much he hate himself da batayi adding salt to the injury ba, yasan he have khadija now amma the guilt still hunts him, dafa tiles dake bango yayi tareda kara sakin sabon kuka.</p><p>Bayan minti talatin ya fito daure da towel, idanuwanshi sun chanza, zama yayi bakin gado tare da yin tagumi.</p><p>Nan ma yafi minti talatin zaune yana tuna halin daya bar mufida ciki, jiki ba kwari ya mike ya dauko short ya saka sannan ya saka white jallabiya Mara nauyi. Fita yayi yq kara komawa part din mufida, kasan tiles ya tardata sai kuka take har muryqnta bai fita, zama yayi nan kasan ya jawota jikinshi sai tirjewa take amma her power is nothing compared to his, danneta yayi kan broad chest dinshi yana shafa bayanta,</p><p>"Baby am sorry... You forced my hands... Kiyi hakuri..." Mufida na kokarin kwace kanta tana cewa</p><p>"Banyi....ka rabu dani....mugu kawai.... Ni ka kyalleni..." Tafada cikin kuka</p><p>"Naji ni mugu ne ...amma baby abinda ya sameni kaddarace Wanda bana fatan ko makiyina ya sama....wallahi khadija is the first gal danayiwa lustful look...itama don na ganta nude...kuma all this is a result of destiny...don Allah ki bar tado wannan maganar... Let's let the sleeping dog lay....pls..." Yafada cikin whisper, cikin kuka mufida tace</p><p>"Don ka ganta naked sai me?... Baka ganin yarintarta?.... Kawai don bata da gata?.... Ai nan gaba in har ta gane abinda kayi mata zaka gane kuranka...." Tafada tana tureshi, murmushi yayi yana kara manneta ga kirjinshi</p><p>"Kar ki damu...zan ajiye kaina cikin heart dinta yanda bazata taba jin haushi na ba... " yafada sounding very naughty, haushi ya kara bata</p><p>"Kuma ka kara rising hand dinka on me wallahi a bakin wannan auren...." Tafada tana kuka, dariya yayi</p><p>"To sorry ban karawa...amma don't insult me again.. Kinga ko ba aure ai ni yayarkine...tunda na girmeki." Ya fda in a funny way, daga kai tayi ta watsa Mashi harara shi kuma ya daga mata gira daya,</p><p>"Muje muci abinci...sai ki zo kan gado ki nunamin how angry you are..." Yafada yana dariya,</p><p>"Lallai ma...ai dakin amarya zaka kwana...kaida kara kwanciya inda nake sai nan da sati daya.. " tafada tana mikewa daga inda yake zaune, dariya ya kara yi</p><p>"Baby you are unbelievable... Just few minutes ago kina zagina kan nayi molesting yarinya...yanzu kuma you are sending me to her...me akyi kenan?..."</p><p>"Ai the deed have been done...so kaje chan Ku karasta...." Tafada ta shiga bathroom, dariya yayi yabi bayanta</p><p>"Hmmm baby kawai kishi ke dawainiya dake...don't worry I understand..." Ya fada yana hugging dinta ta baya. Banza tayi dashi ta tsaya ya cire kayan jikinta sai binta yake da kallon deep down he's greatful for having two youngsters at his beck and call, ruwa ta watsa yana kallon ta amma ko a jikinta, ta gamaya dauko towel ya mika mata ta amsa ta barshi nan tsaye, bedroom ta koma ya bi bayanta, kan dining ta zauna ta bude kaji da drinks, shima zama yayi feeling so hungry for her amma ko kallon shi batayi ta gama ci ta haye gado abinta ta rufe da blanket ta cire towel ta wurga masa ya shafke,</p><p>"Baby yanzu haka zakiyi min?...." Ya fada kaman zaiyi kuka,</p><p>"Hmmm gaskiya bazaa tauye mata hakki ba...it's her night..." Tafada tana kashe bedside lamp. Ahankali ya juya ya ajiye towel din cikin bathroom sannan ya dawo bakin gadon yayi pecking goshinta sannan yace</p><p>"Goodnight sugar...." Banza tayi dashi ya fita ya jawo mata kofa.</p><p>Haka ya Kama hanyan part dinshi yana tafiya kaman Kazan da kwai ta fashewa. Nan falon shiya kwanta har bacci yayi gabadashi.</p><p>The following day tun karfe biyar hayaniyan daake part din dija ya tada dukkan yan gidan. Mikewa yayi yana hamma alaman bacci bai isheshiba. Ahankali ya Mike ya shiga bathroom ya dauro alwallah ya tafi masjid, yana dawowa ya shiga part din mufida ya tardata zaune bakin gado tayi tagumi, gefenta ya zauna ya jawota jikinshi,</p><p>"baby how was your night ?" ya tambayeta yana shafa bayanta, Dan guntun tsoki taja Sannan Tace</p><p>"boring and hectic... Yan uwan amaryarka sun hanamu bacci.... "</p><p>"sorry love... Daga yau shikenan... Kinyi sallah? "</p><p>"no"</p><p>"then tashi kiyi...zanje in Kira a zomin da bus sai breakfast... " yafada yana mikewa. "me zaayi da bus? " ta tambayeshi tana hamma,</p><p>"Wanda zaa maidasu dashi..."</p><p>"OK...." janta yayi ta Mike tsaye, rike mata hannu yayi har bakin bathroom ya bude ya turata ciki yana cewa</p><p>"yi alwallah...zan dawo yanzu...." ya fada mata sannan ya fita. Part dinshi ya koma ya Kira Inda ya sayo abinci ya shaida masu yana bukatan abinci like forty plates sannan ya Kira dad ya fada mashi a taimaka mashi da family bus.</p><p>Dija kam duk fargaban da take bai Hana bacci mai nauyi daukanta ba saidai ta Dan firgita in ta tuna inda take. Itama hayaniyan daake ya tadata , ahankali tasauka daga kan gado ta shiga bathroom saida tayi abinda ya shigar daita ta fito ta zauna kasa tana tunanin rayuwan duniya cikin ranta adua take Allah yasa mafarki tayi jiya don ko a lahira batason zama da wannan mutumin, duk duniya babu Wanda ta tsana kaman shi, in son ranta ne a harbeshi ya mutu kowa ma ya huta don gani take abinda yake wa mutane yayi mata. Wata daga cikin matan da suka rakota ce ta shigo ahankali dija ta daga Kai ta kalleta da swollen eyes dinta, bakin gado matar ta zauna ta Fara cewa</p><p>"Alhamdulillah dija hakika kinyi saa... Allah ya mayarda da yaran mu danshinki... Don ba kowacce yarinya zataci saa dakika ci ba... Don haka ina fada maki kibi mijinki sau da kafa"</p><p>Dija daga Kai tayi ta Kalli matar dake yi mata magana, ji tayi inama zaa iya chanza mata wuri ta koma gidansu akawo wata madadinta don ta gwammace ta koma kan titi data zauna cikin gidan. Haka matar ta dinga bawa dija advice amma abinda take tunani daban don ko a mafarki bazataso yazid sake kusantarta ba, she's so scared.</p><p>Wajen karfe tara aka Fara shiga da abinci side din dija, abinci kala2 da drinks nan suka hau cin abinci, daya daga cikin matan ta kawowa dija abinci amma amsa kawai tayi ta ajiye don ko kadan bata iyaci.</p><p>Mufida hada breakfast tayi su biyu suna zaune a dining table suna cin abinci amma hankalin yazid nakan dija don he's sure bataci abinci ba. Karfe tara da rabi bus yazo da aiken da hajiya babba da hajiya karama sukayi na atampopi da yasa sai perfumes, dadi yazid yaji ya Kara da 100k ya bawa mufida takai masu don yagagara sutafi ko yaga yanda dija ta kwana.</p><p>Karfe goma da rabi suka tashi tafiya nan dija tace batasan zancen ba don ihu ta dingayi ta Kama the last woman dazata shiga motan ta rike gam saikwala ihu take on top of her voice, yazid na tsaye bakin window a part din mufida yana kallon duk abinda ke faruwa jiyake kaman yaje ya kamata amma that will be an act of disrespect, mufida dake zaune mikewa tayi ta zo bakin window Itama tana kallon yanda dija ke rike gam da mata while matar tana kokarin kwace kanta amma ta kasa. Mufida barin dakin tayi ta fita waje zuwa inda dija ke ihu, ahankali takama mata hannu, cikin sauki dija ta saki zanin matar ta Kama hannun mufida tare da daga Kai tana kallon ta da wet face dinta, nan take mufida taji wani irin kaunar dija har cikin system dinta don she looks so innocent akan what's she's going through, batasan lokacin data rungumeta ba, itama dija rungumeta tayi ta kaman her life depends on her. Yazid dake tsaye yana kallon duk abinda ke faruwa lumshe idanuwa yayi tare da dora Kai kan window.</p><p>[6/22, 6:02 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: 💙💚❤💛🧡NA CUCE TA ❤💙💙💜💛🧡</p><p>®zuwairat( ummumaryam)</p><p><br /></p><p> 3⃣7⃣</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> Ajiyan zuciya ya saki "Pls ya Allah let it be like this for ever.... " ya fada yana kallon yanda mufida ya manna dija kan chest dinta tana shafa bayanta, mufida daga Kan dija tayitana kallon how weak, fragile and innocentshe looks, ahankali tadaga hannunta ta gogemata face tana cewa"ko daina kuka kinji?" ahankali dija ta daga mata Kai, mufida mamaki take da bata jinhaushin dija for a bit instead tafi him haushin yazid."kinci abinci?.." ta tambayeta cikin sanyinmurya, Kai dija ta girgiza mata, " to muje kici abinci.... " mufida tafada tana rike da hannunta while going into dijas apartment, Dan tirjewa dija tayi sannan tace" nakoshi.... Gida... Nakeso... Su tafi... Dani.... " ta fada tana kallon bus daya fita daga cikin gidan, "ai yanzu nan ne gidanki.... " da sauri dija ta girgiza mata Kai tana cewa " banso... " tafada tana fashewa da sabon kuka, "hmm ai dole kice bakiso... Don I understand what you went through in his hands...ni naji jiki balle ke? ". Mufida tafada cikin ranta, " bakison zama Dani? " mufida ta tambayeta tana murmushi, cikin kuka dija tace"inaso... " "to kiyi hakuri mu zauna tare kinjiko? " dasauri dija ta gyada mata kai, "to muje kici abinci... " inji mufida, dijabata Kara cewa komai ba tabi bayanta hannunsu rike dajuna. Mufida Kara kallon Falon tayi for the second time tasan yazid ko family dinshi sukayi mata kayan. " kizauna in je in dauko maki abinci... "inji mufida tafada tana zaunar daita kan kujera,"da akwai abinci Chan dakin... Bari in dauko wannan... " dija ta fada tana mikewa, Ahankali ta taka ta shiga bedroom dinta mufida tabi bayanta da kallo tana cewa "maza basu da imani.... " ta fada kasan breath dinta. Dija dauko abinci da aka bata Dazun tayi ta fito dashi kanta kasa, "gashi... " dija ta fada tana nuna mata abincin, amsa mufida tayi ta bude taga it's rice and stew da few slices of plantain,"ki ajiye wannan... Bari in dauko maki wani... " mufida dake maida murfin takeaway din. Amsa dija tayi while itakuma mufida ta Mike tafita daga cikin part din, ajiye abincin dija tayi ta koma tazauna kasa kamar ba matar gidan ba. Mufida na shiga part dinta ta tarda yazid zaune yana ganinta yayi saurin mikewa ya rungumeta, harara ta watsawa bayanshi tana cewa "Wai meye? " Dariya yayi yana cewa "baby you're the best.... ""wato don na nunawa matarka so shine kakejin dadi ko?.. That shows that you care for her happiness more than mine.... " bata idaba ya tari numfashinta yana cewa "you know ba haka bane...kawai am happythat the love you have for me bai rufe maki ido ba.... I love you so much babyna....""naji... " ta fada tana tureshi gefe daya, sakinta yayi ta shiga kitchen yabi bayanta wanting to know what she's up-to, gani yayi tanazuba sauran pepper soup da sukayi breakfast dashi cikin food warmer, "baby ina zaki Kai wannan Kuma? " ya tambayeta dukda yasan it's for dija, banza mufida tayi dashi ta hada tea cikin mug ta ajiye kan tray, ta juyo ta kalleshi, "ka kaiwa matarka.... " ta fada mashi atakaice, murmushi yayi"why not a kirata nan taci... Basai kin Kai mata ba.... " inji yazid, " alright then... " mufida ta fada tana fito da abincin daga kitchen zuwa dining table, kaman walkiya yazid ya fita dagapart din mufida ya shiga part din dija dasallama ya shiga Wanda yasa dija muguwarzaune tare da shan jinin jikinta, bata daga Kai ba sannan bata da karfin halin amsa sallamanshi, maimaitawa yayi amma still kanta kasa Kuma no response karawa yayi for the third time amma bata amsa ba, "khadija.... " da sauri ta daga kanta idanuwanta cike da kwalla don she's expecting her guidance angel not him, "baki amsa min sallamaba... " ya fada mata yana zama kan kujera dake kusa da inda take zaune Wanda yasa jikinshi Dan ta ba nata da sauri ta matsa gaba tana crawling Baisan lokacin da Dariyaya kufce mashi ba don she's acting like taga wani irinmonster, "small baby baki amsa min sallamaba... Koin sake.... " ya tambayeta yana kallon yanda hannunta ke rawa, da sauri ta girgiza mashi Kai alaman Kar ya sake, shuruyayi yana kallon ta, he wants to hear hervoice ko once ne, " baki gaidani ba.... " yafada don yaji abinda zatace, shuru tayi bata daga Kai ba, sai wasatake da crumbling fingers dintakaman ta gudu daga inda take zaune kawai take ji, "Pls baby kigaidani mana... Nifa mijinki ne.... " yafada yana marairaice murya kaman karamin yaro, "kaiba mijina bane... " tafada cikin rantanot knowing its out loud, kallon ta yazid yayi full of surprise "nine na mijinki ba?... " da sauri dija ta girgiza Kai tana fashewa da kuka, shuru yayi yana kallon ta, sai kuka take kamanan doketa, "tashi ki wanko fuskanki kizomuje kici abinci.... " ya fada mata atakaice, da sauri ta Mike tsaye ta shiga bedroom dinta,straight bathroom ya shiga ta wanke face dinta ta fito tayi tsaye bakin kofan bedroom, mikewa yayi "ki taho mana... " ahankali ta taka zuwainda yake tsaye, "ya ciwonki... " ya tambayeta, shuru tayi babu response kura mata ido yayi yanacewa"in bakison mu bata... Duk tambayan da nayi maki ki dinga bani amsa kinji ko? " daga mashi Kai tayi, Kama hannun ta yayi suka Kama hanyan waje, har sun iso bakinkofaya Tsaya ya juyo kawai sai ya mannata ga kirjinshi, nan take ta Fara kuka sosai wanda yasa yayi saurin sakinta "Wai an fada maki wani abu zanyi maki ne?... Ba jiya na fada maki ban Kara yimaki abinda baki so ba?..." yafada sannanya fita daga dakin tana biyedashi sai goge face take da bayan hannunta. Yazid ya shiga part din mufida ya sallamata amsa mashi kusa da ita ya je ya zauna sannan Itama dija ta shigo kanta kasa, "zo kizauna nan.... " mufida ta fada mata tananuna mata kusa da yazid, ahankali ta taka zuwa inda yake zaune amma sai ta zauna kasa"ki zauna kan kujera mana Dan Allah... Kawai sai ki kama zama kasa... " inji mufida, ahankali ta Mike tazauna gefen yazid amma far from him. Yazid kallon dija yayisannan ya Kalli mufida "baby GA kanwar ki... Ai you have seen the way she is... To if you want her to be like this continuesly then take her close to yourself... Kar kibari wata ta shiga tsakaninku... Pls baby...take her as the sister you never had.... " ya fada yana rike da hannunta, "insha Allah... I will try my best... " tafada cikin sanyin murya, kiss yazid yayiwa cheek dinta sannan ya juya ga dija Itama ya kama hannunta, he can feel her trembling amma basar, "small baby... Ya kirata.. Kinga wannan antynki ce... " ya nuna mata mufida sannan yacigaba dacewa "Kar in kuskura inji kinyi mata ba daidaiba... Kome tace kiyi shi zakiyi don nasan bazata sakaki hanya Mara kyau ba..Ki girmamata AI Kinga ba saarki bace don haka Kar inji ko in gani raini ya shiga tsakaninku... Kina jina? " yafada in a soft tune still rike da hannunsu, da sauri ta daga mashi Kai hawaye na rolling "Wai kukan me kike Kuma? " yazid ya tambayeta, da kaman Kar ta amsa amma sai ta tuna maganar daya fada mata sai cewa tayi"gida.... Mu..... Nakeso... " tafadatana Ida fashewa da kuka, da sauri mufidata Mike ya koma wurinta ta Kama mata hannu, da sauri dija ta zare hannunta dagana yazid ta maida cikin na mufida, hawayenta mufida ta goge sannan tace"bakinyi min alkawarin zaki zauna Dani ba?... " "Eh.... " dija ta fada cikin kuka "to kibar cewa gida zaki... Ai nan ne gidanki yanzu kinji" nodding tayi"muje kici abinci kinji dear..." "...to... " tafada sannan ta Mike Damankaman tana zaune kan kaya takeji. Kan dining suka zauna Su biyu while yazid yayi relaxing yana kallon mufida Kuma the more yana jin Sonta na ratsa heart dinshi "hmm inama mata Su gane wannan sirrin..." yafada cikin ranshi. Don abinda mufida keyikoda ba da gaske take ba it's OK by him don hakan na Karamashi sonta cikin ranshi Kuma he hopes it's real. Pepper soup mufida ta bude tatura gaban dija nan ta Fara ci tana shessheka. Yazid mikewa yayi yazo kan dining ya dafashoulder din mufida sannan yace "baby Bari in je in kwanta... Kudinga shiryawa... Zamu wuce after lunch.... " ya fada da mata sannan ya bar Wajen, Hakanya ya bawa dija Daman sakin jikinta taci Tasha ta koshi don she feels free in tana tare da mufida. Yazid na komawa ya Kira hajiya karama yana fada mata ta rokar mashi dad ya amince ya bar dija nan Kano nan hajiya karama tace bata San zancenba, Dan marairaice fuska yayi sannan yace " in barta wajenki mana... Ni wallahi Banason tafiya daita... Nafison hakan...""no... Ka tafi daita kawai shi yafi... "ta sake fada mashi, "yanzu inzo dasu nan gidan kafin mu wuce?" ya tambayeta yana aduan Allah yasa tacekawai Su wuce"let me ask anty... I will get back to you "ta fada mashi sannan ta katse wayan.Load More Pages...</p><p>[6/22, 6:02 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ ˢᴬᴸᴱᴴ: 🧡💛💚❤💙💜</p><p>NA CUCE TA</p><p>💜💙💚💛🧡❤</p><p><br /></p><p>3⃣8⃣</p><p><br /></p><p>Yana tuki suna hira da mufida while yana kallon dija ta mirror, dija ta kurawa waje daya ido tana tunani, ba komai take tunani ba illah daukan dataga yazid yayiwa mufida, abin ya mugun daure mata kai, tambayan da takewa kanta shine Bai taba yiwa mufida abinda yayi mata ba,</p><p>"Killan" ta fada cikin ranta don ta tabbayar da ya taba shayar da ita wannan azaban ko amafarki bazata yarda ya rike mata hannu ba balle ya zagaya hannu ya dauketa kuma ta amince, Dan ajiyan zuciya ta saki tana sake direction din tunaninta zuwa inda zasu, kawai said ta fara aduan Allah yasa gida zai maidata don ko a lahira bata fatan zama 10km to him, kwata2 bata sonshi kusa da inda take, mufidace ta juyo ta kalleta tare da sakar mata murmushi ta sadda kanta kasa batare data maida mata martani ba don wani irin kallon mamaki kawai take mata.</p><p><br /></p><p>Karfe 7 saura suka isa garin abuja, inda ya saba yi masu takeaway duk sanda sukaje outing da mufida ko duksan bayason ta sha wahalan dafa abinci yayi parking, rikewa mufida hannu yayi tare dayi mata kiss a hannun sannan yace </p><p>"Sugar me zakici?..." Ya tambayeta dukda yasan her favourite,</p><p>"The usual..." Tafada tana dariya at the same time tana daga Mashi gira daya, dariya shima yayi yace</p><p>"Daman I know...kawai don in fita hakkinki yasa na tambayeki..." Yafada sounding very romantic, juyawa yayi wearing a lovly smile yana kallon dija da kanta ke kasa don tunda taga ya rike mata hannu ta sadda kanta kasa,</p><p>"Small baby me zakici?..." Ya tambayeta yana wishing ko zata daga kai sama su Dan hada ido amma ko daga kai bata yi ba balle ta amsa Mashi, kara maimaita tambayan yayi Amman no response, mufidace ta juyo daga inda take zaune tace</p><p>"Dear me kike shaawan ci?..." Ta tambayeta cikin natsuwa, ahankali ta daga kai tana kallon mufida tace</p><p>"Babu komai ..." Ta amsa mata in one word ta maida kanta kasa, kallon ta yazid yayi for almost ten seconds sannan ya fita daga cikin motan.</p><p><br /></p><p>After like 25 minutes ya fito da ledas ya bude baya ya ajiye gefen dija sannan ya sjiga suka kama hanyan CBN quarters. Suna shiga gate dija ta bude baki tana kallon new environment dinta don dukda dare ne tamkar rana don wurin kal da haske. Parking lot yayi parking sannan ya fito mufida ta fito, dija kam tana zaune bata fito ba, saida ya bude booth ya dauko bag dinta sannan ya bude mata kofa tayi saurin fitiwa,attitude dinta is so funny and annoying to him and he knows the exact way to stop it. In Baku mance ba I once told you yazid yana da flat a CBN quarters which is four bedrooms and well furnished. To part dinshi ya shiga yana Jan bag dinta, mufida ma shiga tayi while dija na tafiya ahankali tana kalle2 sannan ta shiga ciki. Yazid na rufe kofa ya ajiye bag din ya nufi inda mufida ke tsaye, wani irin hug yayi mata ya baya yana kissing wuyanta, da sauri mufida ta fara cewa </p><p>"Pls baby stop...don't let your wife downgrade me...pls mana..." Tafada ahankali,</p><p>"She won't..." Ya amsa mata yana licking wuyanta, dija ji tayi kaman tayi tsuntsu ta tashi saboda kunya Amman kuma hakan bai hanata kallon su kaman movie ba,</p><p>"Baby pls stop....am begging..." Inji mufida, </p><p>"I miss your body baby... Pls give it to me tonight..." Yafada yana shafa belli dinta da two hands dinshi sannan yadan saci kallon dija ta wutsiyan ido sukayi ido hudu ya daga mata gira daya, da sauri ta dauke kanta,</p><p>"You know sauran six days..." Inji mufida dake kokarin balle hannun yazid daga jikinta, kfa ya fara bubbugawa kaman yaro</p><p>"Pls don't kill me...have mercy sugar...mutuwa zanyi...." Yafada kaman zaiyi kuka kuma loud Wanda yasa dija kara sakin baki. </p><p>"Dear if you love Allah stop..." Inji mufida, da sauri ya balle hannun shi </p><p>"Na bari madame...yanxu wane daki zan kai kanwarki?..." Yafada yana rike da hannun ta, </p><p>"Anyone apart from mine..." Ta amsa Mashi, kiss yayi wa goshinta, </p><p>"You are the best... " ya fada mata sannan ya dauki bag din yana kama hannun dija, mufida relaxing kan wani buoyant sofa tayi tana mai jin dadi sannan tana godewa Allah da mijinta bai wani chanza mata bayan ya kara aure ba dukda tasan he loves dija so much Amman he's trying kar ya bata mata</p><p>"Ya rabbi kasa inci wannan jarabawan... " tafada cikin ranta while tana kallon yazid da dija sunyi wani corridor</p><p> Dija na tafiya jikinta na rawa sabida yanda ya rike mata hannu sanban tana tuna yanda yayiwa mufida, daya daga cikin doors dake inda suke ya bude, taga hadadden daki da komai intact, ajiye bag din yayi yana kallon yanda take kallon dakin, bata ankaraba ya rungumeta, daman hawaye are not that far from her eyes sai kuka, da sauri ya Dora hannu kan bakinshi yana cewa </p><p>"Shush...." Nan take ta hadiye kukan, Dan daga kai yayi yana kallon full boobs dinta da suka fito by force as a result of haihuwan datayi, ahankali ya daga hannun shi daya ya Dora sama while dayan hannun shi na rike da waist dinta, aikam kasa hadiye kukan tayi ta fara kuka tanacewa</p><p>"Dan Allah...." Bata idaba ya kara Dora hannu kan bakinshi yana cewa</p><p>"I said shush...kiyimin shuru tunda baki Iya magana ba..." Yafada yana caressing boobs dinta, cikin kuka ta fara cewa</p><p>"Na...Iya...magana..." Dan saurarawa yayi yana cewa</p><p>"Ni ban shaida batunda in nayi maki magana baki amsa min..." Yafada yana kallon how wet and sexy her lips looks, </p><p>"Na Iya..." </p><p>"Shine nace ni ban San kin iyaba..." </p><p>"Kayi...hakuri...." Tafada cikin kuka, ko kadan bai son ganin tears dinta don it hurts him like hell dongani yake she have cried enough, ahankali ya zare hannun shi daga inda ya ajiye su ya rike shoulder dinta</p><p>"Ki kalleni..." Ya umarceta da sauri ta daga kai ta zura Mashi ido,</p><p>"Kimason inyi maki abinda nayi maki a gidanmu?...." Bai idaba ta kara fashewa da kuka tana girgiza Mashi kai</p><p>"Kina so?..." Kara girgiza Mashi kai tayi</p><p>"To dga yau duk ranarda nayi maki magana baki amsa min ba...to ki tabbatar said nayi maki sau biyar...kina jina?..." Da sauri ta gyada Mashi kai</p><p>"Nafison ki dinga bani amsa da baki bada kai ba..." </p><p>"To..." Tafada tana trembling saboda tsoro. </p><p>"Kuma duk ranar dana ce kiyi abu kika ki yi to ki Sani babu mai hanani yi maki sau biyar... Kinji ko?..." Da sauri race </p><p>"Eh..." </p><p>"Good...yanzu kiyi sauri ki shiga wanka ki sake kaya ki fito waje muci abinci..." Bai idabatace</p><p>"To..." Tana juyawa, bayanta yabi da kallo dariya na Neman kufce mashi.</p><p> Sai da ta shiga bathroom ya fita, dakinsu da mufida ya shiga bayan ya umarci mufida ta tashi tayi sallah. Wanka ya shiga ya rama sallolin da ake binshi likewise itama mufida bayan sun idar mufida ta mike ta bude wardrobe ta fara fiddo kayan yazid dake cikin wardrobe din. Adua ya shafa ya kalleta yana cewa</p><p>"Baby INA zaki kai kayana?..." </p><p>"Your room...." Ta amsa Mashi atakaice, </p><p>"To ba nan bane dakina ?"</p><p>"No...kasan yanzu dole mu raba dakin...we are two now..." Tafada tana ida kwaso sauran, </p><p>"But pls baby da kin bar kayan nan...remember you yourself kinyi complain akan karantan yarinyan nan...so ko kadan ba zaman mata da miji zamuyi ba...it will take sometime kafin wani abun ya kara shiga tsakanin mu... So please don't send me away..." Ya fada kaman zaiyi mata kuka, Dan murmushi tayi tana cewa</p><p>"Baby is not as if am sending you away.... Kawai am doing the right thing..kasan babu ruwan Islam da reasons dinka...nidai raba kwana zaayi..." Tafada tana zipping bag data tura kayanshi ciki, Dan hada kai da gwaiwa yayi for few second sannan ya daga kai yace</p><p>"To naji...na raba one one day...ke kwana daya ita daya..." Yafada kaman baison raba days din, </p><p>"Hmmm dear daya baiyi kadan ba?..." Bata idaba ya katseta dacewa</p><p>"Aa...haka nakeso...kuma about cooking ya zamuyi kenan?... Nasani kuma kema kin San babu abinda zata Iya....ko in sa su mom su samo mai aiki?..." Ya tambayeta, Dan murmushi ta karayi sannan tace</p><p>"Don't worry about that...kawai zamu dinga shiga kitchen tare ina nuna mata what to do..." Ta fada calmly, lumshe idanuwa yazid yayi yana cewa</p><p>"Baby you will do that for me?..." Ahankali ta daga Mashi kai tana cewa</p><p>"Yes dear..." Da sauri ya mike ya rungume feeling so happy and excited, </p><p>"Baby there's no one like you... Baby you are the best...baby I love you so much...baby you are making me the happiest man on earth...Allah yayi maki albarka...indai aljannan yana kafata na daga maki ki shige kawai...." Yafda sounding very excited,</p><p>"Hmmm baby jin dadin na kyautawa matar Kane ko?..." Da sauri ya rufe bakinta da nashi yana kissing dinta in a passionate way, sai da yayi mai isanshi sannan yace</p><p>"Baby it's not like that... Kawai kina surprising dina ne....kina nunamin the real you... Maza da dama basu gane irin halin matan da suka aura sai sadda kaddara ta fada masu...yanzu na kara sanin ko ke wacece...and I love you more because of... Allah ya saki farin ciki fiye da yanda kika Sani...I love you..." Magana ya dingayi har saida mufida ta rufe Mashi baki, daukanta yayi sukayi falo inda suka tarda dija tsaye sanye da blue Arabian gown kaman wacce zata unguwa, bai dire mufida koina ba sai kan dining, dija dake tsaye yazo itama ya dauketa aikam tayi tsuru2 saboda fargaba.</p><p> Ajiyeta yayi kan dining yana dariya cikin ranshi yana cewa </p><p>"Wata rana da kanki zakice in daukeki..." Mufida mikewa tyi don ta jera masu abinci yace </p><p>"Sweetheart just sit and be my guest..." Ya fada mata sannan ya shiga kitchen ya dauko plate, dija dai kanta kasa ko daga kai batayi ba har ya dawo ya jerawa kowa abinci a gabanshi shima ya zuba nashi ya zauna suka fara ci amma dija bata fara ci ba saida suka hada ido ya daga mata gira daya sannan ta maida hankali ta cinye tas ya zuba mata drink tasha. Itama mufida tana gamawa ta mike ta shiga bedroom dinta ta fito da bag da kayan yazid ke ciki ta shiga dashi cikin daya daga cikin bedroom ta jera mashi sannan ta fito ta tarda yazid ya kwace plates yana wankewa, kitchen ta shiga ta rungumeshi ta baya tana cewa </p><p>"Baby good night..." Juyowa yayi ya kalleta yana goge wet hands dinshi da jean dake jikinshi yana cewa </p><p>"Wane good night babu ke kusa dani?..." Dariya kawai tayi ta fito ta barshi har lokacin dija na zaune kan dining waiting ace mata ta mike, wurinta mufida taje ta dafa shoulder dinta sannan tace.</p><p>"Dear sai da safe..." Ahankali dija ta mike tana cewa</p><p>"Anty...wurinki...zan kwanta...." Dariya mufida tayi tana cewa</p><p>"Ina fa...ai dakinki zaki kwanta..." Da Sauri ta girgiza kai hawaye na taruwa tana cewa</p><p>"Dan Allah...wajenki....zan kwanta....tsoro nakeji..." Tafada hawaye da suka taru suna zubowa, kujeran kusa daita mufida ta zauna tana cewa</p><p>"Dear kefa yanzu matar aurece....dole zaki zauna dakinki kuma kibi umarnin mijinki..." Kai dija ta dinga girgizawa kaman agama lizard tana cewa</p><p>"Aa Dan Allah...ni banso....binki zanyi..." Tafada tana fashewa da kuka,</p><p>"Ki bar kuka kinji...tashi kije ki kwanta ..." Aikam dija tirjewa tayi tana cewa</p><p>"Ni wurinki zan kwana..." Mufida mikewa tayi itama dija ta mike tana kuka, mufida na tafiya dija na biye daita mufida juyowa tayi ta fashe da dariya itakuma dija said kara volume din kukanta kawai take, yazid ne ya fito yana goge hands dinshi da wani karamin towel, tsayawa yayi yana kallon su, da Sauri dija ta goge face dinta ita kuma mufida ta shige dakinta. Yazid ne ya karasa inda take tsaye ya sa hannu ya daga jaw dinta, kura mata ido yayi for a moment sannan ya rike mata hannu suka koma falo, zama yayi ya zaunar daita kan kafanshi, sabon hawaye ta fara amma babu sauti, hand dinshi yasa ya goge mata face yana cewa</p><p>" meke damunki?..." Ya tambayeta cikin whisper, da Sauri tace</p><p>"Babu ...komai..." Shuru yayi for a moment sannan ya daga mata face ta fuskance shi,</p><p>"Khadija...." Ya kirata kaman baison magana sannan yana lumshe eyes, </p><p>"Naam..." Ta amsa mashi muryanta na cracking</p><p>"Ki fadamin abinda kikeso inyi maki... Wanda zaisaki farin ciki ki bar zubda hawaye...kome kika fada yanzu nayi maki alkawarin zanyi maki..." Yafada mata sounding very calm, kaman tana jira tace</p><p>"Gida....zan koma..." Bata idaba yace mata</p><p>"Banda wannan...ki fadi wani abun..." still da Sauri tace</p><p>"Boko..." Tafada kaman ana fixgan maganar daga bakinta, shuru yayi yana sauraron abinda tace, few seconds later yace</p><p>"Boko kikeso?..." Da Sauri tace </p><p>"Eh..." Kallonta yayi yana cewa</p><p>"Baby kin taba zuwa makaranta ne?..." </p><p>"Aa..." Ta amsa mashi without delay don his warning bai bar yawo a kunnenta ba, yazid tunani ya farayi yana kallon yanda girmanta yake especially yanzu data taba haihuwa, ajiyan zuciya ya saki </p><p>"To shikenan Khadija... Zakiyi karatu har sai kince ya isheki kinjiko?..." </p><p>"To..." </p><p>"Kiyi min alkawarin duk abinda aka koya maki zaki maida hankali ki koya..." </p><p>"Zan.... koya..." Ta amsa mashi da kyar,</p><p>"To shikenan...." Yafada yana mikewa daita a hannunshi, kofar dakinta ya bude ya direta kan gado, kwantar daita yayi ya tofa mata adua kaman wata yarshi sannan ya jamata blanket ya rage wutan dakin yayi mata kiss a for head ya fita daga dakin missing her like crazy.</p><p><br /></p><p>Dakin mufida ya koma ya tardata kwance lullube da blanket, zama yayi bakin gadon tare da dora hannunshi kan hands dinta dake kan cikinta, ahankali ta bude ido, murmushi suka sakarwa juna</p><p>"Sleeping already?..." Ya tambayeta in whisper, tana lumshe idanuwa ta daga mashi kai sannan tace</p><p>"You should do the same...gobe zaka aiki...." Tafada tana hamma, kura mata ido yayi for a moment sannan yace</p><p>"OK...I wanted us to discuss something... Amma sleep gobe in na dawo daga aiki sai muyi maganar...." Yafada yana kokarin mikewa, ahankaki ta kama mashi hannu tana komawa zaune inda sexy nighty dake jikinta ya bayyana, </p><p>"Tell me mana...am all ears..." Tafada mashi amma ko ji baiyi saboda ya kurawa half naked boobs dinta ido, Dan rufe wurin tayi tare da pinching hannunshi, </p><p>"You were saying?..." Yafada kaman baison magana, dariya tayi tana cewa</p><p>"I said am listening..." Ahankali ya maida legs dinshi kan gadon tare da rufesu da same blanket kaman yanda na mufida ke cikin blanket, </p><p>"Baby I want to make love to you...if you refuses me am definitely not gonna make it till morning... So pls accept me..." Yafada idanuwanshi na kara kankancewa,</p><p>"Baby we are through with this...sauran five days...pls kayi hakuri...besides you said da akwai abinda zaka fadamin..."</p><p>"That can wait....kawai all I want right now is you sugar in my tea...in da zunubi zan roki Allah ya yafe mana...nidai kinsan I can't do this anymore.. Pls...pls... Pls...pls...." Yafada yana matseta a jikinshi, zata bude baki tayi magana ya Dora hannunshi kan bakinta yace</p><p>"Shush...pls...pls...pls...plssssssss....gobe zan kaiki shopping...." Dariya mufida tayi saboda yanda yake magna. Bata kara cewa komai ba ta bashi haddin kai.</p><p><br /></p><p>The following morning sukayi wanka da sallah. Mikewa mufida tayi don shiga kitchen ya rike mata hannu yana cewa</p><p>"Don't worry.. Ki kwanta ki huta...later kuyi abinda zakuci...ni zanyi breakfast a office..." Yafada yana gyara tie dake wuyanshi, </p><p>"OK..." Ta amsa mashi sounding exhausted, gaban mirror ya tsaya yana kallon gray suit dake jikinshi, shi kanshi knows he looks gorgeously breathtaking. Bayan ya gama shiryawa ya je inda mufida tayi relaxing kan gado tana binshi da eyes yayi mata kiss a baki tare da cewa</p><p>"Thanks for yesterday..." Sannan ya fita, dakin dija ya shiga har lokacin bata tashiba amma yana shiga ta bude ido saboda kamshin turarenshi. Bakin gado ya zauna tayi saurin mikewa zaune tare da cewa</p><p>"Ina kwana...." Wani irin dadi yaji don yasan it's a progress,</p><p>"Lafiya lau my little angel...kin tashi lafiya?..."</p><p>"Eh..." Kawai tace atakaice, </p><p>"Ya jikinki?..." </p><p>"Da sauki..." </p><p>"Zan tafi aiki...kiyimin adua...." Shuru tayi batace komai ba cikin ranta tana aduan Allah ysa kar ya dawo da rai</p><p>"Kiyimin adua mana...kice indawo lafiya.. "</p><p>"Ka dawo lafiya..." Ta fada atakaice, murmushin jin dadi ya saki, mikewa yayi don kar yayi late, kiss yayi mata a goshi sannan yace</p><p>"Me kikeso in kawo maki?..." </p><p>"Ba komai..." </p><p>"In kunyi breakfast ki kaiwa antynki maganinki ta balla maki ki sha kinji ko?./."</p><p>"Eh..." Wayanshi ya fiddo ya kanga face dinshi kusa da Nata yayi masu selfie, duk I lahirin eyes dinta waje tana kallon kanta cikin wyan ya dauki hoton which makes her look so astonishing.</p><p>[6/20, 10:29] zuwairat nuhu: Fita yayi ya bar dakin yana saka waya a aljihunshi, duk wanda ya ganshi yasan he's happy.</p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-44190208522084164142021-06-12T13:53:00.003-07:002021-06-12T13:53:31.110-07:00LAILAH-DIZHWAR COMPLETE HAUSA NOVEL<div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-wNg708_ufmU/YMUeC3dvrXI/AAAAAAAAJqA/GAi-QV2cyz0FZnThXb8GnKt7x3TB4QsXgCLcBGAsYHQ/s2048/LAILAH-DIZHWAR.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em; text-align: center;"><img alt="LAILAH-DIZHWAR COMPLETE HAUSA NOVEL" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-wNg708_ufmU/YMUeC3dvrXI/AAAAAAAAJqA/GAi-QV2cyz0FZnThXb8GnKt7x3TB4QsXgCLcBGAsYHQ/w320-h248/LAILAH-DIZHWAR.jpg" title="LAILAH-DIZHWAR COMPLETE HAUSA NOVEL" width="320" /></a></div><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p>*_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(1)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________ </p><p><br /></p><p>Ahankali motar take tafiya kamar ba'a san motsawar ta, motace kirar Rang rover,baka tasha tinted, sai faman kyalli take, haka take tafiya ahankali cikin Layin nasu da yake shimfide,gwanin ban Sha'awa, gidan su ya nufa dake cikin garin *Zamfara State*,Kauran namoda, cikin Yarima Quarters. </p><p> Katan gidan saurautarsu ya nufa, wanda tsananin girmansa yafi karfin a kirasa da Karamin gida saide Mansion.</p><p><br /></p><p>Daidai kofar gidan ya tsaya batare da naga wani ko wata ta zo dan bude masa gate din bah, ya bude da kansa, cikin salo irin nasa ya saka hancin motar cikin gidan, wanda tun farkon shigansa, manyan ma'aikatan gidan da yan aiki suke mika masa gaisuwa duk da ba ganinsa suke bah,amma sanin babu me isar sah da kuma irin yanayin driving dinsa. </p><p><br /></p><p>Saida yayi tafiya me nisa ya isa ga parking space, saida ya dauki lokaci kafin ya gama parking Dinta. </p><p><br /></p><p>Bayan ya gama ya fito, Kafar sace ta fara fitowa sanye da takalmi flip-flops, kafar nan tasa fara tasa da dogayan yatsu tasha gyara tamkar ta jariri. </p><p> Haka ya fito sanye da 3quarter, da riga baka me polo neck. </p><p><br /></p><p>Hannusa rike da waya kirar iPhoneX.</p><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p>Dayan hannun kuma mukulin motar sane. </p><p><br /></p><p>Batare daya kalli duk wanda suke kawo masa gaisuwar bah ya daga wayarsa wanda take ringing, cikin gidan ya nufa yana takunsa cikin kasaita. </p><p><br /></p><p>Kai tsaye part dinsa ya nufa, wanda basaina tsaya ina gayar yanda aka tsara shi bah. </p><p><br /></p><p>Kayan jikinsa ya shiga cirewa bayan ya ajje wayar da kuma key din. </p><p><br /></p><p>ToiToilet ya shiga danyin wanka kasan cewar safiya ce. </p><p><br /></p><p>Ya jima cikin toilet din kafin ya fito yayi shiga cikin manyan kaya, wanda suka masa kyau suka kuma amshi kalar jikinsa.</p><p><br /></p><p>Bayan ya gama shirinsa ya fito ya nufi Part din iyayansa. </p><p><br /></p><p>Koda shigarsa babban falon gidan babu kowa dan haka wata hanya ya nufa be jima yana tafiya bah, ya isa wani falon, nan ya tarda Kuyangi zaune ko wacce da abunda takeyi. </p><p><br /></p><p>Be kula suba ya shige, suna gaidashi, hannu kawai yake daga musu harya shiga cikin dakin. </p><p><br /></p><p>Nan da nan na ciki suka fita, yayin da wata mata wanda a kallah shikarunta sun kai 50,tana xaune taci uwar kwalliya ga lalle hannu da kafa jajir tayi shi, kalar fatarta ba baka bace kuma ba fara bah amma da ganinta kasan tana jin dade, mikewa tayi zaune da murmushi a fuskarta har ana iya ganin hakorin makkah jah, cikin bakintah.</p><p><br /></p><p>Zama yayi gefanta tare da fadin</p><p>_"Hajiya ina kwana? "_</p><p><br /></p><p>_"Lafiya qlau *DIZHWAR*,harka fito bade kanon zaka tafi yanzu bah? "_</p><p><br /></p><p>_"Eh wallahi Hajiya,bana san nayi delay shiyasa, nasan kuma Jafar baya san jira kuma nina dau alkawari"_</p><p><br /></p><p>_"Hakane amma ko karyawa bakayi bah zaka fita bayan kasan bana san kana zama da yunwa"_</p><p><br /></p><p>Kasancewar baya san bata mata rai ko jayayya da ita yasa shi fadin, </p><p><br /></p><p>_"Akira Asiya ta hada min breakfast ta kawomin dakin nan"_</p><p><br /></p><p>_"Yawwah!, ko kai fah bara na kira tah"_</p><p><br /></p><p>_____</p><p> Bayan yan lokuta asiya ta shigo da trey babbah tare da duk abunda tasan Yayan nata yana bukatah. </p><p><br /></p><p>Bayan ta gaida shi ta fara hada masa tana mika masa. </p><p><br /></p><p>Duk cikin gidan babu girkin wanda Dizhwar yake ci daga na asiya saina Mamanshi fulani, haka kuma bame shigar masa daki sai su biyu, sabo da Allah yayi masa kyankyami da tsafta, ko kadan baya san talakawa baya san nakasasshe, haka duk kuyangin gidan da masu aikin gidan babu ruwansa dasu. </p><p><br /></p><p>Bayan ta gama hada masa ya fara ci, suna hira da Hajiya harya gama, mikewa yayi tare da fadin</p><p> _"Hajiya bara in yima su Mami sallama"_</p><p><br /></p><p>Ba'a san ranta bah ta amsa da </p><p>_"Saika dawo Allah ya kiyaye hanya"_</p><p><br /></p><p>Ameen ya fada yana fita daga cikin dakin nata.</p><p><br /></p><p>Kai tsaye bangaran mahaifiyar tasa ya nufa, koda ya isa kannansa ya tarda zaune tare da ita kan gado suna hira da dariya. </p><p><br /></p><p>Ganinsa yasa Asiya da Zakiyyah suka Fito daga dakin suna da da gaidashi. </p><p><br /></p><p>Zama yayi gefan gado yana fadin</p><p> _"Wai dan Allah Mami Na gaya miki Ki daina zama da yaran nan, basu da aiki sai hira"_</p><p><br /></p><p>Kallansa tayi tana fadin</p><p> _"Ni Bana san iyayi, daga zuwanka zaka takura musu, basai anyi hutu bah suke zuwa, kaida yake baka gani ka kyale, bana san takura, babu wanda ya takuraka kaima baka isa ka takura kowa bah"_</p><p><br /></p><p>Shiru yayi dan abun yana kona masa rai, mikewa yayi yana fadin</p><p> _"Naje kano saina dawo"_</p><p><br /></p><p>_"A dawo lafiya ta fada"_</p><p><br /></p><p>Harya fita ganin ranta a bace ya dawo tare da zama kusa da ita yana fadin</p><p>_"Mami kiyi hakuri dan Allah, bana san kina fishi dani, kullum Cikin nunamin fishinki kike"_</p><p><br /></p><p>Murmushi ta danyi kafin tace</p><p> _"Kaima haka Zalika kullum cikin takurawa yarana kake"_</p><p><br /></p><p>_"Toh na daina wallahi, aimin addua saina dawo"_</p><p><br /></p><p>_"Allah ya dawo dakai lafiya"_</p><p><br /></p><p>_"Ameen"_ ya fada yana Murmushin farin ciki. </p><p><br /></p><p>Kasan cewar me martaba yaje gaisuwa gidan wani amininsa yasa be je wajan sabah, cikin mota ya shiga ya nufi Airport.</p><p><br /></p><p>🌸🌸</p><p>______</p><p><br /></p><p>Misalin karfe 5pm, Ta fito daga wani katuwar plaza, hannuta rike da leda, ita da wata kawarta tana gefantah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_"Rauda pls dan rike kin kayan nan ina zuwa"_</p><p><br /></p><p>Wanda aka kira da Rauda ta amsa tare da fadin</p><p> _"Baki da aiki Kullum sai kinyi mantuwa bana san irin wannan"_</p><p><br /></p><p>_"Pls kiyi hakuri mana, wayata fa na manta tana chaji"_</p><p><br /></p><p>Amsar kayan tayi tare da fadin</p><p> _"Allah ya kawo ranar da zaki daina wannan mantuwar taki"_</p><p><br /></p><p>Murmushinta me kyau tayi tare da mika mata kayan ta koma ciki tana dariya. </p><p><br /></p><p>Tana nan tsaye harta karaso tana fadin, </p><p> _"Wallahi na manta ashe na sakata tana chaji kinga kuma na fito na barta"_</p><p><br /></p><p>Ita de wanda aka kira da Rauda batayi magana bah ta mika mata kayan nata. </p><p><br /></p><p>Duk rigar plaza dince jikinsu Red an rubuta sunan plaza din a bayansu,da kuma wando na jeans ajikinsu, sai karamin hijab, sai suka dora dogayan riguna bakake a sama. </p><p><br /></p><p>Rauda da kuma Kawarta Lailah suka tare taxi suka nufi gida. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Kasancewar ba unguwarsu daya bah, saida aka fara sauke Rauda tukun aka nufi Gida da Lailah. </p><p><br /></p><p>Daida unguwarsu dake cikin Zamfara wato *Sabuwar kaura*, Daidai wani gida madaidaici, ana sauketa ta mika masa kudinsa tare da shiga cikin gidan. </p><p><br /></p><p>Tsakar gidan ba babbah bace haka kuma daki biyu ne aciki sai bandaki da kuma kitchen. </p><p><br /></p><p>Zaune take kan tabarma tana tankade gyari. </p><p><br /></p><p>Kasancewar Iyayan nata kuramene, yasa batajin Sallamar da tayi bah sai ganinta tayi. </p><p><br /></p><p>Murmushi tayi tare da ajje garin tana nuna mata da hannu alamun sannuda zuwa. </p><p><br /></p><p>Zama tayi kan tabarmar kusa da ita, tare da janyo laidar, data shigo da ita, ta dauko mayafi daga ciki tare da mika matah, tana nuna mata da hannuntah, </p><p> _"Mamana wannan siya miki nayi sabo da baki dashi, acikin albashina yau an bani, kingani"_</p><p> Ta dauko sauran kudin tana nuna mata. </p><p><br /></p><p>Dadi taji, sai kuma ta nuna mata, </p><p>_"Kudin haya kuma waye xai biya da kika kashe mana su"_</p><p><br /></p><p>Hannunta ta kamo tana murmushi, </p><p> _"Mamana, ina sanku Sosai,duk abunda na samu Nakune, kuma zamu biya kudin haya, lafiya kiyi farin ciki"_</p><p>Tana nuna mata da hannunta yanda zata gane. </p><p><br /></p><p>Dadi Maman taji, ta mike tare da dauko mata abinci, Tana ci tana yima maman hira suna Dariya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(2)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ASALI*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mahaifin Dizhwar wato sarkin Zamfara, Maimartaba,</p><p>*Alhaji Uthman Abdulsalam Shehu*</p><p>Cikin dan garin Zamfarane, yan asalin *Zurmi*</p><p><br /></p><p>yana da ilimin bako da kuma na arabiya, su biyu iyayansu suka haifa shida yayarsa mace, kasancewar shi kadaine namiji shiyasa aka Bashi saurautar garin duk baya so, dan yafi so yayi rayuwarsa. </p><p><br /></p><p>Yakasance yana kaunar yayarsa kuma yana mata biyayyah kamar yanda ya kamata.</p><p><br /></p><p>Tun lokacin kanfin yayi aure yaso Yayar sa *Bilkisu*, ta haihu dan ya barma yaran nata sauratar inya girma, amma har yayi aure Allah be bata haihuwa bah, ita kuma nan garin kano take Aure. </p><p><br /></p><p>Bayan Uthman yayi auran fari ya auri Matar sa wato Hajiya Khadija, wanda suke kiranta da hajiya Babba. </p><p><br /></p><p>Itama har suka shekara, Biyar bata haihuwa, ganin haka yasa hajiya Bilkisu jin tsoro ko atunaninta sune basa haihuwa. </p><p><br /></p><p>Shiyasa ta takurawa Uthman akan ya kara aure. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nan ya auro wata bafulatana yar kauyan su wato Zurmi, me suna *Sakina*,watan Sakina uku gidan sarki ta samu juna biyu, murna wajan Hajiya Bilkisu ba'a magana, kasancewarta yarinya karama yasa take Kula da ita sosai,haka ta buro gidanta ta dawo Zamfara dan bawa Sakina kuwalawa ta musamman. </p><p><br /></p><p>Hajiya Khadijah kuwa bakin ciki kamar ya kashe tah, bata da aiki Kullum Sai Kuma,duk yanda zatayi dan ganin itama ta samu ciki ta kasa hakan ya sa ta shiga tashin hankali, duk tabi ta rame ta lalace kullum cuta. </p><p><br /></p><p>Iko. Na. Allah ashe itama Hajiya Bilkisu tana da ciki jikinta bata sani Bah.</p><p><br /></p><p>Lokacin da cikin Sakina ya isa haihuwa, haka ta samu gata kamar a cinyeta, haka itama Bilkisu farin ciki ganin tana da juna biyu. </p><p><br /></p><p>Nan me martaba ya sanar musu cikin su duk wanda ya riga haihuwa to dansane sarki. </p><p><br /></p><p>Haka Kuwa akayi, Sakina ta fara haihuwar danta namiji, gaba daya saida gari ya dauka kowa cikin farin ciki, sarki kuwa murna da shaagalin da aka sha bashi da adadi, ranar suna yaro yaci *DIZHWAR (strong)*,</p><p><br /></p><p>Bayan wata biyu da haihuwar Dizhwar Hajiya Bilkisu ta haihu itama, sai Allah ya bata Namji, ranar suna yaci Suna Jafar. </p><p><br /></p><p>_____</p><p>Lokacin da yara suka isa yaye, Hajiya khadija ta dauki Dizhwar tare dayin alkawarin ya zama dantah, nan kuwa Sakina ta barmata shi, haka ya zauna awajanta tun daga yaye, ta nuna masa gata iya gata tamkar ita ta haifeshi, har Dizhwar ya zamana baya yarda da kowa sai ita ita ce mamansa haka itama Sakina bata tafa fada masa bah duk da ba wajanta yake zuwa bah. </p><p><br /></p><p>_____</p><p>Bayan Hajiya Sakina ta yaye Dizhwar wanda suke Kira da yarima,da shekara uku tukun ta kuma haihu, amma wannan karan saita haifi mace, ita kuma aka saka mata Aisha, sunan kakarsu kenan ake kiranta da Humaira. </p><p><br /></p><p>Cikin ikon Allah bayan Humaira ta girma dan wajan shekararta bakwai, sai lokacin Allah ya bawa Hajiya Hadiza rabu, nam kuwa ta shiga murna da kuma farin ciki, haka tayi ta rainan cikin nata,da ciki ya isa haihuwa ta haifo yarta mace, duk da ba haka taso ba amma tayi farun ciki sosai, ranar suna yarinya taci Suna Zakiyyah. </p><p><br /></p><p>Nan ta dauki san duniya ta dorawa Zakiyyah da Dizhwar tamkar yarantah,saide kama data babbantah. </p><p><br /></p><p>Tun daga lokacin bata kuma haihuwa bah, haka itama Sakina haka kuma itama sakina. </p><p><br /></p><p>Dama hajiya Bilkisu tun daga kan Jafar bata kara haihuwa bah. </p><p><br /></p><p>Zakiyyah ta fara dan tasawa, Maimartaba Uthman ya kuma yo amarya, yar gidan Abokinsa, nan kuwa yarinya tazo ta mallake gida, sauran matan saisu kwana biyu basuga me gida ba Amarya ta boyeahi, sam! Sakina bata nuna damuwa bah, </p><p> Amma Hajiya babba wato Hadiza saida ta shiga ta fita ta raba kowa da mijin sai ita haka suke ta faman Wani kamar gasa da asiri tsakanin su biyu hajiya babbah da kuma Amarya. </p><p><br /></p><p>Ita kuwa Fulani ta koma. Kamar ba matar shi bah haka taci gaba da hakuri cikin gidan, in har zaizo. Wajanta saide a boye kasan cewar yana kaunarta kuma duk. Asirinsu be hanashi Zuwa wajan ta bah. </p><p><br /></p><p>Cikin wannan hali ta samu Juna biyu, mamaKi duk ya kamasu, nan kowacce ta karama tawadarta ruwa, dan basa kunar fulani ganin ta fisu Komai,</p><p> Tunda ta samu ciki Harta haihu,babu ruwansa da ita dan kusan tare suka haihu da Amarya, haka suke Zaune cikin gidan nan, Hajiya bilki ce take kaunarta ta share mata kukanta. </p><p><br /></p><p>Da yar ya saka ma yarinyarta suna Asiya, ita kuma yar Amarya taci suna Farida. </p><p><br /></p><p>Tun daga lokacin babu wanda ya kuma haihuwa cikin gidan. </p><p><br /></p><p>Sarki babu ruwansa da Sakina da kuma.</p><p> Part dinta haka take Zaune, har yarna nan suka girma, koda aka tashi Bikin Humaira ita da Bilkisu suka mata komai Amma Shi babu hannunsa ciki.</p><p><br /></p><p>Shikuwa Yarima yana kasar waje yana karantunsa, harya gama, ya dawo. </p><p><br /></p><p>Har wannan lokacin Hajiya sakina haka nan take zaune gidan sarki Amma babu ruwansa da ita. </p><p><br /></p><p>Shima Dizhwar besan Sakina bace babarshi bah saida Jafar ya gaya masa,dan ganin yanda ya tsanetah kuma ya rainata tah, yayi nadama sosai. Haka ya dawo ya bata hakuri, amma ko kadan Hajiya babba bataji dadi bah. </p><p><br /></p><p>Amarya samira kuwa duk duniya babu wanda take kauna kamar Dizhwar shikuwa ko wajan ta baya zuwa balle ta gansa, amma kullum Bata da aiki sai Lekensa da kuma. </p><p> Kalan sah hotunan</p><p>Sameera babu ruwanta da Hajiya babbah hasalima. Babu wajan wanda take zuwa, sukuwa yaran sun hade kansu yan matan,Zakiya ce yayarsu kuma tana san Fulani, amma Farida ko part din Kowa bata zuwa kullum Tana wajan su. </p><p><br /></p><p>Allah yayi mata girman kai raini da kuma rashin kunya irin na mahaifiyarta, ga san yawo. Kullum cikin gantali yau tana can kasar gobe tana can, sai tara kwayan banza, ita kuma. Babarta kullum cikin fegen dan mijinta take, bata da buri daya huce ta kasance tare da Dizhwar, haka zalika ta kudiri Niyar duk wanda Dizhwar yake tare da ita saita kashe tah, shiyasa ta kaisa wajan boka babu wata mace da take burgesa a duniya gashi yana da farin jini amma. Babu wanda ta masa shi kansa yana mamankin hakan. </p><p><br /></p><p>Sukuma. Matan suna ganin kamar girman kansa da kuma. Ji da mulkinsa yasa yake. Musu hulakanci. </p><p><br /></p><p>Babu sunan daya tsana a. Kirasa kamar yarima dan baya san sarautar shima gani yake Kauyan cine da kuma bata lokaci. </p><p><br /></p><p>Shiya basa shiri da Abbansa, shi ko. Kadan ma. Baya san zaman garin, dade shine yake takurawa saiya gansa a gida. </p><p><br /></p><p>Babu wanda Dizhwar yake kauna sama da Jafar dan gidan Hajiya Bilkisu, yana kaunarsa yaro. Me hankali nutsuwa da kuma ilimi yana sansa. </p><p><br /></p><p>Haka. Shima me. Martaba yana kaunar Jafar, din, dande alkawarin daya dauka na dyk wanda aka haifa shine sarki amma da Jafar zai sa, yasan yayarsa bazata taba yarda bah. </p><p><br /></p><p>Ita kuma Hajiya babbah so take a hada jafar aure da Zakiyyah. </p><p><br /></p><p>Yayin da shikuma Jafar baya san ta ko kadan dan bata burgeshi. </p><p><br /></p><p>Wannan shine cikakken labarin Dizhwar.</p><p><br /></p><p>🌸🌸</p><p><br /></p><p>________</p><p>*LAILAH*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asalin iyayan lailah yan garin Zamfarane itama suna zaune acan wani kauye wajan hanyar fita daga garin.</p><p><br /></p><p>Mahifinta muktar, shi kadai iyayansa suka haifa, ya kasance yana da lalurura ta rashin ji, amma in akayi magana da karfi yana ji, lokacin da ya taba fadawa rijiya yana yaro tun daga lokacin jinsa ya dauke gaba daya, kasancewar kauyene sosai basu dauki wani mataki bah yana ji yana gani ya rasa ji ko kadan. </p><p><br /></p><p>Haka yake rayuwarsa yayin da jama ke. Masa dariya suna kuma hulakantashi da masu zaginsa dan baya ji. </p><p><br /></p><p>Ganin haka yasa yabi wani abokinsa Rabi'u almajiranta cikin Gusau, </p><p><br /></p><p>Allah da ikonsa suna kara,suna yar Sana'a har Allah ya buda masa, yana, suna aiki,Suna samu har Rabi'u yayi aure, kasancewar Muktar yana da san yara shima yana san yin auran amma yasan babu me auransa haka, shiyasa ya hakura.</p><p><br /></p><p>Suna nam zaune cikin gusau,suka samu wani aiki cin nan zamfara sai suka dawo na da zama, haka suke ta aikinsu har matar Rabi'u ta samu ciki, bayan ta haihune suka zo ganin gida da ita, nan kuwa Muktar ya hadu da Maimuna kurma, ita kuma tun da aka haifeta bata ji dama, gashi babu inda zaka kushe tah, kyakkyawar bafulatana, amma babu ji. </p><p><br /></p><p>Nan kuwa soyayyah ta kullu. </p><p><br /></p><p>Kasancewar itama wajan kishiryar babarta take babu uwa ba uba nan ta aurar da ita, haka. Nan babu wani abun arziki, haka tabiyo Muktar babu wani gata ya tafi da ita. </p><p><br /></p><p>Shikuwa yana san matar sah, haka. Suka zauna a wani daki daya a gidan Rabi'u, amma bata jin dadin zaman gidan sabo da ta koma me bauta ita takeyi komai a gidan gashi ta takura mata. </p><p><br /></p><p>Tana so ta gayawa mijinta amma in yana nan bata nuna mata wani takura, shiyasa yake kara girmama Tah. </p><p><br /></p><p>Suna nan har ogan Muktar ya bashi gida sabo da yana jin dadin aiki dashi rukan amana da kuma aiki tukuru, ganin haka yasa Matar Rabi'u shiga damuwa dan za'a dauke mata yar aikin tata data maida tah. </p><p><br /></p><p>ita kuwa Maimunatu farin cikine ya cikata duk da ba fada zatayi bah. </p><p><br /></p><p>Bayan sun tashi, suka sake shimfida wata sabuwar rayuwa da soyayyarsu, dama tana da ciki sanda suka koma, basu jima da komawa bah ta haifi danta namiji, suka saka masa Aminu. </p><p><br /></p><p>suna kula dashi sosai gashi shiba kurma bane, suna ta murna amma basa jin yan gwarancinsa da yake saide suyi ta kallansa, gashi in yana kuka baji suke bah, haka suke zaman saide in yana kusa da ita, nan ya fara girma har yakan iya nuna hannu in iyayansu suna magana. </p><p><br /></p><p>Shekarar sa uku ta kuma haifar namiji, suka saka masa Ahmad,yamafi Aminu kyau sosai, shima lafiya qlau ba kurma, Bane,haka yana aiki yana samun kudi dan bashi da buri daya huce yaransa suyi karatu,dan yana sha'awar ganin mutun me,Ilimi,</p><p><br /></p><p>bayan sun dan tasa sun shiga makaranta ta kuma haihu aka saka masa,Aliyu,shine yaso yaya su amma yana ji duk da haka, tun daga lokacin basu kuma haihuwa bah, nan suka tsaya dan nunawa yaransu kulawa sosai, babu ahunda suka rasa gata iya gata suna samu, dan Muktar makarantar kudi duk ya saka su arabi da buko.</p><p><br /></p><p>kullum shine zai kaisu makaranta ya dauko su, gaba dayansu sun iya maganar kurame, amma abun yana damun aminu, nan ya sanar da iyayena nasa akan Babansu ya daia kaisu makaranta yara suna tsokanarsu ama ce musu yaran kurame. </p><p>Abun be musu dadi bah, haka suka daina kaisu saide shiyaja kannna sah. </p><p><br /></p><p>Muktar yana ta fadi tashi har yaran suka tasa suna karatu, bayan Aminu ya shiga Secondary, matsa ta fara kunnowa Muktar dan ya ragr samun kudi ba kamar da bah, amma haka ya. ki. nunawa kowa, aiki babu dare babu rana dan wani. zubin baya kwana a gida, gashi gidan da aka basu ba. kyauta bah, haka yaci gaba da aiki yana biya musu kudin makaranta, har Aminu ya gama secondary lokacin kargin Muktar ya fara raguwa sosai dan yana da ciwan siga. </p><p><br /></p><p>Duk da haka baya gajiyawa wajan aikin dan ya rufawa yaransa da kuma. Matarsa asiri dan yana ganin in suka zama wasu nan gaba sune zasuyi farin ciki. </p><p><br /></p><p>Nan abokin Aminu yayi masa hanya yake zuwa kasuwa kuma yana karatunsa, amma shi zuciyarsa ba irin ta maifinsa bace bashi da ra'ayin yin alheri, ko. Iyayan basu da kufi ko babu abinci baya bada kudi saide in sun samu yaci, wani. Lokacin azumi suke dan abincin ya karu subawa yaran nasu suci. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin ikon Allah Muktar baya gajiyawa da abunda yake, saiga wata haihuwar Allah ya basu ya mace, ga kuma halin da suke ciki, haka suka amsheta hanu bibiyu dama suna san yar budurwa, nan aka saka mata Lailah. </p><p><br /></p><p>ita kam. bata zo. lokacin jin dadi bah, shiyasa gatanna kamar yar tsana, tana da kyau dan tafi kowa kyau da haske daga yayyanta har iyayyantah. </p><p><br /></p><p>Nan itama ta kuma karuwa, kumai ya karu gashi,kudin makarnatr tah da kuma kaya da abinci, ganin nauyin yayi mai yawa yasa ya Samu Aminu ya rokeshi dan ya taimaka ya dauki nauyin karatun Lailah tunda yarinya ce, kuma Yana da halin yin hakan, amma ya nuna bazai iya bah in aka takurashi zai bar gida. </p><p><br /></p><p>Nan suka hakura aka rabu dashi, nan suka camzawa sauran makaranta dan bazasu iya bah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Akwana atashi ba huya wajan Allah, kullum kaga muktar jiya iyau duk ya rame duk da karamin jiki garesa. </p><p><br /></p><p>Gaba daya yaransa sun gama karatu dan Lailah kanta ta kusan gama Secondary school tana Ss2 lokacin. </p><p><br /></p><p>Gana dayansu sun samu aiki, danshi Yanzu Aminu babban Lawyer ne vikin garin Zamfara, dama ga yanda halinsa yake daya auri mata irinsa saita kara canza masa ra'ayi, baya san yan uwansa haka gidansu su baya zuwa har yaransa da kuma matarsa data tsani Iyayansa. </p><p><br /></p><p>Haka shima Ahmad soja ne ahikuma dama ba'a gida yake zama bah yana kaduna, saiya jima bezo bah inba uban bane ya neme su, sai suzo gidan matarsa su jima amma bazai zo gida bah, dan yaranshi biyu bama susan kakan subah dan ba'a zuwa dasu.</p><p><br /></p><p>Aliyu shine beyi aure bah, amma baya Katsina yana Sakoto yana kara karatu, koda ya tashi zuwa gida, gidan Aminu yake zuwa baya sauka a gida, gaba faya sunyiwa iyayan nasu butulci. </p><p><br /></p><p>gaba daya gidan ya watse babu kowa sai Lailiha da iyayantah, ita kuwa duk duniya babu wanda take so sama dasu bata da buri daya huce tayi karatu ba saka iayyanta cikin farinciki ta jiya musu dadi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan sun shiga Ss3 an fara batun exam, babu kudi gashi yayanta babu wanda bata da numbersa amma bata rokonsu babu ruwanta dasu sabo da basa kaunar ta ita da iyayansu. </p><p><br /></p><p>Kudin exam da Aka tara mata, baban ya kwanta cuta ta dauko tayi amfani dasu ba'a sanin su bah. </p><p>bayan ya dagi ya wararke,yake ta faman murna atunainsa yaransa ne suka biya komai dan ina zasu samu kudi haka. </p><p><br /></p><p>nan Maimunatu ta sanar masa abunda Lailah tayi,kuka ya kama yana mata fada, </p><p><br /></p><p>Lailah in tana gida kurma take komawa dan bata magana saide tayi yanda suke saide in ta fita waje wajan kawanta. </p><p><br /></p><p>Nan ta nuna masa batasan komai bata san karatun ma, ita su take so, bata so ta rasasu, in ya mutu ina zata waye zai riketa ita da mamanta. </p><p><br /></p><p>Ba karamin tausayi ta basu ba shiyasa suke kaunarta kullum shiku mata Addu'ar samun ci gaba. </p><p><br /></p><p>Nan Baban ya shirya da kansa in ka gansa kamar almajiri kayansa, ya nufi wajan Aminu danya taimaia. mata ta zana jarabawar kar a rufe registration din. </p><p><br /></p><p>kwanna sa uku yana jera zuwa amma baya samun ganinsa, gashi duk nisan wajan haka ya ke zuwa a kasa dan ashi da kudin motah. </p><p><br /></p><p>Koda ya sameshi rana ta hudu zai tafi meeting Abuja. </p><p><br /></p><p>yana ganinsa cikin bacin rai ya karasa wajan wasa yana nuna masa, Mai yasa yazo!?,bazai sa yazo ba shi baya san ganinsa a kofar gidan sah, in yana bukatar abu ya kirashi yaje, nan ya nuna masa macin ransa, haka ya juya zai tafi, ya dauko dari biyar ya bashi ya hau mota, haka ya amsa ya nufo gidan a kafa duk ya gaji ga ciwon kafa, ya nunawa Maimunatu ya gaya mata abunda sukayi musu, kuka tasa tana mamaki irin halin yaransu ace sun haifesu da cikin su amma suke wulakantasu haka. </p><p><br /></p><p>Duk abunda ake lailah tana lafe tana jinsu dan haka,ta amshi dari biyar din nan ta ajje ta awajantah. </p><p><br /></p><p>Nan ta nufi makota gidan wani Alhaji me kudi, yaa da mata daya da kuma yara uku, Yaseer shine babba sai kuma kan nan sa mata guda biyu, Yasmin da yusra. </p><p><br /></p><p>Kasancewar me gidan dan bokone, shiyasa suke da karya da kuma iyaye, sun tsani Lailah musamman da sukaji Yaseer din yana santa, har mahaifiyar tasu bata santa, nan ta shiga ta rikesu dan ta dinga musu aiki zasu ara mata kudin jarabawar in tayi aiki zata biya su. </p><p><br /></p><p>amma Mommyn taki yarda dan haka, ta hakura har zata tafi sai kuma ta kirata tace zata ara mata amma bazata musu aiki ba, zata biyata kudin tah da zarar sun gama jarabawar tasu. </p><p><br /></p><p>Nan ta yarda tana murna da farinciki, ta ara matan. </p><p><br /></p><p>Ita bata san Yaseer din amma yana kaunarta har zuwa yake duk sanda yake gari daye ba anna yake karatu bah yayi. musu alkairi, ya kuma kawo Mata tsaraba, shine yama sai mata waya itama da er ta amsa saida taga ran Maman ta ya bace. </p><p><br /></p><p>Nan ta ara ta biya, cikin ikon Allah sukayi jabarawa suka gama dan,bata da hanyar ci gaba da ajje result din tah, nan ta samu wani me katin unguwarsu yayi mata hanyar fara aiki a wani babban Plaza dake garin Zamfara, gkasancewar sunga tana da hankali da kuma tsafta, gata kyakkyawa suka dauke tah, duk wata 10k ake Biyan ta. </p><p><br /></p><p>Da wannan kudi take alfari sune komai. Nata, allah ya taimketa, ahakan take hiya bukar ta dasu, nan da nan ta biya Mommy kudin ta harda na ruwa ta dora mata, itade ta biya tah, yan huka gidan da suke ciki take san ta siya, tana ta biya ahankali, saura 45k ta gama biya ya zama mallakinsu. </p><p><br /></p><p>Duk wannan abu da ake ciki babu ruwan su Aminu haslima sun manta da wani maganar Iyayansu da yar uwarsu. </p><p>ita kuwa intintinta ta samu kudi ta yima iyayanta, sannan ta da kudirin hukanta yayanta kamar yanda suka mata, saita nyna musu basu da hankali, har yanzu tana rike da wannan dari biyar din, tana jiran ranar da Allah zai hada ta da Aminu saita hukantatshi da kudin nan, dan ita har duniya ta nade yai alkawarin bazata taba jusantar inda suke bama. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR* 🤴🏻🌼</p><p> *🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷*</p><p> *ZAINAB NASEER SARKI*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*VaWattpad@Zeenaseer01*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(3)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*CIGABANA LABARI*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan an kai Dizhwar airport jirgin kano ya nufo, dan inyazo kwana zasuyi sannan su koma Zamfara.</p><p><br /></p><p>Cikin lokaci marar yawa suka iso kano, koda ya sauka a Aminu Kano international airport, tym din da jirgin su Jafar zai iso bashi da yawa, zama yayi cikin daya gada cikin kujerun airport din yana jiransa yayin daya ciro wayarsa yana dubawa. </p><p><br /></p><p>Agogan hannusa ya duba tare da mikewa tsaye yayi wata hanya. </p><p><br /></p><p>Daida wani waje ya tsaya yana kallan agogan hannunsa, daga kan da zaiyi ya hango Jafar din ya nufosa yana murmushi. </p><p><br /></p><p>Dadi yaji tare da karasawa wajansa sukayi masabaha, kafin su rungume juna. </p><p><br /></p><p>_"Mutumin gida fa ya amsheka wallahi kafi kyau yanzu"_ </p><p> Jafar ya fada. </p><p><br /></p><p>Tsaki Dizhwar yayi tare da nufar hanyar fita daga wajan yana fadin</p><p> "Ina wani dadi kullum. Mutun yana cikin takura, ni wallahi komawa zanyi kawai bana san bacin ran Abba ne"</p><p><br /></p><p>Shide Jafar babu abunda yace, haka suka karasa har inda motar take, kasan cewar Jafar bashi da girman kai kamar Dizhwar, nan yayi ta gaisawa da mutanan da suka zo tarbar su har mota uku, sanin Dizhwar baya yarda wani driver ya tukasa aka bar musu mota daya da Key ciki, shiga yayi, yayin da Jafar ya zauna gefan sah, ya jasu,shiru babu meyin magana cikin su. </p><p><br /></p><p>Gidan Hajiya Bilkisu suka nufa dake, GRA, koda isar su aka bude musu gate din suka shiga. </p><p><br /></p><p>Bayan Dizhwar yayi parking cikin gidan ya nufa,batare daya kula kowa bah, dakinsa ya shiga yayi wanka ya canza kaya tukun ya fito ya nufi part din Umma, (hjy bilkisu) kenan. </p><p><br /></p><p>Tana xaune a falo, ganin Dizhwar yasa ta mike tsaye tana murmushi, ta taryoshi ya zauna kusa da ita tana fadin</p><p> _"Munyi waya da Sakina take cemin tun dazo ka taho, hala saida ka jira dan uwan naka kuka taho tare kenan?"_</p><p><br /></p><p>_"Umma ai dama shi nazo tarba, shiyasa ban nufo nan kai tsaye bah, mun sameku lafiya?"_</p><p><br /></p><p>_"Lafiya qlau wlh, ina shi sarkin nawar yake kuzo kuyi lunch nasan kuna jin yiwa"_</p><p><br /></p><p>Dan kwantar da kansa yayi jikin kujerar ya lumshe ido tare da fadin</p><p> _"Wallahi kamar kin sani kuwa, dan nayi missing girkin ki, shi me Martaba baya yima mutane uzuri wallahi bani san zaman Kasar nan"_</p><p><br /></p><p>_"Haba Dizhwar, kaida ake fatan ka zamu shigoba nan gaba kace aa, wallahi ka rage wanann rigimar taka gwarama ka saba da kasarka mahaifarka, bana san fitina"_</p><p><br /></p><p>Batare daya ce mata kala bah, yaci gana da danna wayarsa yana kara hade fuska. </p><p><br /></p><p>Yana nan zaune har Jafar ya fito, bayan sun gama gaisawa da mahaifiyar tasa abincin tayi musu serving da kanta, zama sukayi suna ci suna dan taba hira amma banda Dizhwar da yake ci yana danna waya. </p><p><br /></p><p>Ranar de babu inda suka je, dan anan suka kwana sai washe gari tukun Zasu huce Zamfara. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>________</p><p>Lailah kuwa, yau tunda ta tashi da zazzabi ko aiki bata samu ta fita bah sai Rauda ta kira ta sanar ma. </p><p><br /></p><p>Tana kwance har yamma tayi babu inda taje, da er ta fito danyin wanka, tana tsaye a tsakar gida sanye da zani da hijab ajikinta, tana yima Mamanta magana, da hannu kamar yanda ta saba. </p><p><br /></p><p>Da Sallama Yaseer ya shigo cikin gidan. </p><p><br /></p><p>Amsa sallamar tayi batare data juya bah dan tabbas tasan shine shiyasa bata san ko gidansu ya dinga shigowa. </p><p><br /></p><p>Mama ce ta shiga mai magana da hannu tana dariya. </p><p><br /></p><p>har kasa ya durkusa ya gaida tah. </p><p><br /></p><p>itakam Laila wani haushine ya kamata. </p><p><br /></p><p> Yaseer farine saurayi kyakkyawa ga san jama'a, fara'a da kuma kyauta, yana da tausayi musamman ga marar gata. </p><p><br /></p><p>Nan yasa aka kawo musu kayan abinci da kuma makulashe masu yawa. </p><p><br /></p><p>Nan mama ta shimfida mai tabarma ya zauna, shima kuwa harya iya maganar kuraman, yana ta tambayarta ya suke, ina kuma Baban yake. </p><p> Itade Takaicine ya isheta ta shige bandaki danyin wankanta, har kuka tayi dan bakin ciki, ita bata sanshi gashi yan uwansa da iyayansa basa sansu ita kuwa mezai sa ta hada zuri'a dasu, duk dan sabo da iyayanta kuramene. </p><p><br /></p><p>ta jima kafin ta fito, koda ta fito fuskar nan a hade ta shige daki, shikuwa kansa yana kasa, yana san Laila ko makaranta ya tafi kullum cikin tunaninta yake yana san taimaka mata amma bata sanshi, hakan yasa take masa kurjina yake kuma tsoranta ma. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta jima kusan awa saya tana saka kaya, kafin Maman ta saka ta ta fito. </p><p><br /></p><p>Zama tayi kan tabarmar tare da gaida shi. </p><p><br /></p><p>Cikin jin dadi da murmushi a fuskar sa ya amsa yana tambayarta ya bayan saduwa,</p><p>Shiru tayi masa, yayin da shima ya rasa abunda zaice mata. </p><p><br /></p><p>_"Lailah kamata yayi iya dadewar da mukayi dake mun fahimci juna, na gaya miki ni sanki nake kuma auranki nake san nayi, kuma da kike maganar na mayar daku almajirai ina kawo muku sadaka, wallahi koda ace babu ke, ni zan iya taimakawa su Baba, amma bana san irin wannan fahimtar da kike yimin"_</p><p> ya fada yana me marairaice wa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Saida aka kusan mintina goma kafin itama tace dashi</p><p> _"Tun ba yauba na gaya maka, bana san ka dinga hada kaina dakai, ni bazan iya auran kaba sabo da danginka da kuma Yan gidanku basa kaunar talakawa, musamman iyayena da suke nakasassu, bana san sabawa iyayena, in har da gaske kana sona, toh ka daina duk abunda kake mana, kuma kabar shigowa gidan nan, dan hakan yana jamin matsala in kai baka sani bah"_</p><p><br /></p><p>Shiryu yayi yana ganin kamar abunda bazai yiyu kenan bah, </p><p>gyara zamansa yayi cikin fuskar tausayi ya kaleta tare da fadin </p><p> _"tabbas duk abunda kike so nima ashi nake so, kuma insha Allah dukkan abunda kikeso shi zanyi miki, inde hakan zai saki farin ciki na amince na yarda_</p><p>_"Dan Allah nima inason wata alfarma guda daya a wwajanki, ko a sati sau ukune ki taimakamin ki dinga daga wayata, bakisan hali danake cikibah hala Lailah? "_</p><p><br /></p><p>Shiru tayi dan wani Bakin ciki yake Kara mata. </p><p><br /></p><p>Haka yayi ta magana amma tayi banza ta kwale shi, har ya gaji ya mike yasa takalminsa kamar yayi kuka yayi mata sallama, dan yanda yake ji ko Sallama be yima iyayan nata bah ya fice. </p><p><br /></p><p>Tsaki tayi ta shige daki, dan har taji cutar ta huce dan tsabar takaici. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Haka Yaseer ya koma gida jikinsa duk babu dadi dan yanda yake ji ma kamar yayi hauka, ya rasa wani iri so yake yima Laila amma taki fahimta yana ganin kamar harda yarinta nan gaba zata gane hakan, amma bazai iya jurewa ya hakura da ita bah, zaici gaba da yima ta yanda take so har Allah yasa ta fara Sanshi. </p><p><br /></p><p>Cikin gida ya nufa, dan babu abunda yake Sha'awa yanzu illah ya gansa ya kwanta ya huta da wannan takaicin, in yayi bacci ko yaji dadi. </p><p><br /></p><p> Dakinsa ya nufa kai tsaye dan ya kwanta din,</p><p>Ga mamakinsa yaga Saudat zaune kan kujera a falonsa tana jiransa. </p><p><br /></p><p>Kallo daya yayi mata ya nufi bedroom dinsa. </p><p><br /></p><p>*Saudat*</p><p>{Yar gidan yayan Daddyn suce ake san ayi mata auran zumunci dashi, yayin da shikuma baya kaunarta ko kadan} </p><p><br /></p><p>_"Yaya, tun dazu fa nake anan ina jiranka, ina ka tafi?"_</p><p> Ko kallanta beyi bah ya shige dakin sa, tare da saka key, </p><p> dan yasan halinta, zata iya binsa ciki, dan bata da kunya. </p><p>nan ta kubura baki, ta fita daga dakin kamar zatayi kuka. </p><p><br /></p><p>Falon Mummy ta nufa tana kuka, da shigarta ta samesu duk zaune suna kallo,nan suka hau tambayarta ko lafiya. </p><p><br /></p><p>_"Mommy ni wallahi nagaji da wannan wulankacin da yaya yake min, kamar ba mijin dazai auri ni bah, wallahi zan kira Baffana in gaya masa kawai a fasa auran"_</p><p><br /></p><p>Ita kuwa ganin Saudat yar masu kudi, dan Mommy tana ganin inya rasa ta bazai samu wanda takai taba shiyasa take san ayi ayi,ai auran. </p><p><br /></p><p>_"Kwantar da hankalinki, shi ya isa in gaya masa ga baunda nake so yace ba haka bah, barshi a mai uzuri zai iya yiyuwa ko dan ya gaji a hanya"_</p><p><br /></p><p>Tsaki tayi ta mike ta koma cikin dakinta tana gunguni. </p><p><br /></p><p>Kanwar sace Salima tace da Mommy,</p><p>_"Wallahi Mommy babu wani gajiya, kinsan me akayi, dazu ladi ta fita tagansa ya shiga gidan su Laila, har abubuwa taga ana shiga dasu cikin gidan, kinga kuwa ai ba maganar gajiya"_</p><p><br /></p><p>Cikin jin haushi Mommyn tace,</p><p>_"Ni nasan babu wani batun gajiya,kawai Yaseer so yake ya bani kunya shiyasa, yake wulakanta wannan yarinyar, kuma wallahi ita zai aura saide in bana numfashi"_</p><p><br /></p><p>Sannan ta mike tabar dakin. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Yaseer yana ji ana sallar ishsha'i amma kin fitowa yayi, dan kansa ciwoma yake. </p><p><br /></p><p>Wayar shice ta shiga Ringing, kamar bazai daga bah, sai kuma ya dauka dan besan me kiran bah. </p><p><br /></p><p>Ganin Number an rubuta Jafar, yasashi mekewa zaune tare da karawa akunne,</p><p> _"Hello, Yaseer gani kofar gidan ku, nayi tunanin gwara nazo yau dan Gobe bani da tymne zan huce zurmi, nida Cousin dina muke ka fito pls"_</p><p><br /></p><p>_"Ohk gani nan, ku shigo ciki mana akwai me gadi saiya bude muku gate din"_</p><p><br /></p><p>Bayan ya kashe ya fito, tare da nufar wajan harabar motocin gidan. </p><p><br /></p><p>Lokacin daya fito, sun gama gyara Parking din har sunma fito. </p><p><br /></p><p>Cike da murmushi a fuskarsa ya karasa yana mika musu hannu. </p><p><br /></p><p>Dizhwar de beyi magana bah, illah mika masa hannu da yayi suka gaisa dan baya san zuwa, Jafar ya takurashi. </p><p><br /></p><p>Da kansa ya musu Isu cikin falon bakin. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(4)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan sun zauna, kara gaisawa sukayi, Yaseer ne ya kalli Jafar tare da </p><p> _"Malam banyi tunanin yau zaku shigo ba ai"_</p><p> cewar Yaseer </p><p><br /></p><p>_"Wallahi nima haka, mai martabane, yace mu taho, bama mu dade da zuwa bah, na takura Dizhwar ya rakoni, cos in muka shiga rububi ba lallae na samu tym Nazo wajan ka bah"_</p><p>Jafar ya fada. </p><p><br /></p><p>_"Gaskiyane, kana hutawa abokina"_</p><p><br /></p><p>Sun jima suna hira amma, Dizhwar baya furta ko kalla daya, yana ta faman abunda ya saba wato danna waya. </p><p><br /></p><p>Har suka gama hirar su, tukun sukayi sallama dan tafiya. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Washe gari tunda safe, Mai marta ya hada kan Jafar da Dizhwar suka tafi kauyansu dayake duk karshan wata yakan je, duba garin nasu. </p><p><br /></p><p>Haka Dizhwar ya bisu badan yana so bah. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Laila yau tunda safe aka shirya dan tafiya wajan aiki, bayan ta gama abunda Zatayi, fitowarta kenan,ta gamu da Ladi me aikin gidan su Yaseer.</p><p><br /></p><p>Kallan ta tayi sama da kasa kafin tace </p><p>_"Lafiya ladi, me kike anan wajan yanzu"_</p><p><br /></p><p>_"Hajiya ce take kiran ki? "_</p><p><br /></p><p>Kamar zata bita sai kuma tace</p><p> _"Dan Allah ladi, kice mata kawai na tafi aiki, dan wallahi in aka makara kora ake kuma wannan aikin na rasashi akwai matsala, ina dawo saina zo, yanzu haka ma Na fara lattin"_</p><p><br /></p><p>Batare da Ladi tace komai bah, ta mufi hanyar gida, haka itama Laila ta nufi titi dan hawa mota. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Koda ladi ta koma, duk suna falo zaune, tace da Mommy, </p><p><br /></p><p>_"Hajiya naje gidan na tarar da ita, zata tafi aiki, amma tace dani kiyi hakuri inta dawo zata zo, yanzu sauri take_"</p><p><br /></p><p>Shiru Mommy tayi yayin da Salima tayi carap!, tace, lallai ma wannan yarinyar bata da hankali, harkice kina nemanta ta nuna miki aikinta yafi kiranki, wallahi saikin koya mata hankali.</p><p><br /></p><p>Saudat ce tace da Mommy,</p><p> _"wai wacece wannan da har take gaya muku irin wannan maganar? "_</p><p><br /></p><p>Budar bakin Salima sai cewa tayi,</p><p>_"Hmm, ai nasan wallahi in kikaji ko wacece sai kin je har gida kin mata warning, wata banza ce yar gidan kurame anan unguwar, wai yaya Yaseer ya rasa da wanda zaiyi soyayyah sai ita har wani wulakanci take masa"_</p><p><br /></p><p>Shiru Saudat tayi batayi magana bah ita kadai tasan abunda zatayi mata. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Dizhwar kin kwana sukayi shida Jafar a Zurmi dan haka suka biyo Maimartaba suka dawo gida. </p><p><br /></p><p>Lokacin da suka dawo yamma tayi sosai, gashi suna jin yinwa, balle Dizhwar mesan coffee, gashi babu wanda ya iya hada masa sai Asiya kuma bata nan. </p><p><br /></p><p>_"Jafar wai nan garin kuwa babu wani gurin da zaka ce ka samu abinda zakaci kamar snacks haka da Coffee"_</p><p><br /></p><p>_"Ahh! Akwai mana meka maida mana garin namu ne, akwai *Madina plaza*, wajan yana da kyau sosai, ga ma bangaran Restaurant dinsu, sun iya abinci da kuma coffee, wajan babbane harda mall dinsa"_</p><p><br /></p><p>Mikewa yayi tare da daukar key dinsa, </p><p>_"Taso mana muje mu samu abunda zamuci ni bana cin girkin kowa gidan nan sai Asiya kuma bata nan, gashi bana san saka Mami aiki"_</p><p><br /></p><p>Haka ya mike suka tafi tare, babu nisa sosai tskaninsu da wajan. </p><p><br /></p><p>Kai tsaye bakery dinsu suka nufa, koda zuwansu yayi parking, shiga sukayi suka zauna, basu jima bah, Rauda ta karaso wajan tare da fadin, </p><p> _"Barkanku da zuwa, me kuke bukata a kawo muku?"_</p><p><br /></p><p>Jafar ne ya kalle tah, fuskarshi dauke da murmushi yace da ita,</p><p>_"Coffee muke bukata, 2cups da kuma chocolate cake"_</p><p><br /></p><p>Nan take ta huce dan hado Musu,</p><p><br /></p><p>_"Laila, ke kinga wasu hadaddu yau da suka zo siyan abinmu, wallahi kamar Yarima Dizhwar din nan da ake fada"_</p><p><br /></p><p>Laila dake zaune tana danna waya tace da ita, </p><p>_"Dan Allah kiyi sauri ki gama, 9pm,takusa cika mu tafi"_</p><p><br /></p><p>_"Toh in baki ki Kaimusu?,nikuma sai in kaima sauran mutanan da suke jira, dan Allah kinga har yanzu wanda zasu amshi Aikin ina tashi Basu Zo Bah."_</p><p><br /></p><p>Ba san ranta bah ta amsa ta nufi wajan su, Ahankali ta karasa, ta shiga ajje musu duk Su biyu babu me Kallan ta, haka itama bata damu dasu bah, bayan ta ajje cake din ta koma dan dauko Coffee din, koda ta kusan kara sowa wajansa kamar an tunkuta ta fadi, gaba daya coffee din duk zafin sa ya zube masa a fuskar sah. </p><p>da sauri ya mike tsaye har yana sakin wayar hannunsa ta fadi kasa, </p><p><br /></p><p>Wani irin kara ta saki dan taji zafin faduwar sosai. </p><p><br /></p><p>nan ya mike yana yarfe hannu, ko taba fuskar yaki yi, Jafar ne yayi maza ya yi wajansa yana mai Sannu. </p><p><br /></p><p>Da sauri ta mike, tana rike kugu tace dashi, </p><p>_"Dan Allah malam kayi hakuri wallahi ba'a sanina bane"_</p><p><br /></p><p>Har sunyi hanyar fita, sai kuma ya juyo tare da karasowa wajan ta yana fadin, </p><p> _"Ko wasu irin mahaukatane, bakwa ganewa ne, bazaki iya tafiya a hankali bah, idiot kawai"_</p><p><br /></p><p>duk da maganganun sun mata ciwo batayi Magana bah, sai. Hawaye da yake zubar mata. </p><p><br /></p><p>manyan ma aikata wajan ne suka kaita basu hakuri. </p><p><br /></p><p>wani daya daga cikin masu aikinne ya fara fadin</p><p> _"ke meya kawoki nan, keda ba'a nan kike aiki bah, meyasa baku da tunanine, "_</p><p><br /></p><p>itade Laila kasa magana tayi sabo da yanda take ji, Rauda kuwa kasa magana tayi dan gani take laifin tane. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka ya fita daga wajan yana faman bala'i fuska na masa zafi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(5)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tund suka fita daga wajan beyi magana bah har suka shiga mota.</p><p><br /></p><p>Duk da zabin da yake ji, haka yayi driving din, sanin halinsa yasa Jafar be kuma yimai magana bah, har suka isa gidan. </p><p><br /></p><p>Koda yayi parking fita yayi batare daya cire key din bah, ya shige cikin gida. </p><p><br /></p><p>Toilet ya huce kai tsaye tare da tsayawa jikin mirro din wajan sink yana kallan fuskar tashi da tayi jajir, tsaki yayi tare da dauko ruwa me dumi ya wanke fuskar sabo da kamshin Coco da take. </p><p><br /></p><p>Wanka yayi tukun ya fito, riga da wando na bacci ya saka. </p><p><br /></p><p>Koda ya kwanta, kasa mantawa yayi da abun, zaune ya mike yana tuna abunda ya faru, </p><p> Hanu yasa ya kuma shafa fuskar tasa yana faman bacin rai.</p><p><br /></p><p>Haka ya koma ya kwanta badan yana jin bacci bah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_______</p><p>Ita kuwa Lailah ganin abunda ya faru hankalinta yayi mugun tashi, gashi manager sai faman fada yake musu kamar zai doke su, haka jikin su san yaye suka dawo gida. </p><p><br /></p><p>Koda ta shigo gidansu, an kawo wuta, dadi ta danji cikin ranta. </p><p><br /></p><p>Da Sallama ta shiga dan tariga ta saba duk da baji iyayan suke bah,</p><p><br /></p><p>Ga mamakinta Saudat ta gani da kuma Salima tsaye kamar suna jiran awani abu dan jaraba da karfe 9pm. </p><p><br /></p><p>Ganinsu yasa duk da ranta babu dadi tayi Murmushin dole tare da fadin, </p><p> _"Sannunku, ya kuka tsaya ku shiga ciki mana"_</p><p><br /></p><p>Salima batayi magana bah Saudat ce ta matso gaf da ita tare da kallanta sama da kasa, wani takaicine ya kamata ganin kamannin Lailah, dan ba haka tayi tunanin zata same ta bah. </p><p><br /></p><p>_"ke har kina tunanin, akwai abunda zaisa mu shigo wannan matsiyacin gidan inba warning bah"_</p><p><br /></p><p>Ganin babu kowa tsakar gidan yasa taji dadi dan da alama, Mama tayi bacci, dan Babansu sai 10pm yake shigowa gida. </p><p><br /></p><p>_"Dan Allah in wani abun nayi muku kuyi hakuri, amma ba kuzo har gida kuna neman fada bah"_</p><p><br /></p><p>Wani bakin cikine ya kama Saudat, ta duro wata uwar ashariya tare da fadin. </p><p> _"Hahhhhh lallai baki da hankali, atunanin ki nan gidane, kina rayuwa da dutsunan har kike tunanin ke bil adama ce, wallahi yarin kasheri nazo nayi miki, duk sanda na kuma ganin ki da Yaseer sai nasa an kulle ki,dan ruwa ba sa'an kwando bane"_</p><p><br /></p><p>Mamakine yaso kama Lailah kamar tayi dariya, sai kuma ta ce da ita, </p><p> _"Wallahi har kin bani tsoro, nina zata wani abunne ma ya faru har kike faman fada haka, maganar yaseer shiya gani yana so, duk da yasan akwai wata a gida, dan haka ina ganin bani ya kamata kizo kima Warning bah, dade ana so din shine, sabo da haka Umma ta gaida Aysha"_</p><p><br /></p><p>Tana kaiwa nan ta shige daki ta barsu tsaye a tsakar gidan. </p><p><br /></p><p>Wani abune ya tsayawa Saudat a huyanta, bakin ciki kamar ta rusa kuka haka take ji, dan ta tsani Lailah a rayuwarta. </p><p><br /></p><p>Batare data kula Salima bah tasa kafa ta fice daga gidan itama tana binta abaya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ita kuwa, Laila bayan ta shiga daki, tsaki tayi tare da fadin, </p><p> _"in banda hauka ma irin naku, kowa ya gaya musu ina san wani Yaseer"_</p><p> Tsaki tayi, taci gaba da abunda take. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Yau tunda Safe Mai martaba ya tara gaba daya yan gidan kwansu da kwarkwata, harda Anty Humaira. </p><p><br /></p><p>Bayan an bude addu'a da taro, mai martaba ya fara bayani kamar haka. </p><p><br /></p><p>_"Na tarakune badan komai bah, sai dan in sanar muku da lokaci yana ja, kuma kullum muna dada tsufa kwanaki na raguwa,sabo da haka ina gaf dayin murabus, daga kan kujerata dumin bama wanda ya kamata"_</p><p><br /></p><p>Gaba daya kowa yayi shiru yana jinsa, yayin da Anty Amarya idanta yana kan Dizhwar daya maida hankalinsa ga abunda mai martaba yake fada. </p><p><br /></p><p>_"Kasancewar gaba dayanku, kuna karkashina, kuma na isa na yanke hukunci a duk abunda naga dama, haka zalika, dukkan dukar dana kafa dole abita. </p><p><br /></p><p>Shiru duk sukayi babu wanda yayi magana, har Hajiya Bilki dake zaune kasancewar tazo dumin kiran da yayi mata. </p><p><br /></p><p>_"In baku mantaba, nayi wani alkawari tun kafin Yaran nan suzo duniya, wato Jafar da kuma Dizhwar, sabo da haka yanzu lokaci yazo dazan ciki wannan alkawarin dana dauka"_</p><p><br /></p><p>Gaban Dizhwar ne yayi mugun faduwa, dan ko kadan baya kaunar abunda zai fito daga bakin Maimartaba. </p><p><br /></p><p>_"Kai Dizhwar, da Kai Jafar, da kuma Fareeda haka zalika har Zakiyya, nariga na gama magana, wata mai zuwa duk zan aurar daku"_</p><p><br /></p><p>Gaba daya duk wanda aka anbato Sunan saida ya dago ya kalle shi. </p><p><br /></p><p>_"J afar, zan hada ka da Fareeda, kai kuma Dizhwar yar gidan *Abdulganiyu Governor*,mun yi magana da Mahaifinta, ke Kuma Zakiyya, zaki Auri Dan gidan *Alhaji Uthman Waziri*,"_</p><p><br /></p><p>Gaba dayansu babu wanda yayi farin ciki da abunda Sarki ya fada. </p><p><br /></p><p>Dizhwar batare da ya furta komai bah, yayi shiru babu abunda zuciyar keyi sai bugawa da karfi. </p><p><br /></p><p>Fareeda kuwa, kuka ta kama tana fadin</p><p>_"Gaskiya Nide bana san wanann auran, aiba dole bane haka ake dan Allah Abba a canza magana wallahi bana sanshi"_</p><p><br /></p><p>Kowa mamaki yake abunda take fada. </p><p><br /></p><p>Anty Amarya kuwa bata kowa take bah, itama hankalinta ba karamin tashi yayi ba jin Dizhwar zaiyi aure. </p><p><br /></p><p>Shiru babu wanda ya bata amsa, yayin da shima Jafar wani haushi ya kamasa, dan ko xa'a kashe shi bazai taba auran Fareeda bah, yarinyar data gama watsewa, shi baya santa, Kuma har abada dade ya aureta gwara ya mutu beyi aure bah. </p><p><br /></p><p>Tashi tayi tana kuka ta fita daga falon, yayin da babarta ta mike ta bita itama ranta a bace. Hajiya babba kallan me Martaba tayi tare da fadin , </p><p><br /></p><p>_"Gaskiya gaskiya wanann tsarin beyi ba, ba zai yiyuba wallahi, ai yanzu an waye ba'a auran dole, kabar yarinya ta zabiwanda take so gaskiya"_</p><p><br /></p><p>Itama ta mike ta ja, Yarta suka fita daga cikin dakin, </p><p><br /></p><p>Kowa mikewa yayi yabar Falon, babu wanda aka bari sai Fulani. </p><p><br /></p><p>Itama tashi tayi zata tafi, ya kira sunan ta. </p><p>Ahankali ta karaso wajansa tare da durkusa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_"Kema baki da abunda zaki fada ne?"_</p><p> Cewarsa. </p><p><br /></p><p>Murmushi tayi tare da fadin,</p><p> _"Babu saide ince Allah ya sanya alkhairi ya kaimu lkcn lfy "_</p><p><br /></p><p>Tana kaiwa na ta fice, dan ita ta manta raban data gansa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asiya kuwa, tana Barin wajan taran daki ta nufa ta fashe da kuka, dan ita a duniya babu wanda take kauna kamar yaya Jafar, dan tana jin an bashi Farida taji kamar ta hadiyi zuciya ta mutu. </p><p><br /></p><p>Dizhwar kuwa mota yahau yabar gidan ko yaji dadi cikin ransa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_______</p><p>Kasancewar duk ranar litinan sai wajan 2pm, Laila take zuwa wajan aiki yasa bataje yau da huri ba, dan haka ta shirya dan kai Baba asibiti, haka yasa ta tafi har Mamanta. </p><p><br /></p><p>Bayan sunje sun dawo suna tafiya kafin su fito titi su samu mota,ita dasu sai faman Tafiya suke, </p><p><br /></p><p>Laila tace dasu</p><p> _"bara ta shiyo kati tana zuwa, karsu je ko ina"_</p><p><br /></p><p>Nan suka tsaya suna jiranta. </p><p><br /></p><p>Nan ta gangara ta tsaya wajan masu katin zata shiya, tana nan tsaye ana daukomata ,ta shiga sakawa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dizhwar kuwa yana ta faman gudu a motar bunda be saba bah kenan,yafi yin hakan in ransa ya bace, daidai wajan da Kuraman suke, yaci wani wawan birki dan saura kadan yayi ciki dasu. </p><p><br /></p><p>Wani uban tsaki ya buga dan ganin ko ajikinsu, suna tsaye suna kalle kalle. </p><p><br /></p><p>Hakanne ya kona masa rai ya fito yana faman huci, da sauri ya karaso wajan su tare da dauke Baba da mari, nan ya kifa kasa ,</p><p>Shi kuma yana tsaye yana faman huci. </p><p><br /></p><p>Da sauri Mama ta karasa wajansa ta daga shi tsaye daga faduwar da yayi. </p><p><br /></p><p>_"Ko wasu irin dambobine, baku da hankaline, kuna ganin kun tsaya akan hanya, wallahi dana kadeku na kade banza babu abunda aka isa ayimin, banzaye matsiyata. </p><p><br /></p><p>Duk da basu san abunda yake fada bah, amma yanayin da suke kallan bakinsa da kuma yanda yake masifa sun san fada yake yi. </p><p><br /></p><p>Tun sanda ya kwadawa Baban mari ya fadi kasa, Laila tana tsaye tana kallo, bakin ciki da kuma mamaki lokaci daya suka hadar mata, nan da nan kwallah ta cika mata ido, sakin jikar hannuta tayi tana binsa da kallo, tabbas ta gane sa, kuma wallahi be daki banza bah. </p><p><br /></p><p>Da sauri kamar an koro ta ta karaso wajan tare da wanka masa mari har sau biyu, tana hawaye ta nunasa da yatsa tare da fadin, </p><p> _"Kaima mahaukacin inane kokuma wasu jakanne suka haifeka, baka da iyayene ko bakasan darajar subane, yanayinka da kuma yanayin rashin tar biyarka ya tarbatarmin da ba mamaki a tasha ka haife kah,wallahi duk fadin duniyar nan banga wanda zai hukanramin iyayena ba in rabu dashi ko uban waye kuwa, kuma wallahi wallahi sai Allah ya saka masu marin daka masa, ko kai baka yiam mutane uzurine, sudin kasan wata larura garesune, dahar zaka fito kana wani tinkawo kai gaka mai mota, uwar motar taka"_</p><p><br /></p><p>Ta dauki wani katan dutse ta bugawa glass din gaba ya tarwatse,nan iyayan suka dauke mata jakar tata suka janyeta suka tafi. </p><p><br /></p><p>Shikuwa Dizhwar kasa tattacewa yayi a wata duniyar yake, shine kuwa kode wanine, anya kuwa ba mafarki bane, in kuwa mafarkine addu'a yake Allah ya dauki ransa kafin mafarkinsa ya zama gaske. </p><p><br /></p><p>Ga mamakinsa yaga hawaye yana zuba, wani bakin cikine ya kamasa ji yake kamar zuciyarsa zata tsaga kirjinsa ta fita tsabar bugawa. </p><p><br /></p><p>Batare daya taba motar tashi ba, haka ya dinga tafiya tamkar mahaukaci, har gida ya isa duk inda ya nufa binsa ake da kallo. </p><p><br /></p><p>Koda ya karasa gida, nan ma Mutane mamaki ya kamasu suka shiga binsa da ido. </p><p><br /></p><p>Jafar ne daya hangosa yayi saurin karaso wajansa yana duba jikinsa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(6)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_"Lafiya, menene ya faru na ganka haka, abunda bansan ka da haka bah?"_</p><p> Jafar ya fada yana kallan sah, </p><p><br /></p><p>Maimakon yamai magana koya basa amsa, sai ya huceshi kamar ma besan abunda yake fada bah.</p><p>Mamakine ya kama, Jafar, haka yayi tsaye yana kallan sah, har ya shige ciki. </p><p><br /></p><p>Dizhwar kai tsaye dakinsa ya nufa, be tsaya ko ina ba sai cikin toilet, shower kawai ya kunna ya tsaya cikin Jacuzzi, yana jin saukar ruwan a kansa. </p><p><br /></p><p>Yakai Awa daya ciki,shi kansa besan me yake bah. </p><p><br /></p><p>Haka ya fito a jike ya zauna kasa kan tiles wajan stairs din da zai sadashi da Dining area. </p><p><br /></p><p>Haka iska taita kada shi, har saida kayan jikinsa da sumar kansa ta bushe tamkar be shiga ruwa bah. </p><p><br /></p><p>Yana nan zaune, Jafar ya kuma turo dakin da Sallama, mamakine ya kuma kamashi ganin sa zaune ya dora hannunsa saman gwiwar kafarsa yana tunani. </p><p><br /></p><p>Karasowa yayi wajan yana kallansa, baki ya bude tare da fadin</p><p>_"Dizhwar kuka fa kake"_</p><p><br /></p><p>Abunda ya kuma kona masa rai kenan yayi kukan kura tare da daukar kujera ya jefi glass din kofar kitchen dinsuhi, saida ta fashe, ya durkusa tare da kurma ihu, idanunan sunyi jajir, cikin wani irin karajin magana yake fadin</p><p> _"Wallahi saina kasheta, saina nuna mata karfin mulkina, saina nuna mata asalin koni waye gaba daya danginta sai sun gane kuransu, saisun gwammace ba'a haifi ahalinsu cikin Zamfara bah, saina kashe duk wani me alaka da ita, saina rabata da farin ciki na har abada"_</p><p> Jafar ganin abun yaki karewa, kuma ya tabbata mace ce tamai wani babban laifin, da sauri yayi ta maza ya kamashi ya zaunar yana kwantan masa sa hankali, dan baya san abun yayi nisa, haka yayi ta lallashin zuciyarsa yana controlling dinsa. </p><p><br /></p><p>Haka yayita masa har yaji ya daina wannan nishin da yake tukun, yana san jin menene ya faru amma baya san cukalo ciwan. </p><p><br /></p><p>Ganin ya samu saukin bacin ran yasa shi tashi ya fita daga dakin. </p><p><br /></p><p>Yana san yayi bacci ko yaji dadi amma ya kasa, yana rufe idansa zaiga saukar marin data masa. </p><p><br /></p><p>Mikewa yayi ya shiga toilet yayo alwala ya fita masallaci danyin sallar magriba. </p><p><br /></p><p>__________</p><p>Lailah kuwa haka iyayanta suka jata, tana ta faman kuka har suka je gida, </p><p> Ko bayan sun koma gida, kasa wani katabus tayi, babu abunda take tunawa duk bayan seconds sai saukar marin data gani fuskar Babanta. </p><p><br /></p><p>Wani bakin cikine ya kuma kamata, nan ta kuma fashewa da kuka. </p><p><br /></p><p>Koda dare yayi, kasa bacci tayi, ko kadan bata danasani ko tunanin abunda zai biyo baya akan abunda tayi masa,bata da burin daya huce su kara haduwa domin ta kuma masa sarar data fi wanda tayi masa yanzu, yanda ta dauki iyayanta babu abunda bazata iyabah inhar mutun ya shiga gonar su, ta tsara musu rayuwa batare da wani takura bah ta yanda babu ruwansu da kowa, hakan yasa ko yan uwanta baxata saurarawa ba in har suka taba mata iyayanta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>________</p><p>Washe gari haka Dizhwar ya tashi badan yayi bacci ba, wanka yayi ya shiga gaida iyayansa. </p><p><br /></p><p>Duk wanda yagansa yasan ya canza, koda an tambaya saiya ce bashi da lafiya. </p><p><br /></p><p>Yana zaune a garden din gidan, koya samu saukin bacin ran daya ke ji. </p><p><br /></p><p>Yaji karan tafiya, amma kin dagowa yayi dumin baya bukatar kowa shiyasa ya kuma wajan da babu wani.</p><p><br /></p><p>Ahankali ta karaso wajan, sanye da goduwar riga ja, kasan cewar fatar jikinta farace tas!, sai kayan suka dauki jikin ta. </p><p><br /></p><p>Kujerar da take kallansa ta zauna, batare datayi mai magana bah, ta zaro wayarta tana dannawa tana cin chewgam .</p><p><br /></p><p>_"Sannu Yarima"_</p><p><br /></p><p>Hakan data fada yasa ya dogo da kansa tare da kallanta. </p><p><br /></p><p>Wani sanyi taji cikin ranta, tare da kara gyara zaman ta tana murmushi. </p><p><br /></p><p>_"In bazaka damuba inasan yin magana dakai"_</p><p><br /></p><p>be kalletaba haka kuma be bata amsa bah, saida ta kara, maimaitah tambayar tata. </p><p><br /></p><p>Kamar bazaiyi magana bah ya kura mata ido har saida ta fara tsarguwa, kafin ya shafa sajansa, tukun yace da ita, </p><p> _"Ina jinki"_</p><p><br /></p><p>Saita tsinki kanta da dabarbarcewa yanda ya tsareta da ido saitama rasa abunda zata ce dashi. </p><p><br /></p><p>_"Am dama in bazaka damuba, ina san inyi tafiyane, gashi inasan kaman rakiya"_</p><p><br /></p><p>Still kallanta yake ko ido baya daukewa a kanta. </p><p><br /></p><p>Cikin zuciyarsa kuwa cewa yaye, </p><p> _"Lallai matar nan ta raina min hankali, kenan nine dan rakiyar tatah"_</p><p><br /></p><p>Batare daya bata amsar taba, ya mike tare da barin wajan. </p><p><br /></p><p>bin bayansa tayi da kallo, rungume hannunta tayi a kirjinta tana murna, dan ko kadan kome Dizhwar yayi bata jin haushi dan gani take koma me yayi ya isane.</p><p> Anty Amarya kenna, tana kaunar Dizhwar itade. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shikuwa Dizhwar batasan akwai abunda yake damunsa bah, bashi da burin daya huce su hadu da Yarinyar nan badan komai ba saidan daukar fansa. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Laila yau bata da Niyar zuwa aiki ko kadan, har kusan 10am, tana kwance kan gado taki tashi ta karya ma, kanta ta daga sama tana kallan Ceiling dakin nasu,da duk yayi jirwayan ruwa da hujewa da beraye suka masa, wani takaicine ya kuma kamata, tsaki tayi tare da juyawa tana kallan kasa kuma. </p><p><br /></p><p>Wayar tace ta shiga kara, tana ji amma harta katse vata dauka bah.</p><p><br /></p><p>Saida aka kara kiran nata tukun ta mika hannunta ta dauka ta kara akunne, tare da mikewa zaune, gashin kanta ya zuba bayanta da kuma gaba ya rufe mata fuska hannu tasa tayi gefe dashi tare da fadin, </p><p> _"Hello! "_</p><p><br /></p><p>Daga dayan bangaran kuwa, Rauda ce take fadin, </p><p> _"Hello Lailah, yau bikizo aiki ba, inata nemanki kwangila ta samu, bayan abun duk zamu samu 10k, amma na saka sunaninki ciki, abunne yazo da gaggawa, kisan yar gidan sarkin nan Gimbiya Fareeda?"_</p><p><br /></p><p>_"eh"_</p><p> Lailah ta fada harda, gyada kanta. </p><p><br /></p><p>_"Itace take cika, shekara 22,yau shine zatayi celebrating birthday dinta, kuma Mune masu decorating da ordering na Abinci, Madina plaza ta gaiyata, shine aka ce za'a dauki mutun 20,cikin mu,yanzu haka mun ciki, bayan abunda Za'a biyamu, tace inde komai yayi zata bamu kudi masu yawa, manager yace kowa 10k za'a bashi,yanzu haka duk mun zo, ke kadai ake jira, karfe 12,zamu isa can din mune masu serving food"_</p><p><br /></p><p>Batare da tayi murna ko wani murmushi ba bisa bayanin Rauda dan abunda yake damunta, </p><p><br /></p><p>_"Toh ganinan"_</p><p> Shine abunda ta fada kenan ta kashe wayar ta mike. </p><p><br /></p><p>Gadan ta gyara sharp Sharp, ta gama ta yi wanka, batare data karya ba kota tsaya yima Mama bayani ta tafi. </p><p><br /></p><p>Lokacin data karasa suna kokarin shiga mota su tafi tayi saurin sauka, ta karasa ta shiga, kusa da Rauda ta zauna tana Maida numfashi. </p><p><br /></p><p>Kallanta, Rauda tayi tare da fadin, </p><p> _"Lailah ya naga kamar baki da lafiya"_</p><p><br /></p><p>Lumshe ido tayi, dan yau ko makeup babu, farar Powder kawai ta shafa, sai pink lipstick, tasa riga da wandonta, da after-dree,data dora, tayi rolling mayafinta akanta dayasha gyara, ga abu gashinta da tayi acuci dashi. </p><p><br /></p><p>_"Sunnu, dana sani da bansa sunanin kibah"_</p><p><br /></p><p>Murmushi ta danyi, ta dora kanta kan kafadar Rauda tana fadin, </p><p> _"Ba komai Rauda na gode, zan iya ahakan ma"_</p><p><br /></p><p>Tun daga nan babu wanda ya kara magana, har suka iso gidan sarautar, kai tsaye Bangaran da aka tanada domin aikinsu aka nufa dasu. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(7)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda suka isa already duk ankai musu abunda zasu bakata, dan har wasu sun fara girkin.</p><p>Kana ganin yanayin Laila kasan tana cikin damuwa, aiki kawai takeyi babu wani walwala cikin fuskar tah. </p><p><br /></p><p>Sosai gurin da aka masa decorations din sun iya sosai, dan yasha kayan ado tamkar a india, ga flowers kala kala anyi ado da shi, kofar shiga wajan gaba daya anyi musu ado da purple na flowers. </p><p><br /></p><p>Duk abunda ya kamata suyi sun riga da sunyi kafin magriba. </p><p><br /></p><p>Ganin yamma tayi sosai, bayan sun idar da sallah, ta kalli Rauda dake gefanta tace da ita, </p><p> _"Wai har zuwa nawa zamubar nan wajan, ka idar aikinmu 9pm Muke tashi,in na huce hakan akwai matsala dan ban sanar dasu mama bah, gashi kuma maybe mu huce tym din"_</p><p><br /></p><p>_"Gaskiya kema Laila aida kin gaya musu dole hankalinsu zai tashi tunda bakya huce hakan"_</p><p> Rauda ta fada tana gyara mayafinta. </p><p><br /></p><p>Shiru Laila tayi dan bata da abunda zata ce. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Fareeda kuwa tana can tana ta faman shiri ita da kawayanta, anata faman kwalliya cikin daki. </p><p><br /></p><p>Anty Amaryace ta shigo dakin da yan matan suke, </p><p> _"Wow masha Allah yarannan kunyi kyau wallahi, dole duk wanda ya ganku ku tafi da hankalin sah, yarinyata so nake yau Wannan Faisal din in yazo ya kasa tafiya"_</p><p> Anty Amarya ta fada tana faman iyayi, </p><p><br /></p><p>Gaba daya yan matan daki suka hau shewa da dariya dan suna san matar sabo da yar shafta ce ga bata jin kunya. </p><p><br /></p><p>Kamar yanda yarta taci uwr kwallahiya haka itama tayi kwalliya kamar ba ita ta haifeta bah. </p><p><br /></p><p>Sanin halin Fareeda na girman kai tasan babu wanda ta gaiyata acikin gidan ita kuwa, tana san Dizhwar yazo wjan wannan Party, dan haka da kanta ta mike ta nufi part dinsa. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Zaune suke cikin falon, kowanne cikin kana nan kaya suna kallon ball, </p><p>Suna hira. </p><p><br /></p><p>Tura dakin tayi ta shiga batare da tayi sallama bah. </p><p><br /></p><p>Jin turo kofar yasa suka kalli wajan dukkan su. </p><p><br /></p><p>Ganin me shigowa yasa Dizhwar dauke kai yaci gaba da kallan da yake yi. </p><p><br /></p><p>Karasowa tayi cikin takunta na daukar hankali ta zauna kan kujera tare da dora kafa daya kan daya. </p><p><br /></p><p>Shiru na tsawan lokaci babu wanda yayima wani magana. </p><p><br /></p><p>_"Dizhwar wajan ka nazo"_</p><p><br /></p><p>Jin haka yasa Jafar tashi ya fita daga falon yana murmushi. </p><p><br /></p><p>Shiru Dizhwar be bata amsa bah,ganin bashi da alamar mata magana ta fara magana kamar haka. </p><p><br /></p><p>_"Kasan yaune ake birthday party na Fareeda, so nasan bata gaya muku ba, kasan cewar abubuwa sunyi mata yawa shine nazo da kaina domin na yi inviting dinka, pls ko 5mins ne kayi a wajan bayan ta yanka cake saika tafi"_</p><p><br /></p><p>Ba kallanta yake bah, hankalinsa yana wajan Tv, hakan yasa tayi tunanin ko beji bah, </p><p><br /></p><p>Cigaba tayi da kallansah, tana ji kamar taje ta rungumeshi dan wani Magnet da yake fuzgarta, san Dizhwar yana kara shiga cikin zuciyar ta. </p><p><br /></p><p>Lumshe ido yayi ya bude ya sauke a kanta. </p><p><br /></p><p>Wani iri taji a jikinta ta runtse ido tana wani farin ciki cikin ranta. </p><p><br /></p><p>_"Bani da lokaci, zan bada gift a kawo mata"_</p><p><br /></p><p>Ya mike yana shirin barin wajan, da sauri ta mike tare da rike hannunsa, ahankali ta karaso gabansa ta yanda suna iya shakar numfashin juna, tsayawa yayi yana shirin jin menene tagged dinta na gaba. </p><p><br /></p><p>_"pls Dizhwar kaine fa special Guest dinmu, ur d first person to received ur gift, karka min haka pls kazo dan Allah"_</p><p> Yanda take masa saika dauka wata budurwar sace. </p><p>Hakan da ta fada yasa, be kula taba ya shige ya barta anan. </p><p><br /></p><p>Ido ta rufe tare da fadin</p><p> _"Ya Allah kasa yazo"_</p><p><br /></p><p>______</p><p>Kwance kan sofa ya tarda Jafar zama yayi kusa da kafarsa tare da sa hannunsa biyu ya shafa sumar kansa. </p><p><br /></p><p>_"amma wannan matar bata da hankali wallahi"_</p><p><br /></p><p>Mikewa Jafar yayi xaune tare da fadin, </p><p>_"pls kabar fadin irin haka mana, matar mahaifinkace tamkar uwa take a wajan ka, pls karka bada mutane mana, kayi mata abunda take so"_</p><p><br /></p><p>Kallansa yayi tare da yin tsaki, </p><p><br /></p><p>Dariya Jafar yayi yana fadin, </p><p> _"Abun kuma kaina zai dawo"_</p><p><br /></p><p>Tashi yayi ya nufi bedroom dinsa yana fadin, </p><p> _"ka shirya sai muje, in kuma bazaka ba nima ba inda zani"_</p><p><br /></p><p>Yasan halin Dizhwar in yace bazai je bah, shima haka zaice, kuma gashi tazo da kanta ta roka hakan yasa ya tashi shima dan yaje ya shirya. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Karfe 8pm daidai, lokacin motoci kala kala suka fara shigowa cikin gidan, haka aka dinga shiga kowa yana nuna gate pass dinsa, mata da maza kamar wajan saida motoci haka wajan ya koma, wajan parking daban aka ware musu. </p><p><br /></p><p>Haka wajan ya koma kamar rana tsabar fitilon da aka zuba, kowa ka gani wajan ya kure adakarsa babu wanda zaka ce be burgekaba ko kayansa busuyi kyau bah, yaran manyane wajan, daga gari gari haka suka zo harda wanda ba'a kasar suke bah, haka ga yan jarida da masu daukar hoto, ga masu video covering ,kai abun sai wanda ya gani ba karamin kyau wajan yayi ba. </p><p> </p><p>______</p><p>Gaba daya hankalin Laila yayi gida, dan ji take kamar ta matso da tym din ayi ayi a gama ko zataji dadi. </p><p><br /></p><p>Ga girman gidan da kuma wajan da aka kawo su, dan ji take ko za'a kasheta bata san ta hanyar da zata bi ta fita daga wajan ba.</p><p><br /></p><p>Suna nan zaune kowa yana jiran yaji an fara kiransu, amma sai karfe 9pm daidai tukun aka bukace su. </p><p><br /></p><p>Nan suka shiga wajan dan za'a fara aikin, riga aka basu duk suka canza. </p><p><br /></p><p>Nan suka fara aikin serving jama'a, wasu suna cin abinci wasu suna rawa, kowa da abunda yakeyi, ita kuwa Lailah kallan ikon Allah take ta faman yi, ga uba cake wanda ko yan wajan zasuci su koshi bazasu cinye shi bah, abun sai ya koma mata sabo, kamar yar kauye, cikin zuciyarta kuwa fadi take, </p><p> _"ikon Allah, kudi suna idan suke, Allah ka azurtamu"_</p><p><br /></p><p>Komai yana tafiyar musu daidai kamar yanda suma can basu da wata matsala. </p><p><br /></p><p>Fareeda ce ita da wata kawarta, suke faman yawo a wajan, tasha wata farar riga kamar wedding gown, fara tas ga uban gashin doki data sha tamkar nata, tayi Makeup sai faman iyayi ake,inka ganta sai kace tayi shekara 30,amma yarinya ce karama. </p><p><br /></p><p>Waya ta kuma kira, da alama saurayinta take jira yazo wajan.</p><p><br /></p><p>Can, sai gashi shima ya shigo cikin wajan, yasha Suit ash color, ga escort a bayansa kusan su biyar. </p><p><br /></p><p>Nan Mc ya fara koda shi, waje yahau tafi, kasan cewar kowa yasan shi. </p><p><br /></p><p>Babban dan gidan Minister na kudi na Nigeria, kana ganinsa katan gardi tamkar Arne, farine dogon namiji me kira irin wanda ake kira da Giant, </p><p><br /></p><p>Babu annuri a fuskarsa, sai faman shan kunu yake, haka ya karaso ya nemi waje ya zauna, tana ganin yazo tayo wajansa tana murmushi. </p><p> Nan kawayanta sukayo wajansa aka hau musu hotuna. </p><p><br /></p><p>Daidai lokacin Dizhwar da Jafar suka shigo wajan, cikin shiga ta alfarma, nan yan mata sukayi wajansa shima, dan suna so suyi hoto dashi, watama sabo dashi tazo wajan. </p><p><br /></p><p>Cikin takunsa na kasaita, suka nemi waje suka zauna shida Jafar. </p><p><br /></p><p>Kowa wajan tana ji da mulki da kudi da kuma matsayi, babu wani namiji da zakaga ya mike yaje wajan wani sun gaisa. </p><p><br /></p><p>Haka anata abu, Anty Amarya taja Mc gefe, kome ta gaya masa, nima ban sani ba sai ganinsa nayi ya fito yana fadin. </p><p><br /></p><p>_"All our Friends, sisters and brothers, ur most welcome to ur dearest Sister's special day,once Again, So friends u have to put ur hands together for our Special guest,our King *Yarima Dizhwar*"_</p><p><br /></p><p>Gaba daya waje yahau tafi, shikuwa Faisal da yayi kokarin mikewa komawa yayi ya zauna sabo da haushin da yaji, dan gaba daya ya zata shine, haka itama Fareeda mikewa tsayi tayi tana kallan jama'a dan haushin da take ji, kuma tasan babu wanda yayi wannan abun sai Babarta. </p><p><br /></p><p>Da sauri ta mike ta nufi wajan da uwar tata take. </p><p><br /></p><p>_"Haba Mum wannan wani irin abune, yanzu kinzo kin batamin shirina, menene na wani sa a kira Ya Dizhwar bayan kinsan ni ko inviting dinsan banyi bah, wannan ai cin mutuncine ki bari in birthday dinki ya tashi saiki nemoshi"_</p><p><br /></p><p>Tana fadar haka tayi tsaki tabar wajan. </p><p><br /></p><p>Koda ta koma wajan, babu kowa Faisal da mutanan sa sun tafi, wayar ta ta dauko da sauri ta shiga kiransa amma taji switch off , kamar tayi kuka,ta fita wajan da gudu amma bataga kowa ba, tsaki tayi ta koma dan ba huce haushinta kan su Dizhwar. </p><p><br /></p><p>Lokacin shi kuwa an kirayeshi dan bata gift din daya kawo mata,Anty Amarya sai faman farin ciki take. </p><p><br /></p><p>Tana tafiya kamar zata harde har sauri take ta karasa wajan, fuskarta babu murmushi, tana kara sawa ta tsaya gaban sa, ya dauko gift din ya mika mata, kowa yana dauka. </p><p><br /></p><p>Amsatayi tare da cilla masa kayansa jikinsa.</p><p><br /></p><p>_"Wanene ya baka ikon zuwa wajan nan, da har kake kokarin bani wani matsiyacin gift dinka"_</p><p><br /></p><p>Abun ya bawa Dizhwar mamaki, be kalli kowa ba sai Jafar dake gefe, da sauri ya taso, yana kokarin jan Dizhwar daga wajan. </p><p><br /></p><p>Fareeda kuwa dagewa tayi ta dauke Jafar da mari tana fadin</p><p> _"munafiki ai kaine kake zugashi"_</p><p><br /></p><p>Bata gama Magana bah,Anty Amarya ta bata mari masu kyau har guda biyu, nan fa waje ya hargitse da fada. </p><p>Su Laila suna gefe suna ganin ikon Allah. </p><p><br /></p><p>Nan Jafar ya fara janye Dizhwar daga cikin wajan da yake shirin ballah Fareeda. </p><p><br /></p><p>Yana jansa, har suka fita daga cikin Taron, tsaki yayi ya juya zai fita daga wajan, da sauri ya kuma, juyowa ganin Laila tsaye tana kallo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(8)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sauri ya nufi wajan yana, binta da kallo. </p><p><br /></p><p>Kafin yazo har sun fita waje, nan yaci gaba da binta har ya hangota a wajan.</p><p><br /></p><p>Har ya kusan karasawa wajanta sai kuma ya fasa, </p><p> Ganin suna kokarin shiga mota, yasa yabi motar da kallo, da sauri har gudu yake ya nufi part dinsu, yana sauri ya shiga mota, ya fita waje ya tsaya yana jiran yaga fitowar motar tasu. </p><p><br /></p><p>Ya jima a waje tukun yaga an fito dasu, nan yabi motar duk inda tayi, karfe 10:30pm motar tayi parking daidai Madina plaza, </p><p> Nan suka shiga fitowa, kasan cewar wajan da haske hakan yasa be rasa gane tabah.</p><p><br /></p><p>Yana nesa dasu kadan cikin motar yana binta da kallo har suka yi sallama da kowa, suka nufi taxi ita da Rauda kamar yanda suka saba. </p><p><br /></p><p>Nan yayi ta bin Taxi din har aka sauke Rauda, har kofar gidan su Lailah saida Dizhwar yagani, sunayin parking, ya ga ta fito ta bashi kudin ta shiga gidan. </p><p><br /></p><p>Dariya yayi me karfi tare da shafa gemu, shi kadai yasan dalilinta. </p><p><br /></p><p>Nan yayi baya ya koma gida cike da murna da farin ciki cikin zuciyarsa. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Laila kuwa duk abunda ya faru babu wanda ta gane sai Dizhwar, mamakine ya kamata, kenan dama dan gidan sarkine shidin, ganin hakan yasa tayi mugun tsorata jikinta yayi sanyi, yanda taje haka ta dawo babu wata walwala. </p><p><br /></p><p>Koda ta shigo gidan su Mama suna zaune ita da Abbansu akan tabarma kowa yayi gum!, suna jiran shigowar yar lelansu. </p><p><br /></p><p>Gani ta shigo yasa duk suka Mike suna haskata. </p><p><br /></p><p>Nan ta kalkalo dariya tayi, kama hannunsu ta zauna tana basu labari da kuma basu hakuri da bata sanar bah. </p><p><br /></p><p>Dadi sukaji nan kuma ka hau hira da dariya, amma cikin ranta kunshe yake da damuwa dan abunda idanta ya gane mata. </p><p><br /></p><p>Saida ta tabbata ta saka Su farin ciki tukun ta shiga daki, zama tayi bakin gado tare da rufe idanta ta saka hannunta kan kirjinta tana jin yanda zuciyarta ke bugawa. </p><p><br /></p><p>Koda Maman ta shigo ta ganta haka da fata tayi, </p><p>Da sauri ta bude idan ta wayance tare da dora hannunta kan kirjin uwar tata tana jin yanda tata zuciyar take bugawa ba kamar tata bah.</p><p><br /></p><p>Hannu ta nuna alamun menene yake faruwa? </p><p><br /></p><p>Itama girgiza mata kai tayi alamun babu komai.</p><p><br /></p><p>Sai sannan taji dadi, ta fita daga dakin. </p><p><br /></p><p>Komawa tayi kan gadon ta kwanta tayi reran tare da sauke wani gwauran numfashi, ta rufe ido,a Haka bacci yayi awon gaba da ita. </p><p><br /></p><p>Batayi aune ba taji sallar asbah, da sauri ta tashi ta kunna fitilar, ta canza kaya ta fita danyin alwala. </p><p><br /></p><p>Banyan ta idar da sallah, ta koma ta kwanta, hijab din ta cire, kayan Baccine jikinta riga da wando masu laushi wanda suka sha jiki, ta daure gashinta a baya da ribbon sauran kuma ya zoba har kasan bayanta. </p><p><br /></p><p>Tunda ta koma baccin bata farka bah. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Koda gari ya waye sosai gari yayi haske dan 10am ta kusa, ganin Su Laila sun jima wajan aiki kuma har lokacin bata tashi ba yasa Mama bata tayar da ita bah. </p><p><br /></p><p>Tana cikin kitchen bayan ta gama hada koko ta zuba cikin flash. </p><p><br /></p><p>Jiyowar da zatayi taga kwalaye da kuma buhun shinkafa kusan uku, a tsakar gida, tsoro taji ta fito tana kalle kalle. </p><p><br /></p><p>Ganin mutane tayi anata shigo da abubuwa anki dainawa, ganin haka yasata shiga daki ta fito da mijin nata. </p><p>Shima kawai bi yake da kallo, saida aka ciki tsakar gidan da abubuwa na daban daban. </p><p><br /></p><p>Bayan kamar min10,babu wanda ya kuma shigowa, Dizhwar yayi sallama. </p><p><br /></p><p>Ganinsa yasa suka kara hadewa waje daya suna kallansa da mamaki, shigowa yayi ciki ya tsaya kusa dasu tare da durkusawa, </p><p><br /></p><p>_"Dan Allah kuyi hakuri nasan abunda nayi muku ban kyauta bah, wallahi ba laifina bane sharrin shaidan ne"_</p><p><br /></p><p>Sukama ba jin abunda yake fada suke ba kallansa kawai suke. </p><p><br /></p><p>Jin kamar a mafarki ana magana yasa Laila mikewa da sauri ta fito waje. </p><p><br /></p><p>Mamakine ya kusan kasheta ganin abunda batayi tunaniba, bin komai take da kallo kafin ta kai idanta ga Dizhwar dake tsugunne gaban su Mamanta. </p><p><br /></p><p>Kasa magana tayi sai nunashi da tayi da hannu. </p><p><br /></p><p>Shima binta yayi da kallo,dan tinda yake be taba ganin yarinyar data burgeshi kamar ita bah. </p><p><br /></p><p>Takowa tayi ta karaso wajan iyayan nata ta tsaya, nan suka hau tabata suna mata magana, hannu ta daga musu alamun su dakata. </p><p><br /></p><p>Tsaye Dizhwar ya mike yana kallanta, kafin yace Mata, </p><p> _"Sannu yan mata, na jima ina neman gidanku domin na baki hakuri keda iyayanki bisa abunda nayi miki, nasan nayi kuskure amma bazan kara maimaita makamancin hakan ba, dan Allah kiyi hakuri suma na basu hakuri amma basu cemin komai bah"_</p><p> Yana magana yana.</p><p> Kallan ta. </p><p><br /></p><p>Jin haka yasata ajjiyar zuciya saita tsinci kanta da maida masa magana a hankali, </p><p> _"am, ba haka bane, iyayena basa ji,suna da matsala jine, kayi hakuri"_</p><p><br /></p><p>Murmushi,yayi tare da fadin, </p><p> _"Ba komai kiyi kokarin musu magana yanda zasu gamsu na yi nadama, Sunana, Dizhwar, maybe kin taba jin sunnan ko makamanci haka, Dama abunda ya kawoni kenan, Nagode"_</p><p><br /></p><p>Kasa magana tayi, harya fita daga cikin gidan. </p><p><br /></p><p>Daga ita har iyayan mutuwar tsaye sukayi babu me magana acikinsu. </p><p><br /></p><p>Sai bayan fitarsa, suka kama tambayarta, kasa masu bayanima tayi, tana bin abubuwan daya kowo musu tana mamaki.</p><p><br /></p><p>Ranar batayi niyar zuwa Aiki ba, amma kodan taba Rauda labari saida ta shirya ta tafi. </p><p><br /></p><p>Zuciyarta fal da farin ciki da abun mamaki. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Shikuwa Dizhwar, dariya yayi kamar cikinsa yayi ciwo, sannan yaja motasa yabar kofar gidan, Amma yana mamakin ganin iyayan Laila kurame ita kuma tanaji gata kamar ba yar kasar ba, ga kyau ga gashi komai ta hada, murmushin ya kumayi. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Koda ya dawo gida, kai tsaye part din su yanufa, amma kafin ya karasa yaga kiran Jafar, yana dagawa ya sanar masa yazo babban falo. </p><p><br /></p><p>Nan gabansa ya fadi yasan, sai babbar magana ake haduwa acan. </p><p><br /></p><p>Da sallama ya shiga kamar yanda yayi tsammanin ganin kowa da kowa zaune da alama shi kadai ake jira. </p><p><br /></p><p>Nan ya mika gaisuwarsa ga kowa tukun ya nutsu kamar yanda kowa yayi. </p><p><br /></p><p>Shiru babu me magana kafin daga bisani me Marta yace dasu. </p><p><br /></p><p>_"Kuna ganin yanzu abunda kukayi kun kyauta, kun nunawa duniya cewa bakwa zaune cikin zaman lafiya, wayema yasa ayi celebrating wannan birthday din acikin gidana, meyasa baku da mutunci, ni zaku tozarta a idan jama'a bayan kunsan babu abunda za'ai be fita vah"_,</p><p> nan yayi ta fada ta inda ya shiga bata nan ya fita, bah. </p><p><br /></p><p>BAbu wanda yake magana kowa yayi shiru yana jinsa.</p><p><br /></p><p>Bayan ya gama wannan ya dira da wani sabo. </p><p><br /></p><p>_"Wancan karan na zo muku da magana amma kowa ya gayamin Ra'ayinsa,to wallahi baku isaba, saide duk wanda beji maganata ba yabarmin gidana, kuma maganar aure dana fada babu fashi sai anyita wannan tilas ne, kuma nan da sati biyu za'ai komai dan haka in mutun yana da shirin da zaiyi gwara tun yanzu kuje ku fara na fada kuma bazan canza magana bah"_ </p><p><br /></p><p>Hajiya Babbace tace da shi, </p><p> _"Amma kasan wannan hukunci da ka yanke ba daidai Bane, mumafa muna da hakki akan yaran nan ba bamu dashi bah"_</p><p><br /></p><p>Be mata magana bah,</p><p> Anty Amarya ce tace, _"tunda ya riga ya yanke ai yakamata kowa yabi abunda ya fada, dan be kamata babba yana magana ana masa jayayyabah"_</p><p><br /></p><p>_"ke kuma wa yasa dake bakar munafuka, meyasa wacan karan kika nuna bakya so, har ina magana kina magana sabo da baki da tarbiya"_</p><p> Hajiya Babba ta fada cikin fada. </p><p><br /></p><p>_"Na fada din, ke tarbiyar gareki, ai shima sama yake dake kika saka Masa baki, gakinan Katuwar bakar munafuka, wanda babu abunda ta sani sai Akuyanci"_</p><p><br /></p><p>Nan hajiya babba ta mike tsaye, tana kokarin nufar wajan Ta. </p><p><br /></p><p>Da sauri Fulani ta mike tana fadin, </p><p> _"Haba hajiya kikayi haka girmanki zaki zubar, dan Allah ki rabu da ita"_</p><p><br /></p><p>_"Dallah can matsa ki bani waje, ke dama an gama dake babu abunda zaki iya shiyasa kike fadar hakan ai"_</p><p><br /></p><p>_"Ya isa ya isa haka, bana san hauka, kowa ya tashi ya fita yaban waje"_</p><p> Cewar me martaba. </p><p><br /></p><p>_"wallahi zakisan dani kike wannan zancan"_</p><p> Hajiya Babba ta fada tana jan Zakiyya suka fita. </p><p><br /></p><p>Itama Anty Amarya ranta a bace suka fita daga wajan. </p><p><br /></p><p>Babu wanda aka bari cikin falon sai Dizhwar dame martaba. </p><p><br /></p><p>_"Dan Allah Baba kadan karamin lokaci nifa bana san wannan yarinyar da kake fada"_</p><p><br /></p><p>_"Dizhwar na gama magana, kuma bazaka maidani karamin mutun ba, sabo da haka in baka santa inka aureta ka saketa, kuma in bayan auranku, in yaso duk da wanda ka shirya saika kum aurowa ni ban hana ka ba kuma ka sani bayan auranka da wata biyu zanyi murabus sabo da haka ka shirya"_</p><p> Yana kaiwa nan ya fita daga wajan. </p><p><br /></p><p>Zama Dizhwar yayi, yama rasa abunda yake masa dadi dan bashi da shirin yin duk abunda Baban nasa ya ambata. </p><p><br /></p><p>Kowa kam da bunda ya damesa dan ba shi kadai vane yake da matsa cikin gidan ba. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Lailah tana isa wajan aiki, ta nufi wajan Rauda, nan ta kwashe duk abunda ya faru ta sanar mata. </p><p><br /></p><p>Mamakine ya kama ta, </p><p> _"Lallai Lailah kin ciri tuta kode karya kike, wannan fa wanda yazo nan kika zuba masa coffee wanda muka gani jiya a gidan partyn nan"_</p><p><br /></p><p>_"humm! In kina tantama kizo na kaiki kiga abun mamaki, ga abunda ya kawo mana nan, a ajje a gida"_</p><p><br /></p><p>_"tabdijan, bama saina gani ba wallahi na yarda, amma saide in sanki yake yayi miki haka amma kina ganin wannan da kudinsa da komai har zai tsaya Yana wani baki hakuri"_</p><p><br /></p><p>Daga kafada tayi tare da fadin, </p><p> _"waya sani,nide nayi mamaki"_</p><p><br /></p><p>Shiru Rauda tayi tana jin jina abun acikin ranta. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Fareeda kuwa, kuka tahau yima Anty Amarya dan ita bazata Auri jafar ba saide tabar gidan yanda sarki ya fada, ita za'a yima dole, ita Faisal take so Kuma sun riga sun gama maganar aure dashi za'a mata wata maganar Jafar. </p><p><br /></p><p>Haka tayi ta bata hakuri amma kin hakura tayi, ta hada kayanta ta fita tabar gidan. </p><p><br /></p><p>Anty Amarya tsaye bakin window ta tsaya tana kallnta. </p><p><br /></p><p>_"hmm!, lallai akwai tashin hankali tunda kuwa, Fareeda tabar gida kowa sai ya kuka da kansa, mu zuba mu gani"_</p><p> Abunda ta fada kenan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(9)*</p><p><br /></p><p>*Assalamu Alaikum*</p><p><br /></p><p> *Ina neman afuwa a gareku masoyana, abun alfaharina, kwana biyu nayi rashin lafiya ne, shiyasa bakwa ganin posting dina, ina fatan bakuyi fishi dani bah.*</p><p> _~ina muku fatan alkhairi a duk inda kuke~😍_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_________</p><p><br /></p><p>Koda Laila ta dawo daga wajan aiki zowa tayi ta zauna tana kallan abunda Dizhwar ya kawo Musu, su Mama sunata murna.</p><p><br /></p><p>_______</p><p><br /></p><p>Yaseer kuwa tun ranar daya je wajan Laila ta sanar masa da abunda take so da kuma wanda bata so be kuma zuwa wajan ta ba dan baya san bacin ranta. </p><p><br /></p><p>Yau yana kwance cikin dakinsa, yaji Kiran Daddyn sa, wayar ya dauka ya sanar masa yana zuwa. </p><p><br /></p><p>Tashi yayi ya fita daga dakin ya hau sama dakin sa. </p><p><br /></p><p>Koda yaje Mommy ya gani zaune da Daddyn sai kuma Saudat, ko ba'a fada ba yasan ko maganar menene. </p><p><br /></p><p>Zama yayi kan carpet Bayan yayi musu sannu da gida. </p><p><br /></p><p>Daddyn ne ya kalle shi tare da fadin,</p><p> _"Yaseer ina maganar da mukayi dakai akan yarinyar nan?"_</p><p><br /></p><p>Shiru yayi ya kasa ya magana dan bema san abunda zaici masa bah. </p><p><br /></p><p>_"Magana fa nake maka kana jina"_</p><p><br /></p><p>_"Dan Allah Daddy kayi hakuri kadan karamin lokaci"_</p><p><br /></p><p>_"Bana san wani dogun bayani, zabin da muka maka shine baka so Kenan,yarinyar yar uwar kace, taya zaka ce baka santa?"_</p><p><br /></p><p>Shiru yayi kafin yace, </p><p> _"Dad ni ban taba gaya mata bana santa bah"_</p><p><br /></p><p>_"Toh in baka gaya mata bah, amma ai alamu sun nuna"_</p><p><br /></p><p>_"Yaseer"_</p><p>Daddyn ya kuma kiran sunan sah. </p><p><br /></p><p>_"Naam"_</p><p><br /></p><p>_"Meyasa kake san maidamu kananan yara? "_</p><p><br /></p><p>Shiru babu amsa, Daddyn yaci gaba da magana. </p><p><br /></p><p>_"In har da gaske baka furta kalmar daka furta bah, toh ina so Kafin ka koma ayi auranku da Saudat kafi da matar ka"_</p><p><br /></p><p>Wani iri yaji kamar an kwada masa guduma a tsakiyar kansa</p><p><br /></p><p>Shiru yayi dan bashi da bakin magana. </p><p><br /></p><p>_"Magana nake maka kayi shiru"_</p><p><br /></p><p>_"Dan Allah Dad kadan dada min lokaci, ni akwai wanda nayima alkawarin aurene shiyasa"_</p><p><br /></p><p>Kallansa suka tsaya sunayi har Saudat din. </p><p><br /></p><p>_"Wacece? "_</p><p><br /></p><p>Tambayar data fito saga bakin Daddyn kenan. </p><p><br /></p><p>_"Daddy yar gidan malam Muktar kurma nake So Laila"_</p><p><br /></p><p>Shiru Daddy yayi, Mommy ce ta fara badin, </p><p><br /></p><p>_"Wallahi baka isa ba, wannan yaran fa bashi da hankali, taya zaka auri wannan yarinyar da bata da gata, wallahi bazamu hada zuria da kurame bah, Allah ya kiyayye"_</p><p><br /></p><p>_"Dakata mariya"_</p><p>Daddy ya fada yana kallan Yaseer da kansa yake a kasa. </p><p><br /></p><p>_"Yaseer da gaske kana san yarinyar kuma itama tana sanka?"_</p><p><br /></p><p>Da sauri ya dago da kansa jin tambayar da Daddyn yayi masa, Murmushi ya danyi, tare da fadin, </p><p> _"Sosaima kuwa, Dad, dan Allah kaima karka ce bazan aureta bah"_</p><p><br /></p><p>_"Shikenan, tashi kaje zanyi magana dakai nan da kwan biyu, zan samu mahaifin yarinyar nayi masa magana,inyaso kaima saika mata,tashi kaje"_</p><p><br /></p><p>Wani dadine ya cika Zuciyarsa dan yama kasa boye farin cikin sa gaban iyayan nasa. </p><p><br /></p><p>Saudat kuwa fashewa tayi da kuka, yayin da Mommy tahau fada, bayan fitar Sa kenan, </p><p><br /></p><p>Daddy ya kalli Saudat tare da fadin, </p><p> _"Ki kwantar da hankalinki, karki samu damuwa kinji, in Allah yayi mijin kine shi zaki aure shi inde darai da lafiya"_</p><p><br /></p><p>Haka ta mike tana kuka jikinta duk ya mutu, haka zalika, itama Mommy haka ya mike ya barta anan tana ta faman fada da masifa, kan Ya daurewa dansa gindi yana abinda yaga dama. </p><p><br /></p><p>_______</p><p><br /></p><p>Bayan kwan biyu, Lailah ta kasa jurewa, bata da aiki sai tunanin Dizhwar, fatan ta Allah yasa santa yake har yayi mata wannan abu, dan tabbas ta rasa abunda yake damunta bata da aiki sai fegensa, haka yau da taje wajan aiki babu abunda ta tabuka sai tunaninsa, haka aka sauke ta daga taxi ta fito tana Mika masa kudinsa. </p><p><br /></p><p>Ganin wata hadaddiyar mota kofar gidansu yasata jin wani irin farin ciki da sauri ta shiga tana murna, ganin Dizhwar zaune kan tabarma yasa tayi turus! Tana kallansa. </p><p><br /></p><p>Shima daga kansa yayi yana kallan nata, sai kuma ta tsinci kanta dajin kunya dan tasan ya gane tana murna da ganinsa. </p><p><br /></p><p>Wani arnan Murmushi ya sakar mata, tare da dauke kansa. </p><p><br /></p><p>Ahankali ta karaso wajansa, tama Kasa kai jakar tata cikin daki, zama tayi tare da fadin, </p><p> _"Sannu da zuwa"_</p><p><br /></p><p>_"Yawwah"_ </p><p>ya fada yana kallan ta,</p><p><br /></p><p>_"Na jima anan ina jiranki, haka aikin naki yake sai wannan time din kuke tashi, gaskiya bana san kina kaiwa haka a waje ga wanan hawala da kuke sha, ta zirga zirga"_</p><p><br /></p><p>murmushi ta saki tana wasa da yan yatsun hannunta kanta a kasa. </p><p><br /></p><p>Leka fuskar tata yayi yana murmushi, </p><p> _"Nifa har yanzu ba'a gayamin sunan abokiyar fadan nawa bah"_</p><p><br /></p><p>kunya taji harda rufe ido, cikin sanyin murya ta furta, </p><p> _"Laila Muktar"_</p><p><br /></p><p>_"Wow suna me dadi, kinga nan gaba kuma saiki koma, </p><p> _" *LAILAH-DIZHWAR* "_</p><p><br /></p><p>Shiru tayi bata ce komai ba, dan tama rasa a wani, Stage take tsabar murna da kuma mamaki, tama kasa yarda dan sarkine cikin gidansu kan tsohuwar tabarma yana hira da ita, unbelievable!. </p><p><br /></p><p>_"Lailah kinyi shiru, ko na takura miki ne?"_</p><p><br /></p><p>_"Aa"_</p><p><br /></p><p>_"Toh kunya ta kike ji? "_</p><p><br /></p><p>_"Aa"_</p><p><br /></p><p>_"Meyasa bakya san yimin magana, nima fa haka nake bana san yin magana, amma sai na tsinci kaina ina miki Surutu haka"_</p><p><br /></p><p>_"Nasani ai"_</p><p>Ta fada tare da kallansa. </p><p><br /></p><p>Yana dago kansa suka hada ido tayi maza ta sauke idanta kasa. </p><p><br /></p><p>_"me kika sani toh? "_</p><p><br /></p><p>_"Nasan yayan sarki ko yayan masu kudi basa san yin magana da yawa"_</p><p><br /></p><p>Murmushi yayi me sauti, sannan yace da ita, </p><p> _"Hm haka kika fahimta kenan?,_</p><p> _toh Laila ba haka bane, ya danganta da yanayin mutun, kin gane, kema ai bakya san yin maganar tunda gashi ni harma na fiki yin maganar ke kuma yar gidan President ce?"_</p><p><br /></p><p>Girgiza kai tayi, alamun aa. </p><p><br /></p><p>Agogon hannunsa ya duba tare da fadin, </p><p> _"Dare fa yanayi, karnaje a zaneni a gida bara na tashi na tafi"_</p><p> Ya fada yana mekewa, takalmansa dama suna kafarsa, haka ya fita daga gidan, tana biye dashi a baya har bakin motarsa.</p><p><br /></p><p>Bayan ya shiga ita kuma tana daga jikin glass din, </p><p><br /></p><p>Hasken wayarsa ya haska fuskarta,</p><p>murmushi yayi tare da fadin, </p><p> _"Zan tafi sai kuma in an dan kwana biyu, duk da nasan bazan iya jurewa rashin ganin wannan kyakyawar fuskar taki da kuma wannan muryar me dadi bah, kina da waya?"_</p><p><br /></p><p>_"Eh"_</p><p><br /></p><p>Tana fadar haka ya zira hannunsa gefe, ya miko mata wata waya, kirar *'Samsung X6 edge plus'*,amsa tayi tare da fadin,</p><p> _"Wannan fa?"_</p><p><br /></p><p>_"Ki riketa zan kiraki, bana san kowa ya kiraki ciki saini, kinji Lailah Lollipop"_</p><p><br /></p><p>Bata iya magana ba, illah gyada masa kai kawai da tayi. </p><p><br /></p><p>Nan yayi mata sallama yaja motarsa yabar kofar gidan. </p><p><br /></p><p>Daida lokacin, Yaseer yake kokarin shiga gida, ganin Lailah a tsaye ga wani yabar wajanta yasa zuciyasa susa, abun be masa dadi ba hakan yasa itama ta tsaya tana kallansa, ciki yayi da motar yayin da itama ta shige gida ta kulle. </p><p><br /></p><p>Da gudu ta shiga daki, ta zauna tana kallan wayar, ko ba'a fada ba tasan wayar nada tsada, dadi taji sosai wayar tayi mata kyau, tana kunna screen din wayar taga pic dinsa, wani sanyi taji cikin ranta tare da shafawa tana murmushi. </p><p><br /></p><p>_"Ya Allah"_</p><p> Ta fada dan gaba daya Dizhwar ya kwace mata zuciya, ta gama nisa cikin dunbin soyayyar sah. </p><p><br /></p><p>Da baya ta fada kan gadon ta kwanta tare da fadin, </p><p>*_"LAILAH-DIZHWAR!"_*</p><p> Sunan yayi mata dadi, kara dago wayar tayi ta kunna screen din tana kallan fuskarsa, da murmshinsa. </p><p><br /></p><p>Ganin bata da aiki sai Wannan,yasa ta mike zaune tare da ajje wayar ta shiga cire kayan jikin ta, wanka taje tayi, time din data dawo taga missed call, </p><p> Da sauri ta dauka ta zauna gefan gadan tasan shine ma ya kira, sai taji dama bata shiga wankan bah, tsaki tayi tana kokarina ajjewa taji ya kuma Kira.</p><p><br /></p><p>Da sauri ta shiga kkarin dagawa, karawa tayi a kunne har tana kokarin subucewa. </p><p><br /></p><p>Sallama tayi tare da yin shiru dan jin abunda zai biyo baya. </p><p><br /></p><p>_"Sarauniyar kyawawa na duniya gaba daya, ayimin hakuri na kasa jure rashin muryarki shiyasa kika ga na dameki da kira"_</p><p><br /></p><p>_"Kayi hakuri, wallahi ina wanka ne Shiyasa ban daga bah"_</p><p><br /></p><p>_"Ohk yayi"_</p><p><br /></p><p>_"Kaje gida lafiya?"_</p><p><br /></p><p>_"Lafiya qlau, wallahi na tafi cike da kewanki fa"_</p><p><br /></p><p>Dadi taji ta yarda har ta kasa tsayiwa saida ta zauna. </p><p><br /></p><p>_"Lailah"_</p><p> Ya fadi Sunan tah.</p><p><br /></p><p>_"Wayyo!"_</p><p> Ta fada cikin ranta dan jin yanda ya kirayi sunan nata kamar yafi kowa Iyawa. </p><p><br /></p><p>_"Zaki aureni?"_</p><p><br /></p><p>Da sauri ta kashe wayar, </p><p><br /></p><p>_"Innalillahi wa'inna illaihir raji'un, wayyo wayyo wayyooooh! "_</p><p><br /></p><p>Da gudu ta fito waje tayi tsalle ta koma daki tana ihu. </p><p><br /></p><p>Kasancewar Iyayanta kuramene duk bidiri datake basu sani ba. </p><p><br /></p><p>Komawa tayi ta dauki wayar tana dariya da ihu, </p><p> _"La'ilah! Dizhwar waye zaice baya sanka, wallahi ina sanka Wayyo Allah yasa da gaske yake ina sanshi wallahi"_</p><p> Abunda Lailah ke fada da karfi kenan dan gani take kamar mafarki take. </p><p><br /></p><p>Kallan wayar take tayi tana jira Ya kuma Kira. </p><p><br /></p><p>Har 12am, amma Be kira ba haka ta kwanta badan tana jin baccin bah.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(10)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shikuwa Yaseer tunda ya shiga gida kasa sukuni yayi, har kara fitowa yayi ya duba wajan ko zai kuma ganinta amma bega kowa bah.</p><p><br /></p><p>Cikin gida ya koma ya shiga daki, abun yana bashi mamaki, </p><p> Kenan bayan shi akwai wanda Laila take so shiyasa ta ki amsar soyayyar sah, haka yayita yawo cikin daki yana sake sake kala kala, daran ranar de beyi bacci bah. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Washe gari, ya kama lahadi, dan haka Lailah bata zuwa aiki duk ranar, </p><p> tana kwance cikin dakin tana jiran kiran Dizhwar, amma har lokacin be kira ta bah. </p><p><br /></p><p>Abbanta taga ya shigo daki ya nuna mata ta saka hijab, sunyi bako, tazo zasuyi magana. </p><p><br /></p><p>Mamaki ya kamata, dan ita duk a tunaninta Dizhwar ne, fuskata cike da murmushi da farin ciki, ta saka ta biyo bayan sah, a bunda ya bata mamaki ganin Daddyn Yaseer, </p><p> Da sauri ta durkusa tare da gaida shi. </p><p><br /></p><p>Cikin fara'a da walwala ya amsa mata tare da fadin. </p><p><br /></p><p>_"Kasancewar iyayanki kuramene, inaso zan yi magana daku, bana san ki boye musu abu daya duk abunda na fada miki ki gaya musu"_</p><p><br /></p><p>Kanta yana kasa ta amince da abunda ya fada mata. </p><p><br /></p><p>_"Lailah kina san Yaseer?"_</p><p><br /></p><p>Shiru tayi tama rasa amsar da zata bashi, dan yanda tayi tunin Daddy zai kasance sai kuma taga ba haka bah, sai kuma ta kama jin kunya karta ce bata san danshi yaji babu dadi tunda harya tako yazo da kansa, amma tabbas tasan zata cuci kanta, haka zata hakura, duk wanda Allah yayi shine mijinta haka zata hakura ta aureshi. </p><p><br /></p><p>Cikin jin kunya tace dashi,</p><p>_"Eh"_</p><p><br /></p><p>Kallanta yaci gaba dayi tare da fadin, </p><p> _"Yanzu ina ce miki, zakuyi aure dashi, kuna da kudin da zakuyi dukkan abunda ake bukata in za'a aurar da yarinya"_</p><p><br /></p><p>Shiru tayi dan babu abunda ta dogara dashi sai aikin tah, </p><p> _"Aa Daddy, dama koda auran za'a saka, sai an saka mana da yawa sabo da babu kudi kuma bamu shirya hakan bah"_</p><p><br /></p><p>Dariya yayi tare da fadin, </p><p> _"Ai koda an saka muku me yawan bazaku taba samun kudin bah, sabo da tsiya a gindinku take,in banda karfin hali ma, menene ya kaiki har zakiyi soyayya da wanda yake giwa a bangaran kudi, ke kuma ko Kiyashi vaki kai bah, kenan abunda aka fada gaskiyane, kun asirce Yaseer shiyasa kike juyashi yanda kika ga dama?"_</p><p> </p><p>Jin haka yasa gaban Laila faduwa tayi maza ta dago tana kallan sah. </p><p><br /></p><p>Shikuwa Abba yana gefe yana kallansu, sabo da yanayin yanda Daddyn yake magana kamar ba baka yake fada bah. </p><p><br /></p><p>Kwallah ce ta cika idanta, kamar zata fashe da kuka haka take ji. </p><p><br /></p><p>_"Wallahi wallahi, inma ku dangin mayune, munfi karfinku, dan bazamu taba hada jini da matsiyata nakasasau irin ku bah, sabo da haka zan baki zabi daya cikin biyu, na farko koku hada kayanku da komai naku, kubar unguwar nan, ku tafi can inda bazaku hadu da Yaseer vah, ko kuma ni insa a dauke ku harsai bayan bikinsa da yarinyar danake so tukun a maidoku, na baku nan da kwana uku"_</p><p><br /></p><p>Kukane yaci karfin Laila, kasancewar a cikin Hijab take yasa Abba be gani bah, tayi dana sanin abunda ta fada, sai ta tsinci kanta da tsanar kanta. </p><p><br /></p><p>Yana gama fadar haka ya mike ya tafi,batare daya yima Abban sallama bah. </p><p><br /></p><p>tana fita, ta mike da gudu ta shige toilet ta kulle ta fashe da kuka me karfi. </p><p><br /></p><p>Ganin haka yasa Abbanta mikewa da sauri yana buga kofa da karfi, alamun ta bude masa, Mama data fito taga abunda ke faruwa itama ta taya shi, haka sukaita bugawa, tana jin su amma saida tayi kuka me isarta tukun ta bude.</p><p><br /></p><p>Binta sukayi da kallo suna, tambayarta abunda ya faru, idanta yayi jajir fuskata ta canza kama dukta kumbura. </p><p><br /></p><p>Nan suka tsareta saida tayi musu bayanin komai, </p><p><br /></p><p>Abban ne ya kama kuka, yana nuna hannayansu da Allah ya taimake su ya barsu dan su zauna ya rufa musu asiri. </p><p><br /></p><p>Itama kuka Laila take yi, dan tasan babu inda zasuje inba a titi zasu kwana va, gashi ta kusan siyan wannan gidan gaba daya. </p><p><br /></p><p>Dabara ce ta fado mata ta a saida gidan, sai ta biya wancan mutumin cikon kudinsa, sauran kuma saisu kama haya kafin Allah ya hore. </p><p><br /></p><p>Amma sai Abba yaki yarda yace lallai saide in su hadu suje su gayawa Aminu matsalar su, inyaso duk abunda ya yanke saisuma susan abinyi. </p><p><br /></p><p>Amma Lailah fir taki yarda akan abunda ya fada, haka shima ya kafe dole suka hakura suka shirya domin zuwa wajan nasa. </p><p><br /></p><p>_________</p><p>Koda suka isa, kasancewar me gadin gidan ya san Abba ya bude masa suna gaisawa, </p><p><br /></p><p>Abbane ya yima laila magana kanta tambayi me gadin ko Aminu yana ciki. </p><p><br /></p><p>Nan ta tambaya ya sanar musu da baya nan amma yana kan hanyar dawowa. </p><p><br /></p><p>Shiyayi musu rakiya har cikin gidan. </p><p><br /></p><p>Tunda Lailah take bata taba shiga gidan ko daya daga cikin su ba, nan Su Abba suka shiga kallan gidan suna mamaki wai nan gidan dansune, amma su gasu suna yawo suna neman gidan da zasu zauna, Mama kuka ta fara, amma bata bari kowa ya fahimci hakan ba. </p><p><br /></p><p>Nan suka rabe gefe daya, suka zauna, me gadinne ya shiga ya sanar wa da matar sa zuwansu. </p><p><br /></p><p>Nan ta sanar masa daya gaya musu su jira anan tukun yazo. </p><p><br /></p><p>Nan yazo ya gayawa Laila duk da bata ji dadi ba, ji take kamar ta fita daga cikin gidan. </p><p><br /></p><p>Abba da Mama suka zauna kan tiles suna jiransa, yayin da Laila take tsaye dan taki zama. </p><p><br /></p><p>Tunda suka tsaya anan kusan awa daya babu wanda yazo wajansu. </p><p><br /></p><p>Sai can tukun sai ga wata me aiki ta shigo tace dasu da su shiga ciki.</p><p><br /></p><p>Wani katan falo aka shiga dasu, suka zauna kan carpet, yayin da basu jima da zama ba, Aminu ya fito ransa a bace dan beji dadin zuwan su bah,</p><p><br /></p><p>Suna ganinsa suka fara dariya, farinciki amam banda Lailah. </p><p><br /></p><p>Zama yayi kan kujera tare da gaida su yanda suka saba da kurmanci. </p><p><br /></p><p>Kallan Laila yayi, tare da fadin, </p><p> _"Ke dake zanyi magana tunda su basa ji ni yanzu bana gane wannan abunda suke yi"_</p><p><br /></p><p>Kai kawai ta iya gyada masa dan zata iya fashewa da kuka tsabar bakin ciki. </p><p><br /></p><p>_"Menene kuka zo gaba dayanku? "_</p><p> Aminu ya tambayi Lailah. </p><p><br /></p><p>Kallan Abba tayi, yayin da yayi mata nuni, </p><p>_"da ki gaya masa so muke ya sama mana inda zamu, zauna koya sama. mana gidan haya"_</p><p><br /></p><p>Nan ta gaya masa. </p><p><br /></p><p>_"Gida kuma, ina gidan da kuke zaune, wannan be isheku bah, wani gida kuma kuke bukata?"_</p><p><br /></p><p>_"Yaya wancan fa gidan haya ne kuma me gidan yana san amfani da abunsa shiyasa ya ce zai tashemu nan da kwana uku"_</p><p> Laila ta fada tana kallansa. </p><p><br /></p><p>Shiru yayi kafin daga bisani,yace da ita, </p><p> _"Gaskiya yanzu hidima tayi min yawa, akwai bikin kanwar matata, da nake rukwanta ,nan da sati biyu, kuma ga hidimar gida, kuma nan gidan yayi mana kadan in nace zan zauna daku, zaku takurawa matata da kuma yarana, abunda nakeso dake yanzu shine, zan baki dubu biyar, inyaso saiku samu cuko wajan masu taimako, saiku hada ku kama ko daki daya ne, kafin nima in asamu kudi"_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(11)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Aminu ya fada yana kallan Lailah.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shiru tayi tana jin sa, dan kadan ya hana ta hadiyi zuciya ta mutu tsabar bakin ciki.</p><p><br /></p><p>_"Yanaji kinyi shiru, shawara na baku, ki gaya musu kiji me suka yanke hukunci"_</p><p><br /></p><p>Mikewa tayi tsaye tare da nunawa su,Mama su tashi su tafi, kallansu tayi tana hawaye ta nuna musu da hannu kamar haka, </p><p> _"Nida ku, zamuyi magana ta fahimta, karku saka mana baki, komai zai zama daidai, zamu samu gida me kyau, kunji karku damu"_</p><p><br /></p><p>_"Mungode Yaya kuma Allah da ya haliccemu bazai hana mu gurin zama ba, bama san kudin ka mungode"_</p><p><br /></p><p>Tana fadar haka ta juya, tare da jan iyayan nata. </p><p><br /></p><p>_"Ga #500,ku hau mota naga sun tsufa da yawa karki basu wahalar tafiya a kafa"_</p><p><br /></p><p>Jin abunda ya fada tasa bazata iya jurewa bah, ta juya a fusace, ta amshi kudin tare da Yayyagasu ta watsa masa sannan tace dashi, </p><p> _"Lokacin da zamu zo aiba kai ka bamu kudin ba, da har yanzu zaka bamu wata tsinanniyar dari biyar dinka, Wallahi kuji tsoran Allah, sai kunyi nadamar abunda kukeyi"_</p><p><br /></p><p>Tana fadar haka ya wanka mata mari, da sauri Abba ya karaso tare da wanka masa shima marin,cikin zafin nama ya juya zai rama, ganin haka yasa Mama itama ta mareshi. </p><p><br /></p><p>Lokacin yayi daidai da fitowar matarsa da kuma yaransa guda biyu. </p><p><br /></p><p>_"Ni kike gayawa wanann maganar sabo da basu baki tarbiya me kyau bah"_</p><p><br /></p><p>Lailah tana kuka tace dashi, </p><p> _"Anyi maka rashin kunyar, kai yanzu ba iyayanka kake dagawa hannu ba, zaka mara bah, wallahi na kuma fada saikun hulakanta, sai kun zama abun gudu,tsinannu wanda basu san darajar iyayansu bah"_</p><p><br /></p><p>Jin haka yasa ta kuma tinzira Aminu, yayo kanta zai doketa, yatsa ta nuna masa tana hawaye , tare da fada masa, </p><p> _"Wallahi kasake ka tabani sai kayi nadama, saina maka sharrin da bazaka taba mantawa dani bah"_</p><p><br /></p><p>_"ke meyasa baki da tarbiya"_</p><p> Matar Aminun ta fada. </p><p><br /></p><p>Rasa abunda Lailah zatace da ita tayi, tayi kukan kura tare da shakar ta nan suka hau dambe, duk da yanda Laila take kamar Baby doll, amma tafi Nusaiba, karfi. </p><p><br /></p><p>Da yar Aminu ya raba su, su Mama suka ja Lailah, nan tayi ta zaginsu tana tsine musu har suka fita daga gidan. </p><p><br /></p><p>Bakin gate ta zube ta hau kuka tana bakin cikin abunda aka musu, gaba dayansu kuka suke, abun abun tausayi. </p><p><br /></p><p>Haka ta dawo lallashin iyayan nata, harta tare musu Taxi suka nufi gida, kowa ransa babu dadi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_____</p><p>Bayan tafiyarsu matar Aminu Nusaiba, ta fara kuka tana fadin, </p><p> _"Nagode ai kana sane ka bari kanwarka ta dakeni a gaban yaranka, Nagode"_ </p><p>tana fadar haka ta mike, ta shige daki ya bita yana mata magana amma ta kulle kofa, komawa yayi ya zauna kan sofa yana bakin cikin zuwansu zasu tayar masa da hankalin gidansa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>________</p><p>Koda suka koma gida,kowa ransa babu dadi, tana kwance cikin daki ta rasa abunda yake mata dadi, kiran Dizhwar ne ya fara shigowa wayar ta. </p><p><br /></p><p>kamar ta daga amma ta fasa, tunda yanzu gashi tace tana san dan da be kai Dizhwar ba, an janyo mata bala'i yanzu inta ce tana san Dizhwar killa danginsa kasheta zasuyi.</p><p><br /></p><p>Da sauri ta janyo wayar dan bazata iya hakura ba, sabo da san da take masa, tana daga wayar ta fashe da kuka. </p><p><br /></p><p>Hankalinsane ya tashi jin tana kuka, ya rikice ya fara tambayarta abunda ya faru, nan da nan ya gaya mata yana nan zuwa. </p><p><br /></p><p>Bayan ya katse, wayar gefe ta tura ta taci gaba da goge Hawayanta jikinta duk yayi jajir, haka idanta. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Bata jima da gama waya dashi ba, taga kiransa ya shigo yana kofar gida. </p><p><br /></p><p>Mikewa tayi, ta zira Hijab dinta ta fita daga cikin dakin, tana ganin motar tasa ta karasa ta bude tare da shiga ta kullo kofar. </p><p><br /></p><p>Kallo daya yayi mata yasan tana cikin damuwa. </p><p><br /></p><p>_"Princess Lafiya kike kuka, wanene ya taba ki, gaba daya kin daga min hankali"_</p><p><br /></p><p>Jin haka yasa ta kuma fashewa da kukan ta juyo tana masa magana cikin kukan, </p><p> _"Bansan yaya zanyi ba da rayuwata ba, kasancewar halin da muke ciki da kuma larurar da Allah ya bawa iyayena, hakan yasa babu wanda yake kaunar mu, babu me san mu rabeshi koda jinin mune, yaya zamuyi yanzu,Dan Allah Dizhwar karka gujemu kaima, kaine kawai me kaunarmu, Allah ne gatanmu, kaine me taimakon mu, inka gujemu bansan yaya zanmuyi ba"_</p><p> Ta kuma fashewa da wani saban kukan. </p><p><br /></p><p>Karo na farko daya fara jin tausayin wata ya mace a duniya bayan yan uwansa da mahaifiyarsa. </p><p><br /></p><p>_"Ki kwantar da hankalinki, koba dan soyayya ba, zan taimaka muku domin Allah, zan share muku hawayanku badan komai ba sai dan Allah"_</p><p><br /></p><p>Dadi taji sosai cikin ranta, kuma kallan ta yayi tare da fadin, </p><p> _"Lailah kibar kuka mana, bakisan kukannan yana taba min zuciya bah, Inde *LAILAH-DIZHWAR* ce ta goge hawayanta"_</p><p><br /></p><p>Dagowa tayi ta shiga gogewa, tana Murmushi, </p><p><br /></p><p>_"Ywwah, toh yanzu a gaya ma Dizhwar menene matsalar Lailar sah, kokuma ya hadiyi zuciya ya mutu"_</p><p><br /></p><p>Da sauri ta juyo ta kalleshi da jajayan idanta, tare da fadin,</p><p> _"Gidan da muke cikine aka tashemu, kuma ni aikin da nake ba wani bane da har zan iya kama Mana haya da kudin, dashi muka dogara, abincin mu, rashin lafiya da sauransu"_</p><p><br /></p><p>Sai Kuma tayi shiru, dan abun baya mata dadi, tasan da tayi karato kamar wanda su yaya Ahmad sukayi, zata taimakawa iyayanta amma iya secondary ta tsaya itama din yau taje gobe babu kudin makaranta. </p><p><br /></p><p>_"Insha Allah duk wannan ba matsala bane, a wata unguwa ko gari ko kasa kike san asiya muku gida"_</p><p><br /></p><p>Wani sanyi taji acikin ranta, ji take tamkar ta rungume Dizhwar tsabar farin ciki.</p><p><br /></p><p>_"Ni bani da zabi dik inda Dizhwar ya zaba toh yayima Lailah"_</p><p><br /></p><p>_"hhhh, toh yanzu kam kin yima Dizhwar wayo, amma next time, dole *LAILAH-DIZHWAR*,ta kasance special ce kuma classic lady, ba kamar sauran Lailar jama'a take ba"_</p><p><br /></p><p>Sun jima suna hira, saida ya tabbata babu wata damuwa cikin ranta tunkun yayi mata alkwarin gobe zaizo har gida ya dauketa ya kaita gidan daya siya musu. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Muje zuwa*😇</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(12)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ko bayan Lailah ta koma gida, zuciyarta cike da farincikin, wannan alkawarin da Dizhwar yayi mata.</p><p><br /></p><p>Tana shiga ta samu iyayanta ta sanar dasu, da farko Mama kin yarda tayi, saida Lailah ta dage tukun dan itama bata san wulakanci. </p><p><br /></p><p>Haka kuwa akayi washe gari, bayan sallar azzhr, Dizhwar ya kira lailah ta fita. </p><p><br /></p><p>Bayan sun gaisa yayi mata albishir da Gida daya sama musu, murna kamar ta hadiye Dizhwar haka Lailah take ji. </p><p><br /></p><p>Cike da farin ciki, ya gaya mata su shirya, zai aiko an jima a tafi dasu. </p><p><br /></p><p>Nan Lailah ta koma tana ta faman farin ciki ta hada duk abunda tasan zata bukata, haka suma iyayan, amma basu daukar kayan su na Katako bah, dan a tunanin su, aro ya basu zasu tafiyar Yaseer da Amaryar sah. </p><p><br /></p><p>Yamma nayi, kuwa mota tayi parking kofar gida su, Lailah nan suka shiga aka tafi dasu saban gidansu da yake a, Unguwar Kaura. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_________</p><p>Mamakine ya kama Su gaba daya ganin gidan da Dizhwar din ya saka a kaisu, gidane har gida amma flat ne, yana da kyau iya kyau,ga wadatattun dakuna, sannan babu abunda suka rasa acikinsa, tun daga kan kayan furnitures har zuwa kayan abinci, ba karamin mamaki Lailah tayi ba dan ko amafarki bata tunanin nan kusa zata rayu a gida irin wannan. </p><p><br /></p><p>Haka sukaita shiga suna fita daga daki zuwa daki, parlor daya ne sai bedroom har guda uku kowanne da toilet a cikinsa, sai kuma kitchen da dining area, haka zalika akwai, wajan parking space a harabar gidan da kuma wajan me gadi, sai wajan da aka yishi tamkar karamin garden flowers ne kala kala, gaskiya gidan yayi kyau sosai. </p><p><br /></p><p>Nan da nan kuwa suka raba dakuna, kowanne ya zabi guda daya, Lailah zama tayi cikin dakin ta, kan gado tana faman kallan ko ina a dakin, fadawa tayi kan gado tana maida numfashi, ga wani sanyi da yake shiga illahirin dukkan wata kofa dake jikin ta. </p><p><br /></p><p>Ta jima nan kwance idanuntah a lumshe, mikewa tayi ta shiga toilet dan yin wanka, bayan ta gama ta fito, cikin kayanta masu kyau data dauko ta zaba ta saka. </p><p><br /></p><p>Tayi kyau sosai gashin nan yasha gyara har gadan bayantah tukun,ta zauna tana kallan kanta, bayan ta gama kalle kalle, fita tayi inda ta samu Abbanta da Kuma Mama zaune a falo suna hira. </p><p><br /></p><p>Ba karamin dadi taji ba ganinsu tare haka cikin nishadi, jingina jikinta tayi jikin bango tana kwallah,yau gashi Allah ya kashe ya basu, sanadinta suna cikin jin dadi, wanda dama burinta be huce ta kyautatama iyayanta bah. </p><p><br /></p><p>Wayar tace da tayi kara, yasa ta dawo tunanin da take, dubawa tayi tare da yin murmushi, mayafinta ta yafa ta fita. </p><p><br /></p><p>Yana cikin mota a zaune, tunda ta fito yake binta da kallo harta karaso wajansa. </p><p><br /></p><p>Cikin motar ta bude ta shiga, batare da yayi magana ba ta, rungumeshi tana kuka. </p><p><br /></p><p>Shikuwa kasa hanata yayi, illah bayanta daya fara shafawa yana lallashinta. </p><p><br /></p><p>_"Nagode,Nagode Dizhwar, ina sanka kamar yanda kaima kake sona kuma insha Allah bazan taba cin amanarka ba dan Allah nima kamin alkawarin har abada xaka kasance tare dani, bazaka karyamin zuciya bah, zan maka dukkan biyayyar da mace takewa mijin ta, karka saka in shiga wani hali wallahi ina sanka"_</p><p> Ta karashe maganar tana kuka. </p><p><br /></p><p>Kara rungumetah yayi yana murmushi batare daya ce mata komai bah. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Yau Yaseer yayi niyar komai Lailah zata mai saide tamai amma sai ta gaya masa waye wanda ya gansu tare da dadare. </p><p><br /></p><p>Koda yazo gidan ga mamakinsa yaji gidan a kulle. </p><p><br /></p><p>Hannu yasa ya taba kwadan tare da zaro wayarsa daga aljihu. </p><p><br /></p><p>Amma koda ya kira wayar tata bata shiga,da sauri ya kuma gwadawa amma still switch off, gaban sani yayi mugun faduwa. </p><p><br /></p><p>Nan yayita kira kamar wanda ya zauce dan bama ya sauraran maganar computer. </p><p><br /></p><p>Cikin zuciyarsa salati kawai yake, karde sun tashi daga gidan, ina Lailar sa ta tafi ta barsa. </p><p><br /></p><p>Nan hankalin Yaseer ya rashi, haka yayita tsayiwa anan gashi babu wanda zai tambaya. </p><p><br /></p><p>Haka ya hakura ya koma gida jikinsa duk a sanyaye. </p><p><br /></p><p>Yasan babu yanda zaiyi, gashi gobe ne ranar da Daddyn sa ya daukar masa. </p><p><br /></p><p>_________</p><p>Kasancewar biki ya matso shiyasa Aka shiga shirye shirye gidan Mai martaba,dan har Hjy Bilki ta dawo nan, </p><p><br /></p><p>Kasancewar Fareeda tabar gida yasa ran sarki ya bace dan haka ya yanke hukunci hada auran Jafar da Asiya. </p><p><br /></p><p>Shima Kasan yayi farin ciki da haka, domin koba komai suna dasawa da Asiya amma be sani ba ko ita tana da wanda take so. </p><p> Shine damuwarsa, Karta ki yarda. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ban garan Asiya kuwa babu wanda ya kaita farin ciki, sabo da dama faduwace tazo daidai da zama domin duk duniya babu wanda take so fiye da Jafar. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_________</p><p>Yaune Ranar da za'a kai lefe, kuma ranar da Za'a kawo na gidan sarki, dan haka falani ce tasa ayi abincin kala kala na taryar baki, daga na bangaran Hajiya Babbah harna wajan ta domin ita babu damuwa ko daya cikin ranta. </p><p><br /></p><p>Shikuwa Dizhwar da Jafar basu suka hada lefan su ba, gaba daya Hajiya Bilki ita ta hada musu,da kudin da Sarki ya bada. </p><p><br /></p><p>Kowanne akwati 24,da key din mota, haka aka hada musu gashi gaba daya babu kananan kaya harkar girma akayi. </p><p><br /></p><p>Dan gin Babban jafar yan kano suma ranar zasu zo, haka nan dangin Sarki suna nan mata zasu shirya suma dan kai na Dizhwar, yayin da can Family na Waziri zasu kawo na Zakiyya. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Bayan sallar azzhr, motoci suka fara shigowa cikin gidan sarki kala kala, anata faman buda, familyn Waziri ne suka iso dan kawo lefan Zakiyya, kai tsaye Part din Hajiya Babba aka nufa dasu, dama itama Nata dangin suna nan cike da falon ta.</p><p> Zakiyya kuwa banda kuka babu abunda takeyi dan itama bata sanshi. </p><p><br /></p><p>Da buda suka shiga, haka aka dinga shiga da akwatinan nan,mata Manya da yan mata ko wacce cikin shigar alfarma, duk suka nemi waje suka zauna. </p><p><br /></p><p>Tunda suka shigo babu wanda ya kulasu ko kuma ya kalle su, hakan yasa jikinsu ya fara sanyi. </p><p><br /></p><p>Nan suka zazzauna ga kuma Kayansu sun saka su Gaba,ganin babu wanda ya kulasu suke shirin kokarin tashi su tafi. </p><p><br /></p><p>Hajiya Babbace ta fito tare da fadin, </p><p><br /></p><p>_"Sannuku da zuwa, kwadayayyu dangin mayu, wato Kun dauko kafa da wasu ban zayan kayanku wanda basu kai sun kawo Ba har kuka cikawa mutane gida da ihu, sabo da wannan watsatstsun kayan dako kuyangata aka kawowa bazan yarda ta amsa bah"_</p><p> Nan suka hau kalan kallo. </p><p><br /></p><p>Wata dattijuwa ce ta mike tare da fadin, </p><p> _"Haba hajiya, ai be kamata ki Gaya mana irin wannan bah, nan fah gidan sarauta ne, kuma ba haka aka san gidan sarauta bah, kamata yayi koda ke kina fishi damu,sai ki saka wasu su tarbemu kodan kar kubar abun fadi a bakin duniya"_</p><p><br /></p><p>_"Dallah gafara can yimin shiru, ita duniyar ta dade ba'a fade taba, in banda iskanci Ma da hulakanci taya za'ai Me Martaba ya hadani da wannan mahaukatan"_</p><p><br /></p><p>_"Ke baiwar Allah dakata"_</p><p> Kanwar wazirin ta fada tana bada rikon jakarta wanda itama kana ganinta babbace, dan zata kai 40da wani abu. </p><p><br /></p><p>_"Wallahi karya kike, mulki haukane, ko An gaya miki kowama irin kine jahili Marar ilimi dahar akan yarki zaki dinga gayawa mutane maganar banza, inba daban Mai martaba bama ya hada wannan zumunci ke Kin taba ganin wani ya tako Yazo Wajan ki, ke kin isama har azo Wajan ki, wallahi karyar ki, mune ya kamata muce danmu baya so, in kina takama damijinki Sarkine, toh Nima Mijina Sarkine, kuma babu abunda kuka isa ku Nuna mana,"_</p><p><br /></p><p>juyawa tayi ta kalli wasu mata tare da fadin, </p><p> _"Ku kwaso Kayan nan mu tafi"_</p><p><br /></p><p>Tana fadar haka ta nufi hanyar fita, da sauri Hajiya Babba tasa wasu manyan mata susha gaban ta. </p><p><br /></p><p>_"Haba yarinya, kin isa ki Shigo har cikin gidana ki zageni ki hulakantani gaban mutane kice zaki fita lafiya"_</p><p><br /></p><p>Lokacinne yayi daidai da Shigowar Hajiya Bilki da Fulani da kuma mutanan su, dan tarbar an kawo lefan Zakiyyah tunda su har yanzu yan kano basu karaso ba. </p><p><br /></p><p>Ganin ana hayaniya, Fulani tayi saurin fadin, </p><p> _"Haba Hajiya Babba lafiya kuma kuke hayaniya haka, wannan fa ranar farin ciki ne, yarki Allah ya zabeta cikin mata masu tare yawa, ya bata miji ya rufa mata asiri zatayi aure, amma kuma azo a dosa hayaniya haka,gaskiya wannan ba girma bane, musamman ace a gidan sarauta ake irin wannan abun, gaskiya bayi bane?"_</p><p><br /></p><p>Hajiya Babba tana jin haka, ta kara hasala tare da kallan wannan matan, </p><p> _"ku kamaso Ku saka su a kurkuku"_</p><p><br /></p><p>nan fa aka hau danbe, ana fada, gaba daya waje ya hargitse da yan kawo lefe ana danbe sosai, harda su jini. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(13)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ganin abu yaki karewa yasa Fulani ta shiga neman wayar Dizhwar, jin shiru be daga ba yasa ta fara kiran Jafar,</p><p><br /></p><p>Zuwa wannan lokacin mutanan da suka samu rauni da kuma barnar da akayi a part din Hajiya Babba ta bace. </p><p><br /></p><p>Dan kar hukuma ta shigo cikin abun, aji kunya kamar gidan sarki ana wannan abu, yasa Fulani gayama Jafar halin da ake ciki, nan da nan ya karaso part din. </p><p><br /></p><p>Zuwanshi tare da manyan masu tsoro na gidan, nan da nan duk aka tattara Bakin akayi part din Fulani dasu, yayin da aka saka Family Doctor dinsu tazo dan bawa wasu taimakon gaggawa, dan an zubar da jini ba kadan bah,</p><p> Haka gaba daya kayan lefan da akwatinan duk saida aka wulakantasu. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Bayan duk Jafar yayi kokarin ganin kowa ya samu kulawa daga wajan Hajiya Babba har zuwa masu kayan lefan tukun yasa me martaba a cikin wannan zance, </p><p> Jin abunda ya faru ba karamin bata masa rai yayi bah, sabo da haka nan da nan yasa aka tattara duk wanda abun ya faru. </p><p><br /></p><p>Bayan sun zauna kamar yanda ya bukata, nan Fulani tayi masa bayanin komai kamar yanda Kanwar Waziri ta sanar musu wato Hajiya Zainab. </p><p><br /></p><p>Shiru Sarki yayi yana naxarin abun, kafin daga bisani ya fara magana cikin fishi, da daga murya. </p><p><br /></p><p>_"Magana ta gaskiya Abunda Kikamin Khadija banji dadi bah, wannan yana nuna kamar ban isa da ke ba da kuma yara na, kin nuna wa duniya cewa gidan sarauta bashi da daraja, kin zubar mana da mutunci sabo da wata banzar manufataki, toh wallahi tallahi, koda xaki kashe kanki, Allah ya riga daya saka wannan yarinya itace matar sah, kuma aure babu fashi sai anyi shi, saide in ki bar gidan nan, kuma babu inda Zakije da Zakiyya,tunda har kika nunamin bani da iko akanta sai ke"_</p><p> </p><p>Shiru Hajiya Babba tayi dan tasan laifin tane, kuma yanda ransa ya bace, ta tanka ba karamar matsala zata kunnowa kanta bah, sabo da haka bata ce uffan ba harya gama maganar sah. </p><p><br /></p><p>Sannan ya kara da bawa mutanan hakuri tare da sanar musu suje suci gaba da hidimar biki kamar anyi an gama nan da sati daya. </p><p><br /></p><p>Nan yasa aka musu sha tara ta azriki suka tafi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wannan abu daya faru shine abunda ya kuma tunzura Hajiya Babba,Ranta yayi mugun baci ta yanda ta kudiri yin abubuwa masu yawa domin huce Takaicinta. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Ita kuwa Samira, Anty Amarya kenan,dukkan abunda ya faru taji da kunan ta, haka zalika tayi mutukar farin ciki, domin dama burinta be huce ko wacce ta kasance cikin fishi Memartaba. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Yaseer kuwa kamar yanda Daddynsa ya daukar masa lokaci, lokacin ya cika kuma ya bukaci ganinsa. </p><p><br /></p><p>Suna zaune kamar wancan lkcn, yanda ya tarda su. </p><p><br /></p><p>Bayan ya gaisa da iyayan nasa, ya nemi waje ya zauna, kansa a kasa zuciyarsa tana ta faman dukan tara tara sabo da yasan ba lallai yaji alkairi bah. </p><p><br /></p><p>_"Yaseer, yaune ranar da mukayi dakai zamu kara zama, wato naje na sami Mahaifin yarinyar nan kuma munyi magana dashi, amma ya nuna, akwai wanda ya riga ya bawa ita, sabo da haka ma suka nuna bazasu zauna nan bah, domin sun kusan tashi dama zasu koma kauyansu acan za'ai bikin"_</p><p><br /></p><p>Duk da besan abunda zai fada ba, amma yasan da wuya hakan ta kasance, amma bashi da zabi Allah yasa hakan yafi alkhairi. </p><p><br /></p><p>_"Daddy naji na yarda zan auri Saudat din Allah yasa hakanne yafi alkhairi"_</p><p><br /></p><p>Dadi sukaji gaba daya suka hada baki da Amin. </p><p><br /></p><p>Saudat kuwa murna kamar ta rungumi Yaseer gaban iyayan nasa, tashi yayi ya fita daga dakin badan yana farin ciki bah, tun a Stair hawaye suka fara zubo masa sabo da bakin ciki da kuma kunar da zuciyarsa take masa. </p><p><br /></p><p>Haka ya sauka a daddafe yana goge hawayan nasa harya shiga cikin dakinsa, yayin daya zauna kukan nasa saiya karu, babban namiji dashi amma sai gashi yana kuka shabe shabe harda hawaye, wayarsa ya janyo ya kuma kiran ta amma akashe, da karfi ya buga wayar da bango tare da hade hannayansa waje daya ya shafe a kansa yana me kukan takaici. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Dizhwar kuwa kamar wasa bashi da aikin daya huce zuwa wajan Lailah, yanzu harya saba, kullum yana gidan, amma yaki yarda kowa yasan inda yake zuwa, ya hanata zuwa wajan aiki, kullum Suna tare ana shan soyayyah, gaba daya ya gama siye mata Zuciya, wanda a yanzu dayan biyu wajan Lailah in har ta rasa Dizhwar zata iya mutuwa kokuma ta haukace, haka shima ya nuna mata. </p><p><br /></p><p>Yauma yana gidan,suna harabar gidan a zaune kan kujera suna hira kamar yanda suka saba suna dariya. </p><p><br /></p><p>Jafar ne ya kira shi a waya bayan sun gama ya ajje wayar tare da kallan ta. </p><p><br /></p><p>Itama shi din take kallo tare da fadin, </p><p> _"Wai waye Jafar din nanne?"_</p><p><br /></p><p>_"Kinasan sanin kowaye"_</p><p><br /></p><p>Kai ta daga masa alamun eh, </p><p><br /></p><p> _"Nan da One week zamuyi bikinsa zan gaiyaceki, ai nasan zaki zo ko? "_</p><p><br /></p><p>Murmushin ta me daukar hankali tayi tare da fadin, </p><p> _"Zanzo mana, in har kana so Koda yakai nisan inane"_</p><p><br /></p><p>_"Amma kwana zakiyi"_</p><p> Ya fada yana kallanta, ta kasan ido. </p><p><br /></p><p>_"Ammm!, mezai hana hakan ma, in kana so"_</p><p><br /></p><p>Dadi ya kuma ji tare da murmuyi, </p><p> _"Lailah Ina san nan bada jimawa ba ayi Bikinmu dake,amma ina ganin kamar su Abba bazasu yarda bah"_</p><p><br /></p><p>Da sauri ta kalleshi, </p><p> _"Me zai hana, zasu yarda mana"_</p><p><br /></p><p>Da sauri ta kara matsowa tare da fadin, </p><p> _"Kasan in basu yarda ba, kashe kaina fa zanyi"_</p><p><br /></p><p>Shima da saurin ya kalle tah, tare da kamo hannuwanta biyu ya hade da nasa, </p><p> _"Bana san na rasa ki, koda wasa, Lailah, kece farin cikina, kece mace ta farko dana fara so a duniyar nan in kika barni yaya zanyi?"_</p><p><br /></p><p>Binshi tayi da kallo na tsawan lokaci ,yayin da shima yake kallan nata,kowanne shi yasan abunda yake ji acikin zuciyarsa, da sauri ya Rungumetah, kamar itama Abunda take jira kenan,ta rikeshi sosai a jikinata. </p><p><br /></p><p>Sun jima a haka, kafin yadan janyeta daga jikinsa, kan kurjinsa ta kwanta tayi shiru idanta a rufe, hannunta ya kama guda daya ya hada da nashi yana murzawa, shiru na tsawan lokuta a haka, ita dashi kowanne yana Jin dumin dan uwansa, ji suke kamar karsu rabu, wayar shice ta shiga, Ringing, dauka yayi still tana jikinsa ya kara a kunne. </p><p><br /></p><p>Yana magana tana kallan bakinsa, Ahankali ta saka yatsanta tana shafa lips dinsa. </p><p><br /></p><p>Bayan ya gama wayar ne yace da ita,cikin wata irin murya wanda be taba mata ita vah, shi kansa besan yana da ita bah. </p><p> _"Zanje gida Ana nemana"_</p><p><br /></p><p>Maimkon ta bashi amsa sai ta kuma shigewa jikinsa, tana dada lumshe ido. </p><p><br /></p><p>Jin haka yasa ya janyeta Ahankali tare da kallan fuskarta, suna kusa da juna sosai ta yanda hancinsu ya kusan haduwa, kamar acikin bakinta yake maganar, </p><p> _"Pls Lollipop, Memartabane yake nemana, zan dawo,ko kinaso Amin fada"_</p><p> </p><p>Yana magana tana kallan bakinsa, itama kara kashe murya tayi ta kuma sakin jikinta tare da fadin, </p><p> _"Bana san kayi nisa dani, dan Allah zaka dawo kokuma sai gobe, ina sanka da Yawa Dizhwar"_</p><p> Ta fada hawaye ya zuba ta gefan idanunta. </p><p><br /></p><p>Ahankali ya furta, </p><p> _"I know, I know"_</p><p> Yana shafa gefan kuma tunta da hannunsa, bata yi aune ba ya manna mata kiss, sannan ya jinjinar da ita jikin kujerar, dan yaga duk jikinta ya mutu da er in zata iya Rakashi. </p><p><br /></p><p>Tana ganin ya fita daga wajan, wata ajjiyar zuciya ta ajje dan ita kadai tasan yanda take ji Acikin ranta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mikewa tayi ta shiga gida jikinta duk a sanyayye. </p><p><br /></p><p>Shiga falon tayi da sallama, Mama ta gani tsaye ranta a bace tana kallan ta. </p><p><br /></p><p>Hannu ta wara amalun, Menene?.</p><p><br /></p><p>Ranta a bace, ta gaya mata meyasa ta rungume Dizhwar. </p><p><br /></p><p>Gaban tane ya fadi tare da yin shiru tama rasa abunda zata fada. </p><p><br /></p><p>Kara matsowa tayi tare da dago da kanta ta shiga mata nuni da hunnu, </p><p> _"In kina yarda dashi, zai cuceki ya gudu ya barki"_</p><p><br /></p><p>Da sauri ta rike hannun Mamar, tana girgixa kai, </p><p> _"har abada bazai barni ba, sabo da yana so na kuma aurena zaiyi"_</p><p><br /></p><p>Shiru Mama tayi kafin ta kuma fada mata,</p><p> _"Kibi a hankali sabo da banji dadi ba, kuma Allah yana fishi daku, bana san irin haka, in kika kara zamu Bar masa gidansa"_</p><p><br /></p><p>Tana fadar haka ta juya ta tafi. </p><p><br /></p><p>Ita kuma Lailah binta tayi da kallo, dan bata san koma waye ya fadi Laifin Dizhwar dan hakan ita bata ga wani abu ba, sabo da yana santa in ma yayi mata wani abu ai duk cikin so ne, ita bazata taba rabuwa dashi ba koda yankan naman jikinta yake, balle nuna mata so yake zallar sah. </p><p><br /></p><p>Tuno da subbatar da yayi mata tayi, rufe ido tayi, tsigar jikinta ta tashi, da sauri ta shige daki tana farin ciki. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(14)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p>Yan kano sun iso lafiya, Nan suka kawo nasu kayan lefan harda abunda suka kakkara na al'ada.</p><p><br /></p><p>Nan sukaci suka sha, cikin farinciki da kuma karamci, anan suka kwana dan sai washe gari zasu tafi, nan da sati kuma su dawo domin daukar Amarya dan Kano za'a kai Asiya. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Anty Amarya, yamma tanayi, ta shirya ita da Kuyanginta guda hudu, ta nufi part din Hajiya Babbah, koda isarta Mamakine ya kama Hajiya baba, </p><p> Falonta suka zauna, yayin data bawa kuyangin dama dasu basu waje, bayan sun zauna kowacce tana kallan kowacce, ta fara da fadin, </p><p> _"Nasan zakiyi mamakin gani na a part dinki, ba komai bane ya kawo Ni, illah ina so mu hada kai gaba dayan mu domin yanzu mun riga mun zama daya, hakan zai bawa mutane Sha'awa, sannan mu zama abun kwatance musamma a bikin nan da za'ai, domin kinga ni Babu Kowa a wajena dan nasan kinji Labarin Fareeda ta tafi, nayi miki alkawarin zan Zauna daku lafiya da kuma yaran har ayi biki a gama Lafiya"_</p><p><br /></p><p>Kallanta kawai Hajiya Babba take dan Bata yarda da abunda take fada bah, da kamar zata mata wulakanci sai kuma tayi tunani tare dayin murmushi, tace da ita, </p><p> _"Babu komai Allah ya kara hada kanmu"_</p><p><br /></p><p>Nan ta dan taba hira ta fice ta nufi part din Fulani itama ta sameta da wannan maganar, haka kuwa itama ta yarda. </p><p><br /></p><p>Cikin Farin ciki Anty Amarya ta koma part dinta domin ita kadai tasan abunda take hadawa. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Ana saura kwana biyar biki, dan Har yan gidan su Amaryar Dizhwar sun dawo gidan sarki dan aciki za'ai bikin gaba daya, part daba aka basu da masu Musu hidima har a gama biki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yayi daidai da saura sati guda Bikin Yaseer da Saudat wanda yake ji tamkar ana mai Barazana da Rayuwar sah. </p><p><br /></p><p>_____</p><p>Yaune kamu, dan haka waje daban aka ware aka Masa Kwalliya, aka shirya shi, tamkar ba mutane bane suka hada bah, sai kwalli yake da kuma kamshi turarukan huta kala kala. </p><p><br /></p><p>Anty Amarya tun ranar da aka nuna mata Amaryar Dizhwar Hankalinta ya tashi domin tabbas tasan itama wannan yarinyar yar duniya ce, babu makasa saita kwace Dizhwar ko a hannun wa yake. </p><p><br /></p><p>Ita da kawayanta suka zo da kuma yan uwanta, gida ya koma tamkar wani wajan saida jama'a. </p><p><br /></p><p>Anty Amarya ita ta dauki Nauyin Shirya Shiryan Amare da wani gyaran su, amma Husna, Amaryar Dizhwar tace babu inda zata itama zata iya shiryawa dan an raina musu hankali har wata tsohuwar kilakice zata wani dauki nauyin shirinsu, Asiya ce kawai ta yarda dan ita babu ruwanta. </p><p><br /></p><p>Haka itama Zakiyya bata yarda bah, saida Hajiya Babba ta lallabata. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Dizhwar, shida Jafar suna zaune cikin dakinsu, Jafar yana sanar masa da Amaryarsa tazo fa, amma shi banza yayi da ita dan baya san ya bata masa rai. </p><p><br /></p><p>Ita kuwa Husna tunda tazo babu wanda take san ta gani inba Dizhwar bah, dan haka nan ta dinga tambayar part dinsa saida ta isa ranta yayi mata dadi. </p><p><br /></p><p>Ahankali ta shiga Knocking kofar, dakin.</p><p><br /></p><p>Dizhwar dake waya da Lailah banza yayi, Jafar ne yayi magana. </p><p><br /></p><p>Nan ta turo Ahankali ta shigo, sanye take da Pakistan Yellow riga da wando sai karamin mayafi, tasha makeup kamar aljana, dan ita ba fara bace sosai, ga uban gashi dayasha gyara kamar Bororo. </p><p><br /></p><p>Shigowa tayi ta zauna, batare datayi sallama ba ko ta gaida Jafar. </p><p><br /></p><p>Binta kawai yayi da kallo danya santa Asin shi ta nuna masa ita. </p><p><br /></p><p>Wajan Dizhwar tayo kai tsaye ko ba'a fada mata ba tasan shine tunda taga pic dinsa wajan Abban ta. </p><p><br /></p><p>Zama tayi kusa dashi tana kallansa tare da fadin, </p><p> _"Habibee Dizhwar nayi fishi dakai dan naga ko nemana ma bakayi kamar ba matar ka bah"_</p><p><br /></p><p>Banza yayi da ita yaci gaba da wayar sah, hakan ya sosa mata rai dan ta fara gane da mace yake waya, </p><p><br /></p><p>Ganin zata bata masa rai, yasa yayima Lailah Sallama tare da kallan ta,</p><p> _"Wacece wannan? "_</p><p> Ya fada yana nunata yana kallan Jafar. </p><p><br /></p><p>Murmushi yayi tare da fadin, </p><p>Matar kace mana.</p><p><br /></p><p>Wani haushine ya kamasa dan ko Yar kunyar nan bata da ita. </p><p><br /></p><p>Hakan yayi mugun bata mata rai, </p><p><br /></p><p>_"Amma wallahi baka da mutunci, nidin kake gayawa haka,lallai kayi babban kuskure dahar kake neman wulakantani"_</p><p><br /></p><p>Duka su biyun kallan ta suke dan suna ganin abun kamar a film. </p><p><br /></p><p>Dariya Dizhwar ya kwashe da ita yana nunata. </p><p><br /></p><p>Da sauri ta mike tare da yin wajansa, har saida ta rutsashi a bango tare da fadin, </p><p> _"Dani kake zancan"_</p><p><br /></p><p>Daidai lokacin Anty Amarya ta shigo dakin, ganin Husna jikin Dizhwar yasa ta sakin baki tana kallansu, bata san lokacin data furta, </p><p> _"ke meye haka baki da hankali Ne?"_</p><p><br /></p><p>Juyowa tayi ta kalli, Anty Amary tare da kallan Dizhwar tukun ta sakeshi ta nufi inda take, zagayeta ta fara yi tana leken idanta tah. </p><p><br /></p><p>_"Ohoooo!, Antynmu karfa, ta kashe mata ido daya😉"_</p><p><br /></p><p>Bata ce mata komai ba ta ci gaba da kallan ta. </p><p><br /></p><p>_"Hhhhhh, Allah de ya biya, kenan duk yan soyayyah ne acikin gidan"_</p><p> Husna ta fada tana kallan Anty Amarya.</p><p><br /></p><p>Kusa da kunnan ta ta matsa tare da fadin, </p><p> _"Ki fara sama Zuciyarki ruwan sanyi ko baki fada ba nagani cikin idanki, amma karki manta saura kwana, hudu ya zama Nawa,so better mind ur business"_</p><p> Tana fadar haka ta juya ta yima Dizhwar signa ta fita daga dakin. </p><p><br /></p><p>Jafar ne yace, </p><p>_"Tabdi jan!, Dizhwar akwai aiki a gaban ka"_</p><p><br /></p><p>Ita de Anty Amarya kamar gunki, kasa jurewa tayi ta fita daga dakin ta kullo Kofar. </p><p><br /></p><p>Kallan juna suma Sukayi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(15)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan Husna ta fita daga part din su Dizhwar, wajansu ta nufa ranta a bace.</p><p><br /></p><p>Koda isarta cikin daki da, Babbar yayarsu take, Anty Salima, kuka ta kama. </p><p><br /></p><p>Nan tahau tambayarta abunda aka mata, nan ta bude baki ta gaya mata abunda Dizhwar yayi mata harda karawa da karyarta. </p><p><br /></p><p>Kasancewa babu wanda besan danginsu bah, Sun kasance yan boko, babansu ma Yayi Ambassador, sun zauna da a America, in har ka aure family dinsu babu kai babu kara aure, haka zalika saika koma tamkar bawansu, mahaifinsu Abokin Mai martabane tun na yarinta, kwanan nan yayi hadiri ya rasu, shiyasa Sarki yake tausaya musu,tun Babansu yana dare yaso Sarkin ya Auri Salima amma abun be yiyu bah, shiyasa yanzu ya barwa Sarkin wasiya akan yana so ko bayan ransa ya hada aure da yan gidansa da nan, shiyasa Ya dage akan Dizhwar saiya auri Husna, duk yan gidansu mata Ne, susu biyar Amma dayace kawai tayi aure, duk sai sun gama karatu sun fara aiki ake aurar dasu, dan Ita Kanta Husnar ta kusan sa'a da Dizhwar din. </p><p><br /></p><p>Gaba daya da sauran yan uwansu suka tare gidan sarkin, yayin da mahaifiyarsu da take zaune can gida dan bata gama takaba bah. </p><p><br /></p><p>Bayan Husna ta gama yiwa Dizhwar din Karya, Anty Salima tahau masifa tare da fadin, </p><p> _"Mu zai yiya iskanci dan bamukai sunan saba har yake wani daga kai, zai gane shi yarone saimun koya masa hankali, ki kwantar da hakanlinki ayi bikin nan lafiya a gama lafiya kiga aiki da cikawa, kitashi a fara shiryaki, kinsa karfe 4:00pm za'a fara taran kamun"_.</p><p>_______</p><p>Ita kuwa Lailah tun ranar da Tabar Tsohuwar unguwarsu bata koma ba, dan haka yau Rauda ta kawo mata ziyara dan ganin ta dena zuwa aiki, zuwa saban gidansu. </p><p><br /></p><p>Nan ta shigo ta zauna a falo, ta hado mata kayan kwalam da makulashe. </p><p><br /></p><p>Babu abunda Rauda take sai faman kallan irin daular dasu Lailah suka samu, yake kawai take dan cikin ranta bakin cikine yayi mata katutu. </p><p><br /></p><p>Nan Lailah ta zauna suka gaisa amma Rauda tsabar bakinciki tama kasa cin ko abu daya balle tasha ruwa. </p><p><br /></p><p>_"Rauda yaya wajan aiki, aini wallahi Dizhwar ne ya hana ni zuwa ko ina daga gida sai gida, saide in dashi zamu fita"_</p><p><br /></p><p>Shiru kawai Rauda tayi tana jinta. </p><p><br /></p><p>_"kwana biyu ko kiranama bakyayi yanzu"_</p><p> Lailah ta fada rana murmushi. </p><p><br /></p><p>Yake tayi tare da fadin, </p><p> _"Wallahi abubuwane sunyi min yawa, ai yanzu keya kamata kina kirana sabo da kin zama Madam"_</p><p><br /></p><p>Dariya Lailah tayi,tare da fadin, </p><p> _"Bana san iskanci, kinsan kuwa kwanan nan, zan zama Madam din domin ina gab da shiga daga ciki"_</p><p><br /></p><p>Da sauri Rauda ta dogo kai tare da fadin, </p><p> _"Wai kina nufin dagaske auranki zaiyi"_</p><p><br /></p><p>_"Hmmm kina wasa kenan,ai in gaya miki nidin bata wasa bace, wallahi gaba daya baki ga yanda Dizhwar ya haukace a kaina ba, barama kiga in gwada miki"_</p><p> Wayarta ta janyo tare da kiransa, harta katse be daga bah. </p><p><br /></p><p>Kafin ta ajje ta kan kujera ya kira, nuna mata tayi, tare da dagawa tasa hands-free, </p><p> _"Hello"_</p><p> Lailah ta fada cikin wani salo,</p><p> Da saida Rauda ta hadiye wani kululun bakin ciki. </p><p><br /></p><p>_"Me Babyna take a wannan lokacin?"_</p><p><br /></p><p>_"Wallahi ina kewarka sosai, har na kasa jurewa shiyasa na Kira ka"_</p><p><br /></p><p>_"Ohh!, nima haka, am Busy ne amma ina so in shigo inga sanyin idaniyata, but karki damu soon, zamu zama always together"_</p><p><br /></p><p>_"Yawwa masoyi, ina dan wani abu ina zuwa,love u bye"_</p><p><br /></p><p>_"Ok, Love you too sweetheart"_</p><p><br /></p><p>Sannan ta kashe, kallan Rauda tayi data saki baki tana kallan Lailar. </p><p><br /></p><p>_"Lallai Lailah, gaskiya Malamin da yake muku aiki ba sabo bane"_</p><p><br /></p><p>_"Ban gane bah? "_</p><p> Lailah ta fada tana kallan ta. </p><p><br /></p><p>_"Wai kina nufin, ba sunansa kuka kai bah"_</p><p><br /></p><p>_"Bana san iskanci Rauda, sunansa aina kuma zankai, Allah ya rabani da bin bokaye, ai banga abun alfaharin ba ga soyayyar daba ta Allah da annabi bah, Allah ya tsareni, wallahi Allah ne kawai ya hada jini na da nashi, amma babu wani maganar kai Suna ko wani abu, haba karkibani kunya mana saikace ba musulma ba kike irin wannan maganar"_</p><p><br /></p><p>Shiru Rauda tayi dan abun ya fara huce tunaninta, tabbas yakamata ta tashi tsaye dan bazai taba yiyuba, in har Tana raye, Dizhwar bazai taba auran Lailah bah.</p><p><br /></p><p>_"Toh Lailah nide zan huce sai kuma in an kwana biyu"_</p><p> Rauda ta fada tana kallan ta. </p><p><br /></p><p>_"Toh bara in dauko hijab dina sai in taka miki"_</p><p> Ta fada tare da mikewa ta nufi dakinta. </p><p><br /></p><p>Rauda tana ganin haka tayi maza ta dauki wayar Lailah, ta dauki Number Dizhwar ta saka a tatah tare da maida mata ta ajje ta zauna tana jiran fitowar ta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(16)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ko bayan Anty Amarya ta fita daga part din Dizhwar, kai tsaye wajanta ta nufa, batare data kula kowa ba ta shiga daki, wani wawan ihu ta saki tare da fara bari da duk kayan dake kan bedside dinta, ta zauna idanta yana hawaye, duk kwalliyar tatah tayi wani iri.</p><p><br /></p><p>Bayan tagama hawayanta, ta mike tare da bude wardrobe dinta, wani karamin kwalbar turare ta dauko, tare da kallanta, murmushi, tayi, tare da shiga toilet wanke fuskarta tayi ta fito ta gyara, sai faman yake take yiwa jama'a harta fice daga part dinta. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Amare kuwa sai faman kwalliya ake ko wacce tayi shiga cikin kaya masu kyau da tsada sai faman kamshi suke, </p><p> Duk da Husna ta kasance ba fara ce sosai ba amma kana ganinta kasa wayayyace, haka zalika akwai ta da iyayi, ga gashi tubarkallah. </p><p><br /></p><p>An gama shirya ko ina, ko wacce Angonta kawai take jira domin su fita a huce wajan kamu dan tuni jama'a sun fara taruwa. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Koda Anty Amarya ta isa part din Dizhwar, a kulle ta tarda shi, tsaki tayi ta tsaya tana tunanin inda yayi, ganinsu tayi sun Fito daga mota shida, Jafar, Jafar can cikin gida yayi yayin da Dizhwar ya nufo bangaransu, tana hangosa tayi maza ta boye dan bata san ya hangota. </p><p><br /></p><p>Bayan ya shiga tabi bayan sa itama ta shiga tare da kiran sunan sa, </p><p><br /></p><p>Da sauri ya juyo yana kallan ta, </p><p> _"Ywwah me martaba ne yake neman ka"_</p><p><br /></p><p>Cike da mamaki yake kallanta, kamar zaiyi wani abu sai kuma ya fasa dan baya so ya karyatata, </p><p><br /></p><p>_"Muje"_</p><p> Kawai ya fada yabi bayanta, ga mamakinsa sai yaga sun nufi lambun Baban nasu, amma be mata musu ba yasan yana yawan zama a wajan. </p><p><br /></p><p>Haka ta jashi har ciki, bayan ya shiga falon wajan ganin baya nan yasa ya bita da kallo, </p><p><br /></p><p>Beyi magana bah, ta shiga ciki bata jima bah, sai gata ta fito tare da fadin, </p><p> _"Ka shigo"_</p><p><br /></p><p>Ba musu ya shiga wayarsa tana hannunsa. </p><p><br /></p><p>Yana shiga yaji wani kamshin turare ya bigi hancinsa take ya fara ganin wani iri jiwa yake ji kamar zai dauke sah, da sauri ta karaso wajanta tare da rungumeshi, jin yana kokarin faduwa yasa ya rike ta sosai, haka ta jashi har kan gado, ta shiga rabashi da kayan jikinsa tana murmushi, rigar ta cire masa, yayin da itama ta cire tatah, rungumeshi tayi tahau romancing dinsa iya yanda take so, bayan ta gama ta maida rigar ta tare da mikewa ta dauki Camera data saka tayi musu hotona, ta kunna taga duk gasu nan sun dauku, ta maida ta rufe ta bishi da kallo tare da durkusa ta dauki wayarsa data fadi ta fita daga dakin bayan ta saka masa key. </p><p><br /></p><p>Fita tayi tana Murmushi tare da fadin, </p><p> _"Husna zakisan dani kike, zamuga Dizhwar din da zaizo wajan Kamu"_</p><p><br /></p><p>Haka ta koma cikin mutane akaci gaba da hidima da ita yayin data saka wayar Dizhwar cikin wardrobe dinta ta kulle dakin ta fita. </p><p><br /></p><p>_____</p><p>Tun bayan da Husna ta gama shirin ta ta shiga kiran Number Dizhwar amma yaki dauka, hakan yasa ta sanar da Anty Salima, ba wani jayayya ta nufi wajan Fulani dan sanar mata abunda Dizhwar din yake shirin musu. </p><p><br /></p><p>Nan ta basu hakuri tare da fara trying number tasa da kanta, amma shiru yaki dagawa hakan yasa ranta yayi mugun baci, tunda tasan yana sane zaiki dagawa tunda shima basan Husnar yake bah. </p><p><br /></p><p>Jafar ta shiga nema ko suna tare, amma koda ya dauka, sai yace da ita, shima nemansa yake, ga kayansa an kawo masa shima ya gama shiryawa, hakan yasa Gaban Fulani yadan buga. </p><p><br /></p><p>Wasa wasa lokaci yana ta tafiya ga dangin Husnah sun dame su.</p><p><br /></p><p>Batayi kasa a gwiwa bah, taci gaba da trying number tasa. </p><p><br /></p><p>Anty Amarya kuwa tana zaune gaban Mudubi tana kwalliya taji wayar Dizhwar tana ta faman ringing, mikewa tayi ta dauka tana kallan missed calls da akayi masa dayawa, murmushi tayi ta ajje wayar tana kallan ta, </p><p><br /></p><p>Mami taga an saka tasan Fulani ce dan haka da sauri ta dauka ,batare da tayi magana bah. </p><p><br /></p><p>_"Dizhwar ka kyauta, tun dazu ina faman kiran ka amma kanajina kaki dagawa, bayan kasan jiranka sukeyi, Koso kake Babanku ya shigo maganar bayan kuma an gama komai,toh Wallahi duk inda kake kayi maza ka dawo gida ko ranka yayi mugun baci"_</p><p> </p><p>Babu abunda Anty Amarya take sai dariya kasa kasa, jin Fulani ta gama yasata, kashe Murya tare da fadin, </p><p> _"Kiyi hakuri, yagajine shiyasa yake bacci amma inya tashi zansa ya kira ki"_</p><p> Tana fadar haka ta kashe tana ihun dadi. </p><p><br /></p><p>Bin wayar Fulani tayi da kallo da sake sake kala kala cikin ranta, </p><p> _"Innalillahi wa'inna illaihir raji'un"_</p><p><br /></p><p> shine abunda take ta faman maimatawa kenan,da zuciyarta da take saka mata ko neman mata Dizhwar din yake dama. </p><p><br /></p><p>Hankalinta ba karamin tashi yayi ba kasa kiran Jafar din tayi haka ta kasa bawa kowa masar tambayar da yake mata ta ina Dizhwar din ya shiga. </p><p><br /></p><p>Fita tayi tabar wajan, dan ta samu saukin hayaniyar da akeyi ko kanta zai dawo dai dai. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>________</p><p>Husna kuwa banda kuka babu abunda takeyi, hawaye shafe shafe. </p><p><br /></p><p>Duk ta bata kwalliyar tatah, Anty Salima da sauran yan uwanta sai hakuri suke bata, taje haka nan babu Angon. </p><p><br /></p><p>_"Wannan ma ai wulakancine, dama yasan haka zaiyi mana, shine zaisa mu gayyaci mutane ya ci mana mutunci, wallahi saimun nuna masa damu yake wannan abun, ya za'ai yayi mana irin wannan cin mutuncin"_</p><p> Anty Salima take ta faman balbalin bala'i. </p><p><br /></p><p>Gaba daya yan Bangaran Amarya Husna kowa yayi jugun jugun duk an fara cire kwalliya tunda Amarya kanta itama ta lalata tatah. </p><p><br /></p><p>_"Husna ki tashi a gyara miki fuskar kar kuma yazo a kuma bata lokaci"_</p><p> Wata kawarta ta fada. </p><p><br /></p><p>Dago kanta tayi tare da fadin, </p><p> _"Rabu dashi wallahi ko yazo babu inda kuma zani"_</p><p><br /></p><p>Mikewa tayi kai tsaye ta nufi part din Fulani, koda taje babu mutane sosai duk sun tafi wajan kamun Asiya.</p><p><br /></p><p>Nan suka shiga neman, Fulani yayin da ita bama ta wajan. </p><p><br /></p><p>Babu abunda suke a wajan sai faman habaici,da zage zagen abun da aka musu. </p><p><br /></p><p>Hajiya Bilki ce ta zo wajansu tare da fadin, </p><p> _"ku in baku da tarbiya anan za'a koya muku, in banda baku da mutunci kuzo kona mana fada kamar wasu kannanku ko sa'aninku,ku kiyayi kanku nan Gidan sarautane ba Club bah, kuma fadan ku da zagin da kuke, shine zaisa Dizhwar din yazo? "_</p><p><br /></p><p>Shiru sukayi babu me magana acikinsu, nan ta kira me martaba ta sanar masa. </p><p><br /></p><p>Shima kiran Dizhwar din yasa ayi amma tana ta Ringing ba'a dauka bah. </p><p><br /></p><p>Nan fa Husna ta zauna tana ta faman ihu, babu ji babu gani, kamar yarinya karama. </p><p><br /></p><p>Anty Amarya ce ta karaso wajan tana fadin, </p><p> _"Dan Allah kuyi hakuri ku lallasheta mana,tunda yaki dagawa kuyi hakuri mana, tunda wayar tana shiga in yana gani ai zai daga, kuma bakwa tunanin ko wata matsalar ce ta faru"_</p><p><br /></p><p>_"Babu wata matsala data faru, ai Jafar yace tare suka shigo gida "_</p><p>Hajiya Bilki ta fada taba gyara zamanta. </p><p><br /></p><p>_"Innalillahi,Gaskiya shima ai ba'a irin haka, saiya dauka yace bazai zo wajan ba amma yana gani ana kiransa ai saiya dagawa mutane hankali "_</p><p><br /></p><p> Anty Amarya ta fada tare da mikewa, </p><p> _"Bara muje mu leka nasu Zakiyyah"_</p><p> Ta fada tare da fita daga wajan tana murmushi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(17)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka ta ficewarta ta barsu ana mai da zance.</p><p><br /></p><p>Ranar haka Husna tana ji tana gani sukayi zaman bakin ciki babu kamu, sai mutane aka bawa hakuri kowa ya tafi dan babu yanda basu yiba taje ita kadai ta kiya.</p><p><br /></p><p>Anty Salima so tayima su hada nasu inasu su tafi gida amma Husna ta dage da babu inda zata dan ita tana san Dizhwar kuma duk abunsa saiya aureta. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Lailah ma haka tayi ta faman kiransa amma sai gajiya tayi dan be daga ba hakan yasa hankalinsa yayi mugun tashi. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Bayan an tashi daga wajan party, saida Anty Amarya ta tabbata babu me ganinta takun, ta saka aka dauko Dizhwar din daga can aka kaisa dakinsa, tare da ajjemai wayarsa kusa da shi, yaci gaba da baccinsa hankali kwance. </p><p><br /></p><p>Koda can dare yayi da Jafar ya dawo, cike da mamaki ya shiga bedroom din Dizhwar ya gansa kwance yana faman Bacci. </p><p><br /></p><p>Abun ya bashi mamaki, karasawa yayi ya shiga tattabashi yana tashin sa amma kamar gawa haka ya koma dan bama jinsa yake yi bah. </p><p><br /></p><p>Hakan yasa ya dauki wayarsa tare da duba dumbin missed da aka masa.</p><p><br /></p><p>Zama yayi kusa dashi yana nazari, tabbas yasan Dizhwar akwai dalilin daya hana shi zuwa wajan nan amma sai ya tashi sai yaji koma Menene. </p><p><br /></p><p>______</p><p><br /></p><p>Washe gari saida gari ya waye wajan 8am tukun ya fara motsi,ahankali ya tashi zaune kamar wanda aka masa duka duk jikinsa ya mutu, bude ido yayi ya kalli Jafar dake zaune kusa dashi. </p><p><br /></p><p>_"Sannu"_</p><p> Jafar ya fada yana kallansa. </p><p><br /></p><p>_"Lafiyar ka kuwa, kode shaye shaye ka fara, Dizhwar ?"_</p><p><br /></p><p>Binsa kawai yake da kallo, shima mamakin kansa yake duk da besan iya adadin time din daya bata ba yana Baccin bah. </p><p><br /></p><p>Batare da yayi magana ba ya shige toilet, bayan yayi wanka ya fito, duk Jafar yana zaune yana kallansa ya gama shirinsa yayi sallah, tukun ya dauki wayarsa ya fara dubawa. </p><p><br /></p><p>Mamakine nan ma ya kamasa, yana san tuna abunda ya faru amma ya kasa, ya akai yayi bacci haka,shi kansa yasan ba'a sanin saba kuma gashi beje wajan Kamu din nan bah. </p><p><br /></p><p>Tsaki yayi ya maida wayar tashi cikin aljihunsa. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Ita kuwa Fulani kusan kwana tayi batayi bacci ba, sabo da abunda Kunan ta ya jiye mata, </p><p><br /></p><p>Koda safiya tayi, kasa wani walwala tayi babu abunda take jira kamar shigowar Dizhwar gidan nan. </p><p><br /></p><p>Kamar daga sama kuwa taji sallamar sah. </p><p><br /></p><p>Tana ganin ya shigo ta mike daga inda take ta karaso wajansa tare da marinsa har sau hudu, sannan tana kuka ta fara tambayarsa,</p><p> _"Daga ina kake, ina kaje jiya?"_</p><p><br /></p><p>Kasa magana yayi yana kallanta, ji yake kamar yayi kukan shima, </p><p><br /></p><p>Kwalar rigarsa ta rike tana masa magana. </p><p><br /></p><p>Nan da nan duk wanda suke Dakin suka fita, Humairah ce ta fara kokarin janya Fulani tana bata hakuri, </p><p><br /></p><p>Tureta tayi tare da komawa ta rikeshi tana fadin, </p><p> _"Baza ka gayamin ina kaje ba Dizhwar, dama abunda kake kenan shiyasa kaki yin aure tun tuni, dama abunda kake shiyasa bakasan zaman gidan nan, wallahi ban yafe maka bah"_</p><p><br /></p><p>Asiya da Humairah ke bata hakuri suna rokonta datayi hakuri, yayin da Humaira ta jashi gefe tana masa magana. </p><p><br /></p><p>Ita kuwa Fulani kuka kawai take. </p><p><br /></p><p>Saida ta fita dashi daga inda Fulanin take, tukun ta zaunar dashi, bata mai magana ba, ta fita ta hado masa breakfast, tare da ajje masa tana kallansa.</p><p><br /></p><p>_"Yaya gashinan ka karya tukun, Mami tana cikin bacin rai sosai, tun jiya kasa bacci tayi haka ko abinci bata cibah, munyi munyi ta gaya mana damuwarta amma taki, dan Allah karka koma wajanta ka bari saita huce"_</p><p> Binta yayi da kallo yana san yin amgana amma ya kasa, hawaye kebin kumatunsa sabo da takaicin shi kansa besan abunda zai fada mata bah, gashi besan me take tunani bah. </p><p><br /></p><p>_"Yaya dan Allah kaima kayi shiru, haba sai kace ba Namiji bah, ka samu kasa wani abun acikinka mana"_</p><p><br /></p><p>Cikin muryar kuka yace, </p><p> _"Humairah me nayima Mami, ni kaina bansa ya akayi ba, wallahi kawai tashi nayi na ganni cikin dakin mu, amma ko za'a kasheni bansan abunda ya faru bah"_</p><p><br /></p><p>Jin haka yasa ta bishi da kallo, tasan bazai mata karya ba, toh dole cikin wannan lamari akwai abun dubawa, dan in ba haka ba saide in shaye shaye yake yi, amma ya za'ai ace mutun da ransa da lafiya yace besan ya akai yayi abu ba.</p><p><br /></p><p>Mikewa tayi tsaye tare da fadin, </p><p> _"Kayi hakuri, ka saka wani abun a cikin ka, bara naje na dawo"_</p><p> Tana fadar haka ta mike ta fita daga dakin.</p><p><br /></p><p>______</p><p>Haduwa tayi da Jafar yana kokarin shiga dakin Fulanin. </p><p><br /></p><p>_"Lafiya kuwa meke faruwane wai"_</p><p> Ya fada yana kallan humairah. </p><p><br /></p><p>Shiga dakin sukayi,tare ya zama, Daga Mamin har Asiya kuka suke. </p><p><br /></p><p>_"Kekuma kukan me kikeyi? "_</p><p> Jafar ya fada yana kallan Asiya. </p><p><br /></p><p>Kasa magana tayi, </p><p> _"Shagwababbiya tashi ki hadan abinci"_</p><p> Ya fada yana zama, babu musu ta fita daga dakin tana goge hawayanta. </p><p><br /></p><p>Zama Humaira tayi tana kallan Jafar tare da fadin, </p><p> _"Wai ina Yaya yajene haka?"_</p><p><br /></p><p>_"Wallahi Humairah ban sani bah, nasan tare dashi muka dawo daga wajan aski, toh amma koda muka shigo nasan be kara fita ba yana cikin gidan nan, amma abun mamaki anan shine, dana dawo bayan naci abinci danna shirya baya cikin dakin, amma dana dawo da daddare zan kwanta na gansa yana bacci, kuma wallahi ko sallar asbah beyiba sabo da wannan bacci saida gari ya waye"_</p><p><br /></p><p>_"Amma abun da mamaki, kuma nasan baya shaye shaye"_</p><p>Humairah ta fada. </p><p><br /></p><p>_"Amma ai yana neman mata"_</p><p> Fulani ta fada tana kallan Jafar. </p><p><br /></p><p>_"Neman mata kuma, Mami?, wallahi Dizhwar baya Neman mata"_</p><p><br /></p><p>_"Karya zanyi maka kenan?,jiya dana kirasa macece ta daga, tasanar min da yana bacci"_</p><p><br /></p><p>Shiru Jafar yayi yana nazari, </p><p> _"Amma abun da mamaki, Wallahi Mami ki yarda dani, Dizhwar baya neman mata, Wallahi kinji na rantse miki"_</p><p><br /></p><p>_"Mami ki yarda mana nima abunda nayi tunani kenan,kode sharri aka masa"_</p><p>cewar Humairah </p><p><br /></p><p>_"Sharri kuma, wanene zaiyi masa wani sharri?, shide ya sani amma tabbas mace, ta daga min waya jiya dana kirasa"_</p><p><br /></p><p>_"Toh Mami in ma wajan watan yaje, saide in a gidan nan take amma wallahi be fita daga gidan nan bah, ko masu gadi zaki tambaya"Jafar ya fada, yana kallanta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shiru itama tayi dan abun itama ya daure mata kai, dande ance ba'a saidar mutun, amma tabbas taji muryar mace kuma tasan abunda take tunani Dizhwar bazai aikata bah, </p><p> _"Toh wace wannan?"_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(18)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p>Ranar ne ya kama Dinner, sun so suyi a kano ko lagos amma Memartaba ya hana dole anan aka shirya komai.</p><p><br /></p><p>Dizhwar yasan Mami tana fishi dashi sosai hakan yasa be koma wajan tabah, dakinsu ya koma dan abun ya fara bashi tsoro. </p><p><br /></p><p>Yana nan zaune Jafar ya shigo, shima be kuma masa maganar ba haka zalika shima yayi shiru, nan suka fara shirya yanda abun zai kasance, duk da baya son Husna, yana yin komai ne dan karsu Mami su kara jin haushinsa.</p><p><br /></p><p>Nan Jafar yahau kiran friends dinsu domin ya sanar musu da batun Dinner, dan lokacin ma ya riga daya kure sosai. </p><p><br /></p><p>Harda Yaseer cikin wanda suka gaiyata. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Shima Yaseer an fara hidimar bikinsa,amma ko kadan be gayawa wani abokinsa ba dan ko kadan da er in zai halarci wani party nasu can da suka hada. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Lailah ma yanda taga rana haka taga dare domin babu yanda ta iya, kuka kuwa tasha shi harta gode Allah, sabo da rashin Kiranta da Dizhwar yayi. </p><p><br /></p><p>Tana kwance kan gado kamar marar lafiya, haka Mama ta kawo Mata abinci amma kinci tayi, sabo da tunanin masoyi. </p><p><br /></p><p>Nan ta shiga kiransa, cikin sa'a kuwa tana katsewa ya kira shima. </p><p><br /></p><p>Batare datayi masa magana ba ta fara sakin saban kukan, dama yanda yasan Lailah da shagwabah yasan dole zatayi kuka. </p><p><br /></p><p>Sanin cewar kukan ta yana sashi yaji wani iri, duk da har yanzu ba wani shararran so yake mata ba, banda na yaudara da yake nuna mata. </p><p><br /></p><p>Saida tayi ta gama tukun yace da ita, </p><p> _"Kiyi hakuri pls nace miki ina cikin Busy na bikin Nan da muke"_</p><p><br /></p><p>_"Amma dan Allah kana ganin kirana kaki dauka, wallahi jiya banyi bacci ba duk hankalina a tashe yake"_</p><p> </p><p>_"Ayyah am sorry kinji yan mata na, ki kwanta kiyi bacci, an jima zamuyi waya"_</p><p> Yana fadar haka ya kashe. </p><p><br /></p><p>Bin wayar tayi da kallo tare da saka ta a kirjinta ta rungume tana sauke ajjiyar zuciya, sai lokacin bacci ya dauke ta. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Gurin party ya hadu iya haduwa, komai yayi kyau cikin tsari, yayin da Ko wace Amarya da irin Decoration da akayima Sit dinta ita da Angonta ta, abunde sai wanda ya gani duk da a waje daya za'ai komai. </p><p><br /></p><p>Tabbas yau ba karamin taro za'ai ba a garin Zamfara, domin an sanar a media, ana bikin yaran mayan, haka zalika baki daga waje waje suke zuwa domin wannan dinner ta daran yau, wanda zata kasance da misalin karfe 9pm zuwa 12am. </p><p><br /></p><p>Tun bayan la'asr aka bude gate, sabo da masu shige da fice, an saka manyan masu tsaro a wajan domin checking da kuma bada kyakkyawan tsoro ga jama'a. </p><p><br /></p><p>Gaba Daya Dizhwar yana cikin Busy dan har abokansa sun fara zuwa, </p><p>Ko abinci beci ba daga shi har Jafar din. </p><p><br /></p><p>Jafar ne ya kira Humaira danta hada musu abinci, ta bada a kawo musu. </p><p><br /></p><p>Shikuwa Dizhwar Coffee kawai yasa Humaira ta hada masa. </p><p><br /></p><p>Bayan an gama hada Abincin su Jafar an kai musu, Shima Dizhwar din ta gama hada masa Coffee din, Zata bada akai masa, Anty Amarya ta shigo wajan tana fadin, </p><p> _"An kaiwa Angwaye abinci kuwa?"_</p><p> kasancewa Humaira basa wani shiri da ita sosai kawai tace da ita. </p><p><br /></p><p>_"Eh an kai musu, Dizhwar kawai za'a kaima wannan Coffee din"_</p><p><br /></p><p>Da sauri Anty Amarya ta amsa tare da fadin, bara a bada a kai masa, ta amsa tare da fita dashi waje. </p><p><br /></p><p>Humairah kuwa kasancewar bata waniyi tunanin wani abu ba taci gaba da harkokinta. </p><p><br /></p><p>Yayin da Anty Amarya ta bude, wani magani a takarda ta zuba kadan a ciki, harta juya zata bada akai, sai kuma tayi wani tunanin, ta karasa juye sauran maganin gaba daya aciki, kyalkyalewa tayi da wata irin dariya kasancewar babu me kallan ta, ta hada magani ta juya ta bada akai masa.</p><p><br /></p><p>Shikuwa dama jira yake, ga kuma yinwa da yake faman ji, ana kawowa, Tun daga bakin kofa ya fara sha, yana hira dasu Jafar harya shanye kayansa gaba daya, yayi masa dadi sosai kuma nan da nan cikinsa ya cika. </p><p><br /></p><p>______</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda yamma tayi, Lailah ta tashi tayi wanka tayi abunda xatayi, jin har tym din Dizhwar be kuma kiranta ba, yasa ta kuma neman number sah.</p><p><br /></p><p>Yana ganin itace kuwa ya dauka, </p><p>_"Babyna bade kin tashi daga baccin bah"_</p><p> </p><p>_"Wallahi ban jima da tashi bah,ya hidiman bikin, ai har yanzu kaki ka gayyaceni"_</p><p><br /></p><p>Shiru yayi dan baya san balloma kansa ruwa.</p><p><br /></p><p>_"Hello"_</p><p> Ta kuma magana. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_"Kina so kizo ne?"_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_"Eh, sosai mana"_</p><p><br /></p><p>_"Ok to ki shirya zan aiko mota ta daukeki, saiki shirya"_</p><p><br /></p><p>Cike da murna da farinciki, Lailah ta amsa. </p><p><br /></p><p>Ko Bayan ya kashe wayar, </p><p>yana so in tazo ya Wulakantattah kamar yanda ya tsara, amma ba haka yaso ba, yaga yarinyar in har yana tare da ita, toh dole zai iya kamuwa da santa shikuwa abunda baya fata kenan,dan bazai iya taba hada jini da talaka ba, musamman ita da take yar gidan Kurame. </p><p><br /></p><p>Wani haushin kansa ma yaji daya tuna irin zaman da sukayi shida ita. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Cike da Murna Lailah ta hau dubo kayan da zata saka, wani jan material ta gani wanda suka dinka ita da Rauda da sallah, wani me kyau dan Yadi Biyar dubu takwas, shita dauko tare da mayafinsa da talmin da suka siya, ta dauko fashion dan kunne tukun da abun hannu. </p><p><br /></p><p>Bayan ta gama hada duk abunda zatayi amfani dashi, kasancewar Mama har lokacin bata gama yarda da Dizhwar ba, ta sanar mata da Rauda ce ta gayyaceta biki dan in tace Dizhwar bazata yarda bah, </p><p> Abunda yasa ita kuma ta yarda sabo da taga Raudar tazo bada dadewa bah. </p><p><br /></p><p>Cike da murna da kuma farin ciki ta fara shiri tana kwalliya, dan tana so ace *LAILAH-DIZHWAR* tayi kyau. </p><p><br /></p><p>Nan ta saka material din ya zauna ajikinta yayi mata mugun kyau tamkar itama Amarya ce, nan ta feshe jikinta da turare me sanyin dadi. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Su Dizhwar an gama kashe kala, an gama shiri kowa yayi kyau, nan aka iso da rantsantsun motoci suka jeru kowanne shida Amaryarsa, duk da cikin gidannne amma saida aka hau mota, nan kowa ya nufi part din da Amaryarsa take, har Dan gidan Waziri Umar Pharouk wanda zai auri Zakiyya. </p><p><br /></p><p>Nan Amare aka fara fitowa ana ta musu faman hotona haka ana ta zuba fure a hanyar da zasu fito din.</p><p><br /></p><p>Dizhwar motarsu bata jima da tsayiwa bah, Husna ta shigo ciki, tare da kara matsawa jikinsa har wani kwantawa take tana musu selfie yayin da Ango aka Sha kunu ko murmushi bama yayi. </p><p><br /></p><p>Kara shigewa jikinsa tayi, nan take Maganin Anty Amarya ya fara aiki,Dizhwar ya tsinci kansa ame biye mata, dan yanda yake ji komai ma Zai iya faruwa. </p><p><br /></p><p>haka ya rungumeta har suka karasa, ko kadan beso suka sauka daga motar bah. </p><p><br /></p><p>Haka suka shiga cikin wajan, sai faman janta jikinsa yake, ita kuma Sai wani kara manne mai take, nan fa suka burge kowa, sai faman hotuna ake musu kamar sa cinye juna haka suke ji. </p><p><br /></p><p>Nan kowanne Ango da Amaryarsa suka Zauna a wajan zaman su. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Dizhwar daya jima da aika mota gidansu Lailah, yama manta shab, dan gaba daya yanzu halin da ake ciki ya fita daga hayyacinsa. </p><p><br /></p><p>Yayin da aka shigo Da Lailah cikin gidan sarautar nan, tana zaune bayan mota tana faman kallan irin motocin dake dankare cikin gidan, haka aka karasa da ita har kofar hall din. </p><p><br /></p><p>Ahankali cikin takunta najan hankali, ta shiga wajan tana faman taku daidai, saida taja hankalin mutane da yawa, dan gani ta ake kamar wata yar gidan manyan nan. </p><p><br /></p><p>Karasawa tayi can, tana kokarin zama, Ganin Amare guda uku da kuma Angwaye uku yasa kanta ya juye, dan ita bama ta gane Dizhwar din nata bah. </p><p><br /></p><p>Zama tayi nan aka cika mata gabanta da Abinci da Abinsha, ita kuwa lokacin babu abunda tafi bukata ta gani sama da Dizhwar, sai faman waige waige take, taga ta inda zata hangosa. </p><p><br /></p><p>Jin Mc yana fadin, </p><p> _"Yarima Dizhwar da Amarya Husna suma suna yima bakinsu barka da zuwa"_</p><p><br /></p><p>Da sauri ta mike tana kara kurawa Angwayan ido, </p><p> Nan kuwa idanta suka sauka kan Dizhwar, kasa tsayiwar tayi dole ta nemo waje ta zauna tana me kura musu ido, yayin da Amaryarsa take masa magana yana murmushi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_"Innalillah,innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, ba gaskiya bane Lailah, ba gaskiy bane, Mafarki kike Lailah, Innalilahi !"_</p><p> abunda take ta faman fada kenan zuciyarta tana mata wani irin Abu, da bata taba jin irinsa ba tunda take a duniya. </p><p><br /></p><p>Da sauri tayi kokarin mikewa dan fita waje ko zata shaki iska Me dadi dan iskar wajan tayi mata kadan, sabo da tashin hankali, amma ji tayi kafafunta kamar an daure su. </p><p><br /></p><p>Nan da nan idanta suka kada sukayi jajir dasu. </p><p><br /></p><p>Anty Amarya na zaune a gefanta itama, jikinta yana tsuma sabo da abunda ta bama Dizhwar itama shi tasha jira take kawai taga ya fita waje itama ta bishi dan ta biyama kanta bukata, dan tasan nan gaba kadan in har be kasance da mace ba zai iya mutuwa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(20)*</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>*Dedicated This page to all my Whatapp Fans, love you irin sosai sosai din nan, Allah ya bar zumunci Nagode sosai da irin soyayyar da kuke nuna min Nagode*😍</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin sauri ta shiga, tare da janyo Husna gefe, hular ta nun mata tare da fadin, </p><p> _"Wannan Hular Kamar ta Dizhwar"_</p><p><br /></p><p>Amsa tayi tare da fadin, _"itace mana"_</p><p><br /></p><p>kamar ta nuna mata abun hannun, sai kuma tayi tunanin kar tajI kunya, aje watace ta yarda shi tunda bashi kadai yake bin hanyar bah. </p><p><br /></p><p>_"Amma ya akai, hularsa ta fadi kamar wanda bashi da hankali be sani bah"_</p><p><br /></p><p>_"Toh kode da gasken bashi da lafiya, kuma ina ya tafi"_</p><p> Husna ta fada. </p><p><br /></p><p>Wayarta ta amsa ta shiga kiransa amma harta gama ringing dinta be daga bah. </p><p><br /></p><p>_"Anty Salima barshi kawai koma menene maji da safe, sabo da dolansa ai yaje wajan daurin aure, babu damuwa"_</p><p><br /></p><p>Tana fadar haka ta shige cikin jama'a, batare da ta nuna wata damuwa sosai bah. </p><p><br /></p><p>Binta Anty Salima tayi tana so ta tuno inda taga wannan abun hannun. </p><p><br /></p><p>_____</p><p>Haka aka sha shagali aka tashi daga wajan Party kowa cikin farin ciki amma Banda Amarya Husna, shima Jafar ya duba amma be gansa ba, amma be nuna damuwa ba tunda yasan ai yana nan saide in waje suka fita.</p><p>Itama haka Husnar duk jarabarta ta hakura, amma tasan koma ina ya tafi gobe ahine karahe, tuda za'a daura musu aure kuma dole yaje wajan daurin auran, in yaso in sukayi auran dolansa ya gaya mata ko ina yake zuwa. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Dizhwar kuwa saida yaji ya gamsu dari bisa dari babu wani sauran ciwo da yake ji, </p><p> Gefe ya koma ya kwanta yana maida numfashi, saida yayi kusan awa daya tukun hankalinsa ya dawo jikinsa. </p><p><br /></p><p>Da sauri ya mike zaune ganin inda yake, da sauri ya kalli gefansa, ganin Lailah yasa yayi saurin matsawa gefe. </p><p><br /></p><p>Ganin kamar bata numfashi bare motsi yasa yayi sauran matsowa ya shiga marin fuskarta Ahankali yana saka kunansa kan kirjinta amma shiru.</p><p><br /></p><p>_"Innalillahi wa'inna illaihir raji'un, shikenan na kashe Lailah, ashe dama nine ajalin yarinyar nan shiyasa na gaiyaceta wajan nan"_</p><p> Gaba daya hankalinsa ya gama tashi, haka yaci gaba da tashinta amma babu abunda yake motsi ajikinta, ga fyade da yayi mata, gaba daya daga shi har ita da kuma wajan ya bace da jini. </p><p><br /></p><p>Da sauri ya mike ya dauki wandansa duk da jinin da yake jiki ya saka, ya nemi kayanta ya saka mata,yanayi yana kuka dan yasan bashi da yanda zaiyi, gashi Anata sallah yama rasa yaya ziyi, gashi kayansa duk sun bace da jini balle ya fita. </p><p><br /></p><p>Haka ya dauka ya saka,Ahankali ya bude dakin ya leka ganin babu kowa yasa ya dawo ciki, jin yataka abu ya durkusa ya dauka ganin wayarsa yasa yayi saurin dauka, dubawa yayi yaga lokacin karfe 4:03am, cikin aljihunsa ya saka tare da daukar Lailah ya matsar da ita can gefe cikin kaya ya rufeta da bargunan wajan ya fita daga cikin sakin. </p><p><br /></p><p>Ahankali ya fita yana sauri harda gudu gudu ya nufi part dinsu, kana ganin yanda yake dube dube kasan bashi da gaskiya. </p><p><br /></p><p>Yana zuwa dakinsu ya bude tare da shiga falon, babu kowa dan haka da sauri ya nufi bedroom dinsa. </p><p><br /></p><p>Yana shiga yasa key ya kulle tare da cire kayan jikinsa ya shiga wanka, ya jima a bandakin kafin ya fito, alwala yayi, yayi sallah anan dan bama yasan fita daga Dakin. </p><p><br /></p><p>Bayan ya idarnne yaji wata irin kasala ta saukar masa, amma gaba daya hankainsa baya jikinsa, banda tunanin halin da yake cike ga kuma kisa da yayi. </p><p><br /></p><p>Mikewa yayi ya koma kan gadon ya lullube dan zazzabi yake ji ajikinsa. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Koda gari ya waye, Jafar fitowa yayi daga dakinsa ya nufi wajan Dizhwar dan ko ya dawo. </p><p><br /></p><p>Yana shiga kuwa ya gansa kwance cikin bargo, da sauri ya karaso wajansa tare da budeshi ya taba shi. </p><p><br /></p><p>Zafi yaji sosai ajikinsa. </p><p><br /></p><p>_"Dizhwar"_</p><p> Jafar ya kira sunan sa. </p><p><br /></p><p>Ahankali ya bude ido yana kallan Jafar din. </p><p><br /></p><p>Ganin yana rawar sanyi yasa yayi maza ya rufe shi tare da kiran dr. A wayarsa. </p><p><br /></p><p>Koda yazo ya auna shi magani ya bashi da kuma allura. </p><p><br /></p><p>Sannan ya samu bacci. </p><p><br /></p><p>Jafar yana nan yana faman kallansa ganin duk ya rame lokaci daya, zuwa yayi ya sanar ma da Mami abunda ya faru, nan da nan hankalinta ya tashi gaba daya gida ya dauka Dizhwar bashi da lafiya. </p><p>Nan da nan part dinsu ya cika dan ganinsa. </p><p><br /></p><p>Husna kuwa kuka take dan ganin halin da ya shiga. </p><p><br /></p><p>Koda Anty Amarya taji labari bakin cikine ya kamata sabo da kasancewar da batayi dashi bah, itama abunda ya faru da shi itama ya faru da ita, dadde ita tana da yan iskanta waya kawai zata musu su ,suzo su biya mata bukatar tah,bakin cikinta shine da bata san dawa Lailah ya kasance bah, dan tabbas da be kusanci wata ba saiya mutu, dan haka bokanta ya gaya mata. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Lokacin da ya farka, nan Jafar ya lalabashi danya shirya aje wajan daurin auran. </p><p><br /></p><p>Breakfast yayi dan yaji kafin jikinsa, bayan ya gama ci, gaba daya hankalinsa yana wajan gawar nan, fita yayi waje ya samu wani yaran sa,nan ya sanar masa da wata matsalace ta faru yana so, yaje cikin dakin, yayi masa kwatance, ya dauki gawar mace kuma ya dauke dukkan wata sheda yaje ya yarda ta acan nesa da gari batare da kowa ya san da hakan ba. </p><p> Nan kuwa yayi Naam da abunda ya gaya masan. </p><p><br /></p><p>_____</p><p>Bayan sun gama shirinsu cikin kayansu na alfarma suka nufi wajan daurin Auran anan masallacin gidan sarautar inda manyan mutane suka halarci wajan, dan babu masaka tsinke. </p><p><br /></p><p>Bayan an gama dukkan abunda Za'a yi, aka hada wata babbar walima. </p><p><br /></p><p>Amma duk abunda ake Dizhwar dauriya kawai yake dan bayajin dadi har lokacin. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Ita kuwa Lailah abunda aka saka wannan bawan shi yayi, ya dauketa ya nufi can hanyar Sokoto da ita ya yarda ta cikin wani daji, ya dawo gida ko ajikinsa, sannan yasa a gyara cikin dakin da Abun ya faru,</p><p> Bayan ya dawo ne ya sanar da Dizhwar din aikin gama Ya gama, sai lokacin hankalimsa ya kwanta, sannan yayi masa alkawarin kudi masu yawa, sannan karya sake ya gayawa kowa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(19)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zuwa lokacin babu abunda Lailah take banda kuka,</p><p><br /></p><p>Duk inda yayi sai faman kallansa take, jira kawai take taga ya fita. </p><p><br /></p><p>Idannan yayi jajir dashi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shikuwa Dizhwar zuwa lokacin ya fita daga haiyacinta, sai faman gumi yake, ga wata Mahaukaciyar Sha'awa wanda besan da akwai irin tabah.</p><p><br /></p><p>Ahankali ya rada ma Husna wani abu a kunne, batare data bashi amsa bah, ya fita da sauri. </p><p><br /></p><p>Da Sauri Lailah ta mike haka itama Anty Amarya. </p><p><br /></p><p>Da gudu Lailah ta fita dan tasha gaban sah, yayin da Anty Amarya ta fara sauri, Jafar da Asiya suka iso wajan ta tare da me hoto, nan taji kamar zata mutu, sai faman kallan kofa take, haka suka hanata tafita ana ta hoto. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Lokacin daya fita kofar wajan, yaji cikinsa ya kulle ya tsaya tare dafa bangon wajan, hular dake kansa ya cire tare da yardawa, </p><p> Karan takun mutun da yaji gabansa, yayi saurin dagowa, duk ya fita daga haiyacinsa. </p><p><br /></p><p>Ganin Lailah gabansa yasa ya bita da kallo, Ahankali ta jaraso tana kallansa tana hawaye. </p><p><br /></p><p>Saida tazo daf! da shi, tukun ta fara fadin, </p><p><br /></p><p>_"Amma ban taba tunanin zaka ci amanata haka bah, ashe dama aure zakayi amma shine ka shigo Rayuwata danka cuceni"_</p><p><br /></p><p>Ahankali ya mike tare da nufo ta, </p><p><br /></p><p>Da sauri taja baya tare da fadin, </p><p> _"Karka sake ka matso kusa dani"_</p><p> Tana magana tana nuna shi da yatsa tana kuka. </p><p><br /></p><p>_"Dan Allah Lailah ki tsaya ki saurareni kada kimin muguwar fahimta haka mana"_</p><p><br /></p><p>_"Me zaka gaya min, bayan gashi na gani ido da ido ba lbr aka bani bah, meyasa zaka min haka meyasa ka yaudareni"_</p><p> Ta karasa maganar tare da durkushe kasa tana kuka. </p><p><br /></p><p>Batare daya mata magana bah, ya dauketa cak!. </p><p><br /></p><p>Da sauri ta bude ido tana ihu, tare da mai Masifa danya ajje ta, garin dukan bayansa abun hannunta ya fadi anan wajan. </p><p><br /></p><p>Cikin wani daki ya shiga da ita, inda ake ajje Carpet manya da kuma abubuwan shimfidu kala kala. </p><p><br /></p><p>Saida ya shiga ya kulle kofa tukun ya Ajjeta kasa. </p><p><br /></p><p>Da sauri taja baya tana fadin, </p><p> _"Meyasa zaka kawoni nan, nariga na gama gane ko kai waye, ka bani hanya in huce, Allah ya isa tsakanina da kai"_</p><p><br /></p><p>Tana fadar haka ta nufo wajan zata bude kofar, da sauri yasha gaban ta tare da durkusawa kasa yana mata magana, </p><p> </p><p>_"Dan Allah Lailah kiyi hakuri, ki rufamin asiri wallahi ina cikin wani mahuyacin hali, da in baki taimakaminba zan iya mutuwa"_</p><p> Yana tsugunne a kasan ta ya rike mata kafar ta. </p><p><br /></p><p>Idanta ta rintse, tana jin yanda wani mugun sansa yake Kara shiga dukkan illahir bargo da kuma tsoka na jikin tah. </p><p><br /></p><p>kamar ta juya ta ji damuwarsa amma tayi saurin fizge kafar ta. </p><p><br /></p><p>Ganin haka Dizhwar yaga zata bata masa lokaci gashi kuma jikinsa har ya fara yin weak, yasa ya janyota tare da hada ta da bango ya shiga kissing din tah, tun daga bakinta har huyanta da kirjinta, ga wani Mugun ruko da yayi mata, da karfin tsiya kamar wani Zaki ya fincike yar rigar da take jikinta. </p><p><br /></p><p>Hakan yasa Ahankali ya kara tashi babu abunda take banda ihu da kuka,nan da nan ta tuna abunda Mama ta gaya mata . </p><p><br /></p><p>Da sauri ta samu ta kwace jikinta ta koma can karshan dakin tana kare kirjinta da hannunta tana kuka tana kallansa. </p><p><br /></p><p>_"Dan Allah kayi hakuri, wallahi ni baka cuceni ba, dan Allah karka lalatamin Rayuwarta, wallahi nayi maka alkawarin bazama ka kara gani na bah, zan bar maka gidanka da kuma garin ku, Dan Allah Dizhwar"_</p><p> Tana kuka tana magana harta kai kasa dan rokonsa. </p><p><br /></p><p>Shima Kara sowa yayi tare da durkusa a gabanta, da sauri ta kara makurewa jikin bango. </p><p><br /></p><p>_"Lailah ke nake kauna kece farin cikina, kece matata da koda yaushe nake mafarkin kasancewa dake, in kika barni cikin wannan halin wallahi mutuwa zanyi, karki min haka dan Allah Lailah"_</p><p> Shima kukan yake kamar yanda itama takeyinsa. </p><p><br /></p><p>Babu bakin magana illah,Girgiza kai da takeyi, dan ganin yanda Dizhwar din ya koma kamar bashi ba. </p><p><br /></p><p>Cire rigarsa yayi, yayin data rufe idanta ta dan bata san ganinsa gaba daya. </p><p><br /></p><p>Da gudu ta mike zata fita, cafkota ya kumayi, tare da turata kan Carpets din, tare da Hawa kanta, yana kokarin cire wando. </p><p><br /></p><p>Wani ihu ta saki,kodan mutane zasuji su kawo mata agaji, amma babu wanda yasan tanayin, haka.</p><p> gashi yanayin yanda ya danne ta, ko motsi bata iyawa saide ihun. </p><p><br /></p><p>Suna fada haka ta tattaro dan karfinta tana dukansa da yakushinsa, yanda zai rabu da ita, amma saida ya cire skirt din da pant din tukun ya fara kokarin aikata abunda zuciyarsa da duk illahirin jikinsa yake san yi. </p><p><br /></p><p>kuka kawai Lailah take tana rokonsa amma ko jinta baya yi, saida ya fara aikatawa tukun bakinta ya fara rage ihun sabo da ta fara fita daga haiyacinta, tun tana kallan fitilar dakin har duhu ya mamaye hasken Dakin. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Ganin har lokacin Dizhwar be dawo ba yasa hankalin,</p><p> Husna ya tashi, nan ta fara neme neme, Anty Salima ta sanar ma, nan itama ta shiga duba san. </p><p><br /></p><p>_"Bara na leka waje nagani ko yana can baki yayi"_</p><p> sannan ta fita dan duba sa, amma ganin babu kowa a wajan yasa ta dawo ciki, kan hanyarta na shiga hall din, ta taka Abun Hannu, da sauri ta tsugunna dan dauka, Hular Dizhwar ta gani yarde a kasa. </p><p> Dauka ta yi, tana dubawa tare da komawa cikin Hall din.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(21)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kobayan an gama Walimar da Memartaba ya shirya, kowa gida ya nufa, yayin da Dizhwar yana zuwa, abinci aka kawo masa, sai bayan yaci ya koshi yasha magani ya kwanata.</p><p><br /></p><p>_________</p><p>Mama kuwa tun bayan da Lailah ta tafi gashi time din anyi magriba, tashi tayi ta fita waje dan ganin bata dawo bah, </p><p> Kasancewar tasan gidan su Rauda ta tafi shiyasa bata wani damu sosai bah,</p><p><br /></p><p>Abu kamar wasa har goma tayi shiru, kasa zaune tayi bare tsaye, Daidai lokacin Babansu ya dawo. </p><p><br /></p><p>Nan ta nuna masa ai Lailah bata nan har yanzu bata dawo bah, dan haka shima fada ya kama yima Maman akanme zata bari ta fita duk da sunsan Lailah yarinyace me hankali bazasu zargeta bah. </p><p><br /></p><p>Shiru suka zauna ganin bata dawo ba har 11pm, hakan yasa Abban ya fita. </p><p><br /></p><p>Kai tsaye gidan su Rauda ya nufa, koda yaje gidan kulle da kwado babu kowa, wani gumine ya karyo masa. </p><p><br /></p><p>Yana kokarin tafiya saiga Rauda ta dawo.</p><p><br /></p><p>Ganin shine yasa ta gaida shi, nan ya hau nuna mata Lailah bata zo bah. </p><p><br /></p><p>Haka itama ta maida masa, dan raban da taga Lailah ta jima dan ita yanzu daga wajan aiki take ba wajan biki bah. </p><p><br /></p><p>Batare da yace mata komai ba, ya tafi hankalinsa a mutukar tashe, gashi Lailah bata taba musu irin haka bah. </p><p><br /></p><p>Haka ya dawo gida duk jikinsa a sanyaye, tunda Mama taga ba Lailah ta fara kuka, nan ya zauna tare da sanar mata be gan ta bah, kuma ba gidan su Rauda taje bah. </p><p><br /></p><p>Kuka Mama ta fara tana nuna hannu alamun dama saida jikinta ya bata karya tayi mata. </p><p><br /></p><p>Nan de suka rasa abunyi, suka hakura zuwa wayewar gari, amma koda garin ya waye, duk da ba wani baccin kirki sukayi bah, </p><p> Safiya nayi Mama ta tashi Abban dole sai sunje wajan yan sanda sun sanar musu da batan yar tasu. </p><p><br /></p><p>Haka ya hakaru suka je,</p><p> Suna zuwa kuwa suka samu wasu anan waje suka fara nuna masa magana da kurmanci, kasancewar be gane abunda suke nufi sosai bah, suka dauko musu biro da Paper dan su rubuta abunda ya kawo. Su. </p><p><br /></p><p>Nan suka zauna Abban ya rubuta yakai musu. </p><p><br /></p><p>Bayan sun gama karantawa, suka maido musu da amsar ko tana da saurayi. </p><p><br /></p><p>Nan suka rubuta tana dashi amma dan gidan sarkin Zamfara ne. </p><p><br /></p><p>Koda suka karanta abunda Abban ya kuma Rubutawa, kallan Juna sukayi, tare da fadin, </p><p> </p><p>_"Amma wannan mutanan basu da hankali, taya zasu ce mana dan sarki ne yake san yarsu, kode dan sarkin mahaukata"_</p><p> Haka suka kora su daga police din suka fita suna Rokonsu amma babu wanda ya kula su. </p><p><br /></p><p>Mama zama tayi tana ta faman kuka, ganin abun yaki karewa yasa Abban,fada mata suje su Sami Aminu. </p><p><br /></p><p>Kallan sa kawai tayi, tare da goge hawayanta ta tashi tayi tafiyarta ta barsa anan dan koda Lailah mutuwa tayi bazata nemi daya daga cikin yaran nasu ba, balle kuma bata tayi tana sa ran insha Allah zata dawo gareta. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Har yamma tayi anata faman shagali a gidan Sarki domin yaune za'a kai Amare gidan su. </p><p><br /></p><p>Gaba daya an gama shirya wa su Jafar Jirgin tafiyarsu. </p><p><br /></p><p>Asiya da yan kano suka fara shirin tafiya yayin da Asiya banda kuka babu abunda takeyi, haka itama Husna aka kaita part dinta da Memartaba ya tanadar musu, yayin da Zakiyyah ita Za'a dauketa a kaita gidan ta dake nan cikin garin Zamfara. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Jama'a duk an fara watsewa amma Shi Jafar ya ringa ya fada ba ranar zai tafi ba sai washe gari sabo da Jikin Dizhwar. </p><p><br /></p><p>Sai wajan karfe 9pm tukun ko wacce aka tafi kaita, gidan shiru duk babu hayaniya duk an tafi kai amare. </p><p><br /></p><p>Sai dangin Husna kawai a part dinsu suna shagalinsu. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Lailah kuwa tunda aka kaita wannan wajan aka yarda ta, bata san inda kanta yake ba cikin wannan dajin, tana kwance har zuwa lokacin kamar gawa ko ba numfashi balle Motsi. </p><p><br /></p><p>Gaba daya jikinta ya kumbura, gashin kanta duk ya hargitse ga uwar dauda da tayi, duk tayi baki in baka sanda ba da yanzu bazakace ita bace. </p><p><br /></p><p>_________</p><p><br /></p><p>Bayan an kai Amare, dare Yayi wajan 11pm, har lokacin Dizhwar yana daki a kwance, babu zazzabin yanzu a jikinsa, illah Kasalar jikinsa.</p><p><br /></p><p>Yana kwance akan sofa, shida Jafar, Anty Amarya ta turo kofar dakin nasa. </p><p><br /></p><p>Da sallama ta shigo, wata tana biye da bayan ta, sata tayi ta ajje babban tray din daya cika da flasks akansa, ajje shi tasa ayi sannan wacan din ta fita. </p><p><br /></p><p>Itama zama tayi tare da fadin, </p><p> _"Sunna da jiki Dizhwar "_</p><p><br /></p><p>_"Ywwah"_</p><p> ya fada Jafar yana gefansa.</p><p><br /></p><p>_"Katashi ka dan daure kaci dan farfesun dana sa ayi maka saikasha magani ko kaji kwarin jikinka"_</p><p> Ta fada tana kallansa. </p><p><br /></p><p>Shiru yayi dan baya bukatar komai, amma jin abunda ta fada yasa ya fara Sha'awarci jin ace Farfesune. </p><p> Amma sai yayi shiru be mata magana bah. </p><p><br /></p><p>Jin haka yasa tayi murmushi tunda taji yayi shiru tasan zaici,</p><p> Dan haka mikewa tayi tare da kallan Jafar, </p><p> _"Pls Jafar kasa yaci ko kadanne, Allah ya sauwake"_</p><p> Ta fada tare da fita. </p><p><br /></p><p>Jafar binta yayi da kallo danshi sam!, be yarda da ita bah. </p><p><br /></p><p>Tana fita Dizhwar din ya mike zaune tare da fadin, </p><p> _"Jafar dan zubomin inci dama ina san cin Abu medan yaji yaji"_</p><p><br /></p><p>Anty Amarya dataki kulle kofa sosai dama dan taji abunda Za'a fada, murna ta kama dan ta saka maganin mallaka aciki, burinta Dizhwar yaci, yana ci kuwa ya dawo a tafin hannunta dan sai abunda tace masa shi zaiyi. </p><p><br /></p><p>Banza Jafar din yayi dashi, ganin haka yasa ya mike da kansa ya nufi abincin. </p><p><br /></p><p>Hannu yasa ya bude flask din. </p><p><br /></p><p>Wani irin kamshine ya daki gancinsa, hannu yasa zai Tun aciki ya fara ci dan baze iya jiran ayi serving dinsa bah. </p><p><br /></p><p>Turo kofar da Husna tayi yasa yayi saurin dauke hannunsa daga kai tare da mikewa tsaye. </p><p><br /></p><p>Binshi tayi da kallo, tare da kallan Jafar. </p><p><br /></p><p>Ganin kallan da takema Dizhwar din yasa, Jafar mikewa yabar wajan. </p><p><br /></p><p>Da sauri ta karaso tare da rungumeshi, suka koma kan kujera suka xauna. </p><p><br /></p><p>_"Hubby yaya jikin naka? "_</p><p> Shiru yayi mata yana kallan tah. </p><p><br /></p><p>_"Baka kaunar matar kane, zaka zo na ka zauna bayan kasan wanna shine ranar mu ta farko ranar da ya kasance mu nunawa juna farin ciki da kuma sun da mukewa junan mu, amma shine zaka ki zuwa kayi zaman ka anan?"_</p><p> Bece mata komai ba, illah kallanta da yake yi. </p><p><br /></p><p>_"Kidan zubomin wacan abun, inaso inci yinwa nake ji"_</p><p> Daga shi tayi tare da nufar flask din, tana budewa taji kamshin maganin, kasancewar suma masu harkanne yasa tayi saurin ganewa. </p><p><br /></p><p>Da sauri ta kalle shi tare da fadin, </p><p> _"Wanene ya kawo wanna abun? "_</p><p><br /></p><p>_"Ki Zuba min magana ina ruwanki da wanda ya kawo ki kawo Min mana"_</p><p><br /></p><p>_"Toh wallahi in baka fada min ko waye ya kawo maka ba, bazaka cishi bah"_</p><p><br /></p><p>Shiru yayi mata yana kallan ta. </p><p><br /></p><p>Daukar tray din tayi tayi hanyar fita dashi. </p><p><br /></p><p>_"Husna ki maidomin mana meyasa baki da hankali ne"_</p><p><br /></p><p>Bata kulashi ba sabo da ita tasan abunda ta gani Ta fita, </p><p><br /></p><p>Binta yayi da sauri suka fita wajan 12am, tana tafiya yana binta a baya. </p><p><br /></p><p>Anty Amarya dake kusa dasu, tana jiran DIZWARH ya gama ci ta kirashi, dan yau tana bukatar shi, ganin Husan ta shiga yasa gabanta ya fara faduwa dan tasan wannan jarabarbar bazata barshi ya ci abincibah. </p><p><br /></p><p>Kamar kuwa ta sani ta hangota da flask din tana faman sauri, shikuma yana binta a baya. </p><p><br /></p><p>Da sauri ta mike, da kamar bazata fita ba, sai kuma ta tuna irin kudin data kashe kan maganin da kuma tana da hadama gaba daya ta juye. </p><p><br /></p><p>Da sauri ta fita tare da tarar Husnar, a tunaninta bata san komai bah. </p><p><br /></p><p>_"Ke Husna meye haka baki da hankaline wai ke"_</p><p> Ta fada tare da karasowa wajan. </p><p><br /></p><p>Dizhwar kuwa bata masa rai tayi, tsaki yayi ya kOma dan baxai iya jurewa binta haka bah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Gabanta ta tsaya suna kallan juna. </p><p><br /></p><p>_"Meyasa kike irin wannan, kefa bakuwa ce, nikuma uwar shice, zai iya sakinki kibar gidan nan, nikuma ina nan daram!, akan me nayi masa kirki zaki hana yaci, kuma ma sabo da baki da hankali da tarbiya kika biyo miji sai kace ba mace bah"_</p><p> Anty Amarya ta fada ranta a bace. </p><p><br /></p><p>Tsayiwa Husna ta gyara tare da fadin, </p><p> _"Ashe ke babar shice, kina da sanin cewar yau in ubansa ya sakeki baza kibar gidan bah, har zakizo kina min wannan maganar, ko a tunaninki kece surukata, toni ko ita wanda ta haifeshin bata isa ta shiga tsakanina da mijina ba in rabu dashi, balle ke, ko an gaya miki bansan abunda kika zuba acikin abin cin bah, ninan da kika ganina karshece, a cikin tafin hannu na kike,da naga dama Sarkin zan aura gaba daya, amman ni Dizhwar nake so, ke bara ma kiji in gaya miki, tunda har muka kawar da mahaifinmu, toh duk wani dan iska ya kuka ga kashi sabo da haka"_</p><p> Tana fadar haka ta saki flask din a kasa ya hude abincin duka ya rube a kasa. </p><p><br /></p><p>Bate cewa Anty Amarya komai ba ta nufi dakin Dizhwar din. </p><p><br /></p><p>Binta tayi da kallo tare dayin murmushi itama ta koma dakin ta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(22)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda ta koma dakin nasu, ya kulle kofar, dan yasan zata dawo ta dameshi. </p><p><br /></p><p>Nan kuwa ta murda taji akulle, tayi ta faman knocking amma shiru harta gaji ta koma dakinta, ganin hadari ya hado alamun ruwa zai sauko.</p><p><br /></p><p>_______</p><p>Can tsakiyar dare kuwa Ruwan sama ya sauko me karfi, aka sheke kamar da bakin kwarya. </p><p><br /></p><p>Duk wannan Ruwan da ake akan Lailah ya sauka, lokacinne ta dawo hayyacinta, Ahankali ta fara bude ido jin har lokacin ruwan yana zuba a kanta ga walkiya da akeyi. </p><p><br /></p><p>Tana san ta bude idon amma ruwa da yake sakkowaya ya hanata, tana ji tana gani dole saida ta hakura tukun Aka gama ruwa. </p><p><br /></p><p>Wani mugun sanyi takeji domin kayanta gaba daya sun jike da ruwa. </p><p><br /></p><p>Gashi ko motsin kirki bata iyawa, sabo da ciwan da jikinta yake mata. </p><p><br /></p><p>Hakan yasa ta fara zubar da hawaye, tana daga kwance. </p><p><br /></p><p>Kwata kwata tama rasa abunda ya faru da ita, domin ganinta cikin dokar daji, tunaninta yama kasa kawo mata tayayya har tazo nan wajan. </p><p><br /></p><p>Ahankali ta fara fadin, </p><p> _"Mama, mama,Abbana kuzo ku taimakamin wayyo Allah ni mutuwa nayi waya kawoni nan wajan?"_</p><p> Surutai kala kala take a wajan sabo da rudani data shiga ga kanta daya juye, sai karkarwa take haka hakoran bakinta sai haduwa suke, ta rasa yanda zatayi da sanyin datake ji. </p><p><br /></p><p>Har gari ya fara haske kayan jikinta sun fara bushewa sabo da iskar da akeyi. </p><p><br /></p><p>Duk wannan sanyin a kanta ya kare, tana nan kwance rana ta fara fitowa. </p><p><br /></p><p>Ahankali ta haske inda take kwancan, hakanne yasa taji dadin wajan, harta fara daina jin sanyin. </p><p><br /></p><p>Karfin hali tayi ta fara kokarin motsawa. </p><p><br /></p><p>Amma jin radadi daga kasanta yasa ta kasa, ta koma tana kiran sunan Allah. </p><p><br /></p><p>Saida ta jima tana addu'a, tukun ta kara kokarin tashi tsaye, wani ihu ta saki tare da fashewa da kuka jin zafin da taji yafi na da. </p><p><br /></p><p>Kuka sosai take tana kiran taimako amma ganin babu me jin ta yasa ta fara jan Jiki a kasa tabi wata hanya wanda bata san inda zata kaita bah, tana yi tana kuka tana hutawa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>________</p><p>Koda gari ya waye wajan 10am, Jafar ya gama shirinsa na tafiya, fitowa yayi ya tarda Dizhwar zaune yana shan Coffee. </p><p><br /></p><p>_"Aa naga harka fito bade tafiya bah?"_</p><p><br /></p><p>Kallansa yayi tare da fadin, </p><p>_"an gaya maka nima irin kane, kawai nayi aure saina zauna ina kallanka, tafiya zanyi in yaso kaita zama kaida dakin, Amaryata rana jirana, sabo da Haka, Sokoto zani inna gama abunda zanyi, zan hau jirgi na tafi gida"_</p><p><br /></p><p>_"Amma bazaka kara ko kwana daya ba"_</p><p><br /></p><p>Kalansa kawai yayi dan bashi da amsar dazai bashi, fita yayi daga dakin yana murmushi. </p><p><br /></p><p>Cikin gida ya shiga ya karya tukun yayi musu sallama, sannan ya nufi wajan Memartaba. </p><p><br /></p><p>Saida ya jima tukun ya fito ya koma wajan Dizhwar. </p><p><br /></p><p>_"Toh kai zan huce, sabo da haka,ka kula da kanka kuma ka dinga addu'a sabo da kwana biyun nan duk an rasa kanka, nina huce,aci Amarci lafiya"_</p><p><br /></p><p>Banza Dizhwar yayi masa, sai tasowa da yayi dan masa rakiya, cikin motar ya shiga dan yayi rana sosai. </p><p><br /></p><p>_"Allah ya kiyaye inka isa saika kira ni, ka gaida yan gidan, sai nima nazo"_</p><p><br /></p><p>Kallansa Jafar yayi yana saka Sit-belt tare da fadin, </p><p> _"Haka zaka ce sai kunzo, yawwa nama manta ban yima Anty Husna sallama bah, in kaje saika gaya mata na huce, a kula Abokina"_</p><p> Ya karasa maganar yana murmushi. </p><p><br /></p><p>Cin magani Dizhwar yayi, tare da fadin, </p><p> _"Allah kiyaye sai munyi waya"_</p><p><br /></p><p>Yana fadar hakaya juya ya nufi dakin nasu. </p><p><br /></p><p>Shikuwa Jafar girgiza kai yayi yana dariya tare dajan motar ya fita, masu aiki suna daga masa hannu harya fita Daga cikin gate din. </p><p><br /></p><p>Nan ya dauki hanyar Sokoto yana faman sauri. </p><p><br /></p><p>Wayar shice ya ga tana haske alamun kira na shigowa, ganin Asiya yasa yayi Murmushi tare dagawa. </p><p><br /></p><p>Yana tafiya suna waya, har yayi Nisa tukun ya kashe. </p><p><br /></p><p>Saida yahau kan Tatin Sokoto tukun ya ajje wayar yaci gaba da tukin.</p><p><br /></p><p>________</p><p>Lailah tayi nisa sosai dan ta fara gajiya, kwanciya ta kumayi tana hutawa dan duk jikinta ciwo yake mata. </p><p><br /></p><p>Haka taci gaba da jan jikin dan ta kusan fitowa titi.</p><p><br /></p><p>Tana ganin mota ta huce, ta fara kokarin daga hannu amma ta kasa, haka ta yi kokarin daga murya tayi ihu nan ma shiru, dole ta kuma daurewa danyin sauri ta fita. </p><p><br /></p><p>Ahankali tana fadin, </p><p> _"Wayyooooh Allah na"_</p><p>Tana matsawa harta fito titin gaba baya. </p><p><br /></p><p>Tun daga nesa, Jafar yake hango kamar mutun yana rarrafe ko jan jiki ne, ya kura ido, hakan yasa da ya danji tsoro kawai ya huce warsa. </p><p><br /></p><p>Ita kuwa ganin motar yasa ta daga hannu, dan lokacin duk karfinta ya kare. </p><p><br /></p><p>Ganin ya huceta yasa ta saddakar, ganin wajan dama tudu da gagarene, kawai ta saki jikinta, ta koma baya. </p><p><br /></p><p>Ta jikin mirro dinsa yake hango yanda ta koma, tsayawa yayi da motar tare da yin baya yana addu'a cikin zuciyarsa. </p><p><br /></p><p>Saida yazo daidai inda yake hangota tukun ya tsaya ya kashe motar tasa. </p><p><br /></p><p>Fitowa yayi tare da gangarawa wajan ta. </p><p><br /></p><p>Tana kwance a kasa, gashi a rufda ciki bama ya iya ganin fuskarta. </p><p><br /></p><p>Bismillah yayi tare da durkusawa ya jirkitatah. </p><p><br /></p><p>Zuciyarsa sai bugawa take dan yana da tsoro ba laifi. </p><p><br /></p><p>Hannu yasa ya gyara mata gashin kanta, ya kalli fuskarta da duk tayi dirty ga kuma Kumburi da tayi buga da kari ga ciwo. </p><p><br /></p><p>Hannunsa yakai wajan huyanta ko tana numfashi, nan yaga ta bude ido, Ahankali idanta ya cika da kwallah, tare da fadin, </p><p> </p><p>_"Wayyo Allah na, ciwo Nake Ji sosai, da ciwo Yaya, ciwo nake ji"_</p><p><br /></p><p>Kasancewar Jafar akwai tausayi yasa,ya fara kwallah da kokarin daukarta hannunsa yana Karkarwa. </p><p><br /></p><p>Ahankali take magana wanda shi kansa besan abunda take fada bah. </p><p><br /></p><p>Daukarta yayi, lokacin daya dagota ya mike tsayi ta saki wani kara me karfi, dan ita kadai tasan yanda take ji. </p><p><br /></p><p>_"Ciwo nake ji, ina jin ciwo, ku taimakamin, ku ciremin, wayyo, wayyo AllahNa,Mama ta mama kizo ciwo nakeji"_</p><p> Haka kawai take fada tana kuka har ya karasa da ita wajan motar tashi. </p><p><br /></p><p>Yayin da shima yake goge hawayan nashi idansa yayi jajir, dan ji yake kamar bazai iya driving din bah. </p><p><br /></p><p>A baya ya saka ta, tanata faman surutun nan. </p><p><br /></p><p>Shima shiga yayi hannunsa yana karkarwa ya fara tukin yayin daya juya zuwa Cikin garin Zamfarar. </p><p><br /></p><p>Haka yayi ta faman sauri dan baya san ta mutu. </p><p><br /></p><p>Nan da nan ya shigo cikin gari, kai tsaye babban asibitin kudi dake a garin ya nufa,kafin ya karasa ya kira likitansu dan jin ko yana nan, ya sanar masa gashinan zuwa da patient kuma emergency ne. </p><p><br /></p><p>Kafin su iso har an turo ma'aikata dan daukarta. </p><p><br /></p><p>Yana isowa kuwa suka isa wajan tare da dukota, Jafar sai fadi yake,</p><p> _"Kubi Ahankali tana jin ciwo"_</p><p><br /></p><p>Nan ya bisu aka Nufi emergency da ita, yayin da dr. Ko tsayawa gaisawa basu yiba bayansu, danganin tana cikin neman taikon gaggawan kuwa. </p><p><br /></p><p>Zama yayi a wajan, tare da hada kansa da hannunsa,dan wayar sama cikin mota ya barta sabo da yayi mutukar rudewa. </p><p><br /></p><p>Sun jima a kanta ciki tukun, kafin Dr. Ya fito. </p><p><br /></p><p>Kiran Jafar din yayi, tare dashi suka shiga wajan da take. </p><p><br /></p><p>Tana kwance an saka mata karin ruwa da kuma jini, sun canza mata jaya duk inda yake da ciwo sun saka mata Magani,sun gyarata sosai, sun saka mata ruba a cikin hancinta. </p><p><br /></p><p>Ba karamin tausayi ta bawa Jafar ba ,kujera ya samu ya zauna kusa da ita yana kallanta. </p><p><br /></p><p>Hannunta yake kalla da take bude shi Ahankali, besan sanda ya hada shi da nata ba, wani irin sanyi yaji hannunta ya dauka, damke masa hannun tayi, idanta yana rufe amma kuka kawai takeyi.</p><p><br /></p><p>Dr. Sai binta yake da kallo, shide yasan tunda yake be taba ganin ta cikin family dinsu ba kuma besn taba. </p><p><br /></p><p>Jafar Idansa yayi jajir yayi kuka ya kalli, Dr.cikin Rawar murya tare da fadin, </p><p> _"Dr. Yaya jikin nata, zata warke ko, ina san ta warke ta hadu da iyayanta, ko waye ya mata wannan cin mutuncin wallahi sai na daukar mata fansa, na dauketa tamkar yar uwata da muke ciki daya da ita, nayi alkawarin zan tsaya mata tamkar yayanta"_</p><p> Ya karashe maganar yana kuka. </p><p><br /></p><p>Dr. Din shima tausayi ya bashi, ya dafa shi tare da fadin insha Allah zata samu sauki. </p><p><br /></p><p>Dagowa yayi tare da fadin, </p><p> _"Menene ya faru da itakan hakan?"_</p><p><br /></p><p>Shima zama yayi tare da fadin, </p><p> _"Da farko anyi mata fyade, kuma da alama wanda yayi mata fyade yana cikin maye dan tabbas baya cikin haiyacinsa,dan saida aka mata dinki har biyu, sannan kamar an doketa ko kuma sanadiyar yarda tan da akayine daga waje me nisa yasa, jini ya kwanta a bayan ta saida,akayi aiki aka zuke shi, kuma tasha ruwa sosai, hakan yasa sanyi ya kamata, amma insha Allah komai zai daidaita"_</p><p><br /></p><p>Kuka sosai haka Jafar yakeyi, saida yayi me isar sa tukun ya mike tare da fadin. </p><p><br /></p><p>_"Daga Naira daya zuwa millions dukkan abunda ya dace ayi mata ayi mata, zanje in nemi lawyer da yafi kowanne a garinnan inma ya kama zan nemo wani daga wajen gari, sai nabi mata hakkinta wallahi, inaso a bata private room, dan bana san a takura mata"_</p><p><br /></p><p>yana fadar haka ya fita daga cikin dakin. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(23)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda Jafar yabar asibitin, motar shi ya nufa, be zarce ko inaba sai wajan saida kaya, Boutique ya shiga ya siya mata kaya masu kyau, tare da takalma, sannan ya kuma ban garan kayan provision , da kuma kayan wanka, tukun ya koma ya bawa Dr. </p><p><br /></p><p>zama yayi tare da fada masa, </p><p> _"Dr. ni duk wannan abun da zanyi, zanyi dan Allah, sabo da haka bana san kowa yasan wannan magana, sannan koda bayan na tafi pls a taimaka inta farfado ta fadi inda iyayantah suke a nemosu, ina ganin in tana ganin wani nata kusa da ita Zata fi jin dadi.</p><p><br /></p><p>Babu musu kuwa Dr. Ya bashi amsa da </p><p> _"Insha Allah za'ayi yanda kake bukata, fatanmu Allah ya bata lafiya"_</p><p><br /></p><p>_"Ameen Ameen Nagode sosai, sai munyi waya, sannan dan Allah dukkan abunda take bukata, ayi inyaso sai a sanar min koda kudine"_</p><p><br /></p><p>_"Ba matsala"_</p><p> ya fada tare da masa rakiya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cike da tausayin Lailah haka Jafar ya shiga motarsa dan lokacinsa ya fara kurewa ya nufi Sokoto.</p><p><br /></p><p>_______</p><p>Koda su Mama suka koma gida, sun kasa zaune sun kasa tsaye haka sukaita faman neman Lailah amma shiru har akayi la'asr babu ita. </p><p><br /></p><p>Hakan yasa ko abinci basu iya ci bah, duk inda ya dace suje domin nemanta sunje amma bata nan duk da ba yawo suke bah. </p><p><br /></p><p>Bayan sun dawo gida ne sun zauna shiru babu wanda yake yiwa wani magana. </p><p><br /></p><p>Abbane ya kalli mama tare da mata nuni da hannu kamar yanda suka saba maganar su. </p><p><br /></p><p>Shiru tayi tana kallansa, yana fada mata, </p><p> _"Ko kuma wannan dan gidan sarkin yasan inda take, tunda gashi shima be zoba kwana biyu? "_</p><p><br /></p><p>Kallansa kawai tayi, dan itama abunda tayi tunani kenan,abunda yasa bata yi yinkurin fadin hakan ba sabo da Tana tsoran abunda zai biyo baya, karta yima dan manya sharri azo a kamata, da ace tana da kudi ko akwai wanda ya tsaya musu saita iya tarar aradu, toh amma abunne na zamanin nan sai kana dashi akeyi da kai.</p><p><br /></p><p>_"Baya ma garin gaba daya, ka bar zancan shi kana san kaja mana bala'i"_</p><p> Mama ta bashi amsa, tare da tashi tabar falon. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Tun bayan dasu Abba suka baro gidan su Rauda suka sakata cikin tunanin, ina Lailah ta tafi ita kuwa har ake nemanta haka, dama ita tasan biri yayi kama da mutun, taya za'ai ace, wai Dizhwar kesan Lailah tsakani da Allah har ya gaya mata zai aureta ita kuma ta yarda sabo da bata da hankali, yayan sarakai da basa auran talaka, daga jinin sarauta sai kuma me Naira, dama tasan lalatata zaiyi ya rabu da ita. </p><p><br /></p><p>Ahankali ta janyo wayarta tare da duba number sa da tun ran nan ta dauka, amma kullum in tayi tunanin kira sai taji tsoran karya mata wulakanci, amma tunda yanzu taga dan harkane dole ta neme sa ko itama za'a dama da ita. </p><p><br /></p><p>Ahankali ta shiga duba kudin wayar tatah kartaje tana kiransa kudin su kare ya dauketa kamar harka. </p><p><br /></p><p>Nan kuwa ta duba akwai sauran bal 85:30.</p><p> </p><p>Murmushi tayi tare da kiransa, gabanta sai faduwa yake amma haka ta daure ta na jiran ya daga ta ji abunda abunda zai fada. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shikuwa Dizhwar yau koda yayi wanka kin fita yayi dan baya san takura, haka zalika yaki jinin Husna ta shigo masa daki, gashi gaba daya yanzu tun abunda ya faru tsakaninsa da Lailah ya rasa sukuni duk da ba acikin haiyacinsa yake ba, hakan ya sa bashi da buri domin ya kuma samun hakan, cikin nutsuwa ko yaji dadi a ransa. </p><p><br /></p><p>Ganin wayarsa tana ringing yasa ya dauka yana ganin me kiran, dayaga bakuwar number kin dauka yayi, yaci gaba da kallansa. </p><p><br /></p><p>yana ji harta katse, aka kuma kira amma be daga bah, sa'a na uku tukun ya Daga. </p><p><br /></p><p>Koda ya daga beyi magana bah, haka Zalika itama Rauda tsoro da kuma bugun da zuciyarta take yasa ta kasa magana. </p><p><br /></p><p>tsawan mintina amma babu wanda yace kala, </p><p> Ganin ana ci mata kudi yasa ta fadin, </p><p> _"Assalamu Alaika yakai kyakyawan tauraro acikin taurari, kasaitaccan Jarumi cikin dimbin jarumai, da fatan ka yini cikin koshin lafiya da kuma farin ciki, ina maka fatan alkhairi a koda yaushe ka huta lafiya"_</p><p> Tana fadar haka ta kashe, </p><p><br /></p><p>Rufe idanta tayi tare da Rungume wayar tana sauke ajjiyar zuciya dan bata san ta inda maganar tatah take fitowa bah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shikuwa Dizhwar jin wanga batu, ya shiga da'irar tunani, dan tunda yake babu wanda ta taba kiransa ta gaya masa hakan sai wannan a karo na farko, abun mamakin ma anan shine aina ta samo wannan number tashi, babu wanda yake kiransa da ita daga Jafar sai Lailah. </p><p><br /></p><p>Hakan yasa ya dauki wayar da bin Number badan komai ba dan yasan wacece take masa magana haka. </p><p><br /></p><p>Koda ya kira ta shiga, tana fara ringing bata jin ma ba aka dauka tare dayin sallama. </p><p><br /></p><p>_"Ywwah, dama inasan in tambaya da Allah ko zan iya sanin me magana?"_</p><p><br /></p><p>Murmushi me sauti tayi tare da fadin, </p><p> _"Tabbas mana, mezai hana a baima zuciyar kyakkyawa,ma'abocin Murmushi da kamala abunda take bukata, saida zai dan dauki lokaci kafin kasan hakan, domin gudun karta bata masa rai"_</p><p><br /></p><p>Ajjiyar zuciya yayi tare da fadin, </p><p> _"Look!,ba wani abu nakeso ki gaya min ba face inasan ki gayamin inda kika samu wannan number?"_</p><p><br /></p><p>Shiru Rauda tayi kafin daga bisani tace, </p><p> _"Nasan zakayi mamaki amma, ba abun mamaki bane tunda sauda yawa hakan ta faru musamman ga kawaye ko kuma ince abonkan tarayya, na dauka cikin wayar kawata ne dumin in dinga gaida kai, wato Lailah"_</p><p><br /></p><p>Gaban sane yayi mugun faduwa jin an ambaci sunan Lailah. </p><p><br /></p><p>Jin yayi shiru be bata amsa ba yasa ta fara fadin, </p><p> _"Hello, hello! , ko kayi mamaki ne, dan Allah ka kwantar da hankali wallahi zanyi maka dukkan Abunda Lailah take maka koma fiye da hakan, ka taimaka kar ka ki amincewa dani Dizhwar"_</p><p><br /></p><p>Banza yayi da ita ya kashe wayar, tare da mikewa ya nufi fridge dinsa tare da shan ruwa me sanyi tukun yaji dadi cikin ransa. </p><p><br /></p><p>Yana tsaye a wajan yana kokarin maidawa ya rufe, Husna ta turo kofar falon. </p><p><br /></p><p>Katan Hijab ne ajikinta, fuskata tasha uban makeup sai faman yanga take, ahankali ta cire hijab din jikin nata, wani shegen skinny jeans ne a jikinta yayi mugun kamata sai riga iya jibiyarta, wanda gaba daya ana ganin saman kirjinta ya fito waje sosai, ta zubo da gashinta bayanta da kuma saman kafadunta. </p><p><br /></p><p>Shikuwa tsaye yayi yana kallan ta, dan yama kasa maida Ruwan cikin fridge din ya rufe. </p><p><br /></p><p>Ahankali ta taku, cikin takun jan hankali ta karaso wajansa tare da rungumeshi, numfashin sane ya kusan daukewa dan dama kamar tasan yana bukatar hakan. </p><p><br /></p><p>Be hanata ba kuma be taba tabah, dagowa tayi ta kalli fuskarsa tare da shafa hannunsa har izuwa inda ruwan yake ta amsa tare da sakawa a fridge din ta kulle. </p><p><br /></p><p>Cikin muryar Shagwaba ta furta, </p><p> _"Hubby pls ka kaini Kan kujera in zauna kafata tana mun ciwo"_</p><p><br /></p><p>Kallanta kawai yake dan ta bashi mamaki beyi tunanin haka Husnar take ba, dan ta tafi dashi sosai, ba musu ya dauketa tare da ajje ta kan daya daga cikin sofa wajan, shima ya xauna a gefan ta, ahankali ta matso tare da hawa kan ciyarsa kamar babyn da za'a shayar haka ya dauketa, sai faman masa magana take cikin Shagwaba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yayin da suna cikin wannan yanayi Anty Amarya ta shigo dakin babu sallama, ba karamar girgixa tayi ba ganin Husna kan cinyar Dizhwar gashi shima yana kokarin biye mata harda shinshina huyanta ya rufe ido. </p><p><br /></p><p>Gyaran murya tayi, yayin da Dizhwar dinne ya iya dagowa ya kalle ta ita kuwa, Husna duk da taji shigowar Ta bata fasa abunda take bah. </p><p><br /></p><p>Da er ta iya fadin, </p><p> _"Ina san Magana dakai Dizhwar "_</p><p><br /></p><p>Kallan Husna yayi, ita kuwa bama shi take kallo bah. </p><p><br /></p><p>Shiru yayi mata be bata amsa ba illah kallanta da yake. </p><p><br /></p><p>_"Ke ki dagasa mana inasan magana dashi"_</p><p><br /></p><p>Wani irin kallo Husna tayi mata tare da fadin, </p><p> _"Zance bakiga aikin lada muke ba, sabo da haka zaki iya bari, in ya gama diba sai kuyi, dan nasan maganar taki bata kai abunda yake samu anan bah"_</p><p><br /></p><p>Kamar ta kurma ihu haka taji, dakewa kawai tayi tare da fadin, </p><p> _"Ke kin isa ki hana ni ganinsa kedin banza kedin hofi"_</p><p><br /></p><p>Ahankali ta mike daga kansa bayan tayi kissing lips dinsa, sannan ta karaso gaban Anty Amarya tare da fadin, </p><p> _"Wallahi wallahi Samira kina shige min hanci da kufindine, duk ranar dana fyatoki ina ganin abun bazai mana kyau ba, in banda iskanci da wulakanci kinsan yanzu bashi kadai bane amma sai ina cikin wasa da mijina zakina zuwa kina saka mana ido, in yazo wajan naki ubanme zaiyi miki"_</p><p> Ta fada cike da tsiwa da rashin kunya. </p><p><br /></p><p>Shikuwa Dizhwar da yana zaune an gama dashi baya a cewa ko uffan!. </p><p><br /></p><p>Hannu ta daga xata mareta, matsawa tayi tare da fadin, </p><p> _"Kul! Kada ki sake kiyi wannan gangancin, wallahi kika bari hannunki ya tabani, saikin gammace kida da karatu, ki fitar mana daga daki inba haka ba naci miki mutunci dan Wallahi duk bala'inki nafiki"_</p><p><br /></p><p>Rasa abunda Anty Amarya zatace tayi, illah tsaye da tayi tana juya maganganun dan sun mata ciwo matuka. </p><p><br /></p><p>_"Ni kike gayawa wannan maganar, zaki gane kuranki, zakisan da wanda kikeyi ba, banza karuwa"_</p><p><br /></p><p>Dariya Husna ta kama harda rike ciki, ta juya tana fadin, </p><p> _"zan nuna miki kuwa ni cikakkiyar karuwace"_</p><p><br /></p><p>Tana gama fadar haka, ta daga hanunta sama tare da fadin, </p><p> _"Hubby bacci nake ji ka kaini daki mana"_</p><p> Kamar kuwa rabbot, haka ya dauketa suka shige daki aka bar Anty Amarya tana zara ido. </p><p><br /></p><p>Wani bakin cikine ya kamata wanda bata taba jin irin saba, tabbas tasan ba hakanan Husna tabar Dizhwar ba lallai itama yakamata ta tashi tsaye, kuma sai tayi maganinsu. </p><p><br /></p><p>Juyawa tayi ta fita daga dakin tana masifa ita kadai. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(24)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dakinta Anty Amarya ta nufa, ranta ko kadan babu dadi sabo da abunda Husna tayi mata, ko kadan bata so Asirin Husna ya fara aiki har haka ba jikin Dizhwar taso ace natane ya fara. </p><p><br /></p><p>Yanzu tasan bata da wata manufa daya huce itama ta afka masa nata, amma yanzu ita da bata tare dashi tayaya, zatayi, saide in tayi ma Bokan bayani daya karkato mata da hankalinsa gareta in kuwa ba haka ba bata da wata manufa, ita de ko sau daya ne Dizhwar ya kasance da ita.</p><p><br /></p><p>Dabara ce ta fado mata, babu abunda take bukata yanzu sama data bata ma Husna rai, tasan kuma tabbas abu daya ne zai iya bata mata rai, in har ta ganta tare da Dizhwar, Camera ta dauka tare da fita ta nufi part din Husnar. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_______</p><p>Husna kuwa koda Dizhwar ya kaita dakin, kin yarda tayi daya ci gaba da taba ta, dan kar abun yayi nisa sabo da akwai plan din da suke shiryawa ita da Anty Salima, dan haka haka ta lallabashi har suka fara bacci, tana ganin shima yayi baccin ta mike ta fito falon tare da zira hijab dinta ta fita daga dakin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Part dinta ta koma, tare da yin wanka ta canza kaya, tana zaune bakin gadonta, Hadimanta suna mata gyaran gashi, ita kuma tana chat da wayar ta. </p><p><br /></p><p>Anty Amarya ce ta shiga har cikin bedroom dinta, ganin Anty Amarya yasa duk Suka fita waje. </p><p><br /></p><p>Husna batare data kalle tabah, ta nuna mata wajan zama. </p><p><br /></p><p>Bata xauna ba ta mika mata Camera da take hannunta, kallan Camerar tayi tare da kallan Anty Amarya.</p><p><br /></p><p>Murmushin mugunta tayi mata tare da zama ta dora kafa daya kan daya, tana jiran Husna ta gani, ta ga halin da zata shiga ko Kuma yanda zatayi. </p><p><br /></p><p>Ajje wayar tayi a gefe tare da daukar Camerar, Ahankali ta shiga ganin Pics din da Anty Amarya ta dauka da Dizhwar a dakin garden data kaishi. </p><p><br /></p><p>Da Sauri Husna ta mike tsaye, gaba daya fuskarta da yanayin annurinta ya canza, kallan Anty Amarya tayi, fuskarta cike da damuwa. </p><p><br /></p><p>Kamar zatayi Kuka tace da ita, </p><p> _"Wayyo Allah na, wannan menene haka, garin yaya Dizhwar ya tsaya har hakan ta faru, dama ashe ba suna yake bah, bara na hada kayana nabar masa gidan sah, tunda dama Cin amanata ake, kuma Saina tuna muku asiri"_</p><p> Ta karasa maganar tare da tsayawa gaban Anty Amarya, sannan ta saki fuskar ta tare da cilla mata Camerar ta. </p><p><br /></p><p>_"Haka kike so kiji na fada shine harda wani tasowa da nunamin kenna"_</p><p> Husna ta fada tana kallan tah. </p><p><br /></p><p>_"Toh kin bata lokacin ki a banza, sabo da duk wanda ya fiki wallahi ya riga ya fika, ko An gaya miki Son da nake masa na Karya ne?"_</p><p><br /></p><p> _"Dukkan abunda kika sani game da Dizhwar nikuma Na dame ki, sabo da haka ki koma da baya sabo da wannan yakin ba naki Bane,tun lokacin da mahaifin Dizhwar ya shaida min cewar shine zai auran, toh gaba daya na maida hankalina kansa, dukkan wani Motsi nasa ya kasance tamkar a cikin tafin hannuna yake, kin nuna min kuma Naji babu dadi,amma ki sani nikuma full video garine na abunda kika masa tun daga lokacin da kika Kirashi har lokacin da kika maida shi daki, kin hana shi Yaje wajan kamun bikin mu, banji dadi bah, sannan kin hana shi ya tsaya wajan dinner kinyi kokarin biyan bukatarki dashi, shima, banji dadi bah, hakanyasa ya yima Lailah fyade kuma burinki ya cika, duk da nasan babu abunda kika sani game da haka, Sabo da haka abunda nake so dake,ki bace min daga daki, dan in har kika bari Na fara saka ido a kanki wallahi duniyar ma saita gagareki bama gidan nan bah"_</p><p><br /></p><p>Cike da Al'ajabi Anty Amarya batare da tace komai ba ta fice daga dakin da Camerar ta a hannu. </p><p><br /></p><p>Tsaki Husna tayi tare da hayewa kan gadon ta janyo wayar ta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Ta Yaya Husna tasan Batun Lailah?*</p><p><br /></p><p>Kamar yanda ta fada, tun sanda Baban Dizhwar yayi mata alkwarin auransu, ta saka yara cikin masu aikin gidan dansu dinga kalle mata shige da ficansa da kuma dukkan abunda yakeyi, hakan yasa duk sanda zai fita saita sa an bishi a baya, anan ne ta gane yana zuwa wajan Lailah tun lokacin suna tsowan layinsu, hakan yasa hankalinta ya tashi ganin Dizhwar yana son Lailah, dan haka saita ci gaba da saka Ido akan duk wani motsin su. </p><p><br /></p><p>Ta nanne ta gano kawar Lailah wato Rauda, dan haka har gida tasa aka dauko mata Rauda ta zauna tare da ita, gaba daya ta gaya mata karya da gaskiya a tsakaninsu Wato Lailah Dizhwar din, jin hakan yasa ta bata aiki akan ta dinga bugar cikinta tana gano Mata bayanai akan hakan. </p><p><br /></p><p>Ta nan ne ta gano irin son da Dizhwar din yake mata a ranar da taje gidan nasu, nan take kuwa ta sanar ma da Husna abunda yake gudana, dan hakanne yasa bataji dadi ba kuma ta kara dan marar hallakar da Lailah kota halin kaka. </p><p><br /></p><p>Sabo da haka taci gaba da bincike ba dare ba rana ta hanyar da zatabi Lailah tazo wajan bikinsu dan tasan ta hanyar Dizhwar ne kawai za'a iya hallakar da Lailah. </p><p><br /></p><p>Koda ta sami Dizhwar yana waya akan zai saka a dauko masa Lailah, saita riga shi da hakan, ta tura drivan ta daban, tun kafin na Dizhwar yaje nata ne ya fara zuwa, koda na Dizhwar yaje bata nan dan haka yai ta kiran Dizhwar danya sanar masa da bata fito ba. </p><p> Amma Dizhwar be daga wayar tashi bah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan nan lokacin da Anty Amarya tasa a kaima Dizhwar Coffee din nan, akan idan Husna dan Yarinyar ta aka bawa ta kai masa,saida ta gama gane abunda ke ciki, tunda taga Anty Amarya zata bada akai dan bata yarda da ita ba, bata nuna damuwar taba domin ta riga da tasan dukkan abunda ta zuba aciki shiyasa tayi kokarin kara tayar masa da hankali dan abun yayi aiki. </p><p><br /></p><p>Tunda Lailah tazo wajan Party, Husna tana kallan duk wani motsi nata da kuma Anty Amarya, shiyasa bata hana su ba, tana sane taci gaba dayin abunda dole Dizhwar zai kuma rudewa. </p><p><br /></p><p>Ana cikin hakanne ta janyo shi wajan kunna ta tare da sanar masa da ya fita waje tana zuwa,</p><p>Ba musu kuwa ya fita,sabo da shi kadai yasan yanda yake ji a lkcn, tana ganin haka ta duba wajan Lailah ganin bata nan Farin ciki ya kamata ta tura su Jafar Wajan Anty Amarya danyin Hoto, batare da kowa yasan hakan ba, ita kadai take shirya abundata. </p><p><br /></p><p>Gaba daya dakunan dake wajan hall din tasa aka Kulle su sai guda daya kawai aka bar musu, nanne Inda Dizhwar din ya shiga,tasan bazai iya jurewa yabar wajan ba. </p><p><br /></p><p>Koda gari ya waye, tasan sanda Dizhwar yabar dakin dan haka da kanta ta kuma shiga dakin, nan ta tarda Lailah a kwance, dariyar mugunta tayi mata, tana cikin hakanne taga ashe bata mutu ba tana kokarin farfadowa danta tashi, ganin hakanne yasa ta dauki wani katan katako tayita buga mata a baya har saida taga ta daina motsi tukun ta yarda shi, hakan yasa duk jikin Lailah ya kumbura ga kuma duka da taci har jini ya kume mata. </p><p><br /></p><p>Bayan ta fita ne kuma, Dizhwar yasa aka kai gawar tata aka yarda, hakanne ya tabbatar mata da An yarda Lailah ta gama da babin ta saura kuma Taji da soyayyar Dizhwar da kuma Yin maganin Anty Amarya. </p><p><br /></p><p>Amma kuma bata sani ba, duk ta gama haukanta dan duk Kudin data bawa Rauda a banza domin itama tana shirin shigowa Rayuwar Dizhwar din, dan ko Kadan bata jin tsoran Husna, dan ta gama Sanin ko wacece ita, ko Kuma waninta, bata da buri daya huce Dizhwar din ya amince da ita, itama a dama ta itan. </p><p><br /></p><p>*Wannan kenan*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>________</p><p>Bayan kwana biyu da wannan abun da yake faruwa, babu wanda yasan Halin da Lailah take ciki har yanzu, haka zalika suna bata kulawa sosai a asibitin domin burinsu be huce ta farka bah. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Shima Jafar ko bayan ya koma gida, dama an riga da an kai Asiya part dinta cikin gidan nasu, hakan yasa ta nuna fishinta dan rashin zuwa da huri da beba, nan ya sanar mata da dukkan abunda ya faru, amma baya san ta sanar ma da kowa, itama ta tausayawa Yarinyar Sosai kuma tana mata addu'ar samun sauki. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Yau tunda safe, Dr. Yana zuwa dakin Lailah ya nufa dan duba jikin nata, koda yaje idanta biyu ya sameta. </p><p><br /></p><p>Ahankali ya karasa kusa da ita tare da fadin, </p><p> _"Sannu kinji"_</p><p><br /></p><p>Kallansa kawai take batare data masa magana bah, </p><p><br /></p><p>Haka ya shiga duba ta harya gama ya fita daga dakin. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kallan wajan kawai take dan tasan de asibiti ne, amma tunanin da take anan taya tazo asibiti kode ta haukace, daga ta farka ta ganta acan saita farka ta ganta acan, gashi duk inda ta farka babu wani wanda ta sani, kode a lahira take, shine tambayar da take gashi. Babu me Bata amsa. </p><p><br /></p><p>Dan karfin hali harso take ta mike zaune sabo da ta tabbatarwa kanta, amma taji ta kasa dan har lokacin tana jin ciwo bana wasa bah. </p><p><br /></p><p>Tana kokarin tashinne, wata Nurse ta turo kofar tare da shigowa ganin idan Lailah biyu yasata yin murmushi tare da fadin, </p><p> _"Sannu ya jikin naki"_</p><p> </p><p>Sai lokacin ta danji dadi, ganin mace yar uwarta tana mata magana, </p><p><br /></p><p>Ahankali ta furta </p><p>_"Da sauki"_</p><p><br /></p><p>_"Allah ya kara sauki, ko kina san ki tashi xaune ne"_</p><p><br /></p><p>Gyada mata kai tayi alamun eh. </p><p><br /></p><p>Ajje tray din hanunta tayi tare, da hada mata pillow a bayanta ta taimaka mata ta zauna. </p><p><br /></p><p>Binta kawai take da kallo, </p><p><br /></p><p>_"Ko zakici wani abunne? "_</p><p><br /></p><p>Girgiza mata kai tayi dan bata san cin komai, sabo da har yanzu bata gama yarda da suba tukun. </p><p><br /></p><p>Sannu ta kara mata tare da fita daga Dakin bayan ta canza mata drip din. </p><p><br /></p><p>Cigaba tayi dabin jikinta da kallo, gaba daya ta rame sosai tayi fari kamar ba ita bah, har so take ta ganta a mudubi, sai lokacin Abbanta da Ammi suka fado mata, daurewa tayi dan taba san yin kukan, amma bata san inda xata gansu ba gashi tana san ganinsu ko zata ji dadi. </p><p><br /></p><p>Ahankali ta kuma jingina da pillow, bayanta yana mata ciwon, idanta ta lumshe tana tuna abubuwa da dama. </p><p><br /></p><p>*LAILAH-DIZHWAR*,sunan na ya fado mata. </p><p><br /></p><p>Da sauri ta bude idanta tana kalle Kalle. </p><p><br /></p><p>_"Innalillahi wa'inna illaihir raji'un"_</p><p> Take ta fada cikin zuciyarta dan bata san tuna wani abu me kama da wannan sunan dan tasan ta sanadiyar hakan ta shiga wannan bala'i, toh amma tasan ba ita kadai hakan ya shafa ba, shi ina Dizhwar din yake, ko shima bashi da lafiya, </p><p><br /></p><p>Hawayene ya fara zuba mata, </p><p>Allah yasa shima besha irin wahalar data sha bah, sabo da tana tausaya masa, bata san wani mugun abun ya samu Dizhwar dinta,wajan kofar take kalla ko Allah zaisa wani ya shigo ta tambaye sa inda Aka kai Dizhwar din. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(25)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana nan zaune, tsawan lokaci har zaman ya fara mata rashin dadi. </p><p><br /></p><p>So take wani ya shigo, dan tana so ta tambayi wani dan gidansu ma amma babu wanda ya kara waiwayar inda take ma.</p><p><br /></p><p>Jin an murda kofar yasa da sauri ta kalli kofar, Dr. Din daya shigo da farko ne ya shigo yanzu ma. </p><p><br /></p><p>Shiru tayi gashi tana san masa magana amma ta kasa. </p><p><br /></p><p>_"Sannu, ya kikejin yanayin jinkin naki yanzu?"_</p><p><br /></p><p>Ahankali ta furta da sauki, dan zaman da tayi ta tuna dukkan abunda ya faru da ita tsakaninta da Dizhwar sai lokacin ta tabbata da bata da Laifi laifinsane da yayi mata fyade, to hakan yana nufin baya santa kenan tunda ya nemi ya lalata mata rayuwa ko kuwa hakan soyayyace, abunda ta kasa ganewa kenan. </p><p><br /></p><p>_"Zaki iya tashi ne "_</p><p><br /></p><p>Girgixa kai tayi alamun aa, dan har lokacin tana Jin zafi daga kasan ta, kuma tasan bazata iya tafiya bah. </p><p><br /></p><p>_"Dan Allah aina nake ne? "_</p><p> Ta fada tana kallansa, nan da nan idanta ya ciko da kwallah. </p><p><br /></p><p>_"Kinga, kar kiyi kuka ki kwantar da hankalinki, nan asibiti ne, kuma a garin Zamfara, kinji ki nutsu, dukkan abunda kike bukata ki fada za'a miki"_</p><p> Dr. Ya fada cikin lallashi, dan shima yana tausayin Lailah. </p><p><br /></p><p>_"Menene sunanki?"_</p><p> Ya kuma tambayarta. </p><p><br /></p><p>_"Lailah, Lailah Muktar shine sunana"_</p><p><br /></p><p>_"Ywwah Lailah, sannu kijin, zaki samu sauki ki koma gidanku, yanzu bara azo a kawo miki kaya, sai ki tashi ki lallaba ki daure ki shiga toilet"_</p><p><br /></p><p>Gyada kai tayi, kafin ta kuma dago da kanta,tana kallansa, </p><p> _"Ina Abbana da Mama suke?"_</p><p> Itama ta tambayesa. </p><p><br /></p><p>ya uma tambayarta, </p><p>_"Anan garin suke? "_</p><p><br /></p><p>_"Eh"_</p><p>Ta fada tare da masa kwatancan gidan nasu. </p><p><br /></p><p>Yaji dadi sosai dan shima yana so yaga ta samu nutsuwa kuma hankalinta ya kwanta. </p><p><br /></p><p>_"Toh insha Allah yanzu zasu zo, kinji, ki kwantar da hankalinki"_</p><p><br /></p><p>Naam tayi da maganganunsa, harya fita daga cikin dakin. </p><p><br /></p><p>Be jima da fita bah, saiga matar dazu ta dawo cikin dakin. </p><p><br /></p><p>Batare da Lailah ta kalle tabah, kanta yana kasa taji shigowarta, gaban gadan ta tsaya tare da fadin. </p><p><br /></p><p>_"Sannu, Kozan iya jin sunan patient din tamu"_</p><p><br /></p><p>Dan murmushi Lailah tayi me sauti tana goge idanta tare da fadin, </p><p> _"Sunana Lailah Muktar"_</p><p><br /></p><p>_"Allah sarki Lailah, ni kuma sunana, Sister Zainab Ahmad, ki daukeni kamar kawarki, nice me kula dake, dukkan abunda kike bukata koda wani ya shigo ki ce kina nemana, yanzu zan hada miki ruwan wanka, danki gasa jikinki kiji dadi"_</p><p><br /></p><p>Tunda Zainab ta fara magana babu abunda Lailah ta furta, tana jinta amman kanta yana kasa. </p><p><br /></p><p>_"Toh Nagode"_</p><p> Abunda Lailah ta fada kenan. </p><p><br /></p><p>Murmushi Zainab tayi tare da shiga toilet din, bata jima ba ta fito tare da cire mata drip din, sannan ta taimaka mata ahankali ta sauko daga kan gadon tana dingishi, cikin kayanta ta dauko mata Takalmi ta saka, ahankali take takawa tana rike Zainab din dan tana jin ciwo. </p><p><br /></p><p>Koda ta kaita toilet din, bata ji kunyar tabah, ta yarda da duk abunda zata mata, saida ta gasa ta sosai tukun ta taimaka mata tayi wanka tayi brush da alwala tukun ta fito da ita. </p><p><br /></p><p>Mai ta shafa mata, ta dauko mata kaya mararsa nauyi cikin kayanta, ita kawai kallanta take dan ita bata san daga ina duk wa'en nan abubuwa suke zuwa bah. </p><p><br /></p><p>Duk da ta fada sosai amma tayi kyau kamar ba ita bah, itama kuma taji dadin jikin nata. </p><p><br /></p><p>Zaunar da ita tayi kan kujera, ta hado mata tea tare da chips da Omelet,dadi taji dan cikinta ta dan fara jin yinwa. </p><p><br /></p><p>Da kanta ta riga ci, harta gama, Ita ta amshi kayan ta fita dasu tare da taimaka mata,Sallah tayi,tukun ta koma kan gadan ta maida mata drip din tukun ta fita daga dakin. </p><p><br /></p><p>Ajjiyar zuciya Lailah ta ajje dan ba karamin dadi taji bah. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Har zuwa wannan lokacin Mama ta kasa hakura da Lailah kamar itama tayi cuta dukta rame bata iya cin komai, koda Abba ya takurata amma bata ci, kullum Bata da aiki sai Kuka da addu'ar Allah bayyana mata Lailahr ta, domin duk ta fiye mata tarin mazan da ta haifa. </p><p><br /></p><p>Yauma koda ta tashi da safe, kamar yanda ta saba bata ci abinci bah,tana zaune de akan kujera dan ta rasa abunda yake mata dadi. </p><p><br /></p><p>Koda Abba ya fita ya ganta, zama yayi kusa da ita yana mata magana, amma kin kallansa tayi, dan tasan maganar tasa be huce ta tashi suje wajan Aminu ba ko a samu waya a kira Ahmad,ita kuma taki yarda dan data kirasu gwara kar a nemo Lailah.</p><p><br /></p><p>ganin haka yasa shima ya fara masifa, binsa tayi da kallo yana nunai, </p><p> _"Ke kin fiya taurin kai, ace bazaki yarda a kira su bah, in basu ba muna da wasu ne, da zasu iya taimaka mana, kina batamin rai in har baki yarda ba, wallahi ni zan tafi ni kadai, tunda naga kamar baki damu da Lailah bah"_</p><p> Yana yi da karfinsa yana nuna hannu alamun fada. </p><p><br /></p><p>Abunne ya kona mata rai, ta kama kuka, itama tana bashi amsa, </p><p> _"Ni baxani ba na gaya maka, inda sun damu damu zasu tafi su barmune kamar bamu muka haifesu bah, zance wajan zama ma rasawa mukayi, zakace in basu ba babu me taika mana, yanzu saika gaya min agidan wa muke acikinsu, wallahi nagaya maka bazanje wajan su bah, suje can zasu gani inde duniya ce, ni daman bani na haifesu bah"_</p><p> ta karasa tana kuka tare da fita daga dakin da takalmanta a kafar ta. </p><p><br /></p><p>Shima Yasan basu kyautaba, kuma basu musu adalciba, abunda yaketa gudu gashi yau ta fara dana sani da haihuwarsu, duk da bayinta bane, tana hakuri bata taba nuna damuwarta game da abunda suke mata, amma yasan tabbas akan Lailah babu abunda bazata iya bah.</p><p><br /></p><p>Fita tayi daga gidan tana goge hawaye, tana budewa taga mutun tsaye da alama bugawa yake, tsaye sukayi shida ita suna kallan juna, yana jiran yaji tayi magana amma shiru, amma ya lura da yanayin fuskarta da alama Kuka tayi. </p><p><br /></p><p>_"Sannu baiwar Allah, dan Allah dama tambaya nake ko nanne gidan su Lailah Muktar"_</p><p><br /></p><p>Tunda ya fara maganar take bin bakinsa da kallo dan gane abunda zai fada, </p><p><br /></p><p> Shikuma tsoro yaji yasa yake fadar maganar daki daki dan yaga kamar bata da hankali. </p><p><br /></p><p>Ganin bakinsa ya fadi, Lailah da kuma Muktar yasa ta nuna masa. </p><p><br /></p><p>_"Ita bata jin abunda yake fada, mijinta ma baya ji, amma taji kamar yana neman wani abu"_</p><p><br /></p><p>Kallanta yayi, kamar yace mata sai anjima sai kuma ya biye mata kasancewar ya gane abunda take nufi ya nuna mata, suna da y'a budurwa. </p><p><br /></p><p>Da sauri ta gyda masa kai, alamun eh, ta girma kyakkyawa, amma babu ita. </p><p><br /></p><p>Shikuma ya zata ta mutu, saiya bata hakuri zai tafi, da sauri ta rugasa tare da nuna masa, ya rubuta mata a takarda wa yake nema. </p><p><br /></p><p>Saida ya kalleta sosai, ya tabbatar tana da lafiya, sannan ya dauko biro a gaban aljihunsa tare da memo karami, ya rubuta mata,</p><p> _"Ina neman iyayan Lailah Muktar"_</p><p><br /></p><p>Mika mata yayi, kasan cewar ta dan iya karatu,ta gane abunda ya rubuta, da sauri ta gyada masa kai tana nuna masa sune iyayanta, tana ina, ya tsaya, ta maza ta ruga ciki tare da janyo Mijinta tana nuna masa abunda ya rubuta a jiki, nan kuwa ya nunawa mutumin alamun sune iyayanta. </p><p><br /></p><p>Shima sun Bashi tausayi da dariya, ganin yanda suke kaunar yar tasu, zaisu yaga haduwarsu da ita, shin tabbas shine iyayan nata, maybe itama kuramance, ikon Allah, shi kadai yake magana cikin zuciyarsa. </p><p><br /></p><p>Nan kuwa ya nuna yana son kaisu wajan ta babu abunda Mama ta koma yi cikin gidan, Abbane ya kulle gidan dan ita tuni ta shige cikin mota. </p><p><br /></p><p>Koda ya gama abunda zaiyi shima shiga yayi, batare da sunsan inda aka nufa dasu ba sukayi shiru, abaya suna jiran ganin ikon Allah. </p><p><br /></p><p>Yayin da Mama babu abunda take sai godema Allah. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Yaseer kuwa ansha biki da Saudat duk da kuwa baya so, bayan bikinsu da Kwana biyu ya koma Makaranta tare da matarsa duk da ba hakan yaso Bah, </p><p><br /></p><p>Ai lokacin hankalin Hajiya Mariya ya kwanta dan dama ita bata san tarairayar su da Lailah shiyasa tayi yanda zatayi ta takurashi ya auri Saudat dan yabar Lailah kuma anyi hankalinta ya kwanta yanzu kuma saisu rabu da su. </p><p><br /></p><p>__________</p><p>Daidai baban asibiti Motar tayi parking, bitowa sukayi nan ya jagorancesu har zuwa dakin likitan daya turasa ya dauko su. </p><p><br /></p><p>Koda yasa su tsaya daga waje yana zuwa. </p><p><br /></p><p>Zama sukayi suna kallan wajan, mama kuka ta fara tana nuna hannu , </p><p> _"Ni nasan Lailahta bazata yi abunda ba shikenan bah, nasan saide in hadari tayi shiyasa bata dawo Gida bah,Allah yasa abun beyi muni bah"_</p><p> Shine bunda Mama take ta faman fadi. </p><p><br /></p><p>Koda ya shiga wajan likitan, sanar masa yayi an samo su, amma yasha wahala dan gaba dayansu kurame ne.</p><p><br /></p><p>Mamakine ya Kama Dr. Din jin an fada masa iyayan Lailah kuramene. </p><p><br /></p><p>Koda ya fito ya gansu, hannu ya mikama Abba suka gaisa, sannan ya jasu dan suje wajan Lailah. </p><p><br /></p><p>Yana tafe suna binshi a baya. </p><p><br /></p><p>Ita kuwa tana kwance, dan bama tajin bacci kallan tv, take, amma inka kalle ta a nitse zakaga ba tv take kallo ba, ta tafi duniyar tunani, tunanin ta kuwa be huce, tashin hankalin data fada bah. </p><p><br /></p><p>_"Yanzu ina su, Mama sukazo Mezata fada musu ya sameta,dan bata san susan anyi mata fyade, gashi taji ance wasu in aka musu fyade har ciki suke Samu, yanzu ita inta samu ciki shikenan haka za'a dinga cewa danta shege, gaskiya hakan ba soyayya bace da Dizhwar yayi mata, yaudarar ta yayi ya cuceta kuma, gashi yayi guduwarsa ya barta kuma babu yanda za'ai budurcinta ya dawo"_</p><p> Abunda zuciyarta take ta faman fada mata kenan. </p><p><br /></p><p>Hawaye ke zuba, yayin da hankalinta yayi mugun tashi. </p><p><br /></p><p>Jin an turo kofa yasa tayi saurin juyowa tare dasa hannunta daya ta goge saman kumatunta. </p><p><br /></p><p>Ganin Dr. Ya shigo ga Abba da kuma Mama suna biye da shi yasa ta saurin kokarin tashi tana dariya hade da kuka. </p><p><br /></p><p>Da sauri Mama ta rungumetah itama tana kuka, hannunta daya tasa itama ta rungume Maman tana kuka yayin data kalli Abban nata shima yana tsaye kasa jurewa yayi shima saida ya matsa gareta tare da rungumetan yaji dadi. </p><p><br /></p><p>Dr. Da wannan mutumi dake tsaye tausayi suka basu tare da burgesu, yanda suke san yar tasu itama take sansu, da alama ita kadai suka haifa, abunda duk sukayi tunani kenan,wacan din juyawa yayi ya fita, dan dama abunda yake san gani kenan. </p><p><br /></p><p>Kofar Dr. Ya kulle tare da shigowa ciki yana kallansu. </p><p><br /></p><p>Saida suka gaji dan kansu suka saki juna. </p><p><br /></p><p>Mamace ta zauna gefan gadan tana shafa fuskar ta, tana kallan yanda lokacin kadan haka ta koma kamar wanda tayi jinyar shekara guda. </p><p><br /></p><p>Itama rike hannun nata tayi tana jin dadin ganinsu, idanta daya cika da ruwa ta daga tare da kallan Dr. </p><p><br /></p><p>_"Dr. Nagode da abunda kuka yimin Allah ya saka muku da alkhairi ya kuma biyaku da gidan aljanna, amma dan Allah ina rokanka da karka gayawa iyayena batun fyaden nan, nice komai tasu, na tabbata bazu taba jin dadin hakan bah, bana san na saka Su bakin ciki duk da nasan a tsautsayi abun ya faru, zan sanar musu da kaina dan Allah kayimin wannan taimakon"_</p><p> Batare da ya mata magana ba ya nuna ya gamsu da maganar ta, yaji tausayinta matuka. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(26)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Fita yayi daga dakin batare daya musu magana bah. </p><p><br /></p><p>Kujera Abba ya janyo tare da zama, itama Lailah kokarin tashi zaune take.</p><p><br /></p><p>Da sauri Mama ta mike tare da saka mata pillow a bayan ta, </p><p> Sanna ta taimaka mata ta tashin tare da zama, ajjiyar zuciya ta ajje tare da bin Maman tata da kallo. </p><p><br /></p><p>Komawa tayi ta zauna duk ita suke kallo. </p><p><br /></p><p>Mamace ta nuna mata da hannu, kamar yanda suka saba. </p><p><br /></p><p>_"Lailah kin tafi, kin samu a damuwa, munyi kuka, munyi yawa amma bamu ganki bah"_</p><p><br /></p><p>Murmushin takaici tayi da kuma dana sanin abunda ta aikata din. </p><p><br /></p><p>Hannunta biyu tasa ta kama kunan ta tare da langwabe fuskarta alamun bada hakuri kenan. </p><p><br /></p><p>Ba komai suka nuna mata, sunji dadi sosai da suka ganta. </p><p><br /></p><p>Ita kanta tasan babu abunda suke bukata kamar suji abunda ya faru da ita din. </p><p><br /></p><p>Labarin karya ta shiga hadawa a zuci kafin ta fada musu.</p><p><br /></p><p>Nan tahau musu bayani kamar yanda ta saba, </p><p><br /></p><p>_"Nayi miki karya, zanje wajan Rauda"_</p><p><br /></p><p>Ta fada tana kallan Mama dan, tasan dole sunje gidan su Rauda. </p><p><br /></p><p>_"Banan naje bah, wajan aikinmu nake san inje, najima banje bah, amma nasan inna gaya miki, zaki ki yarda tunda Dizhwar ya hanani zuwa, saina shiga mota ashe mai motar bashi da gaskiya, yana so ya saceni"_</p><p><br /></p><p>Duk su biyun suka tsorata tare da tsine masa cikin zuciya dan sunsan Lailah bazata musu karya ba shiysaa ta samu damar hada lbr. </p><p><br /></p><p>_"Muna tafiya, saiya watsomin wani abu, tun daga nan ban san me yake faruwa bah, sai na ganni anan"_</p><p><br /></p><p>Mamakine duk ya kama su, dan sun tsora, bada ban Allah ya taimaka ba dasun rasa ta. </p><p><br /></p><p>Abbane ya tambayeta inda shi mutumin yake. </p><p><br /></p><p>_"Can hanyar Sokoto ya yardani, shine wannan likitan ya tsinceni"_</p><p><br /></p><p>Mamaki da kuma dadi sukaji lokaci daya na abunda Dr. Yayi musu, gashi ya bata kulawa ta musamman. </p><p><br /></p><p>Abba ma yaji dadi sosai, Mama shafata tayi tana tambayar babu abunda ya sameta itama. </p><p><br /></p><p>_"Aa, kasancewar yardani da akayi, bayana da kuma kafata suna ciwo dan bana iya tafiya sai dingishi, sai kuma aiki da akayi a bayana, aka zuke jinin daya kwanta, shikenan"_ </p><p> Duk Lailah ta yimusu karya dan bata san dukkan abunda akayi mata ba, tayi hakanne danta kwaci kanta kuma sun yarda da hakan. </p><p><br /></p><p>Sai lokacin hankalin ta ya kwanta Sosai dan ba karamin dadi sukaji bah, ganin da sauki jikin nata har take iya tafiya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_________</p><p>Anty Amarya kuwa tun da farar safiya aka shirya ta fita dan zuwa wajan bukanta, cancikin wani kauye a Sokoto, dan inta tashi wannan tafiya tata, ita kadai take zuwa batare da dan rakiya bah, dan haka da safe ta tafi dan dama shine lokacin zuwanta. </p><p><br /></p><p>Dan haka lokacin data isa, babu kowa a wajan nasa, kasancewar duk sanda zata zo yasan da zuwan nata yayi mata iso zuwa cikin wajan nasa. </p><p><br /></p><p>Zama tayi tamai gaisuwa kamar yanda ta saba tare da fadin, </p><p> _"Boko abubuwa sunki yin gaba, kullum jiya iyau na rasa gane kan wannan abun"_</p><p><br /></p><p>Dakatar da ita yayi tare da fadin, </p><p> _"Ba saida na gaya miki Komai kina binsa ahankali bah, amma ke Kina sauri da rawar jiki,wannan yarinya da aka Kawo muku, ba karamar hatsabibiya bace ita, kanta dole saikin tashi tsaye"_</p><p><br /></p><p>Anty Amarya ta girgixa kai dan itama tasan akwai babban yaki agabanta. </p><p><br /></p><p>_"Ina jinka boka, na yarda dakai, kuma nasan bazaka gaji da bukata ta bah"_</p><p><br /></p><p>_"Wannan haka yake,yanzu kina so a raba su, ya kasance yana karkashinki, sai abunda kika fada shine zaiyi, toh tabbas in har kikayi abunda na saka ki za'a samu nasara, kuma dole da kanki Zakiyi wannan abu, ba wani zaki saka bah"_</p><p><br /></p><p>Gyada kanta tayi, tare da mika gaba daya hankalinta gareshi. </p><p><br /></p><p>_"Kamar yanda kika sani har yanzu mace daya ce duk duniya ta taba kusantar shi wannan yaro, kuma tana nan acikin garin Zamfara wato Lailah, sabo da haka, zaki samu fitsarin wannan yarinya na farar safiya kafin taci komai, zaki hada shi da naki, saiki hada masa lemo ko kuma wasu dabarunku na mata, da zakiyi, domin yasha wananwannan abu, mundin kikayi haka kin samu soyayyar sata har abada, sai abunda kikace yayi,amma fa da sharadi, karki sake ki bari Ya sadu da Matar tasa, dan inya sadu da ita gaba daya aikinki ya lalace. "_</p><p><br /></p><p>Dadi taji sosai, sannan kuma ta kuma gyara zama. </p><p><br /></p><p>_"Abu na biyu kuma, shine nasan ki wulakanta Ita matar yaran, wannan yarinya gaskiya na gaya miki, tana tare da manyan aljannu, kuma yan gidansu tsafi sukeyi suma, dan haka dole akwai hadari dangane da aikinta, kuma Mundin aka sami sabani a wajan aikinta dayan biyune, koki haukace ko kuma ki rasa ranki"_</p><p><br /></p><p>Gaban Anty Amarya ne ya fadi, dan har gumi ya fara zubo mata. </p><p><br /></p><p>_"Zakiyi in fada miki kokuma abarshi tukun"_</p><p><br /></p><p>Shiru tayi tana tunani kafin tace, </p><p>_"Ina ganin inde na samu Dizhwar din, ai dole abun zai dinga mata ciwo, kuma dama ni abunda nake bukata kenan,ina ganin abarshi gaskiya"_</p><p><br /></p><p>Boka ne ya fashe da dariya tare da fadin, </p><p> _"Matsiyaciya baxata iyabah😂"_</p><p><br /></p><p>Saikuma ta kuma da cewa, </p><p> _"Boka har tanzu fa, naga kamar tauraruwar Fulani tana haskawa a idan Sarki, kumani harga Allah na tsani matar nan, babu abunda Za'a iya mata tabar duniyar kokuma a saka ta wahala?"_</p><p><br /></p><p>Shiru yayi kafin yayi zabure zaburansa tukun yace, </p><p> _"Za'a iya mana, zaki samu Hawainiya"_</p><p><br /></p><p>_"Hawainiya?"_</p><p> Ta maimata tana kallansa.</p><p><br /></p><p>_"kwarai kuwa, hawainiya tare da jelar bunsuru, za'a binnesu da ranta a kofar dakin Memartaba,zatayita rashin lafiya da kuma Kuma wari, za'a rasa abunda yake damunta, in har wannan hawainiya ta mutu, toh itama mutuwa zatayi, sabo da haka, kema kinsan ladan aikina, bana amsar kudi"_</p><p><br /></p><p>Murmushi tayi tare da fadin, </p><p> _"Ai babu matsala nide burina bukatata ta biya"_</p><p><br /></p><p>Nan kuwa tahau cire kayan jikinta,dan biyama boka bukatarsa, yayin da nikuma Na barota ina fadin, </p><p> (Allah ya shirya).</p><p><br /></p><p>_______</p><p>Husna tunda aka kawo ta bata taba zuwa ta gaida Memartaba ba, ko Kuma wani da yake cikin gidan nan bah, har ita kanta surukar tatah. </p><p><br /></p><p>Abunda yake bama Fulani,mamaki kenan,shi kansa Dizhwar din tunda akayi biki ko Inda take ya daina zuwa,dan haka ta shiga nemansa a waya amma shiru yaki dagawa. </p><p><br /></p><p>Abun yana bata mata rai, ga Asiya kanwarsa da shi kansa Jafar din da suke Nesa, kullum ta Allah sai sun kirata safe da dare dan jin lafiyar tah, ita kuwa bazata je wajan yarinya ba dan mata magana, inda yar gidan masu mutunci ce ai tasan abunda ya kamata tunda tana da iyayye, shikuma da yake sakarai, in ita bata zo ba ai shi ta haifeshi amma shima shiru, kullum Yana cikin daki kamar mace. </p><p><br /></p><p>Abun yana kona masa rai. </p><p><br /></p><p>Jafar ta kira danya kirasa, ya sanar masa da tana nemansa dan ita inta kira baya dagawa. </p><p><br /></p><p>Nan ya bata hakuri kuma ya shiga neman wayar Dizhwar din. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>________</p><p>Yana dakin Husna dan yau ita ta kira sa, kuma yanzu ya rasa abunda yasa baya mata musu dukkan abunda take bukata shi yakeyi. </p><p><br /></p><p>Yana kwance kan gadonta, tana gefe tana masa hira, wayarsa ta fara Ringing, da sauri ta dauka ganin Jafar ke kira yasa ta kashe. </p><p><br /></p><p>Kallanta yayi tare da fadin, </p><p> _"meyasa kika kashe? "_</p><p><br /></p><p>Maimakon ta bashi amsa, saita matso jikinsa tare da fadin, </p><p> _"Hubby bana san a dinga kiranka in muna tare, sabo da takura mana akeyi wallahi"_</p><p> Ta karasa maganar da shigar shagwaba.</p><p><br /></p><p>Be mata musu bah,illah komawa da yayi ya kwanta kan ciyar tah. </p><p><br /></p><p>Murmushi tayi tare da ajje masa wayar a kusa dashi. </p><p><br /></p><p>Wani Kiranne ya kuma Shigowa,harta katse daga shi har ita babu wanda ya daga, Murmushi kawai take dan yaji maganar tatah. </p><p><br /></p><p>Kiranne ya kuma Shigowa a karo na uku. </p><p><br /></p><p>Dauka yayi tare da mikewa zaune, dan ganin Jafar.</p><p><br /></p><p>Yana dagawa batare da yace masa komai ba, Jafar din yahau fada. </p><p><br /></p><p>_"Gaskiyane, ka kyauta, ashe ba Mami ba kadai gaba daya ka daina daga wayar mutane toh da haka mana ba gwara ka Kashe wayar ba gaba daya kowama Ya huta"_</p><p><br /></p><p>Shiru Dizhwar yayi dan yasan be kyauta bah.</p><p><br /></p><p>_"Haba Dizhwar kai haka ake, Aure haukane, shikenan kuma daga ka samu mace saika manta da kowa har mahaifiyarka, kuna gida daya amma kaje ka gaida ta kake ganin abun ya gagara, in ita baza taba kai kaje mana, kuma harta kiraka amma kaki dauka, gaskiya wannan ba wayewa bace"_</p><p><br /></p><p>Shiru yayi dan Jafar ya bata masa rai,ya wani Kirasa yana masa fada kamar wani Babansa ko Yayansa. </p><p><br /></p><p>Tsaki yayi tare da kashe wayar gaba daya ya cilla ta kan gado, mikewa yayi ganin Husna bata nan yasa ya fara dube dube, can ya hangota,jikin window tsaye. </p><p><br /></p><p>Dadi yaji cikin ransa, ya karasa gareta tare da rungumetah ta baya, ya zura kansa tsakanin huyanta da kafadunta. </p><p><br /></p><p>_"Fishi kike dani? "_</p><p><br /></p><p>Banza tayi dashi, </p><p> _"Ki gayamin mana pls"_</p><p><br /></p><p>Bata mai magana ba still, nan fa yaji ba dadi cikin ransa. </p><p><br /></p><p>Hannunsa yasa ya zagaye kugunta, tare da fada mata cikin kunne, </p><p> _"Dan Allah ayimin afuwa baxan kara bah, nayi alkawarin in har muna tare duk wanda ya kira bazan daga bah"_</p><p> </p><p>Da sauri ta juyo tana murmushi tare da fadin, </p><p> _"Dagaske"_</p><p>Tana Murmushi. </p><p><br /></p><p>Kai ya gyada mata, yana maida mata Murmushin shima. </p><p><br /></p><p>Rungumeshi tayi, tare da jansa zuwa gadanta. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Hajiya Babba tun bayan tafiyar Zakiyya kullum ita kadai babu kowa a wajan ta hakan baya mata dadi, shiyasa ta shiga rokan kanwarta danta kawa yarta ta rike a wajanta ko zata ji dadi ta saba da Zakiyya, nan kuwa tasa a kawo mata yarinyar kanwar Tatah daga Kaduna. </p><p><br /></p><p>Tana zaune cikin falonta, abu yayi mata yawa, gashi Anty Amarya munafuka tun bayan biki ta dauke kafa, ga shi dama basa wani shiri da Fulani, sabo da haka abu ya hade mata, </p><p> Ita kuma yanzu burinta a duniya be huce taga ta raba kan Dizhwar da Mahaifinsa ba, dan tabbas ya amshi Sarautar nan tasan dole Fulani tayi farin ciki, sabo da haka dole ta tashi tsaye dan ganin be samu sarautar bah, tama fi san yabar gidan gaba daya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(27)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kwanan Lailah biyar a asibiti tana samun kulawa sosai kuma kamar yanda ta bukata har yanzu Babu wanda yasan da batun mata fyade. </p><p><br /></p><p>Kullum da safe da yamma Sister Zainab zata zo ta dubata ta saka ta cikin abinci sannan ta gasata. </p><p><br /></p><p>Har saida ta saba dasu Abba dan Suna burgeta yanda suke nunawa Lailah so da kuma kulawa.</p><p><br /></p><p>Yau Jafar ya sanar da Dr. Zai shigo garin dan suzo su duba ta, haka kuma zai mata magana dan ta sanar masa wanda yayi mata fyade domin ya daukar mata fansa. </p><p><br /></p><p>Haka kuwa akayi, shida Amaryarsa da kuma Hajiya Bilki suka shirya suka taho domin duk ya sanar musu da abunda Ya faru da kuma zuwan da zaiyi na duba tah. </p><p><br /></p><p>2:00pm,suka sauka a Sokoto, Mami ce ta sanya domin aje a dauko su, dan sun sanar mata da zuwan nasu.</p><p><br /></p><p>Kasancewar motocin gidane, da huri suka iso cikin Xamfara kai tsaye gidan sarauta aka nufa dasu, </p><p><br /></p><p>Mami tayi shirin tarar autar ta, ana saukesu kuwa da guda ta shige cikin wajan nata, suna ta mata dariya masu yima Fulani hidima, Tana shiga kuwa ta ganta ta fada kanta tana murna. </p><p><br /></p><p>Binta tayi da kallo tana dariya ganin yanda ta kara kyau da kuma kiba kamar ba ita bah. </p><p><br /></p><p>Suna nan zaune su Jafar da Hajiya Bilki suka shigo. </p><p><br /></p><p>Zama suma sukayi aka hau gaisawa, kafin a cika musu gabansu da kayan ciye ciye da shaye shaye. </p><p><br /></p><p>Kafin daga nan, Jafar yace, </p><p> _"Mami Yaya Dizhwar din kuwa yana zuwa ko kuma har yanzu be canza bah? "_</p><p><br /></p><p>Shiru tayi dan bata san amanta maganar sah, </p><p><br /></p><p> _"ai bana tunanin zai canza halinsa, wannan hankali gareshi, ya maida mata kamar Allan sa, bazan mai magana bah, yaje wallahi dan bezo ya gaida ni ba baxai rageni da komai bah, kude Allah yayi muku Albarka"_</p><p><br /></p><p>Ko kadan basuji dadin Abunda yakeyi bah, amma shi Jafar gani yake kamar ba laifinsa bane. </p><p><br /></p><p>_"Dan Allah Mami kiyi hakuri, ina ganin ba laifinsa bane, amma zan mai magana tunda gani Nazo ai"_</p><p><br /></p><p>_"Karka masa, karka sake ka bata bakinka, har sai kamai magana bayan shine gaba dakai, zance shima yasan abunda ya kamata da wanda be kamata bah, amma ai yana zuwa ya gaida Baban sa, kodan bani da daraja tun tuni cikin idanunsa"_</p><p><br /></p><p>_"Haba kekuwa fishi ba naki bane, ai irin wannan magana zaki zauna kuyi dashi ta fahimta, amma baxaki dinga fadar irin haka bah abunda ya faru da, aiya riga da ya huce yanzu, shima yasan ke wacece a wajan Sa"_</p><p> Hajiya Bilki ta fada tana kallan ta dan itama san abun be mata dadi bah. </p><p><br /></p><p>_"Haba Yaya, tun yaushe ake abu daya, inda ya daukeni matsayin uwa baxai dinga min irin wannan ba ai, sai kace wata wanda ta tsare masa wani abu dama can baya kaunata, ni ko mutuwa nayi bana san yazo wajena ma"_</p><p> Ta karashe maganar tana kuka. </p><p><br /></p><p>_"Dan Allah Mami kiyi hakuri, kiyi shiru dan Allah"_</p><p> Asiya ta fada itama kamar zatayi kukan. </p><p><br /></p><p>Hajiya Bilki itama abun yana bata tsoro kuma tasan rabashi akayi da ita, in ba haka ba mutun da uwarsa ace baya kaunarta, </p><p> _"Menene na kuka, ki share hawayanki, addu'a Za'a dage a dunga masa, yana cikin wani hali wallahi, kibar masa kuka kina fadar irin wannan maganar, in rai ya bace ai hankali baya goshe bah"_</p><p><br /></p><p>Itade Mami bata kara magana bah, hawayanta kawai take gogewa. </p><p><br /></p><p>Jafar daya kasa magana tun dazu, tashi yayi ya fita daga dakin, koda ya fito wajan me martaba ya nufa, cike da mamaki kuwa, yaga Dizhwar din zaune a wajan sa. </p><p><br /></p><p>Da Sallama ya shiga Falon nashi ya zauna suna gaisawa, sannan suka gaisa da Dizhwar din, daya amsa masa cikin fara'a kamar bashi ya kashe masa waya ran nan bah. </p><p><br /></p><p>Sun jima suna hira kafin su fito tare suna taba hira, kallansa Jafar yayi tare da fadin, </p><p><br /></p><p>_"Angon Husna, kaga yanda ka yi kiba kuwa, gasiya wannan Amaryar tana kula dakai, muje in gaidata mana"_</p><p><br /></p><p>Dizhwar dariya kawai yake, dan yanzu yanda yake jin Husna cikin ransa, duk duniya babu ya ita. </p><p><br /></p><p>Tare suka shiga har falonsu, suka zauna. </p><p><br /></p><p>Dizhwar dinne ya shiga daki dan kiranta su gaisa da Jafar. </p><p><br /></p><p>Sun jima kafin su fito, tukun ta fito sanye da atamfa doguwar riga kanta babu dankwali, da waya a hannunta, tazo ta zauna, shima yana biye a bayansa</p><p><br /></p><p>Kamar ba ita ba suka gaisa faran faran, har take tambayarsa Asiya. </p><p><br /></p><p>Shikansa yayi mamaki, </p><p><br /></p><p>Sun danyi barkwanci kafin ya mike yace da Dizhwar zaidan shiga gari, Adawo lafiya ce kawai ta hada ss dan ba shi da alamun masa rakiyar. </p><p><br /></p><p>Mamaki sosai Dizhwar yaba Jafar dan yanda suke be taba tunanin irin wannan yanayin ba a tsakaninsu. </p><p><br /></p><p>Koda ya fita be koma can ba, dan baya san kara ganin Kukan Mami. </p><p><br /></p><p>Koda ya shiga mota tunaninsa, sam be dace ace Husna bace matar Dizhwar dan sam Yarinyar bata da hankali, gashi kana ganinta idanta ya bude da yawa, babu abunda bazata iya bah Wannan,haka ya nufi asibitin yana tunanin mafita.</p><p><br /></p><p>Parking yayi inda aka tanada domin yin hakan, shiga yayi kai tsaye Office din Dr. Ya nufa. </p><p><br /></p><p>Kwankwasawa yayi kafin ya shiga, da sallama ya bude ya shiga, yana hangosa ya mike yana murmushi suka hada hannu suka gaisa kafin ya zauna suna fuskantar juna. </p><p><br /></p><p>_"Kenan harkun karaso, yaya gida ya Amarya"_</p><p> Dr. Ya fada yana Murmushi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_"Lafiya qlau wallahi, ai tare muka zo garin tazo gaida su Memartabah, yaya me jiki kuma ya faman wahala da ita, kuna ta fama Allah ya biyaku"_</p><p>Jafar din ya fada. </p><p><br /></p><p>_"Jiki Alhmdullh yayi kyau dan yanzu ta warware ina tunanin zata iya tafiya gobema in Allah ya kaimu"_</p><p><br /></p><p>Dadi jafar yaji tare da fadin, </p><p> _"Masha Allah ai haka ake so, Allah ya kara sauki"_</p><p><br /></p><p>_"Ameen"_</p><p>Dr. Ya fada tare da mikewa yace da Jafar, </p><p>_"Muje ka ganta, iyayanta ma suna nan ai"_</p><p><br /></p><p>Ba musu kuwa yabi bayan Dr. Suka nufi dakin nasu. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sallama suka shiga tare da kullo Kofar, </p><p><br /></p><p>Gaisawa sukayi da iyayan nata dan Dr. Yayi masa bayanin su tun acikin waya, kasan Cewar basu san ko Waye ba yasa basu masa godiya bah. </p><p><br /></p><p>Ahankali ta fito daga Toilet, sanye take da doguwar riga baka, tayi kyau harta danyi kiba, ta daura dankwali amma daga baya gashinta ya zubo har gadan bayan ta. </p><p><br /></p><p>Ganin Dr. Yasa ta karaso tare da gaida su. </p><p><br /></p><p>Binta Jafar yayi da kallo dan ta bashi mamaki Ganin yanda ta koma kamar ba ita bah. </p><p><br /></p><p>Dr. Ne ya kalle ta tare da fadin, </p><p> _"Ga wanda ya tsunto mana ke ya bamu umarnin muyi muki dukkan abunda kike so, a takaicede komai da ika samu daga wajan sane"_</p><p><br /></p><p>Dadi Lailah taji ta rasa da wani bakin Zata masa godiya domin ya gama Mata komai,</p><p><br /></p><p>_"Nagode, Nagode Allah ya saka da alkhairi ya kara budi, Allah ya kareka daga dukkan wani mugun sharri ya saka maka da gidan aljanna Nagode "_</p><p> Ta karasa maganar tana kuka. </p><p><br /></p><p>Da sauri ya furta, </p><p> _"Menene na kuka, kefa kika Kirani da yaya, ko an fasa yayan kuma kike kuka, yayan kine fa yayi miki abun alkhairi Nagode da addu'ar amma bana san kuka, ki gogeshi ko kuma ince bana san addu'ar take"_</p><p><br /></p><p>Murmushi take tana goge hawayan nata. </p><p><br /></p><p>Batare da tayi magana ba ta juyo tana nunawa su Mama shi da hannun, shine wanda duk ya biya kudi ayi mata magani kuma ya kawota asibitin. </p><p><br /></p><p>Nan suma Suka hau masa godiya, duk da ba ganewa yake ba amma Lailah tana gaya masa abunda suke fada. </p><p><br /></p><p>Sunji dadi matuka kuma sunyi godiya marar iyaka da kuma addu'a. </p><p><br /></p><p>Bayan haka Jafar yace da ita, </p><p><br /></p><p>_"Ni Sunana Jafar duk da nasan Dr. Ya fada miki"_</p><p><br /></p><p>_"aa ban fada mata ba, dama jira nayi kazo da kanka"_</p><p> Dr. Ya fada yana dariya. </p><p><br /></p><p>Shima Dariyar yayi tare da fadin, </p><p>_" toh Lailah, ni ya gaya min komai tare dake, Sunana Jafar, amma ni ba'a nan nake da zama Ba, ina zaune a kano da iyayena da kuma matata, ina zuwa nan sanadiyar yayan mahaifiyata, kuma kijin matata, wato Memartabah Sarkin Zamfara . </p><p><br /></p><p>Da sauri ta dago tana kallansa, a tsorace tare da fadin, </p><p><br /></p><p>_"Kaine Jafar"_</p><p><br /></p><p>Kallan juna sukayi Shida dr. Kafin yace, </p><p> _"Dama kin sanni?"_</p><p><br /></p><p>Kai kawai ta iya girgiza, kafin kuma ta fashe da kuka .</p><p><br /></p><p>Duk. Kallan juna suka fara, haka suma su Mama. </p><p><br /></p><p>_"Lailah kukan me kikeyi?"_</p><p>Dr. Ya fada yana kallanta cikin damuwa. </p><p><br /></p><p>_"Kaine Jafar dan Uwan Dizhwar?"_</p><p><br /></p><p>Nanma kallan juna suka kumayi tare da girgiza mata kai, </p><p><br /></p><p>Sannan tace, shine _"yasaka ka biya min wannan abunda kamin ko, ka gayamin gaskiya"_</p><p><br /></p><p>_"Wallahi bashi yasani ba, ki mana bayani bamu gane ba, dama kinsan Dizhwar dinne? "_</p><p><br /></p><p>Tana kuka tana fadin,</p><p> _"Nasanshi mana, shine,shine wanda yamin fyade, shine wanda ya yaudareni"_</p><p> Ta kuma fashewa da kuka. </p><p><br /></p><p>Gaba daya Mamaki da kuma abun al'ajabine ya kama su, dan gaba daya sun kasa fahimtar abunda take fada. </p><p><br /></p><p>Da er Dr. Ya lallabata, dan tayi musu bayani, haka tana kuka har saida ta gaya kusu dukkan abunda ya faru tsakaninta da shi. </p><p><br /></p><p>Jafar mutuwar zaune yayi dan ya yarda da maganar Lailah, tunda shi kansa yaga alamun hakan da kuma gaskiyarta, domin tabbas ranar dinner nemansa sukayi suka rasa saida safe ya dawo, gashi abu kadan saika gansa yana waya kamar marar gaskiya. </p><p><br /></p><p>Bayan ta gama sanar masu, Jafar yace da ita, </p><p><br /></p><p>_"Kinga ki kwantar da hankalinki, insha Allah, a yayan da kika kirani haka zan zame miki yayan, zan tsaya miki akan dukkan wata matsala taki, na yarda da abunda kika fada kuma na miki alkawarin zan kwatar miki yancin ki mundin ina raye kede kawai ki bani hadin kai"_</p><p> Kai kawai Lailah take dagawa shikuwa likita shiru yayi yana jin abunda suke fada. </p><p><br /></p><p>_"Yanzu, ki kwantar da hankalin zan samo lawyer sannan zamuyi magaba da Memartabah duk yanda ya yanke hukunci saimu shiga kotu amma nayi miki alkawarin kwatar miki yancinki kamar yanda kike tamkar kanwa a gareni"_</p><p><br /></p><p>Dadi Lailah taji sosai, dan yanzu zuciyarta ta gama tsanar Dizhwar, dan ko wani nayi mata maganarsa bata kauna, danya koya mata hankali kuma, Ya cuceta, yanzu ta gane Yaseer shine masoyinta na ainayi, shine me kaunarta tsakani da Allah,amma ta watsa masa kasa a ido. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(28)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Jafar ya jima cikin asibitin kafin yayi musu sallama ya tafi.</p><p>Daga shi har Dr. din ba karamin mamaki sukayi ba jin abunda Lailah ta fada, koda ya rakasa dukkan su babu me yima wani magana, Dr. Ne yayi dariya tare da fadin.</p><p><br /></p><p>_"Kana ganin kuwa yarinyar na ba karya take masa ba danta bata sunan gidan ku ba, amma taya hakan zata faru shida Dizhwar yan mata ma basa gaban sa balle wannan yarinyar"_</p><p><br /></p><p>Shima de abun yana bawa Jafar mamaki amma yasan dabarar da zaiyi dan gane gaskiyar magana, </p><p> Be bawa Dr. Amsa bah ya fice daga asibitin. </p><p><br /></p><p>Koda ya koma gida danki nsu ya nufa cikin sa'a kuwa ya tarda Dizhwar din ya fito daga cikin daki. </p><p><br /></p><p>Zama yayi kan kujera tare da sauke Gauran Numfashi. </p><p><br /></p><p>Zuwa yayi shima ya zauna kusa da shi, tare da fadin</p><p> _"Daga ina haka naga kamar ka Gaji sosai?"_</p><p> Dizhwar ya fada yana kallansa. </p><p><br /></p><p>Shima juyowa yayi sukayi ido biyu tare da fadin, </p><p> _"Naje gidan gaisuwa ne, wata budurwar abokina ce ta mutu"_</p><p><br /></p><p>_"Allah ya jikanta"_</p><p>Dizhwar ya fada. </p><p><br /></p><p>_"Wallahi kuwa, abunne abun tausayi, an ma kusa bikin su fah, kawai tsautsayi yasa ta fita da dare ta tafi unguwa wallahi sai gawar ta aka kawo, yaban tausayi baka ga yanda ya rame bah, nikuwa kaji sunan Budurwa tasa"_</p><p> Jafar ya fada yana kallan Dizhwar, yanayin yanda yake yin kamar gaske, Shima Dizhwar din kallansa yake. </p><p><br /></p><p>_"Yawwah Lailah"_</p><p><br /></p><p>Yana fadar haka, Dizhwar yayi saurin juyowa ya kalli Jafar din. </p><p><br /></p><p>Kana ganin fuskarsa kasan yasan ta dan yanda ta nuna abun mamaki. </p><p><br /></p><p>_"Kasan tane?"_</p><p><br /></p><p>Jafar yayi masa tambayar. </p><p><br /></p><p>_"Aa, ah, haba aina zan santa kuma?, kawai tabani tausayi nima"_</p><p> Dizhwar ya fada tare da tashi ya fita daga cikin dakin. </p><p><br /></p><p>Binsa Jafar yayi da kallo, dan gaba daya ya gama ganosa, Murmshi yayi tare da tashi ya fita daga cikin dakin.</p><p><br /></p><p>Kai tsaye wajan me Martabane ya nufa, cikin sa'a kuwa yana nan be fita bah, yana can cikin dakinsa na Garden. </p><p><br /></p><p>Babu kowa a wajansa, yana zaune yana shan iska. </p><p><br /></p><p>Da sallama Jafar ya shiga tare da samun saman carpet ya zauna. </p><p><br /></p><p>Kallansa Memartaban yayi tare da fadin, </p><p> _"Kadawo kenan? "_</p><p><br /></p><p>_"Eh wallahi, Baba dama akwai wata magana da nake san muyi me Mahimmanci"_</p><p><br /></p><p>Dagowa yayi daga kishingidan da yake tare da fadin, </p><p> _"Bismillah inajinka"_</p><p><br /></p><p>Shiru yayi dan yana danjin kunya amma kuma inya ki sanar masa kamar yaci amana ne, ahankali yayi gyaran murya tare da fara fada masa abunda yake faruwa tun daga farko har karshe. </p><p><br /></p><p>Shiru yayi dan abun ya daure masa kai Kuma ya basa mamaki,</p><p><br /></p><p>Gaba dayansu shiru sukayi babu wanda yake magana gurin yayi shiru Baka jin komai sai kukan tsintsaye. </p><p><br /></p><p>_"Yanzu yaya ake ciki, menene mafita?"_</p><p> Memartabah ya tambaya yana kallan Jafar. </p><p><br /></p><p>_"Yanzu shi yayan yarinyar ya riga ya shigar da kara"_</p><p>Jafar ya fada masa dan jin abunda zai fada. </p><p><br /></p><p>Abun ya kara jinjinawa tukun yace da Jafar, </p><p> _"Gaskiya abunda Dizhwar yayi min be mana adalciba, kuma saina masa hukunci daidai da abunda yayi, tabbas in har aka bari aka shigar da kara zamu shiga cikin matsala, haka zalika sunan mu Zai baci,manyan mutanan da suke ganin mutuncina duk zasu dena gani, abunda nakeso dakai shine, ka basu hakuri, akan su janye karan In akai hakan sai a lallaba su, Shi Dizhwar din ya aureta kaga ai hakan yayi. </p><p><br /></p><p>Shiru Jafar yayi dan yasan da er in har Lailah zata yarda ta aure Dizhwar amma kuma Bashi da mafita dole ya gwada hakan. </p><p><br /></p><p>Jafar Naam yayi da shawarar da Sarki ya fada tare da mikewa ya bar wajan. </p><p><br /></p><p>_________</p><p>Koda Jafar yabar asbitin nan, abunne ya mutukar daurewa Dr. Kai dan haka waya ya dauka ya kira Dizhwar. </p><p><br /></p><p>Koda ya daga kaisawa sukayi, ya tambayeshi ya karfin jikinsa. </p><p> Bayan sun gama abunda zasuyi, Dr. Yace da Dizhwar, </p><p> _"Kasaan wata Yarinya Lailah?"_</p><p><br /></p><p>Gaban Dizhwar ne ya fadi dan baya san kowa yasan wanann maganar, amma kuma karyace aa abun ya dagule masa, </p><p> _"eh nasanta"_</p><p>Ya bashi amsa. </p><p><br /></p><p>_"Toh wallahi kana cikin matsala, domin kuwa tana nan asibitina, a kwance, Jafar ya tsinceta ya kawota dan amata magani, har suna maganar shigar da kara akan abunda Kayi mata"_</p><p><br /></p><p>Shiru Dizhwar yayi dan tashi ta kare, wani gumi ne ya keto masa dan tashin hankali.</p><p><br /></p><p>_"Am Dr. Nagode da sanar min da kayi, zanzo asibitin in gani in itance"_</p><p><br /></p><p>Sannan sukayi sallama. </p><p><br /></p><p>Dizhwar wani baki cikine ya kamsa, kenan shiyasa Jafar yake masa wannan tambayar ,tabbas dole ya kashe lailah, saiya koya mata hankali harshi zata tunawa asiri, da sauri ya shiga neman key din motarsa. </p><p><br /></p><p>Wayar shice tahau Ringing, kamar bazai daga ba ganin Sarki ke kiransa yasa ya daga. </p><p><br /></p><p>Batare da yayi magana ba ya daga dan jin abunda zai fada. </p><p><br /></p><p>_"Kai ko aina kake kayi maza maza ka dawo cikin gida nanina san ganin ka."_</p><p><br /></p><p>Batare da Dizhwar yayi maganaba ya kashe wayar, kallan wayar yayi kamar zaiyi kuka, ya fita daga dakin. </p><p><br /></p><p>Part din Memartaba ya nufa amma began saba, masu aikinne suka gaya masa inda yake, haka ya nufi wajan nasa gaban ya sana faduwa.</p><p><br /></p><p>Koda yaa isa, shiga yayi ya zauna, dan besan abunda zai sanar masa bah. </p><p><br /></p><p>Ganin Memartaba ya hade rai yasa ya fara jin tsoro, shiru babu wanda yake magana. </p><p><br /></p><p>_"Dizhwar, yanzu ka Kyauta abunda kayi mana kenan,kullum burina be huce ka Zamanto yaro na gari, amma koda yaushe kana cikin bani matsala, meyasa baka sona baka kaunar barin cikin mu, yanzu kaje kayiwa yarinyar mutane fyade, yaya kake san duniya ta kalli abun? "_</p><p><br /></p><p>Innalillahi wa'inna illaihir raji'un, yasan Jafar ne ya gayama Me martaba wannan maganar.</p><p><br /></p><p>_"Dan Allah kayi hakuri wallahi bada sani na hakan ta faru bah"_</p><p>Dizhwar ya fada kamar zaiyi kuka. </p><p><br /></p><p>_"Kamin shiru, ahaka zaka iya mulkar jama'a, da in baka masarautata gwara na mutu a kan kujerata ko kuma inbawa wani bare, kai baka cika adaliba har yanzu, kai mahaukacin inane, bana maka Aure bah, me kuma ya kaika wajan yaran waje, wallahi na yanke hukunci, nan da Kwana biyar zaka aure tah, kuma Wallahi wallahi Sai kayi nadamar abunda kayi"_</p><p><br /></p><p>Hankalin sane ya tashi ya fara hada hannu yana rokonsa kamar me bara. </p><p><br /></p><p>Hannu ya daga masa tare da fadin, </p><p> _"Na gama magana in bazaka yi abunda nace ba, ka fitar min daga gida, can suje su shigar dakai kara, babuni babu kai"_</p><p><br /></p><p>Memartaba yana gama fardar haka ya shige ciki.</p><p><br /></p><p>Zuciyar Dizhwar banda tafasa babu abunda takeyi, shi kadai yasan yanda yake ji. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sauri ya mike ya fita daga wajan, jikinsa har tsuma yake ya nufi Part din Mami yasan nanne kawai inda zaije ya tarda Jafar. </p><p><br /></p><p>Kana ganinsa kasan babu lafiya.</p><p><br /></p><p>Suna zaune a Babban Falon Mami, gaba dayansu suna hira, babu Sallama ya shigo dakin yana ganin Jafar ya hau dukansa. </p><p><br /></p><p>Nan suka mike suna masa magana, Mami kuwa kuka takeyi, dan ganin zai kashe Jafar din. </p><p><br /></p><p>Asiya ma kukan take, Hajiya bilki ce tayi kokarin janye Jafar din daga jikinsa. </p><p><br /></p><p>_"Baku da hankaline, menene hakan kukeyi kamar kananan yara"_</p><p> Ta fada tana kallan ko wanne cikinsu yana huci, ga jini da yake zuba daga bakin Jafar din. </p><p><br /></p><p>Mami ce ta nufo wajan tana duba jikin jafar din tare da taba jikinsa. </p><p><br /></p><p>_"Meka masa menene ya faru Jafar?"_</p><p><br /></p><p>Jafar shima dabe kawo ga abunda yayi masan ba, neman amsa yakeyi. </p><p><br /></p><p>Juyowa Mamin tayi tare da dauke sa da mari, zaiyi magana ta kara masa wani marin. </p><p><br /></p><p>Kallanta yakeyi da hawaye a fuskarta, </p><p> _"meyasa kike marina kinsan abunda yayi min ne, kowa baya bani gasikiya, wannan munafikine kuma wallahi saika gane da wanda kake"_</p><p> Nan ya dage yanata faman masifa. </p><p><br /></p><p>_"Mamice tace dashi, Fitar min daga dakina, banza marar kunya wanda besan darajar mutane bah har iyayansa"_</p><p><br /></p><p>kallanta yayi zuciyarsa tana kara tafasa. </p><p><br /></p><p>_"Ko dukana zakayi nima da kake kallona, ta fada tana ture shi baya, tana kuka, wallahi baka da mutunci Dizhwar, ka dakeni nima sai insan ka cika futsararre"_</p><p><br /></p><p>Hannu yasa ya turata baya shima yana huci, gaba daya mamakine ya kamsu, itama surrender tayi tana kallan sa, ga hawaye yayin da itama Asiya ta nufo wajansu tana kukan, </p><p> Wajan Dizhwar ta nufa, kafin ta karasa Mami tace da ita, </p><p> _"Inde kika kuma Masa magana ban yafe miki bah"_</p><p><br /></p><p>_"Kaikuma fitar min daga daki, karka kuma Zuwa wajena koda bayan raina kazo inda nake ban yafe bah , kamar yanda koda yaushe kake sani kuka, insha Allah kaima sai kayiwa mace kuka, wallahi sai kayi nadama"_</p><p> tana fadar haka ta shige dakinta</p><p><br /></p><p>Kowa tsaye yayi a inda yake babu wanda yake magana, tsaki Dizhwar din yayi tare da fadin, </p><p> _"Ina fita daga dakin mutuwa zanyi, inna kara shigowa nan wajan niba dan halak bane"_</p><p><br /></p><p>Yana fadar haka ya juya zai fita, da gudu Jafar ya bishi yana fadin, </p><p> _"Dizhwar "_</p><p><br /></p><p>Hajiya Bilki ce tace, inka kuma masa magana, </p><p> _"Allah ya isa ban yafe maka bah"_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(29)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cak!, Jafar ya tsaya ina bunda Mamanshi ta fada. </p><p><br /></p><p>Yana san yaje wajan Jafar din, dan gani yake kamar bashi da lafiya</p><p><br /></p><p>Dan ba karamin mamaki yake basa ba in yaga yana irin wannan bun. </p><p><br /></p><p>itama Hajiya Bilki cikin dakin ta shige, Yayin da Jafar ya zauna kan kujera abun ya dameshi, dan be taba tunanin akwai ranar da hakan zata faru tsakaninsa da Dizhwar din bah, be damu da gefan bakinsa daya fashe bah. </p><p><br /></p><p>Ahankali Asiya ta karaso tare da bude karamin First aid kit data dauko bah, goge masa wajan tayi ta saka masa magani,</p><p><br /></p><p>Dogowa yayi ya kalleta, yanda take hawaye, rungumetah yayi tare da fadin, </p><p> _"Kukan ya isa haka"_</p><p><br /></p><p>Kamar ya kara zugata ta kuma fashewa da wanda yafi wancan, shima tausayi ta fashi, hawayanne ya zubo masa dan gaba dayansu tausayin Dizhwar din suke. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Koda ya fita dakinsa ya nufa ya shiga hada kayansa, saida ya tattara komai sannan yasa a dauke masa ya koma part din Husnar, amma tabbas bada ban me Martaba ba babu abunda zaisa ya zauna a cikin gidan nan, babu maganar wanda yake ji saita mai martabane. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Anty Amarya ko bayan data dawo gida, tunanin fara shirinta take, tukun kafin lokaci ya kure mata, ta shiga binciken wacece Lailah dan tabbas tana san burinta ya cika. </p><p><br /></p><p>Saida tasha hawala matuka tukun ta gano, amma ita kanta yanzu bata san inda take bah, shine kuma Abunda ya daure mata kai Kenan. </p><p><br /></p><p>Amma ganin kar tayi biyu babu bara ta fara da Fulani itama,sawa tayi a nemo mata hawainiya da kuma jelar Bunsuru kamar yanda Bokanta ya fada. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Shikuwa dan abunda Dizhwar din yayi yaji kamar an kara masa kwarin gwiwa dan haka, ya nufi asibiti batare da sanin kowa bah haka batare da sanin dr. Din bah, dan yazo Yayi ma Lailah maganar Abunda me Martaba yanke. </p><p><br /></p><p>Koda ya iso, babu kowa cikin dakin, sai ita kadai dadi yaje yanda zasuyi maganar su a tsanake, dan so yake ayi komai kafin ya koma kano. </p><p><br /></p><p>Koda ta ganshi dadi taji sosai. </p><p><br /></p><p>Bayan sun gaisa yasanar mata da </p><p>_"Ashe ba'a sallame kun bah?"_</p><p><br /></p><p>_"Eh wallahi bansan meyasa hakan ba, amma Insha Allah zuwa gobe kila zamu tafi"_</p><p><br /></p><p>_"Lailah dama abunda ya kawoni magana nakeson muyi ta fahimta nida ke"_</p><p><br /></p><p>Hankalinta ta maida kansa dan jin abunda zai fada din. </p><p><br /></p><p>_"Har ga Allah nayi kokarin taimaka muku, kuma har yanzu ma banyi kasa a gwiwa ba domin na gaya miki tamkar kanwa kike a wajena, dukkan wani abu dazai cutar dake bazan yishi ba. </p><p><br /></p><p>kaita gyada masa dan ta yarda dashi dari bisa dari. </p><p><br /></p><p>_"Naje na sanar da Memartabah dukkan abunda yake faruwa, kuma ya nuna rashin jin dadinsa game da hakan, amma ya nemi wata alfarma guda daya, Yana me rokon dan Allah a janye maganar Kara da za'a shigar tunda mutuncin gidansa da kuma iyalansa Za'a tabah, kamar yanda nasan kema baa muku adalci bah,amma ya nemi amafarki dan Allah kiyi hakuri, ki auri Dizhwar ko zaki zamo canji cikin rayuwarsa "_</p><p><br /></p><p>Da Sauri Lailah ta kalleshi tare da fadin, </p><p> _"Dan Allah kabar wannan maganar, cuta an riga da an cucemu amma baxan taba iya auran Dizhwar bah, kayi hakuri kawai"_</p><p><br /></p><p>kara matsowa Jafar yayi tare da fadin, </p><p> _"Dan Allah dan annabi Lailah bada ni bah dan darajar Ubangiji ki daure ki aureshi, dan Allah taimkona zakiyi dan Allah, wallahi matar daya aura gaba daya ta juya masa tunaninsa Yanzu ko mahaifiyarsa baya kauna"_</p><p><br /></p><p>Shiru tayi tana jin abunda yake fada, wanda take ganin ko kasheta za'ai babu abunda zaisa ta auri Dizhwar duk kuwa da irin san da take masa.</p><p><br /></p><p>_"Bazan iya jayayya dakai ko Kuma Iyayanku bah, an Cuceni, kuma abun be mana dadi ba, duk da har yanzu iyayanmu basu san abunda ya faru bah, bamuda kowa sai Allah, bamu da wani me tsaya mana, nice jin dadin iyayena ni nake musu komai, ko yaya aka samu matsala su aka cuta, soba da haka ina kaunar iyayena fiye da kowa, dan Allah ka janye magnar nan, bazan taba tona muku asiri ba kona aibata gidan ku bah, wallahi nayi rantsuwa da Allah babu wanda zai kuma jin abunda ya faru daga ku din nan da kuka sani, zanyi nisa da garin nan inda babu wanda zaiji labarina koya ganni"_</p><p><br /></p><p>Shiru Jafar yayi, dan besan kuma ta inda za'a bullowa abun ba. </p><p><br /></p><p>_"Nagode da karamcin da kika nuna min Lailah, amma duk inda kike karki manta dani, kuma nayi alkawari kamar yanda nayi da, zan tsaya miki tamkar yayanki, zanyi miki dukkan abunda kike bukata dake da iyayanki, Nagode sosai, kuma in kuna Bukatar abu ko ina kikaje kimin magana"_</p><p><br /></p><p>Hannu ya zura cikin aljihunsa ya dauko karamar wayarsa ya mika mata, </p><p> _"Gashi zan dinga nemaki ta wannan wayar, kuma zan dawo gobe insha Allah, insu Baba sun dawo a gaida su"_</p><p> Yana fadar haka ya mike ya fice daga dakin. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda ya fita tausayin sane ya kamata, kuka ta kama dan ganin yana rokonta abu amma taki masa, shida ya gama Mata komai ya ceci Rayuwarta, ya mata abunda ko wanda suke ciki daya bazasu taba mata bah, bazata taba mantawa da Jafar bah, kallan wayar tayi ta kuma fashewa da kukan. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Dizhwar kuwa, dare yayi bayan ya gama cin abincinsa, ya lallaba Husna ya fito daga cikin dakin, mota ya shiga ya bar gidan. </p><p><br /></p><p>Kai tsaye asibitin ya nufa, daya kira Dr. Ya riga da ya tafi gida, dan haka sanar masa yayi daya nemi Sister Zainab Ahmad, zata kaisa dakin da Lailah take. </p><p><br /></p><p>Babu musu kuwa ya nemeta, nan ta rakasa har dakin. </p><p><br /></p><p>Lokacin, Mama tamayi bacci, Lailah ce zaune kawai tana kallo, tana shan ice cream. </p><p><br /></p><p>Koda ta nuna masa dakin bata shiga ba,</p><p>Komawa tayi, shiga yayi tare da sallama, yayin da yaga wutar dakin a kashe, sai hasken tv, Murmushi yayi ganin tana kallan me shigowar, hasken tv ya haska kyakyawar fuskar tah, kunna fitilar yayi tare da kulle kofar, ya tsaya daga bakin kofar yana kallan ta. </p><p><br /></p><p>Da sauri ta saki ice cream din hannunta, ta mike tsaye tare da jan bedsheet din ta kare jikinta.</p><p><br /></p><p>Murmushi ya kumayi tare da karasowa waja ta, zama yayi yana kallan Mama da take kan sofa tana bacci. </p><p><br /></p><p>Kasa magana tayi tana tsaye tana kallansa, shima kuma zama yayi yana kalla nata. </p><p><br /></p><p>_"Menene kike wani boye boye, bayan babu abunda ban ganinbah"_</p><p><br /></p><p>Wani bakin cikine ya kuma kamata. </p><p><br /></p><p>Mikewa yayi tsaye tare da nufo inda take, hannu yasa ya shaketa jikin bango yana fadin, </p><p> _"Duk yanda nayi domin ki fita daga rayuwarta amma bazaki fitaba kenan, Shine yanzu har kike hadani da iyayena da kuma yan uwana, kinsan wanene ni Kuwa, bakya kaunar Rayuwar ki kenan bakya san nakasassun iyayan ki kenna, wallahi in bakiyi nisa dani ba sai na rabai da rayuwarki"_</p><p> Ya fada har lokacin hannusa yana Huyanta. </p><p><br /></p><p>Zuwa lokacin ta gama jigata, idanta duk ya firfito ga hawaye da take, yana sakinta ta durkusa tana tari. </p><p><br /></p><p>Saida ta gama ta dago indanta yayi jajir. </p><p><br /></p><p>Da zafinta ta kwada masa mari, </p><p><br /></p><p>_"Kai kana ganin abunda kayi kaci bulus kenan,wallahi karya kake kasan nida kai kar tasan kar ce, kaci wasan farko amma wanan karan baka isa kayi nasara bah, har kake tunanin yimin abunda Allah bemin ba, kai waye kaidin banxa kaidin hofi, wallahi ni macece, kasan zan iya wulakantama bade kaika wulakantani bah, kuma ka fitar min daga daki kokuma na maka Ihu, tsinanne matsiyace wanda besan darajar dan Adam bah"_</p><p><br /></p><p>Kalanta yake yayin da itam take kallansa. </p><p><br /></p><p>Ahankali aka hau murda kofar za'a bude. </p><p><br /></p><p>Da sauri Lailah ta matsa jikinsa, binta yayi da kallo da kuma mamaki. </p><p><br /></p><p>Zainab ce ta shigo, ganin Lailah kusa da Dizhwar yasata yin murmushi. </p><p><br /></p><p>_"Sister shine fa mijin dazan aura, ya kika ganmu mun dace"_</p><p> Ta fada tana kara rikema Dizhwar hannu. </p><p><br /></p><p>Dariya tayi tare da fadin, </p><p> _"Sosaima kuwa Allah ya sanya alkhairi"_</p><p><br /></p><p>ta fada tare da ajje mata magani kan fridge, </p><p> _"Lailah gashinan karki manta kiyi bacci baki sha bah"_</p><p> Ta ajje tare da fita.</p><p><br /></p><p>kallan Dizhwar din tayi tare da matsawa baya, zaka iya fita ai. </p><p><br /></p><p>Gaba daya mamaki take bashi, ashe dama haka take yana ganinta da innocent face ashe itama kwaru wace. </p><p><br /></p><p>Ba musu kuwa ya fita, dan kara fara shirin da zai bi ya rabu da 'kaya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(30)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cike da mamakin Lailah Dizhwar yaban asibitin nan, tare da kunar zuciya akan abunda tayi masa.</p><p><br /></p><p>________</p><p>Bayan fitar Dizhwar Lailah zama tayi bakin gadan tana ajjiyar zuciya, dan tabbas cikin tsoro da Tarad dadin abunda zai biyo baya, tayi karfin halin yima Dizhwar din hakan, dan tasan any mistakes game over, shiyasa zata tattara inata inata tayi nisa dashi inda daga shi har Jafar din babu wanda zai kara jinsu. </p><p><br /></p><p>Ranar de kusan kwana tayi batayi bacci bah, ga kuma soyayyar Dizhwar din a gefe daya dan tasan ita kam, bazata taba daina sanshi ba saide in numfashi ta dena a doran kasa shine wannan tasan zata dena. </p><p><br /></p><p>_________</p><p>Koda safiya tayi, bata da burin daya huce Dr. Ya shigo ya sallame su. </p><p><br /></p><p>Hakan yasa tayi tsuru tsuru tana jiransa, amma har kusan 10am amma bezo bah hakan yasa ta fara kosawa. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Shima Dizhwar tunda yaga Lailah jiya hankalinsa ya kasa kwanciya domin duk da yana tsanar ta, amma gefe daya ta tsaya masa cikin ransa, ko kadan ya kasa bacci abun yana damunsa, hakan yasa ya kuma tsanar kansa, tabbas yasan inba daina ganinta yayi ba bazai taba samun kwanciyar hankali bah. </p><p><br /></p><p>Gari kuwa yana wayewa ya dauki number dan kiran Dr. </p><p><br /></p><p>Koda suka gaisa, ya shiga tambayar Dizhwar ko lafiya yaga kiransa da wannan time din. </p><p><br /></p><p>_"Ko kana Asibitinne, ina san ganinka ne"_</p><p> Dizhwar din ya fada. </p><p><br /></p><p>_"Wallahi bana nan, ina airport, akwai matsala ne? "_</p><p> Dr. Din ya tambaya. </p><p><br /></p><p>_"Maganar gaskiya aiki nake san kayi min, wanda dole saika yi hakuri da hakan, duk da nasan ba aikin ka bane"_</p><p><br /></p><p>Shiru Dr. Yayi kafin daga bisani ya furta, </p><p> _"Ina jinka babu matsala"_</p><p><br /></p><p>_"Lailah nakesan ka kashe"_</p><p>Dizhwar din ya fada masa.</p><p><br /></p><p>_"Wata irin magana kake haka Dizhwar, kisan kaifa kake san nayi kenan? "_</p><p>Dr. Ya fada cike da rudewa.</p><p><br /></p><p>_"Eh nasani mana shiyasa na gaya maka, in baza kaiyi bah, amsar me sauki ce, abu dayawa, sai in samu wani"_</p><p><br /></p><p>Shiru Dr. Yayi dan yana mutukar jinjina abun. </p><p><br /></p><p>_"Shikenan babu matsala, yaushe kake San ayi hakan kuma a nawa?"_</p><p> Dr. Ya tambaya, jikinsa a sanyaye. </p><p><br /></p><p>_"Yau nake bukata, kuma bana san kowa ya gane hakan, sannan maganar biyanka in ka dowa sai muyi magana, ko nawa kake bukata"_</p><p><br /></p><p>Murmushi Dr. Yayi tare da fadin, </p><p> _"An gama ranka ya dade, Allah ya kara girma magajin sarki"_</p><p><br /></p><p>Dizhwar kashe wayarsa yayi dan, sai yanzu hankalinsa yake shirin kwanciya. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Kasan cewar Dr. Zaiyi tafiya hakan yasa, ya kira Sister Zainab tare da sanar mata inda wata allura take, akan ta dauko taje ta yima Lailah, babu musu kuwa ta yi biyayyah bisa abunda ya fada, taje ta dauki allura tare da nufar dakin da Lailah take,dama ya sanar da ita 12pm tanayi za'a sallamesu. </p><p><br /></p><p>Lailah zaune bayan ta fito daga wanka tana gyara jikinta harda kwalliya tana murnar tafiya gida, lokacin Mama tana cikin toilet. </p><p><br /></p><p>Da Sallama Zainab ta tura kofar tare da shiga. </p><p><br /></p><p>Ganinta yasa Lailah sakin Murmushi tare da fadin, </p><p> _"Ina kwana"_</p><p><br /></p><p>Cikin fara'a itama tace da ita, </p><p> _"Lafiya qlau, yaya aiki?"_</p><p><br /></p><p>_"Alhamdulillah,ya karfin jikin naki, koda yake da sauki ma tunda naga gashi nan harda Kwalliya"_</p><p><br /></p><p>Dariya Lailah tayi, dan ba karamin farin ciki take bah dan zata tafi gida, ta gaji da zaman asibitin nan. </p><p><br /></p><p>_"Toh ga alurar karshe nan, za'ayi"_</p><p><br /></p><p>Da sauri Lailah ta kalle ta tare da fadin, </p><p> _"Allurar Karshe kuma?, gaskiya tunda na samu sauki babu wata allura da za'a karamin"_</p><p> Lailah ta fada tana hade rai. </p><p><br /></p><p>_"Aa, kar muyi haka dake Lailah, sabo da karin lafiyar kine, zakice baza a miki bah, nima nayi mamki dan nayi tunanin an gama sai kuma muka samu waya daga Dr.da sassafe akan ayi Miki ita kafin ku tafi"_</p><p>Sister Zainab ta fada. </p><p><br /></p><p>Shiru Lailah tayi dan bata kaunar allura a rayuwar tah, </p><p> _"Aina za'a min"_</p><p> Ta fada tana turo baki gaba. </p><p><br /></p><p>Murmushi Zainab tayi tana kallan Lailah.</p><p>_"Bakya san alurar Lailah? "_</p><p> Zainab ta fada tana matsowa wajan ta. </p><p><br /></p><p>Shiru Lailah tayi dan haushin da takeji. </p><p><br /></p><p>Ahankali ta dauko Audigar tana goge mata inda zata mata allurar. </p><p><br /></p><p>Bayan ta gama gogewa ta dauko zata soka mata, da sauri ta dan janye hannun tana rufe ido, hakan yasa allurar baduwa kasa ta fashe, dan Zainab bata rike ta sosai bah,gashi kuma syringe din bana roba bane kamar glass haka yake, ita kanta Zainab in za'a kasheta bata san allurar mecece wannan bah. </p><p><br /></p><p>Binta sukayi da kallo har wani kumfa take kafin kace me, gaba daya ta bushe kamar babu abunda ya zube a wajan, ga kan tiles din wajan yayi wani kal, kai da gani kasan allurar ba karama Bace. </p><p><br /></p><p>kallan Juna sukayi, </p><p> Zainab ce ta fara fadin, </p><p> _"Wayyo Allah Lailah yanzu yaya zancewa Dr., Kina ganin allurar kinsan tana da tsada gashi na fasa tah"_</p><p> Gaba daya hankalinta ya tashi. </p><p><br /></p><p>_"Karki damu, Zance kinyimin, kema Saiki gaya masa hakan"_</p><p><br /></p><p>Shiru Zainab tayi, dan tasan Dr. Da fada akan hakan zata iya rasa aikinta, amma bata da mafitar data huce ta fadi hakan. </p><p><br /></p><p>_"Nagode Lailah, Allah ya kara lafiya"_</p><p><br /></p><p>_"Ameen Ameen Nagode nima, sai ki bani number ki dan mudinga waya"_</p><p><br /></p><p>amsar Wayar Lailah tayi ta saka mata number sannan ta fita daga dakin, dan gaba daya bata ji dadin fashewar allurar bah.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_______</p><p>12pm daidai, Abba ya shigo asibitin bayan ya kira taxi tana tsaye a wajan asibitin, Mama da Lailah ne suka dauko wasu kayan a hannunsu dan tafiya dasu.</p><p><br /></p><p>Har sun fito daga dakin, suka ga Abban ya nufo wajan su, koda ya hangosu saiya karaso yana murmushi yana fada musu ya samu taxi, tare da amsar kayan hannun Lailah. </p><p><br /></p><p>Nan Lailah tayi sallama da duk wanda zatayi, sannan suka fita daga cikin asibitin tana me murna da jin dadi, amma babban damuwar tata anan ina suka nufa dan tasan bazasu zauna wa Dizhwar acikin gidansa bah dan haka tamkar bara zana da rayuwarsu ake yi. </p><p><br /></p><p>Dan haka koda suka shiga cikin Taxi shiru tayi dan tunaninta be huce ta samu mafuta bah. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Anty Amarya har zuwa yanzu bata samu wani saban bayani kan Lailah bah, dan haka Kayan aiki na aikin Fulani ta riga da ta samu kuma a daran Yau take san gabatar da wannan aiki, dan tana ganin kamar bata da rabo Akan na Lailah, sabo da Dizhwar ya riga daya kwanta da Husna tasani, yanzu ita tashin hankalinta daya kartaje tayi wannan aiki akan idan Husna ko kuma ta mata video shine tsoran data ke ji. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Yaune Su Jafar zasu koma, kuma Hajiya bata san tafiyar dare, dan haka,amma shi kam yafi san harsai abunda Memartabah ya fada ya tabbata zai tafi batare daya sanar da kowa bah, Sai abun ya tabbata tukun dan yasan tabbas, Inhar Dizhwar ya auri Lailah bashi kadai zaiji dadi bah har Mami ita kanta sabo da dama babu wanda ya dace Da Dizhwar din sai Lailah,haka zai kuma daurewa ya kara gwadawa ko Zata yarda.</p><p><br /></p><p>Saboda haka bayan ya karya, ya nemi uzuri wajan Hajiya akan bazai jima ba yanzu zai dawo. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Amma koda yazo Ashibitin Aka sanar dashi sun riga da sun tafi. </p><p><br /></p><p>Hakan yasa ya shiga neman wayar Lailah amma bata daga bah. </p><p><br /></p><p>_______</p><p>Koda suka isa gidan Dizhwar din fitowa sukayi da kayan su, bata san nunawa Su Abba komai amma bazata iya zama cikin gidan nan bah. </p><p><br /></p><p>Haka ta shiga jikinta duk wani iri kamar Dizhwar din zata gani acikin gidan. </p><p><br /></p><p>Haka kuwa ta shige dakinta, babu abunda ta fara sai binciken kudin da Dizhwar din yake bata da kuma wanda ta tattara na aikinta a baya. </p><p><br /></p><p>Nan ta duko harta hada 100k, ba karamin dadi taji bah, batare data sanar musu ba take san a kama masu haya, su koma tsohon gidan su dan dauko kayan su, ta samu wata dabarar ta sanar dasu Abba, dan su haka Allah ya tsara musu. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Koda ta dauki wayar ta, ganin missed call yasa ta duba gashi Jafar ke kira amma bata san Koda kudi cikin wayr ba bare ta nemesa, gwadawa tayi, cikin sa'a kuwa ta shiga dan shi har ya hakurama yana shirin komawa gida yaga ta kira sa. </p><p><br /></p><p>Da sauri ya dauka tare da sallama. </p><p><br /></p><p>Amsa sallamar tayi tare da fadin, </p><p> _"Jafar kayi hakuri dan Allah, wallahi banga kiran naka bah, Sai yanzu"_</p><p><br /></p><p>_"Ok babu damuwa ya kwarin jikin naki"_</p><p><br /></p><p>_"Alhamdulillah naji sauki sosai wallahi"_</p><p><br /></p><p>_"Nima yanzu nazo asibitin ashe kun tafi"_</p><p><br /></p><p>_"eh"_</p><p> Kawai tace dan tasan bata kyautabah tunda yace ta jirasa. </p><p><br /></p><p>_"Ki turan da address din gidan naku yanzu da Allah"_</p><p> Yana fadar haka shima ya kashe wayar. </p><p><br /></p><p>Kallan wayar ta tsaya tana yi, nan ta shiga ta tura masa full yanda zai gane dan itama yanzu ta yarda da bukatarsa dari bisa dari tana ganin ta hakanne zata samu damar rama abunda aka mata. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p> 🌷🌷🌷🌷🌷🌷</p><p> *🌼👸🏻 LAILAH-DIZHWAR 🤴🏻🌼*</p><p> *_🌷🌷🌷🌷NA🌷🌷🌷🌷_*</p><p> *_ZAINAB NASEER SARKI_*</p><p> *_ (ZEENASEER😘)_*</p><p> 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>*© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_ViaWattpad@Zeenaseer01_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*(31)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>__________</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kasan cewar yasan unguwar sosai yasa be dauke tsawan lokaci ba ya iso, dan bemayi tunanin gidan nan bane inda su Lailah suke zaune bah.</p><p><br /></p><p>Waya yayi mata ya sanar mata da yana kofar gidan nasu.</p><p><br /></p><p>Kallo kawai yake yaga ta inda zata bullo. </p><p><br /></p><p>Hijab din ta,ta saka tare da takalmi ta fito daga gidan, ganin ta fito daga gidan da beyi tsammani bah, mamaki ya kuma kamasa, sai yanzu ya kara yarda akan cewa Dizhwar yasanta ba tun yanzu bah, </p><p> Yana hango ta nufo motar yayi saurin fitowa, murmushi ta kumayi tare da gaida shi, tare suka shiga cikin gaidan, </p><p><br /></p><p>Kai tsaye inda Dizhwar yake zama in yazo ta nufa dashi. </p><p><br /></p><p>Zama yayi ,itama ta zauna gefansa, </p><p><br /></p><p>Shiru babu wanda yayi magana,ganin kamar da magana a bakinsa yasata fadin, </p><p><br /></p><p>_"Wanann gidan Dizhwar ne ya bamu shi akan ku zauna na dan lokaci,kuma nasan yanzu babu abunda zaisa muci gaba da zama acikinsa, na yanke hukuncin zan kama Mana haya kamar yanda muka saba muje mu zauna har zuwa ranar da Allah zai hore mana gidan mu na kanmu."_</p><p><br /></p><p>Ta fada tana wasa da yatsun hannunta. </p><p><br /></p><p>Shiru Jafar yayi Batare da yayi magana bah, sai zuwa can tukun ya furta. </p><p><br /></p><p>_"Be kamata ku tashi ba, zaman haya bashi da dadi, wahala Kike san dorawa kanki Lailah kefa mace ce ba namiji bah"_</p><p><br /></p><p>Murmushin takaici tayi tare da fadin, </p><p> _"Tun kafin nakai haka nake wahala, sabo da bamu da wanda zaiyi mana, ina aiki tukuru dumin na samu abunda zamuci, musha mu saka da kuma mahalli, ni nake biya mana kudin haya tun bayan na gama Secondary school dina,ina ma yanzuma dan nayi wahala ba wani sabon abu bane, zan kara samun wani aikin kamar wanda nayi a baya domin mu rufama kanmu asiri"_</p><p><br /></p><p>Sosai Jafar yake tausaya mata, baya san yaga mata suna shan wahala, musamman yara kamar Lailah, amma tana burgesa sabo da hakan zaisa baza'a rainata bah ko kuma a mata wulakanci sabo da ta tashi ta nema, ga kuma uwa uba soyayyar da take yima iyayanta, da shi kansa hakan yana furgesa, duk da kasancewar ita take musu komai ga halin da suke ciki, amma be hana ta musu biyayya bah, sabanin wasu yaran da sun fara tara abin duniya zasu dinga yima iyayansu yanda suke su, su maidasu tamkar masu aiki ko kuma wasu yan maula,wasuma su gujesu. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_"Hakane Lailah, kuma Gaskiya inajin dadin yanda kike da kokari da kuma jajir cewa wajan neman nakanki, amma mutuncinki shine aure, kamata yayi kiyi aure wallahi suma iyayyan naki zasuji dadi"_</p><p><br /></p><p>Shiru kawai tayi dan bata san amsar da zata bashi bah. </p><p> Yanzu in tayi aure zata shiga damuwa ba karama bah. </p><p><br /></p><p>_"kinyi shiru, dan Allah nide akan maganar da mukayi jiya itace de yauma nazo da ita, zan iya durkusawa a gaban kima, dan Allah ki amince da Auran Dizhwar din mana"_</p><p><br /></p><p>Shiru tayi, dan tabbas tana da burin yin hakan yanzu tunda ta canza shawara amma, Matsalar anan itace, ina zata kai iyayanta kuma basu taba jin dadin rashin ta bah, babu me gane abunda suke nufi sai ita, basu da wanda suka shaku dashi sama da ita, itace komai nasu inta tafi ta narsu wani hali zasu kasance. </p><p><br /></p><p>_"Kinyi shiru Lailah"_</p><p>Jafar ya fada yana kallantah. </p><p><br /></p><p>_"Shikenan Nayarda zan aure sa,amma nima ina san amun abu guda daya"_</p><p><br /></p><p>Da sauri ya fada cikin kaguwa da kuma farin ciki, </p><p> _"Dole Za'a bama iyayena mahallin zama da kuma me kula dasu"_</p><p><br /></p><p>_"Babu matsala wannan ba damuwa bane, kome kike da bukata zan miki shi wallahi, burina be huce ki aminceba kuma kinyi, nagode miki sosai ,saiki sanar da Abbanki, gobe Za'a zo neman auran naki wajansa"_</p><p><br /></p><p>_"Allah ya kaimu, Nagode "_</p><p><br /></p><p>_"Nine da Godiya Lailah,insha Allah bazaki taba tabewa ba, Allah ya hada kanku da Dizhwar, na tabbabata nan gaba zakuyi farin ciki da kuma alfahari da juna"_</p><p><br /></p><p>Itade Lailah shiru tayi, haka suka gama abuda zasuyi yayi mata sallama cike da farin ciki ya tafi. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Koda ta shiga gida ta sanar da mama, tayi farin ciki da hakan sosai dan dama itama burinta Allah ya bawa Lailah miji na gari,kuma ta tabbatar da soyayya ta gaskiya da Dizhwar din yake yiwa yar tasu sun san bazai wulakanta ta bah. </p><p><br /></p><p>________</p><p>Koda Jafar ya koma gida, Memartabah ya nema ya sanar masa da duk yanda ake ciki, </p><p><br /></p><p>Sarki yayi farinciki da yawa kuma yayi alkawarin hada Jafar da manya wanda zasu can gidan su Lailah gobe insha Allah kamar yanda Jafar din ya fada.</p><p><br /></p><p>Shima Jafar din yayi farin ciki, dan haka yana fita daga wajan sarki, nan ya fara kiran ma'aikata domin a fara gyaran wani part dan saka lailah, so yake a gyara mata shi a zuba mata kaya kamar yanda ko wata yar me gata ake mata. </p><p> Nan da yan kwanaki kadan za ai komai a gama, ko kafin a gama gyaran wajan nata ta zauna wajan Mami shide Jafar ya ganta cikin gidan.</p><p><br /></p><p>Yanzu tunda yasan komai ya kammala yana da Guarantee da zai iya gayama Su Mami wannan maganar, kai tsaye can ya nufa. </p><p><br /></p><p>Komar kullum Suna cikin dakin Mami, Asiya tana jikin Mami akan gado, yayin da Hajiya tana zaune kan kujera sun gama shirinsu Jafar din kawai suke jira. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zama yayi, tare da fadin, </p><p> _"Hajiya har kun gama shirin kenan,toh ba yau zamu tafi ba kudan kara mana Sati daya domin akwai wabun da nakesan gamawa dan Allah, in kuma zaku tafi Muje ga motoci can a waje"_</p><p><br /></p><p>Duk su ukun kallansa kawai suke dan suna san jin abunda yake san yi din. </p><p><br /></p><p>_"Menene kuma kake shirin yi kenan?"_</p><p> Hajiya ta fada tana kallansa. </p><p><br /></p><p>_"Amarya"_</p><p> Ya fada yana murmushi. </p><p><br /></p><p>Da sauri Asiya ta mike zaune tana kallansa. </p><p><br /></p><p>Dariya yayi tare da fadin, </p><p> _"Dama ina ta san zama nayi muku Bayani, toh tunda nazo ina busy sosai shiyasa, amma yanzu komai ya kankama, nan da kwana biyar Insha Allah zata tare"_</p><p><br /></p><p>_"Kai bana san iskanci, kayi mana bayani yanda zamu gane"_</p><p>Hajiya ta fada. </p><p><br /></p><p>Dariya Mami tayi tare da fadin, </p><p> _"Jafar shakiyin yarone kai wallahi. </p><p><br /></p><p>Shima Dariyar yake, </p><p> _"Wallahi sabuwar Amarya a gidan nan, nan da kwana biyar ina fada muku"_</p><p><br /></p><p>_"Munji sabuwar Amaryar wa? "_</p><p><br /></p><p>Hajiya ta fada tana kallansa. </p><p><br /></p><p>_"Dizhwar"_</p><p><br /></p><p>Jin abunda ya fada yasa gaba daya suka kalli juna, sannan suka maida kallansu gareshi. </p><p><br /></p><p>_"Dizhwar kuma?"_</p><p>Mami ta fada tana mamakin abun. </p><p><br /></p><p>_"Kwarai kuwa Dizhwar, Mami, kanwata na bashi,nima kwanan nan zan karo wata"_</p><p><br /></p><p>gaba Dayan su mamaki suke dan har yanzu Jafar yana musu yaho da hankali. </p><p><br /></p><p>_"Ku nutsu kuji dukkan abunda ya faru, dama so nake sai komai ya daidaita sannan kuji."_</p><p><br /></p><p>Nan ya fara basu labari tun daga farko har zuwa yanzu. </p><p><br /></p><p>Mamaki da Al'ajabi ya hana kowa magana acikinsu, dan abunda basu taba tunani ba kenan, Mami kuwa ba karamin farin ciki tayi ba da Jafar ya tsaya tsayin daka dan ganinsa sai anyi wannan auran,dan ya nuna musu Dizhwar din baso yake bah.</p><p><br /></p><p>Cike da farin ciki Mami tace, </p><p> _"Ubangiji Allah yayi maka albarka Jafar, Allah yasa ka gama da duniya lafiya, ya baku yara Nagari masu albarka, kayimin daidai, shi Atunaninsa yaci bulus kenan, ya lalata musu yarinya yayi auransa, sabo da tsabar bashi da mutunci harda zuwa da yarda tah yana kokarin yin kisan kai, kayimin daidai wallahi"_</p><p><br /></p><p>Kallanta Hajiya Bilki tayi tare da fadin,. </p><p><br /></p><p>_"Fulani, meye abun daidai anan, shi haka yace yana santa, ubanwa yasa ta zo wajan nasa"_</p><p><br /></p><p>_"Wallahi aa Yaya, dan tazo wajan biki, bashi ya gaiyaceta bah, dan masoyinka ya gaiyaceka waje kaje laifine, shiya janyota kuma kina gani, shine ya takura ta, tunda inda da son ranta akayi da kanta zata koma gida amma kiji fa yanda akayi da ita"_</p><p> Mami taji dadi ba karami bah.</p><p><br /></p><p>Kallan Jafar tayi tare da fadin, </p><p> _"Yanzu an gama magana an samu masu gyaran?"_</p><p><br /></p><p>Mami ta tambaya. </p><p><br /></p><p>_"Eh yanzu zasu je, wajan dama fa bashi da wani matsala dama komai sabone, kawai kaya tarkace za'a kwashe ayi saban fenti, sai furnitures da za'a saka"_</p><p><br /></p><p>_"Masha Allah, ni nan zan mata komai, yarinya abun tausayi haka, zan yima Humaira magana kan furnitures dinta,insha Allah bazai dau lokaci ba"_</p><p><br /></p><p>Dadi sosai Jafar yaji haka itama Asiya.</p><p><br /></p><p>_"Amma Yaya saida nace maka zani na dubo ta kaki yarda,kayi tafiyarka"_</p><p><br /></p><p>_"Menene na damuwa kuma, har gida fa zata zo yanzu ai ta zama Anty kuma"_</p><p> Murmushi tayi. </p><p><br /></p><p>Hajiya Bilki itama taji dadi tana yima dan nata addu'a ko yaushe, amma a fili sai ta nuna rashin jin dadinta dan bata san a takura Dizhwar din. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Dizhwar kuwa babu abunda yake jira sai saka mako daga wajan Dr.</p><p><br /></p><p>Yana zaune cikin falon su,</p><p><br /></p><p>Husna ce ta shigo tare da zama. </p><p><br /></p><p>_"Hubby tafiyar nafa gobe ne, kuma na gaya maka sati daya zanyi"_</p><p><br /></p><p>Kallanta yayi tare da fadin,</p><p>_"Yanzu bikin kawa har sai kinje kinyi sati, nikuma fa"_</p><p>Dan bata rai tayi kadan tare da fadin, </p><p> _"Itama fa tazo min nawa kuma har aka gama tana nan, dan Allah ka barni naje"_</p><p><br /></p><p>Shiru yayi yana danna waya, tashi tayi dan barin wajan alamun tayi zuciya, hannunta ya kamo, Murmushi tayi, </p><p> Janyo ta yayi ta fada jikinsa, ya shafa fuskarta tare da fadin, </p><p> _"Bawai ina hanaki bane, ina tunanin adadin kewarki da zanyi, shiyasa but am sorry,yanda kika ce haka za'ai"_</p><p><br /></p><p>Dadi taji sosai, tare da kara shigewa jikin nasa. </p><p><br /></p><p>______</p><p>Dr. Kiran Zainab yayi dan jin ko tayi abunda ya saka ta domin yana bukatar kudi masu yawa wajan Dizhwar. </p><p><br /></p><p>Haka ta sanar masa kamar yanda sukayi da Lailah, kuma ya yarda dari bisa dari dan yasan tabbas inde anyi allurar nan ba makawa sunan mutun gawa. </p><p><br /></p><p>Cikin farin ciki ya turama Dizhwar text, dan sanar masa da komai ya kammala. </p><p><br /></p><p>*ZEENASEER*</p><p><br /><br /></p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-75842917719029208362021-04-22T21:33:00.001-07:002021-04-22T21:33:07.047-07:00Matsalar Rayuwa Complete Littafin Hausa<p> </p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-vVYY1PHXZ_g/YIJNrdAGIlI/AAAAAAAAJns/kuKrGQNHZLkgEkQK36hjvFcYO2r9B8yCwCLcBGAsYHQ/s2048/Matsalar%2Brayuwa.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="Matsalar Rayuwa Complete Littafin Hausa" border="0" data-original-height="1653" data-original-width="2048" height="323" src="https://1.bp.blogspot.com/-vVYY1PHXZ_g/YIJNrdAGIlI/AAAAAAAAJns/kuKrGQNHZLkgEkQK36hjvFcYO2r9B8yCwCLcBGAsYHQ/w400-h323/Matsalar%2Brayuwa.jpg" title="Matsalar Rayuwa Complete Littafin Hausa" width="400" /></a></div><p></p><p>[8/20, 21:00] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆🏼(1)</p><p>Bismillahir rahmanirraheem wasallAllahu ala nabiyyul kareem.......</p><p><br /></p><p>TSOKACI:wannan takaicaccen labari yana labartarwa akan maraicin wata bafulatanar yarinya fatima bintu da akema lakabi da FANTA tunda fulanine sunfuto daga karamar hukumar Anka awani kauye na fulani na Hayin Ruga.Rugar Baffa Ardo itace rugar tasu Fanta.</p><p> Koyaza'akare kushigo daga ciki....<span></span></p><a name='more'></a><p></p><p> ✍🏽</p><p>Tafe na hango wasu yammata dabasu wuce shekara 13-14 ba dogayene daka gansu kaga fulani.kowacce da sandarta tagado ahannunta suna tafiya suna kora shanunsu da alama daga hayi suke.</p><p> Dayardaga cikin yammatan biyu wadda tafi kyau naga takalli dayar Salah knga duhuwa(duhu) tayi bari naje gida knga jikin innah wuro ba lpy yayi samari(tsamari).</p><p> Salah tadan zaro ido haryanxu jikin innarku bashida lapia.muje naduba shi nima,atare suka rankaya rumfar ta marigayi baffa ardo mahaifin fanta kenan.gwanin sha'awa sunsa kayansu nafulani amma wadatacce da vest aciki sannan ga kitson doka guda biyu da kyalle daga kasa andaure ja!</p><p><br /></p><p>Shanun suka daure agarke sannan sannan suka nufi rugar baffa ardo.kwance nahango wata dattijuwar mata fara sol bafulatana daka ganta kasan itace mahaifiyar fanta dankamar tasu tayi yawa dande ita tamanyantane itakuma yanxu take tasowa!</p><p> Fanta ta aje tacacciyar nonon shanuwar dasuka tatsa ta aje kusada innartata innah katashi kasha yanxu muka tasoshi(tatsoshi)nida salah sannu yagikin?nanma salah tataso tanaiwa inna wuro yajikn nata cikin harshensu na fullanci.dasauki salah awari jam?salah tace jam kalau .nande suka temakawa innah wuron tasha nonon sannan suka maida ita takoma.sallah sukai sannan fanta tatafi taraka salah gidah.</p><p> </p><p>Bayan fanta tadawo wanka tayi takara gyare dan gdannasu tsaf tsaf.sannan tadora sanwar dare.innah wuro se adduu'a take mata.Allah yamaki albarka fanta yakaiki gdan dadi hannu nagari.mahaifinki kullum burunsa bewuce ki karatu kixama wani abun arayuwaba amma gashii rai yayi halinsa.nikuma ba lapia.MATSALAR RAYUWA tasamu agaba.</p><p> Fanta tagoge hawayen daya gangaro mata.bakomai inna inna insha Allahu xanxama wata nima ni burina naxama likita intemakawa marasa lapiya nagida dana asibiti.gashi Allah berasamuna abun Shi da shaba insha Allah MATSALAR RAYUWA baxatai galaba akanmuba.innah wuro tacire tagumin data zabga tabbas ahanknma miyatti Allah. arzikine da Allah ya azurtamu dashi.</p><p><br /></p><p>WACECE FANTA?!</p><p>Fatma bintu wadda akema lakabi da FANTA sunan nasu nafulani yace ga marigayi baffa ardo sunfuto daga karamar hukumar anka akauyen na hayin ruga.dayake duk rugar fulanine ajejin wanda yaxama dankaramin kauye.</p><p> Rugar baffa ardo ba boyayyiya bace akauyen na hayin ruga.kafin rasuwar tass yakasance daya daga cikin manyan masu sana'ar shanu .dan mutane daga garuruwa mostly lagos anan suke sara sutafi da shanun ko zallar nonon danyin yoghurt ko freshmilk.</p><p><br /></p><p>Akauyen na hayi ya auroo matar tasa wuro wacce akem lakabi da innah wuro sundade basu sami haihuwa seda akadau shekaru sannan suka haifi yarsu daya tilo kyakkyawa kamar kasaceta kagudu dankyau.aka samata fatima bintu FANTA.kenan.</p><p> Bayan shekara 7 dahaihuwarta ciwo yakama baffa ardo seda suka saida kusan rabin dukiyarsu daga karshe dae rai yai halinsa.dawannan suka shiga damuwa harde matarsa innah wuro takwnta ciwo,MATSALAR RAYUWA tai musu yawa.yakasance basu da wata dukiya inba shanayensu guda 5 ba. Wanda fanta ce akan ragamarsu itace kefita dasu tasaida nonon wanda yan birni ke siya danyin fresh milk ko yoghurt.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker ✍🏻 and Miss Xoxo</p><p>[8/20, 21:00] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆🏼(2)</p><p>Kamar kullum bayan fanta tadawo daga makarntar asubahinsu tadanyi tulawar karatunta,tashi tae tanufi garken shanayensu taxuba musu abinci.nanta hadu da abokanan baffanta baffa nura da baba wuro sunkuyawatae harkasa tagaydasu:noi camre,noi gyalle,noi cama loji,noi dabbaji?(ina kwana?antashi lapia?yaharkoki?ya dabbobi?)amsa mata sukai sannan suka tafi suna kora shanyensu ixuwa kiwo....</p><p><br /></p><p>Wanka tae tadora ruwan bunu tasiyo kosai da yake innar salah tana saida kosai.sannan taisa bukkar mahaifiyarta. Innah ina kwana katashi lapiya?lapia lou fanta .dayake innah wuro batasan tarunga ma fanta fullanci tafuso yartata takoyi hausa sosai saboda MATSALAR RAYUWA.</p><p> Abinci sukaci sannan fanta ta dau tsintsiya tafara share gdannasu sannan tahada wanke wanke tae.tana cikin gyara saman bukkarsu salah takwada sallama, fanta fanta kijo mutafi shan hayi yar birni sunxo inji hairen gdan baffa sambo.</p><p><br /></p><p>Bashiri fanta tasakko tareda gyara daurin zaninta tadakko dan mayafunta tadaure kanta.gaskiya fanta kyakkyawace farace sol,doguwace amma ba me shahararren tsawo ba,tana yalwar gashi da cikar kai.tsayawa afadi kyanta seyaxama kauyanci.</p><p>Innah muntafi saimundawo,toh fanta Allah yakaiku a sa'a yasa albarka acinikin yau.</p><p> Yar sandarta tadauka sannan takunce shanyen takorasu suna tafiya suna hirarsu da salah dan itakadaice aminiyarta agarin.</p><p><br /></p><p>Canhayi suka nufa duk ga yammatanan kowa ta daure shanyenta tana tatsar nono. Wasu suna sara wasu kuma suna saye.cannagango ilu yanatafe yana rada sandarsa akasa.salah ta tabo fanta ke ga ilu shan yanxu xataxo gurinki.fanta tabata rai sekwa gashi yaxo gurin yaxauna akusada bokitin tatsar nono.fanta meyasa kikemin haka dukshikin yammatan garinnan ke nashe inaso kuma xan aura amma kamar bakyasona kodandali kindena xuwa saboda ni meyasa?</p><p>Tunda yafara magana haryagama fanta batai magana ba harde yagaji da surutansa yabar wajen.</p><p> Salah da fanta suka cigaba da hirarsu dayake sungama tatso nonon jira kawai suke su samu mesiya.</p><p><br /></p><p>Daga mota yafito kirar honda EOD yanatafe yana gyara daurin takalmunsa,kansa da pcap.gurin wadda xesari nononma yarasa yajuyanan yajuya can.can yahango wasu yammata guda biyu se magana suke da alama kuma sunada tsafta</p><p>Idanunsa yabude yadan kara runtsesu kadan abunda idanuwansa suka gani basu amince dashiba sosai,kyakkyawar yarinya fulani acikinsu,wacce yagani suna hira da wata.</p><p><br /></p><p>Hankalinsa, zuciyarsa basu amince da acikinsu takeba, xuciarsa daitabashi kilar itams siyan nono taxo,wannan al'ajabin dayake ciki be hanashi ci gaba da tafiya xuwa inda sukeba.ba'inda yai tsinke sai wajen da yammatan biyu suke.</p><p> Sannunku dae,yawwa sannunki kema salah ta amsa masa dayake bata iya hausa sosaiba.mekike so?yakalli fanta ni shanuwar nakeso uwar garke.dayake yarane basu gane meyake nufi ba.fanta tai murmushi tab mubama saida saida shanu seda katambayi innanmu.nande yalura yarane.atake yace su bashi nonon dasuka tatsa yasae bokiti biyar biyu agurin salah uku agurin fanta.</p><p><br /></p><p>Se mamaki suke dan basu taba ciniki hakaba,yakuma nunka musu kudinsu,harxe tafi yajuya yasaci kallon fanta yasunankune?salah uwarsurutu tace ni sunana salah itakumafa?sunanta fanta.....kaikuma yasunanka inji fanta,wani dadi yaji aransa,ni sunana MAHBUB.makani?daria yarungayi hadda kwalla aa ba makani ba MA..H..BUB.ohhhhh MAAHAABU yace to shikenan hakanma yayi.</p><p> Sallama yamusu sannan yatafi Captain mahbub kenan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker✍🏽and Miss Xoxo</p><p>[8/20, 21:00] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆🏼(3)</p><p>Mahbub yana barin gurin salah da fanta suka kunce shanyensu suka nufi gida.kowaccd murna fal cikinta don ba'ataba masu ciniki hakaba,salah takalli fanta,wannan mahabu yanada kudi sosai knga nifa murtala dari biyu yabani(2k)kekuma murtala dari uku.wallahi nasan yau innah zeenaru xaiyi murna sosae kilama gobe bazayyi kosai ba.</p><p> Fanta takyalkyale da daria lalle salah saboda menai baxe kosaiba ai yaxama dole knsanfa ni daga tsintsiyar roba(taliya)se kosan innarku kawai ne cimata.</p><p><br /></p><p>Da haka har akaxo bukkarsu salah toh se jango fanta.yawwa salah kigayda mn da innarku.itama dahaka tana tafe tana yan wakokinsu na fulani ta isa gidah,tadaure shanayen a garke sannan tashiga yar bukkar tasu,jikin na inna wuro kwa dasauki har tadan kishingida tanajin radio,da sallamarta tashiga bayan ta aje sandar gado akusada randar ruwansu.innah nadawo yajikn naki?dasauki fanta miyetti Allah.fanta tace innah yau kam munyi sa'a ansaye duka nonon .innah wuro dadi yakamata Allah hukkomo sa'a .amin innah.</p><p><br /></p><p>Wai daga bunni yake,wai sunanshi uhmm yama? Uhm uhm mahabu,yasae bokiti 3 akan murtala 300 itakuma salah bokiti biyu,bakiganiba yanada kirki. Kuma muka manta bamu shemushi a'ina yakeba,innah insuka siya dayawa mesuke dashi?!tun baffanki yanada rai sana'ar sa kenan daga gari gari akexuwa a sara sunayin madara ko suyi lemon madara a roba(freshmilk)ohhh ashe hakane lalle yan burni sunajn dadi,Allah nima inna inason xuwa burni dinnan,innah tace kita addu'a watarn sekiga kinje.to ai inna knga muna shikin MATSALAR RAYUWA!addu'a itace mafita fanta kada ki sabo kisauri ki istighfari,AstagfirullAllah!!!</p><p><br /></p><p>Sauri Mahbub yake yakoma gidah dan at any time company dn xasu iya closing gashi yama takusa,5dede ya isa company dnnasu yakira labourers dn suka debi nonon don shiga dashi factory ai freshmilk da yoghurt.</p><p>Sallama ya musu sannan yashiga mora yanufi hanyar gidah koda ya isa gate dn gabanshi se faduwa yake don yasan abunda xe tarar.</p><p> Tsaye take daka ganta kasan babu hasken annuri atattare da ita.yana shigowa sukai kicibis da ita.kallonsa tai kamar xata watsa mai wuta.check ur handwatch yanxu karfe nawa?muryarsa narawa yakara da 5:30.haka mukai dakai mahbub wato karainani kenan ko se mgnar ubnka kakeji ko.gabadaya yarasa meyafaru shide yasan ba'abunda yai.masifartace tadawo dashi.tambayarka nake.gwaggo meyafaru?uwarkace tafaru.wato dankamaidani bawon albasa bacanai xaka kaini unguwaba shine xakasa kafa kabar gdannan tun safe se yanxu.</p><p><br /></p><p>Gwaggo kiyi hakuri wallahy kindemnta baki fadaminba,tass ta mareshi karya namaka kenan,aa kiyi hakuri gwaggo na sha'afane,bani car keys dn yamika mata ta wafce tai waje abinta.murmushin dake cikeda damuwa yai sannan yashiga dakinsa,wanka yai, yai sallah batun abincikwa sede yadafa yaci. Tashi yai ya mike a doguwar sofa dake dakinsa yaname tariyo fuskar yar bafulatanarnan tabbas yaxama wajibi dayardar Allah gobe yakoma yaga FANTA.</p><p><br /></p><p>WANENE MAHBUB?!</p><p><br /></p><p>Mahbub dane ga Alhaji sulaiman anka babban dankasuwa kuma kusa agwamnati.mahaifiyarsa marigayiya hajia aisha itama yar uwace ga Alhaji sulaiman,tarasune lokacin Mahbub yana cyprus yana karatun pilot which was 3yrs back.</p><p>Su biyu ne awajen mahaifiyarsu daga shi se knwarshi nawwara amma ita tayi aure tana lagos.</p><p> Bayan rasuwartatane Alh sulaiman ya auro wata acan kasan line dinsu bazawara anacemata gwaggo hindatu.xuwanta keda wuya tacanxa komai nagidan shikansa uban seyadda tae dashi.abincikwa andaukewa mahbub sede yadafa da kansa .</p><p><br /></p><p>Shekarar mahbub 28 da haihuwa ,dogone amma baki irin kalar waffles,yagama karatunsa na pilot a acyprus aynxu haka yaxama captain.amma gwaggo tahana adole sede yarunga lura da factory dn soft drinks dinsu.da wannan tunanin bacci me nauyi yadaukeshi da mafarkai barkatai dukde akan yar fillon yarinyar nan......Fanta</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker✍🏽and Miss Xoxo</p><p>[8/20, 21:00] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(5)</p><p>Haka Fanta tadinga jinyar innah wuro yinin ranar har dare yai,safiya nayi bayan fanta tagama aikace aikace ta ,ruwan dumi tado dayai xafi tatemakawa innan tai wanka kotaji dadin jikinta..</p><p><br /></p><p>Gari nakarasa wayewa taxubama shanu abincinsu sukaci suka koshi,sannan tasa wankin innah agaba tafara fama,salah nagama aikinta itama takunce shanunta tanufo gdansu Fanta.tasamu fanta na wanki innah wuro tasamu bacci </p><p> Kai kakai haba fanta wanki kikeyi kinsanfa rana tayi kar atsare gurin damuke xama.fanta tayafuto salah Tamata Alama datai magana ahankali innah wuro tasamu tai bacci.tajanyo hanninta suka nufi waje </p><p><br /></p><p>Salah innah jikinta ba lapia shiyasa nashe kimagana ahankali jia Batai bacci ba seyanxu tasamu bacci yadan dauketa.salah tace haryanxu de oh Allah de yasauwaka mata,Fanta tace ameen...</p><p>Salah tace to ynxu xakije hayin ?aa gaskia baxaniba intaji sauki naje.salah tace jinjina Kai to kuntosu ni Nahada da nawa inyaso love awa daya nai se nadawo.</p><p><br /></p><p>Nagode salah Nagode,takunto shanun tabama salah itakuma tahada danata takorasu suka nufi hayi,itakuma Fanta takoma gidah tacigaba da wankinta hade da jindadin abinda salah ta mata,basu taba fashin futa tareba se yau.</p><p><br /></p><p>Salah naxuwa hayi tafara tatsar Nono sedatagama tsaf sannan tarufe takillacesu waje daya ,tasa hannu daya tai tagumi tabbas fanta aminiyartace kuma yar'uwa,Dan surutun data sabayima shiru kmar ruwa yacinyeta .se addu'a Ma data dingayi Allah yabama inna wuron sauki .tafi awa awurin harxata tafi setatino da alkawarin dasukaima mahbub na sabon tatsar Nono.</p><p><br /></p><p>Dakyar gwaggo tabar mahbub yafita danseda tasa yakaita unguwa yajirata sannan yadawo da ita dukko da tarin drivers din dake gidan.yana dawowa da ita yajuya xetafi takirashi Kai mahbub saurin mekakeyine wai shin inama xakaje?gwaggo nonon xankarbo nasa su ajiyemin ne tunjiya,shine kake rawar jiki haka kamar Wanda akabama babbar kyauta .to sekai sauri kadawo .tohm gwaggo.</p><p><br /></p><p>Tana juyawa suka hada ido da Alh sulaiman anka mahaifin mahbub Wata uwar harara tasakar masa ya akai?kansa akasa yace bakomi..shine kaxo katsaya akaina haka?dama dama ...dama me???dama daurin auren diyar alhaji kabiru nakesan xuwa.shine nakeson naje...to baxakaba nace baxakaba wannan alhaji kabirun abokinka da baiso nashigo cikin gdannannba narantse da Allah baxakaba.tawuce tabarshi atatsaye.(Asiri yayi tasiri ajikinsa,inakiran mata da babbar murya Dan Allah muji tsoran Allah aibase da asiri xakijuya mijinkiba addu'a itace )</p><p><br /></p><p>Mahbub yafigi mota dagudu se kauyen hayin Ruga,yana xuwa yafaka motarsa ,yafito daga nesa yahango salah itakadai,se sakawa yake axuciarsa to Ina fantan?to kila tadan xaga wani wurin.yana tafe yana waige waige koxe hango fanta.harde yakaraso inda yasaba ganinsu salah ce takifa kanta akan cinyarta da Alama tagaji kuma tadanyi nisa abarcin datake,hannunsa yasa akan bokitin kusada ita yana bugawa.bashiri tatashi tana salati,yakalleta yai daria ashe matsoraciya ceke to nasamo lagwanki.itama Dariar tai au mahabu kaine shannunki,kema sannunki....</p><p><br /></p><p>Ina Fanta?yatambayeta,Fanta tana bukkarsu,innah wuro she ba lapia,too wacece innah wuro kuma?gyatumar tace.ai tadade ba lapia ba tunsanda Baffa ardo yarasu.baffan fantan ne ae.shiyasa nadakko shanunta xanmana shiniki gaba daya,mahbub yace bokiti nawa kika tatsa?bokati 4 ita biyu ni biyu.nantake mahbub yasiye yasa amota kuma yabata kudinta.to ynxu xaki rakani wajen fantar?eh muje takunce shanayen takorasu tana gaba yana binta abaya yalura kowa da sandarsa babbar da yaro,to meye anfanin hakan?</p><p><br /></p><p>Suka karaso gurin Wata yar bukka salah tace to mahabu kijira anan Bari nashiga shiki nadaure shanunnan,yace toh inajiranki yakara lura da kusan duk Bukkar kusan Iri dayace ga ba abubuwan more rayuwa to yanxu tahaka suke rayuwa?shida kansa yabawa Kansa amsa lalle Allah buwayine kuma gagara misali.salah tafito can tahango mahbub yana kallon wasu yan fulani maxa suna wasan shadi.mahabu kixo mu tafi,daga Kansa yai alamar to sannan yabita abaya bawani nisa tsakani suka Iso Wata bukka haka yar babba ba lefi.kitsaya Bari inshiga inkira fantar.sedata daure shanun fantar sannan tashiga xaune tasamesu itada innah wuron se tari take.</p><p><br /></p><p>Salah tanemi wuri taxauna tagayda innan wadda takasa amsawa sede daga kanta datai sama alamar amsawa.salah tajuya wurin fantar tamika mata kudin sannan ta dorada tare muke da mahabu fa iya waje.fuskar Fanta tacan za alamar mamaki waje kuma?salah tace ehh...nande fanta ta fadawa innah wuro kan wannan me musu cikin ne yaxo yana waje.innah da alokacin tarin yayi sauki tadafe kirjinta dake barazanar fadowa saboda ciwo</p><p>,tace kuce yashigo kwabarshi awaje shi kadai kwi masa iso.</p><p><br /></p><p>Atare suka sheka da gudu Fanta da salah .can suka hangoshi ,mahabuuuuu .waigowa yai idanunsa sukai toxali da hasken idaniyar tasa Fanta.gefen xuciarsa ne yake bugawa dakyar yadafe wurin ya nufuso tabbas Fanta tazamo wani gurbi axuciarsa haryake ganin shin wannan menene SO KO SHAKUWA?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker ✍and Miss Xoxo</p><p>[8/22, 00:02] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(6~10)</p><p>A hankali kuma anutse mahbub yakaraso inda su salah da Fanta suke ,fanta dadi duk ya isheta yauga mahbub agidansu ta washe baki tana aika masa da sakon murmushi Wanda kyakkyawar wushiryarta ta bayyana.shima murmushin yamayar mata Wanda bakowa yakewaba sewanda ya cancanta...</p><p><br /></p><p>Sannu mahabu inayini?lapia qalau fanta,yajikin innah wuron?dasauki sosai .sekuma takalli kasa saboda wani kwarjini dataga ya mata,salah tace innah wuron tashema kashiga.</p><p><br /></p><p>Atare su ukun suka shiga cikin gidan .kwance take tasa hannu daya tadafe kirjinta dayake ciwo.tana ganinsu tai kokarin tashi tadankishingida ,mahbub kuwa sandarewa yai atsaye tabbas dakaga innah wuro Kasan ita tahaifi Fanta.</p><p> Innah wuro takalleshi cikin kamala da dattijantaka irinta fulani,jabbama jabbama tace masa .gaysheta yai tare da doriyar yaya jikinnata?dasauki dannan abinse godiyar ubangiji .yaya kikeji ajikinnaki innah?</p><p><br /></p><p>Jikina zafi ga ciwon kai sannan bana jinkarfi ajikina ga innai bayan gidah xafi kuma kalar dorawa ne ga kirjina xafi kamar ze fado dan ciwo. dana kira kamilu me kyamis seyace wai malariya (malaria)ce .na shashsha maganin amma de haryanxu abinse hamdala kawai ,mahbub yace eh da malaria dinma amma kuma harda shawara(typhoid)Shan gurbataccen ruwa shiyake kawota.Allah de yasawwake.</p><p> Nande mahbub yafada mata sunansa da kuma inda yake atakaice de yabata takaicaccen labarinsa.yakuma dorada inbaxata damuba xaikaita asibitin cikin bunni saboda typhoid idan tai tsamari takan tsittsinka hanji Wanda daga karshe mutum yakan rasa ransa.</p><p><br /></p><p>Innah tajinjina Kai ta kuma yaba da nutsuwarsa kwarai amma kuma meyasa zeta masu wannan wahalar haka?takalleshi takara yabawa da hankalinsa tabbas ba irin matasan nanbane naxamani..,toh mahbub meyasa kake ta mana wannan wahala haka ai abin yayi yawa kwarai dakabar xancen asibitin nan tunda inashan tsimi kuma nakan danji dama ajikina .mahbub Wanda axuciarsa yake ta mamakin ya akai wannan yar dattijuwar bafulatanar take Jin Hausa haka .tambayar data jefomasa ita tagoge tuna nin dayake axuciarsa.</p><p><br /></p><p>Kafin mahbub yabata amsa tajuya takalli Fanta da salah Wanda suka tsura masu Ido sekace masu kallon film .innah wuro tace salah jeki rugar Baffa jauro kisayo fura ta murtala uku ,let kuma Fanta dauki Kwano kitatso Nono ,in salah takawo seki dama mar fura akwai siga(sugar)a cikin leda kusada randa .ansawa sukai sannan kowacce tanufi aikin da aka umarceta tayi.</p><p><br /></p><p>Innah wuro tasake kallon mahbub akaro na uku,Ina sauraronka mahbub....toh innah ni haka natashi Naga babana yana taimakawa marassa shi barin iyaye mata nakasance Ina tausayinsu fiye da komi Dan typhoid itace tai sanadiyar rasa mahaifiyata danai .sannan Abu na biyu wallahy innah sekuma ya kasa karasawa saboda wani nauyi da kunyarta dayakeji.</p><p><br /></p><p>Inna talura da hakan,kakkaji komai mahbub yadda Kasan danda nahaifa haka nakejinka a jinina mekakeso kafadamin?</p><p>Seda mahbub yadau mintina kafin yace Wlhy Inna tunsadda nafara ganin Fanta naji tashiga raina ,kuma bawai yaudaraba da aure nakeson diyarki innah.amma kuma banasan nafada mata saboda naga haryanxu dakuruciya atattare da ita.amma kuma idan har ammata miji babu matsala kuma zumuncina daku baze tsinkeba har abada nidaku munzama yan uwan juna.</p><p><br /></p><p>Toh mijikam ba ayima Fanta ba Dan kaf hayin ruga bawanda Fanta tatsayar amatsayin miji KO saurayi,ilu ma dangidan me unguwa shine yanuna yana Santa amma yarinyarnan taki sarai.kuma ma yanxu de koda tasamu miji anan hayin ruga to KO anyi auren ze zama kullum cikin gori tsakaninta da mijin.</p><p><br /></p><p>Mahbub yakalli Inna wuro cikin zulumi da mamaki saboda meyasa kika ce haka innah? Saboda mu al'adar rugarnan mahaifiyar amarya zata Bawa ango shanu talatin ,tumaki talatin da zabi goma kaji goma.kuma ita Kanta amaryar ita zataba abokan ango duk yawansu raguna kowa dai dai to kaga Ina muke da wannan halin MATSALAR RAYUWA tayi mana yawa.kuma ita kanta fantar aure baya gabanta takance ita karatu xatayi to kuma karatun yaya mata a kauyennan megari yasokeshi yakance wai gurbata tarbiyyar yaya mata yakeyi.to yaya za'ai na arabin de shisukeyi yanxu.kuma nayaba da hankalinka amma Kasan bani da damar Baka Fanta aure aynxu saboda baffaninta duk sunanan sukeda ikon Baka ita,amma nikam daga wajena babu matsala insha Allahu inrabonka ce tabbas Fanta Xara xama mata agareka kaje kaita addu'a Allah yaxaba abinda yafi alkairi.mahbub be furta komai ba illa Amin dayace .</p><p><br /></p><p>Bayan kamar minti 30 Fanta tadawo da furar adame yadda kasan injine yadama dakaganta se ranka yabiya.innah tace Ina kuma salar?fanta wadda alokacin tadan xame murfin furar ,ayyo salah aitatafi gida yanxunnan innarsuce ta aiko yafendo takirata yanxu.</p><p><br /></p><p>Bayan yadansha furar ne wadda adole kawai yake shanta bawai Batai dadi bane a'a yadda innah wuro tace auren Fanta yanaga hannun baffaninta yanxu insunki yadda yaxeyi da ransa?bayan yagama shane yakecema innah wuron gobe xedawo dan yakaita asibiti.</p><p><br /></p><p>Sallama yaiwa innah wuron wadda ta umarci Fanta taimasa rakiya.tabbas innah tayaba da hankalin mahbub kuma tana addu'ar Allah yasa mahbub yaxamto kamar yayewar MATSALAR RAYUWAR fanta.</p><p><br /></p><p>har mota Fanta taiwa mahbub rakiyar Allah yakiyaye yakuma dawo dashi gobe lapia.adaddafe mahbub ya Isa factory dnsu mesuna barnyard fresh yai dropping nonon sannan ya nufi gidah.</p><p> Yana xuwa yatarar da gwaggo da ixzy a parlor Suna hira,KO kallon inda ixzy take beyiba illa key da yabawa gwaggo yaiwucewarsa daki yanaji tanata bambamin masifa amma kota kanta bebiba inda sabo aiya Saba.</p><p><br /></p><p>Sallah yai kawai yai kwanciyarsa dan dama bashi da wurin xuwa ko zaman majalisa tunda gwaggo tahana. kuma friends dinsa duk Suna Cyprus, se amininsa da sukasan sirrikan junansu tunsuna kanana har suka xama aminan juna a yanxu da dr haydar.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker✍and Miss Xoxo</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(10~15)</p><p>Yammacin ranar mahbub yarasa wacce mafita xebi se juyi yake akan gadonsa yana me neman alkhairin Allah akan wannan sabon al'amari daya bijiro arayuwarsa,kuma inma ya fadawa babansa bawani mataki xedaukaba tunda gwaggo ce take juyashi kamar Waina a kasko.dawannan yaga gwarama yakira amininsa dr haydar yafada masa matsalar dayake ciki.</p><p><br /></p><p>Daukar wayarsayai Kirar Samsung Galaxy s7 edge yadanna nambobi yakira dr haydar.ringing daya biyu haydar yadau ka,Sallama yamasa sannan yace dan Allah yaxo yanasan ganinsa.bansan me dr haydar yace ba naji de mahbub yace Bari shi yaxo.</p><p><br /></p><p>Bayan mahbub ya gama wayarne yarasa karyar daxewa gwaggo tabarshi yafita gashi ba ita kadaibace nacacciyar ixzy dinnan taxo.tashi yai yawatsa ruwa.yacanxa shiga cikin English wears jar riga ta polo se jeans baki yasa takalminsa sau ciki yanufi parlor dn gwaggo da addu'ar Allah yasa takyaleshi yafita.</p><p>Zaune yaga gwaggon da ixzy a kujera me uku(3 sitter).sauri yai yadafe cikinsa saboda yagano karyar daze mata.</p><p><br /></p><p>Alamun tafiya gwaggon taji tajuya ganin mahbub tai dafe da cikinsa ,to kaikuma lapia kana tafe kana rike cike saikace me shirin haihuwa?!mahbub yai narai narai da idanunsa gwaggo cikinane yakulle ciwo yakemin .tabe baki tai to ni mezan maka?dama key nakeso kibani xanje asibiti.ixzy wadda tunsanda yafara magana take kallonsa kamar wadda zata cinyeshi takalli gwaggo to bari nai escorting dinka senai driving motar.</p><p><br /></p><p>Harara ya wurga mata lokacin gwaggo ta sunkuyar da kanta zata dakko key din a jakarta.ai base kinrakani ba nagode!gwaggo taxaro mukullin ta wurgo mai,gashinan saura kadade Kasan sauran.daukar mukullin yai yafice dasauri yatashi motar yai gaba dankarma kalatacciyar yarinyarnan tabiyoshi.</p><p><br /></p><p>Tafiya yake ahankali karar sautin kidan Nancy ajram ne yaketashi har ya isa asibitin dake revenue street me suna random hospital yai parking sannan yashiga ciki.kiran dr haydar yai yace masa ya iso yana ajewayar yaxauna a waiting area yana jiransa.bayan kamar minti 5 dr haydar yasakko daga stairs tabbas Kyau awurin haydar ba 'a magana sede ace tubarkAllah masha Allah.</p><p> Tafawa sukai har haydar yake tsokanar mahbub yau kuma wacce karyar kaima gwaggo tabarka kafuto?mahbub yai murmushin takaici Wlhy abokinka canai mata stomachache ke damuna.har kalatacciyar yarinyarnan zata batamin moment wani wai xata rakoni setai driving motar.haydar yai daria aboki aidaka kyaleta yarinyar nasonka dayawa.mahbub yaharareshi Allah yamin tsari na so izzatu ko mata sunkare aibaxanso wannan yarinyar ba.inkai kanaciki to se infadawa gwaggo asha biki.haydar yace rufamin asiri aboki sokake mufeeda(matarsa)takashe ni kenan.ko abuga a weeklytrust ace wani yakarowa matarsa kishiya bayan goma da bikinsa.</p><p><br /></p><p>Mahbub yace yanxu de jokes apart aboki.serious magana naxo miyi dakai .anan zami KO a'ina? No muje bayan surgical ward semi magana.tashi sukai suka nufi bayan surgical ward akan wasu kujeru suka zauna.</p><p><br /></p><p>Aboki nayi new catch and auren ta nakeso inyi,matsalar shine yarinyace karama I think 13-14 take.kuma babanta yarasu saboda haka Neman aurenta yakoma wurin uncles dinta.wannan ba shine ma major problem dinba,matsalar na wurin gwaggo kasan ita tanace wai sena auri izzatu(ixzy)kuma baba baxe iya Komi akaiba.gashi yarinyar taxama wani part arayuwata I don't think zan iya rayuwa without her.aboki shawara nakeso kabani please.</p><p><br /></p><p>Dr haydar yai murmushi lalle koma wacece wannan yarinyar gaskia she's lucky .aboki yau kaine kazama haka akan mace.dafarkode a'ina yarinyar take cyprus ko us?</p><p>Mahbub yai murmushi sunanta Fatma bintu amma Fanta ake cemata,ba filatanace a kauyen hayin ruga take.infact de awurin ta itada kawarta salah nake saro Nono da ake amfani dashi a factory na barnyard fresh.</p><p><br /></p><p>Dr haydar yagwalalo Ido u gat to be kidding me right?aboki u mean yar kauye ce dama .kuma kakkacemin nonon dakakawomin sheka ran jia awurinta kasiya ?mahbub yakalli yadda dr haydar ya dimauce shi a lalle a dole beyadda da abinda mahbub yafadaba.steady abokina duk abinda nafadama ba karya cikinsa.if u truly care 4 me then katsaya tsayin daka Fanta taxama mata agareni.kuma gobe nake planning nakawo mahaifiyarta asibitinnan a mata general checkup.</p><p><br /></p><p>Kasa magana dr haydar yai illa xaro handkerchief dayai a aljihu yagoge gumin daya tsattsago agoshinsa dukkoda na 'urar air conditioner dake turare gurin da sanyi.well aboki bansan yaxanyi da wannan issue dinnakaba ,nima wallhy gwaggo nake tsoro Kasan xata iyasa wannan yarinayar acikin MATSALAR RAYUWA.amma addu'a kawai zami itace kawai solution.Allah yasade yadda kakesan yarinyarnan itama haka take sanka.</p><p><br /></p><p>Aboki banma fadamata inasantaba illade nasan kobabu SO na azuciarta to akwai SHAKUWA.kaga aboki idan kacigaba da wannan tamboyin Wlhy baxakaci abincin gidanaba.dr haydar ya kyalkyale da dariya tuba nake aboki kaina bisa gwiwa .</p><p><br /></p><p>Dawannan suka dan huta suka cigabada magana irintasu ta aminai har dr haydar yakecewa gwarama mahbub yai aure saboda yakusa xama senior bachelor.</p><p>Tashi sukai mahbub xetafi shikuma dr haydar xekoma cikin asibiti.</p><p><br /></p><p>Mahbub yacewa dr haydar aboki aini harna sha'afa rubutamin maganin ciwon ciki inje insiya Kasan gwaggo yadda Kasan EFCC haka take dole setaga maganinnan hankalinta xekwanta.tare suka jera cikin asibitin yafadawa pharmacist din maganin daza'abawa mahbub.sannan sukai sallama mahbub yahau mota se gidah!</p><p><br /></p><p>Yana xuwa yatarar dasu gwaggo a'inda yabarsu .yana shiga yamika mata mukullin tareda ledar maganin,tabude takaranta tabashi yakrba yawuce dakinsa,yaname godewa Allah gwaggo bata gane karyar dayaiba.</p><p><br /></p><p>Laptop yadauko yacigaba da kallon series din empire.zuciyarsa kal da ita idan yatuno hasken idaniyar tasa Fanta..........</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker✍and Miss Xoxo</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(15~20)</p><p>SAFIYA TA GARI FANTAN MAHBUB:</p><p><br /></p><p>washegari da sassafe fanta takammala aikin gidah sannan ta taya innartata tai wanka .itama wankan tayi tasaka doguwar rigarta baka wadda Baffa lado yasayamata sannan tayafa mayafin tanadeshi irin yadda taga yan birni sunayi insunxo siyan nono wajensu.tagyare ko Ina takillace tsaf sannan suka kuma bukkar sauro wajen fita Suna jiran captain mahbub yaxo.</p><p><br /></p><p>To shidinma bayan ya shirya cikin wani yadi brown da milk yai Kyau kamar Wanda za shi gasar zaben kyau.agurguje yai toasting bread yasha da cappuccino ,ya nufi parlor zaune yahango Baba da gwaggo da alama wata maganar suke.karasawa yai cikin parlor dn yaxauna akan center carpet .baba Ina kwana?lapia qalau mahbub ka tashi lapia?lapia qalau baba.sannan yajuya gurin gwaggo tacika fam kamar zata fashe,Ina kwana gwaggo?dauke kanta tai dakyar ta amsa lpy!</p><p><br /></p><p>Mahbub yatashi yanadan sosa keya,alh sulaiman yakalleshi ya akayini mahbub?aa bakomi key nakeso gwaggo tabani.aikwa dama gwaggwan acike takeda dashi.okay wani salon munafuncin katsiro kenan ko?kana wani dukar dakai kamar wani sabon ango.to baxan bayarba karfinka yakwatarmaka.</p><p><br /></p><p>Mahbub kasa magana yai illa juya dayai yana kallon babansa.shi Kansa alh sulaiman din yanasan yatsawatar mata amma karfin sihirin dake jikinsa yahanashi aikata komi .mahbub kuwa ganin zata batamasa lokaci yasa Kai yaificewarsa daga gidan.tsayawai yana kallon motocin dake fake a packing space din gidan kusan EOD dn dayake hawa itace karama daga marcedez Benz se toyota da sauran company.tsaki yai na Allah wadai da muguwar kishiyar uwar dayasamu.</p><p><br /></p><p>Yana tsaye yana tunanin mafita daga karshede yayanke shawarar kiran dr haydar yafadamasa halin dayake ciki.wayarsa yadakko yai dialing dr haydar.hello aboki kana ina?okay kana asibiti to bari naxo.keke napep yatara aka saukeshi a asibitin.yakira haydar yace mashi yashigo consulting room dn bakomi.</p><p><br /></p><p>Kansa tsaye yashiga.atsaye yatarar da dr haydar dn yana cire labcourt dn dake jikinsa.kallon mahbub yai bayan sungaysa aboki lapia kuwa naganka haka?aboki meyake faruwane.aboki very soon xaku nemeni kurasa .aboki lapia?haba nagaji da rayuwar da gwaggo tasani aciki,ace mutum dagidansu amma bashi da walwala kwata kwata,Kasan Allah aboki bansan farin cikiba se Ina tare da kai ko fanta ko inmuna waya da nawwara.kasan gwaggo kiri kiri tahanani mukullin motata hardasu cemin wai karfi yakwata.imagine fa haba .</p><p><br /></p><p>Dr haydar yai ajiyar zuciya .hakuri zakai aboki,nasan tabbas gwaggo xata aikata abin dayafi hakama,kayi hakuri aboki .yanxu ga key dn motata kaje kadakko su nasan sunacan kila Suna jiranka.godia ya masa sannan yanufi packing arena din yadauki motar kirar sportage yanufi kauyen na hayin ruga.</p><p><br /></p><p>Minti 40 yakaishi hayin ruga a bakin hayin yai packing motarshi.sauri yake harya karasa bukkar ta Baffa ardo.sallama Sau uku yayi kafin Fanta ta masa Iso yashiga.numfashinsa har Neman daukewa yai ganin gimbiyar tasa cikin doguwar riga baka sekace balarabiyar Kasar lebanon.gaysheshi tai cikin muryarta me dadin sauraro.amsawa yai dakyar Dan numfashinsa yana barazanar daukewa .</p><p><br /></p><p>Karasa shiga cikin bukkar yai yagayda innah wuron sannan yabata hakurin kan rashin xuwa dayai dawuri.bakomai mahbub Allah deyasaka maka da alkhairi.tashi sukai dukkansu innah tashiga baya taxauna a owners corner ,ita kuma Fanta tashiga gaba.mahbub yaja se asibiti!</p><p><br /></p><p>**********</p><p><br /></p><p>Random hospital yai packing ,Fanta se leke take tana kallon harabar asibitin.futowa sukai daga cikin motar suka shiga ciki .direct office din dr haydar suka nufa Wanda ke xaune yana checking wasu files.da sauri yamike yana kallon wasu kamar jinsin larabawa tareda mahbub,rintse idonsa yai yabude tabbas ba mafarkibane,lalle mahbub yayi dacen mata.</p><p><br /></p><p>Dr haydar yasunkuya yagayda innah wuro bayan mahbub yamata bayanin kowanene haydar din.itama Fantar gayda haydar din tayi.dr haydar ne ya umarci innah wuro kanta kwanta akan gadon dake ajiye agefen dakin ze mata scanning,fantace tatemakawa innah wuron tahau ta kwanta,sannan yace mahbub da Fanta sudan bashi guri xedubata....</p><p><br /></p><p>Bayan kamar minti 5 dr haydar yagama scanning cikin innah wuro inda yagano critical chronic typhoid ce kedamunta kuma harta tsittsinka mata hanji,sannan kuma tana internal bleeding.dakyar ya iya kiran mahbub yashedamasa abinda ake ciki.kan dole se ammata aiki.mahbub be iya cewa komaiba illa nodding knsa kawai dayai.</p><p><br /></p><p>Nurses ne suka tura Inna wuron xuwa theatre room kan operation din gaggawa.dr haydar da dr Haysam suxasu mata operation din.har andakko kayan aiki xa'afara innah wuro tajuya gurin dr haydar kakiramin fanta!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker✍and Miss Xoxo</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(20~25)</p><p><br /></p><p>innah wuro tajuya takalli dr haydar kakiramin Fanta.gyada Kai yai sannan yafice daga theatre room din da sauri yanufi waiting area inda mahbub da Fanta suke .can yahangosu akujerun karshe sunyi jugum da alama kowa da tunanin dayake axuciarsa.karasawa yai gurinsu ya tsaya.mahbub yadago Ido yakalleshi aboki lapia?lapia qalau aboki.yadan kallon gefen inda Fanta take kije innarki na nemanki.</p><p><br /></p><p>Atare suka jera su ukun suka shiga cikin dakin theatre ,ganin haka yasa dr haysam yafuto shidinma dr haydar futowar yai bayan yarakasu.karasawa Fanta tai bakin gadon tana kuka innah gani menene innah ko aikinne bakyaso?murmushin karfin Hali innar tai bakomi Fanta ba aikinne banaso ba fanta.kirike mutuncinki Fanta ,karki xubarda tarbiyyar da aka dade ana ginata akanki.kibi rayuwa ahankali.kikasance me tausayi da jinkai.nande Fanta takara mai akukannata yi take ba kakkautawa.inna wuro tagirgixa mata Kai alamar tai shiru.sannan tajuya takalli mahbub dake gefe yana goge nasa hawayen.</p><p><br /></p><p>Mahbub amanar Fanta nan karikemin ita amana Dan Allah .</p><p><br /></p><p>Dr haysam da dr haydar ne suka shigo,dr haydar yakalli agogonsa,yi shiru Fanta kidena kuka,zafin ciwo ne.insha Allah za'aima innarki aiki lapia agama lapia.yanxu dr kubamu wuri keda mahbub saboda munasan mugama mata aikin da wuri,ko bakyaso innar taki tasamu sauki??mikewa tai tana goge hawayen dake tsiyaya .inaso mana,yawwa kokefa.</p><p><br /></p><p>Futa sukai itada mahbub,gabadaya xuciarsa se radadi take.bayaso yaga kukan mace ballantana na gimbiyar tasa Fanta,hakuri yaketa bata harya samu tai shiru dakyar.</p><p><br /></p><p>Dakyar dr haydar suka tsayda internal bleeding din da kidney din innah wuro keyi.sannan suka koma hanjinta dasuka fara tsittsinkewa nanmade sunata iyakar kokarinsu amma ina jinini yake futa guda guda acikin gashi badamar atoshe.salati innar tafara daga karshe dai tacika da kalmar shahada!</p><p><br /></p><p>Dr haysam ne yakalli dr haydar.dr haydar yadakko oxygen amma Ina badama.adole suka hakura,tsugunnawa yai akasa yana hawaye,shi ba'abinda yake tausayi se fanta da wanne idon ze kalleta bayan daxu yagama karfafa mata gwiwa!dr haysam ne yai patting dinshi akafada kayi hakuri Doctor insha Allah tacika da imani.nixanwuce maternity akwai operation din din daxa'ai wa Wata mata .nurses din sunkasa komai.daganan yai fita!</p><p><br /></p><p>Tashi yai yagoge hawayen dasuka xubomai daya tuno haka Hajia aysha mahaifiyar mahbub typhoid yamata kuma shiyamata operation din.fita yai daga dakin yanufi inda su Fanta sukai,mahbub yanaganinshi yamike yaxo wajensa yaya angama?dr haydar yakalli mahbub yaga duk yatada hankalinsa,girgiza kansa.girgiza kansa yai aboki we try our possible best wallahy.....sekuma yai shiru,mahbub yakalleshi afirgice kana nufin ta rasu???ehh .</p><p><br /></p><p>Wata hajijiyace tafara dibar mahbub yaga baya gani sosai dakyar ya iya dafa kafadar mahbub .tasowa fanta tai taxo wajensu,ganin mahbub nacikin wani hali tajuya ga dr haydar.lapia dakta (doctor)?naga mahabu yana neman yafadi.dr haydar yajuya yakalleta bakomai jiri ne kedibansa xesauka insha Allah.kara rikeshi yai sannan yatemaka masa yaxaunar dashi akan kujera!</p><p><br /></p><p>Bayan kamar minti 3 jirin yasauka,ruwa dr haydar yakawo masa yasha yakece masa yakamata yafadawa Fanta halin da ake ciki,kiran fanta sukai dr haydar yajawo kujera yasamata tazauna.</p><p><br /></p><p>Dr haydar yai gyaran murya ,nasan kina xuwa islamia shin wake bayarwa kuma ya amsa?fanta tace Allah ne,yace to in Allah yakarbi abunda yaba mutum shin xakaji haushi?fanta ta girgiza Kai,yace tohm Allan dayabaki innah wuro amatsayin Uwa yakarbi abinsa saboda yafimu santa,kuma kakkice xaki xubarmata da hawaye ,addu'a itakadaice mafita yanxu.</p><p><br /></p><p>Hawayene suka ringa tsere afuskar fanta,amma ba shessheka ko ihunnan da mutane sukeyi,tasa mayafinta tagoge Allah yajikin ta da rahamarsa.dr haydar da mahbub suka goge hawayen daya xubomusu suma,dr haydar yace Allah yamiki albarka,yanxu se muje can hayin rugar asanar da yan'uwa saboda yanxu karfe daya .</p><p><br /></p><p>********</p><p><br /></p><p>karfe biyu Dede aka Kai innah wuro gidan gaskiya,tasamu jama'a kam ba laipi dayake itan dattijuwace me kamala da mutunci,bata taba samin sabani da mutane ba.</p><p><br /></p><p>Baffanin Fanta su Baffa jauro,Baffa lado,Baffa nura dasauransu sune masu amsar gaysuwa.kuma sun yabawa mahbub da dr haydar kwarai kan kokarin dasukai Akan innah wuron.</p><p><br /></p><p>BAYAN KWANA 7</p><p><br /></p><p>mahbub ne adakinsa yana shiryawa yau shigar jallabiy yai fara da hula fara,turare yafesa da sure sannan ya nufi parking space yadau motarsa yanufi hayin ruga.</p><p><br /></p><p>Bayan yaje sun gaggaysa da baffaninta se yatashi yashiga cikin gidan suma yagaysa da Matan,ganin bega Fanta ba yatambayi salah Ina fanta?fanta tana shikin daki bari nakirata,yawwa inkinkirata Ina Zaure.</p><p> Bayan yan mintina kadan Fanta taxo wajen mahbub gaysheshi tai da idonta Wanda yai jawur kamar wuta.muryarta harta dashe.nasiha mahbub yamata sannan yatambayeta ko akwai Wata matsala ?girgixa Kai tayi alamar a'a.yaciro envelop kudine aciki yamika mata tace a'a .dakyar yatursasata takarba.yake cemata xeje Lagos xeduba kanwarsa daba ta da lapia kwana uku kawai xeyi.ya mata sallama yatafi !</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker✍and Miss Xoxo</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(25~30)</p><p><br /></p><p>Bayan mahbub yakoma gidah shirya kayansa yafarayi a akwati harda toiletries da pajamas dinsa duk yashiryasu,saboda jirgin daxe hau karfe 4 ne nayamma yanxu kuma uku tayi saboda da dan taxara tsakaninsu da airport din. </p><p><br /></p><p>Bayan yagama shiryawa tsaf yafito daga daki yanadubawa parlor yaga su gwaggo basanan hawa stairs yai yatarar se gwaggo itakadai tana karanta magazine .durkusawa yai harkasa toh gwaggo ni xantafi sena dawo kwana uku kawai xanyi insha Allah!</p><p><br /></p><p>Ta kalleshi ba yabo ba fallasa toh sekadawo tadauke kanta .gwiwa asanyaye mahbub yace toh gwaggo baba fa ?kaduba garden inkuma bayanan bansan indayakeba.sakkowayai yanufi garden nan ya hango baba akan garden chairs yana karanta newspaper,yana ganin mahbub murmushin fuskarsa yafadada.</p><p><br /></p><p>Mahbub yadurkusa agaban babansa,baba barka da yamma,yawwa barka kade mahbub Yaya harkagama shirin xaka tafi?eh baba nagama 4 me flight din .to Allah yakaika lapia .tohm baba nagode sena dawo.</p><p><br /></p><p>Driver dinsu yakira nalado kanyai dropping dinsa a airport .karfe 3:40 Dede suka Isa airport yaima nalado sallama sannan yashiga ciki.yana xuwa har anfara boarding mika ticket dinsa yai yashiga ciki 4:00 jirginsu yadaga izuwa lagos.</p><p><br /></p><p>1:30 Dede jirginsu yasauka a airport din lagos,taxi drop yadauka yacema driver din akaishi agege sarumi alawo street.minti 30 dede suka Isa saboda traffic jam din dake garin,sauka yai adede wani duplex din gidah madaidaici,kafin yakarasa kofar gate din har megadin yagano shi ta window yabude kofar saboda hajia(nawwara)tasanar da xuwansa.</p><p><br /></p><p>Yana karasawa kawai shigewa wa yai cikin gidan bayan sungaysa da megadin,kansa tsaye yashiga cikin gidan Wanda kofar shiga tana sadaka da main parlor Dn gdan.sallama yai yashiga ciki ,da gudu nawwara taxo tarungumeshi,kmar su daya dande ita farace ,gaysheshi tai gabadaya murna tacika mata taciki,ya jikinnaki ?Alhamdulillah dasauki. mijintane yataso suka gaysa da mahbub.</p><p><br /></p><p>Bayan sunxaunane mahbub yace a'a Ina twins bangansuba?kabir mijin nawwara yace suntafi Islamiyya tundaxu kwa suke tacewa kaki xuwa Dan meera hadda kukanta neena ce made Batai kukan ba amma fa ranta abace har suka tafi.</p><p><br /></p><p>Nawwara ce taleko daga dinning area to lunch is ready yaya mahbub kaxo Kaci abinci,su ukun suka jeru akan dinning ,simple garnishing dishes tai vegetable rice tai me hanta,se sauce din mushroom da grilled chicken palakash se lemonade .</p><p><br /></p><p>Bayan sungama cin abinci mahbub se yaba girkin yake ga dadi ha cika ciki,Sundade Suna hira kafin yan biyu su dawo meera da neena gwanin sha'awa dasu basufi 5yrs ba .suna xuwa suka rungumeshi uncle M Ina tsarabarmu?tananan my babies xandakko Maku anjima ,Kara rungumesu yai yanaji inama yaransane da fanta tahaifa masa.</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu.........</p><p><br /></p><p>Zaune suke Suna hira bayan sundawo daga kuramo beach,shikuma kabir yafita yaje office Kai wasu files.nawwara take cewa mahbub yaya ni yaushe xaka kawo mana in law dinmune kaga akwai Wata yarinya anan makociyarmu ce inkanaso se in....</p><p><br /></p><p>Kafin takarasa mahbub ya amshe kiyi me?rufamin asiri ni inada matar taxan aura sunanta Fanta she's an orphan a wani kauye take hayin ruga,she's my everything so nake Inna koma gobe insha Allah xanwa baba maganar anemamin aurenta.nawwara tai murmushi Alhamdulillah at long last.</p><p><br /></p><p>Addu'a xaki min kawai kinsan gwaggo tafuso na auri izzatu nikuma nace mata a'a shine take fushi dani for goodness sake mexanyi da ixzy?nawwara ta kyalkyale da Daria gaskia de.nide in anyi fixing date let me know .dandawuri xamuxo insha Allah.</p><p><br /></p><p>SAFIYA TA GARI:</p><p><br /></p><p>safiya nayi bayan mahbub yayi having breakfast exercise yai sannan yai wanka ya masu sallama Wanda dakyar aka bambare yanbiyu dake kukan sesun biyoshi .adole yamusu wayon xedawo yadaukesu sannan yasamu lapia.har airport suka rakashi jirginsu yatashi !!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker✍and Miss Xoxo</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(30~35)</p><p><br /></p><p>jirginsu mahbub yasauka a safiyar ranar asabar bejira kiran driver ba yaxo yadaukeshi danyasan koyakira baxai samu ba.hanxari yai yatsaida taxi yakaishi har gida.begakowa a parlor ba sede masu aiki daketa Kai kawo wajen ganin sun gyara ko ina agidan.</p><p><br /></p><p>Dakinsa yawuce kai tsaye Dan agajiye yake ,wanka yai yabi lapiar gado yakwanta danso yake da sassafe yaje hayin ruga yasanarwa baffanin Fanta abinda ke xuciarsa nagaba da fanta.</p><p><br /></p><p>Safiyar wayewar garin ranar lahadi,mahbub yai wanka yai shirinsa shigar Shadda yaina light golden sannan yasaka hula da takalmi dark golden.</p><p>Indomie yadafa yaci da kwai sannan yadau mukullin mota yafita.hayin ruga yanufa amma kafin yakarasa seda ya tsaya awani store yasai cartons na taliya da lemon roba se lemu da ayaba Dan yasan cimar fulani bata wucce haka.</p><p><br /></p><p>Minti arba'in yai sannan ya Isa kauyen na hayin ruga,ya faka motarsa a'inda yasaba parking.sannan ya'isa kofar gdansu Fanta Wanda yasa almajirai suka tayashi da Kayan,yana xuwa kafin yakarasa gidan wasu yara dake wasa a dakalin kofar gdan suke fadamasa cikin hausarsu wadda bata fita sosai cewar Fanta bata gdan takoma gdan Baffa lado can hayin shanu.nemayai dasu rakashi gidan,nande cikin tafiyar sassarfa suka rakashi rugar ta Baffa lado.</p><p><br /></p><p>Godia yaiwa yaran tare da zaro kudi yamika masu,girgiza Kai sukai tareda doriyar anhanasu karbar abu agida gun wanda basu saniba,yabawa yai kwarai da hankalinsu.sallama yai asauren gidan wata yarinya taleko taga waye ?kice mahbub ne sanin cewar su baffan sunsanshi.komawatai cikin gidah tareda fadawa baffan shikuma yafito hade da bada umarnin shinfida masu tabarma asauran.</p><p><br /></p><p>Bayan sungaysa ne mahbub yasa almajiran suka shigo da kayan suka Saka asauro ,Baffa lado yayi godia sosai haryakewa mahbub wasan ya akai yasan cimarsu ta fulani.mahbub yai dangyaran murya kafin yace Wlhy nima baffa tafiya naine shiyasa banxoba naje Lagos nadubo kanwata datai rashin lapia.</p><p><br /></p><p>Baffa lado yadangutsiri goro aibana kam ana ciwo canjin rani ne,babu komai mahbub Allah deyasaka maka da alkhairi abubuwan dakakeyi.mahbub yace amin baffa,nima de akwai maganar da nakeso miyi dakai idan Kanada lokaci baffa .baffa yawashe baki har inada wani lokaci dayafi yanxu?karkaji komai mahbub fadi komenene karkaji dar dar!yanxu de bari akawomana fura da abinci muci tukun.</p><p><br /></p><p>Fura aka kawo masu damammiya da tuwon dawa miyar kuka dayaji nama ga manshanu ci sukai suka koshi har lokacin sallah yai sukai sannan suka koma suka zaune,Baffa lado yai murmushi to yanxu tunda ciki se ai magana sosai.mahbub yace Baffa kana Hausa kamar bahaushe hakama innah wuro kun iya hausa sosai akan su Baffa Sheri.ehh kam munfisu iyawa dayake ni nafi shekara sama da goma Ina aikin gadi awani gida a habuja(Abuja).itakuma wuro itama ai itada ardo megidanta sunyi zaman bunni,to kaji yadda akai.ohh okay hakane.</p><p><br /></p><p>To dama maganar daxan fadama kashine ehm....Baffa tunsanda nafara ganin Fanta nake Santa,to amma kuma banfadamataba saboda naga da alamin yarinta atattare da ita ,toh sena gayawa innah wuro ko anmata miji?setace Dani a'a ba'ai mata miji ba.amma sede neman auren Fanta ba'a wajenta yakeba yana wajen baffaninta.haka mukai da ita.</p><p><br /></p><p>Baffa lado ya fadada murmushin dayake miji kam ba aima Fanta shiba hasalima yarinyar ita bakula maxan takeba,kuma koda anyi auren da daya daga cikin maxan garinnan batare da anba dangin mijin al'adar da aka Saba yiba to tabbas amaryar xata xama abun nuni kuma gori xeshiga tsakaninta da mijinta.tabbas mahbub naji dadin wannan maganar taka kuma na yaba da hankalinka kwarai dagaske saboda kai Dan mutuncine tunda Kasan mutunci kuma Kanada mutunci .sede inaso Kasan yarinyar nan marainiyace banaso tashiga MATSALAR RAYUWA ,wallahy yadda nakejin Fanta ajinina kamar diyar dana haifa take.sobada haka nabaka auren Fanta katuro magabatanka muyi magana Nima xankira kannena da baffaninta na Uwa.</p><p><br /></p><p>Mahbub dadi yacikashi kamar Wanda akama bushara.gwiwoyi akasa yai godia sannan yamike xe tafi?haryasa Kai xefuta.baffa lado yatsayardashi bari nakira fantan taimaka rakiya ko.nixankarasa can hayi,nagode agaida mutan gidan.sa yaro yai akakira fanta.wadda tafuto sanye cikin hijabi ja.atare suka jera Suna tafiya bayan tatsugunna harkasa tagaisheshi.</p><p><br /></p><p>Mahbub ne yakalleta Fanta jia nadawo daga Lagos nawwara Ma tace tana miki gaisuwa kafin taxo.Allah sarki nagode.</p><p>Munga Kaya ankai shikin gida angode Allah yasaka da alkhairi.</p><p><br /></p><p>Mahbub yakalleta muryarsa Na rawa Dan besan tayaya xefadawa Fanta abinda ke cikin xuciarsa ba nagame da ita.ai munyi magana sosai da Baffa.wato Fanta abunda xanfada maki babu wasa cikinsa ko rainin hankali,nande mahbub yakwashe tunfarkon haduwarsu da ita yadda yaji Santa aransa da yadda sukai magana da innartata dakuma baffa lado.</p><p><br /></p><p>Hawaye Fanta tasoma yi,yanxu xaka iya auren yar kauye dasuke rayuwa cikin bukka?shin xaka iya auren Marar ilimin boko?kaga munashikin MATSALAR RAYUWA!</p><p><br /></p><p>Mahbub yakalleta Wanda idanunsa sunyi ja saboda tsabar bacin ran maganar datai masa..sssh kakki sake yimin irin wannan maganar,yan kauyen ba Allah ne ya hallucesuba ko ko mutan kauyenma basufi na birni cikin kwanciyar hankali ba,ko ko ahadisi akarubuta baxa'a auri mace ba setana ilimin boko?koko kudaine masu MATSALAR RAYUWA???ance maki mu damuke bunnin bamida matsala?</p><p><br /></p><p>Sekuma yasassauta murya cikin sanyi wadda xata dadada mata rai,ke nakeso Fanta ba wai a inda kike RAYUWA ba wannan ba MATSALA tabace,kinada ilimin boko ko baki dashi bashi a lissafina,kuma MATSALAR RAYUWA kowa yanada ita bawanda xece maki RAYUWARSA tana daidai ba MATSALA .so please ke nakeso Fanta dake kadai nakeso inyi RAYUWA har karshen xamana adunia.kitsaida hawayen nan naki Dan Allah inba sokike Nima nafara ba ,inkwa harkinaci gaba da kuka to wallahy Nima kukan xanyi!</p><p><br /></p><p>Da wannan yasamu ya lallasheta tareda fada mata da dadan kalamai masu sanyaya zucia.ahaka sukai sallama haryake cemata acikin satinnan xeturo iyayensa suyi maganar aurensu da baffaninta.yana murmushi yana tuki harya Isa gida dadi yakeji na shima yakuma futa daga bachelor xe more Rayuwarsa in har ya'auri fanta!!!!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>To ko gwaggo xata yadda da wannan sabon al'amari????</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker✍and Miss Xoxo</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(35~40)</p><p><br /></p><p>Bayan mahbub ya Isa gidah dr haydar yakira yake fadamasa baffan fanta yabashi damar neman auren Fanta kan yaturo magabatansa asa ranar aure,dr haydar yatayashi murna kuma yananan tafe shima dashi za'ai komai.</p><p><br /></p><p>Bayan mahbub yagama waya da dr haydar watsa ruwa yayi yadauro alwala yai sallah,tare da addu'ar Allah yabashi nasara akan abinda xefadawa babansa yanxu.shafawa yai sannan yamike yanufi parlor din babannasu dake sama tare yake da yar anacinsa gwaggo agefe ,shiga yai da sallama yaiwa baban barkada yammaci shida gwaggo sannan yanemi guri yaxauna akasa kusa da babannasa.</p><p><br /></p><p>Mahbub yasaukar da kansa kasa baba magana dama xangaya maka.kafin alh sulayman ya amsa gwaggo harta warce to waye bare anan gurin?da har inxaka fadi magana sekanayi kana wani sunkuyar dakai kamar munafiki wani feleke wai baba xanmaka magana.shide mahbub kawai kallon ta yai yakalli baban Wanda dakyar ya iyacewa inajinka mahbub ya akai?</p><p><br /></p><p>Baba dama Kasan tunsadda Mami tarasu kace na nemo matar aure nace maka bansamu ba tukun.to Allah cikin ikonsa de yanxu naga wadda nakeso kuma marainiyace de amma kafin mahaifiyarta tarasu ta amince ta yadda dani dayake fulanine to Neman aurenta yakoma wajen baffanninta kuma dayake sunsanni saboda munsaba dasu sanadiyar zaman makokin mahaifiyarta.to jiya naje canwurin baffan ta kanin babanta ne toshine yabani damar inturo magabatana ayi maganar aure.</p><p><br /></p><p>Dafe kirji gwaggo tai,aure???au Neman aure kajeyi batare da saninmuba?to wallahy Baka isa ba,naga namaka maganar izzatu shine hadda wanicemin Kai aure baya schedule dnka,to wallahy Baka Isa ba lalle kanunamin niban isa dakai ba kenan bani nahaifekaba *seta fashe dakukan munafunci*nande alh sulayman yarude yataso yana bata hakuri,Kai mahbub tashi kaje kasa naji abinda kace xanyi tunani akai.dakyar mahbub yatashi da sanyayyar tafiyarsa dawani abudaya tsaya masa awuya amma lalle gwaggo tacika makira bakomi Allah shine shahidi...,</p><p><br /></p><p>*******</p><p><br /></p><p>Kwana daya,biyu,uku,suka wuce alh sulayman benemi mahbub ba,gashi harwani Rama yake saboda rashin sanin inda xancen yakwana,nande yayanke shawarar samin wan babansa Wanda suke cema uncle rufa'i shima awata unguwa yake can kasansu da akecema ambassadors street.</p><p><br /></p><p>Wanka yai yafito sukai kicibis da gwaggo yatsugunna harkasa yagaisheta tadauke kanta kamar bango tagani.bedamuba rakabawa yai tagefanta yawuce bedamu da tambayarta mukullin mota ba danbaxata bayarba,keke napep yatarar yace ambassadors street aka kaishi yasauka yashiga gidan ,gidane flat (bungalow) mekyau dashi.</p><p><br /></p><p>Ya shiga da sallamarsa parlor ne Wanda xesadaka da kofa amsawa akai sannan yashiga xaune suke uncle rufa'i da matarsa da akecema Ammi laila.gayshesu yai sannan yaxauna.sekwa Ammi Laila tafara Mai wasa lalle farin Wata sha kallo ,yau mahbub ne agidan maraba da mutan cyprus ,captain dakansa,shide mahbub murmushi yai ,uncle rufa'i yace a'a aikwa mahbub yanada xumunci dade dayar ja'irar ce data gudu Lagos sede waya kullum.nande Ammi Laila tatashi takawo masa snacks da milkshake na vanilla sannan tanufi Bari inje in wanka .</p><p><br /></p><p>Mahbub yadan gyara xama uncle wajenka naxo,uncle rufa'i yadan gyara Karin hularsa to to inajinka...wato uncle dama baba yadade yanacemin innemo aure tun Mami naraye to Bayan rasuwarta Ma yakumamin xancen to alokacinde gaskia bansamu wacce nakesoba.to Allah da ikonsa Mina xuwa kauyen hayin rugar fulani saro nono na barnyardfresh factory to anande nahadu da Wata yarinya bafulatana hakade mukasaba muna sarar nono .marainiyace saboda senasami baffan ta kan maganar Seya amincemin Dana turo magabatana.</p><p><br /></p><p>To sena sami baba inaso mi maganar to tare suke da gwaggo.nadanyi jinkiri kan nasanar masa amma gwaggwo tatakura kanse nafada ba bare agurin.nande nafadi komai,wallahy uncle kafin baba yabani amsa gwaggo takarbe wai wallahy ban isaba baxanyi aurenba tunda naki auren kanwarta izzatu kuma wai bandauketa uwaba nande tasa kuka ,hartasa baba kamar yai fushi Dani yakecemin wai naje xe nemeni to wallahy uncle xancen da nake fadamaka yau kwana 3 kenan kuma bansake sa baba a'idonaba.kuma ita izzatun datakeso sena aura wallahy uncle yarinyar batada hali duk wani joint se ance yana gurin hakama night parties .</p><p><br /></p><p>Uncle rufa'i yajinjina Kai xancen banxa kenan wallahy sulaiman yabani mamaki wannan banzar matar tashanyeshi tamaidashi kamar wani waina,wacece kuma izzatu data like seka aureta?wallahy tayi Kadan tatsoma baki amaganar aurenka tunda itan batajan girmanta .kayi hakuri mahbub insha Allah nixanshige maka Bari xankira uncles Dinka anjima su tajuddeen duk xamuje can hayin rugar mune mamaka auren katabbar de kintsattsiyace ko?</p><p><br /></p><p>Mahbub yace eh uncle yarinyacema 14 nakega xatayi,uncle rufa'i yawashe baki oh ashema yarinyace to Allah yaxabi abinda yafi alkairi yasanya albarka aciki kakka damu .yanxude bari nakira Ammi Lailan taimana serving abinci muci xuwa anjima inka huta seka tafi.kuma muxamu nema maka auren batare da sanin daya dagacikinsu ba shi sulaiman da gwaggon.</p><p><br /></p><p>Mahbub yai godia sannan yakoma kan sofa yakwanta tare da daukar milkshake yana sha....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker✍and Miss Xoxo</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(40~45)</p><p><br /></p><p>BAYAN KWANA 2~</p><p><br /></p><p>Zungureriyar mota kirar siena ce uncle rufa'i ,uncle tajudden da uncle sameer Wanda akecemasa uncle sam,se dr haydar da mahbub Wanda ke agaba titin kauyen hayin ruga suka nufa bisa jagorancin mahbub tundashi yasan gidan ,a gefen rugar sukai parking sannan sukatafi gidan akasa saboda mota bata shiga ciki.</p><p><br /></p><p>Hayin shanu gidan na Baffa lado suka tsaya inda mahbub yatura yaro akira baffan dukda cewar yasanar masa daxuwan nasu .ba ajima ba baffan yafito daga cikin gidan tareda sauran baffanin nafanta su uku,bayan sunyi musu jabbama jabbama,atare suka jera suka nufi Wata bukka da akatanade danyin taro kowani meeting .</p><p><br /></p><p>Xama sukai gaba dayansu su bakwai Banda mahbub dayakoma mota bisa umarnin uncle sam,gaggaysawa sukai sannan Baffa lado yasa aka kawo masu abin motsa baki kamarde cikin birni lafiyayyar fura da nono aka kawo da soyayyun kaji se abinci damiyar zabi ga lemo da ruwan roba seda sukaci sukai nak dasu sannan uncle rufa'i yafara magana.</p><p><br /></p><p>Mungode kwarai da wannan hidima da aka nuna mana,Allah yasaka maku da mafificin alkhairi amin.to abunda yakawomu wannan ruga taku me albarka munxone nemawa mahbub auren diyarku fatma bintu.muna neman yardarku bisa hakan.</p><p> Baffa lado yace to Masha Allahu naji dadi kwarai kuma ubangiji Allah yamasu albarka dukkansu,aure kam baxancen hanaku tunda wa'innan yara sundedeta kansu,kuma koda yarinyarnan batasansa tabbas xanbaiwa mahbub ita saboda nayaba da hankalinsa gashi kuma yafito daga xuri'ar gdan mutunci.wallahy nabaku auren fanta babu matsala wallahy,fatanade ubangiji Allah yasanya alkhairi kuma Allah yakaresu daga dukkanin sharrin MATSALAR RAYUWA.yajuya yakalli baffa jaure ko xaka kara wani abin akai?baffa jaure yace a'a duk abunda xanfada kariga kafada dabo (yaya)Allah yasa alkhairi.</p><p><br /></p><p>Uncle rufa'i yace Masha Allahu mungode kwarai dagaske yanxu xamu bada kudin nagani inaso ne koyaxa'ai?baffa jaure yace ehh tohm mude al'adar rugarnan damuka tashi mukaga anayi tun kaka da kakanni shine maimakon kudin dakuke bayarwa munan anabawa diyar da akeso sa da saniya guda biyu kawai sannan ba a baiwa iyayenta sede baffanta shine xekula dasu yana basu abinci ,abincin dayake basu shine gudunmawar baffan,shixeta kiwonsu harse saniyar tahaifi yaya 10 sannan xemaidawa yarinyar wannan dukiya tata.</p><p><br /></p><p>Uncle tajuddeen yace toh yanxu shanun xamu siyo mukawo ko kwa kudi xamu bayar se asiya?baffa lawunde yace eh to duk Wanda kuka bayar yayi.nande akai kudin shanun biyu aka dankawa Baffa jaure saboda yanasaida shanu kuma yana kiwonsu.</p><p><br /></p><p>Uncle rufa'i yace toh yanxu munasan mutsaida ranar daurin aure dan mude kam wajenmu ba matsala ashirye muke yanada gida kuma yanada aikinyi.baffa lado yace eh muma ashiryen muke amma kuma akwai biki da ake na kwana 7 na al'adah xakuganshi bannarakwai bakamar wanda ake abirni ba:1-anayin ranar ice wadda amarya da babbar kawai da kawaye xasu shiga jeji suyo icen daxa'ai amfani dashi har agama biki,</p><p>2-akwai ranar rawar shadi Wanda abokan ango xasuyi shadi ammafa nawasa.uncle rufa'i yaidaria yakalli dr haydar tokai seka shirya kaga kuma akwai ranarku,Baffa lado yace kwarai kuwa sannan akwai</p><p>3-gasar tatsar itama anayi arana ta uku inda kawayen amarya xasuyi gasar tatso nono wadda taruga cika bokitinta to xa'a bata bijimin sa kyauta.sannan akwai</p><p>4-ranar bakin rafi inda xa'akira makida na fulani nan Samari da yammata xasi fati (party).</p><p>5-sannan akwai gada daxa'ai akofar gidan megari da yamma.</p><p>6-itace ranar daxa'ai walima xa'akira malamai suyi wa'azi.</p><p>7-Rana ta akwai itace ranar daxa'a daura aure.to kunji yadda abun yake.</p><p><br /></p><p>Uncle rufa'i ya washe baki kace xamu sha biki ubangiji Allah yakaymu.yanxu sati biyu yayi?baffa lado yace yayi Allah yakaymu lokacin,nande sukacigaba da hira yadda kasan sunyi shekaru da sanin junansu.uncle tajudden yace haydar kira mahbub kace mungama yaxo su gaysa muxamu wuce tohm uncle.</p><p><br /></p><p>Dr haydar yafita yana hangowa koxe ga mahbub,canyahango su shida Fanta akasa karkashin wata bishiyar dogon yaro,mahbub yanaganin dr haydar yamike tsaye ya aboki antsayar?haydar yakyalkyale da daria calm down aboki sekace kaixaka daurawa kanka auren ..yakalli Fanta amaryarmu yakike?kunsan fulani dakunya tasa hannunta dayasha lalle tarufe fuskarta inayini dakta anxo lapia?lapia qalau amaryarmu dan nanda sati biyu kinxama amaryar wannan senior bachelor din yakalli mahbub.</p><p><br /></p><p>Itade murmushi tai,shikwa mahbub dadi kasheshi,Alhamdulillah ya Allah at long last.dr haydar yai Daria to inkagama addu'ar da godiar kaje kagaidasu baffan danxamu wuce yanxu nina koma ciki,mahbub yakalli Fanta .fatma na kinji aurenmu nanda sati biyu ne,xakixama matata Allah nagode maka yakalli Fanta kebaxaki addu'a ba itade murmushi tai yakalleta xaki daina wannan kunyarne very soon.sallama yamata sannan yawuce bukkar dasu baffan suke.</p><p><br /></p><p>Yana xuwa yatsugunna harkasa yagayshesu ,wasa da raha sukai dasu baffan sannan suka tashi tafiya ,akakira Fanta tagayshesu ita axuciarta take fadin lalle so shu'umine jibi iyayen mahbub gakyau gakudi ga asali itade kam tagodewa Allah bisa wannan babbar kyauta dayayi mata sannan tanufi gida.</p><p><br /></p><p>Har sunshiga mota aka biyosu da irin katin katin karkaji cike da nono jarka bakwai hade da fura kulli dayawa acikin irin ledojinnan masu baki da yalo (black and yellow)da zabi da kaji dayawa,godia suka masu na wannan kabakin kyauta dasuka basu.sannan suka ja mota suka tafi!</p><p> Har suka Isa gidah suna maganar karbar arzikin dasuka masu tabbas Fanta tatafito daga cikin gidan dattako .mahbub yamusu godia shida dr haydar sannan suka tafi.har gidah mahbub yaraka dr haydar tareda Kara masa godia,shikwa dr haydar cayai shine da godia wannan kabakin arxikin dasuka kwaso na Nono da kaji da zabi .</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker✍and Miss Xoxo</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(45~50)</p><p><br /></p><p>Ana saura sati daya biki,Ammi laila da nawwara da sauran auntys din mahbub matansu tajudden aunty nafeesa da aunty halima da abokan arxiki sukaje hayin ruga Kai lefe akwati saiti biyu Shake da kaya yan gaske tabbas sunsamu tarba suma saboda ammusu cima Iri iri ankuma basu sa da saniya manyan gaske da kudi dubu dari amatsayin tukwici tabbas sunyaba kuma sun Amina da Fanta amatsayin yar Uwa.</p><p><br /></p><p>Akwana atashi bawuya tsantsar soyaiya mahbub yakewa fanta to ita dinma hakane a wajenta dakyar suke rabuwa kamar wasu Romeo nd Juliet tabbas Suna Bawa soyaiya hakkinta kamar wasu larabawa abinde gwanin sha'awa biki yana dada matsowa dakansa yadauki fanta yakaita spa aka gyara mata jiki sannan akaimata steaming hade da strethening gashin,biki yarage saura kwana biyu yakaita gun lalle akaimata shi both ja da baki,Fanta de tafuto kamar Wata yar Ethiopia abinse yaxama tubarkAllah masha Allah.</p><p><br /></p><p>Ana I jibi daurin auren uncle rufa'i dakansa shida mahbub sukaje wajen alh sulaiman yana parlor dnsa nasama shida manne masa gwaggo,uncle rufa'i yaxauna bayan sungaysa da alh sulaiman da gwaggo wadda ke aikamasa da sakon harara,shiko mahbub tsakarewa yai waje daya kamar wani bako.Uncle rufa'i yace sulaiman tunda kaga naxo dakaina amatsayina na wanka magana naxo muyi kuma gaskia matarka seta Bamu wuri saboda maganace wadda tashafi xumunci idan kuma baxata tashiba to ni xantashi natafi kuma duk abunda yabiyo baya kada kaxargi kowa se kanka.</p><p><br /></p><p>Alh sulaiman yakalli gwaggo wadda tabudi baki xata mayarmasa yagirgixa mata kai,tashi kije.tashi tai tsaye kerere naji xanfita amma kasani duk abunda xaka fadamai kmar naji ne ,kuma nagane Kunamin hakane saboda bana haihuwa ai Allah be mebayarwa.Uncle rufa'i yakalleta ya girgixa kai yafada miki mana babu abinda de xaki iya akai tunda bakya wurin aka fada sannan inke jahilace niba jahili bane haihuwa ai awurin Allah take shike bayarwa kuma shike hanawa,dauke kanta tai tafice fuuu kamar iska jan kofa tai amma talabe tana sauraron mexasuce!</p><p><br /></p><p>Tana futa Alh sulaiman ya dawo kasa yatsugunna yaya Dan Allah kayi hakuri.uncle rufa'i yagirgixa Kai bakomai ai kawaide bakai sa'ar mata bane.abunda yakawoni shine kwanakin baya mahbub yaxo nan yana maka magana kan Neman auren yarinya dayakeso,matarka tayi kane kane tahana kace masa xaka nemeshi amma bakanemeshi ba ,saboda yasan na Isa shiyasa yaje yasameni nakuma share masa kukansa mukaje muka nemamasa auren nida sameer da tajuddeen muka samesu gidan mutunci da karamci sunkarbemu hannu biyu yadda Kasan munyi shekara da sanin juna!</p><p><br /></p><p>Yanxu de intakaice maka xance muka xaune muka sa ranar aure sati biyu a wannan lokaci kenan sannan sati daya za'ai Ana bikin dayake fulanine acan kauyen hayin ruga nan karamar hukamar Anka to yanxu de jibi ne daurin aure abinda yasa kuma banyi saurin fadamakaba saboda nasan na isane nine nabada kudin nagani inaso dukda sa da saniya suka bukata amatsayin yadda al'adar su take.kuma munhada kudi nidasu tajudden munhada lefe ankai kuma dr haydar abokin mahbub gashinan shine yabuga katin daurin aure dama sauran events din daxa'ai dukda bayan ankawo amarya abokan ango sunhada masu dinner.yanxu gashinan katittinan munrabawa yan'uwa yanxu abokanka xaka rabawa.kokanada abun cewa?</p><p><br /></p><p>Alh sulaiman ya girgixa Kai Banda abinda xance Yaya se Allah yasanya alkairi kwarai ai mahbub dankane kanada damar kasashi abunda kaga dama ,shiyasa nawwara tacemin taxo amma tana kaduna duba kanin mijinta amma xata iso yau.yanxu jibi asabar daurin auren kenan?Uncle rufa'i yace kwarai kuwa .</p><p><br /></p><p>Nande suka shiga hirarsu ta xumunci su ukun harda mahbub.....,gwaggo tana labe tagamajin duk abunda suke cewa wani gumi ne yaketo mata yanxu jibi ne daurin auren mahbub?to wallahy basu Isa inko hakan tafaru to wallahy matar seta gwammace bata aureshi ba dansetasan yadda tai tasata a MATSALAR RAYUWA!amma Bari taji mexeje yadawo agurin bokanta bokan Wanda akema lakabi da xokaji aiki.mota tadauka tafice izuwa wani kungurmin daji tashiga ciki tafi minti 30 sannan yamata ixini tashiga xaune yake duk jikinsa wani dige digen ja .shiga tai da sallamarta,tsawa yamata ke mantawa kikai ba a mana sallama anan?ke kanki kinsan sabon Allah muke anan yaxa'ai kimana sallama.jiki narawa tabashi hakuri meyakawoki???</p><p><br /></p><p>Dama xuwanai gurinka kan wannan yaran danwajen mijina mahbub,Ashe wai yau daurin aurensa saura kwana biyu kenan .wan mijina rufa'i shine yakarfafawa yaran gwiwa yasai kudin auren akai komai na shirye shirye yanxu de kawai so nake ahana auren .bokan yasa hannunsa awani kofi ya ajiye yagirgixa kansa baxan iya Hana auren ba saboda yarinyar da yaron sunada karfin addu'a,gwaggo ta narke fuska yanxu baxaka iya komai akaiba?bokan yasake xubarda ruwan kofin yaxuba wani gaskia baniba bawani bokan daya Isa yaraba wannan auren.to yanxu yaxa'ai kenan?abinda za'ai shine kakki bari su tare awani gidan face Wanda kike acikinsa,sannan kakki Bari Wata auratayyar tashiga tsakaninsu,tahaka xansan yadda xanyi daga karshe naraba auren...toh boka mexan bayar na aiki???yai Wata bazawar Daria ladan aikin aikema kinsani !</p><p><br /></p><p>Gwaggo ta gwalalo ido boka da aurena da yanxu,yakalleta yawurga mata harara keyanzu harkiran kanki kike da matar aure ?to inde baki bani hadin kaiba togaskia babu abunda xan iyayi maki.daga kaitai sama alamar toh sannan suka nufi wani daki se bayan awa daya darabi tafito da alama taci wahala dakyar ta iya buda Motar taja tatafi!!!!!</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafe[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(50~55)</p><p><br /></p><p>Afuwan,a previous page munmanta bamu bada yadda aka gudanar da al'adar bikinsu Fanta da mahbub ba.nawwara da cousins dinta mata ya'yansu uncle rufa'i tun ranar da akafarada ranar ice sukaje kauyen na hayin ruga kuma kwana sukai basu kyamaci al'adar ba sema burgewa da abin yabasu dansu safa da marwa ya'yan uncle tajudden har participating sukai aranar bakin rafi.marwa itace Kewa Fanta kwalliya irinta concealing dinnan .</p><p><br /></p><p>Aranar daurin aure kuma itace ranar daxa'ai English dinner wadda friends din ango suka hadawa ango da amarya ,Wata dandatsetsan lace tasa me ratsin fari da blue sannan aka nannada mata abaya blue da takalminta lowhill shima blue gurin Baffa lado aka akaita yamata nasiha bisa jagorancin babbar kawarta salah wadda itama tayi kwalliyarta abunde se Wanda yagani!</p><p><br /></p><p>Baffa lado yadago yakalleta kirike mutuncinki amatsayinki na marainiya,babu ruwanki da irin kishinnan na faccaloli,inayi bari na bari,kakki shiga abunda ba ahada dakeba,kiyiwa mijinki biyayya kakki tauyemasa hakkinsa na aure domin mala'ikun Allah sunkasance Suna tsinewa matar datai haka,kika sance me tsafta,addu'a da kawaici kibi uwar mijinki sau da kafa taxamo abokiyar shawararki in hakan ta kama 🤔.Allah yamiki albarka Fatima bintu kibi mijinki sau da kafa Allah yasa aurennan shine karshen MATSALAR RAYUWARKI !</p><p><br /></p><p>Nande Fanta ta barke da wani sabon shafin kukan Baffa kayafemin ,Baffa lado yagoge hawayen dayaxubomai ba'abinda kikamin Fanta Allah yayafemana baki dayanmu,salah kamala kuje Kunga yan daukar amaryar karsu gaji da jira,muma in an kwana biyu xamuxo tunda innarki lantana tasani.kamata salah tai sannan suka nufi waje se guda ake gari yadauka da Fanta xata tafi binni tabbas ilu yaciji hannu yayi rashin budurwar da aka kasashi....,,</p><p><br /></p><p>Motocine fadar adadinsu seyaxama kauyanci xungureriyar mota kirar hummer jeep itace tatsaya har wurin amarya Fanta ,Ammi Layla matar uncle rufa'i da matar uncle tajuddeen sune suka Kama Fanta suka sata aciki kujerun gabansu kuwa matar uncle sameer ce da nawwara da yanbiyunta se kujerar gaba kuma salah ce.sauran motocin kuwa relatives ne na ango da amarya motoci suka ja daga kauyen hayin ruga xuwa ga unguwar da mahbub yai gida anacemata one in town street gidane duplex daki uku da parlor biyu Dede gwargwado anwa Fanta Kayan daki har daki biyu da parlor daya ko hasidin iza hasada baxe kushe gdanba,shikuma mahbub yagyara sauran daki dayan da da parlor .</p><p><br /></p><p>Misalin karfe 6 aka dakko amarya 6:50 nayamma suka iso ,direct gidan amarya suka nufa Dan da akace xa'akai amarya gurin gwaggo setace ace batanan kome gwaggon tashirya?????sassaskowa sukai aka shiga gdan amarya tabbas gidan yabirge kowa se santinsa ake dankomai nadayan parlor dn purple ne dark da creamwhite,dr haydar ne yabugowa nawwara waya kansu shirya amarya bayan sallar isha'i xa a tafi dinner!!!</p><p><br /></p><p>Ana idar da sallar isha'i nawwara tafara shirya Fanta cikin wani irin hadaddiyar gown yanajan kasa red ce rigar da dishi dishin baki se aka aka nannada mata mayafin rigar shima baki ga clutch bag baka da hill takalmi ga kwalliya kamar mekyaj fandy cetamata hancinnan anyi blending yakara futowa,tabbas inkakalleta seka Kara kallanta tayi kyau (dankoni seda nakara goge medicated glass Dina kode daydreaming nake)nawwara takoyamata irin tafiyar daxatai ,to shima tabangaren angode Kyau nake yake gudana ango yasha kamshi cikin yadi baki da hularsa Baka me ratsin baki.</p><p><br /></p><p>Karfe 8:30 dede ango da abokansa sukaxo daukar amarya da yan Uwa xuwa taron dinner da akatanade shi awani tanfatsetsen hall da ake gudanar da sha'ani kamar suna,biki da taro na meeting da sauransu.fanta nafutowa daga gate xata shiga motar da aka tanada musu itada mahbub .daga mahbub har abokansa daskarewa sukai atsaye wannan Kyau haka,mahbub kwaharda hadiyar yawu tabbas fanta tayi wani irin Kyau mewahalar misaltuwa,baya mahbub yabude mata tashiga motar kirar marcedez Benz sannan yakoma yashiga tadayan gefen .dr haydar neke driving se salah agaba Dan matarsa taso xuwa amma laulayi take!kasa hakuri mahbub yai yajuya yakalli Fanta wadda kanta akasa Kunya takeji yace Fanta itade uhm tace masa hannunsa yasa acikinnata yana murxawa wani shock yaji first time in history kasa jurewa tai tajanye hannunt ahankali Dan inyaci gaba komai xe iya faruwa,murmushi yai sannan yadauke kansa.</p><p><br /></p><p>Kaitsaye motocin suka nufi wani guri mesuna Grand Couples Hall. a convoy motocin suka shiga ,seda kowa yashiga sannan couples din suka shiga tashi akai tsaye Ana musu tafi,ixzy sakin baki tai garin gulma taga kota Ina Fanta tayi bamakusa,cije lebe tai agaskia gwaggo zancen gwaggo kokusa beyi shiga da abunda tace Akan Fanta ba,lalle mahbub yayi dace amma dole gwaggo tasan meyiwuwa taraba mahbub da Fanta.xama tai taxama yar kallo.bayan mc yayi bayani anbude taro da addu'a .kiran dr haydar yai yabada biography din ango se nawwara tabada na amarya amma duk aharshen turanci.se akadanyi refreshment da abinci da lemu friends sukadanyi rawa amma ba liki tunda English dinner ce,sannan suka yanka cake akai toast to d couples sannan akai jawabin tashi bayan anbi kowa dakatuwar jaka ta rabo.</p><p><br /></p><p>Shiga mota sukai straight aka nufi gidan mahbub amma kash ango badama ya kebe da amaryarsa Dan al'adarsuce dole se yanuwanta sunkwana daya agidan.sauran auntys dinsa nabangaren maminsa sukawuce guest house din da akatanadar masu.adaddafe mahbub yaiwa Fanta sallama sannan dr haydar yaja sukatafi ,amota dr haydar yakalli mahbub aboki sewani hade rai kake naga aida haka kake kwana ko?mahbub ya harareshi aboki baxaka ganeba bakasan yadda nakejibane nide kawai Kai dropping dina agidah dama ga sakon gwaggo ammi Laila tace nabata,sunatafe haydar yana tsokanarsa haryasauke shi sannan yawuce gidansa!!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anker✍And Miss Xoxo</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(55~60)</p><p><br /></p><p>Lokacin da mahbub yakoma gidah yatarar babansa yana kallon news amma gwaggo batanan shidakansa yayi mamakin rashin ganinta dayai,xuwa yai yatsugunna har kasa baba barka da dare ,yawwa barkamude mahbub.yaya kabarmasu yarinya dawannan Daren kataho gida yanxu kokamanta kaidin magidanci ne yanxu?kakkamanta yanxu kaidin kagirma Kanada iyali dasuke bukatarka akusa.</p><p><br /></p><p>Mahbub yasunkuyar dakansa kasa baba bamantawa naiba candin tare suke da yan uwanta,al'adarsuce insun aurar da diyarsu to sunayin kwana daya agunta,ynxu haka su nawwara dasu marwa suna can wurinta..</p><p><br /></p><p>Alh sulaiman ya murmusa ohkay Allah yatemaka fulani dama akwai xumunci ,kaje dinning ha abinci nan nasan rabonka da abinci kila tunsafe kaci seka kwanta,Allah yasanya albarka awannan auren yabada xuri'a dayyibah.shikam mahbub kunya yaji da baba yace haka ahankali yace amiin!baba Ina gwaggo dukyau bangantaba?</p><p>Tacemin tafita dubo Hajia ateeka kawarta to tundaxunde batadawoba yanxu haka inaga tana hanyar dawowa.oh okay ,Bari inci abincin inkwanta seda safe baba,to Allah ya tashemu lapia.....dibar abincin yai sannan yasauka kasa dakinsa.</p><p><br /></p><p>******</p><p>Gwaggo nagano tare da ixzy agidansu ixzy ,ixzy tacika fam kamar xata fashe nigaskia gwaggo kisamo mafita ni wallahy mahbub nakeso damacan kinasane kikawani cemin wani wai yarinyar batahaduba yarkauyece ko karatu bataiba sekagashi danaje dinner Wlhy gwaggo duk family dinmu bawanda yakamo ko farcenta akyau ,ni gaskia kisamo mafita shi boka xokaji aikin naga yafada miki abinda xaki amma gwaggo kamar basirarki tatoshe nigaskia gwaggo kawai kijefa yarinyarnan a MATSALAR RAYUWA ta yadda mahbub xerabu da ita yadawo wurina.</p><p><br /></p><p>Gwaggo tadan tsaya tana tunani Aini solution kawai nake nema daxan dauke sha'awar mahbub akan Fanta amma how?ninasan yadda xanyi tunda sena hada da makirci sauran aiki kuwa boka ne xekarasheshi ,shima can daya mugun wai baxe amshi ladan aiki ba sede kabashi kanka Wlhy bakiji rannan gashi doyi yake kamar jaba seda nai wanka sau uku turare kuwa kusan karar dashi nai ajikina dakyar nadena warin wlhy,ixzy tadunga daria aini canake masa seyayi wanka tukunna yatsaftace jikinsa😱gwaggo tabata hannu suka tafa lalle kinfadamin mafita,(Allah yashiryemu shirin addininin musulunci).yanxu de Bari natashi natafi xakiji yadda akeci ta waya seda safe.taiwa ixzy sallama takoma gidah.</p><p><br /></p><p>Gwaggo nashiga gidah tatarar da Alh sulaiman a parlor,ya mata kallon tuhuma seyanxu kika dawo ?hatta bude baki xata gayamai Baka seta fasa saboda makircin datake shirin hadawa,kayi hakuri jikin Hajia ateekanne badadi seda naxauna nabata abinci nagyare mata gidan tsaf sannan nalallabata tai bacci kasan yan uwan sunkoma bauchi jia.kallonta shide kam azuciarsa beyadda ba amma yaya iya da gwaggo adole yahakura,au namnta mahbub yaxo yana tambayarki nace bakyanan,gwaggo ranta yai fari kal to yanxu yatafine koyaya?aa yana dakinsa kasa kinsan fulani da al'adar wai yan uwanta se sun kwana agunta sannan sesu tafi gobe,Dadi yakama gwaggo Allah sarki da safen magaysa dashi su mahbub ango aiyanxu yakai england a bacci!</p><p><br /></p><p>SAFIYA TA GARI:</p><p><br /></p><p>Safiya nayi mahbub yai wanka yadakko sabuwar Shadda fara kal yasa da takalminsa baki hade da hula harda agogo.yagama shiryawarsa tsaf sannan yafito da sauri dandora koda indomie ce yaci tunda yasan babashi za'aiba jia Ma baba ne yabashi danda gwaggo nanan baxata bariba.yana futowa yahango gwaggo tana jera abinci a dinning area komawa yai ciki yadakko jakar shake da kaya da Ammi Laila tace yabama gwaggon sannan yafito .</p><p><br /></p><p>Gwaggo Ina kwana?yaukam su gwaggo dayake anshirya makirci haddasu fara'arta a'a ango kasha kamshi lapia qalau mahbub ankwana lapia?🙆shikam mahbub ganin abinyai banbarakwai wai gada aranar sallah .seyake ganin tayi hakanne saboda yayi aure yabarmata gidan ita kadai..lapia qalau gwaggo.yamika mata Leda gashi Ammi Laila tace nabaki ,gwaggo tadabe baki su Layla hadda wahala aidama tabasshi Wlhy nagani awajen izzatu ma jakar tayi Kyau Wlhy amma nagode.ai naso ace jia inanan mugaysa da amaryar ai tojikin ateeka kawata badadi acan nawuni ..Allah de yasanya alkhairi.(chaii gwaggo kamar gaske).</p><p><br /></p><p>Mahbub yakalleta da mamaki ,ai xankawota anjima kugaysa ,gwaggo tadashe baki kamar gonar auduga😃dako ka kyauta .shide mahbub mikewa yaihanyar kitchen Yadora indomie .takirashi xo mahbub ga breakfast nan nayi Akan dinning aiyanxu girki seka xaba kaje Kai serving kanka. jiyai abin kamar amafarki ahankali ya Isa dinning yaxauna yabude foodflask kusan kala biyar kowanne yabude yadakko plate yaxuba chips da soyayyar doya da daffaffen Kwai se soup din hanta da naman kaxa ,da waffles agefe da yamballs,coffee yahada yai bismillah yafaraci itakuma gwaggo tahau sama.</p><p><br /></p><p>Yana cikinci yama kusa cinyewa su nawwara suka shigo itadasu marwa,suka fara tsokanarsa ango ango kasha kamshi,kallonsu yai yai murmushi bismillah ha abinci,uhm uhm akoshe miki Ina gwaggon ??tana sama.nawwara taja kujerar kusa dashi taxauna nifa tafiya xami yanxu???haba tunyau?wlhy kasan brother din kabir ba lapia to xamubiya ta kd xami 2 days semu wuce Lagos saboda su safa da marwa xasi holiday agidanah.okay Allah yabashi lapia ,kukuma Allah yakaiku lapia...kunyi sallama da fanta?eh munyi wallahy gaskia yaya itada yan uwanta sunada kirki kafin mutashi da safe harsungama mana breakfast kuma kaga tabamu cosmetics dayawa tabawa neena da meera ribbons kala kala,yanxu Ma munbar relatives dinta sunashiri xasu tafi..ah haba ?bari inje mugaysa kafinsu tafi,itama xankawota nan sugaysa dasu gwaggo</p><p><br /></p><p>Ana haka seka gwaggo suka sakko daga stairs itadasu safa,shine ke baki hawoba,nawwara tai murmushi Wlhy gwaggo yanxu nakeson hawowa natsaya mungaysa da yaya ne.ina kwana?lapia qalau nawwara.yagajiyar biki?tabi lapia.ina baba?yanxu xesakko !</p><p><br /></p><p>Sundan jima suna hira har baba yasakko sannan su nawwara sukai masu sallama suka tafi,shima mahbub fitar yai xeyi sallama da yan uwan Fanta yakuma dakko fantar tagayda su baba......😱 </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anka and Miss Xoxo</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(60~65)</p><p><br /></p><p>Yana futa yadau motarsa yanufi gidansa bayan yatsaya a wani store yasai cartons din taliya dayawa da lemu da irin yoghurt dinnan freshyo se biscuit saboda yara .yana xuwa bayan yayi parking shiga gidan yai zaune yaga fantar da yanuwanta da alama sallama sukeyi.fantar tayi Kyau abinka dafarar mace hausawa sukace alkyabbar mata...sanye take tasa Jan material meratsin fari tayi Kyau sosai dinkin ya amshi jikinta dede gwargwado yana Isa parlor din yan uwanta suka fara Mai maraba jabbama jabbama awari jam?jam kalau.</p><p><br /></p><p>Sunkuyawa Fanta tai tagaysheshi bata yadda sunhada ido ba saboda girmansa da kuma kunyarsa datakeji.inna lantana tagyara mayafinta dama tundaxu xamu tafi nawwara takecewa mubari kaxo mi sallama tunda kaxo mubari mutafi mungode mungode Allah yasanya alkhairi.suka futa waje .nan motocin buses suka kwashesu bayan mahbub yacikasu da provisions dn dayasiyo dakuma kudi,Fanta tayi kuka sosai dakyar aka banbare salah ajikinta.</p><p><br /></p><p>dakyar mahbub ya lallasheta suka shiga ciki a parlor suka xauna xaman kurame jugum jugum bamewa kowa magana ita sefaman shessheka take shikuma yayi tagumi kamar Wanda yake acikin damuwa.</p><p><br /></p><p>Tasowa yai yaxauna akujerar datake fatima kiyi shiru pls banasan wannan shesshekar dakike inde kikaci gaba dayi to xanfita inkyaleki Kinga kuma dama xankaiki kigayda gwaggo da baba yanxu,murya narawa tace nadena,yawwa gudgirl kokefa yanxu kije daki kisa abaya akan kayanki semuje mudawo da daddare.tashi tai tatafi sama,yabi bayanta da kallo yagirgiza kansa she's still acting like a kid😏saman shima yahau tana tsaye tana gyara farar abayar jikinta sunkuyar da kanta tai takasa .</p><p><br /></p><p>Sa hannunsa yai yadago habarta kasa hakuri yai sedayabata deep nd warm kiss dakyar yakyaleta dukya birkita yar mutane😏murya kasa kasa yace inkingama shiryawa Ina kasa,Fanta takalli lebanta wanda yai ja ga radadi lalle tanada aiki agaba tabbas wannan shine hakkin auren da Baffa lado kefadi.karasa shiryawa tai sannan tadan faffesa turare tasauka kasa!</p><p><br /></p><p>Xaune yake a drivingseat karasawa tai tabude gaba taxauna,yawwa kinfito nasan sunacan suna jiranmu,itade Fanta murmushi tai Dan bala'in kunyarsa takeji .tashin motar yai sannan yaja suka tafi.yana Isa yai parking sannan suka fito itade kanta akasa.</p><p><br /></p><p>Yana gaba tana binsa abaya har suka isa bakowa a parlor Dn da alama su gwaggon suna sama,saman yahau itama tabishi zaune suke a parlor Dn baba da gwaggo ,gwaggo tana ganinsu tafadada murmushinta a'a sannunku daxuwa shikansa mahbub mamakin hakan yake.</p><p><br /></p><p>Har kasa Fanta tagaishesu baba ya amsa da fara'a gwaggo Ma tadaure ta amsa mata cikin makircinta,sannu bintu Allah de yamaku albarka,nande baba yayi musu nasiha ,gwaggwo Ma tayi musu karintata nasihar da munafunci .</p><p><br /></p><p>Bayan kamar awa daya darabi gwaggo takirasu daga abinci tagama lapiyayyar miyar ugu da tuwon shinkafa se lemon taccaciyar ginger,Fanta de tana tsakura tanaci cike da kunya dayake a dinning table ne,lokacin da mahbub yakira Fanta datai serving dinshi suci tare gwaggo tai makirci a'a nida ya'ta xamuci😏</p><p><br /></p><p>Bayan sunci abincinne wayar mahbub tai Kara dauka yai hello aboki,subhanAllah yanxu?eh eh hakane Allah yasawwake Bari naxo muje amata sannu kafin inkaraso.kallon gwaggo yai Bari naje gidan dr haydar Wlhy matarsace wai take bleeding yakideme wai baxe iya driving motar ba shine yakirani,yamike tsaye bari naje can din,yakalli Fanta toni xanfita sena dawo dandakkomin briefcase dinnan kibiyoni dashi mota.</p><p><br /></p><p>Fanta tamike tabishi da jakar,gwaggo takalli yadda take tafia,murmushi tai Afili kuma tace Alhamdulillah yanxu Bari nakira boka nagaya masa sauran aiki yarage nasa....kome gwaggon tagano???🤔</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Miss Hafsat Xoxo And Nafee Anka</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(65~70)</p><p><br /></p><p>Nafee Anker</p><p> ✍Miss Xoxo</p><p><br /></p><p>Fitar Fanta keda wuya gwaggo tahau sama tashiga daki hadda kullewa sannan takira boka,ringing daya yadauka yakecemata taxo yanxu bayani baxeyiwu awayaba.kashe wayar tai tana xagaye dakin yanxu menene mafita yaxa'ai tafita tabar Fanta ita kadai agidan idan mahbub yadawo fa?murmushi tai sannan tadakko hijabi tasa taxiri mukullin mota tasakko kasa.</p><p><br /></p><p>Fanta ce zaune itakadai a parlor tana kallon film dinda gwaggo takunna na hausa furuci,gwaggo ce takarasa parlor dn tana murmushi nadan hau sama ne Ina answering call wallahy kawatace hajia ateeka dinnan jikinne yai tsamari.fanta ta jinjina Kai alamar jimami Allah yabata lapia.gwaggo tace Wlhy da xuwa xanyi sekuma naga kar inbarki kekadai,Fanta tai murmushi Haba gwaggo kije mana bakomai ai da akwai mutane agidan,gwaggo tamike tsaye da minje kinraka nima dande ba atambayi mahbub ba.bakomai gwaggo kije amata sannu.gwaggo tafice insha Allah xataji bari yanxu xandawo ai.</p><p><br /></p><p>Gwaggo nafita tafigi mota se gurin boka tana xuwa yamata ixini tashiga.gwaggo naxuwa taxube akasa tana mika gaysuwa,mungode hindatu(gwaggo).yanxu kina ba matsala yarinyar wani abu beshiga tsakaninsu da yaron mijinnakiba kintabbata?gwaggo tadaga kanta sama babu abinda yashiga tsakaninsu kamar yadda kasani nace bananan jia hakan akai yakawota gidana yaudin daxu da safe,dayake jiyanma anan gidanmu yakwana to amma yaudin yaje kominti 30 beyi daxuwa ba yadakkota.tanacanma nabarta tana kallo...</p><p><br /></p><p>Yanxu de ninagama nawa aikin senawajenka,,,ai aiki kam baki gamashiba tunda bakisa yaron yabargidansa ba yadawo inda kike .gaskia inhar sunagidansu to gaskia ba abinda xan iyayi maki akai ,inhar kikai haka to sauran aiki kibarshi ahannuna.</p><p><br /></p><p>Ajiyar xuciya gwaggo tai Dan wannan maganace babba,yanxu tayaxatai tai wannan aikin tana mace,dole sede tahada da temakwan ixzy taji yaxasuyi dawannan lamari da boka yabijiro musu dashi.sallama tai masa ranta abace taja motarta takoma gidah!!!</p><p><br /></p><p>Tana shiga Fanta tajiyo da fara'arta gwaggo harkin dawo?nadawo Fanta jiki kam dasauki Tana gaysheki itama tace intaji sauki xataxo narakata gidanki.fanta tace Allah sarki Allah yabata lapia,gwaggo takalli tv au har film din yakare?bari ai akwai wani Bari nasaka miki wani.itade Fanta ta sunkuyar da kanta kasa.gwaggo tasa mata wani film.fanta Bari nadan watsa ruwa insakko.</p><p><br /></p><p>Gwaggo na hawa sama takira ixzy a handsfree(speaker)tasaka.hello izxy.na'am gwaggo,ixzy kinajina ?eh gwaggo inajinki ya akai?ixzy boka yasani amtsala wai lalle insanyadda xanyi su mahbub sudawo daxama gidannan gabadaya,yanxu yaxanyi?</p><p><br /></p><p>Ixzy tai Daria haba gwaggo kamar ba yar gari ba kinaji kibar komai ahannuna ayaudinnan su mahbub xasubar gidan.gwaggo tadafe kirji ta yaya ixzy?hmm gwaggo kenan naga kindamu dayawa ba matsala fa su Shamo xantura musu anjima...</p><p><br /></p><p>Gwaggo tatun tsire da Daria to ai kece se kwana kwana kike,yanxu kikawo idea,Allah de yacika mana burinmu.ixzy tace amiin gwaggo babban burina be wuce na bude ido naganni tare da mahbub amtsayin miji ba,gwaggo tace amin.se anjima Bari insauka kar yarinyarnan taga nadade.</p><p><br /></p><p>Kashe wayar tai sannan tasauka kasa wajen Fanta wadda tabawa tv muhimmanci tana kallo.nabarki ke kadai ko wallahy sedanai wanka naji dadi.itade Fanta murmushi tai kawai.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafeesat Anka (Yarsmeen Anker👸🏻) And Hafsat Xoxo (Miss Xoxo👩🏻)</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(70~75)</p><p><br /></p><p>Nafee Anker</p><p> ✍Miss Xoxo</p><p><br /></p><p>Gwaggo takara kallon Fanta Fatima kece yar fari agidanku ko yar'auta?fanta tagirgixa kanta nice yarfari nikadaice ai Banda addah bare dabo(Yaya tamace da Yaya namiji)gwaggo tagirgixa Kai Allah sarki.afakaice gwaggo takalli agogo karfe 6 saura yanxu yaxatayi?tanacikin tunanin mafita wayarta tai ringing M sulayman ne keyawo jikin screen din Mahbub kenan,dauka tai kamar xata hadiyi zucia tasan kila caxai Fanta tafuto yana waje.</p><p><br /></p><p>Dakyar ta iya furta hello mahbub,Allah sarki mufeedah Kai Allah de yabata lapia,eh bakomai muna tarema gatacan to ayima mufeedan sannu senaxo,Fatima rike waya mahbub ne,Fanta tasowa tai dakyar kunya dukta isheta sa hannu tai takarbi wayar sallama tai sannan tagaysheshi kamar badaxu suka rabuba,murya kasa kasa yake mata magana fatimana kiyi hakuri jikinne na mufeeda haryanxu wllhy amma komai dare xandawo bama xankai 9 ba xanxo mutafi gidah kinji?tagefen ido taga gwaggo kallonta take dakyar yace toh sekadawo agayshesu.sannan tamikawa gwaggo wayarta..</p><p><br /></p><p>Bayan sallar isha'i gwaggo tagama lafiyayyen cous cous da vegetable sauce,dakyar Fanta tacuccusa iyacikinta tabar sauran danba cimar fulani bane,8-30 gwaggo takasa controlling kanta yataji shirune ixzy fa katta mata shiririta.adole tadau wayarta tahau sama.dakinta tashiga takira ixzy hello ixzy yanaji shirune?yarannanfa yanxu xedawo kuma matarsa xedauka sutafi.</p><p><br /></p><p>Haba gwaggo nikedena cewa matarsa,nagaya miki kakki damu kosunje gidan xasu dawo nan ba'abinda xeshiga tsakaninsu everything is going to be okay just bear wit me,haba gwaggo kidinga hakuri mna.to ixzy naji na yadda senajiki.kashe wayartai sannan tasakko kasa.azaune fantar take inda tabatta karasawa gwaggon tai yi hakuri Fatima nabarki kekadai wallahy hadiri nagani agarin seda narurrufe Windows din kar ruwa yashigo😱</p><p><br /></p><p>Karfe 8:50 Dede mahbub yashigo gidan agajiye yake yanaxuwa yaxauna akujerar datake facing ta Fanta ,gwaggo kuma tana dayar kujerar,Kai yaumunsha xirga xirga fa wallahy dakyar de akatsaida bleeding din anmata test Komi lapia.gwaggo tace aini naxata miscarriage ne,a'a wallahy kawai bleeding nede lungs dintane sukai weak shine haka tafaru,gwaggo tace Allah de yasawwake.ga abinci nan a dinning Fatima kawo masa.</p><p><br /></p><p>Tashi gwaggo tai tabasu wuri badan tasoba,Fanta ta aje trays din xata tashi yai sauri yarike hannunta,xauna mana Fanta inakuma xakije?fanta takoma taxauna hade dasa hannunta tarufe fuskarta,kallonta yai yajanye hannun baxaki dena wannan kunyarba?nifa mijinkine Fanta,aurenmu dake Wata warakace akan MATSALAR RAYUWAR mu.yanxu de xubamana muci.aa naci tare da gwaggo.mahbub yawani mata shu'umin kallo next time kakki sakeyin haka tare xamuna cin abinci a plate daya kinji.daga kanta tai sama alamar eh.</p><p><br /></p><p>Yana gama cin abinci Fanta tadibi komi takai kitchen.sannan tadawo,gwaggo ce tasakko daga sama sundan taba hira sannan mahbub yamata sallama sukatafi,su gwaggo hadda Bawa Fanta supersheraton da turare.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kome xefaru????🙆</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(75~80)</p><p><br /></p><p>Nafee Anker</p><p> ✍Miss Xoxo</p><p><br /></p><p>Kafin su karasa gida mahbub yatsaya awani katoton shopping mall hade da suya sport ,drinks yasiyo da chocolates se gasassun kaji.sannan suka wuce gidah,suna xuwa kofar gate din mahbub yai horn amma shiru megadi bebudeba yasakeyin wani horn din nan ma shiru.futa yai dakansa yabude gate din sannan yadawo ya shigar da motar,yana xuwa yayi parking sannan yace Fanta tadan jirashi bariya duba sambo megadi kobashi da lapia ne,shiga yai harcikin dakin megadin azaune yake yanata sharar bacci abinsa,mahbub yasa hannu yadan girgixa kujerar amma shiru,yadan daddakeshi ahannu danya Farka nanma shiru se munshari dayasake ja yanajin dadin baccin,mahbub girgixa kansa kawai yayi sannan sambo megadin yamanyanta yanxu yana bukatar hutawa,futowa yai yaja masa kofar tareda sa sakata hade da padlock a gate din,sannan ya ebo ledojin Fanta ta tayashi sukashiga dashi cikin gidan.</p><p><br /></p><p>Suna xuwa mahbub yacewa Fanta taxuba drinks din a freezer shikuma yahau Sama xe duba email dinsa dan jia yaga anyi emailing dinsa akan yaje Cyprus offer tafuto.yahau sama itakuma Fanta tahau kallon gidan Dan jia ita bawani tsayawa taiba takarewa gidan kallo.tabbas su Baffa sunyi mata bakin kokarinsu kuma Allah yasaka masu da alkhairinsa!!!</p><p><br /></p><p>Tana cikin kallon gidanne mahbub yasakko daga sama yacanxa kayansa yanxu singlet ce ajikinsa da shortnicker,kallon Fanta yai wadda tai kasa da kanta danbata taba ganin katon namiji ahakaba😩kallonta yai yalura da hakan da gaysa yaxo harwajen datake yajanyota tafado kansa akunne yake rada mata meye kike kallona haka kobanyi maki kyaubane??fanta ita kam kunya dukta isheta kasa magana tai,to tunda baxaki bani amsa ba baxansakekiba mukwana ahaka,Fanta takalleshi taga dagaske yake bashiri tarufe fuskarta Kayi kyau...</p><p><br /></p><p>Nagano lagonki ai,yanxu de dandoramin tea xansha .tohm Fanta tace sannan tashiga kitchen din,tana Neman stove(risho)amma babu se gas cooker kuma batasan yaxatai ta kunna ba,komawa tai tatsugunna ehhm nace banga risho ba kuma ba murhu sewani abu irin wanda naga gwaggo tayi girki dashi amma ban iyaba,mahbub yayi murmushi muje nakoya maki,,ka iya girki ne?ai yanxu fatima daxami gasar girki sena cinyeshiki tsaf,Fanta ta kyalkyale da daria yaushe ka koya?lokacin da'ina service ne to bana iyacin abinci siye kona roadside shine nakeyi da kaina harna iya.</p><p><br /></p><p>Atare suka shiga kitchen din yanunnuna mata komi sannan suka dafa tea din hade da toastingbread,parlor suka koma suka xauna sukaci bayan sungamane mahbub yake cewa Fanta xesama mata makaranta ,Fanta harda tsalle dan murna nagode mahabu...nifa gaskia kidena cemin mahabu dinnan Kinga Fatima nake cemaki ko?ehh ,to keki dinga cemin baby kinji?fanta ta gwalalo ido ai naga jarirai ake fadawa haka ko sekuma tarufe fuskarta kuma naga Kai kayi katoto....</p><p><br /></p><p>Mahbub yadinga Daria hadda rike ciki waya gayamaki haka?to inma hakanne ninaxama baby dnki ko?fanta tagirgixa kanta a'a ni kunya nakeji.......</p><p>Sunyi hira sosai kafin suka shiga daki su kwanta ,mahbub ne yashiga ya watsa ruwa itakuma Fanta tana gefen gado tana jira yafito..bayan mahbub yafitone yakashe futalar yabar dimlight itakuma .fatima shiga kifito dare yayi.tashi tai tadauki rigar baccinta harkasa mekauri hade da hijabi Dan ka'idane tasaba da sallah raka'a biyu kafin shiga bandaki tai sannan tarufo kofar.</p><p><br /></p><p>Rufe kofar keda wuya ,aka kunna fitilun dakin,mahbub Wanda ke zaune yana danna system yadago kansa fatima meyasa xaki...kafin yakarasa maganar wani basamuden mutum ne yasa bindiga a keyarsa ,sssh kana ihu xanfasa kanka wallahy,,wasu karti biyu ne suka shigo bayan dayan basamuden kowanne da bindiga amma fuskarsu da facemarsk ba'agane kosuwaye.babban cikinsu ne yadakawa mahbub tsawa kana jina xanbaku minti 30 kacal kubar gidannan kaida matarka idan ka kuskura minti talatin tai baku ficeba to duk abunda yabiyo baya Kai kajiyo!!!!</p><p><br /></p><p>Mahbub yajanyo jallabiya yaxura,ya kwankwasa kofar bandakin Fatima ,Fatima futo isauri yanxu,Fanta wadda alokacin tagama shiryawa tasaka hijabinta tafito.tana futowa Shamo yasaka mata bindiga akai kina magana xan yagaki.hadiye kukanta tai hade da toshe bakin ta musamman dataga mahbub agefe shima bindigar akasa masa akeya,Shamo yakalli wani daga cikin yaransa Kai biliya tasa keyarsu sufice agidannan,karnasake ganin kafarku cikin gidannan dawowarku gidannan babbar hatsarine agareku kuma mafarin shigar MATSALAR RAYUWARKU kusan inda dare yamaku......</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: [8/4, 00:40] Yasmeen Anker👸🏻: MATSALAR RAYUWA 🙆(86-90)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anka </p><p> ✍🏻</p><p>Miss Xoxo</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mahbub ya kwana yana sake² a ransa yana tunanin miye dalilin da yasa wa in nan mutanen suka je masa gida,iyakar tunanin sa yayi amma be fahimci kome ba,shi dai baya da abokin fada bare yace turo masa akayi,a ransa yace koma dai waye Allah baya bacci kuma zaya tona asirinsu da gaggawa,da yaga kwanciya akan sofa baze masa ba,toilet in palour ya shiga ya dauro Alwalah tare da jera na filfili,yana rokon Allah ya kare su daga tarkon azzalumai,ya rufa masu asiri ya kabe ko wace fitina a aurensu ya basu zaman lafiya shida Fatima.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A dai² wannan lokacin kuwa Gwaggo na can tana aikin siddabarun da boka ya bata,ta fitar da bakar tukunya daga karkashin gadon da fanta take kwance akai tana bacci,dama boka yace mata tayi yanda zata yi Fanta ta kwana a dakinta,ta dade Rana wasu surutai na tsafi ka fin ta kira sunan Mahbub Dana Fanta ta saka a farar tukunya,sunan Mahbub kuma da Izzy a bakar tukunya,bayan ta gama ba tare da dubawa ta tura a karkashin gado tare da kwanciya cikin tsananin farin ciki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abban su Mahbub kuwa a ransa yana matukar mamaki meya lalata dakin Mahbub kuma bayan da kansa ya shiga dakin kuma ya gansa lafiya qlau,amma meyasa Hajiya tace haka cewa da gwaggo,a ransa yace koma dai me take nufi ai zangani,a ransa yaji dadin komawarta dakin ta don a nasa dakin takura masa take yi ta zame masa karfen kafa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mahbub yana duke yana kai kukansa ga Allah har saida aka kira sallan asuba sannan ya mike tare da yin raka'atainul fijr, sannan yayi shirin zuwa masallaci,dai² lokacin da Mahbub ya bude kofar falonsu da niyyar zuwa masallaci yayi dai² da fitowan Abbansa wanda a tare suka jera zuwa masallaci.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gwaggo kuwa kaman jiraye take su Mahboub suje masallaci ta sauko da sauri daga kan gadon ta,ta jawo tukunya ta fita da sauri zuwa bayan gida,ta daga tukunyar ta saki a kasa tana fashewa seda gidan ya girgiza</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(80~85)</p><p> </p><p>Nafee Anker</p><p> ✍Miss Xoxo</p><p><br /></p><p>Shamo yakalli mahbub ,kadau motarka da megadinka bama bukatar sake ganinku,biliya sa su ahanya.har parking space biliya yakaiku,sannan mahbub yashiga yatada mota Fanta agaba sambo megadi abaya,jikinsu se rawa yake .bayan sunhau titi ne mahbub yakalli fanta,fatima Dan Allah kiyi hakuri kedana kukannan dakike ai kamata yai mugodewa Allah dayasa basu hallakamuba kosu nakasta wani barin ajikinmu.ko bahakane baba sambo?</p><p><br /></p><p>Sambo megadi Wanda shima jikinsa rawa yake dakyar yaba mahbub amsa,kwarai kuwa mahbub addu'a itace,mahbub ya girgixa Kansa kawai Allah de yashiga tsakanin nagari da mugu amma tabbas wa'innan mutanen sundade da shiga gidan baba sambo inaga lokacin kana bacci sukashigo ko katafi masallaci yin sallah.</p><p><br /></p><p>Baba sambo yace mahbub tabbas wa'innan mutane nagansu naga kuma sanda sukaxo,mahbub yakalleshi kallon mamaki sannan yajuya yacigaba da driving dindayake,baba sambo yace wato mahbub nafuto daga masallaci kenan xanshiga gidah se aka hasko fitila ta haske min Ido to senasa hannuna nakare ,nashiga cikin gidah shigata kedawuya aka fara bubbuga kofar gate,naxata baki akayi ma,to budewata keda wuya sukashigo ciki,nake amasu suwaye sukace banida bukatar nasani,babban cikinsu yasa suka kamani yace wani dagacikinsu yadura mani Valium(maganin bacci)akakawoshi a gora suka kamani iyakar kokarina nayi nakwace amma nakasa haka suka duramin duka to wallahy bankara sanin inda kaina yakeba seyanxu damuka shigo mota,tun karfe 8 seyanxu karfe 1:30.</p><p><br /></p><p>Mahbub yace Allah ya kyauta kosuwaye ubangiji Allah yatona masu asiri,tabbas baba sambo daxu damuka dawo senine nabude gate nakulle nattattashekama Baka tashiba senai tsammanin bacci ne yadan daukeka,ashe abunda suka maka kenan...hmm yanxu de bari muje gidah kawai idan Allah yakaimu dasafe semusan yadda xa'ai..</p><p><br /></p><p>Karfe 2:00 Dede nadare mahbub yai horn kusan sau uku sannan danjuma megadi yatashi dakyar yana mitsiitsike Ido sannan yabude masu gate din ganin motar mahbub ce ,mahbub ne yabude motar suka futo ,mahbub yacewa danjuma megadi ga baba sambo nan yakaishi dakinsu su kwana.sannan yarike hannun Fanta sukai hanyar shiga cikin gidan Wanda nanma akullen yake😩</p><p><br /></p><p>Bubbugawa yai nanmade shiru ,bugunne yai yawa Wanda baba yamike daga kangado yakunna fitila,kunnawar futalar kenan gwaggo tatashi itama.baba yakalleta hindatu kema kinji karar bugun kofako?gwaggo wadda ita allale itama batasan suwaye ba se pretending data karayi😏hadda dafe kirji to waye haka atsohon darennan?sede musamman mugani kila danjuma ne megadi....</p><p><br /></p><p>Sauka Kasan sukai atare,gwaggo tadakko key tabude,ja bayatai hade da salati,mahbub kune haka atsohon darennan?baba was speechless ma kallonsu kawai yake,Fanta tagayshesu duk kunya ta isheta gata ha sirikanta.mahbub ya kakaro murmushin dole,mune gwaggo abinde sede godiar Allah dakuka ganmu ma daranmu da lapiar mu.</p><p><br /></p><p>Shiga ciki sukai duka sannan suka xauna Akan kujeru Banda Fanta wadda akai akai taxauna taki.atake Alh sulaiman yaji yarinyar takara shiga ransa tabbas ya yaba da hankali fantan kwarai..baba yakalli mahbub kasamu aduhu mahbub meyafaru??baba wallahy barayi ne suka shigo mana gidah.gwaggo tace tayaya ba akwai megadi ba?ehh akwai megadi ai forcing dinsa sukai yabude masu gidan tunmisalin karfe 8 nadare sannan suka dura mashi valium to be Farka bade saiyanxu damuka taho,baba yace to ba abinda sukaimakude ko?</p><p><br /></p><p>Mahbub yagirgixa kansa ba abinda sukai mana baba,illade sunce karmu sake mukoma gidan Dan inde muka koma to munshiga mafarin MATSALAR RAYUWAR mu.sunbarni nataho da mota ta ma.amma nabarsu cikin gidan.sede da safe nai wa police magana ai investigating Akan hakan.baba yace to Allah yatona asirin kosuwaye.gaba daya sukace amiin..</p><p><br /></p><p>Baba yace to seku xauna anan gidah kafin asamu wani wurin shi wancan din se asashi akasuwa kawai.mahbub yace eh dama haka nai planning kawai Dan jiama naga Cyprus sunyi emailing dina Akan offer tafuto,so xanje may be by next week naji yadda akecikiba.Allah yatemaka amma da ita matar taka xaka tafi ko?a'a baba saboda nayi planning xansata a school.baba yace eh hakanma yayi.mikewa Alh sulayman yayi yahau sama bayan yace suma suje su kwanta dare yayi.se gwaggo dayabari agunsu.</p><p><br /></p><p>Mahbub yamike yanadan Sosa keya to Bari nimade na kwanta,gwaggo talura so yake tatashi yacewa matarsa sutafi.gwaggo itama mikewar tai to seda safe mahbub ai dama a parlor ka kwana dakinnan Bakaganiba shirgi ne fal aciki aibaxeyuwu Akwana acikiba,ita fatiman seta kwana adakina kafin dasafe delu tagyara nakan,bayadda mahbub ya iya dakyar ya iya furta hakanma yayi gwaggo Allah yatashemu lapia.</p><p><br /></p><p>Hawa saman sukai itada Fanta shikuma yakakkabe kujerar yakwanta,ransa inyayi dubu abace yake,gwaggo tabata Mai moment......</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: [8/4, 00:40] Yasmeen Anker👸🏻: MATSALAR RAYUWA 🙆(86-90)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nafee Anka </p><p> ✍🏻</p><p>Miss Xoxo</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mahbub ya kwana yana sake² a ransa yana tunanin miye dalilin da yasa wa in nan mutanen suka je masa gida,iyakar tunanin sa yayi amma be fahimci kome ba,shi dai baya da abokin fada bare yace turo masa akayi,a ransa yace koma dai waye Allah baya bacci kuma zaya tona asirinsu da gaggawa,da yaga kwanciya akan sofa baze masa ba,toilet in palour ya shiga ya dauro Alwalah tare da jera na filfili,yana rokon Allah ya kare su daga tarkon azzalumai,ya rufa masu asiri ya kabe ko wace fitina a aurensu ya basu zaman lafiya shida Fatima.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A dai² wannan lokacin kuwa Gwaggo na can tana aikin siddabarun da boka ya bata,ta fitar da bakar tukunya daga karkashin gadon da fanta take kwance akai tana bacci,dama boka yace mata tayi yanda zata yi Fanta ta kwana a dakinta,ta dade Rana wasu surutai na tsafi ka fin ta kira sunan Mahbub Dana Fanta ta saka a farar tukunya,sunan Mahbub kuma da Izzy a bakar tukunya,bayan ta gama ba tare da dubawa ta tura a karkashin gado tare da kwanciya cikin tsananin farin ciki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abban su Mahbub kuwa a ransa yana matukar mamaki meya lalata dakin Mahbub kuma bayan da kansa ya shiga dakin kuma ya gansa lafiya qlau,amma meyasa Hajiya tace haka cewa da gwaggo,a ransa yace koma dai me take nufi ai zangani,a ransa yaji dadin komawarta dakin ta don a nasa dakin takura masa take yi ta zame masa karfen kafa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mahbub yana duke yana kai kukansa ga Allah har saida aka kira sallan asuba sannan ya mike tare da yin raka'atainul fijr, sannan yayi shirin zuwa masallaci,dai² lokacin da Mahbub ya bude kofar falonsu da niyyar zuwa masallaci yayi dai² da fitowan Abbansa wanda a tare suka jera zuwa masallaci.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gwaggo kuwa kaman jiraye take su Mahboub suje masallaci ta sauko da sauri daga kan gadon ta,ta jawo tukunya ta fita da sauri zuwa bayan gida,ta daga tukunyar ta saki a kasa tana fashewa seda gidan ya girgiza</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: Cikin tsananin farinciki ta juyo zuwa dakin ta ta gyara kwanciya ba sallah bare salati, *ALLAH YA TSAREMU DA AIKATA SON ZUCIYA* .</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A bangaren su Abban Mahboub kuwa yana sallame sallah yaji kansa ya Sara masa se jiri dake daukarsa,Mahbub na kula da yanayin sa yayi saurin rikosa ya kwanto a jikinsa cirasa yayi tsaye ya fito dashi daga cikin masallacin zuwa gida shigowansu gate in gidan Abban Mahboub yake ce ma Mahboub ya kai sa visitors lodge,Mahboub ya kallesa da mamaki amma bece komai ba,Bayan ya kaisa Abban nasa ya gyara kwanciya tare da cema Mahboub yaje zuwa anjima ya dawo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Fanta kuwa tayi mamakin meya hana gwaggo tada ita bacci tayi sallah,a ranta tace wata kila kuma bataso ta takura mata ne,ta shiga toilet tare da Alwala tayi sallah bayan ta gama addu'ointa,nade sallayan tayi tare da fitowa Neman kitchen domin hadin Karin kumallo (break fast) tana saukowa sukayi kicibis da Mahboub ya tsaya kallonta ta masa kyau sosai though Hijab ne a jikinta,Fanta ta sunne kanta tare da gaidasa cikin siririyar muryarta be karba ba sema jawo ta da yayi a gefen kafadarsa ya raba da jikinsa suka sauke ajiyan zuciya a tare rika hannunta yayi zuwa sama dakin sa ya wuce da ita direct suna shiga ya maida kofa ya rufe da Kadan akan Autar hajiya da Candy sun makale min se sunga meke faruwa ai kuwa mun Riga mun shige nida miss Xoxo mun baro yan sa'idon a waje,Mahboub yace ta tashi zasuyi raka'a biyu ta godiyan Allah bayan sunyi ya mata tambayoyi ta karba daganan ya cire mata hijab,nidai ina ganin haka na jawo Hassi don naga an wuce hurumin mu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A raina nace Allah ya kawo zuri'a ta gari Fanta and Mahboub.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ku biyomu don jin ya zata kasance tsakanin Mahboub da gwaggo idan ta gane abunda ya faru.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Fatan Alkhairi gare ku Mahaifana</p><p><br /></p><p>Hajia kulu s Mafara </p><p>And Hajiya Fatima Musa Barade Anka.</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: [8/5, 22:30] Nafee Anker👸🏻: [8/5, 20:15] Nafee Anker👸🏻: ```MATSALAR RAYUWA 🙆(91-95)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abbansu Mahboub kuwa yana farkawa yayi addu'a yana mamakin meya faru dashi haka yana mamakin abunda ke damunsa a ransa ba abunda yake so a halin yanxu kamar yaga Mahboub da sauri ya hau sama yana bude dakin a hankali se yaga Mahboub kwance tare da wata jawo dakin yayi a hankali ya wuce dakinsa jin yayi gaba daya garin ya ishesa so yake kawai yaje wani guri ya huta</p><p><br /></p><p>```</p><p> ```tattara kayansa ya shiga yi da sauri ya zari makullin mota kwaya daya ya fita ta kofar baya motar sa ya shiga tare da bata wuta yayi horn megadi ya bude masa gidan ya fita yana ta tunanin ina zeje zuciyarsa ta basa ya wuce sokoto kawai,tafe yake a cikin motarsa tsabar tunani ya masa yawa Allah kadai ya kawo sa lfy,Dankane Guest inn ya wuce straight ya kama daki ya ajiye kayansa,shiga toilet in room in yayi tare da Alwala ya gabatar da sallolinsa,sannan ya nemi guri ya kwanta a daina zancen yunwa saboda gaba daya baya jinta```.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*A bangaren su Mahboub kuwa shiga ta dakin naji yana sanyawa Fanta albarka yana gode mata sosai data kawo masa 'yancin ta a gidansa,Fanta kuwa se sunne kai take yi alamun kunya,tsokanarta yayi amaryata zaki iya tashi ko sena taimaka miki zuwa wankan ai kuwa tanajin hakan ta mike zuwa toilet in Mahbub dake cikin dakin tayi wanka tare da shiryawa Mahbub ya kawo mata wani Arab gown me kyau daga cikin kayan Nawwara ya ajiye fitowan ta wanka tayi using da lotion insa a jikinta tare da using gown in da ta gani akan gadon,tunani ta shiga yi ina Mahboub ya shiga ya barta.*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*a bangaren gwaggo kuwa tana can tana bacci cikin farin ciki da annashuwa ganin cewa hakan ta ya cimma ruwa ta tarwatsa auren Fateema da Mahboub yanxu gida ya zama nata ita daya da kanwarta ta San Mahboub be isa ya ketare maganar mahaifinsa ba ita kuwa daga nan zata takura ma uban ya sashi auren Izzy*.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Mahboub kuwa kasa yaje zuwa visitors lodge yayi matukar mamakin rashin ganin Abbansa but se wani tunanin yazo masa may be Abban yana dakinsa a sama bayan shigarsa dakin yayi mamakin ganin kaya a warwatse saurin fitowa yayi tunawa da yayi yanxu fa pass 12 kenan and Fanta batayi break fast ba da sauri yaje kitchen ya tarar an gama break ya hada mata shi kuma ya shiga wanka,yana fitowa fanta ta mika masa towel yana goge jikinsa cikin Dan zaman da sukayi da Nauwara ta koya mata wasu abubuwa na yanda ake tarairayar miji,Mahboub yayi matukar mamaki a ina fanta tasan haka besan duka aikin kanwarsa bane,ta taimaka masa sosai gurin gyaran jikinsa da zaya saka kaya ne ta juya da sauri Mahboub kuwa dariya ya saka mata yana cewa ze iyar da cire sauran kunyar,fanta dai murmushi tayi ta cigaba da hada masa break,Mahboub ya karya ne a nutse yana yi yana tsokanar fanta ita kuwa daga smiling bata kara kome akai,bayan kammalawarsa ne ya jawo tissue ya goge bakinsa tare da janyota a jikinsa yana mata godiya,Fanta ke cema sa ita ya daina gode mata saboda aikin tane,kissing forehead inta yayi tare da saka mata albarka.*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*NAFEE ANKER*</p><p> *~AND~*</p><p>*MISS XOXO*</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: *MATSALAR RAYUWA 🙆 (96-100)*</p><p><br /></p><p>NAFEE ANKER</p><p> ✍MISS XOXO</p><p><br /></p><p>Ringing in wayansa ya katse masa hanzarin abunda yake da niyyan yi yana ciro wayan yaga kiran dad insa,bayan picking call in Mahaifinsa ke gayama sa yana so su koma gidan uncle insa da zama for some purpose,kan Mahboub ya daure sosai coz dix ix d first time babansu yace yaje gidan uncle ya zauna,ba tare da bata lokaci ba yama Fanta bayani hijab inta kawai ta saka ta fito bayanta yabi tare da rufe dakinsa,haka kuma yaje ya rufe na Alhaji Sulaiman, Fanta ke cewa Yaa MB muje muwa gwaggo bankwana,smiling yayi kawai yake cewa kinga bata tashi bacci ba,kyaleta kawai.</p><p><br /></p><p>Futa sukai suka nufi packing space yabude mota seda yaxagaya yabudema Fanta kafin yakoma yashiga yatada motar sannan sukabar gidan.amota ne yakalli Fanta .wato fatima baxakice min baby dinba kenan se yaa Mb?fanta tasa mayafi takare fuskarta ai naga yara akefadawa haka ni gaskia kunya nakeji amma yaa mb aiyafi dadima ko?mahbub yagirgixa kansa dan kinji su marwa suna fada ,aike dabance fatima kefah matatace maganin MATSALAR RAYUWA ta...anywhere yaaa mb dinma yayi amma nangaba sekin canxaminshi dole!</p><p><br /></p><p>Fanta tai murmushi au dole nema?mahbub yakada kansa kwarai kuwa,,,duk wannan maganar dasuke acikin hold off ne seda streetlight tabasu hannu sannan mahbub yaja motar yai kwanar shiga gidan na uncle uncle rufa'i.horn yai megadi yabude masu gate sannan suka shiga,yana xuwa yai packing.fanta tasa hannu xata bude tafita mahbub yaruko hannunta,fatima nan gidan wan babane aikin sanshi ma sanda mukaxo hayin ruga uncle rufa'i,da matarsa ammi laylaa.kinganesu ko?fanta tai nodding kanta eh naganesu!!</p><p><br /></p><p>Yawwa gudgurl,riko hannunta yai suka shiga cikin gidan da sallamarsu,Ammi layla ce kawai a parlor din tana gyara wake,amsa sallamartai sannan tadago kanta a'a manya ne dakansu sannunku daxuwa maraba marabanku,karasawa sukai cikin parlor din mahbub yagaydah ammi Laylan sannan itama fantar tagaysheta a'a lapia qalau fatima yagidah?lapia qalau.</p><p><br /></p><p>Tashi fantar tai xata dau waken tagyara Ammi Layla tahanata,yaushe a'a Wlhy baxaki gyaraba fatima,Kinga wai deboshi nai kafin hinde me aikina tagama mopping dinning area nakedan tayata,ai tagama Ma yanxu xata karba.tashi Ammi laylan tai bari nakira maku uncle dinnaku shima yanxunnan yashiga dubo wasu document,kwalawa hinde kiratai kanta kawo masu refreshment(drinks,snacks)..</p><p><br /></p><p>Uncle rufa'i yashigo parlor dn yana gyara karin hularsa sannan Yadora akansa,xaunawa yai Akan doguwar sofa din dake a parlor dn.mahbub ne yadan dukar dakai alamar girmamawa uncle Ina yini?lapia qalau mahbub,sannan itama Fanta tagaysheshi cikin sanyayyar muryarta,lapia qalau fatimatu..uncle rufa'i yakalli mahbub harkun fara futa gaysheshen xumunci kenan,hakan yanada Kyau,mahbub yadan Sosa keya eh dahakanma uncle,amma babane yakirani awaya yace muxo nan gidan.</p><p><br /></p><p>Uncle rufa'i yace tooh,lapia deko?mahbub yace lapia qalau uncle ai dama muna gidah ma....gidah kuma??wane irin sakarai ne kai ya anyiwa yarinya jere anbaka gidah gotai gotai dakai kuma seka kwasota kutare agidah?sokake kajefata acikin MATSALAR RAYUWA?mahbub yagirgixa kansa a'a uncle ai barayi ne suka shiga gidan ..,kafin yakarasa uncle rufa'i yakarbe barayi agidan naka??bakada megadine?kokuma sakarai kasamu??</p><p><br /></p><p>Mahbub yagirgixa kansa uncle Valium suka dura masa tunmisalin karfe 8 suka shiga gdan,mukuma alokacinma munacan gidah,Wlhy se gurin karfe 1 nadare sannan suka shigo cikin gidan,taredamana kashedin kar mukara xama agidan inkuma muka kuskura muka koma to mafarin shigar MATSALAR RAYUWARMU kenan...Ammi Layla tadafe kirji ammade basu muku komai badeko??mahbub yagirgixa kansa basi mana komai ba ammi sede shi megadin dasuka durawa maganin..agidande mukabarsu.amma nasa Ana investigating akan gidan..</p><p><br /></p><p>Uncle rufa'i yadade yana tunani kafin yai magana to Allah yakyauta nide tunda nake bantaba Jin ance anga ko anji barayi awannan unguwar ba,yajuya yakalli Ammi layla,Layla ba anan salinah matar turaki takeba??ammi Layla tacire tagumin data xabga anan take kuma bata taba kawo complain ba.uncle rufa'i yace to sede inturasu akai Wlhy..yakalli mahbub yanxu Ina sulayman dinyake???mahbub yace baba shima dasafe beji dadiba har nakaishi visitors lodge yadan huta,to daxu seya kirani yace muxo nan,naduba kaf gidan bayanan bansaniba ko yadan futa yadanji karfin jikinsa...</p><p><br /></p><p>Uncle rufa'i yace to Allah yakyauta,yanxu akwai wani gidah can akasan vendors line duplex ne shima,idan angama investigation akan dayan gidan se asayar asiyamaka wancan din.yanxu de Layla kaisu guest site daki make sure everything is okay,nixan futa office ana kirana,yamike tareda gyara malum malum dinjikinsa yakalli Fanta wadda tatsakure,,Fatima nanma gidah ne kakkiji komi duk abinda kikeso kifada kinji feel free nangidankune...itade Fanta murmushi tai sannan tamike tabi bayansu mahbub xuwa guest site.mahbub kuwa wani dadine yabaibayeshi ganin cewar anbasu guest site sukadai wato xasuyi amarcinsu kenan ba Kama hannun yaro se rawar jiki yake yana washe Hakora kamar gonar auduga...</p><p><br /></p><p>••••••••••</p><p>Gwaggo natashi daga bacci Tafada bathroom tai wanka se asannan tayi alwala tai sallar asubah hade da azahar din dataji ana kira sannan ta sallame.juyawa tai tana kallon gefen gadon to Ina yarinyar nan take?????itakadai tabawa kanta amsa dukyadda akai tana kitchen tana Neman abin karin kumallo...</p><p><br /></p><p>Sakko take dagakan stairs hade dakiran sunan Fanta...Fatima ,Fatima ,Fatima ...sa hannu tai tadafe kirji hade da sallallami bade naccaccciyar yarinyarnan tabi yaronnan dakinsaba???aa baxeyiwu ba abinda nariga nagama daga shi har itah..naga tukunyar baka nafasako ko fararcene??xagayawatai bayan gidan ganewa idanuwanta Dedetai ko shirme???</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>SORRY FOR THE LATE POST!!!</p><p> Anker's fault....😏</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(100_105)</p><p> </p><p>NAFEE ANKER</p><p> ✍MISS XOXO</p><p><br /></p><p>Bayan gidan gwaggo tazaga danganewa idanuwanta aika aikan data tafka,dafe kirji tai ganin tukwanen fari da baki jere afashe kuma bata da tabbacin fararce mesunan Mahboub da izzatatu,salati tafariyi ganin cewar wannan shine BABBAN KUSKUREN DATA TAFKA,oh ni hindatu nashiga dubu ma ba uku ba yanxu yaxanyi???wani jiri ne yafara daukarta bashiri takoma cikin gidan tareda dakko gyalenta da keys na mota sannan ta xuba fassassun tukunyoyin a leda ta nufi wurin bokanta danjin yadda al'amarin yake agurinsa......</p><p><br /></p><p>Minti 20 taje gudun datake xubawa a titi,sauri me hade da gudu tai har xuwa inda bokan yake,tana xuwa ta xube agabnsa,Boka inacin matsala,Daria yai harseda hakoransa masu Kama da gansa kuka suka bayyana,MATSALAR mecece hindatu???jawo ledar da fassassun tukunyoyin suke ta aje agabansa boka na tafka babban kuskure wallahy bansan ya akai bade amma nikam inaji ajikina nayi musayar tukunyoyinnan..</p><p><br /></p><p>Jawo ledar yai yafito dasu tareda barbada wata koriyar kasa Akan kowacce,shiru yai na yan mintina kafin yadago Kansa yakalleta,tabbas kinyi kuskuren hada sunan yarannan da matarsa sannan kinhada mummunar kiyyayya hade da kyama tsakanin yaron da izzatu.gwalalo Ido gwaggo tai hade da dafe kirji nashiga uku kana nufin asirina yatonu kenan??gaskia banajin hakan tafaru amma tabbas yaron mijinki yamaida ita fantar babbar mace,,</p><p><br /></p><p>Gwaggo cikin in Ina takarasa maganar kana nufin Wata auratayya tashiga tsakaninsu??amma kuma jia tare muka kwana da ita fantar kuma saboda kattaje har key nasa sannan banyi bacciba se tsakiyar dare,boka ya murmusa ai tukunyar dakikai musaya itace ta hura masa Neman wani abu awajenta,kuma ayadda nagani inaga da safe hakan tafaru,gwaggo tai tagumi tabbas hakane dandana tashi bangantaba kuma banajin suna cikin gidan,yanxu ya ake ciki???</p><p><br /></p><p>Yanxu de kinriga kinyi kuskure,amma akwai wani babban aiki daxan maki amma banajin xaki iya biyana,xan iya mana kudi fa ba matsalata bace,boka yace sanin kanki ne kinsan inada kudi kuma bana bukatarsa,inde har kinasan burinki yacika xaki bani kanki amma gidanki xanxo saboda nandin aikin baxeyiba se acandin kuma ba kwana daya kwana 3 xanyi sannan nagama aikin..</p><p><br /></p><p>Tagumi gwaggo tacire tabbas ta girgixa kwarai da abinda yace ita bawai Neman tadaxeyi bane matsalar,matsalar itace yace se agidanta kuma sanin Kansa ne yasan tanada miji ga yan aiki fal.boka ne yakatse mata tunanin datake naji kinyi shiru ko baxaki iyabane??ba wai xancen baxan iyaba akwai masu aiki sannan miji na yananan..boka yakalleta Karo na uku hindatu idan baxaki iyaba kitashi kifita kawai bana harka da irinku,gwaggo tai kasa kasa da muryarta naji boka kuma natuba ka iya xuwa koyaushema..murmushi kawai yai,gwaggo tace to yaushe xaka xo kenan?boka ya watsa mata harara wannan ba hurumunki bane,hakuri tabashi sannan tai Mai sallama taja motarta tatafi tare da tsoran Allah de yasa kar boka yajawo mata MATSALAR RAYUWA....dakyar ta Isa gidah tana shiga takira wayar Alh sulayman sanin koyana ina?sanar da ita yai yana sokoto yaje General checkup next week xedawo,kashe wayartai bayan sunyi sallama tare dajin dadin hakan daya fada saboda boka xe iya xuwa koyaushe,sannan tasauka Kasan side dinsu masu aiki tareda basu hutun sati2 acewarta wai tafiya xasuyi!!!</p><p><br /></p><p>••••••••••</p><p>Bayan Mahboub yayi sallar isha'i komawa side din da akabasu yai yashiga Dayan dakin yayi wanka sannan yasako pajamas(Kayan bacci)ya nufi Dayan dakin da Fanta take,atsaye yaganta gaban dressingmirror tana shafa Mai da alama itama wankan tayi,Jin takun takalmi yasa tajuya ganin hasken idanun ta tayi yatunkarota cikin tafiyarsa ta kwarjini da kamala.....sakon murmushi ta aikawa dan mutan sokoto Wanda seda dimple dinta ya lotsa,Wanda idan tai itakanta tasan tagama rikirkita mahbub din.</p><p><br /></p><p>Xuwa yai yasakale hannunsa tabayanta suna kallon kansu ta cikin mudubi,murya kasa kasa yake rada mata akunne fatima yakamata mukwanta ko?gaba daya yarikirkitata kasa magana tai illah sakon French kiss data aikamai,sahannunsa yai yakashe fitilar dakin tareda kunna dimlight !!dahaka Nafee Anker tajawoni dan munfara wuce huruminmu wannan Karan harda nusnnim dakesan ganin kwakwaf amma Anker tahana......</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*YARSMEEN ANKER*</p><p> ✍MISS XOXO</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(105_110)</p><p> </p><p> NAFEE ANKER</p><p> ✍MISS XOXO</p><p><br /></p><p>Kiran sallar asubahi ne ya tserar da Fanta daga hannun mahbub,dakyar suka iya tashi sukai sallah tare da karatun alqur'ani adole Fanta tana Kai aya ta aje.dan idonta har rufewa yake da kansa tsabar baccin data keji Wanda shima Kansa mahbub din baccin yakeji tunda ba baccin sukai ba anata faman Abu daya....</p><p><br /></p><p>Karfe 10 dede Fanta tafarka daga daddadan baccin datai bandaki tafada tai wanka hade dayin brush.sannan tadawo daki tana sanda kada mahbub yafarka,kayanta tadauka takoma bandaki bayan yanmintina kadan tafuto sanye cikin atamfar daviva red me ratsin cream,gaban dressing mirror taje tashafa man cocoa butter palmas,hade da shafa powder din ailin sannan tagoga lipbalm purple..tana cikin combing kanta mahbub yatashi yana mika hade da salati.</p><p><br /></p><p>Jiyowatai taimai murmushi sannan tatsugunna harkasa tagaysheshi,sakkowayai daga kan gadon ya nufo inda take yana murmushi,mikewatai xata gudu yaruko hannunta tareda jinginata a drawer yasa hannunsa tabaya bayadda xata gudu,murya kasa kasa yafara mata magana,Fatima na shine baki tashe niba har kikai wanka kika shirya amma baki tasheniba,kayi hakuri yaa mb naga baccin kayayi nisa sosai shiyasa bantashekaba,kallon dan guntun bakinta yai wanda pink lips ne baisan sanda yamata frenchkiss ba sannan yasaketa.</p><p><br /></p><p>Fanta kasa hada ido tai dashi,illa mayafinta data dauka tayafa dan bata zama ba hijabi ko mayafi dantasaba tun a hayin ruga,,bandaki mahbub yashiga yayo wanka bayan yafutone yasa kananan kaya bakin Wando se riga fara me style din polo,sannan suka jera suka futo parlor gurin su Ammi Layla dukda suma akwai parlor din a guest side din da aka basu..</p><p><br /></p><p>Zaune su Ammi Layla da uncle rufa'i suke shiga su mahbub din sukai bayan sungayshe sune sannan Ammi Layla tace suje dinning dancin abinci.fatan dankali ne dayaji hanta se kunun shinkafa da soup din Kayan ciki...bayan sungama cin abincinne uncle rufa'i yakalli mahbub sannan yace mahbub yakamata kasaka fatima a makaranta ko?mahbub yace uncle dama nayi planning akan hakan.ammi Layla tace nikwa daxakubi ta shawarata da homeschool kawai akai mata ko? se akira David da Barr ikram suringa koya mata inyaso tunda muna October,kawai setai SSCE(WAEC,NECO)a November December ko?</p><p><br /></p><p>Uncle rufa'i yace ehh haka yakamata ayi ko mahbub?mahbub yai nodding kansa ehh uncle duk abinda kace ayi..uncle rufa'i yai murmushi toh yaxancan offer din taka ta Cyprus?mahbub yace uncle I want to make it this coming Saturday ,uncle yace jibi kenan xaka tafi?mahbub yace ehhh uncle..to ai kamata yai kakira david da ita ikram din kaji yadda za'ai da kuma abinda ake bukata ko???inyaso kafin kadawo andedeta komai,,,,to uncle nagode Allah yasaka da alkhairi.bari xankira David awaya ita kuma barr ikram senaje wajenta tunda chamber dinta ba nisa daganan...uncle rufa'i yace ehh hakanma yayi to se kuje wajen ta tareda fatiman taganta ko??toh uncle!</p><p><br /></p><p>Tashi sukai itada mahbub din suka fita danxuwa wajen Barr ikram..Ammi Layla takalli uncle rufa'i alhaji..mahbub yayi sa'ar mata Wlhy yarinyarnan tanada tarbiyyah ga bin nagaba,uncle rufa'i yace kwarai dagaske ai shiyasa hindatun sulayman taso tahana auren badan nayi dagaske ba Aida wai Wata ko ikilima xata bashi,Ammi Layla tace izzatu de ko?anacemata wai ixzy...uncle rufa'i yai Daria to Dan mutunci kuwa acanxamai suna wai ixzy sekace biscuit Allah de kyauta ,Amin Layla tace amiin....</p><p><br /></p><p>••••••••••</p><p>Washegarin ranar da gwaggo taje wurin boka xokaji aiki yaxo wajenta,Batai musuba tabashi kanta kamar yadda sukai alkawari.sede kassh meyakwan yakoma gidansa seyace anan xe karasa sauran kwana biyun.daya fada bayadda gwaggo ta iya itade addua kawai tayi kada Allah yasa Alh sulayman yadawo kafin kwana 2...</p><p> </p><p>To tabangaren ixzy Ma abubuwa sunyi mata xafi tadawo daga shopping daga wani makeken wuri da akecema Anker plaza..tayi youturn kenan Wata mota Tasha gabanta adole taja birki tai parking bude moto tai tafuto danganin suwane yan shilolinne sukai mata haka.futowarta kenan idanuwanta sukai toxali da shamo da biliya,mtscewww taja tsaki meye haka?shamo yakalleta hakan ce takawo haka Kinga ixzy wannan ai renin hankali yaxa'ai kisa mimaki aiki amma haryau baki bamu ladanmuba,kullun kice bakida kudi segashi munyi toxali dake a Anker plaza gurin dabakowane ke xuwa siyayyyaba kinje kintulo banxa da wofi wallahy sekinbamu kudinmu kokuma wallahy kiga aiki da cikawa yanxunnan.</p><p><br /></p><p>Bude baki ixzy tai tana mamaki kai da Allah can rufemin baki mekuka Isah kuyi kundade bakwi ba wallahy,banxa soko Dan Allah naga aikin da cika...kafin takarasa biliya yawanka mata mari watch ur tongue bitch...kekin Isah kifadawa oganmu haka karamar yar iska kawai......</p><p> Murde hannunta biliya yai yakwace carkey dinnan sannan suka jata wani kango sukai mata danbanxan dukan dasuka nakasta mata jiki,sannan suka batta jina jina tareda dauke motartata da kayan data siyo sukai gaba abinsu tareda barinta a kwance rai ahannun Allah!!!!!!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>YARSMEEN ANKER</p><p> AND✍MISS XOXO</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(115_120)</p><p><br /></p><p>NAFEE ANKER</p><p> ✍MISS XOXO</p><p><br /></p><p>mahbub ne da Fanta a mota da alama gurin Barr ikram xasuje,dede wani gini dogo yai packing da alama kantinane da kuma offices,floor na uku suka hau anrubuta ajikin wani office madedeci "Barrister Ikram Khaleel chamber" murmushi mahboub yai yakalli Fanta. Kinga ashema bawani wahala nidayan chamber dinnata nasani bawannanba.murmushin itama fantar tai sannan tace eh gaskia ba wahalar nema kam..shiga sukai cikin office din da sallama!!!</p><p><br /></p><p>Wata mata mekama da jinsin larabawa nagani azaune,kyakkyawa da ita. sanye cikin blazer baka (suit)amsa sallamartai tareda da dago kanta danganin suwaye.murmushi tai bayan ganin waye ,have a sit please.mahbub ne yajawo kujera yacewa Fanta taxauna,sannan shima yaja yaxauna thank you barrister,barr ikram tagama Cike file din dake gabanta sannan ta aje agefe,mahboub ne yagaysheta sannan itama fantar tagaysheta...</p><p><br /></p><p>Barr ikram tacire medicated glass din idonta sannan ta bude Dan medium freedge din dake agefanta taciro lemon cway peach guda biyu da ruwan swan ta aje agabansu mahbub da fanta,kallon Fanta tai tai murmushi fatima yagidah? inataso inxo wallahy aiki yahanani naji kunya wallahy.fanta tace bakomi wallahy aunty ikram Allah deyatemaka.(dayake Barr ikram din taje bikin kuma mahbub yayi introducing dinta sosai gun fantar,ikram da fantar tare sukai high sch a cyprus university Ma tarene sede ita takaranci professional nd business law shikuma yatafi aikin pilot)....</p><p><br /></p><p>Mahbub yabude lemon sannan yadanyi sipping ya ajiye..nace ikram wani temako nakesan kimin Dan da uncle rufa'i ne xexoma sekuma yace naxo kawai,Barr ikram tadanyi Daria temako captain?mahbub yace ehh temako xa'ace kenan,zantafi cyprus jibi so yaude da yamma xanje sokoto xanyi sallama da baba kwana xanyi acan tacan xanhau flight natafi cyprus anturomin offer!!dan Allah inde kinada time homeschool xaki yima fatima keda david,shi maths dasu chemistry da physics xeyi mata kekuma English,irk,hausa dasu economics da literature..but if kinada time kenan inbaki da time kuma ba matsala se ayima wani magana Dan da school Ma xansata se ammi Layla tace gwara amata homeschool kawai setai SSCE dis coming November/December...Yaya kikegani???</p><p><br /></p><p>Barr ikram tace ai uncle rufa'i da Ammi Layla sunyi magana I have no choice,sede ko da daddare bayan isha'i haka 8_10 ranar workdays kenan ranar weekends kuma 4_6 saboda ina cikin critical situation wallahy.inada cases 3 danma andaga dayan se after azumi.amma bakomi I will try my possible best,yanxu wane course take so kenan?mahbub yajuya yakalli Fanta,Fatima mekikeso kikaranta?fanta tace nide burina bewuce nakaranci bangaren likita ba saboda intemakawa al'umma dake cikin MATSALAR RAYUWA...Barr ikram tace a doctor indeed,kuma xaki Kyau da likita fa,amma kinsan likitocin bangare bangare ne fa,akwai bangaren hakori(dentist)akwai na ido(optometrist)akwai na theatre surgery masu rike scalpel anacemasu (surgeons)👌🏼kala kala de,wanne kikeso???mahbub yace ikram gaki barrister ga field kinsani a mbbs,Fatima wanne kikeso???</p><p><br /></p><p>Fanta tadade tana tunani nikam nafison masu operation din,Barr ikram tace surgeons kenan,Allah yacika maki burinnaki,Fanta tace amiin... Sannan mahbub yacewa Barr ikram kan agidan uncle rufa'i xata ringa yiwa Fanta lesson din saboda gangsters dindasukakai masu hari,,,nande sukai ta hirarsu sannan sukai mata sallama suka tafi,a mota mahbub yakira David yamasa magana shima yace xeyi...Anker plaza suka je yaiwa Fanta siyayya tagani tafada tareda siyo mata textbooks da notebooks da pens da mathset.gida suka koma bayan sunci amarcinsu sannan mahboub yaima su uncle rufa'i sallama yatafi sokoto dagacan xeyi kwana daya yawuce cyprus.tabbas Fanta taci kuka da mahboub xetafi seyanxu takara tabbatarwa mahboub yaxamto wani waraka acikin MATSALAR RAYUWARTA!!!</p><p><br /></p><p>••••••••</p><p><br /></p><p>Meanwhile bayan su shamo sunyiwa ixzy jina jina,wasu mutanene suka ganta suka wuce da ita wani asibiti Wanda akatemaka mata da ceton gaggawa xuwa emergency unit,ansa mude da ranta amma she's unconcious kuma tashiga comma ga bawaya agunta da za'a sanar da yan uwanta adole doctors dinsuka hakura danceto ranta dayake tana numfashi amma iya ciki kawai.</p><p><br /></p><p> *SOKOTO*</p><p><br /></p><p>Karfe 3:30 Dede mahbub ya isa sokoto,yanaxuwa yakira mahaifinsa kanjin ko yana Ina?yasanar dashi sannan mahbub yatari cab(taxi)yawuce guest inn din...yanaxuwa bayan sungaysa da baban tarar da baban yai yana hada Kayansa a trolley....baba tafiya xakayine??? Ehh xankoma anka dama danbanajin dadine yasa naxo nandin,amma tunda naji dadin jikina gidah xankoma ,,,daxuwanai namaka sallama gobe 8 flight dinmu xetashi.okay ehh haka kace , to ae dama se gobe room din danakama xasi renewing kudin seka kwana anan kafin dasafe kawuce Ina ita fatiman tana gidan Yaya rufa'in?? Ehh tanacan dan ranar Monday xa'afara mata homeschool Ma David da Barr ikram....ehh hakanma yayi Allah yatemaka,....Amiin!!!</p><p> Sunyi hirarsu irinta uba da da kafin daga bisani Alh sulayman yaima mahbub sallama yawuce Anka......</p><p><br /></p><p>Karfe 8:15 nadare Alh sulayman yawuce gidah bayan yatsaya yayi sallar isha'i a masallaci Kai tsaye gidansa yawuce,yayi mamakin rashin ganin yan aikin gidansa dayai sekuma wata bangaren xuciar tasa yabayyana masa kila suna bayan gidan tunda gidan Kato ne yanada girma,dakinsa yabude yashiga yai wanka sannan yanufi bangaren gwaggo dakamar baxeshigaba seya koma yatura kofar,bude idonsa yai yakara rintsewa danwani bangare naxuciarsa beyadda da abinda yaganiba dafe kirjinsa yai dake barazanar fadowa,ganin gwaggo dayai da wani basamuden kato akan gadonsu na kwanciya,rufe kofar yai ganin basumasan dawani akansuba,komawai parlor yaxauna meyatuna oho yatashi yashiga daki yadakko paper hade da biro......</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> WRITTEN BY✍</p><p>YARSMEEN ANKER</p><p> AND MISS XOXO</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(120_125)</p><p> </p><p>NAFEE ANKER</p><p> ✍MISS XOXO</p><p><br /></p><p>Meyatuna oho yatashi yadakko paper hade da biro....dafe kansa yai dake Mai ciwo sannan yasa dayan hannun yadau biro yafara rubutu kamar haka:NI SULAYMAN MUHAMMAD HADEE ANKA NASAKI HINDATU SAMBO SAKI 3 saboda wasu dalilai dasuka gurbata aurenmu......</p><p><br /></p><p>Yana gama rubutawa yagoge gumin daya tsatssago a goshinsa sannan yanannade takardar yasa a envelope fara yalike,komawa daki yai yakara wanka saboda wani irin zafi da kunar rai dayakeji aransa,rigarsa jallabiya yazura sannan yadau mukullin mota yafito packing space dingidan yanufi dakin danjuma megadin wanda azaune yake yajika gari da sugar yana sha,tura kofar Alh sulayman din yayi tareda sallama.amsa sallamar danjuma yai tareda daga kansa danganin waye,tsugunnawa danjuma megadin yai yana kwasar gaysuwa....lapia qalau danjuma nace kaga sauri nakeyi xanje wani conference meeting naga kuma idan nace xantsaya naba hindatu sako xanmakara danjirana suke ,sa hannunai a aljihu yaxaro envelope din yamikawa danjuma,gashi kabata..kace mata xankirata nadanyi tafiya urgently kaji???danjuma yace ehh oga insha Allahu xanfadawa Hajian data fito.....sannan yamai sallama tareda hawa motarsa yabar gidan!!!</p><p><br /></p><p>Kaitsaye Alh sulayman gidan wansa rufa'i yanufa,yanaxuwa yai packing sannan yanufi cikin gidan da sallamarsa Wanda Ammi Layla yagani atsakar gidan taroka Wata da alama rakiya tamata,tana ganinsa tafadada fara'arta a'a yau megidan nawane dakansa kenan,,shide Alh sulayman murmushi yai yana fadin banacin mike sekin shigo ciki de.shiga yai cikin parlor din ganin Alh rufa'i(uncle rufa'i) yana zaune amma akasa yanacin tuwo dawa miyar ganye,tsugunnawa yai akasa Yaya inayini???lapia qalau sulayman yajikinnaka ance bakaji dadiba ko?</p><p><br /></p><p>Ehh Yaya banji dadi ba amma nawarke ai,,,toh alhamdulillahi ....bismillah ga abinci,,toh yaya, </p><p> Sa hannunai yai acikin kwanon suka cinye abincin tass,sannan Ammi Layla tashigo cikin parlor din...gaysawa sukai sosai da Alh sulayman din hatta kira Fanta suka gaysa dashi sannan takoma ciki.basu wuri Ammi Laylan tayi..</p><p><br /></p><p>Bayan sundayi hira irinta yan uwan taka Alh sulayman yadan Sosa keya,Yaya gurinka naxo....uncle rufa'i yace toh ai gani ko?....wato Yaya ni nace mahbub suxo nan wajenka da matarsa Dan dana tashi inarashin lapia sekawai natafi sokoto,to acan dinnede nasamu kaina Nagano cewar hindatu(gwaggo)ba tsakani da Allah take xaune daniba,sedan abun hannuna bata barni ahakaba sedata sanyani cikin sihiri yaxamto bana iya wani abun seda yardarta,nasan nayi muku laipi Dan Allah Yaya kayafemin....Uncle rufa'i yace bakomi sulayman tunda bada sani Kai hakanba ai,yanxude tunda koma meye yakarye kuma kagano gaskia wallahy komai yawuce awurina kaiharma gurinsu tajudeen duk ba matsala wallahy dade kam tabbas kana cikin MATSALAR RAYUWA amma yanxu Allah yakarya komai kuma rayuwarka tadedeta ai Alhamdulillah...batin mahbub da Fatima kuma aibase kace suxo nanba nidakaina Inna San dawannan abin xanje indakkosu dakaina,ai shi mahbub din ai inaga gobe xetafi Cyprus da yanxu mukai wayama ai itakuma Fatima Ma gobe xa'afara mata homeschool David da Barr ikram yar aminina Alhaji sameer ameer....</p><p><br /></p><p>Alh sulayman yace ehh haka yacemin,sannan Yaya Abu nabiyu de yanxu ba auren hindatu akaina,Uncle rufa'i yace what?dankagano gaskia seka saketa haka ake RAYUWA baxaka rufa mata asiri ka xauna da ita ba?haka akesakin ba shawara?....a'a Yaya bahaka bane wallahy nasan kun Isa Dani,amma abinda ita hindatun taine baxan iya xama da ita ba,xamanmu yaxo karshe kenan,,,to seka gayamin ai wanne abin tayi kayanke wannan hukincin???nidama nasan ba lapia ba tunda naganka kaxo karfe 9:30 nadare ...</p><p><br /></p><p>Muryar Alh sulayman narawa yakarasa maganar Yaya hindatu taci amanata ganinta nai suna auratayya dawani agidana...shine kawai narubuta takardar saki nabawa megadi nace yabata kawai,saboda harna bar gidan suna daki...Uncle rufa' yajinjina Kai to gaskia kayi saurin sakinta amma kuma dole kobajima kobadade seka saketa ai,gaskia bata kyautaba kuma tabata kanta,yanxu de kaga dare yayi xami magana dasafe kawai amma inaso kaje aimaka General test dasafen dankare kanka daga kwayoyin cuta..insha Allah Ma bama fatan hakan amma kajedin ko gurin yarannan dr haydar ...toh Yaya insha Allah....hira suka danyi tunda dare yayi sosai sannan Alh sulayman yamasa sallama sannan yanufi hotel tunda dakin dayake kwana fatima ce aciki...</p><p><br /></p><p>********</p><p><br /></p><p>Bayan gwaggo da boka sungama sha'aninsu tashi tai tai wanka duk jikinta tsami yake sannan tasauka kasa tahado abinci.sede sukaci sannan boka yamata sallama yatafi...komawatai daki tagyara dangudun kada Alh sulayman yadawo sannan ta kwanta bacci daddada yadauketa saboda tasamu boka yatafi yanxu jiran sakamako take na aiki.</p><p><br /></p><p>Gwaggo natashi dasafe tasamu Kira awayrta nabakuwar number dauka tai danjin waye,,,hello waye??kina magana da dr Yusuf daga nan model hospital,,toh dr Yusuf inajinka,ehh Hajia mundanyi cigar relatives din patient dinmune harde muka samu number ki,,gwaggo tadanyi Daria gaskia you must be mistaken danbani dawani ko Wata relatives dayake bashi da lapia doctor...dr Yusuf yace well I dunno ko mistake dinne amma de for sure wannan patient din u r related ,,gwaggo tace to waye?dr Yusuf yace izzatu anacemata ixzy ankawo ta nan emergency unit ba lapia infanct she's unconcious lokacin harde tashiga comma to yaude we try our possible best amma daga karshe rai yayi halinsa...munanan model hospital,street din Anker plaza ..bejira mexatace ba yakashe wayar..</p><p><br /></p><p>Wata hajijiyace tadauki gwaggo dakyar ta iya karfin halin daukar wayar tana duba wayar Anya dagaske ne kuwa?to yanxu xan iya tafiya bakomai agurin boka?danna number wayar bokan tai amma taki shiga ,adole tadau mayafinta hade da mukullin mota tafita waje,danjuma megadi yana ganinta yataso Hajia Ina kwana???lapia qalau danjuma,,,da hannu yai a aljihu gashi inji alhaji yace nabaki jia yana sauri xashi meeting yace nabaki inataso nabaki tinjiyan to banga futowarkiba,,sa hannu tai takarba,,to xanfita Nima idan yaxo kace naje asibiti ixzy tarasu acan,,,danjuma yagwalalo ido izzatu mutuwatai hajia??ehh haka naji yanxu bantabbatar bade ammade hakannema..to Allah yajikanta da Rahama amin..</p><p><br /></p><p>Futa tai tanufi asibitin tana xuwa takira dr Yusuf,,yasanar mata cewar suna operation amma yanxu xekira akaita dakin da ixxatun dake tunda har ankaita mutuware an ajiye.ajiyar xuciya gwaggon tai sannan tadakko envelop din da danjuma yabata ajaka Dan dabatai niyyar dubawa bama azatonta kudin dayasaba bata ne ya aikomata dashi dandata Kira wayarsa akashe taji..bude takardar tai amma setaga takardar nanmade azatonta ko check ne,dakkowatai hade dasa glass dankarantawa...tana gama karantawa tafadi awajen ..likitocine sukayo kanta ,ansamu bawata matsala amma daga karshe tadan bugu sosai dayake dama tanada sinuses(ciwon kai mehade da barin fuska)seda akai treating kunnenta sannan sukai mata allurar bacci...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>YARSMEEN ANKER</p><p> ✍MISS XOXO</p><p>[8/22, 14:17] Nafee Anka: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(125_130)</p><p><br /></p><p>NAFEE ANKER</p><p> ✍MISS XOXO</p><p> </p><p> *Cyprus*</p><p>Mahbub naxuwa Cyprus yakira gidah yace masu ya isa Cyprus lapia kuma anjima xeje can inda offer dinsa tafuto Qualified center captains unit anace da gurin (QCCU) a sntjacobs street cyprus!yakuma turowa Barr ikram kudi data siyawa Fanta waya kirar Samsung Galaxy alpha...danbaxe iya bacci batare dayaji muryar Fanta ba gashi besan ranar dawowar saba shide kam one week yakesanyi amma dakyar inxasu barshi yadawo a one week din.</p><p> </p><p>Alh sulayman natashi dasafe asibiti yawuce wajen dr haydar tareda masa umarnin yimasa test kamar na blood,bowel,stool,(jini,fitsari,bayan gida)bayan kamar minti 30 dr haydar yafito da result ,successfully ba abinda yasamu Alh sulayman din sede malaria datake Neman kamashi anan yasai magani sannan yaxarce gidan uncle rufa'i..yana xuwa yatarar da Fanta da David a balcony(baranda)din gidan da alama lesson yakemata ha books nan abarbaje shi David din naxaune Akan kujera itakuma Fanta tana dayar kujerar amma sunada nesa da juna sannan fa board(allo)yana mata solving equations da words...</p><p><br /></p><p>Fanta tana ganin Alh sulayman tamike taxo wajensa tana kwasar gaysuwa,amsawa yai tareda Kara yabawa da hankalinta hijabine harkasa da nikaf hade da safa ta hannu data kafa,shima David din mikewa yai yana gayda alhaji sulayman din da hausar sa wadda bata fita sosai,shikuma Alh sulayman din da turanci yake masa magana,hope everything is okay david?yes yes sir everything was going on smoothly sir,she's smart wallahy very soon she will understand everything...Alh sulayman yai nodding kansa that's great then,please teach her well ,if there's any problem let me knw...okay sir,will let u knw,thank you sir....</p><p><br /></p><p>Sallama yai yashiga cikin gidan,wannan karan Ammi Layla ce kadai a parlor din tana kallon news,amsa sallamartai tana fara'a a'a na karfen kaxo kenan(dayake Ammi Laylan tanada barakwanci ga San yan uwan mijinta bata iya kishin faccalolin nanba..)Daria Alh sulayman din yayi sannan suka gaysa yayan yana ciki kuwa??yana ciki yanxu xefito ,,okay tohm Bari injirashi.sundan jima suna hira sannan uncle rufa'i yafito ,tsugunnawa Alh sulayman. Din yayi yagaysheda yayannasa..Yaya kaje asibitin?ehh Yaya naje ba matsala wallahy sede malaria amma itama it's not that worst ...okay to masha Allahu.ai munyi waya dasu samir duk xasu xo anjima se ai General meeting...</p><p><br /></p><p>Uncle rufa'i yakalli Alh sulayman,Kai ni bana manta ba Ina yarinyar nan kanwar matarka wasunanta nema?iklima ko?ammi Layla tai Daria izzatu de ko ,Alh sulayman yace ehh ixxatu suna cemata ixzy nina jima banga yarinyar nan ba ai.Alh sulayman yace toh ita ,Kasan kanin Barr ikram,wani yaro anacemasa Yusuf toh likita ne ae,Alh sulayman yace ehh naganeshi ai dayake duk yan gidan daga lawyers se doctors ko?uncle rufa'i yace kwarai kaganeshi toh shine ai yau kafin kaxo Alh sulayman din nanyaxo yai breakfast sbd jirgin 8 matarsa da twins dinnan AFRAH DA AMRAH takai India daya zatai anesthetic nursing dayar kuma gynecologist ,,wallahy nande yaxo munata maganar RAYUWA yake cemani wai dr Yusuf din yaje gidah yana bashi labari wai anwa Wata budurwa dukan data xama unconcious harde Abu yatada brain nd nerves dinta wallahy yace daga karshe ma tashiga comma tarasu seyake. Cemin wllhy kamar yataba ganin fuskarta Ma,toh hakade mukabar xancen wallahy seda yakoma wajen karfe 9:30 segashi yakirani yace Ashe kwa ba mantuwar nai ba nasan fuskar wai Ashe izzatu ce kanwar hindatu wallahy yace daga karshe Ma,tracing sukai harsuka samu number ita hindatun awajen Wata nurse data taba mata operation.yace wai ba adadeba seda hindatu taje wallahy wai ance Bari akira massenger yakaita mutuware kafin akira wallahy kamar me stroke kawai akaga tafadi takan fuskarta ,wai tanada sinuses ko?to se abin yai affecting kunnenta yaita bleeding sedaga karshe de tafarfado amma yace anjima xasu sallameta Dan har andau ixxatun to inagama har ankaita Ma,inata Kiran wayarka not reachable Kasan Mtn daga karshe de nahakura nace aixakaxo inyaso semuje mi gaysuwa ko??</p><p><br /></p><p>Tunda yafara magana Alh sulayman yai shiru hakika yaji mutuwar ixxatu,yarinya da kintsattsiya kawaye suka sata ahanyar masha'a suka jefata a MATSALAR RAYUWA.tareda temakwan hindatu rayuwar yarinyar takara lalacewar kasancewar tasangartata da kudi da kuma rashin mafadi tunda iyayensu suka fara mutuwa,awajen kishiyar Uwa suka girma,handkerchief yasa yagoge hawayen dayaxubomai Allah yajikan izxatu da rahama halinta nagari yabita,itakuma hindatu Allah yashiryeta yasa tagane gaysuwa,toh Yaya semuje din...Alhaji rufa'i yace gaskia kam hindatu tabata wayonta,Layla yanxu fa hindatu ba aure tsakaninta da sulayman,Ammi Layla tace ba aure kuma kamar yaya?uncel rufa'i yace ehh wllhy kamata yai tana auratayya da wani acikin gidansa infanct adakinsu Ma sef.ammi Layla tai salati amma hindatu tabata wayonta tabbas,abinnata haryakai haka,toh Allah ya kyauta ..uncle rufa'i yace amiin yanxu seku shirya kedah Fatima in aka gama mata lesson din se akira mahbub din atambayeshi inya batta sekuje kwi gaysuwar Bala driver yakaiku!...hira sukadanyi sannan uncle rufa'i da Alh sulayman din suka tafi gaysuwa!!!</p><p><br /></p><p>Bayan angamayiwa Fanta lesson,komawatai ciki ta tarar Ammi Layla tana shiryawa xata fita,Ammi fita xakiyi?ehh gaysuwa xamuje hadda ke ai amma sekin Kira mahbub kintambayeshi tukun,Ina wayar da ikram takawo maki?tana kan bedside na jona a caji..oya jeki dakko yanxu ai tayi full charge,shiga fantar tai daki ta dakko wayar,gashi Ammi ...Fatima aidaxu na koyamiki yadda xaki kira,duk nasa nambobinmu datasa,dataki data baffaninki da Barr ikram..yanxu shiga daki kikira kitambayeshi kice Dan Allah xamuje gaysuwar izzatun gwaggo tarasu da safe asibiti inybarki toh inbebarki ba kuma ai a adole kinji..toh Ammi......</p><p><br /></p><p>Shiga daki tai tareda pressing number mahbub din,ko ringing daya bata karasa ba yadauka,,,Salam alykm fatimana,inata jiran line din dama yahau nakiraki kiyi hakuri kinji baby,,,Daria fantar tai tareda amsa gaysuwar sannan tagaysheshi,baby kuma kamar Wata yar karama,mahbub yai Daria of course baby tace ke,itade Batai magana ba,fatimana nayi kewarki wallahy wallahy wallahy fatima kinxamo farincikin MATSALAR RAYUWATA ..nanmade Batai magana ba kunsan Fulani da kunya,to Yaya studies hope David yafara maki lessons???eh yafara harmunyi nisa Ma yace nayi kokari kasan harna fara iya mathematics da chemistry yace wai uhm uhm mema yawwa wai mondula of langata(number 6,brain(kwakwalwa)Dina tana ja,mahbub yai Daria that's my wifey haka nakesanki inaso kifi haka iyawa kafin nadawo kinji???ehhh insha Allah..to me labari danyimin kisss tawayamana sena koshi wallahy yunwa nakeji amma inkikamin wallahy xanji nakoshi..</p><p><br /></p><p>Itade Fanta Daria tai,sannan takadar da maganar uhm ya mb,Ammi Layla tace natambayeka wai xaka barni muje gaysuwa yanxu mudawo??mahbub yai salati waye yarasu fatima?wai izxatu gwaggo ce tarasu da safe daxu,,,salati mahbub din yakarayi sannan yace Allah yajiknta da rahama,kwi musu gaysuwa pls Nima xankira awaya namusu kafin nadawo ,ki kuka da kanki fatimana ,kisa hijab da abinnan danasiyo maki na rufe fuska ,,Fanta tace nikaf ko?inasawa ko lesson din da akeminma dashi nake xama,yawwa gudwife shiyasa nake sanki,Bari xankiraki da daddare kidena kirana kar credit dinki yakare flashing kawai xaki namin nixandinga Kira kinji Fatimana??ehh naji,amma kuma Barr ikram tace akwai kudi dubu 10 aciki ko?ehh nasani wannan kidinga kiransu baba dasu Baffa dashi...kuje gaysuwar se anjima xami waya yau ba bacci ta waya xami bacci...kigayda Ammi Laylan se Anjima..itama sallamar tai sannan takashe wayar tareda daga hannunta sama tanamaiwa Allah godia da yabata mahbub amatsayin miji kuma maganin MATSALAR RAYUWARTA......komawatai tafadawa Ammi Laylan yabarta sannan Bala driver yajasu se gidan gaysuwa.....</p><p><br /></p><p>To da haka muma muke mika gaysuwar rashin izzatu damukayi,,,sede mu keke napep mukahau bayan Anker tagama dubibiyeshi da rokon yakaimu anaira hamsin....chai Anker kina kwafsa min😏me keke napep for goodness sake😩....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> WRITTEN BY YARSMEEN ANKER AND MISS XOXO</p><p>[8/23, 20:10] Nafee Anka: [8/23, 20:01] Hansai Xoxo: MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(135_140)</p><p> EPISODE FINALE...</p><p><br /></p><p>NAFEE ANKER</p><p> ✍MISS XOXO</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan wani Dan lokaci:</p><p> Bala driver ne kejan Fanta a mota da Alama daga gidan dr haydar suke,kuma akan hanya suke xekaita hayin ruga...awa daya Dede suka Isa kauyen na hayin ruga.packing motar bala driver yayi sannan yasamu yara suka temaka masa da daukar tsarabar kayan dasukai wa baffaninta xuwa rugar Baffa ardo.sanye fantar take cikin abaya baka ta nannade kanta da mayafin abayar tareda sakale jaka light blue da takalminta shima design din jakar covered shoe,inka ganta baxaka taba cewa fantar bace tabbas yanxu takoma fatiman mahbub,sosai yanayinta yacanxa sede al'adar tade tananan.futowa akai daga ruga ruga Ana kallonta gwanin sha'awa se sha'awar ta ake ganin yadda tacanxa tai Kyau da ita.</p><p><br /></p><p>Bayan tashiga rugarsu Baffa lado.gaysawa sukai sosai dashi dakuma innah lantana.cima aka kawo mata da fura bayan ankaiwa Bala driver nasa kason.sannan itama tasa aka shigo da nasu tsarabar dasuka kawo..sosai aka cika Bala driver da tsaraba sannan yai sallama ya tafi kafin injibi asabar tayi yadawo yadauketa tunda kwana biyu mahbub din yace tayi.bayan taci ta huta shiga ruga ruga tafarayi na baffaninta tana gayshesu sannan tasauka a rugar su salah.tabbas salah taji dadin ganin Fanta to ita fantar haka..sunsha hira irin ta aminan juna kamar yadda suka Saba.bayan tacikata da tsaraba hadda waya irin me torch light dinnan,</p><p>se dare ya ja sannan Fanta ta koma rugar Baffa lado..</p><p><br /></p><p>Kamar kullum bayan Fanta tayi wanka tashirya cikin atamfa dinkin Senegalese atamfar bakace meratsin amber orange ,yafa wadataccen mayafi tai sannan ta rike hannun yar autar Baffa lado wadda akecema fannah suka nufi rugar su salah,a wajen bukkar su salah innar salah ke tatuyar kosai jawur dashi yaji Kayan hadi,Fanta tagaysheta cikin harshen fullanci amsa mata tai sannan tace innah dama kina tuyar kasko biyu ??innar salah tai murmushi wannan cimar kice Fanta nakine neke maki.fanta tai murmushi nagode innah nagode ,ina salah ?innar tace salah naciki tadawo daga hayi shine take sakeyin wanka...Fanta tace oh ehh ,Bari inshiga injirata ja'ira shine tagudu aikwa baxataci kosannaba,innah tai Daria nikam ba ruwana kunfi kusa kam..</p><p><br /></p><p>Bayan salah tafito daga wanka,tacanxa kaya tarar da Fanta tai wadda tatasa plate din kosai agaba tanaci tana xabga yaji,salah ta gwalalo Ido amaryar mahabu,kodai shikine dake kike xabga wannan yajin haka??Fanta tai Daria ciki kuma salah wallahy a'a kinsan muna gidan Ammi Layla to yanayin girkin ta akwai yaji harna saba kuma da dadi wlhy,salah ta gwalalo Ido gidan Ammi Layla kuma?meyafaru da gidannan ku???wlhy barayine suka shigar mna,,salah ta toshe baki barayi kuma Fanta ???ehh wlhy barayi shiyasa muka koma gidansu Ammi Layla amma xamu koma gidan mu in yaa mb yadawo..salah ta gwalalo Ido waye kuma yaa mb?fanta tace mahbub toh,nawwara kanwarshi itace kefadamai haka Nima harna saba..uhm yangayu,,,sunsha hira har Fanta ketambayar salah shin wata tsayar xata aurane???salah tace bukar ,Fanta tace a haba Dan Allah bukar de Wanda yaje karo karatu ababbar makaranta(university)???dan gidan rugar Baffa lando??ehh Shi,,gaskia inai miki murna kice munkusa Shan bikin ranar ice kenan,,salah tace kwarai dagaske ke ilu mafa ankusa bikinsu,ahabade Waze aura??shemau jikar innah lantau,,lalle Alllah yasanya alkhairi kice akwai bukukuwa Allah de yakaimu,,,ameen!!!</p><p><br /></p><p>Adaren ranar Fanta sunsha waya da mahbub haryake cemata yaso xuwa ko two weeks ne yayi amma aiki yasashi agaba ,gashi har SSCE dindaxatai ankusa befi saura 3weeks ba,take cema sa bakomai haka Allah yayi kuma su Ammi laylaa sundauketa kamar ya'r cikin dasuka Haifa,itakam tagodewa Allah takuma yaba masa da yaxama wani ginshiki nayaye mata MATSALAR RAYUWARTA!!</p><p><br /></p><p>Washe gari da yamma Bala driver yaxo daukar Fanta,tabbas Tasha Jan kunne dakuma fada irin na iyaye Wanda su Baffa lado da innah lantana sukai mata,ankuma cikasu da tsarabar fura da Nono zabi da kuma kaji sesu dangin kuka da bushasshiyar Kubewa,,boot seda yacika da kaya da kuma bayan mota.</p><p><br /></p><p> MATSALAR RAYUWA</p><p> 🙆(145_150)</p><p><br /></p><p>Karfe 5:30 Dede su Bala driver suka Isah gidah,tabbas su uncle rufa'i da Ammi Layla sunyi murna da dawowar Fanta danda tatafi gidan yaxama badadi na hausawa sukace Sabo Turken wawa,sunyi mamaki kwarai da Kayan tsarabar da su Baffa lado suka basu,sosai akai miyar kaji da kuma soup din zabi.shima Bala driver yasamu nasa Rabon..washegarin ranar dubin mutane suka sheda daurin Alh sulayman da kuma addah nafeesah yar bazawar kamila kamar su daya da maminsu mahbub.kuma taji ta amince xata xauna dashi.nawwara ma taso xuwa sede tana fama da laulayin ciki.</p><p><br /></p><p>Ana'i saura kwana 5 su Fanta su xana SSCE xaune suke itada Barr ikram tana mata lesson,tabbas yanxu kam acikin 100% ta iya komai 95% sede godiar ubangiji,,,turanci kam sede ta koya wa wasu Dan dama bafulatanin mutum akwai ganewa idan yasan abinda yake seyaxamto turancinta yabada wani salo intana magana yakasance kamar British English takeyi.bayan tagama revising komai kallon Barr ikram tai sannan tadora da nagode aunty ikram bisa tirbar dakika dora ni akai tabbas ba abinda bansaniba a HALIN RAYUWA yanxu.kuma yakasance kedah uncle David kunkoyamin ilimin da duk inda nashiga a RAYUWAR DUNIYA xan iya mu'amala da kowane race(kalar mutane) I just dunno how to thank you,Allah yasaka maki da gidan aljanna ..Barr ikram tai murmushi amin Fatima nagode sosai kuma kema kinmaida hankali sosai Allah yakara haxaka fatima,yaya kin karanta littafin danace maki kikaranta wadda xaki karu sosai??fanta tace nakaranta aunty ikram tabbas Nafee Anker da Billy giro sunyi kokari a littafin IMTIHAL harvanso yakareba,Barr ikram tai murmushi tabbas Nima da rayuwata kusan hakan take harnake tunanin shin khaleel SO KO SHAKUWA? yakemin ganin cewar babansa yanabin babana bashi ,harnake ganin ko AUREN BASHI akai mana sedai khaleel yagayamin daddadan kalaman da har yau suke dadadamin xuciata: KE TAWACE,shi yasa haryau nake godewa kanwata NAZNEEN data karfafamin gwiwar indauki khaleel amatsayin miji dakuma aminiyata kawata maryam.sede ince Allah yasakawa RAYUWAR MARYAM da alkhairi...Fanta tai hugging Barr ikram,nagode aunty ikraam,Allah yabiyaki da duk abinda kike wishing,tabbas nikam yanxu Banda Wata MATSALAR RAYUWA!!!!</p><p> Nande Barr ikram taita Bawa Fanta shawarwari nayadda xata kara rike mijinta,dakuma abubuwan daxata ringa ci suna gyara mata jiki,da Kara mata Ni'ima .dukda mahbub din se nanda months xedawo amma shikam yafadawa Barr ikram cewar xeyiwa Fanta passport da visa taje Cyprus before result dinta yafito xamansa shikadaidin acan badadi..seda dare yai sosai sannan Barr ikram tatafi.</p><p><br /></p><p>Bayan Fanta tagama yin SSCE dinta,successfully taji dadin papers din kusan komai tayi Dankomai Barr ikram da uncle David sunkoya mata Alhamdulillah Allah itama xata xama surgeon. Adaren ranar ne Alh sulayman da addah nafeesah sukaxo har ake labarin cewar ankai gwaggo psychiatrist hospital bayan tagama fadar duk bakin asirin dakuma tuggun munafuncin datayi..shima boka xokaji aikin an nuna alabarai ganin gawarsa da akayi wata gingimari da murjeshi..hakade akaita hira har uncle rufa'i yake bayyana cewar sun tsaida shawarar Kai Fanta cyprus gurin mijinta kafin SSCE tafuto..</p><p> Bayan sati daya da hakan aka gama visar Fanta tareda booking flight dinta ,jirgi xedaga dasu xuwa kasar Cyprus karfe 8 nasafen safiyar washegari,hakan kuwa akai ranar laraba da safe jirgi yadaga da yar hayin ruga xuwa ga Cyprus,abaya tasa ja bisa yadda Barr ikram a umarceta.karfe 7 na dare jirgin yasauka ,mahbub dakansa yadauketa amota xuwaga hotel din dayasauka,,Fanta tayi kallo tagodewa Allah..shikansa mahbub din yaga canji agun Fanta yadda ta kile ta waye shigartama abin kalloce,kasa hakuri yai dakyar yabari sukai having dinner sannan..yadauketa se gado duk kansu basi bacci ba ana Abu daya ,burin ma'auratan yacika har kuka seda kowannensu yai da alkawura dasuka kullada junansu bayama'i mahbub wadda yabirkice yakuma tabbatar sunxama hanta da jini shida Fanta..</p><p> BAYAN SHEKARA DAYA</p><p><br /></p><p>Fanta muka gani Akan gadon turawar nan anshiga da ita,theatre room,mahbub kuwa shabe shabe,Ammi Layla dasu nawwara se hakuri suke bashi,minti 20 kacal dr saratu tafuto tana cire handgloves(safar hannu)dinta da fara'a</p><p>[8/23, 20:01] Hansai Xoxo: a fuskarta,mahbub ne yanufi inda take Yaya doctor?relax captain matarka tahaihu dakanta ,tajuya takalli su Ammi Layla ansamu da namiji gashinan sak kmar ubansa sede yadakko sumar mahaifinsa.yanxu xa'a gama gyarasu seku shiga,,,atake agurin mahbub yai sujjada yagodewa Allah bisa wannan babbar kyauta dayai masa shikam Fanta tagama biyansa arayuwa..minti 10 kacal aka nufi da Fanta dakin hutawa ,nande akace su mahbub sushiga yana shiga yarungume Fanta da dansa yanamewa Allah godia,harda kwallah.yanata faman sunbatu duk yabaibayesu da kiss,kunya dukta rufe Fanta sedatamai nuni dasu Ammi layla kafin yagane sannan yadan sosa keya tareda daukar jaririn yamai duk abinda musulunci yace ayi..awa uku nacika kamar yadda akesan masu jego suyi,aka tattara aka sallamesu asibitin yacika dam da mutane hardasu dr haydar da matarsa muneera da yarsu Nasreen.to mutan hayin ruga Ma ba'abarsu abaya Dan motoci suka ciko fal da mutane ganin baby da babarsa.</p><p><br /></p><p>RANAR SUNA:yaro yaci sunan uncle rufa'i bisa karamcin daya masu arayuwa ,amma nawwara tace abeed xa'aringa cemai tabbas anci cima Iri Iri dakuma savouniers kala kala kowacce jaka da katon hoton baby abeed ajiki.ranar suna da daddare mahbub ne da Fanta Akan gado sunsa babyn atsakiyarsu suna kallonsa,Fanta takalli mahbub ,baby boo ,yakalleta yess honeyboo,,tace thank you for everything ..mahbub yai hugging dinta no I'm the one to thank you Maman abeed..kissing forehead dinta yai tareda Allah yamiki albarka fatimana Allah yakara karemu daga MATSALAR RAYUWA...atare sukace amiin sannan suka rungume dansu tareda kashe dimlight nan daddadan bacci yai awun gaba dasuuu..</p><p><br /></p><p>ALHAMDULILLAH :nan muka kawo karshen littafinmu mesuna MATSALAR RAYUWA abinda mukai na kuskure aciki Allah yayafemana,.</p><p><br /></p><p>SPECIAL THANKS TO:</p><p> EXCELLENT WRITTERS</p><p> NAFEE AND AMRAH NOVELLA</p><p> ONLINE HAUSA WRITTERS</p><p>HAUSA WRITTERS</p><p>MODERN HAUSA WRITTERS</p><p>HAUSA NOVEL</p><p>TASKAR YA'YA MATA</p><p>MUGYARA DA KANMU </p><p>MATAN ALJANNA</p><p><br /></p><p>Da duk Ma sauran wasu grps dabamu lissafaba,,Mungode!!!</p><p><br /></p><p>sekunjimu awani sabon littafin mesuna DR SAMEER AMEER!!!</p><p><br /></p><p> WRITTEN BY NAFEE ANKER(YARSMEEN ANKER)</p><p> ✍NANA HAFSAT(MISS XOXO)❤</p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-22356074907045129212021-04-22T21:29:00.000-07:002021-04-22T21:29:05.022-07:00WACECE SALMA COMPLETE HAUSA NOVEL<div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-UbJNUiuvNJI/YIJMZFq8IHI/AAAAAAAAJnk/f45sAgySzrA3MGa02uxKrOLNIp-nFgU9QCLcBGAsYHQ/s2048/WACECE-SALMA.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="WACECE SALMA COMPLETE HAUSA NOVEL" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="310" src="https://1.bp.blogspot.com/-UbJNUiuvNJI/YIJMZFq8IHI/AAAAAAAAJnk/f45sAgySzrA3MGa02uxKrOLNIp-nFgU9QCLcBGAsYHQ/w400-h310/WACECE-SALMA.jpg" title="WACECE SALMA COMPLETE HAUSA NOVEL" width="400" /></a></div><br /><p></p><p>WACECE SALMA?Na Benaxir OmarMotanta take jaa ciin kwanciyan hankalitasaka wakan bag of money na rick rossyana tashi a motan, parking tayi daidaigaban office din tafito dauke da jakanta nacalvin klein. Pink colour sanye take dadoguwar riga jaa, bata yafa dankwalinabayan ba anma saita daurashi tagabakaman dankwali irin daurin da ake cewaturban,tamanna fuskanta da glass natomford, sanye da takalmin vincci taku takeirina mata masu ji dakansu kuma masu fadaaji, kimanim shekara ,24 arayuwanta, tashigaoffice dinta na FAWU investment ltd, tanashiga taga secretariat dinta na aikintaganinta yasa tamike dasauri tare dacewawelkm maam, batace komi ba ta shige officedin ta ajiye jakanta dakuma wayoyinta kirargalaxy s5 dakuma iphone6, <span></span></p><a name='more'></a>SALMA MUHDFAWU kenan, secretarynta ne tashigo rike dafiles ta ajiye agabanta tareda cewa urappointments maam. Tadauka taduba dayabayan daya, wanine yashigo office dinadaidai lokacin da matar tafita , yakallisalma irin kallon inasonki tareda cewa naxomaganan vontract dakikayi da companynmune, kallon data masa ya gushe duk wanitunaninsa, sannan tace lemme get the files,yamika mata na hannunsa ta duba, shikuwasai tsura mata ido yake, ya rasa yazaiyi dukshiyake jan contract din don ahakamne zaisamu dama yakalli kyakyawan fuskan nata,ta kalleshi fuska a daure tareda cewa amdone with you, inkunga dama ku karbi 50%din inkunga dama karku karba, yadauka taredacewa can we have dinner? Glass dinfuskanta tacire sannan tace am strictly onbusiness, beside that i hate men, so get outof my office and never come back , yayi jumshikam duk da yanaji agari ana fada anmabai daddara ba yau gashi ta maimaita masa.Toh meyasa ta tsani maza? Meye hujjanta?Duk kudin datake dashi kuma ta gada agunmahaifinta daya rasu, bayan mahaifiyartadake raya baa taba cewa anganta dawaninamijiba, inka ganta da namiji to. Businessne, anma maganan salma da saurayi baatabayiba, she keeps repeating she hate men,haka a tsanake tagama komi, tadaujakanta tamikowa sectarynta key din sannantafice motanta ta kunna, gyda tanufa tanaosa megadi yabude mata kafteren gate din,ta isa parking space dinta ta ajiye motan,cikin gyda tanufa tacire gyalen dake lanta,tamike akan kujera, a.c takunna sannantajona wayanta a caji, jitayi ance umminah,dasauri tamike take tarungumi matar wacceakalla takai shekara 45 fara kyakyawa da ita,tace sannu da dawowa babynah, salma tacesannu momy nayi missing dinki, nan sukazauna sukayita tadi,har mai aiki takawomata abinci, salma tanaci suna tadi, tanagama tamike taje tayi sallah tayi wankasannan tabi lafiyan gado, ba ita tafarka basai laasar anan tayi sallan laasar sannan tadauko littafi mai suna namiji ko miji nabenaxir omar, tana karantawa tanajin dadinkaratun ganin yadda ake rikici akai, ba ita tatashiba sai magrib tayi sallan magrib tayiisha tadauko coffe dinta tazo gun momyntatazauna suna tadi har karfe goma kafin tatattara tawuce side dinta domin tayi bacci,haka rayuwar salma yake inbata office tanagyda, rayuwanta ta tashi itakadai ne, kokawa batadashi sannan batada matsalarrayuwa, domin kudi kam mahaifinta yabarmata koda batayi, ga companynsu ma, anmahartagama karatunta tazo tacigaba da aikinda babanta yafara a companynsu, rayuwantaso simple macece wacce hayaniya baidameta ba, asali ma zan iya cewa miskilarmacece, magana aduniya shiyafi komi batawahala, inhar kaga tafi minti goma tana tadito da momynta ne, magana ashirin saitadunkula maka tamayar dashi kalma daya.Batada girman kai saidai rashin maganartane yasa ake ganin girman kanta, salmamuhd fawu kenantoh anma kunsan duk jin dadin mutum inone way or the other yanada problem, tohhakan yasa ni benaxir omar nadaukialkalamina dobaku tarihi da lbrn amal, saikubiyoni,Hajiya hassana itace uwa agun salma,mijinta alh.muhd shine mahaifi agun salmakuma yarasune salma nada shekara 17;hakan ba karamin girgiza hassana yayiba,muhd fawu su bakwai ne agun iyayenshi,Allah yabawa dangin arziki ta mai, dakumadabbobi, bayan sarauta dake hannunsukuma, hakan yasa mutane suke cewa zuriansunada kashin arxiki domin ko naira gomaalh.fawu yabaki kija jari, saikinyi arxiki maialbarka. Ahaka yazo yarasu, yanuwansa sungirgiza anma kasancewar salma ce yarsayasa yayunsa suka dauki nauyin komi nata,haj. Hassana kuwa su biyu iyayenta sukahaifa iya da hussiena. Sun shaku sosaikuma suntashi sosai kasancewar subiyuiyayensu suka haifahussiena tana zaune yanzu a u.k takaishekara 24 da tafiya, ita da danta kwayadaya, basa zuwa nja saidai suyita waya, tohkwanannanne ma hassana taji hussienannacewa tanaso sudawo gyda, duk danginsalma kowa naji da ita, ga ladabi da biyayya,da kare duk wani abu da akace haramun,Tana zaune a saloon anwanke matayalwataccen gashinta suna rolling gakumakafanta ana wankewa yatsunta mahakanema taga wayanta na ringing, hakan yasata gayda matar gefenta wata fara dagaganinta budurwa ce, wayayyiya tareda cewadon Allah kitaimakamin ki daukamin wayataacikin jakata inaso na amsa, matar ta sahannu a jakar lv wanda salma tamatakwatance tare da dauko wayan, tadaukoiphone6 din tasa mata a kunne, nan kuwaamal tafara magana, yadda take maganandaddaya ya balain burge matar, harta kashe,hakan yasa matar tayita kurawa salma ido,salma kuwa bata lura dawannan abu ba,haraka gama zata biya kudi akace mata dayanmatar tabiya tsayuwa tayi tare da tunani azuciyanta, meye na biyamin?ko she thinks idnt have money to pay ne?. Ta mika kudinwa mai sallon din batare da tace komi batasakai tayi gaba abunta, taje gaban motartatabude tashiga sai gyda, tana isa wanka tayitare da sa kayan bacci kasancewar batasallah, tamike kan gado kiranta taji anyi tanadauka taji ance salma ykk? Ta amsa da lao,sai can akace kinkoma gyda lfy? Shiru salmabata amsa ba, saikuma tace. Ya gajiyanhanya, ganin tambayan zasuyi yawa yasasalma tace evrtn lao, wayene?, tayimurmushi sannan tace sunana hauwa ummiyuguda, ina skuling a mansoura universitycairo, nazo hutune shine kuma muka hadu asaloon nd i liked u, so can we be frnds?,salma batare da tunanin ko tantama ba taceNO tare da kashe wayan, saiga txt yashigo"hey gal calm down i meant no harm, justtryna be gud, think abt it being alone aint agud idea salma,' yadda takira sunantaakarshe yasa tayi kasaif. It means kenantasanta, ita batason kawa, kuma for a timebata taba ganin wacce tayi full confidenceakan abunda tayi ba, na confronting dinta,toh baridai tagani, washegari tana officebayan sectarynta takaimata appointmentdinta tana dubawa, office din taji anbudetareda sallama, tashigo cikin mulki tana takuwacce kaima kasan ba karama bace itamatanaji da kanta, abaya ne ajikinta sai jakarprado da takalminsa, tasha space afuskanta, saidata nemawa kanta seatsannan tacire glass din salma naganin ikonAllah , tace sannu, salma ta amsa da kema!,kallon salma take tana kara fahimtarta,Hauwa ummi yuguda ya ce kwaya daya tiloagun muhd yuguda asalinsu yan garinyuguda ne acikin garin bauchi saidaimahaifinta yayi ficen arziki fiyeda tunaninmutum, gata itakadai, duk karatunta batayi anja ba. Saidai tazo hutu, batada kawa kodaya kuma bata shaawan samu aganintafrnds are betrayals, saidai dataje saloonsaitaji salma ta burgeta, koda salma tagwada mata batayi naam da bukatarta ba,bata damuba saboda tasan haka itamatakeyi wa wasu, kenan duniya duk abindakayiwa wani sai anmaka, duk takamarkasaikaga wanda ya takaka, ta fahimci halinsalma cikin dan kankanin lokaci ne, kumahakanne yasa ta binciketa sanadiyar daukowayan salma dazatayi card din salma yafadidata dauka saitasa ajaka,tanan tasamunumban salma da office address dinta,Salma ce ta kure tunaninta tare da cewameya kawoki office dina, ummi tayimurmushi sannan tace ashe am soimportant tunda harkin ganeni, well nakawomiki card dinki ne, tamika mata, bata karakomi ba salma kuma takasa kunne tajisauran bayani, yayinda ummi tayi shirudonlura datayi salma bamaison surutunbane, hakan yasa salma takarba ta ajiyeagefe sannan ta dukufa, ummi tace can wehave a lunch meeting? 2pm pomptirestaurant, ill be waiting, ta tashi ta fita,salma tabita da kallo wannan ko ke mayyacesaidai ki cinye yan gydanku, tacigaba daabunda takeyi, tana gamawa 12 taje gydatayi wanka tayi sallah harta mike zatakwanta tatuna da abunda ummi tafadahakan yasa ta zari key tanufi restaurant din,anan tanemi gu tazauna don ummin bataisaba, sai bayan 10mnts saigata, salmabatace komiba don itakam abun mamakiyabata, kahada abu kuma kayi latti, umminnazuwa tace am so sorry, bata kara cewakomi ba aka kawo musu menu list suka dubakowa tazaba abunda takeso, sai da sukafaraci salma talura wannan tafita iyamiskilanci, tace luk i hate it kinyi shiru nd kekika jawomu nan, ummi tayi murmushisannan tace i tot u want it dat way, u hatetalking hun? Salma ta kauda kai say wat uwant to sayummi tayi murmushi tace nfn much, will ube my best frnd?, salma ta kalleta sannan takauda ido , NO, ta dauki jakanta tabar ummiagun, ummi ma jakanta tadauka ta ajiyemusu kudinsu tayi gaba, daredare salmasaitaji bata kyautaba bata taba ganin mutummai confidence da shiga rai irin ummi ba,hakan yasa tadauki waya da zummar kirantasaitayi wani tunani toh wat if ummi tahakura? Bari tabarta inhar tadamu zatadawo, abun mamaki kuwa sai gashi sati biyuummi bata nemi salma ba, donhaka itamasaita share, watarana tadawo gyda daga gunaiki kawai ta tarar da mota a parking spacetasan tabbas ba motansu bane, hakan yasatayi tsammani ko anyi baki ne, tana shigataga hajiyanta da salma sai tadi sukeyi abinyabata mamaki, don tadin dasukeyi babualamun bakunta aciki, salma ta gaishe damomyn sannan tahaura sama batare datanuna alamun taga mutum a wajenba, ummitashi tayi tabita tare da bude dakin salmanbatareda tayi sallama tana shiga taji karanruwa a toilet alamun salma na wanka zamatayi takarewa dakin kallo lalle dole saalmataji dakanta komi tanadashi a rayuwantagashi dakin shikanshi komi pink ne ,wayansalman tagani batare dawani tunani batadauka tagama iya bincikenta batagaabunda take nema ba, tamayar ta ajiyesalma nafitowa batare da ta kalletaba tacemeya kawoki gydanmu? Tace gydanku kogydanmu? Nazo gayda mummyna ne, salmana bukatan bayani anma ummi tayi tsitbatayi magana ba, hakan yasa itama salmanta share, ummin tafara tunani anya salma tataba magana sama da minti 5 arayuwanta?Mutum saikace mai gaba da magana, tanazaune agun salma tashirya tsaf cikin atamfasuper wax purple dinkin riga da skirt, kayanyamata kyau sosai, tadauko sallayanta tahautafara sallah, tana idarwa zata mike tabilafiyan gado ummi ta ce am asking again,will u be my frnd? Tamika mata hannu donsu gaysa , salma ta kalleta ta kalli hannun,kafin can tamika mata tare dacewa withpolicies, ummi tace i know dem ol, batakaracewa komi ba, tafice tayi sallama da momynsalma ta wuceTph tun daga ranan aka fara kawance, nasanmai karayu zaice ya ake kawance bamagana? Kowa miskili?, hmn kawancen nasudaban ne, koyaushe zasuyi waya, sunayawan haduwa suyi aiki smtyms, sujeshopping rayuwarsu dai so simple saidai batakuri, bawacce take sauraran namijiacikinsu, wataran afita da motan ummiwataran da motan salma, wataran harkwana sukanyi a gydansu ummi watarankuma agydansu salma ahaka lokacinkomawa makarantan salma yayi dama tanafinal year ne medicine take karantawa,lokacin dazata tafi duk sunyi kewan juna,anma dake akwai waya da social networkingsai abun yazo musu da sauki,, ahaka salmatacigaba da zuwa aikin ita kadai rayuwantayadawo kamar da, saitaga ashe frnds marahama ne, saidai batada niyyyan tare tarenfrnds a ganinta raini ne da zubar da aji tarauban frnds yau aganka da wannan gobewancan, rayuwanta dai strictly on policieswatarana tana sauri tafito daga adobayero mall rike da waya ahannunta dakumajakan da tayi shopping aciki, hankalintabayanan don suna magana ne da ummi,yadda taji tabuge wayan yafadi da duk jakanhannunta, dasauri ta tsugunna don tatattare, shima ya tsugunan ne yanatattarewa, tareda cewa am soo sorry, plx kiyihakuri, wlh hankalina bayanan ne, bataceuffan ba bata kuma dago takalleshibasaidata gama tattarewa tamike tare da mikahannunta alamun yamiko mata na hannunsaanma yayi concentrating yanado yagyramata kan wayan dayacire covern jikin iphonedinta, batare da bata lokaci ba tayi gaba aniyyanta tabar mishi wayan, data mishimagana yabata wayan, ya gama sawakenan kafin yajuya yaga tana shirin tadamotan, dasauri yaje yabuga glass din tabudebatare datace komi ba, yawu yahadiyasannan dakyar yahado maganan bakinsayace ga wayan ki karki manta batare darltace komi ba takarba taja glass din tarufe,taja motarta, numban plate din yakarantaSALMA FAWU, baice komi ba yawuce ,restaurant yawuce yaje cij abinci ananyahadu da abokinsa adil, adil nazauje yanachatn yana chan malt , aliyu yazauna tare dabugeshi yana cewa, abokina inaga zuwanagarin nan alkhairi ne daga zuwa sai gamo?Adil yakalleshi yace namefa,?, ya ce mataraure mana, before den wacece saalma fawu,adil yaja tsaki tare dacewa ashe baka samumatar aure bakuwa, aliyu yace banganebadan Allah yimin bayani, adil ya ajiye wayansasannan yace luk my frnd, yar gydan marigayim.fawu ne yamutu yabar mata tsantsardukiya, sannan tunda nake a tarihintabantabajin ance anganta dawani ba, balleace soyayya tahadaku, batason maza tatsanesu bawanda yasan hujjanta dai,donhaka tun kafin kazama victim gwarakafita daga rayuwar yarinyannan kaidamazuwa kayi kuma two weeks zakayi katafigwara kanemi hanyan mai saukin ciretaaranka, aminu yaja tsaki ahap, saidai bamukara haduwa ba duk taurin kanta zatasauko, kamanta wayeni? AMINU GEE nefa!,adil dai baice komiba, ahaka suka mike, sukaficeWashegari salma taje shago donsiyan sabonphone cover ganin wannan jiya yafadi hakanyasa tayi niyyan siyan sabo, mutumim yamiko mata tana zaba, ta ajiye iphone dinakan slap din dake shagon, gani tayi andauki wayan, yayi danne dannensa, saitagayaciro wayansa dake kara tukun ya ajiyenatan, wato kenan yayi dialling numbansayakira anasa, dagowa tayi dontaga waye maiwannan guts din kuma meya taka a fadingarin kano dazaima rayuwanta shishigi,tabbas taganeshi shine yabuge matswayanta jiya sannan gashi sunkara haduwaa shago, batace komi ba, tadauki wayantaga har sunanshi yayi saving aminu ,bataredatace komi ba agabansa tacire sim din takarya sannan tace mai shagon yabata wanisim din, atake tayi register tadauki sim dintatatafi, batasan nata tsiraba don anan mayabasu dubu biyar yakarbi sabon layin datasiya din,tana isa gyda tayi wanka tabi lafiyangado, alokacin tadauko wayanta takira ummiaminiyarta anma ummi bata dauka ba,hakan yasa tamata txt tare da cewa salmafawu ce pick up, kafin takira ummin takiratare dacewa meya samu wayanki?, tacecanjawa nayi, ummi tace dalili? Nahaddudawani maye ne, shine nayi maganinsa,ummi tayi dariya jin for the first time salmata ambaci namiji, ummi tace sunanshi fa?Salma taja tsaki stop being a mean gurl, yshould i knw his name?, nanfa salma takawar da tadin suka gaysa ta kashe wayan,gun momynta taje sukaci tadinsu sannantahauro sama takara wanka kasancewarbata sallah, tsabar tsafta irin na salmainbata sallah ita kanta bata iya kirgawankanta, bini bini tayi wanka,bata canjapad saidai tayi wanka abunta acanja gabadaya, , tahau gado a.c dakin na busata tajiwayanta na ringing tana dauka tayi sallamatare dayin shiru taji waye, ya amsa sallamanbatare da ya karasa ba ta kashe wayan,tacire battery din, itakam wani irin maye newannan tahadu dashi?, tsabar takurinshiharta gane muryarsa, juyawa tayi zatayibacci taji an knocking daki, tamike dontasanbai wuce momynta ko mai aiki ba, tana budekofa gabanta yayi mummunan fadi, shimaduk ya razana, ya daga yatsa zaiyi maganaanma ya kasa, cikin zafin rai tace most ufollow me duk inda naje? Nd who permit uinto my house? Yace my house dai yajuyaya sauka kasa, binshi tayi taga gudunruwansa yana isa falon yace momy na bugamata kofan ashe idonta biyu, momy itace fawacce muke kira yanzu takashe wayanwacce nacemiki sabuwar budurwana dazakugaysa, momy ashe yar gida ce, ta kwanagidan sauki, momy kuwa yake takeyi, donbatasan mezata cemasa ba, tasan halinsalma sarai, yanzu zata masa diban albarka,salma na karasowa tazube ajikin momynta,tareda cewa momy ina wuni, momyn tarungumeta kafin tace lfy lao, ga yayanki fadaga u.s dan gydan hussiena ta ne, yazo yinwani business na sati biyu zaikoma beforesudawo gaba daya, batare data nunadamuwanta ba tace ohk. Sannan takau datadin tareda cewa momy yam balls zanciyau barinje kicin, shikam aminu naganin ikonAllah, tunda tafice momy take bashi hkr,saidai kayi hkr da halin ta, haka take,sannan inzanbaka shawara inbakaso kawahala kabarta kanemo wata na aura maka,yayi dariya tare da kade riganshi yace momyinaga saidai ita tayi hkr dani, don inajiajikina salma matatace, don haka momy kisaalbarka, ki kawaitar da idonki kawai, zannace mata nakuma koya mata yadda zatasoni, momy dai kallonsa take ganin yaddayake exaggerating kaman wani shahrukhan ,azuciyanta tace Allah yasa, tashi yayi yayihanyan kicinanan yaci karo da amal tana soya kayanmiya, mai aikin kuma na daka doyan, yanazaune harsuka zuba kayan miyan acikindoyan suna rolling, nan yajefa hannunsayafarayi tare dacewa mai aikin tatafizaikarasa tace tohm, duk abinda yakeyisalma bata nuna alamun akwai hallitan Allahagun ba, asalima cigaba da abunda takeyitayi, acikin nutsuwa yafara magana, salmatguduna kokuma shareni dakikeyi bashi zaisanafita a rayuwanki kaman yanda sauranmaza sukaji tsoro suka gudu ba, inaso kisanikinhadu da maye mai naci, don inkinganarabu dake toh tabbas na mutu, nadaukiwannan alkawarin wakaina, so is beta kisakeranki muyi soyayyanmu, by the way banyiintroducing kaina ba, sunana AminuGaladima, frnds call me aminu gee, agraduate of harvardth , in business admin.Right now am working wit my dad, ina zamau.s but zamu dawo nja mayb next monthkinga dole kenan zama dani, kuma saigashivo incidence mamanki twins sis din mamanako yakikace?, duk surutun dayakeyi batakulashiba bata kuma ce uffan ba, mikewatayi tafara zubawa a kwai tana soyawaganin haka yasa shima yafarayi, duk batakulashiba, sai yayi murmushi yace kinsanme? Dada birgeni kikeyi naji yadda kike wanisharewa it shows me how expensive u r,gayu bazasuyi wasa dake ba, i love ur styl oflife, kina burgeni,, haushi taji ta harareshi,ganin haka yasa yayi murmushi taredacewakuma hararki ma ta burgeni, u knw u r kindaone in town, i just love u salmat, tanajuyewa tafara zubawa a flask rabawa tayigida biyu tadibi nata tabar mishi nashitawuce yana binta abaya harta haura sama,kafin yaleka dakin tarufo dakarfi, hakan yasayaje kicin yadauko nasa sannan yazaunaakofan dakin nata yafaraci, tana daga dakitasa yam balls din agaba anma tarasameyasa tagagara ci gashi gabanta sai fadiyakeyi tarasa yazatayi da rayuwantaitakam,wannan tashin hankali damai yayikama? Naci kaman me? Haba its too muchshe has to do smfn8 yagamaci hankalinsa a kwance yabi guyazauna, tamike tayi sallah tabi lafiyan gado,anma me?,tagagara baccin itakam yazatayi?Lokaci kadan kadan saitaji kushunsa tawajeyana buga kofa, dabara yafado mata, tamiketa dauko hanga acikin wardrobe dintatabude kafan tare da cusawa dakarfi yamiketare da rike goshinshi data buga, ta karatusawa ita adole yatashi zata wuce shikuwayaki motsi, dataga tagaji cikin bacin rai tacekaiwani irin mayene? Katashimin akofazanwucez sai alokacin ya kishingida taredacewa i tot bakida bakin magana ne, ashe kiniya magana, anan yamike yasauka kasa,haushin kanta taji bashiri tanufi dakinmomynta tareda cewa momy nifa nagaji wlhmutum takuri kaman me? Momy tayimurmushi tace gashi agydan nan zai zaunahar two weeks, bakin ciki ranta ne bata iyahadiya ba, zata fara complain momyn tacekinga karmu fara, wannan dan uwankineaduniyan nan inna mutu dole gydansu zaki,sune gatanki akanme zakina wasu strangebehaviours? Batare da tace komi ba tace tohmomy zankiyayye tashi tayi tabar dakinwayanta tadauko tana dannan wayan ummiyuguda, ummi nadauka salma tafara bayani,nifs nagaji ji nake kaman na kasheshi ummitayi dariya aminiyata talk to me plx, waxgoing on? Dagangan tayi tambayan dontasan ba samun amsan zatayiba, can daitace next week zandaeo, nd get ready u rwelkmn ur one nd only dr. Nan salmatamata adduan samun saa, takashe wayan,wadhegari dasafe ma taje tasameshi agabanmomynta tagayda momynta sannantagaysheshi hakan yasa yaji dadi duk yaddatake da shariya aganinsa kamun kaine, tohtana da ladabi da girmama na gaba, hakanyasa yaji takara burgeshi, tamike takomadaki donta shirya tafiya office tana fitowa taisa office tagani abude ta tambayisecretarynta lafiya? Tace oga ne yace inbudemasa dat kina zuwa, haryamin presentingwayoyinki, anan ta laluba wayanta taji shiru,rTaleka taga wani iskanci yake mata a office,taganshi zaune akan seat yahada dayakan daya, tadauki files dinta tafita saigashitayi abunda zatayi awaje aikuwa yabita dukbata kulashiba, tamike tafice, tana tafiyaahanya tana buga sitiyeri, to cut the storyshort in one week aminu yadawo wa salmapest, ta tunzura ya kawota har wuya, jirakawai take tafashe, duk shariyanta saidayatunzurata ta, ko ina take yana nan, dukmutane datake access dasu yasamu, , gashitana ganin kwarjinibsa saita dago zata mishiRM tagagara taji gwiwanta yayi sanyi, datafara complain wa momynta sai ta tsaremata, momy na hankalce da duk abinda kefaruwa, itakam adduanta salma tasamutasauko ko itama zatayi aure kowa yahuta,tagaji da ganinta haka, kuma tasan damahaifinta nagari daya san yadda zaayi, tunitatafi gydan mijinta,Salma kuwa ta je shopping tagama dibanabunda zata diba, taje biya matan tace waniyabiya mata,tasan sarai shine saita share,harta fito zata tafi taga wani businesspartner dinta, suna gaysawa saikawai ganinaminu tayi agabanta yahada rai sama dakasa kaman zai kasheta, waye wannan?Bata amsa ba, sai partner dintan yayi cukuia tsaye yana kallo, can sai yace am sorry ,am just a partner, aminu yace does dat giveu d guarantee to talk to a married woman?Yabada hkr yawuce, salma kayan hannuntatazubar dakarfi yadda tayi shikanshi aminunya tsorata nan tafara " i dnt knw who you r,but can u plx get out of my life? I hate uuuu,i hatee u cnt u get it?; kayi stalking dina inasharewa kaki ganewa, karabu dani kokumakayi regreting dabaka tabayiba, yayimurmushi donshi baiji haushi ko kunya ba,dadi yaji atleast yaga tamishi magana, kumadama babban burinsa kenan tana gamawataje cikin mota, yadda ta fizgi motan saidayaja hankalin mutanen gun, tana tafiya hawayena zuba mata a ido, ummi ce takirata tanadauka tace gani agyda banganki ba, tacegani zuwa , yadda ta amsa ummi tasanakwai matsala anma tasan tambayanta bashawara bane don bazata gayamatabagwara tabari tazo saisuyi maganan, tana isagyda ummi tazo ta rungumeta, salmatadaure tace yaushe kika iso? Ummi tacetwo hours ago, meya sameki? Bata amsamataba tajata suka nufi cikin gydan, tazaunatasakai akan dinning wanda aka jero musukayattatun girki tana kuka, ummi cikinkwanciyan hankali tace Aminu ne? Salmabatace komi ba, nan ummi tacigaba. Kece atfault kingwada masa tsana kirikiri dax y heremained in ur head, neva hate someonebcox its d same as loving him, zakiyitatunanin shi, nd yagane hakanne yasa yayisticking, ki gwada masa being around doesntbuffles u, salma na sauraronta harta gama,wacce irin macece ummi? Basai tafada matadamuwanta ba nan da nan ummi takeganewa, rayuwanta na tafiya smoothlysaiyanzu ameenu yazo ciki yaruguza, , bataiyacin abinci ba, kwanyanta sai caji yake,bata gama idda tunani ba saigashi yashigodasauri ta tareshi fuska a daure. Idan kai bamaye bane kabar mana gydanmu, mararzuciya, yadda take maganan yatabbatarranta a bace yake saiyaji shima ranshiyabaci baya kaunar ranta yabaci, ya girgizakai tareda cewa toh salma, zanfitarayuwanki da gydanku, yajuya yafice, ummitagane tsantsan meke damunsu, ga alamundukka sun damu da juna anma dey didntrealise it, tayi murmushi ta yi sipping cokedinta tare dacewa"this two will mek aperfect couples", harya fita yadawo yace salmatinajiranki a duk lokacin dakika rage tsanataa zuciyanki, bazan daina sonki ba, i love usalma, wani harara ta jefa mishi bashiriyafice, tunda yafita, haushi da tausayinkanshi yake, gashi yayi alkawarin bazai karatakura mata ba as she wished, anma badamuwa zaicigaba da addua Allahyatabbatar masa da alheri , tunda yafitakuwa salma taja ummi suka wuce daki nanfa suka fara dawainiyan yiwa ummi murnandawowa dakuma kammala makaranta,alokacin mahaifinta yabude mata asibiti,wacce take xuwa gakuma maaikata anzuba,sunan asibitin ummiyu hospital tabbasasibitin yayi farin jini, kowa na son zuwagun, don ummi akwai kirki da tausayin bayinAllah, ga kyauta da taimako, duk abunhannunta bai sole mata ido ba,BAYAN WATA BIYUacikin wata biyu, har aminu yakoma u.sdaganan suka tattaro suka dawo nja gabadaya, tunda yataka kafansa yabar gydanharyau bai koma gydansu salma ba, kumabaikirata ba balle text, saidai tana makale azuciyansa, yazuba mata idone yagani,nufinsa akan insun daidaita toh kawai saiyasanarwa iyayensa, alokacin salma tamantashagaf dashi saidai lokaci lokaci takan tunadashi, taga rashin kyautawanta, duk wandatakkra shikadai ya tsaya mata rai , ana hakawatarana ummi tafito tsaf sunshirya zataraka ummi asibiti, suna zaune wani yakawowata patient saurayi kyakyawa, da alamumahaifiyarsa ce ba lfy, bashiri salma sukashive emergency da ita, yana tsaye a wajeyagagara motsi yagagara tsinana komi,gariganshi yaci squeezing, daga gani kayan yatsufa anma tsaf tsaf dashi, salma nazaunetakare masa kallo, tunda take bata taba jinnamiji yabata shaawan kallo ko taji tanasonshiba sai yau, love at first sight, anahaka saiga nurse tafito, tace masa jini akebukata, dasauri yace yaje adiba nasa, cikinrashin saa jininsu baizo dayaba, nurse dintabashi shawaran yasiya, yakalleta ido cikeda hawaye sannan yace nurse, wlh tlh bandakudin, kutaimaka, da a babban asibiti mukesu sukace mukawo ta nan saboda dr.ummiduk kudina na tattara, nurse kitaimaka, nursedin takawar da ido cikin rashin tausayi tacea a saidai kayi hkr, kanemo jini ba yaddazaayi nasiyarma da jini kyauta,shiru yayi,salma kuwa sarkin tausayi harda kwallanta,tamike cikin tsawa tacewa nurse din hakayakamata kina treating mutane?, nurse dinta tsorata sosai saboda tasan kusancinsalma da ummi zata iya rasa aikinta, salmatace muje ki gwada nawa ko zaiyi. For thefirst tym yajuyo yakalleta, wani yarrr tajiajikinta, yamata godiya sosai donhar idonsayaciko da kwalla, sukaje akayi saa yazodaidai, zata fara complain salma tace ko zanmutune kidiba, baruwana dawani karmafadiko narasa jini, aka diba aka jesawa. Alokacinbayan ansa ummi tafito tanemi salma tarasaanan nurse din take mata bayani, ummi taharzuka sosai dasauri ta isa dakin da akakwantar da salma, taganshi agefentatace wakai akabawa jinin? Ya kalliummi cikin nutsuwa yace wa ummata ne,taji haushi sosai yazaayi kawai tafara badajini batare datasan matsayin nata jikin ba, itstoo risky, tace zaka iya zuwa ganinmamanka, tashi yayi yaje suka masa bill,yazauna akan kujeran yayi tunanin duniyaaina zaisamu kudin yarasa, aikuwa salma nafarkawa ummi tafara fada tace mekikesonacewa momy? Inwani abu yasameki?Wannan bayi bane banason haka, salma tayimurmushi sannan tace ummi, ina yake?,ummi tayi kasaf sannan tace waye? Salmatace wanda kikagani atare dani, ummi taceawh yaje gun mamanshi, bashiri salmatamike kawai tafara tafiya duk da jirindatakeji ummi na rikota anma tana fizgewa,tana isa taganshi akofan dakin, zama tayiagefensa baisaniba yayi nisa cikin tunani,tace meya faru kuna? Da sauri yajuyomikeewa yayi yafara godiya duk yanayi tanakare mishi kallo, sonshi takeyi itakam , zatamutu idan bai amince mata ba wayyo ita,yace babu , ganin list din hannunsa tayitakarba, taga bill din tace shikenan bill din?kaman zaiyi magana sai yadaga kai kawai,tafahimce shima bamaison magana bane,talaluba taga ba jakanta, saita tuna yanadakin dasuka kwantar da ita, tuni taceyabiyota tacire dubu hamsin tabashihannunshi narawa yakarba, yace kiyi hkranma dubu ashirin da biyune, don Allah yayiyawa. Bata kulashiba , tafice dakin da akakwantar da mamansan tanufa taga tanabacci, saita zauna tana kallonta, tunda takekallonta saitaji tana sonta, bata taba sonmutane kaman irinsuba, itakam meyasa takejin haka?, haka tazauna agefrn matan nandakyar salma tajata sukatafi gyda, nan tajetanayiwa momynta labari abun mamakitunda tafara hankalin momy yatashi tacekarta kara wannan garajen, aiwannantsautsayi inya fada fa? Yaxasuyi? Washegarida sassafe tafito tasiyo kayan tea dasaurandu tazo dakin taganshi akwanceagefen gadon tatasheshi tare dacemasa yajeyayi wanka, yamike yafice anan tagaydataummakam kallonta take tayi, ta amsa taredagodiya tana raiham yagayamin yadda kukayi,dayadda kika taimakesa, ta girgiza kaitareda cewa bakomi yanzu dai kici abincinan tayita bata, haka ummi tashigo roundkawai taga salma, abun sai yafara batatsoro, suna zaune a office tace nikammeyene wai? Salma tace sonshi nake, ummitayi dariya tace u r not serious, u knw quiteright he isnt ur type, salma tayi murmushisannan tace but he deserves me, kina ganinsaurayi ga kyau, kuma kina gani kinsanakwai ilmi Allah nedai bai bada dukiya ba,ummi dai shiru tayi sannan tace ni i forgotto tell u, umar na gaysheki, salma tajuyowaye kuma umar? Owwwhhh i gotcha newcatch dinmu ko? Hehe so gist me how is he,nan ummi tazauna tafara bayani hes socute, caring handsome ke i love him, i wantto marry him, salma tayi murmushi sannantace ada in anfadamin haka i used to saysomeone is craxy but yanzu i can feel it, lovecan mek u go mad nd stupid, hakadaisukacigaba da tadi,Haka salma tacigaba da kulawa dasu haraka sallameta tadaukesu a motanta sukayihanyan gydansu yadda taga gydan ba yaboba fallasa, anan suka zauna suka kimtsa .Umman raiham nabata lbr, mijina yarasu tunraiham na karami, kuma dama danginabasuso aurena dashiba, hakadai na aureshiyazo yarasu wahala tamin yawa, hanyan cidakuma ciyar da raiham, anma yau da gobesai Allah kinga bara yagama jamia anmaharyanzu ba aiki, salma tace meya karanta?Ummantace saidai inyazo waya sammishi?Bayan yayi wanka yazo nan takara ganinkyanshi tace wani course kayine,? Yacebusiness admin, tace would u mindnadaukeka aiki? Ya kalleta sannan ya girgizakai no thnx, salma shiru tayi, shifa yake dabukata anma wani irin mutum ne? Yamacisaanta dosai dahartake lallaminshi, lalleduniya juyi juyi duk abinda kakeyiwa wanikaima zaa maka, cikin kwarin gwiwa tacemeyasa? Yajuyo yace babu, candai tagaji tatatafi, haka tacigaba da xuwa duk indaraiham yake tana stalking dinshi kumaharyanzu yaki karban aikin, saida ummansatasa baki ya yadda anma haka kawai bayasake mata fiska, watarana tashigo gydanrike da kaya niki nikiz ummansa sai godiyatake yamike tareda cewa inada maganadake, tabi bayanshi suna fita yace luk salma,i appreciate each nd evrtn u did to me, butcant u get it? M not interested plx leave mealone, kibarmin mahaifiyata kifitaarayuwanmu, , tayi jugum haka yawuceyatafi tunda take namiji baitaba humiliatingdinta irin nayauba, ashe haka aminu yajidata masa,? Ba aminu bama wainda takewulakantawa? Shiru tayi tana isa tafarakuka, itakam batasan yazatayiba, tana sonsasosai harcikin ranta, duk abinda yamata batazuciya dashi, txt tamishi tabashi hkr taredacewa duk da tasan bazata iyaba zatakokarta taga tafita rayuwansu, ummi kamhaushinta takeji tsyaya zaayi da kudinki dakyaunki da ajinki kifara bin wani low classnamiji yana wulakantaki? Salma tace bakigaabunda naganibaCan raiham kuwa ummansa ce tasashiagaba tana masa fada, yace umma dolenacireta arayuwanmu, umma ina sonta, inasonta fiye da yadda nakeson kaina, ummakinsan tafi karfina ba matar aurena bane,idan tacigaba dazuwa abin zaixo yafi karfina,hakan danayi shine daidai, bazan tabagwada mata inasomtaba, umma tafi karfinahakadai salma taci gaba da dannewa,anma inaa tagagara saboda son raiham dakecinta a zuciya gashi uwa uba, ko abincizataci saita tuna dashi, wani lokacin inzatakira ummi ko wani saitace raiham, ummikam soyayya take fafa da umar dinta, aranda tacika sati dayane taga baxata iyadaurewa ba, gwara taje tagansu, ta daukimota tabi ta store tayi musu siyayya sannantaje gydan, tana isa taganshi agefenummanshi tanashafa mishi gashin kai, hakasalma tadaure taje dasauri yamike cike damamaki zaiyi magana tace kayi hkr, gunumma nazo inga yajikinta, baice komiba, donAllah kadai yasan farincikin dayakeyi aransayau yaganta, duk da shi yahanata zuwaanma koyaushe addduanshi shine Allah yasatazo, yanaso yaganta ko zaiji sanyi dagaradadin dayake damunsa, tazauna takaragayda umma sannan sukadan fara tadi, yanasatan kallonta tagefe, tamishi kyau ainun,kominta me kyaune, ita dinma satankallonshi take, nan umma take tambayantayagyda dakowa cikin sakin fuska ta amsa,sukayita tadi, ummi ce take kiranta bashiritamike don ta tafi, tana fita ta aiko yara dakayan data turo, haka akashigo dasu kayanabincine da kuma masarufi na yau da kullum,tana isa gyda suka hadu da ummi tarinkafada, akanme zata shanyata? Tace comoonnnaje ganin habibina ne, ummi taja tsaki sostupid, aina mace ta taba xuwa hira gunnamiji? Salma watz wrong wit u? Ina aji daclass dinki? U r running after a low classguy, salma dai batace komi ba, saicewa tayifor the last time, if forever in ur life u wish tobe wit me, karki kara zagin raiham, u mustlove wat i love, i dnt giv a damn, ummihaushi taji har wuya, tazira mukullin motatafice,Raiham nazaune wani yaro yayi sallamasannan yace ana neman raiham, yafitoxuciyarshi fes, tana zaune a mota sanye daglasses tarufe fuska, tun dayake tahowatakare masa kallo, lallai dole salma ta rikice,namiji a zube , mehn he's so cute, dogonewankan tarwada, gashin kansa ya kwanta lufluf, ga gefen fuskansa da saje wanda yarufodaidai karamin bakinsa, idonsa dara dara gadogon hanci, uwa uba ga six packs, yandayake tafiya kadai dole yaja hankalin mace,yana isota yabuga kofan motan taja tabudetareda cewa zagayo kashigo, bai amsatabakuma bai motsa ba , alamun baida niyyanyin abunda tacetace magana nake!, ya lumshe idosannan yace zaki iya maganarki anan, afterolguna kikazo, be by my rules, ta girgiza kaitareda cewa barito ni infito inyaso sai muyimaganan, tana fita ta tsaya cak da kyau,daga sama yakalleta har kasa, tahadu kominata is gud, farace doguwa, sirririya me kirankalangu, muryarta daidai ke fita, dagaganinta kaga wacce takeda sonjiki dashagwaba, tace nazo ne inma magana akansalma, plx kafita….. Hannu yasa matasannan yace sorry to ask before kicigabawacece salma? Do i knw ha?, ummi taharzuka jitayi kaman tamishi diban albarkasaidai tana jin shakkansa, yana matakwarjini, tace bakasantaba? Den nabakaassighnment kaje kabincikamun wacecesalma??? Yayi dariya sannan yace shikenan?Ta daga kai, saiyace toh lemme mek it clear,u have no right over me to give me orders ,nd whoeva u r or wateva u r to salma i dntkia, u can plx help me tell her she shouldstop stalking me,Tayi shiru, ranta yabaci jitayi kaman tadaukihannu tawanka masa mari, tajuya dakarfitafuzga motan bata nufi ko inaba saigydansu salma alokacin salma nakan gadosai murmushi take taji dadi yautagamasoyinta, yadda ummi tashigo ne yatsorata ta, tace lfy? Ummi tafara fada indatake shiga batanan take fitaba, arayuwantata tsani wulakanci, yazaayi ne ma raiham yawulakantata, saidata gama ummi tayimurmushi sannan tace lez be frank witheach oda ummi yakika ganshi, hes soo cul uknw, i love it if yana magana, yafi kowa iyakiran sunana, kinsan me? Ill propose to himif shi bazai proposing dinaba, ummi jitayibata taba tsanan salma irin nayauba for Godsake salma meke damunki namiji ne zaiciubanki ya kwana lfy, salma tace har uwatayaci ill lay down for him, i love him bunch,tashi tayi tafara tsalle akan gado tana cewai love him bunch, ummi tafita ranta abacetakira umar tana masa bayani, nan yafaramata fadan akan meyasa zataje tayi maganada raiham? Wannan bayibane, itama nansukayi rikici kowa yakashe wayansa, ummanazaune ta nutsar da raiham tana gwadamishi kokarin da salma ke musu, tace kodonni ka saurarawa yarinyan kuma tundakanasonta aishikenan, washegari ya isagydansu salma ya aika akirata acemataraiham, dafarko taki yarda saboda tasanbazaixo ba , anma dataji dagaskene bashirita sauko kasa, suka gaysa nan yabatahakuri sannan yafara #salma tun randanafara ganinki duk da ummana cikina wanihali bai hana inlura dakeba, naji kinkwantamin arai, kuma Allah yataimaken ciknsauki kin shiga rayuwata, inasonki salma dukabinda nakeyi inayi don na samu nabarkikinfi karfina daga ni sai mahaifiyata, bayanita banda kowa kinga kenan dole na rikekaina da mutuncina, nan salma dadi kamanya kashetatace bakomi Allah yasaka, naji dadi wlh,nan fa suka fara soyyaya, abun shaawa,ummi tuni tahakura tabarta, momy ma tasamusu ido tana murna salma tasamu masoyi,abun mamaki shine yadda salma takesoyayya kaman tacinye raiham dama wandabaya abu idan yatashiyi saiyayi nahauka,suka shaku sosai, nan salma tadagomaganan aure yagwada mata baishiryabasaiya samu aiki, dole tasashi yakarbi aikingunta tabashi managern gun, nan da nantamawa momy magana akace ya turo,yajidadi sosai, yazo yazauna yace umma susalma fa sunce natura, umman tayimurmushi sannan tace tohfa yanzu sai asabappanka yaje kenan, aina ne gydansundama? Yana murmushi cikin kwanciyanhankali yace yar gydan muhd fawu ce,marigayi,nan da nan ta turnuke fuskanta,tareda cewa yadai banganeba, yar cikinsa?,yace ae umma akwai matsalane? Ta turnukefuska tareda cewa karabu dawannanyarinyan nagayama, kabarta ba magananaure na haramta, kasaf yayi da baki yanakallonta, haba umma mekuma tamiki? Tatsuke cikin zafin rai tace nace maka kabariko? In nina tsugunna nahaifeka kabarmaganan auren yarinyanan, tashin hankalibaa mata rana, tunda yake baitaba ganinmahaifiyarsa cikin wannan halin ba, tsoroneda firgita karara a fuskanta, rananbaiyibacciba yadda yaga dare haka yagarana, suna waya yacemata yana zuwa yanaisa yazaunar da ita kanshi a tsugune yacekiyi hkr salma ummana tace nabar magananaurenki, bashiri tamike tareda cewa karkakuskura kayiwa umma sharri, kaidai kaceminkafasa anma meya shigo da umma? Raihammeyasa zaka fasa aurena? Mena maka?Inada wani haline? Meye aibuta? Yajuyaidonsa jajur sannan yace wannan tambayanduk ki kwashesu kije kiyiwa umma natayi shiru hankalinta yatashi sosai,gashi bai dace taje tasamu ummanba,wannan rashin kunya ne, tace bakomi, dukyanda kayi ba matsala, tashige ciki da gudufadi tayi akan gado, ummi ne tashigo rike dakaya ahannunta tana murmushi salma gaashoben ankawo, saikuma taga salma akangado bashiri kawai ta isa kanta, sallma lfy?Tana kuka tayi shiru, ganin batada niyyanbata amsa yasa tatashi tashiga toilettadauro alwala sannan tayi sallah alokacinsalma ta tashi itama daniyan sallahn idarwarta tadaga hannu tana addua tana kuka,ummi kam abun yadaure mata kai, tohraiham yamutu ne?,kuma tahadu da momyballe tace momy nr, saitace raiham ne balfy? Salma ta girgiza kai ko mutuwan shi nebazan shiga tashin hankalin danake cikinsayanzu ba, saboda nasan ae narasashi harabada kuma kowama tarasa, anma yanzufa?Ummi tace banganeba, salma ta kawar dakai sannan tace cemin yayi ummansa tacekarya aureni , ummi taja tsaki toh can tamatsemusu, wazai ragu mu ko su?damadazu aminu gee yagama min magananki wlhharyanzu yana sonki yana kuma son yaaureki, salma jitayi kaman takashe ummi donbakin ciki, ummi tamike tareda cewa gaashoben ankawo kixo muje gun tela, inbaidinka mun nawaba ba inda zanje, salma tagirgiza kai, kije kawai ba inda zanje,ummitamike tafice tabarta don Allah yagani tajihaushi kuma taji dadi, haushin shine yanzuhar raihma sunkai suce basuson salma?Dadin kuma shine oho dai Allah yaraba lakai,aranan salma bataci abinci ba, dama bagwanar magana ba, shiru tayi, rayuwantayakoma so miserable tarame sosai, momyabun yamata ciwo, anma ta nuna mata tayihkr mutum baya auren wanda bamatarshiba, aminu jin wannan labari yasayadauki mota ya binciko gydansu raiham,raiham duk na takure yanason salma ainunbaisan yazaiyi daransa ba, but ummansatanuna bataso dole yahakura tunda aduniyannan ko kashe kansa tace yayi zai kashe,tana hankalce dashi anma tasan dalilinta,bazai taba auren salma, koda kuwa zaimutu,alokacin akayi sallama raiham ya amsa yaroyace ana sallama dashi ya figi takalmi yafitaganin aminu kuma baisanshiba yadaga mishihankali, aminu yakalleshi sama da kasasannan yace banazo don mutunci bane karkamanta cewa salma nasonka bahakan banezaibaka daman yin abunda ranka yabakaohkay?; raiham yayi murumshi sannamaminu yaci gaba dacewa tafi karfinka soders no need dama ta aureka, but inaso injidalilinka, raiham yayi murmushi sannan yaceduk kayi arriving at the same question,kanaso kasani meyasa narabu da ita?, tohbansonta, bazan iya da itaba, zaka iya zuwakanemeta inzaka iyaaminu yakaleshi u can continue , i jexwana tell u stay away from salma, raiham yakalleshi sannan yace "dat was wat i did socan u plx leave my compound?, batare da yakulashiba yawuce, raiham azaure yatsayayarike bango sosai, bazai iya rabuwa dasalma ba, sonta na neman masa illa,, aminukuwa da Allah zaisa raiham yamutu dayafikowa jin dadi, gydansu salma yanufa,tanazaune akan dinnig tarike cup a hannunta itabashan juice dintakeyi ita hankalinta bayawurin, saida yakai kusan minti goma yasahannunsa yarike cup din anma bata juyo ba,yabugata kadan tuni ta farga tareda cewaaminu mekakeyi snan? Yayi shiru taredacewa it seems u needed a partner, ta gydakai tareda cewa i will be alright, yayi shirusannsn yace yanzu nadawo daga gun raihamnamishi magana, daga idonta tayi alamuntanado taji mezaice, sannan yaceyagwadamun yahakura donhaka ki hakura,tayi shiru sannan tace i will, its a matter oftime, damuwana shine inaso insan hujjarummansa, nacewa bazai aureniba, innasanishikenan, aminu yace zankokarta naganasamu raiham din muyi magana,Wasa wasa yanzu sati biyu bacanji dukyanda raiham yazo yayi convincingummansa taki yarda, tace indai yar gydanmuhdu fawu, ne bata yarda ba batalamuntaba, sannan ko bayan ranta inyayibata yafeba, wannan abu yadaga masahanksli hankali hskan yaje yadawo ko abincikwarrariya bayaci sosai yatakuru sosai, komia sanyaye saudayawa zai rufe dakinsa yacikuka yafito, toh hakama salma gwaramasalman tasamu ameenu yana dan lallabintayana debe mata kewa, yakan tursasata taciabinci yafita da ita hakan na hanata samunslSpace din damuwa , watarana dasafeummansa taji shiru baifito sallah ba, talekataji shiru hankalinta yatashi dataga shisheme akasa, dasauri takira makwabtaakasamu aka kaishi asibiti, kasancewarasibitin da ummi ke aiki ne akusa,makwabcin nasu saiya kaishi gun, ummi tajeemergency suka samu aka cetoransa,alokacin sunfito kenan, taci karo dasalma da ameenu. Tuni ummi tace salmaraiham nefa, salma nanda nan hankalintayatashi bakaramin haushi ameenu yajibayace ke damukazo tadubaki yanzu kin rikiceakan wani haba salmat! Kuka takeyi sosai,ayanda ummi tace typhoid ne da malaria kedamunsa, toh yayita amai har ruwan jikinsayakare hakan ne yasa ya sandare, sannankanshi tasamu problem. A lokacin fitansusukaci karo da umma. Salma idonta jajurtagaysheta tawuce ameenu ma haka, sunaciki suna zaune ummansa a gefensa saigaummi tashigo bayan tamata bayanin mekedamun danta. Tace mata sannan dankibayacin abinci, akwai alamun damuwaaransa, zai iya masa illa, umma takalletasannan tace likita kitaimaka, wlh shikadai namallaka na wahala a duniyan nan, shikadaina tsira dashi, ummi tace toh ai saikitabbata yacire damuwansa. Umman tasunkuyar dakai tafara kuka tana cewa"raiham ka yafeni, bansan haka zaifaruba,anma babu yadda zaayi ka auri kanwarkauwarku daya . Ubanku daya Ummi tayi jum!Can dai tace banganeba anty, soyayya yakeda kanwarsa?, umma ta daga kai tasharehawaye sannan tace anma baisaniba labarindogo ne, anma kanwarsa ce yake nema yaaura, ummi haushi taji watoma salma nacantana mutuwa akanshi shiyanada wacceyakeso daban? Ummi tace to mama meyasakika bari? Tace bansaniba saidaga baya,ummi tace Allah ya kyauta barinje, harta isabakin kofa sannan tajuya tace umma meyesunan kanwarsan,? Ba tantama ko tsorotunda atunaninta ummi likita ce kawaibatasansuba tace SALMA,ummi gabanta nafadi tawuce office shirutayi tana tunani ba abunda baizo rantaba?,ko dai wannnan matan tana neman hanyanraba salma da raiham ne, anma inbahaka batoh kenan ta taba auren muhd fawu, abunda rikitarwa, tana haka saiga salma tashigotana tambayanta ummi yajikin sa plz? Ummitace ke bawannan ne matsalan ba, can u plxsit down, salma ranta abace tace yazaayikice bawannanne matsalan ba for Godsake ur talking abt my hrt, ummi dai shareta tayidata gama matsifan tazauna, tambayanafarko ummi tace. Dad dinki yataba aurebefore yarasu? Salma taja tsaki kingabanson haka meya kawo wannan maganan,?Momy itakadaice matarsa, ummi tace anmadanake tambayan umman raiham tace yanasoyayya da kanwarsa uwa daya ubaya kumasunanta salma, shiyasa tahana auren, salmata girgiza kai tareda cewa tana nemanexcuse ne kawai, nan dai suka fara jajantamaganan, salma dai abun ya tsaya mataarai, tana isa gyda tace momy akwaimagana, momy nacin abinci tace inajinki tagimtsa sannan tace dady yataba aureawajene? Sannan yanada wani yara bayanni? Momy ta kare mata kallo sannan tacebabu, ko daya meya faru? Tamike taredacewa shiririta ne umman raiham ne waidalilinta nahanashi aurena shine uwarmudaya ubanmu daya, momy dasauri tace. Ainatake? Batare data damu ba, tace suna asibitiyanzu raiham din ba lafiya, ba shiri momytadau waya takira hussienanta mamar aminutareda cewa husiena akwai magana kiyisauri kizo gyda muhadu, tana isowa sukashige daki, nanfa momy tamata bayaninyadda sukayi da salma, hussiena tayi dariyatace mayb shiririta ne anma kinsan hafsatbazata taba kusantarki ba tunda deal dinkuhaka tace, momy tayi shiru tace kar salmatagane gaskiya inyi loosing dinta i cnt carryon, is beta muje asibitin muga ita mamanraiham din , hussiena tace mezamuje cewa?Hassana tace inba ita bace saimuce munjitace uwarsu daya ubansu daya shiyasamukazo muji hujjanta tadena fada tanemiwani hujja intana neman rabasune,dawannan shawaran suka nufi asibitinan ummi na office taga shigewarsuinda suka tambaya inda aka kwantar daraiham sukaje, budewan kofan yasa tadagaidonta dontagansu, ta mugun tsorata batataba tsammani zasu kara haduwa ba, momytazauna jikinta na bari hafsat!!! Tayi shirutareda cewa mufita don Allah karmutasheshi, sukayi shiru suka fito verandernasibitin suka zauna, hussiena ranta abacetafara cewa bamunyi dake zaki nisancemuba?, tace don kuyi deal dani shine zaisakarnasake nayi rayuwata?am also a freecitizen, momy tace haba hafsat kinsan illanabunda kika aikata, yanzu ga yarannansunhadu infact ta ina uwarsu da ubansusukazo daya? Hafsat idonta jajur tacehassana kar kudinki yaruda miki ido, kiminbutulcin taimakon dana miki, kinfi kowasanin salma da raiham yayan waye acikinmu,sannan wanda akayi dominsan naga yabardoron kasa, y not kiyi accepting?, momyranta yabaci sosai donhaka cikin fushi tace,idan danki yawarke inaso ki tattara kibargarinnan, karna kara ganinki, hafsat tayidariya tace ada kenan hassana! Yanzukamsaidai muyi fito na fito, kinsan kuma kexakiyi loosing, so yanzu bazan gudubainanan, inkuma yara suka nace aure, sainafadamusu!, momy ta harzuka zata makurohafsat tuni hussiena tajata suka fice, rantayabaci sosai, salma nazaune akan kujeratana tunanin halinda masoyinta ke ciki saigamomy tashigo cikin rudewa da bacin rai tatashi zataje gunta ta dakatar da ita,salamatu ! Idan nina haifeki! Idan na isadake! Kicire raiham aranki! Kifita harkarsa !Nagayamiki, salma shiru tayi don tunda takebata taba jin momy takirata da salamatu ba,hakanne yasa hankalinta yakara tashi kukatafarayi, dasauri takira wayan ummi tajeasibiti tasameta yadda take kuka ya tsorataummi tace, ummi nazauna agyda anmakirikiri annace sainayi aure, yanzu nafito damiji danfinsa sunhana nima danginasunhana, ummi tayi shiru can tace inagasalma ki hakura, anma akwsi boyeyyenalamari tsakanin iyayenku don dazumomynki da maman ameenu sukazo nansuka hadu da umman raiham, sundade sunamagana kuma dasuka gama maganan kowaranshi abace, salma shiru tayi, can taceummi kitaimaka min plx kinsan dalili? Tayishiru can tace naji dai sunacewa kedaraiham uwarku daya ubanku daya shikeman,anma a tsakanin momy da ummansa bansanwaye daya mamanki ba, salma kantanetafaraji yana juyawa, bata taba sanin tashinhankali irin wannan na existing ba, tamiketsum daniyyan taje dakim da raiham yakedomin taji bayani tanaso tasan dalili meyasabasason aurensu, cak ta tsaya dataji yafaramaganaAcikin dakin kuwa raiham yafarka yazuba wamahaifiyarsa ido yaga tsananij tashin hankalia idonta, yace umma ina neman alfarma takalleshi tareda cewa in akan salma ne karkafara, yace a a, can saiyace umma kinhananiaurenta baki gayamun dalili ba, anma nagamomynta tazo dazu kuma kunyi maganaalamun kunsan juna kenan, umma ni ba yarobane don Allah kigayamun zan fahimta donAllah umma,Ta share hawayenta sannan tace ba aure atsakaninka da salma, gabansa ne tayimummunan fadi yace umma meyasa?, tacesaboda kanwarka ce,Hawayene yazubo masa a ido tareda cewaumma tayaya tazama kanwata, ba aurenmahaifinta kikayiba, da ubanta nima daubana, tace ae, anma nina haifeta! Saidaikwan hassana da muhammadu ne, . Shiruyayi abun yadaure masa kai, ummabanganeba,a share hawayen daya zubo mata taceraiham kabari kagama warkewa, wannan bamaganan asibiti bane, tsuke rai yayi sannanyace nikam na warke, abunda zakiyi shinekigayamun gaskiyan meke faruwa, ta gogehawayen fuskanta sannan tafara bada lbr"Raiham nida mahaifinka usman munyiauren soyayya, duk da nayi makarantanagama diploma na, mahaifinka ma haka,iyayenmu dakyar suka bari akayi auren nan,muna zaune a azare lfy lao cikin rufin asiri,toh sai Allah yabani haihuwarka ahaka nahaihu nasa maka suna Raiham anmainamaka lakani da sultan muna renonka dukda matsala damuke samu na yauda gobe tafannin abinci da sauransu, mahaifinka ya yiniyyan neman mana sauki duk inda yaji ananeman aiko zaije. Ganin haka yasa natausaya mishi sosai,Atake naji makwabciyatananeman masu wanki wanda zaana kawomana wanki muyi, na tambayi usman yakiyadda acewarsa kenanfa zanna xuwa gidanmasu kudinnan ina aiki kayan wulakancihakan bazau yiwuba, toh sai wani abokinsaya gayyace shi suje lagos akwai aikin kanruwa dazasuyi, ahaka usman yatare ni, yalallabeni acewarsa zaije yadawo zainemomana arziki dakyar na amince bayanyafahimtar dani cewa babu aiki akusa indazai samu,toh anan narokeshi ko zanyi aikin?Saboda ina debe kewa, sannan gadawainiyarka, ya yadda min, alokacin muhdufawu na zama a azare, dan gombe ne, anmaharyau bawanda yasan dalilin daya tafiazare don yazauna, yanada kudi sosai, idanbance mishi nafarko ba toh tabbas shinenabiyu acikin tsawon masu arzikin azare,anan nasamu wanki, ina wankin matargydan wato hassana, mata ce mai kirki sosaida kyautatawa, kuma Allah yataimaka jininmu yahadu sosai da ita, dalilin haka yasamuka shaku, harta daukemin nauyin, wankindanakeyi, tafarasa ka a nursery school,sannan taciyar dani dakai, duk wasudawainiyarmu tadauka, har lokacin bansamuaika daga mahaifinka ba, akalla kusanshekara hudu, kowa yanuwa anfara surutaiwasu nacewa na je akunce auren usmanbazai dawoba, wasu nacewa yagudu yabarni,alokacin babu irin tunanin dabanyiba, anmakullum inakan sallayata kullum ina addua,hakanne yasa nakejin saukin radadin rashinmahaifinka, a tsawon wannan lokaci akallahassana da muhmdu sunyi shekara 14 basuhaihuba, tadamu sosai, donkuwa kaikankasonka take kaman yaya, kadawo danta komitace inaa sultan? Tasiya abu tace wannanna sultan, nan da nan maaikata suka faramaka hassada, nikuwa ganin haka naragezuwa dakai gidan ashe ta hankaltu, hakanyasa takira dukkan maaikatan tamusuwarning karkowa yakara treating dinka waniirihankalina duk dahaka bai kwanta ba, saiina kaffa kaffa dakai, ahaka muhmdu dahassana sunje asibiti a u.s nan aka sanardasu itace bazata haihu ba, anma shi zai iyahaihuwa, hakan yasa hankalinta yatashitanemi shawaran likitan, acewarta karsurkuwarta taji ko dangin miji zasusashi yakara aureSannan itama tanaso tahaifi nata, tayi kukawa likitan sosai nan likitan tabata shawarantanemi surrogate mother donta samu Da,hakan kuwa yadan kwantar mata da hankali,sundawo tanemi shawaranshi akai,yanunakin amincewarsa acewarsa wannan alada nena turawa, anma tayi mishi kuka yajitausayinta duk ta rusa masa tunani, nan yaamince mata tareda cewa wazata sakayamata???Ina daki agyda saiga hassana, tazo da lodinkayan dadi takawo maka da kayan sawadasauransu, azatona tazone kawai donhassana takanzo tagayshemu, shine takecemin tazone tarokeni alfarma, "hafsat naduba duk duniyannan ayanzu bawacce naamince da ita kamarki, wani taimako nakesokimin hafsat. Tana fada tana kuka, tuni narude nace mata "hajiya wani irin taimakokike bukata haka dakike kuka akai? Akwaiabinda zakinema aguna kirasa ne? Tanakuka tace wannan hafsat babban taimakone, nan tacemun "likita tacemun bazan iyahaihuwaba hafsat, hafsat ina tsoron danginmijina karsu sani agaba susashi aure,kitaimaka hafsat, duk a tunanina lokacinzatace inbata kaine anma sainaji tace zakihaifamun ne, nayi murmushi nace indaiwannan ne kinsamu, inhar maigida nayadawo idan nasamu nakara haihuwazanbaki na miki alkawari, tarike hannunatareda cewa a a hafsat bahakaba, zaacirekwan mijina sai asamiki, kekuma saiki rikekwan harki haifamun, " tunda nake bantabashiga tashin hankali irin wannan ba,gashinan dai kaman abu mai sauki anmashiyafi komi wahala tana rokona ne daabunda banda tabbas nikaina zanyi rayuwanan na girgiza kai tareda cemata kiyi hkrhajiya anma abunda kike rokona nayi tamkarsaida rayuwata ne, inada aurefa, ta mursukafuskanta sannan tace bayanan fa, yanzuharki haifamun insha Allah bayanan, sannankuma kinga dama dangin mijinki sunsakiagaba keda danki saimu tattara muyi nisadasu, kitaimakamun hafsat, kuka nakeyi nabata hkr, ahaka tatashi tatafi, tundagalokacin rayuwata tafara barazana hafsatnakan rokona, kuma tanamin barazanan idanbanyadda ba rayuwata zata shiga hatsari,raiham kaine farincikina kaine burina, gashiduk rayuwanka na hatsari ga dangin usmansuma sunzo sunsani agaba narasa yazanyi,tashin hankali ga usman yaki dawowa, gashihassana saijara ramewa takeyi rayuwantasaikara dunkukewa yakeyi hakan yasa natausaya mata sosai wata rana nadaukeka nanufi gydanta muna shiga nace mata naaminceyiba murna kaman mushige cikin juna,duk tunanina kaine, anan tanema mana visanida mijinta da ita dakai, mukaje cairo, ananmuka samu asibiti mukaje, anan likitantazaunar damu dontamana bayanin yaddaabun yake tagwadamin shi surrogacy gudabiyune akwai gestational dakuma traditional,toh shi gestational din zaa dauki embryo dinita hassana asamin tru a process(IVF)invetro fertilization, inyaso if ansa so it meansni am not related to yaron dazaa haifa.Traditional kuma da embryo na zaasaka ayiusing kwan muhmdu kaga kenan i amrelated to the child. Likitan tabada optionakan wanne zaamin, ni batare da najira konayi tunaniba nace ayi gestational din,inyaso idan nahaifa musu nasan ba yatabace, hankalina bazai kwanta akansu ba,haka kuwa akayi aka dauki kwan muhmduaka sa a embryo din hassana aka budemahaifata akasamun, muka koma gyda,tumdaga lokacin nafara rainon ciki, nagagata sosai agun hassana da muhmdu duk dasuna yawanyin fada acewarta yana fifita niakanta don yaga inadauke da cikinsu,sunshayin fada bana shiga damuwatamukoma gyda kar usman yadawobaisameniba, zunubin zaimin yawa, mukadawo gyda azare, inda suka nace sainazauna dasu, ahaka muka zauna harna haifisalma, randa nahaifeta sunyi murna sosai,hassana tayi godiya sosai, ahaka yaruwartahussiena da u s sukazo suna, aka radawayarinya suna salamatutundaga lokacin naja gefe dasu, sukacanja mana gyda, suka dauki nauyinkaratunka hassana tadauki kudi miliyan 100tasamun a account sannan takirani wataranatacemun idan ina kaunar Allaah nabarmaganan sirri, itada mijinta zasu tashisukoma abj anma don Allah karkowa yasanimijinta dan siyasa ne hakan zai iya batamasa reputation dinshi, nayi maamaki sosaiaganina hassana tasiyeni ne saidaibawannan bane matsalan, har lokacin usmanbaibada ko aika ba, gashi lokacin kanaprimary 2, bayan tafiyansu banfadawa kowaabunda yafaruba, sannan kudin data samun ,a hankali nake amfani dashi shine nattaranadawo garin bauchi nasiya mana gida ,anma a lokacin banyi tunanin nafara aiki baduk hankalina nakan kayi karatu, sannan kome kace kana so nake siyama bana tunanibiyu, kashiga js1 aka kawo mana labarinhatsari da akayi harda mahaifinka, nayi kukasosai, don aganina namishi laifukadayakamata ace ya gafarceni akai, tundagalokacin nafara ganin laifin abubuwan danaaikata, gani nake zunubaina bazasu barninakwanta a kabariba, tashin hankalin dayasaharyau kake ganin banda lfy, sannan rashinsamun sanaa bakaramin illa ta na yayiba,don daga baya anzo anyi disclaiming kudin abanki, banda right nacirewa gydan damukeciki nasiyar nanema mana karami sabodainsamu inbiya kudin makarantanka kagama,burina ace kagama kasamu aiki, gashi harlokacin dana kwanta ciwio ka kawoni asibiti,shiyasa naji son salma daban yake, anmatunranda kagayamin yar gydan waye nagwammaci rashin xuwanmu nan garin,raiham don Allah kataimakeni kajanyemaganan aurenku, hawayene fur a idonsa,yace umma ai akwai aure, kinga ba yarkibane, tayi shiru sannan tace a a raihammaganin kar ayi kar afara, banma sanmatsayina a addini ba, kabarni naji dawannan guiltyness karka karamin wani,murda hannun kofan tayi hawaye fal a idontahafsat tarazana da ganinta cikin firgita tacesalma? meya kawoki nan? Tana kuka tacenaji duk abinda kikace, tanemi gu tazaunatarungumi hafsat sosai tareda cewa kiyiminafuwa ina miki kallon mai laifi akan rashinyarda da aurenmu, cankuma saitamike taficedasauri ta fizgi motarta tanufi gyda momynakan kujera duk hankalinta yatashi salmatashigo fuska a turnuke, momy tamike lafiyameya faru? Cikin bacin rai tace inafa lfy,inada uwaye biyu, bansan matsayina ba,bansan wacece uwata ta asali ba, shiruhassana tayi tadade tana gudun tashinhankali irin wannan, wannan ranan tadadetana gudunsa, salma tazauna tareda cewa nidukkan wannan tashin hankalin meyasa bakitaba gayamun ba? Haba momy? kuka takeyisosai bashiri tamike tafice tabarta agunA asibiti kuwa ummi tasamu ta sallamiraiham hankakinshi duk yatashi shi babbandamuwansa yanzu yasan matsayinsa, kenansalma tadawo kanwarsa? Ah toh anceummansa tahaifa ne kawai, anma ba uwartabane, toh ta shayar da ita kuwa? Kansa cajitake sosai babu irin tunanin dabaiyiba, tashiyayi yafice sai gaban umma, yace ummainkina kaunar Allah kinemo malami yawarware wannan almaran, tayi shiru taredacewa banki zancenka ba anma inaso kasaaranka cewa bazaka taba auren salma baWasa wasa sati biyu kenan, salma gabadaya tashare hassana, bata shiga hidimarkowa hatta ameenu gee ma yanzu shareshitakeyi, kowa tacire a rayuwanta har unmi,idan tarufe kofa bata budewa sai tsakardare, tagagara gane me daya zata yardadashi waye uwarta na asali?, she has to suehassana to court! Mikewa tayi tadaukowayanta takira lawyernta tareda cewa i wantto file a case, against my so-called mother.Aminu gee yafito daniyan fita yaga lawyertashigo, tambayarta yayi metazo yi tagwada masa akan salma ce takirata, nan danan ran aminu yabaci Wat nonsense!!!! Howcan she be so stupid? Lawyern ta ce noodnt blame her, tunaninta kenan ill handle it,kaje kawaiyafice rai abace, itakuwa tashiga sukashiga daki salma tarufe kofan nan tazayyana mata komi, lawyern ta kalleta tacesalka basai kin kaita court ba, according tothe laws hafsat ce legal mother dinki, tundaita tayi nakudarki, but mayb a addini akwaiyadda akayi bayani so if tanine i thinkkunemo malami yacwarware muku,Raiham,hafsat, hassana,hussiena,aminu saimalam ali, dakuma lawyern su siddiqamuktar suna zaune, kowa nasonjin. Mekefaruwa, nan malam yabude taro da adduasannan yafara "muntaru ne dan fahimtanjuna kuma muntaru ne don asasanta wannanmatsala da ku iyayen kuka shuka shekarudasuka wuce kuka birne don karkowa yasani,anma kunmanta Allah na kallonku , kungaabinda kuka birne yatono, tunda gashi yayasunhadu, maganan gaskiya anan shinesurrogacy dayawan malamai sunce haramunne!, domin kuwa a musulunce haramun neadauki kwan namiji asa ajikin macen dabamatarsa ba, idan kuma har Allah ya kaddaraanyi hakan cikin rashin sani to idan aka saajikin mace budurwa toh wannan danyaxama taharam(ana fuskanatarta da zina) ,kuma bashida gado inkuma matar aurece todan yazama na mijinta, koda kuwa ba kwanmijinta bane ajikinta,kuma hakanne hukuncidaidai da idan andauki kwan wani namijidomin asawa mace tahaihu saboda mijintabaya iya fitarwa, sannan wanda sukabadakwai don amusu hakan basune iyayenyaroba koda kuwa sunyi yarjejeniya akaine,sannan dalilin dayasa aka hana hakan amusulunci shine yakan tado da matsalolikaman wacce batayi aureba idan tayi hakanzata haihu, kunga kenan tarasa yancinta namace , sannan wacce tadau cikin zata zaunaa matsayin uwace, a addini wacce tazohaihuwa tarasu toh tayi shahada kungakenan yaxama advantage akan waccetabada aron mahaifa donhaka ne shariatakafa hujja cewa tunda zaabada aron kwaida mahaifa gawacce ba aureva tsakanitamkar an ketta hiddan ubangiji, acikinyadda Allah yafada acikin alqurani cikinAl'mumin 23:7 (whoever goes beyond thatare indeed transgressors, wannan aiki yanajanyo husuniyar tunani a kwalkwalwan yarowacce tabada kwai a haifeshi ko waccetarike cikinsa tahaifa? Irin wannan yaroyarasa wannene ta asali uwarsa, sannansukansu zasuyi fada, tunda kowacce tanaganin itace da yaron, donhaka ne musuluncibatason husumiya, maganin kar ayi karafara, dafatan kowacce tafahimta inda na4 barrister siddiqa muktar takaleshi tacemalam mungode da bayaninka, yanzu kenanaganinka wacece take da daman salma?Malam yace hafsat ce, sannan koba itabacebabu aure a tsakaninsu da raiham dominkuwa sunsha nono daya, kinga kenan aureya haramta, nan sukayi shiru tsit , gafsat dahassana da salma kuka suke sosai, babuwanda yakai salma rikicewa aganinta anmayar da rayuwanta ball kowa yabuga yaddayakeso, tasha kuka sosai, nan barristersaddiqa ta ce muma a dokanmu nananhafsat ce take da dama akanta, raihamsadaukarwa yayi yarasa mata har abada,shikam yaxaiyi? Ashe kanwarsa ce, doleyahakura, haka suka tashi suka rakamalami, wanda yabada shawaran raiham dasalma su hakura, sannan ya gwadawahafsat da hassana kuskurensu acewarsawannan babban kuskure ne, sannan gashimaxajensu duk sunmutu, balle susan me akeciki akarshe yabawa hassana hkr wacceaganinta laifinta ne na gajen hkrn datayiakan haihuwa, hakanne yasa tazama soodesperate tahaihu hartaje ta aikata abundatayi anma ta amshi laifinta da niyyan rokonAllah gafaran abunda ta aikata, aminu kamfarinciki har kasan tumbinsa aganinsa kofadayace yanzu tsakaninshi da salma. Baudawani matsala, hussiena ta rarrashi yaruwarnata yayinda hafsat da rsiham suka mikedon tafiya salma daki takoma bazata iyakallonsu ba, ace dukkansu suna da bangarena jikintasati biyu kenan salma ta gagara samunnutsuwa, tarasa wani irin karba zata kemusu,ahakadai aminu yake shishige mata,dakyar yasamu tasauko sannan ne tajetatasamu hafsat wacce take kan sallaya,hafsat na ganinta jikinta yayi sanyi bayansungaysa tace mata tanason sutashi dagawannan gydan ne, hafsat batasoba saidaisalman tanace. Hakan yasa suka tashitanema musu gyda ata g.r.a, mai kyau, harwannan lokacin basu samu sunyi magana daraiham ba, shiyanzu kunyanta yakeji. Itamahakan, hafsat ne data lura da hakan takirasutace duk kudena wasan boye boye dakukeyisalma raiham yayanki ne, donhaka ku kauceda maganar aurennan, kinemi wani Allahmuku albarka, agyda ma momy rokonta tayitana kuka salma kitaimaken don Allah ki auriaminu, ganin kowa yasata agaba, balle uwauba ummi yuguda data kasa tsaye ballezsune kullum magananta kenan salma taamince da aminu, shima ogan yana nanamakale da ita, ita tarasa meyasa anmatana ganin aminu ne a matsayin yayantabanda miji, anma babu yanda ta iya, dole taamince, anan nema momy ta shawarcihafsat da su dawo gydanta suhadu suzaunaacewarta salma aure zatayi baxataci dadingydan ita kadaiba, koda suka dawo nan akafara maganan biki, akan zaa hada bikinsalma da ummi tare, tohfa, nikainaalkalamina bushewa zaiyi idan harnacezanrubuto muku yadda akayi bikin nan,abinda nasani kawai shine naira taciubanta!, gydan jaridu da tv kowa na nunabikin, dama jira akeyi aga wazata aura ikonAllah, nan suka tare agydansu bayan sati daakayi ana shagalin biki, salma da aminu. Saiummi da umar, Allah yabasu zaman lfy,washegari aminu yabata kyautan diamond,taji dadi sosai, anma bbatasan shi yafita jindadi ba, yadda takama kanta takai mishibudurcinta, umar din ummi ne yake cewanikam nayi mamakin meyasa bata auriraiham ba, nikam WACECE SALMA? A murdetake,,,,,,,, ummi tayi dariya tace tabbas yaddatake a murde haka komi nata yake a murde,Bissalam, na sadaukar da wannan labari tomy family, The fawu family gombe , i loveyou all, muhadu ana gaba BUDURCINAYANCINA,<p></p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-29994013518420138162021-04-22T21:23:00.003-07:002021-04-22T21:23:41.423-07:00WATA UWAR Complete Hausa Novel<p> </p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-R70cQh9r9fA/YIJLFMyypGI/AAAAAAAAJnc/BcLjzshCiEYSEIb9bFDAVgcmOh1AbdE4QCLcBGAsYHQ/s2048/WATA-UWAR.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="WATA UWAR Complete Hausa Novel" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="310" src="https://1.bp.blogspot.com/-R70cQh9r9fA/YIJLFMyypGI/AAAAAAAAJnc/BcLjzshCiEYSEIb9bFDAVgcmOh1AbdE4QCLcBGAsYHQ/w400-h310/WATA-UWAR.jpg" title="WATA UWAR Complete Hausa Novel" width="400" /></a></div><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p>Ina mai miqa godiya da Allah da yaban iko nai nufin fara wannan novel mai sunan 👵🏻WATA UWAR👵🏻, sakamakon wani labari da aka sanar dani dazu da safe, wanda nima shaida ce abubuwa da dama sun faru akan ido na. Naso barin shi a raina amma duba da cewar akwai wadanda ke min magana akan na fara novel, ina ganin ba zan iya ba,😱 yau nayi tinani nima ina son na bada gudummawa ta ta wannan fanni.😎 Allah yasa yanda na fara lfy na gama lfy, Allah yasa kuma kuso shi ya amfanar da mu baki daya.❤</p><span><a name='more'></a></span><p>Page 1:</p><p>A guge ta fito daga dakin tana kuka, sakamakon dukan da innar ta ta biyo ta da shi, kamar ba ita ce ta haife ta ba , duka ne ta ke mata da wata qatuwar muciya, wanda in da sabo ta saba, amma da yake na yau yafi na kullum shi ya haddasa mata gigicewa, kuka take tana " dan Allah inna kiyi hakuri bani bace hinde ce tai fitsarin ta tace nice ya kamata ki gane vani nake yi ba inna" " sharri kenan kk nufin auta ta zata miki ko?" Inna ba haka nake nufi ba ki duba ni ki gani ki duba ta ita tai fitsarin ta" lallai baki daku ba ne ina fada kina magana ra ra ra ra kamar redion da bata da makashi" ta zaburo tayo kanta tana fadin shegiyar yarinya baqa, ni anya ba canjan ke akai ba a asibitin binni? Saida nace kar a kaini haihuwa birni aka dage sai an kaini ga haihuwar hannun likita bokan turai me ta jawo min haihuwar asara haihuwa ba riba" inna dan Allah ki daina fadan haka Allah ne ke halittan kowa shine yasan arziqin kowa ya zai kasance ba wanda ya san ya rayuwar shi xata kasan ce" tana yi tana kuka kamar ranta zai fice a jikin ta idon ta yai jawur doqon hancin ta sai majina yake fiddawa ta wahala, da dan qaramin bakin ta da ya dade da bushewa, tana tsayen taji an kwado mata bokitin qarfe a gaban ta " gashi nan dan uban ki maza ki tafi ki dakko ruwa ki fara aikin gaban ki dan banga amfanin ki ba da ya wuce aikatau ke dai, tinda nasan ko gaba ba wani mashinshinin kirki zaki ba saidai kiga auta na farar mace alkyabbar mata tana abun arziqi amma banda ke, kin tashi ko saina sheme ki" ta wurga mata takalmin qafarta, ta dau bokitin kenan ta juyo" tace inna da kin bari nai sallah sai na je nai aikin dan Allah" iyeeee ina ga abinda zaki kina ga abinda kk so yo ke ko sallar ma kikai ai nasan ba wata me kyau zaki ba, dan haka ba karbuwa zatai ba, maza kije ki abinda na saka ki inyaso kinyi sallar" ta saka takalman ta ta kama hanyar soron gidan su kenan baban ta ya shigo daga masallaci, tana hada ido da shi ta kauda kanta qasa ya wuce ta wuce dan ya zama sallamamme a gidan bai da katabus innar Hinde ta gama da shi sai yanda tace a gidan akeyi, dan kuwa baya aikin komai dai noma, itan ma ba wani abun kirki yake tabukawa ba, ita ke ci da gidan amma dik da babun shi yana qoqari in ya samu a ci mai dadi a gidan ya faranta masu, topa a lokacin ne zakuga fara'ar innar hinde ba qaqqautawa ranar har mijina zata ce mai amma, a yi wanka a ranar dan wanka ba wai yana cikin tsare2n ta bane ita in kunga wankan ta topa zata biki shima ba kowanne ba, sai wanda ta so.</p><p><br /></p><p> Dawowar ta kenan daga debo ruwan Hinde ta fito da buta da niyyar diban ruwan tana sane ta tankade ta yanda bokitin zai zuba a jikin ta yana ko xuba ta sa ihuuu " wayyoooo Allah na inna ta kashe ni da asubar nan ta kwaran ruwan sanyi wai saita rama dukan da aka mata akaina" tana gunjin kuka dan mamaki Nasreen bude baki kawai tai tana matuqar mamakin wannan qanwar tata da tabawa aqalla shekara uku take hada sharri inta girma ya zata koma? Da gudu ko ta fito tana salati tana kumawa " ashe dama kallon danaga kina mata da ina dikan ki na zamu hadu ne?" Lallai kuwa yau me rabani da ke sai Allah" ai tana jin haka ta diba waje da gudu dan tasan yau sai an kusa kaita binni asibiti inna ta kamata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wasa take da tsinke a hannun ta ya karyo kwana yana isowa ya ganta yai burki ya iso inda take" ya yammata ta Ado bada kanki a sare in kinje gida kice na amshe abuna, me ya faru kuma yau na ganki anan da sassafe?" Bata daga kanta ba ta bashi amsa da " ba komai nidai ka tafi karka jamin magana dan Allah Ado" " haba abar son Ado kema kinsan ba wadda nake so data wuce ki dik karkarar nan irin wahalar da kk sha yasa na maki tayin guduwa lagos amma kin qi, ko kiban dama na fede wa waccan shegiyar qanwar taki fuska naga ta taqama dafarin da suke fan ba abinda ta fiki" da hanxari ta daga kanya ta kalle shi da idun ta masu haske da suka koma ja tace "Aa Ado ni dai na hane ka da irin wadannan maganganun dan basu da amfani dika" to shikenan yanzu fadan yau me ke faruwa ko zan iya taimakawa?" Ruea xaka debon anan " ta miqa mai bokitin ya karba kan minti biyar ya dawo ya bata ya zauna yana jiran ta juye ya qaro a haka suka gama cika gidan tas.......</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 2:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana gamawa ne ta dawo wajen shi ta mai godiya da taimakon ta da yake ta koma ciki ta dakko buta ta debi ruwa ta zaga tai alwala ta koma soro ta dau dankwalin ta ta yafa ta fara sallah ta kai ruku'u kenan raji an dima mata dundu a baya saida ta gantsare dagowar nan da zatai taga qanwar ta Hinde kan tai magana ta durqusa ta fashe da kuka mai tsanani tana kiran inna aiko sai gata a guje zani a hannu " me nake ji kamar an fasa kabewa " tana shidewa ta qarya take fadin " inna Nasreen zata kashe ni zata gama da ni inna duban baya na zan wuce kawai ta diman dundu" jikin Nasreen har rawa yake ta zube a kan guiwowin ta tana kallon qanwar tata tana hawaye daga baya hawayen ya tsaya cak ta kalle ta tace "Hinde me na maki ne? Me kk so dani ne? Ko kin manta ni yar uwar kice ta jini? Uwar mu daya uban mu daya amma kk min abinda kk man ? Burin ki kullum ki hadani da Innar mu" kan ta rufe baki jitai an bige mata bakin ya fashe sai jini ke zuba inna kenan " dan uban ki baki ga me kk mata ba ne ko nace me kk mana duk gidannan wa kk gani baqi kuma mai kyau kamar ki daban kk duk zuri'ar mu ba mai kamar ki" kan ta rufe baki sukaji daga bayan su ance " to in haka ne kenan ba ita za a tambaya ba ko?" Da masifa ta juyo sakamakon gane mai maganar da tai " to uban wa za a tambaya kenan?" Hmmmm Innar Hinde kenan kece fa uwar ta ai ko kinga ba wanda ya dace a tambaye shi dawa take kama in ba ke ba, haba kin bi kinsa yarin ya a gaba sallar ma tinda ku bakui ba kun hana ta" a kufule ta katse shi " sannu sallahu baban ta sallah aaaa nace sannu sallau baban ta sallah banga damar barin ta sallah ba sai ta gama man komai in ba haka ba daga kai har ita yau baku da abinci" a take ya dakko dari biyar ya wurga ma yar tashi wato Nasreen yace "ga shi nan kije ki siyo dik abinda kk son kari da shi yau" habaaaamana ai tini innar Hinde aka koma kusa da shi "habaaa mijin Tabawa mijina abin alfahari na ai yau kam a gidannan kaine sarki sai abinda kace shi za ai" yai murmushi dan yasan yau daga yanzu zuwa dare zai samu kan innar Hinde har a dan raba shi a daki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana fita ta amshe kufin hannun ta ta bi shi ita kuma ta samu damar yin sallar ta tau addu'o'in ta musamman akan halin da take ciki na Allah ya kawo mata mafita ya daidaita ta da yar uwar ta da mahaifiyar ta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sannan ta tashi ta dakko kwanikan wanke wanke tana hadawa waje daya tai shara tas ta wanke bandaki tai wanke2 tai wanka dan ita kome za ai mata ba za a hana ta wanka da wanke baki da gishiri da gawayi ba shiyasa kullum cikin tsafta zaka ganta. Data gama ne ta dau hanyar zuwa gidan qawar ta yar mai kudin garin Barira......</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR. 👵🏻</p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 3:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sallamar ta ta shiga ta tadda innar Barira na shara ta hanxarta xuwa karbar tsitsiyar amma innar Barira ta hana ta anan ta gaida ta ta tambayi aminiyar ta shaida mata tana daki a kwance aiko rai bace tai dakin nata. Daka mata duka tai a duwais din ta irin na (Roumie mutan sahara😂😜) da hanxari ta miqe taga waye dan dai tasan ba innar ta bace saidai ko wannan...... kan ta qarasa tinanin ta suka hada ido, da murnar ta ta sakko ita kuma ta hade fuska, " yanzu Barira abinda kikai kin kyauta kenan? Inna na can na shara kina nan kina shara bacci hankali kwance, yaushe zaki hankali ne? " Aa malama karki matsa min daga shigowa yo kk san ni aikin da nai kan ki zo? Nafa gyra dakina nai wanka ko baki da ido ne? Ta murguda baki ta haye gado abinta Nasreen tai murmushi ta xauna gefen ta tace qawata ina mai maki nasiha da ki dinga taimakawa taki mahaifiyar kinga ke bata takura maki kamar tawa innar duk da nasan tawa innar harda zugar qanwata ki duba ki gani yanzu shekarata sha biyar ba a daina duka na ba a qauyen nan namu ai na isa aure shekara mai zuwa a dau ki da amma kullum kamar jaka haka nake " wasu hawaye masu xafi suka sakko mata anan qawar ta ta share mata ta rungume ta tana buga bayan ta da sigar rarra shi itama nata idon ya cika da hawaye tace " Nasreen hakuri xaki tayi inshaa Allah watarana sai labari kuma dama akwai abinda nake son na fada maki dan dai innata ma tana da niyyar shiga gidan ku anjima, daxu baba ya shigo yace mana zamu koma birni nan da kwana biyu ya samu aiki a can zamu garin Lagos na kasa zuwa na fada maki ne yasa na kwanta ina tinani bacci ya dauke" nam da nan hankalin Nasreen ya tashi ta tsanan ta kukan ta tace "to ni yanzu in kuka tafu ya zan? Wa zai dinga sharen hawayena a duk sanda na kawo kukana? Wa zai..... bata qarasa ba ta fita da gudu tana kuka. </p><p> Itama Barira binta tai amma inaaa ta wuce bata san ma wace kwanar tai ba can bayan garin taje ta zauna qasan wata bishiya taita kuka tana tambayar kanta " anya Innar Hinde ita ta haife ta ? Wace irin uwa ce ita ? Taga iyaye kala2 amma bata taba ganin irin tata ba WATA UWAR kome ya samu yarta itama saita jishi a jikin ta amma tata uwar ko a jikin ta ta share hawayen ta, ta daga hannu sama tana ma Allah kirari da riqon shi ya kawo mata mafita karta wulaqanta a wannan qauye take tinanin Ado ya fadi mata akan maganar su da suke yi kullum.......</p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻 </p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 4:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kamar wadda aka mintsina haka ta tashi ta fara tafiya ganin rana na neman bacewa tana xaune hankalin ta ba qaramin tashi yai ba data tina gida, nan take baqinciki ya bayyana a fuskarta, da tana da hali da iko da ta samu WATA UWAR a matsayin mahaifiya ta canja ta ta, ta goge hawayen idon ta," kaga ta Ado bada kan ki a sare in kinje gida kice na amshi abuna" hmmm Ado daga ina haka kamar anyi halin" hhhhhh ba wani da yawa bane Tawan kawai na dan sha na daidaita haxo ne kin gane" hmmm Ado kenan bari kaga na isa gida dan yau nasan saidai nai kwanan soro rabona da gida tin 12 na rana" tab ke ko ina kk tsaya bayan kin san Halin wannan shegiyar uwar taki" a fusace ta dago ta kalle shi saida yaji hankalin shi ya tashi" kiyi hakuri Nasreen da ina da iko saina canja maki WATA UWAR kema ki dandana dadin mahaifiya domin duk iskanci na innata na so na amma taki bata da burin daya wuce ta lalata ki daga gidan ku nake yanzu naje neman ki ban same ki ba, naga Innar Hinde muka gaisa nace mata kina nan? Budar bakin ta cewa tai " ni na namtsu naji ta fara amai a gidannan ko mun baka ita dika ka qarasa dan wallahi baxata ci gaba da zama da mu ba" a firgice Nasreen ta kalle shi tace " da gaske innata ce tace maka haka?" Ya daga mata kai jikin shi a sanyaye ya qara da cewa" ni dama sallama na zo na miki zan wuce lagos ne anjima da yamma, zamu binni mu kwana mu wuce" Allah sarki Ado in ka tafi sai yaushe kuma" hmmm Nasreen kenan saikace wani damuwa kikai da ni bayan ko dan ina son ka dinnan baki taba fadan ba" Ado ai kaima kasan ba soyayya tsakanin mu da da akwai da tini ka sani yar makarantar nan kaqi sam bayan kana da dama mu da muke so sai an bushi iska ake barin mu zuwa amma kai kaqi zama mutumin kirki" Nasreen watarana sai labari gashi mun iso gida ki shiga kan a gammu ace daga yawon ta zubar kk bayan ni ko hannu ba a taba bari na dan riqe ba ma naji dadi" hmmm to saduwar alkairi"</p><p> </p><p><br /></p><p>Tai wuf ta shige soro tana leqe ta dade a haka taji an tankada ta ciki ta fadi qasa juyawar nan da zatai taga Hinde ansha kwalliya irin ta qauye " Hinde meye haka sai kinji man ciwo?" Hhhhh ciwo indai ciwo ne ki kwantar da hankalin ki yar uwa ai sai na ji maki ciwon zahiri da badini zaki tabbatar da ni Hinde bana qaunar ki sam" Hinde me nai maki ne" wannan karon ta miqe tana fuskantar yar uwar ta ta" me kikai min fa kk tambaya ? Ki duba ki gani a garinnan kaf samari ke suke hari, qawaye ke suke hari, manyan gari da an ganki an hau maki addua ana sa maki albarka ni ko sai tsinuwa da shegen baqin jini" haba yar uwa karki manta malamin islamiyyar mu me ya ce kowacce rai da arziqin ta take zuwa ba wanda zai ci arziqin wani bakisan baiwar da Allah ya miki ba kk sawa tawa ido kuma ma me nake da shi da baki da shi? Ai sai dai ma ki fini" ke uwar tsara zance wallahi na kusa maganin ki kin kusa guduwa da qafar ki ki bar gidannan indai ni ce" ta bangaje ta ta shige gida me tace ma inna oho sai Allah sai gata a zabure ta yo soron da gudu tana xuwa ita kuma ta hada kai da guiwa tana kuka sai saukar duka tashi ko ta ina tana fadin" sallamammiya ina yake kwarton naki kun gama lalube2n naku kenan shine kika zauna harda dukar min yarinya dan ta shigo ta katse ku" ta daga kai ta kalli Hinde dake kukan qarya tana mata gwalo tace inna mari fa wannan qaton ya sakar min da hannun shi kamar katako" Innar Hinde tace zo ki rama a kanta shegiya baqa mai baqar aniya" kan ta gama mamaki da komai taji saukar mari kamar hannun qato amma ko a jikin ta abinda yar uwar ta da mahaifiyar ta ke mata yafi komai damun ta, saida sukai mai isar su suka tafi ta wurgo mata tabarma tace saidai ki kwana anan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Baban Hinde duk yana saurar komai amma yau yana son ya dan labe a dakin Innar Hinde yasa yana jin su yai shiru dan kudin hannun shi baifi dari biyu ba 200 in ya matsa sai a hana shi abun duniya yau. Tana shiga daki ya matso kusa da ita dik da yau an samu wanka amma bakinnan wani wari yake kamar an bude shaddar gidan haya, tana daga hannu da niyyar rungume shi bayan ya miqa mata dari biyun hannun shi saida nunfashin shi ya kusa daukewa domin a wajen shi Nasreen ta gaji tsafta, amma ya zaiyi haka ya fara shafata a yi yan wasanni ita dai inaaa kawai so take taji ya fara bata darussa a wuce wajen dan har gargadi take mai" lokaci ne da kai Baban Hinde in kace tsotse2n nan zaka tsaya lokacin ka ya cika tashi zan nai kwanciyata nai bacci " ai ko baida zabin da ya wuce ya shiga badan rai da kwadayi ba da ba yanda za ai ya ce anan yake sauke buqatar shi waje kamar yana shiga masai dan wari da doyi kaiiiii Innar Hinde ta zame mana qaddara mummuna nida Yata........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 5:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana samu ya gama biyan buqatar shi ya tashi ya koma gefe yana hango da ace Innar Hinde na gyara ai da ba qaramin morewa zai ba tinda ba laifi komai yaji matsalar shi daya qazantar dake damun ta , tsaki yaja a lokacin da yaji tana wani irin munshari mai mugun qarfi ya miqa hannu da niyyar tashin ta akan taje tai wankan tsarki kan ta kwanta baccin sai ya tina kwanaki yanda suka qare maza ya janye hannun shi, bai shirya karbawa iyayen shi xagi ba da darennan, tashi yai taje yai wanka yai alwala ya hau sallaya ya na ta salloli bayan ya idar ne ya hau addua akan Allah ya shiryi matar shi ta zama macen kirki uwa ta gari wadda za ai kwatancen alkairi da ita, yana idarwa ya shafa ya koma gefen ta ya kwanta nan bacci yai gaba da shi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nasreen na kwance a soro duk sauron dunya ya gama cin kasuwa a kanta ya amshi kudin shi yai gaba, tai kuka har ta dena ta zubama bango ido a kan idon ta Baban Hinde ya wuce, yana komawa taga itama ya kamata ai ta tashi ta yi sallah ko ta roqi Allah sauyin rayuwa a tashi tai ta dauro alwala ta hau sallah bayan ta idar ta hau karanta surori daga alqur'ani gwargwadon wadan da malam sule ke koyar da su a islamiyya tana idarwa tai ta addua akan neman sauyin rayuwa, a haka bacci yai gaba da ita.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tashi baqa mai baqar aniya Inna na kiran ki" tana yi tana kada qugu su da masifa ba sa barin ta safe sai rana tayi su dora🙄 miqewa tai jiki ba qwari tai dakin Innar, tana kwance shame2 kamar gawa bata ko farka ba tana shiga Hinde ta hankada ta ta fada kan innar aiko ta bude ido da bakin ta mai mugun wari ta fara hamma tana miqa kula da Nasreen ne ya katse mata miqar ta dura ashar" dan uban ki me kk kallo? Me kk zo yi da asubannan ( kunji wai asuba rana gatso2 dan batai sallah ba shikenan kawai ya zamar mata asuba) saiga Hinde ta shigo ta je kusa da innar ta ta zauna sai cewa tai" hmmm ai Inna baki sani ba na dade a bayan ta ina kallon ta tana leqo ki tana ta kallon ki tana matse qafa dan ina kyautata tsammanin nan ta kwana tana leqa ku keda Baba komai akan idon ta akai har lokacin da kike wani irin kuka ba abinda bata ji ba sai gani nai ta dau buta taje tai wanka ta dawo tai sallah tai karatu" mamakin duniya ya cikawa Nasreen ciki babban mamakin ta bai wuce ya akai yar shekara 12 tasan ya ake in an gama xxx na biyu ashe idon ta biyu kenan duk taga komai labe take ma iyayen nasu wannan wace irin yarinya ce? Tafi tajiyo daga sama ana salati sai kuma duka ko ta ina wanda in da warin da ke fita daga jikin Innar aka barta ai an gama mata hukunci. Tsayawa tai innar taita duka da kyar Baban Hinde ya karbe ta wuya kam ta shata ba ta wasa ba duk inda Hinde tai binta kawai take da ido.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yaune ta yanke hukuncin tinkarar mahaifin ta ta tambaye shi wacece mahaifiyar ta. Zaune hake akan sallaya a daki ta shiga innar hinde tana bayi tai sallama ta xauna a gefen shi tace "Barka da rana Baba" amsawa yai cike da tausayawa dan ko ina tabon duka ne jikin ta da fara ce ba a san ya zata koma ba. Baba dama zuwa nai na tambaye ka dan girman Allah ka fadan gaskiya wacece mahaifiyata ko a ina take nai alqawarin zuwa na nemo ta, in ko mutuwa tai la fadan dangin ta na koma wajen su da xama in ba haka ba ina tsoron randa zaku nemen ku rasa" ta qarasa cikin matsanancin kuka hankalin malam Lawan tashi yai dayaji maganar barin gida, matsoea yai kusa da ita yana kama hannun ta zai magan kenan yaji ihuuuu a tsakar gida leqawar nan da zai yaga Hinde da Innar ta suna kururuwa wai" jama'a kuxo ku kawo mana dauki ga kwarton cikin gida uba na neman yarsa" kuka take tana qarawa malam kao ya riqe yana karanta kome yaxo bakin shi Nasreen kuwa faduwa tai a qasa sumamma. Malam ne yai kanta ya yayyafa maya ruwa ta farka tana kuka mai tsanani ba wanda ta kalla sai Hinde dan tana kyautata zaton cewa ita ta hada wannan sharrin. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tinda ta miqe kan mutane su iso malam ya miqa mata kudin hannun shi dika yace mata ya amince da yawun shi ta canja mazauni dan ba abinda yafi wannan muni ace an maka sharri da mahaifin ka tana kuka ta saka takalmi ta dau mayafi ta fice tana kallon uwar tata da yar uwar ta tana kuka har tai gaba ta dawo ta tsaya a gaban inna tace mata" inna na gode da dawainiyar haihuwata da kikai da kula dani har girmana tinda inda kin so da kin halakani kan kowa ya kula amma ina mai tabbatar maki cewa akwai hisabi tsakanin da da uwa Allah ya yafe maki karna dawo maki da abu dayan biyu ko abinda kullum kk man baki akai ko kuma arziqin da kk kam gori akai" ke kuma Hinde ga gidannan xan bar maki ki ci gaba da kawo ma inna kudin da take so ta hanyar da kk ga dama amma ki sani watarana sai labari kuma ki bi duniya a sannu" ta sa kai ta fice tabar inna na fadin " sallamammiya yo in banda ke da kinbj shawarar qanwar ki ni kullum in dari biyar xata na rabamu da ke banda matsala da baqin ku tinda kina da kyau amma yarinya sai tarin samari ba ko fus ki gaba in kinje kin samo kinna aiko mana" Nasreen rasa ina zata tai nan take ta hango machine ta tsayar tace ya kaita tasha........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻 </p><p> BY HAERMEEBRAEH</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Aisha Aliyyu Garkuwa </p><p>Zahs Surbi yel</p><p>Mrs J moon </p><p>Cute one</p><p>Mrs Habnour</p><p>Maman Sadeeq </p><p>Sawwama Qawwama</p><p>Mero Tsokana😂 </p><p>Roumie </p><p>And many more........</p><p>Wannan page din da dikka sauran da zasu zo gaba naku ne. Ina son ku kamar yanda kuke so na tsakani da Allah ana tare❤ Matan Gidan Tabital Fullaku gaba daya Haermyn Hamma na son ku❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 6:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tashiga tasha da tinani kala2 da ya cushe mata a zuciya, da farko dai ina ta nufa yanzu? Wa take dashi a duniya da zata dosa bayan uwar da ta haifeta ta mata sharrin da har ta mutu bazai goge mata a zuciya ba? "Ya ilahi ka taimaka min" abinda bakin ta ke furtawa kenan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>" kano, kano,kano" da sauri ta fada motar dan bata da wani tinani da zatai again tana shiga mutum uku kawai aka qara mota ta fara tafiya hankalin Nasreen a tashe yake dan bata taba hawa mota ba abin tsoro yake bata in ba ikon Allah ba ya za ai wannan qarfen ya motsa🤔 , tinanin ta ya qare ne a lokacin da barcin ramuwa yai gaba da ita, ba ita ta farka ba sai da suka isa anan me motar ke rambayar ta kudi dan an tashe ta yafi sau nawa taqi bude ido ma bare taji shine dalilin bari saida suka iso ya karbi kudin shi, waige2 take ta faman yi bayan sun sauka a tashar unguwa uku anan ta hango masallaci ta isa tai alwala ta koma gefe ta saka dankwalin ta ta fara sallah ta idar kenan tana tinanin ina ta nufa kuma daga nan ? Taji wasu samari biyu suna magana" sani yanzu kana ganin mu wuce lagos din yau kawai tinda ga mota a arha zamu shiga dubu daya da dari biyar fa kawai zamu bashi har can saidai kawai a bayan motar zamu xauna shine matsalar duk sanyin hanya akan mu" Ah me zai hana me ya rage kawai mu bi shi yafi mana sauqi" nan take Barira ta fado mata arai, matsawa tai kusa da su tai masu sallama suka amsa " bayin Allah naji kuna zancen tafiya lagos ne dan Allah yaushe motar zata tashi? Kuma ana tafiya da mata?" Dariya suka fara sannan daya yace "baiwar Allah ai ba a hana maza ko mata tafiya ina kk son zuwa?" Tace " lagos nake son zuwa nima" kinada 2500? Kuma sai 6pm zamu tashi" tace ina da su ta kunce zani ta dakko masu yace to amma zamu fada maki gaskiya 1500 ne kudin mu zamu raba sauran" tace."ba komai" anan take suka isa wajen mai mota suka hada kudi suka bashi nan ta zauna sai hamma take taga mai awara ta siya bayan taci ta sha ruwa, 6pm nayi suka tashi tin ana tafiya tana an kusa har wani yaji haushi yace " malama sai fa an kwana dan haka in kinada abin yi kan mu isa ki fara kawai dan rage dare" ya koma ya kwanta nan ta koma gefe ta takure take dabara ta fado mata ta fara karanto al'qur'ani mai girma domin kuwa ko a qauye duk da muguntar Innar hinde takan je makaranta ajinta 2 a secodary a qur'ani kuwa ta sauke a hadda izunta 19 nan ta fara rera karatu da muryar ta mai dadin sauraro a take yan tafiyar ta kowa hankalin shi yayo kanta nutsuwa na shigar su , a haka har bacci yai gaba da ita.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Isar su Lagos da safe ne ya bata damar bude ido a hankali ta duva ko ina sai jamaa kala2 take gani kawai ta sakko a hankali wadanda ta taho da su ne wani a cikin su yazo ya kawo mta abin da zata ci da ruwa yana mai girmama ta har ya bata mamaki dan ba a haka suka taho ba, anan yake tambayar ta wajen wa zata tace mai " wajen Barira zani yar malam Bashari na qauyen mu na Langyam" bai san sanda dariya ta kwace mai ba yace" baiwar Allah anan zaki nemi wata da wannan kwatancen tace " eh haka aka san su da shi a can gida" yaga zata bata mai lokaci yace muje na kaiki wani waje kan a samu wadan da kk nema yana dariya............</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 7: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sun samu taxi da ta kaisu wata unguwa mai cike da qabilar hausawa ko ta ina yan kazo nazo mai suna Apapa, a gefen qarqashin gada rumfar Hajiya Asabe mai abinci take macece mai mugun son abin duniya ko ta halin qaqa ita dai kawai taga kudi haka zalika akan cimma burin ta ba irin hakurin da ba zatai ba da canja fuska dan dai kawai a fahimce ta ta isar da saqon ta na son zuciya ta fece, a haka Sani ya iso da Nasreen wajen ta tana hakimce ta ci kwalliya kota ina tana hura hanci, ya kwashi gaisuwa yana mata kirarin su na yan duniya tana murmushin isa da qasaita, ta daga kai ta kai duban ta gefen shi tace "Sani duniya wannan kuma hajar fa?" Kyafta mata ido yai akan suje ciki tako tashi ta bishi tana juya mazaunan ta tana taqama ita dai Nasreen baiwar Allah sai ido take bazawa tana kallon yanda mata keta kai kawo suna wasannin banza da maza, da sauri ta kauda kanta da ta hango wani matashi na mata kallon kurilla.ta juya bayan ta ta rufe idon ta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hajiya wannan yarinyar da kk gani a mota muka hadu, daga dikkan alamu kuma bata san ma gun wa ta zo ba, bayan haka in kin kula da ita bazata wuce shekara sha biyar zuwa sha shida ba, sannan koda zamui qoqarin sata a network sai munyi babban aiki sai mun bullo mata ta hanyar ta wato mu nuna mata muma na Allah ne, dan dan zamana da ita na fuskanci yarinyar akwai tsoron Allah ga ilimin addini" Dariya Hajiya Asabe tai tana kada ido da hannaye irin na yan duniya " yo wannan ai mai sauqi ne dan kuwa wannan yarinyar ta kile gidaje da motoci sai na zaba ba" Hhhhhh Hajiya baqa ce fa" hmmmm Sani kenan meye a cikin farin ne da baqa bata da shi to kasani duk wata baqar mace tana da wani sinadarai da fara bata da shi mai banbancewa sai wanda ya same su su dika ( ba baqa bace ni ehe kar a ce na bi bayan kalar mu lols) " Anyways nidai gata na kawo komai ake ciki ina jin dumus innaji shiru ansan halina ehe" Kana tsorata ni ne Sani ko me kk nufi da hakan?" Aa hajiya ni na isa" yana magana yayin da yake kunna sigari yana kada qafa ya kada kai yai waje. Hangota da yai maza ya kashe hayaqin ya nufeta ya mata sallama ta amsa daidai fitowar Hajiya kenan, "Sannu baiwar Allah, sani yamin bayanin komai dan haka karki damu zan sa cigiya a nemo maki yan uwan ki inshaa Allahu nan kusa amma sai kinyi hakuri Lagos nada girma bamu san inda suka sauka ba balle ace dan haka zaki iya daukan lokaci mai tsaho damu, hakan nne yasa muka yanke shawara ko zaki iya fara tayani koda wanke2 ne ina biyan ki sannan kina da wajen kwana a gidana da abinci zan riqe ki kamar yata, dan baka san wa zai mori wani ba a rayuwa sai Allah" tinda ta fara magana Nasreen kanta ke qasa bata ce komai ba saoda ta kai aya sannan tace" Nagode Hajiya Allah ya qara girma, ina son nai sallah gashi lokaci nata wucewa"anan hajiyar tasa aka nunama Nasreen inda zata iya yin sallah a wajen tai sallah taci abinci tasha ruwa sai bacci mai dadi yai gaba da ita.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da wajen qarfe takwas na dare ta farka taga manyan motoci na zuwa suna diban yammatan nan suna tafiya da su, sai hajiyar tace mata ai suna kaisu gidajen kwana ne Nasreen a lokacin hankalin ta ya kwanta ta kalli y</p><p>Hajiyan tace " amma ni dai hajiya nafi son na kwana wajen ki dan Allah " hajiya tace laaa karki damu yata ai nima bazan so ki nesa dani ba tare zamu tafi yanzu ma motar mu nuke jira mu tafi" ana haka wata mota ta iso hajiya ta miqe ta kama hannun Nasreen suka shige sai gida. Isar su keda wuya ta nuna ma Nasreen wani daki mai kyau da gado da komai daidai buqatar mace mai son gyara da tsafta da bandaki a ciki, hajiya nuna mata komai daya dace ta sani tai ta mata saida safe ta juya ta fita...........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR. 👵🏻 </p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Maman Manal</p><p>Aunty Rumaisa</p><p>Gaisuwa mai yawa gare ku ANA MUGUN TARE❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 8:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Fitar Hajiya Asabe keda wuya Nasreen ta samu kanta da hayewa sabon gadon da aka bata akace nata ne, tai juyi ta kuma, tai murmush, ta gode ma Allah da ya hadata da Hajiya Asabe a matsayin wadda xata taimaka mata. Wanka ta farayi sannan tai alwala tai sallar isha'i ta taba karatun ta sannan tai shirin bacci taji ana buga qofa, zuwa tai ta bude ta koma baya sai Hajiya ta shigo dauke da wata rigar bacci mai kyau kalar pink, " karbi wannan ki sa dan baza kiji dadin bacci da wannan kayan da kkai tafiya da su ba" ta amsa tana qara godiya da adduoi masu dad'ad'a rai, murmushi hajiya tai, tace " to saka rigar na gani in ta maki gobe muje a siyo maki wasu" a take ta je bandaki ta gwada amma ta kasa dawowa dakin sakamakon ganin yanda rigar tabi shape din ta ta kwanta, tana cikin tinani taji an bude qofar Hajiya tace " haba 'yata ai ni uwace kuma dan kinsa wannan ai ba wani abu bane baki gani a TV yan gayu yanda suke saka kaya qanana kuma su fita cikin mutane kowa ya dinga yabawa?" Anan ne ta tina in taje gidan su Barira suna gani a TV, ta daga mata kai alamun "eh" Tace " yauwa kinga in kina son cin ribar zama a wannan garin dole ki fara yin shiga irin tasu, saboda in ba haka ba fada zai iya tashi ya ritsa da ke a kashe ki, amma in kina saka kaya irin nasu ba mai kula ki" ai dajin maganar kisa idon Nasreen ya qara girma , tai wani abin tausayi tace " nidai Hajiya to ko a kidin da zan na maki aiki ki taimaka ki siyo min nima" tana share zufar dake karyo mata, Hajiya tai murmushin samun nasara a tashin farko tace ki kwanta ki bacci ki huta xamui maganar gobe, ta ja mata qofa ta fita dan gulma harda ce mata " kardai ki manta ki addua kan ki bacci" tace to Hajiya mu kwana lfy" tai addua taja bargo tana tinanin gida bacci mai dadi yai gaba da ita.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kin gama shiryawa ko" cewar Hajiya Asabe dake fitowa daga dakin ta, ta kalli Nasreen da ta maida kayan ta masu dauda tace " eh na gama Hajiya Ina kwana" " lfy qalaou, ya baqunta?" Tana murmushi ta amsa da " lfy qalaou" to muje ko in yaso in mun dawo munbi shago muci abinci. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sun sai kayayyaki kala2, takalma,turaruka, mayuka kala2 masu gyara fata daidai kalar ta, shampoo da dai duk abinda zata buqata, a kayan ta babu wasu manyan kaya sosai sai wasu jalbab guda biyar da hijabs biyar amma sauran duk qanana ne matsattsu da na bacci. Sun isa shago a wahale aka kawo masu abinci suka ci suka qoshi, "Nasreen ya kamata mu koma gida, akwai abubuwan da ya kamata a fara koya maki, saboda zaman Lagos dole sai da su, in dai kina son ki tsira da rayuwar ki, dan ko yan uwan ki da zaki wajen su, suma nasan in suna son zaman ki zasu koyar da ke" Nasreen zuwa tai ta durqusa idon ta na zubda hawaye ta ce" Hajiya banda bakin gode maki, kin min abinda tinda nake ba wanda ya taba min, kin zame man uwa, in Allah ya yarda kuwa kome kk so zan miki, indai zaki tiqe amanata" Take Hajiya tai murmushi na samun nasara again Tace habaaaa Nasreen tashi meye haka? Ai yiwa kaine, d'a da dukiya ba a masu mugunta, baka san wa zai mora ba, dan haka karkiji komai kome kk so ki sanar da ni kan ki tsaye kinji" ta daga kai tana goge mata hawayen fuskar ta ta jata suka nufi gida.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Suna isa..........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 9: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Suna isa Hajiya Asabe ta sa Nasreen a gaba ta kaita toilet, tai mata wanka tin tanaqi tana nuna jin kunya, Hajiya tace " Ni fa a matsayin Uwa nak gare ki dan haka ki saki jikin ki na koya maki al'adar garin nan, kar wata matsala ta taso ki ji ban kyauta miki ba, tinda ban koya maki ba" sannan ta samu nutsuwa ta sake sosai. Anan ne Hajiya ta nuna mata yanda ake shaving hammata, HQ, da qafa,da hannaye, ta nuna mata ya ake asalin yin brush yanda zata wanke cikin harshen ta da lungu da saqo na haqori da ko ina na cikin bakin ta, ta koya mata yanda zata wanke kunne har cikin shi ba tare da ruwa ya shiga ba, ta wanke mata gashin ta tas da Shampoo masu qamshi, ga yankan farce ta mata kai in aka nuna maka hoton Nasreen din qauye da wannan cewa zakai qarya ne wata ce ba ita bace, ta dau haske da wani annuri ke fita kawai fatar nan tasha gyara sai santsi take. "Zo ki kalli kan ki ko xaki gane min wannan budurwar " tana fada tana murmushin hango Nira a jikin 'yar mutane 🙄 Nasreen daskarewa ne kawai batai ba ga wata irin riga da Hajiya ta bata ta saka mai kalar red ta matse ta daga sama mai siraran hannu daga qugu ta sake ta gaba cinyoyin ta a waje ta baya ta kai bayan guiwar ta, kannan ya sha gyara wani ya zubo ta gaba, sauran ta baya ga make up ta sha, (koni dana leqa na kalleta na ga kyau na zaci Qawwama ce lols😜) kunya da dadi ne suka kama ta, ta rufe fuska tana murmushi, " Hajiya na gode sosai Allah ya saka maki da gidan Aljanna, amma Hajiya wannan a gida zan dinga sawa ko bazan fita da su ba ko?" Kwarai da gaske ai ke musulma ce, duk da irin su zakina sawa, amma wadan da suka fi wannan mutunci, dan kinga in ba haka kk anan ba aka gano riqon addinin ki kashe ki za sui kawai, su basa son musulmai" da ta ji an ce mutuwar nan ita fa an gama da ita kawai, yanzu za ta fara rarraba ido , tace" ba komai Hajiya Allah ya kare mu, ai Allah na amfani da zuciya ne" Hajiya tace "wannan haka yake 'Yata. A haka dai Nasreen ta wanke kwalliya tai alwala Hajiya kamar ta shaqe ta ganin bata lokacin da tai tana mata amma yar banzar yarinya ta goge ta, ta ce a juri zuwa rafi dai...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sai da sukai sati biyu ana koya mata kwalliya, tafiya, magana, da kallo, wasu girke2n zamani, da duk dai abinda ya dace ace mace mai aji ta san su ta iya, kafin wata uku Nasreen ta kware a duk wadannan abubuwan, wani fanfon karuwanci duk Hajiya ta fara sa mata a qidar saidai duk abinnan baya hanata sallah da karatun qur'anin ta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A kwana a tashi lokaci ya ja sosai Nasreen ta manta da wani tinanin neman su Barira da iyayen ta shekara biyu kenan tana wajen hajiya amma har a wannan lokacin Hajiyar renon ta take so take sai ta samu wanda a tashin farko zai bata damman kudade, kan ta miqa mai Nasreen Aji dan yanzu tsabar ajin ta da iya gaye da turanci, kai da komai ma in tana magana zaka ce rada take, wannan dalilin ne yasa suke kiran ta da Nasreen Aji. A lokuta da dama takan tina gida saitai murmushi tace "Inna ga fata da adduar ki na aiki, dan ko hajiya bata hadani da kowa ba by now i know what she meant, and i am going to give her d suprice of her life."</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sun shiga wani hadadden super market ne suka hadu da shi, wankan tarwada ne shi mai tsayin burgewa jikin shi madaidaici wanda kowacce mace zata so ace ta samu miji kamar shi, ma'ana son kowa qin wanda ta rasa, baida irin kyaun nann da da an ganshi za a ce ga kyakkyawa amma a tsari da dressing da cikar zati ba a magana🤐. Kallon ta yake da yana yin takun ta komai ya mishi, sannu a hankali ya matsa kusa da ita, dan ko kula da Hajiya bai ba, yai mata magana cikin isa ta samarin da suka yarda da kansu," hi" daga kai tai ta kalle shi take taji wani sabon yanayi a tattare da ita, tini ta manta Nasreen Aji ta amsa" hey" kafin yai magana "Hajiya ta ce Nasreen in kin gama ya kamata mu tafi" hmmmm Hajiya Asabe Duniya kenan, kula da tai wannan Yaron akwai manyan fa ( Farare bugun ABJ) shine dalilun da yasa take son su fara da shi and after all dan Nasreen tai loosing mashi komai ba matsala he worth it, dama daidai shi suke nema a fara da shi. " Eh na gama Hajiyata " sunan da Nasreen ke kiran ta kenan yanzu ( dan iyayi🙄) kama hannun ta tai suka fara tafiya, binsu yai dan baiga ta zama ba...........</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tanx alot for reading my novel, i did not espect to c so many of u liking it, to alhamdu lilLAAH all i want is for u guys to read and understand kuma ai aiki da abinda aka ji din, dan Allah kar wata ta zaci na fara novel ko dan a karanta ai nishadi ne, no dis is not my aim, my aim is duk wadda ta karanta a shafi daya tai qoqari ta koyi wani darasi tai aiki da shi shin buri na komai qanqantar abu indai me kyau ne kar a raina amfanin da zai. And for ur information my novel is base on true life story amma dole a kwai abubuwan da sai an qara kar wata taji yanda bai mata ba taji haushi, wadda taji haushi ina me neman afuwar ta da yafiyat ta. Na gode sosai da kulawa ba kadan ba ban tsammani ba. Love u all</p><p>❤</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> </p><p>BY</p><p> HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 10:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sun kai qofa ne yai gyaran murya ya kira sunan ta da wata irin murya mai sace zuciyar wadda akai domin ta" Nasreeen" tsayawa tai cak, ta kasa motsawa ko ina, a hankali ya qarasa gabanta, yana mai neman su hada ido da ita amma ta saukar da kai qasa, sakamakon yanayin daya jefata ciki, musrmushi yai na na ganin tarkon shi na neman kama kurciya, a hankali ta dago ta kalle shi, ta amsa da " Na'am ? " Sunan ki yai kama da ke suna mai dadi a tare da yarinya mai sanyi da Aji" hmmmm maza kenan zuma kuke ga zaqi ga harbi" tana magana ne cikin wani irin salo da ya rikita mai tsayuwar shi saida ya jingina da motat dake gefen su, sai lanqwasa ake tana fari da ido tana lankwasa harshe, miqa maya complimentary card din shi yai sannan yace" ban yarda na tafi ba saina saka digits din ki a waya ta dan nasan ku mata akwai jan aji ni kuwa bazan iya jira yau ban zo inda kk ba" nan take ta fado mai tai gaba tana wani irin takun,da ni kaina sai da na tsorata da anya Nasreen ce kuwa🤔</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sun isa gida kenan hajiya na qara koyar da ita salon yanda zata jawo shi a jiki,su tatse shi kamar toothpast. "Hajiya ta ki daina damuwa, Nasreen Aji kk magana da ita ba Nasreen yar qauyen Langyam ba" tare sika bushe da dariya. Kiran sallah akai,ta tashi taje tai alwala tai sallah, tai karatin ta na duk bayan sallar farilla data saba, bayan tai azkar din kowacce sallah da akeyi, Nasreen bata manta da sallar ta ba,balle karatun ta,dan a haka ma qoqarin ci gaba da haddar ta take,duk bayan asuba. Ta idar ta shiga wanka,ta dade tana gyara jikin ta, ko ta ina musamman bakin ta ( warin baki ga mace bala'i ne mu kula kar muna magana oga na ja baya muji haushi muce ko dan kiss dinnan ma baya som mana ba laifin shi bane namu ne ba mai son wari koda kuwa shi yana yi) fitowa tai ta ga wayar ta nata faman neman agaji, bata daga ba saida ta gama shafa mai daya dauketa kusan 8mnts , ta samu tirare kala2 ta saka a duk inda ya dace kamar, hammata, wuya,bayan kunne, cibiyar ta , bayan ta, da matsematsin hannu da cinyoyin ta, sannan ta bi dukka jikin da humra mai kyau da qamshi, ta shafe ko ina har fuska, kan ta gama komai dama ta wurga kaninfarin ta daya a baki tana ta tsotsa, ta dakko wani riga iyakarta guiwa mai kalar pink ta saka qasan rigar a bide yake fadi ne da ita sosai, ta sama kuma a matse yake da wani net shara2, sai aka yiwa daidai inda boobs dinta yake shafi da dark pink color material , wanda yai shape kamar bra ,ta gyara gashin ta daya sha wanki da qamshi, ta mai da shi tsakiya ta daure,ta dakko takalmin ta kalar kayan ta flat ta saka. Wayar ta ta gama dialing no data kirata kan ta fara connecting kira ya sake shigowa, saida ta kusa katsewa ta daga, " lallai da baki daga ba inajin daga nan sai asibiti dan bazan qara moruwa ba" wata irin siririyar dariya ta saki mai cike da kissa wadda ta haddasa mai kasala tai, " bazaka je asibiti ba saidai zaka iya zuwa gidan mu yanzu dannima na matsu na qara kallon kyakkyawar fuskar ka" Really?" Itake kalmar daya furta, " Amma kin min laifi" ya fada da shagwaba, " name? Har yanzu baki damu da sanin suna na ba" hhhhhh lallai ne, kamanta kenan ka ban katin ka?" Oh yeh na tina" cike da murmushi, ok Dr Naseer Uamar Tafeeda sai na ganka" kit ta kashe wayar ta barshi da mamakin yanda tafi kowa iya furta sunan shi a duniya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wanka yai ya gyara jikin shi, in ba zuqa maku zan ba ma sai nace ya fi ta iya gyaran jiki a matsayin shi na namiji, duk abinda tai ya ninka nata, yana kammalawa ya fito, cikin wata baqar riga mai dogon hannu da baqin wando, da wuya ya canja wata kalar kayan saidai ya qara da fari shigar shi kenan ko a inner wears ma nashi fari da baqi ne, yana fitowa hadaddiyar motar shi ya nufa sai kwatancen da ta turo mai ta waya ya bi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana isowa palo aka mai iso, ya samu daya daga kujerun gidan masu kyau ya zauna yana kada qafa. Wani irin qamshi ne ya daki hancin shi ya ruda shi gaba daya ya maida hankalin shi zuwa qofa, isowarta keda wuya ya miqe tare da bude hannu qarasawa tai ta mai wata iriyar rungumar da yaji kamar zai fadi, amma ita ta basar a zuwan gaisuwa ne kawai hakan ta koma nesa da kujerar da yake ta zauna ta barshi a qame baki bude😮 " Have a seat pls".....</p><p><br /></p><p>..</p><p><br /></p><p>HOOOOO NASREEN KAMAR WATA RENON XINNEE........😂😂😜</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 11: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zama yai yana qoqarin daidaita nutsuwar shi, amma dik da haka saida Nasreen ta gane ya fara shiga tarkon ta, murmushi ta mai mai ratsa zuciya tace " so what next?" Tana daga gira guda daya, miqa hannun shi yai da nufin ta isa gareshi, ba musu ta miqe cike da yanga da taku irin na yan duniya ta isa ta zauna a gefen shi ta raba jikin ta a nashi sosai, ajiyar zuciya yai ya fara magana" Nasreen a gaskiya duk wanda ya ganki ba zai so ki wuce shi ba tare da ya so kasancewa da ke ba, amma abun mamaki adress din da kk ban tin daga shi jikina yai sanyi, meye dalilin ki na zama gidan karuwai?" Murmushi ta sake yi ta kalle shi ido cikin ido ba ko kunya tace" Naseer kenan to ai kaima kasan ba yanda za ai wadda ba karuwa ba ta zauna a gidan karuwai ko?" Dan razana ce ta bayyana a fuskar shi amma ya dake " wannan haka yake, kenan kinaaa nufinnnn keeeee..?" Hhhhhhhh kwarai da gaske, saidai ni akwai bambanci, ni ban taba wannan al'amarin ba ba kuma na son na fara da wanda ya girmen sosai kamar ace irin tsoffin banzan nan masu bin 'ya'yan mutane da matan mutane sun killace nasu a gida da tsattsauran tsaro, nafi son saurayi kamar ka, dalilin amince maka da nai kenan" take kishi mai tsanani ya bayyana a fuskar shi ya dan janye jikin shi yace" kenan kina nufin in na fara yi da ke zaki koma kici gaba da bin qadangarun bariki babba da yaro, talaka da mai kudi, qazami da mai tsafta, sannan nima in zo in hadu dasu na sauke buqatata?" 😡" come down will u? Ba nufina kenan ba in zaka iya daukan nauyi na da bqatu na ni mai iya zama dakai kai daya ne me ka rasa, after all ai buqatar maje hajji sallah" anan ya samu nutsuwa ta shige shi, tqttaunawa sukai tayi yanda komai zai kasance, yanda zasu tafi da rayuwar su sannan kullum nawa zaina bata da dai duk abinda suke ganin ya dace sui da rayuwar su. Kafin ya tafi a ranar ma saida yai wasanni da ita sosai ba kadan ba ya sha mamakin yanda ya tabbatar da eh budurwa ce da gasken, ita kuma tai mamakin dama ashe haka ake ji a wannan abun🤔 lallai tana jira taji nan gaba me zai faru. Sunyi sallama ya bata 30k ya tafi tana daga mai hannu. " Hajiya ta duba ki gani" " me muka samu " qirgawa tai taga 30k tai tsaki, ta fara magana cikin fada da fushin daya tsorata Nasreen " ke wannan yarinyar wace irin shashasha ce ke ta ya ma za ai yazo yai wannan uwar jimawar ya baki wannan dan kudin, duk latsa jikin naki da yai ya qare a wannan sanin kanki ne mayukan da kk amfani da su kan a kaiga turare sunfi kudin wannan, ke da zaki fara mana da dubu daruruwa to bari kiji tun wuri ki nuna mai kuren shi a waya kan yace zai sake dawowa ya mana harkar qaranta" to hajiya kiyi hakuri " idon ta taf hawaye " zo 'yata raina ne ya baci amma ki kiyaye darajar ki nake son dagawa bana son ki fara karuwanci da qaramin kudi qaramar karuwa zaki zama kamar na shagon saida abinci na, so nake ki zama profesional karuwa ke ki zama international karuwa, wadda koda govenor ne zai iya daukan ki, dan haka ke zaki nuna masu ke me tsada ce,sunan ki na Aji ya biki" daga kai kawai take kamar qadangaruwa tana sauraron wannan baiwar Allah.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A kwana a tashi Nasreen ta zama kwararra a fannin karuwanci, ta fara tarayyar karuwancin ta ne da Naseer inda ya dinga binta a hankali har ya cimma burinsu ya samu nutsuwa da ita, dadin da ya samu da gamsuwa bai taba jin shi wajen manyan mata da yammatan da yai hulda da su ba hakan ne yasa yai mata kyautar wani katafaren gida a Oni Reke, bayan sun kai wata biyu tare ya mallaka mata wata katuwar jeep black, saiga Nasreen ana riqe manyan wayoyi, da manyan kudi Naseer ya tsaya mata. Abu na biyu data bata rayuwar ta da shi shine, SHAYE SHAYE, ta fara da busa sigari sai gata tana shan wiwi da sauran kayan mayen da ni bam ma san sunan su ba sam☹ abu daya na burgewa a wajen Nasreen shine rashin wasa da ibada wanda ko me za sui in zai kai ya shiga lokacin sallah fa to sai an jinkirta shi, da dama qawayen ta na bariki da Hajiyar ta da Naseer kan mata dariya suce "duk watsewar da kk kina tsammanin Allah zai amsa sallar ki ne ?" Takan basu amsa da " koma dai me muka dole mu riqe identity din mu mu musulmai ne kuma karuwanci ba dawwama za mui ba muna sa rai da rahamar Allah ai" sai su bushe mata da dariya Naseer ya sha son ya shammace ta da salon shi da bata iya jure mai amma inaaa baya nasara akan wannan. Wannan kenan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p> QAUYEN LANGYAM</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zaune take gaban kayan kwalliya tana ta rangada kwalliya tana murmushi, sakamakon tunawa da tai yanda Nasreen ta fita tasan tana can tana wulaqanta, sai kuma ta kwashe da dariya ita daya, " lafiya Auta keda wa?" Innar Hinde kenan, " hmmmm inna tinawa nai yau Dan liti yace zai ban dari bakwai innaje shagon shi 700 ( sokuwa a dari ba kwai take rabama gayu jikin ta har take murna) " a hayyeeeeeeeee Allah nawa, kai jama'a kice kwanan nan zan fara riqe dari biyar biyar din kaina kullum?" Hhhhh sosai ma Inna duk abinda aka ban ko da dari shida ne ke biyar zaki ci " ta fada tana wre idanu🙄. Kofa wanka ba tai ba amma an lafta mai a jikin an sha kwalliya ba tsaftar ciki balle ta waje su kansu gayun qauyen kamar kai amai ka kalle su amma a haka ake lalacewar ba ko kyankyami🙄 . Baban hinde ne yai magana" Innar Hinde ki kiyayi Allah, baki da magana sai ta kudi kedai ba zaki tsaya ki gyara kanki da gidan ki ba ki min biyayya ki ba yayan ki tarbiyya sai yawon tazubar kk sa a gaba kk koyawa yayan ki habaa?" Ehhhhhh lallai ne, aaaaa nace lallai ne ya kamata ka min wa a zi, tinda in ban fita nida yarinyar nan mun nemo na abincin mu ba bamu kake, ko na wankin da wanke2 da gyara gidan ba saida kudi ake yin su ba?" Aa Innar Hinde, nan nan gidan malam Kalla sun fimu babu amma gidan shi gwanin sha'awa matar shi tsaf yayan shi maza da mata 8 amma kowanne tsaf ga qana'a da tawakkali da son juna kuma wannan aikin na mahaifiyar su ne dan dai shi in aka bi tashi gidan ba zai haka ba, amma ni na kan qoqarta yi maki abubuwan da kan a samu mai irin su karkarar nan za a dade duk baki gani me yasa ne haka dan Allah? Mu zauna mu rufawa juna a siri kinji mata ta " hahaiiiiiii cassssss malam yaufa ko limamin garin nan aka baka sai yarinyar nan ta fita ta karbon darinnan bakwai dan kaji, ka adana wa'azin ka akan yarka in ta dawo daga yawon abinda ka koya matan" tare suka sa dariya ita da hinde yana jin haka ya bar wajen, dama haka suke masa in ya ce zai masu fada.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Subhanallahi me nake ji ne a toilet dinnan ne Nasreen?"😱😱.........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> </p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 12: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A wahale ta fito sanye da pant yellow mai ratsin fari da vest fara mai ratsin yellow, tana kama gini ta iso gado ta kwanta, da sauru Hajiya Asabe ta isa wajen ta tana " 'Yar nan lfy meke damun ki? Na shiga uku ni Asabe me nake gani ha?" Cike da tashin hankali take maganar ta matso ta dudduba ta ta na ta tambayar ta kamar likita, tana gama jin amsoshin ta, ta miqe tsaye cike damuwa, " Yau mun shiga uku to yaushe ma muka fara tara abin duniyar da har zamui baqon cinyewa da shi? Inaaaaa ba zai yu ba sam wallahi dole asan abin yi wannan cikin zubar dashi zamuje ayi tin lafin Naseer ya san da zaman shi ya guje ki" Hankalin Nasreen ya tashi sakamakon kalmar ciki da taji Hajiya Asabe ta ambata, bakinta har rawa yake wajen furta " ci...ciiiiki fa Hajiyata ?a jikin wa ?" A jikin ki Nasreen ba yau na fara aje yan bariki a wajena ba, dan haka alamomin cikine kaf dake" na shiga uku ni Nasreen, ina zan sa kaina, Innar Hinde kinga abinda kk jawo man ko, bakin ki bai zamo alkairi a gareni ba, kullum mugun fata kk man, ga abinda bakin Uwa ya jawo man" tana yi tana kuka sosai mai ban tausayi, Hajiya zama tai tajawo ta jikin ta, tana lallashi, "kiyi hakuri kinji 'yata ki sauqaqawa kanki wannan cikin zubda shi za ai, kuma........." ba wanda ya isa ya zubar min da gudan jini, duk da ba a samar da shi ta hanyar halal ba, dik wadda tai yunqurin zubar min da d'a ko 'ya kotuce zata raba mu da shi, bani da kowa sai uwata a duniya kowa nawa ya rasu mahaifiyata kadai ta ragen, Allah ya ban wannan ba zan qi shi ba, amma akwai maganar da nake son fada maki Nasreen" daga idanuj ta da suka koma jawur tai tana kallon Naseer da ya shigo bayan ya gama jin duk abinda ke faruwa, " in kin amince ni Naseer ina son na aure ki bayan kin haihu na kaima Hajiyata abinda kk haifa ta gani, nasan in Allah ya yarda baza ta qi ba, amma sai kin amince" zuciyar ta ce tai sanyi akan quncin da ta shiga da, Hajiya ko tafi kowa baqin ciki da wannan labarin amma ta danne bata nuna ba, to in yarinyar nan ta tafi wanan gidan kadai tasan wataqila da motar zata tsira da shi amma in tana nan filayen da ta sissiya da kudin datake samu wajen ta ai ta gine su, aranta take wannan tinanin, " Allah to ya raba lfy" fita tai ta barsu yana lallashin ta, wni irin kyau yaga ta mai da ba zai iya jurewa ba saida ya san ya yai yaja ra'ayin ta suka watse.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Akwana atashi asarar mai rai Nasreen ciki ya kai watan haihuwar shi, shigowarta kenan daga kasuwa ta siyo kayayyakin da duk suka kamata, daga qafar nan da zatai ta shiga daki taji bazata iya ba, nan danan naquda mai tsanani ta kama ta gashi ba kowa a gidan Hajiya na wajen abinci tana ganin ya suke tafi da wajen dan tin zuwan Nasreen ta daina zuwa likafa taci gaba. A daddafe ta samu ta isa bakin mota tai kasada ta hau sai asibitin da take awo, nurses ne suka zo suka shiga da ita, tin shigowar ta ta hango ta daga nesa..............</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> </p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Pinkyn Cute One Allah ya bar qauna soyayyar ku da ban ce Allah baku miji daya asha bidiri😂😂😂😂😂😂😂😂😂 kar naji yarinya tace ba Ameen ba kuma😎 😂😜😜😜</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 13: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wannan kamar Nasreen Inna!" Cewar Barira kenan da take gefen motar ta ita da Innar ta, " Aiko dai dan inma ba ita bace kamar to tai yawa, amma ya akai naga wannan kamar tana da ciki haihuwa tazo? And ki duba kayan jikin ta ba ko mayafi, anya itace kuwa?" Inna mu je ciki amsar na can ba zamu gane komai anan ba kar suje inda bamu sani ba" da hanzari suka bi bayan su, suna isa daidai an shiga da ita dakin haihuwa kenan da ganin ta Barira ta qara tabbar ma Innar ta wannan Nasreen ce tabbas, amma ya akai haka ? Meke faruwa? Damun kwakwalwar ta tai da tinani har daga baya ta girgiza kanta ta daga kafada alamar bari ta fito sunji komai. Nurses ne ke magana akan "to ya zamu san yan uwanta ita daya fa tazo sai dai ko ta wayar ta" cewar wata siririya sosai qugunnan kamar an daurawa tabarya zani Sak Cutie dai😜💃🏻</p><p>Barira ce ta matsa kusa tace "mune yan uwan ta me ya ke faruwa " ta haihunne" Eh ta haihu, ta samu namiji, muna buqatar kayan ta ne da za a canja masu ita da babyn" k ba damuwa in ba matsala muna son muje mu dawo tukunna dan bamu zo da su ba"K No p, amma kui sauri pls" da hanzari Barira taje ta siyo duk abinda za a biqata ta kawo masu, karba sukai sukaje suka shiryata da komai, taje office din Doctor bayan ya kirata ya mata bayani akan zasu iya sallamar ta tinda ta haihu lfy ba matsala, biyan kudin komai tai suka je dakin da aka kwantar da ita. Sallama sukai suka shiga ido hudu sukai da juna, Nasreen waroo manyan idanun ta tai kamar zasu fadi irin na Pinky tace " Ba....Bariiiraaa, Barira kece ko mafarki nak?" Nice Nasreen ba mafarki bane" qoqarin tashi take amma ta hana ta ta zauna kusa da ita suna mai kallon juna, ganin Innar Barira ne ya sa Nasreen saukar da idon ta qasa cikin jin matsananciyar kunyar ta da kunyar aminiyar ta ta, nan take hawaye ya fara zuba a idanun ta, wayar ta ce ta katse ma Barira tambayoyin ta, miqa mata wayar tai ita kuma ta karba cike da kasala" Hello Baby kina ina ne naje gida baki nan na hana ki fita a condition din ki so kk ki haihu a hanya ko ki bari na zo na kaiki duk inda zaki mana amma bakijin magana ta ko?" Kayi hakuri Daddy gani a asibiti ma na haihu dazu ina dawowa naqudar ta kama ni na taho nan na haihu lafiya" Cikin wata irin murna da ta ba Nasreen mamaki dan shegen akewa wannan murnar🤔 ya amsa da " Nasreen my baby da gaske i am nw a Dad? With excitement yake maganar kamar ya huda wayar ya ganshi gaban su , kashe wayar tai karya fasa mata kunne ta tura mai Address din asibitin ta aje wayar.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Labarin komai ta basu kafin ya iso, Innar Barira kuka tai tayi ita da Bariran sun tausaya mata amma kuma sunji tsananin baqincikin salwantar da bata rayuwar ta da tai gashi harda rabon dan shege, Barira ce tace "amma Nasreen kin ban mamaki har xaki iya zama ki aikata wannan mumminan abun saboda kawai Innar ki ta miki sharri da yar uwar ki" ba haka bane qawata wannan abun na dauke shi a matsayain qaddarar rayuwa ta ne tinda kowa da tashi, and in kin kula anyi amfani da rashin sani na ne aka fara koyar dani abunda banda ra'ayi da dabara Hajiya ta samin son karuwanci dan haka ni yanzu saina yi kudi na fara aikawa inna taji dadin su kamar yanda take so" kan tai magana aka bude qofa, cikin hanzari ya iso gareta ko kula da mutanen wajen bai ba ya rungume ta yana mata kiss ko ta ina ya samu yana surutan yi mata godiyar sama mai d'a da tai Innar Barira ce taja hannun ta sukai waje bakin Barira bude tana mamakin wannan abu. Suna tsaye sukaga sun fito shi riqe da kyakkyawan yaron su a hannu , ita kuma tana maqale a qugun shi, wajen su Barira suka nufa Inda ya gaida su dan Nasreen ta bashi labarin su, ya masu godiyar komai likita ya sanat da shi sun biya kudin komai yace masu zai biya su in sun koma harda qari dan sun taimaka mashi yaita godiya saida Innar Barira ta katse shi da " Yaro wannan da kake gani 'Yata ce haihuwar tane kawai ban ba dan haka ba godiya a tsakanin mu" nan yace masu shi zai wuce da Nasreen wajen hajiyar shi ne dan haka su su bashi Address din su zasu neme su, Barira ce ta basu Address da no wayar su sukai sallama suna masu kewar juna.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Suna shiga gidan Nasreen baki bude dan tin daga waje dama take mamakin kyau irin na gidan, masu aiki ne suka zo da sauri daya ta kama Nasreen daya ta bude qofar shiga cikin palon gidan suka sa kai, Wata Hamshaqiyar mace ce a kujera ta dora qafa daya kan daya, ana ta latsa waya☹ ganin danta ne ya sa ta miqe cike da fara'a ta tarbe shi amma ganin shi da wata ga jariri ya bata mamaki sosai, duk da haka farincikin ta bai gushe ba, amsar yaron tai tana kallo, wani irin faduwar gaba ne ya sameta, hankalin ta yai mummunan tashi ganin yaron dake hannun ta, ta daga kai ta kalle shi," Wannan dan waye Naseer?" Mum ki taimaka wa wannan baiwar Allahn mana yanzunnan ta haihu tana buqatar kulawa kafin bayanin komai, bata wa dan nata musu kamar wani Uban ta take bin umarnin shi haka ta kama ta suka shiga, ta hada mata ruwan zafi sosai ta kaita toilet ta gyara jariri ta sa mai kayan shi da suka zo da su sabbi, bayan ta fito wanka ne daure da towel, Mum ta bata wasu daga cikin kayan ta ta saka dan Da kadan ta fita qiba tinda Nasreen ba dai diri ba, ta fito sak me jego da ita looking take away😘 fitowa sukai ta kaita palo aka kawo mata abinci da Tea mai zafi da kauri ta sha sosai kuwa dan tunda ta haihu take jin wata muguwar yunwa, bayan kowa ya nutsu ne Mum ta leqa dakin Naseer, kwance ta hango shi ya tallabe haba yana kallon waje daya, zama tai kusa da shi ta dafa shi tace" Son me ke faruwa ne kamin bayani naji wacece waccan? Dan waye kuma?" Mum Dana ne ita kuma budurwa ta ce" cikin tsananin firgita ta miqe tsaye "Dan kaaaaaa ??????.....👀👀👀👀</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> "</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 14: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Baya ta fara ja tana girgiza kai, tana hawaye , dan tasan in ya matso kusa da ita ba abinda zai hana ta sallama mai kanta, hade hannayen ta tai duka biyun waje daya da alamar roqo," dan Allah ka rufa mana asiri ni da dan ka ka fita in Mum taji labarin ka shigo dakin nan which zata ji din dan sai an fada mata, barina gidannan ya zo" kiyi hakuri Nasreen na kasa jurewa ne, yau watan mu shida rabon mu da juna, hakurina ya kare nai ya qoqarina" daidai nan ya iso gareta, hannun shi ya sa ya janyo ta gare shi a hanzarce kamar dai (mero tsokana ta ga masa 😂😜 ) a hanzarce yake aika mata da saqonnin shi masu wuyar fassara, tana jin bakin shi anata komai ya kwace mata sun manta a ina suke, wane hukunci ne zai biyo bayan su, suna tsaka da jiyar da junan su dadin da suka dade basu samu ba aka banko qofar da qarfin gaske, wanda yai sanadiyyar firgitar su dika, jiki na rawa Naseer ya sakko daga kan ta kai a qasa, Mum idon ta kamar gurjiya dan girma, ta shiga mummunan tashin hankali daya sa saida ta jingida na bango na kusan minti 3, kannan Nasreen ta suturta jikin ta ta dakko yaron ta dake bacci zata raba Mum ta wuce, dan ko ba a gaya mata ba tasan zaman ta yazo qarshe, shaqe mata wuya Mum tai tana zare ido tana masifa" jarababbiya wato fitar da nai saida kk san yanda kikai kija jawo ra'ayin shi kanki ko? An dade ba a yi ba shine dan jaraba kk sa yazo wajen ki ko? To fitar tawa ma minti nawa ne? Na gode maki Saude da kk sanar da ni da wuri duk da na makara zuwana, amma van makara ba wajen aika wannan lahira,dan yau, sai dai,ko ni,ko ke, a hanzarce ya isa gaban ta ya kwace ta da kyar yana kuka " Mum kiwa Allah ki auran Nasreen, karki cutar da rayuwa ta dan Allah"😭 "Nasreen zo ki wuce ki bat gidannan yanzunnan kan na budi ido na qara ganin ki" bude jakar ta tai ta debo kudi masu tarin yawa ta bude jakar ta ta zuba mata ta hankada ta waje ta rife qofar, miqewa yai da gudu zai fita waje ya bita Mum ta daka mai wata gigitacciyar tsawa, qamewa yai a wajen jiki na rawa, a fusace ta matso inda yake ta wanka mashi wasu marika masu zafi guda uku, ta nuna shi da yatsa" Naseer indai ni Habee nice na haife ka, kuma ka sa qafa kabi yarinyar nan ko yanzu ko a gaba kai ko a hanya ka gansu ka nuna ka san su to bani ba kai na yafe ka nonona da kasha ban yafe maka ba ka nemi WATA UWAR amma ba ni ba, duk iya alfarma na maka banga dalilin bin wannan karuwar ba na fada maka" ta sa kai tai dakin ta ta bar shi nan kwance kamar xai mutu dan baqin ciki, dirqushewa yai yana kuka mai ban tausayi yana "shikenan ni kuma rayuwata ta halaka, na shiga uku Nasreen na rasaki har abada, ki yafe man , ki kula mana da dan mu" haka yaita sambatu har yai baccin wuya. Mum ce ta fito ta ganshi a wajen tausayin shi ne ya kama ta mai tsanani amma haka ta wucewar ta, ta dakko wayar ta" Hajiya Bilki akan maganar da muka fara dazu ne ni bana son auren ya wuce wata daya komai da komai nake son mu kawo a gama akan lokaci" To shikenan Hajiya ba damuwa data dawo daga Adamawa za ai komai dan dama Naseer shine burin ta a kullum shine dai baya kulawa" to na gode Allah ya bar zaman tare ya qara mana zumunci".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta fita gidan tana kuka sosai Taxi ta tsayar sai gidan su na da, dan dama Hajiya Asabe na sane d komai da ya ke faruwa kawai dai Nasreen taqi yarda da abubuwan da Hajiyar ke fada mata ne, na ta bat gidan ta dawo su dora daga inda suka tsaya. Kuka take sosai tana cewa" dana sani na bi maganar ki hajiyata da duk wannan wulaqancin bam fuskance shi ba" ganin mahaifiyar shi na kuka ne yasa Naufal kuka shima, Nono ta fara bashi tana rarrashin shi suka isa , daidai nan hajiya ta fito daga mota itama da alama unguwa ta fito.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan jajantawa da komai, daga ranar Hajiya Asabe ta fara gyara Nasreen sosai ta maidata hadaddiyar mace, kyau kam ba a magana, irin cika da kyau da Nasreen tai ba a magana , a haka ne Hajiya ta samo mata mai reno ta aje Naufal ta dora daga inda ta tsaya masu kudi kuwa manyan qusoshin gwamnati ne ke zuwa wajen ta, hajiya nada wannan connection din har waje saida Nasreen ta fara fita akan harkar karuwanci, duk abinnan da ake Naufal ya kai shekara biyu lokacin bai san meke faruwa ba, domin in zata hadu da danta cikin shigar mutunci take zuwa tai wasa da shi tai mai komai, ya saba da ita sosai in bata nan ta dawo yaita murna, tsaraba ba irin wadda bata kawi mai, ana haka ne ta yanke shawarar aika wasu kudade masu yawa gida, ta kuma yanke shawarar zuwa ne da kanta ba aike ba.😱</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> QAUYEN LANGYM</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hinde ce take miqawa inna dari biyar duk ranta bace, "ke inna yau fa iya abinda na samu kenan kuma ba sisin da zaki ban yanzu?" Tab ai ko sisi ba zan baki ba, naga in haka ne kin tsira da jin dadin da kikai a can yawon naki ni ba saina tsira da dari biyar din ba?" Allah gobe ba zan kawo maki ko........, sallamar Nasreen ce ta sa dukkan su suka miqe suna zaro ido, " wana ke gani kamar Nasreen ?" Cewar Inna kenan" Inna nice Karuwar yar ki ce ta dawo tare da jikan ki, Hinde bismillah mana ki iso ki dauki dan ki mana ga kaya bako taimakawa? Tana yi tana murmushi, Baban Hinde ne ya shigo riqe da ciyawa a hannu , da gudu Nasreen ta qarasa ta karbi ciyawar ta sauke masa tana masa sannu, baki bude yake kallon ta da kayan jikin ta da suka matse ta yan kanti riga da skirt , "wace wannan kamar Nasreen?" Baba nice</p><p>Muje ciki" ciki suka shiga inda Innar hinde da Hinde suke baki sake. Bayan sun zauna ne Nasreen ta kwashe komai ta gaya wa mahaifin ta ta ce "Yanzu ma kwana biyu kawai zan na koma akwai inda zamu da wani Alhaji zuwa Ingland damu dan yi sati biyu yasa nace bari na zo a gaisa an dade ba a hadu ba" Baban Hinde kuka ya fara yana" Haba Nasreen yanzu tarbiyyar dana maki kenan ? Ina hankalin ki yake? ina tinanin ki ya tafi?" Kuka take son yi saboda jin da take bata kyauta wa rayuwar ta ba da mahaifin ta amma ta danne, " come on Baba meye na kukan, haka fa Innar Hinde take son ganina kuma yanzu gani ba shikenan ba " Innar Hinde ce ta matso for d first time tai magana" 'Yannan rayuwa fa saida kudi ni kuma naga alamar wu a tattare da kw dan haka ki abinda kk so ba mai takura miki a gidannan, Hinde ce ta matsa tace wallahi kuwa, da ace kinbi shawara tin da ai da kin dade da sanin dadin kudi, ni yanzu so nake nima ki kaini nai kudi irin naki dan Allah kiyi dan zumunci ba dan halina ba" dariya sosai Nasreen take yi" Lallai hinde baki da hankali a birni wa zai ma zauna kusa dake balle ya neme ki? Ai ke sai mazan qauye" tana fada tana miqewa tsohom dakin su, a daidai gaban Innar su ta tsaya ta budw jakar ta ta dakko kudi yan dubu2 ta aje mata a gaban ta kimanin dubu dari biyu, Inna hauka ne kawai ba tai ba ranar dan murna, sai ga kirari ana zabgawa Nasreen a haka ta ba baban ta wayar Hannu da kudin da Mum ta bata, ta mai bayanin wannan kudin ga yanda ta same su dan haka da Allah ya karba ya ja jari, kafin ta tafi saida ta bude masu account a qauyen gaban su ta damqa ATM hannun wani maqocin su mai shago, tsohon saurayin ta ne shima yana da hankali yaso auren ta matuqa amma Inna ta qeqasa qasa tace baida arziqi, a haka ta bar qauyen Inna na sa mata albarka Baba na mata nasihar taji tsoron Allab ta gyara rayuwar ta, Hinde kam in banda baqin ciki daya qaru mata ba abinda ya qaru a ranta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta koma Lagos lfy, inda sukai tafiya da Alhajin ta har suka dawo. </p><p>A wata yamma sakaliya ne ta hadu da su........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Na'ima Tabital❤</p><p>Salma qanwa ❤Tabital </p><p>Duk na gaida ku kyauta ANA MUGUN TARE❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 15:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta fito dauke da Naufal a kafadar ta, zata bude mota suka qaraso, dayan ne yabi ta bayan ta ya sa mata bindiga a qugun ta, dayan ya shiga mazaunin driver ya zauna ya miqa mata hannu, yana nufin ta bashi key, shigar da su motar sukai suka bata wuta, a can bayan gari suka shiga wani dakin katako, dauke yake da katifa, shiro, ledar daki, dadai tarkacen da ba a rasa ba, SANI kenan, suna isa suka tura ta cikin dakin suka zauna, " Sani meke faruwa ne naga ka kawo ni nan? Kar ka cutar da ni bayan alkairan da kk samu a sanadina" Alkairai???? Alkairai fa kk ce Nasreen ? Wanne alkairai baya ga cin mutunci da Hajiya ta min d korar kare? Sannan ki budi baki ki kira hakan alkairi? To bari kiji in ba baki san meke faruwa ba ki sani, a kwanakin baya naje shago wajen Hajiya Asabe akan nima adan dinga ban wani abu, duba da ni na kawo ki wannan garin, amma Hajiya ta ci mun mutunci tamin tas, tace i should do my wost in ina so but she cant give me a penny, raina ya baci ba kadan ba, tin a lokacin na qudiri dauke ki amma na kasa ganin kina dauke da ciki, bayan kin haihu na rasa ki, sai shekaran jiya na nan ku ke da wani mai kudi, daga nan na fara bibiyar ki, in da kk ganni ma bacen kikai na je gidan da niyyar na ga ina kk, na hango Hajiya da wasu da muka saba sayar wa da gidaje da dikkab alama gidan da kuke ciki zata siyar, hakan ne yasa na biyo bayan ki na sanar dake dan ki koma ki san abin yi, amma a gaskiya a yanda na ganki ba zan iya bari ki kufcen nima ban mora ba," yana yi yana lashe lebe, yana binta da wani shu'umin kallo da shi da abokin nashi suka tafa, "innalillahi wa inna ilaihirraji'un, kana nufin yanzu ta siyar da gidan da komai nawa a ciki? Kenan jiya bamkwana mukai da ita hirar da mukai mai tsaho? Ban taba zato ba, ban taba tinanin haka Hajiyata zatai min ba,😭yanda na dauke ta kamar uwa" hhhhhh a barikin? Anyway banga laifin ki ba coz ke din ba wani kinsan gari bane har yau, zonan dan baba zamu dan ari uwar ka na dan awanni kaji" ya amshi Naufal ya ba abokin, ta miqe tsaye da hanzari zata karbe dan ta, kan ta isa har ya fice, Naufal nata kuka itama tana kuka tana " kaiwa Allah karka cutar da ni da dana Sani ka tai maka ka kyale ni naje na amso dukiyata mai tarin yawa dana tara karna wulaqanta" hhhhhh wulaqanci na nawa kuma maza nawa kk bari suka wulaqanta ki da sunan karuwanci? Kawai bude nima na dana kamar sauran, matsalar daya ni ba biya zan ba kyauta za a ban, kuka ne mai tsanani da nadama mai yawa suka taru mata, wannan wanne irin wulaqantacciyar rayuwa ta zabawa kan? Gashi yau ana son a mata abinda ba ita take so ba, a take tinanin Naseer ya fado mata, wani sabon kuka ta saki mai ban tausayi, amma inaaa Sani ba ruwan,matsowa yai kus da ita bakinnan sai mugun wari yake, toshe hancin ta tai ga uban warin zufa da yake hannun shi wani irin baqin datti, a haka ya sa ka mata a fuska yana share mata hawaye ya sa dayan ya cire mata punnytail din da tai d gashin kanta, ja ta farayi da baya har ta kai qarshen katakon da yake a matsayin katanga, duqawa take qoqarin yi, amma ya riqe ta ya hade bakin su waje daya, wani irin amai ne ya taso mata da bata shiry ba, kafin yai komai ta zubo shi mai mugun yawa a jikin shi tana maida nunfashi d kyar,ashar ya saki ya wanka mata mari mai zafin gaske, ni zaki wa amai a jiki dan........ to ki tabbata kin gyara wajennan kuma yanzu ba sai najima ba saina dana ki nima kamar kowa yar......... kuka take tana roqon shi ya kyale ta amma inaaa, take dabara ta fado mata tinda abinnan dama yi take da kowa ma amma qazamai irin Sani ne bata taba harka da su ba," naji zakai komai kk so da ni nima zan taimaka maka ma, amma wallahi in bakai wanka ka wanke baki ba bazaka taba samun yanda kk so a wajna ba amai zanta yi" hhhhhhj indai wannan ne karki damu fita yai tana nan ta gyara wajen tana rakube tana kuka, tin tana jiyo kukan Naufal har ta daina ji, alamun yai bacci oho🤷🏻♀ bude qofar yai ya shigo ashe dai kyakkyawa ne qazanta ce ta maidashi wani iri, yana yaqe haqora ya qaraso, a haka dai saida yai abinda zuciyar shi ke raya mai da ita, abu kamar wasa ya aje ta ita da dan ta har na wata biyu, tin yana kawo musu abinci har ya zamana baya kawo wa ya fara wulaqanta ta ta kode ta jeme kamar ba ita ba dama baqa ce sai ta qara duhu sosai, ga rama da tayi, gashinnan da ke shan gyara inaaa tini sai da ruwa take wanke.shi, dan ma mai tsafta ce da haka.zatana xama inda Hinde ce😜 a haka si Sani sika dauke qafa, suka daina zuwa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wata rana tana bacci.goshin asuba taji hayaniyar wasu samari, qoqari suke su shogo, dan sin dade suna noticing din ta a unguwar, sunyi2 su bude qofa abu ya gagara, jin hakan ne yasa ta tsorata ba kadan ba, Allah Allah take gari ya waye ta canja mazauni, a haka suka gaji suka tafi suna zasu dawo ne, suna tafiya ta miqe ta saba Naufal a baya ta tattara sauran komatsan ta ta qara gaba tafiya take batasan ina ma take tafiyar ba, har taje wani waje kamar tasha, anan taji suna lodin arewa, tinani take na gwara ta koma arewa da zama akan nan sai ta mutu da danta ma ba wanda ya sani amma acan tasan da yardar Allah bazata na kwana da yinwa haka ba ko aikatau zatai amma alqawari daya data dauka ta gama.karuwanci, tina hakan ne yasa ta goge hawayen dake zubo mata masu mugun zafi da quna ta nufi wajen driver ta mai bayanin ga inda take son zuwa amma bata da kudi ya taimaka mata dakko ta akai aka kawota nan ita da danta bata san kowa ba, a haka dai ya tausaya ya ce ta jira motar ta cika su wuce</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tafiya mai nisan gaske sukai kafin su iso garin kebbi a nan Jega aka sauke ta suka qara gaba jinta a arewa sai yasa mata wani kwanciyar hankali, gefen wata mai abinci ta je tai mata sallama ta fada mata yunwa take ji ita da danta dan Allah ta bata abinci suci zata mata wanke2, kamar zata kore su amma ta tausaya ta bata shinkafa ce da miya ba ko nama haka sukaci suka sha ruwan da ake tarawa dan ko arziqin na yar ledar ba a basu ba, tana gamawa kuwa mayat ta loda mata uban wanke2 mai tarin yawa, ga mamakin ta sai taga Nasreen na murmushi " baiwar Allah hankalin ki bai tashi da ganin wannan uban wanke2 ba?" Hmmm Hajiya ai ni taimaka min kikai domin wannan dan ragiwar na su inna tattara zamu samu na dare da dana wataqila ma harda na safe" tana magana tana maida wani hawaye dake son zubo mata, cikin tsananin tausayawa matat tace mata muje gidana yar uwa zan baki aikatau amma zakina min shara da wanke2 ne a gida zanna biyan ki dubu 3k a wata inkin yarda akwai daki da bandaki a tsakar gida zaki koma can da zama bazan hana ki yin kowacce sana'a ba in kina so" zubewa tai a qasa tana godiya cikin kuka mai ban tausayi Hajiyar daga ta tai.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan sun tashi gida suka nufa, daki da komai ta nuna mata kamar yanda ta alqawar ta mata godiya mai yawa Nasreen ta qara yi ta shiga ta aje kayan su ta fito ta dan tattara gidan nan danan ya dau haske tana gama wa ta shiga wanka daidai nan mijin Hajiyar ya dawo dan kasuwa ne shi kuma, ganin Nasreen ne yasa shi hade fuska sosai kamar wanda akai wa saqon mutuwa..........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> </p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 16: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bude labule yai" kaltume! Kaltume ! Kaltume ! "Na'am Alhaji, sannu da dawowa, irin wannan kira hk? Mi yaffaru halan?" Shiga palon yai mai dake da kujeru masu kyau da TV plasma sai dan abubuwan da ba a rasa ba, kadaran kada han, gidan masu rufin asiri, " wace ta waccan niggani tsakar gida naga kuma qaramin yaro?"kai amma wallah ka ban tsoro, na zaci wani abu na yassame ka can kassuwa wallah🙄 " Shin baki amsamin tambaya ta na?" Me aikatau ta niddako, ayyukan gidan ga na yi min yawa Alhaji, shi nassa na dakko ta ta zanka taimaka min, sai ina bata 3k a wata, ko mi kaggani? Wallahi tausayin ta na yakkamin nace ta tahowa nan din, don Allah mu taimaka mata Alhajina" magana take tana wani rangwada tana matsawa kusa da shi, cire mai hula tai ta fara shafa sanaqon kan shi, take fara'a ta bayyana a fuskar shi yace " to shi kenan yanda kk so ai haka nan za ayi, debo min ruwa nan na sha da abinci wallahi yunwa nika ji" tashi tai tana kada qugu tana rausaya , shiko bude baki yai kamar wawa yana kallon ta yana hadiye yawu, dan Alhajin ba qaramin mayen mata bane, duk qoqarin ta na ganin ta kiyeye mai buqatun shi dake kanta, hakan bai hana shi shegen son mata ba, baya raina haram a mata shi, ba dan yawan son matan shi ba da dukiyar shi ta fi haka yawa, dawowa tai tana kada qirji, da shigar ta mai burgewa, ta durgusa ta aje mai a gaban shi babban faranti ne dauke da abinci da ruwa na wanke hannu da na sha, zuba mai tuwon alkama da miyar kubewa danya da yaji tantaqwashi, ga jus din lemon zaqi da tsami da danyar citta da abarba da tai masa yaji kayan kamshi da sugar, zubawa take tana mai wani salon daukar hankali" Hajiya do Allah dai ki bari na isuwa cin abincin ga lahiya kar ya maqale min ga maqoshi" hhhhhhhhh Alhajina kenan, me nai kuma 😉" ta qarasa da yar shagwaba" hmmmm kaltume kenan bari na isuwa ki ga wani abu" dariya sukai a tare ta zauna kusa da shi tana mai firfita, tana lumshe ido. Bayan ya gama ne taja shi zuwa toilet ta mai wanka tsaf ta saka mai toothpast a brush ta miqa mai itama ta juya tana son tai wankan" Aa ba za ai haka ba nima yanda kk wanke ni nima saina wanke ke, ke kadai ta kason ladan?" Dariya tai mai daukan hankalin shi ta miqa mai soson, wanka yai mata tas suka fito, goge mai jiki tai ta feshe shi da turaruka masu qamshi, dayake garin akwai zafi sosai, ba ta damu da shafa mai ba , mai ta miqa mai ya fara shafa mata cikin salon shi mai rikita ta, tindaga nan salon su ya sauya, ina ganin haka nace to Mero yar sa ido muo waje😂 har an baza ido ana son aga kwakwaf😂😂😜 .Washe gari da safe kan ya tashi ta farka tai wanka ta yi kwalliya tashiga kitchen ta fara hada abin karyawa, fitowar ta ya bata mamakin ganin Nasreen har ta wanke kwanukan jiya ta gyara tsakar gidan ta wanke bandaki, cike da mamaki tace" eh lallai in a tafe kake wani a hanyar ya kwan" gaisawa sukai Naseern ta tambaye ta ko da abinda za a dafa Hajiyar murmushi tai ta sanar da ita wannan abincin mijin ta ne sai in zatai na siyarwa ta taya ta, daki ta koma ta shirya wanka, wanka taima Naufal itama tayi suka koma ciki, komai akan idon alhaji ya faru dan fitar Hajiyan kenan qarar bude qofa ya tashe shi yana hango su ta windo, ganin yanda mazaunan Nasreen ke motsawa a zanin ta ne ya daga hankalin shi" wannan da gani nan gaba ta murmure za ai kaya😋 motsin qofa ne yasa shi fadawa toilet Hajiya ce ta shigo dauke da doya da kwai da taiwa suya mai ban sha'awa tai souce mai yankakken nama qanana a ciki ta dafa masu Tea daya sha kayan qamshi ta shigo ajewa tai ta leqa bandaki ta qarasa taya shi wankan suka fito ta shirya shi dan daya yagama zai wuce kasuwa, bayan sun gama ne kan ya fita Hajiyar na rungume a gefen jikin shi ta dawo gabam shi ta saqale hannayen ta a wuyan shi tana kallon idon shi tana murmushi" Alhajina Allah ya bada kassuwa mai albarka, Allah shu kare mun kai, ka dawo lahiya Alhajina" yana amsawa shi kuma da Ameen, bakin ta ta kai nashi ta dade tana mai kiss sannan ta janye jikin ta tayo gaba ya biyo ta a baya, qofar dakin Naseeren ta tsaya, tai sallama , fitowa tai cikib shiri ita da danta, duqawa tai kai a qasa "Alhaji ina kwana" " lafiya qalaou" yana amsawa yana wani kauda kan munafurci yana hade gira, " to naji duk bayani daga wajen Hajiya ta fadi man komai ina fata xaki abin da yakkawo ki gidan ga lahiya, bana son kuma naji wani abu mara dadi daga wajen ki, dan wanda zai taba min mata to shina fuskantar fushi na ko, ke jiya" daga kai tai ta amsa da " Na gode Allah ya saka maku da alkairi, in Allah ya yarda ba abinda zai faru mara dad'i" kallon Hajiya yai yace " tau ni sai na dawo" yana mata murmushi, itama murmushi tai "ka dawo lahiya Alhaji na.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka rayuwar su ta kasance, kullum kaga Alhaji zata zakai duniya baya kallon wata mace sai tashi, ita kuma Hajiya bata da burin da ya wuce faranta mishi , Nasreen ko aikin ta take cikin kwanciyar hnkali, ga wata qiba mai kyau data fara, ko ina ya fara dawowa daidai a jikin ta, abu daya ke damun ta ALHAJI, dan yasha nuna mata wasu alamu da ta fara jin tsoron shi, misali: akwai ranar da Hajiyan nawajen saida abinci ya dawo gidan ya tadda Nasreen tana duqe tana share inda Naufal yaci abinci sai ji tai an dakar mata duwais ta baya dagowar nan da zatai kawai suka hada ido ta ja baya da sauri" Subhanallahi meye haka Alhaji?" Au ai na zaci Hajiya ce ashe kece" yana wani shu'umin murmushi, " haba Alhaji ya zaka ce haka bayan kasan ba utan bace?" To ke yanzu yarinya dan na mori jikin ki ma mene a ciki ba fa sani za tai ba" subhanallahi haba Alhaji kamar yanda hajiya ta ban labari da kun samu haihuwa da kana da kamar ni, ai ni 'ya ce a wajen ka, kuma Hajiya na iya qoqarin ta akan ka" ganin da yai lokacin dawowar matar shi yayi e ya sa kai zai fita, " in kka bari mata ta taji labarin nan zaman ki yazo qarshe kuma ba yarda zatai da ke ba in kin kiyaye kin tsira" ya fice ya barta cikin matsananciyar damuwa, "oh ni Nasreen ya zanyi?.......</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> </p><p>BY </p><p>HAERMEEBRAERH</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Masoya novel dinnan na WATA UWA amin afuwa yesterday i was so busy ne yasa ban yi typing ba, dan Allah wanda suka ji haushi har ake sa min red face ayi min choli😂ayi hamfuli inshaa Allah daga yau har sai na gama ban tsaya ba. Tanx for d love and care.❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 17: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tinanin ta ne ya katse bayan sallamar Hajiya da tai, ta dawo daga wajen sana'ar ta, amsawa Nasreen tai ta tashi da hanzari, ta fara karbar kayan hannun ta, tana sauke ma yaran da suke taya ta kwaso kaya su ajiye, "Sannu da dawowa Hajiya, ya kasuwa?" Alhamdu lilLAAH Nasreen, yau da zazzabi mai zafi na dawo gaba daya jikina ciwo yake bana jin dadi ko kadan" Subhanallahi, Hajiya muje ki watsa ruwa sai ki ci abinci ki sha magani, Shifakillah Hajiya" Ameen na gode Nasreen, a gaskiya ina jin dadin yanda kk tafi da al'amuran ki cikin nutsuwa ga hankali, zan so sanin labarin ki" Murmushi Nasreen tai tace," Hajiya kenan labari na ba komai cikin shi ban da abin haushi da dana sani, amma ki gama komai sai na baki labari na inshaa Allahu" shiga ciki sukai ta taimaka wa hajiya ta gama komai ta kwanta a palo, anan Nasreen ta bata labarin ta da komai, Hajiya ta tausaya mata amma ta mata fada sosai na wautar da ta aikata, dan dalilan ta bai kai ja ta fara karuwanci ba sam, wa'azi sosai Hajiyar ta mata wanda ya ratsa zuciyar ta yasa mata jin tsoron Allah sabo a ko ina na jikin ta, kuka take mai cike da nadama da dana sani, Hajiya nuna mata tai ya kamata ta je taga mahaifan ta tanemi gafarar musamman mahaifiyar ta, ta kuma nuna mata abubuwan da ta dora su akai ita da qanwar ta ba mai kyau bane, Share hawayen ta tai, tai mata godiya, ashe duk abinnan da suke fada akan kunnen Alhaji ne😱fita tazo yi taji ta bige mutum,tai maza tai baya tana kallon hanya, Alhaji ta gani yana mata wani mayunwacin murmushi, amma yana daga labulen ya bata rai ya shiga da sallama, fita take qoqarin yi Hajiya ta dakatar da ita," Dan Allah Nasreen debon abincin Alhaji, kin dai ga yanda nake hada mai ko?" Eh Hajiya" fita tai a hanzarce ta kawo, daidai nan Alhajin ya dora ta akan cinyar shi yana wasa da gabibin jikin ta wai tinda ba ta da lfy bari ya mata tausa yasan harda gajiya, bakin shi a wuyan ta yana kissing yana taba qirjin ta da hannun shi daya dayan kuma ya saqalo ta qugun ta, Shigowar Nasreen ne ya sa Hajiya ke son sauka amma ya hana , yana ci gaba yana bin Nasreen da wani shu'umin kallon da yasa tai saurin dauke kanta ta fice, zuciyar ta bugawa take da sauri sosai kamar zata fasa qirjin ta ta fito," Ya ilahi wannan wanne irin karuwan namiji ne haka?😱 anya zamana zai ci gaba anan kuwa? Inna bar nan na bar gidan aminci, ka taimake ni ka barni na zauna cikin rufin asiri" tana fada hawaye na bin fiskar ta, a haka ta zame ta tsugunna ta ci gaba da zubda hawayen rashin sanin abin yi, jitai wani dan qaramin hannu na share mata hawayen kuma ya rungume ta duk da bai iya ritsa jikin ta dika , rungume shi tai sosai a jikin ta itama, kuka mai dan sauti ta fara tinawa da uban shi da tai, ko ya yake? Ko yayi auren? Allahul musta'an, tashi tai ta dauki danta ta koma gefen katifa tana jijjiga shi yai bacci, kiran sallah akai ta miqe taje tai alwala tai sallar isha'i tai adduoin ta, tqi karatun Qur'ani, ta kwanta a gefen katifar ko hijabi bata cire ba, dan tana son tai wankan kwanciya da ya zama dabi'ar ta ko tayi da magrib in xata kwanta sai ta sake, a haka bacci ya dauke ta bata farka ba sai qarfe 11pm, sa hanzari ta miqe ta daura zani ta sa hijab da take wanka da shi ta dau kayan wanka ta fita ta shiga wanka kenan ta saka sabulu a fuska taji kamar an shigo, tsoro ne ya kama ta sosai, kan tai qoqarin wankewa an janye robar wankan gefe, lalibe ta fara, qara ta bude baki zata saki ya saka nashi bakin a nata, kamar mayunwacin zaki haka ya dinga laliben jikin ta kuka take sosai amma ya hana ta bude bakin tayi ajiyo ta, dabara ce ta fado mata, harshen shi ta kama ta cixa da qarfi kan ya janye ta kama leben shima ta kafa mai cizo sosai saida taji alamun jini ta saki, wani wawan mari ya sakar mata ya hada ta da bango, qoqari yake ko ta halin qaqa sai ya cimma burin shi akan ta, wannan dalilin ne yasa kan ya fito ya kunna karatu ya ware volume yanda Hajiya na bacci bazata ji ba, kuka Nasreen take amma ba mai taimkon ta, addua ta fara sosai akan Allah karya bashi sa'a, yana gab da zai karya mata alqawarin ta na daina kusantar kowanne namiji in ba mijin ta ba aka turo qofar, 😱😱😱 Hajiya ya gani a gaban shi tana kuka sosai, bata kula shi ba tai wajen Nasreen dake kuka ta kama hannun ta suka fita a lokacin ne ta kula ma idon ta da kumfa, daura mata zani ta fara sannan ta wanke mata fuska taja ta sukai dakin ta ta rufe qofar, zama tai a qasa tana kuka sosai mai ban tausayi, dukan su ba mai ba wani hakuri saida sukai mai isar su, Hajiya ce ta fara magana" ta shi nai zan fitsari naga ban gan shi ba, sai nai zaton ko ya je waje dakko wani abu ne dan banji motsin shi toilet ba, fitsari na nai na kwanta naji shirun yai yawa bai dawo ba shine na fito ina fitowa naji kamar kuka a toilet kuma naji qarar Alhajin😭 ina bude qofa na ga abinda ke faruwa" ta qarasa cikin matsanancin kuka" ka cutar da ni Alhaji, kacu amanar qaunar da nake maka, qawayena da yan unguwa na ban labarin halin ka na neman mata na kauda kai, na toshe kunne na saboda na zauna lfy, saboda kar na yarda bayan ban taba gani ba, shine dalilin da yasa ban bari nabi ta qawaye na ba na mun girma da zuba soyayya irin ta yara, ba dan komai ba sai dan na kare ka daga fadawa sharrin zina, amma dik da haka ban iya ba" da qarfi take maganar, yana waje hawayen nadama na bin fuskar shi tin da yake ba ta taba kama shi ba, bqi taba jin kunya da tsanar zina ba irin na yau, yayi nadama mara iyaka, amma yasan halin matar shi in tai fuahi da abu, shiyasa ma take kauda kai sosai dan karta sa a ranta ta tsane shi, ya san rabuwa za sui kawai, tina hakan ne ya sa hankalin shi ya tashi ya fara buga qofa yana" Hajiy ki min rai ki hakuri kowanne hukunci ne ki min amma karki rabu da ni mutuwa zan na rasa ki"😭 kukaya ke kamar yaron da aka hana chocolate🙄 Hajiya kallon Nasreen tai tace tashi ki je ki hada kayan ki gobe da safe zan baki dubu 10k ki je gidan iyayen ki nima zamana a nan ya qare.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Washe gari da safe komai ta hada na kayan ta da danta data runquma a baya dan taji dadin tafiya, Hajiya ce ta fito fuska tai mata jawur dan kuka, ta muqa mata kudin itana cikin shiri, a hanzarce ya taso a inda ya kwana a gefen dakin ya durqusa gaban Nasreen yana mai bata hakuri, tace " bani zaka ba hakuri ba, danni daga yau bazaka sake ganina ba, Hajiya zaka nema ta yafe maka,Hajiya ki hakuri ki sassauta wajen yanke mai hukunci, domin kema in bashi bazaki iya rayuwa ba, fatana wannan abuj ya zama hanyar shiryuwar ka, kamar yanda Allah ya shiryar dani" hanya ta dauka zata fita............</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR. 👵🏻</p><p> </p><p><br /></p><p> BY </p><p>HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 18:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> QAUYEN LANGYM</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Nasreen ta isa qaunyen su lfy, kafin ta shiga gidan su saida ta dade a qofar gidan tana jiyo mitar Innar Hinde, akan kudin abincin dare da ba zai isa ba," to dai kaji na fada maka sai dai inna dafa mu muci kai ka hakura, ace mutum ba zai fita ya nema ba kamar yanda sauran maza keyi, sai mun samo ka dinga bude baki ana baka kana amshewa" Innar Hinde wata rana sai labari, babu wani mai arziqi da yae dawwama da arziqi haka ba wani talaka da yake dawwama da taluci? Kowa kk gani da rayuwar da Allah ya tsara masa" hahaiiiiii casssss an iya wa'azin babu ba a iya na nemowa ba, kaini bani wuri na wuce" ina Hinde taje da magaribar nan kina kallo ta fice" taje wajen saurayin ta da yai mata alqawarin in ya qasa tsire gashin farko nata ne" yanzu rayuwa zatayu a haka kuwa?" Sai kuma kayi" sa kai tai ta bar wajen ta shiga madafi. " Assalamu alaikum" sallamar ta ce ta sa Baban.hinde fitowa cikin hanzari </p><p>Kamar a tare suka fito da Inmar Hinde, " Aa mutanen Lagas ke kk tafe da maraicen nan? Sannu da zuwa bismilla shigo lale maraba" tana yi tana kallon jikin ta, kallo take mata na to wannan karon ke da zamu ga kinfi da arziqi, me nake gani kuma haka? Shiga tai ta durqusa gaban mahaifin ta ta gaida shi ya amsa ta gaida Innar su ta amsa, miqewa tai ta aje Naufal ta tafi bandaki, ta fito kenan tai alwala ta kama Naufal ta sa shi yai fitsari yai alwalar shi da ya koya wajen Mummyn shi ya biyo bayan ta, a yanzu ya kai shekara uku, daki suka je ta tada sallah ta rama sallolin ta dika, ta jira isha'i , ta idar ne taji an daga labulen an shigo, " mutanen birni ko dan kudi a hannun ku mu samu na dora abincin dare" tana wani dariya kamar wawuya haqoran nan kamar ta ci dorawa , miqewa tai taje kusa da handbag din ta, ta bude ta miqa maya dubu daya, kallon kudin tai ba yabo ba fallasa, ta sa kai tai waje wani shegen tuwo ta debo mata wani baqiqqirin, aka kawo mata, wato wannan tuwon kudin ta ne ko me? Hmmmm. "Inna ga kinga tsinke uku ya ban" wani burki taci kamar mota a gaban Nasreen da ta dawo tsakar gida ta sa tabarma ita da Naufal, " mutanen birni yaushe a gari inji maqi baqo" Nasreen murmushi tai tace oh Hinde ana nan da halin ashe ke baza ki ma kan ki fada ba, ki duba kiga rayuwar nan yanda ake mutuwa, ga cututtukan zamani da ake dauka ta hanyar saduwa barkatai, ke baki nutsu a matsayin ki na mace kin koyi abubuwan da macen aure ya kamata a ganta da su a same ta da su a gidan aure, sai dai ki ta yawo maqota shaguna, a haka kk so watarana ki aure? Wace irin rayuwa kk son kiyi anan gaba?" Hahaiiiii casssss dakata min limamiyar gidan karuwan Lagos daga zuwana? Daga tambayar yaushe kk zo? To ahir din ki da matsawa rayuwa ta, har kina da bakin magana? Tinda nake yawo na kinji ance na yi ciki bare na haihu? Ni yawona bai nisa ba gaban iyaye nake yin shi, ban kuma nemi ubana ba kan na bar gida ehe" tana kaiwa nan Inna ta bushe da dariya tana kama baki" kaiii yar nan kin san ta kan tsiya" Baban Hinde ne da ya gama jin komai ya leqo ya kira Nasreen, ta shi tai ta isa ita da yaron ta, suna zuwa ta durqusa gaban shi idon ta a bushe ko digon hawaye babu, saboda zuciyar ta ta gama bushe wa ta kuka akan su, " da farko dai duk da ban san me ya dawo da ke ba amma naji matuqar dadin fahimta da nai kin aje harkar karuwanci kin ringumi rayuwar da Allah ya amince da ita, sannan jna maki fatan alkairi da qara maki nasiha akan kiji tsoron Allah, ki qara tsare mutuncin ki, Allah ya miki albarka,ya kawo maki miji na gari"Ameen Baba" anan ne hawaye suka taru a idon ta tasa yatsan ta ta share ace" Baba so nake inna dan kwana biyu zan dan dinga koda wanki ne na tara kudi ina son na koma Lagos na nemo Baban Naufal a qalla yasan inda muke da zama saboda yanayin rayuwa yaron nan wataran zai so ganin shi ban san ina zan same shi ba, gwanda tin da wuri na nemo inda yake" kuka ne ya kwace mata duk son dauriyar da take amma ya gagara, tinda ta rabu da Naseer kullum da son shi take kwana take ta shi, bata jin zata iya auren wani in ba shi ba, hawaye ta share, sallama taiwa Baban ta kafin su fito Naufal yayi bacci, gware sukai sa su Inna komai akan kunnen su, (yan labe kenan, yin labe a abinda ba ai niyyar kaji ba haramunne) to su Inna su wane haram ne basu aikatawa?🤔 sai abinda ba a rasa ba, kada kai tai tace " Allah ya kyauta" tai daki ta barsu suna qusqus" </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Washe gari tashi tai ta gyara gidan tai komai, ta dama koko , ta debo ruwa, sannan ta fita shagon maqocin su data damqawa ATM tai, sallama tai masa, ta sanar da shi ta dawo, dakko mata yai ya bata a hannun ta tai godiya mai tarin yawa ta miqa mai dari biyar ta fito, dan achaba ta dauka ya kaita can inda ake cire kudi farawa tai da gwada cire dubu biyar taga ta cire, wani dadi ne ya kamata ta qara cire wa" Alhamdu lilLAAHI" a haka ta cire dubu sha biyar ta dawo gida cike da murna, kayan da ta dan tsaya ta siyo masu ta aje a kitchen ta je qofar dakin Baban Hinde tai sallama" Baban Hinde amsawa yai ya fito bayani ta mai da komai, sannan ta qara da cewa" ina ganin wata juma'ar zan tafi tinda na ji ance Ado ya zo sai mu tafi tare, in yaso daga nan zan nemo Baban Yaronnan dana ganshi zan dawo" To Allah ya nuna mana, ya kuma sa. Ki dace in kinje" Ameen Baba" miqa mai dubu uku tai, ya karba yana mai sa mata albarka, aiko sai ganin Innar Hinde sukai ta dire a tsakiyar su, miqawa Nasreen hannu tai tana kada qugu" lallai yarinyar nan ashe uba yafi uwa? Ina zaune ina ganin kina mai barin dubunnai kin hadani da wasu kaya kin wuto nan to ahir din ki da baki na, maza2 naji hannuna ya cika da kudi nima" miqa mata dubu biyu tai tai daki abinta, ledar data shigo da ita ta hannun ta ta budewa Yaron ta a gaba nama ne gasasshe ta tura mai yaci, ci ya fara kamar wani mayunwaci( ko dake mayunwacin ne ma ina yake samun hakan?) Sai da ya ci kamar yanka biyar ya dakko ya sa mata a baki, murmushi tai idon ta taf kwalla tace Naufal ke nan ka tina dani na gode amma so nake kaci in ka qoshi sai naci sauran, ni na ci dazu" girgiza kai yai ya miqa mata a baki, daga lokacin wani tinani ya shige ta, yaron nan fa bai taba qoqarta yin magana ba fa daga kuka sai dariya meke damun shi ne ko dai kuma ne😱 tashin hankali taji ya shige ta da ta tina hakan, "Naufal! Naufal!!Naufal!! baya amsawa saidai ya kalle ta ya qara matsawa kusa da ita " ka amsa min in kana jin me nake fada ko baka iya magana ne, girgiza kai yayi yana murmushi, kuka ta fashe da shi ta rungume shi tana "kai min magana dana rashin maganar ka is killing me, pls say something, anything my bby"" Daddy".....</p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Masoya novel din nan na WATA UWA ina fatan zaku gafarce ni na dan samu rashin lfy ne yasa kuka ji ni shiru. Na gode sosai da kulawa da adduoin ku Allah ya barmu tare. Love u all❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 19:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A hanxarce ta dago shi daga kafadar ta tana kallon shi ido taf hawaye " Naufal dear me ka ce? Cikin doki da zaquwa take tambayar shi, dan bata taba zato ko tsammanin hirar da takan mishi na mahaifin shi yana ma saurarar ta ba sai.yau, "Daddy" " Daddyn ka kk son gani Naufal?" Daga mata kai yayi ya kwanta a jikin ta, qara rungume shi tai tana kuka sosai tana cewa" nima ina tsananin son ganin shi Naufal Mum ta raba mu da masoyin mu, ta nesanta mu da shi, da bai aikata kuskuren da ya aikata ba na kuma biye mashi, da tini muna tare, koda kuwa yayi wani auren, bazamu ravu ba, zamu dinga ganin juna" kuka tai sosai har bacci ya dauke ta, cikin dare ta farka ta aje Naufal ta shiga ta watsa ruwa tai alwala ta hau abin sallah taita sallolin nafila bayan ta idar ne tai addua sosai ta shafa, ta nemar wa kanta sauqin samun Naseer in ta koma lagos.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau alhamis da yamma ne ta fita neman Ado, can ta same shi tare da abokan shi, suna shan abubuwan da suka zama masu kamar farilla, yana hango ta ya taso," ashe da gaske ne?" Aka ce wai me?" Aka ce wai kina gari kin dawo" Ado kenan na dawo, amma yanzu ma gobe nake son komawa, amma zan ji dadin tafiyar in aka ce kaima zaka koma din a goben, ba damuwa in ba zaka samu komawa gobe ba,saidai ba haka na so ba"hhhhh to ai faduwa ce ta zo daidai da zaunawa don kuwa yanzu ma sallama nake wa guys dina, gobe zan koma motar asuba zan bi, kinga kawai sai ki shirya ko" kaiiii amma naji dadi sosai, Allah kuma ya nuna mana" to sai mun hadu goben" gida ta tafi ta sanar da Baban Hinde yanda sukai da Ado, addu'ar samun nasara ya mata, da nasihohi masu ratsa jiki wanda yasa taji ko mai rintsi komai wuya bazata iya wulanqanta kanta ba kamar yanda tai a baya, godiya ta mai sosai sannan ta sanar da shi ba zata tafi da Naufal ba dan in taje da shi suna iya amsar shi su barta ta dawo ba dan ba uban, amma in ta tafi ita daya dole zai so ganin dan shi kuma zai biyo ta yaga mazaunin ta ko dan gaba, Baban Hinde yai na'am da shawarar ta, sai dai a qasan ran shi yana tausayin yaron in ta tafi ta bar shi a hannun wadannan mugayen ya zata kasance da shi, itama tinanin dake zuciyar ta kenan amma ta dake, a ranta tace Naufal ka yafe min zan je nemo mana yancin mu ne da gata, wahalar da zaka sha ta lokaci ne inshaa Allahu, a haka ta goge idon ta tai ma babanta sallama ta shiga ciki. Zaune suke ana maida yanda akai da rana ta shiga, tai sallama suka amsa dari biyar ta ba Hinde tace ta siyo masu tsire aiko kamar zata kwata haka ta fizge ta fita da gudu kamar balama, girgiza kai Nasreen tai cikin takaici ta dawo da kallon ta wajen Innar su, kora mata bayani tai akan tafiyar ta da kuma barin Naufal da take son yi, " kan uban can, akan me zaki ta fi ki bar mana shi anan? In ji da ci da uban ki da qanwar ki ko inji da ci da kaina?" Can kuma tai qasa da murya tana murmushi" to me zai hana ma na riqe jikana musamman un uwar shi zata na aiko mana da kayan masarufi?" Murmushin takaici Nasreen tai dan Innar Hinde bata san neman uban Naufal ne zai maida ta can ba, a zaton ta karuwancin zata koma," Inna karki damu yanzu ma zanbar miki dubu uku a hannun ki inna je naga yanda abubuwa suka kaance zan dinga aiko kudi ta wajen me shago kamar da" shewa Innar ta tayi tana mata kirari tana sa mata albarka, hawayen baqinciki ne ke bin kuncin ta masu zafi tana fadin " oh ni Nasreen ban dacen uwa ba, wannan wace irin uwa ce? In zan kashe mutum na kawo mata kudi ba ruwan ta, amma in abun alkairi zan sau dubu ba zata samin albarkar ta ba, da WATA UWAR ce ta gane ma yar ta na bin maza ai sai ta kusa kashe ta, amma tawa Uwar hankalin ta kwance ita ke sani hanya ma" kukan da ya kusa kwace mata ne yasa ta tashi da hanzari ta tafi dakin su, akan shimfidar su ta fada ta na kuka mara sauti, yaron ta tajawo jikin ta ta rungume tana mai kiss, tana kuka tana mai addu'o'in tsari, tana mai magana kamar yana a farke" Naufal ka yafe min, nasan abinda zan ban kyauta ma rayuwar ka ba tin farko ma dana samar da kai ta hanyar zina, sannan gashi yanzu zan tafi na barka, a inda ba qaunar ka suke ba iya soyayyar su da kai iya abinda zan mallaka a hannun su ne, wanda inna ta fi ban san ya rayuwata zata kasance ba, shin zanyi nasarar ganin Daddyn ka ko ba zan gan shi ba? Allahul musta'an" kuka take sosai har yaron ya fara motsawa sannan ta rage sautin muryar ta, daga kai yai ya kalle ta cikin barci ya qara rungume ta ya kwanta kuka mara sauti ne ya qara kama ta ta rungume shi sosai, har a suba idon ta biyu a hankali ta zame shi daga jikin ta ta mai kiss a goshi da kumatun shi, kamar ba zata bar shi ba ta fito da kayan ta a hannu ta kwankwasa wa su Innar ta qofa, fitowa tai tana hamma, da mugun warinnaj na bakin ta, da sauri Nasreen ta kauda kai ta ja baya, duqusawa tai ta gaida ta sannan ta fara mata sallama, kauda kai Innar hinde tai tana kada qugu ta miqa mata hannu" ai ni sallamar ki shine naji kudi a hannuna shine nasan kina sallama, wani na yafe ki ko karna yafe ki duk bai taso ba" kada kai Nasreen tai da takaici ta bude jaka ta miqa mata kudin, Baban Hinde ne ya fito sukai sallama ya raka ta har tasha, amana ya damqawa Ado ita sannan ya koma gida.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sunyi tafiyar kwana daya da wuni daya cur a hanya dab sai jusab 10 dare suka isa garin lagos suna zuwa suka hau mota tace so take a kaita Apapa can wajen Hajiya Asabe dan koma meye data je inda bata sani ba gwanda ta je inda ta san halin su, van kwana sukai da Ado ya bata lambar wayar shi a jikin kwali ta sa a jaka, ya kama hanyar shi ta kama ta ta, ta isa wajen Hajiya Asabe ta tarar suna qoqarin tafiya gida kenan, ganin Nasreen ne yasa Hajiya Asave kusan kifewa, Zata gudu ciki ne yasa Nasreen ta dakatar da ita tace" Hajiya karki damu ni ban zo dan na tambaye komai nawa va nazo ne dan ki taimakan da wajen kwana da aikatau har na gama abinda zan a garinnan na koma, dan ni yanzu ko kin dawon da komai bar miki zan bazan ci ko sisi ba nq haram" yawu ta hadiye ta na zare ido fuskar data sha hoda duk ta jiqe da gumi ta sa kukan munafurci ta rungume ta" 'Yata Nasreen muje gida na baki labarin abinda ya samen bayan na cuce ki na saida maki da komai" kama hannun ta tai suka shiga Taxi suka nufi wata unguwa coconut suna isa Nasreen taga wani gida mara kyan gani da qazanta wai nan zasu shiga nan ne gidan Hajiyar yanzu, dama tun a wajen saida abincin ta kula komai ya ja baya, suna isa ta sallami mai Taxi suka bude wani dakin katako suka shiga daga katifa dai leda da sauran tarkace, zama sukai a qasa Hajiya ta fara bata labari..........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 20:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> " A gaskiya million 5 zan siyar maku da wannan gidan, wannan in kun kula ai ba irin wancan vane, kuma in ba baqin ciki zaku min bama ai ba ku kuke siya va, ku je ku gayama Yallaban ga akan yanda na ce" " Hajiya ke nan karfa ki manta akwai filaye uku da kk ce zaki hade ki siyar kina nufin duk suma a million 1 din zaki bassu?" Kwarai kuwa kunsan da yaya na sane su ne? Wahala na sha kafin na same su, dan haka dole na siyar yan da kudi na za su fito " k ba damuwa, yanzu abun da za ai ki kawo takardun komai har da na motocin kawai ki sa hannu a jiki mu kai masa in yaso yanda dai aka saba kin jimu da kudaden kin, daga nan sai a fiddamu koya baba?" Tafawa sukai a tare suka bushe da dariya, jiki na rawa ta tattaro komai ta basu suka tafi," Hajiya aita hakuri ko da kin dan ji shiru zamu neme ki sabo da kin san yanayin kasuwancin namu ba ke kadai bace zamu tattara na wasu mukai inda za a siya, yanzu mu mun wuce sai kin ji mu" A ba damuwa wannan harka ai an zama daya" ba matsala Hajiya an zama daya" fita sukai suka hau abin hawan su suka bar wajen suna dariyar da ban gane wacce iri bace sai yanzu, ashe dariya ce ta sata ta saci sata😭, zan gansu yau ne?gobe ne? Ga shi har yau shiru basu ba labarin su ban da wajen kwana sai shagon abinci a hankali da na dan samu wasu kudin na kama hayar nan din shima kuma kudina ya kusa qarewa ga wajen abincin duk ya ja baya, Nasreen ki yafe min, tin da na fara harkar nan na sha cin kudin mutane ta hanyar da na ci naki amma ba abinda ya taba samuna sai a wannan lokacin , ba komai ne ya jawo ba sai yarda amanar ki da kk ban da nai saboda kowacce karuwa tasan ba amana amma ke kin ban amanar kanki tin fari kuma na tozarta amanar taki wannan daliline ya jawon wannan qasqancin nasan" kuka take sosai tana share hanci da gefen zani Nasreen ce ta matsa kusa da ita tace" Hajiya kar ki damu kan ki komai ya wuce a waje na , kudinnan duk dama na haram ne yanzu ni akwai abinda nake son na kammala kan na koma gida zan fara yin wasu ayyukan na qarfi na samu abin da zanna ci da kuma wasu buqatun inshaa Allah, bazan qara komawa gidan jiya ba dan ni ko shagon ki ba na jin zan iya yin aiki a wajen saboda gudun faruwar wani abun, na gode kuma da kk bani wajen kwana" Habaaaa Yarnan in da hali ma ai gida zan sama maki mai kyau wajennan zaman shi ai sai mu da muka saba da gararamba dama, tin da unguwaa ce cike da yan kazo na zo" a haka sukai ta tattaunawa har gari ya waye. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nasreen ce ta fara tashi tai sallah, ta fara gyara dan dakin nasu, sannan ta fita lokacin garin bai gama waye wa ba, tafiya take tana shiga gefen unguwar in da taga wasu gidaje masu dan kyau ta fara shiga tana neman wankau, dan shi take ganin zata iya yi ta samu abinci tinda su ta can wanki da dan tsada riga da wando #50, a haka sai da ta zaga gida wajen shida, sannan ta samu a na bakwai din nan fa ta fara tiqar wanki kamar wata jakar aiki, tana yi tana goge zufar sake karyo mata na rashin sabo da wankin, a haka ta gama wankin tas, kudin ta aka qirga ya kai dari 600, durqusawa tai tana ta godiya" i beg oga if u get another one even if na tomorrow i go come back do am" No me i no get oo but make i ask my sister for u" shiga yai ta tambayi qanwar shi tace ta dawo goben, godiya tai ta koma gida, a hanya ta sai Garri da sugar da gyada sai ruwan sha, da wannan Garrin ta karya a lokacin wajen qarfe 12pm yayi tana sha tana tuno Naufal, wasu hawaye ta goge masu zafi" Allah kai ne ka tsara min rayuwata kai ne masanin abinda ka boye a cikin ta Allah duk rintsi kar ka barni na koma karuwanci ka bani juriya da hakuri, Allah ka cikan buri na na ganin Naseer".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Rayuwar Nasreen haka ta kasance in ba tai wankau ba ba zata ci abinci ba a ranar, sannan ba zata nunawa Hajiya bata ci abincin ba, haka zata tashi ta ci gaba da yawon ta, ana haka ne wata ranar larava da sassafe ta fita wata unguwa dake maqotaka da tasu tafiya take a qafa, ga yunwa ga wahalar nisan tafiyar da tasha, ga shi rabon ta da abinci tin washe garin ranar da safe, duk ta fita hayyacin ta hankalin ta baya jikin ta, ga tinanin halin da yaron ta ke ciki dan tabbas tasan ya fara fuskantar wuaqancin mahaifiyar ta da qanwar ta, tinda kudin wajen su tasan ya qare, ba tai aune ba sai ji tai an yi sama da ita da mota, gefen titi motar ta watsa ta, a guje mai motar ya gudu bai tsaya ba, mutane sun cika wajen ana ta kallon ta, masu Yarabanci nayi, masu turanci nayi, Ibo, Da sauran yaruka, wata hadaddiyar mota ce tsaya a wajen sakamakon tare mata hanya da akai zata wuce, ganin cincirindon mutane ne ya sa ta fitowa daga motar ta na son ganin me ya mutane suka cika haka maqil? duvawa tai taga kamar almajira ce a kwance,qarasawa tai da nufin taimaka mata saboda ganin koma dai mene ne musulma ce da dikkan alama kuma ba datti a jikin ta sai dai kayan sun kode kuma bahaushiya ce, dan haka kodan wannan dalilai zata taimaka. Dago ta tai da niyyar daukan ta sai dai wa zata gani............</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Surayyah Tabital </p><p>This page is for u😊 ANA TARE❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 21: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> "Subhanallahi, Nasreen? Tabbas wannan ita ce, to garin ya haka ta faru, why is she looking very poor like this?" Pls come and help me carry her" ta cema wata a kusa da ita, kamata sukai suka sa a mota basu tsaya a ko ina ba sai a gida, kafin ta isa taima Naseer waya, ta tabbatar yana gida, bude masu gate me gadi yayi suka shiga. </p><p>Kira ta kwala ma Naseer ya fito fuskar nan gaba daya ba walwala a tattare da shi, ya zo ya tsaya a gaban ta qiqam kamar wani soja,</p><p>"Naseer kama min ita mu shiga ka duba ta kaga meke damun ta" bata rai yai sosai yana kumbura" ya zan na kama wannan matar na shiga da ita ta taka da qafarta mana dole sai na daga ta zata tash" cikin tsananin jin ciwon da Nasreen ta ke hakan bai hana ta dago kai ta kalle su ba gaba daya, dan ta gasgata kunnuwan ta, hada udanun su ke da wuya Naseer ya zaburo da sauri ya dago ta a hanzarce yai hanyar shiga cikin gidan, gaba daya ya rude hankalin shi na neman barin jikin shi dan tsananin mamakin anya itace kuwa🤔 tambayar Mum ya fara" Mum ina kk gamin farin cikina? ina kk samo man priceless jewel dina? Me ya same ta naga ba kwari jikin ta kuma duk qasa? "Naseer ka dakko kayan aikin ka ka duba ta ta samu hatsari ne ka gani ko akwai buguwa ko wani abu" da sauri ya miqe yana yi yana juyo wa kamar wani zai dauke ta kan ya dawo, a hanzarce ya shiga duba ta tsaf ya ga ba wani abu daya same ta sai kurjewa da tai a hannu yai dressing wajen ya kira mai aiki da aka kawo mata abinci amma a hada mata da Tea mai kauri da zafi,kawo mata akai aiko kamar wadda ta shekara dari bata ga kwano ba ta hau shan abinci da ci Naseer ne cikin hawaye ya riqe hannun ta ya dakko Tea din ya sa mata a baki yace ta fara sha cikin ya warware sannan ta karba tas ta gama da shi, ta koma kan abincin Mum cikin tsananin tausayin ta ta fara goge kwallan idon ta" Allah kadai yasan irin wahalar da yarinyar nan ta sha" wani kallo Naseer ya bita da shi da yasa jikin ta yai sanyi ta kauda kai, bayan ta gama ne Mum ta kai ta dakin da aka taba saukar ta tai wanka ta bata wasu riga da skirt purple ta saka sun mata kyau sosai, sai dai gaba daya ta sauya kamar ba Nasreen mai Aji ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Nasreen ina mai neman yafiyar ku ke da Naufal, ban maku adalci ba, ban kyauta wa rayuwar ku ba, na cuce ku na cuci kaina kuma, gashi abinda nai dan na sawa dana farin ciki abun ya zama na baqin ciki, na mai aure dan na raba shinda karuwa, sai ga karuwa a cikin gidana 😭 "tana fada tana zubda hawaye Naseer kam gaba daya jijiyoyin kashi sun miqe idon shi yai jawur.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Bayan tafiyar ki ne, Mum ta auran yar qawar ta Hajiya Bilki wato Siyama, Siyama a ido ka ganta ba zaka ce mata ko kallon wani namiji ma da ba muharramin ta ba bata taba ba, amma daga ciki gaba daya maza sun gama mata illa ko ta ina, Mum ba ta da masaniya da hakan amma mahaifiyar yarinyar da yarin yar sun san halin da take aikatawa, tsabae iya taku ne kawai, a haka akai aure aka kawon Siyama wadda Hajiya Bilki ta kaita asibiti aka mata aiki a gaban ta dan ta koma budurwa bayan kayan mata da tai ta dura mata, dan kawai a cuce ni😡 a haka aka kawon ita, amma dake ta riga ta saba da maza kuma dama ta dade tana sha'awa ta, bayan mun kammala duk wata sunna da ya kamata ango da amarya su gabatar ne na haye gado xan bacci na, dan duk da gargadin da Mum ta min ai bata ce dile sai na kusance ta ba, ina kwance ina hawaye sabida tuna ku danake , ko a wane hali kuke? Ko ya rayuwar ku ta kasance bayan kun fita daga gidannan? Kawai naji wani qamshi mai dadi na ratsa dakin, amma ban juya ba na dake to be honest zan so ganin daga ina wannan ni'imtaccen qamshin ke zuwa, daga nan naji motsi alamar an hawo gadon a hankali, sai gani nai an kashe fitila sai bedside lamp ce a kunne, kwantawa tai a gefena ta ratayo hannun ta daga bayana zuwa ciki na kanta a kusa da kunne na tana man wani salon da ya birkita ni, in baki manta ba tinda na fara sanin ki na yanke hulda da duk wata mace, har kk haihu Mum ta hana mu ganin juna ta kuma hana mu aure, kuma ni mutum ne mabuqaci sosai, ta haka tai nasara har muka muji amarcin mu, sai bayan komai ya lafa ne na gano ba budurwa bace rainan hankali tai kawai, sannan na fuskanci akwai ciki a tattare da ita daga alamar saman niples din ta dana gani da yaba yin ta dai dika ja masu ciki ne, shiru nai ban ce komai ba, na tsarkake jikina tana wani yauqi wai ita a zaton ta ban gane ba tana jira na taimaka mata na dau sallaya na fara salla ina karatu bayan na idar da sallah" haba Nass Haka zaka barni ko dan irin tattalina dinnan ba zakai ba? Wato kaci moriyar ganga ko?" Wani kallo na wurga mata daya sa ta sakko da qafarta tai toilet ta gyara jikin ta da shege qarin gashin ta ta fito, koma wa tai ta kwanta ta na bacci. Kamar kasa🙄 da safe bata roba nai nasata a gaba nace tai fitsari ta ban jiki na rawa tana ita fa lfyr ta qalaou , zata min musu na kwada mata wani marin da saida ta ban tausayi, da gudu ta amsa tai toilet tagama ta miqon, fita nai asibiti na, na duba komai na tabbatar tana dauke da ciki na dawo zuwa nai palo na tsaya na kwada mata kira"Siyama ! Siyama ! Da gudu ta fiti jiki na rawa fuskar ta da tasha mai tai jawur Mum ! Da qarfi na kira ta sai gata daga kitchen ta fito," lfy irin wannan kira haka" To taho kiga yar Limamin garin Lagos dauke da cikin wata biyu da sati daya, a daren farko, ita ta fara neman mijin ta, Mun ga matar da kk kori karuwar da ta tuba zata auri mazinacin danki su bar sabon Allah su raya sunnar Annabin rahama dauke d ciki ta na mena ango a daren farko, Nayarda Nasreen ta fito karuwanci ne amma nine namiji na farko dana fara sanin ta a cikakkiyar budurwa, sannan ko da ta dauki karuwanci a matsayin sana'a hankalin ta ya tashi a lokacin da na zo kusantar ta, Mum😭😭 kin cutar da d'an ki, kin cutar da jikan ki, kin cutar da baiwar Allahn da take neman ta samu mafaka a wajen mu, da mun taimaka mata mun rungumi dan mu, mun yi ta istigifari, da Allah ya mana rahama, ya yafe mana, amma ki duba ku ga wannan irin abu an gudu ba a tsira ba" kuka nake sosai a lokacin ina tina ki, ina a ina zan gan ki? Ina wannan halin ne naji an riqe qafata ana kuka" Naseer ka yafen ina son ka, bazan iya rayuwa ba kai ba, a da zan naji zan iya hakura da kai kafin auren mu, amma a tsakanin daren jiya da yau bazan iya rayuwa ba kai ba , ka yafen inna haihu mu maida wa uban dan dan shi, sai mu ci gaba da rayuwar mu" wani wawan maruka muka kai mata a tare ni da Mum, dai dai shigowar Hajiya Bilkisu kenan, a guje ta iso tana " na ga abinda ya ishen, kashen yar zakui kuka sa min ita a gaba?" Hankade ta Siyama tai tana kuka sosai" Umma kin cucen, kin sa yanzu dole rayuwata ta zo qarshe, dan Naseer ba zai ci gaba da zama da ni a haka ba, kince an kwantarda cikin ashe ba wani kwanatr wa, ga shinan ya gane, na tsane ki Umma da ke gwanda min WATA UWAR sau dubu" tana kaiwa nan ta tashi da gudu tai daki ta fada kan gadon ta tana kuka sosai, banko qofar yai ya daka mata duka a cinya, taso munafuka ga takardar ki nan na sake ki saki uku 1 2 3, maza zo ki wuce da shegiyar uwar ki gida tasowa tai tana layi zata fadi nai ficewa tai kan na kai da fita naji faduwar ta timmm! A qasa gaba nai abuna na turo Umman ta nace su fice kan na dawo a hannu ta daga ta suka fita jini na zuba mta, ban qara jin labarin su ba, dan ko Mum na son fadan bana yarda ta qarasa, tun daga ranar na bazama neman ki, ba inda ban duba ba har gidan su wannan qawar taki Barira sai da naje tsammanina ko kan mu karbi Number din su da address ke sun fada maki, Barira ta shiga tashin hankali jin labarin dana bata, tayu kuka sosai ita da mahaifiyar ta suma sika min alqawarin duba ki amma bamu same ki ba, Mum ma ba a barta a baya ba wajen neman ku,wannan shine a binda ya faru bayan rabuwar mu , ki yafen Nasreen"</p><p>Bude baki tai...</p><p>........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Aunty Ummu Sokoto😘</p><p>Baba Larens😘</p><p>Sis Rammalek 😘</p><p>Ina ji da ku sosai. ANA MUGUN TARE❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 22:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Naseer bakai min komai ba da zan riqe ka, ko dikkan ku ma, Mum uwa ce tana qoqarin kare danta ne da zuri'ar da za a samar masa, ta manta cewa shima in wasu iyayen kirkin sukaji halayen shi a bayan bazasu so su bashi yar su ba, shikenan dai yanzu komai ya wuce, ni ba komai ne dama ya kawo ni nan garin ba illa na neme ka, na baka address din in da muke kaje kaga danka, sabida rashin ka yai affecting rayuwar shi fiye da yanda ban tsammata ba, Naufal bai taba magana ba😭sannan kuma randa na damu da rashin maganar tashi sunan ka ya fara kira a duniya,"Daddy" shine abinda Naufal ya fara fada, hakan ne yasa naji dole na zo neman ka, ba zan iya zuwa da shi ba coz ban san irin wahalar da zan sha ba, kar muzo muna jigata ni da shi, ya sa na bar shi a gida can, wajen mahaifiyata" anan ta tsaya da bayanin ta, matsawa kusa da ita yai ya riqe hannun ta yana kallon ta cikin ido ya furta " I missed u so much Nasreen, nai missing dib ku Ke da Naufal, kullum ta Allah sai nai kukan rashin ku, ko a fili ko zahiri ban damuwa da wazai ga hawaye na, u mean so much to me dat i can't just forget what we had, u ar d only gurl i ever love and will forever love Nasreen, dan Allah Nasreen ki auren ko zuciyata ta huta da azabtuwar da nake" da hanzari ta dago ta kalli inda Mum take, tsoro duk ya cika fuskar ta, wani welcoming smile ta samu Mum na mata, sannan ne ta fuskanci wannan karon Mum ba zata ja da wannan al'amarin ba, sunkuyar da kanta tai a hankali hawayen farin ciki na bin kuncin ta, da bayan hannu tasa ta goge, kan ta goge daya Naseer ya riga hannun ta, sai dora wa tai a kan na shin, murmushi sukai a tare ta rufe idon ta tana giggling, Mum ce tai gyaran murya tace " yanzu dai na kula wannan love birds din sun manta da ni gaba daya ni kuma yaushe za a dakko mun nawa mijin kenan?" Tana fada tana karya wuya kamar mai shirin musu shagwaba, dariya suka sa dika.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yamma na yi sosai Nasreen tana kusa da Naseer suna hira , daga kai tai ta kalle shi tace" Abban Naufal ni fa ina ganin ta kamata yau ka maida ni gidan su Barira na kwana a can sabida bai kamata na ci gaba da zama anan ba, in yaso ka dinga zuwa can zance" ta qarasa zancen tana dariya, qura mata ido yai yace " Tab lallai kina son nima na kwashe kayana na koma can da zama kenan, ai ba zai taba yuwa ki tafi ki bar ni ba yammata" yana wani kashe mata ido, matsowa yai sosai kusa da ita har suna jin numfashin juna idon su cikin na juna hannun su na maqale da na juna, wani irin yana yi ne ke ziyar tar dikkan nin su, da sauri Nasreen tai breaking feelings din da zare hannayen ta, miqe tace bari na shiga nai wa Mum bayani nasan dama kai bazaka yarda va, saurin riqe hannun ta yai ya jawo ta jikin shi, da sauri ta kwace kanta ta dan hade fuska" Naseer dole ne mui fighting feelings din mu mui facing reality in ba so kk Naufal ya sake qani ba nan kusa, which we all don't want dat to happen again, wannan dalilin ne yasa nake son mu nesanta zaman mu kusa da juna zai leading din mu mu koma wa aikin baya, kaga kenan memakon mu hattawa kan mu juna muna qara nesanta kan mu da juna ne, in dan tani ne Naseer i want to be with u right now, i want to stay in ur arms to feel u so close, amma dole mui hakuri mu jira lokaci, lokaci ba abinda bai bari ba, in lokaci yayi komai da kk so har da wanda ba kai tsammani bama i will give it all to u, i am ur Naseer and u ar mine, i am totally and utterly head over heels in love with u" tana kaiwa nan Naseer ya gama daskarewa a tsaye gaba daya ba laka a jikin shi kan yai wani yunquri har ta vacewa ganin shi, murmushi yai mai cike da sauti, qara ya dan saki yai tsalle yai juyi, sannan ya bi bayan ta. A palo ya tadda su suna hira ita da Mum ta gama sanar da ita qudirin ta, Mum ta amince akab zata koma din.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> QAUYEN LANGYM</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Jar uban can, lallai yau kai dan Lagos zaka ci uban ka bayerabe, Uban wa yace ka zo na aje koko ka shanye ? Iye? Ko ba da kai nake ba ne?" Wani wawan mari ta sauke mai kamar ta mari sa'ar ta, a gigice ya tashi zai fito da gudu ta sa qafa ta kwarfo shi ya kufo ta gaba, nan da nan kuwa bakin shi ya hau jini, wani irin kuka yake a shide tin da yake Mummyn shi ba ta taba dukan shi ba, tsawa ta daka mai ganin fitsarin dake zubowa ta qasan shi" Dan uwar ka gantalalliya anan ake fitsari? Kai in fa ina maka magana kana amsa min " tana yi tana jijjiga shi da qarfi, " ke Hinde ! Baki da hankali ashe wai da wa nake jin kina wannan surutan da doke2n ne ina bayi?" Da wa zan in ba wannan dan Yarbawan ba🙄😚" " iko sai Allah Naufal kai, zo nan" kasa tashi yai, Baban hinde ne ya qarasa ya daga shi baki fashe ga fitsari a wando fuskar nan tai dagaje2 da koko, kama hannun shi yai ya je ya cire mai kaya, ya mai wanka, ya dawo da shi daki yana ta bashi hakuri ya sa mai kaya suka fita, wajen mai shago yaje ya tambaya har yau ba waya, ba wani saqo daga wajen Naufal? Ya tabbatar mai da va komai shiru, nera gomar aljihun shi ya dakko ya miqa mai a bashi biscuit ya karba ya ba Naufal suka koma gida, " ai da ina nan dana barar da su dika har kakan nashi , sallamammu ta aje dan ta tafi ba ko aike, tin ina lissafin kwanan wata har na manta" sannu tijararriya, ni kk cewa zaki hada mu ki barar ko? To bari kiji na fada maki ki kiyaye ni dan gab nake da na sake ki na kore ku ke da wannan yar ta ki na qara wani auren, dan nasan sana sake ki Allah zai duben ya horen nai wani auren, na dauki iya abinda zan iya na qasqanci a wajen ki, iyaka dai nasan ni na nuna kwadayin abin hannun ki har wulaqanci ya shiga tsakanin mu to daga yau na yanke, azabar da kukewa yaronnan ta isa haka, zan tsaya mai har uwar shi ta dawo, ke kuma in ga qafar ki ta qara fita nan da can kiga yanda zan dake kin bar gidannan kenan kuma uwar ki ma kin ja mata dan sakin ta zan" dafe qirji Innar hinde tai tinda ya fara magana" to malam...........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> </p><p><br /></p><p> </p><p> By HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sisters masu cewa suna na akwai wahalar fada😂 naga masu tambayar na da yawa, </p><p>Hamida+ Ibrahim= Hamibrah, Haermeebraerh kuma dan iyayi nai wa rubutun hope yanzu zai dai na baku wuya😂😂 </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 23: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Malam kayi hakuri duk abinda ka lissafa ba zasu faru ba" ( ni haermeebraerh nace hahaiiiiii casssss bari ba shegiya bace da uban ta ashe😂) saiga Innar Hinde har wani sinne kai ake qasa, Hinde ana son ai rashin mutunci baki ya mutu, haka ya wuce ya bar su. Da dare Innar Hinde ta shigo dakin jiki daqa2 da datti, bayan akan idon ta Baban hinde yai wanka yaiwa Naufal wanka, ya sa yai bacci ya kwantar da shi, ya dawo dakin su ya kwanta, amma ita yarkace2 da ita zata tafi ta kwanta mai haka, ai daya buga mata wata uwar tsawa a gigice ta juya taga waye yake maganar, dan tinanin ta aljanu ne suka shigo masu ta bango, waige2 take tayi" Ba dake nake magana b😡 Nace ki wuce kije ki wanka, kin daina kwana min kamar wata mahaukaciyar da ta shekara tana ciwon hauka" dubawa tai da gaske Baban Hinde ne, jikin ta yai mugun sanyi ta dau hanyar fita ya dakatar da ita da cewa" ki tabbatar kin wanke bakin ki tas kin aske gashin jikin ki mai doyinnan kk dawon nan haka saidai ki kwana a tsakar gida yau" amsawa tai da " to me gida" tana fita Baban Hinde yaji wata dariya ta zo mai" ashe haka iko yake a gida na ke wasa da dama ta? Dan Allah ji yanda take wani noqewa kamar wata mutuniyar kirki, Ya Allah kasa addua ta ce ta daidaituwar iyalina da shiriyar su ne ta fara karbuwa Allah ka sani ina son iyalina ina son mata ta, amma baqaqen halaye da qazantar ta na nesanta mu, Allah ka daidai ta mun zuri'ata" yana sauke hannu ne yaji alamun fitowar ta ta shiga madafi, toka ta diba da gawayi da gishiri ta hau wanke bakinnan tayi ta gama tas ta shigo" dauki wankakken zanin ki ku goge kan da kk wanke kafin ya fara mana warin da ya saba, ga dan guntun tirare na can a yar kwalbar durin nan ki shafa"magana yake fuska a daure amma dariya ce fal cikin shi da tausayin ta, dan ko bacci ne cike a idon ta( to an kau da wari da tsami, qofofin gashi sun samu sararin iska, baki ya huta da gumus🙊) tana gama shiryawa ta haye gado, matsowa Baban Hinde yai ya fara sarrafa ta, ba saiga Innar Hinde ta gigice ba, fadi take" Malam na cuci kaina, 😭 ashe haka yan tsotse2n da nake ma masifa suke da dad'i nake bala'i? Malam meyasa da bakai min ba da bala'i?" Dariya ce ta kwace ma Baban Hinde wannan karon yace" To yanzu laifi na kk gani? Da ai ban da wannan ikon zaki fara fada kamar ki hadiye ni, ki na kira min lokaci garen" ni dai daga yau ba zan qara ba ka yafe" to ya wuce in dai zakina gyara jikin ki kuwa yan tsote2n nan kullum sabon salo zan na maki, dan haka share hawayen ki daina kuka, sai abu na gaba, ina so na roqi arziqi ki kula da yaronnan, ki daina mai halayen da kk masa, kiji tsoron Allah akan 'ya'yan ki amanace Allah ya bamu, ba wayon mu bane ya bamu su, ganin damar Allah ne, dan haka ku dage da musu addua, nayi sakaci tin fari da na aure ki, na kula wajen tarbiyya kina da rauni van bada mahimmancin gyara maki ba, dan haqqina ne, sai da abun ya kai yafi qarfi na banda yanda zan dake, har gashi abun ya taba yaran mu" Malam ka yafen😭😭 da yardar Allah komai ya wuce bazaka qara jin wani abu mara dadi daga wajena ba" a haka malam ya qara lalubo ta ya ci gaba da aika mata da saqonnin da yasa ta fara mai koke2 zata tara mai maqota ya rufe bakin ta da nashi🙊</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Washe gari da asuva suka tashi sukai wanka sukai alwala suka fara sallah, sun idar Baban Hinde ya ce ta zauna ya fara koya mata karatun muhammadiyya dan tana buqatar shi, shiko ilimi baya tsufa, ba kuma a jin kunyar shi, bayan sun gama ne ta tashi tai hanyar dakin Hinde tai daidai a shimfidar ta, tana asararren baccin ta, duka ta dasa mata ta ce " tashi kije ki alwala ki zo ki sallah shashanci ya qare a gidannan, maza kafin ranki ya baci" tana zumbura baki tana qunquni tai waje, ita kuma tai madafi, haka rayuwar su ta ci gaba da tafiya Naufal na samub kulawa ba laifi, amma a wajen Hinde sai ta ga idon iyayen ta take jan shi a jiki, har ya gane ta, dan in basa nan shima baya zuwa wajen ta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta gama shiryawa tsaf ta fito, a mota ta same shi, lokacin magrib ta kawo kai sosai, da alwalar su suka fita( Note: yana da matuqar mahimmanci mu koyi yin alwala in zamu fita musamman alokacin magariba mu koyawa yaran mu hakan ko gidan qawaye suka je su kai yamma su fito da alwala, sabida a lokacin aljanu ke yawon su) suna hanya kowa da abinda ke saqawa a ranshi, daga baya Nasreen ta aje tinanin komai ta gyara zama ta rufe ido tana ta tasbihi har suka isa, sakkowa tai ya fito ya tsaya" sai yaushe kuma My priceless jewel?" Duk sanda kk son zuwa My Handsome" hhhhhh lallai baki da dama ni dinne Handsome" hmmmm ni a wajena da duk abinda yafi hakan ma zan kira ka da shi, amma gudun kar a ce na zaqe ne yasa na tsaya a hakan" jiyai kanshi ya wani fasu, a ranshi kuwa fada yake " in ban gaggauta auren yarinyar nan ba ina gab da susucewa" kiran magrib ne ya katse su yace " ni na tafi sai gobe, zan dan tsaya nai sallah a bakin qofar gidan naga masjid a wajen" k no p love, na gode sosai Allah ya bani kai" dariya yai sosai sannan ya amsa ya tafi cike da jin dadi da nishadi.</p><p>Ta shiga ciki ta tadda Barira na alwala a pampo, daidai ta idar kenan, da gudu ta taho ta rungume ta, tna murna," Inna ! Inna ! Inna ! Da sauri ta fito taga wannan kiran na meye.........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Rouqy Zuma ( yar mitsila😂😜) this page is for u, Allah ya sa ki kamo ni😂</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 24:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Allah mai iko Nasreen ke nake gani ko ido na ne?" Inna ni ce " tana dariyar cin dadin ganin su, daki suka shiga sukai sallah, sannan suka shiga hirar yaushe gamo, ranar kusan kwana zaune sukai, Nasreen ta sha nasiha sosai wajen Innar Barira da Barirar kanta, anan take sanin an saka ranar auren bikin Barira wanda ya qarato nan da sati biyu. A tare Inna ke masu gyaran amare, dan a cewar ta, waya sani ko itama ayi lokaci daya? Kwana biyu tsakani Nasreen bata ji daga Naseer ba, tin tana jurewa har ta zo tana zancen da Barira, hakuri ta bata ta kwantar mata da hankali.</p><p>A bangaren Naseer kuwa so yake ya gyara kanshi dan rabon da yai aski mai kyau ya manta, zuwa yai ya gyara kan shi sosai, gyaran da ko da Mum ta gan shi sai da ta bude baki tana kallon shi, rungume ta yai ya dora kan shi a kafadar ta " Mum ya kk ga yaron ki? Kina ganin yanzu ko yar shugaban qasa nace ina so zata so ni? Ya kk ganin Nasreen dina zatai in ta ganni?" Naseer stop feeling nervous , she is in love with u anyway she will never reject u, she is urs, her heart, soul, and body belongs to u son" wani dadi ne ya kama shi ya mata kiss a kumatun ta na hagu ya fita da sauri2 gudu2" Mum sai na dawo na tafi wajen Priceless jewel dina" mota ya fada, ya fita da gudu yana murmushi mai sauti, hango irin farin cikin da zata shiga in ta ganshi ne kawai ke qara ma fuskar shi annuri, a wani butique ya tsaya ya sai mata kaya harda na subhalallah, takalma da jakkuna ma bai barsu ba saida ya diba,kashe kudi yai kamar ba a so, a wani shagunan cusmetics ya tsaya ya sai dangin kayan kwalliya da turaruka masu tsada da qamshi, bayan ya kammala da nan wani fancy super market ya shiga, ya lodar mata fevorite chocolates din ta, sannan ya dau hanyar gidan nasu, a lokacin tsakanin magrib da isha'i ne, yana isa ana kiran sallah a masallacin qofar gidan shiga yai akai sallah da shi domin da alwalar shi yake yawo, ana idarwa ya fito yana neman izinin shiga gidan a wajen mai gadin su. A ban garen Nasreen kuwa ba walwala a tattare da ita, daka ganta kasan tana cikin damuwa, hada ido sukai da Barira tai mata murmushin yaqe, Barira tashi tai ta zauna kusa da ita tace " haba sister, ki kwantar da hankalin ki dan Allah Naseer naki ne ke daya, ina kyautata zaton akwai kwakkwaran abun da ya riqe shi bai zo ba, dan haka na san duk inda yake kina ran shi, kuma yanzu haka kar ki mamakin yazo" tana fada tana dukan kafadar ta da ta ta, murmushi ne ya kwace wa Nasreen tace" lallai da ban san kyautar da zan maki ba in ya zo yau, ban san irin murnar da zan ba ni Nasreen" wasu hawayen missing din Naseer ne ke fitowa daga idon ta, hannu Barira tasa ta goge mata tace" to malama da kk kuka yanzu in aka ce ki fito yazo gashi kin bata yar kwalliyar taki ta yamma sai kije mai fuska a bace da hawaye?" Saurin gogewa tai ta tashi kamar wadda aka sanar wa cewar ya zo ta hau gyara fuska, wata doguwar riga ce a jikin ta kalar golden da ratsin silver, mai dogon hannu, ta kama ta ta sama, ta bude daga wajen qugun ta, kan ta ba dan kwali sai ponytaile da tai da dogon gashin ta baqi, ya sha gyara sai qamshi yake, Nasreen kenan Allah ya yi ta da son gyara, ko da ba su da shi tana da tsafta balle kuma ga samu yanzu? Ai gyara ba kama hannun qazamar mace😜</p><p>Komawa tai ta kwanta bayan ta gama juya jikin ta a madubin dakin nasu, ta limshe ido, tinani take duk wannan kyaun da tai da dan anjima zata cire kayan, ta maida na bacci, dan guntsun tsaki ta saki ta dad'a gyara kwanciya," Assalamu alaikum" muryar Baban Barira kenan, " Nasreen ! Nasreen ! Kafin yai na ukun ta fito sanye da dankwalin rigar a kanta, durgusawa tai," Sannu da dawowa Baba" kanta a qasa take maganar, " Yauwa diyar albarka, Naseer din ku dai yau gashi can a waje, dan na kula wannan rashin fara'ar da bama samu kwana biyu har da rashin shi" kunya ce mai tsanani da dadi suka kama ta ta tashi da gudu tai dakin su, gado ta fada tana tsalle kamar wata yarinya, can ta sakko ta kama hannun Barira tana juya ta suna rawa, Tambayar ta take me ya faru? Amma ba baki sai dariya kawai take, kai bakin ta tai kumatun ta na dama ta mata kiss , sannan ta sake ta ta je gaban madubi ta dau tirarukan su ta hau fesawa, toilet ta koma ta fesa mouth freshner, fitowa tai ta qara powder da lipstick sannan ta zo gaba Barira," ya kk ganni yar uwa komai yaji? Zan iya zuwa wajen mai ni din yanzu? Sister Naseer is here" ta fada tare da rungume Barira itama murn ta fara, sannan tace maza ki fita kina bata mai lokaci, golden takalmin ta ta dakko mai tsini, saka fita tai tana taku daya daya, a palo ta tadda shi yana tsaye hannun shi ya goya su a baya, yana fuskantar windo da hanzari ta je , zata rungume shi ta baya, tinanin haramcin hakan ya tsaida ta, taja ta tsugunna a wajen, qamshin d yaji ne ya sa shi juyowa da hanzari, ganin ta duqe ne yasa shi durqusawa shima, hawaye ya gani suna bin fuskar ta kamar an bude pampo," My Priceless jewel, ki daina kuka, daga idon ki ki kalli masoyin ki, wanda ya susuce a kwanakin da bai gan ki ba, ina fatan zaki yafe min rashin zuwa na da kuma jina da baki ba" daga kai tai suka qurama juna ido a hankali take kallon shi ta tsaida idon ta akan gemun shi da yasha gyara da sajen shi, murmushi sukai wa juna sannan tace" na yafe maka, amma da ka sake ka qara kwana baka zo ba yau hukuncin da zan maka ba kadan bane" dariya sukai a tare ya nuna mata kujera akan su zauna zama sukai suna kallon juna, kowa da abinda ke saqawa a ranshi, Naseer ne yai breaking shirun su " a gaskiya ni dai ina zuwa gida zan sanar da Mum gobe a yi maganar zuwa can garin ku a tambayar man auren ki, kuma bana son ya wuce nan da sati biyu, dan Allahu shahid ba zan iya jure mu wuce hakan ba" murmushi tai idon ta cike da hawayen jin dadi tace" Kai Handsome yanzu ba zaka dan iya bari mui kamar wata biyu ba haka" miqewa yai tsaye a razane yana mata kallon anya kanki daya kuwa? Dariya ta hadiye, tace" mene ne kuma irin wannan kallo kamar yau ka fara gani na" tana yi tana turo bakin ta gaba da shagwaba, idon ta tana kifta shi in a sexy way, qara rikicewa yai yace" yanzu Nasreen in ba mugunta ba ji fa yanda kk sani a gaba kk man sannan ki ce wai a bari bikin mu ya kai wasu watanni, haba babe, ai saiki sa nai zaton baki so na yanzu kuma" kamo hannun shi tai for d first time tun zuwan shi ta zaunar da shi a mazaunin shi sannan ta saki hannun, " ka kwantar da hankalin ka, ni Nasreen ta Naseer ce har abadan, idan gobe kk son a mana aure zan fika murna, fatana Allah ya sanya mana albarka a ciki" jiyai kamar ya rungume ta dan farin ciki, amma ya basar, 😎 sallama akai sannan suka ji shiru ba a shigo ba Nasreen ce ta amsa sannan Barira ta shigo, dauke da faranti a hannun ta, an jera jug din da aka hada kunun aya da mai zobo sai kuma jofuna biy, gaida Naseer tai tana ma Nasreen sherin damuwar da ta shiga na rashin shi, dukan wasa ta kai mata da pillo, ita kuma ta fita tana dariya. Sun gama hira ne ta tashi raka shi, a bakin mota ya miqa hannu ya dakko wani kwali ya miqa mata" Sweery ga wannan ki riqe dan na kula ba waya a hannun ki yanzu dana zo qofar gidan nan ne na tina sai na koma na siyo maki, komai na ciki da digits dina" godiya ta hau yi kamar ba zata daina ba, hannun shi ya sa a kan leben ta " shshhhhhhh, sai kace wadda na ba wa shagon saida wayar dika? Naseer kenan yaba kyauta godiya, godiya tana da da di ga wanda akai wa koda yafi qaruna dukiya, in aka gode mai bayan yai abin kirki yana sa ya ji dadi sosai, dadi ne ya qara lullube shi" nimq na gode to dear da soyayyar ki a gare ni" Sallama sukai, ta tafi, ya bi bayan ta da kallo, murmushi yai" kamar ba yarinyar da tazo bata fi sha bakwai ba ji yanzu yanda ta cika ta zama budurwa sosai, Allah ka mallaka min Nasreen" kayan ya diba ya kira wasu yara a bakin gidan sukai ta shiga da su, ya basu kudi, ya tafi cikin farin ciki sosai.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Washe gari Mum ta samu limamin da yai mai wakilcin auren shi na farko magana, akan zuwan su qauyen Langyam da ke a garin kano, sanar da ita yai ba damuwa, amma su mai hakuri zuwa gobe Naseer ne ya matsa kusa da shi" Dan girman Allah malam mu tafi yau, gani nake kamar za a kwacen ita" idon shi yai jawur kamar zai kuka, murmushi malam liman yai yace to Naseer amma bari naje na gabatar da wani uzuri in na gama kafin shabiyi sai mu wuce in ban gama ba mu bari zuwa gobe, " Malam Liman kana da passport dan Allah muje kano a yau komai dare, in yaso gobe mu isa qauyen nasu"dariya Mum da Malam sukai Lallai Naseer ka fada tarkon so mai tsanani Allah ya tabbatar muku da alkairi" AMEEN" tashi yai yaje ya fara hada kayan shi tsaf, ya sanar da Nasreen ta waya akan ta shirya zai zo yanzu ya dakko ta zasu tafi kano, tambayar ta yai passport din ta, ta shaida mashi ya na wajen ta amma sai ta duba, yace ta hanzarta dai yau yake so su tafi, sallama sukai ta sanar da Inmar Barira da Baban ta addua da fatan alkairi suka mata, Barira ta je suka fara hada kayan su, kudin da Naseer ya hada mata a kayn da yakwo mata jiya ne tace suje super market, tai siyayyar tsaraba, musamman ga dear Naufal......</p><p><br /></p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> </p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>I am once again sorry, readers ban da ra'ayin bude group din kaina tin fil azal gaskiya, har yanzu ma haka, amma zan qoqarin inna kammala dika na dinga turawa group daya bayan daya, in yaso masu nema ta PC sai su na bi, wayata na riqewa in ina tura abu mai yawa, amin afuwa. THANK U FOR D LOVE ANA TARE❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 25: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zuwa sukai suka sai mai kayayyaki, musamman na sakawa, da takalma, sai abun wasa na yara dai haka, sannan tai ma Innar su da Baban Hinde da Hinden tsarabar kayan sawa da turare, sai yan kayan kwalama, da suka dawo duk ta samu babban akwati ta zuba, bata jima da dawowa ba 11:35am sukaji sallamar Baban Barira yana ta fito ga Naseer ya zo, sallama ta musu tare da godiya mai tarin yawa sannan suka tafi, gaida Malam Liman tai sannan ta Kalli Naseer da ke zaune a gefen ta da wani salon dauke mai hankali, " Ina kwana my Handsome" tana wani kifta ido 🙄 amsawa yake son yi amma saida ya hadiye wani yawu sannan ya amsa da" lfy qalaou, and how is my baby doing?" I am gud Alhamdu lilLAAH" murmushi sukai a tare . Sun isa airport lfy jirgin su ya daga zuwa lagos tafiya ce mai cike da nishadi sukai da zaquwa ta qare su isa ayi ta ta qare, Naseer ta matsu su isa yaji an bashi Nasreen din shi, at d thought of that,gaba daya sai yaji kamar ya bude ido ya gan shi a qauyen Langyam" calm down will u? Ko dake u have every right to be nervous dan wataqila Baban Hinde ya bama abokin shi ni, tinda kasan second hand ce ni" ta fada tana teasing din shi, wani irin bata rai taga yayi a hankali ta saki dariya mara sauti" ni dai karka zane ni da wannan manyan idanun naka, wasa nake" better" abinda ya furta kenan ya ja ya lumshe ido, sanar da su akai sun kusa sauka a garin kano, wata murna ce ta kama su dika. Sun isa lfy inda suka sauka a hotel suka ci abinci suka shiya sannan suka kama hanyar qauyen langyam goshin Magrib kenan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> QAUYEN LANGYAM</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Innar Hinde na hango ta fito wankan yamma, ta samu bakin nan tana ta dirza kamar an aiko ta, tin kwanaki da malam ya mata dandanen tsotse2 ta dage da tsafta, gaba daya ta sauya, ita da Hinden haske da kyaun su ya fito, dan dama kyawawa ne daidai su, qazanta ce ta mai da su wani rodi2, Nasreen ce kawai baqa a gidan," hhhhhhhh Inna wallahi sai kinje kin jima kan ki ciwo, ji yanda kk dake kina dirzar baki kamar kina wanke bayan tukun😂" in ji Hinde tana fada tana faman dariya kamar zararriya" hmmmm yarinya me kk sani in ban da shirme ni na san dalilin wankin baki na ai, kiyi dariyar ki ki gama" Baban Hinde ne ya shigo tare da sallama, Naufal ne ya tashi da gudu ya rungume shi yana dariyar jin dadi, Baban Hinde daga shi yai bayan ya aje ledojin Hannun shi," Ke Hinde zo nan ki dau wannan ki gyara mana zuwa anjima kowa ya gama shiryawa mu hadu a dan motsa baki" amsawa tai ta tashi fakam2, dan duk da ta fara tsafta har yanzu wautar na nan, wanka ya shiga ya fito, wanke bakin shi ya qarasa sannan yai alwalar Isha'i, ya shiga daki ya tadda Innar hinde an sha gaye ana ta zuba qamshi da turaren su dan duri da yake siyo masu a masallacin juma'a" Kaiiiii mata ta kinga yanda kikai kyau kuwa, sai kk koma kamar wata budurwa, kin tinan farkon gani na da ke, ranar da kk sacen zuciya, naji duniya ba wata sai ke" wata iriyar dariya ta sake ta jin dadi, kanta kamar ya cika dakin dan girma " Malam irin wannan washi haka? Kar kasa nai kaifi da yawa fa, in kyau ne ai ba kamar ka kaf garin nan, tin daga yarin ta har iyanzu" to shi kenan kin rama dai kawai, amma ni dai ai gaskiya na fada" nima gaskiyar na fada ai" yana yi yana shiryawa, daidai ya gama kuma ana kiran sallar isha'i, sallama ya mata akan za shi sallah, adduar dawowa lfy ta mai itama ta fara ta ta, kama hannun Naufal yai suka fita Shima ya samu arziqin wanka, Hinde ce ta mishi, tana yi tana mitar ita fa ta gaji da bauta, ko yaushe uwar dan Lagos zata dawo oho, an kawo musu jikan yarbawa an aje an koma, ko yanzu jikan wane yare zasu samu kuma oho🤷🏻♀. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mota ya gani a qofar gidan bayan sun iso daga Masjid, tsayawa ya danyi yana nazarin mutanen da yake hangowa suna fitowa, Naufal ne ya cirw hannun shi ya diba da gudu, " Mummy" wata runguma ta mai kamar za a kwace shi, tana hawayen farincikim ganin danta fes da shi, gaba daya tsoro da fargabar ta sun kau, Baban Hinde ne ya iso bakin shi a washe, sai fararen haqoran shi kk hangowa, miqa masu hannu yai suka gaisa, Naseer ya wani noqe ya durqusa ya na kwasar gaisuwa, dariya Nasreen tai ta shiga ciki, sallama tai Hinde ta fito da gudu daga daki, dai dai Innar su ma ta fito, a tare suka furta"Nasreen"</p><p>"Na'am" cike da murna dan da dikkan alamu Innar ta ta sauya dabi'a saidai daga Hinde ne kawai ta samu kallon ban damu da keba🙄 Sallama Vaban Hinde yai sannan ya sanar da su za a shigo, shiga sukai Ciki Innar Hinde ta dakko tabarma ta shimfida tana " lale maraba da baqin lagos" Naseer kai a qasa, haka suka zauna aka fara gaishe gaishe, da gabar ta da kai" wannan da dukkan alamu shine surukin nawa Baban Naufal ko?" Baban hinde ya fada yana murmushi, " Hakane malam" inji Liman, shi kuma qara noqewa yai,Naufal na jin haka ya taso da a hankali, ya tsaya gaban shi , ya kalle shi, sannan ya ce "DADDY?" Naseer idon shi ne ya cika da kwalla ya daga kai, ya kama hannun shi ya jawo shi jikin shi, a take Naufal ya rungume shi kamar zai qara tafiya ne ya bar su, kowa a wajen jikin shi ne yai sanyi, Hinde kanta sai da taji tausayin su, Innar Hinde ce ta iso da faranti a hannu yanke da kayan marmarin da Baban Hinde ya shigo da su dazu, ta aje Nasreen kuma ta taho da ruwa a kwanon sha, Nan take Nasreen ta fita taje ta aiki yaro ya siyo mata balangu da gurasa na dubu uku aka kawo ta debar wa su Malam da Naseer , sannan ta debar ma Inna sa Baba , sai nata da Hinde da Naufal kuma, fafir Naufal ya qi yarda ya bar baban shi ya ma ko sha ruwa ne ta dadin rai, ya qanqame shi sosai ta wuya, tashi Nasreen tai taje ta gyara masu Malam Liman dakin soro tai shimfida ta sanar da su, bayan an gama gaisawa ne da komai, Baban Hinde ya masu jagora akan sai da safe zai kira yayan shi da qanain shi ai maganar saka ranar auren nasu, sallama sukai ma Inna suka tafu makwancin su.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sassafe Nasreen ta tashi ta hada abin kari mai dadi, dubawa tai ba wasu kayan abincin kirki a qauyen da zai masu dadi dabara ce ta fadi mata kawai ta samu naman jiya da bata ci ba ta dan tafasa da albasa da maggi sannan ta yanka qana2 , sai ta ba Hinde kudi ta siyo flour d kwai, hade su tai tai qulli da su ta saka maggi da dan citta da kaninfarin da ta daka sai tafarnuwa, ta saka da man gyada ta fara soyawa tana wainar flour, ba sai ga qamshi mai dadi na tashi a gidan ba, Hinde ce ta matso kusa" yanzu dan Allah waya koya maki wannan irin girki mai sa mutum ya qoshi tin kan ya sa a baki? Ji yanda qamshi ke tashi ta ko ina?" Dariya tai sosai kan ta amsa ta" Hinde shi girki ba wai dole sai an koyawa mace ba, yana da kyau ace kowacce mata ta san yanda zata sarrafa kayan abinci kala2, tanda in iya flour dinnan mijin ta ya aje mata a gida ba zata damu ba, zasui ta cin girki kala2 na flour din je kawai ba tare da sun gundira da flour din ba, ina fatan kin gane" daga kai tai kamar wawiya yawunta sai tsinkewa yake🤤 bayan ta gama ne ta daga ruwan shayin da yasha kayan qamshi ta jera komai ta je daki ta shirya, sannan ta fito ta miqawa su Naseer, ta same shi yana kan sallaya har lokacin, gaida shi tai, ta gaida malam ta futo, bayan ta sanar da su ruwan wanka will be ready in sun gama</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Baban Hinde ne ya shigo da wasu dattijai su biyu, Malam Bala da Malam sale kenan, wan shi da kuma qanin shi, sun tattauna sun fahimci juna, inda Malam Liman ya sanar da su suna son a saka ranar aure nan da kwana takwas, sabida yai daidai dana Barira, inda zasu daura aure a nan, dan iyayen Barira ma nan zasu zo ai daurin aure, sai a tafi da su can Lagos din, sun miqa kudin na gani ina so da sadaki da komai da ake buqata, Naseer ya basu hakuri akan lefe sai sun koma, inda Baban Hinde ya nuna mai ai ba ibada bane, dan haka karya damu. Abincin da Nasreen ta dafa masu mai dadi suka ci, sannan sukai sallama suka tafi, su kuma su Naseer sunyi zasu koma Kano a ranar su tafi Lagos daga nan sai ana gobe daurin aure su dawo. </p><p><br /></p><p>" Priceless dan Allah kar ki na zama ba caji, dan ba zan jure zama ban jin muryar ki akai akai pls" fari tai da ido tace" nima ba zan iya jure rashin muryar ka ba koda na yini daya ne, saidai zaka na min uzuri kasan nan qauye ne, ba koda yaushe ake samun wuta ba, amma zan iya bakin qoqari na, ka kular min da kan ka kaji" ta qarasa cike da shagwaba, murmushi yai yace" zaki bayani ne dalla dalla, ki ta ja min rai randa na kama ki a hannu na sai kin yi larabci( 😂 irin Minaleen Hamma Haidaer😂) dariya sukai a tare sannan ya miqa mata wata envelop ya shiga mota, godiya tai ta yi tana daga masu hannu, gaba daya jin shi yake kamar a akurkin kaji, motar duk qarafa , daga tasha aka kira masu ita qofar gidan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan tafiyar su ne ta dakko akwatin ta, ta fiddo ma kowa tsarabar shi, anan ne Hinde taga ruwan abin arziqi, sai ga kuka," yar uwata ki yafe ni, tabbas kin min nisa, wannan shine fassarar hassada ga mai rabo taki, na maki hassadar da duk zan miki amma gaba kawai kk yi, ban tsane ki dan komai ba sai dan fina komai da kk yi a koda yaushe, gashi yanzu auren ki ma za ai ni ina zaune ko mashinshinin kirki bani da shi" kuka take sosai tana sharce majina da gefen riga, " Haba yar uwata ki daina kukan haka ya isa, bam taba riqar ki da komai ba, fatana Allah ya mana gafarar laifikan mu duka, ya qara hada kan mu" magan ganun da suke dik a kunnen Inna da Baba, Baba ne ya kai hannu ya sharewa Innar Hinde hawayen ta ya jata sukai daki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Rama bata qarya sai dai uwar diya........</p><p>.</p><p>👵🏻 WATA UWAR. 👵🏻</p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 26:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau ne washe garin ranar daurin auren su Naseer da Nasreen Barira da Umar, sun iso qauyen langyam tin da yamma, wannan xuwan a mota suka yi shi, gaba daya jikin Barira yai ciwo, sakamakon shi Umar ba wani mai qarfi bane sosai, da zasu iya tahowa a jirgi, hakanne yasa suka taho da jama'ar shi gaba daya ta mota, Naseer ma da tashi jama'ar abokan da Malam Liman wakilin shi, gidan su Nasreen da Naseer ya sa akaiwa gyara sosai tare da qarin dakuna uku, dan gidan ba dai fili ba, a tsohon gidan su Barira amare suka koma, inda suka zo da mai qunshi da gyaran jiki daga can ta fara masu da gyarab jiki zuwa qunshi," wallahi haishina da garinnan ko saloon babu yanzu dole sai mun koma zani saloon, ke kin samu me makon ki gyara zaki wani ce tinda ban ba bazaki ba kema🙄" eh ban yi sai mun koma😚" harara wasa Nasreen ta mata tace" amma ai baki qi karbar kayan gyaran da Inna tai ta baki ba, da sai ki qi sai na koma" dukan wasa Barira ta kai mata tace" ai wannan gyaran ciki ne, wannan kuwa na fili ne, ke wa yasan me kikai ta banka"dariya qawayen su suka saka, ko nace qawayej Barira dan ita Nasreen ko a da bata da qawaye anan balle a Lagos , qawar ta daya Barira(Bally sunan iyayin da takan fada mata kenan).</p><p><br /></p><p>Naseer na can daya ga mata zai fara baza ido ko zai hango Nasreen dan ko dakin da aka sauke su ya qi shiga, wai tinda ana ce bata ciki, karta wuce bai gan ta ba, Umar dariya ya dinga mishi yana tsokanar shi, amma hakan bai sa ya hakura ba" kai ai dake kana tare da taka amaryar kace na shiga ciki mana" a bu wasa2 har yamma, ga wayar ta bata shiga, yana tsaye ne yaga Hinde zata wuce, magana ya mata, ta juyo tana wani fari ita ga budurwar qauye" dan Allah ina Nasreen ne, in kin san inda take ki wa Allah ki kaini na ganta, bqzan iya jurewa har dare bam gan ta ba ki taimaka" wani fari ta qara yi tace" ikon Allah, ai ni ban gane ka ba ma, gaba daya ka qara kyau, dama maza suna yin gyaran jiki in aure yazo? hmmmm taho na je na kai ka inda take" tafiya suke tana ta zuba shi ko hankalin shi yayi gaba , suna zuwa daidai gidan ta nuna mai zata juya" ki taimaka ki kirawon ita mana ai kinyi mai wuyar ko" tabdi jam na shiga su din ga min kallon yar qauye? Duk fa yan binni ne a ciki? Ai na ma mai wuyar dana nuna maka gidan"hannu yasa a aljihu ya dakko kudi ya miqa mata," dan Allah ki taimakan" hahaiiiiiii cassssss dannan ina ma ace lokacin Hinde na mai idon cin nera ka bata kudinnan ai da har hannun ka sai na kusa tsinkewa wajen karba, amma ka makara Adda Nasreen ta mun wa'azi akan karbar kudi kuma na dauka, dan haka ka barshi zani dan zumunci, da son yar uwata da kake" sa kai tai kamar balama, balam balam ta shige, xaune ta gansu sun wanke qunshi kenan ta zauna, " ina wunin ku, Adda Nasreen ga Abban Naufal a waje yana jiran ki"Wa ni tsallen murna tai ta dakko hijab ta saka, tanaa sauri zata fita taji an riqe hijab din ta baya, tsayawa tai ta juyo taga wace," yo yanzu in da ni ce nai wannan abun ace yar qauye ban da aji , ke yar birnin ma gashi sai bari kk akan saurayi, ni da nice sai na ja aji kan na fita😚" gaba tai ta bar su suna dariya sosai" Hinde hooo" Nasreen ce ta dan gyara sannan ta fita a hankali tana taku daidai."Hayyakallah ya Hubby" Hayyakillah ya Habibty" murmushi mai cike da kewar juna sukai wa juna, iso ta mai zuwa soron gidan suka bude dakin soron, ta shiga ta dakko tabarma, sannan ta koma ta dakko ruwa da abinci, shigowa tai sannan suka zauna, firfita take mai da maficin hannun ta sakamakon zufar da taga yana yi,"My handsome ka ci abinci, da ganin ka ka dade rabon ka da abinci" lallai kin san mijin ki tin kan a daura auren ma, amma kin san bazan taba iya cin abinci ba in ban gan ki ba" murmushin jin dadi tai sannan ta bude ta fara bashi a baki, karba yai shima yana bata har suka gama, zai magana kenan sai suka ji kiran sallah, shiru sukai suka din ga bin kiran sallah bayan an fada suma su fada, da suka gama sukai adduar da aka sunnan ta yi bayan kiran sallah sanan sukai salatin Annabi, a tare suka daga hannu sama suna roqon Allah yafiyar zunuban su, sannan, sukai adduar samun zaman lfyr su da arziqi mai yawa,( Allah na karbar adduar da aka yi bayan kiran sallah , in mutum yayi kamar yanda su Naseer sukai) tashi sukai sukai alwala, Naseer ne ya jasu sallah dan ba zai iya komawa gidan su Nasreen ba,kuma masallacin na ta can ne, gaba daya hankalin shi na kan neman inda Nasreen din shi take, Sallah ya jasu suka ci gaba da hira, har qarfe 9:45pm sannan yabi yaran da suka kawo masu abinci suka koma. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yaune ranar daurin auren su Nasreen, can na hango su sun sha kwalliyar da aka dinga zuwa kallon su a qauyen saboda wani kyau da sukai, dinkin wani material suka saka red head din Yellow, ba qaramin kyau sukai ba, yanda shape din rigar yabi jikin su abin kallo ne da cece kuce a qauyen, wasu suna sun burge, inda wasu suke gani basu burge ba suna yawo cirara, whatever 🙄 sn dai yi kyau musamman Nasreen coz ta fi Bally shape sosai. An daura auren su akan sadaki dubu hamsin hamsin, Naseer harda hawayen dadi saboda gani yake a yanzu ba wanda ya isa ya raba shi da abar son shi, sai Allah, Nasreen ko kuka take kamar me Naufal ganin tana kuka ne yasa shi rungume ta yana kuka shima, " ni dai ki daina wannan kukan karki sa min yaro yai rashin lfy, wannan ai kukan dadi ne kk yi, shi ko bai san name bane zakisa yaga kamar wani abune ya same ki" cewar Hinde da ta sha kwalliya, aikin wata qawar Bally ce dan a cewar ta in hinde ta waye ba qaramar Babe za ai ba a wajen😂, Nasreen ce ta share hawayen ta ta miqe ta kama hannun shi ta kai shi wajen Innar su tai gaba, Inna ce ta kama shi ta kai shi daki ta debo mai abinci ta aje mai tana lallashin shi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>An gama duk wani bikin da zasu gudanar a nan qauyen sannan suka rankaya sukai Lagos, wannan karon amare da angwaye sai wasu qawye na kusa da abokan ango na kusa ne suka tafi ta jirgi, sauran kuma a mota suka koma, isar su ke da wuya kaya kawai suka canja suka tafi wajen dinner, a wani hamshaqin Hotel suka gabatar da dinnar party din, ya qayatar matuqa anci ansha, sannan angwaye kowa ya kama hannun amaryar shi ana rawa a haka suka fita da ga wajen, kowa yai mota da matar shi sukai hanyar gidajen su , kafin su rabu ne Bally ta je da gudu ta rungume Nasreen suka hau kukan rabuwa, a kunne Bally ke fadawa Nasreen" Sister i am scared , bana son a barmu mu biyu tsoro nake ji sosai" jikin tq sai rawa yake," It will be awsome i promise, dont be scared, nasan umar akwai tausayi he will treat u like a princess, kin san lallaba su ake, haka zai lallaba ki, just promise me in ya neme ki ba zaki qi ba, kin san hakan haramun ne, he is now ur husband" I promise i iwll give him what ever he ask for" dats my gurl, i love u" i love u too sis" da kansu suka rabu, kowa ta koma kusa da mijin ta, bude masu qofa sukai suka shiga inda sauran abokai da qawaye sun firfito sukai ta daga masu hannu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bally da angon ta sun isa gida lfy, inda Nasreen da Naseer sun isa gidan su Lfy, ya riga ta fitowa ya bude mata mota, tana fiddo qafafun ta ya daga ta cak in a bridal style yai ciki da ita ta kwantar da kanta a qirjin shi, daki suka nufa............</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 27:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A kan gado ya aje ta, yana mai tsanan ta kallon ta inda ita ma cikin ranta tana son ta daga kai ta kalli fuskar shi, amma a yau kunya take ji sosai, take tinanin da ya fado mata, wato aure daban, karuwanci daban, ajiyar zuciya rai mai qarfin da ya dawo da Naseer daga duniyar tinanin da ya shiga, domin shima tinanin da ke ranshi kenan, duk wata soyayya in ba da aure ba ragaggiya ce, ba ai komai a cikin ta ba, jiyake a yanzu haka daya same ta yana kallon ta a gaban shi, tana a matsayin mallakin shi, wanda komai zai mata na alkairi da jin dadin ta lada zai samu, hannu ya kai fuskar ta ya bude mayafin da ta rufe fuska da shi bayan ya aje ta," haba priceless jewel, yau ai ba ranar rufe fuska bane ko, rana ce ta nuna ma juna yanda muke son juna, rana ce ta nuna ma juna we belong to each other" tini hawayen dadin kalaman shi sun fara bin kyakkyawar fuskar ta, hannu ya sa yana share mata su, daga idanun ta masu haske tai tana kallon shi, inda gashin idon ta masu tsaho suka daga har suna tabo girar ta, kallon da take mai ne ya sa ya miqe da hanzari ya zauna kusa da ita, jawo ta yai kusa da shi yace " priceless tell me, tell me whatever it is dat u want to say pls, ina kwadayin jin abinda ke cikin zuciyar ki pls" ya fada yana mai riqe wrist din ta tare da hada goshin su waje daya,kallon shi tai cikin ido tace" abinda znce ko nake fada a zuciyata shine, Ya Allah na gode maka daka mallaka min Handsome di na, abin so na, wanda nake jin in bashi ba zan iya rayuwa ba, Ya Allah na gode maka da ka tsamar damu daga cikin masu tsananin sabo a gare ka ka tsarkake mu ka mallaka mana juna ta hanyar aure, Ya Rahman ka tausaya mana da tausayawar ka ka yafe mana zunuban mu da muka aikata a baya, ka bamu zaman lfy, ka kiyaye mu daga dikkan sharri, Allah ka bani ikon kyautata ma mijina a zaman mu na bashi dikka n soyayya da kulawa ta" shassheqar kukan angon nata taji wanda ita ta dade da jiqa fuskar ta da hawaye mai tarin yawa, kamo ta yai gaba daya ya rungume ta yana furta"Ameen ya Allah, Ameen ya rahman, Ameen da'iman" sai da sukai kuka mai yawa ba mai lallashin wani, suka gaji, dan kan su suka tsagaita, a nan ne ya tashi tsaye ya daga ta, ya ja hannun ta zuwa toilet din su mai kyaun gaske da ya sha kanay alatu a ciki, alwala ya fara ya sa tai alwala, kauda kai yaga tayi tana murmushi, ba shiri ya fara zaro ido " me kk nifi? Ki taimaken kar ki fadan baki sallah coz i dont even know how to sleep at peace today" dariya ce sosai ta kama ta, tace ni ba haka zan fada ba, duk ka bi ka wani rude🙄, ni dai kawai ka fita tukunna kafin nai alwalar akwai abinda zan yi ne shiyasa" ( Dan Nasreen tana da masaniyar cewa tabbas aka idar da duk abinda zasui sai ba barin ta zai tai watsa ruwa ba ita ko bazata iya bacci ba saita watsa ruwa dan rabon ta da wanka tin a hotel, ga rawa da suka sha duk sunyi zufa, bata qaunar angon ta yaji wani yanayi mara dadi a tattare da ita musamman a yau, da tasan sun dade basu hadu ba) kada kai yai ya fita ya ja mata qofa, wanka tai first tai brush ta qara gyara duk inda ya kamata a jikin ta sannan tai alwala, ta fito da kayan jikin ta, </p><p>Ko da ta fito bata ga kowa ba da alama ya tafi dakin shi kenan, wajen d Innar Bally ta sanar da ita kayan ta suna ke ta dakko abubuwam da zata buqata, ta koma toilet ta saka wasu kayan bacci, bby pink ce rigar, iyakarta guiwar ta hannun siriri sosai shape din ta ya fito sosai a jiki ta qasan rigar silk ne ta sama kuma net ne, sai ta daura zani akai ta saka hijab ta fito, tai wajen tiratikan ta ta fesa kamar ba zata daina ba, tana juyowa yana bude qofar, murmushi sukai sannan ya zo da sallaya biyu, ya shimfida masu, sallah ya ja su sikai, raka a biyu, sannn ya matsa kusa da ita ya dora hannun shi a kanta, ya fara karanto adduar da aka wajabtawa angwaye suyi a daren farko ma iyalan su</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p> </p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAEH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haermeebraerh na godiya mara iyaka ga dukkan masoya wannan novel na WATA UWAR ina mana fatan alkairi a duk in da muke, Allah ya amfanar damu da abinda ke ciki na fadakarwa. LOVE U ALL ANA TARE😉❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 28:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Innar Bally na cewa," Innar Hinde dama saqo ne daga wajen wadan can yaran, su Naseer, Nasreen ta dame shi da son ganin Naufal, shine yace in tambaye ku ko zaku iya basu shi, ya koma can da zama, dan yanzu ya shekara biyar kinga , bai kamata ace kamar shi a ta can birni yana zaune a gida ba makaranta ba, dan haka suka ce, in zan koma gobe na taimaka na wuce da su, dan sunce a ara masu Hinde taje taga yanda birni take itama" murmushi Innar Hinde tai tace " wannan dai dabara suka min su kwashen yaran gaba daya, sai dai sun yi tinani da suka ce a tafi harda Hinde, dan a yanzu yanda take son Naufal da ba ita, wallahi sai ta daga mana hankali dika" dariya suka sa, da jin haka Hinde jiki na rawa ta bazama daki, hada kayan su ta fara masu datti ta fito da su, ta je ta debo ruwa ta hau wanki😂, ( da dane aka ce Hinde tai wanki ai sai an tara yan kallo😂 amma da ta ji birni ba wanda ya sata) wanki tai tas, dan kayan ba yawa dama, tana shanya ne Innar Bally ta fito, ganin tana wanki bata dauka ta ma ji me ake magana akai ba, sai dai ganin fara'a a fuskar ta yasa take tinanin "Oh su Hinde anyi hankali ansan ai wa baqi fara'a unlike b4 ta hau bata rai kamar ta daki mutum" " ai dawowar Nasreen na qarshen nan ba qaramin gyara yarinyar nan yai ba, Allah ya qara shiryar da mu dika" Ameen" suka fada a tare, sallama sukai ta tafi gida, da daddare ba wanda ya sani, Hinde ta gama hada kayanta kaf dana Naufal a jaka, bayan Malam ya dawo ne, yayi wanka, ya gyara jikin shi tsaf ya ci abinci ne, Inna na gefen shi da mafici a hannu, tana mai firfita, tace" Baban Hinde , dama yarannan ne ke son a basu Naufal, kuma inda hali Hinde ta bisu taga wajen zaman yar uwar ta" murmushi yai" dama na san za a rina, dan yanda na kula suna son yaron nan, ba zasu iya rufa wata biyar ba shi ba, gashi wata uku kawai har sunyo aike, yaran zamani kenan" murmushi sukai, Innace ta kwala Hinde kira a lokacin Naufal yao bacci, amsawa tai ta fito ta tsugunna a gefen Baban ta, gaida shi tai, ya mata tambaya akan karatun ta, bayan ta gama bashi amsa ne yake sanar da ita tafiyar tasu a gobe da bayan asuba, fadada murmushin ta tai,"Allah ya kaimu Baba" sallamar ta sukai suna dariyar murnar da take, a wani bangaren Baban ta na godiya ga Allah daya shirya mai iyalan shi, Inna ya kalla yaga yanda take cike da farin ciki, hannun shi ya sa ya shafi gefen fuskar ta yana murmushi shima" kinga ko yanda fuskar ki ke haskawa a cikin farin watan nan? Na kasa gane to iya hasken ki ne ko kuma na dan sammi ki nawa ne?" Yana fada da yanayi zolaya, matsawa tai jikin shi tace" Malam kenan baka rabo da tsikana, ai kaima kasan na fika haske zama dani ne yasa ka qara hasken" dariya suka sa a tare, suna cike da so da qaunar junan su.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da asuba Hinde har tai sallah, tai wanka, ta daura ruwan zafi yana gama yi tai ma Naufal, fadi take" Dan yarabawa gobe iwar haka muna garin su Oduduwa yacin, zakaje kaga yan uwan ka masu kwale, dabaje kasan me zan fara koya? "Girgiza kai yai alamar Aa" yarbanc zan koya, dana dawo ba raini wajen su karime, dan na musi shar wallahi" dariya suka sa ita da shi suka tafa, a haka suka gama shiri dan jakar su tin jiya ta make ta da kaya, Sallamar Innar Bally ne ta dawo da su daga sallamar da take da iyayen ta, Malam ya mata nasiha sosai da ta sa ta kuka da hawaye ba kadan ba, tare da tsantsar nadamar qiyayyar da ta nunawa yar uwar ta a baya gashi tana neman tsufa a gida ba aure. Tasha suka je suka hau motar kano daga kano sai lago shine ur eyes, Idon Hinde kamar zai fadiqasa, hango manyan gine2 da tai da dogaye da tai sai da ya sata kuka,tana share majina da mayafin ta tace" Yanzu inna dan a wahalar da magina shine akai wannan dororon gidan? Ina laifin mai tsahon irin naku, kowa ya huta, duk fa tsayin mutum bai isa ya kai tsahon ginin nan ba, da kudin da zasu bannatar na wajen tsawaita katangar haka, ai da wasu ginin akai a gefe, 😤🤧 share majina ta sake yi, fuska tai mata jawur, daga Innar bally har naufal mai qananan shekaru saida sukai dariyar wautar Hinde" zaki fahimci wannan ginin ne Hinde in lokaci yayi" Sun isa gidan InnarBally lfy, da wajen isha'i gaba daya jikin su yai tsami tafiya kamar za a bar qasa, cewar Hinde kenan, qauyanci kan ranar ya amsa sunan shi wajen Hinde, komai sai da aka nuna mata musamman bandaki, a matse ta shiga, amma ta rasa inda zata hau shadda injita da fada, fitowa tai da gudu tana riqe baya da gaba, irin na masu jin bayan gid, Innar ta tarar da Baban Bally a palo, ko ta kan shi bata bi ba, kuka ta sa" Ni dai dan Allah tinda na kasa gane komai a gidannan ki nuna min ko wata yar duhuwa ce na shiga nai ba haya, a matse nake, na rasa shaddar" kuka take sosai,hankali a tashe, Inna ce ta tashi tana dariya ta kaita ta nuna mata yanda za tai da komai ta fito, bayan ta gama ne kamar yanda aka nuna mata, ta tsaya mamaki, lallai sha'anin bature sai dai ai kurum🤔</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Washe gari ne Naufal ya fara kuka tun asuba, yana kiran Mummyn shi da Daddyn shi, dan shi dai a sanin shi wajen su aka kawo su amma baiga ko daya ba, hakuri Hinde ke bashi, tin tana iyawa har ta fara sharce kwalla da majina, dan yanzu yanda take son yaron ko kukan shi bata son ji, Inna ce ta same su a haka, take tambaya " lfy? Naga kuna kuka?" So yake yaje wajen iyayen shi shine yake kuka tun goshin subahi, ni kuma na gaji da lallashin shi, yaqi shiru" to kui hakuri bari gari ya waye aiwa Naseer waya yazo ya dauke ku" murna suka fara a tare Naufal ya daga hannu alamun su tafa, tafawa sukai yana dariya" Yau zanga Mummyna da Daddy" zabura sukai jin murya mai taushi da dadin sauraro ta qaramin yaro, "Inna kinji me naji kuwa? Ko gidan ku akwai makarai ne" zaro👀 suke kamar ace ar su gudu, Naufal ne yai magana yace "Nine fa" bayan ya kama hannun Hinde, ihu Hinde tasa tana murna sosai harda hawayen farin ciki, ta tabbatar yaron nan rashin iyayen shi a hade waje daya ne yai affecting din rayuwar shi dik.da qanqantar shekarun shi, Innar Bally ce ta fita a hanzarce taiwa Baban magana ta sanar da shi komai,cikin hamdala ya daga waya ya sanar da Naseer sannan ya fada mashi suzo su dau ke su yanzu, ba a jima sosai ba like awa daya da yan mintuna su ka ji tsayuwar mota a waje, da hanzari Naufal ya leqa window, hango Daddyn shi yai yana bude daya bangaren motar, ai da gudu ya fita, daidai mummyn shi ta fito daga motar, rungume ta yai ta daga shi sama, ta qara rungume shi" Naufal honey me kace dazu kan mu zo?" Mummy ina son ganin ku ke da Daddy, shine nake ta ma Hinde kuka" yana fada yana dariya wani irin farinciki ne mara misaltuwa a tattare da iyayen shi, da su Hinde da suka fito harda jakar su, " Ya Allah na gode maka da ka sa yaron nan bai zamo daga masu nakasa ba, Allah ka yafe mana" Naseer ne ya ringume su duka yana buga bayan ta da alamun rarrashi, Baban Bally ne ya ce " to alhamdu lilLAAHi naji matuqar farin ciki nima dan a yanda naji labari baya magana, amma yanzu gashi Allah ya bashi iko yana magana cikin murya mai dadin sauraro, wato kai dama rowa kk mana sai da ka zo kaga amaryata ka fara magana dan ka siye zuciyar ta ko" dariya mai dadi Naufal yai yana riqe da wuyan Mummyn shi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sun isa gida, cike da farin ciki, bangaren su Mum suka nufa, In da suka iske ta ta hada abincin karyawa mai yawa, tana ganin su ta taho cike da fara'a, Naufal ta miqawa hannu ya je wajen ta, gaishe ta yai, tai maza ta kalli iyayen shi" ba kince man baya magana ba?" Hawayen farin ciki Nasreen ta goge tace" Mum ashe Naufal na gane komai da ake, yana fahimtar komai, wataqila da zuciyar shi yake hira? Da ace Allah bai bamu ikon gyara rayuwar mu ba da yaron nan zai iya samun ciwon zuciya, ko ya kurumce da gaske din" Oh thank God he is all okey" cewar Mum Hinde ce ke magana a zuciya" ikona wajen lillahi ko me ta fada oho na ga suna gyada kai kamar qadangaru sai Allah" jitai ance to bismillah Nasreen kaita dakin ki na da" kama hannun ta Nasreen tai ta nuna mata dakin da yanda ake amfani da komai, gudun kar taje tai masu qauyanci dan ba sanin kan abubuwan tai ba" wannan gidan yafu rikitarwa akan nasu Innar Bally" dariya Nasreen tai," to in kk shiga bangare na sai kin kama baki, yafi na Mun rikitarwa" kai habaaa, anya kuwa yan binni na cikakkiyat sallah kuwa, dan ba yanda za ai a kwanta a wannan gadon da asubar fari a tina sallah" Nasreen dariya take sosai, ta kama hannun ta suka fito palo a dinning room suka isko su Mum, zama suma sukai a kan kujerun dake zagate da table din" serve ur self pls" Mum ta fada tana muemushi , Nasreen ne ta bude wani flask da bata san meye a ciki ba ma, budewar da za tai yai daidai da thowar amai da taji...........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 29: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Amai ta shiga toilet din dake cikin palon tai sosai kamar xata amayar da hanjin ta, gaba daya Naseer hankalin shi ya gama tashi kamar ba Dr. Ba , dan ko hint bai dauka ba😜 Mum ce ta ma cike da fara'a da jin dadi ta je inda Naseer ya riqo Nasreen din suna dawowa palo, akan kujera ya aje ta, yana faman jera mata sannu, wani irin tausayi ta bashi amai daya duk ido ya fada tai firi2 kamar Buzuwa😜😂(in ji kince wani abu kum😎) Mum ce tace" Sannu Sweetheart, tin yaushe na samu sabon mai gida ko kishiya ba ko labari?" A dan firgice suka juyo, Naseer ne ya shafa kan shi yana murmushi, gaba daya sai yanzu ya fuskanta, Nasreen ko dan kunya saka kanta tai tsakiyar cinyoyin ta tana dariya qasa2, dafa bayan ta Mum tai " don't be shy, come on tell me?" Mum wallahi nima ban sani ba amma ni tinda aka kawo ni banyi al'ada ba, ban kawo komai ba game da hakan" Sujjada suka ga Naseer yayi ta godiya ga Allah, bayan ya dago ke ya matsa kusa Nasreen kamar zai shiga ciki su gana da bbyn🙄 riqe fuskar ta yai da dikkan hannyen shi biyu ya hada goshin su, ya rasa kalmar da zai magana da ita," Priceless, u ar indeed my priceless jewel, u give me all the happiness in dis world dat i could ever ask for, may Allah reward u, Allah ya miki albarka, domin bam ma san iyakar adduar da zan iya miki ba, amma albarka ta qunshi komai, domin ko a islam ba adduar da tafi a ce maka Allah ya albarkace ka, to ina roqon Allah daya albarkace ki, ya sauke ki lfy, kenan yanzu bbyn mu zai yi wata uku ko biyu da wasu satika?" Murmushi tai tace"Ameen mijina and maybe wata biyun da wasu satikan ko" qarasar da bakin shi yai nata yana kissing yaji an kwade qeyar shi ta baya,"Ouch !really Mum, do u have to do that now?" Yeh i think o have to , for a wake up to u guys🙄 " ko bakuga yanda kuka saka Hinde ta koma bane, juyawa sukai suka gan ta ta takure a bayan labule, wai ita sun bata kunya a dole, dariya ce ta kwace masu, gaba dayan palon, Naufal ne ya zauna a gefen mahaifan nashi yace" Daddy Mummy Allah ya yi muku albarka" Dariya sukai sosai wato yaji me aka fada game da albarka kenan, rungume shi sukai suka hada baki " Naufal Dear/Honey Allah ya maka albarka da dukkan yara" Ameen" Naufal da Mum suka amsa" kin iya futowa daga labulen ko kici gaba da tsayuwa mu kuma mu cinye kajin kan ki fito" da gudu ta fito" to ni dai ba na qi kaji ba ko a gidan surukai ne( waya ga surbajo taga nama a gidan surukai😂) atoh, amma gaba in zakui wannan tsotsen2 kuna yi a daka ku biyu ba wanda ya gani" dariya kowa yake yi a wajen, Nasreen qin komawa tai wajen dan qamshin farfesun Kajin da taji gaba daya dawo mata yake bata son qara shaqa, "My Dear what do u want for breakfirst pls, coz ba zai yu ki zauna da yunwa ba kin sani ko" Mum ni dan wake nake so sai kuma wainar flour mai manja, da yajin da aka sa ma Garlic da thyme please" Ok karki damu just give me a minuts yanzu zan kammala na kawo maki inshaa Allah" da hanzari tai kitchen, su Hinde ana can ana ma kaza dalla2, wani cin chips da fork gaba daya bata gan shi ba hannu take dannawa a plate kawai ta na sawa a baki, Naufal sai dariya yake," Inna Hinde dan ku na kallon kina cin abinci haka, kinga sai dariya yake miki" Yo a yaya yake son naci, in dai dariya ce gaka ga ta yaro" Naseer ne yai tashi dariyar yace "tsaya fa kiga ya zaki yi" Nuna mata yanda ake xin abinci a table yayi, ita kuma tana dauke duk wani salo da ya nuna mata" kinga in kina cin abinci haka zaki samu miji dan birni wanda ya fini kyau da komai, amma in ba haka kowa ya ga yanda kk cin abinci da tafi da magana cewa zai kaiiiii saita waye na je wajen ta" Naufal dariya ya saki sosai data sa Hinde quluwa" Haaaaaa yaro kai dariya yanzu gobe na baka mamaki kai da tsohon ka, in haka ne naga matar taka ma Mun,(Mum)ta fita gayu, dan haka ni wajen Mun zani ta koyan nafi wayewar da kyau" Aaa fa malama yanzu za a ji kanmu dake, waya ce maki Mum ta fi matata gayu? Taya zaki hada sabon jini da tsohon jini" ya fada yana maqe murya yana kai kanshi kusa da ita kar Mum taji, jiyai an sake make qeyar shi a karo na biyu,"Muuuummm" Yesssss, wato nice tsohon jinin ko, to ai da nake tsohon jinin ga shi nan Hinde ta fada maka nafi matar ka gayu" can bangaren Nasreen kuwa shiru kk ji dan hannu ta danna a kwanon itama ta bude qafafu ta baje a qasa ta hau dan waken da ci ta kuma koma kan wainar, haka tai tayi har ta kammala, daidai suma sun gama kenan, wanke hannu sukai gaba daya suka zauna hirat duniya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan wata uku, wata kyakkyawar farar yarinya na gani tana tajewa wata black beauty kwantaccen gashin ta kai, tana yi tana shafawa a hankali suna hira"Adda nasreen ni dai gaskiya ku kaini gidan Adda Bally i really want to see her plssss" cike da shagwaba Hindatu ke maganar,(Dan daga ranar nan ta dage ba wasa, Mum kuwa ta yi iya qoqarin ta da hakuri da juriya, ta koya ma hinde gayu bata mata hausa sam, tin tana hirme yanzu ba abinda bata ji a turanci, saidai wajen yi ne takan dan kwafsa, ga girki kala2 da Mum ta koya mata, tabbas ta koyi abubuwa sosai, lesson teacher aka dakko maya ita da Naufal ga kuma malamin islamiyya na musamman, tsoron Allah da tawadi'u ya shiga Hinde sosai kusan kullum sai ta ba Nasreen hakuri, inda ita kuma tai alqawarin ta qara bata hakuri Ado zata aura mata, daga ranar ta daina ) " to ki bari yayan ki ya dawo sai ki fada masa wataqila nima innaga ina iyawa na biku" Yeeeeeh U ar d best Adda" rungume ta tai ta tura kanta gefe ta dakko wayar ta, danna digits din Adda Bally ta hau yi tana sanar da ita zasu zo da daddare, Nasreen kama baki tai tana tinani a ranta wannan da sauran ta, in Naseer yace ba yau ba fa? Ta bada fake promise kenan. Kshe wayar tai ta juyo, " Hinde yanuzu in Abban Naufal yace ba yanzu ba fa?"😡 " ni Adda bana son sunan nan pls meye kuma wani Hinde dan Allah ko so kk halina na da ya bini😙 ni gaskiya a dena ce man wata Hinde, in baza a ce Hindatou ba ace Auntyn Naufal ko ace min Ke zaifi sauqi😙" hannu Nasreen ta hade alamar ban hakuri tana dariya Naseer da Naufal na tsaye sun na dariya qasa2 dan har suka shigo basu ji su ba, " "Aunty Hinde au Aunty Hindatou" cewar Naseer kenan, buga qafa ta fara ta wuce shi " ga wajen ku nan ku in zaku kori mutum sai kuita neman dalili" tafiya bangaren Mum tai tana ta cika kamar wadda akai ma wani abun" Hindatou dear me ya faru ne wannan long face haka? " Mum ba su Adda da yaya bane, wai sai wani kirana Hinde suke, bayan sun san bana so, kuma Malam Anwar ya hana yace in daina bari ana kirana haka nan" ta turo baki gaba kamar Roumie tayi fushi😂😜Mum dariya take sosai tace " Ohhhhhh ga inda zancen yake nan mana , kice kawai Malam Anwar ne baya so shiyasa bana so nima" da gudu Hinde tai daki tana dariyar kunya( Malamin Islamiyyar su kenan, sun fara soyayya da hinde a sati biyu da fara zuwan shi rayuwar hinde ba abinda bai sani ba ta sanar da shi, a hakan yaji yana son auren ta coz shima has his past, so ya nuna mata kawai su yafi juna su riqe juna da amana, inda ta amince da hakan yanzu haka an sa musu rana bayan wata takwas za ai auren su) dariya Mum tai ta miqe tai daki itama.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sun shirya sunyi fes da su gwanin sha'awa suka nufi gidan Bally inda Naseer ke tuqa su, sun yi tafiyar rabin awa kan nan suka tsaya a qofar wani gida madaidaici mai kyau, shiga sukai bayan Umar ya fito ya masu iso ciki, Bally ce itama da dan cikin ta a gaba tayi kyau hasken ta ya fito sosai ga kuma na ciki, Nasreen ce tace" Maman biyu ana nan na ta turawa" dariya suka sa "Aa wallah na bar maki biyun dayan ma wallahi tsoro nake ji ni" Kaiiiii Adda Bally kar ki sa ta dinga ganin mu ragwaye pls k dage ki haiifo biyunnan kawai" cewar Hinde kenan " Rufan asirisweet qanwa, ba zan iya biyu ba gaskiya" Naseer ne ya amshe" kinga kuwa Priceless zata iya zata baku mamaki kuwa" murmushi tai tace" Allah ya bamu masu albarka, Handsome" shafa gefen fuskar ta yai yai kissing hannun ta" to love birds taso muje mui sallar isha'i" dariya sukai dika Naufal ne ya zauna kusa da Bally yana shafa cikin ta" My Naufal ka matsu a haifo maka budurwar nan naga alama" dariya yai yana sosa kai wai shi yaji kunya🙄( yaran zamani masu zamammiyar qeya wai ya san budurwa🙄)" Yar uwa ina son mui wata magana mai matuqar mahimmanci kafin su dawo shawara nake son ki bani dan Allah wallahi akwai matsalolin da ke damuna sosai, na rasa yanda zan , dan koda baki zo ba nai niyyar na zo da kaina.............</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p> </p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 30: </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Ba komai ke damuna ba sis sai matsalar da nake fuskanta a wajen Umar, kafin auren mu ke shaida ce yanda yake man kalama soyayya, yake nuna min matuqar kulawa, amma yanzu gaba daya abun ba haka bane, ya canja sosai, duk da ina hango tsantsar siyayya ta a wajen shi, sai ma qaruwa da tai ba raguwa ba, amma duk wata kulawa da yau promising me are all lies, ba wani abu da yau keeping da ya wuce satika uku da auren mu, kin ga da farko dai, in mun zo auratayya gaba daya baya tsayawa mu danyi wasanni, dan kar na zo ni i am not ready yazo yana bari na da wahala, inaaa kawai shi da ya matsu zai zo kawai ya fada min da ya gama ya tashi ya barni duk kuka da zan sai yace to shi ya zaiyyi? Sannan kinga in ban da lfy irin ya damu dinnan ya nuna min kulawa a'a kawai sai yai ta harko kin shi bai damuwa, dana ji sauqi kuma ya dora da buqatun shi😭 kuma kinga wallahi in nai laifi ya dinga fada kamar bai sanni ba haka zai ci min mutunci tas ya gama, sai daga baya ya zo yana wani.ban hakuri musamman in yana son kusanta ta,ke abubuwan da yake min suna da yawa na rasa yanda zan bullo mai😭😭" a gaskiya ban ji dadin jin wadannan abubuwan ba domin kamar ba zai yi ba, amma kin san me zaki? Na farko stop especting too much from him, espectation hurts, musamman in akai disappointing din ka , ur heart will break, sannan game da baya wasanni sai dai kawai ya fara kusantar ki, wannan laifin ki na gani, dan me zaki bar shi ya shiga jikin ki ba tare da kin tabbatar kin mai wasannin da zai tada taki sha'awar ba da jikin shi shima zai ji dadin hakan in kk mai yau kk mai gobe ko baya so a hankali zai fara so dan yaji dadin wasan, in kk ji u ar good to go, sai ki bashi dama ku more wa rayuwar auren ku, dan haka ta nan laifin ki yafi yawa, ina son ki gyara pls sis, abu na gaba kuma na rashin lfy, wasu mazan ba sa son raki duk da an san baki da lfy ki zama mai juriya wani nishe2 ki ta ihu bai ba in azaba tai yawa zaki iya yin kuka amma ba wanda zai sa.miji ya ji haushin ki ba, in yaga haka zai san kina cikin azaba amma juriya kk ta haka sai ya tausaya maki kiga yana nan nan da ke, sai in kin yi hakan ne bai kula da ke still, in kk ji sauqi randa kuke raha kk tabbatar ranshi ba zai baci ba da duk maganar da kk gaya masa to saiki fada masa ki ce Wane me yasa kk man kaza in ban da lfy? In ya gaya maki dalili in kina da laifi saiki gyara in babu sai ki qara da wallahi sai in ga kamar baka sona ne saboda masoyi yana jin ciwon da dan uwan shi ke ciki, zai iya baki hakuri ku daidaita kuma ya daina amma in bai baki hakuri ba ya daina nan ma yayi, in ma bai daina ba sai ki dau matakin qarshe, kauda kai, domin ta yu haka yake, kuma hakan na samo nasaba ne daga tatbiyyar shi tin fil azal, sannan da daga wane gida ya fito, sai ki cire a ran ki kina so mijin ki yana baki kulawa , dan ba halin shi bane, a kwai wani abu Bally da ma'aurata ya kamata su sani shine, ita rayuwar aure dole miji da mata su koyi tattauna dukkan matsalar su a tare, ba tare da fada ko yin fushi ba, in kuna haka sai ku shekara dari ba wanda ya ji kan ku, a ce tinda ake ba a taba jin kan su ba , ba dan baku fada ba sai dan kun fahimci juna, ni kin ga ni da Abban Naufal in mun samu sabani, komai dare in mun gama abun da zamui zamu tttauna damuwar mu , kowa ya ba kowa hakuri, shikenan ya wuce, dan haka ki zauna ki gyara rayuwar gidan ki kan lokaci ya qure maki, ina maki fatan alkairi yar uwa da mu dika" hawayen ta ta share ta rungume ta tana murmushi," na gode yar uwata da ban sanar da ke ba da ina jin baqin ciki ya sa min hawan jini" ta fada tana dariya, sallama akai aka leqo "in kun gama hirar ta mu sai ku fito ku bamu abinci yuwa muke ji"😱🙊 dama sun ji kome muke fada? Ban ji shigowar su ba yau na shiga uku na" in ji Nasreen da ta rude ta kasa fita daga dakin" itama Bally ta ji ba dadi amma wani sashen na ranta taji dadi. Sauraran ta da Umar yayi wataqila ya gyara, aiko suna fita ya kamo hannun ta ya rungume ta ta baya ya dora kan shi akafadar ta ya hade hannayen su yana bata hakuri sannan yai mata alqawarin komai zai wuce shima abun na damun shi amma ya kasa gyarawa, amma hirar nan tasu ta sa yaji dole ya gyara ma, musamman da itan tana iya qoqarin ta akan shi, hawayen dadi ne ya gangaro mata daidai lokacin daya juyo da ita yana goge mata kiss ya mata a goshi ya na shafa fuskar ta, gyaran murya Hinde tai tace" Oh ni Hindatou wai ba dama ka sa qafa gidan masu aure sun dinga shinshime shinshine kenan , dan Allah ji yanda Ya Umar ke shinshine mata fuska🤔" dariya suka sa gaba daya har da Naufal " Aunty Hindatou ke kuma in dai kk gani sai kin yi magana" dukan wasa ta kai masa ya fada jikin ta ta rungume shu suka ci gaba da dariya, abincin dare suka ci tuwon farar shinkafa miyat wake da busasshen kifi, da drinks da tai na pineapple da ta zuba kayan qamshi da sugar,( hadi ne mai kyau ga mata harda mazan ma yana sa qamshi daga baki har HQ🙊) sun gama cike da nishadi suka koma gida.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau tin safe Nasreen take jin jikin ta ba dadi sosai, daurewa kawai take Hinde kuma ta zata yana nan dan haka ma tin da safen bata shiga ba, Naseer bai da niyyar fita saboda weekend ne, (sunday) aya aka mai an kawo mara lfyr da suna da buqatar shi, ya fita tin 7:15am har azahar, tin tana daure wa har ta fara safa da marwa, ta kai ta kawo Naufal ne ya shigo daga wajen Mum, ya shigo shirin islamiyya, ganin Mummyn shi yai tana ta wahala, da gudu ya fita, karo yai da mutum, yana daga kai yaga Daddyn shi ai rungune shi yai yana kuka ya nuna mai hanyar shiga palo," Naufal calm down and talk to ur Daddy" Mummy na" kalmar da ya iya fada kenan Naseer ya dauke shi suka shiga da gudu, yana isa yagan ta a durqushe tana nishi mai wahalarwa, daidai nan suka ji kukan jaririya, Naufal ta aje ya ce ya je ya kira mum ya zauna wajen Aunty Hindatou, kafin Mum ta shigo Nasreen ta qara haifar wata jaririyar, jikin Naseer banda rawa ba abinda yake, daga yaran yai ya yanke cibi,sannan ya taimaka mata mahaifa ta fado, aje yaran yai daidai Mum ta shigo kenan, ta kama bakin ta🙊🙊😭😭😭 ga hawaye ga murmushi, she is speechless, qarasowa tai da sauri ta dauki yaran shi kuma yai toilet da Nasreen, ruwa mai zafi ya saka mata ta shiga ta kwanta a ciki tana ta maida nunfashi tana godiya ga Allah sannan ga mamaki fal cikin ta wai yara biyu ta haifa, ita da take zaton Bally ce zata haifi biyu, iko sai Allah, hure mata ido yai ya kamo hanun ta daya adduoin alkairi ba irin wanda bai mata ba har saida yaga tana hawayen farin ciki sannan ya tsiyaye ruwan ya sa mata wani shima mai zafi, saida ya sa mata sau uku sannaj ya saka mata daidai wanka, wankan ya fara mata yana kallon cikin ta kamar ba yanzunnan ta gama haihuwa ba yanda yai, tabbas ya daga amma ba za a ce wai irin tai qaton timbi ba, sai hips din ta da cinyoyin ta da suka qara girma ga girjin ta kamar ai magana su amsa, kallon ta yake yana hadiye yawu" Hey man dont even look me like dat u have no chance here u know dat, dont u?" Hhhhhhh kai babe ni kawai ina yava yanda Allah ya miki kyaun jiki ne kawai Allah yasa yaran mu sui kama da ke" Ameen amma ni nafi son wata tai kama da kai wata tai kama da ni" wowww Allah yasa" daidai ya dakko ta sun fito kenan, shiryata yai suka koma palo, Mum ta gyara yara sunyi fess " Addana sannu da qoqari Allah ya raya mana su akan sunna, ya albarkace su"Ameen Sweery" Mummy kin samo min qanne, na gode Allah ya baki lada mai yawa, Mum tace mata ne dika" Ameen Yaya Naufal dina Allah ya muku albarka dikan k, Mum i am hungry, i want something liquid please" Eh na sa Haulat ta dafa maki farfesun naman rago, da kunun gyada, in kina son na kaji ma nasa duk tayi inna kaine ma haka, ki bari nan da minti kadan zata kawo maki" Tea Naseer ya shigo da shi a hannu ya zauna kusa da ita ya kafa mata a baki, da sauri ta kama ta hau sha, tana shanyewa mum ta miqa mqta yaran," to suma a basu na su abincin" karbar su tai tana ma Allah tasbihi, daidai nan Naseer ya kawo dabino da zamzam inda ya miqawa Nasreen ta tauna ta sa musu sai tandewa suke dan bakinnan yai jawur gwanin shaawa bayan sun cinye ta sa musu ruwan zamzam din a baki suka shanye sannan ta sa musu nonon suka ko hau sha kamar jira suke, dan zafi saida tai kwalla ta rufe ido yanda suke sha kamar wasu manya, ankali ta bude idon ta tana kallon su ,lallai Allah mai halitta, nida uban yaran dika baqaqe amma yaran mu kamar yaran turawa, wannan misali ne akan Innar Hinde dan muddin ta gan su sai an sake sabon kuka da nemab gafara, tinda itama Nasreen duk dangin su farare ne ita daya ce baqa,hawaye ne suka bi fuskar ta, Naseer ne ya karbe su ya msusu huduba ya masu adduoi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hinde har ta yi waya ta sanar da mutane haihuwar, ai ko sai ga Innar Bally........</p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAERH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 31:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Innar Bally bata iso ba sai goshin Asr, tana shigowa ta tadda kowa ya saka yaran a gaba sai kallo ake, kowa da abinda ya ke furtawa, domin kuwa yaran sun debo kyau irin na Innar Hinde, komai da komai, saidai su suna da beuaty point a qasan habar su, da akuma alamun za sui hushirya( irin tawa😎lols) ba abinda ta ke furtawa sai" Fatabarakallahu ahsanul khaliqeen" ta fada ta kuma sai kuma tace" Sannu Nasreen dina" dariyar Hinde ce ta sa ta sassauta kallon t ga yaran ta na kallon ta " Inna Hooo, gaba daya kin kasa ma ko kallon yayan ki, sai kallon kishiyoyi, to wallahi ku shirya ke da Innar Hinde, dan kuwa su Baba suka ga wadannan halitta haka, kwanan zaure zasu fara saka ku" dariya kowa yake a wajen " to ai ni ba zan ga laifin su ba don an aje mu an dau wasannan tsalan yaran ki fa duba ki gani fisabillahi a zuri'a kaf an taba irin wannan haihuwar?" Dariya wajen ya qara dauka, ga sasshen naman da ta zo mata da shi shi ta dakko, ta miqo mata ya sha kayan qamshi da dan wasu hade2n irin na sirrin Innar Bally😜, ci ta fara tana lunshe ido ga gashin harda wani ruwa2 a ciki," A gaskiya ni ba zamu yar da ba ko Naufal? Ya muna zaune sai kwanuka ake miqa mata ita daya🙄" hhhhhhhh in kin ji haushi kema nan da wata goma sha biyu ki haihu zaki ga kwanuka kala2 a gaban ki" rufe fuska tai ta tashi zata gudu dan bata dauka amsar da za a bata ba kenan, kuma ko za a batan ba ta zaci Abban Naufal bane zai fada, ban garen Mum ta gudu, kwanta wa tai tana tinanin baya, "Oh ni Hinde, duba matar da na sa wa qahon zuqa da tsana, da qiyayya yanda Allah ya daukaka ta? Sannan ya sa gani ni ma a sana din ta na samu daukaka, ko shiryar da ni da Allah yayi ai ba qaramin arziqi bane, ga shi harda mijin aure na samu duk irin lalacewar da nai a baya, kaiiiiii amma wallahi qauye ba tai ba da kuma rashin samun tayayyar UWA, da a ca WATA UWAT gareni ba Innar Hinde ba mai hankali da nutsuwa da duk raba ma qazaman qauye budurcina da darajata da nai a baya da ban ba, a yanzu na fuskanci mutuncin mace da qimar ta shine nesanta kanta daga fadawa sharrin zina, Allah kaine ka tsara mana komai kuma yake ta fiya da izinin ka, Allah mun gode maka da ka canja mana rayuwar mu daga mummuna zuwa kyakkyaw, Allah ka barmu na ka duk lalacewar zamani" hawayen daya taru a idon ta ta rufe suka sakko fuskar ta, ji tai ana share mata su, daga kai tai taga Naufal ne, kusa da ita ya qara matsawa, janshi tai ta rungume, ta ci gaba da matse kwalla" Naufal kai yaro ne, amma yaro mai hankali da fahimta, ina sane da cewar a yanzu da shekarun ka suka kai bakwai zuwa takwas ka fuskanci abubuwan da suke faruwa a rayuwar ka, ka yafe min dik abin da na maka a baya kaji dana, ka yafewa Innar Hinde itama, sannan ka sa Allah a rayuwar ka a komai za kai, ka na neman zabin Allah a dikkan abinda ka saka a gaba, to Allah zai tina da kai a lokacin da kk cikin qunci" rungume ta ya sake yi yace"Aunty Hindatou na yafe maki, ki kwantar da hankalin ku kema ki samo min qanwa, amma ni bana son fara fa" hhhhh Naufal hooo" Aunty Malam ya zo, yana waje tin dazu kina nan kina kuka😃" biyo shi tai suka fata zagaye dakin suna dariya, taje toilet bayan ya fice ta wanke fuska ta zo gaban madubi ta gyara fuskar ta ta fice sin sha hirar su ta masoya yai mata barka, bayan ya tafi ne ta koma bamgaren su Nasreen ta tarar Innar Bally na mata wanka, tana ta raki" Oh ikon Allah, to dayan biyu ne wannan rakin, wataqila kin fi son wankan Abban Naufal, ko kuma dazu bai sa maki ruwan zafi da yawa bane" Ina ruwan ki, Allah ya kaimu naki zaki bayani ne ni da kaina zan maki" Nasreen ce ta fada bayan ta tro qofa ta fito, bakinnan ta turo shi gaba, ido ya kumbura alaman tai kuka, tana zama sai gyangyadi, dariya Hinde tai ganin hakan, Innar Bally komawa tai dakin da bbies din suke, ta wanke su tas suna kuka suna komai, kafin ta gama musu suma sai bacci, Naseer ne ya gyara Nasreen ya shiyata, ya gyara mata kwanciya, a dakin yaran Innar Bally ta kwana Hinde tai bangaren su.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kafin suna da kwana biyu Bally ta haihu ta haifi yarta kyakkyawa itama black beauty, kowa ya ganya sai ya tanka, yarinyar qatuwa kamar ni na haife ta, 😂 </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan sati biyu, anyi suna an gama komai, yaran Nasreen sunci sunan NI'IMA & NAEEMA, yarinyar Bally ta ci sunan NAWWARA, Naufal gidan ya tare, kullum yana kusa da bby ko tana hannun shi, kowa yazo sai ya tsokane shi,saidai yai ta dariya. Su Innar Hinde ba su zo ba, a cewar ta da wane ido zata kalli Yaran bayan irin abubuwan da tai ma uwar su, Baban Hinde yayi2, taqi, amma Hinde tace in bikin ta yazo bata zo ba, ba zata ji dadi ba, ta fada tana kukan haushin qaramin dalilin da zai hana ta zuwa ganin jikokin da Allah ya bata, ta wani bangaren kuma tana ganin har yanzu da sauran Innar Innar Hinde a wajen kula su.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kwanci tashi a sarar me rai, yara sunyi bulbul, da su ga wayo, watan su hudu2, yayi daidai da yau saura wata biyu bikin Hinde da Malam din ta, shirye2 sike ba kama hannun yaro gyara ba irin wanda ba sa yiwa Hinde,daga kan Mum, Bally, da kuma Nasreen, ba wanda ya zauna wajen gyarata, saida ta koma tai wani irin kyau, na ban mamaki, kullum da irin abincin da take ci duk dan gyaran jikin ta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> QAUYEN LANGYAM</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" A gaskiya Innar Hinde baki da dalilin qin zuwa wannan auren, domin in baki je ba kina nunawa yarannan halayyar ki ta da na nan ne fa, ki duba ki gani, lokacin da yarinyar nan tana tsalle2n bin samari shago ke kika bata qwarin guiwa, sannan lokacin da Nasreen ta zo da Naufal baki nuna damuwar ki ba musamman da ta baki kudade a hannun ki, sai yanzu sa suka samu abu ta hanyar halal lokacin ne zaki ce wai ke ba zaki je ba kina jin nauyin su? Wanne irin gwari ne wannan?" Kuka take tana share majina" ni malam ba wai naqi bane, gaba daya kunya nake ji na qara hada ido da su a mazaunin su,ganin irin rayuwar dana sa su a ciki a baya, da wanne idon zan kalli yaron nan Naufal, ni nai sanadin da aka haife shi ba ta hanyar halak ba" ki daina sa wannan a ranki, dik abinda ya faru kuma ya wuce ya wuce kenan, fatan mu mu nemi gafarar wanda mukaiwa laifi ko Allah zai yafe mana muma, sannan mu maida hankalin mu wajen gyara gaba da ci gaba da istigfari" kwantar da kanta tai a inyar shi ya shiga shafa kanta, tana sauke ajiyar zuciya" to yaushe zamu tafi?" yanzu kinga sauran wata daya da wasu satika bari zamui sai irin sauran sati daya dinnan sai mu tafi ke ko ana sauran kwana biyu ko daya dan kar ki zama baki sake ba, bana son duk abinda zai sa kiji kin damu" na gode mijina, zanfi son mu je sairan kwana biyu din" Allah ya kaimu to da rai da lfy" Ameen" a haka suka bar maganar. A kullum Hinde da Nasreen abun qara damun su yake ganin kwanaki na qaratowa ba Innar su ba Baban su, Naseer da malam din Hinde kullum basu gajiyawa da kwantar da hankalin su, da basu baki akan zasu zo ne.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau sauran kwana biyu bikin su Hinde, can na hango Innar Hinde tana ta zare ido a tasha bayan saukar su a mota a cikin garin Lagos, motat Baban Bally ce ta tsaya a gaban su, bayan ya fito yana fara'a ya miqawa Baban Hinde Hannu suka gaisa," kai jama'a wannan gari da shi da cikin garin kano a kwai alummar rasulu, badan wancan yaron da ka gani ba, da ko wayar ma ni ban san ya zan da ita ba, tinda muna gida saidai a kira mu" dariya Baban Bally yai yace "tabbas Malam kaima ba zaka koma ba sai ka koyi duk wadannan abubuwan har da wasu ma" mota suka shiga suka hau titi, suna isa a qofar gate din gidan suka tadda Innar Bally tana jiran su, da sauri ta bude wa Innar Hinde motar ta kama hannun ta cike da murna" sannun ku da zuwa ikko ikon Allah, cunkus dakin tsimma" yauwa Innar Barira, ni dai wannan gari tafiha haka kamar za a fita daga qasar, da na san haka ne da ban zo ba sai na shirya" dariya sukai daidai lokacin da suka shiga palon gidan, abinci suka ci sukai wanka, dakin da aka nuna masu nan suka shiga, kwanciya sikai su huta, dan Innar Hinde sai wani shagwaban ta gaji take( kuji man tsohuwa fa🤔lols) tausa ya mata nan da nan ta hau baccin gajiya, murmushi yai a ranshi ya furta" da tin fari haka kk me zai sa mu cikin damuwa da tashin hankalin da muka fuskanta a baya".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Su Nasreen sun san da zuwan iyayen su, inda farinciki mara iyaka ya mamaye su, Hinde ta so taje ta gansu amma su Bally suka ce ba inda zata, ta hakura har su zo, ba zasu zo sina mata gyata tana yawo a rana ba, a cewar ta to zata da dare, sa kyar suka barta, taje da dare amma a ranar zata dawo saboda gobe za a fara biki, sun kwana suna hira ita da Innar ta, hakuri ko ta ba Hinde har saida ta hana ta bata hakurin, ta mata nasihohin da saida ta ba Hinde mamaki, dama tasan wadannan abubuwan? Wajen qarfe tara na dare ta tafi cike da kewar dama tare zasu kwana.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>An yi taron yini da rana inda, qawayen Mum ne yawanci, sai abokan arziqin Innar Bally, su suka halar ta anci an sha, zuwa Asr aka daura auren su, aure kamar auren bazawara ba budurwa ba, hakan sai da ya dami Hinden sosai, daga bayada kanta ta sanar da kanta dalilin kasancewar auren ta ba armashi duk yanda yan uwanta suka so hakan ta kasance kuwa, ba komai bane illa bata rayuwar ta da tai a baya, hawayen ta ta share tace" Allah na gode maka da hakan ma domin kuwa ba kowa ke samun irin nawa ba ma" </p><p><br /></p><p><br /></p><p>An kai amarya gidan ta dake can kusa da unguwar su Bally, amarya dai kun san ba wata wahala da zata sha, dan ta saba da gayun qauye, saidai ta wahalar da ango,😜 sun sha amarcin su sosai kamar ba zasu hakura su barwa gobe ba, ga gyara dama da tasha, tashi tai lokacin qarfe hudu ta yi goshin Subh, sukai wankan tsarki suka fito a tare, sannan suka duqufa sallolin nawafil, tare da adduar godiya ga Allah da kuma neman gafarar shi akan laifukan su na baya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wani matashin saurayi na gano da ba zai wuce shekara sha takwas ba ya biyo wasu yara masu matuqar kama da juna, suna gudu suna dariya shi kuma ya bata rai, bayan Mummyn su suka maqale suna mai kwalo, " wai kai Naufal yaushe zaka girma ne? Dubi dan abin kunya yanda kk bin qannen ka da gudu, me suka maka yau kuma?" Mummy kinga yanda yarannan suka shiga dakina suka hau gado suka tsaya a tsaye suna man rawa? Bayan kunna min laptop da sukai ina aiki akai ko saving rubutuna ba sui ba fa?" Ya fada yana maida numfashi" a gaskiya ba ku kyauta ba My Cuties, Yayan ku kunsan baya matsa maku amma ku kun sa shi a gaba, ba kyau fa, kar yazo ya dawo yan dukan ku bayan ku kuka jawa kan ku, kun kqi shi maqura" fitowa sukai daga bayan ta suka nufe shi, suka kwanta a jikin shi, "we ar sorry sweet broth" daga su yai ya rungume, ya ce "its k, amma kar ku sake,in kuna min rashin ji, My Nawwara will not be happy,kumq b azatai qawance da ku ba" hakuri suka hada baki suna bashi, wai kar ya fda mata plsss, dariya Mummyn su take sosai, da jin wannan maganar ta naufal.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin dare Nasreen na kwance a jikin Naseer yace " a gaskiya Mummyn twins ya kamata a sama masu qani ko qanwa kin huta da yawa fa" murmushi tai tace" hmmmmm not a bad idea, i will love that too"ta shi tai zaune suka fiskanci juna, gyaran murya yai yace mata, " Nasreen" daga kai tai ta kalle shi dan rabon daya kira ta da sunan nan ya jima, and d way his face looks ta san akwai wata magana mai mahimmanci da zai mata.........</p><p><br /></p><p>👵🏻 WATA UWAR 👵🏻</p><p><br /></p><p><br /></p><p> BY HAERMEEBRAEH</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 32:</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>" Da farko dai ina son nai maki godiya ta musamman" tashi yai ya dakko wasu takardu," na gode sosai a kan dukkan alkairan ki a gare ni, musamman na mai da ni mutum da ki kai cikakke, ta dalilin ki na bar neman matan banza, ta dalilin ki na nutsu na san ko ni waye, nasan ya kamata na kama daraja da mutunci na, sannan ke ce kk zama uwar 'ya'yan da nake alfahari nawa ne, har Naufal bana jin haushin samuwar shi, sai dai kullum ya zamar min wani tini na cewar ni mai babban zunubi ne a wajen Allah da bai kamata na shagala da duniya ba, wannan dalilin ne yasa na gina mana masallatai da makarantu da ni da ke, domin ko mutuwa mukai muna saka ran rahamar Allah a gare mu , sannan mu dage da aikin alkairi domin cewar Annabin rahama da yai na" kyawawan aiki na tafiyar da munana" kin ga in muka dage da yin kyakkyawa Allah zai dube mu da rahamar sa inshaa Allah" Nasreen kuka take sosai na jin qaunar mijin ta da kuma qara dasa mata tsoron Allah da yake yi a zuciyar ta, " ki dai na kuka my love ba ina fada maki wadannan abubuwan bane dan na tada hankalin ki, lakin sai dai dan mu ci gaba da shimfida rayuwar mu akan sunnar Annabin rahama, dan haka nasan kin san cewa Naufal ba zai gadi komai daga dukiha ta ba, wannan karatun a wajen ki na same shi malamata😊, so ni da Mum mun yanke shawarar mallaka mai wasu mahimman filaye da kamfani guda biyu na atampopi, daya a England yake daya anan gida Nigeria ne, sannan akwai gidaje guda biyu manya da Mum ta mai kyautar shi, ina fatan ki zama shaida a matsayin ki na mahaifiyar shi, a duk randa ya gama University a ranar zan damqa mai komai da ya mallaka ta hanyar halal na wajen mu, in mun mutu ba su a gado, dan na sanar da Lauya na da duk wanda ya kamat, infact malam Liman ma yasan da hakan" cikin kuka da farinciki Nasreen ta fara magana" Abban Naufal nice zan maka godiya, soyayyar ka ta tsamo ni daga fadawa halaka, ta sa na gane karuwanci ba abin yi bane abin kyama ne, sannan soyayyar ka ta sa na fuskanci kome iyayae zasu maka hakuri zai tadda rabo musamman UWA, soyayyar ka ta sa na zama mai yafiya, domin daga randa na koma gida na aje Naufal na fito neman ka naji na yafe ma 'yar uwa ta dukkan abin da ta min da mahaifiyata, naji zan iya dawwama a halayyar su in dai zan gan ka ko sau daya ne, sannan gashi ka zama babban alkairi a rayuwa ta, ka ban farin cikin 'Ya'ya kyawawa, ga ni ka aje ni cikin hutu da jin dadi, ga soyayyar nan ta ka da baka gajiya da nuna man ko a gaban waye, what would i ever ask for? Sai dai nace Alhamdu lilLAAH sannan na qara da astagafurullahi a kulli zanbin ya rahman, ina mai godiya da Allah ya ban kai a matsayin miji ubam yayana, kuma ina taya Naufal godiya Allah ya qara budi mai yawa mai albarka" aje takardun yai ya rungume ta yana shafa bayan ta da sigar lallashi, daga haka salon Naseer mai mantar da Nasreen dukkan wani quncin ta ya fara aiki, sarrafata yake kamar yaro da abin wasan shi, a ranar jin su suke kamar wasu amare, sun sha soyayyar da suka dade ba su gudanar da ita ba, gaba dayan su ji suke bazasu taba iya mantawa da wannan rana ba, domin kuwa ganin ta suke mai matuqar mahimmanci,"Ya Allah ka taimake ni kasa na dasa yan uku anan yau" ya fada yana shafa cikin ta, dukan wasa ta kaiwa hannun shi tace" tab ai ko da sai dai kai ka dau cikin yan biyun ni na riqe dayan😙" dariya sosai Naseer yake ya dagota ya dora kan cikin shi yana kallon yanda da gaske ta turo baki gaba tana wani narkewa( ni ko nace soyayya ruwan zuma😉).</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan shakara daya da wata Uku, Hinde na hango Malam din ta ya riqo ta ya sata a motar da Nasreen ce ta mallaka masu saboda zirga2, asibiti zasu da dikkan alamu dan wannan qaton cikin haihuwar gida ba zata yu masu ba. Kuka take tana qarawa" Wayyo Innata ki yafe min ni kam mutuwa zan yau, Baban Hinde ka yafen rashin jin maganar ka da taurin kai da na din ga maka a baya, wayyo bayana marata zata balle, Husby ka taimaka min kar na mutu bam qara neman yafiyar Adda Nasreen da Naufal ba" saiga angon Hinde na matse yar kwalla" ba zaki mutu ba My Lady, zaki rayu ke da ya ko dan zaki haifa mana , kuma duk sun yafe maki, ko kin manta kullum kuka hadu sai kin nemi gafara, kuma sai sun yafe maki? Ki kwantat da hankalin ki ki ta addua, inshaa Allahu kome ki ka riqa a wannan stage Allah zai amsa maki dikkan buqatun ki" kukan ta tsagaita ta hau adduar Allahumma la sahla illa ma ja'al tahu sahla...... har zuwa qarshe daga nan ta kamo Allahu Allahu Allahu rabbee la ushrika bihi shai'an wa hussami'ul aleem, kai adduoi dai taf bakin Hinde dai ga su nan yau, ba kalar wadda bata yi har da ta shiga bandaki sai da ta zayyano, sun isa lfy an kuma karbi haihuwar ta in da ta haifi Namiji, bayan ta haihu ne aka kira mijin ta ya miqa kayan haihuwa kan su Nasreen su iso an gama gyara komai an miqo masu jariri, inda na ga Nasreen dauke da cikin da ba zai wuce wata shida ba, zuwa bakwai, An gama komai aka sallame su zuwa gida Nasreen ce zatai ma Hinde wanka zo ku ga kokawa,ita fa sam ba za a jibge ta da ganye ba, kuma in towel ne sai dai a bata tai da kanta, miqa mata Nasreen tai ba musu ta sa hannu zata dauka, data zunduma wani uban ihu saida mijin ya leqo yana Adda Nasreen lfy dai ko, hannu ta daga alamar leqo ka gani ba ruwana, kuka ya ga Hinde nayi dan shagwaba ta na ganin shi ta qara fasa kuka, " Nashiga uku wai ruwan zafin dole ne? Banaji ance in aka hada wa mutum shayi mai kauri da manyan kaji da wasu kayan dadin sun isa ba? " dariya mijin nata da Nasreen suke sosai Naufal na palo yana jiran ta fito ya tsokane ta dariya shima yake va iyaka, Innar Bally ce tace ma Nasreen ta tafu ta barsu kan ta qarasa ta itama tana fama dana ta jikin, tafiya tai tana dariyar wautar Hinde, " eh tabbas akwai ma wani ganye da yare suke amfani da shi mai suna EFIRI. Ko a ce mai ILERU amma ileru a okene ne suke kiran shi haka, mai jego ana mata miya cike da nama da ganyen da gyada ko egusi taci, yana gyara jiki sosai duk wani qaton tumbi da jini ya maqale duk ficewa yake, da damar su ma basa wankan jego iya ganyen suke ci, amma dole ke a hada maki biyun dan muma al'adar mu ne wankan jego kin qara da al'adar wasun, Hinde jan zance tai tayi ruwa na sanyi sannan aka mata wankan suka fito, ta turo baki gaba kamar a jawo shi, " Aunty Hindatou ai shi ruwan zafi ba wani abu bane dan an sa ya tafasa kamar sau uku an miki wanka da shi, ko so kk su Karime qawar ki ta qauye ta fiki dauriya ne" filon kusa da ita ta dauke ta maka mai " to dan ta fini ta nan wajen ruwan zafi ai ba damuwa tin da dai na fita wayewa na fita kilewa ai shikenan dama kalar ruwan zafin ce ita"ranar kam an sha dariya a gidan Hinde. Bayan kwana bakwai yaro yaci suna Na'eem, sosai suke ji da yaron nan kyakkyawa sai manyan ido, ga Hinde da tsoro daya fara bude su yana zaro harshe irin na neman Nono zata miqawa uban da sauri tana " ce mai dan Allah ba sai ya tsorata ni ba zan bashi aboncin shi, ai na shi ne dama ba na wani ba" sosai mijin ke dariya yace" to in banda abinki My Lady ga ki ga shi sai an aika dan saqo?" .</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yaune Su Hinde da Nasreen suka shirya tafiya qauye ganin gida, sun shirya har da Mum zata ganin gidan surukai, kuma a satin da ya wuce ne suka angwance ita da Malam Liman da kyar bayan Nasreen da Naseer sun sha fama, daga qarshe Naufal ne yaci nasarar shawo kanta ta amince, shiyasa ma Malam Liman ke kiran shi da Wakili. Sun isa qauyen Langyam da yamma lis inda suka tarar da gidan su Hinde qal, kamar ba nan ba, ya sha ginin zamani, mai matuqar kyau, ga wani babban masallaci a kusa da gidan, shiga sukai gidan me bangare hudu kowanne da daki daya, bandaki, da babban palo, daya Mum da Malam liman aka sauka a ciki dayan kuma Hinde da mijin ta, daya Nasreen da Naseer dan na musamman dama ya gina masu in sun zo da yara nasu ne kawai mai daki biyu, sai wajen su Inna mai hade da babban kitchen da danning, a babban palon gidan aka hadu dika bayan isha'i an ci an sha, an yi gaishe2, Baban Hinde ne riqe da dan gidan Hinde twins na gefe da gefen shi, sai Naufal wajen qafar shi, inda Nasreen da Naseer ke zaune a one seater mai fadin da zata ci mutum biyu, ya na riqe da ita ta dora hannu kan cikin ya zagayo qugun ta da nashi hannun, Hinde da mijin ta na tasu kujerar, sai malam Liman da Mum ana ta aikawa juna kallon love(lols😉) Ita kuma Inna ta shigo dauke da babban Faranti cike da kayan marmari, ta aje a center table, ta koma kusa da mijin ta ta zauna, ta sha ado ba ka ce ita ta haifi Su Nasreen ba, Baban Hinde ne tai gyaran murya, sannan ya fara da" Assalamu alaikum" waalaikumussalam " kowa ya amsa harda masu tsamin baki," Da farko dai ina mai miqa godiya ta ga Allah mai kowa mai komai daya nuna mana wannan rana, mai cike da dinbin tarihi, domin wannan rana ce ta farko da dukkan mu muka taru anan, don sada zumunci, na gode maku a matsayin ku na kasancewa zuria ta gaba daya, kuma ina mai godewa allah daya amsa addua ta, a kullum ganin halin da zuria ta ta shiga a baya, ya sa ba dare ba rana nake adduar Allah ya shiryan ku, to ga shiriya da albarka ta same mu baki daya, ina fatan kowa iyanzu ya fuskanci kuskuren shi, ya kuma dau damarar gyara da neman gafarar Allah, nasihata gare ku iyaye mata da maza, ku so yayan ku, kar ku nuna banbanci, ba yanda za ai ka haifi yaya ka so su duk so daya, dole akwai wanda ka fi so, amma ana son ka batwa zuciyar ka, karka nuna masu, ka ba su tarbiyya iyakar iyawar ka, ku ilmantar da su? Addini da zamani, ku maida su qawaye abokai , domin su sake da ku kuji damuwae su suji taku, ku san qawayen su su waye da abokan su, ku na masu nasiha lokacu zuwa lokaci ku guji munana zato akan su, ku guji zargin su akan wani abun da baku tabbatar va, ku guji tsangwama da aibata su" in taqaice maku masu karatu ranar Baban Hinde har da Malam Liman ya sa hawaye, dimin ya wa'azantar da su ba kadan ba, ya nuna masu rayuwa da yanda take, daga qatshe kowa ya qara neman yafiyar kowa, tambaya Na'eema ta watsowa Mummyn su" Mummy yaushe zaki haihu" kallon jama'ar wajen Nasreen tai ta shafa kant cikin kunya tace nan ba da jimawa ba sweery" to Mum meye sunan Baby in kin haihu?" Hmmmmmm to wannan kuma ki tambayi yayan ku" wajen shi ta nifa da gudu amma kan taje Ni'ima ta riga ta" Yaya yi sauri ka fadan sunan pls" dariya wajen ya dauka " sunan baby in mace ce Hameeda, in na miji ne Abdul Hameed" yeeeehhhhhhh na riga ta ji" aiko zagaye palon suka hau yi tana bata yarda ba ita saita biya ta jin da ta riga ta, dariya kowa yake cike da farinciki da nishadi.</p><p>ALHAMDU LILLAHI RABBIL ALAMIN </p><p>INA MIQA GODIYA TA GA DIMBIN MASOYAN WANNAN NOVEL AGAIN NA GODE DA QAUNA DA KUMA KULAWA BAN ZATA BA , BAN TABA ZATON NOVEL DINNAN ZAI MASOYA HAKA BA AMMA GODIYA TA TABBATA GA ALLAH , INA FATAN ABINDA MUKAJI NA DAIDAI MUI AMFANI DA SHI SABANIN HAKA MU GUJE MASA, INA RIQON ALLA DAYA GAFARTA MIN DA KU BAKI DAYA YA KUNA BANI LADA A INDA NAI SAIDAI YA MIN AFUWA A INDA NAI KUSKURE. INA QAUNAR KU DOMIN ALLAH INA FATAN KUMA DIMIN SHI KUKE QAUNATA BA DAN HINDE KO INNAR TA BA😂 </p><p>Ga masu tambayar novel tindaga farko kuma pages dan Allah sui hakuri ba zai samu ba wayata na riqewa in ina tura pages wallahi, amma inshaa Allahu zan mai da shi docment nan ba da jimawa ba inshaa Allahu. Tanx for d love, me love u too❤</p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-41668530382956842392021-03-06T05:21:00.001-08:002021-03-06T05:21:43.123-08:00MATATA GIMBIYATA COMPLETE HAUSA NOVEL<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-J63ezQbY9xQ/YEOBgs1QKJI/AAAAAAAAJlI/D8hfzB0f3kIpwxhzpeiwI-1mLsfdjzYVQCLcBGAsYHQ/s2048/MATATA-GIMBIYATA.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="MATATA GIMBIYATA COMPLETE HAUSA NOVEL" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-J63ezQbY9xQ/YEOBgs1QKJI/AAAAAAAAJlI/D8hfzB0f3kIpwxhzpeiwI-1mLsfdjzYVQCLcBGAsYHQ/w320-h248/MATATA-GIMBIYATA.jpg" title="MATATA GIMBIYATA COMPLETE HAUSA NOVEL" width="320" /></a></div><p><br /></p><p></p><p>[9:09PM, 8/3/2017] +234 806 677 6651: 🌸💦 MATA TA , GIMBIYA TA!! 🌸💦 </p><p> 💘 MY WIFE ,MY PRINCESS 💘</p><p><br /></p><p>Story by</p><p>JEEDAH JA'O</p><p><br /></p><p>WRITTEN BY</p><p>FEEDOH DEEDOH</p><p><br /></p><p>EDITED BY</p><p>ROOKIEY KAXS</p><p><br /></p><p>Bamu yarda wani ko wata ya juya muna labari ba yin haka babban kuskure ne, kuma muka kama mutum zai fuskanci hukunci..</p><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p>BISMILLAHI RAHMANIR RAHIM</p><p><br /></p><p> 1⃣➖2⃣ dole sai kin aure shi </p><p><br /></p><p> Attitude miss DEENAH ISMAEEL!! am talking to you right here as a father! Idan da uban ki ne yayi wannan maganar ai babu musu zaki yarda , amma dayake ni kin raina min wayau tunda ba ni na haife ki ba ,shine bari ki nuna min halin ki na y'an duniya ko? Shegiya da ido kamar dattijon biri!!" </p><p> Uncle Khamis ne ke maganar cikin hasala , daga gani ranshi a b'ace yake.</p><p><br /></p><p> Amma Uncle how can you make such drastic decision without my consent? Maganar aure na fa kuke yi! Kuma hakan ma da mijin da ban tab'a gani ba! That too mai shekaru irin na ubana!" Deenah ta fad'a tana mai d'aga hoton wani dattijo wanda zai yi about 49 yrs ,idanun ta taf da hawaye.</p><p><br /></p><p> Ke uwaki! Kin ci uwaki nace!! Har yanzu ashe baki rufe bakin ki ba? Munafuka ke a yanda kike har wani zab'e zakiyi ? Mutum a kod'e kamar fentin white house. Aure de kamar anyi an gama! In ma zaki mutu a chan ne kije ki karata ,Yarinya ta d'ebo duk munafurcin uwarta, Tashi ki bani waje ko nayi majejewa dake a nan wajen Shashasha!" Cikin tsawa Uncle yayi maganar hakan ya tsoratar da Deenah ba kad'an ba kamar zata kifa ta mik'e da gudu ta fice daga falo idanuwa sharbe sharbe da hawaye.</p><p><br /></p><p>DEENAH ' s POV ....</p><p><br /></p><p> Da gudu na shigo d'aki kaina babu abunda yake yi se uban sarawa , fad'awa nayi a kan gado gami da bunne fuska ta cikin pillow babu abunda nake se faman kuka!</p><p>Shikenan nima haka rayuwa ta zata kasance kenan? Babu y'ancin kai babu sukuni ,tabbas k'unci ya aure ni , a rayuwa ban san lokacin da farinciki zai dawo min ba, gashi ina cikin kadaici babu kafad'ar da zan dafa in yi kuka , babu uwar da zata rungume ni yanda uwata ta fad'i ta mutu a cikin wahala da k'uncin rayuwa haka nima zan kasance. </p><p><br /></p><p> Kuka na ne ya tsananta sosai na mik'e zaune na nad'e kafata gami da d'aura kaina a gwiwa, My dreams are shattered already ! My dreams of being a physiotherapist is no longer trending! Am gonna end up like my own late mother! Married! Becomes the cook of the family , get pregnant, have no time for herself but for the husband and then after some times she end up heart broken by the man she called husband and in the end! Died and left me in the hands of the most wicked step mom! Bayan wannan kuma nima Y'ata ko yayan da zan haifa zasu kasance a hannun wata uwar daban kamar yadda na kasance ,daga nan kuma suma ayi forcing musu auren dole kamar dai ni ,haka abun zaita zagayawa! Tir da wannan rayuwar!" </p><p><br /></p><p> Jin an k'ira sallar azahar yasa na mik'e ina k'ok'arin bud'e kumburarrun idanuwa na da 'kyar na fad'a bayi ,bayan nayi wanka na dauro alwala sannan na fito direct closet na wuce na d'auko wata long sleeve Anarkaali dress na zira sannan na d'aura hijabi na fuskanci kibla domin gabatar da sallah! Na dad'e sosai a sujjada ina kai kuka na ga Mahaliccin mu ,ina rok'on yasa wannan auren da za'a min in babu khairan cikin sa yayi watsi da shi ya kuma sauya min da alkahairi " bayan na idar da sallah sannan na koma kan katifa ta na kwanta naci gaba da business d'ina wato kuka" </p><p><br /></p><p> UNCLE KHAMIS POV........</p><p><br /></p><p> Deenah tana shiga ya dubi Aunty Hadiza ( his wife) </p><p><br /></p><p> Wallahi ba don gudun bakin jama'a ba! Da sai na batar da wannan yarinyar! Wai yanzu har tana da bakin da zata iya sa in sa da ni? Har zata iya musayar miyau da ni tsabar rainin hankali? Shegiya fuska kamar an silala karas! Lallai seta yaba wa aya zakin ta! Aure kamar an d'aura " </p><p><br /></p><p> Aunty Hadiza se yanzu tai magana " ai Alhaji ka barni da ita! Kafin a kaita ma sena sauya mata kamanni! Ni d'in de take ji yanzu zan nuna mata true colors d'ina" </p><p><br /></p><p> Ai nasan zaki yi fiye da haka! Mudai mu tura ta chan ko zamu samu hujjar cin wannan makudan kudaden da yaya ya bari , ni bazan bari wannan kyanwar ta kwashe min dukiyar d'an uwa ba,ai da kika ga ina sassauta mata kwana biyu ai sassautawar ta raka taki gona ce! Kinsan idan muka sake wani abu ya gifta Baba Yaji cewar bata son auren komai zai lalace!" Sosai Aunty Hadiza ta kufce da dariya sannan Uncle ya mik'e domin zuwa masallaci...........</p><p><br /></p><p> *************** </p><p><br /></p><p> Deenah! Deenah!! Kut amma wannan yarinyar anyi y'ar kwal uba! Shine ina ta kwala mata k'ira kamar bata nan? Ni wallahy satin ma yayi yazo mu tura ki chan! Mu yada kwallon mangwaro mu huta da kuda! " </p><p> Da gudu ta shigo kitchen d'in jiki na rawa kamar zata mutu se haki take yi " kiyi hak'uri aunty wlhy sallah nake yi shiyasa b....." </p><p><br /></p><p> Ta dakata sanadiyyar wata tsawa da A Hadiza ta yi ,jiki na b'ari tayi gum da baki . " Sannu sayyada wato zaki nuna min kin fini iya addini ko? Ke gaki musulma! Munafuka kawai ,tsabar renin hankali ni zan d'aura girki a gidan nan yau? Shine har kina son yin k'arya d'a addini " ta kwada mata ludayi a tsakiyar kai , wannan ya sanya Deenah rik'e kai hannu biyu tana hawaye tsananin sara mata yake yi amma babu yanda zata yi ,don in da sabo ta riga ta saba" </p><p><br /></p><p> Tunkude ta tayi da k'afa ta wuce zuwa falo tana ta banbami ita kuwa Deenah babu b'ata lokaci jiki na rawa ga uban yunwa ga ciwon kai ta mik'e ta hau k'ok'arin daura dinner.........,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>©M@J@H </p><p>F💘J💘R💘</p><p>[9:10PM, 8/3/2017] +234 806 677 6651: 🌸💦 MATATA GIMBIYATA!! 🌸💦 </p><p> 💘 MY WIFE MY PRIINCESS</p><p><br /></p><p>STORY BY</p><p>JEEDDAH JA'O</p><p><br /></p><p>WRITTEN BY</p><p>FEEDOH DEEDOH</p><p><br /></p><p>EDITED BY</p><p>ROOKIEY KAXS</p><p><br /></p><p>NAGARTA WRITERS ASSOCIATION </p><p><br /></p><p> 3⃣➖4⃣</p><p><br /></p><p> Zaune suke kan brown mahogany wood dinning table yayinda Deenah ke faman serving d'in su , duk idanun su a kanta ne ita kuwa jiki na rawa take faman zuba abincin. </p><p>Wani dogon saurayi ne ya shigo ak'alla zai kai 23 yrs ya sha kayan thugs harda knuckles ring , ya baje a falo yana kallon su a dining area </p><p><br /></p><p> "Ke"! Ke Munafuka zo nan! sunan kenan da kowa ke k'iran Deenah dashi shima ya k'ira ta , luckily ta kammala zuba musu abincin dan haka ta saka gudu ta nufi inda yake ta durk'usa gaban sa</p><p> An gaya miki kyau ne dake da zaki wani zo ki zaune min a gaba? Kazama tashi min ki had'o min coffee yanzun nan! Ba b'ata lokaci ta ruga zuwa kitchen su A. Hadiza kuwa se dariya suke yi khairat ma tana ta aika loma ko d'ago kai bata yi ,idan akwai worst mak'iyan Deenah toh bai kai khairat ba.</p><p><br /></p><p>DEENAH's POV .......</p><p><br /></p><p> Cikin minti uku na kammala masa komai na d'aura coffee mug d'in a kan saucer sannan na saka teaspoon a gefe na ajiye two cubes of sugar na fito cikin rawar jiki na mik'a masa </p><p><br /></p><p> Kurb'a d'aya kawai yayi kafin na ankara se ji nayi an watsa min hot coffee a jiki Allah yaso bai sami fuska ta sosai ba. Wurgi yayi da kofin in my direction hakan yasa na sunkuya cike da tsoro yayinda cup d'in yaci karo da marble floor a take ya yi dagadaga , ban ankara ba naji anyi Ball dani da k'afa hannaye na biyu duk na dafe su kan fashasshen kwalban ,kuka na ya tsananta naji duk na tsani wannan rayuwar . </p><p> ke wato kin maida ni sa'an ki ko? Munafuka! Wato ni kike so in zuba sugar a coffee d'in da hannu na? Wannan d'in sabon falli ne ko kuma me? Sa'an ki d'aya yau y'an mutunci na suna nan Amma ai kin sanni sarai! Zan had'u dake anjima! Duk maganganun da Yaya SAEED yake fad'a kawai jin su nake domin na saba ,bayan ya juya ya fice ne na mik'e na d'aure hannu na sannan na fara aikin kwashe kwalaben , ban jima da gama wa ba Aunty ta kwala min k'ira</p><p><br /></p><p> Tana daga zaune kan dining chair tana d'aukar sauran abincin da suka rage a plate ta had'a a plate d'aya sannan ta ajiye a k'asa tayi wurgi da shi da k'afa , da sauri na d'auka na keb'e a lungu ni kad'ai se daka loma nake! Wannan ma yau d'in taga dama ne don wata rana abincin da ake dafawa karnukan gida shi take cewa naci amma duk muguntar ta babu abunda ya sameni har mayya take k'ira na!</p><p><br /></p><p>***********</p><p><br /></p><p> Yau jumma'a yau ake shirin d'aura min aure da mijin da ban san shi ba balle halayen shi, keep maganar ko yana kaunata aside don nasan ba makawa wannan auren ba na soyayya suka had'a min ba, sannan hoton da suka bani dattijo ne mai kimanin 49 yrs who knows mata nawa yake da su? This taught filled my heart to the extend that yau ko kuka ma na kasa yi, tear duct d'ina ya daina zubar da ko d'igon ruwa, babu abunda nake banda dua ina kai kuka na ga mai duka mai kowa mai komai!</p><p><br /></p><p> Yayinda kowa yake murna a cikin gida , ina k'unshe a d'aki na had'a kai da gwiwa. Wata tsohuwa ce ta shigo tare da Aunty , ta inda suka shiga ba nan suke fita ba wai nasiha , " In har kikayi wani kuskure auren ya mutu toh lallai ki nemi wani wajen ba nan ba!" Kalaman ta kenan na k'arshe daga nan tsohuwar ta d'aga ni muka fita.</p><p> Wani ikon Allah ban tab'a ganin aure haka ba! Babu kayan daki babu komai daga ni se ni kamar wanda suka bada ni sadaka , daga nan ne kuka na ya karu ban san cewa akwai sauran hawaye a idanuwa na ba se lokacin da ake fitar da ni daga gidan ubana mahaifi kamar ana kora ta! Babu wanda zan yi wa kuka yaji ni! Haka suka saka ni a mota ba tsimi babu dabara Aure de an d'aura! Ango of which i regard to as mr unknown!!</p><p><br /></p><p> K'arfe 3:30 pm </p><p>At BEN KALIO HOUSING ESTATE </p><p>DAMATURU YOBE STATE......</p><p><br /></p><p> Wani makeken gate muka ratsa driver ya yi parking daidai entrace ,jiki na rawa yake yayinda na sako k'afa daga mota ,daga cikin dupatta na ( gyale na ) ina iya hango fuskokin su d'aya bayan d'aya </p><p><br /></p><p> Cikin zuciya nace " What a family ! Look how happy they seems ! Basu san yadda nake ji ba wlh da sun sani non of them will give such a wide grinn</p><p><br /></p><p> Har cikin main falour akayi leading d'in mu finally na tsinci kaina zaune kan lallausan italian carpet , haka dai suka sani a gaba suna ta surutu wancan yace kaza wancan ma haka </p><p><br /></p><p> Hmmm da kun san yadda nake ji a raina game da auren nan lallai baza ku b'ata lokaci ba! I mean like seriously? Har ma farin ciki sukeyi wanda na kasa fahimtar me yasa , uwar ango harda hawaye. </p><p> A raina nace " amma de wannan matar ai d'an nata indai shine nagani a hoto ai yafi ta tsufa!" </p><p><br /></p><p>Maganar mahaifiyar sa ne ya dawo dani daga nannauyan tunani da na tsunduma </p><p><br /></p><p> Y'ata ya kamata ki huta , gobe in sha Allah zaku wuce a kaiki d'akin ki! Na gode miki sosai domin mata irin ku kad'an ne a duniya wanda duk da kunji yanda mutum yake kuke amincewa kuyi abu don Allah! Ni na san in Allah ya yarda Allah zai baki ladan abunda kika yi" </p><p><br /></p><p> Ba tare da na fahimce ta ba nayi murmushi gami da amsawa da Ameen daga nan aka kaini wani d'aki inda nan ne na zauna nida wasu y'an mata biyu muna ta hira har bayan isha muka kwanta!</p><p><br /></p><p>Zan iya cewa yau ne rana ta farko bayan rashin iyaye na da na tab'a kwana cikin dad'in rai da kwanciyar hankali! Amma tunani d'aya tak ya hana ni sukuni!</p><p><br /></p><p> Is it because d'an nata tsoho ne? Ko kuma dan na yi auren dole ba tare da wani musu ba? Or akwai wata matsala ce? Kuma how sure am i, wannan Dattijon shine wanda aka aura min?" Wannan tunani dashi nayi bacci ...............</p><p><br /></p><p>© M@J@H</p><p>F💘J💘R 💘[9:09PM, 8/3/2017] +234 806 677 6651: 🌸💦 MATATA GIMBIYATA!! 🌸💦 </p><p> 💘 MY WIFE MY PRINCESS 💘</p><p><br /></p><p>STORY BY</p><p>JEEDDAH JA'O</p><p><br /></p><p>WRITTEN BY</p><p>FEEDOH DEEDOH</p><p> (NWA)</p><p><br /></p><p>EDITED BY</p><p>ROOKIEY KAXS</p><p><br /></p><p> 5⃣➖6⃣ </p><p><br /></p><p> Kiran sallah ne ya tashe ni , a hankali nake bud'e idanuwa na ina mai k'arewa d'akin kallo wanda yanzu kam duhu ne cikin sa a kasalance na kai hannuna kan switch na bedside lamp ina zaune bakin gado ina tuna abubuwa da dama da suka faru yayinda hannaye na suke shawagi cikin messy gashin kai na bayan nayi alwala nai sallah na rok'i mahalicci ya min jagora a wannan alamari , ban tashi daga sallaya ba wata mata ta shigo d'akin da sallamar ta tace " Amarya ga abinci nan ki ci sannan ki shirya da wuri don yanzu zaku wuce " kai kawai na girgiza domin bani da wata ja akan maganar se yanda aka yi dani. Da murmushin ta tafita yayinda na maida dubana ga abincin! Tunda na taso ban tab'a ganin ranar da aka had'a min breakfast irin wannan ba hasalima sedai in ci ragowar yan gida Tsakanin jiya da yau se naji am like free! Yau gashi na wayi gari na tashi cikin nutsuwa babu tsawar Aunty hantara daga yaya Saeed da kuma khairat ! It feels new to me!......</p><p> Bayan na kammala breakfast sannan na shiga bayi na sakar wa kaina shower ban d'auki dogon lokaci ba na fito just to find out kaya na yana jira na a kan gado had'e da tsadadun turare guda biyu ga kuma wani simple gold jewelry ajiye a gefe ban san wanda ya ajiye su ba don haka na shafe jiki na da mai na zauna ina jiran shigowar wani, and luckily se ga matar d'azu ta dawo .</p><p><br /></p><p>" Yawwa kin fito ashe?"</p><p>Tace, "eh nafito"</p><p><br /></p><p> Wad'annan kayayyakin ki ne driver is almost ready ki shirya bari inyi magana da umma kafin nan, nan ma dai kai na girgiza fuska ta d'auke da murmushi sannan ta fice.</p><p><br /></p><p> Doguwar riga ce long sleeve "ja" bodice d'in kuwa black and golden lace ne haka ma boader d'in hannun da kuma borderline na rigar , rigar ba karamin had'uwa tayi ba ni kaina saida nai kauyanci sannan na saka ba wani heavy makeup nayi ba yafa black and gold kashka dupatta nayi sannan na fito zuwa falo bayan yan nasiha da kuma godiya daga mahaifiyar sa wanda ni kaina ban san dalilin yin su ba finally na tsinci kaina cikin wata bak'ar Mercedes Benz muka hau hanyar Maiduguri abun takaicin ma shine daga ni se driver , an saka ni a owners kamar wata matar shugaban k'asa ! To be frank wannan rayuwar bak'uwa ce a gareni...........</p><p><br /></p><p> Bayan tafiyar Awa d'aya da yan mintina suka iso garin Maiduguri direct Airport driver ya direta , to her surprise wai Abuja za'a kaita thank God i know something about Flight and stuffs ! Abunda ta iya fad'a kenan, cikin minti goma jirgin su ya d'aga zuwa Abuja ................</p><p><br /></p><p>*************** </p><p><br /></p><p> A yayinda motar ta tsaya idanuwa na rufe suke ina tuna irin abubuwan da suka faru da ni a baya, tabbas nasha wuya gashi kuma an had'a min aure an katse dukkan mafarki na maganan driver ya dawo dani daga tunanin danake yace "Ranki shi dad'e mun iso " kafin na bud'e k'ofar har ya bud'e min karo na farko a rayuwa ta naci karo da Mansion wanda ya amsa sunan shi Mansion ! Daganan zuciyata ta fara raya min abubuwa guda biyu! Kodai sun aurar da ni don su kwashi arzik'i ko kuma sun aurar da ni don in zama baiwa! Domin ban ga me mai kud'i wanda ya ajiye wannan masarauta in the name of mansion zai yi da low class gal iri na ba! Gaba na fad'uwa ya fara yayinda na juya naga nisan dake tsakanin gate da main House d'in.</p><p> Gida ne nagani na fad'a tall French windows ne suka fara min sallama ya d'auke ni lokaci kafin na fahimci k'ofar gidan daidai lokacin ne wannan tsohon da ke jikin hoton nan ya fito daga cikin gidan yana washe hak'ora " Barka da zuwa ranki shi dad'e ! Ki k'arasa ciki master yana jiran isowar ki tun d'azu , kiyi hakuri da kalaman sa, ba haka yake ba kafin yanzu, larura ce, kuma magana d'aya master yake yi bai cika son shishigi ba. Ummmm kiyi hak'uri madam amma dole ne inyi miki sharar fage a kansa domin he's hard to be with ina son ki kasance mai hak'uri don Allah! Zaki iya shiga.." </p><p><br /></p><p> Like seriously? Wai sharar fage aka yi min akan Master? Wai wane irin game ne wannan? Tsohon da nake tunani shi aka malkala min ba shine miji na ba wani ne daban? Yanzu kam na tabbatar ko daga maganar tsohon nan cewa zaman bauta nazo yi ba na aure ba.......</p><p><br /></p><p> Mahmoud i told you for the last time i don't need any body's help! Ni bana son wannan auren! Naji am paralyzed amma kuma i can use my hands banga amfanin kawo min wata mayaudariya a matsayin mata ba! Ko baka gani ba yadda Zeenat ta watsa min 'kasa a ido? To hell with this married! Now get the hell out of my sight! Ka b'ace min da gani nace!!!" Abubakar SADEEQ IMAM kenan yayi maganar cikin tsaya yayinda ya yi watsi da tray d'in abincin dake gaban shi yana mai k'ok'arin juya akalar wheelchair d'in shi. Mahmoud PA d'in shi ne , tunda larurar ta samu Sadeeq yake iya k'ok'arin shi don yaga ya samar wa mai gidan shi kuma Aminin shi kulawa ta musamman ,amma with every day temper d'in Sadeeq karuwa yake a yanzu babu kalmar da ya tsana irin ya mace.....</p><p> Daidai lokacin na shigo falon kenan hasalima tray d'in abincin saida ya kusan fad'o min a fuska domin da iya k'arfin shi ya wurga, ban san lokacin da na saki ihu ba gami da sunkuya wa jiki na yana rawa, " What the jahannam" Wannan shine master d'in? Allah sarkin Halitta tabbas ko daga zaunen da yake yi bai bani wahala wajen tantance cewa shi dogo ne ba yanayin fuskar sa square shape ne mai d'auke da madaidaitan oval shaped eyes, hanci kuwa kamar zai shige baki, gashin kansa bak'i ne ga dukkan alamu mutum ne wanda yake barin suma a ka ga wani side box bak'in k'irin , gashin idonsa kuwa badon namiji bane zance fixing yayi ga kuma cikar gira daga hannun sa zaka gane cewa maji k'arfi ne kuma ga dukkan alamu baya wasa da nutrition nashi, tabbas Sadeeq yakai namiji ta fannin sura ina ma ace zuciyar shi haka take da kyau? Domin yayin da na had'a ido dashi karo na farko kallon da yayi min ji nayi kamar an jefa ni cikin wuta, a take naji zufa ya karyo min duk da de yaya Saeed mugu ne tabbas wannan ya fishi razanar wa!!</p><p><br /></p><p> Cikin husky voice nashi yace " Dubi Tray d'in ba kanta yayi ba amma tana cilla ihu wannan ne kake tunanin zata kula da ni?" Oh! For God sake me kake tunani Mahmoud? Mace will remain mace in as much as am concerned so pls before i vomit ka d'auke min wannan dirty figure d'in a gaba na !!" Jiki ba kwari Mahmoud ya nuna wa Deenah hanyar d'akin ta......</p><p><br /></p><p> Cikin kuka mai tsanani na zube a kan makeken gadon dake d'akin ina zubar da k'walla ga uban yunwa da kishirwa amma sam babu abunda nake tunawa se irin wahalar da zan sha a wannan prison d'in don lallai ba makawa am in a dungeon! Wannan shi ake kira ba'a rabu da bukar ba an haifi Habu!!</p><p> Kiran sallar Azahar ne ya tasheni daga nannauyan baccin da nake wanda bashida maraba da baccin dole a lokacin ne idona yayi capturing view d'in d'akin Masha Allah shine kalmar da bakina ya fara furtawa yayinda k'afafu na suka saukaa a kan lallausan posh italian carpet ja dake d'akin , daga glass ne dogin French windows ina iya hango had'adden balcony wanda akayi decorating karamin space d'in shi da Arabian lamps da kuma Arabian darduma lallai kudad'e suna inda suke.! </p><p><br /></p><p> Bathroom na shige direct don gabatar da alwala ta amma me? Yayinda naci karo da full length mirrows ga wani chandelier a tsakiya me golden light ,k'ark'ashin sa kuwa jacuzzi ne makeken gaske infact da kyar na iya yin alwala na fito don i prefer the bathroom than the bedroom seriously! Its breathtaking!! And mind blowing!!!.............</p><p><br /></p><p>© M@J@H</p><p>F💘J💘R💘</p><p>[9:10PM, 8/3/2017] +234 806 677 6651: 🌸💦 MATATA GIMBIYATA🌸💦</p><p><br /></p><p>💘 MY WIFE MY PRINCESS💘</p><p><br /></p><p>STORY BY</p><p>JEEDDAH JA'O</p><p><br /></p><p>WRITTEN BY</p><p>FEEDOH DEEDOH</p><p> (NWA)</p><p><br /></p><p>EDITED BY</p><p>ROOKIEY KAXS</p><p><br /></p><p> 7⃣➖8⃣</p><p><br /></p><p>ASALIN LABARIN</p><p><br /></p><p> Alh Umar haifaffen d'an damaturu ne yana da mata d'aya mai suna Zainab da yara biyu, Khamees ne babba sannan Ismaeel shine k'arami. Bawani kud'i Alh Umar kedashi ba saidai rufin asiri, amma duk da haka yaba yaranshi ilimi boko da arabiya.</p><p> shekarar da khamees yagama university Allah yayima mahaifinsu rasuwa ba k'aramin razana sukayi ba kwanan Alh umar talatin da rasuwa Hajia Zainab ta bishi sunyi kuka kamar zasu rasa ransu amma daga baya suka dangana suka barma Allah komai, daga nan Khamees yafara kasuwanci ganin yaba ma d'an uwanshi ilimi, ana haka Allah ya had'a Khamees da Hadiza bai tsaya bincike ba kawai ya aika neman aurenta kuma iyayenta suka amince, cikin kwanaki k'alilan akayi bikin Khamees da Hadiza..</p><p><br /></p><p> Kulawa sosai suke ba Ismaeel daga Khamees har Hadiza, Ismaeel na 300level Hadiza ta haifi d'an ta mai kama da babanshi sak, zoka ga murna wajen Ismaeel ranan suna yaro yaci suna Saeed, tun daga nan rainon Saeed ya dawo hannun Ismaeel. cikin ikon Allah Ismaeel har yagama karatunshi bai samu wata matsala ba.</p><p> Tunda Ismaeel yagama makaranta Khamees yabashi dukiyarshi ta gado nan Ismaeel yafara business import and export, ma'ana yana kai atamfofi materilas Ghana, South Africa yana kuma kuma shigo da nasu Nigeria cikin ikon Allah kasuwancin ya karb'eshi saboda yafi yayanshi nan fa Khamees da Hadiza suka fara yimashi hassada amma bai tab'a canja masu ba kuma komai nashi idan yasamu Saeed...</p><p><br /></p><p> Ismaeel ne tafe cikin motarshi saurayin d'an matashi kenan maiji da naira, tsaye suke bakin titi da Alama abun hawa suke jira, har ya wuce yadawo sallama yamasu amsa mashi tayi yace "yanmata ina zaku haka?" Murmushi tayi tace "wlhi kaganmu nan bak'ine mu biki mukazo shine muke neman abin hawa ya kaimu can gidan bikin" kallon su yayi tabbas ba yan garin baneba, daga wane gari kuke? Tambayar da yamasu kenan, Kausar tace "Maiduguri" murmushi yayi yace "toh kunsan gidan?" Girgiza kai tayi amma muna da address d'in, toh karku damu in shaa Allah zan kaiku godia ta mashi, sai a sannan d'ayar tayi magana, haba kausar taya zamu bi mutumin da bamu sani ba? Nikam ba inda zani, murmushi yayi karki damu yanmata niba mugu baneba trust me. Dakyar aka samu ta shiga motar...</p><p> Tunda suka shiga mota Ismaeel ke masu surutu kausar na tayashi, amma d'ayar k'ala bata ceba, kallon Kausar yayi yace "wai yar uwarki bata magana ne? Ko maganan tsada takeyi" murmushi tayi karkadamu miskila ce haka take dariya yayi yace "aikam yau ta had'u da d'an naci" itadai bata ce komai ba, har suka iso gidan biki godia Kausar ta mashi girgiza kai yayi babu komai fita zasuyi yayi lucking motar juyawa yayi yace "baiwar Allah dan Allah ki daure ki gayaman sunanki" a dak'ile tace mashi "Falmata" lumshe ido yayi yace "nice name" bud'e motar tayi ta fita, exchaging contact sukayi shida Kausar kana sukayi bankwana....</p><p><br /></p><p> Falmata bata bar damaturu ba saida soyayya mai k'arfi ta shiga tsakaninta da Ismaeel, randa Ismaeel yajema Khamees da maganan auren Falmata nan yace mashi bazai aure ta ba akanmi zai auro yar maiduguri kowa yasansu da mallake namiji, nanfa Ismaeel yace "shikuma baiga matar aure ba sai Falmata"</p><p> Bai ankara ba yaji saukari mari a kuncinshi dafe kunci yayi idon shi ya kad'a yayi ja kamar an watsa mashi barkono, tab'e baki Hadiza tayi tace "aidama nasan za'ayi haka tunda yace zai auro yar maiduguri komai zaiyi" saboda kowa ya sansu da mugun asiri, girgiza kai Ismaeel yayi ya fita daga gidan....</p><p><br /></p><p> Fitar Ismaeel bai zame ko ina ba sai gidan yayan babansu, cikin ikon Allah kuma ya sameshi nan ya gaya mashi komai, murmushi yayi yace "ka kwantar da hankalina in shaa Allah anyi auren nan angama" shida ya auro wadda yakeso wani ya hanashi? Gashi tunda ya auro ta ya daina mana abinda yake mana komai daga ita sai danginta, kaje kawai zanzo na sameshi har gida, godia Ismaeel yayi sosai bankwana yamashi ya aje mashi kud'i masu yawa ya tafi..</p><p> Har gida kawu ya sami Khamees yamashi tatas, kuma ya shaida mashi aure ba fashi jibi ma in shaa Allah za'a kai kud'in neman aure kuma dashi za'a kai, ba yanda Khamees ya iya dan dole ya amince, kallon kawu yayi yace "Kawu amma dan Allah Ismaeel karyayi nisa dani ya zauna d'ayan part d'in can" Kawu yace "bakomai zan mashi magana Allah yamaku albarka" amsawa yayi da Amin,...</p><p><br /></p><p>© M@J@H </p><p>F💘J💘R💘</p><p>[9:11PM, 8/3/2017] +234 806 677 6651: 🌸💦 MATATA GIMBIYATA💦🌸</p><p><br /></p><p>💘 MY WIFE MY PRINCESS💘</p><p><br /></p><p>STORY BY </p><p>JEEDDAH JA'O</p><p><br /></p><p>WRITTEN BY</p><p>FEEDOH DEEDOH</p><p> (NWA)</p><p><br /></p><p>EDITED BY</p><p>ROOKIEY KAXS</p><p><br /></p><p> 9⃣➖🔟</p><p><br /></p><p> Kawu na isa gida ya kira Ismaeel a waya, ba'a jima ba sai ga Ismaeel bayani kawu yamashi yanda sukayi da Khamees saida kawu ya nisa kana yace "Ismaeel Khamees ya rok'eni alfarman ka zauna d'ayan part d'inshi ni kuma na amsa mashi" da sauri Ismaeel ya d'ago, murmushi kawu yayi yace "karka damu Ismaeel in shaa Allah ba abinda zai samu matarka" sai a sannan yayi magana yace "to kawu gidan fa da na gina?" shiyasa nace karka damu bawai zaku zauna ba nan har abada ni da kaina zan umurceka da kukoma gidanka, ba yanda Ismaeel ya iya haka yama kawu bankwana yatashi ya fita...</p><p><br /></p><p> Ba a d'auki lokaci ba su Kawu sukaje neman Auren Falmata, gaskia sun ga kara saboda an amshe su hannu biyu, abun har ya dinga ba Khamees mamaki, amma duk da haka tsanar Falmata na nan cikin ranshi bare da yaganta, nan su Kawu suka nemi aure kuma aka basu dangin Falmata suka yanka sadaki dubu hamsin nan take Kawu ya biya, aka tsaida biki sati hud'u da yake ko wane b'angare a shirye suke, kwanan su kawu d'aya suka dawo damaturu cike da karamcin mutan maiduguri....</p><p> Tunda Kawu ya gayama Ismaeel an bashi Falmata kuma an biya sadaki yake cikin murna, lefe ya had'a naji da gani yana kawowa gida Hadiza da Khamees sukace yayi yawa dole sai ya rage nan fa suka fara rigima har saida Kawu ya shiga maganan ya kuma hana a rage, a cewar shi kowa rabonshi yake ci dan haka baiga illar dan miji yama matarshi sutura ba, dan dole Khamees da Hadiza suka kyale lefen ba dan ransu ya so ba...</p><p><br /></p><p> Tun da bikin yazo Ismaeel baya zama, Khamees har mamaki yakeyi yanda Ismaeel ke rawan kai a bikin nan Hadiza tace "ba dole yayi rawar kai ba tun da ya auro mana dangin asiri" ba ayi wani event ba kasancewar Falmata bata san wani event ko d'aya ba yanda Ismaeel ya iya walima kawai sukayi, ranan juma'a aka d'aura aure ana gama d'aura aure aka taho da amarya damaturu, kwanan yan kai amarya d'aya dama turu suka juya maiduguri....</p><p> Hadiza ce tsaye bakin k'ofa tana kwalama Falmata kira ke! Da sauri ya fito kallonta tayi shek'ek'e tace "wakika aje da zai maki gyaran gidan? Dallah fito malama kifara aikinki kina tunanin hutu kika zoyi to bauta kikazo yi" bata ce komai ba ta bita sharan gidan tafarayi tana gamawa ta d'ora girkin kitchen Ismaeel ya tarda ta nan fa yafara masifa, kallonshi tayi da murmushi tace "karkadamu mijina bautan aure nakeyi dan Allah karka masu magana kaga gaba suke damu dole mu bisu". Tunda nazo gidan nan nagane Anty Hadiza da ya Khamees basu sona amma kullum burina na kyautata masu harta Saeed sun dasa mashi k'iyayyata, kwantowa yayi bisa jikinta yace "kiyi hak'uri in shaa Allah kwana kad'an zamu koma gidanmu" murmushi tayi ta cigaba da aiki..</p><p><br /></p><p> Tunda Falmata ta samu ciki take fama da laulayi kullum cikin amai take, amma duk da haka dole sai tayi aiki ba abinda ta dainayi, kullum kuma cikin kwantarma Ismaeel take da hankali akan karya damu..</p><p> Wata tara cif ta sankato d'iyarta mai kama da ita, tunda aka haifeta Ismaeel yake cikin farin ciki, a yayinda Khamees da Hadiza ke cikin bakin ciki..</p><p><br /></p><p> Ranan suna yarinya taci suna DEENAH bayan suna Ismaeel duka k'adarorinshi ya maidasu sunan Deenah, nan fa hankalin Khamees da Hadiza ya tashi, babu yanda basuyi ba dan suga sun kauda Deenah daga dunia amma Allah bai basu iko ba, watanni biyu da haihuwan Deenah Hadiza ta k'ara haihuwa itama tasamu mace ranan suna aka sama yarinya ummul Khairi.. </p><p> Tunda Deenah ta taso cikin so da k'aunar iyayenta komai suka samu ita da zaran ta fita sai tadawo da kuka saboda Saeed zalintar ta yakeyi kuma ba'a hanashi kullum cikin gallaza mata sukeyi har takai ga bata fita saboda da ta fita sai tadawo da kuka tun abun na damun Ismaeel har yakai ga ya hak'ura,</p><p><br /></p><p> Haka rayuwa ta cigaba da tafiya kullum da azabar dasu Khairee kema Deenah, </p><p> </p><p>BAYAN SHEKARA BIYAR</p><p>Zaune suke parlor suna fira da gudu ta shigo tana kuka, jawota yayi jikinshi ya rungume yace "Deenah kiyi hak'uri da irin abinda zaki gani gidannan kinji ko watarana sai ya zama labari" hawayenta ta goge tace "Daddy miyasa su Uncle suka tsaneni?" Bafa mai sona cikin su, Falmata tace "ba tsanarki sukai ba kinji ko" daina kuka, tashi mu raka babanki ke yake jira dama kidawo tafiya zaiyi...</p><p> Har wajen mota suka rakashi, yana shiga mota sai kuma ya fito shafa kan Deenah yayi ya kalleta yace "my dota ki tsaya kiyi karatu in shaa Allah duniya sai tayi alfahari dake" d'aga kanta tayi tana hawaye, kallon Falmata yayi yace "ga amanar Deenah nan nabari a hannunki dan Allah ki bata ilimi" ita kanta hawaye takeyi tace "in shaa Allah saika rayu da Deenah", girgiza kai yayi ya juya ya tafi bud'e mota yayi sai kuma ya k'ara juyowa shima hawaye ya keyi, hawayen ya share kana ya shiga mota, d'aga mashi hannu sukeyi har saida yafita tunda yatafi Falmata ke kuka wanda ta rasa dalilin yinshi....</p><p> Kad'an kad'an Falmata zata duba wayanta, ga bugun k'irji da takeji number d'in Ismaeel tayi try amma sai tajita kashe, k'irjinta ne ya cigaba da bugawa, kamar daga sama taji kuka da sauri ta tashi ta saka hijab taja hannun Deenah suka fita......</p><p><br /></p><p>© M@J@H</p><p>F💘J💘R💘[9:10PM, 8/3/2017] +234 806 677 6651: 🌸💦MATATA GIMBIYATA💦🌸</p><p><br /></p><p>💘MY WIFE MY PRINCESS💘</p><p><br /></p><p>STORY BY</p><p>JEEDDAH JA'O</p><p><br /></p><p>WRITTEN BY</p><p>FEEDOH DEEDOH</p><p> (NWA)</p><p><br /></p><p>EDITED BY</p><p>ROOKIEY KAXS</p><p><br /></p><p> 1⃣1⃣➖1⃣2⃣</p><p><br /></p><p> Suna fita suka ga wasu mutane su biyu sai kuma mutum kwance k'asa, ga Khamees sai rusa kuka yakeyi, matsowa tayi tace "miyafaru?" Babu wanda ya amsa ta, saidai taji d'aya daga cikinsu yace "hak'uri zakuyi accident ya samu kafin ya k'arasa mutuwa shine ya bamu address d'in gidannan" da sauri ta k'arasa dan taga waye...</p><p> Tana bud'ewa ta ganshi kwance kamar yana bacci idonta ta k'ara murzawa taga kodai mafarki take, tabbas ba mafarki bane ba Ismaeel d'inta ne. Kuka ta fashe dashi tace "haba Ismaeel ya zaka mana haka? Ya zaka tafi kabarmu cikin duniyar nan mai cike da k'unci pls katashi nasan baka mutu ba" kuka take sosa ashe dama mutuwa kakeyi shiyasa kake ban amanar Deenah. Matsawa Deenah tayi inda gawar baban take ta kwanta bisa shi tace "please Daddy wake up nasan baka mutu ba wasa kake mana", saboda malaminmu yace duk wanda ya mutu bazai dawo ba, kai ko nasan ba zaka mutu yanzu ba baza ka mutu kabarmu wajen su Uncle ba dan zasu cigaba da zalintarmu please Daddy ka tashi, babu wanda Deenah bata saka kuka ba, jawota Falmata tayi jikinta tace "kiyi hak'uri Deenah Daddynki ya rigamu gidan gaskia" yanzu zamu shiga wata jarabawan, d'aga hannu tayi sama tace "Ya Allah kabani ikon cinye wannan jarabawan, ka bani ikon cikama Ismaeel burinshi na ganin naba Deenah ilimi mai amfani...</p><p><br /></p><p> Haka aka shirya Ismaeel suna gani aka d'aukeshi aka tafi dashi gidanshi na gaskia. Yan maiduguri sunzo saida akayi sadakan uku kana suka sami Khamees dan shaida mashi suna so su tafi da Falmata, Khamees yace "ba matsala amma ba zasu tafi da Deenah ba saboda shine babanta" tunda Falmata taji bazata tafi da Deenah ba tace "bazata je ba itama saboda tanasan cikama Ismaeel burinshi" , dan dole suka tafi suka barsu..</p><p> Rasuwa Ismaeel da kwana bakwai Khamees yazo ya karb'e duka takardun k'adarorin Ismaeel, acewarshi shine ya dace da ya rik'esu ba Falmata ba, haka Falmata ta bashi ba tare da ta nuna wata damuwa ba, burinta kawai taga ta cika ma mijinta burinshi na ganin Deenah tayi karatu...</p><p><br /></p><p> Haka rayuwa ta cigaba kullum su Falmata cikin k'unci suke sunyi bak'i sun lalace kullum da azabar da ake masu ita da d'iyarta. Abinda yafi d'aga mata hankalin yanda Khamees ya cire Deenah daga private school ya mai data LEA ba yanda ta iya haka ta hak'ura amma abin burgewa tun da Deenah ta taso mai k'ok'ari ce komai da an fad'a mata take d'aukewa sab'anin Khairee da bata gane komai....</p><p><br /></p><p> Bayan rasuwar Ismaeel da shekara biyu, kwance take k'udundune Deenah ce kusa da ita tana mata fita da kyar ta d'ago ta kalli Deenah kamo hannunta tayi ta matse cikin nata ta kusa rabin awa haka, can ta sake kallonta kiranta tayi da "DEENAH" amsawa Deenah tayi da naam, kiyi hak'uri da duk halin da zaki tsinci kanki, na tabbata Allah na tare da ke ba zai bari ki wulak'anta ba, ki rik'e mutuncinki duk inda kika samu kanki, ki rik'e ibada in shaa Allah zakiyi dariya watarana cikin kuka Deenah tace "Mummy miki keson gaya mani? Kema zaki barni kamar yanda Daddy yabarni dan Allah Mummy ki zauna dani karki barni" hawaye Falmata ta share tace "Allah bai barin wani dan wani yaji dad'i" da Allah na barin wani da mahaifinki ya zauna damu inaji araina na kusa barin dunia kamar yanda mahaifinkin yabarta, dan ciwon zuciyar nan ba zai barni ba shiyasa nake maki nasiha da ki kula da kanki da mutuncinki dan nasan babu wanda zai damu dake...</p><p> Kuka Deenah keyi sosai, cikin sheshek'ar kuka tace "ya rayuwata zata kasance babu iyayena a duniya?" Inama mutuwa zata d'aukeni nima dana fijin dad'i, jawotw Falmata tayi jikinta tace "kidaina fad'an haka d'iyata Allah na tare dake kuma yasan halin da kike ciki shi zai kareki"..</p><p> Tashi ki d'auko man ruwa, jiki ba kwari Deenah ta mik'e, tana tashi taji mahaifiyarta ta fara kalmatush shahada, da sauri ta k'araso inda take amma kafin ta iso rai yayi halinshi tabbas a yan k'ananan shekarunta tasan mahaifiyarta ta mutu. Kuka ta saki mai tsuma rai tace "shikenan na dawo banda kowa" mutuwa ya zakiman haka kin rabani da iyayena miyasa baki bari na rayu da su ba? miyasa baki had'a dani ba? Haka ta dinga sabbatu, tafiya tayi part d'in Hadiza tana kuka tana isa ta daka mata tsawa dole Deenah ta had'iye kukanta, cikin kuka tace "Mummy ta rasu" da sauri Khamees ya mik'e ya nufi hanyar fita binshi sukayi, yana isa ya tab'ata, tabbas ta rasu abinda yace kenan....</p><p><br /></p><p> Haka aka shirya Falmata aka kaita gidanta na gaskia, duk wanda yaga Deenah sai ta bashi tausai dangin Falmata sunzo, sunyi sunyi Khamees ya basu Deenah amma haka yak'i amincewa sukayi fushi suka tafi... Tunda Falmata ta rasu Deenah ta koma gidan Khamees da zama...</p><p><br /></p><p> Haka rayuwan Deenah ta cigaba kullum da sabuwar azabar da suke mata, wankin khairat ita keyinshi ga duka da Saeed ke mata, da ta d'anyu mistake zasu fara dukanta...</p><p> </p><p> Kullum cikin nacin karatu take saboda burinta ta cikama mahaifanta burinsu, amma ba kullum ake barinta zuwa makaranta ba.</p><p> Shekarar da sukayi SSCE Uncle Khamees yace aure zai mata dan baiga amfanin karatun ta ba, tayi kuka ta rok'eshi akan yabarta ta cika burin mahaifanta tazama cikakkiyar likita, ranan saida tasha duka dan taron dangi suka mata shida Anty Hadiza saida suka ga bata, motsi kana suka kyaleta, kuma ya shaida mata aure babu fashi, da kanshi ya nuna mata hoton mijin da zata aura, cikin kuka tace "Uncle wannan ai ya girmi babana pls karka aura manshi" dariyar k'eta Anty Hadiza tayi tace "wlh aurenki da wannan mutumin babu fashi" ke ko gawarki ce sai an kai mashi, </p><p> Tashi tayi ta shiga d'aki tana kuka, cikin kuka tace "naso na cika maku burinku na ganin na zama likita" amma gashi hakan bai yuwa saboda za'a aurar dani ga mutumin da ya girmi mahaifina, Allah ka kawoman mafita....</p><p><br /></p><p> Tanaji tana gani aka d'aura mata aure da tsohon da bata sani ba.. Abun mamaki tana zuwa taga ba tsoho baneba, amma yanda taga tsanarta a cikin idon mijinta ya d'aga mata hankali dan tabbas tasan wata uk'ubar ce zata shiga...</p><p><br /></p><p>Shin ya zaman Deenah da Abubakar Sadeek Imam zai kasance? Shin zai so ta ko kuma zasu rabu da juna? burinta zai cika naganin ta zama babbar likita? Ku cigaba da binmu in shaa Allah zakuji amsoshinku....</p><p><br /></p><p>© M@J@H</p><p>F💘J💘R💘</p><p>[9:10PM, 8/3/2017] +234 806 677 6651: 🌸💦MATATA GIMBIYATA💦🌸</p><p><br /></p><p>💘MY WIFE MY PRINCESS💘</p><p><br /></p><p>STORY BY</p><p>JEEDDAH JA'O</p><p><br /></p><p>WRITTEN BY</p><p>FEEDOH DEEDOH</p><p> (NWA)</p><p><br /></p><p>EDITED BY</p><p>ROOKIEY KAXS</p><p><br /></p><p>1⃣3⃣➖1⃣4⃣</p><p><br /></p><p>Back to story........</p><p><br /></p><p> A kasalance na fito daga d'aki gabana se dukan uku uku yake duk Allah Allah nake kar in had'a ido da Mr Sadiq Imam , doguwar riga ce ta atamfa wanda na ci karo da shi cikin wardrobe na saka , wani ikon Allah kamar an gwada akayi dinkin. Yayinda nake saukowa daga stairs d'in ina iya hango mutum zaune a dining section na makeken living room d'in, </p><p><br /></p><p> Gosh !! A lokaci guda na kasa d'auke idanuwa na daga gareshi yayinda yake taunar fried potato chips wanda yasha tomato ketchup , the man is breathtaking and charming physically! Allah kad'ai yasan dalilin bacin ransa da mata! Ko me ma ya dawo dashi paralyzed? Oho?.......</p><p><br /></p><p> Ba kamar yadda kike tunani bane cewa am paralyzed! tajiyo husky voice nashi ya doki kunnen ta, ya dawo da hannayen sa kan control na wheelchair d'in ya waigo yana facing inda take yaci gaba da fad'in </p><p> Zaifi miki sauk'i kada kiyi shishigi! Aikin ki a gidan nan bai wuce shara da goge goge ba! Shima kuma na d'auke miki flat d'ina so all i want from you is stay away from me! Kada ki dinga yin garajen had'a ido da ni, also am not interested in your helping hand, zan iya yin komai da kaina tunda Allah ya hore min hannu i don't need anybody's help! Shishigi dai ina dad'a jan kunnen ki akai And don't worry I'll pay you, your salary starting from this month idan hakan yayi miki zaki iya zuwa ki karya, and also Young lady for your information akwai kwararriyar Nutritionist a gida ba se kin yi girki ba am not sure ma zaki iya aiki da appliances d'in so gudun karkiyi wa kanki asarar mummunan fuskar nan zai fi miki kar ki yi garajen girki...</p><p><br /></p><p> Na dad'e a tsaye baki a bud'e cike da mamaki, ko da nake zaman wahala ban tab'a ganin mara mutunci irin Mr Imam ba ,shi d'in na daban ne, Wato ma y'ar k'auye ya maida ni? Ai kuwa ban san lokacin da hawaye suka soma gangarowa ba, na koma d'aki da gudu.</p><p> Fad'awa kan gado nayi nace "daman haka auren yake?" Wannan tozarcin shine sauran mata ke fuskanta? Kodai ni d'in ce kawai? Wannan wace irin kaddara ce?..</p><p><br /></p><p> Nikima tawa k'addaran haka tazo, lallai rashin iyaye ba k'aramin abu baneba hawayen da suka gangaro man ne na share su, Nasihar Mahaifiyata na tuna "inda take ceman Deenah kiyi hak'uri da duk irin abinda zaki gani a dunia, in shaa Allah watarana zaki dariya...."</p><p> Toh yaushe ne zanyi dariyan? Tambayan da banda amsar ta, murmushi nayi in shaa Allah zan jure kowace matsala ce daga wajen wanda ake kirana mijina, dan gaskiya banga k'iyayya ta a idonshi ba kamar yanda na ganta a idon su Saeed, akwai dai abinda mace ta mashi yasa ya tsani mata, koma miye a sannu zan sanshi kuma saina kauda mashi tunanin duk mata haka muke, saina canja mashi ra'ayi...</p><p><br /></p><p> Murmushi nayi na tashi dan naje na karya, ina isa downstaire na ganshi yana k'ok'arin tura wheelchair zai d'auko ruwa, da sauri na isa wajenshi na turashi yana d'auko ruwan daidai muna had'a ido wata zabura da yayi ya dakaman tsawa saida na kusa fitsari, ruwan ya watsoman bansan sanda na saki k'ara ba na duk'e k'asa...</p><p> Wace irin jakka ce ke? Banace bansan taimakon ki ba? i don't need anybodys help, Angaya maki banda hannu ne? Tun yanzu kenan ba'a je ko ina ba kin fara karyaman doka, hmmmm mata duk halinku d'aya na tsaneku wannan ya zama na k'arshe da zaki shiga harkata, dan haka get out from here, kasa tashi nayi saboda tsabar razana nayi, da k'arfi ya k'ara maimaitawa a said get out da gudu na tashi na haye sama ina kuka...</p><p><br /></p><p> Ina shiga d'aki na banko k'ofa kan gado na fad'a ina kuka, ni kuma haka tawa k'addaran take? Mutuwa bakiman adalci ba, inda iyayena na da rai bazasu barni na tozarta ba, ganin kukan baiman magani ya sa na shiga toilet na d'auro Alwalla nazo na tada sallah ina gamawa na d'aga hannu sama nafara adua neman nasara ina gamawa inda nayi sallah nan bacci ya kwasheni.....</p><p><br /></p><p>© M@J@H</p><p>F💘J💘R💘</p><p>[9:11PM, 8/3/2017] +234 806 677 6651: 🌸💦MATATA GIMBIYATA💦🌸</p><p><br /></p><p>💘MY WIFE MY PRINCESS💘</p><p><br /></p><p>STORY BY</p><p>JEEDDAH JA'O</p><p><br /></p><p>WRITTEN BY</p><p>FEEDOH DEEDOH</p><p> (NWA)</p><p><br /></p><p>EDITED BY</p><p>ROOKIEY KAXS</p><p><br /></p><p> 1⃣5⃣➖1⃣6⃣</p><p><br /></p><p> Ban farka ba sai da aka kira magrib, shima saboda kukan yunwan da cikina keyi ne da sauri na tashi na fad'a toilet nayi alwalla, nazo na kabbara sallah ina idarwa nafara adu'o'i ina nan aka kira isha tashi nayi na gabatar da isha ina gamawa nayi adua tare da neman nasara na nufi k'asa gabana na fad'uwa saboda bansan sake had'a ido da Mr Sadiq Imam...</p><p> Luckily ina fita palorn ban ganshi ba hamdala nayi ga Allah, kana na k'arasa a daining table, ina zama na bud'e kuloli tuwon semovita ne sai miyan agushi da taji kifi, d'ayar kula kuma pepper soup d'in kayan ciki ne, zubawa nayi naci mai isata nikaina nayi mamakin abincin danaci, koda yake ba abin mamaki baneba cz tunda nazo gidan banci komai ba, sai azaba danake sha...</p><p><br /></p><p> Ina gamawa na dawo palor na kunna kallo na zauna, banjima da zama ba naji anyi sallama, amsawa nayi yayin da yake shigowa, k'arasowa yayi yace "Mrs Sadiq Imam right?" Saida gabana yafad'i jin yakirani Mrs Sadiq Imam, murmushi nayi na sunne kai k'asa, dariya yayi yace "anyway congratz Allah ya baki miji kamili mai ilimi" amma fa saikin yi hak'uri da halin da kika tsinceshi yanzu saboda illar da mace ta mashi, tab'e baki nayi nace "wannan ne kamili? Mugu dai" duk a cikin zuciya nake magana, a zahiri kuma nace "Thanks" in shaa Allah l'll try my best naga na kyautata mashi kudai tayani da adua, yace "in shaa Allah...</p><p><br /></p><p> Nacika ki da surutu baki san wayeni ba ko? Murmushi nayi nace "bakomai".. My name is Doctor Bilal, ni Aminin Mr Sadiq Imam ne and also nine doctor d'in dake kula da lafiyarshi, yanzu zamuje d'akin tare dake na dubashi sannan nabashi wasu methods na excersice which will help him recover fast, kuma kece zaki dinga taimaka mashi wajen excersice d'in. Da sauri na kalle shi nace "Ni?"</p><p> Murmushi yayi yace "yes you" i know it's deficult amma daurewa zakiyi ina da yak'inin kece zaki canja shi ki daure Allah na tare dake. Ajiyan zuciya nayi nace "shikenan muje"...</p><p><br /></p><p> Da sallama muka shiga d'akin Dr na gaba ina biye, da murmushi ya amsa yace "Bilal na d'auka sai gobe zaka..." Bai k'arasa ba ganina da yayi bayan Dr d'aure fuska yayi kamar bashi baneba mai dariya yanzu...</p><p> Dariya Dr yayi ya bugi kafad'ashi yace "Sadiq rigima" yanzu dai bari nayi abinda ya kawoni, nan yafara aikin dubashi tare da yan rubuce rubuce, yana gamawa ya kalleni yace "Madam zan tardaki palor yanzu kinji" d'aga kai nayi dama kamar yasan a tsorace nake..</p><p><br /></p><p> Ina fiya ya juya ya kalli Sadiq d'aure fuska yayi yace "haba Sadiq wai yaushe zaka daina abinda kake?" Kaifa ba yaro baneba yakamata ka san abinda kakeyi kamanta da abunda yafaru ka d'auka k'addaranka ce haka, yanzu kuma Allah ya maka canji da mafi alkairi dan Allah yanzu kaga yanda yarinyar nan ke tsoronka saikace taga zaki wlhi ka canja, dan da ganin yarinyar nan yar mutunci ce... Murya sanyaye yace "please abokina ka manta da komai ka sake sabuwan rayuwa kaji" tunda yafara magana Mr Sadiq baice komai ba kuma har yagama, yafi k'arfin minti ashirin da gamawa amma baice k'ala ba, murmushi yayi yace "nasan dama da fad'a zamu rabu amma kasani gaskia ce ko kanaso ko bakaso sai an fad'ama" yana kaiwa nan yaja briefcase d'inshi yayi gaba....</p><p> Yana fitowa ya sameni zaune nayi tagumi, murmushi yaman yace "haba Amaryanmu miye na tagumi" kodai ciwon mijinki ne ke damunki? Dont worry in shaa Allah soon zai warke kinji, ajiyan zuciya nayi cikin raina nace "wannan mugun yanama zaune guri guda yana zalintata inaga ya samu k'afa"...</p><p><br /></p><p> Maganan Dr ce tadawo dani daga tunanin da nake, farar leda ya mik'oman yace "magunguna ne ciki ki tabbata yasha safe rana da dare" kuma kece zaki dinga bashi wannan kuma zaki dinga mashi massage dashi ne shima 3times daily har na tsawon sati guda kinga duk idan zaki bashi magani saiki mai massage, in shaa Allah nextweek zandawo. Karb'a nayi namashi godia bankwana mukayi ya tafi nikuma na kashe kayan kallon nayi d'aki ad'ua nayi na haye lafiyayyen gado na kwanta, banjima ba bacci mai nauyi yayi gaba dani....</p><p><br /></p><p> Ban tashi ba sai asuba ina idar da sallah na koma kan gado na cigaba da bacci, tara (9:00am) daidai na tashi wanka na shiga ina fitowa na bud'e wardrob d'in nan ma wata doguwan riga na jawo color d'in purple sai stones suma purple nd white ina sakawa ta zauna jikina cif cif dama kamar danni aka d'inkasu, downstaire na nufa cikin ikon Allah baya palorn nan na zauna nayi break fast ina gamawa na d'auki ledan magungunanshi na nufi d'akinshi gabana na dukan uku uku...</p><p> Sallama nayi na shiga d'akin, bud'e baki yayi zai amsa ganina da yayi tsaye yasa ya zabura laptop d'in dake hannunshi ya wurgoman kad'an ya rage ya samu k'afana, duk ta tarwatse k'asa, niko sai kyarma nakeyi, ubanmi ya kawoki? Abinda naji yace kenan, cikin rawar murya nafara magana dama dama, tsawa ya dakaman wadda tasa na kusa sakin fitsari dama mi? Dama doctor ne yace nazo na baka magani kuma na maka massage a k'afafuwanka har na tsawon 1week kuma 3times daily...</p><p><br /></p><p> Shiru yayi can yace "ban amince ba kuma idan kece zakiyi banaso" dan haka aje magungunan ki ficema daga d'aki, wata zuciya tace mashi "Ah Ah" Sadiq kabari tayi kaga konan ka bautar da ita dama abinda tazoyi kenan gidan kenan...</p><p><br /></p><p> Ina aje magungunan na juya zanfita nakai k'ofa naji yace "dawo kiman" duk'awa nayi na d'auki ledan magungunan na k'arasa cikin d'akin, harara ya wurgaman yace "da kin gama ko second karki k'ara a d'akina kinji ni? D'aga kai nayi alamar "Eh" b'alla mashi magani nayi na mik'a mashi amsa yayi baiko kalli inda nake ba, fridge d'in d'akin na bude na d'auko ruwa bud'ewa nayi na zuba a cup na kai bakinshi, harara ya wurga mani kana ya bud'e bakin, yana saka maganin na bashi ruwa yana gamawa ya wurgaman harara yace "miye kika tsareni da ido?" Nidai bance komai ba na cigaba da yimashi massage a k'afa....</p><p> Ina mashi massage ina satar kalllonshi runtse idonshi yayi alamar yanajin dad'in abun saida nagama tsaf na d'ago da niyar nace mashi nagama, ina d'agowa muka had'a ido dashi, kunnena ya murd'e saida nasaki yar k'aramar k'ara yace "banace ki daina kallona da wannan ugly face d'in naki ba, ina cewa nace maki da kingama ki fitarman daga d'aki ko second kada ki k'ara shine kika tsareni da kallo...</p><p><br /></p><p> Ina hawaye nace "dan Allah kayi hak'uri dama zance maka nagama" idan akwai abinda kake buk'ata kafad'aman tsoki yayi "mtchw" mi zan buk'ata wajenki? Aibaki da dashi dan haka get out of my room, kafin ya ida na ruga da gudu....</p><p> Dariya ya bushe da ita saida yayi dariya mai isarshi kana yace "matsoraciya" ashe haka take da tsoro? K'afafuwanshi ya kalla yaji duk sun d'an saki, murmushi yayi yace "ashe dai ta iya massage haka?" Dole ta zama mai man massage....</p><p><br /></p><p> Ina shiga d'aki na maida k'ofa na rufe fad'awa nayi kan gado nace "mugu azzalumi sai Allah ya sakaman, kuma anjima saina maka mugunta tunda kake cutata."</p><p><br /></p><p>©M@J@H</p><p>F💘J💘R💘[9:11PM, 8/3/2017] +234 806 677 6651: 🌸💦MATATA GIMBIYATA🌸💦</p><p><br /></p><p>💘MY WIFE MY PRINCESS💘</p><p><br /></p><p>STORY BY</p><p>JEEDDAH JA'O</p><p><br /></p><p>WRITTEN BY</p><p>FEEDOH DEEDOH</p><p> (NWA)</p><p><br /></p><p>EDITED BY</p><p>ROOKIEY KAXS</p><p><br /></p><p> 1⃣7⃣➖1⃣8⃣</p><p><br /></p><p> Zaman shiru ne ya ishe ni don haka na yanke shawarar zagayawa cikin gidan bak'in mayafi na d'auko na yafa sannan na fice gami da janyo k'ofar. </p><p> Daidai step d'in k'arshe na d'ago idanuwa na wanda suka sha ado da Mascara by Mary Clair na aza su cikin makeken falon amma me? Idanuwan mu ne suka ci karo da na juna tuni jiki na ya d'au rawa na fara taking steps backwards. </p><p> " Ke!! " ya daka mani tsawa hakan yasa na tsaya chak idanuwa na a rufe . Where did you think you are going? Ya tambaya " </p><p> Cikin zuciya ta nace " Yaushe kuma ka fara karanta minds ? Kuma ma me ya shafeka da inda zani!" </p><p> Murmushi yayi yace " Nasan me kike tunani! Yes babu abunda ya shafeni da inda zaki! Kawai de bana son a lokutan da nake having peace a dinga shige man harkoki! Saboda haka go back in bana falon se kiyi abunda ya kawo ki! " </p><p><br /></p><p> Yanzu don kana zaune a falo tsabar bak'in hali shikenan kar kowa ya shigo? Allah ya sawwak'e !" Ta fad'a cikin zuciya kana ta juya zata koma fuska a murtuk'e kamar zatayi kuka ta koma d'aki ta fad'a kan gado tana ta sak'e sak'e........</p><p><br /></p><p> Zaune yake as usual kan wheelchair nashi yana kallon program na The Doctors. Shirun ne ya ishe shi don haka ya k'ira Sadeeya ( Mai girkin gidan ) da sauri ta fito tana goge hannayen ta a jikin kitchen towel , durk'usa wa tayi a gaban shi tace "Gani Sir" ta fad'a kai a k'asa. </p><p> Ajiye wayar sa yayi kan centre table ya ce " Ga ATM card nawa kije Shoprite zakiyi min siyayya ga list din a kan kujera " yana kai wa nan ya maida duban shi ga TV Sadeeya ta mik'e da zummar komawa kitchen ya dakatar da ita ta hanyar daka mata tsawa </p><p><br /></p><p> where do you think you are going? Sir akwai abinci a kan cooker shine zan sauk'e kum..." Dakatar da ita yayi ta hanyar d'aga mata hannu sannan yace " Ki dawo ki d'auki abunda na saki ki wuce kafin raina ya b'aci , bana son ki 'kara koda second biyu! Jiki na rawa ta d'auki card d'in da list ta fice domin kuwa tasan halin sa , a da can ba ita kad'ai bane mai aiki duk shi ya koresu don haka itama dole tayi taka tsantsan in ba haka ba yanzu yayi waje road da ita...........</p><p> Ina kwance har k'arfe sha biyu sannan na yanke shawarar dawowa ko ya bar falon amma me? </p><p> Kaurin k'one wan abinci duk ya mamaye downstairs d'in , zaune na hango shi ko a jikin sa duk warin nan ko a jikin sa , ganin yanda hayak'i yake fita daga kitchen yasa na sa gudu , har nakai bakin k'ofar kitchen d'in yace " </p><p>" Ke wace irin bagidajiya ce? Shin idonki bai nuna miki makunnin ruwa bane a k'ofar ? Toh in baki sani ba yanzu ki sani an saka su ne saboda emergency na fire outbreak kuma automatically yake kunna kan shi ya kashe wutan , no need ki d'auki wata flamingo leg naki kice zaki shiga coz wutan ya mutu! Bak'auyiyar yarinya kawai! </p><p><br /></p><p> jiki a sanyaye na juya zan bar falon yace " Ina kuma zaki? Wa kike tsammanin zai goge mess d'in kitchen d'in?" Zaro idanuwa nayi Like seriously wai me wannan mutumin yake nufi da ni ne? " </p><p> Ba tare da na furta kalma d'aya ba na koma kitchen d'in na fara aiki komai seda na tabbatar ya koma normal nayi mopping sannan na sauya tukunya bani na gama aikin ba se k'arfe biyu hakan ma na je nayi sallah sannan na cigaba, ina fitowa direct na wuce Upstairs na tube kayan jiki na gami da fad'awa bathroom nayi wanka , fitowa na ke da wuya naji ihun mutum, babu shakka muryar Sadeeya ne don haka na fice d'aure da k'aramin towel don ta tsorata ni . a d'akin shi naji tana k'iran suna na " Hajiya! ( kamar yadda ta saba ) a firgice na shige d'akin only to se Mr Imam a kwance k'asa ruf da ciki ya runtse idanuwa kamar yaji ciwo ga kuma wheelchair a jefe guda. </p><p><br /></p><p> Hajiya nima Nazo kawo mishi orange juice kamar yadda ya buk'ata na same shi a haka" cewar Sadeeya a rikice Ido na mata da cewar ta fita , haka ta fice gami da rufe k'ofar , iya k'arfi na, na ciccibeshi sai nishi nake domin kuwa nauyi ne dashi ba kad'an ba , da 'kyar na iya jinginar da shi jikin gadon sannan na sake k'ok'arin d'aga shi gami da maida shi kan gadon , Duk nayi gumi gashi k'arfi na duk ya tafi ,ina kwantar da shi na zube a kansa jiki ba kwari duk gashin kaina a fuskar sa numfashin mu na gogan na juna , yayinda 'kamshin fresh mint na bakin shi ya bugi hanci na lumshe idanu nayi. </p><p><br /></p><p> Ji yayi zan zame k'asa don haka ya yi wrapping hannun shi guda around my back yana shak'ar 'kamshin Bakhur dake mamaye cikin gashi na , wannan feelings d'in yau kad'ai na taba jin sa , sam ya kafe ni da idanuwa , mun kai mintina biyar a haka kafin na ce </p><p>" Excuse me" jin muryata yasa ya hankad'o ni k'asa yana watsa man harara duk jiki ba kwari na fita se kare jiki na nake yi..</p><p><br /></p><p> Ina fita ya lumshe ido, da sauri ya bud'e sakamakon k'amshin dayaji jikinshi nayi, cire riganshi yayi haryanzu k'amshin na nan, lumshe ido yayi yace "turaren yarinyar nan yana da dad'i how i wish na dingajin shi kullum" wata zuciyan tace Sadiq ka mance matsayin da ka ajeta? Da sauri ya kauda tunanin ya wurgar da riganshi yana huci kamar tsohon zaki....</p><p> Ina shiga d'aki na fad'a kan gado wani irin farin ciki na shiga, tunano abinda ya shiga tsakaninmu na dingayi, rintse ido nayi ina k'arajin feelings, da sauri na tashi na shiga toilet nayo Alwalla na tada sallah bayan na gama na nufi downstair...</p><p><br /></p><p> Ina sauka na had'u da Sadeeya har k'asa ta duk'a ta gaidani, cikin sakin fuska na amsa, tambayarta nayi Sadiq yaci abinci? Sadeeya tace "yace dai na kai mashi d'aki a can zai ci" amsawa nayi da "ok" na juya na tafi d'akin cikin tsoro. Ina shiga nayi sallama shiru akayi k'ara sallama nayi cikin zafin rai yace "malama ki shigo idan zaki shigo bansan yawan magana" tab'e baki nayi nace "shi duk yanda ka mashi baka iya ba...</p><p> Shiga nayi zaune yake yana latsa waya, gaidashi nayi amsawa yayi da lafiya, girgiza kai nayi na d'auko magani na mik'a mashi kallo na yayi yace "a k'auyenku ana shan magani ba'aci abinci bane?" Girgiza kai nayi nace "ai na d'auka kaci" banci ba abinda yace kenan, duk'awa nayi na zuba mashi abinci ina gamawa na mik'a mashi kallona yayi yace "ai yana daga cikin aikinki kibani abinci" da sauri na kalleshi harara ya wurgamani yace "zakiyi ko kuma zaki tsareni da mayatacce kallonki?" zama na gyara na dinga bashi abinci har saida ya k'oshi na bashi ruwa yasha....</p><p><br /></p><p> magani na b'alla mashi na mik'a mashi, k'in amsa yayi bud'e baki yayi na saka mashi maganin na bashi ruwa, ina gamawa nafara mashi massage saida na tabbatar maganin ya shiga jikinshi sosai kana na mik'e na nufi hanyar fita..</p><p> Ina kaiwa bakin k'ofa yace "ke mummuna" cikin b'acin rai na juyo, kallo na yayi yace "wajen takwas zakizo kiman cz zan kwanta da wuri" kuma kika k'ara koda second guda ne wlhi l'll show u my true color, cikin raina nace "yo akwai true color d'inka bayan wannan?" Murgud'a mashi baki nayi na fice d'akin da gudu...</p><p><br /></p><p> Murmushin mugunta yayi yace "zaki gane kurenki yarinya" zakisan kin murgud'aman baki...</p><p><br /></p><p>©M@J@H</p><p>F💘J💘R💘</p><p>[9:11PM, 8/3/2017] +234 806 677 6651: 🌸💦MATATA GIMBIYATA💦🌸</p><p><br /></p><p>💘MY WIFE MY PRINCESS💘</p><p><br /></p><p>STORY BY</p><p>JEEDDAH JA'O</p><p><br /></p><p>WRITTEN BY</p><p>FEEDOH DEEDOH</p><p> (NWA)</p><p><br /></p><p>EDITED BY</p><p>ROOKIEY KAXS</p><p><br /></p><p> 1⃣9⃣➖2⃣0⃣</p><p><br /></p><p> Shiru har k'arfe Tara na dare Deenah bata fito ba tun Mr Imam yana daurewa har ya kai mak'ura don haka ya d'auki telephone ya k'ira line na cikin gida luckily Sadeeya ta d'auka , cikin hasala yace </p><p>" Tell your Madam in akwai abunda yafi b'ata min rai bai fi delay ba, kada ta kuskura ta k'ara ko da minti d'aya kan hour d'aya da ta tsallake"</p><p> Jiki na rawa ta fice bata zame ko ina ba sai d'akin Deenah inda ta iske ta a baje kan gado tana sharara bacci da alama duk na sauk'e gajiya ne. Da kyar Sadeeya ta iya tashin ta sannan ta Isar da sak'o ta fice , nan fa mutumiyar tasan cewa dubun ta ya cika Amma mafitar shine ta je kawai don dai masifar sa a wajen ta ba wani sabon Abu bane.</p><p> </p><p> Na dad'e bakin k'ofa hannuna ya kasa bud'e k'ofar balle nai tunanin shiga, at last nayi ta maza na bud'e ban shiga ba Sai da na lek'a kwatsam mukayi ido hud'u ,hah! Come see yadda na fara muzurai kamar tsohuwar munafuka shi kuwa ya zubamin na mujiya ko kyaftawa babu, ba tare da ya ce komai ba nayi sallama na shige ko ya amsa ma ni ban Sani ba ,direct na nufi bedside drawer na ajiye tray d'in dana d'auko ruwa da glass ,a kai . har na bud'e ruwan zan 6alli maganin naji muryar shi cikin sigar da bai taba min magana da ita ba tunda na zo gidan shi </p><p> Indeed the sweetest ever! </p><p><br /></p><p>" You never listen do you? , nace miki k'arfe takwas and here you are k'arfe Tara da Kusan rabi zaki bani magani , yanzu in na miki fad'a zaki ga laifina ko?" </p><p>A hankali na girgiza kai nace</p><p> " Kayi hakuri I slept in " </p><p> Hakuri! Hakuri!! Hakuri!!! Ya daka tsawa sannan ya dawo normal muryar shi yace </p><p>" meyasa dukkanin ku hali d'aya gareku? " </p><p> Cikin sauri na d'ago kaina na aza idanuwa na cikin nashi tartare da alamar tambaya baki na rawa nace </p><p>" Dukkanin mu? Ni da wa?" </p><p> Da alama bai ma San yayi magana ba don haka ya d'ago yana kallo na kafin yace </p><p>" Get lost! " </p><p>cikin damuwa nace </p><p>"Toh maganin fa?" </p><p> "YOUNG LADY BAKI JI ME NACE BANE? GET LOST !!;" </p><p><br /></p><p>cikin firgici na fice a guje na bar d'akin na fice ma daga cikin gidan zuwa jikin wani window na zauna , wasu zafafan hawaye suka fara tsere daga idanuwa na. </p><p><br /></p><p> Daga kan gadon da yake zaune yana hango ni ta glass na windon shi ,yasan bansan a nan yake ba Amma fuskar shi ya nuna ji yake ya tashi ya bata hakuri and of course give her a warm hug......</p><p> Ina nan bakin window har bacci ya d'aukeni, nice ban farka ba sai k'arfe shida da rabi na safe (6:30am) firgigit na tashi zaune amma abinda na gani yaban mamaki tuni nafara tunanin waya kawoni d'aki nidai iya sanina a waje nake har bacci ya d'aukeni amma gashi na ganni d'aki harda rufeni da blanket da kunna man Ac kodai Sadeeya </p><p>ce ta maidoni? Haka na dinga ma kaina tambayoyin da nikaina bansan amsarsu ba...</p><p> Haka na tashi jiki ba kwari na fad'a toilet wanka nayo da yake ina fashin sallah, turare kawai na saka na d'auko doguwar riga ta material na saka. Down stair na nufa ina sauka muka had'u da Sadeeya da sauri ta duka </p><p>"Ina kwana Anty?"</p><p>"Lafiya lau"</p><p>Na bata amsa, tashi tayi zata wuce </p><p>"Sadeeya" </p><p>"Naam Anty"</p><p>"Dama tambayarki zanyi ke kika kaini d'aki jiya bayan nayi bacci?"</p><p>"Ah ah Anty bani bace ba"</p><p>"To waye ya kaini d'aki?"</p><p>"Wallahi ban sani ba Anty"</p><p> Juyawa nayi na nufi kitchen zuciyata cunkushe da tunani kala kala..</p><p> Abinci na tusa gaba ina kallo ina wasa da spoon, Sadeeya ce ta k'araso inda nake zaune tace</p><p>"Anty ya kamata kici abincin nan"</p><p>Murmushi nayi nace </p><p>"Karki damu Sadeeya nama k'oshi kedai had'oman break din yallabai" </p><p>Mik'ewa tayi ta nufi kitchen..</p><p><br /></p><p> Mik'aman tray d'in tayi karb'a nayi na nufi kofar gabana yana dukan uku uku, sallama nayi har sau uku amma ba amsawa kaina na kutsa ciki, tsawar daya dakaman yasa na kusa yada tray d'in hannuna, ke jakar inace? Da zaki fad'o ma mutum d'aki batare da izini ba? Ko an angaya maki idan kai sallama shigowa kake batare da ance ka shigo ba kodayake ba mamaki k'ila bakije makarantar Islamiyya ba...</p><p> Bak'in ciki yasa nakasa koda d'agowa in kalleshi, cikin tsawa naji yace </p><p>"Get out of my room"</p><p>Ba musu na juya zan fita </p><p>"Ke ugly" </p><p>Tsayawa nayi amma ban juyo ba dan in akwai abinda na tsana bai wuce wulakanci ba shiko naga mutumin nan bai aje komi ba sai wulakanci..</p><p> </p><p> Zokiyi aikin daya kawoki marar kyau da ke, shiga nayi na samu wuri na aje tray d'in tare da goge hawayen da suka gangaro man..</p><p> Gaida shi nayi amma ko kallo na baiyi ba bare nasa ran zai amsa...</p><p> Plate d'in soyayyen dankali da kwai sai tea na d'auka na isa gabanshi, fara bashi nayi ba musu ya bud'e baki na fara bashi sai da ya k'oshi kana na b'allo magani na bashi had'awa yayi da hannuna da maganin ya taune saida na saki k'ara kana ya sakar man hannuna hawaye na share cikin raina nace kaida Allah mugu Azzalumi kuma indai haka zaka cigaba a zaune zaka k'are rayuwarka bazaka mik'eba...</p><p>"Idan kin gama zagin nawa sai kiyi sauran aikinki kitashi kiban wuri nagaji da ganin fuskarki tun banyi amai ba.."</p><p>"Ido na zare nace wallahi ba zaginka nayi ba"</p><p>Ba rantsuwa na tambayeki ba kiyi abinda zakiyi ki b'aceman dagani ugly dai ke.."</p><p> Massage nafara yi mashi inayi yana lumshe ido sai da na gama mashi komi kana na mik'e da zumar barin d'akin..</p><p><br /></p><p> Hannuna ya fizgo har sai da na fad'i amma ko kallo ban isheshi ba.</p><p>"Miya hanaki zuwa jiya da wuri?" </p><p>"Bacci nayi na bashi amsa a takaice dan na fara gajiya da wulakancin shi.."</p><p> Kunnena yaja yace </p><p>"Wakika ma rashin kunya jiya?"</p><p>Hawaye na farayi nace</p><p>"Dan Allah kayi hak'uri"</p><p>Tsawa ya dakaman wadda yasa saida na kusa sakin fitsari</p><p>"Dake nake ubanwa kikama rashin kunya nace?"</p><p> Kuka na fashe dashi, kallona yayi yace</p><p>"Kigama kukan sai kin gayaman ubanda kikema rashin kunya.."</p><p>[9:11PM, 8/3/2017] +234 806 677 6651: 🌸💦MATATA GIMBIYATA💦🌸</p><p><br /></p><p>💘MY WIFE MY PRINCESS💘</p><p><br /></p><p>STORY BY</p><p>JEEDDAH JA'O</p><p><br /></p><p>WRITTEN BY</p><p>FEEDOH DEEDOH</p><p> (NWA)</p><p><br /></p><p>EDITED BY</p><p>ROOKIEY KAXS</p><p><br /></p><p> 2⃣1⃣➖2⃣2⃣</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Shiru nayi ina kuka a hankali, ina jin yadda ya damk'e hannu na nasan bazan iya wafce wa ba don haka na fara tuno dabaran da zan yi ya sake ni.</p><p> Da gangan na saki k'ara kamar Wanda naga abun tsoro ba shiri ya sake Mani hannu yana fad'i </p><p>"Me ne?" </p><p> Ban ko saurare shiba Sai da na isa bakin k'ofa na juyo fuska ta d'auke da exclusive dariya Wanda of course na manta ranar da nayi irin ta a hankali nace </p><p>"Catch me if you can!!"</p><p> Sannan na fice ina murza inda ya damk'e d'in</p><p> Sosai ya dinga dariya shi kad'ai harda rik'e ciki yace </p><p>"yau na farko you tried to fight back in your own style" </p><p> ya d'aga gira sannan ya d'auki wayar shi yana danna wa.....</p><p><br /></p><p> Yau haka na wuni tun dana gudo ban sake had'e ido da shi ba, kuma hakan yayi min dad'i sosai don at least na samu peace yau.</p><p> Horn na mota da naji ne yasa na mik'e na nufi window Matace tare da wata budurwa kyakkyawa kam babu yabo ba fallasa. Matar zata kai shekaru Arba'in plus ta sha liffaya kai kace daga Borno take Amma fuskar nan ba annuri ko kad'an da alama ma masifa take yi gata Masha Allah tana da k'iba Amma ba na tashin hankali ba. </p><p> Da sauri Sadeeya ta iso inda nake tace </p><p>"Tab'l yau kam na shiga uku! Yau Hajiya ce a gidan nan?" </p><p> Deenah ta juyo da alamar tambaya a fuskar ta tace </p><p>"Kamar ya kin shiga uku? Wacece ita?" </p><p><br /></p><p> "Uwar Ki ce! Nace Uwar Ki ce! Hummp! Wato tsabar tsegumi tun kafin na k'ariso har an gama k'are min kallo, Munafukan banza"</p><p> Ta juya gefen Sadeeya tace </p><p> "Toh Munafuka! Sai Ki kai kayan mu ciki ai."</p><p> Jiki na rawa Sadeeya ta fice don d'auko kaya ni kuwa k'asa na durk'ushe ina mai gaida su, ba tare da ta amsa ba ta ja tsaki ta wuce tana fad'in</p><p>"Oh ni Halima! Y'an aiki se tsegumi, munafukai Ke kuma Ramlah je Ki duba yayan Ki don nasan bai San da zuwan mu ba"</p><p> Tana magana tana nishi kamar Wanda taci gudu wai hakan stairs take hawa.....</p><p> Tun da muka rabu da su a Falo na dawo d'aki Jiki na rawa a rai na nace </p><p>"Tab ba'a rabu da Bukar ba an haifi Habu! Wannan wacce irin K'addara ce? Ni Wollah matar nan ma tafi Mr Imam bani tsoro, don Rashin mutunci ma a y'ar aiki ta d'auke ni, like serious? Do I really look like a maid? Ko dai kawai zagi na take yi?"</p><p> Na dad'e ina sak'e -sak'e ban ankara ba naji an chafko wuya na kamar Wanda nayi wata gagarumar sata idanuwa a waje cike da mamaki na juyo ina kallonta ido cikin ido tana taunar chewing gum kamar y'ar tasha </p><p> "Uban wa ya baki izinin shigo min d'aki, kina y'ar aiki da Ke har kin samu hurumin shiga min d'aki har kisa min kaya?"</p><p> Ramlah kenan </p><p><br /></p><p> Zaro idanuwa nayi waje kamar an mahaukaciya baki bud'e nace </p><p>"kamar naji kin ce kayan Ki? Toh mesa Mr Imam ya barni a Wannan d'akin, koda yake daman shima ba mutunci gareshi ba I don't blame him" </p><p>Duk cikin zuciya nake wad'annan maganganun</p><p> Ban ankara ba naji tayi snapping yatsun ta a fuska na tace </p><p>"Wake up stupid! Kafin na bud'e ido na Ki cire min kaya kuma Ki bar min d'aki"</p><p> Gudun janyo magana yasa nayi maza maza na kwashi flamingo legs d'ina na fice ban zame ko ina ba se d'akin Sadeeya , sai a lokacin haushin Mr Imam ya kama ni , don haka na mik'e da zummar zuwa d'akin shi..........</p><p><br /></p><p> Ko sallama babu ta banke k'ofar d'akin ta shiga , idanuwan ta basa ma gani balle taji shakkar sai huci take..</p><p> "Hey! I did not remember you asking for my permission kin wani shigo min d'aki babu ko sallama"</p><p>Ya fad'a kansa a kan laptop screen.</p><p> "Sallama? Sallama ai a mutanen da suka san ma'anar ta ake yi wa? Kai da you do not ever want to maintain peace dalilin me yasa zan maka sallama? You have humiliated me to the extend that naji na tsani kai na yau! First ka bani d'akin da ba nawa ba sannan na saka kayan da ba nawa ba duk ka Sani ka bari Yarinya tazo ta ci Mani mutunci Wollah ban tab'a jin anyi downgrading d'ina haka ba, yau naji cewa dama an barni a inda nake cikin bauta da takura ko ba komai jini na ne su ,Wollah if you had known da baka b'ata lokacin ka har ka bani d'aki ba, nida na kwana a kitchen, na kwana a filin gida ina ne bazan kwana ba, now I want you to explain this to your sister that I did not wear her clothes Intensionally"</p><p> Tana kaiwa nan ta fice gami da banko k'ofa har Saida Mr Imam ya tsorata gami da ajiye laptop d'in ya bi k'ofar da kallo cike da mamakin what she just did.</p><p> </p><p> "How can I tell you My Darling,Cewar kayan sun miki kyau?, bazan iya cewa Ki cire ba coz they seems like they are meant only for you"</p><p> Cikin sanyin murya yake magana bai ma San da mutum tsaye a kanshi ba.........</p><div><br /></div><p> </p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-4699305491930023542021-03-06T05:16:00.000-08:002021-03-06T05:16:58.153-08:00MATAR DR SAYYADA COMPLETE NOVEL<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-6ZpXIFclNoI/YEOAE-o5S8I/AAAAAAAAJlA/kJ4MYGx5ox4Sw1L4khhqNicVhQ18Saj-wCLcBGAsYHQ/s2048/MATAR-DR-SAYYADA.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="MATAR DR SAYYADA COMPLETE NOVEL" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-6ZpXIFclNoI/YEOAE-o5S8I/AAAAAAAAJlA/kJ4MYGx5ox4Sw1L4khhqNicVhQ18Saj-wCLcBGAsYHQ/w320-h248/MATAR-DR-SAYYADA.jpg" title="MATAR DR SAYYADA COMPLETE NOVEL" width="320" /></a></div><br /> <p></p><p class="MsoNormal">[12/07, 21:09] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛1⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Alhamdulillah
Alhamdulillah cikin Ikon Ya Rabbi Nakuma dawowa acikin sabon littafina mai suna
MATAR DR. SAIYADEE INA fatan zaifi ASALIN RAYUWA DAD'I dah darasi,<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>dafatan kowa yayi sallah lafiya Allah
yamaimaita manah Ni Mhiss B~hal Ina muku barka dah shan ruwa All ova pls kada
amanta adaura dah Azumin Sitta Shawwal Fans, Allahu ya amshi ibadun Mu baki
d'aya, AMEEN<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated to SadNaf deary💕Luv U<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Kwance take kan
gado tayi ruf dah ciki idanta biyu Amman tah rufe su tamkar mai bacci, daga
ganintah kasan tanah cikin damuwa dah alamun tayi kuka tayi nak, Oh ni
Ummulkhair Allah kazaba min mafi alkhairi arayuwa abinda naji tah fad'i kenan,
sallah taji ana kira tamik'e taje tayi alwala tayi sallah bayan tah idar neh
tah mik'a hannu kan gado tah dauki wayantah dubawa tayi taga Sam babu missed
call dinshi koh daya, jiki asanyaye tashiga dailing numban sa, saida takira sau
hudu har tah fidda rai sannan yadauka, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Salam'alaikum, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Wa alaiki salam Ummunah, ya kike?<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Lafiya kalau Alhdulillahi ya aiki, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Aiki dah godiya Ummunah gashinan munata fama ai,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Sannu Allah yataimaka kace za.......<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Inazuwa inazuwa Ummunah zankira ki aiki nakeyi,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Baiko bari tak'arasa magana bah sai Jitayi phone d'in yayi
cutting gabad'aya jikinta yayi sanyi kwanciya tayi kan daddumar tanah
kala~kalan tunani har bacci yayi awon gaba dah itah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> <span></span></o:p></p><a name='more'></a><p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Wacece Ummulkhair?<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummulkhair d'iya Ce ga Alhaji Abu Sufyan dah Hajiya Hadiza,
Su biyu neh kadai awajan Iyayen su daga itah sai K'anin tah Affan, Ummulkhair
doguwa Ce height d'intah is average chocolate in complexion very cute tanada
k'iba daidai misali, gashin tah shima curly kuma tsayin shi daidai misali
atakaice dai Ummulkhair yarinya Ce mai kyaun gaske san kowa k'in wanda yarasa
tasamu wadatattan tarbiya daga Iyayen tah Masha Allah, at the age of 15 tagama
secondary school d'intah, Cikin Ikon Allah taci Waec&Jamb d'intah tasamu
admission at Bayero University Kano inda tah karanci Biological science, at the
age of 19 tagama sch d'intah tareda saukan Al~Qur'ani mai girma, Alhamdulillah
tayi service at 20yrs, tah kammala komai Lucky her! Ummulkhair tanada wani
Saurayi maisuna Abubakar wanda ake kira dah Saiyadee shine Wanda takesan aure
in the sense that akwai soyayya mai k'arfi atsakanin su saida kuma kash tanah
fargaba sabida amatsayin tah nah 'yaamace tanah lacking lots of things daga
gareshi kasancewar likita neh, she lacks his time&attention amman kuma
ahakan suke soyyayar su kullum yanah batah hak'uri akan cewa watarana sai
labari dah haka soyayyar su tah d'aure, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Wanene Saiyadee?<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>AbubakarSaiyadee
d'aaneh ga Alhaji kabeer Fahad dah Hajiya Humaira, shine d'ansu nafari saikuma
k'annen sah uku wato Bilal, Amrah dah Autah Amal, Saiyadee yayi karatun sah nah
likitanci a ABU Zaria sannan yadawo garin kano yayi bautan k'asa Idan cikin
ikon Allah yasamu Offer nah aiki a Private clinic nah International Clinics
& Maternity kano, yana cikin wannan neh Allah yakuma d'aukaka sah inda
yakuma samun aiki a AKTH Kano, so sai yahad'a biyun hakan bah k'arramin
tightening schedules d'insa yayi bah, Saiyadee yakasance mutum mai nutsuwa
Wanda koh magana batah damesa bah, kyakkyawa neh, dogo chocolate in complexion,
his Smile kills😆, nutsuwar Saiyadee bah k'arramin Jan hankalin en matah
yake bah, hakan yasah suke yauwan damunsa dah zancen so Masha Allah bah maikula
matah baneh so one way or the other he's always avoiding ladies, acikin rashin
kula matan nasah Allah yahad'a shi dah watah baiwar Allah a asibiti mai suna
Ummulkhair har yakasance shine mai checking d'inta when it comes to health har
takaida yazama Family doctor d'insu yasamu karbuwa awajan iyayen tah sosai
sabida halayyar sah tagari, Ummulkhair dah Saiyadee sun shak'u sosai tun suna
abin nasu kamar brother and sister, har suka fuskanci suna san junansu, tareda
alk'awarin aure, saidai kuma atimes suna samin matsala sabida Saiyadee is so
devoted to his work itah kuma Ummulkhair tanada zafin kishi amman sabida san
datake masah takan danne zuciyar tah akan wasu abubuwan dah take lacking daga
gareshi, sosai take kuka wani sa'in amman sam batah ta'ba nunawa agidan su bah
sabida tasan iyayen natah suna sanshi kuma sun amince dah abinda ke tsakanin
su, saidai kawai idan abin yadame tah sosai takan fad'awa k'anin tah yayi matah
addua Akan auran tah dah Abusaiyeed d'intah!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Tofah gawani sabon salo koya zaman auren Saiyadee dah
Ummulkhair zai kasance? Kubiyoni muji nima nah k'agu fah🙆🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:09] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛2⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 khadeejah Masscom😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Bayan Ummulkhair
tah tashi daga gajeren baccin daya kwashe tah wayan tah neh first thing data
fara dubawa aikuwa taga har lokacin babu missed calls d'in Saiyadee koh kad'an,
batayi mamaki bah dan sunsaba irin haka dashi hakan yasah tah murgud'a baki
tasoma game abinta, kiran Mummyn tah taji tuni tah tashi batare dah k'ara 'bata
lokaci bah dan amsa kiran Mummyn natah, parlour tafara dubawa batah ganta bah
hakan yasah tanufi d'akin tah, sallama tayi kamun tace Mummy gani nazo,
"toh khairat shigo manah, cikin nutsuwa tah murd'a k'ofan tashige ciki
murmushi tasakar wa Mummyn natah, sannan tace Mummy ganinan, kallon tah
mahaifiyar tatah tayi cike dah so sannan tace khairat yau bazamu ci abinci
baneh koh laifi mukayi neh, naga bakya zancen dinner neh, laa Mummy laifin meh?
bakumin komai bah Wallahi kinga game nake awaya nah duk nah sha'afa bara naje
nad'aura, "Mummy meza adafa toh, murmushi Mummy tayi sannan tace waida
cewa nayi funkaso dah miyar gyad'a koh? naga Abbanku yanaso, tam Mummy bara
nakwaba saina had'a miyan, Mummy nah flour koh wheat? Kiyi mixing both er
albarka, tam shikenan Mummy nawuce kitchen idan Affan yadawo kice masa ina
kitchen, murmushi kawai Mummy tayi,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">tuni Ummulkhair tawuce kitchen tah wanke hannun tah sannan
tah kwa'ba flour+wheat d'in tabarshi yatashi batare dah wani 'batah lokaci bah
tafara had'a miyan Fans bakuji k'amshi ya gauraye groups bah, ai Ummulkhair
badaga nanba when it comes to cooking, phone d'intah dake kan freezer neh
yasoma ringing dubawa tayi taga MyHalf, dasauri tayi picking tasaka akunne
murmushi tasoma yi saikuma tayi shuru batace komai, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummunah....<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Shuru batah amsa bah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummunah koh fushi kike dani neh?<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Sai asannan tace, "uhm uhm bah fushi nake bah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">toh kiyi hak'uri aiki neh yayi min yauwa kema kinsan yanayin
aikin namu koh,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Uhm nasani Allah yataimaka, yak'ara d'aukaka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ameen Ummunah mekike yi?<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Girki nakeyi!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Hmmm kice yau su Mummy zasuci jagwalgwalo,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">hmmm bawani nan, dad'i dai,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">ahh toh mutum da iyakar sah abinda ya iya dafa ruwan zafi
inashi ina wani girki,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">dariya tah kyalkyale masah harda rufe fuska kamar yanah
gabanta, shuru yayi yanah sauraran dariyar tah mai sakashi farin cikin gaske
kaunarta yanah ratsa shi tun daga kai har k'afa, Ummunah yace muryan sah
k'asa~k'asa,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Na'am Ya Saiyadee, tah amsa cikin murmushi,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">I miss U, yace<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">I miss U more ai tafad'a kamar maisan yin kuka, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">bawani nan injiwa, nafi missing d'inki kina ganin koh aiki
nakasa yi sosai sabida banji muryan ki bah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">hhhh toh naji nikam kaga harna gamayin miya fah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ai miyan bazata yi dad'i bah tunda bakiji murya nabah kika
yishi<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Laa injiwa toh?<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Injini mijin Ummulkhair<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">dariya tayi sannan tace "hakadai kace ya saiyadee amman
dah dad'i<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">toh Ummunah mezakiyi yanzu?<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Funkaso zan soya shi kadai yarage min,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">toh bara nazo nataya ki karki k'onamin hannun,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">chab saikace yarinya ai kona k'one ni macece,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">toh kajisu su matah, maza suja gefe<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">dariya tasaki sosai tace Ya Saiyadee nibance bah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">toh naji Ummunah bara nacigaba dah aikinah anjima zan sato
hanya nazo naduba ki, kiyi ahankali kada ki k'one kinji pls, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">toh Saiyadeen Ummu, Insha Allah!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Mezan siyo miki?<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Bkomai tah amsa, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Kin tabbatar babu abinda kikeso,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Eh babu deary,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Toh shikenan later deary bye!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Uhm kawai tace kamar tayi kuka sam bataji dad'in yankewar
wayan bah saidah tad'au kunsan 30mins azaune kafin tah dauki funkaso wanda
daman yatashi tasoma zuba shi cikin mai, tanayi tanah tunanin Saiyadeen tah
gaba d'aya jitayi hankalin tah yakasa kwanciya sotake yau taganshi sun dad'e
basu had'u bah sabida yanayin aikin sah, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Wayartah tah d'auko tamishi message kamar haka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Salam Abusaiyeed Dan
Allah yau kazo I badly want to see U kagafa U promised, pls stick to your
promises dear, I miss U tekia! <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ajiye wayan tayi tacigaba dah abinda takeyi bayan tagama
tazuba komai cikin warmers tayi setting table, d'akin Mummy tawuce straight
idan tah sheda matah cewar tah kammala komai hartayi musu ginger drink, sosai
Mummy taji dad'i tah dinga matah Addu'oi dah shimata albarka, dariya tayi kana
tace bakomai Mummynah hakk'inah neh nah taimaka miki ai, Mummy Dan Allah Ya
Saiyadee yace zaizo nan bada jimawa bah, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">toh shikenan maraba d'an Albarka maza kije ki k'imsa kafin
yazo, Allahu ya Albarkaci rayuwar Ku baki d'aya!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ameen tace tah mik'e cike dah farin ciki hartakai bakin
k'ofar d'akin tah watah zuciyar tace matah, hmmm sai wani murna kike kamar kin
tabbatar dazuwan nashi saikinzo kinyi kwalliyar ki abanza ma baizoba kodai bah
Saiyadee bah kinmanta aikin shi yafiye masa komai arayuwa, take taji mood
d'inta yacanza tayi deciding taje tad'au phone d'intah tacigaba dah game
d'intah kawai bayan tayi wanka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>On reaching to her
phone taga hanging message from MyHalf, murna cikin Ummulkhair ba amagana tuni
tah manta dah dukkanin damuwan tah tanah bud'ewa taga reply kamar haka<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>"Insha Allah
Ummunah dah anyi magrib kafin Isha'i zaki ganni nima I also miss U, sonake
naganki heartbeat!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Tsalle tayi dan
murna tuni tayi hanyar fita adaidai k'ofa tah tarar dah Affan tsaye yanah
kallon tah yanah dariya kamun yace, "Sis kawo muraba kyautar kud'in dakika
samu dake sakaki murna haka!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:09] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛3⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 Nakundu& Zeesarkie😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Murmushi tayi,
sannan tace "Affan sai yanzu sarkin yawo bayan tun d'azu nake jiran ka
mushirya dinner tare amman harna gama baka dawoba, kai sis daga cewa kawo kud'i
muraba shine nacanza topic d'in koh, A'a wallahi Saiyadee neh zaizo fah shine
nake murna bah wani abin bah, lallai Sis bah k'arramin so kike masah bah aini
kud'i kadai zan iyawa wannan draman naki, lilbro kenan Saiyadee yafiye min duk
wani jindad'in Rayuwa kawai abinda nakeso dakai kayi manah Addu'a Allah ya
Albarkaci gidan auren mu sabida shine wanda nakeso mu zauna tare har k'arahen
Rayuwa tah saidai kuma yanayin aikin sah ka iya canza manah tsari gaskia hakan
yanah bani tsoro sosai, Sis karkiji komai ai dazaran kunyi aure zaiyi dropping
aiki d'aya for your sake, toh Ameen lilbro tace kawai tashige ciki tanah
murmushi sosai, wanka tashiga tanah fitowa taje gaban mirror tah shafe jikinta
dah mai showerCap d'inta tacire tah taje gashinta tasa mai tah kwashe dah
ribbons, doguwar rigar flay nah<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>atampha
lemon mai ratsin pink ajiki tah tashi tadauko acikin wardrobe d'intah tasaka
sannan tah d'auki d'ankwalin tah tazauna tah tsara d'auri akanta babu wani make
up datayi haka tabar fuskanta plain amman tayi kyau sosai tunda daman mai kyaun
Ce kuma gashi atamphan ya haska tah sosai, shimfid'a tamusu a corridor nah
Sitting room sannan takoma tayi zaman jiranshi aciki, kiran shine yashigo
wayarta dasauri tah d'aga tasaka akunne, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">hello Ummunah yace in a serious tone<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Uhm kawai tace tayi shuru dan tanah tsoron kar yace matah
bazai samu daman zuwa bah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummunah bakya jina neh?<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">inajinka tafad'a cike dah tsoro,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummunah aiki yayi min yauwa bazan samu daman shigowa bah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">tuni hawaye yacika idontah taf, takasa magana<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummunah kinyi shuru bakice komai bah?<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">tasan yanzu kam bazata iya amsa shiba sabida hawayen datake
tah k'ok'arin dannewa ya gangaro hakan yasah tah yanke wayar kawai,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">sai asannan tagode wa Allah daba tayi applying makeup bah
sabida hakan yabata daman kuka sosai,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Wayarta taji yanah ringing kamar bazata d'ago bah saikuma
tah d'ago ganin wanda yake kira yasah tah kauda kanta tacigaba dah kukan tah
wata zuciyar sai cemata take k'ilama wajan watah yake zuwa sai shuka ki yake
kamar gyad'a idan bahaka bah duk aikin mutum ace baya zuwa wajan wacce zai aura
akai akai, toh dutse neh shi bayajin yanason ganinki neh koyaya? haka tah dinga
tunani haryayi matah 3missed calls, Affan neh yayi knocking k'ofar tah saurin
goge fuskarta tayi asanyaye dan tasan wanda ke knocking, shigo tace kamar wata
mara lafiya, shiga yayi yace Sis keda kike tah jiran yayanmu tun d'azu kuma
shine yanzu zaki barshi awaje batare dah kinfita kinsame shiba,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">waro ido tayi alamun batah fahimce shiba, kallon tah yakuma
yi sannan yace pls ki tashi yace dan Allah kifito,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">sabbin hawaye neh yasoma gangaro matah itah tah rasa nah
farin ciki neh kona bak'in ciki, cike dah tashin hankali yasoma tambayar tah
meke damunta kasa bashi amsa tayi sai speed d'in tears d'inta daya k'aru ficewa
yayi yawuce d'akin Mummyn su direct bayan yayi sallama yake matah bayanin
abinda yafaru, aituni Mummy tah tashi hankalin tah tashe tawuce d'akin
Ummulkhair tanah shiga tasoma tambayar tah cikin rud'ani, dasauri Ummulkhair
tasoma goge hawayen tah tana cewa Mummy bakomai fah, kallon k'aninta tayi
sannan tace kaikuma wayace kaje kawani kira Mummy, itadai Mummy sai rakata take
dah ido cike dah damuwa tace dan Allah kifad'a min Ummu meke sakaki kuka? karki
'boyemin komai bakida wacce tafini, wani sabbin hawaye neh yake forming idonta
tah d'ago kai tah kalli Mummy natah tace Mummy bashine bah bayan nagama
shiryawa yace wai aiki yayi masah yauwa bazai samu zuwaba kuma ashe haryazo tah
k'arashe maganar tanah goge hawayen tah dabayan hannu, Mummy taso taji haushi
amman kuma saitaji tausayin tah kasancewar batada hayaniya kuma batah taba kawo
wani gida tace shi takeso bah bayan Abubakar hassali ma batah kula samari tasan
aiki yanah hana Abubakar shigowa yanda yakamata, shiyasa takan tausayawa
ertatah sabida taga alamun cewa Auren su dah Abubakar babu fashi saidai wani
ikon Allah, itadai kawai fatan tah kada Ummulkhair tacutu agidan Dr.Abubakar
ajiyar zuciya tayi sannan tace nidai khairat kink'i kigirma yanzu akan hakan
kike kuka saikace yarinya maza tashi bansan iskanci kije bawan Allah najiran ki
awaje, tashi tayi sannan tace, "toh Mummy sainadawo tafice abunta, zaune
tasame shi kan shifid'ar yanah wasa dah mukullin mota hankalin shi duk atashe,
yanah ganinta yayi saurin mik'ewa idon tah yagani alamun tayi kuka bai iya cewa
komai bah sai<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">"Ummunah.....Ummunah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">basar dashi tayi taraba tah gefen shi tazauna tah d'ayan
side d'in, zama yayi jiki asanyaye yace Ummunah d'azu munah waya kika yanke
wayar kuma inatah kiranki bakya picking wani abun akayi neh, shuru kakeji tak'i
kula shi hakan yasah ya dinga batah hak'uri yanah fad'in shifa wasa yake matah
wallahi dan yanah k'ofar gida sanda yakira tah, fashe masah dah kuka tayi kawai
hankalinsa bah k'arramin tashi yayi bah daidainan Affan yafito masah dah drinks
tuni yamik'e yanah fad'awa Affan yataya shi bawa Ummunsah hak'uri shi baisan
abinda yayi matah bah tak'i kula shi, kasa cewa komai Affan yayi tray d'in
hannun shi ya ajiye sannan yayi ajiyar zuciya! Yace sis kiyi hak'uri anan cikin
haka Daddyn su yadawo!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:10] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛4⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 Ol members of (P~M~L)👄 Pure Moment Of
Life Writers😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>K'asa Affan yayi
yace "ina yini Daddy sannu dah zuwa, tuni shima Dr. yayi k'asa yagaishe
sah cike dah ladabi, amsasu yayi atare yanah fara'a sosai, Dr masha Allah yau
kaine agidan namu toh nayi shigowar sa'a kenan dan daman Inasan ganin kah muje
daga ciki koh, murmushin yak'e Dr.Saiyadee yakeyi kawai dan gabad'aya hankalin
sah yanakan Ummulkhair, biye suke dah Daddy abaya harzasu wuce Daddy yaji ance
"Daddy sannu dah zuwa ya aiki Allah ya taimaka, zuciyan shi fari tas ya
amsa dan yasan it's no any other person than his princess, kuka kikayi
princess, A'a tah amsa kanta ak'asa murmushi Daddy yayi yawuce ciki dan yasan
bazai wuci itada Dr. d'intah bah, bayan sun shiga neh Daddy yake tambayar su
Affan akan sunci abinci inda yace masah A'a tukunnan dai, hakan yasah yace
Affan yamik'a masu warmers d'in dah plates, batare dah batah lokaci bah ya kawo
komai kan center rug Daddy yace yayi serving d'insu tare aikuwa hakan akayi
tare sukaci abinci su ukun, saidai har lokacin Dr.Saiyadee ci kawai yake amman
hankalin sah yanakan Ummunsah, dukda hakan baihana shi jin dad'i abincin bah
danshi baima taba tunanin iya girkin tah yakai hakan bah, bawani cin abincin
yayiba yace yak'oshi gefe yaja yazauna yana jiransu su kammala, bayan sun gama
Affan yatashi ya k'imsa waje sai asannan Daddy suka kuma gaisawa dah Dr. sosai,
shuru neh yabiyo baya kafin daga bisani Daddy yace daman bakomai baneh akan
zancen Ummulkhair neh lokaci yana k'urewa kaga itah kadaice 'ya mace dah Allah
yabamu toh kuma tasamu karatu nah boko dah addini yanda akeso ni ina ganin
yakamata ace yanzu tanah gidan mijin tah tunda yanzu babu makarantar datake
zuwa saidai idan tanah sha'awan yin masters nangaba kuma mijin tah yabarta toh
saitayi, danni gaskia kozatayi masters bazan bari tayi yanzu bah saidai agidan
mijin tah tunda Allah yasa tagama komai cikin k'ank'anin shekaru 20 toh nafisan
tayi auren tah tun tanada sauran k'uruciyar tah shine nace bara nah tuntu'be
kah naji yaya abin yake daga gareka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Saiyadee bah k'arramin jindad'in maganar yayi bah aranshi
shima yanasan d'auko zancen amman kunya tahana shi, kanshi ak'asa yace Daddy
nah k'arasa gidanah dake zooroad jibi idan Allah ya yarda za ayi painting koh
inah daganan kuma an kammala komai, murmushi Daddy yayi dan yasan hakan yana
nufin ashirye yake neh,<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>toh shikenan
Allah ya sanya alkhairi banasan komai yawuce cikin wata d'aya munriga munyi
magana dah mahaifiyar tah kuma yanzu zankuma sanar dah itah yanda mukayi dah
kai, Dan Allah sai afara shirye~shirye akuma sanar dah manya sai azauna akai,
Allah yak'ara rufa manah asiri bakid'aya Nagode sosai, toh Daddy nagode sosai
yace cike dah murna harzai tashi Daddy yace, "meh akayiwa 'yar tawane naga
tanah kuka", murmushi yayi yace Daddy bakomai yarinta neh irin nah
Ummulkhair, toh shikenan Allah yayi muku Albarka Allahu yasah ayi asa'a, Ameen
yace yayiwa Daddy godiya sosai kana yabar parlour, yanah fita yatarar dah itah
dah Affan sai hira suke tanata kyalkyale dariya kamar bah itah tayi kuka d'azun
bah, Affan yanah ganin shi yace aw yayanmu har kafito, sannu Bismillah tashi
yayi yabasu waje, zama yayi yanata kallon tah kunya Ce takama tah tarufe fuskar
tah dasauri tanah dariya, murmushi yayi yace Ummunah yau rowar dariyan kikemin
kuma, kinsan yanda nakesan ganin fuskan nan taki d'auke dah dariya kuwa Dan
Allah kibud'e fuskar ki nagani koh zand'an ji sauki araina kinji Ummunah, A'a
nak'i d'in nima saina rama kaiba sarkin saka mutum kuka bah, tafad'a tanah
murgud'a masah baki tareda kauda kanta, dariya yasoma yi hakan yasah tajuyo dah
kanta tazuba masah ido, menene kike kallo nah kuma, kema aisaiki daina kallo
nah babu ruwan wani dawani, dariya tayi tace Allah Abusaiyeed murmushin kah koh
dariya nakesan gani kawai yanah sakamin wani farin ciki dajin dad'i neh, Chab
aikuwa bazaki gani bah! baya yajuya matah waishi sam<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>bazata ga fuskan shiba balle murmushi, tuni
takoma kallar tausayi tayi shuru sannan tace toh yi hak'uri nadaina, juyowa
yayi, sannan tah kalleshi tace, toh bakaine bah kawani cemin bazaka samu zuwa
ba bayan kazo kasa naci kuka na'bata kwalliya nah tayi magana idon tah harya
soma kawo ruwa, toh yi hak'uri Ummunah Dan Allah kada kimin kuka wlh bansan
hawayen ki koh kad'an yazuba ki tausaya min kimin rai, gogewa tayi sannan tayi
murmushi tace, toh nadaina sannu dah zuwa ya hanya, amsawa yayi cike dah kauna,
drink tadauka zatah bud'e tazuba masah a tumbler yahana tah wai yaci abinci,
Ummunah daman haka kika iya miya, kin iya girki fah, murmushi tayi tace nagode
Abusaiyeed, kodai funkaso kawai kika iyane naga kin kasa magana, dariya tayi
tace eh manah shi kad'ai nah iya sai dafa ruwan zafi, Allah Ummunah toh
shikkenan hakan nakesan abina koh babu abinda tah iya, kallon shi tayi tasaki
dariya tah kauda kai wai itah kunya,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Amaryatah taji yace anutse dah murmushin sah, dasauri
tad'ago kai tanah kallon shi tareda mamakin sunan daya kiratah dashi, shuru
tayi hakan yasah yayi murmushi yafad'a matah komai yanda sukayi dah Daddy, wani
kunyan kowama taji tanaji barima dayayi matah zancen Lefen tah<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">kai nidai ahaka nabaro su suna zancen lefe nayi gaba dan
naga abin nasu bamai k'arewa baneh daga baya maji shawarar su akan lefen!
Ahanya tah nazuwa parlour wajan su Mummy dah Daddy danjin abinda suke
tattaunawa nahango Miss biey cholli tanah yiwa su Ummulkhair la'be oh Allah
yashirye ki zeesarkie takoya matah😌 halin la'be kuma kuyi ku kawo naku
Doctors d'in namuku auren nan nahuta kawai!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:10] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛5⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 My Flesh and Blood khadeejah Yusuf Ahmad my one
nd only Mass communicator with the most Golden voice ever my choosing, My
Oxygen, I heart YOU So Much Sweetheart, Allah ya Albarkaci rayuwar ki duniya
dah lahira, AMEEN<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">I Love U So Very Much😍😍😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ina shiga ciki
natarar dah Mummy dah Daddy sunacan parlour'n Daddy, har Daddy ya fayyace matah
komai yanda sukayi dah Dr.Saiyadee, shuru Mummy tayi kanta jingine ajikin
kafad'ar mijin natah, haba my dear yanaji kinyi shuru bah magana aisaiki Ce
wani abun koh inkika yihakan aisaiki tayar min dah hankali, ajiyar zuciya Mummy
tayi tah kalli mijin nata idanun tah duk sun ciko taf dah hawaye, Subhanallahi
Alhaji AbuSufyan yace tareda jawo matar tasa jikinsa rarrashin tah yashiga yi
harya samu tayi shuru sannan yabuk'aci yaji dalilin kukan tah, shuru tayi kana
tace, "kawai ina tsoron auren Ummulkhair dah Dr.Saiyadee neh Nasan yaro
neh mai tarbiya dah ladabi dah biyayya kuma nasan suna san junansu but amman
kaga he's so occupied with his job that he hardly visits her, kuma am not even
sure zai dinga samun time dinta idan sunyi aure kaga nah tambaye tah time
dayake komawa gida kullum at night tace 12am, and 12am its already midnight fah
sweetheart tafad'a cikin kuka sosai, shhhh Daddy yake cemata sannan tacigaba
dacewa yafita dah sassafe kuma yadawo by that time of the night haka zatah
dinga zama itah d'aya agidan kullum, zaman auren fah? Baza suyiba sabida aiki
sweetheart am not sure about this gaskiya am so confused tak'arasa maganar tah
crying profusely, shhhh sosai Alhaji Abusufyan yake rarrashin tah yanah kwantar
matah dah hankali, bayan duk sunyi shuru sannan yayi ajiyar zuciya yace, Hadiza
kina jina, hak'uri zakiyi daman d'an Adam baya samun komai yanda yaso, kullum
arayuwa bakida buri sama dah kisamu Namiji mai ladabi, dah hankali dah Imani
wanda zaikula dah 'yarmu, toh yanzu ansame shi yanada, tarbiya, Ilimi nah
addini dah boko, yanada aikin yi, yanada gidan dazai ajiye tah, kuma musulmi
neh mai imani kema kuma kin tabbatar dah kaunar dayake wa 'yar tamu, shin kin
ta'bayin sujjada kin godewa Allah akan wannan qualities d'in nashi? baki
ta'bayi bah sabida hankalin ki yanah hangen 'yarmu zatasha wuyan zaman gidansa
sabida yanayin aikin sah, toh duk qualities d'in daya had'a asama shine burin
kowacce 'yamace kuma iyakar addua dah uwa take nemawa 'yarta kenan akan miji
nagari, batun lokacin dayake barin gida yakoma wannan bah hurumin ki baneh ai
'yar tamu tasan dahakan tah amince tanah kaunar shi kuma tayarda tah aureshi
kuma tunda har take iya jiranshi yaje gida shabiyun daren kafin suyi waya tofah
shi takeso kawai, bafa bashi khairat zamuyi hakannan bah AMANA CE fah( AMANA CE
is one of my upcoming novels Insha Allah) kinga kowa yasan nauyin AMANA idan
yadauka tareda alk'awarin kulawa dah itah shikenan kawai munamu yanzu shine
addua dah fatan Alkhairi agare su sabida yazama dole idan sunyi aure yayi
adjusting kuma namiji neh dole idan yanah buk'atar matar sah koh yanasan ganin
tah yaje gida, sabida haka abinda nakeso dake kiyi listing kayan kitchen dah
duk wani abinda take buk'ata zanbaki kud'in asiya matah Insha Allah, idan yaso
saimu siya matah furnitures awajan aboki nah Alhaji Ashraaf Amsaad mai
Company'n Furnitures d'in <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🚪Amsaad
Brand New London🛏<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;">
</span>Furnitures🛋<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Make ur home🏡 ur palace🏩🏨)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">saimuje wajan nashi taza'ba achan kawai koh?<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Murmushi Mummy tayi sosai tareda cewa toh dan yanzu hankalin
tah yakwanta dah kalaman mijin tah kwanciya tayi jikin shi yakunna musu news
suna kallo, Knocking sukaji atare duk suka kalli k'ofar Mummy Ce tayi adjusting
zaman tah sannan Daddy yace Bismillah shigo manah, Ummulkhair Ce tashigo dah
Sallaman tah durk'usawa tayi, "tace Mummy, Daddy ina yininku, lafiya klau
princess sarkin shagwa'ba harkin gama kukan neh, murmushi tayi tace mummy daman
zuwa nayi nafad'a muku cewar yace.......<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Saikuma tayi shuru tanah raba idanu tashi tayi takoma jikin
Mummyn tah tah mak'ale sannan tafad'a matah wani abu akunne dariya Mummy tayi
tace toh lefen naki neh bazaki iya had'awa bah har sai kintambaye ni, yanzu ke
khairat bakisan abinda kikeso bah waini yaushe zaki girma neh haka, cinno baki
tayi waje kamar tayi kuka tace, "Mummy shine nafad'a miki abu akunne shine
kika fad'a Daddy yaji koh, kallon tah Mummy tayi tace, "shi Daddyn naki
kenan", hijjabin tah tad'an jaa gaba kad'an fuskanta yadaina nunawa sabida
wani kunyansu dataji, murmushi Daddy yayi yace toh ai princess dacewa kikayi
natoshe kunne nah kawai, tashi tayi dah gudu tafice sai asannan Mummy take cewa
Daddy wai Doctor Saiyadee neh yace tayi listing dukkah kayan lefen tah idan
tanaso tayi dakanta tayi mishi costing komai zebata kud'in idan kuma bazata
iyaba zai saka Aunty sah tayi matah, shide duk abinda takeso yake buk'ata
acikin list kuma kaga 'yar taka batasan abinda takeso bah wai saini zanmata,
A'a gaskia kiyi matah list d'in aikinfi kowa sanin abinda ake buk'ata tunda ke
zaki had'a nah d'anki Affan bansan sankai itama saikin yimata, lallai Alhaji
zakah aurar dah Ummulkhair d'inma bazaka dena shagwa'ba tabah toni wannan abu
har ina, matse hannun tah yayi cikin nashi yace dear pls kiyi list kibata
tabashi sukawo lefen kawai ke kyaji dah kitchen utensils d'in kawai kinji
tawan, toh Abban kids d'inah naji, dariya duk sukayi yajawo matarsa jikin sah
nima najawo k'ofar nak'ara gaba.<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>3 weeks later<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:10] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛6⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 My Momma Nafisa Nuhu SadNaf my half my
sweetheart Allah yabar kauna 'yar Gatan SadNaf tanah Alfahari dah itah, Sannu
dear nah mai kaifin baseerah Allah ya Albarkaci rayuwar ki duniya dah lahira,
AMEEN<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">I Love U So Very Much😍😍😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>3 weeks later<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ummulkhair ce
zaune tayi uban tagumi duk tabi tah rame tah lalace hawaye neh yake tsiyaya
daga fuskarta shaf tama manta dah AntyMuna dake gabanta, mtww wai Ummulkhair
menene hakan akan za ayi miki aure kike manah shegen kukan nan kinbi kin lalace
sabida zakije gidan miji akanki akafara neh kokuwa bakya zuwa bikin friends
d'inki haka kikaga suna tada hankalin su akan aure, U beta use your brain
kifara cin abinci sabida in the next one week kina gidan mijinki haka za akaiki
gidan doctor d'in a k'anjame jibi k'ashin wuyanki uwa nayi ajiyar phone d'inah
aciki, ga kankanar dah ayaba chan nah yayyanka miki juye gwangwanin peak uku
aciki kizauna ki shanye, kallon AntyMuna take kawai takasa daina kukan AntyMuna
tah lura dah yanda take duba wayan tah akai akai koda yaushe kuma as soon as
tah ajiye phone take fara kuka kasancewar yanzu satin tah biyu agidan tunda
akace ansaka date d'in bikin tazo, kallon tuhuma take matah kafin tace
Ummulkhair idan kinajin kunyar Mummyn ki bazaki iya fad'a matah abinda ke
faruwa bah ni kifad'a min menene matsalar ki, karfa kicutar dakanki abanza
speed d'in tears d'intah k'aruwa yayi jikin AntyMuna bah k'arramin mutuwa yayi
bah, Ummulkhair koh kinyiwa wani alk'awarin aure neh bayan doctor mesah kike
yawan duba phone d'inki akai~akai kamar mara gaskiya, koh bakya san auren
doctor kinfasa? duk cikin tambayoyin dah AntyMuna takewa Ummulkhair babu wanda
tasamu amsa saidah Ummulkhair tayi kuka mai isanta sannan cikin kakarwa tace
Anty Maimuna nashiga uku ina zansaka kaina wallahi tun ranar dah doctor yazonan
yace nayi mishi list d'in lefe<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>ban k'ara
ganin shibah k'arshe sai Affan nabawa list d'in yakaimasa office, kullum saidai
text yanzu kuma sau d'aya muke waya asati wayan ma bayafin 2mins zaicemin he's
sleepy he needs to sleep sabida zaje aiki washe gari saidai text kullum cikin
bani hak'uri yake wai aiki yamishi yauwa kuma as soon as he gets back home
bacci yake kwashe shi due to much stress wai natausaya masah namishi Uziri, but
Anty am confused at this very stage I can't, yanzu nake buk'atan Abusaiyeed
yanuna min irin kaunar dayake min nakusan rabuwa dah iyayen nah zuwa gidanshi
shin wani irin rayuwa zamuyi dashi agidan ni ina ganin yakamata ace no matter
how busy he can be yayi creating time for this very special events of our life
is not as if we are going to get married thrice Anty wlh am scared nah rikice waishi
Abusaiyeed baya ganewa neh dawanne zanji barin iyaye nah koh halin daya jefani
bashida emotions neh koyaya?tah k'arashe maganar tanah tsananin kuka, rungume
tah AntyMuna tayi tanah rarrashin tah tabbas tasan wannan bah k'arramin zance
baneh ace biki saura 1week babu labarin ango tun 3weeks back and kuma suna gari
d'aya bawaiba wannan wani irin aiki neh haka, ajiyar zuciya AntyMuna tayi
sannan tace khairat are U really sure about getting into this? I fear for U
dear, its so Unfortunate ace mijinki baisan bikin ku yakusa bah, kada kije
gidanshi asamu matsala fah idan bazaiyuba afasa mu farincikin ki mukeso nisaina
gudu dake abu maisauk'i!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>A'a Anty Maimuna
wallahi ina san Abusaiyeed fiyeda tunanin ki wlh ina kaunar shi bazan iya
rayuwa tah babu shiba shinake so nah aura idan baku auramin shiba zan shiga
mawuyacin hali ni bazan iya barin garin dayake bama, itadai AntyMuna kallon tah
take baki wangalau cike dah mamaki kafin tace wani abu sukaji anabuga k'ofa
shigo cewar AntyMuna, Mummy Ce tashigo dah sallaman tah, kallon khairat tayi
wanda har yanzu takasa stopping tears d'inta sannan tace aw kuka kikeyi? zakima
daina neh, Maimuna kibar khairat indai itace zaki gaji, daman zuwa nayi nah
tambaye ki za aje bugo miki katin events d'inki ayi harda nah d'aurin auren
sabida banga alamun mijinki yasan dah bikin nanba, kai ak'asa tace Mummy Kuyi
hak'uri zankira shi naji aiki neh yayi masah yauwa, toh Allah yakyauta, ina
jiranki fah Mummy tace sannan tafice abinta, tanah fita Ummulkhair tafashe dah
sabon kuka tace AntyMuna Kinga irinta koh, katin d'aurin auren nasama
dayakamata ace angama rabawa en uwa dah abokan arzik'i bai bugo bah, shuru
AntyMuna tayi kamun tace lefenki fah, bayan ankawo baizoba, eh baizoba amman
yazuba min kaya masu kyau kuma komai awadace kinga fah babu abinda bansa alist
bah amman still saida aka k'ara dah abinda babu cikin list d'inmu, eh hakane
tabbas lefenki yayi kyau dan babu inda bazai shigaba, hakanma yanuna yanah
kaunar ki tunda baya kyashin yimiki abu kona nawane wani namijin yanada shi amman
sabida yadauki yiwa matarsa abu Asara bazaiyiba (Maza Ku Gyara Hali), hakane
Anty daman yanada zuciyar yineh yakan fad'amin dukkan mai nema yanah tareda
samu kuma maibayar wa baya rasawa, toh amman atimes banah gane Abusaiyeed wlh
dabadan naga yanda iyayen sah suka tak'ura ayi wannan auren bah toh dacewa
zanyi Dr.Saiyadee ya yaudare ni yagudu yafasa aurena iyayen shine kawai suke
k'arfafa manah gwiwa kullum yace aiki~aiki it's sickening wlh, pls shhhhh dear
dauko wayarki ki kirashi yanzu, batayi niyya bah dan tasan abanza amman kawai
tah dauko dan batasan tah musawa Antyn tah kiranshi tashiga yi lucky her tayi
mamaki sosai yayi picking,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Hello Ummunah kokuma nace Amaryatah wanne kikafi so,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Rai a'bace tace ni badan hakan nakira kabah kah kawo katin
d'aurin auren za arabawa mutan arzik'i,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummunah fad'a mukayi neh I dnt get U why being so naive u're
acting strange wifey<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">U really got some nerves Abusaiyeed kanada bakin tamabaya
namah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Alright am so sorry I kno its all about rashin zuwana kiyi
hak'uri sha'anin aiki neh kud'ad'en danah miki transfer zasu isheki koh, pls if
U need anything don't hesitate to text me zanyi transfer immediately,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">And kuma about the I•V wlh deary bansamu time d'in bugawa
bah zantura miki kud'i kutaya ni buga wanda za araba anan idan yaso ni I will
juz invite my friends nd colleagues via text messages<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummulkhair juz couldn't believe her ears batasan sanda
tafashe dah kuka mai k'ona raiba,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Hankali atashe yasoma cewa Ummunah wani abun namiki neh? Dan
Allah kiyi hak'uri U kno I love U pls halt those tears wlh aiki neh, Ummunah
idan bah aiki bah akwai abinda zai nisanta ni dakene for 3 good weeks aisaidai
aikin!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Cikin kuka Ummulkhair tace wallahi Abusaiyeed I promise U
idan har baka kawo katin d'aurinmu this night bah nafasa wannan auren har abada!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:10] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛7⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 My deary khadeejah Nakundu my one nd only Rigima
girl, with the most confident character ever, 'yar Gatan Mhiss B~hal, Allah
yajik'an Momma yahad'a Ku Aljanna Allah ya Albarkaci rayuwar ki duniya dah
lahira daduk abinda kikasa agaba, AMEEN<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">I Love U So Very Much dije😍😍😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Wayar tah jefar
k'asa tanah kuka sosai, tuni jikin Dr.Saiyadee yafara rawa duk yarasa inda zai
saka kansa wani zufa neh ke keto masah tako ina he can't even stand on his own
yayi loosing feet balance gabad'aya, Sudais abokin saneh yayi saurin rik'eshi
zaunar dashi yayi kan kujera saidai dukda azaune yake baidaina jin jiri bah
saima abinda yayi gaba, Man put urself together what's wrong haka menene cewar
sudais cikin rud'ani, hannun shi Dr.Saiyadee yarik'e cike dah rud'ani idon shi
yacika taf dah hawaye yace, "wai bazata aure nibah tafasa friend wallahi
bazan iya rayuwa bah Ummunah bah she's my happiness, she's all I ever wanted
bazaka gane farin cikin datake sakani bah idan tak'i aurena tah ina zanfara in
fact zuciya nah fashewa zaiyi kawai namutu, Ummunah Ce Ummunah Ce babu wanda
zan iya barwa, Ina sonta ina kaunar tah tawace tawace!!! sosai sudais yatausaya
masah ruwan sanyi yayi saurin bashi bayan yad'an samu nutsuwa neh yake tambayar
sah abinda yahad'a su dah Ummulkhair a hankali yake fad'a masah abinda yafaru
Sudais shima saida ranshi yaso ya'baci sabida it doesn't make any senses ace
mutum bashida time nah buga katin d'aurin auren sah, haba friend wlh baka
kyauta matah bah aidole tayi fushi idan da k'anwata Ce wlh bazan bakaba saidai
kayi hak'uri tashi muje duk inda zamu samo kati Emergency yau sai anbuga manah,
wlh tanah hak'uri dakai sosai kuma shiyasa kasamu damar yimatan hakan daa
kanayin 3weeks d'in kafin kaje wajanta amman lokacin ba ayi fixing date d'in
bikinku bah amman yanzu neh yakama ace kanah sintirin zuwa harsai tah dakatar
dakai gaskia bakah kyauta bah tashi muje, jikin shi nah rawa yamik'e yace muje
Dan Allah friend am confused tashi sukayi Sudais yakarbi mukullin mota yayi
driving dan yakula Dr.Saiyadee ba iyawa zaiyi bah haka suka dinga yawo harsuka
samu wajan printing nah <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{Deejjah's pinkflaw Printing Materials}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Anan suka samu aka buga masu kati harda jakama sudais yabada
ayi amatsayin gudumowar shi saidai jakan ranar laraba zai amso amman saida
sukayi adding to the original amount, aikuwa Dr.Saiyadee cikin hanzari yakalli
Sudais yace muje yisauri Dan Allah Ummulkhair tanah jirana pls friend, sallan
fah Saiyadee bazakayi Magriba bah? A'a muje idan munje kawuce masjid ni zanyi
awajan tah, girgiza kai yayi yace kaga amfanin zama dah iyali kenan saikasan
damuwan su Dan Allah koh kunyi auren tryna adjust friend, shuru yayi kawai
kafin daga bisani yace pls k'ara speed d'inka pls, within a short period of
time saigasu<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>ak'ofar gidansu Ummulkhair,
Affan neh yaganshi yayi saurin kar'ban shi tah back door yabud'e masah sitting
room kasancewar bak'i sunfara cika gidan, gaisawa sukayi saidai Affan yaga
yanayin sah, shiru kawai yayi yace bara nakira tah gabad'aya kasa zama yayi
saikai kawo yakeyi,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummulkhair kuwa cewa tayi sam babu inda zataje Affan ya
kar'bo katin kawai idan kuma babu ga lefensa yawuce dashi tafasa auren wallahi,
saidai AntyMuna tashawo kanta dakyar sannan tah dauki hijjab d'inta tawuce
sitting room, shiga ciki tayi aiyana hango tah yanufo tah kamar zaitashi sama
hannun tah yarik'e a rikice yace Ummunah wai bazaki aureni bah, Ummunah dagaske
neh? harga Allah taji yausayin sah aranta sabida batah ta'ba ganin shi cikin
wannan yanayin bah duk ya rikice idanunsa sun rina zuwa jaa gashi sun cika taf
dah hawaye, kauda kanta tayi cikin hawaye tace bani katin idan kuma babu nasa
Affan yafito makah dah lefenka, k'asa yayi akan gwiwowin sah gabad'aya jiyayi
kamar blood yadaina running a vein d'insa, Ummunah dagaske bazaki tausaya
minbah ai ina tunanin masoya sunayiwa junansu uzuri wlh bazan iya rayuwa tah
babu ke akusa dani bah yak'arashe maganar yanah maijin wani zazza'bi, k'asa
itama tayi cikin kuka tanah kallon shi tace wasa nake makah Inasan kah nima
bazan iya rayuwa tah babu kaiba amman Dan Allah kadinga kyautata min ya Saiyadee,
kaima kasan kafisan aikin kah akaina amman Dan Allah kadaina nunamin hakan kaji
alfarma nake rok'an kah pls Mylove, kuka sosai take, jikinshi sosai yamutu
jiyake kamar yajawo tah jikin sah hakan kawai ya danne yazuba matah ido jakar
hannun sah d'an k'arramin yamik'a matah tah kar'ba katine nah d'aurin aure mai
kyaun gaske yasha ado d'iba tayi aciki tabasa kamar guda 120, sannan tayi
murmushi tace Mungode Allah yasanya Alkhairin sah aciki Allah yasah ayi asa'a,
harta tashi zatah fita yamik'e arikice yace Ummunah zaki aureni zaki zauna dani
har k'arshen rayuwa tah, wlh Ummunah ina sonki sosai pls Ummunah Dan Allah
kirufa min asiri muyi auren nan cike dah tausayin sah tace, indai zancen soneh
toh 'bayan kai Abusaiyeed duk wani namiji dutse nake daukan shi arayuwa tah
kainake so kai zuciya tah taza'ba zan aure kah kuma zanyi hak'urin zama dakai
Insha Allah, tanah kaiwa nan tah kwaci hannun tah tafice dasauri, saida yadau
time sosai kafin ya iya barin cikin gidan cikin mota yasamu abokin nashi, suna
fita daga unguwan su Ummulkhair Sudais ya tambaye shi koh gida zasu wuce and
his reply was A'a Asibiti zan koma inada aiki akwai patients suna jirana shidai
Sudais kam mamaki yacika shi amman<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>bace
masah komai ba yawuce dashi International Clinics and Maternity straight!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ranar Biki<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:10] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛8⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 My Oxygen khadeejah Yusuf Ahmad{D Choosing
Masscom} my one nd only Ebony Beauty, My Queen with the best royal Qualities
Eva, The blood that runs tru my vein, ina kaunar ki ina Alfahari dake My
Valuable Jewel, Allahu ya JIBANCI AL'AMURAN ki fid dunia wal Akheera Sakallahu
BIL JANNATY deary nah! AMEEN! I hrt U So Very Much Myn😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ranar Biki<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Wai wai wai!!! zanso
kuga cikar dah gidan Alhaji Abu~Sufyan yayi mutane neh makil tah ko'ina
kasancewar wannan neh karo nafarko dazai aurar da 'ya kuma Ummulkhair kadaice
Ce 'yar tasah hakan yasah en uwa dah abokan arzik'i suka garzayo dan achashe
dasu, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Hajiya Hadeeza sai kar'ban baki takeyi akai~akai Masha
Allah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummulkhair jikin tah duk asanyaye dukda cewar tun ranar dah
Abusaiyeed yakawo matah katin d'aurin aure bai k'ara dawowa bah sabida yanayin
aiki itadai yanzu bah abinda takeji bah kenan dan tasan duk tsiya dai gidan shi
za'a kaita, ita yanzu tunanin tah rabuwa dah gida hakan bah k'arramin rama
yasaka tabah bikin kwana uku neh haka akayi Yini dah kamu jiya jumma'a babu
aikin dah takeyi saina kuka, yau asabar yakama lunch by 1pm to 4pm inda za kuma
ad'aura dah mother's night 5pm to 10pm sannan washe gari ayi d'aurin auren
dasafe walima dah rana 1pm-4pm bayan angama kuma dah yardar Allah akai Amarya
gidan mijinta dake unguwar Zooroad dah yamma, tofah Allah yanufa, Masoya biyu
zasu mallaki junansu, naga fans d'inah awajan ba amagana duk inda nah waiga
saina hango su cikin ankon su nah Blue Cord Lace dah Silver Head Attire gaskiya
kunsha kyau groupies saidai nace daku Sakallahu khairan dah karar dah kukayi
manah naganku iyaye dah enmatah, ahab ni daman nasan Zeesarkie, DeejahNakundu
dah ZeeMiss biey cholli bazasu fasa kwaso shoki bah adaiyi ahankali kada akarya
k'ugu😌, ga subulluwa ana lomar shinkafa ungo ruwa kada ki kware fah,
Sannu Maman Sadeeq Lagos, tun daga Lagos har zuwa kano bikin Dr.Saiyadee gaskia
nad'au nauyi ajirgi sama zaki koma, Allahu yaraya khady dah Sadeeq! chan
nahango khadeejah Yusuf Ahmad Masscom tanata aikin Ovation Allah yabada lada, ahaka
aka gama bikin lunch dah Mother's night lafiya mungode Allah yamaida kowa gida
lafiya,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">D'aurin Aure<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Masha Allah naga
ango Saiyadee cikin fararen Shaddah masu shek'i yasha babban Riga dariya naga
yayi saina ga fararen hak'oran shi sun saje dah fararen kayan shi naga wannan
kwalliyar tayi ga farin idanu dah hak'ora, hula fari, takalmi fari kayan ma
fari wannan to match haka Allah yasanya alkhairi😌!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Mutane nagani makil wai gaskia yau unguwar kuntau tayi
jama'a mara adadi, wai shima fah Dr.Saiyadee mai d'ubin jama'a neh, nidai bazan
iya cemaku ga wa enda suka halacci filin d'aurin auren nanba domin Allah yayi
yauwa dasu naga jama'an Rasulillah [S•A•W] awajan ga mahaifin ango danah Amarya
gakuma shedu dah wakillai sun cika, tuni aka zazzauna,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Muryan Sheik Malam Aminu Daurawa naji yanah tashi a speaker
inda yafara bud'e taron dah Addu'a sannan yasanar dah Al'umma abinda za ayi,
cikin d'an k'ank'anin lokaci aka daura auren <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">ABUBAKAR SAIYADEE KABEER FAHAD danah amaryar sah<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">UMMULKHAIR ABU~SUFYAN akan sadaki naira dubu hamsin 50k, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Jama'a kun sheda? Eh mun sheda naji muryan en uwa dah abokan
arzik'i natashi dah k'arfi, dabino sweets dah goro nah d'aurin aure naga ake
rabawa tah kowani angle, mutane sunata musabaha da junansu tareda yiwa juna
fatan Alkhairi!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ummulkhair Ce zaune
tunda taji d'unbin Al'umman dasuka taru ak'ofar gidan mahaifinta dake Unguwar
kuntau tasan fah yauce ranar fitar tah nabiyu aduniya amaysayin tah nah 'yamace
batah tabbabtar dahakan bah har saida taji ana karanta Suratul fathia d'aya biyu
har uku kamun taji daurin auren tah yabiyo baya, jikinta sosai duk yaya sanyi
babu abinda takeyi sai kuka kamar ranta zai fita gawani zazzabi datake ji kasa
fita tayi ayi hoton dah itah juyin duniya AntyMuna tayi dah itah sam tace
bazata fitabah sai text tayima Dr.Saiyadee akan yayi hak'uri bazata samu fitowa
bah,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Murmushi yayi bayan yayi receiving text d'intah and his
reply was Ummunah....Ummunah!!! nah mallake ki Ummunah<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>kin zama tawa duniya dah lahira Ummunah, I
love U so very much Ummunah, Ummunah I promise zan kula dake, Ina sonki
Ummunah, Ina sonki ina sonki My life joy nd happiness in kaunar ki rabin raina
ina sonki Ummunah! I love U!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Tofah irin wannan kauna haka Allah Muma yabamu masoyan kirki😌<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Gidan Alhaji Kabeer Fahad dake unguwar kabuga nah lek'a dan
ganin yanda suke gudanar dah wannan taron biki mai Albarka, aikuwa ba abarsu
abaya bah su Hajiya Humaira ansha hidima, kasancerwar suma wannan shine karo
nafarko dazasu aurar dah d'aa jama'a kam Masha Allah kawai, naga kwalliyar
Bilal tayi dan gaskia harna fad'a cikin kogin So😍! Amal dah Amrah
nagani kai kace sune amaren lallai yayanku yanah aure irin wannan had'uwa haka,
kuma Allahu yakawo miji nagari, AMEEN! gaskia suma sunyi k'ok'ari sunsha events
iri~iri Allah yabada lada!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:10] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛9⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 My two best Zainabs round the globe (Zainab
Zeesarkie) and (Zainab Miss Biey cholli) I love U so much berries, Allahu
yabiya muku buk'atun Ku duniya dah lahira, Allah yakawo miji nagari dah yara
masu Albarka, One Love Dearies😍👄!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Wai duniya agogon
zomo, Allahu Akbar har anyi walima anfara shirye shiryen kai Amarya, Ummulkhair
tasha nasiha dah fad'a daga gurin mutane dayauwa saidai har yanzu kukan yak'i
tsayawa jitake kamar zatah mutu kasan cewar batah ta'ba barin gida bah tah
shak'u dah mahaifiyar tah sosai batada abokin hira daya wuce Affan dah
mahaifinta koh sanda take BUK kasa zaman hostel tayi sabida sabo dah gida hakan
yasah takejin kamar bazata iya barin gidan su bah, Haba Ummulkhair Dan Allah ki
tashi kishiga wanka nakaiki wajan Ummanki dah Abbanki kizo kije gidan mijinki, sabon
kuka tafashe dashi tanah fad'in wayyo Anty Maimuna ina zansaka kaina nashiga
uku shikenan yau zanbar gidanmu dah Mummynah dah Daddynah wlh Ku cewa
Dr.Saiyadee ga sadakin sanan dah lefen wlh nafasa auren nibazan bar gidanmu bah
tafad'a tanah kuka sosai, dariya AntyMuna tayi sannan tace daga baya kenan
Ummulkhair gidan Dr.Saiyadee zuwa babu fashi yauma kwanan chan zakiyi, tashi
maza kiyi wanka dakyar Ummulkhair tayarda tashiga wanka bayan tafito, shirya
tah AntyMuna tayi tsaf sannan taja hannun tah zuwa parlour'n mahaifin tah, yana
ganin 'yar tasa idanun sah suka sauya yasan yau hankalin tah atashe yake babu
abinda takeyi sai kuka ahankali tah durk'usa k'asa kusa dah k'afar mahaifin tah
sannan tace "Daddy Ina yini Sannu dah hidama Allah yarufa asiri yak'ara
bud'i Allah yasaka muku dah gidan Aljanna tah k'arashe maganar tah muryanta
narawa sosai, Daddy jiyayi wani abu ya turnuk'e masah zuciya cause If there is
one thing he will miss about his princess is Duas kullum tana cikin yimusa
Addu'a, haka yadaure yace "Khairiya, babu abinda zance miki daba afad'a
miki bah kokuma ince dabaki sani bah, kinje Islamiyya kinsamu wadatattan Ilimi
kuma kinsan abinda Allah yace akan aure, kinsan abinda Annabi Muhammad
Rasulillah [S•A•W] ya umarce mu muyi dakuma dokokin aure, Khairiya kinga yanda
mahaifiyar ki takemin biyayya har yau har gobe dukda girman Ku, banajin
tarbiyan ki ko kad'an sabida kin ginu akan tarbiya mai kyau falillahi hamdi,
Dan Allah Dan Annabi kibi mijinki babu ruwanki dah fad'in sirrin mijinki awaje
ban yarda bah, ki kasance wacce batah fashin gaida mijin tah duk safe dah yamma
koh dare idan yadawo, babu ruwanki dah shige~shige abun amince miki bah, babu
ruwanki dah k'awayen banza kada kiyi k'awaye fiyeda biyu, babu ruwanki dah
k'azanta tsafta addini ce, karki sake kibar cikin mijin ki yayi kukan yunwa,
idan kinada matsala kituna cewa babu wanda yake yayewa wani matsalar sah face
Allah, kada kimanta Aljannar ki tanah k'arkashin tafin mijinki, kada kisake ki
k'auracewa shinfid'ar mijinki, ki kasance mai hak'uri dah juriya ki kyautata wa
en uwan mijinki, ki mutunta iyayen sah yanda zaki mutunta Mu, yakasance ace
gidan ki kullum k'amshi yakeyi daddad'an k'amshi rahama Ce kuma sadaka ga duk
wanda ya shak'a, ki kasance mai kyakyawan lafazi ga mijin ki, Allahu ya Albarkaci
rayuwar ki duniya dah lahira, Allah yabaku zaman lafiya, Allah yasah anyi Asa'a
Albarkacin daren dah aka haifi shugaban hallitun duniya, Ameen tace tanah
hakk'i kamar numfashin tah zai d'auke, kuka take sosai uncontrollably shima
Daddyn hawaye yake yanzu, k'afar shi takama tah rungume tanah fad'in Daddy Dan
Allah kayafe min idan namaka laifi, bakimin komai bah er Albarka tashi kitafi
gidan mijinki Allah yayi miki Albarka yak'arasa maganar sah cikin tsananin
kuka, dakyar AntyMuna taraba Ummulkhair dah k'afan Daddy tayi waje dah itah😳😳,
madallah dah Uba nagari, Allah sarkie Iyaye wayyo Daddyn Mu, Gaskia fita daga
gidan Iyaye zuwa gidan miji wani Hissabi neh daban😓!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Gaskiya MATA Allah yabamu hak'uri, Matan aure inayin Ku🙋🏾!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>d'akin Mummy AntyMuna
tawuce dah itah straight dah isartah d'akin tafad'a jikin Mummyn tah tanah kuka
mahaifiyar tatah manayi dakyar muryan Mummy yake fitowa babu abinda take cewa
sai Ummulkhair kibi mijinki, kibi mijinki, kibi mijinki nayafe ki duniya dah
lahira, tashi kije Allah yasah anyi asa'a, kishiga gidan ki dah Bismillah dah
k'afar dama Allah yasah kinje asa'a, Mummy ma yanzu kuka take sosai har mutanen
dasu ke d'akin kuku suke sabida kowa yasan shak'uwar mummy dah ertatah😭,
AntyMuna nahango tanata kuka itama nima waje nasamu nazauna naci kukana,
motocin daukan Amarya neh sukazo hakan yasah manya suka tashi k'awaye dah
sauransu, dakyar aka raba Mummy dah Ummulkhair har sunzo harabar gidan saura
afitar dah Ummulkhair zuwa cikin motah, tah koma ciki aguje tah rungume Mummyn
tah tanah fad'in wayyo Mummy nah Dan Allah Dan Annabi Kuyi hak'uri kubarni
nafasa auren,<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>wallahi Mummynah Nafisan
ku akan Doctor ni wallahi bansan zuwa gidan shi, Dan Allah kubarni nazauna
daku, dakyar aka kuma rabata dah jikin Mummy, Mummy kai tah d'auke kawai
tashige d'akinta tanah mai sharar hawaye sosai,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Wayyo Uwa...Uwa...Uwa Wayyo Iyaye Sakallahu Bil Jannah😭😭😭😭😭!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Affan nahango shima ya ajiye batun namiji agefe yaci uban
kuka sabida bashida k'awar datah wuce Ummulkhair sun shak'u dah er uwar tasah
sosai😢, dakyar aka shigar dah Ummulkhair motah batare dah 'batah lokaci
bah suka nufi gidan tah dake zooroad!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Gidan Dr.Saiyadee<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Masha Allah gidan
Ummulkhair yayi kyau sosai 3rooms neh 2 parlours sai 'bangaren Dr.Saiyadee a
room and parlour kowani d'aki dah parlour nagidan yanada toilet Masha Allah,
kayan gado set biyu aka kaita taza'ba sai kujeru suma set biyu, ancike matah
2rooms d'inta dah parlours dah kaya, kitchen dintah ma duk girman shi ancika
matah shi dakaya store d'intah madai kai abin saidai Masha Allah kawai,
Abangaren Hajiya Humaira itace wacce tayi designing 'bangaren d'an natah
parlour'n shi yayi kyau sosai hakama d'akin shi sauran d'aki d'aya daya rage
kuma Hajiya Humaira batah barshi hakaba saida tacika shi tam dakaya kai amman wannan
had'in kan yayi madallah dah iyaye nagari haka kowa ya dinga santin gidan
Ummulkhair ga k'amshi duk inda kadosa Gaskia nasara muku dah turare en
Maiduguri domin wani k'amshi nadaban Ummulkhair takeyi dah itada gidan tah!
Haka kowa ya watse akabar Ummulkhair itah kadai tanata cin kukan tah! toh bara
muje neman ango Saiyadee!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:11] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛10⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 All My lovely Groupies gaskia ina kaunar Ku Ina
Alfahari daku, Allah yabarmin Ku, Allah yabar kauna NI TAKUCE, One Love😍😍😍😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Kut, kunsan menene
Fans😡 ahanyata nafita nemo ango Saiyadee naci karo dah ZeeSarki ashe
batah tafiba wai itah adole er zooroad unguwan su take, kowa yatafi saike uwar
taurin kai toh malama tashi kiwuce gida Harda wani murna zooroad aka kawo
Amarya toh wlh bamasan yauwan ziyara ehe zauna inda kike😕😙😏!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">ANGO SAIYADEE<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Daga asibiti yafito
yaduba agogon sah yaga shad'ayan dare saura Wani murna yake nadaban daya tuno
Ummulkhair d'insa tazama mallakin sah kuma tanah gida tanah jiran sah, Gas
roasted Chicken ya tsaya yasiya guda uku dah Nagari&Farm Fresh yoghurt sai
chocolates daya lodowa babyn sah cikin ledan snacks dah Hajiya Humaira tabasa
yahad'a komai sannan yanufi hanyar gidan sa cike dah murna, phone d'insa neh
yayi ringing yanah dubawa yaga Sudais saurin picking yayi yana maiyi masah
godiya akan hidimar dayayi saidai sam kuka sudais yakeyi sosai kamar yaro,
cikin rud'ani yake tambayar sah abinda yafaru, Friend Dan Allah kataimake ni
it's my wife tafad'i abene tah gangaro k'asa dah tsohon ciki she's not moving
not even a finger nazuba matah ruwa all in vain, then take her to the hospital
manah Saiyadee yafad'a cikin tashin hankali, no friend I cant bazan iya barin
tabah and banida courage d'in driving, Dan Allah kazo kataimake ni, hankali
atashe Dr.Saiyadee yace haba friend U kno this is my wedding night bazan iya
zuwaba, daga asibiti nakefa yanzu Ummulkhair tanah jirana tun d'azu nah
tabbatar tagaji tayi bacci 11pm nah dare fah yanzu, Dan Allah karufa min asiri
mezan Ce matah idan nakoma gida, Save my marriage Friend, Innalillahi wa Inna
ilaihi rajiun friend banida wanda zai taimake ni saikai dan Allah kada kabari
komai yasamu matata kazo kataimake ni, Save my Wife bayan much pleas finally
Dr.Saiyadee ya yarda yaje haka yaja motar shi in 360 zuwa gidan Sudais dake
Unguwar sharad'a, yanah zuwa yatarar dah matar Sudais unconscious with bruises
all ova her face, lafiyar babyn yafara dubawa yaga the baby is in great danger
due to internal bleeding data samu which was the main reason nah maidata
unconscious tuni yafara aikin ceto ran uwa dah d'anta bashi yasamu yagama bah
sai 2:45am midnight alokacin matar Sudais Zainab was already breathing silently
but calmly, godiya Sudais yayi masa sosai yakuma basa hak'uri, shidai Saiyadee
kawai jinsa yake amman hankalin shi yayi gida motah yashiga yakama hanyar
gidansa dake zooroad he was happy ya ceto rai har biyu at the same time Sad
yad'au hakk'in Ummulkhair ranar farkon tah agidan shi,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Gidan Dr.Saiyadee<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ummulkhair tunin
daman tayi alwala tayi sallan Isha tunda taga 1am yayi baishigo bah, wanka tayi
tasaka wani doguwar rigan tah nah material sanan tasaka hijjab d'inta tayi
kwanciya saidai sam takasa bacci yau taji tah awaje daban ahankali take kuka
bayan tah tuno dah iyayen tah dakuma k'anin tah Affan, agogon d'akin neh yayi
k'ara kasancewar duk 1hour saiyayi k'ara dubawa tayi taga k'arfe uku neh yayi
sosai jikin tah yayi sanyi tsoro yakama tah tafara tunanin inda mijinta yake
kuka tafashe dashi sanin sarai bazai wuce yanagun aiki bah haka tadinga sharara
kuka har taji ana bud'e k'ofar gidan k'aran shigowar mota taji, hakan yasah
tasan shine yadawo duk'unk'unewa tayi cikin bargo kamar wata jaririya tah rufe
idanunta,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Parking yayi a parking lot jikin shi duk amace yasan yaci
amanar tah kuma bashida bakin dazaiyi matah bayani hakan yasah ya yanke
shawarar shiga ciki kawai yabata hak'uri, ciki yashiga dah sallama wani k'amshi
yaji mai dad'in gaske, ahankali kamar wanda aka daurewa k'afa yataka zuwa
d'akin tah, murd'a k'ofan yayi yashiga dah sallama jikin k'ofa ya tsaya yanah
kallon tah duk yaji tausayin tah yakama shi yaji koh kad'an bai kyauta matah
bah k'arasawa yayi zuwa bakin gado! <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Sai gobe hannun nah ciwo yakeyi😰<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:11] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳11⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 Halima<span style="mso-spacerun: yes;">
</span>Ahmad Yusf(Agric kust), the most stubborn creature I have known so far🤦🏻♀,
Allahu ya shirye ki yabaki miji nagari mai shegen aron Earpiece😼,Love U
so very much Sweet👄😍👄😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>K'arasawa yayi
bakin gado ya zauna, kallon tah yayi nawasu en mintuna kafin yasoma yaye bargon
dake jikinta, yacce take rirrik'e bargon neh ya tabbatar masah dah cewar idanun
tah biyu, Ummunah m so sorry pls ki tashi I love U, k'ara rik'e bargon tayi
dakyau hawaye nah zubo matah d'agota yayi sannan ya yaye bargon kanta ak'asa
tace sannu dazuwa, kallon tah yake kamar yayi kuka yace "yauwa Ummunah
sannu dah gida bakiyi bacci bah Uhm kawai tace masah, agogo yaduba yaga har k'arfe
uku tah gota kallon tah yayi yace tashi kije kiyi alwala muyi Sallah Ummunah,
babu musu tah tashi tah nufi bathroom tayi alwala shima tashi yayi yawuce
d'akin sah yayi wanka sannan yayi alwala yanah dawowa ya tarar dah itah tah
had'e kai dah gwiwa ak'asan d'aki gabanta yaje ya durk'usa yakomo hannayen tah
dukkah biyu yace, "Ummunah menene?" kai tayi saurin d'agowa tace masa
babu komai, toh tashi muyi sallah kinji Ummunah, babu musu tah mik'e yajasu
sallah bayan sun idar neh yajuyo yakama kanta yayi matah Addu'oi itadai babu
abinda takeyi sai kuka, tabashi tausayi sosai yace Ummunah dan Allah kidaina
kuka d'ago fuskarta yayi dah hannun shi biyu yayi matah kiss agoshi, Ummunah I
love U, Ummunah ina sonki, Ina sonki Ummunah karkimin kuka dan Allah bansan
hawayen ki nazuba, harshe yasa ya lashe hawayen fuskan tah tuni tah d'ago
azabure tace nadaina hijjab d'inta tashiga goge fuskan tah dashi sannan takalle
shi tace nadaina bazan k'araba,murmushi yayi yace daa kukan nah shagwa'ba neh
daman, batace komai bah sai sabon hawaye dake forming a idon tah, kafad'ar tah
yadafa yace Ummunah Dan Allah meke sakaki kuka? d'agowa tayi takalle shi tace
"ya Saiyadeen Ummu, Na'am Ummunah menene fad'amin, dan Allah kah rik'eni
amana ai kayiwa Daddy dah Mummy alk'awarin zaka r'ikeni AMANA koh? ya Saiyadee
nabaka AMANAR kaina, ya Saiyadee nabaka AMANAR kaina, ya Saiyadee nabaka AMANAR
kaina, Dan Allah karik'e ni AMANA Saiyadeen Ummu, karik'e ni AMANA!!! tak'arasa
magana tanah mai tsananin kuka, jawota yayi jikinsa ya rungume tah kamar zai
maidata tah cikin ciki, har tayi tunanin zamewa saita tuno dah nasihar iyayen
tah dah en uwa dah abokan arzik'i, madallah Ummulkhair Amarya tagari, Ummunah I
love U, Ina sonki Ummunah Insha Allah zan rik'e ki AMANA, anbani AMANAR KI kuma
nadauka Ummunah bazan cutar dake bah zan rik'e ki dah so dah kauna kibar yimin
asaran hawaye banaso, I love U, k'ank'ame tah yadad'a yi ajikin sah sosai, luf
tayi ajikin shi tah k'ank'ame jikin tah waje d'aya, yauwa Allah yakawo mu nazo
fad'ar gaskia😌<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ina kuke en mata Ku aramin kunnuwan Ku,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Agaskia yake sabuwar Amarya kina bani mamaki, wai sai kaga
ankai mace gidan miji adaren ranar tanah gudun shi koh tanah tsoron shi akan
me? shin ai kinsan abinda za ayi tunda Sunnah Ce tah Manzo, kuma anmiki nasiha
akai it's very normal kiyi finding d'inshi uncomfortable kuma kiji kunya tunda
you are not familiar with it, amman batun tsoro baitaso bah, ai bah dodo kika
aura bah kuma koh dodon nema kinsan bazai ajiye ki kamar mudubi bah saiya
kar'bi hakk'in sah, ni gaskia Ummulkhair tabirge ni wannan shine daren tah
nafarko agidan Saiyadee ya rungume tah amman batayi kuka akai bah ko tah gudu
toh wallahi kuyi koyi dah itah, ai ansan abinda zai miki aka kaiki gidan shi
tareda guzurin katifa dah bargo, kuma hakan akeso, shiyasa ake Addu'ar zuri'a
thaiyiba, kubar gudun mazazen Ku adaren farko bashida wani amfani duk munafirci
neh sabida kin riga kinsan abinda akeyi, duk littafan kwanciyar Aure dah kike
shiga kasuwa kisiya a'boye dazaran ansaka miki rana fah? Kingama karanta wa
zakizo manah dah rainin hankali Abeg ajiye k'auyancin wani guduwa agefe waike
adole kinajin tsoro ki kwashi Albarkan mala'ikun Allah! Kuji tsoron Allah
adaina dennewa maza hakk'insu sabida kin kar'bi sadakin ki RAW CASH ahannu ooo,
dahaka nake kiranku akan Kuyi koyi dah Ummulkhair awannan 'bangaren fah tanada
wayo, wannan kenan <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Matan Aure Ina Yinku fah🙋🏾, En matah
zantashi Sallan dare Allah yakawo nagari mai albarka😍👄❤<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Cigaban labari<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:11] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛12⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 groupies of Mhiss B~hal Novels, Bunch of love
dearies😍👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ahankali yasake
tah yad'ago tah yayi pecking d'intah a cheeks, Ummunah kiyi hak'uri yau
banshigo dawuri bah kinji Dan Allah, bakomai nasan yanayin aiki neh ya
Saiyadee, tafad'a tanah kalon k'asa sosai yakuma jin tausayin tah yakuma
rungume tah, kwanciya tayi ajikin shi tayi shuru tanah tunanin gida, kinci
abinci Ummunah? Uhm naci, bawani nan yaushe rabon ki dah abinci daman dachan
basan ci kike bah balle yanzu dah aka kawomin keh, ai nasan tunanin barin gida
bazai barki bah tashi kici abinci, kallon shi tayi ido rau~rau tace banjin
yunwa Allah ya Saiyadee, hannu yasah acikin tah yashafa yace, "ahakan
cikin nawa kamar plate", jikin tah rawa yake sosai amman agidan su tatuna
ance matah hakk'in saneh karta kauracewa duk abinda zai matah hakan yasa
tadinga kwantarwa dakanta hankali, bara nadauko miki abinci kici, tashi yayi
yaje kitchen yadauko plates guda hudu dah mug biyu, yanah shiga yatarar harta
kuma kwanciya ak'asa Ummunah wai gajiyar Ce haka kidaina kwanciya ak'asa ni
banaso fah, murmushi tayi tah tashi tace bacci nakeji neh shiyasa, tam bara
nabaki abincin saiki kwanta koh, nama yazuba matah acikin plate dah snacks
yazuba matah nagari cikin mug sannan yadawo kusa dah itah d'ago tah yayi ya
kwantar ak'irjin sah, sannan yace, "haa Ummunah kiyi Bismillah",
uhm~uhm Allah ni nah k'oshi ya Saiyadee banci, Dan Allah kitaimaka min kici
abinci Ummunah bud'e kici koh kad'an neh, Ni a'a ya Saiyadee Allah am full,
shikenan Ummunah nagode, gani tayi baiji dad'i bah hakan yasa tace masa zansha
milk din gobe zanci wannan tafad'a kamar zatayi kuka, d'ago fuskan tah yayi ya
k'ura matah ido sannan yace, "Ummunah I love U, Ummunah ina sonki ina
kaunar ki nagode dah kika aureni fuska tah saukar k'asa murmushi yayi dan yasan
kunya taji mug d'in yadauka yakai bakin tah ahankali tasoma sha bayan tayi Bismillah,
kallon tah yake yana maijin dad'in yanda takeshan hankali akwance, tasha fin
rabin mug sannan tacire bakin tah tace "tak'oshi", toh Ummunah hakan
ma nagode sosai Allah yayi miki Albarka wifey, Ameen tace, hanky tagani acikin
aljuhun shi tace, " ya Saiyadee", na'am Ummunah mekike so,
handkerchief zaka aramin, kafin tah k'ara wani magana yajata jikin shi ya lashe
bakin tah tas, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">wai ni Mhiss~B naga abu kaji iyayen soyayya, Toh Allah yabar
kauna😌,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">ido tah zaro sannan tah rufe su gum, dariya yayi yace koh
bah abinda zakiyi dah hanky bah kenan, ai that's my job Ummunah remember u're
my halal, shuru tayi sannan tace bacci nakeji bacci zanyi, agogo yaduba yaga
har 4am tayi it's almost time d'in tashiwar sah ma and she's tired hakan yasah
yayi tunanin k'in yimata komai kawai, toh muje ki kwanta d'agata yayi harkan
gado yakwantar dah itah bargo rufa matah zuwa k'irji sannan yayi matah rumfa
yanah kallon cikin idontah, kasa cigaba dah kallon shi tayi kawai tasaukar dah
idanun tah, light kiss yakai matah kan baki yace, "Ummunah kece murad'i
nah ina sonki ina kaunar ki, kece abinda nake nema Allah yabani kuma nagode
masah, murmushi tayi kad'an tah d'auke kai, karan hancinta yaja yace, "say
something sweetheart, U keep on being silent, bargo taja kanta tace, "ya Saiyadee
ni bacci zanyi fah, gudnight sweetheart sleep well! Yace sannan murmushi yakoma
k'asa yasoma cin abinci ahankali, kad'an yaci yaji harya k'oshi milk d'in yasha
shima yatashi, komawa yayi danya duba tah sai yaji tanah shek'ar kuka ahankali,
Ummunah yafad'a hankali atashe bargon yayi saurin yayewa yaga fuskan tah
sha'be2 dah hawaye, jikinsa yajawo tah, Shhhhh baby it's ok, am here for U
sweet, cikin tsananin kuka tace, "ni wajan Mummynah dah Daddynah zakah
kaini, ni gidanmu zanje bazan iya kwana anan bah, k'ank'ame tah yakuma yi yanah
shak'ar daddad'an k'amshin dake tashi ajikin tah, cikin kuka takuma cewa,
"ni wlh kah kaini ni gidanmu, ni banason nan wajan babu Mom nd Dad
d'inah", kuka takeyi sosai sai rarrashin tah yake yanah jijjiga tah ahankali,
kamun yace, " Ummunah nifah? kinga Abbanah dah Ummanah anan neh?, Ummunah
wannan shine auren fah daman ai dole kirabu dasu kifara sabon rayuwa, sauran
kuma sakaiyar ki tanah gun Allah, ni bakya tausayi nah idan kika tafi kika
barni, koh bakya So nah bakya san zama dani? bazan iya rayuwa babu kebah
Ummunah, inazan saka kaina yau idan kika koma gida wlh nima bazan iya rayuwar
nan gidan bah, kinga sabon gida neh yau muka tare yazama wajan zaman mu inda
zamuyi rayuwa kuma mu raini yaran mu, Dan Allah kiyi hak'uri Ummunah muzauna
lafiya, kidaina d'aga min hankali dah kukan nan, I love U Ummunah, I love U so
much, banasan kinamin asaran hawaye Dan Allah yafad'a yanah k'ara rungume tah
sosai, shuru tayi tanata haak'i, bayan tah yake bugawa ahankali gamida yimata
sannu akai2, shuru neh yabiyo baya sai saukar numfashin tah dayake ji ahankali,
gyara musu kwanciyar yayi sabida taji dad'in baccin sosai saidai shi yakasa
baccin kallon tah yake kawai yanajin kaunar tah aransa tamkar yamaida tah ciki!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[12/07, 21:11] Aysha Mai Group Nd Zahra Group Bauchi: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛13⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 Ol MATAN AURE round D globe, Ina kuke MATAN AURE
Inayin Ku🙌🏿, ya aiki, ya kula dah miji dah yara, ya d'iban lada
kuma? toh ad'iba dayauwa fah dan samun tsira ranar gobe, ya wanke2 dah shara,
Allahu yabada lada yasaka da gidan Aljanna Mhiss~B tanah gaisuwa🙋🏾🙋🏾🙋🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Asuba nayi Ummulkhair
tah farka, ita tama manta duk tunanin tah tayi sallah tazo tah d'aura breakfast
kafin Daddyn su yashirya fita aiki, tunowa datayi ba agida take bah hakan yasah
tah tafashe dah kuka, wayan tah tadauka tah kira numban mahaifiyar tah bugu
d'aya Mummy tah dauka dasauri, Ummulkhair ya kike tafad'a cikin muryan kuka,
kin kwana lafiya khairat? khairat nakasa bacci babu ke acikin gidan! koh kad'an
ban iyayin bacci bah, danma mahaifin ki yakwace min wayana dasai nakira ki
cikin dare sabida nakasa jurewa Khairiya, tafad'a tanah hawaye masu zafi, kinga
Daddyn naki ma baiyi bacci bah shima kasawa yayi tun yanah rarrashi nah har
shima saida yayi kukan, Affan mah kwana yayi idon sah biyu abud'e munyi kewar
ki Khairiya, we all miss U, Dan Allah kizauna lafiya dah mijinki Allah yayi
miki Albarka, Ummulkhair tunda mahaifiyar tah tafara magana take wani irin kuka
wanda takejin zuciyar tah kamar wuta, daman tasan hakan zai faru iyayen tah sun
daura masu san duniya sabida subiyu kadai neh kuma bayan an haife tah saida
akayi shekara biyar aka haifi Affan so bah k'aramman shak'uwa sukayi dah itabah
ita cikin Daddy dah Mummy mah tarasa wanda yafi kaunarta, tasan dole zasuji
daban agidan jiya kuka take sosai, kasa cigaba dawayan tayi tah katse tafad'a
band'aki tayi alwala sallah tayi tah karanta Alkur'ani mai girma sannan tad'an
samu nutsuwa, wayan tah tadauko takuma kiran layin mahaifiyar tah, Affan neh
yadauka, Sis yakike? kina lafiya ganinan zuwa gidan ki, murna tayi sosai tanah
sharar hawaye dake zubo matah toh Affan ina Daddyn mu kabashi waya, gashinan
yace sannan ya mik'a masa wayan, cike dah farin ciki Daddy yakar'bi wayan,
yace, "Khairiya Ce", uhm tah amsa sabida batason yasan kuka take,
yakike? kinanan klau koh? ya mijin naki Allah yabaku zaman lafiya, sannu koh
sannu Khairiya Er Baba yafad'a muryan shi atok'are saurin mik'awa Mummy wayan
yayi ya kauda kai, khairat Mijin ki fah jiya yashigo dawuri koh? cewar Mummy,
eh Mummynah bayan ankawo ni bai jima bah yadawo,toh fita fah, yau da gobe babu
inda zaije koh? Zai zauna dake agidan koh? Ummulkhair Eh tace, sannan tace,
"Mummy harda jibi ma", toh shikenan naji dad'in hakan sosai, tun
k'arfe biyar nagama miki abinci yanzu Affan zaizo yakawo yace zai gane gidan
naki, ogogon sama takalla taga 6:15am tace Mummyn mu nagode Allah yabiya ki dah
gidan Aljanna, Ameen khairat Er Albarka, Mummynah, na'am khairat, Mummy Dan
Allah kema kuci abincin dah Daddy sosai naga kwana biyu bakwacin abinci yanda
yakama tah, toh Khairiya Insha Allah zamuci, Allah ya Albarkaci rayuwar ki
Duniya dah lahira, Ameen tah amsa a nitse<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Wayyo Allah nah Allah Sarkie UWA...UWA...UWA!!! Gaskia UWA
tafi komai wanda baisan darajar Iyaye bah especially Mahaifiya wallahi Allah ya
kwashi Asaran Duniya, Allah kah sakawa Iyayen mu dah gidan Aljanna, kah
d'and'ana masu ruwan Alkausar cikin sauk'i! AMEEN<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Sallama sukayi dah mahaifiyar tata saida taci kukan tah
sannan tah tashi da nufin zuwa gaida mijin tah, saidai taduba koh ina bata
ganshi bah side d'inshi taje tayi knocking tareda yin sallama nanma shuru hakan
yasa tah murd'a k'ofan tashige ciki shuru babu kowa, d'aki tak'arasa nanma
shuru babu kowa, tayi tunanin koh wanka yakeyi, saikuma taji shuru, knocking
k'ofar bathroom d'in tayi taji alamun babu kowa, budewa tayi taji k'amshi fresh
bath hakan yatabbatar matah dacewar yayi wanka, toh ina yaje take tambayar
kanta? koh breakfast yaje dauko musu? toh amman ai akwai remnants d'in jiya
basu cinye bah, ganin babu mai batah amsa yasah tah fice harzata koma d'aki tah
tuno bata duba main parlour bah, hakan yasa tunanin tah yakarkata dah cewar
yanacan yanah kallo, takawa tayi ahankali zuwa main parlour sannan tashiga dah
sallama shuru babu wanda ya amsa, wayam parlour'n babu kowa ciki, ruwa tah
hango kan dinning table tanufi wajan dan tasha kasan cewar every morning ruwa
take farasha kafin taci komai, bayan tasha cup d'aya harzata juya takoma d'aki
idanun tah suka sauka kan farin paper anyi folding d'inshi neatly!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[16/07, 18:43] +234 703 125 8794: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛14⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 ZAINAB YAKASAI (Shukrah Er Gatan Miemiebee, Er
Autan Pure Moment) marubuciyar RAYUWAR ABDULLAH gaskia banida abinda zan cemiki
dear saidai kawai nace Allah yahad'a mu a gidan Aljanna, U're Unique Love, I
heart U so much deary😻😍👄!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Gabanta neh
yafad'i dan tasan tabbas Saiyadee neh yayi dropping note toh amman menene
aciki, kujeran dinning taja tazauna sannan takai hannun tah ahankali tadau
paper'n cike dah tsoro tafara unfolding d'inshi har tagama bud'e shi saidai tah
runtse idon tah har saida tad'an samu nutsuwa tabud'e su tasauke akan note d'in
wanda yake kamar haka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Good morning
sweetheart, finally U're awake & reading this, Ummunah bazan iya daukan
hutun kwana biyu bah due to wani aiki dah I must attend to, nayi signing
Operation din wani yaro tun last 2weeks kuma yaune ranar kinga dole nah naje
nayi masa aikin, so sorry i just had to leave, U slept well on my chest last
night I miss U badly, I promise to pay back, Eat well baby & lastly I hope
U'll understand! <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">rasa abinyi tayi hawaye nah zubar matah tunani take yanzu
da'ace abu yashiga tsakanin su last night haka zatah tashi taneme shi tarasa
saikace wanda yabiya tah yayi tafiyar sah, kuka take by now wani zafi takeji
aranta k'ofa taji ana bugawa tashiga share hawayen tah sannan tamaida hijjab
d'intah wanda tacire dan zafi taje dubawa, Anty bud'emin nine Affan dasaurin
tah tabud'e tanah dariyan murna sosai, tanah bud'ewa tah rungume sah tanah
fad'in lilbro saikace jirgi neh yakawo kah har yaushe Mummy tace min kanah tafe
lallai kayi missing d'inah, wallahi naji dad'in ganin kah sosai U juz don't kno
hw happy I am, Sis ai jiya banyi bacci bah wlh naji gidan duk babu dad'i koh kad'an
nibanma san nafisan ki akan su Mom bah sai jiya, lilbro harda su zak'in baki
tace tanah dariya, muje ciki, gidan suka zagaye tah nuna masah ko'ina gaba
d'aya ya yaba dah gidan natah kuma yayi matah Addu'a sosai sannan sukayi zaman
cin abinci, serving d'insu takeyi tare, yace "laa Sis tare zamuci
abinci"?, "why not dear tare zamuci manah, toh Sis naji dad'i, laa
namanta ban tambaye ki yayanmu bah naga munzagaye gidan ban ganshi bah kuma
sabida yananan Mummy tace karna zauna, baya nan yatafi dauko min magani a
Asibiti dah zazzabi nakwana jiya Ummulkhair tayi k'arya, amman banason kah
fad'awa Mummy koh Daddy bansan hankalin su yatashi muyi zaman mu muci abinci
muyi hira kawai, toh shikenan Anty amman idan naci abinci anan idan naje gida
fah Mummyn mu tayi fad'a, a'a kace matah Abusaiyeed neh yayi insisting yace
saika ci, toh shikenan anty wainar shinkafa neh dah miyar agushi sai farar
shinkafa dah miyan naman rago, sai drinks data aika masu dashi Bismillah sukayi
suka shiga ci tare cike dah farin ciki kai kace sunyi shekara basu had'u bah,
Ummulkhair kallon yanda k'anin tah yamaye gurbin mijin tah take tasan kamata
ace dah mijin tah sukecin abinci awannan lokacin wani hawaye mai zafin gaske
neh yasauko matah saurin gogewa tayi kada Affan yalura sannan tah godewa Allah
daya bata d'an uwa ma, bayan sun gama ya tattara plates yakai kitchen yawanke
mata tas, yadawo yazauna suna kallo, har shabiyun rana Ummulkhair ido tazuba
koh zataga su Amal amman shuru babu labarin su ita tayi tunanin zasuzo wajan
tah sabida basuda nisa sosai, toh kodai sunsan Yayan nasu baya nan neh, itah
yanzu idan Affan yatafi yazata yi, haka kuwa akayi Affan yayi tafiyar sah sai
itah kadai kamar mayya, bak'i neh en unguwa suka soma d'an shishigo matah ciki
harda zeesarkie daman nasan za ayi hakan, zee Allah ya shirye ki! Lol<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Kar'ba cikin mutunci
dah k'ima tadinga wa bakin natah sosai tareda had'a masu dah kayan marmari
snacks dah drinks take tah basu sai ruwan sanyi,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ahaka Ummulkhair tah dinga baki har saida akayi magriba suka
daina shigo matah daganan kuma tah tsaftace gidan tah tak'ara shiga wanka tayi
kwalliya cikin atamphan tah mai kyau tayi zaman jiran mijinta shuru taji hakan
yasah tah dauki phone d'intah tasoma kiran number Saiyadee amman sam baya
picking, saida tamishi missed calls goma sha sannan yayi matah reply kamar
haka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Am busy we talk later pls!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">bayan tah karanta tashi tayi kawai tayi sallah tah mik'a
kukanta ga Allah, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Anan kan dadduma
yakira akayi Isha bayan tayi sallan Isha neh bacci yadauke tah, bacci take
sosai kasan cewar tah jima batah samun bacci agida, chan wajajan to 12am taji
anta'ba tah kafin tah ankara taji anyi sama dah itah ido tabud'e atsorace
zatayi k'ara taji yace, "shhh baby its me, am the one so calm down OK U're
safe", babu abinda tace masah kan gado yanufa dah itah ya kwantar sannan
yakwanta gafenta cikin idon tah yake kallo kafin yace Ummunah am sorry, agogo
taduba taga 12am saura juz 2mins tafashe masa dah kuka, jikin sah yajata yanah
fad'in shhh sweetheart I juz said m sorry ok tryna understand the situation
pls, kuka take sosai k'ank'ame tah yayi yanah "fad'in it's OK Ummunah I
love U OK, Inasan ki fiyeda rayuwa tah kibar min kuka banaso, nayi laifi kiyafe
min Dan Allah" kinji, shuru batace masah komai bah raba tah yayi dah jikin
sah yakalle tah yaga idon tah taf suke dah hawaye sosai yaji tausayin tah rasa
abinyi yayi hakan yasah yayi owning lips d'intah ahankali, ido tazaro masah
sannan tayi saurin rufesu, k'ank'ame tah yayi sosai yaci gaba dah kissing
d'intah romantically!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[16/07, 19:14] +234 703 125 8794: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⌛15⏳<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 all EN MATA round D globe, Ina kuke EN MATA ADON
GARI IDAN BABU KU BABU GARI IDAN KUNYI YAUWA GARI YA 'BACI😖, ya samari,
ya kyautatawa Iyaye kuma? Toh adage fah bin maganar Iyaye bin maganar Allah!
Allahu yahad'a mu A Aljanna yakawo mazaje nagari masu Albarka dah rik'on amana
AMEEN Mhiss~B tanah gaisuwa 🙋🏾🙋🏾🙋🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Kissing d'inta
yakeyi kawai dukda cewa yakula she's not comfortable hawayen dake tsiyaya
afuskar tah yake share wa idanun sah arufe, a hankali yayi patting lips d'insu
yayi whispering akunnen tah Ummunah m sorry kinji? shuru batace komai bah, Ummunah
Dan Allah kiyi min magana koh zanji dad'i, ya aiki sannu dah zuwa, kah gaji
koh? tafurta ahankali, k'ank'ame tah yakuma yi sosai yanah shafar gashin kanta,
Ummunah ina sonki bazan iya rayuwa tah babu kebah kece farin ciki nah Ummunah
zuciya tah taki ce keh kadai ina kaunar ki kissing forehead d'intah yayi sannan
nose tip d'intah sannan yakuma sauka bakin tah yanah sucking calmly, Ummulkhair
batayi yunk'urin hanasa bah zuciyar tah amace take tunanin tah ya auren su zai
kasance shin haka zai dinga dawowa shabiyun dare toh mesah bah zaiyi
considering ita Amarya ce bah? shafar bayan tah yakeyi, yanah kissing wuyan tah
azabure tamik'e zaune, tanah kallon sah, jawota yayi jikin sah yace "it's
OK sweetheart I understand nadaina, Ummunah banace kidena kwanciya ak'asa bah
bakisan sanyi k'asa yayi miki yauwa bah koh sokike pneumonia yakama
minke"? kai tah girgiza masah alamun a'a, toh kice min kidaina Ummunah,
nadaina Insha Allah bazan k'ara bah, nagode Ummunah, rungume tah yayi and by
now she has no choice than to hug him back sabida tayi missing d'inshi sosai
tun kafin bikin su, dad'i yaji da yaji hands d'intah sunyi wrapping d'insa,
Ummunah kinada dad'i dariyar ki kadai noor ce acikin rayuwa tah everything
about U is juz so perfect thanks to Ya Allah for making everything possible,
dah bansan inda zansaka kaina bah idan narasa ki, Ya saiyadee tafad'a cikin
sanyin murya, na'am Ummunah inajin ki, k'arfe nawa zakah dinga dawowa gida, yau
naji tsoro sosai Dan Allah kadinga dawowa dawuri kaji, baki yasah awuyan tah yayi
matah kiss sannan yace, "naji Ummunah Insha Allah zanyi kokari kinji,
amman kinsan akwai call when am on call aw have to leave ANYtime sweetheart so
pls bear with me", toh kawai tah iya cewa shuru neh yabiyo baya yayinda
kowa yake nasa tunanin, ya Saiyadee, na'am sweetheart, how was the operation?
Successful Ummunah! Toh Alhamdulillah hubby, kira neh yashigo masah waya bayan
yad'aga dah sallama yayi shuru amman daga gani hankalin sah atashe yake kawai
bayason tagane neh, OK kawai yace yakashe wayan, bakin su yahad'e ya gyara
matah kwanciya ajikin sah suka kwanta, bayan yayi kissing d'intah for almost
10mins yace, "let's sleep sweetheart aw be late for work tomorrow"!
gudnight tace tanah kwance kan k'irjin shi mamaki take why the sudden change
mesah yace su kwanta cikin sauri haka and what's with that awful look on his
face?, shuru tayi tarufe idanun tah tamkar mai bacci, jin numfashin tah yafara
sauka ahankali yasah yayi tunanin tayi bacci and without wasting anymore time
yaraba tah dah jikin sah ahankali sannan yamaida pillow gur'bin sah, phone
d'insa yadauka cikin sauri naji y yace, "am on my way", cikin sauri
yafice, bud'e ido tayi wanda suka riga suka cika taf dah hawaye tah kwanta jiki
asanyaye tanah tunanin wannan wani irin aure neh haka, ga so dai iya so amman
babu farin ciki, tanaji Abusaiyeed yabud'e gate yaja motar sah yaficce daga
cikin gidan, kuka tafashe dashi sosai kamar ranta zai fita, "toh ina zaije
wai? waya kira sah awaya? meyasa bai fad'amin zai fita bah"? ganin batada
amsa kuma babu mai bata yasah tah kwanta taci kukan tah tagode wa Allah kafin
bacci 'barawo ya sace tah!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[03/08, 02:10] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳16⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M ~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 My SADNAF, Allah yabiya buk'atu yasaka dah gidan
Aljannah deary😻, Allah yasah kigama littafin ki lafiya! I heart U alot,
one love👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Waya yad'auka
yanah kira hankali atashe naji yanah fad'in nakusan k'arasawa cikin speed ya
k'arasa Asibiti, wasu doctors naga sunata jiran shi, koh kaya bai canza bah
yak'arasa gun yaron dana gani rai ahannun Allah, cikin hanzari Dr Saiyadee
yace, "what exactly happened he was stable when I left", nurse Hamza
neh yace "sir I tink it's Internal bleeding", Internal bleeding ya
maimaita confused, this is serious the operation was successful amman am sure
matsala aka samu awani waje withing a short period of time Dr Saiyadee yafara
aiki dashi dah wasu ma'aikatan, sai wajajan uku dah rabi nadare suka samu suka
ceto ran yaron, alluran bacci yayi masa yakoma office yakife kansa akan table,
nurse Hamza neh yashigo ya ajiye masa wasu files akan table, harzai<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>fita ya tsaya yace, " Sir lafiya kuwa
naganka haka cikin wannan yanayin kada kadamu patient d'inka will be fine Insha
Allah", d'agowa Dr Saiyadee yayi yace, "dole ka ganni haka it's my
wife batasan nafito bah kuma ban sanar dah itah bah I kno idan tafarka bataji
ni kusa bah she will be confused nikuma bansan abinda zance matah bah idan
nakoma, toh sir kace matah daga office kake manah, tell her what happened, hmmm
bakasan mace bah she knows the operation was successful yanzu idan nace matah
something went wrong somewhere do U tink she will listen, and kuma yaune kwanan
mu nabiyu dah aure yakama tah ace nad'auki casual leave amman I was not granted
sabida wannan operation d'in, hakane sir abu neh mai wuya Allah yashige manah
gaba ya daidaita tsakanin Ku, Ameen nagode yatashi yadau car keys d'insa
yafice, parking yayi agida yafito dah briefcase d'inshi yayi ciki kallo biyu
yayi wa k'ofan d'akin tah yawuce side d'inshi,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>4am agogo nayin
k'ara kamar ance tah farka taji shigowar sah, kwanciya tah gyara tah runste ido
dataji yawuce side d'inshi, baccin tanema tarasa hawaye nabin fuskan tah
ahankali, wato yadawo mah bazai zo wajan tabah, toh daga ina yake, kuka take
har akayi sallan asuba tashi tayi itama tayi sallan, bayan tah idar tanah zaune
kan dadduma tanah karatun Alkur'ani taji yashigo dah sallama, k'arasa ayar tayi
tah amsa, sannan tah tashi tah ajiye shi a mazaunin sah, juyowa tayi tah
durk'usa har k'asa tace Ina kwana, katashi lafiya, bai iya amsa tabah shima
k'asan yazauna yad'ago fuskan tah kasa had'a ido tayi dashi, hakan yasa yajata
jikin shi yanah patting bayan tah ahankali, Ummunah kin kwana lafiya, kuka
kikayi yanaga idon ki haka, murmushi tayi tace uhm uhm banyi kuka bah, rungume
tah yayi yace, "juz kno that duk abinda zai faru duk duniya babu abinda
nakeso kamar ki Ummunah", then prove it Abusaiyeed prove it pls tafad'a
tanah kuka, sosai yaji kalamun tah sun ta'ba shi harcikin ransa,<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>k'ara k'ank'ame tah yayi ajikin sah sai
asannan yakula dah temperature d'intah jikin tah yayi zafi sosai, bakya jin
dad'i neh? It's nothing am fine Abusaiyeed, but Ummunah u look sick ai kifad'a
min menene, nifa nace makah lafiya nah kalau, kodai kina gudun magani koh
allura bah, allura kuma aibabu wanda zaimin allura saidai maganin koh, bangane
babu wanda zaimiki bah nikuma fah, kai toh kaiba namiji baneh, taya zanbari
namiji yamin allura, lallai Ummunah kin bani dariya wato ni namiji neh bazan
miki allura bah, Eh manah tace tanah 'boye fuskan tah ak'irjin shi, aikuwa
yanzu zan miki alluran zazzabi, dasauri tah d'ago kai tace nifa banaso lafiya
nah kalau, toh Ummunah taya zan tabbatar lafiyar ki kalau, yimin abinda zan
tabbatar dah hakan, dariya tayi masa tace, "toh gashi nayi ai kasan mara
lafiya bazai iyayin dari....... cikin bakinsa tah k'arasa maganar kissing
d'inta yake calmly idanun shi arufe, bud'e natah tayi tanah kallon sah kaunar
sah taji yak'aru aranta hannun tah d'aya tasah ahankali tanah shafa eyebrows
d'inshi aranta tanah fad'in my gentle hubby, har yanzu be daina kissing d'intah
bah ahankali itama tafara sucking lips d'inshi ido yabud'e sabida tsananin
mamaki dayayi hakan yasah ita kuma tayi saurin rufe natah taci gaba dah kissing
d'inshi kamar tanashan alawa, hijjab d'in jikin tah yake k'ok'arin cirewa tayi
saurin rik'ewa, kai tah girgiza masah tace kayan bacci neh ajiki nah zani
nadaura nayi sallah, Ummunah ai kayan baccin nakesan gani pls kinji, sake
hijjabin kad'an zangani Ummunah, sakewa tayi amma tayi saurin saka hannayen tah
k'ark'ashin hijjabin takare k'irjin tah!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[03/08, 02:10] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳17⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 My All Members of PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
sannun ku matan dababu kamar Ku acikin💪🏾 WRITERS iyayen hak'uri
masu kaifin kwakwalluwa dah basira Allah yak'ara daukaka Sisters One love 👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Cire hijjabin yayi
yanah kallan yacce tah rufe k'irjin tah dah hannun tah dukkah biyu, Ummunah,
Na'am tace kai ak'asa, cire hannun naki toh, uhm uhm tah kwantar dah kanta
peacefully akan k'irjin sah, Ummunah ni d'in? shikenan nagode, tashi toh ajiki
nah, yitayi kamar bataji shi bah ta gyara kwanciya abinta, kiss yamata agoshi
sannan yace toh bud'e nagani Ummunah Er Albarka, ahankali tasauke hannun tah
amman tayi hugging d'inshi tightly yanda bazai iya taba tabah, chakulkuli yayi
matah tuni tasake shi tanata kyalkyale dariya kamar bah gobe, kallon tah yake
cike dah so yakuma janta<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>jikinsa yahad'e
bakin su suka fara kissing junan su, ahankali yad'aga rigar baccin yafara
shafar cikin tah soothingly sannan yafara yin sama zuwa k'ark'ashin k'irjin tah
yanah shafar tah ahankali yakula dah yacce jikin tah keh rawa amman koh kad'an
beh biye matah bah yakai dah ta'ba abinda yayi niyya kenan wayan sah yasoma
ringing tsayawa yayi yakalli wayan sannan yak'ara kissing d'inta for 1 more
minute kafin yayi picking, ganinan zuwa taji yace, hankalin tah atashe takalle
shi tace ina zakaje kuma, babu inda zanje bayan gurin aiki Ummunah, kinga muna
nan ashe har lokaci yatafi k'arfe shida yayi bamu sani bah, uhm kawai tace, toh
d'agani Ummunah inje inyi wanka koh, uhm tace yad'aga tah ahankali, kwallan
idanun tah yagoge yakuma rungume tah yace, "Allah yayi miki albarka kinji
Ummunah, Inasan ki sosai I love U sweetheart, I love U too tace tareda k'ank'ame
shi dakyar yaraba tah dah jikin shi tafad'a kan gado tanah kuka saurin barin
d'akin yayi sabida besan jin sautin kukan tah koh kad'an wanka yayi yashirya
kafin yafita yakuma zuwa wajan tah jikin gado yasame tah zaune ak'asan d'aki,
tanah ganin shi tayi saurin tashi tafad'a jikin shi takuma fashe masa dah kuka,
shhhh wifey pls manah wallahi idan baki daina min kukan nanba bazan iya tafiya
nabarki bah, aikin fah ana jira nah fah, shhhh fad'amin mezan siyo miki yau
idan zandawo, bakomai tafad'a muryan tah narawa, a'a zan siyo miki abubuwa
kinji my love, uhm kawai tace sannan takalle shi tashafa fuskan shi peck takai
masa agoshi sannan kan lips d'insa tace karka dad'e kaji Abusaiyeed, bak'aramin
dad'i yaji bah yace matah, "uhm naji toh yimin dariya", uhm uhm nibazan
yi bah, toh shikenan had'e min rai, dariya tayi sosai takai masa bugu ak'irji
tace ban iya bah Abusaiyeed, AOuchh, Ummunah zafi, sorry sweetheart bansan zai
maka zafi bah, winking ido yayi yace "namiki wayo kinyi min dariya",
I love U Abusaiyeed tafad'a tanah masah murmushi, I love U too yace tareda
jawota jikin sah kunnen tah ya lasa sannan yace "bakida kunya koh Ummunah
sunan mijin naki kike kira kai tsaye haka", k'ank'ame shi tayi cikin
shagwa'ba tace, "toh ni ba dad'i yakemin bah, aini inaso akwai dad'i sosai
sunan, bakin tah yaja yace, "dad'i kamar bakin ki, ai bekai bakin ki dad'i
bah, fuska ta'boye ak'irjin shi sabida kunyan sah dataji, wayan saneh yakuma
ringing, tanah jin haka tayi saurin d'agowa suka had'a ido, hannun tah ya rik'e
yace, "make sure U eat wifey kinji pls", m late already take care
hannun tah yayi pecking sannan yajuya har yaje doorstep, yakuma dawowa yayi
hugging d'inta yace, " pls eat I love U so very much Ummunah zandawo
dawuri Insha Allah, hawaye neh yafara forming a idontah rapidly ganin haka yasa
yajuya yafice daga d'akin batare dah 'batah lokaci bah yabar cikin gidan!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[03/08, 02:10] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳18⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 All My Groupies & All Fans Of Matar
Dr.Saiyadee Novel, Nagode dah kauna Allah yabarmu tare dearies,Bunch of love
berries😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Kukan tah taci
tagode wa Allah jitayi she wants to be with her hubby tayi missing d'inshi
sosai, jikin tah asanyaye duk wani kasala takeji takasa yin komai dakyar tayi
wanka tazo tah gyara d'akin tah sannan tawuce d'akin sah tah gyara tsaf kayan
shi tagani daya cire tah ninke su tasaka acikin basket d'in kayan datti, toilet
tafad'a tadau towel d'inshi tareda shorts d'inshi duk tawanke su tsaf sannan
tawanke toilet d'in tsaf tagyara koh ina sannan tasaka turare tuni koh ina ya
mamaye dah k'amshi mai dad'i, Masha Allah Ummulkhair sannu dah aiki, d'aki
takoma tafad'a bathroom takuma rinsing body d'inta sannan tafito anutse ta
shirya kanta tasaka doguwar riga nah peach material d'aure kanta tayi tadawo
parlour tazauna tah kunna kallo, tunawa tayi dah Abusaiyeed d'inta yace taci
abinci hakan yasah tah tashi tanufi fridge, chocolates tagani dah popcorn sai
Nagari fresh milk, kallo tah tsaya yi chan kuma tah hango wani wrapped abu
hannu takai taga shawarma neh amman har yayi freezing d'auka tayi taje tayi
heating d'inshi a oven tadawo tazuba fresh milk d'in a cup, bayan yayi tadauko
aplate tadawo tacigaba dah kallon tah tanaci ahankali, phone d'inta neh yayi
k'ara juz after a bite bayan tayi swallowing taduba taga Abusaiyeed neh yayi
matah message cike dajin dad'i tabud'e message d'in mai kamar haka, Salam my
crying princess kinci abinci, pls kidena kuka kozan samu nayi concentrating I
love U kinji sweetheart, Insha Allah yau zandawo dawuri, tekia! Murmushi tayi
bayan ta karanta tayi kissing wayan sannan taci gaba dah cin abincin tah cike
dah murna bayan tagama taji ana buga k'ofa tashi tayi taje tah bud'e bak'i tayi
har yanzu tanata yin bak'i jama'a sunata shigo matah, bayan tah tar'be su
tawuce kitchen tabud'e freezer dubawa tayi taga tomatoes dah dukwani kayan
lambu komai fresh tsalle tayi nah murna tawuce store tah de'bo rice cikin 1hour
tagama had'a fried rice d'intah tuni gidan ya mamaye dah k'amshi cikin warmers
tazuba takai kan dinning haka tadinga kar'ban bak'i dashi har yamma dasuka
daina shigo matah sannan tazo tayi wanke~wanke tah gyara koh ina cikin gidan, shuru
babu kowa sai ita kadai harta d'aura towel zatayi wanka saikuma tayi tunani
kiran Saiyadee kafin tashiga, kiran numban tayi lucky her yayi picking kiran
farko murya yasauke mata chan k'asa kamar baby yace I love U babynah, I love U
too Abusaiyeed, yaushe zakah dawo I miss U, nima nayi<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>missing d'inki bakin ki nakesan sha yanzu
dariya tayi tace, "Abusaiyeed bakada kunya koh, baka jin kunya nah koh,
toh akanme zanji kunyan ki Ummunah, mata tah ce kefa, nifa bakyason shan baki
nah, murmushi tayi tace, "ni kabarmin wannan tambayan Abusaiyeed",
pls Ummunah kifad'a min kinji, inaso kadawo dawuri, dagaske Ummunah? Uhm
dagaske nake Abusaiyeed, toh nagode Ummunah Allah yayi miki Albarka, yanzu
mekike yi, bakomai wanka zanyi har naje bathroom nadawo nakira kah, dagaske
Ummunah, uhm gaske nake, kinyi kyau, kai taya kaganni dazaka ce nayi kyau, eh
manah nasan towel d'in jikinki yamiki kyau sosai, kinga dah inagida nizan zama
towel d'in, chab nibazan yarda bah tafad'a kamar tayi masa kuka, toh babynah
kinci abinci koh, uhm naci, toh sau nawa kika ci, sau biyu naci, dagaske
Ummunah, eh dagaske nake, toh nagode sosai sosai sweetheart, toh Abusaiyeed
mezan dafa makah anjima, Ummunah plantain nakeso dah fried egg, toh shikenan
angama, zakasha tea kokuma wani abun kakeso daban, uhm zansha sweetheart,
Abusaiy......................<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummunah inazuwa inazuwa zankira ki anjima am busy pls d'ip
taji yakashe wayan!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[03/08, 02:10] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳19⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 Sweetheart Maryam Mahmud Sky(Mama Sky), Insha
Allah the Sky will be 4rever be ur limit, tnx deary for being a great supporter👌🏾
ANATARE OneLove Maryama👄😻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Kasa tashi tayi
tashiga wanka kwanciya tayi still hoping zai kirata yanda yafad'a, saidai kash
har 10pm tanah kwance tanah jiran kiran shi shuru bai kira bah, babu abinda
takeyi sai karanta messages dasuke exchanging tun kafin suyi aure har tagama
karanta su kaf, bai kiraba bini bini taduba phone d'inta babu call from him,
disappointedly tah tashi tashiga bathroom tayi wankan tah bayan tagama koh
shirya wa batayi bah tawuce kitchen fresh bunch of plantains tad'auko tah fara
ferewa amman gaba d'aya hankalin tah yanah wajan mijin tah Addu'a take kawai
yadawo jitake kamar zatah mutu idan bata ganshi bah, tanah wannan tunanin neh
tah yanke dah sharp knife dake hannun tah, Aouchh tayi groaning in pain, jini
neh yasoma rushing daga yatsan tah, d'auraye hannun tayi amman jinin bai tsaya
bah hakan yasah tayi applying vaseline tadaura wool akai tacigaba dah aikin
tah, wajan soya plantain d'inma saida tah k'one kasan cewar towel neh ajikin
tah mai ya tasar matah ahannu daga sama har kuka saidah tayi amman hakan bai
hanata soya mashi kwan bah, bayan haka takuma daura masah tea komai tahad'a tah
ajiye a parlour kan dinning tawuce d'aki tanah maijin rad'ad'in ciwukan tah
sosai, waya tah d'auka tah kira Mummyn tah bah k'arramin dad'i dah nutsuwa tasamu
bah murna take sosai gaisawa sukayi dah Maman natah inda Mummy take tambaya ina
Saiyadee, shuru tayi babu amsa saikuma tace, "Mummy ai sai gobe zai fara
fita aiki yau tun safe beje koh inaba sai yanzu ma yafita siyo manah bread nah
breakfast d'in gobe", toh mamanah nagode masah sosai Allah ya Albarkaci
rayuwar ku<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>baki d'aya, Ameen Mummyn mu
mungode, yauwa er Albarka dasafe mayi waya koh? kai Mummy ai bamuyi wayan bah
gaisawa kawai mukayi fah, ahh kuji min 'ya wani wayan zamuyi bayan wannan
maza~maza jeki gun mijin ki, ni Mummy ina Affan yake? sai gobe naakira ki kwa
gaisa dah k'anin naki go to bed Sweetheart, shagwa'ba tasoma yiwa Mummyn natah
Mummy takashe wayan, kallon wayan tah tsaya yi taji wani mugun son mahaifiyar
tah nah fisgan tah kuka tafashe dashi tayi matah message kamar haka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Assalam Mummy nah
rayuwa tah, yakike aikin gida yanah miki yauwa koh?, babu mai tayaki girki
koh?, kiyi hak'uri Mummy zanzo nataya ki, nayi kewar ki sosai, Mummynah I love
U kicewa Daddynah nayi kewar sah inason sah sosai!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Upon receiving her text Mummy dariya tayi kawai tah nunawa
Daddy, Allah sarkie Khairiya tah d'iyar arzik'i mai tausayi iyaye Allah yabata
zaman lafiya yasa tagama dah duniya lafiya, cewar Daddy!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Wanka Ummulkhair
takuma shiga tafito tasaka kayan baccin tah sannan tasaka hijjab har gwiwa
takwanta bacci yadauke tah, chan wajajan shabiyu saura cikin bacci taji phone
d'inta yanah ringing dubawa tayi taga Abusaiyeed neh! Hello tafad'a muryan tah
chan k'asa, Ummunah, Na'am Abusaiyeed yakake? Ina abinci nah Ummunah?, wanne
toh, wanda kika dafamin manah, yanakan dinning ai nagama tun d'azu, toh
kawomin, ina d'in zankawo makah Abusaiyeed tafad'a dah d'an k'arfi, dariya
tabashi yace office manah, uhm uhm niban zuwa, toh shikenan bara nakira Mummy
nace gashi nace kikawo min abinci kince ban isa bah, laa Abusaiyeed yaushe
nafad'a hakan tafad'a cikin tsantsar shagwa'ba kamar zatayi kuka, sannan tace,
"kumama kona fad'i hakan ai banida laifi dare yayi babu 'ya mace tah
kwarai awaje by this time, dariya yayi yace, "toh maza~maza kawomin ina
part d'inah"!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[03/08, 02:11] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳20⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 Sweetheart Maman Sadiq Lagos Allah yabar kauna
my sweet sis Allah yaraya min khadeejah dah Sadiq, Allah ya Albarkaci rayuwar
ku baki d'aya nagode sosai dah kauna deary👄😻,ANATARE Sis🤝<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Yeaah dagaske
Abusaiyeed kanah part d'inka, Eh manah Ummunah maza kowamin, uhm zoka d'auki
abinka bacci nakeji ni, Ummunah shikenan nagode tunda so kike nakwana dah
yunwa, shikenan saida safe yakashe wayan, tashi tayi<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>tawuce dining tadauki abincin tareda
k'arramin flask d'in ruwan zafi sai cup, part d'inshi tawuce straight
bataganshi a parlour bah hakan yasah tawuce d'aki dah sallama tashiga kamar
wata mara gaskiya wani k'amshi yaji mai shegen dad'i d'agowa yayi yakalle tah
yayi murmushi, ita kwa suna had'a ido tah murgud'a masah baki dariya yayi yace
matah, "Ummunah ni d'in toh laifin menayi haka", baki tah zumburo
tace toh ni ina ruwanka dani bah kallo kake bah, aw baruwa nah dake shikenan
Ummunah nagode toh, abinci tah ajiye a bedside table zatah juya ya fisgota tah
hannu tafad'a jikin sah K'ara tasaki wayyo Allah nah zafi, tuni ya rikice ya
d'ago tah idanun sah har sun sauya yace Ummunah menene meya sameki, inane
kemiki ciwo, meya saki k'ara, kanki nayi dah k'arfi koh, am so sorry babynah,
bakai baneh zafi yakemin Abusaiyeed, meyake miki zafi yafad'a tareda manna tah
akan k'irjin sah, d'an yatsan tah tanuna masah, cike dah rud'ani yarik'e hannu
yanah fad'in Ummunah anya kina tausayi nah kuwa yanzu sabida Allah ina kikaje
kika jimin wannan ciwon haka, dariya tayi tace, "girki nakeyi
nayanke", girki meh kike girkawa haka, plantain d'inka manah tafad'a tanah
dad'a shigewa jikin sah, Ummunah nine koh?, nasaka ki girki kin k'one koh? toh
kiyi hak'uri kiyafe min sweetheart, bugun shi tayi ak'irji tace, "ka jimin
wannan Abusaiyeed d'in toh abinda har k'onewa ma nayi", tuni ya rikice
matah yanah fad'in, "toh gaskia Ummunah adaina wannan girkin awani dalili
princess d'inah take jin ciwo wajan girki kinga ni abincin ma nafasa ci kawai,
tashi tayi tad'auko plate d'in sanan tad'au guda d'aya tasaka masah abaki,
tace, "wlh Abusaiyeed gwanda ma kaci koh babu ruwana dakai duk ciwon
danaji duk abanza ai bazai yuba, toh nikam banza ci bah nace ki koyi girki tun
agida bah kink'i bah aiga irinta nan kina k'onewa harda yanke2, dariya tah
kyalkyale dashi tace, "Abusaiyeed d'inah koh yanzu yazama d'anyan abinci
zan dafa shi tsaf, afad'ar kiba zadai kimaida ni jagwalgwalo, hancin shi taja
tace, "ci abincin zaiyi sanyi", abincin yashiga ci ahankali, sauka
tayi zatah had'a masah shayin taji marar tah tarik'e hakan yasah tayi saurin zama
tareda saka hannun tah daidai marar tah, abinci yayi saurin turewa gefe yaje
gabanta yanah fad'in, "bakya jin dad'i koh? lumshe ido tayi tace,
"uhm uhm babu komai, C'mon sweetheart bakyajin dad'i nakula dake tun jiya
jikin ki yanah daukan zafi tell me what's wrong, wuyan tah yata'ba yaji zafi,
tashi yayi yad'auko first aid wani kwalban allura taga yad'auko tuni tamik'e
taje tasame shi tace ni fah Allah kalau nake nace makah, jawota yayi jikin sah
yace, "shikenan tunda bazaki fad'amin bah zanmiki guda goma kuma dolenki
ki tsaya, A'a tafad'a cikin shirin yin kuka, toh fad'a min menene yake damunki,
toni bah mesturation d'inah baneh zaizo kuma nakejin ciwon mara, tak'arasa
maganar tanah kuka, shhhh ya isa toh daina min asarar hawayen, bara namiki
allura guda biyu kawai Ummunah saiki samu relief Insha Allahu, a'a nibanso
kabarni kawai ya Saiyadee, Chab kina matar likitan guda bakida lafiya nabarki,
toh menene amfanin iya aikin nawa indai bazaki mora bah uhm Ummunah, Allura
babu fashi, kwace kanta tayi tasamu waje tazauna tafara kuka Shikuma yakoma kan
gado yacigaba da cin abincin sah ciyake kawai amman hankalin sah na wajan tah,
tashi tayi tayi hanyar k'ofa batare daya kalle tabah yace, "ina zakije
zonan", plate d'in ya ajiye gefe, yabud'e matah hannayen sah biyu tafad'a
jikin sah, nifa banason alluran kah, toh Ummunah yakike son namiki neh kiga fah
yanda yake saki zazza'bi kuma......, toni kabari idan yazo saika min kaji pls
Abusaiyeed, idan banah gida fah lokacin Ummunah, a'a kanama gida My Dr•, toh
shikenan naji, hawayen tah yagoge yaja kumatun tah yace, "sarkin kuka
kawai, kissing idanun tah dukkah biyu yayi yace, " haka kawai ayita sa
idona yanah hawaye kullum, lips d'inta yakama yafara kissing itama kissing
d'inshi take by now sosai yafara zarcewa saidai yanzu Ummulkhair fama take dah
ciwo irin nah matah, kuka take silently, Shikuma saiyadee yadage romancing
d'inta yake kawai, ihu tasakar masa wanda yasa shi tsayawa chak!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🎍🐚NoVel👇🏿WriTter 🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳21⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 Nana Aisha deary, Tnx Allah yabarmu tare, Allah
yaza'ba miki mafi Alkhairi aduk inda kike, love U so very much sweetheart😻ANATARE<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ummunah...Ummunah!
tashi yayi azabure yad'ago tah, menene Ummunah, cikin kwalla sosai tace,
"mara nah ciwo yakemin sosai kuma bah kaine kah danne min bah", manna
tah yayi ajikin shi sosai yace, "Ummunah zaki fasa min zuciya koh, kinsan
yanda kika d'aga min hankali kuwa, kidaina kinji wifey? uhum nadaina
Abusaiyeed, yauwa babyn Dr., Abusaiyeed ni wanka zanyi, Ummunah yanzu zakiyi
wankan?, uhm yanzu idan nayi zandawo kaji, toh tashi kije kiyi ina jiran ki,
mik'ar dah itah yayi tawuce d'aki, shikuma yakoma yayi ruf dah ciki akwance
yanah tunanin tah soyayyar tah nadad'a ratsa shi, Ummulkhair kuwa yanzu period
d'inta har yazo k'afafun tah duk sun rik'e sai rawa suke mata gabad'aya tayi
loosing balance, kuka take sosai dakyar tasamu tayi wanka tafito towel neh
ajikin tah tah kwanta arigingine tanah mai juyi ak'asa pant neh dah pad akusa
dah itah amman sam takasa sakawa saida taji kamar zatah mutu kuma jikin tah zai
soma 'baci tayi k'arfin halin rarrafawa zuwa part d'inshi dakyar tasamu tashiga
dah kuka koh k'arasawa d'akin batayi bah yaji kukan tah aguje yafito yasame tah
a parlour tanah rarrafawa hawaye nabin juna sha'be~sha'be afuskan tah, jawota
yayi jikin sah, yashiga goge matah hawayen ita kuwa babu abinda take cewa sai
ya Saiyadee akwai zafi ni zafi yakemin, gabad'aya tah rikita shi yarasa gane
kanta d'agata yayi ahannun sah ya jijjiga tah, sannan yace, "Ummunah
fad'amin menene, uhm menene yake rikita min ke haka yafad'a cikin tashin
hankali, jitayi jini yataho matah hakan yasa tayi saurin mik'a masah pad dah pant
d'in hannun tah, tace sakamin ajiki pls "kar'ba yayi, yace
"sweetheart ina pack d'inshi", yanah d'aki nah, ajiye tah yayi
ahankali yaje yad'auko ledan pads d'in gabad'aya sannan yadawo yazauna gefen
tah yadinga bin Image Instruction najikin pack d'in har yasamu yayi attaching
pad d'in to pant d'inta, d'agowa yayi cike dah murnan ya iya yace,
"Ummunah oya gyara in saka miki" d'agota yayi yajata jikin shi, amai
tashiga kwarara masah ajiki hankalin shi atashe yaduba temperature d'inta yaji
jikin tah rau dah zafi, mik'e wa take k'ok'arin yi tanah fad'in am so sorry
Abusaiyeed I wasn't able to get hold of it, baran gyara makah jikin kah,
kingama aman shine tambayar dayayi matah, koh amsa shi batah iyayi bah towel
d'in jikin tah ya kalla yaga duk ya'baci dah jini sosai yaji tausayin tah,
yace, "sorry kinji wifey"<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Awwwwnn dirty Ummulkhair😱😧<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">d'agata yayi yawuce dah itah toilet sannan yacire rigan
jikin sah yasaura singlet, toilet d'in yawuce yafara matah shirin wanka, sam
tak'i yarda wai itah bataso harda cewa yabata hijjab d'inta, aw sai yanzu kika
kula bada hijjab d'in kikazo bah idan kinga nabar bathroom d'inan toh nah wanke
ki tas, fuska yahad'e matah shima yashiga tube d'in towel d'in jikin tah yake
k'ok'arin kuncewa tafara masa kuka, khairat yafad'a dah k'arfi, kallon shi tah
tsaya yi kukan tah yak'aru sosai wani amman takuma yi hakan yasa bayan tagama
koh sauraran tah bai kuma yiba yakunce towel d'in jikin tah yashiga yimata
wanka tariga tah galabaita itama koh tanka shi batayi bah, wanka yayi matah
sannan yamata brush, cikin towel d'inshi ya nad'o tah kamar baby yakaita kan
gado attached pant&pad d'in yad'auko yasaka matah sai ruwa full cup yabata
tasha sannan ya kwantar dah itah yad'auki rigar sah datayi amai ajiki yawuce
toilet, kayan jikin shi yacire gabad'aya yahad'a dah towel d'inta dah rigar sah
ya wanke su tas, sannan yawanke toilet d'in shima yayi wanka yafito, drying
jikin yayi agurguje yazira jallabiyan sah yad'auko first aid treatment, allurai
uku yahad'a matah, matsowa yayi kusa dah itah yace, "allura za ayi kuma
bansan kuka, kina ji koh, tashi take k'ok'arin yi tanah fad'in nidai d'aki nah
zanje kabarni natafi, jawota yayi jikin sah yace, "Ummunah wlh Allah saina
miki alluran nan dan haka kiyiwa kanki mai kyau ki tsaya babu zafi, kuka tasoma
yi masa kwantar dah itah yayi not minding her yasoma shirin yimata alluran,
tashi tayi azubure tah k'ank'ame sah cikin kuka tanah fad'in, Abusaiyeed
dagaske allura zaka min? mugayen doctors neh sukeyin allura fah, kuma kai bah
mugu baneh Dan Allah banso, dariya tabashi sosai, dariya yayi yajawo tah
jikinsa fuskan su yahad'e in such a way that hancin su dah baki nah gogan juna,
calmly yake whispering yanah fad'in, Ummunah lafiyar ki fah tafi min komai a
duniya, yanzu ke bakya san kisamu sauk'i Dan Allah kiyi hak'uri nayi miki
wifey, babu zafi nace miki, idan ban miki bah amai zakimin kuma dah zazzabi
zaki kwanar min toh idan bakida lafiya tayaya zanfita aiki gobe, kinsan mutane
nawa zan taimakawa wajan aiki gobe? Dan Allah Ummunah ki tausaya min namiki
alluran nan kinji, batace komai bah yakuma kwantar dah itah, toni acinya
zakamin Abusaiyeed kaji, A meh kikace? cinya nah tafad'a tanah murza idanun
tah, No way abaya za'ayi yisauri kafin kiji wani aman namiki, dakyar yasamu
yayi matah allura babu abinda takeyi sai kuka dah fad'in ya Saiyadee, ya
Saiyadee tah maimaita sunan yafi ak'irga jawota yayi jikin sah bayan yagama
yanah lallashin tah tareda mulmula matah wajan, k'irjin shi take bugu tanah
fad'in mugu bakace babu zafi bah, dariya yakeyi kafin yahad'e bakin su waje d'aya
calmly take sucking lips+tongue d'inshi soothingly!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[29/07, 16:33] +234 703 125 8794: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳23⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 all Fans of Matar Dr Saiyadee Novel ANATARE
MASOYA🤝<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Assalamu Alaikum Ni Mhiss B~hal Ina mai bawa masoyan wannan
littafin hak'uri dah babban murya bisa jina shuru dah kukayi banida lafiya neh
amman Insha Allah zan daure nadinga muku typing koyaya neh maganar gaskia naji
dad'in kira dana samu daga masoya nah especially en group d'in Mhiss B~hal
Novels sakallahu bil jannah berries😻👄😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>ASUBA<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Rik'e yake dah
itah gam saidai kash har yanzu yaji jikin tah akwai zafi ahankali yake
k'ok'arin raba tah dah jikin sah, ido tabud'e ahankali tanah kallon shi, wifey
yace ahankali, Abusaiyeed tafad'a muryan tah baya fita sosai, tashi yayi zaune
yaja tah jikin sah, yace, "sweetheart hw re U feeling?, sick Abusaiyeed
tafad'a tanah mai zagaye hannun tah awuyan shi, sannu ak'ara allura d'aya koh
wifey? kai kad'ai tah girgiza masah alamun a'a, Dan Allah sweetheart ki taimaka
min ayi yarad'a matah akunne, uhm~uhm tafad'a set to cry, guda d'aya zanmiki
Ummunah kinji pls? ni banso nace makah, toh shikenan meh kikeso, gida tah amsa
frantically, gida kuma Ummunah ya maimaita with confusion, eh gida tah amsa
atak'aice ni ka kaini idan kana dawowa kabiyo kah daukeni zanji sauk'i agurin
Mummy nah, gurin Abusaiyeed fah mezaki ji yafad'a tareda kai matah kiss agoshi,
Ummunah kin ta'ba jin amaryan data fita bayan juz 3days agidan mijin tah? Eh
manah anayi, toh shikenan bara nakira Mummy nace zankawo ki, ni A'a surprise
zanyi matah, eh tunda kinsan bakida gaskia bah dole kice surprise, k'ank'ame
shi tayi tanah shak'ar turaren jikin sah, Ummunah lokacin sallah yayi fah kin
rik'e ni, toh ni kacire rigan kabani k'amshin turaren nakeso, murmushi yayi,
sannan yacire rigan idanun tah tarufe dariya yayi yasauka daga kan gado tareda
batah rigan, kar'ba tayi takife kanta akai not minding him anymore, shikuma
yawuce yaje yayi sallah bayan ya idar yanah karatun Alkur'ani tashige bathroom
tayi wanka, tanah fitowa tawuce d'akin tah taje tah k'imsa kafin tadawo shima
har yayi wankan yayi shirin wajan aiki, tanah shiga yaware matah hannun sah
taje tafad'a jikin sah, kai Ummunah har yanzu jikin ki dah zafi alluran dah ya
riga yahad'a agefen sah yadauka yace bara muyi koh sweetheart, hannun shi
tarik'e tanah fad'in Abusaiyeed nifa babu ruwanka dani nace, kwanciya yagyara matah
yad'aga skirt d'in jikin tah paying deaf ears to her pleas yayi matah alluran,
zamewa take k'ok'arin yi daga jikinshi wai itah adole yayi matah laifi yayi
matah allura, rik'e tah yayi gam yanah dariya, ni kyaleni tafad'a cikin kuka
bakin tah ya lalabo yahad'e danasa, kissing d'inta yake kafin ahankali yasake
tah, Ummunah zan tafi wajan aiki kinji, I love U Abusaiyeed tace tah dad'a
shigewa jikin sah, rungume tah yayi yace kici breakfast immediately kinji
alluran yanada k'arfi Ummunah, toh Abusaiyeed gidan Mummyn fah?, a'a Ummunah
bar wannan batun Mummy zatayi fad'a idan ba ayi sa'a bah harda duka, tashi tayi
ajikin shi tah bige shi akafad'a tanah mistsik'e idon cikin shagwa'ba, hannun
tah yakama yakai masu kiss yace matah tayi hak'uri, toh ni yaushe zaka kaini
gida Abusaiyeed? Sai kinyi wata d'aya Ummunah, kwanciya takuma yi ajikin shi,
kafin tace Allah yakaimu, Ameen that's my sweetheart akwai ki dah fahimta dah
hak'uri ina sonki sosai kinji, nima Inasan kah sosai Abusaiyeed d'inah, yauwa
babyn Dr. Saiyadee, bara naje aiki koh, uhm tace kafin tah k'ara binne kanta
ak'irjin shi tanah shak'an k'amshi jikin sah, dariya yayi sannan ya shafa cikin
tah yace, "wai tunma banyi ajiya cikin wannan cikin bah kenan, idan kuma
nayi fah, toh ya kenan, bugu takai masa abaya tah murgud'a masa baki, dariya
yayi abinsa yace, "Ummunah ina kaunar ki kina birge ni sosai, I love U, I
juz love everything about U, Ummunah U're juz so perfect, U're my world,
mine&mine alone Allahu yaraya minke dah abinda zaki haifa min, Ameen Abusaiyeed
tace tanah yimasa dariya kafin su mik'e rik'e dah junan su suyi parlour!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Masu Neman littafin nan daga farko it's very easy basai kun
tambayi kowa bah just click on that link at the beginning it's my blog zaki
samu har inda aka tsaya opera koh browser yanah bud'e link d'in! Shi zandinga
bayarwa tah private ma Tnx all!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[29/07, 16:33] +234 703 125 8794: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳22⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 all Fans of Matar Dr Saiyadee Novel ANATARE
MASOYA<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">ATTENTION PLS: Naga mutane dayauwa suna tambayan Matar Dr.
Saiyadee daga farko zuwa k'arshe maganar gaskia Novel d'in 2017 neh In fact
July dinnan nafara rubuta shi, ina fatan zaku daina tambayan k'arshe kucigaba
dah bibiya nah! ANATARE🤝 🤝🤝INSHA ALLAH Mhiss~B tanah
gaisuwa🙋🏻OneLove<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ahankali yasaki
bakin tah badan yaso bah, murmushi yasakar matah yace, "am sorry Ummunah
bakida lafiya nah tak'ura ki", kai tah sunkuyar batace komai bah, kwanta
ki huta kinji, kwantar dah itah yayi yanah kallan tah, ya maran naki, dasauk'i
koh Ummunah, toh ni bah yanamin ciwo bah har yanzu, Ummunah kenan uwar raki toh
bara namiki massaging towel d'inta yad'aga zuwa upper thigh d'inta kamar tahana
shi sai kuma tadauke kai ahankali yafara matah massaging abdomen d'inta within
a blink of an eye tafara samun relief daga abdominal cramps d'in da takeji,
kallon shi take yanda yake massaging mara tah genuinely interested, jitayi son
shi yak'aru aranta sannu yake matah akai~akai murmushi tasakar masa, yanzu kuwa
he seems more interested to her navel, kallon cibiyan tah yake yi tah kula da
hakan amman tah basar lips d'insa taji ya d'aura akan cibiyan tah yayi mashi
slight kiss, saidai bai d'ago kanshi bah, batah ankara bah taji harshen sah
akan cibiyan tah yanah lasa ahankali, Abusaiyeed tafad'a ahankali, stop that m
sick kaji, saida yayi kamar nah 5mins yad'ago yakalle tah yace, " m sorry
kinji, kai tah d'auke tace, "me too m equally sorry", ya jikin wifey?
dasauk'i, toh kice wa cikin ki inji Abusaiyeed wai Dan Allah yadaina wahalar
min dake, murmushi tayi tah bige shi akafad'a tace kafad'a masah dah kanka,
kanshi ya sunkuyar zuwa daidai cikin tah yace, "laifin me mukayi kake wahalar
min dah Ummunah haka? Dan Allah kadaina, na'am banji bah mekace, dariya tah
kyalkyale dashi tace, "Abusaiyeed harda yi kaman dagaske cikin magana yayi
makah wallahi kabani dariya sosai", matsawa yayi yad'an sha bakin tah
sannan yace, " baki tambaye ni amsar dah cikin yabayar bah ai, fuskan shi
ta shafa tace, "I love U sosai Abusaiyeed d'inah, nima haka yafad'a muryan
shi baya fita, d'an yatsan tah guda yasaka cikin bakin sah yanah tsotsa, yanah
kuma shafa tah, Abusaiyeed nifa bansan menstrual cramps akwai wahala sosai, toh
shikenan MyUmmu I will prevent it next time Insha Allah, but how Abusaiyeed oh
sorry namanta ashe fah kai doctor neh, oh no sweetheart mu ajiye doctor aside
aw prevent it myself, zaro idanu Ummulkhair tayi sannan tace, "toh tayaya
zakayi preventing d'inshi", sweetheart aw get U pregnant and there wunt be
pains next month yarad'a matah akunne, bugun shi tasoma yi tanah fad'in ya
Saiyadee wlh ni banaso babu wani pregnancy, dariya yayi yaja karan hancin tah
yace kinsan me, a'a saika fad'amin Abusaiyeed, that was what ur stomach said
juz awhile back, cikin nawa toh yaushe tafad'a sounding surprise? eh manah
cikin naki, cewa yayi yana san babyn Abusaiyeed acikin shi, sai yadaina miki
ciwo murmushi tayi tarufe fuskan tah dah hannu, murmushi yayi shima yace,
"Ummunah ina sonki dayauwa bazan iya zaman duniya babu ke bah ina kaunar
ki nagode wa Allah daya bani ke, I love U Ummunah, nima Inasan kah sosai
Abusaiyeed, shuru yayi yanah kallon tah itama kallan nashi take kafin tace,
"ni kayana zansaka", oh C'mon sweetheart there's no need, u look sexy
in my towel, uhm uhm nikaya, kwanciya yayi yad'ago tah ya kwantar dah itah
asaman shi, kwantar dah kanta tayi akan k'irjin shi, yanah shafar kanta
ahankali yace, " Ummunah ya jikin, naji sauk'i no more pains Abusaiyeed,
Perfect glad to hear that sweet, sannu kinji, uhm naji kaima sannu, kasan me
kamar amai nakeji, A meh kikace, amai tafad'a kamar tayi kuka, Ummunah kinason
bulala kenan, kika yimin amai duka zan miki meh kika ci dah zaki dinga yin amai
meh acikin naki, dariya tayi tace, "Allah kaban dariya jubi yanda kadage
kamar dagaske dukan zakamin ai bakayi kama dah mai dukkan mace bah, I love U
Abusaiyeed d'inah Dr. mai Allura dah Bulala, murmushi yayi sannan<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>ya gyara kanta zuwa saitin zuciyar sah, yace,
"kinajin yanda zuciya tah ke bugu sabida sonki Ummunah, bazan iya rayuwa
babu kebah, kidinga hak'uri dani kinji karki ta'ba barina Ummunah dariyan ki
kadai noor ce acikin rayuwa tah, bata amsa bah sabida yanda tayi concentrating
tanajin bugun zuciyan nashi, Ummun........ bakin shi tayi saurin kamawa tanah
sha hankali akwance hakan yasa bai iya k'arasa kiran sunan tabah balle yayi
magana! shima kuwa dagewa yayi yanah shan abinsa, ahaka har bacci yayi awon
gaba dasu, saida asuba yafarka har alokacin suna k'ank'ame dah junan su, Masha
Allah Ummu dah Saiyadee!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">ASUBA @ pg23<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">NOTE:👇🏿👇🏿👇🏿<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Wannan novel din nah 2017 neh In fact wannan typing d'in
21st July neh, kudaina tambayar k'arshe kudinga tambayan cigaba ina kan rubuta
wa adinga min Uziri, sannan adinga min hak'uri masu bina private akan turawa
daga farko, Masu kira nah dah text nagode Allah yabar kauna ina Alfahari daku!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[29/07, 16:33] +234 703 125 8794: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳24⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2U My Mufeederh (Meenah) Ina sonki nagode dah
kaunar dakike nuna min deary😻 MUNATARE Insha Allah 🤝🤝🤝<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">ASSALAMU ALAIKUM Sisters and Brothers yau ina cikin farin
ciki sosai, sakamakon haihuwar dah sweetheart (MAGE) d'inah tayi, nasamu
k'aruwa MAGE nah tah haihu dah Asuba tasamu En biyu ina fatan zaku min Addu'a
Allah yaraya minsu kuma ina gayyatar kowa dah kowa bikin suna next week Insha
Allah😍👄😻 wlh sai murna nake Inasan MyCAT🐱🐱
sosai2 Rejoice Wit Me fah😻💃🏻💃🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Manne tah yakuma yi
jikin sah tareda kissing d'inta kafin yasake tah yace, "m so sorry sweet
kinga nayi latti pls eat well kinji I love U", I love U too sweetheart, I
kno Babynah lemme get going kinji, uhm bye tekia kaji, shafa tah yakuma yi
kafin yajuya cikin sauri ya fice yanah shiga mota yayi matah text kamar haka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ummunah if I must
say, I am the luckiest man on earth to have U as my wife, I love U so very much
darling pls tekia nd get well soon kinji heart desire! Bayan hakan neh yaja
mota yaficce daga cikin gidan, bayan tah karanta waje tasamu tah kwanta tanah
tunanin shi har bacci yadauke tah gate dah ake bugawa neh ya tashe tah, hijjab
tah d'auka taje tanah bud'ewa taga Affan neh cike dah murna take tsalle, oyoyo
lilbro tadinga fad'i kallon tah yake yace, "gaskiya sis U're amazing wai
keh abu k'adan neh yake saki murna koh yaya? Chab wannan neh abu k'adan wlh
babu wani k'adan shigo meh kah kawo min? Wammers d'in hannun shi tah kallah
tace, "kamar kasan yunwa nakeji had'e dah k'iwuya", laa keda kikeyin
abincin gida daa inaga nake dah mijin ki kad'ai?, kai sis bakya jin yunwar dai,
hmm bro bazaka gane baneh chan daban nan daban, cooler taja gabanta tabude wani
k'amshi yabigi hancin tah, white rice neh dah doya sai stew d'in naman rago ai
tama kasa jiran plate spoon d'in coffee dah Abusaiyeed yasha tah Zara tafara
ci, wai wannan abincin akwai dad'i lilbro Allah yasaka wa Mummy dah gidan
Aljanna har bayan aure tanah d'auwainiya dani, mungode sosai, murmushi yayi
yabud'e system d'inta yafara game, Ummulkhair kuwa abinci taci tak'oshi har
takira Abusaiyeed tah sheda masa cewa taci abinci sosai kuma tah k'oshi, sosai
yaji dad'i ya dinga shi mata Albarka harda yimata Alk'awarin kyauta kafin yakashe
wayar dacewar zai kirata anjima aiki yakeyi, basar wa tayi sabida Affan dukda
cewar taji babu dad'i hira su kasha sosai dah Affan har yamma kafin suyi
sallama yatafi, sam bataji dad'i bah saida tayi kwallah dazai tafi tafad'a
masah yagaida Mummy dah Daddy yafi sau ak'irga,<span style="mso-spacerun: yes;">
</span>bayan tafiyar sah neh Ummulkhair tasoma jin wani azababben ciwon mara
tun tanah daurewa har saida taji kamar ranta zai fita waya tasamu takira numban
Abusaiyeed har saida tamishi missed calls wajan goma babu amsa rasa yacce zatayi
tayi take taga jini yafara rushing yanabin k'afar tah rapidly kuma tasan this
is unusual<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>something must be wrong with
her kasa jure azaban tayi tafara kuka cikin wani irin yanayi, kuka take sosai
tanah dailing numban sah, baiko d'aga bah taga yayi matah message kamar haka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Inazuwa wifey aiki
nake am busy!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Kuka tafashe dashi dan batada k'arfin yimasa message wayan
ma dakyar take rik'e shi sabida yanda jikin tah yake rawa sosai, gashi batasan
takira Affan tanah tsoron karya fad'a agida kuma bazama tah iya tashi tabud'e
masah k'ofa bah idan yadawo hakan yasa tadinga kiran mijin tah sabida tasan
yanada spare keys nashi ahannu, by now she's unstable sabida yanda jini ke fita
ajikin tah gashi taji ana buga k'ofa amman bazata iya tashi bah, Allah Allah
take wani yakawo matah d'auki, Affan neh yadawo sabida mantuwa dah yayi, abakin
gate d'in gidan Ummulkhair yatarar dah bak'i irin en shiga wajan amaryan nan
suna buga k'ofa har zasu tafi yace, "ku tsaya nak'ara bugawa ai yanzu
nafita saidai koh wanka tashiga, nima mukulli nayi musanye shine nadawo d'aukan
nawa namaida natah", cike dah fara'a suka amsa shi tareda tsayawa
patiently yayin dah shikuma yasoma buga k'ofa anxiously with the hope of zatah
bud'e masah on time, saida yabuga yabuga amman shuru har saida abin yafara
bashi tsoro, numban tah yashiga dailing nanma yana ringing amman ba'a d'auka
bah, hankalin shi bah k'arramin tashi yayi bah jiki narawa yajuya yarasa yanda
zaiyi sabida yasan idan ma wanka take yaci ace tafito toh shidai lafiya
yabarta, bak'in sunga yanayin sah hakan yasah suka dinga kwantar masa dah
hankali tareda fad'in Insha Allahu tanah lafiya babu komai!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[29/07, 16:22] +234 703 125 8794: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳25⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 My fantastic sweetheart FATIMA USMAN DIKKO,
nagode dah kaunar dah kike nunamin ina Alfahari dake deary, ANATARE🤝 🤝🤝⛹🏻♀INSHA
ALLAH 😻😍😻👄💋👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Zufa Affan yakeyi
kawai yarasa abinda keh masa dad'i she can't be OK d'azunan earpiece d'inta ya
lalace ahannun shi balle yace earpiece takeji, lek'awa yake tah gefen gate
amman sam babu abinda yake gani, mukullin hannun shi yakallah kana yaduba ramin
keyhole d'in jikin gate yaga pattern iri d'aya neh without hesitating yayi
plugging key d'in ya murd'a cikin sa'a k'ofa yabud'e ciki yanufa direct bai
ganta a main parlour bah, d'ayan<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>yaduba
yaganta daidai corridor d'in d'akin tah dah alamun rarrafawa tayi daga d'aki
zuwa wajan, ak'asa akwance take kamar babu rai ajikin tah jini koh ina tsoro
neh sosai yakama shi ganin yanda jini yayi yauwa ak'asa kasa ta'ba tah yayi
sabida yanda yaga skirt d'inta ya'baci dah jini cikin hawaye dah tashin hankali
yafita tsakar gida inda yatarar dah bak'in<span style="mso-spacerun: yes;">
</span>azaune, cikin hanzari yake masu bayani bah tareda wani 'bata lokaci bah
sukayi ciki dasauri, nan suka sameta kwance yanda yamusu bayani, d'aga tah
sukayi inda d'ayar takuma fita aguje dan kiran wata Midwifery dake unguwa,
cikin mintuna ashirin Midwifery d'in tah k'araso dah kayan aikin tah Affan babu
abinda yake sai kuka yakasa kiran kowa ma shi yama manta Dr.Saiyadee<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>gabad'aya hankalin shi yayi dubu atashi sai
up~down yake tayi, excusing d'insu Midwife Nafeesah tace yayi, haka badan yaso
bah yafita zuwa main parlour, aikin tah tashiga yi, allurai tah matah sannan
tabata kulawar gaggawa bayan tagama Ummulkhair tah farfad'o, tuni bleeding d'in
yakoma normal saidai ita dai kawai numfashi take, dah taimakon bak'in tasamu
tah k'imsa wa Ummulkhair jiki tareda yi matah wanka, pad dake side drawer tah
dauka tareda pant data gani a bathroom tuni tah shirya tah tsaf cikin wani d'an
k'arramin kayan bacci wanda dah k'adan ya k'arasa gwiwar tah dan tasamu tasha
iska, har alokacin Ummulkhair numfashi take kawai amman kwata2 batada k'arfi
she's very weak bisa gado aka d'aura tah sannan aka saka matah drip d'aya
babban Leda, bayan 30mins har tafara motsi dah magana ahankali take fad'in, Ina
Abusaiyeed? Abusaiyeed yakira? Ni ku kiramin Abusaiyeed, shhh midwife Nafeesah
tace matah sannan tashiga matah bayanin abinda yasame tah kamar haka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Toh nafarko dai Malama from what I saw u're ON, kuma
MENORRHAGIA is one of the most common types of abnormal bleeding from the
uterus, toh in some cases kuma the cause of heavy menstrual bleeding is
unknown, in some cases kuma some of the common causes are:<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Hormone Imbalance sabida idan ansamu matsalar hormone
Imbalance the endometrium develops in excess and eventually sheds by way of
heavy menstrual bleeding, and malama kinada Fibroids neh midwife tah tambaya,
kai kad'ai Ummulkhair tah iya girgiza wa alamun A'a, toh kidai je kiduba sabida
it can happen very fast kinga Fibroid shima yanah kawo much bleeding kinsan shi
haihuwa yake dazaran kuma yaje uterus d'inki it can cause heavier than normal
or prolonged menstrual bleeding, sai kuma medication U're have to be careful
when using drugs especially during menstrual period sabida certain drugs including
anti~inflammatory medications and anticoagulants can contribute to heavy or
prolonged menstrual bleeding, sannan other medical conditions includes pelvic
inflammatory disease (PID), thyroid problems, endometriosis, and liver or
kidney disease is likely to be associated with menorrhagia, wannan kenan we
have so many others, gaskiya mata we need to be extra careful sako nake isarwa
gareku sisters, In severe cases, heavy mensuration can interfere with sleep and
daily activities, LADIES blood loss from heavy periods can lead to ANEIMIA, and
symptoms are fatigue and shortness of breath. Dan Allah mata mukula sosai kada
kiyi amfani dah drugs bah tareda kinyi consulting doctor bah that's very bad U
know, kiyi avoiding kayan zak'i in excess kuma make sure ur bleeding is normal!
Tnx muhad'u @pg 26<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[29/07, 16:22] +234 703 125 8794: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳26⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 Mhiss B~hal Yes Myself I love Myself like sosai
d'innan🙈🙊<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Bayan Ummulkhair
tagama jin bayanin Midwife Nafeesah, godiya tayi matah har yanzu muryan natah
bawani fita yakeba mijin ki fah? Wajan aiki kawai tah iya cewa toh shikenan
u're stable Allah ya sauwake zandawo by 09:30pm tunda banida nisa sosai nazo
naduba ki, godiya Ummulkhair tayi matah hawaye nah zubar matah tanah tunanin
da'ace mijin tah yananan dashi zai matah komai, bak'in tah neh suka dinga matah
sannu duk atunanin su zafin ciwo neh, gida suka tsaftace matah tas suka yimata
sallama sabida duk dah auren su zani tasamu tad'an rufe jikin tah sannan Affan
yashigo, kwance yasame tah kamar yayi kuka duk jikin shi amace waje yasamu
yazauna kan kujera sannan yace, "sannu sis ya jikin naki? Alhamdulillah,
Affan zo katafi gida dare yayi kaga Mummyn mu hankalin tah zai tashi kuma Dan
Allah kada Kafad'a masu komai, Sis bangane kada nafad'a masu bah dah ban manta
dah keys d'inah bah fah? wazai san halin dakike ciki kokuma daba mukullin gate
d'inki nah mu sanya danawa bah daya kenan, haba sis wlh bakisan yanda hankali
nah yatashi bah idan mutum yayi loosing alot of blood mutuwa neh fah saidai
kawai Allah ya tsare, naji lilbro we would talk this ova next time pls zo kah
tafi, it's late already, yeah zantafi nah yarda amman saikin kira mijin ki
sabida gaskia barin ki keh kadai anan gida dah matsala tunda har yanzu mere
looking at U ma nasan U're still sick and weak so ki kira yayanmu idan yazo
saina tafi kawai, kaje I promise U yakusan zuwa ai midwife takira shi yananan
tafe, dak'yar Ummulkhair tasamu Affan ya yarda yaje gida kuma tasa yayi mata
alk'awarin bazai fad'awa iyayen su bah, baya tafiyar sah takaici neh yarufe tah
asanadiyar rashin wadataccen lokacin dah bata samu daga mijin tah gashi har
bak'i neh en unguwa yau suka shiga matrimonial room d'inta harda wanka akayi
matah kuma wai mijin tah doctor neh babbah wannan wace irin rayuwa ce mesah
Abusaiyeed bazai tsaya ya saurare tabah sabida aikin sah, ita batada gatan
lokacin sah saidai jama'a, kuka tafashe dashi sosai anan baccin wahala yayi
awon gaba dah itah, sai chan wajajan 10 tafarka jin ana buga k'ofa yanzu tad'an
ji dama2 saikuma zazzabi dake k'ok'arin rufe tah tasan bakowa baneh a doorstep
illa Midwife<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>saidai batajin zatah iya
tashi, ahankali taduba wayan tah taga har izuwa lokacin babu kiran Saiyadee
cikin bak'in ciki tah tura masa msg kamar haka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Eh tabbas aikin kah
yanada muhimmancin gaske wanda koh ni banida shi, kazo ka dauki gawata kah
binne! Abusaiyeed ina makah fatan Alkhairi! haba Khairiya er arzik'i, bayan tah
tura tah kwanta tanajin zuciyar tah kamar zatah buga har yanzu tanaji ana buga
k'ofa har aka daina bata iya tashi bah wani baccin neh yakuma d'auke tah, ya
Saiyadee yanacan yanata faman aiki yaji shigowar msg amman koh kad'an bai damu
yaduba bah sai chan bayan ya amsa wani important call yaga hanging message daga
Ummulkhair hakan yasa yabud'e ya karanta, gumi neh yafara keto masa time yaduba
yaga 11 har tayi babu abinda yasake yi yad'auko carkeys nashi yayi waje shidai
kawai driving yake yanah farautar gidan sah besan abinda yake bah Allah neh
kadai yakai shi gida awaje yayi parking yabud'e gidan yashige direct yayi
d'akin tah, ahankali yabud'e k'ofa yahango tah abin tausayi kwance akan gado
k'arasawa yayi yad'an ta'ba goshin tah yaji zafi kallon tah yake dah drip dake
gefenta kunya yaji sanin sarai wani doctor d'in aka samo yayi treating d'inta,
ranshi neh yayi bak'i yana tunanin Allah yasah bah namiji baneh yata'ba masah
hannun matah wajan saka drip, towel yasamu yasamu d'an k'arrami yasa aruwa
yanah saka mata agoshi in other to relief her from slight fever'n daya kamata,
cikin bacci taji hakan k'amshin turaren sah neh yasah tasan shine bakowa bah,
k'in bud'e idon tah tayi kallon tah yake, k'arshe tagaji tabud'e ido amman tah
kauda kai,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">"Wifey", yace muryan sa chan k'asan mak'oshi, m so
sorry, d'an Allah ki kula ni karna mutu, Ummulkhair babu abinda tace sai wasu
hot tears dasuka fara forming a idonta rapidly!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[31/07, 22:55] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳27⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 Maman Hanan deary Allahu yabar kauna tnx for
being in support deary, Allah yaraya manah Baby Hanan musha biki😻😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Kwanciya yayi
tah abayan tah ya rungume tah kanshi ya zura tah wuyan tah ya k'ank'ame tah
bece komai bah sai shak'ar k'amshin tah dayake yi kuka take sosai, har cikin
ranshi yaji abin na sukan sah sabida kukan datake, "Ummunah pls"
yace, muryan shi chan k'asan mak'oshi, ture shi take dah sauran k'arfin tah
amman ina takasa drip d'in taduba taga ai yama k'are hakan yasa tah cire shi
ahannu tah dan tasamu daman ture shi dakyau, kallon tah yake dah idanun sa dah
sukayi jaa sosai, Ummunah yace kafin ya manna tah ak'irjin sah dah k'arfi duk
k'ok'arin tah takasa tashi tureshi take amman ina k'arfin tah bekai bah,
rapping d'inta yayi dah hannun shi hiding her in his chest kamar baby, fuskan
tah ya d'ago yanah kalo sam tah kauda kai tak'i bari su had'a ido, manna tah
yakuma yi ak'irjin sah kamar baby kafin yace, "Ummunah meya sameki kikamin
irin wannan mumunar text d'in haka, kinsan bansan yanda nazo gida bah daa kin
bari abu yasame ni fah, kinsan yanda kika d'aga min hankali kuwa har yanzu
nakasa nutsuwa, waye yayi treating d'inki namiji neh? shuru batace komai bah
d'ago tah yayi daga k'irjin sah yarik'e kafad'an tah yace, namiji neh yata'ba
minke? shine yata'ba min hannun ki wajan saka drip? Kallon shi tayi angrily
tace aiba drip kad'ai bah harda allura ma yayi min a inda kakemin kaima,
hannayen shi dake kan Kafad'ar sah taji suna wani rawa jijiyoyin kanshi duk sun
mik'e meh kika ce Ummunah yafad'a muryan shi bata fita, maimaita masah tah soma
yi kafin tah k'arasa ya manne tah ajikin shi yace, " Ummunah karki k'arasa
min idan bakyasan zuciya tah tafashe, hawaye taji yayi dropping abayan tah
tasan bah makawa hawayen saneh batasan sanda tah rungume shi bah, wani kishi
yakeji kamar yamutu zuciyar sah tayi bak'i, Ummunah yanzu kin kyauta min kenan
kinmin adalci?, haba Ummunah babu mata dazasu iya miki allura sai namiji, kaima
kah kyauta tafad'a tanah bugun bayan sah nifah Abusaiyeed? idan namutu fah
kasan halin danah shiga neh toh indan namijin nefah yake nan yabarni nah mutu,
matan mutane nawa keke yiwa allura Abusaiyeed kai barinsu kake su mutu baka
basu taimakon gaggawa, shikenan kanka kakeso kishi nah kake kawai lafiya tah
fah? nidai banasan gidan kah mutuwa zanyi abanza tanah kaiwa nan tah tashi
zatah fita tabar masa d'akin jawota yayi tafad'a kan gado bakin tah yakama
yanah sha azazzauce batada k'arfin hanasa shiyasa tayi still zanin jikinta ya
kunce yayi wurgi dashi yafara shafan tah tun daga K'asa har sama numfashi kawai
yake saukewa gabad'aya yahana tah sakewa kuka tafara masah sabida yanda takejin
jikin tah duk babu k'arfi, hankalin shi yad'an tattaro sannan yace,
"Ummunah kukan meh kikeyi bafa zan barki bah", nika tashi Abusaiyeed
banjin dad'i, bakin tah yakuma kama wa yana sha kamar wanda ya shekara baici
abinci bah, hannu ya zira tah k'ark'ashin rigar tah yanah shafa cibiyan tah,
hannun shi tah rik'e tanah girgiza masa kai sabida yak'i sakin bakin natah,
kwanciya yayi yad'ago tah yadawo dah itah saman shi kallan cikin idonta yake
ita kuma tarufe natah, Ummunah bazaki yafe min bah koh? Dan Allah kiyafe ni,
wlh yau neh aiki yamin yauwa kuma wlh bansan bakya jin dad'i bah, Ummunah kaf
duniya fah kema kinsan babu abinda nake kauna kamar ke, kiyi hak'uri abisa
rashin sani hakan tafaru kinji Dan Allah Ummunah kiyafe ni Dan Allah bakin su
ya kuma had'ewa yanah hawaye itama tanayi saidah yayi kissing d'inta sosai yasaki
bakin natah ahankali yace Ummunah jikin ki akwai zafi sosai, menene koh har
yanzu zazza'bin neh, kallon shi take wani sabon kaunar shi yanah d'auwainiyya
dah itah, kaci abinci Abusaiyeed?, A'a banci bah nayi breakfast dai @ office
karki damu banajin yunwa, kefa kinci? eh banah kira kah bah sanda nakeci mah
katuna, kai Ummunah kina nufin tun abincin dake cikin ki kenan? Haba Ummunah
baki kyauta bah tun safe Ummunah, d'aga ni toh naje nasamo miki abinda zaki ci!
Next Episode @ Pg.28 Happy Reading 2u all Fans<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[31/07, 22:55] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳28⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS.*<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>_PML_ ]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">{ *We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖*}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 Maman Mannal deary Nagode dah kauna fah,
nagaishe ki kyauta babu kud'i Allah yaraya Mannal yakuma raba lafiya sannu dah
k'ok'ari dear nah😻💋👄😍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mik'e wa
yakesan yi amman tah danne sah tafara kissing d'inshi with all that she's got,
mamaki neh yacika shi sabida batajin dad'i kuma yayi matah laifi babbah tabbas
Ummulkhair bamai rik'o bace, Masha Allah haka akesan MUTUM musanman mah MACE,
rik'e tah yayi sosai giving her more access harshen sah tah lalubo tanah
suckling on to, babu abinda yake yawo azuciyoyin su sai so dah kauna junan su
ji yake kamar ya dauke tah ya maida tah cikin zuciyar sah itah kuma ji take
kamar tah maida shi cikin cikin tah, ahankali yaraba bakin su, kallan shi tayi
takuma had'e bakin nasu tah nasha kamar bazata sake bah chakulkuli yamata hakan
yasah tasake shi tanah dariya sosai, Ummunah bakya son kici abinci koh shiyasa
kike tah shan baki nah sabida kada natashi koh? Uhm ai yafi dad'i zan k'oshi
dashi, kumatun tah yaja yayi kissing d'inta akan hanci, yace baran naje koh
Ummunah cikin nawa yayi flat dah yauwa babu abinci aciki yafad'a yanah shafa
cikin tah, cikin mota yaje yaga shawarma dah kilishi wanda ya kar'ba a eatery
tun bayan sallan Isha daukowa yayi ya shigar masu dashi ya nufi d'akin tah,
yanah zuwa ya tarar dah itah atsaye ajikin window tanah duban stars tah baya ya
rungume tah yace "Ummunah cikin nawa babu komai acikin tah kizo kisaka
mashi abinci Dan Allah, kinga har shabiyu yakusa fah", goga kanshi yake
tayi awuyan tah yana lasan wuyan tah yanah shak'ar k'amshin jikin tah, dariya
tayi tace, "meh kake min Abusaiyeed", so dah kauna ya amsa atak'aice,
shafar kan shi take yi kafin tah juyo tashige k'irjin shi k'amshi take shak'a
tace, "Abusaiyeed?, yace "Na'am wifey" yau bana san k'amshin
jikin kah yana min irin nah Asibiti toh shikenan Ummunah zanyi wanka nah chanza
kaya nasaka turaren dakike so kinji, uhm naji Abusaiyeed kayi hak'uri sabida
period d'inah neh idan inayi bakomai nakeso bah, bakomai sweetheart yauban saka
lab wears d'inah baneh shiyasa I perfectly understand ur condition kinji
Mylove, batace komai bah sai bakin shi dah tafara sha kuma, gate sukaji ana
knocking shine tah saki bakin shi, Ummunah keda bakin nandai yau sai Allah,
naje naduba gate koh, A'a tace tareda girgiza kai tace idan 'barayi nefah
Abusaiyeed kaga fah dare yayi shabiyu yakusa tafad'a ido rau~rau cike dah tsoro
kamar tayi kuka, dariya yayi yajata jikin sah yace "bah 'barayi baneh
Ummunah sarkin tsoro kin manta profession d'inah neh?, ur hubby is a doctor
maybe wasu neh suke buk'atar help amman zan basu hak'uri nace suje nearby
clinic cause my oxygen is also sick 2day kumatun tah yaja yace, "baby
lemme check we're keeping them waiting", uhm kawai tace still very scared,
yafice yanah zuwa yabud'e yaga dah alamun mata dah miji neh agate matar ce tace
sannu Sir. yayinda mijin tah ya mik'awa Abusaiyeed hannu sukayi musabaha, how
may I help pls? ya tambaye su with the best niceness in him, actually matata is
a Midwife so d'azu matar gidan nan batada lafiya tazo duba tah tayi treating
d'inta shine tace, zata dawo toh unfortunately sanda tadawo tah duba tah bata
samu shiga bah sabida tayi knocking shuru shine takoma gida yanzu muke kwance
and I was asking ya jikin patient d'inta and she was like aina buga k'ofa ba'a
bud'e minba so I came back, shine nace mata sam bah ayin haka tah tashi muje
nah rakata muji koh lafiya tunda condition dah tasamu lady d'in d'azu was very
bad, hannu Saiyadee yakuma mik'a masa cikin tsananin farin ciki suka k'ara
gaisawa, pls ku shigo binshi sukayi abaya yayi leading d'insu to main parlour
sannan yace bara nakira tah, yanah shiga ciki yatarar Ummulkhair tah shiga
wanka komawa yayi yabasu ruwa dah Lemu sannan suka kuma gaisawa kafin yace bara
naduba tah, yanah shiga yatarar dah itah tafito tanah goge jikin tah rungume
tah yayi murna fal yakashe shi namiji beh ta'ba masa jikin matar sah bah! Hmmm
Nawa ooo Abusaiyeed sarkin kishi Abeg Mu had'u Next @ page 29 fans😂<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[01/08, 19:47] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳29⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 all 💋#Team# 💋 Ummulkhair😻
Allah yasah kuyi koyi dah halayyar tah nagari, wlh Inayin ku MASOYA wannan
Littafi🙋🏻🙋🏻🙋🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Lower lips d'inta
yayi sucking kamar nah 5secs<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>kafin ya
shafa fuskan tah yayi murmushi, itama murmushin tayi tace,"baby who's at
the gate?", bak'i mukayi baby, at this hour tayi lamenting eyes widely,
yeah C'mon let's go, jallabiyan tah ya d'auko mara nauyi yazura matah sannan
yacire towel d'in tah k'ark'ashi, hijjab yasa matah yace muje Ummunah, dariya
tayi takai masa bugu kafin tace, my tampons kamanta am on my period, ohhc
whatha f*ck totally forgotten sorry baby yace, kafin yafara fixting matah pad a
pant bayan yagama yazo zai saka matah rik'e shi tayi tace, "Abusaiyeed I
can do it pls", kallo d'aya yayi matah ya girgiza matah kai sannan ya saka
matah, kissing d'inta yak'ara yi sannan ya d'auke tah chak har saida sukaje
doorstep d'in main parlour tace alallai saiya ajiye tah tah k'arasa dakan tah
dakyar ya yarda ya ajiye tah, sannan suka shiga ciki dah sallama, murna sosai
tayi daganin Midwife, duk'ufawa tayi kad'an tah gaida mijin sannan taje tazauna
gefen Midwife tace, "Anty ina yini barkan ku dah zuwa ashe kune
agate" tafad'a tanah murmushi, ah Masha Allah sister jiki yayi sauk'i
Alhamdulillah, ai d'azun nazo around 10pm nabuga nagaji nakoma, kunya neh
yarufe tah kafin tace, "m so sorry anty wlh banda strength d'in tashi neh
alokacin, bakomai m so glad to see U like this, gaisawa suka kuma yi dah mijin
midwife d'in yayi matah ya jiki, sannan Midwife tah shiga yiwa Abusaiyeed
bayanin abinda yasami Ummulkhair dah irin mumunar halin data same tah aciki
inda tah k'ara dacewa it's very dangerous kamata asamu mai zama dah itah sabida
rana irin tah yau, Dr.Saiyadee babu abinda yakeyi sai gumi, he Neva thought the
situation was as bad as the midwife's explanations, jiki asanyaye ya amsa
dacewar Insha Allah za asamu nima dan yanayin aiki nah neh, Allah dai ya
kaddara amman it's been a day yanzu dah tafara mensis and tayi treatment mah I
dnt kno what actually happened, sir sorry to ask amman wani aiki kakeyi haka
sabida matar kah tunda tah farfad'o sunan kah take tah ambata kuma we were
unable to reach U, kai yafara sosawa kunya duk takama shi yarasa yanda zaice
shi likita neh, Ummulkhair takula dah hakan tace Anty d'an kasuwa neh baya wuce
magrib yake dawowa akwai abinda yake rik'e sa neh kwana biyu shiyasa baya
shigowa dawuri, toh shikenan Allahu yak'ara bud'i bara muzamu koma daman
maigida nah neh yace sai munzo mun duba ki, godiya ango dah Amarya sukayi sosai
sukayi exchanging digits dah mijin midwif d'in, kafin Abusaiyeed yaje yarufe
masu k'ofa, ciki yadawo asanyaye kafin nan Ummulkhair takoma d'aki tanah gyara
gashin tah, d'akin shi yawuce yaje yayi wanka goge jikin shi yayi yasaka turare
yadawo dah shorts nd singlet, yanah shiga yatarar dah itah gaban mirror har
tagama drying gashin tah dah hand dryer mai tagama applying about to park her
hair, ribbons d'in ya kar'ba yayi mata parking d'in, "kinyi kyau sosai
Ummunah" yace har yanzu feeling very bad akan abinda yafaru yaji tausayin
tah sosai, k'amshin turaren sah taji tah tashi dah sauri tashige jikin sah
tanah shinshina sah, My Abusaiyeed mai k'amshi wlh ina kaunar kah my hubby!
Ribbons d'in kanta yacire yanah shafa gashin tah wani k'amshi mai dadi neh
katashi kissing d'inta yayi akai yace, "Ummu?" Na'am, I love U, me
too hubby, d'azu mesah kika kareni agaban midwife Nafeesah, kai Abusaiyeed toh
ni idan kace kai doctor neh zatayi mamaki kuma zatayi makah fad'a nikuma banaso
tayi wa miji nah fad'a shiyasa, Ummunah yace, tareda d'ago fuskan tah kallon
cikin idon tah yake, kafin yace Ummunah yau nayi laifi babbah gani nake naci
AMANAR su daddy, halin dakika shiga yau mai wahala neh Allah yasah Affan yayi
mantuwa daya zanyi dah rayuwa tah Ummunah nayi babban laifi wallahi Dan Allah
ki duke ni, hannun tah yadauka yanata bugun kanshi ak'irji dah k'arfi,
"stop this Abusaiyeed tafad'a tanah kwace hannun tah, Ummunah yau danah
rasa ki fah saina fi kowa shan wahala a duniya wlh ina sonki bazan iya rayuwa
babu ke bah yafad'a hawaye nah gangaro masa, saurin manne tah ak'irjin shi yayi
ya k'ank'ame tah sosai yanah fad'in am so sorry am so sorry wifey kinji! See
love 🙆🏾Next @Pg.30<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[01/08, 19:47] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳30⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 To all #Team# Abusaiyeed😻 yasin kudaina
zagin shi koh natafi yajin aiki 🙉🙊🙈, Inayin ku dukkah🙋🏻!
ANATARE🤝<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ummunah Dan
Allah kiyafe min, k'ank'ame shi tayi tace kabari pls cikin muryan kuka, jitayi
jikin shi nah rawa sosai hakan yasah taja shi zuwa bakin gado suka zauna, fuskan
shi tarik'e dah hannun tah dukkah biyu, matsawa tayi tah lashe hawayen sah
sannan tayi kissing d'inshi a ido, pls kadena komai yawuce Allah ya kiyaye
gaba, jikin shi tashige tah rungume shi, ni sai kince kin yafe min Ummunah
yafad'a hankalin shi atashe, d'agowa tayi tace babu abinda kamin Abusaiyeed
yawuce, Ummunah namiki laifi sanda nadawo fushi kike dani, kanshi tah kwantar
akan k'irjin tah, tace, "toh ai lokacin kenan yanzu nadaina fushin dakai
ai, no Ummunah yafad'a yanah girgiza kai, idanun shi duk sun kuma ciko wa
kinsan fah duk wanda yaci amana amana saita ci shi Dan Allah kiyafe min, shhh
sweetheart wai mekake cewa neh, pls stop this babu abinda kamin baka ta'ba cin
AMANAR kowa bah kuma bazaka ta'ba ci bah Insha Allah, toh ni kice kin yafe min
kawai, Abusaiyeed Darling na yafe kah duniya dah lahira, nagode Ummunah Allah
yayi miki Albarka yasaka miki dah alkhairin duniya dah lahira yace, Ameen
tareda kaima tace cike dah farin cikin Addu'an daya matah, Ummunah wlh nayi
sa'an mata duk abinda yafaru kin yafe min har kareni kike nibansan dah bakin
dazan miki godiya bah inda Aljannar ki tanah wajena toh nah mallaka miki shi
har abada, Ummunah samun mace kamar ki akwai wahala ina sonki I love U MyNoor
nagode miki sosai dah kike rik'e sirrin gidan ki danah Mijin ki, kuma nima
Insha Allah I promise to adjust koda little neh, kallon juna suke tayi har
alokacin kanshi akan k'irjin tah yake hakan yasa yaji he's getting aroused,
tashi yayi ya jawo tah jikin shi lips d'inshi take kallo eagerly tafara sucking
d'insu kamar feeder shikuma yashiga shafa tah ahankali yasake tah yace,
"Ummunah kaina yanamin ciwo" OMG sannu kaji Sweetheart tace, za kasha
magani koh, uhm sai anjima, idan munci abinci, A'a bara muci yanzu kasha
maganin kah, shawarman tah dauko idan tayi biting tah bashi yayi shima ahaka
suka cinye suka kora dah fresh milk, kafin takuma shigewa jikin shi, Abusaiyeed
d'auko maganin kasha, uhm zansha sai anjima chab wlh bah zakamin wayo bah idan
nice kah iya zagewa kabani magani nasha harda allura daman kaci sa'a ban iya
allura bah shine bakaso toh Allah saika sha koh nakira Umman mu nace kak'i shan
magani, dariya yayi yace rigima kenan toh angaya miki kowa kene Ummunah, aini
banah tsoron magani zansha wlh, toh tashi kasha kaga jikin kah yafara yin zafi
Allah, jawota yayi jikin sah yace Ummunah aikece maganin nawa kawai ki kasance
tareda ni kissing d'inta yafara yi again yanah shafa jikin tah bayan tah yake
shafa yaji babu alamun bra ajikin tah sosai yaji yanasan wasa dah itah ahankali
yake zagayo dah hannun sah har yazo k'asan cikin tah yanah shafar tah kwantar
dah itah yayi sannan yamata rumfa, rigar tah yake d'agawa sama idanun shi duk
sun canza shafar tah yake sosai harya sauke hannun sah akan k'irjin tah,
Ummulkhair wani irin tsoro taji wannan neh karo nah farko daa hakan tah ta'ba
faruwa a rayuwar tah, taushin k'irjin tah bak'aramin rikita sah yayi bah, kamar
yayi matah kuka haka yakoma, yanda yaji jikin tah narawa neh yasa yacire hannun
sah daga k'irji tah bah tareda yamata komai bah yafara lasan wuyan tah,
Abusaiyeed sunan shi take kira ahankali amman koh kad'an baya sauraron tah
d'agowa yayi idanun shi jajir yace Ummunah I want SEX pls, tashi tayi saurin yi
tace, period d'in fah it's Haram U can't have me, sai a lokacin ya tuna batada
tsarki, sosai taji tausayin sah tah kwantar dashi akan k'irjin tah tanah shafa
masa baya, m sorry kaji, bece komai bah sai rungume tah dah yayi, jijiyon
kanshi taga duk sun mik'e hankali atashe tah d'ago shi tace, "koh ciwon
kan neh haka Abusaiyeed, dariya yayi yace, "U mean the veins", yes
sweetheart tafad'a idanun tah duk sun ciko,<span style="mso-spacerun: yes;">
</span>no it's nothing baby C'mon bakomai kinji karki damu kanki, toh mesah
jijiyoyin kah suka tashi haka, It's desire sweetheart all I need now is U and I
can't have U, so karki damu zasu kwanta nanda jimawa k'adan, kunya taji tah
sauke kanta k'asa jawota yayi jikin sah suka kwanta bacci suna kissing juna as
usual! Next @Pg.31 Mayun Kiss kawai😏<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[03/08, 19:39] hassan: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳31⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 To Maman Hanan deary tnx 4 the Airtime I really
appreciate it so much, And Please Get well soon sweetheart😪😓 🤝ANATARE
🤝<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Tun cikin dare
Ummulkhair taji jikin Saiyadee yad'au zafi sosai, tasan tabbas zazzab'i neh mai
k'arfi ajikin sah, kuka tah fara yi sosai, wani b'angaren kuma dad'i taji
sabida tayi tunanin idan baida lafiya toh babu inda zashi, kukantah yaji yanah
fita ahankali dukda cewar bah yajin k'arfin jikin sah koh kad'an yaja tah jikin
sah, "Shhh Ummunah please not now kinji",baby U're sick I can't bear
it mumbled Ummulkhair, sweetheart barmin kukan nan haka please am fine I can
manage dah asuba zansa drip kuma zansha drugs kinji, bata daina bah haka tah
dinga kallon shi har asuba yayi, bayan tah taimaka mashi yayi sallah yazauna
daga bakin gado yasawa kanshi drip d'in yana zaune tah rik'e hannu shi sai
sannu take mashi akai akai, murmushi yayi yace Ummunah kenan sarkin tsoro, taho
toh yace yanah bud'e mata hannun sah d'aya, kai tah girgiza masa alamun a'a
cikin kuka tace, Abusaiyeed u must persevere! dry those eyes of urs
Ummunah,without uttering a word she turned to take her exit leading herself to
the parlour, coffee tah had'o masa tadawo d'aki jikin gado tasame shi ya
jingine, ahankali tah kwantar dah kanshi akan kirjin tah tanah masa sannu
sannan takai masa cup d'in baki ahankali yake sipping harya shanye, tnx Ummunah
I love U kinji, uhm me too, tace sannan tazauna gefen shi ahaka har drip d'in
yak'are kafin nan yaji dad'in jikin shi sosai yanajin k'arfin jiki bah kamar
daa bah, Ummunah bara nah shirya gurin aiki koh, d'ago kai tayi cike dah mamaki
tah kalle shi, Abusaiyeed gurin aiki kace fah tafad'a with shock shining all
over her cute face, uhm Ummunah koh karna fita, bakada lafiya fah, jikin sah
yajata yace, "naji sauk'i ai Ummunah, bara naje koh", Abusaiyeed pls
Kafad'a min yanayin aikin kah sabida ni U're too busy working 24\7 always kaga
amatsayi nah nah matar kah ya kamata nasan yanda aikin kah ke tafiya, kissing
d'inta yayi yace, kinga idan naje AKTH tun safe normal days ina tashi by
04:30pm sai nawuce International clinic anan nake kaiwa 11to12am nadare, kin
gamsu yanzu Ummunah yafad'a yanah shafar kanta, a'a idan kuma kanah call fah,
ai zakah iya barin Asibiti kadawo gida, eh Ummunah idan am On Call
International nake zuwa dana d'an samu tazara, batace komai bah amman taji
zafin hakan sosai, calmly tace, "Abusaiyeed why not idan kana call and
U're free kadinga dawowa gida Instead, tunda daga nan zuwa AKTH babu nisa sosai
kaga zakah dinga hutawa kuma zakah dinga cin abinci kai bakah gajiya dazuwa
eatery neh?", Ummunah I had love that also but that's a difficult nd cruel
decision u know, aikin fah ya zanyi dashi Dr.Path there at International bazai
yarda bah, pls try to Understand kinji wifey wata rana sai labari, that's it
Abusaiyeed u keep saying this repeatedly even b4 we got wedded, amman wata rana
yak'i zuwa labarin yak'i zuwa nifa baka tausayi nah kullum ina cikin missing
d'inka and time dah kake dawowa gida is not accurate I can't even get enough of
my husband, please reconsider I beg of U tafad'a cikin kuka sosai, bece komai
bah sai manne tah daya kumayi ajikin sah kamar zai maida tah cikin sah, bayan
wani d'an lokaci yace, tashi Ummunah kada nah makara zan shirya, one more look
takai masa sannan tace, "tunda lafiyar kah bata dame kah bah aikuwa babu
abinda zai dame kah, amman kasani lafiya garkuwar jiki kuma saida itah akan
iyayin komai, Good luck adawo lafiya, tanah kaiwa nan tafice daga d'akin
banging the door very hard, d'ayan d'akin tawuce tafashe dah kuka cike dah
bak'in ciki dah takaici, tanaji yagama shiryawa yazo yanah kiran tah, Ummunah
please open up I beg of U kinji pls wifey, babu abinda tace yanajin kukan tah
kamar ana tafasa masa zuciya dakyar yabar cikin gidan bayan kusan 30minutes
shima sabida he's on call neh, Ummunah nabar miki note pls read it at least
kinji, bye natafi ki kula dah kanki and please eat well kinji, Ummulkhair
jitake kamar tafito amman tah basar dashi she wanted a hug badly haka tah
hakura tanaji yabar cikin gidan, har ya k'arasa wajan aiki tunanin tah yake
kawai, dakyar ya iya saita kanshi sabida yasamu damar concentrating, bayan isar
sah yakira layin tah yafi sau goma amman sam no answer hankalin shi bah
k'arramin tashi yayi bah message yamata kamar haka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ummunah kina lafiya
pls Dan Allah pick my call, am scared are U really OK, what's wrong why ain't U
picking my calls, am stuck I can't come back home at this very moment, Dan
Allah kiyi replying d'inah Sweetheart nayi laifi m on my knees tuba nake
please, kidauka ko zan samu nutsuwa!<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[03/08, 19:39] hassan: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳32⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 My Fatima Usman Dikko, tnx for the Airtime also
gaskia ina miki godiya dah kaunar dah kike nuna min, it's obvious Fans d'inah
suna ji dani recharging my account with Airtime!, Awwn U guys really made me
loaded, Wlh Am So glad Guys I really Appreciate ur love&care😅,
Happy Mhiss~B tanah gaisuwa dah Babban Murya🙋🏻😅 ANATARE
🤝<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ummulkhair kuwa
anan inda tayi kuka tah k'oshi bacci yayi awon gaba dah itah tanah farkawa
tashiga wanka tadawo tah tsaftace gidan tah gaba d'aya, d'akin tah takoma nanma
tah gyara bayan tagama tah dauki wayan tah nan taga Missed calls dah yawa ciki
harda nah Mummy yatsine fuska tayi tah kalli numban Abusaiyeed tace, "koh
nakira kah basa mun kah zanyi bah aiki kakeyi, cike dah murna tayi dailing
numban Mummyn tah, sallama Mummy tayi tah amsa tareda gaishe dah itah, khairat
kinanan klau koh, eh Mummy nah lafiya nah klau kefa, Nima Inanan klau Abbanki
yanah kula dani sosai, dariya tayi tace, " toh Mummyn mu nagode wa Daddy
sosai", haka suka gaisa suka d'an ta'ba hira inda Mummy take dad'a yimata
fad'a musamman akan hak'uri dah juriya dah zaman duniya, sosai taji dad'i
sannan tagode wa Mummy sosai bayan sunyi sallama neh taji bazata iya hak'ura
dah kiran Saiyadee bah hakan yasa tayi deciding tah kira shi saida tabud'e
hanging message d'inshi sannan tayi dailing numban shi cike dajin tausayin sah
dan tasan hankalin shi yatashi sosai, yau bai b'ata lokaci bah yayi picking,
Haba Ummunah yanzu fushi kikeyi dani, duk kinbi kin d'aga min hankali kinsa
narasa nutsuwa laifin meh nayi haka, ina kike nake tah kiran wayan ki, ni toh
ya jikin kah, kaji sauk'i kadaina jin jiri?, uhm naji sauk'i wifey kin daina
fushi dani koh? pls kidena kinji, kyaleni toh ni ina ruwanka dani, Ummunah dah
ruwa nah dake kuma yanah fridge yayi sanyi harda k'ank'ara, dariya tayi tace, "nidai
Dan Allah kasamu sauk'i nadamu dakai, eh Ummunah nasamu sauk'i saidai hankali
nah yakasa kwanciya tunda kina fushi dani, toh nah daina kayi hak'uri kayafe
min dasafe nayi makah rashin kunya kuma sanda ka kira ni wayan yanah d'aki
nikuma sai yanzu nadawo d'akin, Ummunah bakimin komai bah kuma koma kinmin nah
yafeki duniya dah lahira, nagode Abubaby nah, laa kai kai Ummunah mekika ce
yace cikin dariya sosai, eh manah babynah neh kai Abusaiyeed, toh nagode idan
nadawo ki ajiye min abincin dah ake bawa babies kinji, kunya neh yarufe tah
sosai dan tsaf tasan abinda yake nufi hakan yasa muryan tah chan k'asa tace,
"ni yunwa nakeji banci abinci bah natafi ci", dariya yayi yace, toh
kici naki yanzu idan nadawo kinbani nawa, ci sai muyi wayan koh, magana taji ya
nayi dawani kafin yace, "Ummunah sai anjiman mayi waya aiki nakeyi
pls" d'ip taji wayan tah yanke, haka jikin tah duk babu kwari tah tashi
tasoya plantain dah kwai taci! Bayan tagama tazo takira layin shi bai d'auka
bah bata hak'ura bah tah dinga kira har saida yaturo matah dah message cewa
he's busy anjima zasuyi magana wayar dabasu yiba kenan sai chan wajajan 11pm
yayi matah text akan tah soya masa plantain dah egg kasan cewar that's his
favorite, tashi tayi tah soya masa sannan tah ajiye bayan yadawo yau part
d'inshi yawuce bayan yayi wanka yasaka pyjamas d'inshi yakira tah awaya yace
takawo masa abincin, tanah kaiwa tahau gado tah haye bayan sah tace,
"Sannu dah zuwa Abusaiyeed, ya aiki, sarkin aiki tah rad'a masa akunne,
dariya yayi yace, " Alhamdulillah Ummunah yunwa nakeji sosai wlh",
sorry tace tanah ta'ba wuyan shi, murmushi yayi yace, "ai naji
sauk'i" sannan yaja warmer'n gabanshi plate tah d'auko tajuye dukka aciki,
what Ummunah yayi yauwa saidai muci tare, murmushi tayi kawai tafara bashi
abaki shima haka yadinga batah har suka cinye Fanta one of her favourite drink
take sha shikuma coke bayan sun gama yakunna musu kallo, tanah kwance ajikin
shi suna kallo, silk d'ankwalin tah yacire yanah shafar kanta, Ummunah kinyi
kyau, kaima haka Abusaiyeed bawani nan ni wani kyau nayi ai kinfi ni kyau, nifa
farar ki yace, yanah nuni dah tsala~tsalan cinyoyin tah dasuke awaje, dariya
tayi ya gyara matah kwanciya, Ummunah ina alqawarin, "wanne" tace
looking surprise, kin manta neh so soon, dasafe kince min baby kuma yanzu ni
bazan yarda bah saikin bani abincin babies, kai tayi saurin 'boye wa ak'irjin
sah sannan tabige shi tareda cewa banaso Abusaiyeed kadaina bah kaci abinci kah
k'oshi bah, injiwa yace miki ana k'oshi dah wannan ya rad'a matah akunne aishi
baby 24\7 yakesha, dariya tashiga yi tanah dad'a b'oye fuskanta d'ago tah yake
k'ok'arin yi amman sam tak'i bari su had'a fuska dashi, Dan Allah kibani wasa
zanyi kad'an kinji Ummunah, jikin tah tasake sani cewa hakk'in shine kuma yayi
matah k'ok'ari, ahankali yasoma kunce hook d'inta tah baya, jikin tah rawa yake
hakan yasa yace matah toh bazanyi komai dashi bah Ummunah kawai gani zanyi,
jitake kamar tah rik'e shi sai tah tuna dah nasihar dah aka mata agida, barin
shi tayi yacire bra d'in ya ajiye shi gefe kallon tah yake acikin ido kafin
yahad'e bakin su, ahankali yafara zura hannun shi cikin rigar tah tareda
k'ok'arin cire shi.... <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Matan Aure ina gaisuwa Ina yinku🙋🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">'Yan matah ni taku Ce ku nawa ne😻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[05/08, 16:19] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳33⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 All MATAN AURE gaskia kuna k'ok'ari Allah dai
yabada lada Allah ya raya yaran Albarkah masu nema Allah yabasu, Ina yinku
matan aure Allah yasaka dah gidan Aljanna Mhiss~B~hal tanah gaisuwa🙋🏻🙋🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ahankali yafara
zura hannu cikin rigar tah tareda k'ok'arin cire shi gaba d'aya, cikin tah ya
tsaya kallo, sannan ya kalle tah yaja kumatun tah yace, "Ummunah jubi
fatar ki fah yanda take shek'i kamar diamond I love ur black, Ummunah black is
beautiful, murmushi tayi batace komai bah, U're nervous Ummunah Dan Allah
kibari nayi wasa dasu banasan nah miki abinda bakya so neh kinji yafad'a yanah
shafar fuskan tah, kai tah kauda tace, " toh" muryan tah chan k'asa,
one more look yak'ara matah yayi proceeding d'in cire matah rigan gaba d'aya,
half dead yatsaya kallon tah gabad'aya yarasa sukuni yama rasa tah ina zai fara
ta'ba tah, rungume tah yayi ajikin shi dah k'arfi yanah shinshinar tah all
over, Abusaiyeed tace, cikin kukan shagwa'ba, koh kad'an bai nuna yaji abinda
tace bah, shafar naked back d'inta yake kawai bah control, Ummunah Inasan su
sosai inaso nata'ba su pls zanyi wasa ki barni kinji, hannun shi biyu yayi
placing akan k'irjin tah wanda yayi daidai dah shigowar kira awayar sah, wani
sanyi dah nutsuwa yasamu dah hannun shi suka ta'ba k'irjin tah, kallon juna
suke duk su biyun Ummulkhair tamanta dah yanayin dasuke hankalin tah yayi dubu
atashi kiran menene? badai fita zaiyi bah awannan tsohon daren shima kuma
Saiyadee tunanin dayake kenan, ahankali yasauke hannun sah dake kan k'irjin tah
ya d'auki phone d'inshi, kafin nan Ummulkhair tariga tasaka riga tah 'boye
k'irjin tah cike dah jin kunya tayi k'asa dah kanta, daukan call d'in yayi
yace, ganinan zuwa, sannan ya kashe, kallo tah yatsaya yi tashin hankali zallah
ya hango afuskar tah dan hawayen dah take k'ok'arin 'boyewa ma takasa, tashi
yayi yad'aga tah sama gabad'aya yanah rarrashin tah, Ummunah Dan Allah kiyi
hak'uri nafi kowa tak'aici dah tashin hankalin wannan kiran daya shigo min
awannan lokacin domin tah katse min jin dad'i dah kyautar Allah, nafad'a miki
when am on call u have to bear it Ummunah sabida koh cikin dare emergency
yataso dole nah naje, Dan Allah kiyafe min, kinji Ummunah, shure shi takeyi
amman ya rik'e tah gum, Ummunah yace yanah k'ok'arin had'e bakin su amman sam
tak'i ajiye kanta guri d'aya, sai kuka take kamar dad'a tunzura tah yake,
Ummunah pls manah kiyi hak'uri kinji, kuka take kamar batajin abinda yake cewa,
toh shikenan Ummunah nafasa zuwa tunda bakya so saina bari, sai asannan tad'an
nutsu, Ummunah bakya tausayin patient d'in? Kinsan halin dayake ciki neh?
Bakyaso nah taimaka mishi? Kinsan yanda yake Addu'a nazo aranshi? kinsan irin
abinda yakeji neh?<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Uhm Ummunah?
K'ank'ame shi tayi sosai dagajin yanayin rungumar dah tayi masah yasan batasan
abinda zai rabasu kona minti d'aya, toh kiyi hak'uri kinji Insha Allah yanzu
zandawo Ummunah, koh mu tafi tare neh, natafi dake Ummunah? ya tambaye tah
yanah kallon cikin idon tah, Uhm~Uhm niban zuwa Allah ya kiyaye hanya saika
dawo, adawo lafiya tafad'a sounding so sad, Ameen Ameen sweetheart Allah yayi
miki Albarka I love U to the core kinji, kira neh yadinga shigo masa ajere
hakan yasah tafara k'ok'arin kwatar kanta, ahankali ya kwantar dah itah sai
faman shure~shure take, bargo yaja ya rufe tah zuwa kirji, kissing d'inta yayi
a goshi tareda fad'in am so sorry kinji heartthrob "it's an emergency i
need to attend to till we meet again wifey, I miss U and pls barmin asaran
hawayen nan haka banaso gaskiya, ya k'arasa magana yanah shafar bayan tah kafin
ya saka jallabiyan sah ya fice cikin sauri! Kuka taci sosai harta godewa Allah
jitake kamar tah bishi dan gabad'aya sotake taji tah ajikin mijin tah amman
babu dama gashi batada yak'inin cewa zai dawo kafin Asuba sai sanda tagan shi
kawai Addu'ar tah shine Allah yakare shi aduk inda yake Abin godewa Allah anan
shine baya Neman mata koh kad'an kuma baya shaye~shaye koda kuwa taba neh! Next
@ Pg.34<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[05/08, 16:20] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳34⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 All 'YAN MATA, Ni taku Ce ku nawa Neh, Ina
Alfahari daku abi iyaye asamu dacewa agidan miji dah Albarka mai tarin yauwa
Allah yahad'a fuskokin mu agidan Aljanna Mhiss~B~hal tanah gaisuwa🙋🏻🙋🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Abusaiyeed
bayan yaje asibiti yadawo wajajan 3am nah dare dah sallama yashiga gidan part
d'inshi yawuce straight ad'aki akwance yasame tah daga itah sai pant tah kare
k'irjin tah dah rigar tah dah alamu anan bacci yadauke tah, kallon laptop yake
wanda suke kallo dashi kafin kira ya shigo masa ga popcorn d'insu ma agefe,
gabad'aya komai yanda yatafi yabari haka yadawo ya tarar, sosai yaji tausayin
Ummunsah wani sabon kaunar tah neh yake d'auwainiyya dashi, shafar bayan tah
yafara yi ahankali tuni tafarka azabure taja dah baya sabida tsoron dataji, ido
tah k'ura mishi dataga shine sannan tasauke kanta tace, "ashe kaine sannu
dah zuwa, kadawo lafiya kallon tah yake with total lust, uhm nine wifey fushi
kike dani koh? a'a nibah fushi nake bah, hannun shi yabud'e yace, "toh
taho", dasauri tafad'a jikin shi tanah mishi wani irin runguma nah
tsantsar so dah kauna I miss U tace ahankali, naga alama Ummunah, rigar datah
kare k'irjin tah dashi yake k'ok'arin cire wa takuma k'ank'ame shi d'ago kanta
yayi ya matah ido kanta takuma maida wa k'irjin shi dasauri, Ummunah karki
hanani I want to feel them bare ajiki nah, rigar yacire ya rungume tah gagam,
Ummunah akwai taushi yarad'a matah akunne gaskia jarirai suna manah wayo duk
dad'in nan sai abasu dukkah biyu iya san ransu, Ummunah pls ni kada kimin haka
kinji ki maida ni babyn ki kafin Allah yabamu kinji, wani kunyi takeji kamar
tah nutse batah ta'ba tunanin kalamai irin haka zasu fita daga bakin Saiyadee
bah sabida shurun sah dah nutsuwa ashe bah anan take bah domin duk wannan
kalaman nasa cike dah nutsuwa suke fita daga bakin sah, kwantar dah itah yayi
yasoma wasa dasu, gabad'aya ya sauya mata wayan shi dake gefe tah d'auka
ahankali tah kashe batare dah sanin sah bah badan komai bah sabida tasan yanah
bukatar abinda yakeyi, tuni ya sauya matah, wasanni yake dah abincin baby iya
san ransa sunan tah yake kira ajere kamar wanda zaiyi kuka tausayin shi neh
yakama tah kuka tafara yi masa tanah rik'e fuskan shi tanah fad'in menene
Abusaiyeed, kallon tah yake jijiyoyin sah duk sun mik'e, za kasha ruwa
Abusaiyeed? Nabaka ruwa kasha tah tambaye shi cike dajin tausayin sah hawaye
nah tsiyayar matah, yaushe zaki gama mensis d'inki Ummunah pls, nakusa tafad'a
tareda kwantar dashi akan k'irjin tah tanah shafa kanshi in a suitable manner,
juya musu kwanciyar yayi tadawo saman shi yanah shafar koh ina ajikin tah wani
tsantsar so yake nuna matah itah kuma luf tayi ajikin shi tanah mai tausaya wa
halin dayake ciki, Abusaiyeed am sorry tafad'a tears rolling down her cheeks,
k'ank'ame tah yakuma yi yace for what? bakimin komai bah, ahankali takai bakin
tah daidai wuyan shi tafara lasa tun daga saman kunne har k'asa, wani irin yanayi
yakuma tsintar kanshi aciki kira sunan tah yake akai akai, ahankali tajuya shi
tasa tip d'in harshen tah tah lasa tun daga bayan wuyan shi har zuwa tsakiyan
bayan shi, menene kuke kallo nah😳, idan kin iya shikenan idan baki iya
bah d'auki darasi awuce gurin, Madallah Ummulkhair! Numfashi Saiyadee yake
saukewa ahankali Ummunah pls kizo yace tareda juyowa, hannu yabud'e tafad'a
jikin sah, I love U tace, Ummunah I love U more, sonake najiki ajiki nah daman
Allah yayi miki Albarka Allah yabar minke, nagode dah kaunar dah kike nunamin
Ummunah ina Alfahari dake kece farin ciki nah MyNoor, cikin tah ya shafa yace,
"Allah ya Albarkaci rayuwar duk abinda zan shuka cikin cikin ki, Ummunah
U're 1 in a million, Ina sonki Ina kaunar ki, Kin shayar dani kad'an daga cikin
zumar soyayya, Allah yasaka miki dah gidan Aljanna, <o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Matan aure😅 ya aiki dafatan komai yanah tafiya
daidai koh, Allah yabada zaman lafiya Ina gaisuwa🙋🏻 Next@35<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[06/08, 22:51] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳35⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 All Groupies of Matar Dr Saiyadee Novel Allah
yabar ❤kauna yasaka muku dah gidan Aljanna Ngd Mhiss~B~hal tanah gaisuwa🙋🏻🙋🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Ameen Abusaiyeed
tace tanah shak'ar k'amshin turaren sah, nagode sosai dah yanda kake yimin
Addu'oi kamai Allah yatabbatar dasu akan kah, kallon cikin idan juna suke cike
dah zallan so ahankali ya lalabo lips d'inta yayi owning d'insu har bacci yayi
awon gaba dasu dukkah, wajajan Asuba ya farka amman bai tashi bah sabida yanda
yaga tabah baccin tah peacefully akan k'irjin shi yadad'e yanah kallon tah kaunar
tah yanah ratsa mishi kwakwalluwa kafin yasoma raba tah dah jikin shi ahankali
bai gama janye tabah tafarka kuma k'ank'ame shi tayi cikin bacci tace Ina
zakaje kuma MySaiyeed, idan tah yasa hannun sah biyu ya bud'e ahankali yace
bud'e idon toh kiga inda zanje, bugu takai mishi cikin bacci dah kukan
shagwa'ba tace, "ni kah bari zakasa bacci nah ya gudu", dariya yayi
yace, " toh ki kamo shi kada kibari yagudu", murmushi tayi tah dad'a
k'ank'ame shi tareda gyara kwanciya, saitin kunnen tah yarad'a Ummunah it's
time for Subh fah, nifa bance miki ina mensturation bah dan haka free me let me
prostrate to Allah accurately, sakin shi tayi tayi rolling two foots away from
him sannan tayi murmushi tace Allah ya shirye kah, yi sallahn pls k'irjin kah
yafi dad'in pillow fah, murmushi yayi yasauka yawuce toilet brush yayi tukunnan
sai wanka kashi biyu sannan yafito dah alwalan sah yatada sallah, Ummulkhair
datayi ceasing opportunity d'innan tayi grabbing towel d'inta tawuce bathroom
tayi wanka sannan tayi brush tadawo dah towel tah kwanta bayan tafashe koh ina
ajikin tah dah turere masu dad'i dah k'arfi tareda lelaye gadon tah, karatun
Alkur'ani mai girma yayi ya d'aura dah azkar kafin yatashi yakoma kan gado koh
gadon bai k'arasa hawa bah tafad'a jikin shi tanah mishi shagwa'ba, Abusaiyeed
k'arfe nawa zakah fita yau, Ummunah am at ur service harsai ansamu patients
idan ankira ni I have to leave MyUmmu for sometime, for the whole day dai tace
kamar tayi kuka, saikuma tah galla masa harara, dariya yayi yace, "sake
mugani Ummunah yayi miki kyau sosai daman kin iya harara", kai koh tafad'a
tanah girgiza kai, wai Abusaiyeed bakah iyayin fushi baneh?, jawota ya kuma yi
jikinsa yace fushi dah abinda nake so? Anayi daman gani nake nidai bazan iyaba
kinsan kaunar danake miki kuwa Meh dad'inah, nima haka ina kaunar kah sosai
sosai Abusaiyeed, nagode toh Allah yasaka miki dah Alkhairi, wayan shi ya
d'auka saurin k'wacewa tayi tah b'oye abayan tah bani Ummunah pls Allah missed
calls kadai zan duba nah baki, k'in bashi tayi har saida ya kar'ba ahankali
dubawa yayi yaga it's switched off OMG Ummunah yaushe wayan ya mutu bansani bah
am on call fah dah anneme ni fah this isn't proper am being unfair, Ummunah
kinga waya nah yamutu ban sani bah, shigewa jikin shi tayi saurin yi kafin tace,
"nice na kashe wayan yesternight am so sorry harna manta nasihar Mummynah
so soon akan san zuciya tacemin koh akan farin ciki nah kada nayi k'arya domin
batada riba", ni kah yafeni Abubaby nah, kallon tah yake yacce take
jijjiga shi take fad'in saiya yafeta cikin kukan shagwa'ba kamar baby, tah
birge shi sosai, kinga Ummunah idan kika k'ara kiran wannan sunan wato Abubaby
asafiyan nan zakiga aikin babies shigewa jikin sah tayi saurin yi sannan takira
sunan shi in whisper, " Abusaiyeed bakada kunya yanzu koh shikenan, toh ai
bakace kah yafe ni bah, nah yafe ki ai, daman baki min komai bah wifey I
understand why U did that so pls karki damu don't make it hard on urself
thinking kinyi wani babban laifi, babu wanda yaneme ni ai dah inada patient har
gida za abiyo ni, waro ido tayi tace, "dah gaske?" Abusaiyeed, yace,
"Eh manah idan layi nah akashe yake zasu biyoni har gida", koda kace
motar kah tah lalace bazaka samu zuwa bah fah, Ummunah akwai non faulty cars
for irin purpose d'innah tuni duk inda nake zasu zo sutafi dani Ummunah ai
aikin gwamnati neh Allah neh mai raya wa kuma shine mai kashe wa amman alot of
lives depends on us and our work, being a doctor is not easy Ummunah saidai
Allah yabamu lada kawai amman the stress is nothing to talk of yafad'a yanah manne
tah ajikin shi tareda fad'in ni abincin babies nakeso pls kinji! Next @ Pg.36<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[06/08, 22:58] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳36⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M ~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 All Groupies of Matar Dr Saiyadee Novel Allah
yabar ❤kauna yasaka muku dah gidan Aljanna Ngd. Mhiss~B~hal tanah gaisuwa🙋🏻🙋🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Bajewa tayi
akan k'irjin shi tah zumburo baki tace, "I don't believe in work
Abusaiyeed no matter what, creating time for the ones U love is the best gift
ever, su wanda kuke nemawa lafiya ai suma dansu kasance dah iyalan su dah en
uwa dah abokan arzik'i suke son lafiyar dah sauk'in, toh ku mesa bazaku ware wa
iyalan naku lokaci bah, sabida meh? Aiki ba takai hujja bah gaskiya, My husband
always remember that family is over everything fah, toh My wife naji, Insha
Allah komai zai daidaita wata rana sai labari Insha Allah yafad'a yanah kissing
wuyan tah in a sexy manner, toh My Abusaiyeed Allah yakawo labarin nan lafiya,
Ameen toh baki bani bah Ummunah, "wai meh?" tace tanah murgud'a masa
baki nifa Allah kanah damu nah meh zanbaka, Abincin babies ya amsa matah
atak'aice, Chab dah safiyar Allahn nan wallahi nidai akwai kunya fah, tashi
muje nasoya manah plantain muci toh, a'a nibah plantain nakeso bah gaskia
Ummunah, toh meh kakeso Abusaiyeed, planchest nakeso yafad'a sounding serious wani
dariya neh ya kub'uce matah sabida bah k'arramin dariya dah kunya yasaka tah
bah all in accurate, rad'i ya matah akunne yace, "tashi kibani planchest
yafi dad'i, kuma shi basai kinsha wani wahala bah harki k'one dah mai agirke
yake readymade neh dah gishirin sah dah maggi full spices daga indallah, yanzu
kam wani mugun kunya Ummulkhair takeji nah daban k'ok'arin d'aga tah yake
dariya takeyi tanah kai masah slight bugu non stop tareda fad'in stop it spoilt
Abusaiyeed, nibabu ruwa nah dakai kasan fah kayi wanka koh kanaso saika sake
yin wani kuma zakah fita, gashi bamusan sanda za asake kiran kah bah remember
U're on call, kwantar dah itah yayi ya matah rumfa sannan yace, "Ummunah
wato harkin san zan sake wani wanka ashe duk kukan matar tawa bah yarinya bace",
Oh Allah help me ya zanyi dah wannan hubby d'in nawa, kunne tah yad'an ciza
yace, "kaunatar shi zakiyi ki kula dashi ki rik'e shi amana", toh ai
baida kun... akan lips d'inshi tayi crushing 'ya' d'in, "Allah
dagaske" yace releasing her lips uhm manah gaske nake hubby, nan yasake
owning lips d'inta haka suka dinga magana owning and releasing each other's
lips making their words crash on their eager lips, Madallah masoya☺, ahaka
zance yasha banban inda Abusaiyeed yasamu enough of his planchest sosai, har
wani jinshi yake @ sky10 cloud12, Ummunah pls don't leave me I still can get
enough of U yace tareda rik'e Ummulkhair dake k'ok'arin sauka tah soya masu
plantain for breakfast, wayyo yau naga tah kaina wai idan kai kasamu planchest
nikuma fah Abusaiyeed ni mezan ci nifah yunwa nakeji d'aga ni nayi preparing BF
ooo, Ummunah ai it's menu kema u can go for Planchest or any other thing for
this morning dai<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>breakfast d'inmu yana
nan right on this bed so U're going no where, dariya tafashe masa dashi kamar
er tsana, MySaiyeed funny U ina zanga planchest d'in? Wai awajan kah tah
tambaya tareda zaro ido, nayi kad'an neh Ummunah koh banda? It's dry U know
tafad'a pointing at his chest tareda winking ido d'aya, sannan tafashe dah wani
dariyan nan yashiga romancing d'inta sosai itama kuma tanah responding to his
call har annamimiyar wayar sah inji fans d'inah tafara ringing, Abeg comot make
I pass sef, My fingers hurts so baldly🚶🏻♀🚶🏻♀🚶🏻♀!
<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Matar Aure wallahi Ina gaisuwa🙋🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Inayin ku dukkah daga ku har en matan Allah yahad'a nu
agidan Aljanna! Next @ Pg.37<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[08/08, 21:14] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳38⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 All My groupies indai kina cikin group d'inah
kowanne toh page d'innan nakune, Ina Alfahari daku dah kaunar dakuke nunamin
Ngd sosai ANATARE Insha Allah🤝<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">2days Later<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Tun daga wannan lokacin dah Abusaiyeed yatafi Ummulkhair
batah k'ara ganin sabah yau kwana biyu kenan, adaren nafarko bataji shigowar
sah dah fitan sabah so batah tabbatar koh agida ya kwana bah amman tamishi
uziri sabida yamata bayani cewa schedules d'insa are very tight sai adare nah
biyu taji shigowar shi wajajan 2am midnight lokacin tanayin sallan nafila bayan
tah idar tah tashi takoma tah kwanta akan gado tayi tunanin Abusaiyeed zaizo
wajan tah amman sam tunda taji shigewar sah part d'inshi bai k'ara fitowa bah
haka tah kwanta zafafan hawayen bak'in ciki nah tsiyayo matah bacci dai takasa
haka tah dinga tunanin koh wani abun tayi masa, toh wai haka auren yake neh
koyaya?, haka tadinga wannan tunanin har saida bacci ya sace tah, abu kaman
wasa yau kwana hud'u tanaji yanah shigowa amman part d'inshi yake wuce wa kuma
tanajin fitar shi dah Asuba amman still baya zuwa wajanta har tayi kuka tah
k'oshi idan abin yadame tah saita kaiwa Ubangijin mu kukanta tareda karatun
Alkur'ani dan samun nutsuwa, yau dai tah tashi dah wani mugun kasala dah
zazzabi jitake idan bataji muryan Abusaiyeed bah mutuwa zatayi dan takasa yin
komai kullum part d'inshi take zuwa dazaran yafita tah d'auki kayan sa tasa
ahanci tanah shak'ar k'amshin jikinsa dahaka take d'an jin dama2 toh Amman yau
hakan ba zaiyi sustaining d'inta bah dan har turaren nashi tah dinga feshewa
ahannu tanah shinshina wa Amman kamar dad'a haukacewa take dasan rungume shi
dah jin muryan shi hakan yasa tah ajiye mulkin tah agefe tayi deciding tah kira
shi taji muryan sah koh zatah samu nutsuwa, waya tah dauka without wasting of
time tashiga dailing numban shi kira take ajere babu adadi ita burin tah
yadauka koh sallama yamata taji muryan shi tasamu biyan buk'ata amman sam baya
picking, kasa hak'uri tayi tacigaba dah kuka har saida yayi matah msg kamar
haka,<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">Ummu ina meeting let's talk ltr pls, on receiving the text
tayi collapsing akan gado tah rushe dah sabon kuka, yanzu yazata yi Abusaiyeed
yadaina sonta neh or what, what actually happened to the 'nah' dah yake
attaching asunan tah, juz Ummu ya kira tah yanzu? Why? kasa bawa kanta amsoshi
tayi hakan yasa tah kira Mummyn tah dan tasamu nutsuwa k'ok'ari take tah saita
kanta sabida kada mahaifiyarta tah fuskancin komai, Mummy tanah picking tayi
Sallama, Ummulkhair dajin muryan Mummyn tah taji wani nutsuwa ya ratsa tah tun
daga saman kanta har k'asan tafin k'afafun tah, Allah Sarki UWA, gaskiya UWA
daban Ce, kowacce UWA tafi k'arfin Wulak'anci, UWA bakida kama, UWA kinfi komai
dad'i kice MOWA azuciyoyin wanda sukasan darajar ki, Allah yasaka miki dah
Gidan Aljanna UWA, Allah mungode makah dakayi UWA, duk mai zagin UWAR wani
rashin sanin darajar tasa Ce, toh kusani wlh Allah Iyaye koh wanne sunfi
k'arfin wulak'anci ta'ba IYAYE jawowa kai targad'en rayuwa ayi hattara musan
abinda mukeyi, IYAYE koh banaka bah IYAYE neh ai sunan UWA dah UBA baya canzawa
kuma idan dah kara IYAYEN wance IYAYEN wance neh, wani ma maraya neh gaba dah
baya baida IYAYEN wani kuma UBAN neh babu Wani Kuma UWA, kai\ke da kike\kake
dasu dukkah kin\ka kasa sanin darajar su, toh wallahi Allah idanma bakya\baka
kyautata masu karki\karka wuce yau baki nemi yafiyar su bah domin Wlh indai
babu kyautata wa IYAYE musamman UWA tofa mutum bazai ta'ba ganin daidai
Arayuwar sabah, Idan kazagi IYAYEN wani wallahi Allah naka kazaga, sai ayi
hattara idan kunne yaji jiki ya tsira, Allah yashige manah gaba! Cigaban
labari, kukan dah Ummulkhair take k'ok'arin dannewa neh ya ku'buce matah
batasan sanda tafashe dah kuka bah, itama Mummyn dajin hankalin Ummulkhair
atashe tafashe dah kukan tareda tambayar dalilin kukan dah take, Ummulkhair
saida taji hankalin Mummy ya tashi sosai sannan tace, "Mummyn mu kiyi
hak'uri ki yafe min Dan Allah nasa kin zubda hawayen ki akaina, "Khairiya
nah" Mummy tafad'a cikin kuka, menene kifad'a min kinji, Mummy bkomai
Missing d'inki nayi kuma nayi nayi yace bazan zo bah sai nayi wata d'aya, Mummy
sam bata gamsu dah amsar bah tace, "Khairiya nice nah haife ki kuma babu
abinda zaki b'oye min, kigaya min menene matsalar"?, Mummynah nifa sonake
naganki nayi missing d'inki dayawa jinake kamar zan mutu, a'a bar fad'in haka
kinji, kin tabbatar min dah iya matsalar kenan? Uhm Mummy ni kawai sonake
naganki! toh maza share hawayen ki bazan ta'ba barin Khairiya tabah, mahaifiyar
ki tanah kaunar ki haryau har gobe har kullum harta mutu har alahira, kidena
kuka Dan Allah khairat kina d'aga min hankali sai naga kamar zaman auren neh
baya miki dad'i, a'a Mummy bahaka baneh kiyi hak'uri daman ni sonake nah
rungume ki mundad'e bamu had'uba, toh shikenan tunda kin d'an kwana biyu zan
tambayi Abbanku Insha Allah zanzo naduba ki kinji koh?, kuma har goya kima
zanyi! Dariyan murna tafara yi tanah share hawayen tah, Mummy dagaske? Eh manah
Khairiya ke Alkhairi ce arayuwa tah, toh naji Mummynah nagode Sosai Allah
yabiya ki dah gidan Aljanna, Ameen toh yanzu hankalin Khairiyan Mummy ya kwanta
koh? kuma bazata k'ara kuka bah koh? Eh Mummy bazan k'ara damuwa bah ina sonki
sosai rayuwa tah, murmushin farin ciki sukewa junansu kamar suna ganin juna,
nan suka d'an ta'ba hirar su kafin suyi sallama inda Mummy take ce matah Allah
ya Albarkaci rayuwar itah dah mijin tah yabasu zaman lafiya, koda Ummulkhair
tah ajiye waya saida tayi wani kukan sabida tsananin missing Mummyn tah datayi
wani kaunar mahaifiyar tah neh yake d'auwainiya dah itah, tashi tayi tayi
sujjada cikin kuka tah godewa Allah daya batah Mummy had'e dah Daddy, Gaskia
IYAYE NAGARI KAT NEH👌🏾 Muna tafe Sweet Fans Next Episode @Pg.39<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">[08/08, 21:14] Matar Doctor Sayyada: 🎍🐚NoVel👇🏿WriTter
🐚🎍<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">☣👄Mhiss~B~hal🙇🏻♀👄☣<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">⏳37⌛<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">🤦🏻♀🤦🏻♀<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🌡🌡🌡<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🤦🏻♀🤦🏻♀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">🍀☘Matar DR. Saiyadee☘🍀<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💉👨🏾⚕💉<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>👄<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>💅🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>🙍🏻<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">(Love&Pain Story Based On Reality)<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">PURE MOMENT OF LIFE WRITERS<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>✍🏾[P~M
~L]✍🏾<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">{We don't just Entertain & Educate,we Touch the Hearts
of the Readers📖}<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span><o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal">www.mhissbhal.WordPress.com<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal">Dedicated 2 Aysha Ali Garkuwa, (Garkuwan Fulani tah) Aisha
Allah ya jibanci lamuran ki yak'ara miki hak'uri, ANATARE Insha Allah Antynah🤝<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>One more look
yamata withdrawing back from his laying position sannan yace, "Ummunah nah
d'auki wayan?", eh manah tah amsa masa dah fara'ar tah, dubawa yayi yaga
ashe Umman sah ce, feeling relieved yace, "thanks gee it's mom",
kinga Ummunah Umma ce take kira ashe, saurin kar'be wayan tayi tah d'auka tace,
"Umman mu Ina kwana ya Abban mu dasu Amal dah Amrah, cike dah fara'a Hajiya
Humaira tah amsa tah, Umma shine bakizo bah koh, toh ni zanzo kice yabarni,
pinching d'inta Abusaiyeed yayi dayaji tafad'i hakan, Umman mu kinga wai bazai
kawoni bah tafad'a idon tah har yafara cikowa dah hawaye, a'a My daughter
zakizo manah ai har gida zanzo nah d'auke ki kimin Hutu, dagaske tafad'a
sounding delighted, eh manah daughter, Abusaiyeed kallon tah yake curiously
wanting to know abinda Ummansu tafad'a dake saka Ummulkhair murna haka, wayan
ya fisge dah alamun akwai abinda yake b'oye wa sannan yace, "kuyi wayan
dah wayan ki, naga kema kinada phone kowa yayi bazar shi dah tasa ya k'arasa
had'e dah yimata gwalo zatah kwace min Umma nah kawai, yatsine fuska Ummulkhair
tayi tace, "tun wani zamani ai tafi so nah akan kah", Hajiya Humaira
tanajin su tayi dariya kawai tareda yimisu Addu'an Allah yabasu zaman lafiya,
hello son ya aiki? Kwana biyu kun dawo daga Lagos d'inneh, a'a tukunnan dai
Umma ya amsa, lallai honeymoon yayi dad'i toh adawo lafiya Allah yayi muku
Albarka, Ameen Umman mu, ina su Bilal nayi missing d'insu ki gaishe su Umma
zasuji son daman cewa nayi bara naji lafiyar ku tunda Allah yasah lafiya toh
shikenan, sai jimawa koh? Toh Umma mungode Allah yasaka dah gidan Aljanna,
Ameen tace sukayi sallama bayan Umma tabashi amanar Ummulkhair, sannan ya yanke
wayar kallon shi Ummulkhair take cike dah mamaki yanzu Abusaiyeed ni kah hana
gaisawa dah Umma harda kashe wayan maimakon kabari muyi sallama tashi tayi wai
itah adole tayi fushi tawuce kitchen fresh plantain tah fitar daga freezer tafara
peeling d'inshi tabaya taji ya rungume tah ya rad'a matah "am sorry wifey
bazan sake bah koh nakama kunne nah"?, baki tah zumburo tace, "ni
bance bah zaka kaini wajan tah", a'a Ummunah bah yanzu bah kinji sainan
gaba kad'an, "naji" tace kamar tayi kuka, ahaka ya lallashe tah<span style="mso-spacerun: yes;"> </span>suka gama had'a breakfast d'in tare cikin
murna tun a kitchen suka zauna gefe d'aya sukaci abinsu, sannan sukayi wanke
wanke tare, parlour suka koma tanah daga kwance akan k'irjin sah suna kallon
Korean movie, Ummunah, yakira tah dah sweet voice d'inshi d'agowa tayi tah
kalle shi tace, "Na'am" peck yakai matah a forehead sannan yace,
"this week my schedules are extremely tight inada alot of meetings to
attend to harda Seminars, so saikin yi hak'uri kinji"?, shigewa tayi jikin
shi takuma k'ank'ame shi tace, "toh Abusaiyeed" naji bakomai tafad'a
with pain yet still giving him the very best of her killer smile, bayan tah
yake bugu ahankali yace, "Ummunah kimin Addu'a kinji akwai meeting dah
zanyi attending a jigawa Kaduna dah zamfara, toh MySaiyeed Allah yakaika lafiya
yadawo min dakai lafiya, Ameen Ummunah, kwana zakayi? A'a duk aranar zan dinga
dawowa Insha Allah, toh Allahu ya kiyaye hanya Ameen My Oxygen, mezan kawo miki
tsaraba ya d'ago fuskan tah yanah tambayar tah, babu komai kadawo min kanka ni
kai nake so ai bah komai bah, toh nidai zan siya miki abubuwa kinji Ummunah,
toh nagode my sweet hubby Allah yabarmu tare yabamu hak'urin zama tare,
Allahumma Ameen Ummunah, kanta tamaida kan k'irjin shi tace, "muyi bacci
ni inajin bacci Allah, "toh yi baccin ki" yace, tareda gyara matah
kwanciya! bayan kusan awa d'aya k'arar wayan saneh yatashe tah daga bacci tashi
tayi anitse tanah murza idanun tah tace, "adawo lafiya Allah ya
kiyaye" Ummunah ina sonki son dah bana yiwa kaine keh tah daban ce nagode
sosai kinji Allah yamiki Albarka dah duk abinda zaki haifa min, d'aukan tah
yayi yakaita dak'i kan gado ya kwantar dah itah sannan yayi bidding d'inta
goodbye tareda blowing matah kiss cikin sauri ya ficce zuwa wajan aiki, Ummu
baccin tah tacigaba dayi peacefully hoping that one day surely everything will
change! Next @Pg.38<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>
<p class="MsoNormal"><span style="mso-spacerun: yes;"> </span>Mhiss B~hal Ce💅🏾👄💞💕<o:p></o:p></p>
<p class="MsoNormal"><o:p> </o:p></p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-26091007451230769282021-01-30T21:00:00.003-08:002021-01-30T21:00:02.075-08:00Tsuntsu Me Wayo Hausa Novel Complete<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-vklbyWLg-I0/YA2R6XD07NI/AAAAAAAAJhQ/OkoBrxgDa7kvFmMiA71j9TS5dRcZ-8BYACLcBGAsYHQ/s2048/Tsuntsu-me-wayo.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="Tsuntsu Me Wayo Hausa Novel Complete" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-vklbyWLg-I0/YA2R6XD07NI/AAAAAAAAJhQ/OkoBrxgDa7kvFmMiA71j9TS5dRcZ-8BYACLcBGAsYHQ/w320-h248/Tsuntsu-me-wayo.jpg" title="Tsuntsu Me Wayo Hausa Novel Complete" width="320" /></a></div><br /> [10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_<p></p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> ( ta wuya ake kamashi)</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Biamillahir Rahamanir Rahim</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>1-3</p><p><br /></p><p>✏Wata kyakyawar bafulatana ce tafe sai faman sauri take, sakamako wani gaggarimin hadari daya hadu yayi bakin kirin lallai idan ruwannan ya sameta ahanyar nan zata yabawa aya zaki ,gashi ba gida gaba ba gida baya waigawa tayi sosai ta kalli bayanta wani laffiyayyan iska ta hango ya nufuta dan haka ta kwasa da gudu ,amman ina tuni kasa ya cika mata ido dole ta tsaya tana share idon tana kuka wani kara ta faraji abayanta wanda bata tabaji ba, dan haka ta fara tunanin ko iska takaita wani duniyar daban ne, kara dunkulewa tayi waje daya tana kuka meban tausayi</p><p><br /></p><p>muryan wasu maza ta faraji akanta daya daga ciki yana fadi ke baki da hankali kinajin mota bazaki kwauce ba.</p><p><br /></p><p>" shiru tayi batace komai ba "</p><p><br /></p><p>ya cigaba da magana ke bazaki tashi ba saina sa mota na latse ki dayan ko ban da yan wake waken shi babu abin da yake. jitayi ya sake cewa big boy yariyar nan fah inajin kurma ce.</p><p><br /></p><p> da katawa yayi daga wakar da yake rairawa yace </p><p><br /></p><p> " Ok yayi kyau d'aga mun ita mugani ko tana da kayan marmari "<span></span></p><a name='more'></a><p></p><p><br /></p><p> dariya dayan yayi sannan yace </p><p><br /></p><p> " kai fah matsalar ka kenan ba dama kaga mace sai ranka ya biya"</p><p><br /></p><p>kama ta yayi ya d'aga ta, tanajin an d'aga ta tafara kokarin guduwa amman rokon da yayi mata bana wasa bane dan haka ta kasa gudu gashi idon ta har yanzon ta kasa budewa bare tasan wacce duniyar iska ta kawo ta, ji tayi yana fadin big boy zo ka duba ta yamma nayi.</p><p><br /></p><p> wanda aka kira da suna big boy ne ya fara takowa yana zuwa gaban yariyar yayi birki yana kare mata kallo yana wani ya mutsa baki zuwa cen yace</p><p><br /></p><p> " babu laifi sai dai tayi kankanta da yawa amman babu komai samun ita amota na d'an matsa ta "</p><p><br /></p><p> fashewa tayi da kuka tana tunanin wannan wani gari ne iska ta kawota wanda ake matsa mutane</p><p><br /></p><p>tanaji suka sakata acikin abun da suka kira da suna mota dan haka kukanta ya karu ,</p><p><br /></p><p>hannun taji yana yawo asaman kirjinta bige hannun ta fara amman ina karfin namiji da mace ba daya bane tuni ya yaga rigar dake jikinta ya rage daga ita sai zani uhu take iya karfinta amman kaman dad'a ziga shi take zuwacen ta farajin abu na yawo atsakanin cin yoyinta tun daganan bata kara sanin inda take ba, zuwacen ta farajin hayaniyar mutane akanta wasu daga ciki suna fadin daniju ce yar gidan malam habu.</p><p><br /></p><p>itako tana kwance tanajjin su ,wasu suna fadi adauketa akaita gida wasu kuwa cewa sukayi kar ataba ta.</p><p><br /></p><p> daker aka samu wata tsuhowa da tace ita zata kaita gida domin kuwa dana kowa ne hijjabin ta ta cire tasawa daniju domin kayan dake jikin ta sun yage ahankali ta riketa sukka nufi cikin gari.</p><p><br /></p><p>abunka da karamin gari tuni lbr ya isa kauya kafin su isa yara da manya suncika kofar gidan malam habu.</p><p><br /></p><p> hayaniyar mutane ne ya fito da malam habu dan dawowar shi daga kasuwa kenan.</p><p><br /></p><p>sallaman da tsuhuwar tayi shi ya da katar da malam habu cikin mamaki ya kalli daniju dake rike hannun tsuhowa tana dingishi cikin tashin hankali yace</p><p><br /></p><p> " ke kuma daga ina Allah yasa ba wani bala,in kika kwaso ba"</p><p><br /></p><p>daga bayanshi aka bashi amsa ahaiye nanaye yau dai ga abinda muke fada ana karyata mu ai tuni na fada yariyar nan bin maza take amman uwarta ta karyata ni toh yau dai ga zahiri.</p><p><br /></p><p> cikin fada malam habu ya daka mata tsawa tare da fadin badake nake magana ba.</p><p><br /></p><p> bayan tsohuwar ta zaunar da daniju sannan ta kalli matar dake kusa da malam tace</p><p><br /></p><p> ina mahaifiyar yariyar nan take?</p><p><br /></p><p> malam ne ya fara kiran salamatu.</p><p><br /></p><p> cikin sauri ta fito idonta cike da hawaye.</p><p><br /></p><p> tana daga tsaye ta kasa cewa komai .</p><p><br /></p><p>tsohuwa ta shiga yi musu bayanin ayanayin da ta same ta.</p><p><br /></p><p>cikin kuka salamatu tayiwa tsohuwar godiya har kofar gida ta rakota .</p><p><br /></p><p> bayan ta koma cikin gidan ne ta isa gaban daniju ta kama ta tanufi bandaki da ita basukai ga shiga ban dakin ba malam habu yace</p><p><br /></p><p> " dakata salamatu "</p><p><br /></p><p>cikin sauri ta tsaya tajuyo takalleshi.</p><p><br /></p><p>cikin tashin hakali yace salamatu lokaci yayi da zaki tura yariyar nan wajjen ubanta indai tana dashi, inkuwa ba haka ba zata barmin gida yau dinnan dan bazan yadda ta lalata min tar biyan yara ba.</p><p><br /></p><p>cikin kuka salamatu ta tsuguna tana ba malam hakuri amman yace ina sam bazai amince ba mikewa yayi ya fara hankad'a daniju kofar gida .</p><p><br /></p><p>biyosu salamatu tayi tana kuka tana rokan sa yayi hakuri tuni yaran dakke kofar gida suka zagayeta suna mata wakka.</p><p><br /></p><p>cikin matsanan cin tashin hankali salamatu ta koma cikin gida cikin sauri ta fara hada kayanta dana danijju domin kuwa bazata taba bari daniju ta bar garinnan ita kadaiba gara ta kaita gidan uban ta inyaso saita dawo.</p><p><br /></p><p>fitowa tayi cikin sauri ta nufi kofar gida malam ya bita da kallo yace</p><p><br /></p><p> me kk shirin yi ne?</p><p><br /></p><p>cikin kuka tace zan kaita katsina ne gurin babanta.</p><p><br /></p><p> atakaice malam yace ban yadda ba babu inda zaki idan ko kika sa kafa kk bar gidannan abakin auren ki.</p><p><br /></p><p> murmushin takaici tayi sannan tace babu komai malam na amince domin kuwa fatima itace 'yata kwaya 1 wanda na haifa aduniya dan haka bazan bari ta salwanta ba dan idan na barta batasan inda zata nufaba Allah yasa haka shine mafi alheri.</p><p><br /></p><p>bece komai ba har tabar gidan ila tashin dariyar baraka da takeji.</p><p><br /></p><p> </p><p>🕊🕊</p><p>_Ummu Yazeed_</p><p> 🕊🕊</p><p>[10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> ( ta wuya ake kamashi)</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Biamillahir Rahamanir Rahim</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>4-5</p><p><br /></p><p>✏Karfe 4:00pm suka isa gidan su salamatu dake cikin garin katsina, tana, rike da hannunn yarta Fatima,</p><p><br /></p><p> salama tayi acikin rauna nanniyar murya.</p><p> wata dattijuwar mata ce ta amsa tare da fadin muryar wa nakeji kamar ta salame.</p><p><br /></p><p>cikin sauri salamatu ta saki daniju ta rungume matar tana fadi nice dada.</p><p><br /></p><p> itama matan kara matseta tayi cikin kuka tace</p><p><br /></p><p> " yau Allah ya karbi addu,ar da na dade inayi shekara da shekaru, ta sake cewa me yasa kika tafi kika barmu haba salamatu baki kyauta min ba kin azaftar dani kinsamu cikin ma muyuyacin hali nida mahaifin Fatima, yasha wahala wajen neman ku.</p><p><br /></p><p>kukan salamatu karuwa yayi, zamewa tayi ta duka kasa tace</p><p><br /></p><p> " dada dan Allah ki yafemin ba ason </p><p>raina na aikata haka ba nayi ne dan na gujewa furucin yusuf dan idan na bashi fatima alokacin zan shiga wani hali kuma bansan ya rayuwar ta zata kasan ce a wajen dangin yusuf ba da suka dauki tsana suka daura min, sai kuma gashi wuyar da na gudar mata beyi tasiri ba dan ayanzu anlalata mata rayuwa cikin kuka ta zaiyanewa dada abinda ya faru.</p><p><br /></p><p>lallashin ta dada ta shiga yi sannan ta mike ta dafa daniju dake zaune sai tsiyayar da hawaye take tace</p><p><br /></p><p> " karki damu fatima insha Allahu Allah saiya saka miki kuma yabi miki hakkin ki da izinin allah"</p><p><br /></p><p>itadai fatima batace komai ba illah share hawaye da take.</p><p><br /></p><p>mikewa dada tayi ta hada ruwan zafi ta kai ban daki sannan ta dawo ta daga fatima da kanta tayiwa fatima wanka .</p><p><br /></p><p>bayan sun fito dada ta kwance daurin kayan da suka taho dashi ta zabi me dan dama dama ta mikawa Fatima</p><p><br /></p><p> sannan ta nemi guri ta zauna ta shiga tunanin lallai idan yusuf ya samu lbrn dawowar salame ba karamin farin ciki zaiyi ba domin kuwa ya dauki son duniya ya daura akan fatima.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Tushen Labarin*</p><p><br /></p><p>Alhj salisu asalin dan jahar katsina ne kuma shahararren dan kasuwa, zaiyi wuya alissafa yan kasuwa 5 ba asa sunan shi ba.</p><p><br /></p><p> yana da mata 1 da yaranshi maza 2, kasancewan Allah be bashi haihuwa da yawa ba ya taso yana matukar kyaunan yaranshi 2 da Allah ya bashi kasim shine babba wanda ayanzon haka yana da aure yaranshi 3, sai yusuf wanda ya kasance mahaifin fatima.</p><p><br /></p><p>itako salamatu mahaifiyar fatima, mahaifin ta ya kasance me gadi agidan alhj salisu dan haka lokacin da yasuf ya furta wa mahaifin shi yana son auren salame yaki amincewa.</p><p><br /></p><p>acewarshi bazai taba bari dan shi ya auri yar me gadin gidan shi ba.</p><p><br /></p><p>mahaiyar salamatu ta kasance bafulatana ce dan haka salamatu ta kwaso kamannin mahaifiyar ta.</p><p><br /></p><p>shikuwa yusuf wani irin soyayya yake wa salame Wanda har takaiga kinjin maganar mahaifin shi </p><p><br /></p><p> " lokacin da alhj salisu ya lura dan nashi yana da niyar nijire mishi sai ya yanke hukuncin koran baba megadi.</p><p><br /></p><p> haka ko akayi malam bello ya shiga tashin hankali lokacin da me gidan nashi ya gayamai ya sallame shi.</p><p><br /></p><p> kudi ya bashi masu yawa dan haka ya nemi wani dankaramin gida ya saya .</p><p><br /></p><p> duk da haka yusuf be hakura ba saida ya bisu har gidan da suka koma </p><p><br /></p><p>wasu mutane ya samu ya kaisu amatsayin yan uwan mahaifin shi suka nemar mai auren salamatu.</p><p><br /></p><p> bayan an daura musu aure ta tare batare da sanin dagin shi ba.</p><p><br /></p><p>bayan shekara daya ta haifiyar ta mace wadda yasa mata sunan mahaifiyar shi wato fatima fatima nada wata uku alhj salisu ya samu lbr dan haka ya dira gidan , yusuf yaji mamakin yadda akayi ya gano gidan </p><p><br /></p><p>yayi mishi umarni da ya saki salame ko kuma ya sallama shi, cikin rawan baki yusuf ya saki salamatu yana kuka tana kuka suka rabu da goyon fatima abayan ta, gidan iyayenta ta nufa bayan wasu kwanaki alhj salisu da kansa yaje har gidan su ya jaddada musu dazaran Fatima ta isa yaye zasu karbeta dan haka salame ta daukki yar ta ta bar garin.</p><p><br /></p><p> guduwa salamatu da ya tada hankalin family alhj salisu domin kuwa suna matukkar bukatan yara , shikowa yusuf yafi kowa gargiza dan haka har yanzo be kara maganar aure ba iyayen nashi ko sunyi mgn sungaji.</p><p><br /></p><p>bayan salamatu ta isa kano acinkin wani akauye ana kiran sa mai giginya bata kara marmari komawa gida ba agidan me unguwa aka sauketa bayan wani lokaci ta samu mijin aure wato malam habu.</p><p><br /></p><p> lokacin da ta aure malam habu tasame shi yana da uwar gidan shi me suna baraka tasha matukar wahala awajen baraka ita da yarta fatima zagi iri iri babu wanda ba,ayi musu ba ita ta Fara kira fatima da suna daniju saboda tsabar bakin cikin cikin da takeyi da ita kuma sai sunnan ya beta acikin kyauyen.</p><p><br /></p><p> kazafi kuwa kullum cikinyin sa take</p><p><br /></p><p>*Cigaban Labarin*</p><p><br /></p><p> bayan fatima ta gama shiryawa direct gadon dada ta nufa ta kwanta tana mai bakin cikin abun da ya faru da ita.</p><p><br /></p><p> sai dare malam ya shigo gida ya tararda abinda ya cire tsanmani woto salamatu da jikar shi fatima .</p><p><br /></p><p> bayan kwana 2 dada ta kira salamatu bayan ta zauna tace</p><p><br /></p><p> " nakiraki ne domin na fada miki shawaran da muka yanke da baban ki kuma dole ne ki daure ko ya miki dadi ko be miki ba"</p><p> baffan ki yace yau dinnan akai fatima gidan kakan ta, saboda idan suka samu lbrn dawowar ki batare da munfada musu ba zasu zargemu kuma dama kyawun da gidan uban sa.</p><p> </p><p> ahankali ta bude baki tace shi kenan Allah yasa haka shine maffi alheri.</p><p> </p><p> fitowa tayi ta leka dakin da fatima take taga sai hada kaya take, ahankali ta kira sunan ta ta dago ta kalleta tace</p><p><br /></p><p> " karki dauke komai daya danganci kayan sakawa naga sai wani rawar jiki kikeyi"</p><p><br /></p><p> turo baki fatima tayi sannan tace toh mama ba dole nayi rawar jiki ba, ban fah taba ganin babana ba kuma idan na tafi babu kaya wani kayan zan rinka sakawa.</p><p><br /></p><p>murmushi mama tayi sannan tace fatima kenan ai wannan kayan naki ko goge kitchen din su bazasuyi dashi ba dan gida ne namasu hali, babanki kuwa harsai kingaji da ganin sa , dan nasan idan ya ganki bazai kuma bari kizo gurina ba, dan haka zanci gaba da miki andu,a Allah tsareki aduk inda kk</p><p><br /></p><p><br /></p><p> maganar dada sukaji dana fadin toh fatima fito mu tafi.</p><p><br /></p><p> cikin sauri ta fito domin kuwa bakaramin kosawa tayi ba tana tafiya tana fadin mama na tafi </p><p><br /></p><p> toh kawai salamatu ta iya furtawa zuwacen ta kira sunan fatima ta dawo ta tsaya tace gani</p><p><br /></p><p> ahankali tace kicewa babanki inagaida shi</p><p> </p><p>toh kwai tace tabi bayan dada aguje,</p><p><br /></p><p>suna fita ta saki kuka me ban tausayi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Ummu Yazeed</p><p> 🕊🕊</p><p>[10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> ( ta wuya ake kamashi)</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p>: *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>9-11</p><p>Tafe suke kowa yayi shiru babu mema wani magana salis ne ke jan motar yayin da taslim take gefenshi daddy da ummi ko suna baya sunyi shiru kowa da kalan tunanin shi duk da dai baya wuce tunanin dansu suke wato haydar dan uwan haihuwan salis, da haka suka isa gidan, salis nayin pakin taslim ta fita da gudu tayi cikin gidan.</p><p><br /></p><p> bin bayan ta sukayi suna shiga suka sameta ta kwakume fatima tana kelketa dariya yayin da fatima kebinta da kallo tana murmushi.</p><p><br /></p><p> yadidko ce ta fito daga daki tana fadin muryar wa nakeji, daidai lokacin iyayen suka shigo ummi ce ta kalli fatima tace</p><p><br /></p><p> taho nan yata bayan ta zauna tazo gabanta ta zauna Hannun ta tasa ta kwatar da ita jikinta tana shafa kanta yadidko nakallon su tana murmushi.</p><p><br /></p><p> taslim tace ummi muwuce da ita gida.</p><p><br /></p><p> kafin ummi tayi magana yadidko tace ina aibaku isaba nan zata zauna.</p><p><br /></p><p> " sai alokacin salis yayi magana danshi baifaye surutuba ahankali yace</p><p><br /></p><p> " kunjita saikace ke kika haifet.....</p><p> </p><p>bekai ga karasawaba daddy ya dakatar dashi da fadin kafara ko ?</p><p><br /></p><p> yadidko tace barshi yayi ai bashi da kunya waima ina daya fitsararren ne?</p><p><br /></p><p> shiru daddy yayi yasa kan sa akasa sai ummi ce tace yana cen wajen gantalin sa.</p><p><br /></p><p> fada yadidko ta farawa ummi tace</p><p><br /></p><p> " karna sake jin kince masa gantalalle kefa uwace addu,a ne ya dace dake ba mugayen kalamai ba Haba aiko dan sunan mahaifinki da yake dashi kyaraga masa.</p><p><br /></p><p> kan ummi akasa tace toh nabari hjy.</p><p><br /></p><p> suna cikin haka alhj yusuf ya shigo da kaya riki riki acikin manyan ledoji.</p><p><br /></p><p> salis ne ya mike ya karfi kayan </p><p><br /></p><p>alhj yasuf yace</p><p> kasa kayan amotar ku kayan kanwar ka ne gobe sai kakai mata dinki.</p><p><br /></p><p> cikin sauri taslim tace baba yaufa da sister fatima zamu tafi.</p><p><br /></p><p> murmushi yayi sannan yace Allah ya bada sa,a taslim.</p><p><br /></p><p>mikewa tayi ta daka tsalle sannan tayiwa yadidko l gwalo .</p><p><br /></p><p> murmushi dada tayi sannan tace ja,ira zanyi maganinki ne.</p><p><br /></p><p>mikewa daddy yayi yayiwa mahaifiyar shi sallama sannan ya kalli ummi yace idan kungama ku fito </p><p>yana fadin haka ya juya ya fita. alhj yusuf ne ya mike yabi bayanshi.</p><p><br /></p><p> bayan kamar 11 minutes suma suka fito harda fatima.</p><p><br /></p><p> bayan sun isa gida taslim da fatima daki daya suka kwana.</p><p><br /></p><p> the next day</p><p> 9:5am</p><p>daddy ne ya tura kofar dakin su salis ahankali ya shiga ganin shi yayi zaune yana karatun alkur,ani zuwa yayi dafdashi ya zauna.</p><p><br /></p><p> salis ya juyo yakalleshi ya rufe kur,anin sannan yace inkwana daddy?</p><p><br /></p><p> cikin fara,a daddy yace lfy lau babana, saidai abu daya dake damu danyau nakwana banyi bacciba idai kunne na yajimin gaskiya toh lallai haydar bekwana gida ba dan banji shigowar shi ba .</p><p><br /></p><p> shiru salis yayi yasa kansa akasa.</p><p><br /></p><p> daddy yasake cewa babana gayamin komai karka boyemin dama haydar ya saba kwana awajje ne?</p><p><br /></p><p> kai ya daga alamar eh.</p><p><br /></p><p> shiru daddy yayi nadan wani lokaci zuwacen ya dago yace mamanku ta sani ?</p><p><br /></p><p> nanma daga kkai yayi</p><p><br /></p><p> daddy yace toh yayi kyau, kunyi waya dashi ne.</p><p><br /></p><p> kasan akasa yace a,a</p><p><br /></p><p> toh kanemeshi awaya idan kasame shi kacemai nace idan ya wuce 2 hours be dawo gida ba ya neme wani uban.</p><p><br /></p><p>cikin sauri ya juya ya fita adakin.</p><p><br /></p><p> mikewa salis yayi ya dauki wayar shi ya fara neman layin haydar zuwace aka dauki wayar saidai abinda ya bashi mamaki muryar mace yaji cikin lankwasa harshe tace waye</p><p><br /></p><p><br /></p><p> shiru yayi nadan wani lokaci sannan yace iname wayar yake.</p><p><br /></p><p> itama kamar bazatai mgn ba tace yana bacci, </p><p><br /></p><p>cikin takaice ya kashi wayar yamike ya fara shiri zuwa Office.</p><p><br /></p><p> yana kokarin fita agidan yaci karo da alhaji yana shigowa yace kasameshi kuwa?</p><p><br /></p><p> cikin sauri yace a,a daddy bansame shi ba amman zuwa anjima zankara gwaawa.</p><p><br /></p><p>4:02pm salis ya dawo gida yana ardu,a azuciyar shi Allah yasa haydar ya dawo.</p><p><br /></p><p> afalo ya samu taslim da fatima suma kallon wani film a TV, fatima ya gani tasa wasu kaya masu kyau riga da siket na atamfa bakaramin kyau suka mata ba ya dade tsaye yana kare mata kallo suko hankalin su na wajen kallo hannun shi yasa acikin aljihun shi sannan yayi magana ahankali yace sister zahra.</p><p><br /></p><p>dukkan su suka juyo suka kalleshi murmushi fatima tayi taslim tace yaya yaushe kashigo?</p><p><br /></p><p> zuwa yayi dafda fatima ya zauna sannan yace zahara kinga yadda kikayi kyau kuwa.</p><p><br /></p><p> cikin sauri taslim tace nifa yaya?</p><p><br /></p><p>kema kinyi kyau amman zahara ta fiki kyau, tsaki yaja sannan yace haydar ya dawo kuwa.</p><p><br /></p><p> nidai bansani ba ammafa kamar be dawowa ba.</p><p><br /></p><p> mikewa yayi sannan yace kuje Ku shirya na kaiku kuyi gidan alhj</p><p><br /></p><p> da gudu taslim ta tashi ta shige daki fatima ma mikewa tayi tabi bayan ta sumi sumi dan har yanzon bata gama sabawa da gidan ba.</p><p><br /></p><p>bayan sungama shiryawa taslim tace nidai fatima ki sameni dakin yaya.</p><p><br /></p><p> bayan fatima ta saka hijjabinta tace ummi mun tafi murmushi tayi sannan tace adawo lfy fatima.</p><p><br /></p><p> tana fitowa falo ta hango salis kwance akan kujera idonshi rufe saidai abida ya bata mamaki kananan kayane jikinshi sun matseshi kuma daidai da takalminshi be cireba dashi ya kwanta kara matsowa tayi ta kalli shi sosai wani gashhi ne cike akan sa cibiri cibiri irin na samarin zamani tabe baki tayi sannan tace azuceyar ta toh ina taslim tayi, </p><p>gani tayi bata da mafita dole ta tasheshi wata kela ita suke jira gashi yaci uban kwalliya dan hakka ta matsa dafdashi tace yaya katashi muje nagama fah.</p><p><br /></p><p> ahaukaci ya bude ido yakai mata tokari aciki ,cikin sauri ta duka ta rike cikin</p><p><br /></p><p><br /></p><p>matsowa ya Farayi yana fadin dan kutumar uban ki wacece ke dazaki zo ki tadani ina bacci.</p><p><br /></p><p> a sittin ta mike rike da ciki tayi dakin</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊</p><p>[10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> ( ta wuya ake kamashi)</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>12 -14</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummi na kwace akan gado taga fatima rike da ciki arude ta diro da kafafuwan ta tace</p><p><br /></p><p> " fatima lfy me ya sameki aciki ?</p><p><br /></p><p> kasa magana tayi illa kuka da ta keyi.</p><p><br /></p><p> ummi ce ta kamota ta kwantar da ita jikinta tana rarrashinta ,ta gayamata me yasame ta </p><p><br /></p><p>daidai lokacin salis da taslim suka shigo dakin, salis yace sister ya haka muna ta jiran ki kuma kinki fitowa,</p><p><br /></p><p> kallonta yayi sosai yaga ashema kuka take ya sake cewa ummi me ya sameta.</p><p><br /></p><p>nima abinda nake tambayanta kenan taki magana.</p><p><br /></p><p> tsugunawa yayi gaban su yace sister gayamin me ya sameki?</p><p><br /></p><p> cikin mamaki take kallon salis azuciyar ta tace lallai wannan munafiki ne wato har yaje ya cenzo kaya dan tsabar mugun ta ahankali ta dago jajayen idonta ta harare shi sannan tace </p><p><br /></p><p> bakai bane kasa kafar ka ka naushe ni aciki.</p><p><br /></p><p> zaro ido yayi sannan yace ni kuma ? gaskiya bani bane ,sister toh me kikamin da zan dake ki?</p><p><br /></p><p> ummi ta kalli salis tace haydar ya dawo ne?</p><p><br /></p><p> Ok eh ummi sanda muka fita nida taslim naga shigowan shi.</p><p><br /></p><p>batace komai ba ta mike ta fita adakin salis ya matsa gabanta ya kamo hannun ta yana wasa da yatsuta yace kiyi hakuri, zahara bani bane kisan mu yan biyu ne kuma muna matukar kama nan gaba kad'an zaki fara banbance mu dan akwai dan banbanci, </p><p>kallon idonta yayi sannan yayi murmushi yace ban da abinki ma sister ai shigar mu ba iri daya bace shi bakiga ya tara gashi bane saikace mahaukaci.</p><p><br /></p><p> taslim ce ta saki dariya tace wlh brother ni yanzon ma tsoro yake bani haka ranar nan daga naje wucewa ta kusa dashi lokacin yana waya saiji nayi ya jifeni da cup wai nazo naji abinda yake cewa ne naje na gayawa ummi.</p><p><br /></p><p> salis yace ai yana da matsala haka dai zakuita hakuri dashi.</p><p><br /></p><p> ji sukayi anturo kofar ummi na gaba haydar na bin ta abaya zuwa yayi ya tsuguna agaban fatima kamar yadda yaga salis yayi kamar me ciwon baki yayi mgn ahankali sister kiyi hakuri na manta acemin kina gidan nan na dauka wata ce daban.</p><p><br /></p><p> shiru tayi ko kallon shi batayi ba sai dai ko ahaka ta gane banbancin murya atsakkanin su domin kuwa muryar salis tafi na haydar sanyi.</p><p><br /></p><p> jinda yayi tayi shiru yasa ya waiga ya kalli salis yace brother katayani bata hakuri </p><p><br /></p><p> salis yace bakumai haydar ya wuce sai dai akiyaye gaba.</p><p><br /></p><p> sai alokacin haydar ya kalli fatima daniyar yayi mata godiya amman yana kallon fuskarta ya kasa cewa komai sakamokon muguwar kama da tayi masa da wata yariya da yake marmarin sake kasan cewa da ita</p><p><br /></p><p>mikewa yayi cikin sauri ya nufi kofa dukkansu binshi sukayi da kallo ummi ce tace ikon allah, Allah ka shirya wannan bawa naka</p><p><br /></p><p> salia ko mikewa yayi daga gaban fatima yana fadin toh yanzo dai shikenan haydar ya hanamu fita.</p><p><br /></p><p> </p><p> Haydar na fita ya nufi dakin mahaifin shi kamar yadda ummi ta umarceshi ahankali ya tura kofar ya shiga neman guri yayi ya zauna sannan ya daga kai ya dubi mahaifin shi dake zaune yana karatun jarida, ahankali yace</p><p><br /></p><p><br /></p><p> " daddy ina yuni?</p><p><br /></p><p> baza yayi dashi kamar ma besan da shigowar shiba zuwa cen yace a inakakwana?</p><p><br /></p><p> kanshi akasa yace daddy mun je zaria ne muna kan hanyar mu ta dawowa motar ta lalace amman dan Allah kayi hakuri bazan....</p><p><br /></p><p>tsawa ya daka mishi wanda yasa dole yayi shiru sannan yace Karka maidani mutumin banza haydar guda nawa kake, nine ubanka babu wani dubara da zakamin, batun yauba na kula kai mutumin banza ne, toh bari kaji daga yau kar magriba ta sake maka awaje kuma daga office ban amince ka wuce ko Ina ba kanajina ?</p><p><br /></p><p> eh kawai ya iya furtawa domin hukuncin yayi masa tsauri.</p><p><br /></p><p> da daddare salis ne zaune adakin su yana karatun Qur,ani yayin da haydar ke kwance akan gado sai juyi ya keyi.</p><p><br /></p><p> zuwacen salis ya rufe Qur,anin ya iso bakin gadon ya zauna sannan yace</p><p><br /></p><p> " brother meke damun ka ne naga sai juyi kake?</p><p><br /></p><p> tashi yayi ya zauna sannan yace kasan matsalata brother bana iya bacci ni d'aya.</p><p><br /></p><p>murmushin takaice salis yayi sannan yace haydar al,amarin ka yana bani mamaki kai wai bakajin tsoron Allah ne, ga hanya mafi sauki kabi kaki sai anyi amma mgn kacei Allah ne ya daura maka toh naji Allah ne ya daura maka kayi aure mana, ko mata hudu ne kana iya hadawa.</p><p><br /></p><p>hannu haydar ya dagawa salis haba wai kai sai ka rinka cewa nayi aure duka duka guda nawa nake ko 30 years ban hadaba fah.</p><p><br /></p><p> kulewa salis yayi cikin fada yace kananufin sai mutun yakai 30 sannan zaiyi aure wani malamin ne ya fada maka?</p><p><br /></p><p> nidai kawai ka rufamin asiri na dan fita da suba zandawo.</p><p><br /></p><p>cikin fada salis yace wlh bazan rufama ba kana fita zan fadawa daddy</p><p><br /></p><p>tsaki haydar yaja ya tura kanshi cikin bargo yana fadin muna fuki kawai</p><p><br /></p><p> naji ni munafuki ne kaikuma dan iska me lalata yaran muta ne.</p><p><br /></p><p> hankade bargon yaye ya duro ya cefkke wuyar rigar salis nan danan dabe ya kyaure atsakanin su.</p><p><br /></p><p> ummi da yan matanta suna falo suna kallon wani film suka farajiyu hayaniyar su aguje suka nufi dakin.</p><p><br /></p><p> salis naganin su ya tsaya cek amman haydar be daina kaimai doka ba.</p><p><br /></p><p> ummi ce ta fara kokarin jan haydar tana cewa haydar duk yadda akayi kana shan kayan maye ka rasa dawa zakayi fada saida dan uwanka innalillahi wa ina ilaihir raju, un.</p><p><br /></p><p> salis ne yazo ya rike ummi yana fadin ummi jeki abinki ya wuce taslim zahra kuje ku kwanta.</p><p><br /></p><p> ummi kuka takeyi dan haka su fatima suka fara kuka.</p><p><br /></p><p> shiko haydar sai maida numfashi yake yana hararar salis ya koma bakin gado ya zauna.</p><p><br /></p><p> salis ko ganin ummi tana kuka hankalin shi ya tashi, yayi daya sanin biyewa haydar yace ummi dan Allah kije ki kwanta babu abinda zai sake faruwa.</p><p>suna fita haydar ya mike ya koma kujera ya zauna hannu yasa a aljihunshi ya dauko sigari ya kunna ya fara zuka yana fesar da da hayakin</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊</p><p><br /></p><p> Comment 07014197556</p><p>[10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> ( ta wuya ake kamashi)</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>15 - 16</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Salis tsaya wa yayi yabishi da kallo cikin mamaki yasan haydar yana shen sigari tunda yasha gani amotar shi amman betaba sha agaban shiba sai yau ,</p><p><br /></p><p>filo ya dauka ya nufi falo dan baxai iya shakan wannnan warin ba.</p><p><br /></p><p> washegari</p><p><br /></p><p>salis yakai fatima makaranta secondary akasata jss 1 </p><p> itako taslim tuni ta kare secondary ayanzo haka tana cigaba da karatu, dan haka kullum salis kekai fatima makaran ta drive kuma ya dakota saboda lokacin salis yana gurin aiki.</p><p><br /></p><p> shakuwa ce tashiga tsakanin salis da fatima me karfi dan ayanzon har fatima ta saki jikin ta dashi sosai.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> shiko haydar tun ranar da su kai hayaniya da salis kwata kwata baya mai maga gashi har an hada one week amman daddy yake cire takunkumin shi saima kara samai ido da yake haka kullum zaita juyin shi akan gado sai dai salis yayi tsaki ya juyamai baya dan haka abin ya fara damun shi.</p><p><br /></p><p> yauma kamar kullum haydar ne kwance agado rike da ciki yana murkusu ya hada uban zufa.</p><p><br /></p><p> salis ne ya taro kofar ya shigo kallon haydar yayi cikin sauri ya karasa bakin gadon yace make damunka.</p><p><br /></p><p> daker ya iya bude baki yace cikina ne.</p><p><br /></p><p> mikewa yayi ya nufi kofa ahankali haydar ya kirashi bayan ya dawo yace Ina zaka.</p><p><br /></p><p> zan fadawa daddy ne.</p><p><br /></p><p> zaro ido haydar yayi yace dan Allah karka gayamai nasha magani zuwa anjima zai sauka.</p><p><br /></p><p> shiru salis yayi ya zauna abakin gadon ganin inda haydar yake hada zufa ya sake mikewa ya kunna mai A.C amman duk da haka zufa yake zuwa cen hawaye ya fara zubowa a idon shi hannun shi kuwa yana kasan cikin shi yana dan matsawa </p><p>zuwa cen bacci ya kwashe shi.</p><p><br /></p><p> ajiyan zuciya salis yayi sannan ya gyara kwanciyar shi .</p><p><br /></p><p> washegari</p><p><br /></p><p> sunfito cikin shirin su na tafiya Office salis ya kalli haydar yace au me ciwon ciki ya cikin naka?</p><p><br /></p><p> tsaki haydar yayi sannan yace sai yanzon zaka tambaye ni.</p><p><br /></p><p> fashewa yayi da dariya sannan yace</p><p><br /></p><p> " wlh brother mamaki kake mani jibeka one week kawai dobi inda kayi zuro zuro, kasan Allah kamata yayi ahada maka mata hadu dan daya ta maka kadan.</p><p><br /></p><p> tsaki haydar yayi ya shege motar shi yabar wajen.</p><p><br /></p><p> yana isa Office yayi amfani da wayar shi ya kira babban aminin shi anas, </p><p><br /></p><p>ba ajima ba anas ya shigo, wata budurwa nabinshi abaya.</p><p><br /></p><p> haydar naganin su ya miki yariyar ya rungumo yana kissing dinta itama yariyar yar duniya ce dan tuni ta fara aika mai da makata nan suka lalace.</p><p><br /></p><p> jin nurfarfashin da haydar keyi yasa anas barin office din dan yasan idan ya zauna zasu tasomai da tsumin sa.</p><p><br /></p><p> saida ya kwashi awa 3 yana zaune abakin office din sannan yamike ya tura kofar ya shiga ganin yariyar yayi kwance tana barci akan kujeran dake cikin office din tayi matashi da cinyar haidar shima bacci yakeyi hannun shi acikin rigarta..</p><p><br /></p><p> hannun shi ya hada yayi tafi nan danan suka mike anas yace toh waikai yau baka da aiki ne, tsaki yaja sannan yace bar aikin nan gobe nayi, juyawa yayi ya kalli yariya yace </p><p><br /></p><p> babyna naga alamar kin</p><p> gaji da yawa yau nabaki wahala am sorry nayi missing dinki ne dawa.</p><p><br /></p><p> cikin shagwa tace zani gida nayi wanka na kwanta.</p><p><br /></p><p> OK baby badamuwa anas zai maidake gida amdai gobe zaki dawo KO, saboda kar mukuma samun irin matsalar yau.</p><p><br /></p><p>cikin shagwaba ta mike tana buga kafa kamar zatai kuka take mgn ciki ciki</p><p><br /></p><p>haydar kara rudewa yayi dan yana balakin son yaga mace na irin wannan shagwabar bare wannan yariyar da komai dake jikinta rawa yake besan lokacin daya isa gareta ba ya zura bakinshi cikin nata saida yayi son ransa sannan yabarta.</p><p><br /></p><p>karfe 4:00 hayadar ya baro office cike da farin da walwala domin yau ya samu abinda zuciyar shi take muradi yana shiga gida ya samu salis da fatima suta hira suna dariya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>bebi ta kansuba ya shige daki bayan yayi wanka ya biya basussukan sallah da ake binshi ya fito falo .</p><p><br /></p><p> suna nan yadda ya barsu saidai ayanzon harda taslim, zama yayi agefe ya kure fatima da ido shi dai yana ganin kamar yasan yariyar nan, idan ma ba itabace toh sunada dankantaka tv ya kurawa ido amman lokaci zuwa lokaci yana satar kallon fatima.</p><p><br /></p><p> zuwacen taslim tace fatima kitashi muje gidan yadidko.</p><p><br /></p><p> salis yayi karaf yace ke bazata ba ni banason yawace yawace.</p><p><br /></p><p> cikin sanyin murya taslin tace haba yaya gidan yadidkon ne yawace yawace kuma fa bajimawa zamuyi ba.</p><p><br /></p><p> kalon fatima salis yayi cikin ido yace zahra kinason zuwane?</p><p><br /></p><p> cikin sauri fatima ta dukar dakai dumin duk lokacin data kalli cikin idon salis saitaji gabanta ya fadi.</p><p><br /></p><p> riko hannunta yayi tabi hannun shi da kallo yana wasa da yatsun yake fadin idan kinason zuwa ki tashi kuje amman karki irin shigar taslim, kisa hijjab ne kuma karku dade.</p><p><br /></p><p> da mamaki taslim take kallon salis shima haydar shi yake kallo .</p><p><br /></p><p> suna fita haydar yadawo dafda salis ya zauna yace</p><p><br /></p><p> " brother kardai son yariyar nan kake?</p><p><br /></p><p> a,a haba meka gani, kodan nace tasa hijjab dama shiyasa naga kana kallo na.</p><p><br /></p><p> hannu haydar ya daga mai kaga malam bawani kwana kwana da zakamin ka fito fili kace sonta kake.</p><p><br /></p><p> dariya sosai salis yayi sannan yace ni dai bance maka inasonta ba nidai kawai nasan yariyar tana birgeni kuma idan muna tare ina samun kaina cikin nishadi har inji manason mu rabu.</p><p><br /></p><p> shine zakace bason ta kake ba wlh sonta kakeyi kuma wlh bazaka aureta ba.</p><p><br /></p><p> murmushi yayi sannan yace tunda kaine ubana ba</p><p><br /></p><p> mikewa haydar yayi sannan yace</p><p> sai kawai friends din na suga wannan yariyar amatsayin amaryar ka aisai sumin dariya idan bazaka iya fita ka nemo mata ba ka bari ni zannemo maka.</p><p><br /></p><p> dariya salis yayi sannan yace ni kuma narasa wanda zai nemomin mata sai wanda ya kauce hanya</p><p><br /></p><p>azuciye haydar ya miki daidai lokacin su fatima suka fito cikin shirin tafiya dan haka yadan tsaya.</p><p><br /></p><p>kallon su yayi ya yamutsa baki saboda ganin su sanyi da hajjab har taslim shiko salis sai mumushi yake yace gaski kunyi kyau takawa yayi zuwa gaban fatima ya daga hannu shi daidai fuskar ta yana kokarin cire mata wani dan zare daga jikin hijjabin bayan ya cire zaran yakai bakin sa daidai kunnen ta yana mata mgn acikin taslim da haydar babu mejin me yake cemata saidai fuskarshi tana dauke da murmushi yayin da fatima ta kamo hijjab dinta ta rufe fuskarta tana dariya.</p><p><br /></p><p> haydar ya kara kulewa kuma lallai yanason yasan me salis ya fadawa yariyar nan har take dariya, tana nufin itama tasan love ne yar kauye da ita wani dubara ne ya fado masa cikin sauri ya nufi kofa yana fadin kuzo muje nakaiku</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Gaisuwa ta musamman ga duk wanda yake cikin wannan group *Farfazaz novels* _kunfi ko wani group comment da nuna soyayyar ku akan wannan lbr Tsuntsu me wayo inajin dadin kasan cewa daku_ 💃💃💃😘</p><p><br /></p><p><br /></p><p>21 - 23</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zama yayi nesa da salis kanshi akasa dan duk abin shi yana tsoron daddy shi ahankali yace gani.</p><p><br /></p><p> daddy ya dago ya kalleshi yasa hannu ya cire gilas din dake idon shi sannan yace me ya had'a ku ?</p><p> </p><p> d'ago kai yayi ya kalli salis ya sake mayar da kanshi kasa yayi shiru.</p><p><br /></p><p> ummi tace wai ba dakai ake mgn ba ne</p><p><br /></p><p> bece komai ba kuma har yanzo kansa na kasa.</p><p><br /></p><p> daddy yace kyale su tun da bazasu fada ba ai sunfi kusa, amman nasan haydar ne baidan gsky wata kila ka kule shi ne amman ni araina banason kuraba daki nafiso sai kunyi aure kowa ya samu abokiyar zama ko ya kuka gani?</p><p><br /></p><p> haydar ne ya fara magana daddy ai ko munyi aure gida daya zamu zauna.</p><p><br /></p><p> cikin sauri salis yace dawa dakai Allah ya kiyaye wlh ba zan zauna dakai ba.</p><p><br /></p><p> sakin baki haydar yayi yana kallon salis sannan yace salis nine fah.</p><p><br /></p><p> fuskar salis adaure yace kaidin fah ina hauka ne zan zauna dakai.</p><p><br /></p><p> daga daddy har ummi basuji dadin maganar salis ba, </p><p><br /></p><p> ummi ta juyo da kallon ta gurin salis tace </p><p><br /></p><p> " ni bansan ka da fushi haka ba banji dadin mgnr ka ba idan baka zauna da dan uwan kaba dawa zaka zauna banajin dadin ganin ku cikin wannan halin dan Allah ku zauna lfy.</p><p><br /></p><p> juyawa tayi gurin haydar ta harareshi sannan tace kai kuma kabashi hakuri dan nasan kaine mara gaskiya.</p><p><br /></p><p> ahankali yace kayi hakuri in Allah ya yarda bazan kara ba.</p><p><br /></p><p> har yanzon fuskar salis adaure take dan haka daddy ya kira su gaban shi kama hannun su yayi ya hada yace ya wuce kutashi ku tafi.</p><p><br /></p><p> suna rike da hannun juna suka fita.</p><p><br /></p><p> ummi ta dawo da kallonta gurin daddy sannan tace</p><p><br /></p><p> " salis akwai hakuri amman idan ransa ya baci be iya fushi ba shiko haydar idan be nemi fitana ba bayajin dadi.</p><p><br /></p><p> ajiyar zuciya daddy yayi sannan yace Allah ya shirye su.</p><p><br /></p><p> haka rayuwa taci gaba da kasancewa agidan alhj kasim tsakanin salis da haydar yau ayi fada gobe ashirya zuwa anjjima kaga kamar basune suka yi ba.</p><p><br /></p><p> kwanci tashi ba wuya wajan Allah dan yanzon kusan shekara fatima uku aku agidan, zuwa wannan lokacin shakuwa ce me karfe tsakanin fatima da salis.</p><p><br /></p><p> yayin da haydar ya hura wutar kiyayar fatima azuciyar shi dan ko mgn bata hadasu da ita</p><p><br /></p><p> duk da cewa ayanzon idan ka kalli fatima baza taba cewa tayi zaman kauye ba </p><p><br /></p><p>acin wad'an nan shekarun so daya babanta ya kaita gurin mahaifiyar ta yanzon fatima tana ajin karshi na secondary sakamakon kwanya da Allah ya bata.</p><p><br /></p><p> ta bangaren ummi kuwa wato mahaifiyar su haydar bata nunawa fatima wani banbanci tsakanin ta dasu haydar dan haka tana cikin kwanciyar hankali matsalar ta daya haydar.</p><p><br /></p><p>ayanzun dai fatima ta zama cikekiyar budurwa komai na jikin ta ya fito sosai </p><p><br /></p><p> fatima ce kwace jikin kakarta yadidko tana danna waya yayin da taslim tana gefe tana cin abinci suna fira da taslim.</p><p><br /></p><p> sallaman alhj yusuf ya katsa musu hira, bayan yazaunaya kalli fatima dake jikin mahaifiyar shi yace ke ashe baki da hankali katuwarki dake zaki kwanta mata ajiki, yajuya ya kalli taslim sannan yace ke kuma bakiyi mata fada.</p><p><br /></p><p> murmushi taslim tayi sannan tace baba tausa fah take mata.</p><p><br /></p><p> hararanta yayi sannan yace wai ma me kukeyi agidan nan yau kusan 3 days kenan inaganin ku anan ku koma gidan ku mana.</p><p><br /></p><p> taslim ce ta amasa munzo tayata zama ne ai yauma zamu wuce.</p><p><br /></p><p> yace gara dai kutafi hira sukaci gaba dayi shi da yadidko.</p><p><br /></p><p> zuwa cen su fatima suka fito cikin shirin ta fiya alhj yusuf ne ya kawosu har gida bayan sun gaisa da ummi ya wuce.</p><p><br /></p><p> washegari fatima nata zuba ido taga shigowar salis har wan 12 na rana bata ganshi ba dan haka ta shiga neman layin shi saida ta kira su uku ba adauka ba dan haka tashiga damuwa.</p><p><br /></p><p> lokacin da taslim ta kawo musu abincin rana kasa ci tayi tana juya cukalin.</p><p><br /></p><p> taslim tace sister wai meke damun ki tun jiya naga duk kinyi wani iri.</p><p><br /></p><p> meko ni bawani abunda yake damu na.</p><p><br /></p><p> taslim shiru tayi taci gaba da cin abincin ta.</p><p><br /></p><p> bayan sungama dakin ummi suka nufa suna shiga fatima tace</p><p><br /></p><p> ummi wai yaya salis baya nanne?</p><p><br /></p><p> eh bayanan bakuyi waya bane halan?</p><p><br /></p><p> tace nakirashi yaki dagawa.</p><p><br /></p><p>ummi tayi murmushi tace kila baya kusa da wayar ne, munyi waya danzon yace min suna hanya.</p><p><br /></p><p> dariya taslim tayi tace dama shi yasa kika ki cin abinci wai ku soyayya kuke ne?</p><p><br /></p><p> fatima ce ta harari taslim sannan tace wani irin soyayya.</p><p><br /></p><p> ummi tace ke rabu da ita neman mgn ne da ita.</p><p><br /></p><p> dariya taslim ta sakeyi sannan tace wlh ummi soyayya sukeyi.</p><p><br /></p><p> daure fuska ummi tayi sannan tace wai taslim ina wasa dake ne nace kibar mgnr ina ruwanki da su.</p><p><br /></p><p> hannu tasa ta rufe bakinta sannan tace na bari ummi.</p><p><br /></p><p> daidai lokacin salis da haydar suka shigo bayan sun gaisa da ummi fatima gaida su haydar kadai ne ya amsa shima dan yaga ummi ne hakalin fatima ya kara tashi idonta ya cika da hawaye</p><p><br /></p><p> ummi ta lura da halin da fatima take ciki bata dai ce komai ba dan bata faye son shiga tsakanin su ba</p><p><br /></p><p>basu dade ba suka fita zuwa dakin su, fatima ko na gefe tayi tagumi.</p><p><br /></p><p> ummi ta juya ta kalleta tace</p><p><br /></p><p> fatima cire tagumin nan tashi maza ki kai musu abinci.</p><p><br /></p><p> har ta dauki abincin ta tuna salis beson ya ganta babu hijjab dan haka ta koma dakin ummi ta dauki hijjab ta fita.</p><p><br /></p><p> samun su tayi zaune haydar na nunawa salis wani abu acikin wayar shi sunata dariya aje abincin tayi tajuya har takai kofa haydar yace ke dauki ledar cen ki kaiwa ummi.</p><p><br /></p><p> dawowa tayi ta dauka ta fita, kafin takai dakin ummi hayawaye ya fara zubo mata saida ta share hawayen ta shiga dakin ummi ta aje ledar ta koma kusa da taslim ta zauna ummi ta bita da kallo batace komai ba ta mike ta fita.</p><p><br /></p><p> dakin su haydar ta shiga cikin mamaki</p><p> suke kallonta.</p><p> kallon salis tayi sannan tace waikai yaushe aka daura maka aure da fatima ne bansani ba</p><p><br /></p><p> da mamaki yace ummi bangane me kk nufiba.</p><p><br /></p><p> aidama bazaka gane ba kawai dan fatima ta tafi gidan hajiya bata fada makaba kk wannan fushin, matarka ce?</p><p><br /></p><p> da sauri ya girgiza Kai.</p><p>ummi ta sake cewa toh karage wadan nan dokokin takasa mata suyi yawa kuma kazo ka rarasheta</p><p><br /></p><p>adakin su ya sameta tana kwance tayi rufda ciki ahankali ya kira sunan ta amsawa tayi batare data waigo ba ya sake cewa toh tashin mana.</p><p><br /></p><p> kintashi tayi dan batason yaga idon ta</p><p> gaban gadon yaje ya zauna yace zahara tashi mana kosai nakira ummi ne?</p><p><br /></p><p>tanajin ya kira sunan ummi ta miki ta fara sakkowa daga gadon binta yayi da kallo dan rabon da ya ganta babu hijjabi ya manta sai yaga ta kara kyau bayan ta zauna ya kalleta yace wato abin harda su kuka?</p><p><br /></p><p> cikin muryan kuka tace toh bakai bane kake fushi dani.</p><p><br /></p><p> cikin sauri yace nabari indai nine banason nasake ganin hawayen ki </p><p><br /></p><p>daidai lokacin haydar ya shigo dakin abakin kofa ya tsa dan haka salis ne kawai yaga shigowan shi</p><p><br /></p><p>juyawa yayi barayin fatima yace tashi muje gurin ummi.</p><p><br /></p><p> tana mikewa yace toh kisa hijjab mana.</p><p><br /></p><p> buga kafa ta fara kamar karamar yarinya cikkin shagwaba tace ni gaskiya a,a nan da dakin ummi saina saka hiijjbi.</p><p><br /></p><p>binta yayi da kallo zuwacen yayi murmushi yace ji abinda kikeyi saikace wata karamar yarinya </p><p><br /></p><p> kara shagwabewa tayi </p><p><br /></p><p> haydar ko dake bakin kofa tuni ya Fara rikicewa dan babu abinda yafi tayar mai da hankali kamar yaga mace tana wannan shagwaban, idon shi nakan kirjinta </p><p><br /></p><p> salis kuwa ji yake kamar ya rungumita dan betabajin irin yanayin da yaji yau ba, juyawa yayi ya kalli haydar yace waikai wani gulman ne ya kawoka</p><p><br /></p><p> sai alokacin fatima tasan da shigowan haydar juyar da kallonta tayi gareshi </p><p><br /></p><p> yace ke dena kallona munafuka kawai me suffar aljanu</p><p><br /></p><p> salis yakalleshi ya karasa gaban shi sannan yace muje </p><p><br /></p><p> *******</p><p>da daddare duk yan gidan ne suka hadu a falon daddy suna hira zuwa cen daddy yace mun kusa shan biki agidan nan.</p><p><br /></p><p> Ummita tace dama kuwa inason nama magana tunda su sunki yi .</p><p> cikin sauri salis yamike zaibar wajen. alhj yace inakuma zaka dawo ka zauna </p><p><br /></p><p> bayan yazauna daddy yace yakamata kuyi aure salis kaida nake ma ganin ka kamar me hankali.</p><p><br /></p><p> ummi tace alhaji ai haydar zakawa mgn shi yariga ya kama tashi gatanan kusa da kai duk da dai ba fada sukayi ba amman duk me hakali yasan sun amice da juna</p><p><br /></p><p> murna ce ta kama daddy yace toh shine ni baki sanar min ba</p><p><br /></p><p> dawai inajira ne su fada da bakin su gatanan ansa mata takunkumi zama da hijjab saikace matar liman </p><p><br /></p><p> taslima ta kwashe da dariya shikuwa salis tunda ya dukar da kansa ya kasa dagowa fatima ma tana kudun dune cikin hajjabin ta</p><p><br /></p><p> daddy yajuyar da kallon shi ga haydar yace kaifah</p><p><br /></p><p> Sosa keya yayi sannan yace daddy ni ba yanzon ba.</p><p><br /></p><p> sai yaushe?</p><p><br /></p><p> daddy idan na shirya zanyi mgn</p><p><br /></p><p>cikin fada daddy yace baka isaba rana daya zakuyi aure KO kaki KO kaso kanajina?</p><p><br /></p><p>daga kai yayi sannan yace daddy inason zamuyi mgn amman su taslim su fita tukum</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Gaisuwa ta mussaman gareku*</p><p>_matar abbatie barno_</p><p> _hussaina faji_</p><p> _murjanatu_</p><p> _yahancy_</p><p> _hajju_</p><p> &</p><p> _zinat_</p><p>*all in Fadeela Lamido novels group*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>24 - 26</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Daddy ne ya umarci su taslim da fatima da su fita</p><p> </p><p> bayan sun fita daddy yace toh inajinka.</p><p><br /></p><p> saida haydar yayi kasa da murya sannan yace daddy dama shawara zan bada yariyar nan fa be kamata salis ya aure ta ba, dan sai da ta gama yawon ta tukun aka kawo ta gidan nan.</p><p> </p><p> da mamaki daddy da ummi suke kallon haydar </p><p><br /></p><p> daddy yace a ina kaji wannan lbrn ?</p><p><br /></p><p> kanshi tsaye yace yadidko ce ta fadamin</p><p><br /></p><p> sai alokacin salis ya dago kai ya kalli haydar</p><p><br /></p><p> daddy yace hjyr da kanta ta fada maka haka, toh gaskiya bahaka lbrn yake ba kuma ko ba ayi haka ba dama zangawa salis halin da fatima take ciki sannan yajuya barayin ummi yace ke dama tun zuwan fatima gidan nan nafada miki halin da take ciki.</p><p><br /></p><p> kai kuma haydar karna sakejin wannan kallamar abakin ka fatima bata yawo fayd'e aka mata shine dalilin da mahaifiyarta ta kawota.</p><p><br /></p><p> kan salis na kasa har yanzun be dago ba hawaye ne kawai ke zubo masa.</p><p><br /></p><p> ganin halinda salis ya shiga daddy yace wa haydar tashi ka tafi.</p><p><br /></p><p>mikewa yayi yana kallon salis yana mai farin cikin yau ya dana tarkon shi adai dai.</p><p><br /></p><p> yana fita daddy ya mike ya taho kusa da salis hannun shi yasa ya dago kansa ganin fuskar yayi tajike sharkaf da hawaye ahankali ya fara sharemai hawayen sannan yace kayi hakuri babana kar kace wannan abun zaisa ka fasa abinda kayi niya inason ka yadda da kaddara mekyau da mara kyau wannan abinda ya faru da fatima zai iya faruwa DA kanwar ka taslima kuma baza mu so taki aurowa ba saboda wannan dalilin, dan haka ka daure, </p><p><br /></p><p> bece komiba ya mike ummi tace kuma duk abinda haydar zai fada maka karka saurareshi dan na kula so yake ya lalata mgnr.</p><p><br /></p><p> daker ya bude baki yace toh</p><p><br /></p><p> yana fita falo yaga wata yariya ta shigo</p><p> riga da wando ne jikin ta sunyi matukar matseta cikin mamaki yace lfy wa kk nema.</p><p><br /></p><p> cikin hausarta wacce bata fita tace dan Allah Ina Neman haydar ne</p><p><br /></p><p> bece mata komi ba ya yamutsa baki ya shiga daki, yana shiga yacewa haydar kayi bakuwa kaje ka sallameta tunkafin ummi ta fito.</p><p><br /></p><p> atsorece haydar ya fito yana fadi axuciyar shi wacci yar iskar ce zata Jamai masifa</p><p><br /></p><p> yana fita sukai arba da ita, wata budurwar shice wacci suka kwashe kusan shekara biyu basu hadu ba suna hada idon suka sakar wa junan su murmushi cikkin sauri ya kamo hannun tasuka fita</p><p><br /></p><p>salis na lekensu ta window har suka fita sannan ya koma kankujera ya zauna yayi tagumi yana bakincin wannan abu dazai ga wanda yayiwa zahara wanna abu lallai bazasu rabu lfy ba, daren ranar kasa bacci yayi haydar kuwa tunda ya fita sai 7:33am ya dawo lokacin salis ya fito wanka yana kokarin saka riga.</p><p><br /></p><p> yana shigowa ya fara fadin angon fatima meye lbr kodai haryanzon kana kan bakar ka .</p><p> </p><p>banza yayi dashi ya dauki key din motar sa yayi waje</p><p><br /></p><p> haydar ko bayan yayi wanka yau be nufi office ba, gidan su wata budurwar shi yaje ya daukota yakaita dakin anas.</p><p><br /></p><p> ad'akin ya wuni da mubaraka saidare ya maidata gida har ya kama hanyar gida yaji shifa har yanzun hakalin shi be kwanta ba so yake ya sake kasan cewa da wata nan ya fara tunanin wacce yariya zai d'ako wadda zata kwantar mai da sha,awar shi.</p><p><br /></p><p> tunani ya fara yi cikin yan matan shi wad'an da yake harka dasu wan da besan yawan suba dan sufi dozin, kasa tuna ko guda daya yayi sai dai abinda ya bashi mamaki daya fara tunanin girjin fatima yake gani lokacin da takewa salis shagwaba, lashe baki yayi sannan yace inama nine salis na samu damar da yariyar nan takema wannan girgiza kasa daina tunanin fatima yayi dan haka daganan ya wuce mashayar su yasha yayi tatil besabo komawa gida aranar ba sai washe gari.</p><p><br /></p><p> damuwa ya taro yayiwa salis yawa abin duni ya isheshi yau haydar kwana biyu kenan be kwana gida ba yana cikin tunanin nan wayar shi tayi kara yana dubawa yaga anas ne abokin haydar da sauri ya dauka cikin faduwan gaba yace anas ina haydar.</p><p><br /></p><p> daga cen cikin wayar aka bashi amsa gayin nan dama nakiraka ne kazo ka shiga dashi cikin gida bayajin dadi ne, cikin sauri yadar ya mike ya fita.</p><p><br /></p><p> ganin haydar yayi rike ahannun anas idon shi rufe, yana isa gurin warin giya ya daki hancin shi.</p><p>ja yayi da baya daidai lokacin hancin motar daddy ta sawo kai cikin sauri salis ya kama haydar yana kokarin barin wajen dashi, amman ina tuni daddy ya karaso guri yana fadin lfy meya sameshi, salis kasa mgn yayi anas ne yace beda lfy ne</p><p><br /></p><p> daddy na isa gaban haydar yace innalillahi wa inna ilaihir raju,un haydar dama abinda kake kenan .</p><p><br /></p><p> juyar da kallon shi yayi gurin anas yace kamayar dashi inda ka dauko shi nabar makushi kar ya Kara dakowa inda nake na yafeshi acikin 'ya'yana.</p><p><br /></p><p> salis yace dan Allah daddy kayi mai hakuri.</p><p><br /></p><p> kai salis babu abinda ya dameka dan haka maza ka shiga gida, Ku kuma Ku fitar min agida</p><p><br /></p><p>juyawa yayi yana waiwayen dan uwan shi har ya shiga gida.</p><p><br /></p><p> shiko haydar sai dare hakalin shi ya dawo jikin shi anas ya shiga fadamai abinda ya faru.</p><p><br /></p><p> tashin hankali ya shiga sosai nan da nan ya mike ko sallama bema anas ba.</p><p><br /></p><p> gidan alhj yusuf ya nufa ya sameshi zaune yana duba wasu takarddu</p><p><br /></p><p> alhj yusuf yaji mamakin ganin haydar acikin daren nan dan basu cika zuwa gidan shiba sabo da ba mata gareshi ba binshi yayi da kallo sanan yace kai kuma daga Ina?</p><p><br /></p><p> cikin rawar murya yace baba dan Allah ka taimakeni muje kaba Abba hakuri cewa yayi wai Karna kara shigo mishi gida.</p><p><br /></p><p> atakaice alhj yusuf yace me ka masa?</p><p><br /></p><p> kasa magana yayi sai hawayene keta zuba afuskar shi.</p><p><br /></p><p>alhj yusuf ya sake cewa haydar me yasa bakajin maga ne ,alhj ya dade yana fadamin bakajin mgn kana mutukar bata mishi rai, jiya ya gama cemin wata ranama baka kwana agida, haka ne?</p><p><br /></p><p>dukar dakan sa yayi kasa bece komai ba.</p><p><br /></p><p> shima shiru yayi yana kallon haydar zuwacen yace tashi muje </p><p><br /></p><p> bayan sun isa gidan atare suka fito daga cikin motar alhj yusuf ya dafa haydar yace haydar ko dai aure kk so?</p><p><br /></p><p>dasauri ya girgiza kai.</p><p> murmushi alhj yayi sannan suka shiga har falon daddy </p><p><br /></p><p> daddy na ganin su ya mike cikin fada yace</p><p><br /></p><p> meyasa ka shigon min da wannan mashayin cikin gidana.</p><p><br /></p><p>alhj yusuf yajuya ya kalli haydar yace mashayi kuma.</p><p><br /></p><p> eh katon mashayi ne ka tambaye shi giya yake sha.</p><p><br /></p><p> tsayawa alhj yayi shiru daga bisani ya dawo da kallon shi gasu taslim, yace kai ku tashi ku fita, ya juya ya kalli haydar yace kaima jeka dakin Ku.</p><p><br /></p><p> suna fita alhj yace yaya ni inaganin koran haydar bashi bane mafita ai sai abin ya kara lalacewa addu,a zamuyi tayi Allah ya shiryeshi, kuma ni Ina ganin yakamata amai aure kila ta sanadin haka saikaga ya shiryu, haka yayita wa daddy nasiha cikin dabara har ya saki jiki suna hira.</p><p><br /></p><p> bayan kwana biyu salis ne zaune shi da fatima ababban falon gidan suna hira kallon shi fatima tayi ta d'a hannunta tanuna mai yaya wai bakaga nayi lalle bane,</p><p><br /></p><p> nagani Zahara yayi kyau sosai amman ni banason kinayi ki bari sai munyi aure, kinga kayan nan ma na jikin ki da zakiji mgn ta danace ki daina sawa idan kuma zaki saka toh ki daura hijjab akai.</p><p><br /></p><p> turo baki tayi sannan tace waikai badama nayi ma kwalliya saika gwale ni.</p><p> murmushi yayi sannan yace bahaka bane zahara nagani kuma ya burgeni.</p><p><br /></p><p> cikin muryan kuka tace toh ai baka kallaba.</p><p><br /></p><p> ahakali ya mika hannun shi ya rike nata duk 2 yana kallon su ,zuwa cen yayi ajiyar zuciya cikin muryar rada yace zahara. dagowa tayi da sauri ta kalleshi cikin ido. yace hannunki laushi.</p><p><br /></p><p> da sauri ta kwace hannunta tana rufe ido.</p><p><br /></p><p>ahankali ya sake cewa zahara zaki iya gane mutumin da ya keta miki mutuncinki?</p><p> gabanta ne ya fadi dan bata taba zatan salis yasan wannan mgn ba .</p><p><br /></p><p> muryar haydar sukkaji daga bayan su yana fadin toh iidan kasan shi me zaka mai?</p><p><br /></p><p> cikin sauri sukka kalli gurin haydar ne tsaye hannun shi cikin aljjihun shi.</p><p><br /></p><p> salis ya bude baki zayi mgn aka turo kofar falon ,wata budurwa ce agaba bayanta kuma wata matace dagani mahaifiyar yariyar ce</p><p><br /></p><p> suna hada ido da haydar ya zaro ido yace me kika zo yi agidan mu?</p><p><br /></p><p> babu ko alamar tsoro atattare da ita tace niba gurinka nazo ba, nazo ne ingayawa iyayen ka ina dauke da cikin ka</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>27 -29</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sauri ya farajan yariyar yana kokarin barin gidan da ita ummi ce taji hayaniya yayi yawa da sauri ta fito, ganin haydar najan yariyar ta fara dakamai tsawa cikin sauri ya saki yariyar yana mazurai, ummi takalli dadtijuwar matar da suke tare da yariyar tace sannu da zuwa hajiya shigo ki zauna.</p><p><br /></p><p> ba musu tahau kujjera ta zauna fatima da salis ko kallo sukabi yariyar dashi.</p><p><br /></p><p> haydar ko yana jingine jikin bango sai aikawa yariyar harara take</p><p><br /></p><p> ummi ce taji shirun yayi yawa tace baiyawar Allah ban fah ganeki ba.</p><p><br /></p><p> kamar jira matar take tace dama ai bazaki gane ni ba amman ai d'aki haydar bazai ce be gane mu ba, atakai ce dai hajiya Nazo ne na shaida miki 'yata zinat ta dauke da cikin danku haydar</p><p><br /></p><p><br /></p><p>wani zufa me dumi ya karyo ma ummi take ta Fara fadin innalillahi wa Inna ilaihir raju,un maimaitawa taitayi zuwa cen ta daga jajayen idonta ta kalli haydar kanshi akasa yace ummi nifa karya suke min.</p><p><br /></p><p> bata ce komaiba ta mayar da kanta kasa wasu hawaye ne masu dumi suka zubu mata zuwa cen ta miki ta nufi falon alhj salis ne yabi bayan ta yana fadin ummi karki gayamai Dan Allah .</p><p><br /></p><p> waigowa tayi tace salis wannan ba abun da za,abuye bane , dole ne yasan halin da haydar yake ciki dan ni yanzon ban san yadda zanyi da wad'an nan mutane ba, tana fadin haka ta shige dakin.</p><p><br /></p><p> bata dade ba saiga su sunfito tare da daddy yana huce.</p><p><br /></p><p> fatima naganin fitowan daddy tamike ta nufi dakin su cike da tsananin tsanar haydar azuciyar ta.</p><p><br /></p><p> daddy ko kallon haydar yayi cike da bacin rai sannan ya juya ya kalli bakin nasu sannan yace kai haydar fita kabar min gida, ku kuma kutashi ku bishi karku kara gigin nufumin gida da nufin Ku kawo min shege bazan taba karba ba.</p><p><br /></p><p> haydar ne ya bude baki yace daddy nifa karya suke min.</p><p><br /></p><p>idan kasakemin Wata mgn zan illataka ka fita kabar min gida wai gawa yayi barayin matar cikin tsawa yace kutashi ku bishi, cikin rawar jiki suka mike suka fita dan tuni haydar ya fita salis ma mikewa yayi zaibi bayan su </p><p> daddy yace karka fita tsayawa yayi ya jingina kanshi ajikin bango.</p><p><br /></p><p> ummi ko kuka take yi tana fadin alhj wannan hukunci beyi ba, matar tabani tausayi be kamata amata hakaba ,yanzon yaya zatayi kenan?</p><p><br /></p><p> Oho nidai bazan karbi shegeba d'an karamin shi dashi ya lalata rayuwuwar shi, yace na mashi aure ne ban mashi ba? wacce irin jaraba ce wannan yariyar nan ma ai inbanda jaraba ta girmeshi haka daddy yayita fada wata mgnr ma besanin sanda ta fito bakin shi.</p><p><br /></p><p> ummi ko kuka take sosai yayin DA salis ke tsaye jikin bango</p><p><br /></p><p>haydar ko yana fita ko waiwaye babu ya nufi motar shi shiga yayi ya zauna daidai lokacin zinat da mamarta suka fito harara ya wurgawa Zinat itama ta mayar da nata hararan motar shi yaja yabar wajen.</p><p><br /></p><p> yana fita agidan ya fara kuka hawaye ne yake zubomai kaman karamin yaro yana bakin cikin batawa iyayen shi rai da yakeyi amman ya kasa cen zawa, tsawa yayi bakin hanya yayi kuka sosai sannan ya kama hanyar gidan alhj yusuf.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf naganin haydar gabanshi ya fadi sakamako idanuwan shi dasuka kunbura tahowa yayi ya kamashi ya zaunar dashi ya fara tambayan shi me ya faru amman ina haydar babu baki domin kuwa ya kasa cewa komai illah hawaye dake bin kuncin shi.</p><p><br /></p><p>alhj yusuf ne ya lura haydar bazaiyi mgn ba, dan haka ya daga waya ya kira daddy.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> daddy na daukan waya yace au gurin ka ya taho, toh maza ka ko reshi karka sake kabar shi a gidan ka mazinaci ne dan iska .</p><p><br /></p><p> takaicine ya kama alhj yusuf yace yanzo yaya dan daka haifa kake kira da wad'an nan mugayan kalamen.</p><p><br /></p><p>ba d'ana bane ayan zun tunda yace shi d'an iskane na barma duniya kuma kaima karka kuskura ka tareni da mgnr haydar yana fadan haka ya katse wayar.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf ya sauke wayar ya kalli haydar yaga har yanzon hawaye ne a idon sa kamar anbude fanfu</p><p><br /></p><p>ya mayar da kanshi kasa zuwa cen ya d'ago ya kalli haydar sannan yace haydar aure za,amaka kuma ba ina neman amincewan ka bane za ayi auren ne ko kana so ko baka so.</p><p><br /></p><p> *Kuyi hakuri yau banyi typing da yawa ba insha Allahu gobe zanyi me yawa*</p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>30 - 32</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bece komai ba har yanzon kuka yake yana mamakin zinat anya kuwa ba karya suka shirya mai ba domin shi rabon daya ganta ya dade kuma ai bakai tsaye yake shigarta ba.</p><p><br /></p><p> kwanan haydar 2 agidan alhj yusuf zuwa yanzon ya dan saki jikin shi saidai ya dan rame gashi zama agidan ya isheshi dan alhj yusuf ba mata gareshi ba, dan haka gidan babu dadin zama.</p><p><br /></p><p> shima alhj yusuf zaman ya isheshi Dan haka ya fara tunanin dawo da salame saidai be saniba ko haryanzo iyayen nashi nanan akan bakan su.</p><p><br /></p><p> washegari yanufi gidan dada sallama yayi ya shiga dada ta tareshi da Fara,a itako salamatu tana ganin shi ta shige daki bayan sun gaisa da dada shiru sukayi nadan wani lokaci sannan alhj yusuf ya fara fadawa dada kudurin sa.</p><p><br /></p><p> farin cikine ya rufeta har ta kasa boye murnanta daki ta shiga cikin farin ciki amman saita tarar da salamatu tana kuka.</p><p><br /></p><p> tana ganin dada tace dada nifa bazan koma gidan sa ba, shekarana uku da dawowa garin nan betaba lekomuba tunda ya karbi yarshi sau 1 ya barta tazo gidan nan be mason tayi alaka dani sabo da ayanzo bana gaban shi dan haka ni bazan saurareshi ba.</p><p><br /></p><p> fada dada ta fara tana fadin wani irin tunani ne wannan da baki gabanshi aida bezo gidan nan da niyar zai maidaki dakin kiba kikasan dalilin shi nayin haka ki tunafah tunda ya rabu dake haryau beyi aure ba dayake ke butulu ce har kk wannan mgnr toh tashi maza kije ki saurareshi .</p><p><br /></p><p>koda alhj yusuf yayiwa salamatu bayani batace a,aba aman fuskar ta adaure take tam kamar bata dariya dan haka hankalin alhj yusuf ya tashi yace salamatu kodai yanzon baki ra,ayi nane?</p><p><br /></p><p>cikin fushi ta fara zaiyanane mishi kamar yadda ta fadawa dada.</p><p><br /></p><p>farin ciki ne ya kamashi ashe har yanzon yana nan makale azuciyar ta yana murmushi yace Allah ya huce zuciyar ki nayi kuskure kuma ina neman afuwarki ki yafemin kuma idai fatima ce harsai kin haji da ganin ta haka alhj yusuf yayita rarrashi salamtu harta yadda ta amince sannan ya fada Mata shifa baya son abun ya dau lokaci dan haka suka tsaida akan ranar juma,a me zuwa.</p><p><br /></p><p>yana barin gidan gidan mahaifin sa ya nufa ya fada masa kudurin sa.</p><p><br /></p><p> murnace ta kamasu gaba daya har yadidko godiya sukayiwa Allah tare dayiwa dansu fatan alheri.</p><p><br /></p><p> *Ranar juma,a*</p><p><br /></p><p>taslima da fatima zaune adakin su suna hira taslim tace wlh fatima na kosa atsaida ranar bikin ku.</p><p><br /></p><p> tsaki fatima tayi sannan tace</p><p><br /></p><p> nidai gaskiya ban kosa ba keni idan ma naji anyi maganar bikin gabana fadowa yake shima yaya kullu maganar shikenan wai ya kosa ranan nan fah har cewa yayi zai gayawa daddy, waishi hakurin shi ya fara karewa</p><p><br /></p><p><br /></p><p>tintserewa tayi da dariya sannan tace ai yadai fad'amiki ne amman ba iyawa zayiba , da dai yaya haydar ne, sake kallonta tayi sannan tace yauwa sister naga wani abu acikin akwatin ki acikin wani d'an karamin akwati.</p><p><br /></p><p> "murmushi fatima tayi sannan tace eh yaya ne ya bani"</p><p><br /></p><p>" taslim ta sake cewa menene aciki?</p><p><br /></p><p>dafata fatima tayi sannan tace kai taslim kin cika gulma toh nima bansan menene aciki ba kuma yace karna bude sai ranar da akadaura mana aure.</p><p><br /></p><p> cafdi ai inda nice wlh saina bude yasan..........</p><p><br /></p><p> gud'an da ummi ke rangad'awa ne ya dakatar dasu daga hiran mikewa sukayi atare suka fito suna rige rigen tambayan ummi .</p><p><br /></p><p>cikin farin ciki ta dafa fatima tace </p><p> fatima ki godewa Allah yanzon haka mahaifiyar ki tana gidan babanki an mayar da auren su, yazon salis yayi waya yace gashima agidan.</p><p><br /></p><p>wani farinci ne ya kama fatima ta saki murmushi zuwacen kuma ta fashe da kuka.</p><p><br /></p><p>ummi ce ta kamota ta rugume tana fadin haba fatima keda zaki godewa Allah kuma, meye na kuka .</p><p><br /></p><p> saidare salis ya dawo hannun shi rike da ledoji bayan yayi wa ummi sannu da gida ya kalli taslim yace ke Ina zahara?</p><p><br /></p><p> kallon shi tayi sannan tace tana daki, yaya wai meye acikin ledar?</p><p><br /></p><p> "yana tafiya yake fadin inaruwan ki"</p><p><br /></p><p>washegari</p><p><br /></p><p>salis ne ya dauki taslim da fatima zai kaisu gidan alhj yusuf murna ce ba kadan ba azuciyar fatima.</p><p><br /></p><p> suna shiga gidan suka samu haydar kwace akan kujera yana danna wayar shi salis ne ya nufi gurin shi ya kama kafafuwan shi ya d'aga sannan ya zauna agurin tsaki haydar yaja sannan ya tashi ya zauna salis ne yace wa haydar ina mama?</p><p><br /></p><p> atakaice yace tana ciki.</p><p> daidai lokacin salamatu ta fito daga daki fatima ta tashi da sauri ta nufe ta, tureta tayi ta jawo taslim dake bayanta ta rungume sannan tacewa fatima aike babu ruwana dake.</p><p><br /></p><p>komawa tayi kusa da salis ta zauna tana turo baki.</p><p><br /></p><p> kallonta kawai salis yayi ya sunkuwar dakai.</p><p><br /></p><p> mama ko tana rungume da taslim tana tambayan ta karatun ta.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf ne yayi sallama ya shigo zama yayi cikin su bayan sun gaisa ya tashi ya nufi d'aki</p><p><br /></p><p> itama mama mikewa tayi sanna tacewa taslim tashi ki shiga kitchen ki debo muku abinci, tana fad'an haka tashiga d'aki</p><p><br /></p><p> haydar ko sai, satan hararar fatima Yake</p><p><br /></p><p> salis ko kallon fatima yayi yace ke wai baki iya bada hakuri bane?</p><p><br /></p><p> kara turo baki tayi sannan ta kauda Kai, daidai lokacin taslim ta kawo abinci ta ajewa salis nashi sannan tacewa fatima sister zo muci.</p><p><br /></p><p> azuciye tace banzanci ba.</p><p><br /></p><p>" har salis yakai abincin dafda bakinsa yadawo dashi sannan ya kalli fatima yace sabo dame bazakici ba?</p><p><br /></p><p>saida ta kara turo baki sannan tace toh aini batace dani ba kuma saina kamaci sai kace mayya.</p><p><br /></p><p>dariyace taso kubucewa haydar amman sai ya dake yaci gaba da danna wayar shi.</p><p><br /></p><p> salis ma dakewa yayi sannan yace toh ke wai baki iya bada hakuri bane, kitashi maza tun kafin raina ya baci kije ki bata hakuri.</p><p><br /></p><p> mikewa tayi ta fara kuka tana buga kafarta akasa kamar karamar yariya tana fadin nifah ba abinda na mata ni yaushe ma naganta bare na mata wani abu.</p><p><br /></p><p> tun salis na kallon fatima har ya gaji ya rufe idonshi dan ya lura yau fatima so take ta rud'ashi.</p><p><br /></p><p> shiko haydar baki ya saki yana kallon fatima tuni yanayin shi ya fara cenzawa ji yake kamar ya tashi ya rungume ta</p><p><br /></p><p> fatima ce ta lura haydar ita yake kallo dan haka ta tsaya cak tana mamakin shi kuma wannan me yake kallo.</p><p><br /></p><p> salis ko yanajin fatima ta daina kuka ya bude ido cikin bacin rai yace meyasa kike min haka ne zahara dan Allah idai baso kk kijamin fushin Allah ba toh ki dakata da irin wannan abun, kije kiyiwa mama sallama kizo mutafi.</p><p><br /></p><p> sumi sumi ta wuce ta tura dakin mama tana shiga haydar ya kalli salis yace wlh kai wawane d'an kauye.</p><p><br /></p><p> murmushi salis yayi tare da mikewa yana fadin Allah ya shirye ka.</p><p><br /></p><p> zuwacen mama da alhj yusuf suka fito fatima na rike hannun babanta .</p><p><br /></p><p>alhj yusuf yaga salis da taslim tseye yace kardai har zaku wuce?</p><p><br /></p><p> salis ne yabashi amsa eh baba zamu tafi.</p><p><br /></p><p> yace toh daman Ina son ganinku kaida haydar tsakanin ku wanene akace sun daidaita da fatima?</p><p><br /></p><p>da sauri haydar ya d'akai ya kalli salis shima salis d'in kallon shi yayi</p><p><br /></p><p> 🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>33-37</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Alama salis yakewa haydar ya fad'a aman haydar sai make kafad'a yakeyi.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf yace daku nake mgn fa .</p><p><br /></p><p> " taslim ce ta lura salis kunya yakeji dan haka tayi sauri tace baba yaya salis ne.</p><p><br /></p><p>haidar ne ya d'ago kai ya harari taslim yace ke dan ubanki dake ake mgn</p><p><br /></p><p> alhj yusuf yace haydar me yasa bakin ka ya iya furta zagi ne, ai taslim batayi laifi ba abin da tayi kai ya kamata ace kayi amman sai kayi shiru, juyawa yayi ya kalli salis yaga ya dukar dakai yace salis ni dama nasani baban ku ya fad'amin dama naso ne naji daga gareku amman tunda kun kasa magana taslim ta fanshe ku.</p><p><br /></p><p> ya juya ya kalli haydar yace toh kai kuma fah.</p><p><br /></p><p> baba ni bayanzon zanyi aure ba .</p><p><br /></p><p> bata rai baba yayi yace toh sai yaushe?</p><p><br /></p><p> idan salis yayi ni daga baya zanyi.</p><p><br /></p><p> baka isaba kafison kai ta d'ako mana mgn ai ni inda sosamu ne nan da one week kayi aure dan haka duk abinda akeci nan da Wata 1 kawo yariyar da kk so,Dan mun riga mun yake rana nan da wata biyu dan haka kuje kufara shiri.</p><p><br /></p><p>haka suka koma gida cike da farin cike sai dai azuciyar salis ranar da akasa yayi mai yawa</p><p> dan haka da suka kebe da fatima yace zahara gaskiya ranar nan da akasa yayi yawa.</p><p><br /></p><p> haba yaya wata 2 ne yayi yawa toh ni wlh kusa ma naga yayi min dan nifah wlh tsoron ma ranar nakeji.</p><p><br /></p><p> da sauri ya kalleta tsoro kuma toh tsoron me kikeji, kardai ki kecemin tsoron miji kike, toh idai haka ne gara ma tun yanzon ki cire shi dan gaskiya bazaki takurani ba , zahara kinsan fan nayi hakuri</p><p><br /></p><p> haharara shi tayi sannan tace hakuri me kayi?</p><p><br /></p><p> murmushi yayi sannan yace Zahara Kenan kisan fah kina da kyau kuma na kusa najiki jiki na</p><p><br /></p><p>kawai daurewa nakeyi karne abin kunya, kasa ya yayi da murya ya Kira sunanta sannan yace kifah shirya dan idan mukayi aure akan kirjin ki Zan rinqa kwana.</p><p><br /></p><p> hannuta tasa ta rufe ido dan be saba mata irin wannan maganganun ba.</p><p><br /></p><p> murmushi yayi sannan yace zahara idan akace yau andaura mana aure bakaramin farin ciki zanyi ba, bare kuma na ganki ad'akina, Hmmm ranar zan nuna miki irin son da nake miki zan tarairayeki kaman kwai zan nunamiki soyayyar daba kowane namiji bane zai iya nunawa matar sa irin saba.</p><p><br /></p><p> kwashewa fatima tayi da dariya sannan tace amman dai yaya sambatu kk KO, wannan irin cin buri ne haka.</p><p><br /></p><p> shima dariya yayi sannan yace aidama nasan bazaki gane ba amman ahankali zan ganar dake, mikewa yayi tare da fadin bari naje gurin haydar.</p><p><br /></p><p> dasauri tace bayan zon ,muka dawo ba shine har zaka koma, ni wlh natsani haydar d'in nan banason ganin shi.</p><p><br /></p><p> shima cikin mama ya kalleta yace zahara kinada hankali kuwa d'an uwan nawa, meya miki ?</p><p><br /></p><p> toh yaya ai shima ya tsane ni dan haka nima bana sonshi wlh ko sunan shi aka kira gaba na faduwa yakeyi.</p><p><br /></p><p> kallon ta yayi cikin ido yace xahara haydar ba tsanar ki yayi ba haka halinsa yake nima bakiga yana min ba, kuma dan Allah ki yafe masa karki kara kullatan shi aranki kinga d'an uwanki ne , koya miki wani abu kijin haushi toh ki gayamin ni kuma xan faranta miki rai kinji KO ?.</p><p> </p><p> da sauri ta d'aga kai .</p><p><br /></p><p> yace kin yafe masa?</p><p><br /></p><p> eh tace ahankali.</p><p><br /></p><p>Shirye shiryen biki nata kankama acikin wannan family ummi shiri take sosai komai ta gama had'awa da dan ganci na</p><p> fatima dan yazun bikin saura sati 2 kuma har wannan lokacin salis be kawa yariyar da zai aura ba dan haka akabar batunsa dama alhj yusuf ne yaso ahad'a amman daddy tuni yabar zancen haydar kamar yadda yace ya cireshi acikin 'ya'yan shi.</p><p><br /></p><p> haydar ne zaune shida abokin sa anas a harabar gidan su anas sigari kawai yake sha daya shanye wani sai ya kara d'akkowa </p><p><br /></p><p> anas ne ya lura haydar ya kusa shanye kwalin sigarin dauke ragowar yayi sannan yace big boy waikai meke damun ka?</p><p><br /></p><p> yana fesar da hayakin dake bakin shi yana fadin fatima.</p><p><br /></p><p> Hmm daman aikai ya kamata ka aureta sai da fad'a maka kace bahaka ba sai yanzun da lokaci ya kure zakace wani fatima, kana nufin sonta kk?</p><p><br /></p><p> niba sonta nake ba amman ni banason salis ya aure ta, saboda Ina matukar sha,wan yariyar dan haka nafison wani daban ya aure ta, yanzun fah duk tarin 'yan matan dana ke dasu basa birgeni Dana rufe ido fatima nake gani</p><p><br /></p><p>tsaki anas yayi cikin takaici yace toh yanzon dai saidai kayi hakuri garama ka cireta aranka dan tafi karfin ka.</p><p><br /></p><p> tsaki shima yayi yamike yabar wajen tundaga ranar haydar ya zama kamar mara lafiya baya mgn sosai besan me yake damun shiba.</p><p><br /></p><p> Yau sauran kwana biyu biki dan haka yan baki sun fara isowa fatima da taslim sai shirye shirye sukeyi daddy na cikin farin ciki.</p><p><br /></p><p> ummi ce ad'aki zaune da kawayenta suna kallon akwati ta zuwa cen saiga salis rike da hannun haydar ummi ce ta kalli haydar tace meya kawoka?</p><p> </p><p> haydar ne yace ummi ninace yazo yaga akwati.</p><p><br /></p><p> cikin fad'a tace to tunda kai ka kirashi saika shirya amsan da zakaba babanku idan yadawo ya samu haydar agidan na, mikewa tayi tafita adakin ahankali mutane dake dakin suka fita daya bayan daya.</p><p><br /></p><p> haydar ya tsuguna gaban akwati yana dariya yana duba kayan zuwace yace brother kaya sunyi saidai kacika hijjab dayawa aciki.</p><p><br /></p><p> murmushi salis yayi sannan yace ra,ayina kenan.</p><p><br /></p><p> anagobe daurin aure da daddare salis ya shiga har d'akin su fatima fatima ya hango manne jikin gado ta rufe fuskarta gefe ko kawayen su ne zaune suna hira sunna ganin shigowan shi suka bar daki gaban Fatima yaje ya tsuguna dariya yayi sosai sannan yace zahara duk tsoron auren ne haka, </p><p><br /></p><p> batace kome ba ya sake cewa zahara dan Allah ki kwantar da hankali bana son ganinki cikin wannan halin .</p><p><br /></p><p>cikin kuka tace yaya kwata kwata banajin dadi, azuciyata taki natsuwa nayi nayi in natsar da ita nakasa gani nake kamar wani abu zai faru.</p><p><br /></p><p> da sauri yace babu wani abu dazai faru zahara sai alheri kiyi tunani dakau kila akwai abinda yake damunki.</p><p><br /></p><p> shiru tayi zuwacen tace yaya jiya nayi mafarkin na auri yaya haydar.</p><p><br /></p><p> dariya yayi sannan yace ni daman nasan akwai abunda yake damunki dan Allah ki cire tsanar haydar azuciyar ki, kuma kidaina wannan tunanin mafarki ne kawai insha Allahu gobe warhaka burin mu ya cika saida muyi fatan cikawa da imani, haka haydar yayi ta rarrashin fatima harta fara dariya.</p><p><br /></p><p> washe gari aka tashi da shirye shiryen dauren aure tun 12:00 bakin daddy suka fara halara kofar gidan ya ciki makil da jama,a sai hada hada ake salis ne ya fito cikin babban riga farare kal yayi matukar kyau waige ya farayi yana neman haydar amman ko alamar shi begani ba dan haka ya shiga neman no barshi tsaki yaje sabo da layin kwata kwata yaki shiga ya koma cikin abokan sa ya tsaya ranshi bace zucen yaga guri ya kara cika duba agogo yayi yaga karfe 12:43 cikin sauri ya nufi motar shi wani abokin sane yabi bayan sa yana fadin inakuma zaka?</p><p><br /></p><p> yana kokarin barin wajen yace tahir yanzon zandawo zanje na dauko haydar ne.</p><p><br /></p><p> gidasu anas ya nufa yana tura kofar anas dakin yaga haydar zaune ya tasa sigari cikin zafin zuciya yace haydar kana nufin bazaka halarci daurin aure na bane?</p><p><br /></p><p> bece komaiba dan haka yasa hannushi ya fara jawoshi bayan motar ya turashi anas ma ya shiga sun kamo hanya kenan kiran daddy ya shigo wayar salis cikin fada yace kana ina?</p><p> yace daddy ganinan zuwa naje dako haydar n.......</p><p><br /></p><p> salatin dasu anas kiyine ya dakatar da shi yana d'ago kanshi yaga Wata babban mota ta nufosu salis yayi kokarin kaucewa amman Ina tuni motar ta fara watan gaririya akan titi.basu kara sani me ya faru ba</p><p>zucen haydar ya bude ido ganin shi yayi kwace cikin jini muryan salis yaji yana kiran sunan shi daker yaja kashi ya kalli gurin kwance yaganshi jini na bulbulowa ta cikin shi jan jiki ya fara har ya isa gaban shi ya kama hannun shi babu abun yake kira banda zahara zuwace yayi kalmar shada be kara motsawa ba haydar ya farajan shi duk da shima ajikace yake.</p><p><br /></p><p> karan wata mota yaji yana kallon gurin yaga daddy da baba yusuf suna tahowa, gurin salis suka nufa daddy ne ya daga hannun shi yace ya innalillahi wa inna ilaihir raju,un Allah ya karbi abun sa😭😭</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊🕊</p><p>[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p>*Gaisuwa da fatan alheri gare ku*</p><p><br /></p><p>*Zainab bobbo adamawa*</p><p>*Yahancy gombe* </p><p><br /></p><p>*bilkisu muhammad*</p><p><br /></p><p> *xeeshata*</p><p><br /></p><p>*mmn abdulnasir*</p><p><br /></p><p> *hajju lokoja*</p><p><br /></p><p> *Fatyma*</p><p><br /></p><p>*harda wadan da bankira suna ba inajin dadin yadda kuke nuna sayayyar ku ga wannan lbr*😍😍😘</p><p><br /></p><p>38 - 39</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tattara su akayi gaba daya aka nufa asibiti har anas.</p><p><br /></p><p> nan danan wannan mummunan lbr ya isa kofar gidan daddy dake cike da jama,a yan daurin aure.</p><p><br /></p><p> itako ummi daddy ne yamata waya ya gaya mata amman be gayamata rasuwan salis ba yadaice gasu sun wuce asibiti.</p><p><br /></p><p>hakalinta ne yayi mummunan tashi dan ta dade tana munanen mafarkai akan salis da haydar</p><p><br /></p><p> itako fatima tun safe ta kulle kanta ad'aki tana kuka dan haka ummi tace abarta kar agaya mata abari aga abinda allah zaiyi.</p><p><br /></p><p> haka gidan ya zama jugun kowa da abin da yake sakawa.</p><p><br /></p><p> zuwacen daddy ya sake kiran ummi.</p><p><br /></p><p> tana ganin kiran daddy gabanta ya fadi tana dauka tace</p><p><br /></p><p> " alhj yaya abin da sauki kodai na taho ne kuna wanne asibiti?</p><p><br /></p><p> " cikin jarinta irin na maza yace basai kinzo ba muma gamunan tahowa kuma nasan ke musulma ce kin yadda da kaddara mekyau da marakyau.</p><p><br /></p><p>kuka ta fara tace alhj kardai kacemin mutuwa sukayi?</p><p><br /></p><p> "a,a haydar yanan araye sai dai ya samu karaya acinya"</p><p><br /></p><p> kara rushewa tayi da kuka sannan tace salis fah ?</p><p><br /></p><p> cikin shashshekan kuka yace sai dai muyi hakuri hafsat salis ya koma ga mahalicin sa.</p><p><br /></p><p> ummi jitayi kafafuwan ta bazasu iya daukanta ba take ta yar da wayar ta shiga fadin innalillahi wa inna ilaihir raju,in.</p><p><br /></p><p> jin salatin da ummi keyi gaba daya hankalin mutane yadawo gurinta ummi tana kuka tana gaya musu salis ya rasu.</p><p><br /></p><p>fatima dake kule ad'aki kunnen ta ya fara juyo mata koke koke da sauri ta bude kofar ta fito idon ta jajur bisu tayi da kallo daya bayan daya kowa afalon kuka yake.</p><p><br /></p><p> " cikin tsawa tace menene wani abu ne ya faru?</p><p><br /></p><p> Wata yayar ummi ce ta jawo ta jikinta nasiha ta shiga yimata sannan ta gaya mata rasuwan salis.</p><p><br /></p><p> jitayi kamar an buga mata guduma hawaye kuwa kamar an bude fanfu cikin kuka take fadin nashiga uku na lalace meyasa yayimin haka jiya fah yace min yau tare zamu kwana shine kuma zai tafi ya barni kai ban yadda ba be mutu ba,nasan shi me cika alkawari ne.</p><p><br /></p><p> daidai lokacin daddy ya shigo mutane ne abayan sa dauke da gawar salis d'akin ummi aka shigar dashi da sauri fatima ta kutsa ta cikin mazan ta shige d'akin ,hannu tasa ta bude fukar shi girgizashi tayi tana kuka tana fadin yaya katashi dan Allah.</p><p><br /></p><p> daddy na tsaye abayan ta ya kasa cewa komai alhj yusuf ne ya d'agota yace fatima salis yariga ya tafi ki daina mai kuka soyayyar da zaki nunamai yanzun shine kibishi da addu,a</p><p><br /></p><p> wani hawaye ne me dumi ya zubo mata alhj yusuf najanta tana waiwayen gawar salis.</p><p><br /></p><p> bayan angama gyara salis aka kira ummi tamai addu,a cikin kuka tamai addu,a albarka ko tasamai babu adadi, daddy ne yace akira fatima suyi sallama.</p><p><br /></p><p> kamota akayi dan ayanZon bata iya tafiya saitin kunen shi taje babu meji metake cewa.</p><p><br /></p><p> daddy ne yoga abin nata bana kare bane dan haka yace afita da ita </p><p><br /></p><p> haka sunaji suna gani aka tafi da salis gidan sa na gaskiya</p><p><br /></p><p> fatima ko mawa d'akin su tayi ta fashe da kuka kallon hannuta tayi taga zanen fulawa wani haushine ya kamata tunani yadda zatayi ta goge lallen ta fara </p><p><br /></p><p><br /></p><p>dan haka ta fara buga hannun ta ajikin bango tuni kyawawan warwaro dake hannun ta suka lanlan kwashi.</p><p><br /></p><p> dada ce tahigo taga halin da Fatima take ciki da sauri ta riketa tana fadin meye haka fatima saikace ba musulma ba, dan Allah dan darajan annabi ki dainawa bawan Allah nan kuka.</p><p><br /></p><p> suna cikin haka salamatu mahaifiyar fatima ta shigo, fatima ta daga kai tace mama kin ga haydar ya kashe salis KO ?</p><p><br /></p><p> cikin tsawa mama tace waye yace miki haka, kifah dai na irin wannan surutun ki kama bakin ki, haydar d'in da kike mgn shima yana cen akwance bemasa inda yake ba.</p><p><br /></p><p> cikin kuka tace</p><p><br /></p><p> " ai dama bazai san inda yake ba kuma da ikon Allah shima mutuwa zaiyi"</p><p><br /></p><p> cikin zafin zuciya mama ta nufi gurin ta gadan gadan</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[10:36AM, 3/31/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> ( ta wuya ake kamashi)</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>17-20</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Taslim ce ta zaro ido dan tunda suke da haydar betaba kaita unguwa ba fatima ko idonta ne ya cika da hawaye dan ko muryar haydar taji sai cikinta ya murd'a</p><p><br /></p><p><br /></p><p>salis ya lura da halin da suka shiga ci dan haka yace haydar ai inaga kubar tafiyar nan sai gobe dan nalura zahara batajin dadi sosai </p><p><br /></p><p> ysaki haydar yayi ya bar wajen.</p><p><br /></p><p> da dadare anas ya kawowa haydar ziyara har dakin ummi yaje ya gaisheta domin shi ba bako bane agidan adakin ya samu salis dan haka ya dan zauna suna hira bayan sundan taba hira anas ya nufi dakin su haydar </p><p><br /></p><p> hira suka barke acikin hiran tasune haydar yake cewa anas akwai wata yariyar kanin daddy da ta dawo gidan nan tana min kama da yariyar nan da na huta da ita a wannan kauyen.</p><p><br /></p><p> dariya anas yayi sannan yace kace dai yariyar nan tasamu matsayi tunda gashi har gizo take maka</p><p><br /></p><p> yatsuna fuska yayi sannan yace bahaka bane anas kaima nasan idan ka ganta zaka gane tsananin kamar su.</p><p><br /></p><p> suna cikin haka taslim tashigo da kula ahanun ta ta ajiye agaban anas tace gashi injji ummi.</p><p><br /></p><p> hayadar yace ke ina wannan yariyar ?</p><p><br /></p><p> wacece fatima?</p><p><br /></p><p> tsawa ya daka mata dan ubanki ina tambayanki kina tambaya na, koni sa,an wasanki ne</p><p><br /></p><p>yamusha fuska tayi sannan tace toh ai ban gane wacce kake mgn bane idan fatima ce tana dakin ummi.</p><p><br /></p><p> atakai ce yace jeki kirata</p><p><br /></p><p>zuwa cen saigata ta shigo tare da sallama tsugunawa tayi akasa dan balakin tsoron haydar take ta bude baki ahankali tace yaya haydar taslim tace kana kirana.</p><p><br /></p><p>be dago ya kalleta ba cigaba yayi da danna wayar shi cikin kasaita ya bude baki yace ke baki ganin bakone bazaki gaida shiba nifa ba salis bane wlh saina zaneki dan ni bana daukan raini.</p><p><br /></p><p> shikuwa anas har yanzon be kalle fatima ba illa cin abincin da yake dan haka lokacin data gaida shi ya dago kai ya kalleta.</p><p><br /></p><p> sakin abincin yayi ya fadi kasa ya mike da sauri</p><p><br /></p><p> ganin inda anas ya rude yasa shi yace ke tafi kiba ni guri</p><p><br /></p><p> tana fita anas yace wlh itace kai anya kuwa yariyar nan ba aljana bace.</p><p><br /></p><p> musu suka fara haydar na fadin kamace yayin da anas yace itace.</p><p><br /></p><p> ganin da anas yayi musun yaki karewa sai ya bude wayar shi ya bude hoton da ya dauki yariyar lokacin tana kwace amotar haydar zuwa yayi daf da haydar yanuna mai photo.</p><p><br /></p><p> karban wayar yayi ya shiga kallon hoton, wayar shi ya jawo ya tura sannan yayi delete na wayar anas cikin tashin hakali yace zanyi bincike akanta.</p><p><br /></p><p> shiru sukayi gaba dayan su kowa da abinda yake sakawa.</p><p><br /></p><p> aranan haydar yaje gurin kakar su yadidko tsayawa yayi ahanya yasai mata lemo dan yasan idan tana shan Orange saitai zuba zance.</p><p><br /></p><p> murna tayi sosai daganin haydar da kansa ya yanka mata lemon ta fara sha tana zubo masa wani lbrn daban .</p><p><br /></p><p> yana ganin haka ya fara saita mata hanya niba wannan ba hajiya nifa gaskiya fatima na bani tausayi ace yariya kamarta tana jss1 waisu toh garin su ba asa yara makaranta ne?</p><p><br /></p><p> cikin takaici tace ai bari kawai haydar baban ta ma yana bakin cikin wannan abu amma ai uwarta ce sula haka kawai ta dauki yariya ta kaita kauyen kayayau ko mota bata iya shiga.</p><p><br /></p><p> daukan wani lomon yayi yamika mata sannan yace kina nufin kauyen babu mota.</p><p><br /></p><p> saidata matsa ruwan lemon abakin ta sannan tace inafah suka ganta ai wanda ma ya keta mata mutuncin ta badan garin bane dan ita saima allokacin tasan sunan mota nandai ta kwashe komai ta gayawa haydar.</p><p><br /></p><p> haka haydar ya baro gidan cike da tashin hankali, yana fadi azuciyar shi lallai nayi abin kuya yazon wani hali </p><p>iyayen mu zasu shiga idan sukaji nine na aikata Wannan abun gashi yaji kakar tasu sai fadan mugayan kalamai take ga Wanda ya aikata ma jikarta wannan aika aika</p><p><br /></p><p>gidan su anas ya nufa ya labarta masa cin matsanan cin tashin hankali ya mike yace </p><p><br /></p><p> " toh yanzon sai ka aureta kawai haka shine abinda ya dace saida nace maka karka taba ta amman kakiji kaga da duk haka bata faru ba"</p><p><br /></p><p> cikin zafin zuciya haydar yace dallah gafara ina neman mafita kuma zakawo min wata magana daban banason irin wannan.</p><p><br /></p><p> toh shi kenan tonda bakason agayam gaskiya amman ni bazan kara zuwa gidan ku ba dan idan daddyn ku yasamu wannan lbr harni saina shiga ciki.</p><p><br /></p><p> aniyarka ta bika in Allah ya yadda daddy bazaiji wannan maganar ba kuma kai nifa bazanma bari taci gaba da zama agidan muba saina san haryar da zanbi tabar gindan nan wlh dama tunda naganta agidan mu naji natsaneta gashi naga salis kaman sonta yake yi amman nasan abinda zanyi.</p><p><br /></p><p> shiko anas kallo yabi haydar dashi yanason yaba abokin nashi shawara amman yasan yanzon sai su kwashi yan kallo dan haka yayi gum.</p><p><br /></p><p> *********</p><p><br /></p><p> bayan haydar ya koma gida dakin su ya nufa ya cire kayan dake jikinshi sannan ya dauki jallah biyar salis ya saka ya haye gado ya kunna sigari yana sha</p><p><br /></p><p> zuwacen salis ya shigo yakali hayadar yayi tsaki cikin takaici ya fara magana wato dan iskanci ma yanzon har adakin ma shan sigari kake toh wlh abun ya isa haka bazan iyaba zan fadawa daddy.</p><p><br /></p><p> </p><p>kashe sigarin yayi ya mike yaje har gaban salis sannan yace baka isa ka hanani shan sigari adakin nan ba kai Ina hanaka kayi wani abu dakin nan ne ? , abin da kaga dama kakeyi dan haka baka isaba wlh.</p><p><br /></p><p> toh naji ban isaba amman me yasa </p><p>ka saka min daya daga cikin rigar da nake sallah da ita bayan kasan ni bashan sigari nake ba kuma ina kyamar me Shanta</p><p><br /></p><p> Kara matsowa yayi dafda shi yace</p><p><br /></p><p> " nasa din kayi abinda zakayi "</p><p><br /></p><p> ran salis ya bacci idon shi yayi jawur kallon haydar kawai yake zuwa cen yayi kwafa sannan yace wlh darajan ummi kake ci dan banason na tayar mata da hankali amman ba komai wata rana zanyi maganin kka</p><p><br /></p><p> yana fadin haka haydar ya kamo wuyar rigar shi yahada ya matse yace </p><p><br /></p><p> " dan Allah idan kacika kai jarumi ne kayi maganina yau basai wata ranba"</p><p><br /></p><p> rufe ido salis yayi zuwacen yace sakeni.</p><p><br /></p><p> cikin daga murya yace bazan sakeka ba</p><p><br /></p><p> salis gani yayi haydar na neman kure shi dan haka yasa hannun shi ya hankad'a shi ya fadi kasa cikin sauri ya bar dakin.</p><p><br /></p><p> falon daddy ya nufa ranshi bace, aciki ya samu ummi bayan ya zauna ummi tace</p><p><br /></p><p> lfy kuwa yanzon ka fita kana dariya kuma naga kadawo ranka bace wani abu ya faru ne?</p><p><br /></p><p> a,a babu abinda ya faru ummi amman dai inason dan Allah araba mana daki nida haydar</p><p><br /></p><p> daddy ya dago da sauri ya kalli shi, sannan yace kunyi fada ne?</p><p><br /></p><p> kanshi akasa yace bahaka bane kawai dai nafison ne na zauna ni daya</p><p><br /></p><p> murmushi daddy yayi sannan ya daga waya ya kira haydar, ba adade ba saiga haydar ya shigo atsora ce dan yazaci ko salis ya fadi abinda ya faru ne .</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>_©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Gaisuwa ta musamman ga duk wanda yake cikin wannan group *Farfazaz novels* _kunfi ko wani group comment da nuna soyayyar ku akan wannan lbr Tsuntsu me wayo inajin dadin kasan cewa daku_ 💃💃💃😘</p><p><br /></p><p><br /></p><p>21 - 23</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zama yayi nesa da salis kanshi akasa dan duk abin shi yana tsoron daddy shi ahankali yace gani.</p><p><br /></p><p> daddy ya dago ya kalleshi yasa hannu ya cire gilas din dake idon shi sannan yace me ya had'a ku ?</p><p> </p><p> d'ago kai yayi ya kalli salis ya sake mayar da kanshi kasa yayi shiru.</p><p><br /></p><p> ummi tace wai ba dakai ake mgn ba ne</p><p><br /></p><p> bece komai ba kuma har yanzo kansa na kasa.</p><p><br /></p><p> daddy yace kyale su tun da bazasu fada ba ai sunfi kusa, amman nasan haydar ne baidan gsky wata kila ka kule shi ne amman ni araina banason kuraba daki nafiso sai kunyi aure kowa ya samu abokiyar zama ko ya kuka gani?</p><p><br /></p><p> haydar ne ya fara magana daddy ai ko munyi aure gida daya zamu zauna.</p><p><br /></p><p> cikin sauri salis yace dawa dakai Allah ya kiyaye wlh ba zan zauna dakai ba.</p><p><br /></p><p> sakin baki haydar yayi yana kallon salis sannan yace salis nine fah.</p><p><br /></p><p> fuskar salis adaure yace kaidin fah ina hauka ne zan zauna dakai.</p><p><br /></p><p> daga daddy har ummi basuji dadin maganar salis ba, </p><p><br /></p><p> ummi ta juyo da kallon ta gurin salis tace </p><p><br /></p><p> " ni bansan ka da fushi haka ba banji dadin mgnr ka ba idan baka zauna da dan uwan kaba dawa zaka zauna banajin dadin ganin ku cikin wannan halin dan Allah ku zauna lfy.</p><p><br /></p><p> juyawa tayi gurin haydar ta harareshi sannan tace kai kuma kabashi hakuri dan nasan kaine mara gaskiya.</p><p><br /></p><p> ahankali yace kayi hakuri in Allah ya yarda bazan kara ba.</p><p><br /></p><p> har yanzon fuskar salis adaure take dan haka daddy ya kira su gaban shi kama hannun su yayi ya hada yace ya wuce kutashi ku tafi.</p><p><br /></p><p> suna rike da hannun juna suka fita.</p><p><br /></p><p> ummi ta dawo da kallonta gurin daddy sannan tace</p><p><br /></p><p> " salis akwai hakuri amman idan ransa ya baci be iya fushi ba shiko haydar idan be nemi fitana ba bayajin dadi.</p><p><br /></p><p> ajiyar zuciya daddy yayi sannan yace Allah ya shirye su.</p><p><br /></p><p> haka rayuwa taci gaba da kasancewa agidan alhj kasim tsakanin salis da haydar yau ayi fada gobe ashirya zuwa anjjima kaga kamar basune suka yi ba.</p><p><br /></p><p> kwanci tashi ba wuya wajan Allah dan yanzon kusan shekara fatima uku aku agidan, zuwa wannan lokacin shakuwa ce me karfe tsakanin fatima da salis.</p><p><br /></p><p> yayin da haydar ya hura wutar kiyayar fatima azuciyar shi dan ko mgn bata hadasu da ita</p><p><br /></p><p> duk da cewa ayanzon idan ka kalli fatima baza taba cewa tayi zaman kauye ba </p><p><br /></p><p>acin wad'an nan shekarun so daya babanta ya kaita gurin mahaifiyar ta yanzon fatima tana ajin karshi na secondary sakamakon kwanya da Allah ya bata.</p><p><br /></p><p> ta bangaren ummi kuwa wato mahaifiyar su haydar bata nunawa fatima wani banbanci tsakanin ta dasu haydar dan haka tana cikin kwanciyar hankali matsalar ta daya haydar.</p><p><br /></p><p>ayanzun dai fatima ta zama cikekiyar budurwa komai na jikin ta ya fito sosai </p><p><br /></p><p> fatima ce kwace jikin kakarta yadidko tana danna waya yayin da taslim tana gefe tana cin abinci suna fira da taslim.</p><p><br /></p><p> sallaman alhj yusuf ya katsa musu hira, bayan yazaunaya kalli fatima dake jikin mahaifiyar shi yace ke ashe baki da hankali katuwarki dake zaki kwanta mata ajiki, yajuya ya kalli taslim sannan yace ke kuma bakiyi mata fada.</p><p><br /></p><p> murmushi taslim tayi sannan tace baba tausa fah take mata.</p><p><br /></p><p> hararanta yayi sannan yace wai ma me kukeyi agidan nan yau kusan 3 days kenan inaganin ku anan ku koma gidan ku mana.</p><p><br /></p><p> taslim ce ta amasa munzo tayata zama ne ai yauma zamu wuce.</p><p><br /></p><p> yace gara dai kutafi hira sukaci gaba dayi shi da yadidko.</p><p><br /></p><p> zuwa cen su fatima suka fito cikin shirin ta fiya alhj yusuf ne ya kawosu har gida bayan sun gaisa da ummi ya wuce.</p><p><br /></p><p> washegari fatima nata zuba ido taga shigowar salis har wan 12 na rana bata ganshi ba dan haka ta shiga neman layin shi saida ta kira su uku ba adauka ba dan haka tashiga damuwa.</p><p><br /></p><p> lokacin da taslim ta kawo musu abincin rana kasa ci tayi tana juya cukalin.</p><p><br /></p><p> taslim tace sister wai meke damun ki tun jiya naga duk kinyi wani iri.</p><p><br /></p><p> meko ni bawani abunda yake damu na.</p><p><br /></p><p> taslim shiru tayi taci gaba da cin abincin ta.</p><p><br /></p><p> bayan sungama dakin ummi suka nufa suna shiga fatima tace</p><p><br /></p><p> ummi wai yaya salis baya nanne?</p><p><br /></p><p> eh bayanan bakuyi waya bane halan?</p><p><br /></p><p> tace nakirashi yaki dagawa.</p><p><br /></p><p>ummi tayi murmushi tace kila baya kusa da wayar ne, munyi waya danzon yace min suna hanya.</p><p><br /></p><p> dariya taslim tayi tace dama shi yasa kika ki cin abinci wai ku soyayya kuke ne?</p><p><br /></p><p> fatima ce ta harari taslim sannan tace wani irin soyayya.</p><p><br /></p><p> ummi tace ke rabu da ita neman mgn ne da ita.</p><p><br /></p><p> dariya taslim ta sakeyi sannan tace wlh ummi soyayya sukeyi.</p><p><br /></p><p> daure fuska ummi tayi sannan tace wai taslim ina wasa dake ne nace kibar mgnr ina ruwanki da su.</p><p><br /></p><p> hannu tasa ta rufe bakinta sannan tace na bari ummi.</p><p><br /></p><p> daidai lokacin salis da haydar suka shigo bayan sun gaisa da ummi fatima gaida su haydar kadai ne ya amsa shima dan yaga ummi ne hakalin fatima ya kara tashi idonta ya cika da hawaye</p><p><br /></p><p> ummi ta lura da halin da fatima take ciki bata dai ce komai ba dan bata faye son shiga tsakanin su ba</p><p><br /></p><p>basu dade ba suka fita zuwa dakin su, fatima ko na gefe tayi tagumi.</p><p><br /></p><p> ummi ta juya ta kalleta tace</p><p><br /></p><p> fatima cire tagumin nan tashi maza ki kai musu abinci.</p><p><br /></p><p> har ta dauki abincin ta tuna salis beson ya ganta babu hijjab dan haka ta koma dakin ummi ta dauki hijjab ta fita.</p><p><br /></p><p> samun su tayi zaune haydar na nunawa salis wani abu acikin wayar shi sunata dariya aje abincin tayi tajuya har takai kofa haydar yace ke dauki ledar cen ki kaiwa ummi.</p><p><br /></p><p> dawowa tayi ta dauka ta fita, kafin takai dakin ummi hayawaye ya fara zubo mata saida ta share hawayen ta shiga dakin ummi ta aje ledar ta koma kusa da taslim ta zauna ummi ta bita da kallo batace komai ba ta mike ta fita.</p><p><br /></p><p> dakin su haydar ta shiga cikin mamaki</p><p> suke kallonta.</p><p> kallon salis tayi sannan tace waikai yaushe aka daura maka aure da fatima ne bansani ba</p><p><br /></p><p> da mamaki yace ummi bangane me kk nufiba.</p><p><br /></p><p> aidama bazaka gane ba kawai dan fatima ta tafi gidan hajiya bata fada makaba kk wannan fushin, matarka ce?</p><p><br /></p><p> da sauri ya girgiza Kai.</p><p>ummi ta sake cewa toh karage wadan nan dokokin takasa mata suyi yawa kuma kazo ka rarasheta</p><p><br /></p><p>adakin su ya sameta tana kwance tayi rufda ciki ahankali ya kira sunan ta amsawa tayi batare data waigo ba ya sake cewa toh tashin mana.</p><p><br /></p><p> kintashi tayi dan batason yaga idon ta</p><p> gaban gadon yaje ya zauna yace zahara tashi mana kosai nakira ummi ne?</p><p><br /></p><p>tanajin ya kira sunan ummi ta miki ta fara sakkowa daga gadon binta yayi da kallo dan rabon da ya ganta babu hijjabi ya manta sai yaga ta kara kyau bayan ta zauna ya kalleta yace wato abin harda su kuka?</p><p><br /></p><p> cikin muryan kuka tace toh bakai bane kake fushi dani.</p><p><br /></p><p> cikin sauri yace nabari indai nine banason nasake ganin hawayen ki </p><p><br /></p><p>daidai lokacin haydar ya shigo dakin abakin kofa ya tsa dan haka salis ne kawai yaga shigowan shi</p><p><br /></p><p>juyawa yayi barayin fatima yace tashi muje gurin ummi.</p><p><br /></p><p> tana mikewa yace toh kisa hijjab mana.</p><p><br /></p><p> buga kafa ta fara kamar karamar yarinya cikkin shagwaba tace ni gaskiya a,a nan da dakin ummi saina saka hiijjbi.</p><p><br /></p><p>binta yayi da kallo zuwacen yayi murmushi yace ji abinda kikeyi saikace wata karamar yarinya </p><p><br /></p><p> kara shagwabewa tayi </p><p><br /></p><p> haydar ko dake bakin kofa tuni ya Fara rikicewa dan babu abinda yafi tayar mai da hankali kamar yaga mace tana wannan shagwaban, idon shi nakan kirjinta </p><p><br /></p><p> salis kuwa ji yake kamar ya rungumita dan betabajin irin yanayin da yaji yau ba, juyawa yayi ya kalli haydar yace waikai wani gulman ne ya kawoka</p><p><br /></p><p> sai alokacin fatima tasan da shigowan haydar juyar da kallonta tayi gareshi </p><p><br /></p><p> yace ke dena kallona munafuka kawai me suffar aljanu</p><p><br /></p><p> salis yakalleshi ya karasa gaban shi sannan yace muje </p><p><br /></p><p> *******</p><p>da daddare duk yan gidan ne suka hadu a falon daddy suna hira zuwa cen daddy yace mun kusa shan biki agidan nan.</p><p><br /></p><p> Ummita tace dama kuwa inason nama magana tunda su sunki yi .</p><p> cikin sauri salis yamike zaibar wajen. alhj yace inakuma zaka dawo ka zauna </p><p><br /></p><p> bayan yazauna daddy yace yakamata kuyi aure salis kaida nake ma ganin ka kamar me hankali.</p><p><br /></p><p> ummi tace alhaji ai haydar zakawa mgn shi yariga ya kama tashi gatanan kusa da kai duk da dai ba fada sukayi ba amman duk me hakali yasan sun amice da juna</p><p><br /></p><p> murna ce ta kama daddy yace toh shine ni baki sanar min ba</p><p><br /></p><p> dawai inajira ne su fada da bakin su gatanan ansa mata takunkumi zama da hijjab saikace matar liman </p><p><br /></p><p> taslima ta kwashe da dariya shikuwa salis tunda ya dukar da kansa ya kasa dagowa fatima ma tana kudun dune cikin hajjabin ta</p><p><br /></p><p> daddy yajuyar da kallon shi ga haydar yace kaifah</p><p><br /></p><p> Sosa keya yayi sannan yace daddy ni ba yanzon ba.</p><p><br /></p><p> sai yaushe?</p><p><br /></p><p> daddy idan na shirya zanyi mgn</p><p><br /></p><p>cikin fada daddy yace baka isaba rana daya zakuyi aure KO kaki KO kaso kanajina?</p><p><br /></p><p>daga kai yayi sannan yace daddy inason zamuyi mgn amman su taslim su fita tukum</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p>[8:17PM, 3/24/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Gaisuwa ta mussaman gareku*</p><p>_matar abbatie barno_</p><p> _hussaina faji_</p><p> _murjanatu_</p><p> _yahancy_</p><p> _hajju_</p><p> &</p><p> _zinat_</p><p>*all in Fadeela Lamido novels group*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>24 - 26</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Daddy ne ya umarci su taslim da fatima da su fita</p><p> </p><p> bayan sun fita daddy yace toh inajinka.</p><p><br /></p><p> saida haydar yayi kasa da murya sannan yace daddy dama shawara zan bada yariyar nan fa be kamata salis ya aure ta ba, dan sai da ta gama yawon ta tukun aka kawo ta gidan nan.</p><p> </p><p> da mamaki daddy da ummi suke kallon haydar </p><p><br /></p><p> daddy yace a ina kaji wannan lbrn ?</p><p><br /></p><p> kanshi tsaye yace yadidko ce ta fadamin</p><p><br /></p><p> sai alokacin salis ya dago kai ya kalli haydar</p><p><br /></p><p> daddy yace hjyr da kanta ta fada maka haka, toh gaskiya bahaka lbrn yake ba kuma ko ba ayi haka ba dama zangawa salis halin da fatima take ciki sannan yajuya barayin ummi yace ke dama tun zuwan fatima gidan nan nafada miki halin da take ciki.</p><p><br /></p><p> kai kuma haydar karna sakejin wannan kallamar abakin ka fatima bata yawo fayd'e aka mata shine dalilin da mahaifiyarta ta kawota.</p><p><br /></p><p> kan salis na kasa har yanzun be dago ba hawaye ne kawai ke zubo masa.</p><p><br /></p><p> ganin halinda salis ya shiga daddy yace wa haydar tashi ka tafi.</p><p><br /></p><p>mikewa yayi yana kallon salis yana mai farin cikin yau ya dana tarkon shi adai dai.</p><p><br /></p><p> yana fita daddy ya mike ya taho kusa da salis hannun shi yasa ya dago kansa ganin fuskar yayi tajike sharkaf da hawaye ahankali ya fara sharemai hawayen sannan yace kayi hakuri babana kar kace wannan abun zaisa ka fasa abinda kayi niya inason ka yadda da kaddara mekyau da mara kyau wannan abinda ya faru da fatima zai iya faruwa DA kanwar ka taslima kuma baza mu so taki aurowa ba saboda wannan dalilin, dan haka ka daure, </p><p><br /></p><p> bece komiba ya mike ummi tace kuma duk abinda haydar zai fada maka karka saurareshi dan na kula so yake ya lalata mgnr.</p><p><br /></p><p> daker ya bude baki yace toh</p><p><br /></p><p> yana fita falo yaga wata yariya ta shigo</p><p> riga da wando ne jikin ta sunyi matukar matseta cikin mamaki yace lfy wa kk nema.</p><p><br /></p><p> cikin hausarta wacce bata fita tace dan Allah Ina Neman haydar ne</p><p><br /></p><p> bece mata komi ba ya yamutsa baki ya shiga daki, yana shiga yacewa haydar kayi bakuwa kaje ka sallameta tunkafin ummi ta fito.</p><p><br /></p><p> atsorece haydar ya fito yana fadi axuciyar shi wacci yar iskar ce zata Jamai masifa</p><p><br /></p><p> yana fita sukai arba da ita, wata budurwar shice wacci suka kwashe kusan shekara biyu basu hadu ba suna hada idon suka sakar wa junan su murmushi cikkin sauri ya kamo hannun tasuka fita</p><p><br /></p><p>salis na lekensu ta window har suka fita sannan ya koma kankujera ya zauna yayi tagumi yana bakincin wannan abu dazai ga wanda yayiwa zahara wanna abu lallai bazasu rabu lfy ba, daren ranar kasa bacci yayi haydar kuwa tunda ya fita sai 7:33am ya dawo lokacin salis ya fito wanka yana kokarin saka riga.</p><p><br /></p><p> yana shigowa ya fara fadin angon fatima meye lbr kodai haryanzon kana kan bakar ka .</p><p> </p><p>banza yayi dashi ya dauki key din motar sa yayi waje</p><p><br /></p><p> haydar ko bayan yayi wanka yau be nufi office ba, gidan su wata budurwar shi yaje ya daukota yakaita dakin anas.</p><p><br /></p><p> ad'akin ya wuni da mubaraka saidare ya maidata gida har ya kama hanyar gida yaji shifa har yanzun hakalin shi be kwanta ba so yake ya sake kasan cewa da wata nan ya fara tunanin wacce yariya zai d'ako wadda zata kwantar mai da sha,awar shi.</p><p><br /></p><p> tunani ya fara yi cikin yan matan shi wad'an da yake harka dasu wan da besan yawan suba dan sufi dozin, kasa tuna ko guda daya yayi sai dai abinda ya bashi mamaki daya fara tunanin girjin fatima yake gani lokacin da takewa salis shagwaba, lashe baki yayi sannan yace inama nine salis na samu damar da yariyar nan takema wannan girgiza kasa daina tunanin fatima yayi dan haka daganan ya wuce mashayar su yasha yayi tatil besabo komawa gida aranar ba sai washe gari.</p><p><br /></p><p> damuwa ya taro yayiwa salis yawa abin duni ya isheshi yau haydar kwana biyu kenan be kwana gida ba yana cikin tunanin nan wayar shi tayi kara yana dubawa yaga anas ne abokin haydar da sauri ya dauka cikin faduwan gaba yace anas ina haydar.</p><p><br /></p><p> daga cen cikin wayar aka bashi amsa gayin nan dama nakiraka ne kazo ka shiga dashi cikin gida bayajin dadi ne, cikin sauri yadar ya mike ya fita.</p><p><br /></p><p> ganin haydar yayi rike ahannun anas idon shi rufe, yana isa gurin warin giya ya daki hancin shi.</p><p>ja yayi da baya daidai lokacin hancin motar daddy ta sawo kai cikin sauri salis ya kama haydar yana kokarin barin wajen dashi, amman ina tuni daddy ya karaso guri yana fadin lfy meya sameshi, salis kasa mgn yayi anas ne yace beda lfy ne</p><p><br /></p><p> daddy na isa gaban haydar yace innalillahi wa inna ilaihir raju,un haydar dama abinda kake kenan .</p><p><br /></p><p> juyar da kallon shi yayi gurin anas yace kamayar dashi inda ka dauko shi nabar makushi kar ya Kara dakowa inda nake na yafeshi acikin 'ya'yana.</p><p><br /></p><p> salis yace dan Allah daddy kayi mai hakuri.</p><p><br /></p><p> kai salis babu abinda ya dameka dan haka maza ka shiga gida, Ku kuma Ku fitar min agida</p><p><br /></p><p>juyawa yayi yana waiwayen dan uwan shi har ya shiga gida.</p><p><br /></p><p> shiko haydar sai dare hakalin shi ya dawo jikin shi anas ya shiga fadamai abinda ya faru.</p><p><br /></p><p> tashin hankali ya shiga sosai nan da nan ya mike ko sallama bema anas ba.</p><p><br /></p><p> gidan alhj yusuf ya nufa ya sameshi zaune yana duba wasu takarddu</p><p><br /></p><p> alhj yusuf yaji mamakin ganin haydar acikin daren nan dan basu cika zuwa gidan shiba sabo da ba mata gareshi ba binshi yayi da kallo sanan yace kai kuma daga Ina?</p><p><br /></p><p> cikin rawar murya yace baba dan Allah ka taimakeni muje kaba Abba hakuri cewa yayi wai Karna kara shigo mishi gida.</p><p><br /></p><p> atakaice alhj yusuf yace me ka masa?</p><p><br /></p><p> kasa magana yayi sai hawayene keta zuba afuskar shi.</p><p><br /></p><p>alhj yusuf ya sake cewa haydar me yasa bakajin maga ne ,alhj ya dade yana fadamin bakajin mgn kana mutukar bata mishi rai, jiya ya gama cemin wata ranama baka kwana agida, haka ne?</p><p><br /></p><p>dukar dakan sa yayi kasa bece komai ba.</p><p><br /></p><p> shima shiru yayi yana kallon haydar zuwacen yace tashi muje </p><p><br /></p><p> bayan sun isa gidan atare suka fito daga cikin motar alhj yusuf ya dafa haydar yace haydar ko dai aure kk so?</p><p><br /></p><p>dasauri ya girgiza kai.</p><p> murmushi alhj yayi sannan suka shiga har falon daddy </p><p><br /></p><p> daddy na ganin su ya mike cikin fada yace</p><p><br /></p><p> meyasa ka shigon min da wannan mashayin cikin gidana.</p><p><br /></p><p>alhj yusuf yajuya ya kalli haydar yace mashayi kuma.</p><p><br /></p><p> eh katon mashayi ne ka tambaye shi giya yake sha.</p><p><br /></p><p> tsayawa alhj yayi shiru daga bisani ya dawo da kallon shi gasu taslim, yace kai ku tashi ku fita, ya juya ya kalli haydar yace kaima jeka dakin Ku.</p><p><br /></p><p> suna fita alhj yace yaya ni inaganin koran haydar bashi bane mafita ai sai abin ya kara lalacewa addu,a zamuyi tayi Allah ya shiryeshi, kuma ni Ina ganin yakamata amai aure kila ta sanadin haka saikaga ya shiryu, haka yayita wa daddy nasiha cikin dabara har ya saki jiki suna hira.</p><p><br /></p><p> bayan kwana biyu salis ne zaune shi da fatima ababban falon gidan suna hira kallon shi fatima tayi ta d'a hannunta tanuna mai yaya wai bakaga nayi lalle bane,</p><p><br /></p><p> nagani Zahara yayi kyau sosai amman ni banason kinayi ki bari sai munyi aure, kinga kayan nan ma na jikin ki da zakiji mgn ta danace ki daina sawa idan kuma zaki saka toh ki daura hijjab akai.</p><p><br /></p><p> turo baki tayi sannan tace waikai badama nayi ma kwalliya saika gwale ni.</p><p> murmushi yayi sannan yace bahaka bane zahara nagani kuma ya burgeni.</p><p><br /></p><p> cikin muryan kuka tace toh ai baka kallaba.</p><p><br /></p><p> ahakali ya mika hannun shi ya rike nata duk 2 yana kallon su ,zuwa cen yayi ajiyar zuciya cikin muryar rada yace zahara. dagowa tayi da sauri ta kalleshi cikin ido. yace hannunki laushi.</p><p><br /></p><p> da sauri ta kwace hannunta tana rufe ido.</p><p><br /></p><p>ahankali ya sake cewa zahara zaki iya gane mutumin da ya keta miki mutuncinki?</p><p> gabanta ne ya fadi dan bata taba zatan salis yasan wannan mgn ba .</p><p><br /></p><p> muryar haydar sukkaji daga bayan su yana fadin toh iidan kasan shi me zaka mai?</p><p><br /></p><p> cikin sauri sukka kalli gurin haydar ne tsaye hannun shi cikin aljjihun shi.</p><p><br /></p><p> salis ya bude baki zayi mgn aka turo kofar falon ,wata budurwa ce agaba bayanta kuma wata matace dagani mahaifiyar yariyar ce</p><p><br /></p><p> suna hada ido da haydar ya zaro ido yace me kika zo yi agidan mu?</p><p><br /></p><p> babu ko alamar tsoro atattare da ita tace niba gurinka nazo ba, nazo ne ingayawa iyayen ka ina dauke da cikin ka</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[8:37PM, 3/25/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>27 -29</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sauri ya farajan yariyar yana kokarin barin gidan da ita ummi ce taji hayaniya yayi yawa da sauri ta fito, ganin haydar najan yariyar ta fara dakamai tsawa cikin sauri ya saki yariyar yana mazurai, ummi takalli dadtijuwar matar da suke tare da yariyar tace sannu da zuwa hajiya shigo ki zauna.</p><p><br /></p><p> ba musu tahau kujjera ta zauna fatima da salis ko kallo sukabi yariyar dashi.</p><p><br /></p><p> haydar ko yana jingine jikin bango sai aikawa yariyar harara take</p><p><br /></p><p> ummi ce taji shirun yayi yawa tace baiyawar Allah ban fah ganeki ba.</p><p><br /></p><p> kamar jira matar take tace dama ai bazaki gane ni ba amman ai d'aki haydar bazai ce be gane mu ba, atakai ce dai hajiya Nazo ne na shaida miki 'yata zinat ta dauke da cikin danku haydar</p><p><br /></p><p><br /></p><p>wani zufa me dumi ya karyo ma ummi take ta Fara fadin innalillahi wa Inna ilaihir raju,un maimaitawa taitayi zuwa cen ta daga jajayen idonta ta kalli haydar kanshi akasa yace ummi nifa karya suke min.</p><p><br /></p><p> bata ce komaiba ta mayar da kanta kasa wasu hawaye ne masu dumi suka zubu mata zuwa cen ta miki ta nufi falon alhj salis ne yabi bayan ta yana fadin ummi karki gayamai Dan Allah .</p><p><br /></p><p> waigowa tayi tace salis wannan ba abun da za,abuye bane , dole ne yasan halin da haydar yake ciki dan ni yanzon ban san yadda zanyi da wad'an nan mutane ba, tana fadin haka ta shige dakin.</p><p><br /></p><p> bata dade ba saiga su sunfito tare da daddy yana huce.</p><p><br /></p><p> fatima naganin fitowan daddy tamike ta nufi dakin su cike da tsananin tsanar haydar azuciyar ta.</p><p><br /></p><p> daddy ko kallon haydar yayi cike da bacin rai sannan ya juya ya kalli bakin nasu sannan yace kai haydar fita kabar min gida, ku kuma kutashi ku bishi karku kara gigin nufumin gida da nufin Ku kawo min shege bazan taba karba ba.</p><p><br /></p><p> haydar ne ya bude baki yace daddy nifa karya suke min.</p><p><br /></p><p>idan kasakemin Wata mgn zan illataka ka fita kabar min gida wai gawa yayi barayin matar cikin tsawa yace kutashi ku bishi, cikin rawar jiki suka mike suka fita dan tuni haydar ya fita salis ma mikewa yayi zaibi bayan su </p><p> daddy yace karka fita tsayawa yayi ya jingina kanshi ajikin bango.</p><p><br /></p><p> ummi ko kuka take yi tana fadin alhj wannan hukunci beyi ba, matar tabani tausayi be kamata amata hakaba ,yanzon yaya zatayi kenan?</p><p><br /></p><p> Oho nidai bazan karbi shegeba d'an karamin shi dashi ya lalata rayuwuwar shi, yace na mashi aure ne ban mashi ba? wacce irin jaraba ce wannan yariyar nan ma ai inbanda jaraba ta girmeshi haka daddy yayita fada wata mgnr ma besanin sanda ta fito bakin shi.</p><p><br /></p><p> ummi ko kuka take sosai yayin DA salis ke tsaye jikin bango</p><p><br /></p><p>haydar ko yana fita ko waiwaye babu ya nufi motar shi shiga yayi ya zauna daidai lokacin zinat da mamarta suka fito harara ya wurgawa Zinat itama ta mayar da nata hararan motar shi yaja yabar wajen.</p><p><br /></p><p> yana fita agidan ya fara kuka hawaye ne yake zubomai kaman karamin yaro yana bakin cikin batawa iyayen shi rai da yakeyi amman ya kasa cen zawa, tsawa yayi bakin hanya yayi kuka sosai sannan ya kama hanyar gidan alhj yusuf.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf naganin haydar gabanshi ya fadi sakamako idanuwan shi dasuka kunbura tahowa yayi ya kamashi ya zaunar dashi ya fara tambayan shi me ya faru amman ina haydar babu baki domin kuwa ya kasa cewa komai illah hawaye dake bin kuncin shi.</p><p><br /></p><p>alhj yusuf ne ya lura haydar bazaiyi mgn ba, dan haka ya daga waya ya kira daddy.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> daddy na daukan waya yace au gurin ka ya taho, toh maza ka ko reshi karka sake kabar shi a gidan ka mazinaci ne dan iska .</p><p><br /></p><p> takaicine ya kama alhj yusuf yace yanzo yaya dan daka haifa kake kira da wad'an nan mugayan kalamen.</p><p><br /></p><p>ba d'ana bane ayan zun tunda yace shi d'an iskane na barma duniya kuma kaima karka kuskura ka tareni da mgnr haydar yana fadan haka ya katse wayar.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf ya sauke wayar ya kalli haydar yaga har yanzon hawaye ne a idon sa kamar anbude fanfu</p><p><br /></p><p>ya mayar da kanshi kasa zuwa cen ya d'ago ya kalli haydar sannan yace haydar aure za,amaka kuma ba ina neman amincewan ka bane za ayi auren ne ko kana so ko baka so.</p><p><br /></p><p> *Kuyi hakuri yau banyi typing da yawa ba insha Allahu gobe zanyi me yawa*</p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[9:26PM, 3/27/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>30 - 32</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bece komai ba har yanzon kuka yake yana mamakin zinat anya kuwa ba karya suka shirya mai ba domin shi rabon daya ganta ya dade kuma ai bakai tsaye yake shigarta ba.</p><p><br /></p><p> kwanan haydar 2 agidan alhj yusuf zuwa yanzon ya dan saki jikin shi saidai ya dan rame gashi zama agidan ya isheshi dan alhj yusuf ba mata gareshi ba, dan haka gidan babu dadin zama.</p><p><br /></p><p> shima alhj yusuf zaman ya isheshi Dan haka ya fara tunanin dawo da salame saidai be saniba ko haryanzo iyayen nashi nanan akan bakan su.</p><p><br /></p><p> washegari yanufi gidan dada sallama yayi ya shiga dada ta tareshi da Fara,a itako salamatu tana ganin shi ta shige daki bayan sun gaisa da dada shiru sukayi nadan wani lokaci sannan alhj yusuf ya fara fadawa dada kudurin sa.</p><p><br /></p><p> farin cikine ya rufeta har ta kasa boye murnanta daki ta shiga cikin farin ciki amman saita tarar da salamatu tana kuka.</p><p><br /></p><p> tana ganin dada tace dada nifa bazan koma gidan sa ba, shekarana uku da dawowa garin nan betaba lekomuba tunda ya karbi yarshi sau 1 ya barta tazo gidan nan be mason tayi alaka dani sabo da ayanzo bana gaban shi dan haka ni bazan saurareshi ba.</p><p><br /></p><p> fada dada ta fara tana fadin wani irin tunani ne wannan da baki gabanshi aida bezo gidan nan da niyar zai maidaki dakin kiba kikasan dalilin shi nayin haka ki tunafah tunda ya rabu dake haryau beyi aure ba dayake ke butulu ce har kk wannan mgnr toh tashi maza kije ki saurareshi .</p><p><br /></p><p>koda alhj yusuf yayiwa salamatu bayani batace a,aba aman fuskar ta adaure take tam kamar bata dariya dan haka hankalin alhj yusuf ya tashi yace salamatu kodai yanzon baki ra,ayi nane?</p><p><br /></p><p>cikin fushi ta fara zaiyanane mishi kamar yadda ta fadawa dada.</p><p><br /></p><p>farin ciki ne ya kamashi ashe har yanzon yana nan makale azuciyar ta yana murmushi yace Allah ya huce zuciyar ki nayi kuskure kuma ina neman afuwarki ki yafemin kuma idai fatima ce harsai kin haji da ganin ta haka alhj yusuf yayita rarrashi salamtu harta yadda ta amince sannan ya fada Mata shifa baya son abun ya dau lokaci dan haka suka tsaida akan ranar juma,a me zuwa.</p><p><br /></p><p>yana barin gidan gidan mahaifin sa ya nufa ya fada masa kudurin sa.</p><p><br /></p><p> murnace ta kamasu gaba daya har yadidko godiya sukayiwa Allah tare dayiwa dansu fatan alheri.</p><p><br /></p><p> *Ranar juma,a*</p><p><br /></p><p>taslima da fatima zaune adakin su suna hira taslim tace wlh fatima na kosa atsaida ranar bikin ku.</p><p><br /></p><p> tsaki fatima tayi sannan tace</p><p><br /></p><p> nidai gaskiya ban kosa ba keni idan ma naji anyi maganar bikin gabana fadowa yake shima yaya kullu maganar shikenan wai ya kosa ranan nan fah har cewa yayi zai gayawa daddy, waishi hakurin shi ya fara karewa</p><p><br /></p><p><br /></p><p>tintserewa tayi da dariya sannan tace ai yadai fad'amiki ne amman ba iyawa zayiba , da dai yaya haydar ne, sake kallonta tayi sannan tace yauwa sister naga wani abu acikin akwatin ki acikin wani d'an karamin akwati.</p><p><br /></p><p> "murmushi fatima tayi sannan tace eh yaya ne ya bani"</p><p><br /></p><p>" taslim ta sake cewa menene aciki?</p><p><br /></p><p>dafata fatima tayi sannan tace kai taslim kin cika gulma toh nima bansan menene aciki ba kuma yace karna bude sai ranar da akadaura mana aure.</p><p><br /></p><p> cafdi ai inda nice wlh saina bude yasan..........</p><p><br /></p><p> gud'an da ummi ke rangad'awa ne ya dakatar dasu daga hiran mikewa sukayi atare suka fito suna rige rigen tambayan ummi .</p><p><br /></p><p>cikin farin ciki ta dafa fatima tace </p><p> fatima ki godewa Allah yanzon haka mahaifiyar ki tana gidan babanki an mayar da auren su, yazon salis yayi waya yace gashima agidan.</p><p><br /></p><p>wani farinci ne ya kama fatima ta saki murmushi zuwacen kuma ta fashe da kuka.</p><p><br /></p><p>ummi ce ta kamota ta rugume tana fadin haba fatima keda zaki godewa Allah kuma, meye na kuka .</p><p><br /></p><p> saidare salis ya dawo hannun shi rike da ledoji bayan yayi wa ummi sannu da gida ya kalli taslim yace ke Ina zahara?</p><p><br /></p><p> kallon shi tayi sannan tace tana daki, yaya wai meye acikin ledar?</p><p><br /></p><p> "yana tafiya yake fadin inaruwan ki"</p><p><br /></p><p>washegari</p><p><br /></p><p>salis ne ya dauki taslim da fatima zai kaisu gidan alhj yusuf murna ce ba kadan ba azuciyar fatima.</p><p><br /></p><p> suna shiga gidan suka samu haydar kwace akan kujera yana danna wayar shi salis ne ya nufi gurin shi ya kama kafafuwan shi ya d'aga sannan ya zauna agurin tsaki haydar yaja sannan ya tashi ya zauna salis ne yace wa haydar ina mama?</p><p><br /></p><p> atakaice yace tana ciki.</p><p> daidai lokacin salamatu ta fito daga daki fatima ta tashi da sauri ta nufe ta, tureta tayi ta jawo taslim dake bayanta ta rungume sannan tacewa fatima aike babu ruwana dake.</p><p><br /></p><p>komawa tayi kusa da salis ta zauna tana turo baki.</p><p><br /></p><p> kallonta kawai salis yayi ya sunkuwar dakai.</p><p><br /></p><p> mama ko tana rungume da taslim tana tambayan ta karatun ta.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf ne yayi sallama ya shigo zama yayi cikin su bayan sun gaisa ya tashi ya nufi d'aki</p><p><br /></p><p> itama mama mikewa tayi sanna tacewa taslim tashi ki shiga kitchen ki debo muku abinci, tana fad'an haka tashiga d'aki</p><p><br /></p><p> haydar ko sai, satan hararar fatima Yake</p><p><br /></p><p> salis ko kallon fatima yayi yace ke wai baki iya bada hakuri bane?</p><p><br /></p><p> kara turo baki tayi sannan ta kauda Kai, daidai lokacin taslim ta kawo abinci ta ajewa salis nashi sannan tacewa fatima sister zo muci.</p><p><br /></p><p> azuciye tace banzanci ba.</p><p><br /></p><p>" har salis yakai abincin dafda bakinsa yadawo dashi sannan ya kalli fatima yace sabo dame bazakici ba?</p><p><br /></p><p>saida ta kara turo baki sannan tace toh aini batace dani ba kuma saina kamaci sai kace mayya.</p><p><br /></p><p>dariyace taso kubucewa haydar amman sai ya dake yaci gaba da danna wayar shi.</p><p><br /></p><p> salis ma dakewa yayi sannan yace toh ke wai baki iya bada hakuri bane, kitashi maza tun kafin raina ya baci kije ki bata hakuri.</p><p><br /></p><p> mikewa tayi ta fara kuka tana buga kafarta akasa kamar karamar yariya tana fadin nifah ba abinda na mata ni yaushe ma naganta bare na mata wani abu.</p><p><br /></p><p> tun salis na kallon fatima har ya gaji ya rufe idonshi dan ya lura yau fatima so take ta rud'ashi.</p><p><br /></p><p> shiko haydar baki ya saki yana kallon fatima tuni yanayin shi ya fara cenzawa ji yake kamar ya tashi ya rungume ta</p><p><br /></p><p> fatima ce ta lura haydar ita yake kallo dan haka ta tsaya cak tana mamakin shi kuma wannan me yake kallo.</p><p><br /></p><p> salis ko yanajin fatima ta daina kuka ya bude ido cikin bacin rai yace meyasa kike min haka ne zahara dan Allah idai baso kk kijamin fushin Allah ba toh ki dakata da irin wannan abun, kije kiyiwa mama sallama kizo mutafi.</p><p><br /></p><p> sumi sumi ta wuce ta tura dakin mama tana shiga haydar ya kalli salis yace wlh kai wawane d'an kauye.</p><p><br /></p><p> murmushi salis yayi tare da mikewa yana fadin Allah ya shirye ka.</p><p><br /></p><p> zuwacen mama da alhj yusuf suka fito fatima na rike hannun babanta .</p><p><br /></p><p>alhj yusuf yaga salis da taslim tseye yace kardai har zaku wuce?</p><p><br /></p><p> salis ne yabashi amsa eh baba zamu tafi.</p><p><br /></p><p> yace toh daman Ina son ganinku kaida haydar tsakanin ku wanene akace sun daidaita da fatima?</p><p><br /></p><p>da sauri haydar ya d'akai ya kalli salis shima salis d'in kallon shi yayi</p><p><br /></p><p> 🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[8:46PM, 3/28/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>33-37</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Alama salis yakewa haydar ya fad'a aman haydar sai make kafad'a yakeyi.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf yace daku nake mgn fa .</p><p><br /></p><p> " taslim ce ta lura salis kunya yakeji dan haka tayi sauri tace baba yaya salis ne.</p><p><br /></p><p>haidar ne ya d'ago kai ya harari taslim yace ke dan ubanki dake ake mgn</p><p><br /></p><p> alhj yusuf yace haydar me yasa bakin ka ya iya furta zagi ne, ai taslim batayi laifi ba abin da tayi kai ya kamata ace kayi amman sai kayi shiru, juyawa yayi ya kalli salis yaga ya dukar dakai yace salis ni dama nasani baban ku ya fad'amin dama naso ne naji daga gareku amman tunda kun kasa magana taslim ta fanshe ku.</p><p><br /></p><p> ya juya ya kalli haydar yace toh kai kuma fah.</p><p><br /></p><p> baba ni bayanzon zanyi aure ba .</p><p><br /></p><p> bata rai baba yayi yace toh sai yaushe?</p><p><br /></p><p> idan salis yayi ni daga baya zanyi.</p><p><br /></p><p> baka isaba kafison kai ta d'ako mana mgn ai ni inda sosamu ne nan da one week kayi aure dan haka duk abinda akeci nan da Wata 1 kawo yariyar da kk so,Dan mun riga mun yake rana nan da wata biyu dan haka kuje kufara shiri.</p><p><br /></p><p>haka suka koma gida cike da farin cike sai dai azuciyar salis ranar da akasa yayi mai yawa</p><p> dan haka da suka kebe da fatima yace zahara gaskiya ranar nan da akasa yayi yawa.</p><p><br /></p><p> haba yaya wata 2 ne yayi yawa toh ni wlh kusa ma naga yayi min dan nifah wlh tsoron ma ranar nakeji.</p><p><br /></p><p> da sauri ya kalleta tsoro kuma toh tsoron me kikeji, kardai ki kecemin tsoron miji kike, toh idai haka ne gara ma tun yanzon ki cire shi dan gaskiya bazaki takurani ba , zahara kinsan fan nayi hakuri</p><p><br /></p><p> haharara shi tayi sannan tace hakuri me kayi?</p><p><br /></p><p> murmushi yayi sannan yace Zahara Kenan kisan fah kina da kyau kuma na kusa najiki jiki na</p><p><br /></p><p>kawai daurewa nakeyi karne abin kunya, kasa ya yayi da murya ya Kira sunanta sannan yace kifah shirya dan idan mukayi aure akan kirjin ki Zan rinqa kwana.</p><p><br /></p><p> hannuta tasa ta rufe ido dan be saba mata irin wannan maganganun ba.</p><p><br /></p><p> murmushi yayi sannan yace zahara idan akace yau andaura mana aure bakaramin farin ciki zanyi ba, bare kuma na ganki ad'akina, Hmmm ranar zan nuna miki irin son da nake miki zan tarairayeki kaman kwai zan nunamiki soyayyar daba kowane namiji bane zai iya nunawa matar sa irin saba.</p><p><br /></p><p> kwashewa fatima tayi da dariya sannan tace amman dai yaya sambatu kk KO, wannan irin cin buri ne haka.</p><p><br /></p><p> shima dariya yayi sannan yace aidama nasan bazaki gane ba amman ahankali zan ganar dake, mikewa yayi tare da fadin bari naje gurin haydar.</p><p><br /></p><p> dasauri tace bayan zon ,muka dawo ba shine har zaka koma, ni wlh natsani haydar d'in nan banason ganin shi.</p><p><br /></p><p> shima cikin mama ya kalleta yace zahara kinada hankali kuwa d'an uwan nawa, meya miki ?</p><p><br /></p><p> toh yaya ai shima ya tsane ni dan haka nima bana sonshi wlh ko sunan shi aka kira gaba na faduwa yakeyi.</p><p><br /></p><p> kallon ta yayi cikin ido yace xahara haydar ba tsanar ki yayi ba haka halinsa yake nima bakiga yana min ba, kuma dan Allah ki yafe masa karki kara kullatan shi aranki kinga d'an uwanki ne , koya miki wani abu kijin haushi toh ki gayamin ni kuma xan faranta miki rai kinji KO ?.</p><p> </p><p> da sauri ta d'aga kai .</p><p><br /></p><p> yace kin yafe masa?</p><p><br /></p><p> eh tace ahankali.</p><p><br /></p><p>Shirye shiryen biki nata kankama acikin wannan family ummi shiri take sosai komai ta gama had'awa da dan ganci na</p><p> fatima dan yazun bikin saura sati 2 kuma har wannan lokacin salis be kawa yariyar da zai aura ba dan haka akabar batunsa dama alhj yusuf ne yaso ahad'a amman daddy tuni yabar zancen haydar kamar yadda yace ya cireshi acikin 'ya'yan shi.</p><p><br /></p><p> haydar ne zaune shida abokin sa anas a harabar gidan su anas sigari kawai yake sha daya shanye wani sai ya kara d'akkowa </p><p><br /></p><p> anas ne ya lura haydar ya kusa shanye kwalin sigarin dauke ragowar yayi sannan yace big boy waikai meke damun ka?</p><p><br /></p><p> yana fesar da hayakin dake bakin shi yana fadin fatima.</p><p><br /></p><p> Hmm daman aikai ya kamata ka aureta sai da fad'a maka kace bahaka ba sai yanzun da lokaci ya kure zakace wani fatima, kana nufin sonta kk?</p><p><br /></p><p> niba sonta nake ba amman ni banason salis ya aure ta, saboda Ina matukar sha,wan yariyar dan haka nafison wani daban ya aure ta, yanzun fah duk tarin 'yan matan dana ke dasu basa birgeni Dana rufe ido fatima nake gani</p><p><br /></p><p>tsaki anas yayi cikin takaici yace toh yanzon dai saidai kayi hakuri garama ka cireta aranka dan tafi karfin ka.</p><p><br /></p><p> tsaki shima yayi yamike yabar wajen tundaga ranar haydar ya zama kamar mara lafiya baya mgn sosai besan me yake damun shiba.</p><p><br /></p><p> Yau sauran kwana biyu biki dan haka yan baki sun fara isowa fatima da taslim sai shirye shirye sukeyi daddy na cikin farin ciki.</p><p><br /></p><p> ummi ce ad'aki zaune da kawayenta suna kallon akwati ta zuwa cen saiga salis rike da hannun haydar ummi ce ta kalli haydar tace meya kawoka?</p><p> </p><p> haydar ne yace ummi ninace yazo yaga akwati.</p><p><br /></p><p> cikin fad'a tace to tunda kai ka kirashi saika shirya amsan da zakaba babanku idan yadawo ya samu haydar agidan na, mikewa tayi tafita adakin ahankali mutane dake dakin suka fita daya bayan daya.</p><p><br /></p><p> haydar ya tsuguna gaban akwati yana dariya yana duba kayan zuwace yace brother kaya sunyi saidai kacika hijjab dayawa aciki.</p><p><br /></p><p> murmushi salis yayi sannan yace ra,ayina kenan.</p><p><br /></p><p> anagobe daurin aure da daddare salis ya shiga har d'akin su fatima fatima ya hango manne jikin gado ta rufe fuskarta gefe ko kawayen su ne zaune suna hira sunna ganin shigowan shi suka bar daki gaban Fatima yaje ya tsuguna dariya yayi sosai sannan yace zahara duk tsoron auren ne haka, </p><p><br /></p><p> batace kome ba ya sake cewa zahara dan Allah ki kwantar da hankali bana son ganinki cikin wannan halin .</p><p><br /></p><p>cikin kuka tace yaya kwata kwata banajin dadi, azuciyata taki natsuwa nayi nayi in natsar da ita nakasa gani nake kamar wani abu zai faru.</p><p><br /></p><p> da sauri yace babu wani abu dazai faru zahara sai alheri kiyi tunani dakau kila akwai abinda yake damunki.</p><p><br /></p><p> shiru tayi zuwacen tace yaya jiya nayi mafarkin na auri yaya haydar.</p><p><br /></p><p> dariya yayi sannan yace ni daman nasan akwai abunda yake damunki dan Allah ki cire tsanar haydar azuciyar ki, kuma kidaina wannan tunanin mafarki ne kawai insha Allahu gobe warhaka burin mu ya cika saida muyi fatan cikawa da imani, haka haydar yayi ta rarrashin fatima harta fara dariya.</p><p><br /></p><p> washe gari aka tashi da shirye shiryen dauren aure tun 12:00 bakin daddy suka fara halara kofar gidan ya ciki makil da jama,a sai hada hada ake salis ne ya fito cikin babban riga farare kal yayi matukar kyau waige ya farayi yana neman haydar amman ko alamar shi begani ba dan haka ya shiga neman no barshi tsaki yaje sabo da layin kwata kwata yaki shiga ya koma cikin abokan sa ya tsaya ranshi bace zucen yaga guri ya kara cika duba agogo yayi yaga karfe 12:43 cikin sauri ya nufi motar shi wani abokin sane yabi bayan sa yana fadin inakuma zaka?</p><p><br /></p><p> yana kokarin barin wajen yace tahir yanzon zandawo zanje na dauko haydar ne.</p><p><br /></p><p> gidasu anas ya nufa yana tura kofar anas dakin yaga haydar zaune ya tasa sigari cikin zafin zuciya yace haydar kana nufin bazaka halarci daurin aure na bane?</p><p><br /></p><p> bece komaiba dan haka yasa hannushi ya fara jawoshi bayan motar ya turashi anas ma ya shiga sun kamo hanya kenan kiran daddy ya shigo wayar salis cikin fada yace kana ina?</p><p> yace daddy ganinan zuwa naje dako haydar n.......</p><p><br /></p><p> salatin dasu anas kiyine ya dakatar da shi yana d'ago kanshi yaga Wata babban mota ta nufosu salis yayi kokarin kaucewa amman Ina tuni motar ta fara watan gaririya akan titi.basu kara sani me ya faru ba</p><p>zucen haydar ya bude ido ganin shi yayi kwace cikin jini muryan salis yaji yana kiran sunan shi daker yaja kashi ya kalli gurin kwance yaganshi jini na bulbulowa ta cikin shi jan jiki ya fara har ya isa gaban shi ya kama hannun shi babu abun yake kira banda zahara zuwace yayi kalmar shada be kara motsawa ba haydar ya farajan shi duk da shima ajikace yake.</p><p><br /></p><p> karan wata mota yaji yana kallon gurin yaga daddy da baba yusuf suna tahowa, gurin salis suka nufa daddy ne ya daga hannun shi yace ya innalillahi wa inna ilaihir raju,un Allah ya karbi abun sa😭😭</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊🕊</p><p>[9:04PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p>*Gaisuwa da fatan alheri gare ku*</p><p><br /></p><p>*Zainab bobbo adamawa*</p><p>*Yahancy gombe* </p><p><br /></p><p>*bilkisu muhammad*</p><p><br /></p><p> *xeeshata*</p><p><br /></p><p>*mmn abdulnasir*</p><p><br /></p><p> *hajju lokoja*</p><p><br /></p><p> *Fatyma*</p><p><br /></p><p>*harda wadan da bankira suna ba inajin dadin yadda kuke nuna sayayyar ku ga wannan lbr*😍😍😘</p><p><br /></p><p>38 - 39</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tattara su akayi gaba daya aka nufa asibiti har anas.</p><p><br /></p><p> nan danan wannan mummunan lbr ya isa kofar gidan daddy dake cike da jama,a yan daurin aure.</p><p><br /></p><p> itako ummi daddy ne yamata waya ya gaya mata amman be gayamata rasuwan salis ba yadaice gasu sun wuce asibiti.</p><p><br /></p><p>hakalinta ne yayi mummunan tashi dan ta dade tana munanen mafarkai akan salis da haydar</p><p><br /></p><p> itako fatima tun safe ta kulle kanta ad'aki tana kuka dan haka ummi tace abarta kar agaya mata abari aga abinda allah zaiyi.</p><p><br /></p><p> haka gidan ya zama jugun kowa da abin da yake sakawa.</p><p><br /></p><p> zuwacen daddy ya sake kiran ummi.</p><p><br /></p><p> tana ganin kiran daddy gabanta ya fadi tana dauka tace</p><p><br /></p><p> " alhj yaya abin da sauki kodai na taho ne kuna wanne asibiti?</p><p><br /></p><p> " cikin jarinta irin na maza yace basai kinzo ba muma gamunan tahowa kuma nasan ke musulma ce kin yadda da kaddara mekyau da marakyau.</p><p><br /></p><p>kuka ta fara tace alhj kardai kacemin mutuwa sukayi?</p><p><br /></p><p> "a,a haydar yanan araye sai dai ya samu karaya acinya"</p><p><br /></p><p> kara rushewa tayi da kuka sannan tace salis fah ?</p><p><br /></p><p> cikin shashshekan kuka yace sai dai muyi hakuri hafsat salis ya koma ga mahalicin sa.</p><p><br /></p><p> ummi jitayi kafafuwan ta bazasu iya daukanta ba take ta yar da wayar ta shiga fadin innalillahi wa inna ilaihir raju,in.</p><p><br /></p><p> jin salatin da ummi keyi gaba daya hankalin mutane yadawo gurinta ummi tana kuka tana gaya musu salis ya rasu.</p><p><br /></p><p>fatima dake kule ad'aki kunnen ta ya fara juyo mata koke koke da sauri ta bude kofar ta fito idon ta jajur bisu tayi da kallo daya bayan daya kowa afalon kuka yake.</p><p><br /></p><p> " cikin tsawa tace menene wani abu ne ya faru?</p><p><br /></p><p> Wata yayar ummi ce ta jawo ta jikinta nasiha ta shiga yimata sannan ta gaya mata rasuwan salis.</p><p><br /></p><p> jitayi kamar an buga mata guduma hawaye kuwa kamar an bude fanfu cikin kuka take fadin nashiga uku na lalace meyasa yayimin haka jiya fah yace min yau tare zamu kwana shine kuma zai tafi ya barni kai ban yadda ba be mutu ba,nasan shi me cika alkawari ne.</p><p><br /></p><p> daidai lokacin daddy ya shigo mutane ne abayan sa dauke da gawar salis d'akin ummi aka shigar dashi da sauri fatima ta kutsa ta cikin mazan ta shige d'akin ,hannu tasa ta bude fukar shi girgizashi tayi tana kuka tana fadin yaya katashi dan Allah.</p><p><br /></p><p> daddy na tsaye abayan ta ya kasa cewa komai alhj yusuf ne ya d'agota yace fatima salis yariga ya tafi ki daina mai kuka soyayyar da zaki nunamai yanzun shine kibishi da addu,a</p><p><br /></p><p> wani hawaye ne me dumi ya zubo mata alhj yusuf najanta tana waiwayen gawar salis.</p><p><br /></p><p> bayan angama gyara salis aka kira ummi tamai addu,a cikin kuka tamai addu,a albarka ko tasamai babu adadi, daddy ne yace akira fatima suyi sallama.</p><p><br /></p><p> kamota akayi dan ayanZon bata iya tafiya saitin kunen shi taje babu meji metake cewa.</p><p><br /></p><p> daddy ne yoga abin nata bana kare bane dan haka yace afita da ita </p><p><br /></p><p> haka sunaji suna gani aka tafi da salis gidan sa na gaskiya</p><p><br /></p><p> fatima ko mawa d'akin su tayi ta fashe da kuka kallon hannuta tayi taga zanen fulawa wani haushine ya kamata tunani yadda zatayi ta goge lallen ta fara </p><p><br /></p><p><br /></p><p>dan haka ta fara buga hannun ta ajikin bango tuni kyawawan warwaro dake hannun ta suka lanlan kwashi.</p><p><br /></p><p> dada ce tahigo taga halin da Fatima take ciki da sauri ta riketa tana fadin meye haka fatima saikace ba musulma ba, dan Allah dan darajan annabi ki dainawa bawan Allah nan kuka.</p><p><br /></p><p> suna cikin haka salamatu mahaifiyar fatima ta shigo, fatima ta daga kai tace mama kin ga haydar ya kashe salis KO ?</p><p><br /></p><p> cikin tsawa mama tace waye yace miki haka, kifah dai na irin wannan surutun ki kama bakin ki, haydar d'in da kike mgn shima yana cen akwance bemasa inda yake ba.</p><p><br /></p><p> cikin kuka tace</p><p><br /></p><p> " ai dama bazai san inda yake ba kuma da ikon Allah shima mutuwa zaiyi"</p><p><br /></p><p> cikin zafin zuciya mama ta nufi gurin ta gadan gadan</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[9:32PM, 3/30/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>40 - 41</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dada ce tace haba salamatu ki rabu da yariyar nan, kisan yazon hankalinta ba jikinta yake ba dole abita ahankali.</p><p><br /></p><p> fita mama tayi adakin dan bazata iya sauraran irin kalamen dasuke fitowa daga bakin fatima ba.</p><p><br /></p><p> bayan sati biyu</p><p><br /></p><p>fatima ce ita kadai agidan su ummi sun tafi duba jikin haydar dan haka ta wuce dakin su salis gurin kayan shi ta nufa gasunan jere kamar meshi yana raye tana kamshin turaren shi ke dukan hancin ta dan kaha tasaki kuka meban tausayi da sauri ta juya barayin da takalman sa suke nata kallo tana kuka </p><p><br /></p><p> zuwacen ta farajin muryan ummi tana kiranta tashi tayi da sauri ta fito tana share hawaye </p><p><br /></p><p><br /></p><p> ummi da daddy ta gani tsaye afalo taslim nagefe tana share hawaye daddy ya kalli fatima yace</p><p><br /></p><p> " me yakai ki d'akin su haydar me kike zuwa yi d'akin ?</p><p><br /></p><p> kasa tayi dakai sannan tace bakomai tana cikin fad'a ta fashe da kuka.</p><p><br /></p><p>daddy yace fatima dan Allah ki kwantar da hankalin ki wannan koke koken zai iya jawo miki matsala kiyi hakuri kidaina masa kuka, kuka bashi da amfani agurin mamaci addu,a yafi bukata ayanzon, fatima idan har kin cika masoyiyar shi toh karki sake mai kuka, yanzun nagama ma haydar fad'a tun da ya farfad'o bashi da aiki sai kuka yana kiran salis sai kace ba musulmi ba.</p><p><br /></p><p> ummi tace wlh alhj ya kara tayar min da hankali sai mutuwan ta dawo min sabowa.</p><p><br /></p><p> " ahankali fatima tace wlh ummi kukan munafunci yakeyi, bayan duk abin da ya faru shi ya jawo"</p><p><br /></p><p><br /></p><p> gaba dayan su binta sukayi da kallo baki sake, zuwacen ummi tace</p><p><br /></p><p> " fatima ashe zargin haydar kk shi yasa tunda ake zuwa dubashi baki taba cewa zaki ba"</p><p><br /></p><p> kallon ummi daddy yayi sannan yace kubar wannan maganar, ke Fatima tashi ki wuce d'aki</p><p><br /></p><p>haka acigaba da tafiya babu wani kwanciyar hankali agidan alhj kasim fatima ta rame tayi baki duk wanda yasan ta da ya ganta yanzun bazai gane taba.</p><p><br /></p><p> duk bayan kwana buyu ummi da taslim suke zuwa doba jikin salis kuma duk randa zasutafi sai suncewa fatima tazo su tafi amman sai tace bazata ba dan haka ummi ta farajin haushin fatima.</p><p><br /></p><p> yauma kamar kullum su ummi sun fito cikin shirin tafiya, lokacin fatima na zaune afalo tana karatun Qur,ani taslim tace </p><p><br /></p><p> sister dan Allah yau kizo muje ki gaida yaya haydar jiya fa sai da ya tambaye ki har yana cewa yasan kina cikin damu....</p><p><br /></p><p>ummice ta d'akawa taslim duka abaya tace wuce muje kada Allah yasa taje ke da yake d'anwan ki ne yazama dole kije amman ita be zaman mata dole ba, sabo da makiyin tane, tana fadan haka suka fita adakin.</p><p><br /></p><p> fatima na zaune tun bayan fitansu tana kuka domin kalaman ummi sun bata haushi woto haydar har tambayan ta yake yaji wani hali take cuci saboda yasan yasata cikin tashin hankali afili tace shega dan iska kawai.</p><p><br /></p><p> wayarta taji tayi kara ta juya ta kalli wayar no baba ta gani da sauri ta dauka, daga cen cikin wayar baba yace maza ki fito drive ya kawoki asibiti.</p><p><br /></p><p> dasaurin ta tace baba kaina ke ciwo bazan ...</p><p><br /></p><p> bana son musu fatima koma me yake damunki ki fito kawai .</p><p><br /></p><p> tana kuka ta mike tasaka hijjabin ta tayo waje</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*kuyi hakuri da wannan*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p> Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[6:52PM, 3/31/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>42 -45</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Suna tafe tana kuka har suka Iso asibitin drive ne yayi mata jagora har cikin dakin da haydar yake.</p><p><br /></p><p> daurewa kawai tayi ta shiga dan babu inda zata yi.</p><p><br /></p><p> mutane ne cike ad'akin wasu ma bata san su ba har kakar su yadidko batace wa kowa kome ba ta tsaya cen gefe.</p><p><br /></p><p> dadace tace Oh ikon Allah KO sallama bazaki mana ba kenan.</p><p><br /></p><p> ahankali tace nayi fah.</p><p><br /></p><p> yace ke bamu son shashanci wane irin tunani ne wannan ace ke har yanzo bazaki yadda da kandara ba.</p><p><br /></p><p> ai lefin ku ne alhj da bakuci ubanta ba, wawiya kawai mara wayau mama</p><p>ce take wannan fad'a</p><p><br /></p><p> daddy ya matsa gaban godon da haydar yake yace </p><p><br /></p><p> " haydar ga kanwar ka tazo gaishe ka"</p><p><br /></p><p> cikin muryar dake nuna mutun yana jigata yace wacece?</p><p><br /></p><p> "fatima ce daddy ya fada atakai ce"</p><p><br /></p><p> hannun shi ya fara mikowa yana fadin ina take?</p><p><br /></p><p> mama ta jawo fatima ta kaita jikin gadon, d'agowa yayi ya kalli fuskar fatima yace</p><p><br /></p><p> fatima kinga salis yatafi ya barmu bamu shirya ba ,a lokacin da muke tsananin bokatar sa.</p><p><br /></p><p> idon ta akasa yake amman yana kallon hawayenta na sauka akan hijjabin ta.</p><p><br /></p><p> shima cikin kuka ya sake cewa fatima ki daina kuka salis bazai so kukan ki ba, lokacin da abin ya faru sunan ki ne abakin shi gashi ya jigata amman sunan ki radau abakin shi yana fadi zahra zahra sai lokacin da Allah zai karbi numfashi sa sannan ya bari yayi kalmar shahada, idan na tuna wannan abun hakalina na tashi.</p><p><br /></p><p> kuka fatima take sosai harda shsheka.</p><p><br /></p><p> haydar ma haka zuwa ,cen yace fatima kiyi hakuri ki daina kuka</p><p><br /></p><p> daddy yace ya zaka ce ta daina kuka bayan kai gashi kana yi.</p><p><br /></p><p> da sauri ya fara share hawaye yana fadin daddy ni ba kuka nakeyi ba.</p><p><br /></p><p>. yace toh naji haydar Allah yaye muku abinda yake damun Ku.</p><p><br /></p><p> mikewa fatima tayi zata bar waje idanun ta suka sauka akan kafar haydar kubure take tayi suntun kamar zata fashe dauke idon ta tayi domin har yanzun ganin bakin sa take.</p><p><br /></p><p> koda suka koma gida ummi batawa fatima mgn ko gaishe ta tayi ayatsune take amsawa.</p><p><br /></p><p> haka sukaci gaba da tafiya gidan babu dadi ko kadan har salis yayi arba,in.</p><p><br /></p><p> fatima ko ta kara lalacewa.</p><p><br /></p><p> daddy ya lura fatima dakin salis take shiga shi yasa hakalinta yaki kwanciyai dan haka yasa aka kwashe komai dake d'akin aka fitar dashi aka rufe dakin</p><p><br /></p><p>ranar taci kuka kamar ranta zai fita.</p><p><br /></p><p> shi ko haydar sai da yayi wata uku cur asibiti amman duk da haka kafar bata takuwa dan haka aka bashi sanda anas ko tuni aka sallame shi.</p><p><br /></p><p>taslim da fatima ne zaune afalo kowa yayi shiru dan yanzon gidan haka ya koma gani sukayi anfara shigo da kaya ana shiga dashi dakin dake kallon na ummi fatima tacewa taslim wannan kayan fah?</p><p><br /></p><p> atakaice tace yaya haydar ne zaidawo dakin yau za,a salamamoshi .</p><p><br /></p><p> mikewa fatima tayi zata bar wajen taslim tace sister dan Allah ki rage nuna ma yaya haydar kiyayya abin da kk yi sister yayi yawa gashi har kinsa ummi ta farajin haushi ni ban san me yamiki ba har kk tsane shi haka.</p><p><br /></p><p> cikin kuka fatima tace bakisan abin da yamin bafah kk ce ?, duk wannan abun da ya faru waya jawo shi inba shi ba, ai yasan yaya salis bazai so ace baya gurin ba amman ya wuce gantalin shi inda beje neman shi ba da yanzun muna cikin farin ciki, dan haka ni gaskiya bazan taba ganin farin haydar ba, ya cuce ni ya rabani da farin ciki na, ke badan ina tsoron Allah ba dasai na kashe haydar in yaso nima akasheni, dan rayuwana bata da wani amfani</p><p><br /></p><p><br /></p><p>muryan ummi sukaji tana fadin aiko zaki bar gidan nan tun da kin fara fado kalmar kisa bari alhj ya dawo.</p><p><br /></p><p> batace komai ba ta koma daki taci gaba da kukan ta zuwa cen taji shigowan su daddy harda babanta azuciyarta tace ankawo Dan iskan nan kenan.</p><p><br /></p><p> baya su alhj yusuf sun rako hayadar gida sun koma, ummi da daddy suna zaune abakin gadon da haydar yake ummi tace alhj Ina da magana.</p><p><br /></p><p> toh inajinki me ya faru?</p><p><br /></p><p> alhj ni gaskiya nagaji da zama da fatima ta koma gurin mahaifiyarta.</p><p><br /></p><p> damamaki akan fuskarshi yace me kuma ya faru?</p><p><br /></p><p>komai ta kwashe ta gayawa alhj haydar najin su .</p><p><br /></p><p> nufasawa alhj yayi sannan yace </p><p><br /></p><p> " wlh hafsat kin ban mamaki yazun sabo da Allah fatima zaki biyewa wa , menene ke damun fatima yan zun ban da kuruciya da zafin mutuwan salis dan Allah karki kuma saka wannan mgnr a lissafi idan kinji tana irin wanna mgnr nasiha zakiyi mata ina tabbatar miki da ace nasiha kike mata da tuni ta bari, kuma daga yau inason ki dauki fatima kamar taslim.</p><p><br /></p><p> ummi tace shikenan alhj dama ni tsanar da naga tana nunamai ce tayi yawa.</p><p><br /></p><p> wannan babu ruwan ki ni nasan maganin abun zama ta bari ne.</p><p><br /></p><p> suna cikin haka haydar yace daddy inason na dan watsa ruwa.</p><p><br /></p><p> da sauri daddy ya mike ya kama haydar ya mikar dashi tsaye ummi ta mikamai sandar sa daddy na rike da daya hannu shi har suka isa toilet din dake dakin , ummi fitowa tayi ta barshi da daddy zuwa cen shima daddy ya fito.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> washegari da daddare daddy yace wa ummi ki shirya maza kizo muje cen babban gida.</p><p><br /></p><p> kallon shi tayi tace</p><p><br /></p><p> " alhj kana nufin haka zamu tafi mubar haydar shi kadai idan wani uzunrin ya tasan masa fah gashi taslim tana cen gidan.</p><p><br /></p><p> gaba daddy yayi yana fadin nifa banason mita kizo muje yan zon zamu dawo.</p><p><br /></p><p> haka ummi tabi bayan shi badan ranta yaso ba.</p><p><br /></p><p> fatima ko tana ganin fitan su ta sake wani murmushi wanda rabon da tayi irinshi tun kafin rasuwan yaya salis tashi tayi da sauri ta nufi dakin haydar ahankali ta tura kofar ta shiga</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[9:33PM, 4/1/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>46-48</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ganin shi tayi kwance yana bacci a hankali ta isa gaban shi kare mashi kallo tayi sannan taje saitin kafar dake da ciwon ahankali tasa hannu ta rike kafan.</p><p><br /></p><p> ganin da tayi be motsaba yasa ta dage iya karfinta ta murde kafan, kara ya saki me firgitarwa.</p><p><br /></p><p>uhun da yake besa ta saki kafar ba ci gaba tayi da murdewa.</p><p><br /></p><p> haydar ya hada zufa yana kurma ihu zuwa cen ta saki kafar ta matsa nesa da gadon ta kwashe da dariya.</p><p><br /></p><p> haydar ko ihu yake yana salati yana kiran ummi da dadddy .</p><p><br /></p><p> bayan fatima ta gama dariyarta ta tsaya ta hada fuska sannan tace haydar kadan ka gani indai ni ce kuma da izinin Allah sai an yanke kafar nan, fita tayi adakin ta koma nasu dakin ta kwanta daga dakin tanaji uhun da yake, amman ko ajikin tana cikin bargo ta shige ta rufe idanuwa.</p><p><br /></p><p> zuwacen taji shigowan ummi aguje tana fadi ihun me kk yi haydar.</p><p><br /></p><p> ganin shi tayi kwance inda ta barshi sai dai ya mirgina yana kokarin kai hannun shi kafar yana fadin zan mutu daddy Ku taimake ni.</p><p><br /></p><p> adaran ranar dai basu runtsa ba suna kan haydar kwana yayi yana kuka da kafa dan haka washe gari aka fara cukucukun barin kasar dashi.</p><p><br /></p><p> </p><p> fatima ko ranar tayi kwanan farin ciki</p><p><br /></p><p><br /></p><p>da safe alhj yusuf yazo suka dauki haydar aka maidashi asibiti.</p><p><br /></p><p>bayan tafiyan sune ummi ta shigo dakin su fatima ganin ta tayi zaune tana duba takardun makarantar ta saida ta kare mata kallo sannan tace.</p><p><br /></p><p> yanzon sabo da Allah fatima abin kikayi ya dace kenan?</p><p><br /></p><p> jitayi gaban ta ya bada dam dan ta zata haydar ya fada abin da tamai ne dan haka ta kasa cewa komai.</p><p><br /></p><p> ummi ce ta sake cewa yanzon fatima zakice bakiji ihun da haydar ya kwana nayi ba.</p><p><br /></p><p> mikewa tayi mama ni gaskiya banji ba bari naje na duba shi.</p><p><br /></p><p> mama tace ai an mayar dashi asibiti inagama kasar za,a bari dan abin yayi tsanani</p><p><br /></p><p> washegari aka wuce da haydar London domin asake duba lfyr kafan shi.</p><p><br /></p><p> *******</p><p><br /></p><p>bayan tafiyan haydar hankalin fatima ya kwanta dan yazon har tana sakin jiki da kowa na gidan ayi hira ayi dariya amman fah duk ranan da salis ya fado mata haka zata zauna taita kuka har ummi ta saba dan dataga fatima na kuka sai tace abin ya motsa.</p><p><br /></p><p> kwanci tashi ba wuya gashi har haydar ya cika wata hudu da tafiya kuma da alamun ansamu na sara dan ayau daddy da baba yusuf zasu dawo dan haka yau ummi taketa garke girke taslim da fatima ke tayata.</p><p><br /></p><p> 4:13pm su daddy suka iso gida anas ne ya dauko su.</p><p><br /></p><p> bayan sunci abinci sun huta ummi ta kalli alhj yusuf tace baku bani lbrn haydar ba.</p><p><br /></p><p> yace keda kuke waya kullum kuma kike tambaya na jikin shi, ai nace abin naki ko kara babu ke ki kira salamatu ta kira.</p><p><br /></p><p> dariya ummi tayi sannan tace wlh alhj ciwon ne ya bani tsoro dashi nake kwanciya dashi nake tashi dan gani nake kamar za,a yan ke.</p><p><br /></p><p> dariya su alhj sukayi sannan daddy yace ai shima har roko yake wai dan Allah ayan ke mai .</p><p><br /></p><p> ummi tace Allah sarki babana ai yaji jiki.</p><p><br /></p><p> taslim tace baba yanzon yaya haydar yana tafiya kamar da?</p><p><br /></p><p> yace ras yake tafiya taslim ai sati me zuwa zai dawo</p><p><br /></p><p><br /></p><p>fatima ko daure fuska tayi domin kuwa bata ji dadin lbrn ba dan ta tabbatar haydar ba zai bar ta ba dan haka hankalin ta yafi na barawo tashi, sai faman zare ido take.</p><p><br /></p><p> ummi tana lura da halin da fatima take ciki zuwa cen tace alhj na gaya muku abin da kuke kokarin shiryawa bazai yiyuba yanzon ka dubi halin da fatima ta shiga.</p><p><br /></p><p> hakalin kowa komawa gurin fatima yayi daddy yace fatima me ya faru ?</p><p><br /></p><p> dukar dakai tayi sannan tace babu komai.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf yace dan Allah ku rabu da ita nasan maganin ta ya nunata da hannu sannan yace wlh karki yadda ki kaini bango dan wlh zanci mutuncin ki fiye da inda bakya zata.</p><p><br /></p><p>daddy ne yaja alhj yusuf suka fita waje</p><p><br /></p><p><br /></p><p> bayan sati daya</p><p> ummi da taslim ne keta girkin tarban haydar ummi ta kalli taslim tace taslim fatima tana bani mamaki kiri kiri take nuna tsanar haydar yanzon ki duba fah hatta me gadin gidan nan murna yake haydar zai dawo amman ban da fatima... wayar ummi ce tayi kara cikin rawan jiki ta dauka tana Fara,a tace haydar yaya ka sauka ne?</p><p><br /></p><p> daga cen cikin wayar aka bata amsa eh ummi gamu nan ma anas ya dauko ni.</p><p><br /></p><p> murna ce ta rufe ummi ta mike ta nufa daki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 2:58pm suka iso gidan fira suke suna dariya shida anas amman abin da yaba anas mamaki suna shiga gidan haydar ya daure fuska zuwa cen ya fara kwafa anas ya kalleshi yace haydar lfy kuwa ?</p><p><br /></p><p> Hmmm anas ina tunanin abin da zanma yariyar nan ne kasan Allah sai tayi nadamar zuwanta duniya</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊🕊</p><p>[7:55PM, 4/2/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>49-51</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Anas yace wacce yariya kenan?</p><p><br /></p><p> " saida yayi kasa da murya sannan yace fatima"</p><p><br /></p><p> da mamaki anas yace meta maka, ai kamata yayi yanzon ka rinka tausayawa yariyar nan tun bayan rusuwan salis saboda ta shaku da salis.</p><p><br /></p><p> Hmmm dan ta shaku da salis kuma saita nemi kashini ita fah ta tayar min da ciwan kafar nan saboda taga bana iya tashi tabini har daki ina kwance akan gadona dan tsabar mugunta tazo ta bankaremin kafah.</p><p><br /></p><p> ,dariya anas ya fara sai da yayi me isarsa haydar na kallon sa zuwa cen yace toh ya isheka wlh ka kiyayeni ina nan yadda kasanni ba cenzawa nayi ba </p><p><br /></p><p><br /></p><p> anas ya gintse dariyar shi sannan yace abin ne yabani dariya kaiko kana kwance kabari karamar yariya kamar fatima ta gana maka azaba, kodai mafarki kayi?</p><p><br /></p><p> dariya haydar yayi sannan yace wlh ba mafarki bane toh yazanyi bacci fah nakeyi kawai naji anrikemin kafah ni kasan ma abin da yafi bani haushi idan na tuna uhun da na kurma amman sai naga ta koma gefe tana kyalketa dariya wato zatace tunda salis ya mutu gara nima na bishi.</p><p><br /></p><p> anas yace ni kuma atunani na kodai fatima ta gane cewa kaine wadda ka lalata mata rayiwa?</p><p><br /></p><p> zaro ido haydar yayi sannan yace bana tunanin haka kaima ka daina wannan tunanin idan ba haka ba zaka sa na fasa abinda nayi niyya.</p><p><br /></p><p> da haka suka shiga falon ummi , ummi ko kunya babu ta mike ta rungume haydar shima kwaciya yayi ajikin ta tana buga bayan shi kamar me lallashin yaro yayi bacci tana fadin mu godewa Allah babana Allah ya karbi addu,a mu.</p><p><br /></p><p> yana murmushi yace ummi ina godiya da nuna soyayyar ki agareni bansan kuna sona ba ummi sai da ciwon nan ya kama ni.</p><p><br /></p><p> daga kanshi ummi tayi sannan tace haydar akwai wadda zai haifi dansa yace baya so daman cen munason ka halinka ne bama so dan Allah ka gyara halayen ka ka koma kaman salis</p><p><br /></p><p> " kasa yayi dakai cikin sanyin jiki yace ummi nima ba ason raina nakeyi ba amman ku tayani da addu,a.</p><p><br /></p><p> aidama cen muna maka addu,a amman tunda kace haka zamu daura akan na da, kuta shi kuje kuci abinci, anas ga abinci cen.</p><p><br /></p><p> *******</p><p><br /></p><p> da daddare daddy da ummi suna zaune afalon daddy fatima tayi sallam ta shigo sanye da hijjab gaban kujeran da daddy yake zaune taje ta zauna ummi ta bita da kallo.</p><p><br /></p><p> bayan ta gaida su daddy ya kare mata kallo sannan yace fatima me ya faru akwai wani matsala ne?</p><p><br /></p><p> kanta akasa tace daddy Dama inason nakoma gidan yadidko ne.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> murmushi daddy yayi sannan yace kina nufin ki koma cen da zama?</p><p><br /></p><p>da sauri ta daga kai.</p><p><br /></p><p> gyara fuskar shi yayi sannan yace saboda me?</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p> ummi ce tayi karaf tace alhj ka mata ne makiyin ta ya dawo</p><p><br /></p><p> da sauri yace kash haba hafsat wai me yasa kk haka wani irin makiyi kuma ita da d'an uwanta ai babu wata kiyayya tsakanin su , fatima haydar d'an uwanki ne baki da wani d'an uwan da ya wuce shi sai kuma taslim dan Allah ku rungumi juna kinga bayawa gareku ba Ku hudu Allah ya bamu kuma ya karbi daya yanzo sauran ku 3 dan haka muke fatan kuhaifa mana yara masu yawa tunda mu Allah be bamu masu yawa ba</p><p><br /></p><p> batacewa daddy komai ba tamike tana share hawaye duk suka bita da kallo.</p><p><br /></p><p> tana kaiwa kofar haydar na sayo kai ko kallon gurin dasu ummi suke beyi ba ya d'aga hannu ya sharara mata Marika har guda 3</p><p><br /></p><p>wani wawan tsale ta daka takoma gefe ta fasa wani uban ihu domin kuwa Marin sun shigeta.</p><p><br /></p><p> daddy da ummi kuwa mikewa sukayi kowa bakin shi bude suna kallon haydar </p><p><br /></p><p> sai alokacin haydar ya kalli su daddy nan da nan ya fara sosa keya , meta maka, tambayan da daddy yayi wa haydar kenan</p><p><br /></p><p><br /></p><p>ahankali yace bigeni tayi.</p><p><br /></p><p> " shine kamata wannan dukan toh Bari kaji daga yau karka kuma kai hannun ka jikinta , in ban da mugunta ma ko kusa dakai bataje ba , mutumin baza kawai.</p><p><br /></p><p> ummi ce ta kamo fatima tana ,duba gurin da haydar ya dake ta fatima ko sai kuka takeyi.</p><p><br /></p><p> itama ummi fada ta shigawa haydar yana tsaye kanshi akasa itako fatima tana kwance jikin ummi.</p><p><br /></p><p> bayan haydar ya fita ummi takai fatima har daki sannan ta fito ta nufi dakin haydar.</p><p><br /></p><p> </p><p> tana turo kofar idonta yayi mata mugun gani haydar ne zaune yana kalon film din batsa ga sigari ahannun shi yana zuka </p><p><br /></p><p> har takai tsakiyan dakin besan ta shigo ba saboda shagala da yayi da kallon salatin da ummi ta rafka ne ya dawo dashi cikin hayyacin shi da sauri ya kashe tv cikin tashin hankali ummi tace haydar daman abinda kk yi kenan?</p><p><br /></p><p> kasa cewa komai yayi jiyake kamar ya nutse cikin kasa.</p><p><br /></p><p> ta sake cewa kai dai bazakaji tsoron Allah ba KO?</p><p><br /></p><p> nan ma bece komai ba dan haka ummi ta juya ta fita ranta bace.</p><p><br /></p><p>washegari da yamma alhj yusuf da alhj babbba suka iso gidan su haydar, daman tun kafin sukaraso daddy yasanar musu da zuwan mahaifin shi gidan dan haka ummi ta tanazan musu komai dazasu bukata duk da cewa bata da lfy dan tun sandda tashiga dakin haydar tarasa abun da ke mata dadi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>fatima da taslim KO sunajin tsayowar mota suka rutumo aguje ganin haydar agaban su yasa taslim ta tsaya itako fatima gefen shi tabi aguje taje ta d'ane alhj babba taslim da haydar tare suka iso haydar sai hararar fatima yake.</p><p><br /></p><p> alhj babba ko farin ciki ne ya lulubeshi ganin inda jikokin sa suke murnan ganin shi, gaba daya suka rankaya sukai cikin gidan afalon daddy su ka zauna.</p><p><br /></p><p> bayan sun natsune alhj babba yace ni banga salamatu ba.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf yace baba bata jin dadi ne shiya sa bata zoba.</p><p><br /></p><p> shiru yayi sannan yace toh Allah ya bata lfy ,juyawa yayi ya kali muta nen dake dakin yace toh duk kubani hankalin ku, wani abun alheri muke shirin kullawa tsakanin haydar da fatima .</p><p><br /></p><p> da sauri cikin fatima ya bada kululuuuuluuu yayin da zufa ya fara karyowa haydar.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊🕊</p><p>[7:55PM, 4/3/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>52-55</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Alhj babba yace in Allah ya yarda nan da sati 2 za,a daura musu aure.</p><p><br /></p><p> tuni fatima ta fara kuka, xuwa cen ta koma kusa da daddy ta kama kafar shi tace </p><p><br /></p><p> " daddy dan Allah karka bari ayi haka wlh daddy bana son shi ,ni da ku had'a ni da yaya haydar gara asamu ko almajiri ne ahada ni dashi daddy haydar fah mazunaci ne kuma.... alhj yusuf ne ya daka mata tsawa , hunnun ta tasa dukka biyun ta toshe bakin ta tana fadin na shiga</p><p>uku.</p><p><br /></p><p> alhj babba yayi tariya irin nasu na manya ,sannan ya kalli haydar yace haydar kai baka ce komai ba.</p><p><br /></p><p> kan shi akasa yace ai alhj da dai zaku cenza shawara da yafi danni inason in aure wayayyiyar yariya ne kuma ma ni ai jinin mu be hadu da wannan fatimar ba.</p><p><br /></p><p> daddy ne yace zai hadu nan gaba dan babu wani uzurin ku da zai lalata mana shiri, mun riga mun gama shiryawa.</p><p><br /></p><p> haydar babu abin da yake sai share zufah itako fatima kuka take harda majina.</p><p><br /></p><p> ummi ko tana gefe ta hada rai maganar fatima ce take mata yawo wai fatima ce ke cewa haydar mazunaci wato ita ta manta da tabon da yake jikinta dan ma ta samu za,a rufah mata asiri tunanin ummi kenan acikin zuciyar ta.</p><p><br /></p><p> alhj babba ya dubi ummi yace hafsat naga kamar bakiyi farin ciki da wannan auren da muke son hadawa bane?</p><p><br /></p><p> nan danan ummi ta saki fuska tace alhj ba haka bane akwai dai abin da nake tunani ne kaga yaran nan bashiri suke ba ina jin tsoro abarsu agida su biyu dan ni dake zaune dasu ni nasan halin su.</p><p><br /></p><p> alhj na dariya yace ki daina jin tsora hafsat, babu abin da zai faru dalilin dayasa nace ahada su aure kenan, yusuf ya gayamin halin da suke ci ,dan haka naga idan muka barsu ahaka zasu haifar mana da gadaddiyar gaba, kinga auren da zamu hada su zai dakatar da gabar daman bahaushe yace _*tsuntsu me wayo ta wuya ake kamashi*_</p><p><br /></p><p>cikin kuka fatima tace alhj indai dan muna gabane za ahadani dashi toh wlh daga yau na bari ,bazan kara gaban dashi ba, dan Allah ajanye maganar auren nan .</p><p><br /></p><p><br /></p><p> duk falon dariya sukayi ban da ummi da haydar.</p><p><br /></p><p>bayan alhj ya gama darawa yace fatima ni zakima wayo toh naki wayon aure nan babu fashi idan kinga ba ayiba toh dayan ku baya nunfashi, ya waiga gurin ummi yace hafsat na amshi uzurin ki dan haka acikin gidan nan zasu zauna kicigaba da lura da irin zaman da sukeyi kafin wani lokaci.</p><p><br /></p><p> nan danan ummi ta washe baki tanawa alhj godiya.</p><p><br /></p><p> sanna ya sake cewa ke kuma fatima tashi ki hada kayanki kibi baban ki ya kai ki gurin mahaifyar ki kafin ranar daurin auren</p><p><br /></p><p> </p><p> sumi sumi ta mike ta fita shima haydar mikewa yayi ya fita</p><p><br /></p><p>gaba daya kayanta dake gidan ta hada ta fara fitowa dasu ta sawa amotar alhj yusuf har ta gama kuka takeyi motar ta shiga ta zauna har sun fara kokarin fita daga gidan alhj babba ya kalli Fatima yace</p><p><br /></p><p> " kinyiwa ummin taku sallama kuwa?</p><p><br /></p><p> cikin kuka ta girgiza kai.</p><p><br /></p><p> cikin fada baba yusuf yace aiko ranki zai baci.</p><p><br /></p><p> da sauri ta fita daga motar har tana tuntube.</p><p><br /></p><p> kofar ummi ta tura tare da sallama ganin haydar tayi kwace akan ciyar ummi sai buga bayan shi take kamar me lallashin karamin yaro.</p><p><br /></p><p> duk d'agowa sukayi suka bita da kallo har haydar.</p><p><br /></p><p> ahankali tace ummi muntafi.</p><p><br /></p><p> cikin ya tsuna ummi tace hmmm fatima kenan wai har ke ce kike cewa haydar mazinaci ke kin manta tabon dake jikin ki, ai haydar rufah miki asiri zaiyi kuma kome d'a namiji yayi ado ne .</p><p><br /></p><p> har ummi ta gama maganar ta haydar be d'ago ya kalli fatima ba.</p><p><br /></p><p> itako fatima kara rushewa tayi da kuka tana me bakin cikin abun da ya same ta gashi har an fara goran ta mata lallai kowaye yaketa mata mutuncin ta ya cuceta take ta tuna sunan da taji abokin sa na kiran sa da shi wato big boy tana tafiya tana fadin big boy ka cuceni in Allah ya yarda sai Allah ya karbamin hakki na dahaka ta isa motar ko ahanya kuka take sosai dan haka alhj babba yita mata nasiha.</p><p><br /></p><p> bayan sun sauke alhj suka nufa gida</p><p><br /></p><p><br /></p><p>har suka shiga gida alhj yusuf ko kallon inda fatima take beyi ba, afalo suka samu mama tana kwance akan kujera, tana ganin su ta mike tace alhj lfy na ganka da fatima?</p><p><br /></p><p> zama yayi yacire hula sannan ya kwashe komai ya fad'a Mata, sannan ya kara da cewa kiyi mata fad'a sosai dan na kula so suke su kawo mana rabuwan kai , ya kalli fatima yace</p><p><br /></p><p> " fatima kece karama Ina rokon ki da ki kwantar da kai kinga haydar ya fiki wayo tunda yayi mgn su daya yaga ba,a goyi bayan shi ba ,be sake cewa komai ba, dan haka kema kiyi hakuri da hukuncin da aka yake akanku , bana son naji kin sake cewa baki son haydar.</p><p><br /></p><p>cikin kuka tace toh.</p><p><br /></p><p> daga nan be sake cewa komai ba ya tashi ya shiga d'aki.</p><p><br /></p><p> mama tasowa tayi ta dawo kusa da fatima ta dafata sanan tace </p><p><br /></p><p> " fatima wai me ya had'aki da haydar ne wannan abin naki yayi yawa fah.</p><p><br /></p><p> cikin shashekar kuka tace mama wlh bansan dalili ba nima haka na tsinci kaina.</p><p><br /></p><p> shawarwari mama taita bawa fatima har ta dan saki jiki.</p><p><br /></p><p>ranar da fatima tayi sati 1 dawowa gidan tana kwace afalo hannuwan ta duk suna kan fuskar ta hawaye ne ke tsiyayo mata, tana cikin haka taji sallaman haydar , kara damke idonta tayi kamar me bacci tana jin su suka shigo har takiyan falon shida anas.</p><p><br /></p><p> zama sukayi anas na fadin maryan tamu ma bacci take, haydar yaja tsaki yace</p><p><br /></p><p> " bawani bacci zama tashi ne"</p><p><br /></p><p> daidai lokacin mama ta fito tace a,a su haydar ne?</p><p><br /></p><p> eh mama ai mushigo ba kowa afalon sai fatima tana bacci sai ma asace ta bata sani ba</p><p><br /></p><p> dariya sukayi har mama amman mama tasan cewa fatima ba bacci takeyi ba.</p><p><br /></p><p> komawa d'aki tayi tabarsu afalon .</p><p><br /></p><p> mama na barin falon haydar ya mike yaje gaban kujeran da fatima take ya sauke ahannuta ya kama hancinta ya matse.</p><p><br /></p><p> da sauri ta fara cikicikin kwacewa tana bige hannu shi.</p><p><br /></p><p> sakinta yayi yana fadin munafukkar yariya ai kin kusan shigowa hannu na sai kin gane baki da wayo yar kauye kawai kuma bari kiji na fada miki kin ga wannan hijjaban naki karki sake kizomin dashi gida na ,idan kuma kin ki ji toh kizo dashi ki gani, dashi zan shake ki, ni ba salis bane ni nan da kika ganni mugu ne </p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[8:17PM, 4/4/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>56 - 58</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bata ce komai ba in ban da binshi da kallo da take.</p><p><br /></p><p> komawa yayi ya zauna sannan ya sakke kallon ta yace </p><p><br /></p><p> meye kika tsare ni da kallo dawani idon ki sai kace na mujiya.</p><p><br /></p><p>mikewa tayi tana tafiya tana fadin toh me zankalla agurin ka inban da kayan haushi tsaki taja ta shige d'aki.</p><p><br /></p><p> haydar ya girgiza kai sannan yacewa anas yariyar nan tana wasa dani, amman ba komai bata sanni bane ba dai zata shigo hannuna ba, saita gane shayi ruwa ne.</p><p><br /></p><p> anas ya tabe baki yace kai matsalata dakai baka daukan shawara, matsalar ka yawa gareta</p><p><br /></p><p><br /></p><p>suna cikin haka sukaga fatima ta dawo ranta bace nesa dasu ta zauna tana zubura baki.</p><p><br /></p><p> anas ya dube ta yace fatima dama munzo muji ko akwai wani abun da kk bukata sabo da kinga lokaci yana zuwa yama zo.</p><p><br /></p><p> kasa cewa komai tayi hawaye na tsiyayowa a idon ta tayi matukar bawa anas tausayi.</p><p><br /></p><p> haydar KO yi yayi kamar besan sunayi ba, sai danna waya yake.</p><p><br /></p><p> ahankali anas yace fatima kin yi shiru bakice komai ba, kodai na samu taslim ne muyi mgnr?</p><p><br /></p><p> kuka ta kara rusawa ta kasa furta komai.</p><p><br /></p><p> anas ya mike yaje har kusa da ita yace haba fatima me yasa kikeyin haka irin wannan ai sai kijawa kan ki wani ciyon.</p><p><br /></p><p> sai alokacin haydar ya kalleta yace</p><p><br /></p><p> " kai kake wani lallabata karabu da ita mana tayi kukanta idonta ne zaiyi zafi, kuma bari kiji na fad'a miki kinga irin wan nan kayan dake jikin ki karki zomin dashi gida na dan ni bana ra,ayin su .</p><p><br /></p><p> " ahankali tace ni dama nace ne kayi ra,yin su, ni Ina ruwana dakai"</p><p><br /></p><p> mikewa yayi da sauri ya fizgota anas ne ya rike shi yana fadin ya haka ne, kamanta a inda ka ke ne.</p><p><br /></p><p> da sauri ya saketa yace ai zan rike ki, kuma karkiga kaman wai ina son ki ne ,ni bason ki nake ba, kuma bazan taba sonki ba amman yazaman miki dole kisamin irin kayan da nake so ,ke dole ne ki kumin biyayya ko kin ki ko kinso.</p><p><br /></p><p> mikewa tayi tana tafiya tana fadin wlh baka isa ba wai kai nan har kana ganin kai namiji ne, katon banza dan daudo kawai.</p><p><br /></p><p> binta yayi aguje ya ya damke ta ya fara kai mata duka abaki </p><p><br /></p><p>fatima ihu take tana kiran mama amman taki fitowa.</p><p>.</p><p> daker anas yaja haydar suka fita agidan .</p><p><br /></p><p> fatima d'akin mama ta fad'a ta fashe da kuka tace mama kinaji yaya haydar na duka na shine kk barni ya sheni ko?</p><p><br /></p><p> muryan mama taji cikin kuka tana cewa</p><p><br /></p><p> Fatima me kk son nace muku sai da baban ki yace miki haydar ba sa,an ki bane kece karama ke ya kamata ki kwantar dakai, ya kamata ace yanzon kin hakura kibin umarnin mu kuma da kk cewa na Bari ya kashe ki, idan na ceceki yau idan kk je gidan shi zan biyu ku ne domin inceceki?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>tana kuka take fadi mama toh ai shine yake fadamin bakaken maganganu shi baku ganin lefin shi sai nawa.</p><p><br /></p><p> toh shikenan karki bari ke zaki sha wuya ni babu ruwana.</p><p><br /></p><p> haka kwanaki sukaita tafiya mama da ummi a nata shirye shirye fatima ko sai ramewa takeyi kulum cikin tunani.</p><p><br /></p><p> fatima ce kwace akan sallaya ta kudun dune kanta cikin hijjabi hayaniya muta ne ta faraji afalo ,dumin yau sauran kwana biyu daurin auren.</p><p><br /></p><p> cen ta ffara jin gud'a, tsaki taja ta kara kudun dunewa har da toshe kunne.</p><p><br /></p><p> tana nan kwace taslim ta shigo da gudu tace sister , da sauri fatima ta mike tace</p><p><br /></p><p> taslim sai yau kk ga damar zuwa?</p><p><br /></p><p> dafah ta taslim tayi sannan tace fatima meya sameki kk rame haka baki da lfy ne?</p><p><br /></p><p> hawaye ne ya fara zubo mata ahankali ta bude baki tace toh ba dole na rame ba, wai arasa wadda za,a had'ani dashi sai haydar dan dai kawai anga babu yaya salis nasan daya nan bazai bari ayi wannan auren ba sabo dashi yasan waye haydar .</p><p><br /></p><p> itama taslam kuka ta fara sannan tace</p><p><br /></p><p> sister kibar wannan mgnr kema kisan da ace yaya salis nanan baza,ace ki aure yaya haydar ba kuma kema ya kamata kiyi hakuri da yaya haydar din kinga fa kamar su daya banbancin kadan ne.</p><p><br /></p><p> cikin fad'a tace wace miki kyaun fuska ko na jiki nake nema, niba kyaun su ke gabana ba nasan naso yaya salis ne saboda kyawawan d'abi,un sa bawai dan wani abu nasaba kamar yadda kk tunani.</p><p><br /></p><p> taslim share hawayen fuskarta tayi ta mike sannan tace sister bazaki gane ba, yazon dai ki tashi muje anas najiramu zai kaimu lalle.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>itama mikewa tayi tana bin bayan taslim tana fadin ni bazayi lalle ba.</p><p><br /></p><p> suna fitowa falon fatima taga mutane cike afalon suna kallon akwati sai d'aga rigunan suke suna dariya daidai lokacin da wata mata tace ikon Allah dube wata riga saboda lalacewa wannan ai da ita gara babu kuma duk su sukafi yawa acikin kayan.</p><p><br /></p><p> hjy amina kawar mama tace ai wannan kayan da kika gani Allah kadai gasan kudin da aka kashe gurin sayan su.</p><p><br /></p><p> dayar ta sake cewa komai tsadar su ni basu dameni ba dan wlh da ace 'yatace aka kawo wa wannan kayan mayar dasu zanyi haba dubi fah dan Allah sai kace na 'yar arna daga wandona sai wasu yan iskan riguna sake daga wani tayi tace wannan kuma menene?</p><p><br /></p><p> gaba daya falon akasa dariya ban da mama dumin matar ta fara bata haushi .</p><p><br /></p><p> itako fatima kitchen ta nufa tanajin maganar da matar ke fad'a dan haka ta fara kuka.</p><p><br /></p><p> saida mama tasa baki sannan fatima ta yadda tabi taslim, sai dare suka dawo , mama ta kalli fatima tace</p><p><br /></p><p> kinga har kinyi kyau, dan Allah kirinkka cin abinci kidan ciko kafin jibi..</p><p><br /></p><p> turo baki tayi tare dasa hannuta ta goge fuskarta.</p><p><br /></p><p> ana gobe dauri auren ne fatima taita addu,a Allah yasa abin da ya samu salis shima haydar ya faru akansa kafin daurin auren.</p><p><br /></p><p> washegari da rana aka daura auren haydar da fatima acen gidan kakan su alhj salisu.</p><p><br /></p><p> tunda fatima ta samu lbri an daura auren hankalinta yayi mummunan tashi.</p><p><br /></p><p> daddare abokan haydar ne sukazo daukan amarya.</p><p><br /></p><p> kuka tayi ba kad'an ba da za,akaita gidan haydar.</p><p><br /></p><p> wani sabon gini kayi kafen nasu ummi nan aka nufa da fatima fuskar ta rufe yake.</p><p><br /></p><p> abakin gado aka zaunar da ita tana rusa kuka, bayan kowa ya wuce aka barta ita kai tana kuka ta mike ta cire gyalen dake jikin ta dauko wani zunbulelen hijjjabin ta, ta saka ,komawa tayi cen lungun gadon akasa ta kwata ta kudundune acikin hijjabin</p><p><br /></p><p> zuwacen ta farajin takun ta fiya alamar ana tahowa dakin cen taji an daki kofar garramm.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[8:15PM, 4/5/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Aslm 'yan uwa da abokan arziki Ina mika gaisuwata agare ku bansan taya zan nuna muku farin ciki naba akan yadda kuke nuna soyayyar ku ga wannan lbrn musam man 'yan group d'ina fadeela lamido novels 👍✔✔✔❤❤*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>59 - 60</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kara takurewa tayi guri daya, jikin ta ya hau kerma dan jitayi yau balakin tsoron shi take ji.</p><p><br /></p><p> shikuwa haydar ganin bata cikin d'aki ya tsaya yana kallon kofar toilet zuwacen yaje ya tura kofar toilet din ganin da yayi babu kowa yasa shi zagayowa lungun gadon , da saurin sa yasa hannu ya jawota saida ya jawota har saitin kafarshi sannan ya cikuikuyeta acikin hijjabin , zama yayi bakin gadon sannan ya dauki kafarshi daya ya daura akan cinyarta, saida ya kureta da ido sannnan yace </p><p><br /></p><p> " ina wasa dake ne, bana ce karkizo min da wad'an nan hijjaban ba?</p><p><br /></p><p>jikinta na rawa tace mantawa nayi.</p><p><br /></p><p> yana murmushin mugunta yace eh ai naji dadi da kk manta daga yau idan nabaki umarni bazaki manta ba, mike tsaye.</p><p><br /></p><p>da sauri ta mike sannan yace ki cire hijjab d'in' ki mikomin</p><p><br /></p><p> tana rawar jiki ta cere ta aje agefen shi.</p><p><br /></p><p> haydar ya lura fatima ta firgita dashi dan haka yayi murmushi ya kara cewa ki bude kunnuwan ki da kyau daga yau karna kara ganin ki da hijjab, wai ke adole kina boye min breast d'in ki, toh indai nine ko abude kika barsu babu abin da ya dameni dasu idan kuma bakiji ba toh kikara sakamin hijjab kiga ni dake da abin da kk boyewa zaku gane baku da wayo.</p><p><br /></p><p> cikin sauri yabar daki fatima taja Wata ajiyar zuciya ta koma bakin gadon ta kwanta ,kasa bacci tayi sai cen wajen asuba bacci ya kwasheta.</p><p><br /></p><p>washegari</p><p><br /></p><p>bayan haydar ya gama shiryawa bebi takan fatima ba dakin ummi sa ya nufah.</p><p><br /></p><p> yana shiga ta washe baki bayan ya gaidata tace</p><p><br /></p><p> " haydar sai yanzon da na ganka hankali na ya kwanta dan d'azon taslim taje kai muku breakfast ta dawo wai tata mugawa ba,a bude ba, sosai hankalina ya tashi dan gaskiya fatima tana bani tsoro.</p><p><br /></p><p>murmushi haydar yayi sannan yace </p><p><br /></p><p><br /></p><p> ummi ki kwatar da hankalin ki bazata yimin komai ba duk cika baki ne kawai.</p><p><br /></p><p> shiru tayi zuwa cen tace toh ina fatiman ko bazata gaishe mu bane.</p><p><br /></p><p> dukar dakan shi yayi sannan yace </p><p><br /></p><p>ummi bacci take har yanzon bata tashi ba .</p><p><br /></p><p> tiren dake dauke da kayan kari taslim ta aje gaban shi nan da nan yahau ci suna hira da ummi.</p><p><br /></p><p> be dade da faracin abin cinba fatima ta shigo sanye da riga da siket na atamfah tayi matukar kyau .</p><p><br /></p><p> ummi ce ta fara ganinta kyau taga fatima ta kara yi mata dan ita kanta rabon da taga fatima babu hijjabi ta manta Kai Allah yayi halitta babu makusa .</p><p><br /></p><p> sakin fuska tayi sannan tace</p><p><br /></p><p> a,a fatima har kin tashi.</p><p><br /></p><p> kanta akasa tace eh ummi ina kwana.</p><p><br /></p><p> cikin fara,a ummi ta amsa.</p><p><br /></p><p> shiko haydar tun da ummi ta kira sunan fatima ya d'ago kai ya kalleta kasa dauke idonshi yayi har ummi ta lura da haka.</p><p><br /></p><p> murmushi ummi keyi sosai tace haydar gyarawa fatima ta zauna kuci abincin tare.</p><p><br /></p><p> sai alokacin ya sauke idon shi.</p><p><br /></p><p>ummi ta sake cewa fatima matsa kuci abincin </p><p><br /></p><p> bata da abin cewa dole ta mike ta isa gurin aksa ta zaune haydar ko yana kan kujera, amman saboda tsabar mugunta yana ganin ta zauna shima ya sakko, hannu ta saka ta fara kai wainar bakin ta ahankali domin tsoron take karta bege haydar.</p><p><br /></p><p> takai luma ta biyu bakinta taga ya aje cukalin dayake ci dashi agefe ya saka hannu.</p><p><br /></p><p> tana saka hannun ta akan wainar ya daura nashi ya danne mata hannu 'yan yatsun yadinga bi daya bayan daya yana matsewa.</p><p><br /></p><p> idon fatima yayi jajur sabo da azaba tun tana daurewa har ta fara mutsu mutsu duk da haka haydar be bari ba dan haka ta saki wata yar Kara.</p><p><br /></p><p> ummi ta waigo tace yaya dai fatima?</p><p><br /></p><p> da sauri haydar ya saki hannun sannan yace ummi mgn muke.</p><p><br /></p><p> tun daga nan fatima bata sake saka hannuta ba har ya gama ci ya mike yayiwa ummi sallama ya fita</p><p><br /></p><p><br /></p><p>yana fita ummi ta dubi fatima tace</p><p><br /></p><p> " fatima tashi ki d'ibi wainar kici naga haydar ya hana ki ci</p><p><br /></p><p> damama ki fatima takalli ummi azuciyar ta, tace au dama matar nan tana kallon shi yana gana min azaba mikewa tayi sannan tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[4:13PM, 4/7/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>61 - 63</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nina koshi ta fad'a atakaice.</p><p><br /></p><p> kallon ta ummi tayi sosai sannan tace me kk ci dazaki ce kin koshi, tashi maza tun kafin raina ya baci</p><p><br /></p><p>tashi tayi badan ranta yaso ba guda 2 ta d'iba ta koma kusa da taslim ta zauna.</p><p><br /></p><p> bayan fitan ummi ne taslim ta kalli fatima tayi murmushi sannan tace</p><p><br /></p><p> " sister wlh yau kin ban mamaki a she dama kina son yaya haydar amman kk cewa kin tsane shi.</p><p><br /></p><p>fuskar fatima cike da bacin rai tace ni na ce miki inason shi aini tsakani na da yaya haydar babu soyayya har abada.</p><p><br /></p><p> tsaki taslim taja sannan tace haba sister ni zaki sa akwana bayan gashi nan har wata kwaliya kk masa na mussaman kuma nagama yau kin aje hijjab a gefe.</p><p><br /></p><p> </p><p> toh yazanyi yace baya son hijjabi har fah cewa yayi idan na kara sawa saiya shake ni dashi, </p><p><br /></p><p> dariya taslim tayi sannan tace</p><p><br /></p><p> "Allah ya shirye ku"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>fatima bata kara tunawa tana da d'aki ba har dare tana barayin su ummi, ci gaba sukayi da harkokin su kamar yadda suka saba.</p><p><br /></p><p> kwance take tayi d'aid'ai akan gadon taslim cen ta fara juyo muryan haydar yana fad'a.</p><p><br /></p><p> sai alokacin ta tuna da wani haidar da sauri ta karasa bakin kofar, jitayi yana cewa</p><p><br /></p><p> " ummi ni gaskiya bazan iya ganin irin wannan kazantan ba a indafah na cire rigata agurin na same shi ba ,abin da ta gyara a d'akin.</p><p><br /></p><p> ummi tace nace kayi hakuri, bata kyauta ba, wuce ka tafi gata nan zuwa.</p><p><br /></p><p> juyawa yayi da sauri ya fita ummi ko Fatima ta fara kwala ma kira.</p><p><br /></p><p> da sauri ta fito gabanta na faduwa, tana isa gaban ummi tace gani ummi.</p><p><br /></p><p> saida ummi ta kalleta sosai sannan tace fatima me ya hanaki ki gyarawa haydar d'aki.</p><p><br /></p><p>ummi ai bece na gyara mai ba, kuma ni mantawa ma nayi da bangaren gaba daya.</p><p><br /></p><p> daure fuska tayi sannan tace toh ki wuce ki gyaramai yanzon kuma daga yau karki sake mantawa, dan haydar yaji haushi sosai.</p><p><br /></p><p> fatima tana tafiya tana tunanin ummi ita wato bata son ran haydar ya baci, na wani kuma ko oho.</p><p><br /></p><p> tana tura kofar falon warin sigari ya daki hancinta.</p><p><br /></p><p> da sauri tasa hannunta ta tushe hancinta .</p><p><br /></p><p> haydar dake zaune akasa ya mike kafafuwan shi yana busa hayaki ya bita da kallo.</p><p><br /></p><p> tana gafda zata shiga d'akin ta yace ke.</p><p><br /></p><p> da sauri taja ta tsaya.</p><p><br /></p><p> yana mikewa yana fadin me kk toshewa hanci.</p><p><br /></p><p>bata ce komai ba har ya iso gaban ta, fesa mata hayakin ya fara yana fadin wannan kike toshewa hanci .</p><p><br /></p><p> kara matse hancin tayi tace nifah banason warin ta ne </p><p><br /></p><p>murmushi yayi me fitar da sauti sannan ya had'aata da bango ya cire hannun data toshi hancin ya matse da daya hannun shi sannan ya fara fesa mata hayakin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> nan da nan fatima ta rikice tari ta shiga yi babu kaukautawa</p><p><br /></p><p>ganin da yayi tana neman shidewa yasa ya saketa da sauri.</p><p><br /></p><p> tsugunawa tayi tana rige da ciki zuwa cen ta fara amai.</p><p><br /></p><p> haydar na tsaye yana kallon ta, tun tana aman abin da taci har ya koma wani koren ruwa ne yake fita </p><p><br /></p><p> bece mata komai ba har tayi ta gama zuwa cen taja jikinta gefen aman ta kwan ta.</p><p><br /></p><p> binta da kallo haydar yayi sannan ya kashe gutun sigarin dake hannun shi ,yayi jifah dashi , gaban fatima yajje ya tsuguna yace ke tashi kije kije kiyi wan ka.</p><p><br /></p><p> ko motsi fatima bata yi ba dan haka haydar yaja tsaki, azuciyar shi yace kodai na kira ummi ne, da sauri ya girgiza Kai , agogon dake daure ahannun shi ya fara kwance wa sanan yacire rigar dake jikin shi</p><p><br /></p><p><br /></p><p>daukan fatima yayi cek ya nufi dakin sa da ita.</p><p><br /></p><p> fatima najinshi babu damar tayi mai musu dan aman da tayi ya galabaitar da ita, jira take taji ya ajeta akan gado domin kwanciya tafi bukata ayanzun , amman sai taga ya nufe toilet da ita.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> kuka ta saka tana kokarin zamewa, kara matseta haydar yayi a jikin shi sannan ya turo kofar toilet din</p><p><br /></p><p> zuwa cen sai gasu sun fito haydar rike da fatima ga dukkan alamu haydar ne ya mata wanka, dan na hango tsananin tashin hankali atattare da shi.</p><p><br /></p><p> fatima ko ban da kuka babu abin da take dan haka suna fitowa haydar ya sake ta sannan yace</p><p><br /></p><p> duba fatima kiyi hakuri ki dai na kuka bazan kara taba ki ba, yauma lalura ce, bari naje d'akin ki na dauko miki wata riga ki sanya.</p><p><br /></p><p> haydar na fita fatima ta haye gadon haydar lokacin da ya dawo ya sameta ta rufa da bargo bece kome ba ya aje rigar ya fita ad'akin.</p><p><br /></p><p> koda haydar ya koma falo kasa zama yayi surar fatima ke masa yayo, wata matsanan ciyar sha,awa ce ta tasarmai wadda rabon dayaji irinta tunkafin rasuwar salis ji yayi bazai iya hakuri ba , gashi bazai iya tunkaran fatima da bukatar saba dan haka ya dauke key din motar sa ya fita</p><p><br /></p><p>sai da safe haydar ya dawo wanka kawai yayi sannan ya leka d'akin fatima kwance ya sameta akan gado saida ya daure fuska sannan yace</p><p><br /></p><p>" yaushe kika dawo nan, nace ne ki fito?</p><p><br /></p><p> a hankali tace mezanyi toh acen d'in, ni nafi son na zauna ad'aki na.</p><p><br /></p><p> gashin ta ya kama ya rike sannan yace </p><p>tashi ki koma idan kuma ba haka ba wlh yazon idan kk fara amai sai kin amaye hanjin ki, kuma ni ba taikonki zanyi ba.</p><p><br /></p><p> kafin ya gama mgnr ta sauka da sauri tana fadin zanje dan Allah karka kunna.</p><p><br /></p><p> tana fita ya kwashe da dariya tashi yayi yabi bayanta, sai da yaga ta hau gadon shi tukuna ya juya yabar dakin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>barayin su ummi ya nufah yana shiga ya washe baki.</p><p><br /></p><p>ummi ma murmushi tayi sannan tace ya dai haydar.</p><p><br /></p><p>yana murmushi yace ummi yau ina cikin farin ciki.</p><p><br /></p><p>d'aura fuska tayi? tace haydar niko yau akwai abin da ke damuna.</p><p><br /></p><p> shima hadiye murmushin shi yayi sannan yace meye shi ummi?</p><p><br /></p><p> sai da tayi kasa da murya sanan tace</p><p><br /></p><p> " haydar kwana biyun nan ina yawan tuna wannan yariyar da sukazo da maman ta, ko kana da lbrn su ? nasan zuwa yanZon ta haihu KO ?</p><p><br /></p><p>kanshi akasa yace ummi nifa tun daga ranan ban Kara ganin ta ba kuma ko lokacin da suka zo gidan nan Mufi wata 5 bamu had'u ba dan haka ummi ki kwantar da hankalin ki.</p><p><br /></p><p> shiru ummi tayi zuwa cen tace.</p><p><br /></p><p> " haydar bakin mgr ka nayi ba amman inason ka kaini gidan su yariyar zanyi mgn da ita.</p><p><br /></p><p> kanshi akasa yace shike nan ummi duk ranan da kk shirya sai kiyimin mgn</p><p><br /></p><p> shiru sukayi gaba dayan su zuwa ce ummi tace ina fatima yau ban ganta ba</p><p><br /></p><p> da sauri ya d'ago yace tanan akwance bata jin dadi.</p><p><br /></p><p>da mamaki aka fuskarta tace meke damunta?</p><p><br /></p><p>sun kuyar dakai yayi sannan yace ummi itama kanta batasan kinda yake mata ciwo ba tace nan tace cen, gaba daya ta hanani bacci kuma gashi ta cika shagwaba yan zon ma fah ummi daker ta barni na fito.</p><p><br /></p><p> farin ciki ne ya kama ummi cikin sauri ta mike tana fadin bari naje na gano ta , shima haydar bayanta yabi</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[10:03PM, 4/14/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>64 -66</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummi na gaba haydar na binta abaya,</p><p><br /></p><p> dakin fatima ta nufah, haydar ne ya fara sosa keya yana fidin ummi tana daki na fah.</p><p><br /></p><p> da saurinta ta juyo atare suka shiga dakin , fatima ko tanajin motsi ta kara damke idonta.</p><p><br /></p><p> muryan haydar taji yana fadin ummi kin gani ko , ni jiya kwata kwata ta hana ni bacci amman ita gashi tana yi.</p><p><br /></p><p> fatima najin ya kira sunan ummi ta duro daga kan gadon.</p><p><br /></p><p> da sauri ummi ta riketa tace kiyi ahankali mana ke da baki da lfy.</p><p><br /></p><p> fatima ta bude idonta akan ummi sannan tace</p><p><br /></p><p> ummi kin ganshi ya hanani fita wai dolle sai na zauna adakin shi ,ka rashe mgnr tayi cikin kuka</p><p><br /></p><p> murmushin munta haydar yayi sannan yace </p><p><br /></p><p> ummi waifah nan kunya taji dan kin ganta adakina.</p><p><br /></p><p> itama ummi murmushi tayi sannan ta kara rugumo fatima jikin ta tace fatima menene abin kunya ke da d'akin mijin ki aini yau hankali na ya kwanta, Allah ya kara had'a kawonan ku , ko ma kiyi kwanciyar ki.</p><p><br /></p><p> kuka fatima ta kara fashewa dashi tana buga kafarta akasa take fadin wlh ummi ni d'akina zan tafi ai ko jiyama bani nazo ba shine ya kawo ni.</p><p><br /></p><p> da sauri ummi tace toh ya isa haka ni ban tambaye ki ba.</p><p><br /></p><p> haydar na kallon fatima yana fadin ummi ji abin da take yi haka fah taitamin jiya.</p><p><br /></p><p> fatima ce ta wurga mai wani kallo cikin ido tace wlh ummi ni karya yake min.</p><p><br /></p><p> daure fuska ummi tayi sannan tace toh ya isa haka ke fatima meke damun ki?</p><p><br /></p><p> tana share hawaye tace ni wlh karya yakemin lfy ta lau.</p><p><br /></p><p> cikin sigar wasa ya harareta sannan yace amman dan tsabar muguta shine kika hanani bacci daga yau ko zaki kwana kina koke koken ki bazan kara kulaki ba.</p><p><br /></p><p> ummi juyawa tayi tana fadin kudai kuka sani</p><p><br /></p><p><br /></p><p>ummi na fita fatima ta fashe da kuka.</p><p><br /></p><p> haydar ko daure fuska yayi sannan yace ke fatima kk KO wa, daga yau duk ranan da nayi magana kk sake cewa karya nakeyi zaki gane shayi ruwa ne, tafiya ya farayi sannan yace kuma kafin ki fita ad'akin nan ki tabbatar kin gyara shi , dan ni bana son kazan ta.</p><p><br /></p><p> yana fita fatima ta mike tana kuka take gyara dakin bayan ta gama d'akinta ta nufa saida ta gyara ko ina sannan tayi wanka tayi ras da ita.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>shiko haydar yana fita bayan gidan ya nufah cikin dan wani lungu ya zauna sigari ya ciro aljihun shi ya kunna ya fara sha, besan meye dalili ba haka nan yaji baya son ya batawa fatima rai dan haka besha ad'akin ba ,sai da yasha ya koshi sannan ya nufa dakin ummi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> yana turo kofar fatima na sawo kai zata fita ad'akin , da saurin ta kalle shi tatoshe hancita ta kwasa da gudu tayi bayan ummi, tsugunawa tayi ta kudundune abayan ummi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> da sauri ummi ta mike ta rike ta daidai lokacin haydar ya karaso wajen.,</p><p><br /></p><p> KO me ya tuna kuma sai ya fita da sauri.</p><p><br /></p><p> fatima na ganin fitan shi ta mike . ummi ta kalleta sosai sannan tace anya kuwa fatima ba aljanu gareki ba, ya za,ayi daga ganin mijinki ki daka wannan uban tsalle.</p><p><br /></p><p> wasa da yatson hannun ta take ga kuma hawaye na fitowa afuskarta ahankanli tace ummi nifah banason warin sigari, kuma yaya haydar sai ya dinga sha yana shakamin hayakin.</p><p><br /></p><p> da sauri ummi ta dafa kirjin duk da cewa bataji mamaki ba domin kwanakin baya tasan har giya haydar na sha </p><p>saidai tana ganin kamar mutuwan salis yasa </p><p>ya bari , da sauri ta dago kai tace fatima haydar d'in ne yake shaka miki hayaki kina nufin har acikin gidan nan yana shan taba?</p><p><br /></p><p> da saurinta ta daga mata kai.</p><p><br /></p><p> tace toh shenan zanyi manin abin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> haka kwanaki sukaita tafiya har aka kwashe wata uku babu wani jituwa tsakanin haydar da fatima , saidai wani abu da fatima bata saniba tun ranan da ya labe yasha sigari yadawo gida yaga fatima na toshe hanci be sake sha ba</p><p>dan haka yayi kyau ya Kara haske.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> kaman kullum yau haydar na zaune a office d'inshi anas ya shigo tare da sallama.</p><p><br /></p><p> mikawa juna hannu sukayi cikin Fara,a , anas na zama yasa hannu a aljihu ya</p><p>dauko sigari yana kokarin kunnawa ,cikin sauri haydar yace</p><p><br /></p><p>" dan Allah akarka kunna min ita anan kaje waje </p><p><br /></p><p>kasha abinka kasan fatima bata son warinta karkajamin na koma gida tana toshe min hanci</p><p><br /></p><p> </p><p> dariya sosai anas yayi sannan yace</p><p><br /></p><p><br /></p><p> " a lallai Fatima ta samu shiga yanzun kana nufin kabar sha kenan tunda bata so, ko shiyasa naga kwana 2 kabar daukan yariyar ka?</p><p><br /></p><p>Murmushi haydar yayi sannan yace</p><p><br /></p><p>" bawai na daina sha bane, inason sha hakura kawai nakeyi ban san me yasa ba konayi niyar sha dana tuna fatima saina maida kasan wani abu dayake bani mamaki kofah awaje nasha sigari ina shiga gidan take ganewa har fah wani toshe hanci zakaga tanayi kamar taga kashi.</p><p><br /></p><p> dariya anas ya sakeyi yace nikuwa wlh yadda na saba da sigari babu wata soyayya dazata sa na bari.</p><p><br /></p><p> mikewa haydar yayi tare da fadin dallah gabara waya fad'a maka sonta nake inma tunanin ka kenan toh gara ka cenza nime zanyi da fatima yariyar da ko kwalliya bata iya ba tsaki yaja yabar wajen.</p><p><br /></p><p> yana shiga gida barayin su ya nufah fatima ya gani zaune tayi tagumi hawaye nabin kuncin ta, har ya wuce ta ya dawo ya tsaya agaban ta , hannuwan shi ya zuba cikin aljihu wandon shi sannan yace ke menene?</p><p><br /></p><p> </p><p> cikin muryan kuka tace toh ba ummi bace ta hanina zuwa gidan baba, kuma tabar taslim ta tafi.</p><p><br /></p><p> murmushi yayi harda sauti sannan yace</p><p><br /></p><p> " shine kika zauna kina kuka zaman kanki kikeyi kin tambaye ni ne ko ummi ce take auren ki , tamin daidai dan wlh da ace nadawo na samu baki nan harcen zan biki naci miki mutunci.</p><p><br /></p><p> mikewa tayi cikin kuka ta nufi d'aki.</p><p><br /></p><p> shima bayanta yabi tana shiga dakin ta fad'a kan gado tsaye yayi ya bita da kallo wani yanayi yaji ajikin sa wanda ya kasa fassara shi da sauri yasa hannun shi ya d'ago ta yana fadin tashi ki zauna zan kaiki amman da sharadi .</p><p><br /></p><p> tona kuka tace eh naji kafada ni koma menene zanyi indai zaka kaini.</p><p><br /></p><p> yana d'an dariya yace ai bawani abu me wahala bane kawai inason ne nizan baki kayan da zaki saka.</p><p><br /></p><p> da sauri ta fara share hawaye tana fadin wlh zan saka.</p><p><br /></p><p> yana murmushi ya fita adakin zuwacen ya dawo da wasu kaya rike ahannun shi mike mata yayi ta bude riga da siket musu d'an karan kyau aciki sai wani d'an karamin gyale.</p><p><br /></p><p> daga kayan take tana kare musu kallo zuwacen tace</p><p><br /></p><p> " yaya wadannan kayan fah sumin kadan bazasu shigeni ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p> tafiya ya fara yana fadin babu wani kad'an da zasu miki idan kinason zuwa ki sa saiki sameni amota.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ba yadda ta iya tanason zuwa dan haka ta saka ta fito bata shiga barayin ummi ba Kai tsaye ta nufi motar haydar tundaga nesa yabita da kallo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> bayan sun dauki hanya ma satar kallon ta yake dan idan kaga yadda kayan ya amsheta sai ka rantse da Allah ta saba sakawa, sunyi nisa da tafiya mutar ta tsaya sakowa haydar yayi ya fara yan tabe tabe har ya gaji motar bata tashi ba, dan</p><p> haka yace da fatima ta sakko su karasa da kafah.</p><p><br /></p><p>koda fatima ta sakkko sai da ta jajjawo rigara sannnan suka fara tafiya</p><p><br /></p><p> yamma ce dan haka unguwar cike take da gungu gungu na maxa kuma abin da haydar ya lura dashi duk inda sukabi fatima akebi da kallo take yaji wani haushi ya kamashi, duk da cewa wannan bashine karon farko da ya fara yawo da mace ahakaba, toh meyasa naji haushin wannan tambayan da haydar yayiwa kansa Keenan</p><p><br /></p><p>wani majalisar samari ya sake hangowa agaban shi gani yayi tun kafin sukai gurin samarin suna waigowa dan haka ya juya ya kalli Fatima ya daure fuska sannan yace</p><p><br /></p><p> " ke kina nufin tacikin mazan nan zakibi kuma a haka</p><p><br /></p><p> turo baki tayi sannan tace to bakai bane kace na fito haka.</p><p><br /></p><p> cikin sanyin murya yace bar wannan maganan fatima kinga ga wani gida nan kishiga ciki kice dan Allah su aramiki hijjab</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mmn Yazeed</p><p>[8:52PM, 4/15/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>67 - 69</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kallon shi tayi sosai sannan ta turo baki tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p> " ni dai gsky baza ni ba haka kawai bansa mutanen gidan ba kuma sai naje aron hijjab.</p><p><br /></p><p> kara daure fuskar shi yayi sannan yace fatima Ina wasa dake ne?, maza ki shiga tunkan raina ya baci.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> buga kafa ta fara tana fadin ni dai kazo kawai mutafi nina gaji da tsayuwa.</p><p><br /></p><p>haydar sakin baki yayi yana kallon fatima komai dake jikinta rawa yake, hankalin shi kara tashiyayi dan haka ya matsa daf da ita cikin tsawa yace</p><p><br /></p><p><br /></p><p> " baki da hankali ne bakyaganin mutane na kallon ki?</p><p><br /></p><p> "tace toh kazo mutafi mana"</p><p><br /></p><p> cikin tsananin bacin rai yace bazamu ba idai har baki shiga kin ara hijjab ba toh sai dai mukoma gida.</p><p><br /></p><p> tuni fatima ta fara ganu haydar kishin ta yake , dan haka ta kara dakewa tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p> " aiko sai dai mukoma dan wlh bazanje aro ba, toh wai kai meya da meka dani dazaka ce saina saka hijjab.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> da saurin sa yace bansani ba mara kunya kawai ai zan kamaki ne .</p><p><br /></p><p> murmushi fatima tayi tana kallon haydar ta gefen idon ta sai wani hura hanci yake idon shi ko jawur waya taga ya dauko daga aljihun shi ya fara dannawa matsawa yayi cen gefe dan haka bata san dawa yayi waya ba, tsaye sukayi gaba dayan su, zuwacen ta hango motar anas na tahowa, gaban su ya tsaya da sauri haydar ya bude gaban motar ya shiga.</p><p><br /></p><p> anas ne yaga fatima bata da niyar shiga dan haka yace madam shigo mana.</p><p><br /></p><p> ahankali ta fara tafiya kamar wadda kwai ya fashewa aciki tana shiga anas yaja motar.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> haydar yana zaune ne ya had'a fuska becewa anas komai ba, ahankali anas ya kalleshi yace</p><p><br /></p><p><br /></p><p> big boy ya dai ?</p><p><br /></p><p>take gaban fatima? ya bada damm dan bazata taba manta wannan sunan ba, kuma tun bayan mutumin da ya keta mata haddi bata sakejin ankira wani da irin sunan ba sai yau,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> muryar haydar taji yana fadin wannan fitsarariyar yariyar ce ta batamin rai.</p><p><br /></p><p>murmushi kawai anas yayi adai dai lokacin suka isa gidan .</p><p><br /></p><p> fatima bata saurare suba ta bude motar tafita ko waiwaye babu .</p><p><br /></p><p> da murnanta ta shiga d'akin mama dan tunda akayi bikisu bata taba zuwa ba.</p><p><br /></p><p> mama na kallon fatima tayi salati sannan tace yau kuma mezan gani fatima abin da bakiyi kina budurwa bane sai yanzon zaki tsiro dashi , duba jikin ki fah duk awaje.</p><p><br /></p><p> suna cikin haka haydar ya shigo daga ganin shi kasan yana cikin damuwa dan kuzarin shi ya ragu.</p><p><br /></p><p>har kasa ya tsuguna ya gaida mama, cikin sakin fuska ta amsa.</p><p>.</p><p> kallon shi mama tayi sosai sannan tace.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Aliyu yau kuwa lfy kake?</p><p><br /></p><p> kanshi akasa yace kaina ke min ciwo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>mama tace toh kuma ban da abin ku kai na ciwo bazaku zauna agida ba sai ku kamo hanya sai kace dole, juyawa tayi ta kalli fatima tace </p><p><br /></p><p> maza tashi ku koma gida mun gode da gai suwan.</p><p><br /></p><p> kuka fatima ta fara matso wa tana fadin wlh mama lfyr sa lau yanzo....... mamace ta dakatar da fatima da fadin kinga fah banason mgnr banza ki tashi maza ku wuce gida</p><p><br /></p><p> atare suka mike da haydar fuskar shi ayamutse har ya fara tafiya yaja ya tsaya fatima ko tuni tayi waje.</p><p><br /></p><p> da mamaki mama ke kallon shi zuwacen tace haydar kanaso wani abune?</p><p><br /></p><p>ahankali yace mama daman cewa zanyi idan akwai wani hijjab abawa fatima ta saka.</p><p><br /></p><p> shiru mama tayi nad'an wani lokaci sannan tace toh bari na dauko mata.</p><p><br /></p><p> mama na shiga d'aki haydar ya fita amota ya samo fatima dan anas barin musu motar yayi .</p><p><br /></p><p> bayan ya zauna ya kalli fatima yace kije mama na kiran ki.</p><p><br /></p><p> cikin haushi ta bude motar ta fita har d'akin mama ta shi tace mama gani.</p><p><br /></p><p> wasu zafafan mari taji saukan su har guda uku akan fuskarta, sabo da azaba saida takai kasa.</p><p><br /></p><p>tuni idanuwan ta suka rine sukayi jawu hijjab taga mama ta wirgu mata akan cinyar ta dauri ta kalli mama.</p><p><br /></p><p> hararan ta mama tayi sannan tace maza ki dau ki hijjabin kisan ya idan ba haka ba ko saina jimi ki ciwo wawiya mara wayo yaro dan karami dashi kina neman kisamai hawanjini</p><p>ni bansan yadda akayi kika cenza hali daga mutuniyar kirki kika koma ta banza ba</p><p><br /></p><p>kara matso wa mama ta fara dan haka fatima ta mike da gudu ta saka hijjabin tayi waje.</p><p><br /></p><p> bayan motar ta shiga ta zauna haydar na jiyo sautin kukan ta, bece mata kome ba dan ya zaci saka hijjabin takewa kuka.</p><p><br /></p><p>itako fatima wani irin haushin haydar ne damfare azuciyar dan haka taitama zuciyar ta alkawari itama saita kullamai sharri da har ya mutu bazai manta ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*kuyi hakuri da wannan*😘</p><p><br /></p><p> 🕊🕊</p><p> Mmn yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 07014197556</p><p>[7:33PM, 4/17/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Godiya Ta Mussamman ga wad'annan group's*</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Fadeela Lamido novels*👈🏻</p><p>*Faty Afreen's novel*👈🏻</p><p>*Billy Galadanci's novel*👈🏻</p><p>*Firstclass woman's*👈🏻</p><p>*Matan Muminai*👈🏻</p><p> *Zee & Hussy novel's*👈🏻</p><p>*Big Girl Hausa*</p><p>*novels*👈🏻</p><p>*HAMA🀠GEE'S NOVEL CHAMBER*👈🏻</p><p>*Aisha Hanwa novels*👈🏻</p><p>*MF &J Hausa novels*👈🏻</p><p>❤❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>70 - 72</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Har suka isa gida babu wanda yacewa kowa komai tun haydar najin kukan fatima har ya dai naji.</p><p><br /></p><p> </p><p>bude motar tayi ta fita fuuuu haydar ya bita da kallo cike da damowa sannan ya shiga tunani a fili yace waini meke damuna ne akan yariyar nan sau nawa ina yayo da mata wayayyu wad'an da had'uwar su ta zarce ta fatima kuma da shigar da tafi wannan lalacewa dan an kallemu baya damu na, amman me yasa na fatima ya dame ni haka, tsaki yaja sannan ya juya ya fita agidan</p><p><br /></p><p><br /></p><p>itako fatima tana shiga d'akinta cire hajjab d'in tayi taje gaban mudubi ta tsaya tana kallon fuskar ta wasu hawaye ne suka sake zubu mata masu dumi saka makon ganin fuskarta da tayi yayi suntum idon ta ko guda daya har jini ya kwanta sabo da marin da mama ta mata.</p><p><br /></p><p> tsayawa tayi tai shiru zuwa cen kuma kamar an tsunguleta ta fara tafiya tana fadin wlh bazan yadda ba dan yaga ina mai shiru saiya dinga kullami sharri , da yasan yana da kishin ya dauko kayan da kanshi ya bani, bata cenza kaya ba ahaka ta fita tana shiga barin su ummi ta fashe da kuka kai tsaye ta wuce falon daddy, tana shiga ummi ma ta shigo arude tana fadin fatima lfy?</p><p><br /></p><p> Shima daddy arude ya mike yace mamana meya sameki waye ya tabaki?</p><p><br /></p><p>cire hannuwanta tayi akan fuskarta cikin kuka tace yaya haydar ne yamare ni.</p><p><br /></p><p>da sauri daddy ya taho ya kama fatima arude yace</p><p><br /></p><p> " yanzon haydar d'in ne ya miki wannan duka har gurin ya tashi haka, yasha wani abu ne? , dasauri ya sake hannun fatima ya fara neman no haydar, bugu 2 ya dauka cikin fad'a daddy yace kazo yanzon nan inason ganin ka.</p><p><br /></p><p> ummi ko tana zaune tayi tagumi agefe fuskar ta daure</p><p><br /></p><p> daddy komawa yayi kan kujera ya zauna sannan yacewa fatima mamana yi hakuri kizo ki zauna idan haydar yazo zai rubuta min sakin ki dan bazan laminci auren duka ba, ai nazaci ya gyara halinsa ne shi yasa har na bari aka had'aki dashi .......</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ummi ce ta katse daddy alhj me kk nufi da wannan mgnr ai yazon tsaka ninsu baza,asan waye me gsky ba sai haydar yazo, kuma ma alhj da kk wannan mgnr ai duk abin da namiji yayi adone ita ka manta cewa rufah mata asiri yayi, dan naga kana nunawa kamar fatima ce kadai taka kuma idan gsky ne ai hannun ka baya taba rubewa ka yanke ka yar.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>cike da mamaki daddy ke kallon ummi, juyawa yayi gafen fatima hawaye ne ke zubuwa kamar anbude fanfo, bece komai ba ya maida hankalin shi gurin ummi </p><p><br /></p><p>yace naji duk abin da kk fad'a Amman inason ki sani ni agurina da haydar da fatima dukka daya ne, inko har kikaga nafison d'aya acikin su toh shine yafi kyautata min, kuma da kk ce idan hannun ka ya rube baka yankewa ka yar, toh saidai idan kace bazaki iya ba amman ni tuni yaushe zan yanke shi nayar dashi har abada, koko dan haydar yana dan da kk hayfa shikenan baza,a fadi lefin shi ba, kuma bari kiji, Zan baki last warning duk ranar kk kara cewa haydar rufawa fatima asiri yayi abakin auren ki.</p><p><br /></p><p> " cikin sauri ummi ta dafah kirjin ta tace alhaji abin har yakai haka ?</p><p><br /></p><p> " mikewa yayi tare da fadin ai yama wuce hak . .....</p><p><br /></p><p><br /></p><p> turo kofar da akayi shine ya dakatar dasu, haydar ne yayi sallama ya shigo jikin shi asanyaye kallon su yayi yaga kowa fuska bace gakuma Fatima agefe tana rusa kuka.</p><p><br /></p><p>cike da mamaki ya karasa tsakiyan falon , ganin daddy yayi ya fara takowa gare shi be ankara ba yaji saukan wasu zafafan mari har guda 2, ji yayi kamar antsintsika masa jijiyoyin kan shi, muryan daddy yaji yana fadin Marin da kayiwa fatima ne na rama mata, kuma na baka nan da kwana uku ka kawomin takardan ta, juyawa yayi barayin fatima sanan yace mamana tashi muje na kaiki asibiti</p><p><br /></p><p><br /></p><p> suna fita ummi ta mike tana share hawaye ta rikewa haydar hannun tace tashi muje.</p><p><br /></p><p>ba musu ya mike dakinta takaishi sannan tace</p><p><br /></p><p> " haydar meta maka ka mareta?</p><p><br /></p><p>kwanciya yayi akan gadon ummi</p><p><br /></p><p> sannan yace ummi wlh ban daketa ba nifah na sauke ta sannan na wuce.</p><p><br /></p><p>toh ai kuma haydar akwai shedan duka ajikin ta</p><p><br /></p><p>bece komai ba gyara kwaciyar shi yayi jefi jefi kuma yana share hawaye babu abin da yafi daga mai hankali kamar maganan daddy na karshe.</p><p><br /></p><p> ummi ko tana kula haydar kuka yake dan haka tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p> " haydar wai kukan me kakeyi , zafin marin ne koko sakin da akace kamata ne?</p><p><br /></p><p>bece komai ba yaci gaba da share hawayen sa</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>gajiya ummi tayi da mgn dan haka ta fita ta barshi </p><p><br /></p><p><br /></p><p> washegari 10:00am haydar ne ke zagaye afalon shi sai kaiwa yake yana dawo wa, saka mokon yau fatima a barayin su ummi ta kwana wai daddy yana nufin dgsk yakeyi toh wai ma ita fatima da tace na mareta meye ribar ta, koda yake ai dama yariyar bakar muguwa ce, tunanin da yayi tayi kenan azuciyar shi, shiru yayi zuwacen ya nufi barayin su ummi.</p><p><br /></p><p> ummi na zaune afalo haydar ya shigo tare da sallama </p><p><br /></p><p>ko kallon inda ummi take be yi ba, kai tsaye ya nufi d'akin taslim.</p><p><br /></p><p> ummi ta bishi da kallo azuciyarta tace kar dai haydar ya kamu da son yariyar nan tun jiya na kula baya cikin hankalin shi.</p><p><br /></p><p> shi kuwa haydar yana isa bakin kofar turawa yayi ya shiga dai dai lokacin da fatima ke kokarin saka riga dan haka ya sauke jajayen idon sa akan ta.</p><p><br /></p><p>cikin sauri ta karasa saka rigar sannan ta d' auki d'an kwali tana daurawa tana hararan haydar.</p><p><br /></p><p> bakin gadon yaje ya zauna taslim ko tana daga gefe tana duba wasu ta kardu </p><p><br /></p><p> cikin sanyin jiki yasa hannu ya jawo fatima jikin shi, bata ankara ba saijin ta tayi zaune akan ciyar shi, wannan shine karo na farko da ta haujikin haidar dan haka ta firgita sosai tana ciki cikin tashi amman ina yayi mata irin rokon da bazata iya kwatan kanta ba.</p><p><br /></p><p> tun taslim na kauda ido har ta gaji ta mike ta nufi kofah</p><p><br /></p><p> haydar yace taslim dawo in dan nine kiyi zamanki, yanzon zan fita</p><p><br /></p><p><br /></p><p>komawa tayi tazauna har yanzon fatima kokarin kwace kanta take.</p><p><br /></p><p> haydar ya maida hankalin shi gareta yace meyasa baki dawo d'aki ba kk kwana anan?</p><p><br /></p><p> ban sani ba.</p><p><br /></p><p>murmushi yayi sannan ya sake cewa </p><p><br /></p><p> " dame kika dake fuskar ki kk ce ma daddy nina dake ki?</p><p><br /></p><p> cikin rashin kunya ta sake cewa ban sani ba.</p><p><br /></p><p> nan ma murmushi ya sakeyi sannan yace</p><p><br /></p><p> " fatima dan Allah kiyi hakuri kije ki fad'awa daddy gsky kinga jiya yayi fushi dani sosai, duk abin da kk ji ni kiyi min bana son sharri.</p><p><br /></p><p> Kan fatima akasa yake dan batasan me yasaba sam bata son had'a ido da haydar kuka ta fara tana fadin wlh idan baka sakini ba saina had'aka da daddy</p><p><br /></p><p>turo kofar akayi ummi ce tsaye gaba daya dakin suka d'ago suka kalli ummi nan danan fatima ta kara rikecewa tana tura hannun haydar </p><p><br /></p><p> shiko haydar kara rukuta yake yana kokarin mannata akirjin shi.</p><p><br /></p><p> ummi ta kallesu ta tabe baki sannan ta juyar da kallonta ga taslim tace ke taslim tashi kibasu guri.</p><p><br /></p><p> har ummi da taslima suka fita haydar na ciki ciki da fatima sai da yaga ta fashe da kuka sannan ya saketa.</p><p><br /></p><p> kan gadon ta fad'a tayi ruf da ciki tana cigaba da kuka.</p><p><br /></p><p> yayin da haydar yayi tsaye yana kallon ta, kasa tafiya yayi, zuciyar shi na saka mishi wasu abubuwa wanda bazai su faruwan su yanzon ba, ahankali ya sake zama abakin gadon yasa hannun shi ya riko kwankwason ta.</p><p><br /></p><p> zabura tayi ta mike aguje tuni d'ankwalin ta ya zame gashin ta ya watse agadon bayanta saida ta kai bakin kofa sannan ta tsaya tace</p><p><br /></p><p> Allah ya isa, d'an iska kawai.</p><p><br /></p><p> da sauri haydar ya zaro ido fatima ni kk zagi?</p><p><br /></p><p> eh anzageka d'in, in banda iskanci Ina ruwanka da kwankwaso na.</p><p><br /></p><p> Mikewa yayi hannuwan shi na cikin aljihun shi yace dan na taba jikin ki ne kk cemin d'an isaka, toh wlh idan kk bari na rike ki saikin yabawa aya zakin ta.</p><p><br /></p><p> saida ta bude kofar d'ankin sannan tace ai Nina ba kanwar lasa bace sai kace wata wawiya zan tsaya ka rikeni.</p><p><br /></p><p> tahuwa ya farayi Dan haka fatima ta kwasa aguje, sai da taje gaban ummi ta tsaya tana haki.</p><p><br /></p><p> ko da haydar ya iso gurin be tsaya ba zuwa yayi zai rike fatima.</p><p><br /></p><p> muryan ummi yaji tana fadin taslim d'auko min mayafina kizo mubar musu gidan su karaci iskacin su</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>07014197556</p><p>[3:02PM, 4/19/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>73 - 75</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sauri haydar ya Saki fatima ya dawo kusa da ummi ya tsaya yace ummi yi hakuri na bari.</p><p><br /></p><p> taslim ta mikawa ummi gyalenta daidai lokacin da ummi ke fadin a,a aini sai nabar muku gidan bazan iya kallon wannan fitsaran ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> da saurin sa yace bafah wani abu bane ummi taki tsayawa ne mgn kawai zamuyi.</p><p><br /></p><p> daker haydar ya shayo kan ummi ta koma ta zauna.</p><p><br /></p><p> fatima ko wucewa tayi sumi sumi ta shige daki.</p><p><br /></p><p> idon haydar akanta har ta shige.</p><p><br /></p><p> ummi ma shi tabi da kallo sannan ta Kira sunan shi .</p><p><br /></p><p> zabura yayi yace na,am ummi.</p><p><br /></p><p> ahankali ummi tace banga kana da niya bawa fatima takarda ba kamar yadda daddyn ku ya bukata.</p><p><br /></p><p> wata guntuwar murmushi yayi sannan yace </p><p><br /></p><p> kai ummi yanzon daga kan wannan yar karamar maganan sai ace na saketa, haba ummi ai koshi ma daddyn daya fad'a wasa yakeyi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> waye ya fad'a maka wasa yake Kai bakasan yadda ya dauki abin ba dan yadda yake son fatima ko Ku daya haifah baya sonku haka.</p><p><br /></p><p> nan danan fuskar haydar ta sauya ya fara kokarin mikewa ummi ta kalleshi tace ina kuma zaka muna mgn?</p><p><br /></p><p> cikin daure fuska yace ummi kaina ne yake min ciwo zanje na kwanta anjima idan daddy ya dawo zan bashi hakuri.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> murmushin takaice ummi tayi sannan tace aidama nagane nufin ka kaje Allah ya baka sa,a tunda ban isa nabaka shawara kaji ba .</p><p><br /></p><p><br /></p><p>tsayawa yayi yai shiru zuwacen yayi mgn ahankali ummi bahaka bane amman bari naje nadawo sai muyi mgn.</p><p><br /></p><p>toh kawai ta furta dan haka haydar ya fita da sauri.</p><p><br /></p><p> be dawo gidan ba saida daddare guri karfe 9:30 lokacin daya tabbatar daddy yana gida</p><p><br /></p><p> barayin su ya shiga yayi wanka ya feshe jikin shi da turare masu kamshi.</p><p><br /></p><p>tsayawa yayi ya taje gashin dake kanshi sosai , kyau yayi ba kadan ba dumin kuwa Aliyu haydar namiji ne me cikar suffa da kyan kira duk wani abu da ake bukata awajen namiji Aliyu gadan ga kusar yaki ya had'a su, nima kaina tsayawa nayi na kare masa kallo gsky Allah yayi halitta anan gurin , take tunanin *hafsat* ya fado min ta cikin Fadeela Lamido novels group da tace wai haydar bayi da kyan kira, Hmmm wlh badan ina tsoron kar haydar ya hada miki jini da majina ba dana fad'a mishi😜 dan gsky haydar fa akwai zuciya.</p><p><br /></p><p> fitowa yayi cikin kasaita amman zuciyar shi cike yake da fargaba ko daddy zai saurare shi?</p><p><br /></p><p> sallam yayi abakin falon ya shiga</p><p><br /></p><p><br /></p><p>ummi na ganin shi ta daure fuska kasa yayi da kansa ya nemi guri ya zauna.</p><p><br /></p><p> bayan ya gaida daddy be sake cewa kome ba , ummi da daddy hirar su suka ci gaba dayi .</p><p><br /></p><p><br /></p><p> zuwa cen daddy ya kalli agogo yace</p><p><br /></p><p> " kai bazaka tashi kaje ka kwanta bane?</p><p><br /></p><p>gyara zama yayi ya zauna akan gwuiwan sa yasa hannun shi daya yana sosa keyan sa.</p><p><br /></p><p> daddy ya kara daure fuska yace ko akwai wani abu ne?</p><p><br /></p><p><br /></p><p> cikin sanyin murya yace daddy nazo na baka hakuri ne naga jiya fatima bata dawo d'aki ba, wlh daddy ni ban dake ta ba..... daddy ne ya katseshi ai dama baza kasan ka daketa ba tun da kasha ka koshi katashi maza kabani guri.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> shiru yayi kuma yana nan a inda yake sai yau yasan fatima ta zama wani bangare na jikin sa domin ji yake yau idan daddy be bashi fatima ba , toh yau bazai iya bacci ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> hawaye ne suka fara zubo mai daddy ya bishi da kallo take tausayin sa ya kamashi Amman sai ya dake yace wai haydar banace ka fita kabani guri bane.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Saida ya share hawayen sannan yace daddy wlh zan iya rantsewa da Qur,ani ban dake fatima ba.</p><p><br /></p><p> shiru daddy yayi zuwa can yace jeka ka kiramin fatima.</p><p><br /></p><p> zuwacen suka shigo yana gaba fatima na baya ummi ko tana zaune ta had'a fuska.</p><p><br /></p><p> daddy ne yayi mgn cikin kausasassiyar murya fatima haydar yace wai be dake kiba, yace zaiyi rantsuwa ko kema zaki iya rantsuwa cewa ya mare ki?</p><p><br /></p><p> shiru tayi tana wasa da yatsun hannun ta hankalin ta tashe.</p><p><br /></p><p> daddy ma kallonta yake yana na zari zuwa cen ya sake cewa mamana yanaji kinyi shiru?</p><p><br /></p><p> nan ma bata ce komi ba.</p><p><br /></p><p> daddy ya danyi murmushi sannan yace</p><p><br /></p><p> ga dukkan alamu mamana bata da gsky.</p><p><br /></p><p>kuka ta fara duk suka bita da kallo, ahankali daddy yace fatima ki gayamin menene ya faru.</p><p><br /></p><p>Cikin kuka tace ai shine yaje gurin mama ya kullamin sharri yasata ta dake ni, ta kwashe komai ta fad'a .</p><p><br /></p><p>dariya daddy yayi sosai San nan yace toh ai baki yi lefi ba kinyi daidai ' san nan yace kai kuma kaSan bakaso me yasa ka bata kayan kace ta saka.</p><p><br /></p><p> cikin sauri haydar yace daddy aini bance ma mama kome ba, nidai kawai nace ne abata hijjab.</p><p><br /></p><p> fuskar daddy sake yace toh yanzon dai haydar kayi kuskure Saika kiyaye gaba, ya juya ya kalli ummi yace baki ce kome ba.</p><p><br /></p><p> toh Alhj me zance aini yanzon haydar yafi karfi na.</p><p><br /></p><p>nisawa yayi sannan yace nagama duku kutashi Ku tafi.</p><p><br /></p><p>fatima ce ta fara mikewa tayi gaba tana kuka.</p><p><br /></p><p> tana fita daga barayin su ummi kafin ta karasa nasu taga wata bakar mage, aguje ta juya tana ihu daidai lokacin haydar yafito , ji yayi kawai an cikuikuye shi duk da haka bata natsuba sai kara kwakume shi take.</p><p><br /></p><p>rungumeta yayi sosai ajikin shi yana fidin fatima menene?</p><p><br /></p><p> gani yayi bata da niyar mgn dan haka ya dauketa cek .</p><p><br /></p><p> kan gadon shi ya ajeta amman sai taki kwanciya tana dad'a kamashi, tuni yanayin jikin shi ya fara cenzawa shima gadon ya hau ya jawota jikin shi sannan yace fatima menene ya baki tsoro ?</p><p><br /></p><p>ahankali tace mage ce.</p><p><br /></p><p>murmushi yayi sannan yace yanzo magen ce tasa kk rude haka?</p><p><br /></p><p> bata ce kome ba ta Kara mannewa ajikin shi tana maida ajiyan zuciya.</p><p><br /></p><p> ahankali ya fara buga bayanta ji yayi kamar tayi bacci dan haka ya fara shafata.</p><p><br /></p><p> zabura tayi ta mike sakamakon hannu haydar da taji akirjin ta.</p><p><br /></p><p> saida takai karshen gadon sannan ta tsaya.</p><p><br /></p><p> shiru haydar yayi yana maida nunfashi gsky yau banzan iya hakuri ba dan tariga ta motsomin sha,awa ta ,tunanin da yayi kenan azuciyar shi , dan haka ya dauki wani filon shi me laushi ya jefeta dashi.</p><p><br /></p><p> ihu ta kurma ta daka wini uban tsalle ta dire jikin haydar tana fadin yaya haydar dan Allah ka rakani gurin ummi</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊🕊</p><p>[7:59PM, 4/20/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>76 - 78</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kara menneta yayi ajikin shi sannan yace ki kwanta kawai babu abinda zai same ki.</p><p><br /></p><p> cikin kuka tad'an ture shi tace nidai gsky kazo karakani bazan iya kwana anan ba.</p><p><br /></p><p> daure fuska yayi sannan yace ke babu inda zani idan zaki kwanta ki kwanta ni karki dame ni.</p><p><br /></p><p>bata kara cewa komai ba ta lafe ajikin shi, zuwa cen taji ya ci gaba da taba ta , da sauri tasa hannunta tana tura nashi daga jikin ta.</p><p><br /></p><p> cikin raunanan niyar muryar yace ki bari mana nifah mijin ki ne.</p><p><br /></p><p> a,a bawani miji ni gaskiya ka bari bana so.</p><p><br /></p><p> ahankali ya sake fadin nima ai ba cewa nayi kina so ba nine nake son hakkina.</p><p><br /></p><p> tashi tayi tsam daga jikin shi tana kokarin sauka agadon.</p><p><br /></p><p> da sauri ya jawota yace wlh idan baki daina ba zan fita na rufeki ad'akin nan bagen ta kashe ki.</p><p><br /></p><p> cikin sauri ta tura kanta cikin kirjin shi tana fadin nabari</p><p><br /></p><p> ai daga nan haydar ya samu abin da yake so domin kuwa kwanciya tayi kamar me bacci haka haydar yayita wasa da ita, jin da fatima tayi yana neman ya wuce iyaka yasa ta fara kuka domin har ya fara raba ta da kayan jikin </p><p><br /></p><p> koda yaji tana kuka be saurara mata ba illah ma karfi daya fara gwada mata dan yaga kokarin guduwa take.</p><p><br /></p><p> Nidai danaga haydar da gaske yakeyi tashi nayi suf suf nabar musu d'akin.</p><p><br /></p><p> ina daga bakin kofah, zuwacen na fara jiyo ihun fatima tana kuka meban tausayi tana ma haydar magiya kayi hakuri dan Allah dan darajan annabi ka kyaleni, waiyo Allah na nashiga uku , haka fatin taita kuka saida aka kira sallahn subahi sannan haydar yabar fatima, idan me karatu be manta ba haydar dama ta wannan fannin ba daga nan ba.</p><p><br /></p><p> ********</p><p><br /></p><p> wanka ya fito ya tsaya yana karewa fatima kallo kai gaskiya yau ya kwashi garan da be taba jin irin shiba Ashe duk tarin yan matan da yake dashi duk shirme ne, fatima da yake rainawa yake ganinta kamar wata yar kauye ta fisu gard'i kallonta yayi yaga ta kwanta kamar gawa azuciyar shi yace Allah sarki Fatima anya kuwa zaki iya daukan d'awai niya ta, da wannan tunanin ya wuce masallaci, </p><p><br /></p><p><br /></p><p> yana fita fatima ta bude idon ta ahankali hawaye ne ya biyo baya, ahankali ta zame ta sauka akan gadon, da rarrafe ta shiga toilet.</p><p><br /></p><p> zuwacen ta fito tana bin bango ahankali ta tsuna ta dauki duguwar rigarta dake yashe akasa ta maida jikinta domin babu kayanta ko guda daya adakin haydar , taso ta fita adakin ta koma nata amman bazata iya ba dan haka ta koma kan gadon ta kwanta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> bata dade da kwaciya ba haydar ya dawo, kai tsaye ya nufi bakin gadon yana kallonta ya gane tayi wanka amman idonta har yanzon arufe yake.</p><p><br /></p><p> saitin kunneta yaje yace zahra shine kk koma kan gadon baki bari na gyara miki ba.</p><p><br /></p><p> da sauri ta bude idonta dan ji tayi kaman salis ne ya kira sunan ta tana ganin haydar tamai da idonta ta rufe, ta fashe da kuka.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>hannun shi yakai ya taba gushinta yace yi hakuri fatima ki daina kuka.</p><p><br /></p><p> itama hannunta takai ta bige nashi taci gaba da kukanta.</p><p><br /></p><p> shiru yayi na wasu dakikai yana tunani zuwacen yace</p><p><br /></p><p><br /></p><p> fatima dan Allah kiyi hakuri ki daina kukan nan zai iya jawo miki wani ciwon, kinji</p><p><br /></p><p> batace dashi komai ba haka yayita mgn har ya gaji karfe 8:00 yace fatima zantafi Office kinga lokaci ya kure.</p><p><br /></p><p>banza tayi dashi har ya fice.</p><p><br /></p><p> ummi naganin haydar gabanta ya fadi saboda yadda ta ganshi da ganin shi akwai abin da yake damun shi tace haydar yadai me kake yi har yanzon baka wuce office ba?</p><p><br /></p><p> jikin shi asanyaye yace makara nayi yazon zan wuce, Ina taslim ne ?</p><p><br /></p><p> da sauri ta fito daga kitchen tana fadin gani.</p><p><br /></p><p> ko kallonta beyi ba yace fatima na kiran ki.</p><p> toh kawai tace a takaice.</p><p><br /></p><p> koda taslim taje fatima bata daina kuka ba kuma bata ci abinci ba haka ta gaji da tambayan ta meya sameta, amman babu amsa.</p><p><br /></p><p>ahaka har aka kwashe kwana biyu yadda aka aje abincin fatima haka ake dauka, haydar ko yayi lallashin har ya gaji dan haka abin ya fara bashi tsoro.</p><p><br /></p><p>ranar da suka cika kwana 3 ahaka da safe haydar yana zaune afalo taslim ta shigo, gaidashi tayi ta nufi dakin fatima.</p><p><br /></p><p>muryan haydar taji ya kira sunnanta ta dawo ta tsaya ,cikin sanyin murya yace</p><p><br /></p><p> taslim wai fatima batacin abinci ne kwata kwata ko akwai wani abun da take sone daban.</p><p><br /></p><p> tace yaya wlh nima ba yadda banyi da ita ba, ta fadamin abin da take so na dafa mata, amman ko mgn bata min.</p><p><br /></p><p>cikin mamaki yace kina nufin kema bata miki mgn?</p><p><br /></p><p>kaita daga. yasake cewa ummi ta sani?</p><p><br /></p><p> eh nagaya mata tace wai babu ruwanta.</p><p><br /></p><p>Shiru yayi zuwa cen yace shike nan jeki.</p><p><br /></p><p>tana shiga haydar ya mike gurin ummi ya nufah.</p><p><br /></p><p>tana zaune afalo tana amsa waya kusa da ita yaje ya zauna ya daura kanshi akafadar ta.</p><p><br /></p><p> tana gama wayar ta waigo ta kalleshi tace yadai na fatima meya same fatiman taka kwana 2 ?</p><p><br /></p><p> cikin shagwaba yace ummi bayan kinsan halin da muke ciki amman baki kula muba.</p><p><br /></p><p> d'an murmushi tayi kad'an tace aini baku sakani aciki ba, sai kanwarka ka kira.</p><p><br /></p><p>murmushi yayi kadan sannan yace</p><p><br /></p><p>toh ummi ai ta kasa dole sai kinsa mana baki.</p><p><br /></p><p> tace toh inajin ka menene ya faru?</p><p><br /></p><p>saida yayi kasa dakai sannan yace ummi laifi na mata kuma na lallasheta taki kulani.</p><p><br /></p><p>da saurinta tace toh yanzon me kk son ayi?</p><p><br /></p><p>dagowa yayi suka hada ido da ummi sannan yace ummi hakuri zaki bata.</p><p><br /></p><p>kallon shi tayi sosai sannan tace ikon Allah ashe akwai lokacin da zanga wannan ranar, haydar ashe taurin kanka na banza ne tunda gashi lokaci 1 mace na shirin susutaka, wai yau kaine ke rokon aba fatima hakuri.</p><p><br /></p><p> mumurshi yayi sannan yace nimafah bansan yadda akayi na samu kaina ahaka ba, ummi idan fatima na cikin damuwa sainaji duk banajin dadi</p><p><br /></p><p> itama tana murmushi tace aini tuni na lura da haka, saidai fani gsky yadda fatima take nuna kiyayyar ka haushi take bani.</p><p><br /></p><p>da sauri yace ummi ki daina jin haushin ta, in Allah ya yarda Wata rana zata bari.</p><p><br /></p><p>mikewa ummi tayi tace toh shikenan haydar tunda kaji ka gani tashi muje naga ginbiyar taka.</p><p><br /></p><p>suna cikin tafiya ummi ta kalli haydar tace haydar bari na baka wata shawara kaga wannan kananan kayan kadaina saka su karinka saka manyan kaya kamar yadda salis keyi, d'aga kanta tayi ta kalli gashin kanshi tace haba haydar ai ko nice fatima bazan soka ba jifa inda ka tara gashi saikace bishiya, wannan gashin naka bazai rasa wari ba.</p><p><br /></p><p> da sauri ya tintsere da dariya ya tura mata kan yace haba ummi shinshina kiji kullum fah sainaje an gyaramin shi.</p><p><br /></p><p>da sauri ta kauda fuskarta tace bazan shinshina ba, kaje ka askeshi kawai.</p><p><br /></p><p>yana dariya yace toh shikenan ummi zan aske</p><p><br /></p><p>da haka ummi ta tura d'akin fatima ta shiga haydar nabinta abaya.</p><p><br /></p><p> taslim ko na zaune agefen fatima tana danna wayar ta yayin da fatima ke kwance agado tayi ruf da ciki.</p><p><br /></p><p> ummi ta kalli taslim tace har yanzon dai zaman kuramen kuke?</p><p><br /></p><p> taslim tace toh ummi taki magana.</p><p><br /></p><p>karasawa bakin gadon ummi tayi ta zauna sannan ta dafah bayan fatima tace fatima</p><p><br /></p><p>can ciki ciki ta amsa, ummi ta sake cewa tashi ki zauna.</p><p><br /></p><p>ahankali ta fara kokarin tashi haydar ko nacen gefe kamar munafi hannuwan shi cikin aljihun shi.</p><p><br /></p><p> baya ta zauna ummi ta kalleta sosai taga har tadan fad'a tace.</p><p><br /></p><p> fatima wai meke damunki ne haka me yayi zafi?</p><p><br /></p><p>nan danan hawaye ya fara zubo mata zuwacen ta fashe da kuka.</p><p><br /></p><p> da sauri ummi ta jawota jikinta ta rugume tana fadin ya isa.</p><p><br /></p><p>daker ummi ta shawo kan fatima tayi shiru , shiko haydar tunani yake azuciyar shi wannan wacce irin yariya ce.</p><p><br /></p><p> ummi ta sake cewa haba 'yata kidaina daukan abu da zafi haka, haydar ya fad'amin shine ya miki laifi , kisan abin da nake so dake daga yau idan ya sake bata miki rai kizo ki gayamin duk hukun daya dace dashi ni zanmai karki kara tada hankalin ki, kinji ?</p><p><br /></p><p>ahankali ta daga kai.</p><p> </p><p>ummi tace yauwa ko kefah yanzon dai mgnr ta wuce ko?</p><p><br /></p><p> murya cen ciki tace eh.</p><p><br /></p><p>toh Sakko kici abinci.</p><p>sakkowa tayi ummi da kanta ta zuba mata .</p><p><br /></p><p>kwana biyu haydar ya dan samu sauki gurin fatima dan yanzon bata harara shi kuma yanaji tana mgn da muta ne </p><p><br /></p><p> </p><p> fatima ce zaune adakin ummi suna hira ummi tace fatima yaushe zaki fara girki ko kunfi son kuyita cin namu.</p><p><br /></p><p> ta bude baki kenan zatayi mgn haydar ya yayi sallama ya shigo.</p><p><br /></p><p> tana daga kai ta kalleshi,tsaye yake cikin manyan kaya wad'an da suyi matukar karban shi ta zabura aguje ta nufeshi kamshi turaran da taji shi ya tabbatar mata dawa cewa ba salis bane dan bada wannan turaren yake amfani ba tsugunawa tayi ta fashe da kuka.</p><p><br /></p><p> ummi ma hawaye ne ke zuba a donta, shima kansa haydar d'in fatima ta bashi tausayi </p><p><br /></p><p> juyawa yayi ya koma barayin su cikin tashin hankali yana zama ya fashe da kuka.</p><p><br /></p><p> fatima ko bataso haydar ya fita ba ji tayi tana balakin son ta hada ido dashi dan idan ta kalleshi ji take kamar taga salis dan haka cikin sauri ta mike ta nufi dakin su.</p><p><br /></p><p> tana shiga ta samu haydar zaune afalo idon shi jawur.</p><p><br /></p><p> zama tayi akujeran dake kallon nasa ta kure shi da ido tana hawaye.</p><p><br /></p><p> mikewa yayi yazo gabanta ya tsuguna ya fara share mata hawayen yana fad'in baxan kara saka irin wannan kayan ba fatima, da nasan cewa zaku shiga wannan yanayin har kuna zubar da hawaye ke da ummi da banyi ba, cire hular dake kansa yayi aje agefe.</p><p><br /></p><p> da sauri fatima takai hannunta ta dauka ta daura mai akai tana fadin karka daina yaya wad'an nan kayan sunfi maka kyau.</p><p><br /></p><p> ya bude baki zaiyi mgn wayar shi tayi kara, ciro wayar yayi a aljihun sa ya duba sannan ya aje agefen fatima, mikewa yayi ya fita da sauri yana fadin Ina zuwa fatima.</p><p><br /></p><p> harya kule fatima na kallon shi , yana fita ta juyar da kallon ta gawar da ya bari da sauri ta dauki wayar tana share hawaye, ta shiga dannawa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Toh masu karatu gadai fatima ta dauki wayar haydar KO me zai faru ?*</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p>🕊🕊</p><p> Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[8:59PM, 4/21/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>79 -80</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tsinta kanta tayi dason kallon hoton dake wayar dan haka ta fara dubawa.</p><p><br /></p><p>dayawa daga cikin hotonan haydar ne shi da salis wani suna dariya wani kuma kaga sun ware kamar zasuyi danbe, kallo take tana hawaye tana tuna soyayyar da salis ya nuna mata, kai da ace har yanzun salis na nan tohni yar gata ce, da wannan tunanin ta fita daga gurin .</p><p><br /></p><p>wani gurin ta sake bud'awa innalillahi wa inna ilaihir raju,un shine kallaman daya fara zuwa bakin ta domin kuwa hotunan haydar ne birjik tare da yanmata kala kala cikin shigar lalacewa da nuna tsaraici domin kayan dake jikin su dashi gara babu, kwata kwata babu kyan gani.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> take taji wani haushi ya taso mata wani bacin rai taji wadda rabon da taji irin shi tunda akace za,a had'ata aure da haydar.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> hawaye taji suna zubu mata, da sauri tasa hannunta ta shafo ta kallah, menene wannan ? tabayar da tayiwa zuciyar ta kenan, kardai ace son haydar nake, dakuwa naci amana, naso wa kuma dan bani da hankali sai naso kani.</p><p><br /></p><p>mike wa tayi ta aje wayar har ta juya sai kuma ta dawo ta sake daukan wayar wani bangaren ta sake shiga hotun haydar ne shida anas zuwacen ta ?fara cin karo da wasu hotuna da suke neman dauke numfashin ta. bakinta bude ido bude duk sun firfito waje take kallon hotun tabas wannan itace lokacin da take amsa sunan daniju, wanda ko ke kanta haydar ne gashi nan danne da ita akan kujerar motar yana kokari yage mata riga take sunan da anas ya kira haydar dashi kwanaki ya fado mata BIG BOY</p><p><br /></p><p> take ta kwallara wani kara saida gidan gaba daya ya amsa, jitayi kafafuwan ta bazasu iya daukan ta ba dan haka ta fadi kasa timm.</p><p>,</p><p> aguje su ummi suka shigo ita da taslim haydar nabin su abaya.</p><p><br /></p><p> a gaban fatima suka tsuguna suna kokarin dagata suna tambayan ta menene.</p><p><br /></p><p> shi ko haydar fadi yake ummi yanzon haka mage ta gani kisan matsoraciya ce.</p><p><br /></p><p> fatima KO hannu ta daga tana kuka take nuna haydar tana fadin shine wlh haydar ne shine wanda ya cuceni , wlh shine ummi, shine gashi nan agaban ki Allah ya tonamai asiri.</p><p><br /></p><p> haydar sakin baki yayi yana kallon fatima</p><p><br /></p><p><br /></p><p>ummi ko gani take kamar fatima aljanu gareta.</p><p><br /></p><p> dan haka tacewa taslim kiramin daddyn ku ya samo mana malami amata rukiya.</p><p><br /></p><p> Matsowa haydar yayi yana fadin babu wani aljanu ummi yanzun haka be wace mage ta......... wayar shi daya hango agefen fatima shine ya dakatar dashi da sauri yakai hannun shi ya dauki wayar , zamewa yayi akasa ya zauna sannan ya cire hular dake kansa ya fara fifita yana fadin Inna lillahi wa inna ilaihir raju,un.</p><p><br /></p><p> da sauri ummi ta juya gurin haydar tace toh kaikuma meya same ka.</p><p><br /></p><p> basu ankara ba sukaga fatima tayi waje aguje, yayin da haydar ke fadin shikenan ummi nashiga uku.</p><p><br /></p><p> taslim ce tabi bayan fatima da gudu ummi ko tana gun haydar sai fifita take mai zuwacen ta fara girgiza shi tana fadin haydar wai meke faruwa kar ku maidamu mahaukata mana.</p><p><br /></p><p> itako taslim ko da ta fita kofar gidan babu fatima babu alamarta juyawa tayi tana kuka.</p><p><br /></p><p> tana shiga tace ummi ban ganta ba.</p><p><br /></p><p> da sauri haydar ya daki bango.</p><p><br /></p><p> cikin bacin rai ummi tace taslim wuce muje tunda bazai gaya min abin da ke faruwa ba, Allah ya baku sa,a.</p><p><br /></p><p> ummi tana komawa barayin su ta kira daddy awaya ta fad'a mishi halin da suke ciki.</p><p><br /></p><p> ba,a dade ba saiga daddy ya shigo d'akin su haydar ya fara shiga, samun shi yayi ya hada kai da gwaiwa.</p><p><br /></p><p> kiran sunan shi yayi haydar, da sauri ya dago kai ya kalleshi yace taso muje.</p><p><br /></p><p>mikewa yayi sumi sumi yabi bayan shi bayan sun shiga motar daddy sun zauna daddy ya kalleshi sosai yace </p><p><br /></p><p> " me ya hadaka da fatima harta wuce gidana ta tafi gidan mahaifin ta?, babanta yayi min waya cewa gata tazo ko mayafi babu kuma tunda taje ta kasa mgn illah fadin haydar ne, haydar ne, me ka mata dahar ta shiga wannan yanayin ?</p><p><br /></p><p><br /></p><p> kasa mgn yayi ya dukar da kanshi cikin matsanan cin tashin hankali.</p><p><br /></p><p>daddy yasake yin mgn haydar badakai nake mgn back.</p><p><br /></p><p>nan ma shiru babu amsa</p><p><br /></p><p><br /></p><p>daddy yace kana nufin bazakayi mgn ba kenan?</p><p><br /></p><p> kara dukar da kanshi yayi kasa danji yake kamar kasa ta bude ya shiga.</p><p><br /></p><p> kallon shi daddy yayi cikin takaici sannan yace </p><p><br /></p><p> nakula baka da gsky tunda gashi ka kasa mgn , ummi ya kira awaya tana dauka yace dauko gyalen ki kizo muje , basu juma ba ummi ta fito.</p><p><br /></p><p> gidan alhj yusuf suka nufah.</p><p><br /></p><p> suna shiga cikin falon fatima ta mike da saurinta tace baba gashinan yazo shine macucin dakace idan ka ganshi zaka karban min yanci na , yau gashi agaban ka.</p><p><br /></p><p> baba ne ya daka mata tsawa sannan yace koma ki zauna .</p><p>batayi musuba ta koma ta zauna sannan ta runtse idonta tace wlh baba bana son ganin haydar arayuwata tunda na fara sanin kaina yake cuta ta.</p><p><br /></p><p>ahankali daddy ya matso inda take yace fatima gayamin wanne irin cutar dake haydar keyi?</p><p><br /></p><p> kowa afalon ita yake kallo , haydar ne kawai kansa ke kasa.</p><p><br /></p><p>cikin kuka fatima tace daddy haydar shine mutumin da yayi min fyade tun da kankanin kuruciya ta.</p><p><br /></p><p>ummi ce ta mike dafe da kirji tace lallai fatima yau na tabbatar baki kaunan haydar ai basai kinmai sharri ba, dan kina son rabuwa dashi , muyar daddy taji yana fadin </p><p><br /></p><p> ke banson mgnr banza keda kk wannan surutun shi haydar din kinga ya musa ne.</p><p><br /></p><p> da sauri ummi ta kalli haydar taga ya kasa daga kan shi sai hawayen dake digowa, itama kuka take tace haydar da gaske ne?</p><p><br /></p><p> bece komai ba illah kukan sa daya karu har mutanen dake falon na iyajin sheshshekan kukan sa.</p><p><br /></p><p> kuka ummi ta fashe dashi tana fadin nashiga uku Allah ka dauki raina na huta daganin wannan abin takaici.</p><p><br /></p><p>mama ce ta dafah ummi tace bar kuka dan Allah ai tama kona gidan sauki.</p><p><br /></p><p> cikin fada daddy yace wanne sauki ai babu wani sauki, Kai haydar maxa katashi kabar wajen nan tun kafin na kwashe maka albarka, kuma aure tsakanin ta dakai babu dan iska me abin kunya kawai ina takaicin ka amatsayin dana tari ya fara babu kaukautawa haydar ya tashi da sauri ya nufeshi, tun kafin ya karaso daddy ya daga mai hannu cikin tsananin tarin yace idan ka sake ka tabani Allah ya isa tsakani na dakai.</p><p><br /></p><p> kuka ya tsaya yanayi , baba yace kai haydar jeka kawai .</p><p><br /></p><p> cikin matsanan cin tashin hankali ya fita waje, wani haushin anas yaji yana taso mai, wai wace ma ya dauki hoton, duk shine yaja mai wannan tashin hankalin dana ke ciki, cikin zafin zuciya ya nufi mota yau anas saiya ci uban shi,zai gayamin uban waye yasashi ya dauki hoton</p><p><br /></p><p> </p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊</p><p>[8:33PM, 4/22/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>79 - 81</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kai tsaye gidan su anas ya nufah yana isa ya fito daga motar ko rufeta beyi ba, d'akin anas ya tura.</p><p><br /></p><p> anas naganin haydar abirke ce ya mike da sauri kafin ya bude baki haydar ya kaimai duka abaki, tuni bakin ya fara jini amman duk da haka bebari ba duka kawai yake aika mai , shiko anas yana dafe da bakin shi yake fadin haydar ka bari mana menene haka baka da hankali ko, mena maka, ganin da yayi haydar besan yanayi ba yasa ya fara ramawa.</p><p><br /></p><p> mahaifiya anas ce ta fito da gudu tsakiyan su ta shiga tana fadin kai kai ku bari menene haka kuma, kai haydar anas kubari, bazaku bari ba ko saina kira maza, basuma san tanayi ba gashi gidan babu kowa me gadin ma ta aikeshi dan haka ta fashe da kuka.</p><p><br /></p><p>ganin mahaifiyar anas na kuka yasa suka saki juna , da sauri haydar ya juya ya fita momy nakira kai haydar zo nan , ina harya tada mota.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> yana shiga gida dakin ummi ya shiga ya sameta zaune kanta babu dan kwali ta kwanta akan kujera ta daga kanta sama tana girgiza kafah ga kuma hawaye nabin fuskar ta.</p><p><br /></p><p> jikin shi asanyaye yaje gabanta ya tsuguna ya rike kafar ta yace</p><p><br /></p><p> " ummi dan Allah kiyi hakuri ki yafe min, ummi kidaina zubar da hawaye akaina"</p><p><br /></p><p><br /></p><p> cikin kuka tace haydar ka tashi kabani guri bana son ganin ka , dan ka bani mamaki kuma kabani kunya idan banyi kuka ba me kake son nayi, haydar ashe ka dad'e kana shiga kyauye kyauye kana lalata yaran mutane.</p><p><br /></p><p> cikin kuka yace ummi wlh ba haka bane itama wannan tsautsayi ne, momyn su ansa ce ta aikeshi gurin yayanta , shine yace narakashi, wlh ummi muna kokarin shiga wauyen ne muka hadu da ita.</p><p><br /></p><p> da sauri ummi tace kaikuma dayake bunsuru ne baka gani ka bari KO, ashe shiyasa lokacin da salis yanuna yana sonta kaita tsoro da tsurfa kala kala, wlh haydar bakayi ba kayi asara wlh, ni kuma kasani takaici ka shayar dani bakin ciki , inama kai aka dauke aka barmin salis</p><p><br /></p><p><br /></p><p>kuka haydar ya fashe dashi sosai sannan yace kiyi hakuri ummi in Allah ya yarda zan zama kamar shi.</p><p><br /></p><p> cikin kuka ummi ke girgiza kai tana fadin bazaka taba zama kamar shi ba salis mutumin kirki ne , kwata kwata ba halin ku daya ba har yabar duniya bazan ce ga abinda yamin ba kai kuwa fah, tun kana karami kake batamin rai .</p><p><br /></p><p> yana kuka yana rokon ummi ta yafe mai amman ina daga karshe ma tashi tayi tabarshi agurin.</p><p><br /></p><p>tashi yayi ya koma barayin su yaci kukan shi ya koshi gashi besan wanne hali daddy yake ciki ba.</p><p><br /></p><p> haka ya kwashe kwana biyu adaki dan ko sallah agida yakeyin ta babu ci babu sha duk yayi baki ya rame.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ummi ma zuwa wannan lokacin tayi kuka harta gaji.</p><p><br /></p><p> </p><p> daddy ne kwance a turakar sa yayin da alhj yusuf ke zaune agefen shi yana mai yajiki.</p><p><br /></p><p> ahankali daddy yace naji sauki yusuf, Ina fatima fah?</p><p><br /></p><p> fatima tana nan lfy tace agaida ka.</p><p><br /></p><p> dan murmushi yayi kadan sannan yace nagode.</p><p><br /></p><p> zuwacen ya sake cewa kaga abinda haydar yayi KO, ashe duk surutun da mukeyi kallon mu kawai yakeyi , ya maida mu shashatai.</p><p><br /></p><p> dan dukar dakai alhj yusuf yayi kad'an sannan yace toh ya za,ayi sai hakuri kawai, itama fatiman tana cen tana cigaba da haukanta wai ita sai dai ya sake ta, nace zama tayi tabari ne.</p><p><br /></p><p> cikin zafi daddy, yace ai indai ina raye mamana baza dawo dakin haydar ba, me zatayi da dan iska.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf da sauri yace yaya dan Allah ka dunga gyara kalaman ka akan haydar kai fah uba ne, kuma ai wannan abun daya faru da ne yanzon ya natsu.</p><p><br /></p><p>Hmmm haka kake gani.</p><p><br /></p><p>*****</p><p><br /></p><p>ranar da haydar ya cika kwana 4 adaki hankalin ummi ya tashi dan ko motsin shi bata ji</p><p><br /></p><p><br /></p><p>kasa hakuri tayi taje ta samu daddy domin ta sanar dashi halin da ake ciki.</p><p><br /></p><p> tana shiga tace alhj haydar fah bana ganin wucewan shi kuma na tambayi me gadi yace shima ya dade be ganshi ba.</p><p><br /></p><p> da sauri ya daka mata tsawa bana son na sake jin kin kiramin sunnan haydar a gidan nan idai kina son zaman lfy, hannushi ya kad'a sannan yace fita ki bani guri.</p><p><br /></p><p> tana kokarin fita daddy ya fara kwalawa taslim kira.</p><p><br /></p><p> lokacin da ummi ta zauna afalo taga wucewan taslim aguje zata gurin kiran daddy, zama tayi ta dafe kai.</p><p><br /></p><p> zuwa cen sai ga daddy ya fito taslim na binshi abaya ko sallama bema ummi ba ya fita abin shi, taslim ko zama tayi kusa da ummi.</p><p><br /></p><p> ummi juyowa tayi ta kalli taslim tace taslim tashi kije dakin haydar ki gani lfy yake.</p><p><br /></p><p> wasa taslim ta fara yi da yatsun ta sannan tace ummi daddy fah yace idan naje gurin yaya haydar be yafemin ba.</p><p><br /></p><p> da sauri ummi ta dafa kirji wato alhj abin har yakai haka afili tace au haka ya fad'a miki zumunci zai raba kenan toh bazai yiyuba ainima ina da hakki akan ki, maza kije ki duba dan uwanki.</p><p><br /></p><p>kuka taslim ta fara tana buga kafa asa tana fadin dan Allah ummi karku sani acikin wannan mgnr.</p><p><br /></p><p>mikewa ummi tayi tana fadin kada Allah yasa kije ,fita tayi ta shiga dakin su haydar.</p><p><br /></p><p> makure ta sameshi akan gadon shi ya rufah da bargo, tana zuwa ta yaye bargon , kallonta yayi da jajayen idon shi, ya fara kokarin tashi.</p><p><br /></p><p>ahankali tace baka da lfy ne?</p><p><br /></p><p> wasu safbin hawaye ne suka zubo masa sannan yace.</p><p><br /></p><p>hakalina ne yaki natsuwa ummi damuwa yamin yawa saiyau nasan nayi rashi, ummi wlh nasan da ace salis na nan bazai gujeni ba kuma ko ya guje ne bazai wuce kwana daya ba, ummi dan Allah karki gujeni kizaman min kamar salis.</p><p><br /></p><p> da sauri ummi ta toshe mai baki tace ya isa ya wuce haydar</p><p>tashi kaje kayi wanka.</p><p><br /></p><p>itako fatima yau tun safe take kuka tun da mahaifinta ya shaida mata ta shirya yau haydar zaizu su tafi gida.</p><p><br /></p><p> dan haka ta wuni tana kuka.</p><p><br /></p><p> 4:15pm mama ce ta fito daga d'aki ta kalli Fatima tace</p><p><br /></p><p> " wai har yanzon kukan kike, menene naki na tada hankali tunda kema kisan abinda kk so ba faruwa zaiyi ba.</p><p><br /></p><p> cikin kuka tace mama tohni wai meyasa baki sona ne ,daga ke har baba naga baku damu da abinda haydar yamin ba bayan da har cewa kukayi idan kuka samu wadda yamin haka sai inda karfin ku ya kare.</p><p><br /></p><p> shiru mama tayi zuwa cen tace fatima dama wulakanci muke guje miki amman kinga tunda Allah yasa shine ya aikata babu wani wulakancin da zaiyi miki.</p><p><br /></p><p>mama bata rufe baki ba fatima tace mama ai an mun wulakancin tun yaushe ummi ke fadin dan nasamu za,arufamin asiri ba dama nace bana son haydar saita gayamin irin wannan mgnr kuma duk ranar da naga ummi saina gaya mata mgnr da har ta mutu bazata manta ba.</p><p><br /></p><p> cikin fada mama tace karki fara fatima ni bana son fitsara, ai ko baki ce mata komaiba ta daiji kunya, kitashi maza ki shirya anjima zaizo ku tafi.</p><p><br /></p><p> muryan hjy yadikko sukaji tana fadin babu inda zata indai ina raye bazata koma gidan haydar ba me ake da dan iska, ke Fatima taso muje.</p><p><br /></p><p>tuni murna ya kama fatima da sauri ta dauki gyalenta tayi waje</p><p><br /></p><p> mama ce ta biyo bayan su tan a fadin hajiya dan Allah kiyi hakuri babanta ya riga yayiwa haydar waya anjima zai zo ya dauketa.</p><p><br /></p><p> hajiya na kokarin shiga mota take fadin waye baban nata, shima zaizo ya sameni.</p><p><br /></p><p> da daddare haydar ya nufi gidan alhj yusuf ciki da farin ciki saidai yana isa mama ta shaida mai abinda ke faruwa.</p><p><br /></p><p> be firgita ba domin shi aganin shi kakar tasu kayan sauki ce batare da bata lokaci yayi sallama da mama ya wuce gidan.</p><p><br /></p><p>yana sallama yaga hajiya zaune afalo, da sauri ta mike tana fadin waye nan, me ya kawo ka?</p><p><br /></p><p>ahakali yace hajiya nine fah.</p><p><br /></p><p>Eh ai nasan kaine mara kunya fitsararre, maza ka fitamin agida tun kafin nama uhu barawo.</p><p><br /></p><p>dan murmushi yayi kadan ya zauna akujera.</p><p><br /></p><p> tana ganin ya zauna ta fara kira me gadi zoka taimake ni barawo ne ya shigo min.</p><p><br /></p><p> aguje me gadin ya shigo yana fadin ina yake.</p><p><br /></p><p> haydar na kokarin kwanciya akujeran yana fadin baba jeka abinka rudun tsufa ke damunta.</p><p><br /></p><p> cikin fada tace uwarka ce mahaukaciya mara mutunci kawai.</p><p><br /></p><p> dasauri haydar ya tashi ya zauna yace karki kara.</p><p><br /></p><p> idan nakara fah dukana zakayi?</p><p><br /></p><p>nadai cemiki karki kara.</p><p><br /></p><p> cikin fada tace dan ubanka kai ba sa an yina na bane kaje ka turomin uwar ka dama ina da cikin ta.</p><p><br /></p><p> baza yayi da ita taita mgn ta gaji yaki kula ta dan yaga nema take tamai sharri.</p><p><br /></p><p>itako hajiya jinda tayi yayi banza yasa ta dauki wayarta no mahaifin haydar ta kira yana dauka ta fashe da kuka tana fadin kazo ka fitan min da d'anka daga gida gashinan yana neman duka na </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[6:38PM, 4/24/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>82 - 84</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mikewa haydar yayi yana fadin lallai hajiya abin kuma harda sharri.</p><p><br /></p><p>yana kokarin shiga dakin hajiya yana fadin kuma baki isa ki hanani ganin fatima ba.</p><p><br /></p><p> bayan shi tabi da sauri tana kai kai karka shigar min daki .</p><p><br /></p><p> yana sakai dakin yaga wayam babu fatima ya waiga gurin hjy yace Ina take?</p><p><br /></p><p> da saurinta tace tana gidan uwarka</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana kokarin bata amsa alhj yusuf shigo.</p><p><br /></p><p> da sauri haydar ya fara gaida shi hajiya ko tuni ta fara babatun tana fadin yauwa gara da Allah ya kawoka ka ganshi nan tun d'azon yake min rashin kunya kamar zai gogi kafada dani.</p><p><br /></p><p> Shiru alhj yayi zuwa cen yace kai haydar tashi ka tafi .</p><p><br /></p><p> mikewa haydar yayi cike da takaicin tsohuwar kakar su ya so ace ta bari ko ganin fatima ne yayi haka ya wuce yanata hararan hajiya.</p><p><br /></p><p> hajiya ta kalle shi ta juya tana cewa alhj yusuf kana ganin Inda yake gallamin harara ko?</p><p><br /></p><p> dan murmushi yayi sannan yace hajiya ai ba me shiga tsakanin ki da haydar zaku shirya ne.</p><p><br /></p><p>tana kokarin zama tace aini mun riga mun raba jaha, auren dama tuni tace banyi , itama fatima tace batayi sai akai kasuwa.</p><p><br /></p><p> shima zama yayi sannan yace hajiya hakuri za,ayi bawan da baya kuskure, kuma kinga yayi nadama.</p><p><br /></p><p>ina sam bazai yuwuba haka kawai yariya yar karama da ita yaje ya dauko cutar zamani ya manna mata, babanshi da kansa ya gayamin kwanaki har gida aka biyo shi da cikin shege, dan haka idan ku baku damu da lfyr yarku ba, ni kubarmin inaso.</p><p><br /></p><p>daidai lokacin daddy yayi sallama ya shigo, bayan ya zauna yace ina haydar din.</p><p><br /></p><p>alhaji yusuf yace ai ya tafi tuni.</p><p><br /></p><p>cizon lebe yayi sannan yace ai naso nazo na sameshi agidan nan , dana nuna mishi karyan iskanci yake, dan beda mutunci sai yaje yayi shaye shayen sa beje ya sauke akan mahaifiyar shiba saiya nufu tawa mahaifiyar.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf ya bata rai sannan yace babu abinda yasha ai nazo na sameshi , shi neman matar sa yazo, dan ninamai waya yazo ya dauketa toh kafin yazo kuma ashe hajiya taje tafi da ita.</p><p><br /></p><p>da sauri daddy yace da izinin wa zaka bashi matar tasa?</p><p><br /></p><p>shiru yayi zuwa cen yace nidai nafi son ta koma dakinta dan zaman beda wani amfani.</p><p><br /></p><p>daddy yana huci yace toh bazata koma ba, ko kanason ka nunamin karfin ikonka ne akanta, toh baka isa ba dole ne nayi iko da fatima kamar yadda zanyi da taslim, dan haka ninace bazata koma ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>cikin fara,a hajiya tace Allah yama albarka.</p><p><br /></p><p>shiko alhaji yusuf shiru yayi ranshi bace zuwa cen yace nidai alfarma nake nema dan Allah ayi hakuri abashi mat...... cikin fada daddy yace baza abashi ba idan kana iyawa kazo ka dauketa ka bashi.</p><p><br /></p><p> da sauri alhj yusuf ya mike ya fita fuuuuu.</p><p><br /></p><p>duk suka bishi da kallo hajiya yadikko tace au fushin banza kai tayi komawa ne dai bazata yi ba.</p><p><br /></p><p> shima daddy be dade ba yayi sallama ya tafi.</p><p><br /></p><p>washegari</p><p><br /></p><p>alhj yusuf na zaune afalon gidan sa, yana labartawa mama abinda ya faru, bayan ya gama mata bayani, tayi shiru tana nazari.</p><p><br /></p><p>zuwa cen tace alhj ajima zanje na ruki hajiya nasan data amsa daddyn su fatima shima zai sakko.</p><p><br /></p><p> da sauri yace a,a karkije yanzon kinayin mgn zasu fassara ta da wata munufa ninayi alkawarin bazan sake cewa ta koma ba, kuma shima haydar din zanbashi hakuri ga yanmata nan da yawa agari ya neme wata</p><p><br /></p><p><br /></p><p>shiru mama tayi ba dan ranta ya so ba, alhj yusuf na zaune agurin ya daga waya ya kira haydar ba,a dau lokaci ba haydar ya iso bayan ya zauna ya mika gaisuwa.</p><p><br /></p><p> jiki babu kwari suka amsa, shiru sukayi na dan wani lokaci sannan alhj yusuf yace</p><p><br /></p><p><br /></p><p> " haydar kasan dalilin kiran ka?</p><p><br /></p><p> cikin dasheshshiyar murya yace a,a.</p><p><br /></p><p> alhj yace akan mgnr ki da fatima ne, kasan daddyn ku ya dauki zafi akan mgnr dan haka nake son na baka shawara , ko da bani bani bane mahaifin ka amman nasan zan baka shawara ka dauka, dan haka inason kayi hakuri ka rubutawa fatima ta karda , dan na kula daddyn ku ya shirya daukan matakin da idan haka ta kasan ce bazakaji dadin rayuwar ka ba, sabo da bakin iyaye da kake gani babban masifa ne.</p><p><br /></p><p> 'kasa yayi dakai ya kasa daguwa , ko motsi bayayi.</p><p><br /></p><p>shima alhj shiru yayi zuwa cen yace haydar nasan mgn ta zatama tsauri da yawa, amman inason ka daure kayi haka din, idan Allah ya nufah zaman ku be kare ba sai kaga ta koma daga baya, kaje ka nemo ko yar waye ni zan tsaya maka ayi auren.</p><p><br /></p><p> a hankali haydar ya dago kai, idon shi cike da hawaye yace baba wlh ni babu wata wadda nake so fatima kawai nake so dan Allah baba karka bari daddy ya rabani da ita, nasan kai ka dai ne zaka iya tsaya min, karashe mgnr yayi cikin kuka.</p><p><br /></p><p>shiru alhj yayi yana sauraran haydar sautin kukan shi kawai kakeji.</p><p><br /></p><p> </p><p> mama ko tuni tausayin haydar ya kamata dan haka cikin sauri tabar wajen.</p><p><br /></p><p>alhj yabita da kallo sannan ya juyar da kallon shi ga haydar yace</p><p><br /></p><p> " kai haydar ya isa haka, ya kake yin abu saikace ba namiji ba, karna sake ganin ka kana kuka akan fatima, fatiman me, ga yan mata cen birjik agari, ko hadu kake so sai ahada maka.</p><p><br /></p><p> ahankali haydar ya fara share hawaye zuwa cen ya mike yace na tafi.</p><p><br /></p><p> shima alhj asanyaye yace toh ka gaida mutan gidan.</p><p><br /></p><p>har haydar ya isa gida kuka yake yi, kai tsaye ya dakin ummi ya shiga.</p><p><br /></p><p> ummi na ganin haydar ta dawo da baya ta zauna akan kujera sannan tace haydar dan allah ka kwantar da hankalin ka.</p><p><br /></p><p> cikin kuka yace ummi bazan iya ba, bazan iya rayuwa babu fatima ba kuma su daddy nema suke su rabani da ita, kuka yake sosai.</p><p><br /></p><p> hankalin ummi ya tashi ahankali tace haydar yanzon fatima tana ina?</p><p><br /></p><p> atakaice yace gidan hajiya.</p><p><br /></p><p> shiru tayi zuwa cen tace tashi muje gidan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[6:12PM, 4/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_</p><p><br /></p><p> 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>85 - 87</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*SLM masoya wanna lbrn Tsuntsun me wayo, kunjini shiru kwana 2, haka ya faru ne sanadin ciyon kai da nayi, nasamu sakonnin ku na gaisuwa agereni babu adadi, kuma nagode da nuna kulawar ku agareni, wannan ya nuna min kuna biye dani kuma kunajin dadin wannan lbrn😍😍😍*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haydar ne kejan motar cikin garaje dan ya balakin kosawa su isa gida.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>ummi ta bishi da kallo tace haydar kajamu ahankali garajen me kake.</p><p><br /></p><p> bece komai ba yaci gaba da tafiya idon nan zuro zuro.</p><p><br /></p><p>suna isa ummi ta sauka, har ta kusa shiga gidan ta waigo tace haydar kasan menene, ka zauna ka jirani na fara shiga zuwa anjima sai ka shigo.</p><p><br /></p><p>Haka ya hakura ummi ta shiga badan ranshi yaso ba.</p><p><br /></p><p>Lokacin da ummi tayi sallama afalon hajiya, ta hango fatima kwance akan cinyar hajiya, kibiya ce ahannun ta tana tsafewa fatima kai.</p><p><br /></p><p>Ciki ciki hajiya ta amsa sallaman ummi fatima ko tana ganin ummi ta fara kokarin mikewa, hajiya tasa hannunta ta dan danne fatima sannan tace kwanta abin ki.</p><p><br /></p><p>Bayan ummi ta gaida hajiya, sai shiru ya ziyarci falon.</p><p><br /></p><p>Zuwa cen ummi taga shirun na hajiya yayi yawa, bayan tasan cewa surukar tata mutun ce me sakin fuska da wasa da dariya, amman yau tazo taga sabanin haka.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Bayan ummi ta gama tunanin ta tayi kundun bala tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p> " Hajiya nazo ne akan maganar fatima da haydar"</p><p><br /></p><p>Kan hajiya na kasa tana kokarin tajewa fatima kai, tace toh inajin ki, yaya akayi?</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tace bawani abu bane hajiya daman hakuri nazo nabaki dan Allah kiyi hakuri komai ya wuce.</p><p><br /></p><p> Dariya hjy tayi sannan tace ashe baki da kunya haka ban sani ba, ai banzaci zakizo ki tareni da mgnr haydar da fatima ba, kokin manta lokacin da kikecewa rufawa fatima asiri haydar zaiyi, saboda kawai tsautsayi ya fada mata, yazun badan Allah ya tona mai asiri ba, nan da shekara ishirin saikin goranta mata, kuma babu abin da yafi bani mamaki duk abinda haydar yake yi baki gani, wai har kece kike bude baki kina fadin duk abun da namiji yayi ado ne, toh yaje ya karaci adon acen munan bamu bukata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ummi jitayi kamar kasa ta bude ta shige sai yanzon ta gane be kamata ta biyewa haydar akan duk abin da yake so ba, cikin kuka tace</p><p><br /></p><p> " Hajiya tabbas nayi kuskure amman ina neman gafara dan Allah ki tayani bawa fatima hakuri ta yi haru ta yafemin.</p><p><br /></p><p>Fatima dake kwance jikin hajiya ta kara matse idonta kamar me bacci.</p><p><br /></p><p> Haydar ne yayi sallama ya shigo, be ko kqlli inda ummi take ba, kai tsaye ya wuce gaban hajiya ya tsuguna yana leka fuskar fatima, hajiya bata ce komai ba, illa binshi da kallo da take.</p><p><br /></p><p> zuwacen ya daga hannu zaikai jikin fatima, muryar hajiya yaji tana fadin wlh ka taba yariyar nan saina barka kwance.</p><p> </p><p> Ko ajikin shi hancinta ya kama yadan matsa kadan</p><p><br /></p><p>. zabura tayi da sauri ta mike tsaye cikin dakin hajiya ta nufa tana fadin Allah ya isa.</p><p><br /></p><p> tashi yayi zaibi bayanta sai alokacin ummi tayi magana cikin muryar da taci kuka ta koshi tace karka bita haydar , kayi wa fatima lefi yanzon neman gafarar ta ya dace kayi.</p><p><br /></p><p> daidailo kacin hajiya yadidko ta fitoh daga kitchen rike da wata yar karamar muciya tana fadin barshi ya bita idan ka fasa ka raina uwarka mara kunya kawai fitsararre.</p><p><br /></p><p> Juyawa yayi ya kalli fuskar ummi yasan lallai tayi kuka wani haushi ne ya taso masa ya juya ya kalli hajiya yace towai ke da kike wani shishshigewa yarkice..... </p><p>ummi ce ta daka mai tsawa sannan ta mike tace muje</p><p><br /></p><p> Haydar na gaba ummi na binshi abaya suna kokarin fita ummi tace muntafi.</p><p><br /></p><p> ta bude baki zatayi mgn haydar yace kuma wlh zan dawo idai baki bani Fatima ba bazan taba daina zuwa ba</p><p>na dinga sintiri kenan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>har suka koma gida haydar cike yake da haushin hjy</p><p><br /></p><p>ummi kuwa kalaman hajiya ne suka tsaya mata amakoshi, babu abin da yafi bata mamaki wai yau fatima ce taki gaisheta har tana wani bacci dan dai kawai karta gaida ta, taslim ce ta katse mata tunanin da fadin ummi kun dawo?</p><p><br /></p><p> Ajiyan zuciya ta sauke sannan tace mundawo taslim.</p><p><br /></p><p> taslim ta sake cewa ina fatima ai na dauka tare zaku dawo.</p><p><br /></p><p> Saida ummi ta share hawaye sannan tace ai fatima inaga saidai muyi hakuri domin fatima ta hada kai da hjy suna neman ganawa haydar azaba, saboda sun fahimci haydar ya kamu da son fatima, nima kaina bakiga yadda hajiya ta rufe ido tacimin mutunci ba, fatima ko,ko kallo ban isheta ba, bare nasa ran zata gaidani.</p><p><br /></p><p> Tuni taslim ta dafah kirji tace ummi fatiman ce tamiki haka, toh ai ba dole bane saita dawo, shima yaya haydar dinne ya cika naci ya rabu da ita mana.</p><p><br /></p><p> ummi tace ai haydar bazai iya ba yariga ya zama kamar wani wawa akan fatima, wlh tunda nake bantaba tunanin akwai yariyar da zata juya haydar haka ba, yaunzo fah ko mgnr fatima yakeyi babu wuya kiga hawayen shi. </p><p><br /></p><p>mikewa taslim tayi tace ummi aikuwa yanzun dai dole ne ya rabu da ita .</p><p><br /></p><p> suna cikin haka haydar shigo jiki asanyaye bayan ya zauna yace ummi wai yaushe alhaji babba zai dawo.</p><p><br /></p><p>cikin daure fuska ummi tace</p><p><br /></p><p> " Ni ina zan sani ai wannan saidai ka tambaye daddyn ku ko kuma alhj yusuf dan nasan ko hjy yadikko batasan sanda zai dawo ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Shiru yayi zuwacen yayi kwalkwal da ido yace toh ni yanzon ummi ya zanyi hakuri nafah ya fara karewa narasa ya zanyi, ummi dan Allah ki taimakeni mana.</p><p><br /></p><p> taslim ce ta bude baki ahankali tace </p><p><br /></p><p> " toh yaya kaima dai kayi hakuri mana ka rabu da ita, tunda tace bataso ga yanmata nan ka neme wata mana.</p><p><br /></p><p> yadda taga haydar na kallonta ya sa tayi shiru tayi kasa dakai , mikewa yayi azuciye ya fara takowa kusa da ita, ummi ta mike da sauri ta shiga tsakiyar su, dan haka haydar ya fara fadin dan ubanki ina wasa dakene ni sa,an wasanki ne, daker ummi ta samu ta fitar dashi adakin.</p><p><br /></p><p> Kwanci tashi babu wuya yau fatima satin ta 5 agidan hajiya yadikko haydar yayi sintiri har yagaji dan haka haydar ya koma ruwa dan yanzon hargida yake kawo yan mata, ummi tayi mgn harta gaji kuma tayi tayi dashi ya nemo wata yaki gashi duk yayi wani iri yayi baki ya rame, dan haka ta yake shawaran zatamai aure ko yana so ko baya so.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Fatima ce kwance kan gadon hajiya yadikko sai sharara bacci take, hajiya ta bita da kallo tace</p><p><br /></p><p> " ke wai baccin nan naki na lfy ne kuwa"</p><p><br /></p><p>mika tayi sannan tace hajiya gajiya fah nayi .</p><p><br /></p><p> da sauri hjy tace aikin me kikayi, zakice wani kingaji, toh kitashi ga iyayenki cen sunzo.</p><p><br /></p><p> fatima na kokarin tashi hajiya yadikko ta bita da kallo sannan tace.</p><p><br /></p><p> fatima anya baciki gareki ba kuwa, yaushe yabon ki da al,ada?</p><p><br /></p><p> cikin fatima ne ya bada wani tsurrrrrr saboda tsaban tsoro.</p><p><br /></p><p> hjy ta sake cewa bada ke nake mgn ba, budemin tafin hannun ki nagani.</p><p><br /></p><p> kara damke hannun ta tayi sannan tace hajiya dan Allah kibari, karki jamin bala,i ni bani da kome dan ko yanzon ma al,ada nakeyi</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[8:25PM, 4/30/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>88 - 90</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kallon ta hjy tayi shekeke sannan tace ke karki kawomin iskanci, bafa yau aka haifeni ba, batun yau na lura ba ciki gareki.</p><p><br /></p><p> hawaye ne ya fara zubowa fatima cikin kukan tace nifa bani da ciki haka kawai sai ki kalleni kicemin ina da ciki, ke likita ce, toh ko likita sai ya duba yake fad', karashe mgnr tayi cikin turo baki, sanan ta mike tayi falo.</p><p><br /></p><p> daddy ta gani tare da baban ta, daddy na ganin ta ya washe baki, yace mamana yayadai ko baki da lfy ne duk sanda naxo sai hjy tace kina bacci.</p><p><br /></p><p> yar dariya tayi sannan ta zauna tace lfy lau nagaji ne daddy, daganan ta shiga gaishe su daddy ne kadai ya amsa, amman alhj Yusuf yiyayi kamar bejita ba tare da kallon wani gefe.</p><p><br /></p><p> hajiya ta bishi da kallo, tace waikai kana nufin fushi kake da fatima, toh ai nima saika daina mgn dani tunda nina hata komawa.</p><p><br /></p><p> cikin sanyin murya yace toh hajiya ai wannan be kamata ba, tunda da haydar da fatima duk daya suke awajen ki, gashi nan yanzon duk kusa shi yazama wani iri duk ya bi yarame.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> da sauri hajiya tace yazama tsinken sakuce ma ni babu abinda ya dame ni, aishi ya daura wa kansa fita.</p><p><br /></p><p> daddy shiru ya musu bece kome ba zuwacen ya juya barayin fatima yace ke tashi ki kawo min ruwa.</p><p><br /></p><p> shiru yaji kanta na bisa hannun kujera kwace.</p><p><br /></p><p> ya sake cewa fatima dake fah nake.</p><p><br /></p><p>nan ma shiru, hajiya ta juyar da kallonta ga fatima sannan ta mike tana fadin bari na kawo maka, ita fatima yanzon inda kasan kasa haka takoma.</p><p><br /></p><p>zuwa cen ta dawo dauke da ruwan tana cigaba da fadin kunga wannan baccin tun asuba takeyin sa, yanzon haka ko sallar azahar batayi ba, data bude ido zata sake mayarwa.</p><p><br /></p><p> cikin ta kaice alhj ya mike ya nufi fatima yana fadin kuma kika barta ai wannan iskanci ne ga la,asar na tahowa, daidai lokacin daya zafga mata rankwashi.</p><p><br /></p><p>da sauri ta mike tana rike da kai take kallon su, cikin fad'a yace maza kije kiyi alwala kizo nan kiyi sallah.</p><p><br /></p><p> wucewa tayi sumi sumi zuwacen ta fito sanye da hijjab, gefen hajiya ta shinfida sallaya, tana idarwa kuwa ta shige cikin hijjab din taci gaba da baccin ta.</p><p><br /></p><p>wannan karon daddy ne yayi mgn yace hajiya wai waccen yariyar baccin nan nata na lfy ne kuwa, jifah saikace wata yar maye.</p><p><br /></p><p> alhj yusuf yace kashhh kayi shiru kawai jira nake na tashi na bugata da bango.</p><p><br /></p><p> cikin sauri hajiya tace a,a a,a karka fara, kana son kajawo mana bala,i kenan, kubarta tayi baccin ta wannan baccin nata me daliline dan ko tatama banayi ciki gareta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> shiru sukayi kowa da abinda yake sakawa zuwacen daddy yace amman hajiya ya kamata akaita asibiti dan atabbatar da haka.</p><p><br /></p><p> hajiya ta kalli alhj yusuf tace toh ko kai zaka kaita?</p><p><br /></p><p> da sauri ya mike yace wa, Allah ya kiyaye ai mijinta ya kamata ku kira bani ba, waje ya fito cikin shi cike da dariya, dan wannan mgnr ba karamin dadi tamai ba.</p><p><br /></p><p>hajiya kuwa alhj na fita tabi bayan shi da harara sannan ta mike tace ni bari naje nakaita.</p><p><br /></p><p> daddy ma mikewa yayi yace toh ki tasheta saina kaiku.</p><p><br /></p><p>haka ko akayi suna zuwa bayan yan gwaje gwaje likitan ya shaida musu tana dauke da cikin sati 6.</p><p><br /></p><p> ranar daddy ya koma gida cike da farin ciki wanda ya kasa boyewa, yana kokarin shiga gida ne suka hadu da haydar zai fita, ya dan rusuna ya gaida shi.</p><p><br /></p><p> amsawa yayi sannan yawuce, abin kuwa yabawa haydar mamaki dan tunda abun nan ya faru daddy baya amsa gaisuwa shi, dan haka haydar ya shiga tatama kodai daddy be ganeshi bane dan yaga kamar arude yake.</p><p><br /></p><p> ******</p><p><br /></p><p>ummi na zaune ita da taslim acikin dakin ummi, shiru sukayi kowanne cikin su da abinda yake sakawa itako ummi tunanin mijinta ne fal azuciyar ta, sabo da tun da abun nan ya faru baya mgn da kowa agidan sai taslim , acewar sa ita kadai ce take mishi biyayya.</p><p><br /></p><p> itako taslim haydar ne ya hanata sakat agidan daya ganta neman dukanta yakeyi dan gani yake taslim munafuka ce bata son farin cikin shi , dan yaga almar harda ita ason ya rabu da fatima</p><p><br /></p><p>suna cikin haka sukaga anturo kofar da sauri ummi ta kalli gurin dan zatonta haydar ne, baki ta saki tana kallon daddy shima ita yake kallo fuskar shi cike da murmushi , zama yayi bakin gadon, dan haka taslim ta gaidashi tamike ta fita cike da mamaki dan tunda take da wayon ta bata taba ganin daddy adakin ummi ba sai yau.</p><p><br /></p><p> itako ummi dadi taji bakadan ba, amman saita dake ta buye farin cikin ta ahankali tace lfy kuwa?</p><p><br /></p><p> d'an murmushi yayi sannan yace waike bakisan ina fushi dake bane , bazaki iya zuwa ki bani hakuri ba.</p><p><br /></p><p>tace lefin me namaka kawai dai lefin haydar ne ya shafeni, kuma ni bani na turashi ba, kuma nima abin ai bemin dadi ba.</p><p><br /></p><p> d'aga hannu daddy yayi sannan yace ni bawannan ne ya kawo ni ba, albishir nazo na miki.</p><p><br /></p><p> ummi tace to ijinka.</p><p><br /></p><p> daddy ya sake cewa amman fah zaki bani tukuici.</p><p><br /></p><p>murmushi tayi sannan tace indai ya cenceci abaka ai sai nabaka .</p><p><br /></p><p>saida ya cire hular dake kansa sannan yace fatima nadauke da ciki.</p><p><br /></p><p> farinciki ne ya rufe ummi nan da nan tace alhj da gaske?</p><p><br /></p><p> shima yana dariya yace zan miki da wasa ne, daga nan ya shiga labarta Mata yadda akayi.</p><p><br /></p><p> tace kai naji dadin wanan lbrn anjima zan baka tukuici🙈</p><p><br /></p><p> da daddare ummi zama tayi tana jiran haydar ya dawo tamai albishir amma har bacci ya kwasheta be dawo ba.</p><p><br /></p><p> sai 12:15 na dare ya dawo kai tsaye dakin sa ya nufah domin yu tun safe cikin sa ke ciyo kuma yasan bawani abu ke damun saba illa sha,awa dake damun sa, ko yau ya fita ne da niyar ya samu wacce zata biya mai bukata, amman ga yan matan yana gani ya kasa amfani dasu kusan yan mata 5 ne suka neme su kebe dashi, saiya tafi da niyar yayi saiya kasa, dan haka ya tattara ya dawo gida.</p><p><br /></p><p> kwace yake yayi daidai akan makeken gadon sa dagashi sai garen wando, wani irin zafi yakeji amarar shi, murkusu yaitayi zuwa cen yaji numfashin shi na neman daukewa dan haka ya fara neman no alhj yusuf, yana dauka yace </p><p><br /></p><p> " baba kazo ka kaini asibiti zan mutu"</p><p> abunda ya fada kenan ya kashe wayar, salis ne ya fado masa arai, dan da ace yana nan bazai galabaita haka ba, zai taima ke shi, koda kuwa ba gida daya suke ba, nan danan ya fara kuka.</p><p><br /></p><p>bayan mintinan da bazasu wacce 30 ba alhj yusuf yazo ya dauke shi suka nufi asibiti, cike da bacin rai.</p><p><br /></p><p>karfe 8:00 na safe suka baro asibitin alhj yusuf ne kejan motar yayin da haydar ke zaune agefen shi.</p><p><br /></p><p>lokacin da suka kusa karasawa gidan daddy ne alhj yusuf ya tsaya ya kira no mahaifin su alhj salisu, bayan ya dauka ya fara gayamai matsalar haydar da fatima komai ya gaya, cikin da fatima ke dauke dashine kawai be fad'a ba.</p><p><br /></p><p>bayan ya gama sauraran shi yace Ku saurareni ina tafe acikin satin nan.</p><p><br /></p><p>kashe wayar yayi sannan suka karasa gidan daddy.</p><p><br /></p><p>duk suna zaune afalo, sukaji sallaman alhj yusuf tare da haydar suka shigo.</p><p><br /></p><p> daddy ya kallesu yace daga ina haka?</p><p><br /></p><p>cikin takaici alhj yace dole ku tambaya tunda kun kwanta hankalin Ku kwace kubar haydar cikin halin rashin lfy, badan Allah yasa yayi dibara ya kirani ba kila da saidai ya mutu.</p><p><br /></p><p>murmushi daddy yayi sannan yace toh me d'a tunda Allah yasa kai yaga mahimmancin ka ya fada ma aishi kenan, ai yasan damu agidan amman be nememu ba, juyawa yayi ya kalli haydar yace meya sameka?</p><p><br /></p><p> cike da mamaki haydar ke kallon daddy, ya kasa furta komai yayi, mamakin sakkowan daddy yake.</p><p><br /></p><p> ummi ta sake cewa dakai fah ake mgn.</p><p><br /></p><p> daker ya bude baki yace ciwon ciki ne.</p><p><br /></p><p> shiru ummi tayi tana nazari, muryan daddy taji yana tambayan haydar daman yana ciwon ciki ne?</p><p><br /></p><p> murya ciki ciki yace Eh.</p><p><br /></p><p> shuru ne ya ziyarci falon, zuwacen alhj yusuf yamike yayiwa ummi sallama ya fita, daddy ma mikewa yayi yabi bayan shi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>suna fita ummi ta dube haydar tace toh yajikin?</p><p><br /></p><p> "yace yayi sauki"</p><p><br /></p><p>ummi ta sake cewa jiya inata jiranka kadawo nama albishir, har nayi bacci baka dawo ba.</p><p><br /></p><p> da sauri ya waigo yace ummi daddy yace naje na taho da fatima ne?</p><p><br /></p><p> itama cikin sauri tace a,a bece ba amman dai fatima nada ciki.</p><p><br /></p><p> mikewa yayi da sauri ya dungule hannuwan shi yace yesss thank God, komawa yayi ya fada kan kujeran da karfi</p><p><br /></p><p> ummi kallon shi kawai take tana murmushi.</p><p><br /></p><p> ganin inda ummi ke kallon shi, sai kunya ya kama shi, yana sosakai yace ummi kiyi hakuri mantawa nayi kina gurin.</p><p><br /></p><p> mikewa tayi tana fadin a,a kayi abinka ai zamani ne.</p><p><br /></p><p> tana wucewa shima ya mike jiyayi yajishi garas, yanzon dole abashi matar shi , dan haka motar sa ya shiga har ya zauna yaji alhj yusuf na kwalamai kira da sauri ya sakko ya nufi gurin da daddy da alhj suke zaune.</p><p><br /></p><p> tsugunawa yayi agaban su yace gani.</p><p><br /></p><p> alhj yace toh kaida baka da lfy ina kuma zaka, banson yawace yawace fah</p><p><br /></p><p> keya ya fara sosawa sannan yace gidan hajiya zani.</p><p><br /></p><p> shiru yayi sannan yace toh saika dawo.</p><p><br /></p><p>itako fatima tunda suka dawo daga asibiti take kuka' hajiya tayi tayi da ita tayi shiru taki ahaka suka kwana, kuka harda majina.</p><p><br /></p><p> ganin inda hankalin ta duk yabi ya tashi yasa hajiya ta fara tunanin karfa damuwan fatima yasa cikin ya zube, idan ko haka ya kasance bazataji dadi ba, domin suna da bukatan yara, dubara ce ta fado mata, dan haka ta dafa fatima tace</p><p><br /></p><p> haba fatima daga cewa kinada ciki saiki tada hankalin ki, idan kina tunanin za,ace saikin koma gidan haydar ne saboda kinada ciki to ki kwantar da hankalin ki, bazan taba bari ki koma gurin sa ba.</p><p><br /></p><p> cikin kuka tace ni dai so nake kawai aciremin cikin, haka kawai ina zama na za,ace wai wani ciki gareni.</p><p><br /></p><p> zaro ido hajiya tayi sannan tace fatima kina hauka ne, toh daga yau karna sakejin zancen zubar da ciki abakin ki idan ba hakaba kuwa kwanan nan zamu raba jaha</p><p>angaya miki nima bani da hankali ne kalanki ,kaga min yar banzan yariya, ta inda hajiya take shiga batanan take fitaba.</p><p><br /></p><p> cikin sauri fatima ta mike cike da haushin hajiya daki ta shiga, zuwa cen saigata ta fito sanye da hijjabi hannun ta dauke da akwati.</p><p><br /></p><p> cikin fada hajiya tace ina zaki?</p><p><br /></p><p> turo baki tayi sannan ta share hawayen dake kan fuskarta tace toh haka kawai sai kitayimin masifa, ni gidan babana zan koma.</p><p><br /></p><p> da sauri hajiya ta mike tace kinci bantan ubanki</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[6:42PM, 5/1/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>91 - 92</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ke wacce irin yariya ce da babu damar a gaya miki gaskiya, dan uban ki Allah ya miki kyauta kice maki so, bayan kina gani ba yawa gareku ba, naso ace na haifi yara da yawa amman Allah be yarda ba, guda 2 ya bani, nayiwa Allah godiya kuma naita addu,an ta sanadin biyun nan zamuyi yawa, toh gashima yanzon suma ku uku kawai kuka rage musu, kuma idan Allah yaso ku ukun nan sai kuntara mana uguwa guda</p><p><br /></p><p><br /></p><p> cike da haushi fatima ta kalle ta tace caff dayake ke za,abarwa gadin duniya.</p><p><br /></p><p> itama hajiya cikin fad'a tace to ai saikizo ki karasa ni.</p><p><br /></p><p> dariyar haydar sukaji daga bakin kofah duk suka maida hankalin su gurin shi.</p><p><br /></p><p> har yanzon dariya yake yi hannuwan shi cikin aljihun shi, zuwa cen ya tsagaita da dariyar ya fara takowa cikin falon ya zauna sannan yace </p><p><br /></p><p> yau dai na ganku arana har kun gama kule kulen naku?</p><p><br /></p><p>hajiya ta kara daure fuska kai bana so shashanci ni nake maka kule kulen?</p><p><br /></p><p> toh hajiya idan ba kule kule ba ya za,ayi daga abu ya faru ki wani kanai naye kita zuga yariya, ya juya barayin fatima yace yi hakuri fatima zo ki zauna ni zan miki duk abin da kike so, badai cikin kike so araba ki dashi ba, toh karki damu, ta shi yayi ya isa gabanta ya rike akwatin sannan yace wannan bawata Matsala bace, yanzun kizo muje na kai ki asibiti</p><p><br /></p><p> bige hannu shi tayi ta saki akwatin ta koma daki tana share hawaye.</p><p><br /></p><p> cikin sauri yabi bayanta, hajiya ko ido kawai tasa musu.</p><p><br /></p><p> yana shiga ya sameta ta kwanta tayi rufda ciki, bakin gadon ya zauna yasa hannun shi ya dago ta</p><p><br /></p><p><br /></p><p>duk da kokarin kwacewan da yake besa ya saketa ba saima kara matseta da yayi a jikin shi yana kai mata sunba, tun tana kwacewa har ta gaji tayi lakwass ajikin shi, dan ta gane wahala kawai zatasha bazata iya kwatan kanta ba.</p><p><br /></p><p> zuwa can ya saurara mata ya bude baki ahankali yace </p><p><br /></p><p> fatima dan Allah kiyi hakuri ki yafemin nasan na miki laifi, ina rokon alfarma ki yafemin ki dawo gareni, ki daina biyewa zugar hajiya rudun tsufa ne yake damunta, kara kwatar da murya yayi yace fatima idan kika amince kika dawo gareni zan nuna miki son daba kowane namiji bane zai iya nunawa matar sa, ko kuda bazan bari ya tabaki ba.</p><p><br /></p><p> tuni hawaye ya fara zubo mata domin kaman haydar ya tuna mata da salis, shima haka yake fada.</p><p><br /></p><p> cikin kukan take fadin wlh bazaka iya ba, dan ko yaya salis daya fadi haka gashi ya tafi ya barni, naso ace yana nan asirinka ya tonu, da kaji kunya.</p><p><br /></p><p> cike da takaici yace fatima har akwai wata kunya da ta wuce wadda naji yanzo kowa fah acikin dangin mu yasan halin da muke ciki, hatta taslim karamar kanwata ta daina girmamani , kuma da kike mgnr salis, wlh ni nasan da salis na nan shine mutun na farko da zai fara gafarta min, nasan zaiji tausayi na kuma zaiyi kokari yaga ya fitar dani daga cikin kunci, dan haka ina rukonki albarkacin son da kikeyiwa salis kiyafe min.</p><p><br /></p><p> kuka take sosai dan haka ya jawota kan kirjin shi yana fadi Allah yajikan salis, Allah ya gafarta masa ubangiji Allah ka haskaka kabarin sa.</p><p><br /></p><p> cikin kuka fatima ke amsawa da ameen ameen, dan haka ya kara matseta kamar zai sakata ciki.</p><p><br /></p><p> saida suka kwashe kusan minti talatin ahaka, sannan fatima ta daga kanta ta fara share hawayen, cikin ido ta kalli haydar tace</p><p><br /></p><p> kace duk abinda nake so zaka min ?</p><p><br /></p><p> da sauri yace eh</p><p>me kike so ko menene ki fadamin.</p><p><br /></p><p> cikin sauri tace toh cikin za,a cire min.</p><p><br /></p><p> shiru yayi zuwacan yace to shikenan gobe zan zo na dauke ki, kamar karfe na zanzo?</p><p><br /></p><p> tace ko da yaushe ne amman dai da wuri zaka zo .</p><p><br /></p><p> mikewa yayi tare da fadin angama ranki ya dade, sannan ya zuba hannu cikin aljihu yace to zan wuce baki ce nagaida kowa ba.</p><p><br /></p><p> dan ya mutsa fuska tayi sannan tace nidai inajiran ka, kazo da wuri.</p><p><br /></p><p> shima murmushi yayi sannan yace toh saikin ganni.</p><p><br /></p><p> </p><p> yana fitowa ya kalli hajiya dake saune afalo yace duk d'an bakin ciki sai dai ya mutu.</p><p><br /></p><p> yana fita hajiya tayi murmushi tace ja iri.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> cike da farin ciki ya koma gida, washegari kuwa 9 agidan hajiya tamai, lokaci fatima na bacci saida yajirata tashi, tana bude ido kuwa ta fito falo da niyar tambayan hajiya ko haydar yazo, tana fitowa kuwa ta ganshi zaune kusa da hajiya, cikin sauri ta koma ta dauko gyale ta fito tana fadin muje.</p><p><br /></p><p> saida hajiya ta kalli fuskar haydar sannan ta kalli ta fatima tace ina kuma zaku.</p><p><br /></p><p> haydar ne ya mike sannan yace ina ruwan ki.</p><p><br /></p><p> itama hajiya mikewa tayi sannan tace babu fah, amman dai fatima anyi wayon banza.</p><p><br /></p><p> basuce komai ba suka bar gidan.</p><p><br /></p><p> koda sukaje asibitin haydar ne kadai ya shiga zuwacen yaxo ya kira fatima.</p><p><br /></p><p> bayan ta zauna agaban likitan ya juyo gareta ya fara mata bayani madam mijiki ya riga yamin bayani , zan baki magani amman kisani komai yana bukatar sirri, ki kama bakin ki karki gayawa kowa, dan maganin dazan baki yana da kyau bakowan ni asibiti ake samun shi ba, idan kika sha maganin ta fitsarin ki cikin zai fita, saidai maganin yana da duko ki.</p><p><br /></p><p> sosai fatima ta maida hankalin ta gare shi.</p><p><br /></p><p>yaci gaba da cewa kadan daga cikin ka idojiji sune cin abinci akan lokaci, ba,aso meshan wannan maganin na zama cikin damuwa</p><p>sannan idan zaki kwata bacci ki kwata ta gefe dama ko hagu idan kika kiyaye wad'annan dukokin ko kwana 1 baza ayiba zaki fitsarar dashi.</p><p> </p><p>mika mata manin yayi sannan yace koda cikin ya fita kuma badaina shan maganin zakiyi ba idan ya kare saiku dawo na cenza muku wani, dan idan kina shan maganin bazaki dauki ciki ba sai ranar da kika daina shan maganin.</p><p><br /></p><p>godiya sukayi sosai sannan sukayi mai sallama suka tafi</p><p><br /></p><p><br /></p><p>suna cikin tafiya haydar ya kalli fatima data zauna tayi shiru, yace fatima tunanin me kikeyi, kina son cikin ya fita da wuri kuwa?</p><p><br /></p><p> inaso mana ai insha Allahu yau zai fita, shiru sukayi zuwace fatima ta sake cewa yaya haydar daman kai baka son yara ne?</p><p><br /></p><p> daidai lokacin dazai karya kwanan gidan hajiya yace</p><p><br /></p><p>ina so amman ba yanzun ba.</p><p><br /></p><p> tabude baki zata sake mai wata tambayar taji yana fadin toh fah alhaji babba yadawo.</p><p><br /></p><p> tana daga kaikuwa taga jerin motocin dake gaban su, ta tabbatar eh lallai alhaji salisu ne ya dawo</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[8:59PM, 5/2/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>93 - 94</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kusan tare suka isa gida, alhj babba na saukowa a mota suma suna fitowa, cike da fara, alhj ke kallon su, bayan sun shiga gida cike da anna shuwa alhaji salis ya zauna yaran shine guda 2 agaban shi gefe kuwa ummi ce da mama duk sunzo taryan sirikin su,</p><p> </p><p> hardar da fatima ma suna zaune akasa, taslim ce kawai ta shige dakin hajiya ta boya domin yanzon basa zama inuwa daya da salis.</p><p><br /></p><p> abinci aka baje kowa yaci ya koshi har fatima sake jiki tayi taita tura abinci, duk da cewa bason ci take ba.</p><p><br /></p><p>bayan sun kammala ne kakan su alhj salis ya shiga tattaunawa da iyalan shi, haydar Allah Allah yakeyi yaji an sako zancen su da fatima.</p><p><br /></p><p> zuwa can alhj yusuf yace baba bakace komai ba akan mgnr haydar da fatyma.</p><p><br /></p><p>dasauri alhj salis ya maida kallon shi gare su yace ai na dauka kun gama komai, kuna nufin yanzon ba daga gidan su , suke ba, toh me kuke jira.</p><p><br /></p><p> hajiya yadikko tayi caraf tace ai alhj bazata koma ba, sakin ta zaiyi idan Allah ya sauketa lfy tayi aure.</p><p><br /></p><p> cikin sauri alhjn yace da wani dalilin, ai bazai yiwu ba wannan auren da kuke gani ko bayan raina ban yadda arabashi ba, abun da ya faru ya riga ya faru, gashi har ma naji kina cewa ansamu rabo.</p><p><br /></p><p> duk shiru sukayi suka samusu kunne.</p><p><br /></p><p> zuwa can hajiya tace alhj kana nufin duk rashin kunyan da haydar yayimin yace bulusss kenan, wacce kalma ce be kirani da ita ba, har fah habaici yake min, ko dazon saida ya kalli cikin idona yacemin duk dan bakin ciki saidai ya mutu.</p><p><br /></p><p>d'an murmushi yayi sannan yace yamin daidai daya fad'a miki haka, yaga zaki kwace mai mata, ya juya ya kalli haydar daya dukar da kansa kasa yace</p><p><br /></p><p> kai ka tashi ka dauki matar ka ku tafi gida, idan kana da hankali wannan kadai ya isheka ishara.</p><p><br /></p><p> cike da farin ciki haydar ya fara godiya, fatima ta dago fuskarta cike da hawaye, hararar da alhj yusuf ya zafga mata yasa ta maida kanta kasa.</p><p><br /></p><p> haydar kuwa tuni ya mike yaje gaban fatima yace tashi muje, ko saina d'aga ki?</p><p><br /></p><p> hajiya ce tace to kuji irin rashin kunyar tashi ko.</p><p><br /></p><p> cikin dariya alhajin ya kalli hajiya yace haba fatima me yasa kikeyin abu kamar wacce rikicin tsufah ya kama, me yakai kunnen ki gurin su.</p><p><br /></p><p>shidai haydar tunda fatima ta mike tayi waje be tsaya jin me suke tattaunawa ba, </p><p>haka suka isa gida saikace kurame, fatima ko jifi jefi tana share hawaye.</p><p><br /></p><p> suna shiga barayin su ta ganshi duk yayi kora duk da batajin kwarin jikin ta haka ta zage tashiga gyara gidan tana hawaye, shima haydar be zauna ba tayata ya shigayi.</p><p><br /></p><p> zuwa can haydar yace wai fatima kukan me kikeyi inace mun riga mungama mgn, hannusa yasa ya riketa yace kibar aikin zan karasa, kije kiyi wanka sai kizo kisha maganin.</p><p><br /></p><p> bayan fatima tayi wanka tasha magani nan bacci ya kwasheta batare da tasan lokacin ba, haydar kadai ya karasa aikin dan haka lokacin da ya fito wanka shima nan kusa da fatima ya kwanta gani yayi baccin nata yayi nisa dan haka ya dago kanta ya daura akan kirjin shi yasa hannun shi duk biyun ya zagaye ta</p><p><br /></p><p>Sun dade ahaka gabadayan su bacci suke shararawa </p><p><br /></p><p> su ummi kuwa sai yamma likis, suka dawo ita ma yau cikin farin ciki take dan haka suna dawo wa ta shiga kitchen domin daura abincin dare , tare da taslim sukayi komai suka gama.</p><p><br /></p><p> sai kusan 5:59pm haydar ya farka yayi mamakin gudun lokacin, ahankali ya fara tashin fatima, ahankali ta fara bude idon, bata gama was tsakewa ba taji wani fitsari ya kulle mata mara dan haka ta tashi da sauri tayi toilet.</p><p><br /></p><p> aguje haydar ya bita fitsari ya samu tana yi, saboda yadda fitsarin ya matseta har wani lumshe ido take.</p><p><br /></p><p> haydar na rike da kofar yana kallon ta zuwacen yaji tace Alhamdulillah yaya haydar ka gani cikin ya fita.</p><p><br /></p><p> dariya ce taso kwace mishi daker ya iya daurewa, yaje ya dagata yana fadin sannu fatima, har wani langabewa take wai ita adole ga me mara lfy</p><p><br /></p><p> cikin haydar cike da dariya har suka fito falo, kan kujera ta kwanta tace toh kaje ka gayawa su ummi.</p><p><br /></p><p> daure fuska yayi sannan yace kin manta abinda likita yace, ko bakisan komai da sirri yafi ba.</p><p><br /></p><p> turo baki tayi sannan tace toh idan sukaga ban haihu ba fah.</p><p><br /></p><p> yace babu ruwan ki ,kibarni ni zansan yadda zanyi nagaya musu.</p><p><br /></p><p> ********</p><p><br /></p><p> washegari da daddare haydar ya shiga dakin fatima cikin shigar da fatima keson gani zama yayi kusa da ita sannan yace fatima ya kamata ace zuwa yanzon musan abinda muke yi , ya kamata mugyara zaman mu, mudunga sauke hakkin junan mu, muyi zama naso da kyauna, bana umarni ba.</p><p><br /></p><p> ahankali ta daga idon tace waye zai so ka yayama za,ayi naso yaya salis sannan kuma naso ka.</p><p><br /></p><p> fuskar shi daure yace fatima ki daina yaudaran kanki, kuma ni banason kinamin maganar salis indai ba addu,a zakiyi mai ba, matata ce ke, kuma nina san kina sona yaudaran kanki dai kawai kikeyi.</p><p><br /></p><p> cikin rashin kunya tace aiko baka isa ka hanani zancen yaya salis ba ina ruwan ka.</p><p><br /></p><p> azuciye ya mike har yakai bakin kofah ya tuna matsanan ciyar sha,wan daya kwana da ita, dan haka ya fara takowa ahankali ya dawo gabanta ya tsaya,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>kome ya tuna kuma saiya koma.</p><p><br /></p><p>yana fita fatima taja tsaki ta gyara kwaciyar ta.</p><p><br /></p><p> shiko haydar cike da tunani ya koma dakin sa, tunanin fatima ya shigayi yana son su kasan ce amman ya rasa ya zaiyi shiru yayi , zuwa cen wani tunani ya fado masa dariya yayi sosai sannan yace azuciyar shi, akan me ma zan damu kaina akan fatima yariyar da ba wayo gareta ba, dariya yakarayi daya tuna fatima wai har murna take, tayi fitsari ciki, dariya yayi sosai har yana rike ciki sannan ya fesa turare ya nufi dakin fatima cike da kwarin guiwa, dan yasa yiwa fatima wayo bawani abin wahala bane</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[8:52PM, 5/3/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>95 - 96</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Lokacin da haydar ya shiga dakin fatima samunta yayi tana bacci kuma dagani tanajjin dadin baccin dan haka bazai iya tashinta ba.</p><p><br /></p><p> Ahankali ya hau gadon daf da ita ya kwanta ya manne da jikinta, zuwa cen yasa hannu ya rugumota jikin shi, yaso ya hakura ya barta tayi baccin ta Amman ina bazai iya ba, hannun shi ya fara wasa dashi ajikin ta.</p><p><br /></p><p> da sauri tasa ahanun ta tarike nashi ta tura hannun nashi baya sannan tace yaya meye haka?</p><p><br /></p><p> Hannun shi ya Kara daurawa ajikinta ahankali yace dan Allah fatima kiyi hakuri ki bani hakkina, wlh amatse nake.</p><p><br /></p><p> da sauri ta tashi ta zauna tace nidai gaskiya kayi hakuri bazan iya ba.</p><p><br /></p><p> Shima tashi yayi ya zauna yace bazafah ki iyaba kikace , ko bakisan hukuncin matar da mijinta ya nemeta taki amince bane?</p><p><br /></p><p> da sauri tace nasani aini bani da lfy ne, kuma ni ina ganin kamar ma cikin be fita ba, dan duk abinda nakeji ban daina jiba, har yanzon.</p><p><br /></p><p> Daure fuskar shi yayi sanna yace ya fita mana toh ya za, ayi ki daina ji, bayan har yazon mgni kike sha, hannun shi ya kara kaiwa jikinta yace fatima kiyi hakuri mana amatse nake kuma inada matsala idan kk hanani cikina zai iyayimin ciwo.</p><p><br /></p><p> Mikewa tayi ta fara buga kafa, tana fadin nidai gaskiya ka rabu dani bacci nakeji.</p><p><br /></p><p> Abin da fatima bata sani ba wannan abin da take kara riketa haydar takeyi.</p><p><br /></p><p> Zuba mata ido yayi kamar me kallon TV</p><p>ganin da yayi ya fara shiga yanayin da indai fatima ta hanashi zai iya shiga Matsala, dan haka muryar shi ciki ciki yace toh ya isa haka, na hakura , zoki kwanta.</p><p><br /></p><p> Cigaba tayi tana fadin toh kazo ka tafi dakin ka mana.</p><p><br /></p><p>Daure fuska yayi sannan yace anan zan kwana, kuma wlh idan kika batamin rai, dasafe zanje nagayawa baba abin da kk min.</p><p><br /></p><p> Tanajin ya fadi haka ta tsaya cek kamar me tsonron kar wani abu ya kamata ta fara hayowa gadon nesa dashi ta kwanta, ba dadewa kuwa bacci ya kwasheta.</p><p><br /></p><p> Cen cikin barcin ta tafarjin nishin haydar wasa wasa taji abin na kara yawa , dan haka ta bude Ido ganin shi tayi cen gefe ya kudundune yana rike da ciki, dasauri ta matsa daf dashi tace yaya menene ?</p><p><br /></p><p> babu amsa sai wani irin numfashi daya ke fitarwa gawani uban zufah dake karyo mishi, kalmar shice ta fado mata idan kika hanani cikina zai iyamin ciwo.</p><p><br /></p><p> Kallon shi tayi sosai sannan tace ciyon cikin ne?</p><p><br /></p><p>Hawaye ta fara gani suna zubo mishi, yana wani irin kamar numfashin shi zai dauke, dan haka itama kuka ya kwace mata, acikin kuka take fadin bari nakira ummi.</p><p><br /></p><p> Da sauri ya rike hannun ta yana girgiza mata kai, kuka take sosai domin abun ya balakin bata tsoro.</p><p><br /></p><p>Cikin sauri takai hannun ta kan cikin haydar gurin dataga yana rikewa ta ture hannun shi tanayin kamar yadda taga yanayi, hawayen ta na sauka akan ruwan cikin shi.</p><p><br /></p><p>Sun dade ahaka daga cen ta fara jin kamar numfashin na sauka ahankali, dan haka ta gyara zamanta sosai ta dauki kanshi ta daura akan ciyar ta, taci gaba da abin da take.</p><p><br /></p><p>Zuwa can taga bacci ya dauke shi dan haka ta bishi da kallo gani tayi harya fada yayi zuro zuro.</p><p>dan haka ta fajin haushin kanta dan ta dau hakkin haydar.</p><p><br /></p><p>Ahaka fatima ta kwana bata runtsaba dan gani take kamar data cire hannun ta zai tashi, kiran sallan subahi ne ya tadashi, da sauri ya miki ya kalli fatima, da sauri ta dukar dakai, yace fatima bakiyi bacci ba, baki da hankali ne?</p><p><br /></p><p>Kanta akasa tace banajin baccin ne.</p><p><br /></p><p> Shiru yayi sannan yace toh tashi kiyi sallah saiki kwanta.</p><p><br /></p><p>Wanka yayi sannan ya wuce masallaci bayan ya dawo ya samu fatima zaune akan sallaya, wuceta yayi ya isa bakin gadon ya fara gyarawa, da sauri fatima ta miki ta rike zanin gadon.</p><p><br /></p><p>Haydar yace sake mana zan gyara miki ne saiki kwanta.</p><p><br /></p><p>Tace kabarshi zan gyara da kaina.</p><p><br /></p><p>Yace a,a nizan gyara </p><p> Sakimai tayi dan yanzun batason yimai musu</p><p> </p><p>Yana gamawa yace toh zoki kwanta.</p><p><br /></p><p>Kokarin cire hijjab takeyi dan haka haydar ya nufi fita.</p><p><br /></p><p>Harya fara tafiya fatima takira shi ahakali tace yaya.</p><p><br /></p><p> Dawowa yayi ya tsaya yana kallon ta kanta akasa tace ya jiki?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Murmushi yayi sannan yace naji sauki.</p><p><br /></p><p> Yana kallon fuskarta yaga hawaye na zubowa.</p><p><br /></p><p>Hannu yamika ya kawota jikin shi yace meyasa kike kuka ?</p><p><br /></p><p> Cikin kuka tace dan Allah kayi hakuri ka yafemin jiya na jawo maka......hannun shi yasa ya rufe bakin ta sannan yace karki damu ai dama cen inayi, kitaya ni rokon Allah, ya yayemin.</p><p><br /></p><p>tace eh amman dai ai nice sanadi, tunda ka fad'a tun kafin hakan ta faru</p><p><br /></p><p>dariya yayi sannan yace toh naji ya wuce yanzon kije ki kwata, inason zaje na shirya kinga lokaci na wucewa.</p><p><br /></p><p> haka fatima ta wuni da tunanin haydar dan gsky ba karamin tausayi ya bata ba zama tayi tai tagume tace a zuciyar ta toh yanzun da haydar ya mutu ya rayuwa ta zata kasance, afili tace Innalillah wa ina ilaihir raju,un.</p><p><br /></p><p>haka taita tunani daga baya ta wuce dakin ummi acen ta wuni har yanma ita da taslim.</p><p>.</p><p>shima haydar daya dawo barayin ummi ya shiga sai dare ummi tace su tafi dakin su.</p><p><br /></p><p> fatima bata jira haydar ba gaba tayi tana shiga ta fada toilet wanka tayi ta gyara jikin ta.</p><p><br /></p><p> zama tayi tana jiran shigowan haydar amman har kusan 10:30 be shigo ba , zuwa cen taji motsin shi afalo dan haka ta mike, ta dauki karamin hijjab dinta ta saka ta nufi falon .</p><p><br /></p><p>koda ta fito falo baya nan, dan haka ta nufi dakin shi, sallama tayi ta turo kofar yana kwance akan gado yana danna waya, ya dago ya kalleta ya saki murmushi.</p><p><br /></p><p> Alama yayi mata da tazo ta zauna a gaban shi, tana zama ya jawota jikin shi ya rungume dan bakaramin dadi yaji ba dayaga ta kawo kanta da kanta.</p><p><br /></p><p> *******</p><p><br /></p><p>washegari fatima sai kusan sha biyu na rana ta fitoh dakin haydar, kwana 1 kawai da tayi adakin haydar harta fita hayyacin ta , tun daga wannan ranar fatima bata sake yinkurin hana haydar hakkin sa ba, koda sonawa zai nemeta bata hanashi, saidai idan bayanan ta zauna taita kuka, kuma dataji dawowar shi gabanta ke faduwa.</p><p><br /></p><p> ahaka har suka kwashe wata 5 fatima sai ramewa take,gashi al,adanta shiru har yanzon, kuma cikinta nata kara kunbura harda wani motsi yake , bata manta lokacin da tacewa haydar har yazun fa al,dan ta be dawo ba kuma gashi cikin ta sai girma yake , kodai cikin be fita bane yana nan, amman sai yace mata ya fita mana ,ai kece bakishan magani akan lokaci shiyasa yake kumbura miki ciki ,nan gaba ma har mutse zai dinga miki.</p><p><br /></p><p>tagumi tayi tana kallon cikin zuwa cen ta fara tuno lokacin da haydar ke magana saitaga kamar yanayi ne yana boye darigar sa, dan haka ta fara tunanin anya kuwa ba wayo suka shirya mata ba, hanya kuwa ciki yana fita ta fitsari, afili tace koda yake likitan yace sabon magani ne, toh amman meyasa cikina yake girma kamar na me ciki kuma meyasa yaya haydar yake boyewa yana dariya, mikewa tayi tare da fadin nasan abinda zanyi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> barayin ummi ta nufah acen ta samu haydar dan haka ta wuce dakin taslim, ta bar haydar da ummi suna hira .</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tana shiga samu taslim zaune ko zama bata yi ba tace taslim zo na aikeki gurin ummi amman karkice nice na aiko ki.</p><p><br /></p><p> tace toh anty babba inajinki.</p><p><br /></p><p>fatima tace dan Allah kije ki tambayo min ummi wai dagaske ne ciki yana fita ta fitsari?</p><p><br /></p><p> taslim ta zaro 😳 tace ni wlh bazani ba, kina ganin dazon daga Mubarak yazo gurina ummi tace wai tunda aure nake so nace mishi ya turo, yazun kuma sai naje mata da zancen ciki?</p><p><br /></p><p> shiru fatima tayi zuwa cen ta sake cewan dan Allah taslim kije mana.</p><p><br /></p><p> Taslim rufe ido tayi tace bafah zani ba, idan kin matsu kitashi muje na raka ki.</p><p><br /></p><p> Ba yadda fatima ta iyi Dan haka tace muje.</p><p><br /></p><p> suna fitowa haydar ya daure fuska kamar baya dariya sabo da ganin taslim.</p><p><br /></p><p> zama sukayi guri daya kamar munafukai kowa bakin shi na motsi.</p><p><br /></p><p> ummi ta kallesu tace fatima yaya meya faru?</p><p><br /></p><p> shiru tayi kamar bazata yi magana ahankali tace ummi wai ciki yana fita ta fitsari?</p><p><br /></p><p> dasauri haydar ya dago ya kalli fatima sannan ya harari taslim</p><p><br /></p><p> Cike da mamaki take kallon fatima tace wanne irin ciki ne kuma yake fita ta fitsari ke waye ya gaya miki?</p><p><br /></p><p> haydar ta kalla sannan tace yaya haydar ne yacemin cikin ya fita ta fitsari.</p><p> </p><p> dariya tayi irin tasu ta manya tace wane cikin ne ya fita bayan wanda yake jikin ki, tsokanan ki yakeyi, ta juya barayin haydar tace kaikuma ya zaka dinga firgita ta ai irin wannan sai kasa jininta ya hau</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Daure fuska yayi sannan ya kalli taslim yace ke tashi kibar nan gurin.</p><p><br /></p><p> Gudu gudu ta mike har tana tuntube ya juya ya kalli ummi yace ummi kisan meye?</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> 🕊🕊</p><p>Mmn Yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[8:12PM, 5/6/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>97 - 98</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ban sani ba saika fad'a, ummi ke fadin haka cike da haushin haydar.</p><p><br /></p><p>Dariya yayi sannan yace ummi toh ki sallame fatima sai muyi maganar.</p><p><br /></p><p> Tace bazan sallameta ba idan ma bazakayi mgnr ba ka barshi, ta juya gurin fatima tace ke kuma ki kwantar da hankalin ki karya yake miki, cikin ki na nan lfy kalau, kema ban da shashanci irin naki ina kika taba jin ciki ya fita ta fitsari.</p><p><br /></p><p> Turo baki tayi tana hararar haydar tana fadin wlh ummi shine yace min wai yanzon haka akeyi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Juyawa ummi tayi ta rufe haydar da fada, dan haka ya warware mata kome.</p><p><br /></p><p> Bayan ummi ta gama sauraran haydar komawa tayi kan fatima , daga karshe ta koma nasiha tare da lallashin ta da ta kwantar da hankalin ta.</p><p><br /></p><p> Hawaye take sharewa, haydar ko ido ya zoba mata.</p><p><br /></p><p> zuwa cen ummi tace toh kutashi ku tafi dare nayi.</p><p><br /></p><p> Fatima bata tsaya jiran haydar ba gaba tayi , tana tafe yana binta abaya.</p><p><br /></p><p> Suna shiga barayin su haydar ya rike fatima, yace</p><p><br /></p><p> Wai fushi kk yi dani?</p><p><br /></p><p> Rufe idon ta tayi domin ko ganinshi bata sonyi.</p><p><br /></p><p> Saidai azuciyar ta koda taji cikin nanan batajin tsanar shi, saima wani sabon so da takeyiwa cikin, abin da kawai yabata haushi rainin wayon da su haydar suka mata.</p><p><br /></p><p> Muryar haydar ce ta katse mata tunanin dayake fadin , fatima banayi haka da niyar yaudararki bane, naga awannan lokacin bani da kalmar da zan rarrashiki da ita ne idan ba wannan ba. amman kema inda kina da wayo zakisan baxan dauke ki da hannu na nakaiki acire miki cikin ba, ni yanzon abin da nakeso dake ki kwantar da hankalin ki, insha Allahu nan bada dadewa ba salis karami zai iso.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Murmushi ta saki har zuciyar ta taji dade kanta tasa akasa saiga hawaye yana zubo mata.</p><p><br /></p><p> Haydar ya kalleta yace toh meye abin kuka kuma, ke babu damar ayi maganar salis saiki kama kuka, kina nufin kin fini sonshi ne?</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Cikin kuka tace ban fika son shiba amman nafika kaunar shi.</p><p><br /></p><p>nan danan fuskar haydar ta cenza, yace toh naji mubar maganan kawai.</p><p><br /></p><p> Shiru tayi zuwacen ta sake cewa kaima wlh idan har zaka fadi gaskiya kasan har son na shima na fika.</p><p><br /></p><p> Mikewa yayi cikin daga murya yace nace miki kibar mgnr ko bazakibar ta bane, juyawa yayi har ya fara tafiya ya bude kofar zai fita sai kuma ya dawo idon shi jawur cikin fada yace ai dole ne ki fini sonsa tunda tare aka hayfeku, kuma ni banson kina sonsa ba sai ranar da kika....... kasa karasawa yayi ya dafa kanshi da duk hannuwan shi guda 2 sannan ya girgiza kai ya fita.</p><p><br /></p><p> Binshi da kallo tayi itama hawaye ciki da idonta azuciyar ta tace kodai haydar kishi yake da yaya salis idan ba haka ba yaya za,ayi daga mgn sai ya dau zafi haka, mikewa tayi tabi bayan sa ta sameshi adakin shi ya hada kai da gado.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Karasawa tayi ta dafa shi ko d'agowa beyi ba, tace yaya dan Allah da gaske kk yi sunnan salis zaka saka min idan nahaihu?</p><p><br /></p><p> Wani sabon haushi ne ya kamashi domin da ace fatima tasan zafin dayake ji azuciyar shi idan tayi maganar salis da bazatayi ba, badan yanajin kunyan kar ummi tace yana kishi da d'an uwan shiba dasai ya fasa mata baki wata kila daga lokacin zata kiyaye shi, dagowa yayi da jajayen idonshi ya kalli fatima sannan yace</p><p><br /></p><p> Ai badan ke zansa sunan ba dan kaina zan saka dan d'an uwa nane tare muka kwanta acikin mahaifiyar mu aka kuma hayfemu tare kuma mukasha nono tare muka girma ,dan haka duk wata kyauna dazaki nuna kina mai a bayan nine, dan ku su ummi da sukai sular zuwan mu duniya bazasu fini kaunar shi ba, bare ke.</p><p><br /></p><p> Cikin fatima cike da dariya tace meda wukar, yaya daga wasa saika dauki abu da zafi aini wasa nake maka ni son da nake mishi ma ai dane, Allah ya huci zuciyar ka.</p><p><br /></p><p> Fuskar shi adaure yace ke kika sani, fita kibani guri.</p><p><br /></p><p> </p><p> Kalon shi fatima tayi damamaki azuciyarta tace wannan wani irin kishi gareshi dan tunda suka shirya baya taba bari su raba shinfida amman shine yau harda koran ta.</p><p><br /></p><p>Mikewa tayi da niyar ta fita adakin amman saitaji batason yin hakan saboda tafi kowa sanin halil haydar idai ko har ta fita adakin yau bazaiyi bacci ba wata kila ma sai yayi ciwon ciki, dan haka ta fara kokarin hawa gadon, gefen shi ta kwanta ta daura kanta ajiki shi.</p><p><br /></p><p> Ahankali yace wai banace ki fita bane?</p><p><br /></p><p>Itama daure fuska tayi sannan tace nifa bazan fita ba, kwanciya zanyi, kuma ai nace maka kayi hakuri.</p><p><br /></p><p> Baza yayi da ita ya rufe ido dan haka fatima ta zuba hannunta duk 2 cikin rigar shi tana mai cakulkuli tun yana fadin meye haka bari mana, har ya fara dariya, daga karshe ya shiga ramawa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tun daga wannan rana suka kara kullewa kamar sa ahad'iye juna sabo da yadda suke nunawa junan su so, tun da fatima ta gane haydar baya son tana mgnr haydar ta daina yi agaban shi, saidai data tuna salis zata shiga daki tai kuka dan son da takeyiwa salis ajininta yake.</p><p><br /></p><p> Ayanzun haka dai cikin fatima ya isa hayhuwa girma yayi sosai dan yanzo fatima zama da ker dashima haka, wani zubin idan fatima ta kalli cikin tsoro yake bata, daidai wannan lokacin ne aka tsaida bakin taslim ita da mubarak dane agun kawar ummi , kuma mahaifin shi hamshakin me kudi ne, ba,asa rana me tsayi ba sati 2 kawai akasa</p><p><br /></p><p> Fatima bataji dadin saranar da akayi a wannan lokacin ba dako tafiya daker takeyin ta, dan haka lokacin da daddy yake sanar musu ta fara kuka.</p><p><br /></p><p> Daddy ne ya lura da ita dan haka yace mamana yayadai?</p><p><br /></p><p> Goge hawayen ta fara sannan tace daddy da anbari bayanzun ba, kagani fah bana iya tashi</p><p><br /></p><p> Dariya sukayi sannan haydar yace ton idan kina iya tafiyar me zakiyi?</p><p><br /></p><p> Bata kulashi ba ta sake cewa daddy dan Allah abari sainan da wata 1.</p><p><br /></p><p> Fukar daddy cike da dariya yace mamana ki cire mgnr biki azuciyar ki mu fatan mu Allah ya rabaku lfy, wata kila ma kafin bikin ,kiga kin haihu, ina fatan dai duk kunsaya kayan haihuwa?</p><p><br /></p><p> Kan fatima akasa tace nima ban sani ba.</p><p><br /></p><p> Daddy ya waiga ya kalli ummi sannan yace kuna nufin ba,asai komai ba har yanzun?</p><p><br /></p><p> Murmushi tayi sannan tace alhj komai yana hannu itace dai bata sani ba.</p><p><br /></p><p> yace toh yayi kyau ina fatan dai komai 2 kuka saya?</p><p><br /></p><p> ummi ce ta bashi amsa eh , daddy yace to ai yakamata ku nuna mata ko akwai wani abun da take so ba,a saya ba.</p><p><br /></p><p> Ummi tace toh mijinta ne yace kar anuna mata.</p><p><br /></p><p> Fada daddy ya farawa haydar akan me zaice kar anuna mata, daga karshe yace maza aje anuna mata.</p><p><br /></p><p> Dakin ummi suka shiga ummi ce ke nuna wa fatima kayan haydar na zaune agefe.</p><p><br /></p><p> Gani tayi komai 2 ake daukowa, daidai da bahon wanka ma guda 2 ne, dan haka tace ummi meyasa naga kayan komai 2?</p><p><br /></p><p> Haydar ne yayi sauri yace, sabo da idan wani ya lalace ad'ako wani.</p><p><br /></p><p> Harara fatima ta galla mai sannan tace ni bakai nake tambaya ba.</p><p><br /></p><p> Ummi ta kallesu tayi murmushi sannan tace fatima haydar boye miki yake, likita yace yan 2 ne acikin ki, dan haka ki kwantar da hankalin ki, insha Allahu lfy lau zaki hayhu.</p><p><br /></p><p> Watsi tayi da kayan dake hannun ta tafara kuka.</p><p><br /></p><p> Ummi ta bita da kallo nan danan hankalin ta ya tashi ,zuwacen ta mike tayi daki, saboda tsoro amai ta dinga kwarawa, haydar na biye da ita, zuwacen ta rike ciki.</p><p><br /></p><p> Hankalin haydar ya tashi, wayar shi ya daga ya kira ummi ya gaya mata halin da fatima ke ciki, ba a dau lokaci ba saigata ta iso.</p><p><br /></p><p> Ummi naganin inda fatima keyi tace wa haydar yi maza ka fito da ita muje asibiti.</p><p><br /></p><p> Arikece haydar ya wawusu fatima yayo waje da ita</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🕊🕊</p><p>Maman yazeed</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>[10:01PM, 5/7/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊</p><p> 🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>🕊🕊🕊</p><p>*_Tsuntsu Me Wayo_*</p><p> 🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Storry & written_</p><p> By</p><p> *_Fadeela Lamido_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Na sadaukar da wannan page din ga iyalan 👇marigayi*</p><p><br /></p><p> _Alhj Lamido Bello_</p><p><br /></p><p> *Godiya ta mussaman ga yan group d'ina Fadila lamido novels ,bansan taya zan nuna farin cikina akan yadda kuke bani goyon baya ba, gasky Ina alfahari daku wannan page din bazai isa nakira sunan ku ba saidai nace Allah ya barmu tare*😍😍</p><p><br /></p><p> Jinjina gareku</p><p> </p><p> Faty Afreen</p><p> Cwtjiddah </p><p> zeezee</p><p> Billy galadanci</p><p> Ummi jafar</p><p> hussaina ubandiya</p><p> zeenasir</p><p> Aisha big girl</p><p> Yar gatan hudah</p><p> Yar mutan yudil</p><p> Hamagee</p><p> Fatima umar abdallah</p><p> Nana zee</p><p> Meenat tabacco</p><p> Anty sa,adatu</p><p><br /></p><p> Marubutan👆 mu kenan</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p>99 - 100✋</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kai tsaye asibiti suka nufa, daka kalli haydar kasan hankalin shi tashe yake, bayan anshiga da fatima dakin haihuwa ummi ta kalli haidar taga duk jikin shi yayi sanyi, dan haka ta matsa ta dafah shi tace ya haka kaida zaka mata addu,a Allah ya rabasu lfy kuma saikabi ka tada hankalin ka.</p><p><br /></p><p> yace ummi ina tausayin fatima sai nake ganin kamar bazata iya hauhuwan yara har guda 2 ba.</p><p><br /></p><p> Ummi tace Hmmm haydar kenan in Allah ya yarda lfy zata haihu lokacin dana haifeku nima ai kamar fatima nake .</p><p><br /></p><p> Shiru sukayi kowa da abinda yake sakawa.</p><p><br /></p><p> Zuwacen ummi tace haydar tashi kaje gida ka karbo min sako gurin taslim.</p><p><br /></p><p> tashi yayi badan ransa yaso ba.</p><p><br /></p><p> yana kokarin shiga gidan ummi ta kira wayar shi, cikin sauri ya dauka.</p><p><br /></p><p> Muryan ummi yaji cikin fara,a tana fadin Alhamdulillah fatima ta sauka.</p><p><br /></p><p> Alhamdulillah ya fara furtawa komawa yayi ya fada mota batare da ya karbi sakon da ummi ta tura shi ya karbo ba.</p><p><br /></p><p> Yana isa dakin da fatima take ya nufah ya samu ummi da mama zaune adakin.</p><p><br /></p><p> cike da fara,yake kallon su, mama tayi dariya sannan ta mike ta mikamai jaririn dake hannun ta, sannan ta dauko dayan ta sake mikamai , rugume su yayi ya kuresu da ido ganin yaran sunyi kama dashi sosai, idon shi cike da hawaye yace </p><p><br /></p><p> Mama ina hasan din yake?</p><p><br /></p><p> Ummi ce ta mike ta taho gurin ta leka fuskar yaran sannan ta nuna mai hassan din tana fadin kaga yadda yaran nan suke kuma haka kuke sak lokacin da na haife ku, naso ace salis nanan aka haifi yaran nan.</p><p><br /></p><p> Nan danan haydar ya fara kuka, daidai lokacin da dada ta fito da fatima daga toilet ahankali take tafiya fukarta kumbure da gani taci kuka ta gaji.</p><p><br /></p><p> Ummi ya mikawa yaran ya karasa gurin fatima ya rike mata hannu ahankali cikin rada yace sannu fatima.</p><p><br /></p><p> Wani sabon hawayen ne ya sake zubo mata.</p><p><br /></p><p> Haydar yasake cewa meyasa kk kuka fatima, keda zaki farin ciki kuma saiki na kuka.</p><p><br /></p><p> cikin kuka tace na tuna da yaya salis ne.</p><p><br /></p><p> Yace karki damu muyi hakuri kuma ai gawani salis din Allah ya bamu.</p><p><br /></p><p> ********</p><p><br /></p><p> Washegari suka koma gida cike da farin cike, agidan suka samu yadikko lokacin da haydar yaga yadikko abarayin su daure fuska yayi yace meya kawoki gida na, ko burin kunya kk zoyi.</p><p><br /></p><p> Itama daure fuska tayi tace tafiya da fatima nazoyi dan aguri na zatayi wanka.</p><p><br /></p><p> Haydar yace wlh baki isaba babu inda zata ina hauka ne zan baki matata ki tafi da ita.</p><p><br /></p><p> Dariya sukayi gaba daya dakin.</p><p><br /></p><p> Da daddare haydar na xaune adakin ummi saiga anas da mahaifiyar shi sunyi sallama adakin ummi.</p><p><br /></p><p> Bayan sun gaisa da ummi anas yazo ya mikawa haydar hannu suka gaisa sannan anas yayi mishi barka</p><p><br /></p><p> Kunyace ta kama haydar dan haka ya rike hannun anas sukayo waje, hakuri ya bashi akan abinda yaje har gida ya mishi.</p><p><br /></p><p> Anas yace aini daman ban rikeka azuciyata ba, amman abinda ya bani mamaki watannin danaga ka share baka nemeni ba, shine yasani tunanin kodai haryanzon kana kullace danine.</p><p><br /></p><p> Dafashi haydar yayi sannan yace baka ba ne , naki zuwa wajen kane saboda ina tunanin indai naje gurin ka zan iya komawa harka da nakeyi ada , wadda bazanso hakan ya kasance ba, dan ni yanzon bana shan komai kuma natsaya ga matata ce kadai, bana bin mata ayanzo.</p><p><br /></p><p> Anas yayi murmhshi sannan yace aini ma tuni na daina banayi yanzon bani ma da lokaci yazon tare muke kasuwanci da abban mu duk inda ya saka kafa ina biye dashi, kuma nima ayanzun inada iyali watan na uku da aure.</p><p><br /></p><p> Haydar ya zaro ido sannan yadan daki anas yace shine kayi aure baka nemeni ba.</p><p><br /></p><p> yace yazan nemeka bayan ka shareni yanzon badan naji lbr nazoba ai bazaka nemeni ba.</p><p><br /></p><p> Haka suka cigaba da tattaunawa saigurin karfe 10 suka bargidan.</p><p><br /></p><p> Ranara suna ta zagayo yaran sukaci sunan salis da haydar, suna sukayi sosai domin nuna farin cikin so da wadan yaran da Allah ya basu, kowa acikin wannan family daya bude baki cewa yake Allah yama wadan yara albarka.</p><p><br /></p><p> Shiko haydar azuciyar shi cewa yake Allah yasa duk su biyo halin salis.</p><p><br /></p><p> Itako fatima kirikiri take nuna tafi son salis din dan koda yaushe shi zaka gani ahannuta idan ma nono ne salis din take fara bamawa sannan tabawa haydar.</p><p><br /></p><p> Yadikko ce ke zaune da Fatima, ita ke kula da ita.</p><p><br /></p><p> Satin fatima 2 da haihuwa akai bikin taslim , zagewa fatima tayi akayi komai da ita dan idan ka kalli Fatima baxakace mejego bace tayi d'as da ita komai nabikin tare akayi da ita kai amarya ne kawai haidar ya hana fatima zuwa.</p><p><br /></p><p> Haka zaman su yaci gaba da kasancewa cikin farin ciki da annashuwa gashi yau kwanan fatima 34 , suna zaune ita da yadikko daki haydar ya kira wayar fatima , bayan ta dau suna gama mgn saita miki ta nufi fita.</p><p><br /></p><p> Hajiya tace ina zaki kuma?</p><p><br /></p><p> Tace inazuwa hajiya yanzon zan dawo yaya ne yake kira na, bata jira me hajiya zatace ba tayi gaba.</p><p><br /></p><p> Hajiya taita zaman jiran dawowan fatima shiru har 12:00pm gashi yaran suntashi sai kuka sukeyi , haka hajiya taita lallashin su amman inna kwana sukayi suna kuka haka hajiya ta kwana babu bacci.</p><p><br /></p><p> Da asuba ummi taji kukan su yayi yawa dan haka ta shigo har dakin fatima, samon hajiya tayi tsaye sai faman jijjigasu takeyi .</p><p><br /></p><p> Tace hajiya meya same su ina uwar su take.</p><p><br /></p><p> Hajiya tace tana gurin mijinta cen ta kwana.</p><p><br /></p><p> ummi batace komai ba tamika hannu ta karbi yaran ta wuce barayin ta dasu.</p><p><br /></p><p> Sai shidda da rabi na safe ta shigo tana sanye da jallabiyar haydar ta reke kasan da hannun ta saboda ta mata yawa</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hajiya na zaune akasa tana hada kayanta kallonta fatima tayi sosai sannan tace inakwana.</p><p><br /></p><p> Amsawa hajiya tayi ba yabo babu fallasa, fatima ta kalli gadon ,ganin shi tayi babu yaran kuma gashi ta kasa tambayan ta ina yaran suke.</p><p><br /></p><p> Zama tayi tai tagumi .</p><p><br /></p><p> Zuwacen hajiya ta gama hada kayan ta tamike ta yafah mayafin ta bude kofar zata fita.</p><p><br /></p><p> Mikewa fatima tayi tabi bayanta tana fadin hajiya ina zaki?</p><p><br /></p><p> Atakaice tace gida zani tunda naga kiyi arba,in harkin koma gurin miji.</p><p><br /></p><p> Bata rai tayi kamar zatai kuka tace bacci ne fah ya kwasheni ban sani ba dan Allah kiyi hakuri, </p><p><br /></p><p> Ko sauraran ta batayi ba ta fita adakin.</p><p><br /></p><p> Kukun fatima ne ya fito da haydar yana tambayan ta menene yafaru.</p><p><br /></p><p>Bayan ta gama gayamai yaja tsaki yace toh ai gwara ta tafi daman ta takuramin.</p><p><br /></p><p> Bin bayan hajiya sukayi suka sameta afalon daddy su ummi na bata hakuri tana fadi wlh gida zani bazan zauna ba, yara basu da kunya mezan zauna nayi.</p><p><br /></p><p> Haydar ko ganin inda yadikko take fada sai dariya yakeyi, daddy yakalle shi yace kai fita kaba mutane waje.</p><p><br /></p><p> juyawa yayi ya fita fatima ko sai share hawaye takeyi.</p><p><br /></p><p> Daddy yamike ya zubawa fatima yaran sannan yace wa hajiya muje na kaiki gida.</p><p><br /></p><p> Suna fita fatima ta kalli ummi tace wlh ummi yaya ne yahanani...... </p><p><br /></p><p> Ummi ce ta katse fatima da fadin ni ban tambayeki ba ai mijin kine bakiyi laifi ba, hajiya tana guje miki wahala ne tanason yaranki suyi kwari tukuna.</p><p><br /></p><p> Haka fatima ta wuni sukuku saboda damuwar tafiyan hajiya.</p><p><br /></p><p> Da daddare ummi ta kira haydar fada tamai akan barin yaran da sukayi gurin gajiya san tace batason ta karajin kukan su dan idan taji kukansu kuma har taga da ganga akabarsu toh fa zata dauke fatima harsai ta yaye yaran Zatw dawo dakin ta.</p><p><br /></p><p> Wani sabon amarci suka bude wadda ba,ayishi daba, haydar dakansa yana tunanin wai ya kayi ya zama haka akan fatima ji yake kamar ita kadaice mace aduniya.</p><p><br /></p><p> Lokacin nata tafiya yanzo yan biyu watan su 7 kuma a daidai wannan lokacin ne fatima ta fara rashin lfy duk abinda taci saita amayar dashi ta dade tanajin cenji ajikin ta, dan haka yau data wuni amai abin ya dame ta, haydar na dawowa ta tareshi da zance.</p><p><br /></p><p> Haydar karame ya dauka yasashi akan ruwan cikin shi sannan yace mekika ce?</p><p><br /></p><p> Bakinta cike da miyau tace aikaji abin da nace.</p><p><br /></p><p> Haydar ya daga ya daura mata akan ciyarta sannan ya dauki salis ya rugume yace to kodai ciki ne.</p><p><br /></p><p> Cikin muryan kuka tace nima abinda nake zargi kenan , dan Allah kazo muje asibiti aciremin.</p><p><br /></p><p> Haydar yace kina hauka ne kinga karki sakemin mgnr zubar da ciki kisan dai yanzon ba da bane , idan bakina son ranki ya baci bane karki sakemin wannan maganar.</p><p><br /></p><p> Mikewa tayi ta wurga mai haydar , cikin sauri ya saka hannun shi ya rike shi kuka ya saka saka makon firgita da yayi.</p><p><br /></p><p> Fatima ko waigowa batayi ba , dan haka haydar ya kule.</p><p><br /></p><p> Lallashin shi ya shiga yi amman yakiyin shiru, zuwacen salis ma ya fara, haydar ya rasa ya zaiyi dasu, ummi ce taji kukan yayi yawa ta shigo. salis ta gani tsaye ya hada su duk biyun yana jijjigawa.</p><p><br /></p><p> Ummi ta mika hannu ya saka mata haydar tace ina mamar su?</p><p><br /></p><p> Idonshi jawur yace ummi ki rabu da ita kawai zanje na sawo musu madara.</p><p><br /></p><p> Tace akan me wani abune ya faru?</p><p><br /></p><p> Cikin fada yace kibarta kawai yariyar nan ta riga ta raina ni kwata kwata bata ganin mutun ci na.</p><p><br /></p><p> ummi ta fara kwalawa fatima kira.</p><p><br /></p><p> Saigata ta fito sanye da hijjabi , ummi ta bita da kallo tace fatima yazaki bar yara kinaji suna kuka, idan ma wani abu ne ya faru tsakanin ki da haydar aisu babu ruwan su , dan Allah karki kara hucewa akan su, zoki karbe shi kibashi nono.</p><p><br /></p><p> Mikewa tayi ta wuce ummi taje gaban haydar tace kawo shi.</p><p><br /></p><p> Daure fuska yayi sannan yace bazan bayar ba kije ki fara bawa haydar shine yake kuka.</p><p><br /></p><p> Itama cikin fada tace ai yafishi jin yunwa kawai dan dai yana da hukuri ne kabani shi, waccen dama rigimar tsiya gareshi.</p><p><br /></p><p> Ummi tace wai meyasa kuke irin wannan ne, ke rabo dashi kizo ki karba haydar din.</p><p><br /></p><p> Tana kuka take shayar da haydar karami, haydar ya bita da kallo yace ummi kinga arin abin da fatima takemin ko, wlh banbanci take nunawa atsakanin su wai ita tafison haydar danayi magana saitace wai ai yana da hakuri ne, ummi metake nufi da wannan mgnr Zagina takeyi kenan, ita har yanzun akwai wani abu azuciyar ta, wlh....</p><p><br /></p><p> Ummi tace ya isa haka haydar kubar mgnr ni banason fitana ta juya gurin fatima tace waike fatima me yasa kike haka, wadan nan yaran dukka fah yaran ki ne, kefah kikayi yunkuri kk haifesu meye naki na nuna banbanci atsakanin su, kinason su taso da rabowar kaine, yazun kamar wannan dan yaron har kin fara mai shedan rashin hakuri, nasiha ummi ta mata meshiga jikisa</p><p>sannan tace tabawa haydar hakuri.</p><p><br /></p><p> Ahankali ta fura kayi hakuri.</p><p><br /></p><p> Be amsa ba ya juya yace ummi, yanzon ma ciki gareta shiyasa take fushi .</p><p><br /></p><p> Zaro ido tayi tace ciki, toh fah, ai shikenan Allah ya rabasu lfy</p><p><br /></p><p> Haydar ne ya amsa da ameen.</p><p><br /></p><p> Washegari ummi ta shirya kai fatima asibiti haydar ne kejan motar, bayan sunje suna kan hanyar su ta dawowa Fatima taga wata me gasa masara tace</p><p><br /></p><p> Ummi kalli me masara ummi tace zakici ne?</p><p><br /></p><p> Tun kafin ta bada amsa haydar ya tsaya agurin da kanshi ya sauka.</p><p><br /></p><p> Zuwacen ya dawo ya mikawa fatima masarar sannan ya shiga motar ya zauna yace ummi kin gane yariyar cen.</p><p><br /></p><p> Kallon yariyar tayi cike da mamaki ta bude murfin mutar ta fita,</p><p><br /></p><p> Tana zuwa gurin tace ke ina yaron da kk hayfa?.</p><p><br /></p><p> Cikin firgici ta mike tace hajiya dan Allah kiyi hakuri wlh daman cen bani da ciki kawai nayi haka ne dan haydar ya aure ni dan allah ki gafar ceni.</p><p><br /></p><p> Tsaki ummi taja sannan ta koma motar suka kama hanyar gida.</p><p><br /></p><p> Haka rayuwa taci gaba da kasancewa agidan daddy cikin kwanciyar hankali shekaran yan biyu daya suka fara yawo ko ina lokacin fatima cikinta wata shidda, kuma adaidai wannan lokacin ne taslim ta haifi yarta mece wacce akasawa sunan Aisha, wantan Aisha 4 fatima ta sake haihuwan yan biyu mace da namiji.</p><p><br /></p><p> Murna ce ta kama haydar har ya fara cika bakin wai shekara me zuwa yan uku fatima zata haifar mai.</p><p><br /></p><p> Alhj yusuf da daddy kuwa ji suke kaamar sunfi kowa farin ciki, bare kuma hajiya yadikko me fatan tara uguwa guda, </p><p><br /></p><p> Ayanzun salis karami yana gun ummi shiko haydar yana gurin mama, dan haka fatima daga ita sai yan biyun ta .</p><p><br /></p><p> Ranar da fatima tayi arba,in haydar ya biyo ta har daki da bukatar shi, ke meme taki amincewa domin tsoran karta dau ciki,amman saida haydar yasan yadda yayi ya mata dubara suka lula.✋</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Alhamdulilah</p><p><br /></p><p>Sai mun hadu a sabon novel din na nagaba</p><p><br /></p><p> ~*_Ta mishi illah_*~</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p>Maman yazeed</p><p><br /></p><p>07014197556</p><p>🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊</p><p><br /></p><p><br /></p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-17939297775717771562021-01-28T21:00:00.001-08:002021-01-28T21:00:04.908-08:00SURUKATA CE SILA COMPLETE HAUSA ROMANTIC NOVELS WATTPAD<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-1B2aBK2UIf8/YA2RKn6X-RI/AAAAAAAAJhI/Yq4cf_6mjMEI0A9koEwjQVnVGX8oB_5jACLcBGAsYHQ/s2048/SURUKATA-CE-SILA.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="SURUKATA CE SILA COMPLETE hausa romantic novels wattpad" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-1B2aBK2UIf8/YA2RKn6X-RI/AAAAAAAAJhI/Yq4cf_6mjMEI0A9koEwjQVnVGX8oB_5jACLcBGAsYHQ/w320-h248/SURUKATA-CE-SILA.jpg" title="SURUKATA CE SILA COMPLETE hausa romantic novels wattpad" width="320" /></a></div><br /> [19/12, 18:07] Hassan Atk: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀<p></p><p> *SURUKATA CE SILA*</p><p>🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀</p><p><br /></p><p>*TRUE LIFE STORY*</p><p><br /></p><p>BISSIMILLAHIRRAHMANIRRAHIM</p><p><br /></p><p>BA MUYISHI DAN WANI KO WATA BA LABARINE DAYA FARU DA GASKE,DA WATA BAIWAR ALLAH,DAN HAKA IN KINCI KARO DA WANI ABU DAYAYI SHIGE DA RAYUWARKI ARASHINE.</p><p><br /></p><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p>*BY*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ZAHRA SURBAJO*</p><p><br /></p><p> *AND*</p><p><br /></p><p>*HUMMY LUV*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*1-2*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"wallahi baze yiwuba hakurina ya kare a gidannan,yarinya kamar mayya kin nace kin like aguri alhalin baki da amfani,wlh idan bakisa dana ya sakekiba sena kashe ki tunda ni kinsa yafi karfina kin mallakeshi"cewar wata mata dattijuwa,me kimanin shekaru hamsin aduniya,</p><p><br /></p><p>Tsugunne take agabanta tana kuka,se digar ruwa take dan kayan jikinta gaba daya ya yi sharkaf da ruwa.</p><p><br /></p><p>Bakinta na rawa sabida sanyi take fadin.</p><p><br /></p><p>"inna don Allah kiyi hakuri,wlh ban mallake miki yaroba,kigafarceni,don Allah"</p><p><br /></p><p>Wani wawan mari ta dauketa dashi wanda sabida zafinsa seda ta fadi kasa daga tsugunon da take.</p><p><br /></p><p>ita ko tsohuwar cigaba tayi da masifa.</p><p><br /></p><p>"Dan ubanki ni fes nake kallonki ke baki isa kimin kwarkwasa ba,da har zaki wani shake murya kina ban hakuri,Wallahi Jawahir na tsaneki natsani rayuwarki,duk sanda naganki kina numfashi ni nawa yi yake kamar ze tsaya,ina me shawartarki dakifita daga rayuwar dana tunkan nai miki illah"</p><p><br /></p><p>Wayyo jawahir hannu tasa ta kama kafar innan,tana kuka me tsuma zuciya tana fadin.</p><p><br /></p><p>"inna ki tausayawa zuciyoyin da basu san komai ba se kaunar junan su,don Allah karki rabani da Jabeer ina masa son dani kaina bansan adadinsaba,shima kuma yana sona,Daki rabani sa Jabeer ciwon sonshi da rashinshi ya kasheni na yarje ke ki kashenin da kanki,amman don Allah karki rusamin farincikina"ta karasa maganar cikin matsanancin kuka.</p><p><br /></p><p>"Uban waye ya shaida miki ina son farincikinki jawahir?nifa kaunarkice banayi,sam bana sonki ki kyalemin dana,amman matukar baki amince da zancena ba wlh sena sabauta rayuwarki,mayya kawai me gadon maita"</p><p><br /></p><p>Tana kaiwa nan azancanta ta hankadeta tabi takanta ta wuce tana ci gaba da masifarta.</p><p><br /></p><p>Da kyar Jawahir ta mike daga inda ta yar da itan,jikinta duk ya baci da kwata haka ta nufi dakinta tana dingishi dan da dukkan alamu taimata targade akafa takatan da tayi.</p><p><br /></p><p>Tana shiga dakinta Toilet ta shige,ta tube kayan,ta yi wanka,sukuma ta daurayesu da ruwa,dan ko sabulun da zata wankesu se taje gurin inna ta amso yanzu ko inna fushi take da ita tasan ko taje bazata bata ba.</p><p><br /></p><p>Cikin uwar dakanta ta shiga inda ta dauko wata doguwar riga tasaka,bata tsaya shafa maiba tabi lafiyar gado,badan taji dadiba,sedan tayi kuka kamar yadda tasaba kullum kwanan duniya.</p><p><br /></p><p>Bacin ranta na yau yafi na kullum,tunda yau ne Jabeer ke dawowa daga Abuja inda yake ayki,tayi kwalliyar tarbarshi gashi mahaifiyarshi ta bata mata su,tayi girki me dadi dominsa tazo ta shirya masa adaki mahaifiyarshi tasata ta kwaso ta kai dakinta dan kawai ta kuntatawa rayuwarta,</p><p><br /></p><p>karshema jikata tayi da ruwan sanyi sabida tsabar keta,haka taci gaba da tunaninta tana kuka gamida tausayin kanta,</p><p><br /></p><p>Tananan kwance ta jiyo karar mota,alamun Jabeer ya dawo,gabanta ne yayi wani mugun faduwa dan tasan dawowarshi daidai yake da karuwar tashin hankalin da take ciki.</p><p><br /></p><p>Kan tayi wani yunkuri tuni ya shigo cikin gidan,se jiyowa tayi anata hayaniyar murnar dawowarshi,dan dama ya kwana biyu be dawoba.</p><p><br /></p><p>Shiko jabeer ido kawai yake rabawa yaga ta inda Jawahir dinshi zata bullo amman shuru kakeji,karshema innarshi suka hada ido da ita ta shiga doka masa harara dole tasa yadauke idonsa daga kallin ƙoɗar dakin nasu.</p><p><br /></p><p>Duk yadda yaso ya je yaga jawahir dinshi amman fafur mahaifiyarshi ta hana shi fita yana gurinta ta tsareshi da zance wanda beda kai bare kan gado.</p><p><br /></p><p>Wasa wasa har karfe goma na dare jabeer na gurin Inna taki barinshi ya tafi,daga karshede kwanciya yayi adakin yafara baccin karya.</p><p><br /></p><p>Ganin hakane yasa inna ta tada shi tace yatafi dakin matarsa,kar yay mata bacci a daki.</p><p><br /></p><p>Ayko cike da farin ciki ya mike ze fice dauke da jakarshi,da sauri ra shaidashi.</p><p><br /></p><p>Bayan ya tsayane,ta taso da kanta tazo,ta amshi jakar ta ajiye,sannan tasa hannu a aljihunsa ta cajeshi tsab ta cire kudin jikinshi,shide binta yake da kallo,kasa daurewa yayi yace.</p><p><br /></p><p>"inna meye maanar hakan don Allah?"</p><p><br /></p><p>Harara ta watsa masa gamida cewa.</p><p><br /></p><p>"kai tafi can soko kawai wanda besan abinda yakeva,wato so kake na barka ka tafi dasu dakinta ta yasheka ko?"</p><p><br /></p><p>dafe kanshi yaƴi alamar takaici yace.</p><p><br /></p><p>"inna jawahir bata sata,kuma kinfi kowa sanin hakan,danme zesa to na gujeta da kudina?"</p><p><br /></p><p>"ni ficemin da gani shasha namijin hotiho kawai,wato ira bata sata ni nakeyi kenan ko?"</p><p><br /></p><p>"Ni bance haka ba,amman de gaskiya inna kidena yiwa jawahir haka dan in aka yiwa zainab bazakiji dadiba"</p><p><br /></p><p>Afusace tayo kansa tana fadin.</p><p><br /></p><p>"Jabeeru ka kitayenifa,wlgnatashi daukar mataki akanka bazaka ji dadiba,kodan kaga kai ina daga maka kafa shine har kasamu damar fadamin magana?kudine nace bazaka dasuba,inkaji zafi ka rufeni da duka"</p><p><br /></p><p>"Allah ya baki hakuri"yace gamida ficewa daga dakin,ya nufi dakin gimbiyarsa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Allah sarki tana kwance tana kuka,dan ko kadan tagaza yin bacci kewar mijinta na damunta ta kosa tasashi a idonta,ko zataji dadi.</p><p><br /></p><p>Da sallamarshi ya shigo dakin,ganin bata falone yasa ya shiga cikin dakin,akwance ya hangota kan gado ko baa fada masa yasan kuka takeyi,ji yayi zuciyarshi tai masa baki ranshi na kuna dan ba abinda ya tsana kamar ganin hawaye a idon jawahir.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Takawa yayi a hankali ya hau kan gadon,dagota yayi gaba dayanta ya mannata da kirjinshi ya rungumeta.</p><p><br /></p><p>Ayko fashe mishi tayi da kuka tana kara shigewa jikinshi,Rarrashinta yashiga yi yana shafa bayanta,dan ko bata faɗa masa ba yasan ita da inna ne.</p><p><br /></p><p>Da kyar yasamu tayi shuru,tayi lub ajikinshi tana ajiyar zuciya,se alokacin yaji hankalinshi ya kwanta ganin ta dena kukan.</p><p><br /></p><p>Dagowa tayi ta kafeshi da idanuwanta da suka rine sabida kuka,tace.</p><p><br /></p><p>"Don Allah Hubby ka roki inna karta rabani da kai,wlh bazan iya rayuwa babu kaiba don Allah"ta karasa maganar cikin kuka.</p><p><br /></p><p> da sauri ya hade bakinshi da nata dan yasan in yabarta taci gaba da magana karshenta shima tasashi kukan.</p><p><br /></p><p>Cikin salo da kwarewa yake tsotson bakinta,wanda hakan ya tilastawa jawahir yin shuru ta maida hankali gurin amsar sakon nashi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Muje zuwa.</p><p>[19/12, 18:07] Hassan Atk: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀</p><p>*SURUKATA CE SILA*</p><p>🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀</p><p><br /></p><p>*BASED ON TRUE LIFE STORY*</p><p><br /></p><p> *BY*</p><p><br /></p><p>*ZARAH SURBAJO*</p><p><br /></p><p> *AND*</p><p><br /></p><p>*HUMY LUV*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*2-3*</p><p><br /></p><p>Tun tana ajiyar zuciya har ta sake gaba d'aya suka Lula duniyar masoya, sai wajan share d'ayan dare suka dawo cikin hayyacin su ,Tashi jawahir tayi suka shiga toilet bayan sun fito Jabeer yaji cikin sa na kukan yunwa kallon jawahir yayi sannan yace "happy yunwa nake ji"zaroo ido Tayi sai lokacin ta tuna bata bashi abinci ba </p><p>,hawaye ya shiga Xuba Mata, ta Matso kusa dashi ta manna kanta a k'irjin sa tana magana cikin muryar kuka"hubby kayi hakuri abincin ka na gurin Inna na d'auka kaci acan gurin ta Kafin ka shigo"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hmm Banci komai ba </p><p>had'a min tea Mai Kauri nasha"kuka ta saki Wanda yasa shi rud'ewa "happy what's wrong with you again? su Zainab sun kwashe komai ne?"kai ta d'aga masa alamar Eh!.</p><p><br /></p><p>DafE Kansa yayi sannan hannu yace "OK don't worry,mu kwanta dare yayi"a'a Bari naje d'akin Inna na d'auko maka" Yauwa ngd sosai happy" murmushi tayi doguwar rigar tasa ta nufi d'akin Inna. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tayi sallama yafi biyar ba Amsa ba kawai ta shiga ganin su Tayi suna barci ahankali take tafiyar har takai gurin Kular abinci tasa hannu Zata d'auka taji an rik'e Mata hannu nan da nan ta Fara kuka tafi Inna tafara Yi Tana fad'in </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Na shiga uku ban Lalace ba yau zan ga fitina, kaiiii tirrrr,kaambuu dama sata Kike min a d'aki idan bana nan? " </p><p><br /></p><p>Kai ta shiga girgizawa tana hawaye "Inna abincin jabeer nazo d'auka kiyi hakuri Kibani yunwa yake ji"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Eh! Lallai kin rik'a wato ni Zaku rainawa hankali ke da mijinki kud'in da na k'arba shine ya Turo ki Kizo ki sata dake ke kinfi Sanin yadda akeyi"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zatayi magana taji muryar jabeer "jawahir hayaniyar me nake ji haka? "</p><p><br /></p><p>Shiru ta Masa bata Ce komai ba kukan da yaji Inna keyi yasa shi rud'ewa ya k'ara so kan Gado "Inna meya Faru?" </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Jabeer Zaku Samin ciwon zuciya kai da matar ka,shikenan wlh ta wanke ta baka Kasha," </p><p><br /></p><p>"kai yake girgiza Mata alamun Tayi Shiru amma ina sai masifa take Tana fad'in </p><p><br /></p><p>"Sbd na k'arbi kud'in ka shine Zaka gaya mata, ita kuma ta kasa barci Saida ta biyo cikin dare Dan ta sata, to Allah ya Fiki munafuka sai rik'a Yi Kamar Saliha,ta k'ara fashewa da kuka"</p><p><br /></p><p>jabeer dake tsugune ya Zauna Ya rasa abinda zaice ya dubi Jawahir da ta had'a kai da gwiwa Tana kuka yace "happy let's go an sleep"</p><p><br /></p><p>Inna Najin haka ta rik'e baki Tana mamakin jabeer "Allah sarki jabeer Allah ya baka lfy Dan wannan annami miyar ta gama dakai"</p><p><br /></p><p>Jawaheer Najin kalmar da inna Ta fad'a Ta kai hannu Ta d'auki Kular abinci ta fita jabeer</p><p><br /></p><p>Yabi bayan ta,suna shiga d'aki ya rungume zaiyi magana ta sa hannu Ta Rufe masa baki "shhhh Zauna kaci abincin ka Bakomai jarabawa Ce kowa da irin Tasa" </p><p><br /></p><p>"happy kenan mu kwanta kawai muddin naci cikina zai Lalace"hmmm kuma Fa hakane kar ka kumburamin ciki Kafin safiya" </p><p><br /></p><p>"haha zo Kiji" ya Jawo ta jikin shi suka kwanta cikin Kunnin ya rad'a Mata.</p><p><br /></p><p>"happy I love you so deeply don't allow anybody to separate us pls,bazan iya rayuwa babu ke ba"</p><p><br /></p><p>"Hmmmmmmmm in-sha-Allah but ina fargaban gobe" </p><p><br /></p><p>"Inna ko? "kiyi hakuri tabbas gobe akwai Tashin hankali"</p><p><br /></p><p>"Bakomai INSHA Allah,amma ni canzswar inna yana bani mamaki sosai"</p><p><br /></p><p>"bake kad'ai ba har sister Hauwa Ma ta fad'a min haka,nikam Anya Inna tace kuwa? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Karka k'ara fad'in haka kawai sona ne batayi Shiyasa take maka haka"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zai k'ara yum magana ta Rufe masa baki tayi addu'a Nan da nan barci ya d'auke su.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Washe Gari* sai k'arfe Tara suka Farka salati suka shiga yii ganin sun makara dayawa toilet suka shiga Alwala sukayi sannan suka fito atare sukayi sallah bayan sun gama ta jawaheer ta kalli jabeer fuskar Ta d'auke da murmushi tace </p><p><br /></p><p>Barka da Safiya Mijina,ya gajiyan hanyar? "Barka dai happy ina fatan kanki bays miki ciwo"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Baaya yi bari na had'a mana breakfast"tsaya mu tafi tare na gaida Inna daga nan</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>muje xuwa💃🏻</p><p><br /></p><p>🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀</p><p> *SURUKATA CE SILA*</p><p>🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀</p><p><br /></p><p>*BASED ON TRUE LIFE STORY*</p><p><br /></p><p>*BY*</p><p><br /></p><p>*ZAHRA SURBAJO*</p><p><br /></p><p>*AND*</p><p><br /></p><p>*HUMY LUV*</p><p><br /></p><p>*Bilkisu U Hamza surbajo na gaisuwa Allah yabarmin ke ki jima ki karko,ina yinki irin sosai dinnan♥*</p><p><br /></p><p>*Last page munyi mistake na numberring*</p><p><br /></p><p>*5-6*</p><p><br /></p><p>Har takai bakin kofa da sauri jabeer ya bita a baya ya kamo hannunta,yana fadin.</p><p><br /></p><p>"happy ba jira irin wannan sauri haka"</p><p><br /></p><p>Murmushi tayi gamida kokarin kwace hannunta daga nashi,amman fafur yaki sakar mata hannun,cike da fargaba tace.</p><p><br /></p><p>"hubby pls ka sakarmin hannu kamin inna ta ganmu"</p><p><br /></p><p>Ko ajikinshi haka yajata zuwa waje tana tirjewa,</p><p><br /></p><p>Abinda ta guda shine ya afku,domin inna ce tsaye kofar dakinta ta kafesu dana mujiya,</p><p><br /></p><p>Shi kanshi jabir ya tsorata da ganinta amman se ya maze,ita ko jawahir tuni fitsari ya cika marar ta sabida tsananin firgita.</p><p><br /></p><p>Kwace hannunta tayi daga nashi ta matsa gefe da sauri</p><p><br /></p><p>budar bakin inna se cewa tayi</p><p><br /></p><p>"innalillahiwainnailaihirrajiun,yau ni ina zansaka rayuwata?yanzu jawahir karuwancin naki har yakai ki fito gabana ki nunamin,koda yake gado ay sedan gado barewa batai gudu danta yay rarrafeba"</p><p><br /></p><p>Da sauri jabeer ya karasa gurin inna,yafara bata hakuri.</p><p><br /></p><p>"Don Allah inna kiyi hakuri,wannan ba abun magana bane dan na rike mata hannu agabanki,dan haka don Allah kibar maganar"</p><p><br /></p><p>"kai dallah tafican shanyayye kawai,ni zaka duba kace ka rike mata hannu,agidan ubanwa ka rike matan bayan uta ta ruko ka,to wlh baka isa ba dole sena dauki kwakkwaran mataki akanku"</p><p><br /></p><p>Ita de jawahir sum sum tayi ta wuce inda ake girkin,inda ta tarar zainab ta dora ruwan zafi har yakusa tafasa,matsawa tayi kus da zainab din tana murmushi tace.</p><p><br /></p><p>"Yi hakuri zainab yau mun makarane shiyasa nabarki ke kadai,don Allah kiyi hakuri"</p><p><br /></p><p>A fusace zainab ta mike ta fara magana muryarta asama dan inna ta jiyo.</p><p><br /></p><p>"ke dallah can juya kawai,dan ubanki har kin isa kuzo gabana kicemin wai innace bata barku kunyi bacci da wuriba,yanzu kuma ta tsaidaku da masifarta?wlh baki isaba ni nasan darajar mahaifiyata,wawiya mayya kawai"</p><p><br /></p><p>Tsananin mamakin sharrin zainab ne ya hana jawahir koda motsine,baki kawai ta saki tana kallonta.</p><p><br /></p><p>lokaci guda inna da Jabeer suka karaso gurin.</p><p><br /></p><p>Jabeer na zuwa ya daga hannu ya wanke zainab da mari,beyi wata wataba ya rufeta da duka,badan komaiba sedan zagin matarsa da tayi tana kanwarsa wacce a girme ma jawahir din ta girmeta nesa ba kusa ba.</p><p><br /></p><p>"wayyo na shiga uku mayya ta shigomin rayuwar da gashinan tasa ze nakasa yar uwarsa,Jabeeru ka sakarmin yarinya wlh ka kuma dukanta sena baka mamaki"</p><p><br /></p><p>Kobi takan inna beyiba,dan so yake yau ya kotawa zainab hankali dan tana daya daga cikin masu haddasa fitina tsakanin inna da jawahir.</p><p><br /></p><p>Da gudu jawahir taje gurinshi tana janshi,tana kuka tana fadin.</p><p><br /></p><p>"hubby kayiwa girman Allah ka kyaleta don Allah kabarta wlh ni banji haushiba"tanayi tana janshi.</p><p><br /></p><p>Tureta yayi ta fadi batare daya saniba,hakan yay dadidai da karasowar inna dauke da tukunyar tafasasshen ruwan zafi,bata jira komaiba ta juyewa jawahir tafasasshen ruwan zafin a kafa.</p><p><br /></p><p>Wata razananniyar kara ta saki,wacce ta janyo hankalin jabeer gurinta,tiririn da yagani na tashi ajikinta da tukunyar da yagani a hannun inna shi tabbatar masa da abinda inna ta aykata.</p><p><br /></p><p>Aguje yayi kan Jawahir,wacce zuwa lokacin sabida tsananin azaba tuni ta sume,Agigice ya dauketa ze fice da ita daga gidan,</p><p><br /></p><p>Da suri inna tasha gabanshi gamida cewa.</p><p><br /></p><p>"wlh kasake kafita da wnnan bakar kadarar daga gidannan ban yafemakaba"</p><p><br /></p><p>Idonshi jawur yadubi inna yace afusace.</p><p><br /></p><p>"Allah yace,ci da shanta da suturarta da gurin kwananta da lafiyarta duka nauyine daya rataya awuyana,wanda inbanyiba inada halin yin se wutarsa tacini,kuma yashaida mana,la daata li makalukina fi maasiyatil kaliki,dan haka inna zan fita da jawahir daga gidannan koda bada izininkiba inyaso kije kaaba ki tsinemin acan"</p><p><br /></p><p>Yana kaiwa nan yas kai yafice dauke da uta rai ahannun Allah,motarshi ya nufa yasata aciki,yaja da gudu zuwa asibiti mafi kusa.</p><p><br /></p><p>Ita ko inna baki bude tabusu da kallo,ganin yafitanne yas ranta yasake baci tasake dauka mummunar aniya akansu.</p><p><br /></p><p>A asibitin kuwa sun anshesu da gaggawa unda sukayi nasrar farfadowarta,duk inda ta kone sukabi suka cire fatar gurin gamida wankewa,sukamata dressing din gurin,azaba iya azaba tashata se kuka take jabeer na tayata .</p><p><br /></p><p>Gado aka bata a asibitin,inda jabeer ke jinyarta gar tsawon sati biyu,be taba zuwa gidan inna ba sede yaje gidan abokinshi yayi wanka acan yasa kayan abokin yayinda itakuma matar abokin ke zuwa mata da kayan da zata sa,kuma su suke kawo musu abinci.</p><p><br /></p><p>Ranar da aka sallamesu ma dakyar take taka kafafunta,da taimakon Jabeer ta iya zuwa mota,yaja suka nufi gidan inna.</p><p><br /></p><p>Suna zuwa Allah tataimakesu tana bacci dan haka da sauri suka shige dakinsu,sede sunyi shuka a idon makwarwa dan zainab tagansu da gudu taje ta shaidawa inna.</p><p><br /></p><p>Ayko afusce inna ta nƴfo dakinsu,jabeer ya hangota d sauri yaje ya kulle kofar koda tazo tadunga bugawa yaki budewa,ayko nan tashiga laantar jawahir.</p><p><br /></p><p>Itako tana dakin tan kuka tana tunanin sauyawar halayyar inna,koda was akace mata inna zatamata haka zata karyata,innan da da ko bacci vata iyayi inde ita batayi ba yau itace ke hanata bacci,inɓar da da inbata da lafiya cikin kuka take yau itace ke janyo mata ciwon fashew tayi da kuka tashiga tuno rayuwarsu acan baya.</p><p><br /></p><p>FARKON LABARIN</p><p><br /></p><p>Muje zuwa</p><p><br /></p><p>🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀</p><p>*SURUKATA CE SILA*</p><p>🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀</p><p><br /></p><p>*BASED ON TRUE LIFE STORY*</p><p><br /></p><p> *BY*</p><p><br /></p><p>*ZARAH SURBAJO*</p><p><br /></p><p> *AND*</p><p><br /></p><p>*HUMY LUV*</p><p><br /></p><p>*Mzeeta,Ermeenart Auta BK, wannan Shafin nakune ina yinku irin sosai dinnan*❤</p><p><br /></p><p>*6-7*</p><p><br /></p><p>*Farkon Labari*</p><p><br /></p><p>Jawaheer 'yace ga Alhaji Ja'afar ma'aikacin Wani company shine manager agurin Mutum ne Mai son mutani yana da rufin asiri gidan sa d'an Mai daidaici Suna RAyuwar su cike da jin dadi da son juna shi da matar sa d</p><p>hajiya Rakiya suna zaman lfy Allah ya azurta su da yara Guda bakwai jawad shine Farkon Dan su,Juhaifat, Junaid jawaheer,</p><p><br /></p><p>jadwat,Jameelu,sai d'an autar su Jabeer, inkiyar gidan su shine *J-J house* Yawan cin su da wannan sunan ake Kiran su,jawaheer ta kasance yarinya Mai farin jini Tun Tana y'ar k'aramar ta gata kyakkawa Fara Ce Sol gata da jiki maikyau y'ar Duma Dumaa, </p><p><br /></p><p><br /></p><p>mutani na son ta Sabida fara'ar ta gata da son mutani saidai bata d'aukar wulakanci ko kad'an Tana da son Tara, </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mahaifin SU banufe ne suna zaaune a Zaria sabon Gari,sun Sami karatu sosai both Arabic and English gaba d'ayan Suna zaune lafiya soyayya tsakanin Momy da dad d'insu yaja baya Sanadiyyar komawa da yayi Lagos acan ya Auri wata yaroba,</p><p><br /></p><p>Ya kan dawo gida every weekend daga baya Yakoma karshen wata.</p><p><br /></p><p>Haka suke Rayuwa da d'adi ba d'adi Suna zaune karatun su ya tsaya Sanadiyyar rashin school fees hakan yasa Maman Yankee hukuncin Fara sana'a, Tana cikin wannan tunanin sukaji sallamar Dadyn su da gudu jameelu da jabeer suka je masa Oyoyo,wani Abun mamaki shine Alhaji Ya marii jameelu sbd ya taka shi rik'e baki sukayi ganin sabon lamari agurin sa,hakan MA bai gama Basu mamaki Saida yace akwai general meeting yanzu a parlour ,</p><p><br /></p><p>wannan Rana Baza su ta a taba mantawa da shi ba, Suna zaune a parlour dukkan su Harda Dadyn su ya dubi Jawad yace "Son tunda kun girma kai da Ja'afar ina ganin Zaku iya rik'e k'annen ku.</p><p><br /></p><p>Ya dubi Mom yace"Rakiya na Kiyi hakuri da abinda zan gaya miki Nima ba'ason Raina bane,na sauwak'e miki,ni Na tafi Dan sauri nake ana jirana,"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Har yakai bakin k'ofar gida ta bishi da gudu ta rik'e masa k'afa "Alhaji karkamin haka agaban Yarana dan Allah Ka gayamin laifina wlh zan gyara"</p><p><br /></p><p>"kiyi hakuri Rakiya baki min komai ba Baffa ne ya umarce ni da cewa idan nasan bana sonki yanzu na sauwak'e miki Tun Kafin yayi fushi Dani Wai ina shiga Hakkin ki dayawa"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana kai karshe ya fita Tun daga wannan ranar suka Fara shiga Halin mairaici ga mahaifin su a rayee amma Suna maraicin UBA ,bayan watanni uku Hajiya Rakiya ta Yankee hukuncin kafa shagoo tafara Saida abinci ta kashewa yaranta mata xuwa makaranta sbd ba kud'i,amma Mazan sun cigaba da xuwa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Jawaheer kullum Tana tare da momynta a shagoo. ita ke kaiwa baki abinci saidai baka taba ganin fuskar ta a sake,kwakwata Zaka d'auka bata Tab'a yin Dariya ba,wannan dalilin Ya hana maza dayawa tunkaran ta da zancen soyayya daga Cikin su kuwa Harda jabeer Dan Kwakwata soyayyar jawaheer na nimar hana sa aiki, </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wataranar laraba haka kawai Jawaheer taji Tana sha'awar yin kwalliya bayan Tayi wanka Tana </p><p>Nufi Gaban mirror Zaman dirshan Tayi Ta fara kashe lokaci Tana tsala makeup doguwar riga Tasa sannan Ta rolling gyalen akan ta,ta d'auko wata bakar eye 👓 tasa Ita kanta ranar tasan Ta hadu,hand pose ta d'auka pink da takalmi pink Tasa, sannan Ta nufi parlour Tace "Momy how did I look"?"Woow J-J You look gorgeously, gsky Jawaheer ba inda kika rage dadynki komai Nak'i sak ja'afar"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hmmmmmmmm haka Kaka yacemin jiya da natafi,Momy mu tafi Na shirya"</p><p><br /></p><p>"Yanzu kuwa Dan yau Friday kinsan yawancin Masu dawowa gida weekend daga Abuja Suna tsayawa suci abinci Kafin su shige"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yauwa ni kuwa Momy ina yaron ki Dinnan Mai sunan d'an Auta yana xuwa kuwa? "</p><p><br /></p><p>"yama cemin yau zai shigo fride rice yace na mishi mai hanta aciki zai kaiwa Innar sa"Hmmm ki bani nayi masa Mai d'adi"wato ni ban iya Mai d'adi ba ko?"a'a ni na haka nake nufi backyard, "jawaheer kenan"</p><p><br /></p><p>Suna hira har suka fito Titi suka tare adaidaita ya kaisu shago,suna xuwa Jawaheer ta Fara had'a girki banda k'amshi ba abinda yakeyi Rashid murmushi kawai take itadai gayen Yana burgeta Gashi ba ruwansa,ita k'adai take zancen cikin xuciyar ta har ta gama ta wanke hannun ta sannan Ta Nimi guri ta zauna Tana baza idoo ta ina zai shigo.kamar ance jawaheer d'aga idon ki ta hango wata Motar k'irar Lamborghini Black Tana shigowa layin Shagon su</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Masoyan mu bafa Afara komai Dan Lbrn jawaheer labarine Mai rikitarwa tausayi burgewa musamman RAyuwar auren ta Matar aureee ku shirya Dan kuwa Surbajo da Humyluv sun shirya Kawo muku abubuwan karuwa cikin wannan novel din*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>mujee xuwa</p><p><br /></p><p><br /></p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-18423538188593856402021-01-26T21:00:00.004-08:002021-01-26T21:00:02.747-08:00Sirrin zuci Complete Sabbin Hausa Novels<div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-ZJQb6ADDPbs/YA2MFOr1d1I/AAAAAAAAJg8/rG1k4HEjJEAFeOdmn04ZeuYZyky-kaddwCLcBGAsYHQ/s2048/Sirrin-zuci.jpg" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="Sirrin zuci Complete Sabbin Hausa Novels" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-ZJQb6ADDPbs/YA2MFOr1d1I/AAAAAAAAJg8/rG1k4HEjJEAFeOdmn04ZeuYZyky-kaddwCLcBGAsYHQ/w320-h248/Sirrin-zuci.jpg" title="Sirrin zuci Complete Sabbin Hausa Novels" width="320" /></a></div><div>💧💧SIRRIN ZUCI........</div><div> </div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div>1 to 2</div><div><br /></div><div> البسم الله الرحمن الر حپم</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Lumshe Ido yayi sannan ya budesu tar bisa kan wata karamar yarinya dake zanen yar galala ....</div><div><br /></div><div> Fito yayi da bakinsa a hankali ....da sauri yarinyar ta kallo sama tana murmushi tare tsalle tana daga mashi hannu ...</div><div><br /></div><div> Iska ya huro mata ...sannan ya daga mata hannu ....itama hannun ta daga mashi ....</div><div><br /></div><div> Wata tsohuwa ta fito daga wani karamin gida wanda duk unguwar babu talaka sama dasu ....</div><div><br /></div><div> Meenalle ...Meenalle. ..ta fara kwada kira ....</div><div><br /></div><div> Yar karamar yarinyar ta juyo da sauri tana bata fuska ...cikin shagwaba tace .....Kai kaka ke kullun sae ki batawa mutun suna ...nasha fada maki Meenal fa ake cewa? ...</div><div><br /></div><div> tsohuwar tace ...to naji sarkin hakuri zo muje ki sayo mana kwaki ko bakijin yunwa?</div><div><br /></div><div> Saman benen ta kalla. ..har yanzu yana tsaye ita yake kallo ...daga mashi hannu tayi tare da langwashe kai ...sannan taja hannu tsohuwar suka koma gida ....</div><span><a name='more'></a></span><div><br /></div><div><br /></div><div> Kudin ta karbo sannan ta sako hijab ta fito ...tana zuwa bakin kofa taja birki tare da dafe kirji ....hal ka ban tsoro ...ta fada hakoranta waje ...</div><div><br /></div><div> Hararanta yayi...ke kuma sarkin tsoro ko ...ya fada yana gyara mata hijab dinta ...</div><div><br /></div><div> Kai ...aikena fa akayi ...ta fada tana neman cire agogon dake makale a hannunsa ...</div><div><br /></div><div> Hannunsa ya janye don karta bata mashi...sannan yace ...Me zaki sawo?</div><div><br /></div><div> Baki ta tabe tana kokarin wucewa sannan tace ...kaini Kaka tace kabar sawo man komae ..wae ku yan yankar kaine ...kuma tace wae kaina zayayi tsada ...</div><div><br /></div><div> Dariya ya sake a hankali kafin yace mata. ..ni kuma kakata tace man indae mace na yawo to kasa ake rufeta ...ya fada idonsa na kallonta ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Ido ta waro cike da tsoro ...da gaske Mai kamshi?</div><div><br /></div><div> Ganin ta tsorota ya saka yace ..eh mana ai bana so a rufeki shiyasa ma nace ki fada man in sawo maki ...</div><div><br /></div><div> Kamar jira take ya rufe baki tayi saurin mika mashi naira hamsin din da ta gama nannadewa ...</div><div><br /></div><div> Amsa yayi ..yace me zaa sawo. ..</div><div><br /></div><div> Kwaki na talatin sae sukari na ashirin ...ta fada a hankali ..</div><div><br /></div><div> kai ya girgiza kana ya tafi. ..har yayi nisa ta kwala mashi kira...ya juyo. .tace ...Dan Allah kace a maka arha ..kuma kayi sauri kar kaka tace na dade ...</div><div><br /></div><div> Kai ya daga mata sannan ya tafi ..</div><div><br /></div><div> Baifi minti goma ba ya dawo rike da manyan ledoji. ..tana hangoshi ta tareshi tana dariya ...</div><div><br /></div><div> Duka ledojin ya mika mata ya juya ...tayi saurin janyo hannunsa ..to ka tsaya mana na duba inda canji ba sae ka bani ba ...ta fada tana bata rai ..</div><div><br /></div><div> Dariya ta bashi sossae ..ya dawo suka shiga zauren gidan ...</div><div><br /></div><div> Zama tayi kasa ta zazzage kayan tsaf ...ido ta waro lokacin da ta daga katon gwangwanin madara ..tace ...Nawa ka sayo wannan ...ta fada tana kallonsa ..</div><div><br /></div><div> Naira biyar ...ya ce idonsa yana kallon karamin bakinta ...</div><div><br /></div><div> Uhmm saura arba'in da biyar kenan ta fada ...biscuit ta cigaba da fitowa da chocolate sae ledar cos cos da sugar sae lemuka kala kala ...duk wanda ta daga sae ta tambayeshu kudinsa ...daga wanda zayace biyu biyar sae na biyar ....har ta fito da tiyar garin kwaki ...</div><div><br /></div><div> Wannan nawa yake? ...</div><div><br /></div><div> Kura mata ido yayi ..sannan yace ...wannan a shagon wani abokina ya bani su ...</div><div><br /></div><div> Dariya tayi kana ta maida kayan tana kallonsa ...to bani canjina ...ta fada lokacin da ta gama maida kayan ...</div><div><br /></div><div> Ido ya waro ...wane irin canji kuma?</div><div><br /></div><div> Harara ta balla mashi ...sha biyar mana. .ba yanzu mukayi lissafi ba naira Talatin da biyar ka kashe ...</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi ..ya lalubi ajihunsa ...babu ko naira 500 bare kananan canji. ..</div><div><br /></div><div> dubu daya ya mika mata ...ta make kafada ...ni canjina zaka bani ....ta fada a shagwabe </div><div><br /></div><div> Dukawa yayi dae dae tsawonta ....kiyi hakuri Meenatou ...banda canji...kinji. ki bari anjima zanyi canji sae na baki ....</div><div><br /></div><div> aa Ni dae ban yarda ba ....muje a canzo su ...ta fada. .</div><div><br /></div><div> To naji shiga da kayan sae ki fito muje. ...ya fada idonshi a lumshe ...</div><div><br /></div><div> Ka gudar man da canji ...tace </div><div><br /></div><div> Hannunta ya kamo ...baran gudu ba ....ya fada har lokacib idonshi a rufe ...</div><div><br /></div><div> Shiga gidan tayi tana waigenshi ...aje kayan tayi ta fito da gudu ...kaka nata kiranta. ..amma ce mata tayi ....Kaka Kawata ta mutu ake kiranmu muyi mata addua ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>Feedohm💞</div><div> </div><div>.</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI......</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>3 to 4</div><div><br /></div><div> </div><div> Suna fitowa daga zauren Gidan ...dae dae lokacin mota ke horn kofar gidansu ....da sauri ya kalli motar sannan ya kalli kofar get din ...babu alamun mai gadi zaya bude ....hannunsa ya zame ya nufi kofar zaya bude ...</div><div><br /></div><div> Ka tsaya wallahi duk wayonka bara ka gudar man da canji ba ...ta fada lokacin da ta bishi da gudu ...</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi a ranshi yace ...Meenatou kenan ....</div><div><br /></div><div> Gate din ya bude sannan ya matsa jiki. motar ...na ciki ya rage glass din dauke da faraa ...yace</div><div><br /></div><div> Ma'aruf ...ina mai gadin ne ...</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi wanda ya zame mashi dabi'a sannan yace ...wallahi ban san inda ya tafi ba ...amma ko ma meye na tabbata baya kusa. ...ya saka hannun ya bude motar ....</div><div><br /></div><div> Dae dae lokacin Meena ta iso gurin tana sheshsheka ....</div><div> </div><div> Hararanshi tayi ...sannan tace ..wallahi yau ko'ina zaka shiga sae ka bani canjina dan ba asi ta yayeni ba ...na gaji mutun sae wayau ..dama ranar nan na biyoka canjin Biyar baka bani ba to yau sae ka hada man da ita ...don na gaji da wahala. ..ta karasa maganar kamar zatayi kuka </div><div><br /></div><div> Mutumin yafito cikon motar dauke da murmushi ...ya dafa kanta yace ...Mamata canjin nawa zaa baki ? </div><div><br /></div><div> Dariya tayi kana tace ...Abba canjin sha biyar ne biyar din wancen satin dana biyoshi amma ya gudu wae bayya da canji .....Au na manta Abba Ina wuni...</div><div><br /></div><div> Dariya yayi yace ...dama mamana ina zaki tuna idonki ya rufe da kudi ...Ma'aruf bawa mamana canjinta....</div><div><br /></div><div> Murmushi ..yayi yace ..Wallahi Abba banda canji kuma kasan halin Meenatou ...</div><div><br /></div><div> Shima dariyar yayi yace ...Mamana bata da wani hali mara kyau ...mu shiga gida sae yasamo Maki Canjinki ko mama..nima na gaji da cinye maki kudi kullun ....</div><div><br /></div><div> Dariya ta sake tana kallon Ma'aruf din ...hannunta Abba ya kama suka shige ciki...</div><div><br /></div><div> Da Sauri ta karbe kayan da wata kyakykyawar mata ta fito dashi daga kitchen ...sake mata tayi tana murmushi ...</div><div><br /></div><div> Yau Mamanmu ce a gidan mu ...Ta fada tana dauke da murmushi. ..</div><div><br /></div><div> Meena tayi dariya sannan tace ...Eh man ae mai kamshine ya cinye man kudi naira ashirin har da ta rannan ...</div><div><br /></div><div> Dafe kanshi ma'aruf yayi ...sannan yayi sama da sauri yana fadar ..Wayyo Meenatou kamar na cinye maki Million bara dole na samo maki canjin ki yanzu. .</div><div><br /></div><div> Matar tayi dariya tace ...Sae kuwa ka biya mamanmu canjinta yau ....zo kici abinci kafin. ya samo maki ....</div><div><br /></div><div> Girgiza kai tayi tana murmushi...na koshi..</div><div><br /></div><div> Abba ne yace. .. ai kuwa na kusa batawa da ke mamana </div><div><br /></div><div> Da Sauri ta matsa kusa dashi ...Abba me nayi ...</div><div><br /></div><div> Matar ta tareta tace ...da bakicin abinci kullun a gidansu Mai kamshi ..</div><div><br /></div><div> Ido ta waro ...In ci abinci ku sayar dani ? </div><div><br /></div><div> waye zaya sayar dake ...inji Abba ..</div><div><br /></div><div> Ni dae ba ruwana ...ta fada sannan ta fara kwalawa Ma'aruf kira ...Matar ta nuna mata inda yake ...</div><div><br /></div><div> Ta kuwa shige dakin da sauri ...lokacin da kyar ya samo naira sha biyar ...ya mika mata ...sae da kyar ya samu ta karba shima da kashedin da ta gansho sae ya biyata ko kuma ta cire mashi agogo ...</div><div><br /></div><div> To kawae yace mata don so yake ta barshi da wannan masifar canji ....sae da ya hada mata da sweet sannan ta tafi tana mita..</div><div><br /></div><div> Bayan ta fita ya dafe kai. ..sannan ya kwanta saman gado...shi kanshi yasan yau duk inda ta ganshi sae ta nunashi tana binshi canji ...iska ya huro ...sannan yace ...yau ba abunda zaya saka na fita indae ban samo naira biyar ba ....idonshi na lumshe fuskar dauke da murmushi ...bacci ya daukeshi ..</div><div><br /></div><div> ••°°</div><div><br /></div><div> Kunnenta Kaka ta rike ...wane shegene ya kiraku kuyiwa gawa addua ...</div><div><br /></div><div> Ido ta waro ...wallahi Allah kaka wa ...</div><div><br /></div><div> Bakinta ta buge....rufe man baki ke yanzu ko dabbobin gidannan ai sun bar kama rantsuwarki ..</div><div><br /></div><div> Baki ta turo waje ...tana kefta idanuwa ...</div><div><br /></div><div> Ma'aruf kika bawa kudin ya sawo maki ko? ....ta tambayeta tana kallonta </div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm*💞.</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI......</div><div><br /></div><div> 💞 </div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>4 to 6</div><div><br /></div><div> Ido ta waro waje ...Hauka nake da zan bashi...ae in fada maki kaka wani shago naje mai saukin tsiya komae naso naira biyar suke sayowa ..su fa ko daga kasar Dandiyana suke siyo kayansu ...ta karashe maganar hakora bude ..</div><div><br /></div><div> Gwagwanin madara ta dago tace ..naira nawa kika sayo wannan ? ...</div><div><br /></div><div> Shiru tayi tana tunanin nawa ma Ma'aruf yace mata ...da sauri tace Naira biyar ...ta fada tare da nunota da hannu ...</div><div><br /></div><div> Kwafa tayi sannan ta fito da wata naira biyar din ta miko mata ...kije ki sayo man irinta karba. ..</div><div><br /></div><div> Babu tantama ta karba ta fice da gudu ...daga zaure ta tsaya tana hangen saman benen gidansu Maaruf ...ganin baya nan ya saka ta sake murmushin jin dadi tare da fadar ...Allah ya soni da yanzuma sae yaci zalina. ..ta nufi babban shagon dake unguwar ...</div><div><br /></div><div> Cikin saa tana zuwa taga gwangwan madarar jere ...ta washe baki sannan tace a miko mata ...aka saka mata a leda ...ta fito da naira biyar ta mika mashi ..</div><div><br /></div><div> Mai shagon ya karba yace mai zaa baki da wannan ...</div><div><br /></div><div> Rufe ido tayi sannan tace a hankali ..Mai kamshi Ma ya iya cuwa cuwa ashema har da canjina yace naira biyar to bara na koma ya jama kanshi sae ya fito man da kudina ...? </div><div><br /></div><div> Sanna ta nuna wani karamin sweet aka miko mata ...ta juya ...mai shagon yace ke kawo kudin madarar mana ..</div><div><br /></div><div> Wani kallo ta mashi sannan tace ..wanda na baka fa ..</div><div><br /></div><div> Yaushe kika bayar ...ya tambayeta ...</div><div><br /></div><div> Malan Dallah biyar din da nabaka fa ka miko man canjin alawa ko bashi kake bina ..</div><div><br /></div><div> Tsaki yaja ya fizge ledar sannan ya nuna mata hanyar fita ..fice ki bawa mutane guri ..sakaran banza ..Ubanwa ke sayar da katon Gwangwanin peak naira biyar ..fice dallah ...</div><div><br /></div><div> Kuka ta sake gurin ...wallahi ba inda zanje sai kun biyani kudina ai bani nace ka tambayeni me zaa bani da biyar din ba ...gashi ka saka na kashewa kaka kudi kuma ka hanani abunda na saya .kuma dazu anan aka sayeta naira biyar din ...ni sae ka bani kudina kuma wallahi baran sake siyan komae ba anan ...</div><div><br /></div><div> Cikin tsawa yace ...zaki fice ko sae naci ubanki anan ...kaga marar kunyar yarinya</div><div><br /></div><div> Tsaye tayi gurin taki wucewa sae da ya dauko bulala ya biyota a guje sannan ta wuce tana kuka .....</div><div><br /></div><div> Tana shiga dakin ta fada saman cinyar kaka tare da sake kukan da babu digon hawaye ko kadan a idonta ....</div><div><br /></div><div> Cikin kula tsohuwar tace....Me kuma ya faru Meenalle. ..</div><div><br /></div><div> Kafa ta fara haurawa tana fadin ...ba kudin da kika aikeni bane naje shagon da zan saya babu sae na fito wata akuya ta fizgesu daga hannuna ...</div><div><br /></div><div> Murmushi tsohuwar tayi ..duk da tasan karya take....kuma ta tabbata bara ta kashe kudin ba ..sae dae ko faduwa sukayi ...</div><div><br /></div><div> Ta shafi kanta ...to yi shiru mana Aminatuta ...dan akuya ta fizge biyar ba sae kiyi hakuri tunda kin san dae baran maki fada ba ...banda abunki nima na wuce irin akuyar data fizge naki ta fizge hannuna ...yi shiru Meenalle share hawayen mana ...</div><div><br /></div><div> Kin shirun tayi sae ma sabon salon turje turje da ta sake ta hambare duk inda taso ido rufe kuma ko hawaye babu ....</div><div><br /></div><div> Saukar tsintsiyar kwakwar da taji a kafarta ya saka ta bude idonta da sauri tare da kallon kafarta. ..ganin ledar garin kwakin Da Ma'aruf ya sayo mata ta fashe gashi duk ya zube a kasa ya saka ta gane bannar da tayi ....</div><div><br /></div><div> Lokaci guda ta tuno da zafin tsintsiyar kwakwar kaka ta zuba da gudu ta fice daga gidan ...</div><div><br /></div><div> Tana jin Kaka na kiranta amma bata tsaya ba ta fice daga gidan ...</div><div><br /></div><div>°°••</div><div><br /></div><div>Tulin kayan wankine jibge gaban Yar mashiyar budurwar da bata wuce shekara 17 ba ....ta saka hannu tana daga kayan a yatsine tana kauda fuska gefe ...</div><div>. </div><div> Wata mata ta fito daga wani karamin daki ...tace Haba luba kiyi sauri ki wanke mashi mana su zaya saka ...</div><div><br /></div><div> Yatsina fuska tayi tace ...ni gaskia innarmu baran iya wankewa baba wannan kayan ba ...kaya sae wari suke ...ga kudi a kai mashi wanki ....ta mike tsam ta shige daki ...</div><div><br /></div><div> Ficiciyar Sallamar Meena ne ya katse mata hanzari ...</div><div><br /></div><div> Matar ta kalleta da faraa ....Su Aminatu ne a gidanmu ...</div><div><br /></div><div> washe baki tayi tana fadin ....Eh Man inna ..fada mukayi da Kaka na taho nan ...Mamata tana ciki? .ta tambayeta. </div><div><br /></div><div> Tana ciki Aminatu.....</div><div><br /></div><div> Da gudu ta fada dakin tana kwalawa Mamanta kira ....ta zaune saman darduma tana addua ....ta juyo tana kallonta har ta karaso ...bata tsaya gurin mamar ba ta wuce gurin wani dan karamin tebur ta dauki ayaba ta saka baki tare da lumshe ido ....da sauri ta budesu tace ..mama karki ga na rufe ido ba fa ki dauka wani abu ..ni ba Mai kamshin unguwar mu ba.. nake kwaikwayo kawae nayine naga ko zai man kyau ...kinsan dazu sae da yaci man zalin biyar muka rabu ...shi wannan shegen taurin bashine dashi kamar babansu Luba .. ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*.</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>7 to 8</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Sallamar babansu luba ce ta katse mata sauran maganarta .....da sauri ta koma bayan mamarta....</div><div><br /></div><div> Ya shigo fuska daure ...Idonshi na kan Meena ...ya Nuna Nuna mamar da Hannu cikin daga murya yace ...Banda iskanci Rabi kina ji ina kwala maki kira kikayi shiru ...</div><div><br /></div><div> Dukar da kai tayi ...tace wallahi Malan banji ba kayi hakuri ...</div><div><br /></div><div> Yace ...baki ji gidan ubanwa ba ...sau nawa ina kiranki dan rashin mutunci har muryata ta dashe ..</div><div><br /></div><div> Meena tace. . .to tunda bata ji ba kuma ba shikenan ba . kai babansu Lubar nan ka cika masifa ...ko dan baka da ko sisine ? ....</div><div><br /></div><div> Mamar tayi saurin zaunar da ita tare da buge mata baki ....</div><div><br /></div><div> Girgiza kai yayi yana fadin ...owo Rabi har kin haifi diyar da zata fadawa mijinki magana ..to nima ina da yaron da zai mata dan banzan duka ....ya fice daga dakin</div><div>....Dafe kai tayi idonta cike da hawaye tace ...Nashiga Uku Aminatu waya ce ki zo gidannan ...ba na hanaki zuwa ba ...kinga yi maza ki fice ki koma gidan Kaka yanzun nan ....</div><div><br /></div><div> Ai kuwa da gudu ta fice dae dae zaune Musa( _babban dan Malan_)Ya shigo rike da wata doguwar bulala ..tayi saurin boyewa bayan kaure. ..yana shigewa gidan ta fice da gudu ta koma gidan Kaka .....</div><div><br /></div><div>••°°°••</div><div><br /></div><div> Wallahi Malan Kaka ce ta aikeni shi yasa na makara ...tafada tana daga hannu ...</div><div><br /></div><div> Babu Abunda Ya dameni da wadda ta aikeki ita bata san lokacin Islamiyya ba ...? </div><div><br /></div><div> Tace .. Lah Malan ai lokacinsu babu islamiyya ta tsofa ba ..</div><div><br /></div><div> Yace Aminatu Abubakar ki matso ba bugeki ki shiga aji ...don yau ba wani da uzurinki da zan karba .... </div><div><br /></div><div> Matsowa tayi ...yana daga bulalar ta matsa da sauri..hannu ya saka ya fizgota tare da zuba mata bulala a baya. ....wani tsalle tayi ta shiga cikin babbar rigarshi ta aza mashi cizo a kirji .....</div><div><br /></div><div> kokarin fiddota yake amma taki sakinshi ...da kyar ya samu ta fito lokacin ta sake mashi cizo yafi 5 .. shi kadae yasan azabar da yake ji ...idanuwansa sunyi jawur. ..yana ganin ta fito ya shige toilet din makarantar da sauri ya cire rigar ...duk inda ta cijeshi ta fasa shi ...wani karamin kwalla ya goge tare da yi mata Allah ya isa ...duk islamiyyar babu mai son dukan Meena saboda irin wannan abun shima yau tsautsayi yasa Headmaster yace yayi taren yan makara ...</div><div><br /></div><div> Sae da ya gama kananan kwallan shi sannan ya fito daga toilet ...Headmaster ya ganshi yace ...Ustaz Har ka gama dukan yan makaran ..</div><div><br /></div><div> Harara ya balla mashi ya wuce office abunshi ....daga cikin office din yana hango Meena nata wasanta ...Allah kadae yasan iya Allah ya isar da ya ja mata ...bai kuma fita ba har aka tashi ...</div><div><br /></div><div> ••°°°••</div><div><br /></div><div> Ganin motar gidansu Ma'aruf ta fito ya saka ta karasa gurin da sauri tana washe baki. ..</div><div><br /></div><div> Abba ta gani ciki ...yana ganinta ya sauke glass din ...ta gaidashi ...ya amsa mata cikin Faraa .</div><div><br /></div><div> Abba kaga Mai Kamshi har yau bai biyani bashina ba ...ta fada tana bata fuska ..</div><div><br /></div><div> Dariya yayi yace ...to ae mamana Mai kamshi baya lafiya. ..</div><div><br /></div><div> Ido ta waro ...me ya sami Maikamshina ? ta kareshe maganar kamar zatayi kuka. ..</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi ya fito daga motar tare da jan hannunta suka shiga gidan ...Mamanshi bata falo suka wuce dakinshi ....yana kwance yana bacci ...tana hangoshi ta janye hannunta daga Hannun Abba ta duka kusa da gadon da yake ...tana kallon fuskarshi ...fita Abbah yayi ...</div><div>Hannunsa ta damke tana kallon fuskarshi .sajen dake kwance a fuskar ta taba .....Mai kamshi ...ta fada a hankali ...</div><div><br /></div><div> Idonsa yana rufe amma ba bacci yake ba ....ta kara kiran sunanshi. ..ganin bai amsa ba ya saka ta sake mashi kara dae dae kunnenshi ...</div><div><br /></div><div> Da sauri ya bude idon yaji karar har cikin kanshi ...dariya ta sake ...sannan ta shafi wuyanshi ...saurin dauke hannunta tayi tana kallonshi shima ita yake kallo ..</div><div><br /></div><div> Mai kamshi jikinka Zafi ..ta fada kamar zatayi kuka ..</div><div><br /></div><div> Daga mata kai yayi tare da lumshe ido ...itama idon ta lumshe sannan tace. ..Amma mai kamshi wannan ciwon naka har da taurin bashi ke kara mashi yawa ...</div><div><br /></div><div> Dariya ta bashi yayi saurin janyo drawer dake jikin gadon ya fito da sabuwar naira biyar ya daura mata a hannu ...</div><div><br /></div><div> Baki ta washe tace. ..ka gani ko Mai kamshi yanzu ko mutuwa kayi babu bashin kowa akanka ...lokacin guda idanunta suka ciko da kwalla tace ...kuma ko bana so ka mutu Mai kamshina ...ta fada lokacin kwallar ya gangaro kumatunta ...</div><div><br /></div><div> </div><div>*Feedohm*💞</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI.....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>9 to 10</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Zaune ya tashi tare da janyota ya zaunar da ita bisa cinyarshi ya share mata hawayen </div><div><br /></div><div> Yace ...ai mutuwa dole ce Meenatou ..</div><div><br /></div><div> Girgiza mashi kai tayi ..aa ni bana so ka mutu ...</div><div><br /></div><div> Shafa kanta yayi yace ...to kiyi addua meenatou Allah ya bamu tsawon kwana kinji ko ...Na furta maki Sirrin Zuci ...mai dadin saurare...</div><div><br /></div><div> Film din dake kunne a dakin ta maida hankali gareshi .....zuwa can ta mike tana washe baki ...tace Mai kamshi kaci abinci ...</div><div><br /></div><div> Film din ya kalla shima ciki wata budurwace take bawa saurayinta abinci abaki ...murmushi ya sake ya girgiza mata kai alamar aa ...</div><div><br /></div><div> Ta fice ...zuwa can sae gata da abinci cikin Plate ya kalleta da mamaki yace ...ina kika samo ...</div><div><br /></div><div> Baki ta washe gurin Mamanku naje nace zaka ci abinci ta bani ...</div><div><br /></div><div> Zama tayi saman cinyarshi ...tare da debo abincin a spoon ta mika mashi ...ahankali yace ..bana cin abinci da spoon sae da hannu Meenatou</div><div>Ido ta waro ..Kai mai kamshi dazu dana zo cizon malan na taba hammatarshi kuma wari take ....</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi ya bude ...wani abu ya tokare mashi makoshi baya kaunar Meenatou ta taba wani namiji duk da tana karama ....</div><div><br /></div><div> Shiga toilet ki wanke hannun ki fito ...ya fada a hankali ...</div><div><br /></div><div> Sae da ta bashi abinci sannan ta fice ...ya bita da kallon ....gida ta koma ta sakewa Kaka kusa sae tazo ta gaido mai kamshinta baya da lafiya ...</div><div><br /></div><div> Da farko kaka cewa tayi bara tazo ba amma da taga masifar ba mai karewa bace ta ziro Hijab ta biyota ...</div><div><br /></div><div> Mamar Ma'aruf taji dadi sossae sanna ta kara son Meena a ranta ...haka shima Ma'aruf murmushi kadae yake yi tare da lumshr ido har suka tafi ....</div><div><br /></div><div> Kasancewar an koma Boko kullun kafin ta tafi makaranta sae ta shiga ta ganshi ...ta bashi abinci .. sannan take wucewa haka idan ta dawo sae ta shiga ta bashi abinci ko da kuwa zata dade bata dawo ba to zaya jirata ....Abincin Rana tare suke ci ...tana bashi tana ci ...amma da anzo gurin nama nanne zancen zai canza salo ...don sae taci Yanka 4 kafin ta bashi guda ...idan kuma kazane to sae ta cinye tsokar sannan tace ya gashi ya cinye ...sae dae kawae yayi murmushi. yace ya koshi. ..haka zata sake mashi kuka sae yaci ...hakanan zaya danci abinda zai iya ya bar sauran kashin ...Har Allah ya bashi lafiya ....</div><div><br /></div><div>••°°</div><div><br /></div><div> Kaka nidae wallahi wannan wanke wanke wanken yayi man yawa ...ta fada cike da shagwaba ...</div><div><br /></div><div> harara ta dalla mata ...sae ki nemi wanda zaya tayaki ...</div><div><br /></div><div> Sallamar Ma'aruf ce ..yasa ta sake Murmushi tana cewa ...Yauwa Maikamshi zoka tayani mu gama na fada maka wata magana</div><div>Kaka tace ..bara ya tayaki ba dan kaniyarki ....Ma'aruf ko za zauna ka kyaleta ...ta shimfida mashi tabarma ..</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi yace ...barta na tayata Kaka naga kayan sun mata yawa ita kadae. ..</div><div><br /></div><div> baki ta washe ...Yauwa mai kamshina ..kayi wanke wanke sae in maka dauraya nafi iya dauraya kai kuma kafi iya wanke wanke ...</div><div><br /></div><div> Yana wankewa tana daurayewa har suka gama ..kaka na kallonsu cike da fata kala kala aranta ....</div><div><br /></div><div> Bisa tabarmar ya koma ya zauna ...zonan Meenatou ...ya fada a hankali. ..</div><div><br /></div><div> Kusa dashi ta koma ta zauna ta harde kafa tana kallonshi ....</div><div><br /></div><div> Wani karamin zobe na gold ya fito daga cikin jikkanshi ...ya zura mata a hannu ...</div><div><br /></div><div> Kallon zoben take ..tana kallonshi ..ni ka sawo mawa ? </div><div><br /></div><div> Daga mata kai yayi ...ta kare washe baki tace .... don kar na fadawa kaka kace idan aikeni na dinga karbowa kyauta a shago ...</div><div><br /></div><div> Ido ya lumshe sannan yace aa ...kinsan Zuciya ? </div><div><br /></div><div> Lallae ma Mai Kamshi tun muna primary one muka ganin zuciya ....</div><div><br /></div><div> Yace Good ...to ki aje wannan itace zuciyata ...</div><div><br /></div><div> Dariya take har da kwalla ...kai kuma wannan itace zuciyarka ...to nima bara na baka taea zuciyar ...ta kwance dankwalinta ta zare ribbon din dake kanta ta mika mashi ...</div><div><br /></div><div> Amsa yayi yana daga shi ...sannan yace na meye wannan ...</div><div><br /></div><div> Hararanshi tayi sannan ta saka hannu zata fizge ....to bani abuna tunda baka so ...</div><div><br /></div><div> Aa sorry Meenatou ina so mana ...wannan shine zuciyarki ? </div><div><br /></div><div> Eh man mamana ta bani shi da sallah ...ina sonshi ...</div><div><br /></div><div> cikin jikkarshi ya saka sannan ya mike ya ma kaka bankwana ya wuce ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div> *Feedohm💞*</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI.....</div><div> </div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>11 to 12</div><div><br /></div><div> </div><div> Wani karamin yarone ya shigo office din headmaster yana kuka rike da ya gaggen littafi ...</div><div><br /></div><div> Ustaz ya kalleshi Yace..me ya faru kake wa mutane kuka...</div><div><br /></div><div> Yaron yace .Meena ce ta yaga man littafi ...</div><div><br /></div><div> Wani wahallalen miyau ya hade tare da shafa kirjinsa ...sannan yace ...Jeka Allah ya saka maka ...ya juya yaci gaba da duba lttafin dake gabanshi ...</div><div><br /></div><div> Wani sabon malamin da bai dade da zuwa ba ya kalli Ustaz yace ..Haba ustaz wane irin Allah ya saka mashi ...ya nuna yaron tare da fadin ..jeka kirata. . </div><div><br /></div><div> Bai fi minti biyu ba ta shigo da uwar sallama. ...Sabon malamin ya ce ta rage tsawonta ...</div><div><br /></div><div> Zama tayi tsakar office din ta mike kafa ....tsawa ya daka mata. ..babu shiri ta yi kneeldown din ...Kallon Ustaz tayi tace ...Ustaz Dan Allah kayi hakuri shi ya fara daukar man goriba ya cinye ..</div><div><br /></div><div> Da sauri Ustaz ya juyo yace. .Meena Abubakar bani na kiraki ....ya kakkabe riga ya fice daga office din ...</div><div>Sabon malamin ya bata punishment din wanki toilet din makarantar duka tare da share ko wane glass. ...tana kuka ta gama ko aji bata koma ba ta wuce gida ...</div><div><br /></div><div> Sae da ta bari lokacin tashin malamae yayi saboda suna tsayawa meeting kullun ...lokacin mangrib tayi kowa na sauri yaje masallaci sannan ta nufi hanyar islamiyya. ....tun kafin ta isa ta cika jikkarta da duwatsu ...</div><div><br /></div><div> Wani lungu mai duhu ta samu ta shige wanda ta san dole tanan sabon malamin zaya wuce ...Cikin saa sae gashi ya taho kanshi na kasa yana tafiya ....katon dutse ta samu ta saita keyarshi ta jefa mashi ....dafe gurin yayi ya juyo yace ...Uban waye ke yo jifa ...bai rufe baki ba ya kara jin wata a goshinsa har sae da jini ya zubo ....</div><div><br /></div><div> Tana ganin ya dafe gurin da sauri ta fito daga maboyarta ta kukan kura tayi ta shige cikin rigarshi ...rudashi tayi ta dinga sake mashi cizo tare da yakushi ta ko ina ...</div><div><br /></div><div> Da kyar ya samu ya babbareta ...tare da zubawa da gudu ...don duk tunaninshi aljanace ....</div><div><br /></div><div>••°°°</div><div><br /></div><div> Ustaz ya kalleshi cike da tausayi yace ...Malan isiya sae naji headmaster yace ka samu hadari jiya a hanyarka ta komawa ...</div><div><br /></div><div> Sosa kai yayi yace ...wallahi kuwa Ustaz ina saman mashin wani mai mota ya bangajemu ...</div><div><br /></div><div> Meena dake tsaye ta kalli ustaz tace. .Malan meye hukuncin mai karya...</div><div><br /></div><div> Dan wuta ...ya bata amsa don yanzu tsoronta yake ji ...</div><div><br /></div><div> to Malan isiya ma dan wutane ...jiya gabana akayi ...wata aljanace ta rotsa mashi cizo sannan ta shige a rigarshi ta yakusheshe ta ruga ...</div><div><br /></div><div> Wata dariya Ustaz yake har da dafe cikin sannan ya kalli malan isiya da sae yanzu ya gane wannan shegiyar yarinyar ce ta masa rashin mutunci ...</div><div><br /></div><div> Ustaz yace. ...Malan da mai motar ya bugeku sae ka fada kan aljanar ? </div><div><br /></div><div> Shiru yayi ...yana nan tsaye kuma duk yaron da yazo wucewa to Meena zata tareshi ta bashi labarin malan yayi karya yace hadari yayi alhalin aljana ce ta shige rigarshi ta yakusheshi ...wani ma har yadda aljanar tayi masa take nuna masu da bango .... yana tsaye da uwar palasta a goshi ...cikin dubara ya sulale ya fice daga islamiyya....Tun daga lokacin malan isiya bai kuma dawowa ba ...</div><div><br /></div><div>••°°°•• </div><div><br /></div><div> Mai kamshi ina irin wannan alawar daka sawo man jiya ...ka tunata ...ta fada rike da hannunshi tana murmushi ...</div><div><br /></div><div> Daga mata kai yayi ...na tunata ..</div><div><br /></div><div> Yauwa to ita zaka kara sawo man ...ta mika mashi wata rabin naira biyar ...</div><div><br /></div><div> Dan Hararanta yayi ...waye zaya amshi wannan rabin kudin ?</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*.</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI......</div><div> </div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>13 to 14</div><div><br /></div><div> </div><div> Hararansa tayi ...Kai baka san yarda ake cuwa ba ...ai murdeta zakayi ka mika masu da sun baka sae ka rugo da gudu. ..</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi yace. ..Idan Allah ya kamani fa ..</div><div><br /></div><div> Washe baki tayi tace ...ai zan maka addua ya yafe maka tunda yana saurin amsar adduar mu ...</div><div><br /></div><div> To kawae yace mata ya juya ya koma cikin motarshi ya fice daga unguwar ...har ta bar ganinshi tana daga mashi hannu ...nan ta zauna tana zanenta a kasa. ...sae da tayi budu budu da kasa sannan ta koma gida ....</div><div><br /></div><div> Tana shiga kaka tace sae tayi wanka....rantsuwa ta hauyi wae mamarsu Ma'aruf ta mata wanka daga gidansu take ....kaka tace bata yarda ba. ....</div><div><br /></div><div> Turo baki tayi tace ...ni wallahi na gaji da wannan cacar kullun wanka ...</div><div>Kaka ta rike baki tace. ..yanzu dan kaniyarki Meenalle wankan ne wahala ....to ai kuwa indae kina nan gidan ki dinga irin wannan wahalar ..tashi tun kafin na taso ...</div><div><br /></div><div> Mikewa tayi ta nufi hanyar zaure tana amsa sallamar karya ...Girgiza kai kakar tayi tare da fadin Allah ya shiryaki Meenalle ....Zaure ta ci zamanta har sae da kaka ta fara gyangyadi sannan ta dawo ta kwanta kusa da ita ...</div><div><br /></div><div> ••°°°••</div><div><br /></div><div>Kai ta daga tana kallon benen gidansu Ma'aruf sannan ta fito tana tafiya tana kallon gidan ko zaya fito ya bata sakonta ....har ta bar unguwar bata ga kowa ba .....Ledar dake hannunta ta saka hannu ta fito da biscuit daya ta fasa ta ci rabi ta maida rabi ta kulle ...</div><div><br /></div><div> A bakin kofa ta tarad da Malan Musa mijin mamarta zaune ya kallon masu wucewa ....gaidashi tayi yaki amsawa. ..har ta shiga zauren ta dawo baya ta tsaya gabanshi ...</div><div><br /></div><div> Angon mamarmu ina wuni _Kamar yadda taji wasu mutane na kiranshi da can baya_...ta sake gaidashi ..</div><div><br /></div><div> Ko inda take bai kalla ba ...ta sake cewa ..kodae mamansu Luba ta ci maka Uwa shi yasa ka dawo nan ka zauna ...ta kefta ido daya ...</div><div><br /></div><div> Cakumota yayi ya hade da dakalin da yake zaune ...Uban me kikace ....ya fada da karfi. .</div><div><br /></div><div> Wani mutumin dake zaune nesa dashi ya taso ya amsheta tare da bashi hakuri sannan ya jashi suka tafi kasuwa dan gudun abunda zaya je ya dawo ...</div><div><br /></div><div> Miyan wahala ta hade sannan ta ida shiga cikin gidan ....</div><div><br /></div><div> Musa Ustaz ....ta fada lokacin da taga musan zaune tsakar gida daga shi sae gajeren wando ..kusa da Luba </div><div><br /></div><div> Harara ya banka mata tare da yin kwafa ....</div><div><br /></div><div> Kara cewa tayi ...su musa da luba ba magana. ..kunyi zaune kamar turmi ...</div><div><br /></div><div> Zanci Ubanki Meena ...Luba ta fada tare da tasowa ...dakin mamarta ta fada da gudu ...amma bata tsira ba sae da ta biyota ta mata zagin uwa da uba sannan ta fice ...</div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Meena dan Allah ki rufa man asiri kizo ki koma gidan kaka wallahi bazan iya da masifarki ba ...ke kamar jaka kowa ya bugeki amma bara ki natsu ba ...dan Allah ki zo ki shirya ki tafi ....Mamarta ta fada idonta taf da hawaye ..</div><div><br /></div><div> Ni Ba inda zan koma wallahi ..ai gidan ma bana baban Luba bane ashe na bakine ...ta turo baki ..</div><div><br /></div><div> Waya fada maki nawane Meena ki rufa man asiri. ....</div><div><br /></div><div> Shiru tayi taci gaba da baccin karya. .. .</div><div><br /></div><div> Can kuma ta mike kamar an tsikareta tare da kallon mamarta sannan tace ....ni mama waye babana ? .....</div><div><br /></div><div> Kallonta take sannan ta dauke kanta gefe guda tace ...tashi kije kiyi wanka kizo ki koma gidan kaka ....</div><div><br /></div><div> ••°°•••</div><div><br /></div><div> Tsaye yake ya harde hannuwanshi kofa gidansu Meena ya kurawa ido kamar yana kirga kasar gurin ...</div><div><br /></div><div> wayarshi tayi kara ya duba message ne ya shigo ...da sauri ya buda sannan ya sauko tare da daukar keys din motar ya fice daga gidan ....</div><div><br /></div><div> </div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI......</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div> 15 to 16</div><div><br /></div><div> </div><div> Office dinsu ya nufa ...yana zuwa aka bashi takardar tafiya karo karatu kasar indiya nan da wata biyu ake so ya tafi ...Course din na shekara 5 ne suna so ya zama cikkaken Pilot ....Karba yayi yakoma gida ...dama Abba ya dade yana nemar mashi sae akace sae gurin aikinshi sun saka mashi hannu ...sae yau ya takardar ta fito suka saka hannu ....Mamarsa ya bawa takardar sannan ya kara fita da sauri ....</div><div><br /></div><div> Meenatou. ..ya kirata ahankali ...</div><div><br /></div><div> Ta juyo cike da masifa tace ...kai me yasa ka cika cin zali na ...tun yaushe nake nemanka ka bani kudina shine ka boye dan kasan ka kashe man kudi ko</div><div>Dafe kanshi yayi tare da lumshe ido sannan yace ...Meenatou na nemeki bakyanan ..</div><div><br /></div><div> Baki ta bude tana kallonshi sannan tace ..ni dae bani kudina ..ta mika mashi hannu ..</div><div><br /></div><div> shiru yayi yasan ko ya bata kudin dake jikinshi bara ta amsa ba ...dan naira dari biyarce karama ciki ...a hankali yace ...banda canji bara na shiga gida na dauko maki ...</div><div><br /></div><div> Gefen rigarshi ta tace ...sae dae mu tafi a haka karka kuma guduwa ....</div><div><br /></div><div> Meenatou haka zaki rikeni kamar kin kamo barawo ..please ki sakeni kinji ..</div><div><br /></div><div> ta daure Fuska Allah mai kamshi idan kaga na sakeka to ka bani kudina ...</div><div><br /></div><div> Kaka ta leko tana mata dakuwa. ..Meenalle uwaki nace ...zaki sakeshi ko sae na fito ...</div><div><br /></div><div> kafa ta fara bugawa tana fadin ...kaka kudina fa ya cinye kusan sati guda ...ganin tsohuwar ta fito ya saka ta sake mashi riga tare da fashe da kuka ta zauna gurin ...</div><div><br /></div><div> Daukarta yayi da hannu yana bawa kaka hakuri ...ce mashi tayi ya sauketa kasa amma yayi murmushi ya shige da ita gida</div><div><br /></div><div> Falo ya zaunar da ita yana lallashi sannan ya dauko mata rabin biyar dinta ..dama tana aje saman mirrow ..ya bata tare da sweet din ....Haka Mamanshi ta shigo ta isketa tayi bacci saman kirjinsa ta wuce tana kallonsu ....</div><div><br /></div><div> ko motsin kirki kasa yi yayi gudun kar ya tayar da ita ...sae da ta dade tana bacci shi kuma yana kallonta sannan ta tashi .....gida ya rakata sannan ya bawa Kaka hakurin karta dake ta sannan ya fice ...</div><div><br /></div><div>*Meena*</div><div><br /></div><div>Diyace tilo ga alhaji Abubakar mai zinari </div><div>..wani hamshakin mai kudine a cikin garin kaduna ...Sunyi aure da Rabi'at..Auren soyayya ...ko shekara basu datse ba Allah ya albarkacesu da Meenatou ...Mahaifinta yana mutuwar sonta amma matsakar uwar Alhaji Abubakar bata san danta ya haifi diya mace don tace dawainiyace da wahala haihuwar mace ...Tunda Rabi ta haifi Meena zaman gidan Alhaji Abubakar ya zame mata zaman makoki ...kullun mahaifiyarshi tana gidan ...wulakancin yau daban na jibi daban ...har Meena takai wata Takwas. ..sae Uwar Alhaji Abubakar ta kawo wata diyar kawarta tace sae ya aureta ....sannan ya saki mahaifiyar meena ko ta tsine mashi ...suna kuka suka rabu ...Sannan mahafiyarshi tace ko bayan ranta kar ya neme su idan kuma ya nemesu bata yafe mashi ba .....</div><div><br /></div><div> Da dan kudin da ta samu ta gina gida ta ginawa mahaifiyarta kaka itama karamin gida ...gida daya suka fara zama da kaka tana rainon diyarta ...</div><div><br /></div><div> Meena nada shekara 5 Malan Sani ya fito yace zaya aureta ....lokacin yanada rufin asiri dae dae gwargwado ..sannan yana da mata daya mai suna Saratu ..itace mahaifiyar su Luba da Musa ....</div><div><br /></div><div> Ta aureshi ashe bata sani ba dan cacane ...dan haka duk abunda ya mallaka sae da ya kare gurin caca ...harta gidan da suke zaune sae da ya sayar ..sannan ya roketa suka dawo karamin gidan da ta mallaka ...ita da mamansu luba kuwa ...kowane yana daraja dan uwanshi ...matsalar tana gurinsu luba da Musa ...ko kadan basu da tarbiyya wanda sak halin Malan Sani ya biyo ...da yake rabi macace mai hakuri bata taba gayawa wani mutun cewa ga zaman da take gidan mijinta sannan bata nunawa kowa gidanta suke zaune ba ..da farko auren ya yarda Meenalle ta zauna gidanshi amma daga baya sae yace sae dae ta koma gidan ubanta ..haka ta mayar da Meenalle gidan kaka....lokacin da Meenalle tace mata gidantane tayi mamaki sossae dan bata san wanda ya fada mata ba ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm*💞</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div> 17 to 18</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Mai kamshi wae ina kake samun kudin da kake rabawa mutane ....</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi yace ...Allah ke bani meenatou</div><div><br /></div><div>Dariya ta sake tare da tarba hannu sama tace. ..Allah ka bani kudi irin na Uncle Ma'aruf nima na dinga bawa mutane ...</div><div><br /></div><div> Kallonta yayi tare da fadin Uncle Ma'aruf a hankali ...</div><div><br /></div><div> Da Sauri ta kalleshi tace ..Mai kamshi kaji nace maka Uncle Ma'aruf ko ..haba nima yanzu na zama baby ...ina Musan gidansu Luba ..ka ganeshi? </div><div><br /></div><div> Uhm yace mata duk da bai sanshi ba ...</div><div><br /></div><div> Ta wash baki tace ...to shi naji yana cewa I love dinshi ta gaida mashi Uncle ..kila ko babanta yake nufi ko kuma i love you dinta itama ...uhm ohon mashi dae shima dae ya sani ...kuma yake ce mata I Kiss me wallahi ...in gaya maka Mai kamshi kamar a film dinnan daka kunna man rannan ....Ni kuma naga duniya ba kullun ake kwana gado ba. ...kasan ko jiya kaka kasa ta saukeni na kwana </div><div> </div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi tare da mikewa tsaye yace. . Meenatou tashi kije kiyi sallah ...</div><div><br /></div><div> Miyau ta hade sannan tace ..ni bana Sallah yau ..</div><div><br /></div><div> Ido ya waro gwanin shaawa yace ..Me yasa bara kiyi sallah ba Meenatou ...</div><div><br /></div><div> Sae da tayi dariya sannan tace ...yo malamarmu ta boko naji rannan tace wa kawarta wae bata yin Sallah nima kuma naga da kadan ta fini tsawo ...shi yasa nima nace banayi ..</div><div><br /></div><div> Tunda Take magana yake kallonta har sae da diga aya sannan yaja numfashi a hankali ..ya wuceta ...</div><div><br /></div><div> Hannunsa ta kama tare da rike kunne...Mai kamshi zanje nayi kaji? ..</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi tare da shafar gefen fuskarta yace ...Yauwa Meenatou ta ..kije kiyi zanzo na tambayi kaka ki rakani unguwa ...</div><div><br /></div><div> Wani uban tsalle da daka tare da rungumeshi cikin sabo ta dankara mashi cizo a hannu ...</div><div><br /></div><div> Da Sauri ta janye bakinta lokacin da ta lura da cizon da ta sake mashi</div><div>Idanuwanta suka kawo ruwa ta duka gabanshi tare da kallon kasa ....</div><div><br /></div><div> Meenatou ...ya kira sunanta a hankali ...ganin bata dago ba ya saka ya duka shima tare da dago kanta da hannunsa ..hawaye ya gani bisa fuskarta ...murmushi yayi sannan ya share mata hawayen ...</div><div><br /></div><div> Hannunta ta daura saman lebenshi tana kallon fuskarshi ...lumshe ido yayi tare da zura hannun cikin bakinshi ...kadan ya hade hakoranshi da hannunta ....ga mamakinshi sai ji yayi ta sake mashi ihu tare da murginawa kasa tana fadi ..</div><div><br /></div><div> Wallahi sae na rama ai ni ba da karfi na cijeka ba ....</div><div><br /></div><div> Dariya yake sossae sannan ya mika mata hannu yace ...Rama Meenatou ...babu kunya ta murje idonta ta dana mashi cizo sannan ta mike tana dariya ta shige gida .....</div><div>Dariya yayi ya shige masallacin kofar gidansu ....daya fito sae da ya shiga gida yayi wanka ya saka blue din shirt data fito da zaharin kyanshi tare da bakin jeans ...ya fito sae kamshi yake ...</div><div><br /></div><div> Daga zauren gidansu taji kamshinshi ta sake ihu tana kewaye zatayi wanka tana fadi ...naji kamshin mai kamshi bara na fito ...</div><div><br /></div><div> Ruwa ta shafawa kafafuwanta tare da wuyanta da hannunta sannan ta zubar da ruwan ta dauro zani ta fito ...</div><div><br /></div><div> Tsakar gida ta tarad dashi suna zaune da kaka suna fira. ..</div><div><br /></div><div> Kaka ta bita da kallon tuhuma. .nan da nan ta hau rawar sanyin karya tana fadin. ..kaka ruwan sanyi....dakyar na watsawa bayana don hannuna rawa yayi tayi. ..</div><div><br /></div><div> Aa Meenalle. ...kya ma fadi gaskia dan kaniyarki ..muje dakin ki gwada man bayan naki ...</div><div><br /></div><div> Bata fuska tayi tace ..na fara nonuwa fa ...</div><div><br /></div><div> tashi tayi ta bita da fada daki da gudu ....</div><div><br /></div><div> Ma'aruf da kusan suman zaune yayi ...bashi yayi magana ba amma kunya ta rufeshi ....da kyar ya iya tambayar kaka meena zata rakashi gidan mamarta ya gaida ta ...</div><div><br /></div><div> Taji dadi sossae tace ..ba komae Ma'aruf ko da duniyar zaka bari da Meenalle wallahi na yarje maka bara ka taba cutar da Meenalle ba ...ina fatan Allah ya nuna man girman Meenalle na nuna mata mijin da babu kamarshi a duniyarnan Ma'aruf...</div><div><br /></div><div> Dukar da kai yayi cike da kunya ....Meena ta fito taci uban jan janbaki duk fuskarnan duk tasha digon baki sae washe baki tayi ....</div><div>suna hada ido suka lumshe ido tare ...tayi saurin bude idon tare da warosu ...Mai Kamshi ? ...ta fada da karfi ...bafa kai nake kwaikwayo ba hakanan nayi abuna ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI...... </div><div> </div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>19 to 20</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div> A mota ta isheshi da surutu duk surutun akan babansu luba ya kare tana fada mashi shima babansu luba taurin bashine dashi ..wae idan ya karbi kudin mutane dakin mamarta yake boyewa. da anzo kiranshi sae dae yayi karya yace baya nan ...</div><div><br /></div><div> Har sae da taga an tsaya kusa da wata katuwar plaza a jiki an rubuta MIMA Plaza ...parking yayi ya fita ya zagayo ya bude mata. ...murmushi yayi tare da jan hannunta ....</div><div><br /></div><div> Kaya sossae taga ya jida sannan aka biyoshi dasu a baya ...sannan tun da suka shiga taga kowa yana bashi girma kuma bai biya kudi ba ...kasa hakuri tayi ta kalleshi tace ...</div><div><br /></div><div> amma Mai kamshi kai babban barawone..</div><div> ....</div><div><br /></div><div> Kallonta yayi ya tada mota sannan yace ..da nayi me kenan Meenatou ...</div><div><br /></div><div> Uhmm banda sata zaka shiga shago ka debo kaya ka fito bakq basu kudi ba ...ko bashi suka ba ...</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi yace ...eh bashi suka bani ...</div><div>Uhmm Allah to ya fito masu da kudinsu ...nima da kyar kake biyana bare wasu ..uhmm .. ta tabe baki ...</div><div><br /></div><div> Idan ban biyasu ba ai sun zo su kamaki don dake nayi kwatance .....ya fada hankalinshi naga titi ..</div><div><br /></div><div> Dadinta ma nasan gidanku sae in kaisu ka biyasu ....</div><div><br /></div><div> Dae dae gidansu Mamarta taga ya tsaya ta budeshi. ...mai kamshi ba dae labarin da na baka na babansu luba ba kazo zaka fada mashi ..</div><div><br /></div><div> Hararanta yayi ...yace ...kinsan baki so a fada mashi kuma kike fadawa mutane ..</div><div><br /></div><div> Dan Allah kayi hakuri mai kamshi wallahi rannan ma da kyar wani ya kwaceni gurinki. .kuma ma kai kadae na fada mawa da yan ajinmu ...</div><div><br /></div><div> Ki fito muje mana ...ya fice daga motar ...da sauri ta biyoshi tana rantsuwar bara ta kara bawa wani labari ba ....data isheshi yace mata ba za gaya mashi ba ...sannan ta kyaleshi ...sun gaida sossae da Mamarta sannan ya aje masu kayan da ya siyo masu ya tashi ...taji dadi sossae tare da godiya don dama tuni ta san shi ...</div><div><br /></div><div> °°••°° </div><div><br /></div><div> Kaka jiya kinsan me ya faru</div><div>....</div><div><br /></div><div> ya zaayi na sani Meenalle ....</div><div><br /></div><div> Uhm kema fa kar na baki labari kizo kici amanata yarda mai kamshi yaman gidansu mama ....ta fada a hankali ...</div><div><br /></div><div> Dariya tayi tace ...indae kinsan gulmar mutanece karki fada man nima amanarki zanci ...</div><div><br /></div><div> Shiru tayi ...zuwa can ta kasa hakuri tace ...Kaka babansu Luba fa dan iskane ! ..</div><div><br /></div><div> Meenalle kaniyarki nace ..tashi ki wuce ki bani guri ....sae ki saka a daure mutun yana gani ....</div><div><br /></div><div> ••°°••</div><div><br /></div><div>*Two month*</div><div><br /></div><div> Shiru tayi tana kallonshi ...a hankali tace Maikamshi ...</div><div><br /></div><div> Yaakae Meenatou ...ya fada idonshi na kallonta ..</div><div><br /></div><div> Zaka manta dani? ...</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi tare da dawo kusa da ita...Zuciyarshi ya nuna da hannu ...tare da lumshe Ido...kina nan ciki Meenatou ....ya furta a hankali</div><div>Zuciyarshi ta dafa tare da daura kanta a bisa tafi minti goma Sannan ta janye tana kallonshi ...idanuwanta suka ciko da kwalla ...tace ..Mai kamshi Ka dawo da wuri na dinga ganinka.. ...</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi ...zan dawo Meenatou amma kiyi alkawarin nima zaki sakani a taki zuciyar ...</div><div><br /></div><div> Da sauri ta janyo hannushi ta tura a rigarta ..tana fadin. ..taba kaji Mai kamshi akwaeka ciki Allah. ..da karfi zuciyarta ke bugawa ....janye hannushi yayi daga jikinta ya mike tsaye ....Tashi muje Abba na jirana a mota ...</div><div><br /></div><div> Hannunshi ta rike yana janye da ita ....har harabar gidan ...nan ne ta sake sabon kuka sae ya tafi da ita ...da kyar kaka ta cireta daga jikinshi ...shima idonshi ya kada yayi jawur .....</div><div><br /></div><div> Mamarshi ta dauketa ta dinga lallashinta ranar nan gidan ta kwana ...sae da daddare Tayi shiru lokacin Ma'aruf ya kira waya ...kuka ta sake mashi sae ya dawo ...lallashinta yayi sossae ...wayar na kunnenta tana kwance jikin Mamarshi bacci ya dauketa ...daga cikin wayar yake jiyo saukar numfashinta lumshe ido yayi ...sannan yaki kashe wayar ya daurata a kirjinsa..yana sauke numfashi ...ganin tayi bacci ya saka mamarshi ta zare wayar ...gani tayi har lokacin wayar na kunne .. wayar ta kanga a kunnenta tana jiyo bugun zuciyarshi ...Shafa kanta tayi tare da sumbatar kanta sanna ta maida mata wayar a kirjinta ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI...... </div><div><br /></div><div> 💞 </div><div><br /></div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞 </div><div><br /></div><div><br /></div><div>21 to 22</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div> Haka rayuwa ta cigaba da tafiya kullun da safe Ma'aruf zaya kira Mama AWaya ...haka itama Meena tana gama shirin makaranta zata shiga gidan ...bara ta fito ba har sae ya kira sunyi magana ...kullun idan suna wayar tambaya dayace yaushe zaya dawo ....sae dae yace maka nan ba da dadewa ....wata irin shakuwa ta kara shiga tsakaninsu ....haka Mama na kokarin ganin ta taimakawa da kaka da komae na bukata ...</div><div><br /></div><div> wani lokacin idan ya kira da daddare anan gidan take kwana rungume da wayar... </div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°•• </div><div><br /></div><div><br /></div><div> Gab da zasu gama primary lokacin Meena ta gama fadawa kaf yan makarantarsu cewa gidan mamanta babansu luba ke zaune ...duk inda ta zauna bata da labari sae na babansu luba....sannu sannu magana ta koma kunnenshi ....ranar sae da yayiwa Rabi wulakanci sossae dan har cewa yayi zaya daketa ...da kyar maman su luba ta shiga tsakani .. </div><div><br /></div><div><br /></div><div> Abokan cacarshi ya fadawa mawa wasu suka bashi shawarar indae yana so ya zauna cikin gidan dole ya dauki mataki ...in kuma ba haka ba to yana ji yana gani Meena zata girma ta fitar dashi cikin gidan ...hankalinshi yayi mummunan tashi domin wannan gidan shine rufin asirinshi ... </div><div><br /></div><div> A rude ya sami wani babban abokinshi wanda tare suke komae nasu ...shine ya bashi shawarar indae yana so ya gaje gidan to dole yasan yadda zai hada auren da Musa da Meena .... </div><div><br /></div><div> Shawarar ya dauka ...ya kuwa samu rabi da maganar ...daga farko taki amincewa ...amma daga baya daya sameta akan cewa ta nuna mashi bashi ya haifi Meena ba ...hakuri ta bashi amma ya tashi ya fice daga dakin ...tun daga ranar yake fushi da ita ...</div><div><br /></div><div> Rabi tana da ilimin addini kuma tasan darajar miji ga matarshi don haka har daki ta sameshi ta bashi hakuri sannan ta nuna ta yarda ... Da yake munafukine ranar soyayya kala kala ya nuna mata ...tunda ga ranar yakoma yana lallabata ... </div><div><br /></div><div> Ita da kanta ya tura ta sami kaka da maganar amma fifir taki yarda ...wasu malaman unguwarsu ya turo mata suka dinga mata sharhi akan Meena tare da bata baki ....da kyar suka shawo kanta ta yarda ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Bayan sun tafine Meena ta dawo daga islamiyya sanye da uniform ...tun daga zaure ta fara kwalawa kaka kira ... </div><div><br /></div><div> Kaka tace ..Meenalle ta yau kuma me aka samo ... </div><div><br /></div><div> dariya tayi ta zube bisa kafarta ...sannan ta kalleta tace ...Kaka Maikamshi yace ya kusa dawowa ...kinsan idan ya dawo ko ..uhmm kaka kenan ..ranar zan kwashi adashena na hada mashi abinci mai dadi kuma ba bashi zan mashi ba kyauta ...kinga ko ranar zan saka wadannan kayan Sallan da Mamana ta dinka man ...inyi kyau sossae wallahi ko ke bara ki ganeni ba ......Yana zuwa zance I Love you Uncle Ma'aruf..I Kiss Me Mo Uncle ...kinsan waya koyaman wannan turancin ? Girgiza kai ..kaka tayi a hankali ....tana kallonta ... </div><div><br /></div><div> Zama ta gyara sannan tace ...wani littafine na samu na kaiwa Mamansu kausar kawata ta koya man ...Allah ko Kaka Ina son Mai kamshi ... ...tashi tayi ta shige daki ta cire Unifoam dinta sannan ta dawo ta zauna tare da sake sabon surutu kuma duk kan Ma'aruf ...wanda kullun dama firanshi take ..</div><div><br /></div><div> ••°°•• </div><div><br /></div><div><br /></div><div> Rabi na zaune daki babansu Luba ya shigo rike da goro a hannu ...gabanta ya zube mata sannan ya zauna yana washe baki ... Ga goron auren danki....ya fada yana dariya ... </div><div><br /></div><div> Zumbur ta mike ..tana fadin na shiga uku ni Rabi ...Aminatu Malan shekararta 12 kenan ..haba Malan ...wani kuka ta fashe dashi tare da dukewa gurin ..... </div><div><br /></div><div><br /></div><div> Mikewa yayi ya fice daga dakin tare da barin goran a kasa ....Musa ya shigo cikin babbar riga yana washe baki ... Dukawa yayi ya gaisheta yana washe baki ...kasa amsawa tayi har ya mike ya fice daga dakin yana tattare riga ...dakin uwarshi ya shiga ..Wanda itama sae yanzu take jin labarin ..kallonshi tayi sama da kasa ta wuce su tare da tur da halinsu ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Feedohm💞</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ...</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>23. to 24</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div> Cikin sauri Rabi ta fito daga cikin gidan Malan ...yana shingide bisa dakalin kofar gidan ...mutane ke zuwa tare da mashi murna ...bata kalli kowa ba ta tsayar da mai adaidaidata ...tasha tace ya kaita cikin saa ta samu motar kaduna mutun daya ake jira .....ta hau suka tafi ...</div><div><br /></div><div> °°••°°</div><div> </div><div> Kofar gidan Alhaji Abubakar ta sauka ...bakin gate taga motarshi da alama yanzu ya Dawo ...</div><div> </div><div> Yana hangota yayi saurin fitowa ya tareta ...Rabi dama kina raye ? ....ya tambayeta a rude ..</div><div> </div><div> tambayar ta sosa mata rai ...saurin daga mashi hannu tayi sannan tace ..Muna Raye ko muna Mace abubakar wannan ba damuwarka bane ...nazone na tuna maka da amanar Da Allah ya baka tana bukatar taimakon Ubanta Abubakar ..Idan har kabar Ameenatu ta wahala a duniya daga ni har ita sae Allah ya tsayar damu ya mana hisabi ....Wata takarda ta fito da ita daga jikkarta ta daura mashi saman motar ta juya sannan tace ....Duk lokacin daka shirya daukarta ka nememu ta nan Abubakar ....Bata jira cewarsa ba ta haye adaidaitar da ta kawota ....</div><div> </div><div> </div><div> bata isa gida ba sae wajen sha biyu na dare ....gidan kaka ta wuce ta buga masu gidac...cikin bacci Meena taji bugun gidan da yake bata da tsoro ta fito ta tsaya jikin kofar tace ..</div><div> </div><div> waye ke bugawa kamar barawo ...baka ga gidanmu bane ...to mugu idan ma kudin adashe na kazo nema to ban amso ba ...</div><div> </div><div> Ki bude Ameenatou ....</div><div> </div><div> Mama kene ...hala wani abu mugun babansu Luba ya maki ..kema dae Mama kawae kice ya fitar maki daga gida ...</div><div> </div><div> Ameenatou nace ki bude ko ....ta fada da karfi ..</div><div> </div><div> Da sauri ta bude tare da tsayawa tana kallonta ...amma mama banga wani ciwo a jikinki ba ....</div><div> </div><div> Shiru tayi ta shigo tare da rufe gidan da sauri ...kaka ta tada ...ta kalleta a dan tsorace tace ...Rabi lafiya da wannan daren hakan ? ...</div><div> </div><div> Da Sauki dae ...daga kaduna nake ...ta fada tana kallon meena dake zaune ta kura mata ido. .</div><div> </div><div> Gurin wa kika je kaduna yanzu rabi ...</div><div> </div><div> Gidan Abubakar Gwaggo can naje ..na tuna mashi da amanarshi ...na kasa Hakura gwaggo ko taimakeni ...idonta ya kawo ruwa. .</div><div> </div><div> Da sauri meena ta matsa tare da dafa mamanta tace ...Mama Shi Abubakar din zai taimaki babansu luba ya sakeki ne ? ...</div><div> </div><div> A a Ameenatu babanki ne ..shine mahaifinki ...ta fada da sauri ..</div><div> </div><div> taba baki tayi ..su babana manya ni bana sonshi ..mai kamshine komae nawa...babana baya sona bai taba zuwa ya dubani ba ..amma mai kamshi yana sona ..ni bani da wani baba ...</div><div> </div><div> Kina da Ameenatu babanki yana sonki karfinshi aka fi ....ta fada hade da dafa ...</div><div> </div><div> Ba wani Mama ...baya sona ...nima bana sonshi ...ya taba zuwa ya kaini makaranta kamar yarda babansu sauran kawayena yake kaisu ...ko ya taba man kayan sallah ...Duka ba Ma'aruf yake man ba ...shike kaini makaranta idan an koroni ya har goyani yake idan ina kuka ya man komae ...shi kadae na sani arayuwata cikin maza ...sae ke da kakata ...kawae ki bar maganar babana ....kwanciya tayi bata sake cewa komae ba ...</div><div> </div><div> </div><div> °°••°°</div><div> </div><div> Meenatou ...ya Fada Ahankali ...</div><div> </div><div> Rufe idonta tayi sannan ta bude ...</div><div> </div><div> Bara ki amsa ki ...ko bakya jina ...ya kara fada ahankali ..</div><div> </div><div> Yaushe ka dawo ...ina son na ganka Mai kamshi ..dan Allah ka dawo ...ta fada cikin kuka ....</div><div> </div><div> duk ya rude bai taba jinta ahaka ba koda take mashi kukan ya dawo kullun ba irin wannan kukan bane ...na yau yasha banban dana kullun ...asalin kuka take mashi mai shiga zuci ....</div><div> </div><div> Zan dawo Meenatou ...zan dawo gobe kinji ko ...kiyi shiru please Meenatou nima na so nazo na kara ganin inga ya kika zama Meenatou ....Kiyi Hakuri gobe zan dawo ...ya fada cikin lallashi ...</div><div> </div><div> Da gaske Mai kamshi ...ta fada cike da doki ...</div><div> </div><div> Da gaske Meenatou..kin tuna Ranar da zamuje gidan Mama dake ...ya fada cikin wasa ...</div><div> </div><div> Uhm na tuna Mai kamshi ..ina lissafawa shekara 3 da sati 5 yau ...ta fada tana murmushi kamar yana ganinta ...</div><div> </div><div> sae da yayi dariya sannan yace ...kin tuna abunda kika fadawa kaka. ..</div><div> </div><div> Aa ban tuna ba ...ta fada a hankali. ..</div><div> </div><div> ya shafi sajensa yace ...a wancan ranar Meenatouta ta fadawa kaka cewa ta fira kirgar dangi ..to na tabbata ...</div><div> </div><div> da sauri ta kashe wayar tare da rufe fuska ...Mamansa na ganinta tayi murmushi tace ...aa su mamana an fara kunya kenan .</div><div> </div><div> </div><div> </div><div> Wayar ta kara ringing amma har ta tsinke bata dauka ba ....text ya turo ...dan lokacin Meenatou na js one. .kuma babu abunda ba zata iya karantawa ba ...</div><div> </div><div> _Please Meenatou ki daga wayan baran sake cewa komae ba_</div><div> </div><div> reply ta mashi tace ... _Uhm Uhm sae da safe Maikamshi_</div><div> </div><div> Yana ganin text din yayi murmushi sannan ya tura mata </div><div> </div><div> _Wow Meenatou ta fara hankali ...am Very Happy na kusa Furtawa Meenatou Sirrin Zuci ..._</div><div> </div><div> tana karantawa ta yi murmushi tare da mikawa Mamanshi wayan ...kin karba tayi tace mata. ...</div><div> </div><div> Jeki da Ita mamana taki ce ..dama bari mukayi ki gama primary sannan ....</div><div> </div><div> tsaye tayi rike da wayar ta kasa koda motsin kirki ....</div><div> </div><div> °°••°°</div><div> </div><div> Babansu Luba ya shigo cikin dakin tare da nunata da hannu ....Dan Iskanci Rabi shine kika wucemu shekaranjiya ko gaisuwa babu ...sannan ma da zaki fita ubanwa kika tambaya .....</div><div> </div><div> Ganin bata kulashi ba ya saka yace ...kuma ki shirya Musa yace yana bukatar matarshi nan da wata biyu ..kije ki sanar da innarki ku shirya duk abunda ake bukata na samo masu gida a kauye ...acan zasu zauna don bazan cuci yaro ba ace sae nan da wasu shekaru zai tare da matarshi ...tunda har ya nuna yana bukatarka ...don haka kuje ku shirya ni na gama koma ....</div><div> </div><div> </div><div> bata ce mashi komai ba har ya karaci fadanshi ya tafi don kanshi ....</div><div> </div><div> </div><div>*Feedohm💞*..</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI .....</div><div> </div><div> 💞</div><div> </div><div> Na Feedohm 💞</div><div> </div><div> </div><div> 25 to 26</div><div> </div><div> </div><div> Tun da asuba Meena ta bar gida ...inda take adashen kudin taranta ta nufa ..tana zuwa ta karbo kudinta sannan ta shige wani shago ....shinkafa ta sawo dan kwati ....Tare da gwangwani biyu na wake...Cefane tayo tare da namanta na dari biyu ...</div><div><br /></div><div> Wani karamin littafi ta dauko tana karantawa ...alalan shinkafa tayi kokarin yi tare da miyar wake. ..ba laifi tayi kokari don duk inda bata ganeba zata ruga da gudu gidansu Ma'aruf ta tambayo mamanshi. ...ta dawo ...nan da nan gida ya fara kamshi ...bayan ta gama ta dauko wasu kwanukan kaka sababbi ta zuba ....sannan ta kai markaden kunnun aya ta hada mashi ...kaka ta gwada mata yarda zatayi har ta gama ..duk kwadayi irin na Meena bata ci ko yankar nama ba .....</div><div><br /></div><div> Wanka ta shiga tayi ...wannan karon wankan gaskia da gaskia tayi ...tana shafa vasline Ma'aruf yayi Sallama ....wata kara tayi tare da fitowa da gudu ta makalleshi ....</div><div><br /></div><div> tsigar jikinshi ta tashi yar. ...don daga ita sae zani .....kokarin zameta yayi cikin wayau don gani yake yanzu yana iya daukar zunubi indae zaya yarda ta dinga hade jikinsu. ...</div><div><br /></div><div> Galala ta tsaya tana kallonshi ...lumshe ido yayi a hankali...hakan ya kara mata damar kare mashi kallon ...</div><div><br /></div><div> a hankali tace ...Mai kamshi ya zama ba indiye .....</div><div><br /></div><div> Uhmm Meenatou fa ? ...ya tambayeta ....tare da kura mata ido ...</div><div><br /></div><div> murmushi tayi sannan ta dauko tabarma ta shinfida mashi ...tana fadin ..</div><div><br /></div><div> Mai kamshi Allah yasa dae yadda na bar surutu kaima kabar cin zalin .....</div><div><br /></div><div> Ya zauna yana fadin ...ayya Meenatou har yanzu baki bar surutu ba .....</div><div><br /></div><div> Da gaske na daina ...yanzu Allah idan na rantse har kaka na yarda ....ta fada tare da shigewa daki ..</div><div><br /></div><div> Kaya ta sanyo sannan ta fito. ..lokacin har ya mike zaya tafi ....</div><div><br /></div><div> Bata fuska tayi tana kallonshi ....murmushi yayi yace ...zan koma gida Meenatou ko tsayawa banyi na gaisa da mama na fito ....</div><div><br /></div><div> Cikin shagwaba tace ...uhm uhm ni dae ban yarda ba ...</div><div><br /></div><div> Ido ya lumshe. .Meenatou kin canja komae ya canza daga gareki Sossae ...kyanki ya fito kamar bake ba Ameenatu ....</div><div><br /></div><div> Nidae ka zauna dan Allah ....ta fada a hankali ...</div><div><br /></div><div> yanzu zan dawo .....mamaki sai ganin hawaye yayi a idonta. ..</div><div><br /></div><div> Ya Salam ....ya fada a hankali ...Meenatou wallahi yanzu zan dawo ..</div><div> </div><div> To ka cire takalminka kaje kadаwo ...</div><div><br /></div><div> Na tafi ba takalmi Meenatou ...ya fada a hankali..</div><div><br /></div><div> To muje tare sae mu dawo ....ta langwabe kai ...sallama yayi da kaka sannan suka tafi ...</div><div><br /></div><div> ••°°••</div><div><br /></div><div> Wallahi Abubakar koda rana daya ka sake man maganar Rabi ..to zan daga maka nono ...Ta fada a fusace ...</div><div><br /></div><div> Kuka ya fashe dashi tare da dafa guiwarta ta yarje mashi yaje ya dauko Meena amma fir ta kiya daga karshe tashi tayi ta bar mashi Falon .....yafi Awa zaune gurin ...duk lokacin daya bude ido Rabi yake hangowa tare da jinjirar diyarta lokacin da take kuka zasu rabu ...hannu ya saka ya share hawayen tare da fadi. ...Allah sarki diyata ina sonki ...Hannu ya daga Sama yace ...Ya Ubangiji Allah ka saukar da zuciyar Mahaifiyata na karbo diyata na nuna mata gatan da baa taba gwadawa wani shi ba Allah ka kare man Aminatu Ya Allah .....hawayen dake idonshi suka idasa fitowa ...ko yaya Aminatu ta koma. ...ya fada tare da mikewa shima. .....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> ••°°••</div><div><br /></div><div> Baki ta turo tana fadin ...wae mai kamshi babansu kausar ya bani dog (kare) amma kaka tace bara na karbo ba ...wae mala'inkun rahama basa shiga gidan dake da kare ....</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi yace ...to kiyi hakuri mana Meenatou ...</div><div><br /></div><div> Kafada ta make sannan tace ...To Dan Allah mai kamshi ba idan na tara karnukan da yawa ba sae ka dauko man mota ba na kaisu lagos a saya a bani kudin ....kuma banda bakin ciki irin na kaka ba sae na ajeshi a zaure ba ....idan mala'ikun sunyi niyar zuwa ko ta katanga ba sae su diro ba...tunda katangar gidan mu ba irin taku bace ...ko na baka ka aje man ? ....</div><div><br /></div><div> Dariya ya sake sossae tare da mikewa ya dauki hanky dinshi ....gam ta rike hanky din tana kallonshi ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Ki saki Mana Meenatou ....ya fada a hankali ..</div><div><br /></div><div> Uhm uhm. ..ka bari na wanke maka wallahi na iya ..kuma da kyau zan wanke maka ....ta karbe hanky din daga hannunsa ....</div><div> </div><div> girgiza kai yayi tare da sanya takalmi yana fadin ....Idan kaka ta gama baccin kice mata nazo muyi bankwana amma zan dawo ...</div><div> </div><div> Da gaske dae komawar zakayi Maikamshi ...ta fada kamar zatayi kuka ...</div><div> </div><div> Meenatou ba mungama wannan maganar ba tun dazu ...nace maki saura 1yr na gama na dawo baki daya ..mu zauna tare mu rayu a tare ko Meenatou ...karkiyi kuka kinji ko .....ya rike hannunta yana kallon cikin idonta ...</div><div> </div><div> kanta ta sadda kasa tana kokarin hade hawayen dake neman zubo mata ....kwantar da kanta tayi bisa cikinsa tana shakar kamshinsa ....</div><div> </div><div> Ji yayi wani sabon lamari na neman hargitsa mashi tunani ...yayi saurin janyeta tare da ficewa daga gidan</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm*💞</div><div>.</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ......</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>27 to 28</div><div><br /></div><div> </div><div> Zaman dirshan tayi gurin tare da hade kai da guiwa tana kuka .....</div><div><br /></div><div> Haka shima tunda ya koma gida kasa samun natsuwa yayi ...wani zafi zuciyarsa ke masa ..har Mamanshi sae da ta mashi magana amma yace mata bakomae ....</div><div><br /></div><div> Kwanciya yayi ...yaki hada komai ...sae da Mamansa ta shigo dakin da kanta ta hada mashi jikkanshi ...lokacin Abba na cikin mota yana jiranshi .....</div><div><br /></div><div> Bayan sun gama bankwana da Mamanshi sannan ya shiga gidan kaka da sauri. ...</div><div><br /></div><div> kaka na tsaye tana kwashe shanya ...tace ..Ma'aruf ba dae Tafiyar bace ko ...</div><div><br /></div><div> Murmushin yake yayi yana raba ido cikin gidan tare da fadin ...Har ma mun fito Kaka ...ina Meenatou ? ..</div><div><br /></div><div> Meenalle ...ta kwala mata kira ....amma shiru bata amsa ba ...aje kayan dake hannunta tayi ta leka daki amma bata ciki ....dawowa tayi tana kwala mata kira shiru duk gidan ba inda bata leka ba amma Ba Meenalle. ..tayi mamaki sossae don tasan bata aiketa ko ina ba ...sannan lokacin data fito ta ganta tsugunne tana kuka ....</div><div><br /></div><div> dawowa tayi inda ta barshi tana taba hannu ...tace...kaga Ma'aruf wallahi bata gidan bansan inda ta tafi ba ....</div><div><br /></div><div> Wani abu ya tokare mashi kirji ...duk irin daurayi irinta Ma'aruf sae da yaji hawaye na neman zubo mashi ...</div><div>Lumshe ido yayi tare da ciro wani karamin abu mai shape din heart da envelope daga cikin jikkarshi ya daurawa Kaka bisa hannu tare da fadin ...Na Meenatou ne Kaka....ya fice kamar kwae ya fashe mashi a ciki.....</div><div><br /></div><div> Yana fita aka bude mashi mota ya shige ba tare da ya juyo ba ko sau daya ...daga karshe ma kanshi ya daura saman cinyar Abba ...</div><div><br /></div><div> Tana daga bayan gidansu tun da taga ya Shiga gidan kaka tasan tafiya zayayi dole ...ta rabe jikin bango tana kuka ita kadae. ..har fito ya shiga mota tana kukan ...tana ganin an tada motar ta fito da gudu tana kuka da karfi ...motar tabi da gudu .....tana daga hannu. ...</div><div><br /></div><div> Karo tayi da mutun da yasaka dole ta tsaya daga bin motar ......</div><div><br /></div><div> Tsinka mata mari yayi tare da fizgarta yayi gidan kaka da ita ....bata dago bare tasan wanda ya mareta ...kuka take har idonta ya bushe ....</div><div><br /></div><div> Suna shiga gidan kakar mutumin yayi wurgi da ita tsakar gida ...da sauri kaka ta fito daga daki tana kiran lafiya kuwa ...</div><div><br /></div><div> Turus tayi ganin musa cikin gidanta ....Meenalle ta kalla gefe guda kwance a kasa idanuwannan sunyi jawur da fuskar .....da sauri ta matsa tare da dagota </div><div><br /></div><div> Meenalle ina kika je. .me ya sameki Meenalle ....ta fada duk ta rude ...</div><div><br /></div><div> Ma'aruf dina ya tafi kaka. ..ya kuma tafiya ya barni ...kaka kice mashi ya dawo dan Allah ....ina Sonshi Kaka ....ina so ya zauna tare dani ...ta rungumeta tare da fashewa da wani sabon kukan</div><div>Kiyi Hakuri Meenalle zaya dawo kinji ko ...dan Allah ki bar kukan karki karya man zuciya nima ...ta fada lokacin da itama idonta ya kawo ruwa. ..</div><div><br /></div><div> Kutmar uban can ...kina matana kina son wani don Uwarki. ...musa ya fada da karfi ...</div><div><br /></div><div> Ba Meenalle ba har kaka sae da ta firgita suka dago suna kallonshi .....ya nuna Meenalle da hannu yace. ....Ki tashi muje dan Uwarki tun kafin na maku shegen duka ku duka biyu. ....</div><div><br /></div><div> Meenalle ta kalli kaka tace ...da gaske yake kaka ....</div><div><br /></div><div> Rashin amsar data bata yasa ta dan fahimci wani abu ...don tasha ganin ana yiwa kananan yara aure a kauyensu Kaka lokacin da sukaje wani biki tun ma kafin ta kai haka </div><div><br /></div><div> </div><div> Kaka ta nunashi da hannu ...Kai Musa ko ubanka bai isa ya nuna man hannu ba bare kai ...</div><div><br /></div><div> Gurin Meenalle ya nufo da sauri kaka ta tareshi ...hannu ya saka cikin rashin imani ya buge tsohuwar tare da jan Meenalle kamar kayan wanki ya fice daga gidan ....</div><div><br /></div><div> Duk mai adaidatar daya tsayar baya tsayawa sae da kyar ya wani ya tsaya ya shigar da ita sannan ya shiga ....</div><div><br /></div><div> Kuka kawae take ...amma ba kukan abunda ya mata ba ...aa kukan dukan da yama kaka da kuma kukan rashin Ma'aruf. ....</div><div><br /></div><div> Ba gidan Malan sani ya wuce da ita ba aa tasha suka nufa ...</div><div><br /></div><div> Duk abunda yake kallonshi kawae take ita kadae tasan abunda ke ranta ....yana cewa ta shiga mota ta shige babu matsala ....</div><div><br /></div><div> wani gari aka ajesu ...sae da suka hau mashin sannan suka shiga kauyen .....wani karamin gida mai cike da jamaa yan tarar amarya suka nufa ....tun daga kofar gidan ta gane danginsu Babansu Luba ne don daga ganin hancinsu zaka gane ...</div><div><br /></div><div> Ji tayi ana ga amaryar musa ....ta kuwa kalli gefenta taga sae washe baki yake. . </div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>SIRRIN ZUCI.....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>29. to 30</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Duk abunda suke kallonsu kawae take har kowa ya watse ya barta ita kadae ....</div><div><br /></div><div> Dakine da tabarma shinfide sae tukunyar ruwa ...zoben dake hannunta take murzawa ta kurawa kofar ido ...zuwa can ya shigo sae uban wari yake ...tayi saurin goge hawayenta tare da maida hannunta baya ....</div><div><br /></div><div> Gefe ya zauna ya kura mata ido yana washe baki yace ...Meena an kawo maki tuwo ko ...</div><div><br /></div><div> Harara ta balla balla mashi tace aa ...Babansu Luba aka kawo man ...</div><div><br /></div><div> da yake sakarae ne bai san darajar iyayenshi ba sae washe baki yayi yace ...Danshi dai yanzu yazo ...ya matso kusa da ita ...</div><div><br /></div><div> Matsawa tayi tana hararanshi tace ...bansan iskanci wallahi.. kai musan nan dama dan iskane ...ta murguda baki. ...</div><div><br /></div><div> Tashi yayi ya cire riga ...ta kalli kirjinsa duk da yanzu ta bar cizo amma ba abinda zai hana ta cije wannan shegen ba ....ta fada a ranta. ..</div><div><br /></div><div> kafin ya ankara tayi kukan kura ta fada saman jikinshi ai kuwa ya fada kasa ya bugu ....ta dankara mashi cizo ta saka hannu ta murde abun fitsarinshi da karfi .....wani kara ya sake don tabbas yaji azaba sossae ...</div><div><br /></div><div> Tana ganin ya fita hankalinshi ta mike da gudu ta fice daga dakin ...</div><div>Lokacin da ya dawo hankalinshi ya fara nemanta yana sabbatun Sae yaci Uwarta ...babu inda bai duba amma bai ganta ba. ...</div><div><br /></div><div> Meenalle tana cikin gidan kuma duk neman da yake tana kallonshi bayan wani rumbu. .....har ya gaji da neman ya koma daki ....</div><div><br /></div><div> Nan gurin tayi baccinta ....tun da asuba kuwa ta farka ....ta leka dakin yana kwance kamar gawa.... alwala tayi tayi sallah ...sannan ta fita ta debo kaikayin gero ta zo ta zuba mashi ruwa ta koma ta sheka mashi ....kamar aljana kafin ya gama hauka kaikayin ta koma inda ta kwana ta lafe .....</div><div><br /></div><div> Sae da safe sannan suka hadu. ... ya bita zaya daka yana zagi ...ta kuwa fice daga gidan da gudu .....shima binta yayi amma ya kasa kamota dole ya kyaleta amma ya dauki aniyar duk lokacin daya kamata sae ya mata dan uban duka. ...</div><div><br /></div><div> Bata dawo ba sae dare ...lokacin tayi kawaye yara da yawa kamarta ....tare sukayi wasa sannan tabi wata gidansu taci abinci ....kasancewar kauyen scattered ne shi yasa ba kowa ya san kowa ba ...wani gidan ma bara kayi tunanin akwaeshi cikin garin ba ...don tafiyace ba karama tsakanin gidajen ....</div><div><br /></div><div> Tana dawo ...ta leka dakin ta make murya tace ...Kai Shege Musa .....</div><div><br /></div><div> ya taso kamar mahaukaci amma kafin ya fito har ta boye inda ta kwana ....bai ganta ba ...haka ya karade gidan har ya hakura. ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Bayan kaka ta mike gidansu Musa ta nufa tarad da Malan Sani kofar gida ....duk abunda ya faru ta fada mashi amma sae ce mata yayi ai matar musa ..kuma yana da ikon ya kaita duk inda yaso ...</div><div><br /></div><div> Tana jin abinda ya fada ta shige cikin gidan ta sami Rabi zaune bama tasan abunda ke faruwa ba ....ta hauta da fada ta inda ta shiga ba tanan ta fita ba ...sannan ta fada mata har da dukan da musa ya mata ....</div><div><br /></div><div> Ran Rabi idan yayi dubu ya baci ...fita tayi ta samu Malan sani a zaune ...</div><div><br /></div><div> Ina kuka kaiman diyata Sani ...ta fada cikin tsawa ...</div><div><br /></div><div> Mijinta ya dauke abunshi ..ko bada saninki akayi auren ba ne ? ....shima ya fada cikin harguwa. .</div><div><br /></div><div> A ranan dai anyi ba dadi tsakaninsu ...sae ranar ya fahimci wacece Rabi sannan zata iya komae akan diyarta ...dan cewa tayi ma sae ya saketa amma fur yaki sakinta ....</div><div><br /></div><div> Bata koma gidan ba taja hannun kata suka bar unguwar ...babu irin neman da basuyi wa Meenalle ba amma babu labarinta ...hakanan suka hakura suka dawo ....</div><div><br /></div><div> ••°°••</div><div><br /></div><div> Ma'aruf duk wani kuzarinsa ya tafi kullun ka ganshi cikin damuwa yake ...duk yan matan dake juyi gabanshi yanzu sun shiga taitayinsu don sun gane jiran kowa yake yaci mashi mutunci. ....</div><div><br /></div><div> Abokanshi kuwa sunyi tambayar duniya kullun amsa dayace ....karsu dameshi .....mutun daya kawae yasan labarin Meenalle .....</div><div><br /></div><div> Yau ma kamar kullun ya kira Mama ..yace ta bada wayar akaiwa Meenalle ....</div><div><br /></div><div> Cikin lallashi tace mashi ..An kai Meenalle boarding school .....</div><div><br /></div><div> Tunda ya yanke wayar ya fitar da sim din bai kuma kiran wani ba a nigeria. ...Su Abba sunyi neman duniya amma wayar bata shiga ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm*💞.</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>31 to 32</div><div><br /></div><div> </div><div> Watansu Biyu da aure amma Musa duk ya kare yayi baki dama abunka ga bakin ....fitinar meenalle ta bi ta dameshi kullun da irin muguntar da zata mashi sannan sau daya ya taba kamata ya daketa ...shima ya wahala gurin dukan don duk sae da ta yakuceshi ta cijeshi .....shi bai ma daketa ba kamar yadda ta wahalar dashi .....</div><div><br /></div><div> Sannan ma duk ta gama zubar mashi da mutunci ga mutanen kauyen ...duk gidan da ta zauna bata da labari sae nashi dana ubanshi ....daga inda zata ce Babansu Musa dan iskane yara yake wa iskanci a garinsu sannan kuma dan cacane ...alhalin bata taba ganin yana iskanci ba ..gara ma cacar ta fadi gaskia ....</div><div><br /></div><div> Idan kuma ta shiga wani gidan sae tace Babansu Musa barawo ...don tsabar karya irinta meenalle har cewa take ya taba dirawa gidansu Maikamshinta ya sace masu jarkar mai ja....</div><div><br /></div><div> Haka idan ta kuma shiga wani gidan su kuma tana iya ce masu ...Musa Mijinta dan iskane su yi kaffa kaffa da yaransu ....</div><div><br /></div><div> Mutanen kauyen duk sun yarda don sun tabbata meenalle bara tayi masu karya ba a tunaninsu. ...</div><div><br /></div><div> Idan kuma Labarin kirki ya tashi ...to labarin mai kamshine ...wani sa'in ta fadi gaskia wani sa'in kuma har da karya. ..duk kauyen ba wanda baisan Maikamshin Meenalle ba ...haka ba wanda baisan yana da taurin bashi ba</div><div>Har labarin irin ciwon da taurin bashi ya sake mashi ba sae da taba yan kauyen ...</div><div><br /></div><div> Lokaci guda tayi farin jini a kauyen kowa sonta yake ...duk inda ta gifta sae kaji ana Meenallen Maikamshi ...sae ta washe baki....haka mamanta da kakarta kowa ya sha labarinsu ....har fada masu take ...kakarta da tana da wani buje duk ya yage ...ita ta sace bujen ta yarda don ta gaji dashi .....</div><div><br /></div><div> Musa kuwa duk wanda ya ganshi da yaronshi to zaiyi kokarin ganin ya raba su</div><div>Don kar ya bata masu yara ...kauyen ya isheshi .... yaje har gida ya fadawa Malan sani halin da yake ciki ...</div><div><br /></div><div> Rufeshi yayi da fada akan shine ya kyale Meenalle ...amma amsar da ya bashi ita tayi matukar girgizashi ...don ce masa yayi ...yana matukar son Meenalle ....</div><div><br /></div><div> Yafi Minti ashirin kafin yayi magana.. . yace mashi to yayi hakuri zaya sake nema mashi wani gida acan kauyen dangin uwarshi ....haka ya koma gida jiki a salube. ....</div><div><br /></div><div> Amma yana zuwa kofar gida yaja burki don ganin Meenalle ta tara mashi yara sun cika gidan wae yan kwana ta debo yara sunfi Ashirin ...dole ya zauna kofar gida anan yayi bacci ....</div><div><br /></div><div> Da Allah ya taimakeshi yaran duk suka koma gidajensu zasuyi kalaci ....ya shiga gidan jiki a sabule ya sameta sae wanka take tsakar gida ta saka karamin siket duk ya jike ya bi mata jiki ...ta dan fara kirgan dangi ga kuma hips da take dasu dama can .....tayi jawur kamar baa kauye take zaune ba .....</div><div>Kamar sakarae haka ya zauna yana kallonta har sae da ta gama sannan ta juyo tana kallonshi tare da watsa mashi harara. ...tace ..</div><div><br /></div><div> Kai Musa lafiya kake kallona kai dai mayena ne wallahi .....</div><div><br /></div><div> Bakomae Meenalle ...ya fada da sauri. ..don bala'in tsoronta yake tare da sonta yanzu ..</div><div><br /></div><div> Tabe baki tayi ta shige daki ....ta sanyo kaya sannan ta fito ta zauna kusa dashi tana washe baki .... </div><div><br /></div><div> Tace ...Musa bani hamsin ...</div><div><br /></div><div> haka ya ciro yana kyarma ya mika mata ...ta fice tana mashi ....awara ta saya taci sannan ta shige gidan kawayenta suka fito wasa .....</div><div><br /></div><div> ••°°•• </div><div><br /></div><div> Kaka da kanta ta koma gidan Alhaji Abubakar amma sae aka ce mata an kwantar dashi asibi ...haka ta dawo bata samu ganinshi ba ...don ta tabbata shi kadae zaya iya kwatarma Meenalle Yan'cinta ......</div><div><br /></div><div> Abban Ma'aruf ma da kaka ta fada masu da cewa yayi zaya shigar da kara ...amma wani amininshi ya bashi hakuri tare da lallabarshi ...indae ya shigar da kara to duniya zata dauka yana son kashe auren ne don Ma'aruf ya aureta ....haka ya suka hakura amma basu yarda Ma'aruf ya sani ba ...kawae sun barta a cewa Meenalle ta tafi boarding school ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> *Feedohm💞*</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI ....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div> *Ban ma san me zan fada ba ...am speechless wallahi ...duk irin godiyar da zan maku bara ta gamsar dani ba na fahimci kun yarda da ina tare daku ....Nagode sossae Allah ya bani ikon faranta maku ...ina yinku sossae ...Thanks For your support and cares .....08066598868 Shine real number na ta yanzu wadanda ke fadar bana masu magana wancan number da suke messages na bar amfani da ita ..*</div><div>💞</div><div><br /></div><div>33 to 34</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Haka Musa ya tattara kayanshi da Meenalle suka koma kauyen Ruhogi can cikin zariya .....acan ma Meenalle cikin Kwana kadan ta zama yar gari ....kasancewar gida daya suka zauna da dangin Uwarsu musa ....</div><div>Cikin wata biyu zaman ruhogi ya fi karfin Musa ..ga kuma wani bala'in son meenalle da yake ...ko mi tayi mashi baya iya ko da mata maganar banza ne ....abunda ta fada a wancen garin sae ma ya zama wancen garin da suka baro yafi mashi dadin zama ...dan a ruhogi cewa ta dinga yi ko rosu akayi saboda Musa dirawa yake gidan matan aure yana kwartanci ...sanna ga muguwar satar awaki da yake masu ...har cewa take wae ya dira gidan maigari ya shiga dakin amaryarshi mai garin ya saka aka mashi mugun duka ...sannan abincin mutane yake sacewa idan sun aje a waje kafin su shigar dashi gida ....</div><div><br /></div><div> Fitinar Meenalle ta isheshi dole ya tattarota ya maidota gidan malan sani ......</div><div><br /></div><div> Ranar da suka dawo garin kuwa. ..kafib keftawar ido suka nemi Meenalle suka rasa ....gidan kaka ta koma ...acan ta iske Mamanta da kaka zugum ...</div><div><br /></div><div> Ranar sunyi murna sossae da ganinta ...rabi ta rungumeta tana tambayarta rayuwarta ...bata boye masu komae ba ta basu labari ..sunsha dariya sossae sannan duk wani takaici dake zuciyarsu sae da ya fita ...don ko ba komae sun tabbata Meenalle ba inda zata shiga a cuceta ....</div><div>Daga nan gidansu mai kamshi ta shiga ...ta tarad da ba kowa gidan sun tafi Umara su duka ...sannan Ma'aruf kuma bai dawo ba ...haka ta dawo tana share hawaye ...anan gidan kaka ta kwana ...</div><div><br /></div><div> Tun da Safe sukaji sallamar mutane ...Kaka ta fita tana binsu da Kallo ...ko baa fada mata ba tasan Malan Sani da dansa ne suka dauko masu yan Sanda ...</div><div><br /></div><div> Ta kallesu tace ...Bayin Allah Lafiya kuma ...</div><div><br /></div><div> Wani daga cikinsu yace ...idan munje office kunyi bayani ....</div><div><br /></div><div> tace to Allah ya kaimu lafiya ...ta shiga ta dauko hijabi ...tare suka fito da Rabi da Meenalle ......</div><div><br /></div><div> a Police Station akace wae ana tuhumarsu da sacewa musa mata. ....daga kaka har rabi kasa rufe baki sukayi saboda maki ...</div><div><br /></div><div> Meenalle ce ta kwashe da dariya tace ...ni ba wanda ya saceni ...Musane yace na je gurin kaka wae zai sa babanshi ya rude saboda a yana binshi bashi. ....</div><div><br /></div><div> Dan Sanda ya kalli dayan yace mata. ..Kece Meenalle ...</div><div><br /></div><div> Ta daga mashi kai tana washe baki. ...yace. .kece matar tasa. ....nan ma daga mashi ...</div><div><br /></div><div> Tace. ..haka nima naji ana fada. ..amma kasan ko ..ina kazar nan da ake sawowa amare to ni ko ita baa bani ba ...kai ko kumshi ma baa man ba. .ina dae jin wannan auren na irin su shegu Musa ne. ....</div><div><br /></div><div> ya Kalli Rabi yace zasu iya ganin Uban Meenalle ....</div><div> </div><div> aa tace mashi. .....sae gasu musa sun shigo .....nan dae aka bawa musa matarshi sannan aka ce su kaka su koma gida. .....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> ••°°•• </div><div><br /></div><div> Alhaji Abubakar na zaune a office dinshi ...babban amininshi Alhaji Sadee ya shigo ....ya dade tsaye yana kallonshi kafin ya dafa kafadarshi....</div><div><br /></div><div> Alhaji Abubakar wae lafiya kake kuwa. ....</div><div><br /></div><div> Gumi ya goge sannan ya dago idanuwanshi sunyi jawur yace ...ba komae Sadee ..</div><div><br /></div><div> Zama yayi saman kujera yace ...A tunani Abubakar yanzu mun zama daya ....duk wata damuwarka ni ya dace na santa. ..ka dubi girman Allah ka fada man meye Matsalar. ...Sirrin zuci ...baya da wani amfani har sae an fito dashi an warwareshi .....</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi ...nan take ya fada mashi duk abunda yake faruwa dangane da diyarshi tilo da mahaifiyarshi ta hanashi dauka ..sannan yanzu yarinyar na bukatar taimakon Mahaifinta. ....</div><div><br /></div><div> Ajiyar zuciya yayi sannan yace. ..lallae Abubakar kana cikin damuwa. ..amma me yasaka tun farko baka fada. man ba ?</div><div><br /></div><div><br /></div><div> *Feedohm*💞</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>35 to 36</div><div><br /></div><div> </div><div> Shin Abubakar Aminatu ba jininka bace ? ...ya tambayeshi cikin natsuwa </div><div><br /></div><div> Tabbas Jininace Sadee kana sane ko da hajiya ta sakani auren Lami bamu taba samun haihuwa ba sannan ba kwanciyar hankali nake samu ba ...babu kwanciyar Hankali ina kake tunanin samun zuri'a ...</div><div><br /></div><div> In Kuwa Aminatu jininka ce to tabbas itama tana da hakki akanka ba mahaifiyarka kadae ba. . Abubakar dole mubi umarnin Mahaifanmu indae bai sabawa Musulunci ba ....shin barin diyarka kana tunani baka sabawa Allah ba ...tunda aka haifeta ka taba zuwa ka ganta. ..kana sane da cinta shanta tufafinta yana wuyanka ....</div><div><br /></div><div> Shiru Abubakar yayi sae uban gumi dake kyeto mashi ....</div><div><br /></div><div> Sadee ya cigaba da cewa ...Aminatu Diyata kamar yarda take diyarka ...bani address din Aminatu zanje ni na daukota na riketa kamar yarda na rike Ahmed da Mus'ab ....zan daga darajarta har sae mahaifiyarka ta hankalta ....</div><div>Sannan ba zan baka Aminatu ba har sae mahaifiyarka ta rokeni akan hakan ...inaso wannan ya zama sirrin zuci ...daga ni sae kae sae matata .....</div><div><br /></div><div> Tabbas duk abunda Sadee ya fada gaskia ...Aminatu nada Hakki mai girma gareshi ....Takardar da Rabi ta bashi ya laluba ya mikawa Sadee .....bai ce mashi komae ba ya fice daga office din ....</div><div><br /></div><div> kasancewar dare ya kusa ya saka ya koma gida ...acan ya sami matarshi Mai suna Saadiya ya fada mata komae dangane da matsalar Amininshi ...</div><div><br /></div><div> Mace ta gari. ...nan take ta goya mashi baya tare da bashi karfin guiwar abunda yake shirin aikatawa .....</div><div><br /></div><div> Tun da Safe suka shirya tare da Babban danshi Mus'ab suka nufi garin su Meenalle ....basu sha wahala ba suka gane gidan Malan Sani ....nan sukayi parki g Mus'ab ya fita daga cikin motar .....</div><div><br /></div><div> Meenalle na tsakar gida tana ta uban bala'in Malan Sani yacewa Mamanta yar iska .....malan na duke bai ce mata komae ba har sae da ya gama alwala sannan ya nade babbar riga ya biyota da gudu ...ta kuwa kwaso a guje. ..a bakin kofa tayi karo da Mus'ab dake ta faman sallama .....tureshi tayi ta wuce da gudu ...ya bita da kallon ....</div><div>...</div><div><br /></div><div> Gidan kaka ta nufa ....a hanya ta tsaya ta gama wasanta sannan ta wuce ...tana shiga gidan taja birki tana fadi ...</div><div><br /></div><div> Kai Aljani bakae ne na baro gidansu Luba ba ....</div><div><br /></div><div> Mus'ab da tunda yaga yarinyar ta kwanta mashi a rai ...yace ..bayan wasa kika tsaya a hanya ...</div><div><br /></div><div> Kilbibi ...ta fada kafin ta gaida Alhaji Sadee dake ta faman kallonta ....</div><div><br /></div><div> sannan ta kalli Mus'ab tace ...to mujiya sae a daina kallona kuma ko ....ta murguda baki ...</div><div><br /></div><div> Murmushi ya sake mata yace ....Meenalle da alama kina da dadin zama</div><div>Ta shige daki abunta ...Alhaji Sadee bai boye komae ba ya fada masu komae dangane da yadda sukayi da Alhaji abubakar......nan da nan ya kirashi a waya sukayi magana da kaka ...dan. Rabi cewa tayi bara ta amshi wayar ba ...</div><div><br /></div><div> Kaka ta kira Meenalle ta fada mata zaa tafi da ita ...amma kememe taki yarda sae tayi bankwana da Ma'aruf idan ya dawo sannan suzo zata bisu ....da lallashi sannan ta bisu ....</div><div><br /></div><div> Suna tafiya Musa na zuwa yazo daukar matarshi ...kallon banza suka mashi sannan sukace ya duba inda ya ganta ya dauka ...daga karshe ma kaka bori tayi tace sae ya fito mata da Meenalle ...haka ya tafi jiki ba dadi ....</div><div><br /></div><div> </div><div> *Feedohm*💞</div><div>SIRRIN ZUCI......</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>37 to. 38</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Ina Labarin Ma'aruf ....Bai kuma kiran iyayenshi ba har sae da ana saura kwana biyu ya dawo ...shima magana dayace ..shin Meenatou sunyi hutu ta dawo gida ....</div><div><br /></div><div> Abba yace. ..aa Ma'aruf Mamana bata dawo ....</div><div><br /></div><div> Abba ka fada man gaskia. ..kodae Meenatou ta rasune kuke boye man ...idonshi ya ciko da kwallah ..</div><div><br /></div><div> Calm down Ma'Aruf Meenatou bata rasu ba kaji ko ...yaushe zaka dawo ...</div><div><br /></div><div> Jibi Abbah ...ya fada tare da kashe wayar ....</div><div><br /></div><div> Raliya ta dafa mashi kafada tare da tausasa murya ...What wrong Ma'aruf .....ta langwabe kai</div><div>Fuskarta ya kalla sannan ya kalli kafadarshi ..da sauri ta janye hannunta daga jikinshi tare da zama bisa kujeran dake facinng dinshi...</div><div><br /></div><div> Ta kura mashi ido har tsawon mintina sannan ta sauke ajiyar zuciya ..tace. ..Ma'aruf please meke damunka ...</div><div><br /></div><div> ya juyar da kai gefe guda tare da fadin ...Tashi kije Raliya ....</div><div><br /></div><div> Haba Ma'aruf tafiya fa zamuyi atleast ka tsaya muyi magana da. girman Allah ...</div><div><br /></div><div> Ido ya lumshe tare da mika mata wayarshi ....drop your number zan nemeki ....</div><div><br /></div><div> Wani dadi taji don ta dade tana jiran wannan rana sae yau Allah ya bata ...jikin kyarma ta karba tare da saka mashi number. ....</div><div><br /></div><div> Thank you Ma'aruf you completed my life....am very happy ....ta fada dauke da murmushi ...</div><div><br /></div><div> Idonshi ya lumshe ya nuna mata hanya ...amma ta tsaya tana fadin ...please Ma'aruf muyi pictures mana ...</div><div><br /></div><div> To the hell of you and ur bullshit pic ....ya fada cikin tsawa tare da nuna mata hanya ...</div><div><br /></div><div> Haka ta wuce tana waigenshi ...</div><div><br /></div><div> _Raliya Saad yar nigeria ce cikin garin kaduna tazo karatu india itama tunda ta kyalla ido taga Maaruf take binsa bai taba tsayawa ya mata magana in ba yau ba Raliya irin matannan ne Yan bariki duk abunda take so sae tayi yarda tayi ta sameshi ...Yar guntuwa ce ..sae dae tana da hips amma ba irin cikkakar matan nan bane ..haka tana da gashi dae dae gwargwado amma duk da haka tana karawa dana doki ..sannan farace tas da ita ...tana dauke da kananan ido kamar yar china_..</div><div><br /></div><div><br /></div><div>°°••°°</div><div><br /></div><div> Su Meenalle tun da aka sauka gidan Alhaji Sadee take washe baki ganin gidan mai kyau ... Hajiya Saadiya ta mata tarba mai kyau ..kamar ita ta haifeta ...</div><div><br /></div><div> Suna zaune bayan mangrib Alhaji Abubakar yayi sallama ya shigo ...tunda ya shigo yake kallon Meenalle. ..har dae ta kasa hakuri ta matsa kusa da Hajiya Saadiya tare da zungurinta ....</div><div><br /></div><div> Lafiya Meenalle ...ta fada tana kallonta</div><div><br /></div><div> Bata fuska tayi tace ..to tunda na zama yar gayu ba sae adaina ceman Meenalle ba ....ta kifta ido ..</div><div><br /></div><div> Tayi murmushi tace to yaakae Aminatu. ...</div><div><br /></div><div> Baki ta washe tare da nuna mata Alhaji Abubakar tace ...Kinga wancan sae kallona yake da idanuwanshi kamar na magen gidansu kausar... oh na manta ban baki labarin kausar ba ko ...Haba Itama kawata ce in gaya maki kullun mamarsu Idan tana girki sae ta barbada wani abu a ciki ...ai ko nace zan fada wa babansu kausar sae ta bani naira hamsin tace kar na fada ..in gaya maki da kaka ta aikeni na yarda kudin sae naje gidansu kausar din nace zan fada tana barbada magana....rannan da naje ta bani kwakwa da dabino tace dan Allah kar na kuma zuwa gidansu ...sae nace mata to na tafi ....</div><div><br /></div><div> Hajiya tayi dariya tana kallon Alhaji Abubakar ..sannan tace mata ...Ni kam naga kamar kuna ma kama Meenalle ...</div><div><br /></div><div> Kai ta juyar tana fadin ...ki nemi Meenalle. .....Sanna ta kurawa Alhaji Abubakar ido tace ...Kuma kamar da gaske dan dae shi kamar yana shafa jan baki ..shi yasa lebenshi yayi ja ....ni kuma nawa hink ne ....kinga na fishi haske ..wae bashine yazo nema gurin Wancen ta nuna Alhaji Sadee .</div><div><br /></div><div> tace ...tashi ki matsa ki gaidashi ....</div><div><br /></div><div> Ta mike ba gardama ta isa gurinshi </div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI ......</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>39 to 40</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Maimakon ta gaisheshi ...sae lekewa tayi gefen fuskarshi tace mashi ....Ka daina kallona ni matar musan gidansu Luba ce ...kasan waye Musa ? ..</div><div><br /></div><div> Girgiza mata kai yayi ...tace ..Kai yanzu duk girmanka baka san Musa ? ..Uhmm to Dan Mijin Mamata ne. ..In Gaya maka Sunan babanshi Sani wae sae ace in dinga jin kunyarshi ni kuma nace bazan ji kunyar ba ..kasan me yasa?...</div><div><br /></div><div> Nan ma girgiza kai yayi tare da kamo hannunta ...tayi saurin janyewa tana hararanshi ...sannan tace ...</div><div>Ranar jumaa mamansu Luba tayi alala ...kasan Mayen alala ne ..aiko ya ci sossae ya dinga banka mana tusa mai shegen wari ..nima kasan cikina ya kumbura naje zanyi kashi haba can naji babansu Luba yana zawo da karfi ...aiko tunda lokacin na daina jin kunyarshi</div><div>Dariya ta bashi sossae ...gata kyakyawa da ita sannan ga surutu da saurin shiga rai ....ya dade tana bashi labarin musa. ..amma sam ya kasa yarda da zancen wae an mata aure ...haba ubanwa ya isa ya aurar man diya tana karama ...ya fada a ranshi .....sannan ta zuba mashi labarin mai kamshi sossae ...ayadda take bashi labarin yaji yana son ganin yaron ...don har zoben da ya bata sae da ta nuna mashi ....</div><div><br /></div><div> Dan zaman da yayi da ita ta shiga ranshi sossae sae wajen karfe Sha daya na dare sannan ya tafi ...shima sae da Sadee ya mashi da kyar sannan ya tafi ....cike da kewarta ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> ••°°••</div><div><br /></div><div> Mus'ab ya shigo rike da ledar chocolate ..Meenalle na zaune saman carpet da duwatsunta tana yar carabke ...</div><div><br /></div><div> Ya samu guri ya zauna yana kallonta tare da mika mata ledar ta amsa tana kallonshi tace ...Kai dae Mayenane Allah ...dan kawae kana samo man chocolate da yanzu na maka rashin kirki ....</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi mata yace ..har kin iya wani rashin kirki ....</div><div><br /></div><div> Harara ta balla mashi tace. ..kai Malan ni mai kamshi kawae nake kyalewa a garinmu. ..</div><div><br /></div><div> Wae waye wannan mai kamshin Meenalle ...</div><div><br /></div><div> Baki ta washe ..ta fito da zoben dake hannunta tace ...Shi wata irin zuciya gareshi ..ka ganta nan shi ya cirota tana ta jini shaaa...ya saka man a hannu sannan ya saka wani abu ya kulle hanjinshi dashi don kar ya fado kasa ...abun gwanin ban tausayi ......</div><div>ta mayar da zobenta a hannu....</div><div>Ni kuma kasan me na bashi ? ...</div><div><br /></div><div> Ya girgiza mata kai yana murmushi ....</div><div><br /></div><div> Nima zuciyata na bashi amma ni da reza na cirota tana ta jini sae da aka kaini asibiti fa .....nasha wahala sossae kamar zan mace ...ranar da ya tafi ko ..ranar Shege Musa ya daukeni .....</div><div><br /></div><div> Tayi dan karamin tsaki ta mike tsaye. ...nina yi tafiyata tunda ko sannu bara kace man ba ...ta shige dakin hajiya saadiya. .....</div><div><br /></div><div> Kwanciya yayi saman carpet din tare da rufe idonshi yana murmushi</div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°•• </div><div><br /></div><div> Ranar da Ma'aruf ya dawo kamar zayayi hauka daya samu labarin wae an wa Meenalle Aure ?,...Abunda ya dinga maimatawa kenan ....Shin waye Meenalle ta aura ....Bata san yana mutuwar sonta ba ....kuka ya dinga yi ..kamar karamin yaro ...a ranar ya tsani duk wata mace .....</div><div> </div><div> Abba da ya fada mashi sae da yayi dana sanin fada mashi da yayi .....</div><div><br /></div><div> Tun safe ya bar nigeria ....Ya koma india ...don bara ya iya cigaba da rayuwa a gurin ba </div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ......</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>41. to. 42</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Meenalle zo ki mikawa Mus'ab Wannan jug din....Momma ta fada ..</div><div><br /></div><div> Da gudu ta amsa ta shige part dinshi ....yana ta game abinshi ta dire mashi saman cinyarshi ...sannan ta bi falon da kallon ....</div><div><br /></div><div> Hannunta ya janyo ya zaunar da ita barinshi ....Me kike kallo .....</div><div><br /></div><div> Tabe baki tayi tace ...wani gulma na gani ...</div><div><br /></div><div> falon ya bi da kallo sannan yace ...ina kika gani ..</div><div><br /></div><div> wani frame ta nuna tare da fadin ...in ba gulma ba komae na dakin maikamshi sae ace sae an kwaikwaya ....</div><div><br /></div><div> fuska ya bata don ya gaji da labarin Ma'aruf Yace ...Karki kuma man maganar maikamshi anan ...</div><div><br /></div><div> Harara ta balla mashi tace ..don kasan ya fika kyau? ..</div><div><br /></div><div> Cikin tsawa yace ...zan bata maki rai wallahi kika kuma fadin sunanshi anan</div><div> </div><div><br /></div><div> Baka sonshi ne don ya fika tsada? ..ta fada a hankali. .</div><div><br /></div><div> Eh bana sonshi ....shima ya fada ...</div><div><br /></div><div> Idonta ya ciko da kwallah ..sannan ta fara tafiya da baya da baya zata bar dakin ....har ta kai kofa ta tsaya tare da fadin ...Karka kuma man magana ba ruwana da kai ...nima bana sonka ..Bana Sonka tunda baka son Maikamshi .. ....ta fice da gudu tana kuka .....</div><div><br /></div><div> Da sauri ya bi bayanta ....a corridor ya tarad da ita ta hade kai da guiwa tana kuka ...tsugunnawa yayi ...</div><div><br /></div><div> Meena ....ya kira sunanta a hankali ...</div><div><br /></div><div> Banza tayi dashi ....lallashinta ya cigaba dayi amma bata kulashi ba ...so take yace yana son mai kamshinta amma shi ya kasa .....</div><div><br /></div><div> ••°°•• </div><div><br /></div><div> School bag din dake hannunta ta yarda a kasa tare da dukewa tana kallon Momma .....</div><div>Mus'ab ya shigo falon yana ganinta duke yayi sauri zubewa gabanta ...Meena me ya faru .....</div><div><br /></div><div> Momma na zauna tana kallonsu bata ce masu ķomae ba don tasan Halin Meenalle. ..</div><div><br /></div><div> Duk ya rude yana tambayarta amma taki bashi amma ....kamar ya mata kuka ganin yanayinta ya canza ..Please Meena Meke damunki ...</div><div><br /></div><div> Sae da taga dama sannan ta dago tana hararanshi tare da fadin ...Kaini karka dameni ...</div><div><br /></div><div> Ya kwantar da murya . .ba damunki zanyi ba Meena kinji ...fada man zakiyi abunda ke damunki ...</div><div><br /></div><div> Kaini ciwon ice Cream ke damuna .....ta fada tana turo baki ...</div><div><br /></div><div> Mtss ya saki tsaki tare da mikewa. ....takaicin tsakin ya sakata ta fashe da kuka. .....yayi sauri dawowa yana fadin ...tashi ki cire unifoam dib kizo muje</div><div>Bai rufe baki ba ta mike da gudu ta fada daki ....bata fi minti Goma ba ta fito sanye da doguwar riga da karamar hijab ....</div><div><br /></div><div> Hannunsa ta rike ...Suka fice ...</div><div><br /></div><div> </div><div>Ice cream ta kwasa a gurin tare da chocolate kala kala ...sannan suka dawo gida ...bakin gate din gidan tace ya tsaya ....ta fice ta shige wani gida dake facing dinsu ...binta kawae yayi da kallo har ta rufe kofar sannan ya shiga gida ...</div><div><br /></div><div> Tayi Sallama yafi biyar amma ba wanda ya amsa mata... dage labulen falon tayi ta shiga ...mutane zaune a falon da alama magana suke ....</div><div><br /></div><div> ta tsaya tsakiyarsu tana kare masu kallo...wata yar budurwa da ta kasa daurewa tace mata ...Ke lafiya ...</div><div><br /></div><div> Harara ta watsa mata tare da kara yin sallama da karfi ....</div><div><br /></div><div> Wae lafiya ko bakya da hankali ne .....budurwar ta sake fada tare da tasowa ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Bata kulata ba ta sake yin Sallama ....wata daga cikinsu ta amsa sallamar ...sannan Meenalle tace ...Ni makarantarmu an hanani kula wanda bai amsa sallama ba ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div> *Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI.....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div>43. to 44</div><div><br /></div><div> </div><div> wata tace amma bai hanaki shiga gidan mutane ba ..? ..</div><div><br /></div><div> Kallonta tayi ..itama budurwace tana kwance jikin wata daga ita sae bra da pant. ...</div><div><br /></div><div> Ido ta waro sannan ta sake kallon wadda ke tsayen itama duk uwar darin ce.... duka yan matane gidan su kusan 8 amma babu mai kayan kirki. .</div><div><br /></div><div> Miyau ta hade ta samu guri ta zauna tsakiyar tafalon sannan tace ...Ina Mamanku ...</div><div><br /></div><div> Wata daga cikin yan matan ta taso ta zauna kusa da ita tare da dafa ta tana kallonta .....sannan tace ...Ya sunanki ...</div><div><br /></div><div> Keni sunana Meenalle a garinmu anan kuma Meena ...Maikamshi kuma yace man Meenatou ...kinsan duk yafi iya fadin sunana ...shi kuma wancen kilbabben yace man wae Sweet Meenah. ..kinsan ai kilbabben da nake nufi ko?</div><div>Hannunta ta kama tace .. meenah ...</div><div><br /></div><div> Harara ta balla mata ...tace wancen Mayen nawa fa ..ai mayena ne Allah ...ke ni dae bara na tafi ...dama zuwa nayi naga ko zan samu kawa ..sae na ga kuma duk baku sa kaya yan iskane ....ta mike ...</div><div><br /></div><div> Da Sauri ta janyota ta fado jikinta ...tare da matseta a kirjinta...nan da nan idonta ya canza kala ta saka hannunta cikin pant din Meena tana shafata. .</div><div><br /></div><div> Hannun Meenah ta buge tana kokarin kwace kanta. ...amma ta kasa .....kuka ta sake mata tana zaginta tare da kai mata duka amma duk abanza ....</div><div><br /></div><div> Wata ta taso tace. ...Ruky meye haka ki kyaleta bana so ...</div><div><br /></div><div> harara ta sake mata ...ina sonta ne ...</div><div><br /></div><div> Nifa. ...ta tambayeta a fusace ...</div><div><br /></div><div> Idan na gama da ita zanji dake ...ta fada ta shiga ba da shafa. ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Duk falon ba wanda ya kulata kowa harkar gabanshi yake ....daga karshema budurwar daukar meenalle tayi ta shigar da ita daki ta rufe dakin ta cire mata kaya tsaf ...ta dura mata wani abu a baki ....tun daga lokacin Meenalle bata kuma sanin inda take ba ...har sae da ta gama Shafeta tsaf tare da daukarta pic sossae sannan ta fito dakin ta rufota ...</div><div><br /></div><div> °°••°°</div><div><br /></div><div> Mus 'ab kuma tunda ya shiga gida hankalinshi ya ki kwanciya don basu harka da mutanen wancen gidan ...bama su san juna ba...amma wani sashen na zuciyarshi ya tuna mashi Meenalle face ..kila ma ta dade da sanin mutanen gidan sae kawae ya aje mata kayan da suka sawo a dakinta ya shige dakinshi ya kwanta. ...</div><div><br /></div><div> Bata Farka ba sae kusan Laasar ...jikinta ta duba babu kaya wani miyan wahala ta hade tare da share hawayen da suka zubo mata ...ita dae taji seniors na fadin lesbian ...amma bata taba ganin anyi ba ..</div><div>To ko shine wannan ...ta tambayi kanta ...aiko baza manta ba Ustaz ya taba fada masu duk wanda ke lesbian baya shiga aljanna</div><div><br /></div><div> Hawayen ta share ta saka kayanta sannan ta fito har lokacin suna zaune ....tana fitowa budurwar ta taso tana fadin </div><div><br /></div><div> Baby har kin tashi .....</div><div><br /></div><div> Bata ce mata komae ba ta rabe ta fice daga falon ....kwado ta gani sagale jikin kofar ta janyo kofar da sauri tare da rufesu ta baya .....ta tafi da keys din ..</div><div><br /></div><div> Bata fadawa kowa ba abunda ya faru ...haka bata kuma bin ko ta kofar gidan ba ....tun daga lokacin ta hankalta da shiga duk gidajen unguwar .....</div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Dafe kanshi yayi tare da lumshe ido ...Again Raliya ForGod sake me ya kawoki gidan infact me ma ya maidoki nan kasar bayan kin tafi..</div><div><br /></div><div> zama Tayi tare da goge hawayenta ....Ma'aruf Kaine ka maidoni ...bazan iya rayuwa babu kai ba ..Ma'aruf dad dina baya lafiya...amma na baroshi nazo gunka please ka amsheni </div><div><br /></div><div> Tausayi ta bashi don yana ganin yarda take son dade dinta kuma ita kadae ce dashi ....ya lumshe ido tare da zama a kujeran dake facing dinshi ..Me ya sameshi ...ya fada a hankali ....</div><div><br /></div><div> Paralysis ya kamashi ....</div><div><br /></div><div> Ya Salam Raliya ..Allah ya bashi lafiya ...amma raliya ki fahimceni bawae nayi rejecting naki ba san raina ..wallahi Zuciyata tuni tana gurin Meenatou ..ko da na aureki bazan baki farinciki ba ...</div><div><br /></div><div> Na yarda Ma'aruf indae zan zauna dakai. ...please wacece Meenatou zan zauna da ita ka hada mu ...</div><div><br /></div><div> Kinga Meenatou can ...ya nuna mata wani frame dake makale jikin bangoshi ....</div><div><br /></div><div> Sauri tashi tsaye tayi tana nuna Photon. ..Waccen Yarinyar ce Meenatou da kake fada ....waccen yar iskar yarinya ...</div><div><br /></div><div> Tsawa ya daka mata ....Tare da nuna mata hanya ...fice man daga gida ..</div><div><br /></div><div> Indae akan waccen yarinyar ce wallahi sae ka rabu da ita ...komae nake so duniya sae waccen shegiyar yarinyar ta kwace man ...bazata yiyu ba wallahi ...wannan karon bazan bar maki ba ....</div><div><br /></div><div> Ta fice daga gidan da sauri ..mota ta shige ta fizgeta da karfi ta bar unguwar ....</div><div><br /></div><div> </div><div> *Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div>💧💧SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>45 to 46</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Dome Hotel din da suke zaune ta nufa. ..Ruky na kwance bisa gado tare da Precious. ..tajanye mayafin da suka rufa dashi ..</div><div><br /></div><div> ...Ruky muga phone dinki please ....ta fada da karfi</div><div><br /></div><div> Idonta na rufe ta lalubi Phone din ta mika mata ...</div><div><br /></div><div> amsa tayi ta koma falo tana bincikar wayar ....Gallery ta shiga ta fara scrolling pictures din dake cikin ....</div><div><br /></div><div> Murmushi tayi tare da marking din pictures din da take bukata ta tura a tata phone din sannan ta mayar mata ...ta sake fitowa ..</div><div><br /></div><div> Gidan Ma'aruf ta koma ...falo ta iskeshi ...yana ganinta ya mike kamar zaki yayo kanta</div><div>Uban me kika zo nema Kuma. ..ya fada lokacin daya shakare mata wuya ....</div><div><br /></div><div> Da kyar ta mayar da numfashi tare da mika mAta mashi wayarta .....da kyar ta buda baki tace ka duba ciki zaka Meenatou ..</div><div><br /></div><div> Sakinta yayi ya amshi wayar ...jikinshi ya fara kyarma ganin photon Meenalle tare da wata babu kaya jikinsu .....</div><div><br /></div><div> Karya kike raliya ...Ba Meenatou bace forcing dinta akayi ....Why ...ya fada da karfi ...</div><div><br /></div><div> Wayar ya tandara da kasa tare da sulalewa gurin ...ko'ina jikinshi kyarma yake ...da hannu yake nuna mata kofa amma taki fita ...kasa controlling kanshi yayi ya mike tare da shakaranta ....sae da kyar ta samu ta kwaci kanta ta fice da gudu ...</div><div><br /></div><div> .kamar mahaukaci ya fara wurgi da kayan dake tsakiyar falon yana kuka ....</div><div> </div><div> Why Meenatou .... ..Me yasa haka . ...rayuwar da nafi tsana fiye da komae. ...Rayuwar da karuwa mai bin maza ta fiku daraja ....shin bara ki barni da bakin ciki daya ba Meenatou...sae kin hada man da wannan mummunan rayuwa ba kyasona Meenatou ....Me yasa kika bari na tsaneki Meenatou? ....na tsaneki Meenatou ..na tsani duk wata mace yanzu. ....haka ya dinga sabbatu shi kadae. .....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Alhaji Sadee ya dauki Meenalle kasancewar Weekend ne ..gidan Mahaifiyar Abubakar ya nufa da ita. .kasancewar ta sanshi sossae ya saka ta amsheshi hannu biyu ....</div><div><br /></div><div> Ina ka samo wannan kyakykyawar yarinya haka tubarkallah ....ta fada tare da janyo Meenalle ta zaunar da ita gefenta ...</div><div><br /></div><div> Alhaji Sadee yayi murmushi yace. ..Diyar Kanwata ce Hajiya shine na daukota ...</div><div><br /></div><div> Meenalle ta kalleta ...gata dae tsohuwa amma taci kwalliyarta. tace ...tsufa dae yayi shawagi ...ni Kakata bata abun yara amma ke tsohuwa dake kin shafa jan baki ....</div><div><br /></div><div> Sadee ya tashi yace bara yaje ya dawo zaya bar Meenalle anan ....tace mashi to ...</div><div><br /></div><div> Tunda ya tafi take ta mata uban surutu kamar dama sun saba ....nan da nan tashiga ranta ...sae bayan isha'i ya dawo ya dauketa kamar karta tafi haka hajiya taji ...don cewa tayi ya bar Meenalle amma yace tayi hakuri zaya dinga kawota suna gaisawa ....</div><div><br /></div><div> Ranar koda Alhaji Abubakar ya shigo gaidata ...sae da ta mashi firar Yarinyar da Sadee ya zo da ita ....uhm kawae yace mata. ....</div><div><br /></div><div>Duk bayan kwana biyu Sadee zaya sauki Meenalle ya kaita gidan Hajiyar Abubakar. ...</div><div><br /></div><div> Sannu sannu shakuwa ta shiga tsakaninsu sossae wanda in har aka dade Meenalle bata je gidan Hajiya ba to da kanta zata taso tazo ta ganta ta koma ....</div><div><br /></div><div> A lokacinne Hajiya ke fadawa Abubakar tana Shaawar yarinya kamar Meenalle ...har take fada mashi ..da yanzu Aminatunshi tana nan da takae kamar Meenalle ko ta fita ...</div><div><br /></div><div> Cewa yayi shima bai sani ba .....</div><div><br /></div><div> Akwae lokacin da tace mashi ko dae zaya nemi Rabi ya karbo diyarshi don tana bukatar ganin jinin danta ..tunda har yanzu bai kuma samun Haihuwa ba ...</div><div><br /></div><div> Nan ma ce mata yayi bai san inda suke ba ....</div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>47 to 48</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div>°°••°°</div><div><br /></div><div> Kwanci tashi ba wuya har Meenalle ta gama Secondary school ...</div><div> Alokacin ne Mus'ab ya fara nuna mata abunda ke ranshi ...amma fur taki yarda ...har ta manta da wani aure a rayuwarta ...duk wata zaa kaita garinsu gurin su kaka da mamanta har lokacin mamanta bata koma gidansu Musa ba ....haka Musa ya kasa Hakura da Meenalle kullun cikin bala'i yakewa ubanshi ya nemo mashi matarshi ...su duka hankalinsu ba kwance ba ...</div><div><br /></div><div> Wani zuwa da tayi har bangazar musa tayi amma sam bai ganeta ba ...don kwata kwata ta canza hutu da jin dadi sun canzata. ..bara ka taba cewa diyar hausawa bace</div><div>Duk zuwan da zatayi sae ta shiga gidansu Ma'aruf haka zaa ce mata baya nan sannan babu mai numbershi tunda ya tafi bai nemi kowa ba ...haka zata ci uban kukanta har ta taho ...</div><div><br /></div><div> Shima mus'ab kokarin cusa kanshi yake amma hakan bai samu ba ......</div><div><br /></div><div> Lokacin da waec and neco. ta fito a lokacin Alhaji Abubakar ya ce zaya fitar da ita kasar india karatun lawyer ....Alhaji Sadee ya yarda don har lokacin bata san waye ubanta ba ....</div><div><br /></div><div> Cikin saa ta samu Visa cikin sauri ...Su biyun suka kaita indiya tare da mika amanarta gurin wani lecturer amininsu dake can ....</div><div><br /></div><div>°°••°° </div><div><br /></div><div> Batayi wata uku ba ta goge wata wayewa tazo mata ta kara kyau da diri duk wanda ya kallu meenalle alokacin sae ya kuma kallonta</div><div>Kyakykyawa first class ...duk fadin makarantar ba wanda bai san MMA _Meenat Ma'aruf Abubakar_ ...</div><div><br /></div><div> Sun fito daga lecture su kusan Uku a jere ...Shamy ta dauki ihu tare da fadin ....Wow *Mr M*...da sauri suka kalli wani ginin dake kallon makarantar .....</div><div><br /></div><div> Yana rike da glass cup hannushi guda dauke da magzine sannan idonshi sanye da farin siririn glass ....</div><div><br /></div><div> Feena ta daka uban tsalle tana fadin Yaushe ya dawo ...</div><div><br /></div><div> Shamy tace jiya sajan Sadam ke fada man ...Kai *Mr M* ji yanda ya kara uban kyau ....Wallahi Ina mutuwar kaunar ...nayi missing dinshi wallahi.....kissing hannunta tayi tare da Nunashi</div><div><br /></div><div> Sae lokacin Meenalle ta da ido ta kalli wanda suke maganar akae ....</div><div><br /></div><div> Tafi minti ashirin tana kallonshi har sae da soofy ta buga mata littafi a kai sannan ta sauke ajiyar azuciya</div><div>Soofy please meye real name dinshi ....ta fada a hankali ...</div><div><br /></div><div> Tsayawa sukayi suna kallonta cike da mamaki. .....karo na farko kenan da suga Meenalle a wannan yanayin ....kamar tayi kuka tace....Please i need to know ....</div><div><br /></div><div> Shamy tace ...lallae MMA har kin kamu da sauri haka ...ina cika bakin ?...injin yau kin yarda akwae mutumin da yafi Maikamshin kyau ....</div><div><br /></div><div> Please ku fada man dan Allah ...ta kwantar sa murya ...</div><div><br /></div><div> Soofy tace ...kyaji da gulmarki yadda kike da class wancen babanki ne a wannan fannin ...sunanshi *Mr Ma'aruf* .....</div><div><br /></div><div> Ihu ta kurma ta ruga da gudu dakinsu ........</div><div><br /></div><div>Feedohm💞</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI......</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>49 to 50</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Wae Meena me ya sameki kike ta murna ko dae Dady zaya zo .....Shamy ta tambayeta. ..</div><div><br /></div><div> Ido ta waro tare da lumshe ido. . Sirrin Zuci ne ..ba bukatar ku sani .....tana gama fada ta shige toilet ...wanka tayi sannan ta fito ...ta dade tana shafe shafe ...sannan ta dauko wani sabon turare cikin jikkanta ta fesa ta dauko kayan fulani ta saka tare da takalmi mai tsinin ...babu abunda bata saka ba cikin kayan fulani har abunda suke daurawa a kai sae da ta daura ....ta fito ....su shamy suka bita da kallon mamaki har ta fice daga makarantar ...</div><div><br /></div><div> Ba tare da shakkar komae ba ta shige gidan Mr Ma'aruf ....</div><div>.</div><div> Da Sallama ta shige falonshi ....ba kowa ciki sae kamshi dake tashi .....bisa kujera ta samu ta zauna ....ga wani tafkeken hotonshi manna jikin bango a gefen dama. ...tana kara juyawa ta hango abunda ya saka dole fararan hakoranta suka fito ...photon Meenalle ne kafe a gefen haggu anyi rubutu da gold a jiki ...Meenatou ...amma duk ya farfashe..</div><div><br /></div><div> Bata fuska yayi lokacin daya shigo falon ....</div><div><br /></div><div> Me kike bukata ...ya fada lokacin da ya dauki remote ...</div><div><br /></div><div> Shiru tayi tare da kura mashi ido ...jin shirun yayi yawa ya saka ya dago da kanshi .</div><div> </div><div> Suna hada ido yayi saurin janyewa ....</div><div><br /></div><div> Hanya ya nuna mata tare da fadin ...idan kallo ya kawoki ga kofar da kika shigo a bude .....</div><div><br /></div><div> zuwa nayi mu gaisa dakai ...kullun Sae na ganka amma baka taba ko da kulani ba irin dan kallon ma da akeyi a kauda fuska idan an kamaku baka yi man ...ko baka kula mata ?..</div><div><br /></div><div> Ido ya dago yana kallonta sannan ya maida kallonshi ga tv ....</div><div><br /></div><div> Allah sarki ashe magana kadan kake kayi shiru ....ta sake fada a hankali .....wae ma dan rowa ko ruwa bara ka bani ba nazo gidanka...ko ka bani baran karba ba....Mai rowa dae dan wuta</div><div><br /></div><div> Da sauri ya kalli photon Meenalle ..ya tuna lokacin da tazo gidansu ta zauna tana zuba mashi surutunta .. yana rike da ice cream take ce mashi...Gidanku fa nazo Mai kamshi dan rowa bara ka bani ko ruwa ba ..ni bana ma shan abunda kake sha..ko ka bani so daya kawae zan sha ..shima sae kace man please sannan. ...Maikamshi me rowa fa dan wuta ...</div><div><br /></div><div> itama photon ta kalla tare da kallon fuskarshi ...ga mamakinta sae taga hawaye na zuba ....</div><div><br /></div><div> Da sauri ta dawo kujeran dake kusa dashi tana kallonshi cikin rawar murya tace. ..nayi wani abu daya bata maka raine Mr Ma'aruf?..please ka yafe man ...</div><div><br /></div><div> wannan karan ma da sauri ya kalleta ...kije please ..ki tafi ...ya fada a hankali ...</div><div> </div><div>A hankali ta mike ta juya tana tafiya kallo ya bita dashi ...yana ganin zata juyo yayi saurin dauke kanshi ....</div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Har kusan sati daya bata kuma ganin Mr Ma'aruf ba inda yake zama .suna fitowa daga lecture ta ...ta bar su Shamy ta shige gidanshi ...</div><div><br /></div><div> Falo ta zauna tana jiranshi ...amma har kusan minti 39 bai fito ba ...sae dae tana jin nishi sama sama yana fitowa daga dakin dake facing dinta .....tun yana fitowa a hankali har ya fara fitowa da karfi ....zaune tayi tana son taje ta duba kuma tana tsoron ...</div><div><br /></div><div> Jiki ba karfi ta mike tana Sanda ta tura dakin ...Ganinshi tayi kwance kasan tiles ...hannunshi rike da kirjinshi ....da sauri ta ida bude dakin ta dago kanshi tare da daurawa saman kafarta tana girgiza shi ...</div><div><br /></div><div> *Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI.....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>51 to 52</div><div><br /></div><div> Mr Ma'aruf me damunka ...ta fada a rude ...</div><div><br /></div><div> Lunshe ido kawae yake ...ya kasa budesu gaba daya....sannan bakinshi ya kasa furta wata kalma</div><div><br /></div><div> Kuka take iya ranta ..tare da girgiza shi tana kiran sunanshi ....</div><div><br /></div><div> Jin kukan yake cikin ranshi ..sannan so yake ya bude idon yaga wacece amma sam ya kasa ......</div><div><br /></div><div> Ma'aruf ka tashi dan Allah ....</div><div><br /></div><div> Please Ma'aruf ka bude idonka don Allah ka kalleni ...nice Meenallen Maikamshi ..ka tashi bana so na rasa ka wannan karan ....</div><div><br /></div><div> Yana jin Lokacin data fadi Meenalle kokari yake ya bude idonshi ...amma ya kasa ..bakinshi kawae yake motsawa. ..ita kadae ke iya jiyo sautin ..Meenatou ...da yake fada ....</div><div><br /></div><div> Rungumeshi tayi tana kuka ...sannan ta fice daga dakin ganin baya numfashi ta kira security dinshi suka sakashi mota aka wuce dashi asibiti .....</div><div><br /></div><div> Emergency aka shiga dashi ...abu na farko da aka fara bukata shine jini .....Har lokacin Meenalle kuka take .....</div><div><br /></div><div> Amma tana jin ance zaa kara mashi jini ta mike tace a debi nata ...</div><div><br /></div><div> Doctor yace ..Madam baa Fiye dibar jinin mace ba ...amma akwae jinin fresh anan sae a sanya mashi ...</div><div><br /></div><div> Aa Ku debi nawa ku saka mashi na yadda ...ta fada tana kuka. ..</div><div><br /></div><div> Kiyi hakuri ..wanda muke dashi normal yake ...</div><div><br /></div><div> Bana so a gauraya mana jini da na wani ...koda jinina idan kuka diba zaya kare na yarda ki dauka indae Ma'aruf zaya tashi ....</div><div><br /></div><div> Ganin ba yarda zaayi da ita ya saka aka auna nata cikin saa tana da isasshen jinin da zata bashi ...nan da nan aka kwantar da ita gadon da yake kusa da nashi aka diba .....</div><div><br /></div><div> Kafin a saka mashine suka dibi nashi jinin jikinshi aka auna sannan aka kara mashi da na Meenalle ...</div><div><br /></div><div> </div><div> Har 10 dare bai farka ba ...secutity din yace ta tafi zaya kula dashi ...amma hararan data zabga mashi itace amsarshi ....</div><div><br /></div><div> Anan ta kwana ...ganin har da asuba shiru ya saka taje ta samu nurse din tana kuka ta fada masu ...ce mata sukayi karta damu zaya iya tashi ko da yaushe tayi hakuri ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>°°••°°</div><div><br /></div><div> Duk wani test da zaa mashi an gama ...doctor ya kira Meenalle kamar yarda tace mashi ita matarshi ce ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Bayani ya mata mijinta nada Kidney problem ( _Nephropathy_) kuma yayi attacking dinshi sossae dole a saka shi adjoining room zuwa wani lokacin kuma baa bukatar kowa yaje inda yake akwae nurse. din da zasu dinga kula dashi ...idan kuma har lokacin da suka yankar mashi baiyi ba to gaskia sae dae ayi mashi transplant na kidney ...</div><div><br /></div><div> Yarda ta dinga kuka ...shi kanshi likitan sae da yayi nadamar fada mata ...</div><div><br /></div><div> Wata nurse ta tambayi doctor din ko mai ke saurin kawo ciwon ...</div><div><br /></div><div> Rashin bacci na saurin haifawa da mutun ciwon koda ...ke har ciwon sugar da ciwon zuciya duk rashi isasshen bacci na kawosu .....amma indae mutun zaya samu isasshen bacci to lalurar zata iya gushewa ...idan kuma har tayi illar da sae an mata aiki to bayan anyi insha Allah zata gushe ...</div><div>Harta ta ruwa gurbatattu zaka iya daukar ciwon koda ...don haka ya kamata mu dinga kula da rayuwarmun ....</div><div> </div><div> Sannan rashin shan isasshen ruwa ..mussaman lokacin zafi. ...sannan rike fitsari. ..shima yana nakasa koda ...sannan yawan cin gishiri...sannan yawan cin nama shima yana kawo matsalar koda ....haka kuma yawan amfani da magungunan saukaka zafi ko antibiotics ..sanna yawaita shan lemuka masu gas ...kamar coca cola ...lacasera da ire irensu ..</div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Kwananshi 5 A gurin amma ko fardadowa baiyi ba ...duk da an hana kowa zuwa gurinshi amma Meenalle na makale ta glass kullun ...abinci ma sae da likitan yayi mata da gaske take ci ...</div><div><br /></div><div> Maganar makaranta kuwa ta manta da labarinta .....sae a kwana na 6 ne Ma'aruf ya fara bude idonshi ....lokacin tana tsaye inda take zama ta hango yana motsa bakinshi .....</div><div><br /></div><div> Da sauri ta matsa gurin .tare da dafa glass din gurin tana hawaye mai dauke da murmushi ....</div><div><br /></div><div> ..Meenatou ..yake fada a hankali .... Why Meenatou ? Me ya maidoki rayuwa. .ko kinzo kiyi proving abunda kike aikatawa ...Karki kuma zuwa inda nake ...i hate you Meenatou ...Bana son ganinki ...kin cutar da zuciyata da yawa...idan ina ganinki baran iya rayuwa ko kinzo ki kasheni ne Meenatou ..na rokeki karki bari idona yayi tozali dake in dae har soyayyar yarintarki gaskiyane ....hawaye ke bi ta gefen idonshi kamar an bude fanfo ...yayinda da kirjinshi ke sama da karfi</div><div><br /></div><div> Baya tayi da sauri ta jingina da bango ...kanta ya fara juya mata ....</div><div><br /></div><div>*Feedohm*💞</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI.....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div>53 to 54</div><div><br /></div><div> </div><div> Da Gudu ta fice daga asibitin ...dakinsu ta koma ta fada saman carpet tana kuka ....su shamy dake nemanta sukayo kanta suna tambayar inda taje ..ganin ba magana zata masu ba ya saka suka kyaleta sae ta koma ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Bata koma Asibitin ba sae da ta tabbatar ya koma bacci ..sanna taje tana lekenshi tana hawaye ...ji tayi an dafa kafadarta ta juyo da sauri.</div><div><br /></div><div> Ganin Nurse din dake taimaka mashine ya saka ta goge hawayen ...</div><div><br /></div><div> Kiyi hakuri Mrs Ma'aruf ..mijinki zai samu sauki Soon ....</div><div><br /></div><div> daga mata kai tayi tare da share hawayen ...taji dadi sossae ko ba komae yau an kirata da Mrs Ma'aruf .....</div><div><br /></div><div> Murmushi tayi mata sannan tace ..doctor yana bukatar magana dake ....</div><div><br /></div><div> Binta tayi suka shiga office dinshi ...ya zaune da uwayen takaddu gabanshi ....yace ta zauna ....</div><div><br /></div><div> Mrs Ma'aruf nasan dae ke musulmace ..kuma zaki yarda da kaddara mai kyau ko mara kyau. ....</div><div><br /></div><div> Kallonshi kawae take tana hawaye ...so take ya fada mata kai tsaye abunda yake son fada ...amma sae da ya mata waazi da yake balarabene sannan ya fada mata gaskia sae sun wa Ma'aruf dashen koda ..don duk yarda suke tunanin abun ya wuce nan .....</div><div><br /></div><div> Tun da yake maganar take kuka har ya gama sannan yace dole ta kira yan uwanshi domin ciki wani zaya bashi kidney daya ...</div><div><br /></div><div> Meye amfani doctor? </div><div>.komae zaa bukata na yarje a cire nawa indae Ma'aruf zaya tashi ...ko da zuciyata a cire a saka mashi ..Doctor nafi sonshi da kaina a duniya ...ku shirya duk abunda zaa kashe zanje na kawo ...ina so ayi mashi aiki ya samu sauki da wuri ....tana gama fadar haka ta mike tana kuka ...</div><div><br /></div><div> Dady ta kira tace tana bukatar kudi masu yawa ...babu musu ya turo mata 10 million. ..da ta ga kamar bara su isheta ba ta fitar da sarkar gold dinta da Alhaji Abubakar ya sawo mata da wata sallah ...ta sayar naira million 5.5</div><div>Wanshekare da safe ta hada kudin ta kai masu ...naira million 9 kadae suka amsa suka bata sauran. ..ko a ranar sae da doctor yayi encouraging nata aka ta kira wani ko mahaifiyarshi ta bashi wanda baya da wata damuwa a tare dashi ...amma ta saka mashi kuka ...dole suka fara preparing cire tata daya a saka mashi ...duk wani aune aune da yakama suyi sae da sukayi ...suka tabbatar idan an cire tata daya wadda aka barta zata iya fuctioning sossae a jikinta ...sannan aka shiga dasu dakin tiyata .....</div><div><br /></div><div> </div><div> *4 Hours*</div><div><br /></div><div> Aka fito gangaro su sannan aka kaisu adjoining room su biyu aka jerasu ......</div><div><br /></div><div> Ta fishi jin jiki sossae don har sae da ta kwana biyu bata farfado ba ...shi kuwa kwana daya ya farka. ..tana kwance kusa da gadonshi ...ya kura mata ido. ...har doctor ya shigo. ....</div><div><br /></div><div> Ya mashi alluran da ya kamata sannan ya fice don baa cika son a takura masu da magana ba ....</div><div><br /></div><div> </div><div> Ranar da ta farka tana bude ido suka hada ido ...murmushi ya sake mata tare da lumshe ido ...ita murmushin ta maida mashi ..sannan ta kawar da kanta gefe guda ta goge hawayen dake neman zubo mata .....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Lokacin da likitan ya shigo ..ya sameta ta farka shi kuma yana bacci ....</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi mata yace ...Congrat Mrs Ma'aruf ...yanzu hankali ya kwanta ya samu sauki ko ...</div><div><br /></div><div> Murmushi tayi ta lumshe ido....a haka ya mata allura ya fice ...</div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Satinsu biyu acikin asibitin suka samu sauki ...sae dae har lokacin suna daure da belt don sae yayi wata shidda zaa cire ....</div><div><br /></div><div> Haka har lokacin Ma'aruf bai san taka maimai wanda ya bashi kidney ba. ..don tun kafin ayi aikin ta roki Doctor din da kar ya fada mashi ita ta bashi ....</div><div><br /></div><div> Meenalle na kwance bisa gado Ma'aruf ya fito daga toilet dinshi sanye da jallabiya ...kallonta yayi dauke da murmushi yace ...</div><div><br /></div><div> Fateema ya jikin ... _kamar yarda ta fada mashi sunanta_</div><div><br /></div><div> Murmushi tayi tace Alhamdulillah....</div><div><br /></div><div> Good ...ga abinci nan an kawo ki tashi kinji ko ...</div><div><br /></div><div> Tashi tazo yi amma ta kasa ...ya matso tare da dagota ta ya jingina ta da kirjinshi kafin ya dauko filo ya saka mata abayanta ya janye jikinshi ...yana fadin Sorry Sister kinji</div><div>Zama yayi yana bata abincin har sae da ta dauke kai sannan ya tashi yayi sallah ....</div><div><br /></div><div> Da yake ya fita lafiya kuma doctor yace mashi tare akayi masu aiki. ..shi yasa yake tausayinta da yaga shi har ya samu sauki amma ita ba wani sauki sossae ....</div><div><br /></div><div> A wani bangaren na zuciyarshi ...yana jinta sossae matsalar ya riga ya saka mata tsanar soyayya ....</div><div><br /></div><div> Idan tana bacci bashi iya dauke idonshi a kanta ...haka idan yana bacci bata iya dauke idonta daga kallonshi ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Ana Gobe zaa sallamesu ...doctor ya shigo ....Ma'aruf yayi ta rokanshi akan kar ya bar asibitin sae ya fada mashi wanda ya bashi koda ...</div><div><br /></div><div> Doctor ya saci kallon Meenalle yaga idonta na kanshi ...sannan ya mai da kallonshi ga Ma'aruf ....yace ...gobe zan fada maka ...ya fice ...</div><div><br /></div><div> Yana fita ta bi yanshi ta sameshi da kuka kar ya fada mashi ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Yace Mrs Ma'aruf mai yasaka baki san yasan ke kika ceceshi? </div><div><br /></div><div> Bakomae doctor dan Allah karka fada mashi ..</div><div><br /></div><div> wannan ba hujja bace Aminatu ...dole a nuna mashi wanda ya bashi ...</div><div><br /></div><div> Zaa nuna mashi amma bani ce zaa nuna mashi ba doctor</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div>55 to 56</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Me yasa bake ba Aminatu Abubakar? ...sannan wacce kike so a nuna mashi ...</div><div><br /></div><div> Doctor ni zan kawota ..kawata shamsiyya ita nake so ka nuna mashi ..ka taimakeni ...ta fada cikin kuka. .</div><div><br /></div><div> Me yasa to Mrs Ma'aruf?..</div><div><br /></div><div> Wannan Sirrin zuci ne ....</div><div><br /></div><div> Wayarta ta fito ta kira Shamy tace ta zo ta yanzu ta mata kwatancen asibitin da suke .....</div><div><br /></div><div> bata fi 10 mints ba sae gata ...tana zuwa doctor ya mata bayanin abunda suke so tayi ...</div><div><br /></div><div> </div><div>Dadi kamar ya kasheta don dama tana mutuwar son Mr Ma'aruf ..kuma ta tabbata idan aka ce ita ta bashi to babu abunda bara ya iya yi mata ba ....don doki kasa barin asibitin tayi sae da wata nurse tace mata baa kwana ba wani dalili sannan ta tafi ...</div><div><br /></div><div>°°••°° </div><div><br /></div><div> Murmushi ya sake yana kallon Meenalle sannan yace ....yau zan huta da tashin dare da kukanki ..</div><div><br /></div><div> Hararansh tayi lokacin da take neman maida hawayen da suka zobo mata tace ...ni kuma zanyi kewarka ..</div><div><br /></div><div> Nima ai zanyi kewarki Fateema wasa nake maki kinji ko ...karki bari hawaye ya kara fitowa daga kyawawan idanuwannan ..</div><div><br /></div><div> Lumshe ido tayi tace ...Da Zan iya da tuni na tsaidasu Ma'aruf ......</div><div><br /></div><div> Yauwa ga doctor nan ...ya fada lokacin da ya mika mashi hannu ...lokaci guda kuma ya bata rai yana cewa ...ya na ganka kai daya ..tana ina ? </div><div><br /></div><div> Doctor yayi murmushi tare da daga murya yace ...Mrs Ma'aruf ...</div><div><br /></div><div> Da sauri Meenalle ta kalleshi lokacin da gabanta ya yanke ya fadi ...ganin ya kira wata da sunan da ta dade tana mafarki...Sunan da tun tana karama ta so ta amsa sunan ...hawaye suka zo mata. ..tayi saurin Mikewa daga kujeran da take ta juya da niyar ta bar dakin...</div><div>Hannunta taji an rike da sauri. ..ta juyo tana kallon Wanda ya rike mata hannu ....</div><div><br /></div><div> Kanta ta sadda ta kasa cigaba da tafiyar ganin Ma'aruf rike da hannunta. ...</div><div><br /></div><div> Ina zaki Fateema bara ki tsaya kiga wadda ta taimakeni ba ...lokacin da lumfashina ya nemi ya bar jikina dalilin wata?....ya fada yana kallonta</div><div><br /></div><div> Shamy ta shigo taci uwar kwalliya ...</div><div><br /></div><div> Meenalle ta girgiza kai tana toshe bakinta ...</div><div><br /></div><div> Ma'aruf yace ..Doctor baka ga wata yarinya ba Wadda ta kawoni Sunanta Meenatou ..ko ba ita ta kawoni ba ... </div><div><br /></div><div> Doctor ya nuna Shamy yace ..Shamsiyya ce ta kawoka kuma ita ta baka kidney dinta daya ...bansan wata mai suna Meenatou ba anan ...</div><div><br /></div><div> Da sauri Meenalle ta kwace hannunta ta fice daga dakin tana kuka. ...Ma'aruf duk dokin ganin wadda ta taimaka mashi da yake ..sae da ya yunkura zaya bita amma doctor ya tareshi ....lumshe ido yayi duk da ba karan kukan yake ji ba amma yana jin zafin kukanta a ranshi ....</div><div><br /></div><div> Gurin Shamy ya juyo yana mata godiya sae washe baki take</div><div>Yace ...kin taimaki Rayuwata Shamsiyya ..banda bakin da zan gode maki ...amma ina neman Alfarmar ki aureni a lokacin ne zan nuna maki tsantsar godiyar da nake maki ....</div><div><br /></div><div> Mr Ma'aruf. ..ta fada lokacin da take washe baki ...da gaske zaka aureni ...</div><div><br /></div><div> daga mata kai yayi yana kallon gadon Meenalle ...</div><div><br /></div><div> Shi daya kamata ya nuna zakewa amma itace ta nuna zakewa a gurin ...</div><div><br /></div><div> Tare suka koma gidanshi...sae rawar kai take mashi ...kokari yake ya sakata zuciyarshi amma ina ..babu wani babi face na Meenalle ....</div><div><br /></div><div> Sae dare ta tafi shima sae da ya lallabata sannan ...</div><div><br /></div><div> Da safe ya yanki ticket ....sannan ya kira Shamy sukayi bankwana ta bashi address din iyayenta ya tafi akan bara ya dawo ba sae angama maganar komae akansu ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI ....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div> _Godiya ba adadi gareku .....💞_</div><div><br /></div><div>57 to 58</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Ina labarin Musa?</div><div><br /></div><div><br /></div><div>Da musa ya matsawa Malan sani lamba sae an nemo mashi matarshi ...</div><div><br /></div><div> Malan sani ya rasa yarda zayayi ...gashi abokanshi na bashi shawarar ya shigar da kara don Uwar Meenalle da kakarta su suka boyeta ....</div><div><br /></div><div> Alokacin baida ko sisi ga musa ya addabeshi ...dole ya sayar da gidan da suke ciki _Gidan Rabi_...ya shigar da karar ...</div><div><br /></div><div> Su kaka na zaune tsakar gida aka kawo masu sammaci daga kotu ....</div><div><br /></div><div> Wae ana tunanin sun sace matar Musa ....ana nemansu ranar litinin akotu ...</div><div><br /></div><div> Haka suka shirya suka tafi kotu da safe ...aka karanto masu da karar da akayi akansu ..tare da tambayarsu sun san da zance ...</div><div><br /></div><div> Kakata ta murje ido tace bata san da zancen ba kuma sae an fito mata da diya ....</div><div><br /></div><div> Da Alkali yaga kamar zaa rainawa kuto hankaline sae ya kori karar .</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Da yake akwae kudin gidan sae Malan sani ya daukaka kara tare da daukar lauya ....</div><div><br /></div><div> Lokacin da suka shiga kotun ...anan ne aka rufe kaka don ana tunanin ita ta sace kaka ...aka rufeta sati biyu a sail ....</div><div><br /></div><div> Ran Rabi in yayi dubu ya tashi ...taje har kano tasami Alhaji Sadee ta fada mashi</div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Meenalle tun da ta koma hostel ba abunda take sae kuka ....Friends dinsu sunyi lallashin duniya amma taki kulasu </div><div><br /></div><div> Kwata kwata rayuwar garin ta fita ranta. ...haka shamy bata da Labari sae na Ma'aruf ...wata sa'in idan suna waya sae dae Meenalle ta bar gurin tana kuka .....Sannan taki fadawa Shamy din dalilin da ya saka take hakan ...</div><div><br /></div><div> Sae a hankali sannan ta fara komawa dae dae har ma ta fita lecture ...</div><div><br /></div><div> Da marece ta fito daga lecture ta daga idonta ta kalli benen Ma'aruf kamar yadda take kullun ...suka hada ido ....alama ya mata da ta jirashi yana saukowa .....gurin tayi tsaye kanta na kasa har ya karaso ...</div><div><br /></div><div> Dariya ya sake bayan ya leka fuskarta tare da lakutar Hawayen yakae baki ....Bara naji ko hawayen nada zakine shi yasa basu wahalar fitar ....</div><div><br /></div><div> Murmushi tayi ta saka hannu zata share ...yayi saurin saka hanky dinshi ya share mata yana girgiza kai ......</div><div><br /></div><div> Guri ya samu ya zauna ...yana tambayarta ...Meke faruwa Fateema ...ko har yanzu baki warke ba ....</div><div><br /></div><div> Girgiza mashi kai tayi tare da juyawa bangare guda ....</div><div><br /></div><div> To me yasaka kike kuka ? ...Wani ne ya sakaki kukan? ..ya sake fada a hankali yana leken fuskarta ..</div><div><br /></div><div> Kamar tace Kaine Ma'aruf ...amma ba dama ...sae dae girgiza mashi kai tayi ...</div><div><br /></div><div> To kiyi hakuri kinji Fateema ...bana son ganin hawayenshi ko kadan ...kin koma gida bayan kin warke? ...</div><div><br /></div><div> Nan ma girgiza mashi kai tayi tare da share hawayen dake binta .....</div><div><br /></div><div> Kinci abinci ? ....ya tambayeta lokacin da yake kallon bakinta ...</div><div><br /></div><div> Uhm ...tace mashi ..</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi yace ban yarda ba. ..tashi muje kinji ko ...kamar kin taba zuwa gidana can baya ...kece ? </div><div><br /></div><div> Daga kai tayi tana murmushi ....</div><div><br /></div><div> Hararan wasa ya sake mata yana fadin. ..lokacin kinje kallona ne ko kinje ki saka man ciwon da zamu hadu asibiti .....</div><div><br /></div><div> bata ce komae ba sae murmushin da tayi..wanda har hakoranta suka bayyana</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI ....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div> _Godiya ba adadi gareku ..... Wadanda suka man magana ban mayar masu ba ...su gafarceni ba yarda na iya ne ....💞_</div><div><br /></div><div> *Wannan page din kyautane ga Masu Yara kanana Allah ya raya Mana ku bisa turbar addinin musulunci ya saka masu tausayi da imani🙏🏻*</div><div><br /></div><div>57 to 58</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Ina labarin Musa?</div><div><br /></div><div><br /></div><div>Da musa ya matsawa Malan sani lamba sae an nemo mashi matarshi ...</div><div><br /></div><div> Malan sani ya rasa yarda zayayi ...gashi abokanshi na bashi shawarar ya shigar da kara don Uwar Meenalle da kakarta su suka boyeta ....</div><div><br /></div><div> Alokacin baida ko sisi ga musa ya addabeshi ...dole ya sayar da gidan da suke ciki _Gidan Rabi_...ya shigar da karar ...</div><div><br /></div><div> Su kaka na zaune tsakar gida aka kawo masu sammaci daga kotu ....</div><div><br /></div><div> Wae ana tunanin sun sace matar Musa ....ana nemansu ranar litinin akotu ...</div><div><br /></div><div> Haka suka shirya suka tafi kotu da safe ...aka karanto masu da karar da akayi akansu ..tare da tambayarsu sun san da zance ...</div><div><br /></div><div> Kakata ta murje ido tace bata san da zancen ba kuma sae an fito mata da diya ....</div><div><br /></div><div> Da Alkali yaga kamar zaa rainawa kuto hankaline sae ya kori karar .</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Da yake akwae kudin gidan sae Malan sani ya daukaka kara tare da daukar lauya ....</div><div><br /></div><div> Lokacin da suka shiga kotun ...anan ne aka rufe kaka don ana tunanin ita ta sace kaka ...aka rufeta sati biyu a sail ....</div><div><br /></div><div> Ran Rabi in yayi dubu ya tashi ...taje har kano tasami Alhaji Sadee ta fada mashi</div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Meenalle tun da ta koma hostel ba abunda take sae kuka ....Friends dinsu sunyi lallashin duniya amma taki kulasu </div><div><br /></div><div> Kwata kwata rayuwar garin ta fita ranta. ...haka shamy bata da Labari sae na Ma'aruf ...wata sa'in idan suna waya sae dae Meenalle ta bar gurin tana kuka .....Sannan taki fadawa Shamy din dalilin da ya saka take hakan ...</div><div><br /></div><div> Sae a hankali sannan ta fara komawa dae dae har ma ta fita lecture ...</div><div><br /></div><div> Da marece ta fito daga lecture ta daga idonta ta kalli benen Ma'aruf kamar yadda take kullun ...suka hada ido ....alama ya mata da ta jirashi yana saukowa .....gurin tayi tsaye kanta na kasa har ya karaso ...</div><div><br /></div><div> Dariya ya sake bayan ya leka fuskarta tare da lakutar Hawayen yakae baki ....Bara naji ko hawayen nada zakine shi yasa basu wahalar fitar ....</div><div><br /></div><div> Murmushi tayi ta saka hannu zata share ...yayi saurin saka hanky dinshi ya share mata yana girgiza kai ......</div><div><br /></div><div> Guri ya samu ya zauna ...yana tambayarta ...Meke faruwa Fateema ...ko har yanzu baki warke ba ....</div><div><br /></div><div> Girgiza mashi kai tayi tare da juyawa bangare guda ....</div><div><br /></div><div> To me yasaka kike kuka ? ...Wani ne ya sakaki kukan? ..ya sake fada a hankali yana leken fuskarta ..</div><div><br /></div><div> Kamar tace Kaine Ma'aruf ...amma ba dama ...sae dae girgiza mashi kai tayi ...</div><div><br /></div><div> To kiyi hakuri kinji Fateema ...bana son ganin hawayenshi ko kadan ...kin koma gida bayan kin warke? ...</div><div><br /></div><div> Nan ma girgiza mashi kai tayi tare da share hawayen dake binta .....</div><div><br /></div><div> Kinci abinci ? ....ya tambayeta lokacin da yake kallon bakinta ...</div><div><br /></div><div> Uhm ...tace mashi ..</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi yace ban yarda ba. ..tashi muje kinji ko ...kamar kin taba zuwa gidana can baya ...kece ? </div><div><br /></div><div> Daga kai tayi tana murmushi ....</div><div><br /></div><div> Hararan wasa ya sake mata yana fadin. ..lokacin kinje kallona ne ko kinje ki saka man ciwon da zamu hadu asibiti .....</div><div><br /></div><div> bata ce komae ba sae murmushin da tayi..wanda har hakoranta suka bayyana</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>59 to 60</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div> Haka kawae yake jin farinciki idan yana tare da ita ...tare suka jera har cikin gidanshi ...ya dauko mata abinci ..tare da lemon ..sannan ya zauna yana tsokanarta har ta koshi ....</div><div><br /></div><div> Komae nata na burgeshi ...bata tafi ba sae da ta gyara mashi gidan sae kamshi yake sannan ta tafi ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Bayan ta tafi ya kira Shamy ya mata bayanin komae ...yace mata duk wata magana an riga an gamata ...iyayenshi sunje gidansu an kuma bashi ita .....</div><div><br /></div><div> Haka ta koma hostel Meenalle na kwance ta fada kanta sae hauka take ..ta kusa zama matar Mr Ma'aruf ....</div><div><br /></div><div> Kamar saukar aradu Meenalle ke jinta ...har ta gama ta haukanta bata motsa ba ...sae da ta leko fuskarta tace mata ...You're not happy MMA</div><div><br /></div><div> Am very happy Shamy ...Allah ya sanya albarka ...tana gama fadar haka ta fice .....</div><div><br /></div><div> Ma'aruf dinne yazo ya kira Shamy ...tana zaune bisa wani dutsi tana hango su....sae wannan iyayi yi Shamy take .....</div><div><br /></div><div> Dukar da kanta tayi daga barin kallonsu ...motsi taji a bayanta ...ta dago a tsorace ....Ma'aruf ta gani ya harde hannuwa ya zuba mata ido ....</div><div><br /></div><div> Saurin juyar da fuskarta tayi tana kakaro murmushi ...</div><div>Fateema. ..ya kira sunan a hankali ...akwae abunda ke damunki kawae baki so na sani ....</div><div><br /></div><div> Allah ba komae Mr Ma'aruf kawae kaina ke ciwo na fito na sha iska. ..ta fada tana murmushin yake ..</div><div><br /></div><div> A nan zaki huta ...? ..ta so muje na kaiki inda ciwon kan zaya tafi kinji ko ..? ..</div><div><br /></div><div> Shamy ta iso gurin tare da dafa Meenalle tana fadin ...Hubby wallahi mu kanmu bamu san Meke damun MMA ba ...</div><div><br /></div><div> Ido ya waro ..dama kin santa ne ..</div><div><br /></div><div> Yeah friend dinta ce... Shamy ta fada tana murmushi .</div><div><br /></div><div> Tashi muje to kinji ko ...ki bar nan gurin akwae sanyi da yawa kinji ko ...rigar sanyin dake jikinshi ya ciro tare da rufa mata ...sannan Shamy ta dagata suka jero tare ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Ma'aruf ..yace su shiga mota bara su tafi a haka ba ...Shamy mai miji aka shige gaba ....ta glass din yake kallon meenalle ...duk wani motsi da zatayi a idonshi take ...yaso ace itace ta bashi kidney don ya masifar tausayin yarinyar ...sannan kallonta yake Meenalle komae tayi burgeshi take ....</div><div><br /></div><div> Wani guri ya kaisu ...ya masu shopping sossae ...aka saka a bayan mota ...sanna ya dauko wasu kananan ledoji guda biyu ...ya mikawa Shamy daya ..ta karba tana godiya ....</div><div><br /></div><div> Sannan ya mikawa Meenalle guda ...ta saka hannun dama zata karba ...ya kurawa zoben dake hannunta ido sannan yaki sakin ledar ....</div><div><br /></div><div> Da Sauri ta janye hannun ta maidasho baya ...</div><div><br /></div><div> Yaso ya ce ta fito da zoben ya gani amma sae wata zuciya tace mashi ba abunda yake tunani bane ...don yanzu tuni zoben yamata Meenalle kadan ...haka ya kauda tunanin zoben a ranshi ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div>°°••°°</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Lokacin Alhaji Sadee na tunanin case din karamine ...ko Alhaji Abubakar bai fada mawa ba ...ya shirya ya tafi ...</div><div><br /></div><div> Ranar da sukaje kotun ..Alkali ya tambayi Rabi shin da saninta aka aurar da Meenalle .....</div><div><br /></div><div> Rabi tace eh da saninta aka aurar da Meenalle ..</div><div><br /></div><div> Alkali ya tambaya ..shin ko ubanta ya san da auren ? ..</div><div><br /></div><div> Tace. ..aa ubanta baisan da auran ba domin ba gurinshi ta tashi ba. ...</div><div><br /></div><div> Alkali yace a kira mashi Wadanda aka daura auren gabansu ....babu shamaki malan sani ya kirawo har wanda ya daura auran ...Alkali yace aure ya dauro kuma ba wanda zaya warware auren ba tare da wata kwakwkwaran hujja ba ..</div><div><br /></div><div> Alkali ya nemi a kira Meenalle ...Alhaji Sadee yace sam bata kasar ...</div><div><br /></div><div> Alkali yace to nan da sati biyu a kawo Meenallen ...sannan aka sake kaka suka tafi da ita ..</div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Hajiyar Abubakar ta tasa Abubakar dole sae ya karbo diyarshi don tana bukatar ganin jikarta ...</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi yace shi yanzu baisan inda zai ga su Rabi ba ....sae dae tayi hakuri ...</div><div><br /></div><div> Kuka ta saka mashi amma ya tashi ya fice daga gidan ...</div><div><br /></div><div> Lokacin tayi nadama sossae ...kuma Meenalle ta bar mata son diya mace ...don ta gane Rahamace ...itama so take ta ga jikkarta ko da ace musakace bama mai lafiya ba ...</div><div><br /></div><div> </div><div>*Feedohm💞*</div><div>SIRRIN ZUCI......</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦Talented writers forum💦</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>61 to 62</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Alhaji Sadee ya kira Meenalle yace ta taho gida nan da sati biyu ...</div><div><br /></div><div> Taji dadi sossae ko ba komae dama garin ta isheta ...</div><div><br /></div><div> Ranar ta fito zata tafi asibiti ...taga motae Ma'aruf inda yake ajeta idan yazo gun Shamy ....</div><div><br /></div><div> Hanya ta canza tayi uban zagaye ...ta fice daga School din ...Taxi ta tara ta kaita asibitin ..</div><div><br /></div><div> Tana zaune doctor na mata bayanin yarda zata kula da lafiyarta idan ta koka gida ...kanta na bisa table din doctor din .</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Magunguna ya rubuta mata ...wanda zatayi amfani kafin ta dawo ...mika hannu tayi zata karba taga an karba ....</div><div><br /></div><div> Lumshe ido tayi ba tare da ta dago ba ....kujera yaja ya zauna kallon doctor din ...</div><div><br /></div><div> Ya jikinta ...ya fada tare da kallonta ...</div><div>Alhamdulillah ...bata da matsala ...doctor ya fada ..</div><div><br /></div><div> Lafiya lau kuma ta zo asibiti ...Ya kalleta. ..Fateema ki fadawa doctor abunda ke damunki ...</div><div><br /></div><div> Babu komae ...ta fada ahankali ...</div><div><br /></div><div> Doctor yace ...Tazo ne tana so ta koma gida shine na rubuta mata maganin da zatayi amfani dashi ...sannan bara tasha wani ruwa ba sae swan har tsawon wata shidda ....</div><div><br /></div><div> Ido ya lumshe sannan ya mike. . tashi muje Fateema. ..</div><div><br /></div><div> Ba musu ta mike suka fice tare da yi ma doctor din godiya. ...</div><div><br /></div><div> Gaban mota ya bude mata sannan ya zagaya ya shiga .....kura mata ido yayi yana karantarta ...</div><div><br /></div><div> Fateema. .....</div><div><br /></div><div> Kamar tace mashi Meenatou dae ..amma babu dama ...sae dae ta juyo da fuskarta gefenshi idonta na rufe. ..</div><div><br /></div><div> Ba da wata manufa ba ya kamo hannunta ya rike. ..Fada man meke damunki ...</div><div><br /></div><div> Girgiza kai tayi idanuwanta suka ciko da kwalla ...</div><div><br /></div><div> Babban yatsanshi ya saka ya share kwallan ...sannan ya tada motar hannunta na rike cikin nashi suka fice daga asibitin .....</div><div><br /></div><div> Kafin ya maida ta makaranta jikinta ya hau rawar sanyi ...</div><div><br /></div><div> Ya shafi wuyanta ...ya dauki zafi kamar wuta ...kwantar mata da sit din yayi baya ta kwanta ...sannan ya wuce da ita gidanshi ...tun kafin su isa ya kira Shamy yace ta tarad dashi gidanshi .....</div><div><br /></div><div> Suna isa ya yi Parking ya fita ba tare da ya mata magana ba ya dauketa ya shigar da ita gidan ...dakin shi ya kaita ya kwantar da ita saman gadon ...</div><div><br /></div><div> Sannan ya fita ya shiga kitchen ya hado mata coffee ....lokacin da ya dawo idonta a. rufe ...sae yayi zaton ko bacci take ...ja aje coffe din ya gyara mata kwanciya sannan ya rufe ta da bargo ya fita daga dakin ya koma falo ..</div><div><br /></div><div> Yana fita ta bude idonta tare da tashi zaune ..tana kallon dakin ...duk kusurwar dakin hoton Meenalle ne ...wani photon ma bata san inda ya dauketa ba ....</div><div>Kanta ta daura saman cinyarta tana kuka ....hannu ta saka ta janyo pillown dake gefenta ....</div><div><br /></div><div> Ribbon din da ta bashi tun tana yar yarinya ta gani cikin wani glass cover an Rubuta _*My Heartcherry*_.. _*They say you only fall in love once, but that can't be true... Every time I look at your Pictures, I fall in love all over again Meenatou*_</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Glass din ta dinga shafa tana hawaye ...ita kadae .....Motsin magana ta taji ya saka ta yi saurin komawa ta kwanta ..</div><div><br /></div><div> Tana jin lokacin da yake cewa Shamy ta shiga dakinshi friend dinta na ciki .....</div><div><br /></div><div> Ta turo dakin ta shigo tana fadin ..Meena meke damunki . .ta zauna bakin gadon tare da dago kanta. ...</div><div><br /></div><div> Ayya ...me kike wa kuka kuma ...dan Allah ki daina Meena ...tashi ki sha magani zaki samu sauki ....ta fada kamar zatayi kuka ..</div><div><br /></div><div> Ma'aruf ya shigo yana tambayar ta farka ...amma sae ganinta yayi jikin Shamy tana kuka. ...</div><div><br /></div><div> Bara ya iya jin kukan ba shi yasa ya juya da sauri ya fice daga gidan ....</div><div><br /></div><div> Da kyar Shamy ta samu tayi shiru ta hada mata ta hada mata Coffee sannan ta bata maganin da Ma'aruf din ya bata ...ta koma tayi bacci ...</div><div><br /></div><div> Shamy ta kira Ma'aruf din tace yana ina. ..</div><div><br /></div><div> Ce mata yayi ...Ina Fateema ...</div><div><br /></div><div> Da yake ta san Fateema yake cema mata ...sae tace mashi tayi bacci ..</div><div><br /></div><div> Ya sake ajiyar zuciya yace gashinan zuwa. ......</div><div><br /></div><div> ko da ya dawo ce mata yayi ta tsaya su kwana anan ta kula da ita ....</div><div><br /></div><div> Murna tayi don ko ba komai yau zasuyi fira sossae da shi ...</div><div><br /></div><div> Amma sae taga hankalinshi sam ba gareta yake ba. ...duk minti biyu ..zaya leka dakin yaga ko ta tashi ...</div><div><br /></div><div> Meenalle kuwa ta dade da tashi amma taki bude idonta ...tana jin lokacin da suka shigo da shamy ya daga bargon tare da shafar wuyanta yaji ko zazzabin ya sauka ...</div><div><br /></div><div> Shamy ta wani hade rai tana fadin Meye zaka wani tabata bayan ba aurenta zakayi ba ...ni bana son wannan wulakanci ..</div><div><br /></div><div> Shima daure fuska yayi yace. ..bakya ganin bata lafiyane. .</div><div><br /></div><div> Don bata lafiya sae ka tabata har da wani lumshe ido ..me kake nufi ...</div><div><br /></div><div> Bai ce mata komae ba don baya son ganin fushinta ...sae towel daya mika mata tare da fadin ...please ki jikashi ki dinga goga mata a jikinta ..</div><div><br /></div><div> Hararanshi tayi tace..tunda har ka iya taba wuyanta wannan ma bara ya maka wuya ba...</div><div><br /></div><div> Kwantar da murya yayi yace. . Please Shamy kiyi mata mana. .friend dinki ce fa ...</div><div><br /></div><div> Bafa zanyi ba ..ta fada kai tsaye ..</div><div><br /></div><div> Ok ...to fita ...ya nuna mata kofa ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>?</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI ......</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦Talented Writers Forum💦</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>63. to. 64</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Tsaye tayi tana kallonshi cike da mamaki ...tunda take bata taba ganin ya daure mata fuska ba sae yau ...kullun cikin lallashinta yake ...</div><div><br /></div><div> Tsawa ya daka mata lokacin da ya fito daga toilet rike da bucket a hannu ...</div><div><br /></div><div> Baki ji abunda nace maki ....Get out ...ya nuna mata kofa ...</div><div><br /></div><div> Fita tayi a fusace tare da banko masu kofar ...shima karamin tsaki yaja ...sannan zauna gefen gadon tare da cire bargon .....</div><div><br /></div><div> har ya kai hannu zaya daga mata riga ya tsaya cak yana kallon fuskarta ...mikewa yayi ...ya rasa ta yaya ma zai mata ...tana jinshi sae dukan hannunshi yake ...sannan ya mike ya fita daga dakin ...he decide yaje asibiti ya kira wata nurse tazo ta mata ya bata kudi</div><div><br /></div><div> A falo ya wuce Shamy zaune ta kasa fita daga gidan ....tana ganin ta fito ta tareshi ...</div><div><br /></div><div> am sorry Habibi ...</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi tare da kallonta bai ce mata komae ba ...</div><div><br /></div><div> Kayi hakuri Please bara naje na mata kaji dan Allah...Please Hubby ...</div><div><br /></div><div> Kofar dakin ya nuna mata tare da zama kujeran falon ....</div><div> </div><div> Da Sauri ta shiga dakin. ..ta tarad da Meenalle zaune tana goga towel din a jikinta a hankali. ..</div><div><br /></div><div> Tayi saurin amsa tana fadin ..Sorry MMA kawo na maki ...</div><div><br /></div><div> A hankali tace. ..barshi ma nayi. ...</div><div><br /></div><div> Sorry please ta fada tare da rike mata hannu ...</div><div><br /></div><div> Komawa tayi ta kwanta ....rigarta ta cire sae dae ta kasa kwance belt din dake kirjinta na aikin da aka mata ...</div><div><br /></div><div> Ma'aruf ta kira ya kwance sannan ya fita ya basu guri ...</div><div><br /></div><div> Sae da tayi sati daya a gidan tare da shamy ...kula yake bata sossae idan ya shigo ya ga tana kuka ...ya dinga tambayarta meke damunta sae dae tace ba komae ....</div><div><br /></div><div> Ranar da zasu koma ..ya shigo dauke da iv card na bikinsu ya mikawa Shamy ta gani ....</div><div><br /></div><div> Wani Tsalle ta buga ganin designing din da aka masu da ratsin gold ...ta makale Meenalle tana nuna mata ...</div><div><br /></div><div> murmushi tayi ta kallah tana karantawa </div><div><br /></div><div> *Conjugal Bless* 💖</div><div><br /></div><div> _MR MA'ARUF IBRAHIM_</div><div><br /></div><div> *weds*</div><div><br /></div><div> _SHAMSIYYA A MAMMAN_</div><div><br /></div><div>_on 21 July 2017_</div><div><br /></div><div><br /></div><div> sae decoration din da aka bishi dashi da gold ana rubuta meenatou ...idan ba sani kayi ba bara kace mae aka rubuta ba ...zaka dauka kwarewace gurin wanda ya buga IV din ...</div><div>Wow yayi kyau ...ta fada tana waro ido ...</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi ya wucesu ...sae uban murna Shamy take. ...sae da ya canzo kaya sannan ya fito rike da ticket guda uku ya mika masu ....</div><div><br /></div><div> Da nashi dana Meenalle Sae na amarya Shamsiyya ....</div><div><br /></div><div> Meenalle ta kalleshi ido a waje tace Mr Ma'aruf ..ni ba gobe zan tafi gida ba ...</div><div><br /></div><div> Gobe zaki tafi Fateema ..ya fada a hankali tare da bude coca cola ya zuba a cup ...</div><div><br /></div><div> Da Sauri ta tashi ta je ta dauke cup din da sauran lemun tana kallonshi ...doctor yace ka daena shan lemun dake da gas a ciki ...</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi sannan ya bude su yana mata wani irin fitinanne kallo ...</div><div><br /></div><div> Da sauri ta juya ta koma kusa da shamy ta zauna tare da daura kanta saman bayanta ....</div><div><br /></div><div> Zo nan Fateema ....ya fada tare da mika mata hannu ...</div><div><br /></div><div> Makale kafada tayi tana kallon shamy ...wacce ita hankalinta ma naga wayarta sae daukar photon IV din take tana turawa a social media ....</div><div><br /></div><div> Ido ya lumshe yace ...me zaki bani tunda kin dauke nawa ...</div><div><br /></div><div> Mikewa tayi ta je ta bude fridge ta dauko mashi lemun kankana da abarba da ta hada dazu ta tsiyaya mashi a cup ta mika mashi ...</div><div><br /></div><div> Hannunta da cup din duka ya hade ya rike yana kallonta ...</div><div><br /></div><div> Bata fuska tayi ya saketa da sauri tana yarfe hannu. ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI ........</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦Talented Writers Forum💦</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>65. to. 66</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Tun da safe suka tafi Airport ...shi da Shamy suka zauna side daya sae Meenalle na gabansu ita da wata mata .....</div><div><br /></div><div> Ko da suka sauka Meenalle har ta kira su Alhaji Sadee tace sun iso ..don haka tare motocinsu Ma'aruf suka iso da wadanda aka zo sauka Meenalle dasu ....</div><div><br /></div><div> haka ta shige mota ba tare da ta kallesu ba ...har suka fice daga airport din ...sae lokacin ta sake kuka tare da fadawa jikin Mus'ab don tare suka zo ...</div><div><br /></div><div> Bawan Allah duk ya rude ..duk da yayi aure</div><div> har da yaro daya baya. tafiyarta ......</div><div> </div><div> Haka suka isa gida ...</div><div><br /></div><div> Sae da ta huta sannan Alhaji Abubakar da Sadee suka kirata Falo ..</div><div><br /></div><div> Alhaji. Abubakar yace ...da gaske Aminatu an maki aure ...</div><div><br /></div><div> Gabanta ya fadi don tama manta da wani aure a rayuwarta ...daga masu kai a hankali ...</div><div><br /></div><div> Alhaji Abubakar yace ...da yardarki aka maki auren ? ..</div><div><br /></div><div> Nan ne tace aa ...bata san anyi auren ba sae dae kawae musa ya zo ya dauketa ..</div><div><br /></div><div> Alhamdulillah ...Ya fada tare da tashi ya fita ...</div><div><br /></div><div> Sadee ne ya. bude mata komae a ranar har da ba shine ubanta na Asali ba sae da ya fada mata ...sannan ta fada mahaifinta na sonta don ba yarda zayayi ne shi yasa har ya barta hannu. mamanta ..</div><div><br /></div><div> Tabbas bata mu sa mahaifinta na sonta ba .don zaman da tayi tare dashi ya nuna mata so ..sae dae bashi da dalilin da zai banzatar da ita don Mahaifiyarshi ta umurceshi don Haka tace Ma Sadee ..yayi hakuri tacigaba da kallonshi a matsayin ubanta ..</div><div><br /></div><div> Nan ya nuna mata matsayin da uwa ke da shi ga yayanta tare da mata waazi sossae har jikinta yayi sanyi ta cire kalmar da take fada cewa bata daukeshi uba na kirki ba ..</div><div><br /></div><div> A Ranar ta dauke Abubakar a matsayin Ubanta amma ta kasa yarda da hajiyarshi a matsayin kakarta</div><div>Basu bar falon ba sae ga hajiyar ta shigo tana murna an fada mata Meenalle ta dawo </div><div><br /></div><div> ta janyota jikinta tana fadin ...yaushe kika dawo yata ..</div><div><br /></div><div> zare jikinta tayi ta fita daga falon ta barta zaune tana kallon Ikon Allah</div><div><br /></div><div> Sadee lafiyar Aminatu kuwa ? ..ko wani abu kukayi mata</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi yace ...babu abunda ya sameta Hajiya ...</div><div><br /></div><div> Anya kuwa Sadee ...ta fada tana taba hannu ..</div><div><br /></div><div> Me kika gani ne Hajiya ..ya fada yana murmushi ..</div><div><br /></div><div> Ahto ..naga yarda Meenalle ke nan nan dani amma yau ta nuna kamar bata sanni ba ...kasan Allah Sadee ..ina kaunar Aminatu ..da iyayenta zasu. bar man ita da ta zauna hannuna har na aurar da ita ..shin ni kau sadee baka san inda Rabi da diyarta suke ba ..idan nama abubakar maganar baya saurarena ..</div><div><br /></div><div> Hajiya kenan . yanzu kuma jikkar har mace kina so ..? </div><div><br /></div><div> jikinta yayi sanyi tace ..to tunda ita Allah Ya bani ba dole na rungumeta ba ? </div><div><br /></div><div> Hmm Aa Hajiya ki tsaya ki gani ko Allah dae zai baki namijin ....yana gama fadar haka. ya tashi ya shiga ya kira mata matarshi ta fito ...</div><div><br /></div><div> Sama Sama suka gaisa ta tashi ta tafi cike da tunani </div><div><br /></div><div><br /></div><div> *Feedohm💞*</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI. ....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦Talented Writers Forum💦</div><div><br /></div><div> 🔝</div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>69. to. 70</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Tun da safe Meenalle ta shirya tace wa Sadee zata je ta Gida gurin Mamanta ...</div><div><br /></div><div> Direba ya saka ya kaita har zarian sannan ya bata kudi masu yawa ...</div><div><br /></div><div> A Zaure ta tarad da Mamanta na waina ...ta rungumeta cike da murna ..suka shiga cikin gidan ...ta sake maman ta fada cinyar Kaka tana kuka ....</div><div><br /></div><div> Yaro ya shigo wae ana kiran Meenalle ....</div><div><br /></div><div> Kamar tace bata zuwa sae kuma taga kara taje kila drivern da ya kawota ne zaya juya ...dan haka ta dauki gyalenta ta fice ...</div><div><br /></div><div> Sae da ta daga kai ta kalli Benen gidansu Ma'aruf kafin ta fita ...</div><div><br /></div><div> Tsaye ta ganshi rike da robar swan yana waya ...sae murmushi yake da alama da shamy yake ...</div><div><br /></div><div> Ajiyar zuciya ta sake ba tare da ta fita ba ...sae aikawa tayi tace wanda ke kiranta ya shigo tana zaure ...</div><div><br /></div><div> Kamar mahaukaci ya shigo duk ya rame yayi baki ...sa sauri taja baya tana bata fuska ta nuna shi ...Kai ke nemana? ..</div><div><br /></div><div> Washe baki yayi yana fadin ...kece Meenalle ...Meenalle ke kika koma haka ...Allahu Akbar ...kin ganeni ...nine Musa ..</div><div><br /></div><div> Musa ta fada tana kallonshi sama da kasa ..sannan tace ...daga ina. ..</div><div><br /></div><div> Baki ya washe yace...Musa dae Mijinki har kin manta ni ..gaskia an cuceni ...</div><div><br /></div><div> Ido ta waro. ...oh wae Musa dan Sani na gidansu Luba? ..</div><div><br /></div><div> Shi ma Meenalle ....bara naje na fadawa Baba kin dawo sae a janye karar sae mu koma ko ? ..</div><div><br /></div><div> Dariya tayi tare da nuna shi da hannu. . ina jin har yanzu baka manta da ko wacece Meenalle ba ko .....</div><div><br /></div><div> Bata jira amsarshi ba ta koma gida ta barshi tsaye ...</div><div><br /></div><div> ••°°••</div><div><br /></div><div> Mamanta ta kalleta tace ...wa nene ya aiko kiranki ..</div><div><br /></div><div> Mama wae Musa ne ..ta fada a hankali...sannan ta kalli kaka. tana goge hawayen da suke neman zubo mata tace ..</div><div><br /></div><div> Kaka Maikamshi ya shigo ....</div><div><br /></div><div> Daga mata kai tayi tace ..yazo Meenalle ..Kullun sae ya tambayi shin kin dawo Meenalle ..ko dazu da safe ya shigo ya gaidamu ....jiya ya dawo ma ..</div><div><br /></div><div> </div><div> Lumshe ido tayi a hankali tana kallon wainar da suketa lodawa a Coler ..wannan fa ta mecece..</div><div><br /></div><div> Tsohuwar ta kaudar da kai tace ...gudunmuwa nakewa Maikamshi ta bikinshi ...aure zayayi ..jibi ake daura auren ma Meenalle ....</div><div><br /></div><div> Kaka ta goge hawayen da suka zubo mata tace ...naso Meenalle ...naso ki zama matar Ma'aruf ...amma aka cucemu ...Yana sonki sossae. .</div><div><br /></div><div> Tashi tayi tana fadin ...zan koma kaka.......</div><div><br /></div><div> Da sauri ta fice daga gidan ta shige mota tace su koma kawae .....haka driver ya jata suka koma gida ba tare da tayi kwanakin da ta zo yi ba. ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Tana shiga gidan ta tarad da Shamy tazo ....suka rungume juna suna ihu ...</div><div><br /></div><div> Shamy tace tazo daukarta ne ...ana ta hidimar biki amma babu ita ....sannan Mr Ma'aruf duk yabi ya damu baki zo ba ...gaskia ki shirya ..don ni na riga na tambayi dady da mommy ashe ba wanda kika fada mawa ...da banzo ba da bara ki zo ba kenan. ..</div><div><br /></div><div> Murmushi tayi tace ..Shamy ai kinsan dole nazo bikinki ..</div><div><br /></div><div> Harara ta sake mata tace ..Banga alama ...ni dae yanzu ki shirya muje ...</div><div><br /></div><div> Duk wani abunda zata bukata sae da ta dauka ...sannan ta shiga tayi wa Mom bankwana suka shiga mota da yake shamy tare da driver suka zo ...suka koma zaria ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> ••°°•• </div><div><br /></div><div> Tun a mota Shamy ta kira Mr Ma'aruf tace tare suka taho da Fateema ...</div><div><br /></div><div> Yana tsaye ta bene ya kurawa gidan kaka ido ya waro ido yana murmushi ..yace da kun shigo gari ki kirani ..</div><div><br /></div><div> Ok hubby ..ta fada tare da kissing din wayar sannan ta kalli Meenalle tace ..</div><div><br /></div><div> Gaskia dole ki saki jikinki wannan bikin ..in ba so kike ki dagawa hubby hankali ba. .ni na rasa wane irin mutuncine tsakaninku ..karfa kiyi man snatching. ..</div><div><br /></div><div> Murmushi Meenalle tayi tace ...kisha kurumin Shamy sanin kanki ne banda niyar maki snatching karki manta kidney dina daya tana jikinshi ..kuma silar hakan ne na hadaku ..kinga kuwa fadin kalmar snatching kamar butulci ne kika mani .....</div><div><br /></div><div> Zatayi magana ta dakatar da ita .. please mu bar wannan maganar Shamy. ..</div><div><br /></div><div> Shamy ta kwantar da kanta a bayanta tare da fadin ...Am so sorry Meena. ..</div><div><br /></div><div> Lumshe ido meenalle tayi ..itama ta daura kanta saman cinyarta ..a haka har suka isa ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Suna shiga garin ta kira Ma'aruf ta fada mashi sun iso ..yace su jirashi bakin gari ..zaya zo yanzu ..</div><div><br /></div><div> </div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧 SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦Talanted Writers Forum💦</div><div> 🔝</div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>71. to 72</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Ko 15 Mints basuyi ba ya iso tare da kwankwasa masu glass din motar ..da yake side din Meenalle yayi knocking sae ta sauke glass din ...</div><div><br /></div><div> Kamshinshi ya bugeta bata san lokacin da ta furta ..Maikamshina....</div><div><br /></div><div> Saurin kallon bakinta yayi tare da fadin Me kika fada fateema ..</div><div><br /></div><div> Lumshe ido tayi tare da bude kofar ta fito ..sannan tace ..Ango ina wuni ..</div><div>No ba haka kika fada ba ...abunda kika ce shi zaki maimata ..</div><div><br /></div><div> Dan hararanshi tayi tace ...Cewa nayi ..sae Kamshi kake ...</div><div><br /></div><div> A hankali ya lumshe ido tare da dubar Shamy yana fadin muje na kaiku ...shi ya tafi</div><div>Motarshi suka shiga ...Har gida ya kaisu ...Meenalle ta shiga ciki ta barsu a mota .....gidan ya cika da kawayensu ..har da soofy. ..sae murna suke ana labarai .....</div><div><br /></div><div> Da daddare kowa yayi bacci aka bar Meenalle sae juyi take ...Soofy ta farka ta dade tana lura da ita ...sannan ta gangaro kusa da ita ta kira sunanta a hankali ...</div><div><br /></div><div> Meenalle ta bude ido tana kallonta tace ...Bakiyi bacci ba ...</div><div><br /></div><div> Soofy ta mike tare da jan hannunta suka koma falo ...zama sukayi sannan ta kalli Meenalle tace ...Meena meke damunki ..</div><div><br /></div><div> Me kika gani Soofy ...ta fada tana kallonta ...</div><div><br /></div><div> Meena komae ma na gani ...Mr Ma'aruf shine Ma'aruf dinki ko? ..</div><div><br /></div><div> Da sauri ta rufe mata baki ...tace ...waya fada maki Soofy ..dan Allah ki bar wannan maganar ...bashi bane . </div><div><br /></div><div> am not kid ...Meena...me yasa zakiyi haka ...kuma ba Shamy ce ta bashi kidney ba kice Meena ...duk wannan sirrin na meye ....Shin baki sonshi ne yanzu ....Dole zan fada mashi gaskia gobe ..</div><div><br /></div><div> kuka ta sake tana fadin ..</div><div>aa Soofy. ..karki fada mashi dan Allah ...wallahi baya sona yanzu ...</div><div><br /></div><div> Karya kike Meena ..har yanzu akwae kaunarki ..duk da bai san ke bace Meenalle amma ki kalli idonshi kaunarki ce ke cike dashi ...kuma sae na fada mashi ...</div><div><br /></div><div> Cikin kuka ...wallahi Soofy baya kaunata naji yana fada ne ..ya tsaneni ..bansan me na mashi ba. ....</div><div><br /></div><div> Ke dae kika sani ..ni zan fada mashi idan kinso idan zai aureki sae ki ki aurenshi </div><div><br /></div><div> Soofy ni matar aurece ...ta fada a hankali</div><div><br /></div><div> A masifance ta juyo tana fadin karya ne wallahi ...</div><div>Hannunta ta ruko tana kuka ...ki yarda dani Soofy ina da aure ..da banda aure da babu abunda zai hani bude *SIRRIN ZUCI* ...sun aurar dani ga wani ...wani wawa Soofy Wawa irin Musa ...Tabbas ina son Ma'aruf ..amma katanga babba ke tsakanina dashi ...sun dasa mashi tsanata ta yarda har yake furtawa ....ya zanyi Soofy ....ta kara fashewa da kuka. .</div><div><br /></div><div> Tausayinta yayi balain kamata ...dukawa tayi tare da rungumeta a jikinta ...kiyi hakuri Meena...in sha Allahu dole musa ya sakeki ...kin sani mahaifina Justice ne ...zan mashi magana dole a bi maki hakkinki ...kiyi hakuri dan Allah</div><div><br /></div><div>°°••°°</div><div><br /></div><div> Karfe biyu dae dae aka daura Auren Ma'aruf da Shamy gaban dunbin mutane. ...Amarya baki yaki rufuwa haka ango ...Sae shirye shirye ake ..don bayan biki da kwana uku zasu bar kasar saboda karatunta da kuma aikinshi ...</div><div><br /></div><div> Wajen karfe 9 ne akace a fito da amarya zaa tafi dinner ..</div><div><br /></div><div> Amarya ta shigo hall tare da manyan kawayenta guda biyu ....</div><div><br /></div><div> Chanchadi Mazakwae ...uhmm abun baa magana ..idan kaji ana Carai ..to wannan amaryar ta wuce anan ...Sky blue din gown ne a jikinta ...fuskarta na rufe da wani golding din net daga samanshi ya fitar da wani shape kamar an daura crown ......</div><div><br /></div><div> Ango na zaune suka shigo ....lumshe ido yayi tare da jingina da kujeran da yake kai ..sannan ya bude su a hankali tare da sakin wani fitinannen kallo yana kallon right side din amarya ....</div><div><br /></div><div> Sae lokacin na kalli inda yake kallo ....</div><div><br /></div><div> Ido na waro sannan na lumshesu nima kamar yarda yayi ...Phone dina ta sulale ta fadi kasa ...duka glass din ya dargaje😒😥😥...bansan lokacin da nayi zaman dirshan ba ...ina kallo.. .sae da na lalubi wayar da niyar na fada maku me na gano ...sae lokacin na lura ashe ta dargaje 😒😒😒</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm*💞</div><div>💧💧 SIRRI ZUCI ....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦Talented Writers Forum💦</div><div> 🔝</div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>73. to 74</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Meenalle nagani tsaye rightside din amarya ...sanye da gown itama amma Pinch colour ....sae head maroon ...ta gaji da haduwa ..fatar har wani kyalli take. ....</div><div><br /></div><div> Ma'aruf ya taso a hankali har ya iso kusa da amaryarsa ...hannnuta ya kama tare da matsawa kusa da Meenalle ...</div><div><br /></div><div> Natural beauty ...ya fada mata dae dae kunnenta ....phone dinta tayi kara ....</div><div><br /></div><div> Ta dan saci kallonsu ta dauke kai ..tare da ficewa daga hall din ....ta dauki sayar. ..</div><div><br /></div><div> Aminatu ...gamu a bakin gate amma kamar baku ciki ko ? ...aka fada daga dayan bangaren ...</div><div><br /></div><div> Muna ciki. mana ku shigo har zaa fara dinner ....</div><div><br /></div><div> ki fito. ki shiga damu please ...ko mun shigo bamu san inda zamuyi ba ...don gurin da alama yana da girma. ....</div><div><br /></div><div> Okey ..gani nan fitowa ta fada ...tare da juyawa ta kalli su Shamy ...Ma'aruf rike da hannunta ...wani abu ya tokare mata kirji ta fita da sauri ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Daga can side din ta hango wata bakar jeep ....ta fito da wayarta ta kira number. ..kuna ina ...</div><div><br /></div><div> Ki tsallako muna cikin jeep din dake tsaye gefe guda ....kafin tayi magana an kashe wayar ..</div><div><br /></div><div> Tabe baki tayi ta tsallaka tare da knocking din glass din motar na gaba ....</div><div><br /></div><div> Kofar baya aka bude ...wani kato ya fito ya toshe mata baki ya jata cikin motar suka hau titi da gudu ...</div><div><br /></div><div> Hannun ta cire daga bakinta tare da jan uban tsaki ta gyara zama cikin motar tana watsa masu wani uban kallo ..</div><div><br /></div><div> Da cewa kuka yi na fito kunzo sace ni ne da baku wahalar da kanku ba ....ta fada tana kallonsu ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Torch light din wayarta ta kunna ta haska su daya bayan daya. ..sannan ta maida hasken ga na kusa da ita ..</div><div><br /></div><div> Musa Sani ..ta fada tana kallonshi ....matsalata dakae wawa ne ...bakka ganewa ..dan zaka dauki yarinyar da kake tunanin matarka ce sae ka hado da wadannan jakunan ....? ..</div><div><br /></div><div> Ke.....wani ya daka mata tsawa ...tare da nunata da hannu. </div><div><br /></div><div> Hannun yaji an murde da karfi har sae da yayi kara alamun karewa .tare da angazashi baya ....daga lokacin bai kuma cewa komae ba ..</div><div><br /></div><div> Meenalle ba tsoro ...haka ta dinga wankesu ..har suka shiga wani tsohon daji ...sae lokacin ta lura sun bar titi ....</div><div><br /></div><div> Bata kuma cewa komae ba sae kallon ikon Allah da ta tsaya tana yi ....har suka isa wani dogon gini ..baraka iya cewa ga karshensa ba . ..</div><div><br /></div><div> Daya ya sauka ya bude masu gate din suka shigar da motar ciki. ...</div><div><br /></div><div> Ba wani babban gida bane ...duka kofarshi daya ta shiga ciki sae ta gate ..duka gidan arufe yake ...suka faka motar suka fito ...</div><div><br /></div><div> da yake akwae hasken wuta ...ta bisu da kallo ..kamar mahaukata haka suke ko wane bakikkirin dashi sae mazurai suke ...</div><div><br /></div><div> Ta hadiyi wahalallen miyau sai lokacin gabanta ke faduwa ....amma ta dake ta na hararansu ....</div><div>Mu shiga ciki Meenalleta ...Musa ya fada yana dariya ...</div><div><br /></div><div> Murmushin ta sake mai cike da takaici ...tace ..ai ko bakace ba Musa kasan zan shiga sannan na zauna daku har sae kun gaji dan kanku ku mayar dani kuma na kwanta idan kai dan iskane kayi gigin zuwa kusa dani ...</div><div><br /></div><div> Girgiza kai yayi yana wata dariya ..Meenalleta kenan ..kiyi hakuri ki soni muyi rayuwa a duniyata ..ki haifa man ya'ya kyawawa irinki ...</div><div><br /></div><div> Wace duniyace gareka Musa...duniyar karnuka ..Sannan ba Ya'ya zan haifa maka ba ...Uwaye zan haifa maka. ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Gaba yayi yana dariya ta bi bayanshi ...sauran suka take masu baya. ..har wani karamin daki ya kaita mai dauke da karamin gado sae wasu akwatuna guda uku ...</div><div><br /></div><div> Meenalle ga lefenki nan ...wanda da ban baki ba ....akwae english wears a ciki kinsan ni mayan sune ....ya fada yana washe baki ..</div><div><br /></div><div> Dariya ya bata sossae har tana rike ciki ...sannan ta nufi gurin gadon ta cire pillow ta aje a kasa ta kwanta ..tunda dama tayi isha'i ..</div><div><br /></div><div> Tana kwance ya shigo tayi saurin tashi zaune tana kallonshi...kazar amaryace na kowa ..ya fada yana kallon kirjinta ...</div><div><br /></div><div> Babu tsoro taja ledar ...tana dubawa ....je ka dauko plate ..ta fada ba tare da ta kalleshi ba ...</div><div><br /></div><div> Da sauri ya mike yana fadin Meenalle har kin sauko zaki ci kazar amare ..kila dama dan ban nuna maki ita ba shi yasa kike zagina dazu ..</div><div><br /></div><div> Musa baka gane ...ko dae Mamansu luba hada maka da nonon awakai lokacin da take shayar da kai....ta fada tana murmushi </div><div><br /></div><div> Da kuwa ta cuceni yasin ...ya fada sannan ya fice daga dakin ...</div><div><br /></div><div> Da Sauri ta mike ta rufe dakin da keys din dake jikin kofar ta koma ta harde kafa ta fara cin kazarta ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦Talented Writers Forum💦</div><div> 🔝</div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>75. to 76</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Meenalle bude ga parantin ....ya fada yana buga kofar ...</div><div><br /></div><div> Musa Aje akwanta sae Allah ya hada mu gobe ....ta fada daga cikin dakin ..</div><div><br /></div><div> Haba Meenalle ke fa kikace na dauko ..ki bude dan Allah ...wallahi ni bama kazar zanci ba ..ke nake so...</div><div><br /></div><div> ashe ma kai sakaraine .....ta nannade ledar tare da gyara kwanciya ..</div><div> </div><div> Yayi lallashin duniyar nan ..amma taki ko kulashi ..daga karshe yace ...Meenalle ke yar iskace ko...kinsan ba tare zamu kwana ba kika cinye man kaza ko...to wallahi da safe sae na maki shegen duka ....ya bugi kofar da karfi ya wuce ....</div><div><br /></div><div> Tana kwance taji alamar mota ta fita daga gidan ...ta mike ta leka ta taga ...taga sun fice sae mutun daya zaune bakin kofar an barshi gadi .....</div><div><br /></div><div> Ta bude kofar ahankali tare da lekawa ...babu kowa sae falon dake gauraye da hasken wuta ...ta fito tana sanda ta rufe kofar shigowa ciki sannan ta shiga wani karamin daki mai shegen duhu. ...da wayarta ta haska taga duk kayan fadane aciki ..sae bindiga da bata wuce 5 ba kirar AK ....sae uwayen akwatuna da da buhu cike da kudade ....</div><div><br /></div><div> Sae lokacin ta tabbatar yan fashine .. ..dakin da aka bata ta koma da kwanta ..</div><div><br /></div><div> Su Musa suka dawo babu irin bugun duniyar da basuyi ba amma Meenalle bama ta sani ba tana baccinta ...</div><div><br /></div><div> Da Asuba ta farka ta iske missed call kusan 76 ...50% duk na Ma'aruf ne ...sae Soofy itama ta kirata ...sae Mamanta ....</div><div><br /></div><div> Mamanta ta kira ..tace fada mata duk abunda ke faruwa ...sannan tace mata ta kwantar da hankalinta ...ta dinga mata addu'a in Allah ya yarda zata dawo ....</div><div><br /></div><div> Sannan ta kira Soofy ..itama addu'arta ta roka ta kashe wayar ...</div><div><br /></div><div> Text ya shigo mata na Ma'aruf ne ... _Fateema ina kika shiga ne ? kina dae lafiya ko ,? ...._</div><div><br /></div><div> Reply ta mashi _Na koma gida fatan Alkhairi kai da amarya_</div><div><br /></div><div> Ta kashe wayar gaba daya ...cikin saa taga toilet acikin dakin ...ta shiga tayo alwala ..cikin akwatin da Musa ya nuna mata ta duba ko zata ga hijab ...amma babu ...sae Zanin atamfa ta dauko ta lulluba tayi sallah .....</div><div><br /></div><div> Sae da gari ya waye sannan ta fita daga dakinta ...lekensu tayi babu wanda ya farka ..kamar matattu ...tsaki tayi ta bude kofar ...</div><div><br /></div><div> Firgigi suka farka ...ko wane sae ya taso da zuciyarshi ...da sun hada ido da musa sae ya koma ya kalli kasa ...</div><div><br /></div><div> Musa kuwa duk bala'in da yayi niyar ya mata sae ya kasa ...ya matsa yana washe mata baki.....ba kuma wani abu ya hana ya mata ba .aa tunowa yake da lokacin da suna kauye ..idan zai bugeta azabar da take mashi ...</div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Tun kafin a shiga court Alhaji Abubakar ya sami Alkali ya mashi bayanin Musa ya sace Yarinyar ...Haka aka nemi Malan Sani shima bai zo kotun ba .....</div><div> </div><div> Alkali ya aika a daukoshi ...yana zaune bisa dankali aka daukoshi sae masifa yake</div><div><br /></div><div> </div><div>Aka zo dashi office din Alkali ...aka tambayeshi ina Musa ....kada kai yayi yace bai sani ba ..</div><div><br /></div><div> Juyin duniyar nan Amma Malan sani ya yace bai san inda musa yake ba ....</div><div><br /></div><div> Nan take Alkali ya raba auren tare da tsare Malan Sani har sae Musa ya dawo da Meenalle lafiya ..idan kuma wani abu ya sameta to hukunci mai tsanani zai hau kanshi ...</div><div><br /></div><div> Lokacin da labari ya isa gurin musa sae cewa yayi ...indae sae ya dawo da Meenalle zaa saki Malan sani sae dae ya mutu a daure ...</div><div><br /></div><div> Ran Malan sani yayi bala'in baci ...ranar ya tsinewa musa yafi a kirga. .sannan yayi nadamar abunda ya dinga yi akan musa gashi yanzu ance ya maido Yarinyar a kwanceshi yace sae dae ya mutu a daure .....</div><div><br /></div><div>••°°•• </div><div><br /></div><div> Ma'aruf da amarya aka koma india ...rayuwa suka bude mai kyau ...matsalar daya ce Shamy bata san yarda zata kula da mijinta ba ....illa iyaka ta dafa break ta ta fi school ...amma abincin rana dana dare sae dae ya sawo masu ...</div><div><br /></div><div> Lokacin suna gab da fara exam amma babu Meenalle ..hankalin Ma'aruf yayi bala'in tashi ..har rigima sukayi da Shamy lokacin ...wae sae ya fada mata dalilin da yasa ya damu ....</div><div><br /></div><div> Bai ce mata komae ba ...yaja har school din ya saki iyayen kudi sannan ya samu wata wadda ta riga ta gama school din aka sakata ta zaunawa Meenalle ...</div><div><br /></div><div> Shamy ta shiga dakin Ma'aruf rike da cup din coffee ...bai san ta shigo ba yana rike da photon Meenalle ....ji yayi an fuzge photon tare da fasashi kasa ...</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi ba tare da yace mata komae ba ya duka yana tattara photon ..</div><div>kafa ta saka tayi wurgi da wanda ya tattara ....</div><div><br /></div><div> Azuciye ya mike ya wanka mata mari ...tare da jan hannunta ya fitar da ita daga dakin ya saka key ...</div><div><br /></div><div> Bugun kofar ta dinga yi kamar mahaukaciya tana bala'i ....har sae da ta gaji sannan ta yi shiru ...sae da tayi Wata ba tazo shinfidarshi ba ...haka bata mashi magana ba ...</div><div><br /></div><div> Ma'aruf ba mai son hayaniya bane ganin abun nata bana karewa bane ya saka ya kirata da kanshi ya lallasheta ganin lokacin tana dauke da ciki .....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ......</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦 Talented Writers Forum💦</div><div> 🔝</div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>77 to 78</div><div><br /></div><div><br /></div><div> An baza ko 'ina ana neman Meenalle amma ko labarinta baa samu ...an kirata a waya an tambayeta ina take amma sae dae tace wallahi bata sani ba ....</div><div><br /></div><div> Haka musa ma nemanshi ake ruwa jallo ..amma da yake munafukine ..suna da wani tsari indae ana neman su to basu taba haduwa da masu neman nasu ....</div><div><br /></div><div> Kuma bai fasa shigowa zaria ba ....duk lokacin da yaso zaya shigo kuma ya fita ba tare da wadanda ke neman nashi ba sun ganshi ...ko da kuwa zaya wuce ta gabansu to shi kadae zai gansu ....</div><div><br /></div><div> Meenalle kuwa tana can zaune ...duk tabi ta ishesu ....akwae ranar da suka bata girki ...Shinkafa da miya ...sae da ta juye masu quatern gishiri cikin miyar ....ranar Musa kamar yayi hauka don baya cin gishiri .....</div><div><br /></div><div> Sannan babu shegen da ya isa ya nuna mata hannu ....komae tayi masu kuwa ...Musa ma ya taba gigin dukanta ranar da suka dawo daga fashinsu sa daddare suka iske kofar bude ...sukayi ta murna don sun saba kwana a waje ...ga sauro ..ga kunamu ....Suka shiga falon babu wuta su duka sukayi mamaki don babu inda zaka tarad ba da wuta a gidan ...</div><div><br /></div><div> Gashi babu mai ko waya ...haka suka shiga cikin ...ko wane da ya shiga sae ya fito da gudu yana ihu rike da kafa ....</div><div><br /></div><div> Zuwa can wuta ta kawo ...sae lokacin suka lura da cewa kwalbace farfashe a kasan gurin ....kuma sun tabbata Meenalle ta sakata ....</div><div><br /></div><div> Musa ya shiga dakinta a fusace tana kwance ya fizgota tare da daura mata mari ....bai sauke hannu ba yaji kalan nata a fuskarshi. ..afusace ya cire belt ya zura mata...</div><div><br /></div><div> Zafi da azaba bata san lokacin da ta murde mashi abun fitsari ba tare da aza mashi cizo a idon dama .....</div><div><br /></div><div> A rude ya fito yana ihu rike da wando ....suka tareshi suna rikeshi ...wasu na Allah ya kara wasu na tausayinshi ....kafin safe ido ya kumbura ....</div><div><br /></div><div> Sae da yayi sati baya fita ...don daga karshe ma zazzabi ya rufeshi ...tunda lokacin bai kuma gigin dukanta ba ...</div><div><br /></div><div> kowa ta isheshi a gidan ...bayan ya warkene. ..yayi alkawarin ko zata mutu sae ya kwanta da ita ranar ..don haka suna gama fashinsu ya sawo mata kaza ...har wani karamin gidansu ya tsaya yayi wanka sannan suka taho ...</div><div><br /></div><div> Da yake generator dinsu ya lallace ...babu wani shamaki suka kutsa kai cikin falon ....</div><div><br /></div><div> Meenalle na tsaye bayan kaure rike da tabaryarta ...Musa ya kutso kai rike fa ledarshi .</div><div>.</div><div> ta daga tabaryarta iya karfinta ta buga mashi a goshi ...ya dafe gurin tare da sakin ledar ya koma baya da gudu ...</div><div><br /></div><div> Lafiya oga ...wani ya tambaya ...</div><div><br /></div><div> Saboda azaba da hannu ya nuna mashi cikin gidan ...ya daga labubalai ya shiga yana lafiya ....dukan da yajine ya bashi amsa ya yo baya dafe da goshi ga jini na zuba ...</div><div><br /></div><div> Cikinsu babu wanda bai yi kokarin shigowa ba haka babu wanda baiji ciwo ba ...da Meenalle ta tabbata kowa ya samu rabonshi ta dauke ledar ta shige dakinta da gudu ta saka makulli .</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Safe suna zaune kowane fuska a kumbure ta fito ta saka su gaba tana ta dariya ..</div><div>wani Sale cikinsu sae da yayi kuka ranar saboda takaici ...gashi sun san ita tayi masu wannan rashin kirkin amma babu halin magana ...</div><div><br /></div><div> Bayan sati daya ne suka dawo suka iske ta kona masu duk abunda aka tara a gidan ...</div><div> </div><div> Ranar sukayi Meeting musa baya nan suka sami Meenalle suka roketa tazo su fitar da ita cikin gari ...</div><div><br /></div><div> Cewa tayi bata so bara ta tafi ba ...don bata gaji da zaman ba ..</div><div><br /></div><div> Suka dinga hada ta da Allah ..Da kyar ta yarda ta shiga motar suka taho ....Har kofar gidan Kaka suka ajeta sannan suka juya da sauri ...</div><div><br /></div><div>*Feedohm*💞</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦Talented Writers Forum💦</div><div> 🔝</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>79. to 80</div><div><br /></div><div> Lokacin da musa ya dawo ya iskesu tsaye bakin gate ....ya taresu yana tambayar lafiya...sae suka ce masu police ne suka zo suka tafi da Meenalle basu nan ...</div><div><br /></div><div> Kamar mahaukaci ya juya ya tafi police station din rike da bindiga ...da yake shashasha ne yama manta da nemanshi ake soyayya ta rufe mashi ido ...</div><div><br /></div><div> Yana zuwa ya fara harbe harbe yana zage zage ...nan da nan suka kamashi suka daure ...</div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Ina Raliya ..</div><div><br /></div><div> Da Raliya ta tabbatar Mr Ma'aruf ya rigaya ya mata nisa ...don ko tana tsafi da bakar jaba bara ta sameshi ba ...har office dinshi taje messenger shi ke fada mata yayi aure ...sae ta tattara kayanta ta koma nigeria ...ta sayi gida ta bude wani bariki na yan lesbian ...da yake dama maza ba damunta sukayi ...ba ...dama Mr Ma'aruf ne take bala'in so kuma bata samu ba ...</div><div><br /></div><div> Haka ta lallashi partner ta Ruky da ta rude tana son Meenalle tun tana yarinya don tun lokacin da Meenalle ta shigo gidansu har ta dauketa bata kuma kara kula Raliya ba ...suka shirya suka koma kamar da ..</div><div><br /></div><div>°°••°°.</div><div> </div><div> Bayan an rufe musa ne aka sake Malan Sani ....Lokacin Ya koma yana so rabi ta koma gidanshi ...amma fur kaka tace bara ta koma ba ....</div><div>Sannanne kaka ta murje ido tace Malan Sani sae ya tashi daga gidan ...</div><div><br /></div><div> Malan sani ya tsorata ganin Kaka zata maidashi kotu ...gashi ya sayar da gida kuma ba kudi. ...yayi nadama sossae Rabi tace a kyaleshi amma ya saketa dan bara ta koma gidanshi ba ...</div><div><br /></div><div> Jiki na kyarma ya bata takardar saki ... .</div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Meenalle kuwa tana dawowa kaka ta mayar da ita gidan ubanta ...ko sati bata kara ba ta koma makaranta ...</div><div><br /></div><div> Ranar da ta isa kasar bata san wanda ya fadawa Ma'aruf ba sae ganin kiranshi tayi ..bata dauki kiran ba sae da suka hadu School da Shamy take mata tsegumi ..... .</div><div><br /></div><div> Duk yarda Shamy taso Meenalle taje gidanta amma taki yarda taje ...haka ta hakura ta kyaleta ...Shima Ma'aruf yayi kokarin su hadu ya ganta amma duk ta toshe hanyar da zasu hadun ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°•• </div><div> </div><div> da Hajiya ta ishi Abubakar maganar diyarshi ...sae ya dauko mata Sadee ..ya gaya mata gaskia ....</div><div><br /></div><div> Su hajiya har da kuka tana neman gafararsu. ..sannan tace akaita gurin Rabi ta roki gafara ...haka suka shirya suka tafi ....</div><div><br /></div><div> Lokacin da Abubakar yaji auren Rabi ya mutu ..ba karamin farinciki yayi ba. ...ya fadawa Hajiya yana so ya maido rabi ...da yake hajiyar tasha wahala gurin matar da ta sakq ya aura ..sae ta amince dan da nan ...</div><div><br /></div><div> ••°°••.</div><div><br /></div><div> Cikin wata hudu akayi komae aka gama ..rabi ta koma gidan tsohon Mijinta ...wancan matan kuwa tana jin zayayi aure tace bara ta zauna da kishiya ba ..ta tattara komatsunta ta yi tafiyarta ....</div><div><br /></div><div> Da Hajiya kuwa ta gyara halinta suka zauna lafiya da Rabi. ...da labari ya sami Meenalle har kukan murna sae da tayi ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦Talented Writers Forum💦</div><div> 🔝</div><div> </div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>81 to 82</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Nine Month*</div><div><br /></div><div><br /></div><div>Tun da Safe Ma'aruf ya kira Meenalle ...yace tazo Shamy na kiranta bata lafiya ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Taxi ta hau ...kasan cewar tsakanin makarantar da gidansu Shamy din akwae nisa ...minti biyar tayi ta isa gidan ...</div><div><br /></div><div> Lokacin har an fito da Shamy din daga cikin gida zaa kaita asibiti ...</div><div><br /></div><div> Da Sauri ta isa gurin Ma'aruf tana tambayarshi lafiya ....</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi yace tana labour ne wallahi ...tun jiya ...</div><div><br /></div><div> Bayan sun je asibitin ne akace. ..sae an mata CS saboda haihuwar tazo amma kuma Mahaifar ta rufe. ...</div><div><br /></div><div> Canza mata asibiti yayi ya maidata asibitin da aka masu aiki ...yana tunanin ko zasu iya mata wani abu ...don baya kaunar CS ...Cikin Saa ya tarad da doctor din da ya mashi aikin Kidney ...</div><div><br /></div><div> Thesame nan ma cewa akayi sae anyi aikin don barata taba iyawa ba ...</div><div><br /></div><div> Haka aka shigar da ita dakin tiyata ...Meenalle duk ra rude. ..bayan minti 45 ..wata nurse ta fito da baby boy ...</div><div><br /></div><div> Ta nufi wani room dashi da sauri ...Meenalle ta bita tana tambayarta lafiya. ...</div><div><br /></div><div> bayan ta fito daga dakin ta zo tana masu bayanin ...boy dinne yasha ruwan mahaifa kuma akwae matsala. ...</div><div><br /></div><div> Abunka da ruwa ruwa nan da nan idon Meenalle ya ciko da kwalla ...don tasha jin inda yaro ya samu irin wannan matsalar da wuya ya tashi .....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Minti Talatin da shigar nurse din ta fito ta fada masu cewa baby boy din ya koma ga Allah ....</div><div><br /></div><div> Meenalle ke ta hawaye ...amma Ma'aruf lumshe ido yayi kawae yana kallon dakin da Shamy ke ciki ....</div><div><br /></div><div> Zuwa can aka gangarota ....aka shigar da ita wani dakin ....lokacin idonta biyu tana kallonsu ...ta yafito Meenalle da Hannu ....</div><div><br /></div><div> Doctor din ya girgiza mata kai ...yace tana bukatar hutu ....</div><div><br /></div><div> Bayan an shiga da itane ..ta dinga rokan doctor din akan ya barta tayi magana da Meenalle minti 30 kawae ....daga farko cewa yayi tayi hakuri ...amma daya fahimce ta sossae sae yaga bai dace ya hanata ba ....</div><div><br /></div><div> Shi da kanshi ya kira Meenalle yace ta shiga patient din nason magana da ita ....</div><div><br /></div><div> ta shiga da gudunta ...Ma'aruf ya bita da kallo ....</div><div><br /></div><div> Shamy ta rike mata hannu suna kuka ...Ma'aruf dake kallonsu ta cikin glass ya kura masu ido ...ya rasa wace irin shakuwace tsakaninsu ..wadda har daga fitowarta da operation take son magana da ita bayan gashi ...</div><div><br /></div><div> Meena ...Shamy ta kira sunanta ahankali ...</div><div><br /></div><div> Meena ya maimata a ranshi tare da matsawa saitinsu yana kallonta ..</div><div><br /></div><div> Ki fadawa Ma'aruf gaskia...Dan Allah Meena ko bayan na mutu ki fada mashi ki gaya mashi bani na bashi kidney ba Meena. . ki fada mashi ke ki bashi ..kece masoyiyarshi ta gaskia bani Meena ..ki fada mashi kece Meenallen shi ....</div><div><br /></div><div> Girgiza mata kai tayi tana kuka ...aa Shamy zaki warke dan Allah ki bar wannan maganar ...zaki warke insha Allah ..</div><div><br /></div><div> Hannuta ta kawo ...bazan tashi ba Meenalle ..baby din na haifa ki rikeshi Meenalle ke na bawa amanarshi ..ki auri Ma'aruf dan Allah ...idanuwanta suka fara rufewa </div><div><br /></div><div> Kuka ta saki da karfi tare da ficewa da gudu ...a kofa ta bangaji mutun tsaye amma ta wuceshi ...ta fita tana kiran doctor ...</div><div><br /></div><div> Ma'aruf na tsaye idonshi a lumshe doctor yazo ya jashi yana fada mashi matarshi ta rasu ....</div><div><br /></div><div> Meenalle kuwa gurin ta suma ....ko bude ido Ma'aruf baiyi ba bare yaga yarda akayi da ita ...</div><div><br /></div><div> Bayan sun shiga office da doctor din ..Ma'aruf ya tambayeshi ...wacece cikin su ta bashi Kidney ...</div><div><br /></div><div> Ganin babu bukatar boyewa yanzu doctor din yace ...Meena Abubakar ....</div><div><br /></div><div> Idonshi ya lumshe hawayen dake makale suka gangaro ...</div><div><br /></div><div> Waya ya fito ya kira wani friend dinshi dake aiki airport yace yana son helicopter yanzu ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> bai kuma cewa komae ba ya nemi a bashi gawar Shamy ..</div><div><br /></div><div> Cikin wani box aka sakata sannan aka nufi airport da ita ...suka koma nigeria ......</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm*💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div>💧💧SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦Talented Writers Forum💦</div><div><br /></div><div><br /></div><div> *Godiya mai tarin yawa ga talented writer Allah ya hada kanku tare da hakuri da juna*</div><div><br /></div><div>_Islah tee_</div><div>_Zahra_</div><div>_Smart_</div><div>_Halieymerh_</div><div>_Mufeedah_</div><div>_da sauran mu gurin bara ya isa ba na rubutu ku duka💞_</div><div><br /></div><div>*Thank you so much for your well nd eniest wishes*</div><div><br /></div><div>*Mum twins*</div><div>*Aunty Sis*</div><div>*Khadija Candy*</div><div>*Bilkisu bilyaminu*</div><div>*Namesy Classic*</div><div>*Aunty Maijidda*</div><div>*Salamatun Inna*</div><div>*nd Ladies Novel world members*💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>83 to 84</div><div><br /></div><div><br /></div><div> A gidan Iyayenta aka mata sutura ...bayan sati biyu ...ya taka har gidan Kaka ...ya fada mata komae sannan ya nemi yaje gurin iyayen Meenalle ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Kaka baki yaki rufuwa ...ita da kanta ta kaishi har gidan Alhaji Abubakar ..lokacin su Rabi an murje ..ni kaina kasa ganeta nayi ...</div><div><br /></div><div> Maganar da Ma'aruf ya gayawa kaka ita ya maimatawa Rabi da Alhaji Abubakar ....sannan ya nuna yana bukatar aurenta kafin ya koma ..</div><div><br /></div><div> Alhaji Abubakar yace sae an nemi Meenalle anji ta bakinta ....</div><div><br /></div><div> Haka aka kira Meenalle a waya aka tambayeta ...</div><div><br /></div><div> Kasa cewa komae tayi ..sae kaka ta ce ...ta yarda ...</div><div><br /></div><div> ••°°••</div><div><br /></div><div> Biki ake amma bada sanin amarya ba ...komae an mata cikin gata da aminci ....</div><div><br /></div><div> Kaka kuwa baki yaki rufuwa .....haka hajiyar Abubakar sae nan da nan ake da dangin rabi ...</div><div> </div><div> Kudi kawae Abubakar ya tura aka sayar mata komae acan.....aka hada mata komae na jin dadi ....</div><div><br /></div><div>°°••°°</div><div><br /></div><div> Ma'aruf kuwa sae da aka gama komae sannan yama iyayen Shamy bayanin duk abunda ya faru sannan ya taho ...</div><div><br /></div><div> Meenalle kuwa tunda Kaka ta kirata ta fada mata an daura mata aure gabanta keta faduwa ...haka Ma"aruf bai kirata ba ko sau daya ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Karfe 8 din dare Ma'aruf ya dawo ...direct makarantar su ya nufa ...Soofy ya kira yace ta kira mashi Meenalle din ...</div><div><br /></div><div> Yana cikin mota ta iso sanye da maroon din hijab mai hannu ...cikin sanyin murya ta mashi sallama ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Ya amsa kasa kasa tare da dagowa ya kalleta ..wani abu ya tokare mashi kirji ....ya lumshe idonshi ....</div><div><br /></div><div> Shiga tayi ta zauna ...tana zama ya rufe kofar yaja motar .....</div><div><br /></div><div> bata ce mashi komae ba ..har suka isa wani katon gida ..ba wanda aka aje Shamy a ciki ba ....</div><div><br /></div><div> Ya fito ya yi gaba abinshi ...haka itama ta biyoshi cikin sanyi jiki har ta iskeshi falon tsaye ....</div><div><br /></div><div> Bayanshi ta tsaya kanta na kasa tana wasa da yatsunta da suka sha jan lalle ....</div><div><br /></div><div> Juyowa yayi idonshi a lumshe ya kira sunanta ...a hankali ...</div><div><br /></div><div> Bata dago ba ...amma ta amsa a hankali ...</div><div><br /></div><div> Na dawo dake rayuwata Meenatou ba wae don ina son haka ba.....</div><div><br /></div><div> Idonta ya ciko da kwallah ...bata yi tunanin gogesu ba ...</div><div><br /></div><div> Ya cigaba ....Meenatou duk da irin son da nake maki kina yarinya lokaci guda kin gogeshi ...zan maki adalcine saboda abunda kika man ...amma maganar so ..babu sam ...bazan so yarinyar da ta yada darajarta ba. .....</div><div><br /></div><div> Da sauri ta kalleshi ....tana nuna kanta da hannu .....daraja Ma'aruf ....</div><div><br /></div><div> Yes Meenatou ...ya fada idonshi na kanta ...</div><div><br /></div><div> Girgiza kai tayi ...tana fadin ...Nagode sossae ..Meenalle Maikamshi ...na fita fitina Allah ..ko ka manta</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Murmushi yayi kasa kasa yace ...Ta ya zan manta ....wucewa yayi ya shige wani daki ya barta tsaye ....bayanshi ta bi itama ta shiga ....</div><div><br /></div><div> Bai kalleta ba....ya cire suit din dake jikinshi ya fada toilet ...hijab dinta ta cire ...ta haye saman gado ta kwanta .....</div><div><br /></div><div> Tana kwance ya fito daure da towel ya tsaya gaban mirrow daga ya shafa wannan sae ya shafa wannan ...kamar mace ...nan da nan dakin ya dauki kamshi .....</div><div><br /></div><div> Da gefen ido ya kallota tana kwance ta rufe ido ....takowa yayi a hankali ya sauko pillow a kasa tare da shimfida bargo ...ya dawo ya sabeta ya dire ta saman shimfidar ya koma ya kwanta saman gado ....</div><div><br /></div><div> Wallahi Ma'aruf baran kwana a kasa ba duk abunka ..ta fada tana kallonshi ...</div><div><br /></div><div> Hararanta yayi yace ...idan bara ki kwanta anan ba ki koma dakinki ..</div><div><br /></div><div> Itama hararan ta sake mashi tana fadin ..haka kuma baran kwana ni kadae ba ...Na rantse maka da Allah baran kwana ko ina ba...</div><div><br /></div><div> Juya baya yayi ya kyaleta ...yana jin lokacin da tazo ta kwanta gabanshi ...don neman magana ma daura kanta tayi a hannunshi tayi pillow ...</div><div><br /></div><div> Baice mata komae har tayi bacci a haka ..gangarowa tayi ta shige kirjinshi ...ajiyar zuciya ya sake tare da gyara mata kwanciya ...sannan shima baccin ya daukeshi .....</div><div><br /></div><div> Ya rigata tashi da asuba ...yayi wanka tare da alwala ...ya dawo ya tadata yaga har ta tashi ...jallabiya ya saka ya tada sallah ...sae da yayi nafila sannan ya jirata ta fito ya ja masu jam'i ......</div><div><br /></div><div> Yana kwance wajen 9 ta fito cikin shirin makaranta ...tun daga sama har kasa ya bita da kallo ...sannan ya kau da kai. ...</div><div><br /></div><div> Ki sako Hijab ..sannan ...ya fada ahankali ...</div><div><br /></div><div> Bata ce komae ba ta sako hijab din ta fito tana tura baki ...mikewa yayi ya dauki keys yayi gaba ..Kamar kurame suke tafiya...</div><div><br /></div><div> Restaurant ya biya da ita sae tayi breakfast sannan ya wuce da ita makaranta ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ......</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div> 💦Talented Writers Forum💦</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>85 to 86</div><div><br /></div><div><br /></div><div>kasuwa ya wuce ya sawo masu duk abunda zasu bukata sannan ya dawo gida ya aje kayan ya wuce office ...</div><div><br /></div><div> lokacin da Meenalle ta dawo ...sannan ta samu damar zagaye gidan ...ba karamar dukiya aka kashe mata ba ...dakin da take tunanin nata ne ta shiga .....buda baki tayi tana kallon ikon Allah ....drawer ta bude akwatuna ta gani set Hudu masu shegen kyau ...da kyar ta saukosu duka ta zazzagesu kaf kasa tana dagawa ....</div><div><br /></div><div> Dae dae lokacin Ma'aruf ya shigo dakin ...jingina yayi da kofar ya kallonta ...sae da ta gama daga komae ...sannan ta dauko wata sarka da yan kunne ta aje gefe guda ....tana fadin ....Duk da bana magana da maikamshi bara ya dawo ya fada man yarda ya sawota ...</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi tare da barin dakin ba tare da ta sani ba ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> da kyar ta mayar da kayan cikin akwatunan ..amma ta kasa maida akwatunan inda suke .....</div><div><br /></div><div> Cikin lefen ta fito da Riga da siket na material milk colour ta aje bisa gado .....wanka tayi sannan ta saka kayan tare da sarkan da ta fito ....</div><div><br /></div><div> Yana kwance falo daga shi sae farar singlet da boxer ja idonshi a rufe ...... </div><div><br /></div><div> Ta dade tsaye tana kallonshi ....sannan ta matso kusa dashi ta dafa kujeran ...Uncle Ma'aruf ta fada a hankali...</div><div><br /></div><div> Banza yayi da ita kamar bacci yake. ...sajenshi ta shafa...shiru ya mata ...amma wani zafi yake ji a ranshi </div><div>..</div><div><br /></div><div> Ma'aruf dan Allah ka tashi kayi hakuri ...wallahi bansan me na maka ba ka yafe man ....ta fada kamar zatayi kuka ...</div><div><br /></div><div> shiru ya mata .....tasake cewa ...kaji to Dan Allah idan bara ka bude idon ba ka fada man nawa ka sayi wannan sarkan mai stone a ja ta cikin wadannan akwatinan ...</div><div><br /></div><div> Dariya sossae ta bashi ...amma ya danne ya bude idoshi ...ya murde hannun da ta shafi sajenshi dashi ...ta sake kara tana kokarin janyewa ....</div><div><br /></div><div> Tashi yayi zaune ...sannan ya sake mata hannun yana hararanta ....duk lokacin da kika kuma tabani sae na karya hannu ....yana gama fada ya shige daki ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Zama tayi gurin ta sake kuka tana rike da hannun....</div><div><br /></div><div> Jin kukan yake har cikin ranshi ...keys ya dauka ya fice daga gidan kwata kwata</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Lokacin da ya dawo da daddare har tayi bacci a inda ya barta ...wuceta yayi ya shige daki yayi wanka sannan yayi kwanciyarshi .....juyi kawae yake amma babu alamun bacci a idonshi ....ganin kwanciyar ba zata fishsheshi ba ya saka ya fito falon .....</div><div><br /></div><div> Kanta na bisa hannun kujera ...ya dauketa ya daura saman doguwar kujera ....</div><div><br /></div><div> Cikinta ya shafa yaji kamar bata ci komae ba ...ledan da ya shigo dashi ya dauko ...kazane da fresh milk sae dugheese ya zazzage cikin plate tare da knife ...</div><div><br /></div><div> Kumatunta ya dinga shafawa tare da hura mata iska ...tayi saurin mikewa tare da sakin sabon kuka ...</div><div><br /></div><div> Shiiiiiitttt ya daura hannunshi saman lebenta ...sannan ya tura mata plate din ....</div><div><br /></div><div> Mikewa yayi ya koma saman kujera ya kunna TV ...hararanshi kawae take ...suka hada ido ...jira take yace.. taci ..amma ya shareta ...</div><div><br /></div><div> Hawayen takaici suka gangaro mata ...ya dan saci kallonta ...ta bashi tausayi ...</div><div><br /></div><div> Kici mana Meenatou ....ya fada a hankali don ya gane abunda take so taji kenan ..</div><div><br /></div><div> Hawayen ta saka bayan hannu ta share tana fadin ...dama ko baka ce na ci ba yanzu nayi niyyar ci ....</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi kasa kasa ....baice mata komae ba ...</div><div><br /></div><div> Har ta koshi sannan ta dawo kusa dashi ta zauna kasan carpet .</div><div>..</div><div><br /></div><div> Plate din ta mika mashi ...tana kallonshi ..</div><div><br /></div><div> Harara ya banka mata ....tayi saurin dauke kai tana fadin ..</div><div>dan Allah kaci kaima ...</div><div><br /></div><div> Murmushi ya sake kasa kasa yace ..ba bukata ...</div><div><br /></div><div> Please ....ta fada ..</div><div><br /></div><div> Girgiza kai yayi yace ...A da Meenatouta tayi forcing dina naci irin haka .. yanzu ke ba tawa bace ...kuma baran ci ba ....ya mike ya shige daki ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Ni din taka ce ...ta fada a hankali sannan ta mike ta shiga dakin </div><div><br /></div><div> Kayanta ta cire daga ita sae inners...sannan ta daura towel ta shige toilet ....akan idonshi tayi komae har ta fito ....duk abunda yake shafawa sae da ta shafa ....sannan ta leka fuskarshi taga idon a rufe ...murmushi ta sake tana murza hannu..</div><div><br /></div><div>..</div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>87 to 88</div><div><br /></div><div>Pillow ta sauke kasa tare da shinfida bargo ....sannan ta hawo gadon ta koma gabanshi ta dinga murginoshi kasa ....</div><div><br /></div><div> Yana jinta yayi banza da ita yasan dai barata iya daukarshi ta maidashi kasa ba. ..sae uban nishi take ...sae da ta gaji dan kanta taga bara ta iya maidashi kasa ba ....sannan ta janyo hannunshi ta daura kanta ....bata fi minti 10 ba ya gane bacci ya dauketa ta gangaro jikinshi ...ya saka hannun ya gyara mata kwanciyar sannan shima baccin ya daukeshi ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°•• </div><div><br /></div><div> Ganin bata fito ba har karfe 9 ya saka ya leka dakinta ....tana kwance saman gado ido a rufe ....</div><div><br /></div><div> Meenatou ...ya kirata a hankali ....</div><div><br /></div><div> Shiru ta masa ....Ki fito ina jiranki falo ....ya wuce abunsa ...</div><div><br /></div><div> Yayi minti 20 yana jiranta amma shiru bata fito ba ......</div><div><br /></div><div> Dan karamin tsaki ya sake lokacin da ya duba agogon dake makale a hannunshi ....</div><div><br /></div><div> Ya koma dakin a fusace ya tsaya bakin gadon tare da dago kanta ....</div><div><br /></div><div> Da sauri ya taro kan ...ganin ya koma da kanshi ....jijjiga yayi ...yana kiranta ....sae lokacin ya lura da ba lumfashi a jikinta .....</div><div><br /></div><div> Daukarta yayi ya sakata mota ya ja motar da gudu ...tun yana tafiya ya kira doctor </div><div><br /></div><div> Yana zuwa suka amsheta emergency ....kusan 1hours sannan aka samu numfashinta ya dawo normal shima da taimakon oxygen ...</div><div><br /></div><div> Ma'aruf na wajen dakin sae..kae da kawowa yake ...doctor na fitowa ya tareshi yana tambayar lafiya ...</div><div><br /></div><div> ce mashi yayi ..zafin masassara ne ke damunta ... da marece aka sallamesu suka koma gida ....</div><div><br /></div><div> A gate din gidan ta saka mashi kuka wae barata iya takawa ba ....jikinta ya taba yaji da zafi ...sannan ya dauketa suka shiga ...</div><div><br /></div><div> </div><div>Dakinshi ya direta ...ya shiga kitchen ya dafa mata ruwan zafi ..sannan ya dafa mata kwae guda biyu ya kawo mata ....Ya aje saman stool din dake gefen gadon ya fita ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Sae da yayi kusan Awa daya sannan ya dawo ...yarda ya aje haka ya tarad da abunshi ...ya kalleta ta gefen ido ...ta maida hankalinta kan wani dan karamin littafi dake aje gefen gadonshi ...</div><div><br /></div><div> Bakya jin yunwa ne Meenatou ...ya fada tare da zama gefen gadon ...</div><div><br /></div><div> Bakya jin yunwa ne Meenatou ...ta maimaita abunda ya fada tare da sake mashi harara ..sannan tace ....ko wannan abun zaya shekara anan baran ci ba duk da ina jin yunwan ..tunda nima lokacin da baka lafiya idan naje gidanku ai a baki nake ba ...nima din sae ka rama man ..har dukana ake a makaranta idan na makara ..to wallahi sae ka rama man .. </div><div><br /></div><div> Murmushi yayi kаsa kasa tare da fadin ...Dama Halinki ne Meenatou ...gori ba ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Sannan ya janyo flask din ya hada mata tea din tare da dauko sandwitch ya mika mata ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Ka Wanko hannunka ta fada tana hararanshi ...</div><div><br /></div><div> Ni ai ban taba hamatar ko wane kato ba ...ya bata amsa ba tare da ya kalleta ...</div><div><br /></div><div> Nima da nake tabawa ai yanzu na daina ....</div><div><br /></div><div> Sae ta mata? ...ya tambayeta tare da kura mata ido ...</div><div> </div><div><br /></div><div> Bata ce komae ba ta koma ta kwanta tare da rufe idonta .....</div><div><br /></div><div> Ki tashi kici ....ina da aikin yi da yawa ...ya fada tare da kallonta ...</div><div><br /></div><div> Bata motsa ba tace ...Alhamdulillah ...</div><div><br /></div><div> Kafada ya dage tare da ficewa daga dakin .....</div><div><br /></div><div> Bai kuma dawowa ba sae bayan isha'i ....</div><div><br /></div><div> lokacin ta dan tashi tayi wanka tare da sallah sannan ta koma ta kwanta amma jikinta kamar wuta ga Uwar yunwar dake damunta. ..kuka take a hankali ...</div><div><br /></div><div> Ya shigo da sauri ya shige toilet yayo alwala tare da kabbara sallah .. ..</div><div><br /></div><div> Sannan ya janyo ledar daya shigo da ita ya fito da abunda ke ciki ...</div><div><br /></div><div> Ya zauna yaci ya koshi sannan ya yo wanka...sae lokacin ya leka fuskarta ...tare da duba duba abunda ya bar mata ...</div><div><br /></div><div> Da Sauri ya kira sunanta ....Meenatou ...</div><div><br /></div><div> Tana ji tayi banza dashi ...hannu ya sanya ya cire hannunta dake saman goshinta ...</div><div><br /></div><div> Zafi sossae yaji jikinta ...nan da nan ya rude ..ya janyo kayan da ya. shigo dasu ..ya fito da Fresh milk ya bata ...da yake yunwa take ji ..batayi gardama ba ta amsa. ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div><br /></div><div><br /></div><div>💧💧SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>89 to 90</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Towel ya jiko da ruwa sannan ya dawo zaya jika mata jiki ....</div><div><br /></div><div> Bargon data nannade jikinta dashi ya cire tare da tadata zaune zaya cire man shirt din dake jikinta ....</div><div><br /></div><div> Hannunshi ta rike ...duk da zafin masassaran dake damunta bai hana ta sake mashi harara ba tare da fadin. ...Meye zaka cire man riga ...</div><div><br /></div><div> Karamin tsoki yaja ..yace ...cire hannunki daga jikina Meenatou ...</div><div><br /></div><div> Allah Ma'aruf bara ka ga jikina ba ....ta fada kamar zatayi kuka ..</div><div><br /></div><div> Hararanta yayi tare da fadin..Meye a jikin naki da zan kalla Meenatou ...jikin da kowace kazama ta gama kallo ..mtsee ..</div><div><br /></div><div> Hannunta duka biyu ya hade ya rike da hannu guda tare da cire mata rigar ...ya barta daga ita dae bra .....haka ya zare Siket din ya bar mata Pant ...sae uban ihu take mashi amma ko kulata bai yi ba ....</div><div><br /></div><div> Har sae da zafin jikinta ya ragu sannan ya sake hannun sae lokacin ya lura da tayi bacci ....</div><div><br /></div><div> Har ya dauko rigar zaya maida mata ya tsaya tare da kurawa surarta ido ...tabbas Meenalle ta hadu ta ko ina ....</div><div><br /></div><div> Sauke ajiyar zuciya yayi tare da jefar da rigar gefe guda ...ya mike yayo wanka ya kashe haske sannan ya dawo ya kwanta ....janyota yayi ya rungume yana maida numfashi a hankali ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Da asuba ta rigashi tashi ....ta kwace kanta daga rikon da ya mata ...tare da sake ihu ganin yarda take ...lokacin jikinya ya koma lafiya lau ...</div><div><br /></div><div> Jikinshi ta haye tare da dukanshi da pillow tana fadin Allah ya isa ka gani Maikamshi ...ganin hakan bai mata ba ya saka ta daga jallabiyarshi ta zare hannuwan ta cireta ...ta barshi daga shi sae boxer dake jikinshi tare da sake mashi cizo a kumatu tana fadin ...Nima na rama ...kuma baran kara kwana da kai da mugu ....ta dauki rigarta ta fice daga dakin ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Tana fita ya mike tare da girgiza kai ..don duk abunda take yana jinta shareta kawae yayi ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> ••°°••</div><div> </div><div> Lokacin sun gama Exam ba makaranta ..da safe ta hada masu Break su zauna su ci tare sae dae babu magana sae harare harare ... </div><div><br /></div><div> Ranar da daddare taki zuwa dakinshi ...duk da take ...haka shima ya kwanta sae juyi yake ...kusan Karfe biyu yaji ta bude kofa a hankali tare da kwanciya kusa dashi .....bai yi motsi ba sae da ya tabbatar bacci ya dauketa sannan ya janyota jikinshi ...a haka bacci ya daukeshi ......</div><div><br /></div><div> tunda Asuba ta sulale ta koma dakinta a tunaninta bai sani ba ...</div><div><br /></div><div> Da Safe da ya fito ..kamar abun arziki ta tareshi tace ..</div><div><br /></div><div> Good Morning ...</div><div><br /></div><div> Ya dan kalleta kafin yace ....Morning ...sannan ya ja kujera ya zauna ...</div><div><br /></div><div> Ta hada mashi komae sannan ta tura mashi gabanshi tana fadin ...kasan me yasaka na gaidaka ?,..</div><div><br /></div><div> Girgiza mata kai yayi yana kallonta ...</div><div><br /></div><div> Ta washe baki tana fadin ...so nake bakin ciki ya dameka na kwana ni kadae ban mutu ba ...ta watsa mashi harara ...</div><div><br /></div><div> Dariya ya sake har da rike ciki .....</div><div><br /></div><div> Me kakewa dariya ..? ta tambayeshi tana hararanshi. ..</div><div><br /></div><div> Hararan ya maida mata ba tare da yace mata komae ...har ya gama breakfast dinshi ya mike ya tafi office ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Haka da daddare ranar yana jin lokacin da ta dawo jikinshi yayi murmushi ya janyota ya rungume ...da asuba yana jin tana kokarin kwace kanta amma yaki sakinta ....</div><div><br /></div><div> Tayi kwance sae Mazurai take ...ya bude ido tare da zuba mata harara ...</div><div><br /></div><div> Ta hadiyi yawu tare da zuba mashi harara itama sannan tace ....</div><div><br /></div><div> Daga zuwa tayar dakai Sallah sae ka rikeni ....</div><div><br /></div><div> Harara ya zuba mata yace ...ta ina kika shigo ...</div><div><br /></div><div> Ta kalli kofar tare da fadin ...ta kofa mana ...</div><div><br /></div><div> Keys din kofar ya fito daga kasan filon daya daura kanshi ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div><br /></div><div><br /></div><div>💧💧SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>91 to 92</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Turo baki tayi tare da fadin ...To Maikamshi na dawo din dakinka sae akayi me ..dadin abun ma ba cire maka kaya nayi ba nace zan gasa maka jiki don na kalleka ..kuma anan din ma zan dinga kwana kullun duk tsiyarka....tana gama fadar haka ta mike tare da fadawa toilet ..</div><div><br /></div><div> dariya ya dinga yi sossae yana jinjina baki irin na Meenalle ..gashi dae ya nuna mata ya san nan take kwana maimakon ta nuna taji kunya sae ma ta nuna ta fishi baki ....</div><div><br /></div><div> </div><div><br /></div><div>°°••°°</div><div><br /></div><div> Zamansu haka ya fara damunta ..har lokacin bai fada mata asalin laifinta ba ..sae dae ya dinga jifarta da maganganu ......</div><div><br /></div><div> Soofy ta kira a waya ta fada mata matsalarta ....</div><div><br /></div><div> Shawarwari ta bata sossae tace ta dameshi ya fada mata laifin da tamashi ..sannan kar tayi zuciya baa banza yake mata haka ba ....</div><div><br /></div><div> yana zaune falo ...rike da wani novel .. tayi sallama ba tare da ya kalleta ba ya amsa mata ...</div><div><br /></div><div> Hannushi ta bude tashige jikinshi tare da maidawa ta rufe ....</div><div><br /></div><div> Ya dan Saci kallonta ...tana sanye da karamar riga pink sae three quater baki ....manyan kalaba ne akanta ....ya saki ajiyar zuciya tare da maida kallonshi ga littafin ....</div><div><br /></div><div> Ta rasa yarda zata mashi magana ...shimq ma ya gaji da zaman da take a jikinshi Allah kadae yasan me yake ji ....</div><div> Ya rufe littafin tare da zareta ya maidata saman kujera yana fadin .</div><div><br /></div><div>Menene Meenatou ..</div><div><br /></div><div> Bakomae ...Dama magana nake son muyi ...ta fada a hankali ...</div><div> </div><div> Ina saurarenki ....ya fada tare da lumshe ido..</div><div><br /></div><div> Dan Allah ina so ka fada man abunda na maka ....</div><div><br /></div><div> Banda lokacin wannan maganar Meenatou ...tashi ki fitar man daga falo indae wannan ya kawoki .</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div> Kayi hakuri dan Allah .....Da Kana sona Ma'aruf ...amma yanzu me yasa kake man haka ...ta fada a hankali ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Saboda bana sonki yanzu ...ya fada kai tsaye ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Kana sona mana ...ta fada tare da sakin kuka ..</div><div><br /></div><div> Idanuwanshi sukayi jawur ..cikin tsawa yace ..karya kike bana sonki Meenatou ...ya karashe maganar tare da fadawa saman kujera ya dafe kanshi</div><div><br /></div><div> Kai ta girgiza tare da fadawa dakinshi da gudu ...</div><div><br /></div><div> Drawer dinshi ta dinga janyowa tana kuka har ta fito da glass din da ribbon din da ta bashi yake ...sannan ta fito dakin ...</div><div><br /></div><div> Yana ganin ta fito ya mike da sauri tare da nunata yana fadin ...ki mayar dashi Meenatou .</div><div><br /></div><div> Cikin kuka tace.. idan baka sona me kake da wannan ...</div><div><br /></div><div> Ki maidashi nace Meenatou ..ya fada tare da nufota ...</div><div><br /></div><div> Kasa ta jefar dashi da karfi glass din ya fashe ...</div><div><br /></div><div> Daga hannu yayi da niyar marinta yayi saurin rufe ido ....ta cikin fasasshen glass din ta bi zata wuce ....</div><div><br /></div><div> Da sauri ya duka tare da saka hannunshi inda zata taka saman kwalaban ...</div><div><br /></div><div> Rufe ido tayi zata daura kafar a hannunshi Ta taka ta wuce ....amma ta kasa ...kuka ta sake da karfi tare da juyawa ta canza hanya da gudu .....</div><div><br /></div><div> Binta yayi da kallo ...hawayen dake makale a idonshi suka sauko ...ya dauke ribbon din ..sannan ya kwashe kwalbar ya koma daki ....</div><div><br /></div><div> °°••°°</div><div><br /></div><div> Kusan satinsi biyu a haka ...gurin bacci kawae ke hadasu </div><div><br /></div><div><br /></div><div> Duk rintsi basu raba makwanci duk da ba wani abu ke shiga tsakaninsu ba ...sae dae ta daura kanta a hannunshi ...idan tayi bacci ya maidota jikinshi ...</div><div><br /></div><div> Soofy ta sake kira tagaya mata yarda sukayi ...</div><div><br /></div><div> Cewa tayi Meenalle kiyi hakuri ki sake jaraba tambayarsa karkiyi zuciya ...indae kinyi imani da soyayyar da yake maki tun ta yarinta to har yanzu akwaeta ....</div><div><br /></div><div> To kawae tace ...zata je amma wannan shine na karshe ...idan ya fada mata to ..idan kuma bai fada mata ba. ..sae dae su cigaba da zama haka ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ....</div><div><br /></div><div> </div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div> 93 to 94</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div>Shigowa Meenalle tayi yana zaune yana kallo ....ta samu guri ta zauna ..tana kallonshi ...</div><div><br /></div><div> Mr Ma'aruf ....ta fada a hankali ....</div><div><br /></div><div> Ido ya dago a lumshe ...yace . Meenatou Wani abu kike bukata ....</div><div><br /></div><div> Girgiza kai tayi a hankali tana wasa da zoben dake hannunta. ...</div><div><br /></div><div> Ok. .ya fada tare da cigaba da kallonshi ...</div><div><br /></div><div> Ganin baida niyar kulata ya saka ta mike ta koma kusa da kujeran da yake zaune. ..</div><div><br /></div><div> Ta kwantar da murya tace ...Kayi hakuri Ma'aruf ...wallahi bansan laifin da na maka ba ...Dan Allah ka yafe man ...</div><div><br /></div><div> Ya danyi murmushi ciki ciki yace ...Meenatou kenan na rasa kalmar zan bi wajen fada maki ki daina zuwa inda nake amma kin kasa ....please ki fice daga falon nan ....</div><div><br /></div><div>Daga kai tayi tana kallonshi idonta cike da hawaye tace ..Dan Allah Ma'aruf ka fada man laifin da na maka ...wallahi bansan nayi maka shi ...tun ina karama muka rabu ..yaushe har mukayi haduwar da ka tsaneni kuma wane kalar laifi na maka ...</div><div>Kayi hakuri dan Allah nice fa Meenalle Ma'aruf ka tausaya man mana. ...</div><div><br /></div><div> sossae yaji tausayinta ...sae dae yana tunano pictures din da Raliya ta nuna mashi ...tsawon shekaru masu yawa da suka wuce ....lumshe ido yayi ...yace ...Idan har Meenatou zaki iya bawa wata wace jikinki shekaru da suka wuce tun kina yarinya to yanzu fa ....</div><div><br /></div><div> Kuka ta fashe dashi tace ...ban fahimceka ba Ma'aruf ...wallahi ban gane me kake nufi ba .....</div><div><br /></div><div>Mikewa yayi ya daga hannunta sama tare da janta har zuwa kofar falonshi...ya bude tare da turata waje. ...karki kuma zuwa falona ...</div><div><br /></div><div> Kuka ya kwace mata ta toshe bakinta ta juya da gudu ...sae ji tayi ya kamo hannuta tare da sakata a jikinshi ya rungumeta ....</div><div><br /></div><div> Daga kai tayi sossae tana kallonshi ...sannan ta maida kanta a kirjinshi ...tana jin lokacin da ya sake ajiyar zuciya ...a haka ya zauna saman kujera tana kirjinshi ...sun dade a haka sannan ya dago kanta yana kallonta ...</div><div><br /></div><div> Meenatou ...yaja sunan...</div><div><br /></div><div> Bata amsa ba sae da ta kalleshi ...kin san Raliya ...ya tambayeta ..</div><div><br /></div><div> Girgiza kai tayi a hankali tana share hawaye ......</div><div><br /></div><div> Mikar da ita yayi ya zaunar da ita sannan ya shiga dakinshi .</div><div>ya fito dauke da wata waya ya kunna tare da mika mata a hannu ...</div><div><br /></div><div> Da sauri ta yardar da wayar tare da sakin kuka ....take ta tuno da abunda ya faru lokacin da ta shiga gidan wadannan yan iskan ...</div><div><br /></div><div> Wallahi dole suka man Ma'aruf ...ta fada tare da buga kanta jikin hannun kujera ...</div><div><br /></div><div> Fuskarta ya kamo ya saka hannunsa cikin gashinta ...yana kallonta ...</div><div><br /></div><div> Kwantar da kanta yayi bisa kirjinsa ...Sorry Meenatou ...i trust you yanzu kinji ko ...kiyi hakuri ..na yarda baki aikata ba ...</div><div><br /></div><div> Kuka take sossae bata ga laifinshi ba abunda ya mata ...don ta tabbata kara karuwa mai bin maza da yar lesbian ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Cikin kuka take fadin wallahi banyi ba Ma'aruf ...me yasa ka yarda ...</div><div><br /></div><div> Lallashinta ya dinga yi har ya samu tayi shiru. ..shima yayi nadamar abunda ya dinga mata ...ashe bada hakkinta ba .....</div><div><br /></div><div> a haka bacci ya dauketa sae ajiyar zuciya take ....Allah kadae yasan iya kissing din da ya mata ...kafin ya dauketa ya kaita dakinshi ya kwantar da ita saman gado ya fita ....</div><div><br /></div><div> Cikin wayar ya duba ...number raliya ya gani ...yayi hamdala Allah yasa bai gogeta ba ...tunda dama tunda abun ya faru da ya dauki wayar bai kuma kunnata ba ....</div><div><br /></div><div> Ringing daya ta dauka ...ya tambayeta inda take ...da yake bata ganeshi ba tunda ba da numbershi ya kirata ba. . ta mashi kwatancen gidan da suke ...da yake ta dawo da taga nigerian ba harka</div><div><br /></div><div> Direct can ya nufa ....yana zuwa yacewa mai gadin ya kira mashi ita ....</div><div><br /></div><div> Ta fito rike da sandar guragu tana tafiya .....lumshe ido yayi lokacin da ta iso ...</div><div><br /></div><div> Mr Ma'aruf ...ta fada tana washe baki ...</div><div><br /></div><div> Alhamdulillah Raliya ...yaushe kika zama haka ....</div><div><br /></div><div> Tabe baki tayi tace ...accident muka samu wallahi ..amma dad yace zaa gyara man kafar ta koma kamar yarda take da ...idan aurena kazo karka damu da wannan ...</div><div><br /></div><div> Dariya ya sake ...yace ai ta riga ta zama haka Raliya ..wannan shine makomar munafiki...kin rabani da Meenatou kike tunani ...well da zuwa nayi ki fada man wace shegiyace tayi forcing din Meenatou ...amma yanzu yarda na ganshi ma naji dadi ..dan nasan soon itama waccen zata hadu da tata kalar masifar ....</div><div><br /></div><div> Yana gama fadar haka ya shige mota ya barta tsaye .....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div>95. to. 96</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Kwafa tayi ta shige cikin gidan tana dogara sandarta ....</div><div><br /></div><div> Yan matane birjit sunata shashansu ....kusa da wata taje ta zauna ...tana rada mata magana a kunne ...murmushi sukayi tare da tabawa ...</div><div><br /></div><div>••°°•• </div><div><br /></div><div> Zaune ya isketa tana cin Apple ...kusa da ita ya zauna yana murmushi ...</div><div><br /></div><div> Har kin tashi ....ya fada tare da kanne mata ido ...</div><div><br /></div><div> Da kai ta bashi amsa sannan ta mika mashi wanda ke hannunta ...</div><div><br /></div><div> Bai amsa ba sae dae ya bita da ido tare da janyota jikinshi ....</div><div><br /></div><div> Am sorry Meenatou ....ya fada a hankali ...</div><div><br /></div><div>Batace komae ba ta saka mashi apple din a baki tare da mikewa ta dauko mashi dinner ....</div><div><br /></div><div> A plate ta zuba mashi ta tura mashi gabanshi kamar yarda ta saba ...sannan taja nata ...</div><div><br /></div><div> Kujeran da take zaune ya dawo ya dagata sama ya zauna sannan ya daurata saman cinyarshi ....ya karbi plate din ya debi tare da bata a baki ....</div><div><br /></div><div> aa Maikamshi ....ta fada tare da kau da kai gefe guda ....</div><div><br /></div><div> Why Meenatou ....? .</div><div><br /></div><div> Ka manta abunda kace ...ta fada tare da kura mashi ido ...</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi tare da girgiza kai ...Me na fada Meenatou ...</div><div><br /></div><div> Hararanshi tayi tare da fadin ...ka manta kace bara ka taba bani abinci da hannunka ba ...</div><div><br /></div><div> Dafe kanshi yayi ...dama yasan zaa rina. yanzu komae ya mata baya yasan sae ta dinga tunawa tana fada mashi ...</div><div><br /></div><div> Cikin lallashi ya shafi wuyanta ....tare da langwabar da kai yace ...To ai lokacin Meenatou kin bata man raine ...</div><div><br /></div><div> Harara ta banka mashi tace ...yanzu fa. ...</div><div><br /></div><div> to yi hakuri na tuba kinji ko ...ya fada tare da mika mata abinci ..</div><div><br /></div><div> Karba tayi tare da kwafa ....</div><div><br /></div><div> Shi ya rigata fitowa daga wanka ...ya shinfida tarduma yana jiranta ....</div><div><br /></div><div> Sanye da kayan bacci ta fito daga toilet din....</div><div><br /></div><div> Sabon salo ...ya fada a ranshi ...bai san taji shi ba ...sae da ta banka mashi harara tare da hayewa gado abinta ..</div><div><br /></div><div> Meenatou ...ki sauko muyi sallah ko ...? .</div><div><br /></div><div> Nayi a toilet ...ta fada tare da gyara kwanciya ...</div><div><br /></div><div> Girgiza kai yayi ya tada sallah shi ya gama sannan ya hawo gadon tare da janyota ...</div><div><br /></div><div> Kin tuna?,...ya fada cikin kunnenta ..</div><div><br /></div><div> Girgiza kai tayi tana kallonshi...</div><div><br /></div><div> Lumshe ido yayi ..yace ...lokacin da kika ceman malamarku bata sallah ..yanzu ai kin gane dalilin rashin yinta ...</div><div><br /></div><div> Duka ta kai mashi a kirji tare da lafewa tana dariya ...</div><div><br /></div><div> Shima dariyar yayi yana fadin ...I love you Meenatou you're my everything ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Tana zaune taji Sallama ...ta mike tare da daukar hijab ..</div><div><br /></div><div> Tana bude kofar ta sake uban Tsalle tare da rungume kaka ...</div><div><br /></div><div> Imagine kakata ...ta fada tana dariya ...</div><div><br /></div><div> Hajiya tayi zuru tana kallonta ...sae da kaka ta buge mata hannu tana fadin ...baki ga hajiya bane ..</div><div><br /></div><div> Turo. baki tayi tace. ..na ganta ..ai bata sona ...</div><div><br /></div><div> naki kaniyarki Meenalle ..bata sonki ta hawo jirgi kamar zamu fado tazo inda kike ....</div><div><br /></div><div> Ma'aruf dake tsaye jingine da kofa tunda suka shigo ..sam bata lura dashi ba ...</div><div><br /></div><div> Ya ja hannu hajiya yana murmushi yace ...Taho hajiya rabu da ita zata neme mu ne da kanta ...</div><div><br /></div><div> Sae lokacin tasan tare suke ...ba kunya ta nufeshi tare da rungumeshi ta mashi kiss a kumatu ...</div><div><br /></div><div> Oyoyo ......</div><div><br /></div><div> Hancinta yaja a hankali har ta saki kara ...yace ...baran amsa ba ..</div><div><br /></div><div> Ta dan ja baya kadan tare da waro idanu tana kallonshi ...acikin shagwaba tace ...Why ..</div><div><br /></div><div> Hannu ya mika mata ta matso kusa dashi sannan ya kalli hajiya ya kalleta ...</div><div><br /></div><div> Murmushi tayi taje ta rungumi hajiyar tana mata sannu da zuwa ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>97 to 98</div><div><br /></div><div> </div><div> Bayan sun hutane Kaka ta kurawa Meenalle ido tace ..</div><div><br /></div><div> Meenalle banga alamar samun da ba da wuri ....</div><div><br /></div><div> Kaka a Ina ...ta tambayeta cikin rashin fahimta ..</div><div><br /></div><div> to ba hausa ina nufin banga ciki ya fito ba ...</div><div><br /></div><div> Ta sake dariya tare da kwalawa Ma'aruf kira ....yana tsaye yana shan ruwa gaban fridge ya iso yana tambayarta lafiya da ido ..</div><div><br /></div><div> Hannunshi ta janyo tare da zaunar dashi kusa da kaka tace ....Fadawa kaka me kace ..</div><div><br /></div><div> Me nace kuwa Meenatou ....ya tambayeta a hankali ..</div><div><br /></div><div> Harara ta sake mashi ...ya saurin dafe kai ...yasan Meenalle da naci ta yiyu wata magana ya mata shine bata hakura ba zata tada ta yanzu ...</div><div><br /></div><div> Lokacin da kace bana da ko. ...</div><div><br /></div><div> bata karasa ba ya tashi tare da jan hannuta da karfi ya shige da ita kitchen ...</div><div><br /></div><div> Am sorry Meenatou ...baran sake fadar komae ba ...</div><div><br /></div><div> Harara ta sake mashi tana fadar ...naji to ka sake man hannu ko ....</div><div><br /></div><div> Zan sake amma karki sake fadar komar kinji ko ...ki manta ...</div><div><br /></div><div> In manta me ..har cewa da kayi karuwa ta ...</div><div><br /></div><div> bakin ya murde ta sake kara ...ya daure fuska sossae ...yace ...</div><div><br /></div><div> Kar na kuma jin wannan kalmar a bakinki ....me kika hadawa su kaka .</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Yanzu dae zaka tayani mu hada masu ..ta fada tare da kwantowa jikinshi ....</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi suka fara aikin tare sae da suka gama girkin suka gyara kitchen din tare </div><div><br /></div><div><br /></div><div> Kwanansu goma cif ...tun Meenalle bata sakin jiki da Hajiya har ta koma tana sakin jikinta kamar yarda take da kaka ...</div><div><br /></div><div> Ranar da suka tafi kuwa kuka ta yini mashi ...sae da kyar ya samu ya lallasheta tayi shiru ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Da yake rigima take ji ...ko abinci bata masu ba ...fita yayi ya sawo masu abinci ...inda yake sawo wa ya samu sun rufe ...sae ya sawo mata kaza da ice cream ya dawo ....</div><div><br /></div><div> Tana kwance bisa kujera ya dawo ko dan oyoyon da ta saba mashi batayi ba ...ya wuceta ya shiga kitchen ya dauko plate ya juye da knife sannan ya dawo falon ...</div><div><br /></div><div> Ya leka fuskarta tare da kiran sunanta a hankali ...Meenatou ...</div><div><br /></div><div> Zaune ta tashi tana sharar kwalla ...da sauri ya rungumota ..</div><div><br /></div><div> Ya Salam Meenatou ...kukan ne har yanzu ...Sorry yi shiru kinji ko ...Muna next month zamu je ....</div><div>Da sauri ta washe baki ...tana fadin da Gaske ...</div><div><br /></div><div> Daga mata kai yayi alamar eh ...tare da janyo plate din </div><div><br /></div><div> sauko kici ...</div><div> </div><div>Saukowa tayi tana cin abunta ba tare da ta sake cewa komae ba ...sae da ta koshi sannan ta kalleshi tana murmushi tace ...</div><div><br /></div><div> Kasan dama ina son kazar amare ..amma wadda na taba ci bata kai dadin ta nan ba ...</div><div><br /></div><div> Hararanta yayi yana fadin ..waya baki wata kazar amare ...</div><div><br /></div><div> Musa ya sawo man ita ...amma karamace bata isheni ba ...</div><div><br /></div><div> Baki ya tabe yace. ..Bata amaren bace shi yasa kika cinye...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Allah itace....kuma ban rage ko kadan ba ....</div><div><br /></div><div> Dawowa yayi kusa da ita tare da janyo hannunta yana murzawa ....</div><div><br /></div><div> Idan na sawo maki ta amaren zaki cinye ...ya fada dae dae kunnenta</div><div><br /></div><div> Harara ta sake mashi tana fadi ...dukanta kuwa .. .</div><div><br /></div><div> Girgiza kai yayi tare da jan hancinta .....</div><div><br /></div><div> Idan na sawo maki ta amaren ma Meenatou bara ki ci ba ....</div><div><br /></div><div> Giranta ta hade tana fadin Kana wasa da ni ...</div><div><br /></div><div> Ko ? .. ya tambayeta .....</div><div> </div><div> Eh .....</div><div><br /></div><div>Zakiyi bayani da kyau ...ya fada tare da mikewa tsaye ...</div><div><br /></div><div> Kaima din zakayi bayani .....ta fada tana hararanshi ...</div><div><br /></div><div> Hannunta ya janyo ta mike tsaye yana kokarin zura hannunshi cikin rigarta </div><div><br /></div><div> </div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div>99 to 100</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Saurin rike hannunshi tayi ..Meye haka ...ta fada kamar zatayi kuka ...</div><div><br /></div><div> Bayanin nake so ki sakani nayi da kyau ...</div><div><br /></div><div> Bafa irinshi nake nufi ba ....ta fada tare da dukar da kanta kasa ....</div><div><br /></div><div> Hmm ....kawae yace ..ya saketa ya shige daki ...bayanshi ta bi ....tana murmushi ita kadae ...ya dan juyo ya kalleta tayi saurin juya baya itama ....murmushi ya sake sannan ya juya ....</div><div><br /></div><div>°°••°°</div><div><br /></div><div> Kayan Sport ya aza mata saman jiki ....</div><div><br /></div><div> Ta waro ido tare da kallonshi ..har ya sako nashi ...riga da wando sae hula tare da safar hannu da takalmi ...da yake kayan yellow ne ...sae sukayi bala'in mashi kyau ...abunka da fari ....</div><div> </div><div><br /></div><div> Ki tashi kin canza kayan ..ko sae na canza maki da kaina ...ya fada tare da kamo hannunta ....</div><div><br /></div><div> Harara ta sake mashi tare da cire siket din dake jikinta ta saka wandon ...sannan ta juya mashi baya </div><div><br /></div><div> Bude man zip din ...ta fada a hankali ....</div><div><br /></div><div> Zip din rigar ya zage mata ...ya kai hannu ya shafi wani digon baki dake tsakiyar bayanta ...sannan ya saka hannu ta baya ya karbi rigar daga hannunta ...</div><div><br /></div><div> Hannunta ta daga sama ya zura mata rigar ...sannan ya duka ya dago kafarta ya daura saman cinyarshi ya saka mata takalmin ...tare sa safar hannu sa hula ...ya ja hannunta ...</div><div><br /></div><div> Wani labule ya daga ...wanda ke facing din side dinta ....ta bishi da kallon mamaki ganin koface a gurin ...don duk zamanta bata san meye a gurin ba ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Wani abu ya danna a jikin kofar ...glass din ya bude suka wuce ....sae da suka wuce wani dan corridor sannan suka isa wani katon fili ....</div><div><br /></div><div> Ido ta bude tana kallon gurin ...kamar baa gidan ba ...</div><div> </div><div><br /></div><div> Gurin yayi masifar kyau ...har da filin football gefe guda an zagayeshi da net ...sannan swimming pool shima zagaye da net din...</div><div><br /></div><div> Sae gurin table tennis da volley ball hade ...</div><div>Gefe daya kuma flowers ne masu shege kyau ....ganin ta sake baki tana kalle kalle ya saka ya kwanto bayanta ...</div><div><br /></div><div> Me kike so muyi aciki ...</div><div><br /></div><div> Ido ta waro tare da nuna mashi Volley ball din ...</div><div><br /></div><div> Oya let start ....ya dauko kwallon tare da wullo mata ...</div><div><br /></div><div> Ka fara buguwa ...ta fada ban mata iya komae ba .....</div><div><br /></div><div> Sae ya bugo mata Ball biyar bata maido mashi ko daya ba ...amma da ta samu ta bugo mashi sae ta hau tsalle tana mashi gwalo ..</div><div><br /></div><div> Bata iya komae ba Sae masifar rintu ....har sae da aka fara kiran magrib sannan ya ce ta taho su koma ciki ...</div><div><br /></div><div> Zubewa tayi gurin ta mike kafa tana nishi ...</div><div><br /></div><div> Mene Meenatou ...kin gaji ko ...ya fada tare da dagata sama ...</div><div><br /></div><div> kafana baran iya tafiya ba ....ta fada kamar zatayi kuka ..</div><div>Da sauri ya duba kafar baiga abunda ya sameta ba ...</div><div><br /></div><div>haka ya sabeta a kafada ...ya direta gaban fanfon dake gurin sukayi alwala ..sannan ya sake daukarta ya kaita dakinshi ya shinfida mata darduma ...</div><div><br /></div><div> Ya fice masallaci ..</div><div>Ya saba dawowa da anga Sallah ...amma ranar sae da ya tsaya aka yi Isha'i sannan ...ya dawo ...</div><div><br /></div><div> Tana tsaye bakin kofa kamar zatayi kuka ...ya shigo ...da sauri ta juya mashi baya ...</div><div><br /></div><div> Rungumota ta baya yayi tare da daura kanshi saman wuyanta yana shakar kamshinta</div><div><br /></div><div> Nayi laifi ...tuba nake ....ya fada cikin kunnenta .....</div><div><br /></div><div> Make kafada tayi tana murza idonta ....</div><div><br /></div><div> am sorry Meenatou ...ya fada a hankali ..</div><div><br /></div><div> juyowa tayi tana kallonshi tace ..To ina ka tsaya ...</div><div><br /></div><div> juyota yayi tana facing dinshi yace ....Kazar amare naje sawo maki...sae da na nemo wadda zata maki wuyar cinyewa....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> *Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div> Nagode sossae da sakonninku ...wanda ban bawa amsa ba dan Allah suyi hakuri wallahi yayi man wuya nabi kowa na bashi amsa ...Kuyi Hakuri🙏🏻</div><div><br /></div><div><br /></div><div>101 to 102</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Gabanta yayi mummunar faduwa tayi tsuru tsuru tana kallon carpet ..</div><div><br /></div><div> Tsaf ya gama karantarta ....lebenta na kasa yaja ..tare da jan hannunta ...bai tsaya falo ba ...ya wuce bedroom dinshi da ita ...</div><div><br /></div><div> Tana zaune kamar mutun mutimi ya fito wanka ...sannan ya mika mata towel ...</div><div><br /></div><div> Sae da ta dauki kayan baccin da zata saka ta shiga toilet din dasu ...gudun kar ta fito yace ta saka gabanshi ....</div><div><br /></div><div> Yana zaune bisa abun sallah ta fito ..ya mika mata hijab ...</div><div><br /></div><div> Raka'a biyu sukayi ...ya dafa kanta ..ya dinga kwararo mata addu'a ....tana zaune kamar gawa ...sae binshi take da ido ....</div><div><br /></div><div> Ledar ya janyo ya juye cikin plate ..</div><div><br /></div><div> Gata nan kici Meenatou idan ma bata isheki ba akwae wata a leda don bana so kice nima na kawo maki karama bata isheki ba ...</div><div><br /></div><div> Harara ta banka mashi tare da fadin ...ni na koshi ...</div><div><br /></div><div> Dariya ya sake Kasa kasa yace ...da sauri haka Meenatou...ko dai na matso na baki da kaina ...</div><div><br /></div><div> Saurin ja da baya tayi ganin ya matsota .</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Dariya ma abun ya baci ...kamar ba Meenatou dake bala'in sae ta kwana kusa dashi ba ...amma yau tana gudunshi ...</div><div><br /></div><div> Yau naga abunda ya daure man kai ...Meenatou ni kike jiwa tsoro ...</div><div><br /></div><div> Bawae shi takewa tsoro ba ...aa abunda zaya mata shi takewa tsoro. ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Sae da kyar ya samu ta karba sau daya ta kau da kai ...duk cika bakin Meenatou yau ga kazar amaren a gabanta amma ta kasa ci ...ko ta manta da Musa ya kawo mata ..ba sonshi take ba kuma tana da yakinin da bara ya mata komae ba shi yasa ta sake jiki ta cinye .... </div><div> </div><div> Amma Yau ta Ma'aruf mai dadin ma ta kasa ci ....</div><div><br /></div><div> Da kanshi yaja hannuta ya kaita toilet sukayi brush sannan suka fito ....</div><div><br /></div><div> Can karshen gado ta koma ta makure ....</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi ya fita ya rufo kofar falon sannan ya dawo ya hawo gadon tare da kashe fitila ...</div><div><br /></div><div> janyota yayi tayi saurin mikewa zaune tana fadin ...Yau zan iya kwana a dakina ni kadae ...</div><div><br /></div><div> Ko ..ya tambayeta yana kokarin rabata da rigarta ...</div><div><br /></div><div> Wallahi kuwa ...ko gidan musa na taba kwana ni kadae. ..ta bashi amsa da sauri ..</div><div><br /></div><div> Gidan Ma'aruf fa ...ya tambayeta ....</div><div><br /></div><div> Shima zan iya kwana ...please ka sakeni ...ta rike hannunshi ...</div><div><br /></div><div> Maidata yayi ya kwantar da ita tare da hade bakinsu guri daya ......</div><div>*</div><div>*</div><div>••°°••</div><div> </div><div> Ba karamar jarumta Meenalle tayi ba ...duk ihun da zakaji ana cewa amare nayi ko daya batayi ba ....sae dae hawayen da suka dinga fita daga idonta ..haka wani Allah ya isa da zakaji amare nayi duk batayi ba ...kuma hakan yayi bala'in kara mata value a gurinshi ...ba kamar shamy ba da yasha cizo da zagi a first night dinsu wanda ko kwatar matsewar Meenalle batayi bare ashe ta fita shan wuya</div><div><br /></div><div> Ma'aruf baiyi tunanin zai sameta virgin ba ..don duk tunaninshi Musa ya riga ya warga mashi farinciki ..amma sae ya sameta budurwa mai tarin Ni'ima ...albarka tashata kala kala ...don har cewa ya dinga yi ...</div><div><br /></div><div> Meenatou indae ni zan daga kafa ki shiga Aljannah ..to na daga maki ita ki wuce Meenatou ....</div><div><br /></div><div> Da asuba ya shiga toilet sae sauri yake ya fito ya taimaka mata . .</div><div>Dama already ya daura ruwan zafi ya zuba kanunfari aciki ...</div><div><br /></div><div> Yana fitowa ya ganta bakin kofa tana dafa bango zata fita ...</div><div><br /></div><div> Yayi saurin isa gurinta ya riketa yana tambayarta. ..</div><div><br /></div><div> Meenatou ina zaki ...</div><div><br /></div><div> Bata ce mashi komae ba sae hawayen da ke fito mata ....lips dinsa ya kai gurin idonta ...ya tsotse idon tas ...sannan ya dauketa ya shige da ira toilet ...</div><div><br /></div><div> Cikin zuwan zafin ya sakata ...bai saka detol ba sae kanunfarin da ya dafa ruwan dashi ...don ya riga yasan detol na bata gaban mace sossae saboda chemicals din daka hadashi dashi ...</div><div><br /></div><div> Kara ta sake tare da rikeshi gam..</div><div><br /></div><div> Sorry kawae yake ce mata ...don ya san tayi bala'in shan wahala ...</div><div><br /></div><div> Sae da ya tabbatar ta gasu sannan ya canza mata wani ruwan zafin da babu komae a ciki yace tayi wankan tsarki ya fita ....</div><div><br /></div><div> Suna azkar bacci ya dauketa ...ya kwantar da ita saman jikinshi sae da ya gama sannan ya maidata saman gado ya rungumeta kamar zaa kwace mashi ita. ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>103 to 104</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Shi da kanshi ya shiga kitchen ya soya masu bread da kwai da kifi ...sae ya dafa masu tea ....</div><div><br /></div><div> Kafin ya dawo har ta fito daga wanka tana sha mai ajikinta ...</div><div><br /></div><div> Da Sauri ya karba ya shafa mata sannan ya taimaka mata ta saka kaya ...riga da siket na atamfa ....</div><div><br /></div><div> Hannunta ya kamo yana kare mata kallo sannan yace ...</div><div><br /></div><div> Kinyi kyau Meenatou ..duk da ma ke din mai kyauce...ina matukar kaunarki kinji ko. ..Allah ya maki albarka ..ban san wace irin godiya zan maki ba ...kin adana man jikinki duk da kin auri wani kafin ni ...naji dadi sossae ...</div><div><br /></div><div> ••°°••</div><div><br /></div><div> Da Daddare kuka ta saka mashi bara ta kwana a dakin ba ...sae da ya mata alkwarin bara ya mata komae ba sannan ta yarda ta kwanta shima karshen gado ....sae da tayi bacci ya maidota jikinshi ...</div><div><br /></div><div> Tun daga ranar bai kuma neman wani abu ba ..ta koma ta saki jikinta dashi kamar da ...soyayya suke zubawa kamar ba gobe ...idan yana office waya ba makale a kunneshi ...idan kuma yana gida gwanin ban shaawa ...</div><div><br /></div><div> Yana kwance ya saka eyepiece a kunneshi yana sauraren wani waazi ..ta shigo falon ...sanye da kayan sport don yanzu ta kware sossae da wasanni ....</div><div><br /></div><div> Ta dade tsaye tana jiran ya tashi suje ...sae ya ware mata hannunshi ta shiga ciki tare da kwanciya saman kirjinshi ...ya maida hannun ya rufe.</div><div><br /></div><div> Eyepiece daya ya cire daga kunnenshi ya makala mata akunne ...suka cigaba da jin wa'azin tare ...wasan da baayi ba kenan ranar ....</div><div><br /></div><div> ••°°••</div><div><br /></div><div> Da daddare suna zaune ta kalleshi tana bata rai ...tace</div><div><br /></div><div> Ina kazata ta rannan ...ta tambayeshi tana hararanshi ...</div><div><br /></div><div> Wace ciki Meenatou .....</div><div><br /></div><div> Ka manta ...ba fa ta jiya ...bana sonta don bata kai ta ranan nan dadi ba ...wacce ka sayo man nace bana ci ...ka tunata ? to ita zaka biyani .....ta fito da ido waje ..</div><div><br /></div><div> Dariya ya sake yace ...Kazar amarya zaki ce man ...ita kike son kici yanzu ...</div><div><br /></div><div> Bata kawo komae ba tace ...eh Please ...</div><div><br /></div><div> Cak ya dauketa ya direta saman gado ..yana fadar bara yanzu zan baki ...</div><div><br /></div><div> Hadashi ta fara yi da Allah ganin abunda yake shirin yi mata ...amma ko saurarenta baiyi ...ba ..ranar ma tarihi ya maimaita kanshi ...tayi nadamar tambayar kazar da tayi ...</div><div><br /></div><div> Meenalle irin matannane wanda ko yaushe zaka jisu kamar ranar aka fara saninsu ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Tun daga ranar bata kuma mashi maganar kaza ba ...ko kawo mata yayi ...sae an zauna anyi alkawarin bara ya mata komae ba ...sannan take yarda taci ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°••</div><div><br /></div><div> Safiyar wata litinin suka dira A nigeria ...gidanshi dake kaduna GRA Unguwar sarki suka sauka ...tun kafin su iso dama ya saka an gyara ko ina tsaf ...</div><div><br /></div><div> Kwanansu biyu suna hutawa sannan ta je gidansu ....</div><div><br /></div><div> Hajiya sae nan nan take da ita ...taga gata sossae ...kuma ta iske mamanta cikinshi ......</div><div><br /></div><div> daga can gidan Sadee ya kaita ...sae da tayi kwana biyu sannan ta dawo gida ...</div><div><br /></div><div> Da ta dawo Ko kulata baiyi ba ..don fushi yake da ita ...wae ta tafi ta barshi ...da ta fara rikitashi nan da nan ya huce yana dariya ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm*💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div><br /></div><div>💧💧SIRRIN ZUCI...</div><div><br /></div><div> </div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div> </div><div> 105 to 106</div><div><br /></div><div> </div><div> Satin daya a garin suka je zaria ...a gidansu Ma'aruf din ta sauka ..sae dae ta kwana gidan kaka ....</div><div><br /></div><div> Suna zaune tace mashi tana so suje islamiyyarsu ta gaida malaman ...</div><div><br /></div><div> Ya harareta yace. . ki dai nemo gafara. ..</div><div><br /></div><div> Zagayo wa tayi bayan kujeran da yake ...ta sagalo hannunta bisa wuyanshi ....kanshi ya dago yana kallonta ...ta dauro fuskarta saman tashi ....suna fitar da numfashi tare ....</div><div><br /></div><div> Baka so Ustaz ya yafe man ..? ta fada dae dae bakinshi ....</div><div><br /></div><div> Nan da idanuwanshi suka canza ..ya zagayo da ita ya daura saman cinyarshi ....tare da kwantar da kanshi a kirjinta ........</div><div><br /></div><div><br /></div><div> ••°°••</div><div><br /></div><div> Wani dan karamin gida ya fara biyawa da ita ...ya fito da key ya bude gidan tare da jan hannunta cikin ...</div><div><br /></div><div> Cherii ...ina ne nan ..ta fada tare da kallonshi ...</div><div><br /></div><div> Daki dayane cikin gidan babba ...yana bude kofar ...ya duka yana fadin ....Teeta ......</div><div><br /></div><div> Wata kare ta fito ta tsaya gabanshi tana sinsinanshi tare da haushi ...sannan ta duka gabanshi ...</div><div><br /></div><div> Ya kalli Meenalle ...yace ..kin tunata ? ..</div><div><br /></div><div> Girgiza kai tayi a hankali cike da mamaki</div><div><br /></div><div> Hannunta ya janyo ta duka kusa dashi ...sannan ya juya yana kallonta yace ....</div><div><br /></div><div> Kin tuna ranar da na fito gida na ganki kina kuka ...na tambayeki me aka maki ...sae kika ceman ...wae mamansu kausarce tace idan karensu ya haihu zasu baki guda ....Sae kikace kaka tace bara ta aje kare a gidanta ba ...saboda mala'ikun rahama basa shiga gidan .....Sae kika ce ko zan aje maki shi a gidanmu bakin gate ..idan mala'ikun sun zo sae su shigo ta katanga ...to shine na karbo maki anan....ya kara maganar tare da dago habarta ...</div><div><br /></div><div> Rungumeshi tayi tana murmushi ....</div><div><br /></div><div> Sannan suka tashi sukaje islamiyyar...</div><div><br /></div><div> Ustaz na ganinta ya ganeta ....Aminatu abubakar ..</div><div><br /></div><div> Ta amsa da fara 'a....duka malaman islamiyyar suka taso suka gaisa da Ma'aruf ...</div><div><br /></div><div> Ustaz ya kalli gefen fuskarshi ya shafi wani tabo yace ..Aminatu gaskia ba karamar cuta kika mani ba ...</div><div><br /></div><div> Tayi murmushi tace ...Ustaz sae dae a yafe dan Allah .....</div><div><br /></div><div> Yace ..ai an yafe Aminatu...</div><div><br /></div><div> Tace Ustaz ina wata shaddarka da ka taba zuwa da ita sabuwa ..daka koma gida kaga an yageta ta baya ....</div><div><br /></div><div> Da Sauri yace Kece ko aminatu .....</div><div><br /></div><div> Eh Ustaz sae dae a yafe ...Wallahi lokacin banda abun goge majina ..sae na Yaga da reza ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Basu bar gurin ba sae da Ma'aruf ya masu alkhairi mai yawa sannan suka tafi ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>°°••°°</div><div><br /></div><div> A gurin kaka take samun labarin Musa ya kara guduwa daga prison sannan har yau baa kara ganinshi ba .....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>•°°••</div><div><br /></div><div> Ma'aruf bai san Meenalle na da ciki ba sae da yakai wata shidda sannan ya fito ....wata sabuwar soyayya da kulawa yake bata ....Ko karatu zayayi in yana gida sae dae ya zauna tana jikinshi ta karanta mashi ....</div><div><br /></div><div> Karyar Rashin lafiya kuwa ya sha yayita gurin aiki sae yayi sati bai je ba ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div>Ranar wata litinin ta tashi da mugun ciwon mara ...Ma'aruf na kwance gefenta ...yana bacci ..ta mintsineshi da karfi ...</div><div><br /></div><div> Ya mike yana kallonta ....cikin kuka tace ...sae aja wa mutun ciwo sannan a kwanta ayi bacci ...</div><div><br /></div><div> Me ya faru kuma Meenatou .....</div><div><br /></div><div> Maimakon ta bashi amsa sae ta fashe da kuka .....da farko ya dauka rashin jin Meenalle ne ..</div><div>sae daga baya ya fahimci da gaske take ......</div><div><br /></div><div><br /></div><div>Feedohm💞</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI .....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>107 to 108</div><div><br /></div><div> Da sukaje asibiti cewa akayi sae an mata CS itama ...</div><div><br /></div><div>Please doctor kuyi wani abu mana ...bana son CS dinnan wallahi ...ya fada tare da rike hannun doctor din ya rufe idonshi gam ....</div><div><br /></div><div> Calmdown mana ...in Allah ya yarda ba wata matsala Mr Ma'aruf ...</div><div><br /></div><div> taya zan kwantar da hankalina bayan Meenatouta tana can tana labour ...ni dae kawae ayi mata komae amma banda CS ....ya karashe maganar da karfi ....</div><div><br /></div><div> Nurse ta shigo tana fadin Sir zata iya haihuwa da kanta mahaifar ta bude da kanta ...</div><div><br /></div><div> Daga doctor din har Ma'aruf din rigen shiga ake dakin duk da mutane basu shiga amma haka suka kyaleshi ....</div><div><br /></div><div> Yana Zuwa ya zauna tare da tallabo kanta ya daura saman cinyarsa ....</div><div><br /></div><div> A wahale ta bude ido tare da rike hannunsa tana kallonshi da i</div><div>Cheri...ta fada tare da lumshe idanu ...</div><div><br /></div><div> Iska ya hura mata yana shafar kanta ganin yarda take zufa duk da sayin AC dake dakin ...</div><div><br /></div><div> Hannunta ya damke sossae tare da daura gudan hannun a goshinta</div><div>Sorry ..Meenatou ...ki daure please kinji ko ...ya fada dae dae kunnenta ..</div><div><br /></div><div> Girgiza mashi kai tayi ..aa Cheri mutuwa zanyi kamar yarda shamy tayi ..ka yafe man kaji ka sakawa babyn mu sunana ...</div><div><br /></div><div> Bazaki mutu ba Meenatou ki barni ...da rayuwarki nake rayuwa ..idan babu ke Meenatou Zan kasance kamar gawa da raice ..kin manta alkawarin da kika man ..kince Tare zamu rayu sannan mu mutu a tare ..ko kin karya alkwarin ne Meenatou?,......</div><div><br /></div><div> Zafin ciwo bai hanata girgiza mashi kai ba ....</div><div><br /></div><div> Yauwa Meenatou ...zaki daure ko?..ki daure ki haifa mana baby ki bashi tarbiyar ..Ina Matukar sonki da kaunar ko da can da kika ga na shareki Meenatou dan ba yarda zanyi ..amma soyayyarki tana cikin Zuci ...ta zama Sirrin Zuci ...zan iya rayuwa babu abinci Meenatou ..indae kina tare dani ...Dukiya da duk jin dadin duniya yana tare dake Meenatou ..kece hasken dake haskaka rayuwata ...idan babu ke zan dawwama cikin duhun da bazaya taba gushewa ba ...</div><div>Kin kasance wani bango Wanda akayi shi da azurfa a gareni ...ki daure Meenatou ...Ke din kamar Hurul 'ain ce wadda Allah ya sauko man domin cikar rayuwata ....</div><div><br /></div><div> Idonshi ya lumshe tare da daura lebenshi saman nata yana tsotsa ya mata katanga da faffadan kirjinsa ...yana jin lokacin da taja numfashi da karfi tare da kara rikeshi. ...hawayen dake zuba a idanunta. ...suke gangarowa saman lebenshi ....</div><div><br /></div><div> Doctor dake tsaye da baby a hannunshi ya dafa bayan Ma'aruf tare da daura babyn a bayanshi ...</div><div><br /></div><div> Ya dago da sauri yana kallon Dr din ...</div><div><br /></div><div> Murmushi yayi mashi yana fadin ..Congrat Mr Love ..ya mika mashi baby din. .</div><div><br /></div><div> Yaron ya kallah dauke da murmushi a fuskarshi sannan ya kalli Meenalle wadda har lokacin Idonta a lumshe yake</div><div>Dukawa yayi Dae dae kunnenta ...ya kira sunanta a hankali ...</div><div><br /></div><div> Meenatou...</div><div><br /></div><div> Bude idonta tayi tare da kallonshi ...Deep kiss ya manna mata a goshi...sannan ya dago da idanuwanshi da suka rike zalla soyayya ya na kallonta ...</div><div><br /></div><div> Barata iya jure irin kallon ba ta juyar da kai gefe guda tana murmushi ....</div><div>Tsam ya mike tare da komawa inda ta juya ...zata sake juyar da kanta ..ya saka hannu daya ya rikota ...</div><div><br /></div><div> Me kike so a rayuwarki Meenatou ...fadan me nene gurin ..ko da lumfashina zaya kare zan cika maki shi ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Hannunshi ta rike tare da daurawa saman kirjinta ...Kai nake so Ma'aruf .kai kadaene gurina ...daga kai bana son komae ...</div><div><br /></div><div> Babyn ya daura mata a kirjinta ya duko da kanshi ya sumbaci lebenta ...kin Samu Meenatou dama can ni naki ne ...kin saka man farinciki mara misaltuwa a rayuwa. .dame zan saka maki ..?..</div><div><br /></div><div> Ka barshi a sirrin zuci ...ni kadae zan fahimci haka ...</div><div><br /></div><div> °°••°°</div><div> </div><div> Dama Already ya fadawa dangi tana labour ....tun da safe jirgin su Hajiya da kaka da mahaifiyar Maaruf ya dira ...farinciki kamar baa taba haihuwa ba a dangin ....</div><div><br /></div><div> Hajiya tace. zaa koma da Meenalle nigeria ...amma Ma'aruf yayi kememe yace ba inda matarshi zata tafi ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div>💧💧SIRRIN ZUCI ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div> 💞</div><div><br /></div><div>Na Feedohm💞</div><div><br /></div><div><br /></div><div>109 to 110</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Juyin duniyar nan amma ya kiya ...da daddare ya samu Meenalle zaune daki ...yaron na hannu kaka zaa mashi wanka ...</div><div><br /></div><div> Hawa yayi saman gadon tare da kwanciya ya daura kanshii saman cinyarta ..yana kallonta ...</div><div><br /></div><div> Murmushi tayi tare da shafar sumarshi ...</div><div><br /></div><div> Bara ka bari a tafi dani ba Cheri....ta fada tare da juyar da kai ga barin kallonshi ...</div><div><br /></div><div> Kina so ki bisu ne. .? ..ya jeho mata tambayar..</div><div><br /></div><div> Tasan da biyu ya tambayeta tayi saurin kallonshi ..har ya janye kanshi daga jikinta ...</div><div><br /></div><div> Girgiza mashi kai tayi a hankali ...</div><div><br /></div><div> Idan kina son binsu Meenatou baran hanaki ba. .kinji ko ..ki shirya ku tafi ....</div><div><br /></div><div> Ya mike yana shirin sauka daga gadon ...hannunshi ta rike tare da kwantar dashi ...sannan ta kwanta jikinshi ...tana fadin ...</div><div><br /></div><div> Cheri idan har kai baka so nayi nisa dakai ...ni taya zanyi tunanin nesa dakai. ... *Muna Tare* </div><div><br /></div><div> Mirginata yayi tare da sake mata kiss ya mike yana murmushi jin motsin kaka na zuwa ..</div><div><br /></div><div><br /></div><div>••°°•• </div><div><br /></div><div> Allah Cheri ka tashi ...ta fada tare da mintsininshi a kumatu ..</div><div> </div><div> Gyara kwanciya yayi yana mata dariya kasa kasa</div><div><br /></div><div> ...pillow ta dauko tana dukanshi ...amma yaki kulata. ..</div><div><br /></div><div> Kuka ta sake mashi ..tare da daukar Sudais dake faman mata kuka ta sauka daga gadon..ta nufi kofar fita ....</div><div><br /></div><div> Da sauri ya mike tare da rungumota ta baya yana dariya ...</div><div><br /></div><div> Ka sakeni ...ta fada tare da share kwallanta ..</div><div><br /></div><div> Am sorry ...ya rike kunnanshi ..sannab.ya saka hannu ya karbi Sudais ya daura saman baya ...ya juya mata ta saka mashi zani</div><div><br /></div><div> Dama abunda take so kenan ...ta sake mashi harara tare da daura mashi zanin a baya .....</div><div><br /></div><div> Sae da ya goyashi sannan ya dauketa cak ya maidata saman gadon ...ya fara jijjiga Sudais har ya koma bacci ...</div><div><br /></div><div> Ya maidashi saman gadonshi sannan ya dawo ya janyota jikinshi ....romancing dinta ya fara ....</div><div><br /></div><div> Hannunshi ta rike idonta na lumshe haka shima nashi ...</div><div><br /></div><div> Cikin kunnenshi tace ..Cheri ka tuna fa ..kace wae banda abunda zai ...</div><div><br /></div><div> Bakinta ya kulle da nashi ya hana sauran maganarta fitowa ...sannan ya dago yace .</div><div> Oh Meenatou nace na tuba Wallahi ..wannan magana bara ta kare ba haka nan ...dan Allah ki rufa man asiri ...na tuba wallahi ...</div><div><br /></div><div> Murmushi tayi tare da rungumoshi .....dariya yayi ...yana fadin Meenatou ta bara ki canza ba ...idan aka maki abu har mutun ya mutu kina tunawa ....</div><div><br /></div><div> bayanshi ta buga a hankali tare da zura halshenta a kunnenshi tana lasa ......</div><div><br /></div><div> Fatan Alkhairi Meenalle ....</div><div><br /></div><div><br /></div><div> Godiya mai tarin yawa ga masoyana ...Allah ubangiji ya bar mu tare. ...</div><div><br /></div><div><br /></div><div>يا يهل الذين ء ا مبو اتقو. الله ولتظزنفس ما قد مت لغد..... ..</div><div><br /></div><div>ALLAH YA YAFE MANA KURA KUREN MU .....MU HADU A SABON LITTAFINA ... *_AHLUL KITAB_*</div><div><br /></div><div> Ina kaunar masoyana baran iya lissafo ku ba ..dan page bara ya isa ba ..amma ku sani kuna raina ....</div><div> Namutu kanku ...😅😅</div><div><br /></div><div> 08066598868 </div><div><br /></div><div><br /></div><div>*Feedohm💞*</div><div><br /></div>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-66654762228144254582021-01-24T07:00:00.001-08:002021-01-24T07:00:13.382-08:00Siyamah Walidah Complete Romantic Hausa Novels<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-52TbTbmwa_0/YA2LOZgrXRI/AAAAAAAAJg0/k_fcjipFGocrndMFOr0hVrUDWDQ3d5QsgCLcBGAsYHQ/s2048/Siyamah-Walidah.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="Siyamah Walidah Complete Romantic Hausa Novels" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-52TbTbmwa_0/YA2LOZgrXRI/AAAAAAAAJg0/k_fcjipFGocrndMFOr0hVrUDWDQ3d5QsgCLcBGAsYHQ/w320-h248/Siyamah-Walidah.jpg" title="Siyamah Walidah Complete Romantic Hausa Novels" width="320" /></a></div><br /> [10:28PM, 11/21/2016] Rynt: [10:57PM, 10/26/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹<p></p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊 08140674366/08105689666</p><p>1⃣ Fara ce doguwa kyakyawa,'yar siririya,tanada dan fadin fauska kewayayya,hadi da yalwa tacciyar gira, da kuma eyelashes,idnwnt kamar mai jin bacci,gata da dogon hanci,da dan karamin baki,tana da hips da kuma dukiyar fulani,ga gashi sai kace ba india,Kwance take tana game da laptop, sai taji sauti alamar ana kiranta.Siyama!siyama!!siyama!!!</p><p> Na'am ina zuwa umma! yayanki ne ya bugo waya,yana so Ku gaisa,sunyi rabin awa suna waya,sannan suka ajiye waya, sai ga abnanta ya fito daga dakinsa. Walidana ya akayi? dai dai Abbana😊.....Abba fita zakyi , Eh zanje gaida hjyt ne,Abba ina zuwa... je dauko mayafinki mu tafi,umma bye muntafi,to Allah ya kiyaye hanya,ku gaidamin,hjy.</p><p>Tafiya suke yana bata lbr sai dry take......saukar mari taji hakan ne ya dawo mata da dogon tunanin da take.<span></span></p><a name='more'></a><p></p><p> Ke dan baki da tarbiya tun yaushe nasaki aiki bakiyi ba,kina nan sai dan banzan tunaninki da kika saba yi kullum...... Maza ki tashi ki yimin aikin da nasaki,Yar iskar banza karuwa,wadda tayi gadon karuwanci, haka ta mike,jiki ba kwari,idanunta cike da kwalla,duk da dai aikin kenan kullum inda sabo ta saba, bayan fama da take da mahafiyarta na rashin lfy, bt iya yin komai sai anmata,ta kuma dawo ma aikin,gida, wanke2,shara,Abinci, zuwa kasuwa cefane, duk Ita daya, bawai dan an rasa kudin daukan masu aiki ba.</p><p> Saboda masifa irin na hjy bintu.</p><p><br /></p><p>2⃣Aiki take tana hawaye,tana tunanin wnan rshn imani na hjy bintu, da wane zf takeso taji, da rashin mahaifi, ko rashin lfyr umma,gashi kuma yaya abdallah bai san duk halin da muke ciki ba,hawaye ne shar, ke fita a idonta,ta share tn mai cwa Allah ka fitar da mu.</p><p> Bayan ta kmla aikin ne,ta shigo gurin umnta,cike da murmushi,umma sannu ya jkn?da sauki symh wldh,ta amsa mata ne cikin mry ta mrasa lfy.Symh wldh!Na'am umma, nasan cewa,akwai dmw a tare da ke, kuma abin na dmnki kawai kina boye mn dmwr ki ne,ko rashin lfy ta kadai abn dmw wane a gare ki,ballanta ayuka hadi da zagin da kike sha, inaso kiqara hkr,fiye da yadda nasanki dashi,kuma kar zafin zuciya ya debeki wataran ki maida mata martani,ko kiyi tuananin daukar fansa,kawai ki barta,ga mabuwayi Allah, in Allah ya ydda komai zai wuce kamar bai taba frwa ba.</p><p> Kallon ummanta tyi cike da tausayi, wacce kwance take,ba abinda ke motsi a jknta face bakinta,da idanu,sai kuma shedar da takeyi.</p><p>in Allah yaso umma zan kasance a yadda kikeso.</p><p><br /></p><p> 3⃣Kwance take wuraren karfe 11pm bacci ya ksa daukanta,tunanin mafita take, akan wannan ciyo na mahaifiyar ta, yakamata a fita da Ita waje,domin bata son ta rsa mhfyr ta tana ji tana gani.</p><p> To amma yazanyi?kj ki sami hjy bintu mana ko Allah zai sa a dace, dayan bangare na zcyr ta ne k bata amsa, lallai haka ya kamata ny.Tashi tyi ta dauro alwala tayi sallah tana kai kukanta a gurin Allah,sai wuraren 12:30am ta kwanta.</p><p> Da safe byn ta gama duk wani aiki da tsn tanayi,taje da sallamar ta dkn hjy bintu, sai da tayi 5 mnt sannan ta amsa sallamar, ba yabo ba fallasa,hkn ne yaba symh wld jin karfin shiga,domin da alamu akwai nasara,ta shiga ne tare da yi mata antashi lfy?lfy,ya akayi ne, ko ko ciwon mhfyr naki, ne?don nasan bai xai wuce shi ba, kallonta tayi, kafin take cewa, eh akanshi ne, dama wai cewa nayi mai zai hana,ki taimaka don Allah a fitar da umma qasar waje ko Allah nasa a dace,.... lallai ma yarinya nan har tayi kwarin da zata zomin da, wannan xance...... ko da yake nama samu damar da zan aiwatar da aikin da nake niyar yi.tana magana ne a cikin zcyr ta, sannan tace, hakan kina ganin za'ayi nasara?inshaAllh mama, to yayi kar ki damu zan duba, na gode mama, ba komai ai taimako ne.</p><p> Cike da mamaki ta fita a dkn domin bata taba tnanin abin zai zo da sauki haka ba.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:29PM, 11/21/2016] Rynt: [11:43AM, 10/28/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDA!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹4⃣🌹Wata irin dryr qeta take,tana cewa"abin tausayi symh wldh,da kinsan ko ni wacece, da baki zo gurina neman alfarma ba.</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu da faruwar hakan, sai ga hjy bintu har cikin dakin su symh wldh, wacce rabonta da dakin tun bayan wata biyu da suka wuce, cike da mmki symh wldh ta gaisheta, ta amsa gaisuwr ne tare da cewa ya jkn nata, Alhmdllh mama,tana bacci ne?eh bacci take yi, to ki shirya nan da kwana 2 zaku je India a dubata, wani irin dadi taji tana mai cewa"mama na gode Allah ya saka da alkhairi,Ameen.</p><p><br /></p><p>Da daddare wuraren 8:30pm ta kwashe kwanikan abincin da suka ci,ta dawo ta zauna a kusa da mhfyr ta,tana qara yi mata ya jki, yauwa symh wldh,dama akwai maganar da nake so ny da ke, mgnr Ita ce,"ko bayan raina symh wldh,bana so ki canza hlnki mai kyau dana sanki dashi,inshaAllh idan kika ci gaba da hk baxa ki samu mtsla a rawuyar ki ba,sannan nasan yau da gobe in Allah yaso, zaki kasance a gdn wani a mtsyin mtr sa, don hk nake so da ki kasance mai yimasa da'a ki kasance mai hkr,ki kasance mai kauda ido akan abin da bai shafe ki,ki ksnc mai toshe kunnuwanki,ki kuma ksnce mai kyautatama dngnsa,har dai iyayensa,kar ki mnt nasha gaya maki cewa"ki riqa girmama dan Adam domin ba abin wlqantwa bne,koda wasa domin watarana zaki so ya taimaka miki.</p><p><br /></p><p> 🌹5⃣🌹 Cikin yanayi na muryar kuka ta fara da cewa"Umma kar ki damu insha Allah baza a samu matsala a guri na ba,amma umma meyasa kike min wadannan magnganun, ai sai kisa hnkali na ya tashi,sai nayi tnanin kamar tafiya zkiyi ki barni,tafiya dole ce symh wldh,domin ranmu ba'a hannun mu yake ba,akoda yaushe z'a iya karbansa,ko nawa ko naki sbd ba'a san gawar fari ba.,kar fa ki manta mhfnki yasha gaya miki,cewa "kisa a ranki ako wane lkc zaki iya mutuwa....... haka ne umma ban manta ba,kuka take sosai😭 tare da rngme umma, sbd a duk lokacin da aka ambaci mahaifinta, bata da aiki sai kuka,ji take kamar ace yau ya dawo garesu yaga halin da suke ciki a dalilin rashinsa.</p><p><br /></p><p>Sai da safe ne take gayama umma zancen tafyr su,zuwa India,kuma a gobe.</p><p><br /></p><p>Zaune take tana karatun Qur'ani,sai ga hjy bintu da wani, da alama doctor ne,suka shigo tare.</p><p>kina iya ki bamu guri za'a duba mahfyr ki ne....amma mama wannan ba shi ne doctor dinda ya saba zuwa ba, haka ne doctor din baya gari, shiyasa kuma gashi gobe ne tfyr Ku,tashi tayi ta fita,amma tanaji a jkn ta kamar akwai wani abu da zai faru da ita.</p><p><br /></p><p>Da safe ta shirya tsaf domin tafiyar da safe ne zasu yita,taje gurin mhfyr ta, da niyar ta duba in ta tashi dg bacci dmn tun lkcn da aka shirya ta tayi bacci,gashi tana so tasha ko dan tea kafin sutafi.</p><p> 🌹6⃣🌹umma!umma!!umma!!!....yadai me ya ke frwa ne?mama tun dazu umma ke bacci bata tashi ba,doctor duba muna ita muga ko lpy, cewar hjy bntu,duk wani bincike da yaka mata Dr yayi,yayi amma baiga alamar rywa a tare da ita ba,gls dinsa ya fara cirewa kafin ya ke cewa"sai dai kuyi hkr hjy,umma ta riga mu gidan gasky.....a razane symh wldh tace What!qarya ne wlh umma na bata mutu ba doctor,gun umma tje tana girgizata tana kuma kiran sunanta,umma!umma!!umma!!!pls kitashi ga tea na hada mki kisha, mu tafi,ganin yadda take girgizar ta baisa ta motsa ba,hnkln ta ya qara tashi, ta saka wata irin qara mai qarfi, tare da cire dankwalin kanta tyi jifa dashi, se duk gashin kanta ya zubo a bayanta,ummaaaaa!!!...umma pls ki tashi..... sai kuma kuka😭😭😭 yaci qarfin ta,dawo wa tayi wurin doctor,tana ce mishi, doctor don Allah ka tashe ta, wlh ita kadai ce ta rage mn wcce zn kallah inji sanyi a raina,ba Abbana,ba kakata, yayana kuma yamin nisa,yzanyi da rayuwata ne?😭😭😭kanta take bugwa a jkn gina,hadi da hannayenta,tana kuka mai ban tausayi.</p><p><br /></p><p>Amma kunsan me?ko a jikn hjy bintu.</p><p><br /></p><p>😭muje zuwa..........</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:29PM, 11/21/2016] Rynt: [7:40PM, 10/29/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDA!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹7⃣🌹Hjy bintu ce ta jawo ta jknta tana mata lallashin munafurci ganin doctor a tsaye.</p><p><br /></p><p>Bayan an mata sutura ne xa'a fita da ita cikin gdn,nan ne fa hknli symh wldh yayi qololuwar tashi, miqewa tayi tsaye,cikin tsananin rudu ganin za'a fita da gawar mhfyr ta,ta fara da cewa,don Allah Ku banni naga umma ta kafin a fita da ita,ina so zan mata addu'a,ba musu suka aje gawar, cikin natsuwa tyi mata addu'a,,tana gamawa ta rungume ta tana fitar da kuka marar sauti,da kyar aka samu aka banbare ta daga gawar,akatafi da Ita, ummaaaaaa!!don Allah Kar ki tafi ki barni, qoqarin binsu take, ganin hk ne yasa mutanen da ke gurin suka rirriqe ta,don Allah kubar ni na tafi inyaso a samu tare, kuna gani fa sun tafya min da umma, Umma!......nan kawai shedar ta ta dauke,ta fadi qasa sumammiya.</p><p><br /></p><p>Daukan ta akayi aka je da ita asibiti,sai da tayi kusan sati kafin a shawo kanta, domin komar musu tayi Kamar zautacciya,har ma bata gane waye a kanta. To Alhamdulillah yanzu tana gane kowa,hkn ne yasa aka mai data gida.</p><p><br /></p><p>Bayan sun dawo gd ne, take roqon hjy bintu, da ta aramata waya tana so tayi magana da yayanta,ko xa'a yi nasarar,samunshi</p><p>🌹8⃣🌹Symh waldh kenan baza ki taba samun sa ba, domin na riga da na canza numbar,cikin zcyr ta ne take maganr.miqa mata wayar tayi tare da murmushin qeta, btare da symh wldh ta lura dà hkn ba,ta amshi wayar,ta nemo numbar sa ta Kira, ko yau ma haka wayan bata shiga ba,Kira take har ta gji bata shiga,miqa wayr tayi,tana godiya,sai cewa hjy bintu tayi dama nasan idan zaki shekara kina buga wayar, bazata shiga ba,baqin nacin tsiya ne kawai dake, mayya kawai, fice min da gani kina kallona da maiyun idanuwan nan naki,</p><p> Jiki a sanyaye ta fita, tana mai zubar da kwalla,shigar ta daki keda wuya,hjy bntu ta shigo,da dan uban wankinta, ungo jeki ki wanke min kayannan, kuma ki tabbatar sunyi fari tas,.....mama don Allah ki bari gobe na miki,jkna bai yi qwari sosai ba,ba rwana da wannan,kawai muradina a wanke min kaya na,kuma idan suka bushe ki goge min su, dama dalilin da yasa bana baki wanki,ina tausaya miki ne sbd rashin lfyr mhfyr ki,to yanzu babu ita,sai ki riqa yimin wankin a madadin kulawar da kike mata. Ta fita ba tare da taji me zata ce ba,kuka take mai ratsa zcy tana kallon photon su da sukayi, Ita da,Abba,umma,yaya abdallah,ciro ptn tayi ta rungume tana ji kamar ace zata gansu a fili.</p><p><br /></p><p>Bayan wata daya da frwar hakan 🌹9⃣🌹wuraren 11:30,ta sallame sallah tana addu'a,sai ta fara jiwo surutun maza kadan kadan, kuma da alama daga dakin hjy bintu ne, tashi tayi sannu a hankali,ta labe a bakin qofar dakin, ga mamakinta sai ta hngo jibjibgan maza har su 6, tji hjy bintu na cewa,"na tabbata yanzu tayi bacci,so nake kuje dakinta Ku aiwatar da aikin da nsa ku, kuma ku duka 6 sai kowa yayi a cikinku, inyaso idan kuka gama kuje Ku yadda ita a wani gari mai nisan gaske kuma zku zauna a can, Ku riqa bibiyar ta ba tare da ta sani ba.....daya daga cikin su ne yake cewa, hjy me zai hana ayimata gunduwa gunduwa,kawai a huta..... Sam! bana so symh wldh ta mutu yanzu sai taga wulaqantar duniya, inyaso daga baya,na kashe ta kamar yadda na kashe mahaifinta,da mhfyr ta.</p><p>Symh wldh dake labe, hnklnt yayi matuqar tashi, har bata san lokacinda tace, innalillahi wa inna ilaihirraji'un!!,hkn ne yabasu damar juyowa baki dayansu,tana ganin sun ganta ta sheqa da gudu, suko suka biyo ta, baji ba gani,har suka fita daga gidan,ga shiyar su irin shiyar masu kudi ce tsit ba alamun mutane,gata daji ce,gudu take tna waiwaye,garin waiwayen ne taci karo da qaton iccen dalbejiya ta fadi,kafin ta tashi daya ya same ta tare da cafko qafar ta, yaja ta da qarfi,anan ne ta saki qara mai qarfi, wadda nima sai da na firgita na yadda biro ta.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:29PM, 11/21/2016] Rynt: [6:19PM, 10/31/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹🔟🌹Dube dube take ko zata sami wani abinda xata buga mishi,can Allah ya nuna mata wani qaton dutsi, rarumoshi tayi tare da buga mi shi a akai,ba shiri ya saketa, da qyar ta samu ta miqe sbd ya jimata rauni a qafa,hango sauran tayi,saura kadan su kawo inda suke,gashi bata iya gudu sosai,haka dai ta lallaba,ta bar gun sauri sauri, tanayi tana labewa a bayan bishiya,har ta samu ta kai a bakin titi, cikin ikon Allah ta hango hskn mota tafe,da sauri sauri take dakatar ta motar,motar kuwa ta tsaya, wata mata ce a ciki amma ba sosai ake gane wadda ke ciki ba, sai da ta fito ne, hklin symh wldh ya qara tashi,sbd ba kowa bace face hjy bintu.</p><p><br /></p><p>Tafe take cike da murmushin qeta, symh wldh na tunanin yadda zata yi, gashi ta kusa qarasowa inda take,nan ta ke dabara ta fado mata,duk da dai inda take da niyar bi akwai duhu sosai,amma hkn ta daure ta keta a cikin dajin gudu take baji ba gani hade da yin duk addu'ar da ta fado mata, yanzu ma wani titin ta sake gani,ga kuma mota, a tafe sai dai wannan karon bata tsaya ba ci gaba tayi da gudu tana mai qoqarin qetare titin dai dai motar ta kawo,sai wani qiiiiiiiiiiiiiiiiiiiiirt,nji koda na duba kadan ya rage a bankade ta,domin ita hr ta yafe an kade ta,ta qame wuri daya tare da rintse idanuwanta,sai wani ya fito tare da wata mata.</p><p><br /></p><p> 🌹1⃣1⃣🌹Da alama direba ne da hjyr sa,hjyr ce ta fara da cewa, "innahu min sulaimana wa innahu bismillahir rahmanirrahim,ku kuke ganin mu bamu muke ganin Ku ba,don Allah baiwr Allah kiyi hkr, ba laifunmu bane.</p><p><br /></p><p>Symh wldh dake tsaye,sai alokcn ta bude idanunta,cike da mamaki ganin matar ta maida ta aljana, ta fara da cewa hjy wlh ni mutum ce ba aljana ba, kallon ta hjy keyi cike da rashin yadda da zncnta,sbd tsananin kyaun ta yawuce ace mutum ce, sai da ta kai dubanta ga qafafunta, taga ba qofato sannan ne tayi sassanyar ajiyar zcy,can ta tsinkayo muryar symh wldh na cewa, "don Allah hjy ki yadda dani, wlh biyoni akayi zasu iya kashemu gaba dayanmu, idan suka same mu anan don Allah ki taimaka min.......innalillahi wa inna ilaihi ilaihirraji'un! kin gansu gasu can tafe motar tace,da sauri hjy ta jwo hannunta suka shiga mota, dreba ya jasu a shanshame,gudu suke suna biyar su har suka fita daga garin, a nan ne suka bace musu,domin dreban yasan hanyoyi daban daban,hkn ne yabasu damar bace musu, tare da taimakon Allah, har suka iso gdn basu sake ganin suba.</p><p> </p><p>Wane qatoton gida ne mai kyaun gaske,dagani gdn dala ta zauna. Horn yayi ba jimawa aka bude gate, suka shiga, bayan sun shiga daga cikin gdn ne hjy ta nuna mata wani daki,tana mai "cewa kije ki samu kiyi bacci inyaso gobe da safe mayi magana, tayi gdy,ta shiga dakin, hjy ma nata dakin ta nufa.</p><p><br /></p><p>🌹 1⃣2⃣🌹Da asuba, da qyar ta tashi sbd gjyn gudu da kuma zfn da qafar kemata,tana qoqarin shiga toilet ne, sai taji sallamar hjy ta shigo dakin, hjyr ke cewa dama zuwa nayi na tashe ki,ashe har kin tashi,sai dai naga kamar kina dingishi,eh nji rauni ne a qafa, ayya Allah ya sauwaqe, Ameen nagode. </p><p><br /></p><p>Ta gama sallah tana a kishingide akan kafet din sallah, hjy ce ta koma shigowa,tashi tayi zaune ta gaida ta ta amsa gaisuwar cike da 😊,ga kayan sawa nakawo miki idan kikayi wanka sai ki saka,hannu biyu tasa ta karba tana mai godiya.</p><p><br /></p><p>Qarfe 10:00am na safiyar ranar, hjy ce ke duba break fast din da 'ya'yan nata suka hada, akan dining table,taga yayi ba mastala.</p><p><br /></p><p>Ruqayya!Ihsan!...umma gamu zuwa, bayan sun zo ne,ta ke cema Ihsan tje ta kiramata wata baquwa tana can dakin da baki ke sauka, cike da murna taje domin yarnyr akwai ta da son mutane,da sallamarta tashiga,tare da gaisheta,sannan ta fadi saqon ta fito, tafe take tana dingishi har ta iso, hjy ce ta nuna mata kjra, ta zauna ne hade da gaidasu, kowa ya amsa amma banda Rqy da tunda ta kalleta sau daya bata sake dubanta ba.</p><p><br /></p><p>🌹1⃣3⃣🌹Ke dai Rqy Allah ya shiryeki, har da baquwar kuma sai an nuna mata hali....Allah kuwa umma duk halin yaya sa'eed ne da ita, miskilanci tsiya ne dasu.....umma kin ganta ko,me ya shafe ta dani,kina min magana zata tsoma bakinta a ciki, ai gsky ta fada,walaqanci dai ba abinyi bane, inkina dainawa ki daina. nan dai sukayi breakfast ba tare da kowa ya sake cewa qala ba.</p><p><br /></p><p>Baiwar Allah idan muka gama, inaso nayi magana dake cewar hjy.sai da, su Rqy suka fice zuwa dakinsu, take cewa, nikuwa yaya sunanki?sunana symh wldh..... SIYAMAH WALIDAH!duk sunan ki ne eh, Mahaifiyata ke kirana da symh mhfna kuma Walida, meyasa .......koda yake ba yanzu ya kamata muyi wannan maganar ba,domin na fahimci qafar nan na damunki sosai, kamata yayi muje asibiti a duba,inyaso bayan kinji sauqi sai muyi mgnr ko? to yayi hjy nagode, ba komai 'yan nan ai yiwa kaine.</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyar da frwr hkn,zaune suke a falo suna fira, Rqy ce ta kalli symh wldh tana cewa wai umma ya z'ayi muna zama da yrnyr da bamu san asalinta ba,kuma gashi da alama bata da niyyar tfy ta bar mana gd, sai wani qara gyara zama dama naga tana yi, wai har tana tayamu aikace aikacen gd,gashi kuma kince tsinto ta kukayi, akan hnyr Ku ta dawowa,shiyasa umma bana so kina yin tfyr dare wlh, gashi yanzu kin kwaso wacce bamu san ko wacece ba,wata qil ma agurin yawon karuwancinta ne kika hadu da ita.... Bana son shashanci rqy wannan wace irin magana ce hka babu dadin ji,kar ki sake in qara jin irin wannan Kalmar a bakinki. Symh wldh kallon Rqy kawai tayi batare da tace komai ba.</p><p><br /></p><p> 🌹1⃣4⃣🌹Sannan da kike cewa ba kya so ina tfyr dare yaushe ne na taba dare irin na ranar, ko shi motar muce ta lalace, shi ya kawo</p><p> hkn. </p><p>Symh wldh, dama kinsan nabar maganar ne har kiji sauqi, gashi kuma Alhmdllh qafa tayi sauqi,yanzu inaso ki fadamin me ya fitar da ke a cikin wannan dare? me kuma yasa wadannan mutane ke neman halaka ki?sai da ta nisa tare da gyara zmnt sannan ta fara da cewa, "hjy an turo su ne domin sumin fyade......fyade!?cike da mamaki hjy ta maimata,...eh hjy fyade aka turosu su min, saidai Allah bai basu nasarar aikata hkn akaina ba........ba wani sun aikata, tunda koda kika zo ko tfy bakya iya yi da kyau, gsky umma bazata zauna muna a gida ba ayi rashin sa'a ciki ya shiga azo ana zaginmu......Tass!tass! Kakeji umma ta wanke ta da mari tana mai cewa maza ki tashi ki bamu guri,abinda umma bata taba yimata ba a ryw sai gashi yanzu ta mareta akan wata can banza,hkn ya qara sa taji ta tsani symh wldh a ranta, tashi tayi ta fice cikin bacin rai, tare da ba mhfyr ta hkr domin bata taba ganin ranta ya baci haka ba.</p><p><br /></p><p>Inajinki symh wldh.... kiyi hkr da halin Rqy kinji, ai ba komai ya wuce,waye yasa ayimiki fyade?hjy bintu,wacece ita? me kuma yasa take so ayi miki fyade,ita mata ce a gurin mhfina,wato abokiyar zmn mhfyta,to ke ina mhfinki yake da kuma mhfiyr ki, da har hjy bintu tasa amiki wannan danyen aikin basu sani ba,kuma da alama ke 'yar masu kudi ce sosai, yakamata ace kwanakin nan da kikayi an nemeki,amma shiru ko da wasa bnji ana nemanki ba,hjy bazaki gane bane idan har ba lbrna nabaki ba tunfarko, to ina sauraren ki symh wldh.</p><p><br /></p><p>Kubiyoni domin jin labarin SIYAMAH WALIDAH.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:29PM, 11/21/2016] Rynt: [8:54PM, 11/4/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 </p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹2⃣0⃣🌹Koda nje dakin Abbana ban same shi ba,nayi tunanin ko ya shiga toilet ne,njira shi hr tsawon 30mnt amma ba alamar fitowa,zuwa nayi a bakin toilet din inji ko akwai alamun mutum a ciki nji ba motsin komai,sai nyi knocking namma shiru, bude toilet din nayi naga tabbas baya ciki, ba tare da nayi wani tunani ba,na koma a falo na zauna ina danne danne a waya ta.</p><p><br /></p><p>Lkc sai qara tfya yake amma banga alamun abbana, nada niyar zowa mu tafi ba, hkn ne yasa nje gurin umma ina mai cewa,umma ya akayi ne har yanzu daddy shiru, kuma yace da qarfe 10:00am ne tfyr, sai cemin tyi ai nazata kina tare dashi? bamu tare kuma baya a dakinsa sai dai idan yana a bangaren mama, to ai yakamata kije kiran sa domin yanzu hr 9:30,ya kamata ace kuna filin jirgi yanzu, to umma bari nje na duba.</p><p><br /></p><p>Ko a can din baya nan umma, asali ma yau duk bata ganshi ba,kira wayarsa muji, da na kira wyr,rngn take ba'a dagawa.</p><p><br /></p><p> 🌹2⃣1⃣🌹Haka nci gaba da kiran wayarsa amma ba'a dagawa,sake komawa nayi dakinsa,ina mai ci gaba da krn wayr,ina shiga dakin sai nj ashe yabar wayar ne a daki,bai fita da Ita ba.</p><p><br /></p><p> Hr goma tyi ba Abba...muna cikin hk ne sai mami ta krni a waya,tana mai cewa ya akyi ban ganku ba gashi jirgi yana batun tashi kuma daddy ya kira abbanki ba'a daga wyr ba, shiru nyi ina tunanin abinda xan cemata,kafin nake cewa eh Abba suna meeting ne kuma hr yanzu basu fito ba,sai dai gobe zamu sameku inshaAllah, to yayi Allah ya kaimu gbe lfy, Ameen mami na gode.</p><p><br /></p><p>Da gudu na haura zuwa sama a dakin umma, na same tana krn wayar kaka ko Abba yaje gdn,amma baya can, hk aka ci gaba da kiran duk wani wanda ake tunanin Abba zaije grnsa amma ba inda aka samu nasarar samun sa.</p><p><br /></p><p>Abu kamar wasa akace qaramar mgn tazama babba, hr akayi sati ba Abba ba lbrn sa.</p><p><br /></p><p> 🌹2⃣2⃣🌹Ako ina an bada sanarwa,an kuma buga jaridu amma ba inda aka ce anga ko mai kama dashi.</p><p> Nayi kuka kukanda ko cewa akayi abbana ya mutu a nan na tsaya,hk muka ci gaba da ryw cikin baqinci marar misaltuwa,ga kuma kaka bata da lfy tun lokacin da akace Abbana ya bace, ta kwanta ciyo,hr akayi wata daya, ba alamar lbrnsa, ciwon kaka sai gaba yake,a safiyar laraba ce kaka tace ga grinku, wani bqn cikin sai ya qaru,kuma duk abin nan da ake ciki yaya abdallah bai sani ba, sbd nyi kiran wayar sa hr na gaji baya dauka,na karbi wayar umma na kira still bai daga ba,bansan lokacinda nyi jifa da wayoyin ba,duka suka tarwatse, da tawa hr ta umma, sbd tsananin baqin cikin da na tsinci kaina a ciki.</p><p><br /></p><p>Ina zaune ina tunanin yadda sauyin ryw ya zomana,cikin qanqanin lokaci.......sai kawai nji umma na rafka salati a bangaren hjy bintu, da sauri na tafi, ina isa umma ta yanke jiki ta fadi,tana mai nunin hjy bintu,sosai hnklin hjy bintu ya tashi, da ita hr qawar ta,tmbyr ummana na Shiga yi amma ta kasa cewa komai,ganin hk ne yasa nje da gudu na kirawo dreban mu muka kaita asibiti,bayan sun gama duk wani bncke da yakamata suyi, suke cemana,umma ta samu mtwr rabin jiki, sbd akwai mummunan abinda tji ko tagani wanda yayi bala'in tayar mata da hnkli.</p><p><br /></p><p>Kuka nake sosai ina kallon umma dake kwance bata iya motsa rabin jikin ta,ina kuma tuna awa biyu,da suka wuce ita ke ma kanta komai, amma yanzu sai anmata komai.</p><p>To wai mene ne umma tj ko ta gani wanda yayi matuqar tayr mata da hnkali hk?</p><p><br /></p><p>Muje zuwa domin jin ko mene ne,umma tji.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:29PM, 11/21/2016] Rynt: [8:54PM, 11/3/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>1⃣5⃣Ta fara da cewa,sunan mhfna Alhj usman sadiq mai gwal,ya kasance mutun ne mai tarin dukiya,akwai shi da son mutane da kyauta ta musu,kuma da wuya kiji ance yana da abokin fada balle har ya kai ga abokin gaba.</p><p><br /></p><p>Mhfna shahararren dan kasuwa ne,a fannin saida gwala gwalai,da motoci, yana da mata biyu,uwargidansa Ita ce hjy bintu,sun hadu ne a dalilin kasuwanci, ta nace mai tana sonsa, amma mhfna bai karbi tayin soyayyar ta ba, sbd ba budurwa bace ta taba aure ta fito, gashi kuma shekara daya ya bata da hfw,shi kuma baya da buri daya wuce ya auri budurwa amatsayinsa na wanda bai taba aure ba.</p><p> </p><p>Haka taci gaba da nuna mai so,har ya kai ga ya amince amma tare da sharadin zai yi aure idan har ya samu yrnyr da yakeso,ta nuna masa ba matsala,akayi aure suna zamansu lami lfy, sai dai matsalar ta daya tana da tsananin kishi,ko kiran sa akayi a waya sai ta duba idan ba mace bace.</p><p><br /></p><p>Ranar kwatsam yaje gaida mhyfr sa,wato hjy maimunatu, ya hadu da mhfyta a can, kuma tayi matuqar birgeshi, komai nata yaji yayi mai, sai faman kallonta yake, anan ne kaka ta fahimce shi,har take ce masa ya akayi ne, ko kana nfn baka gane ko wacece ba?Allah hjy bangane ta ba, amma fa kamar na santa.</p><p><br /></p><p>🌹1⃣6⃣🌹Qanwar ka ce fa 'yar gidan mrgy alhj Aliyu,wato qanin kaka uwa daya uba daya,kenan kakannin su daya da mhfyta da mhfna.</p><p> Qwarai kuwa hjy niko na santa sai dai tana qarama,ba itace Zainab ba?Ita ce fa, ksan kai tn lokacinda akyi rasuwar sai ka tafi dubai kasuwanci, to shine aka kaita a gurin qanwar mhfyrt,hjy Saudat,yanzu kuma Allah ya amshi ranta a gurin hfw ba dan ba uwar kuma gashi bata taba hfwa ba,Allah sarki ai nima da nje gaisuwa nkejin yadda abin ya ksnce,cewa da mhfna, to shine yanzu ta dawo da zama a gurina, ynzn ne ma isowr ta, Allah yaji qansu yasa sun futa,ameen.</p><p><br /></p><p>Tun a wannan ranar mhfn ya fada ma kaka yana sonta, har abin yakai ga mgnr aure, anan ne hjy bintu tace sam bazata taba yadda yayi aure ba, duk da, bata mnt da sharadin mhfna ba kafin ya aure ta, ta tada hnklinta sosai amma hkn baisa mhfna ya fasa auren ba,akazo akayi aure, ga mamakinsa sai yaga hjy bintu, ta hkr sai wani kula ta ke ba umma,amma fa a gbns kadai ne take nuna mata so, zgi da hntr ba wnda bata sha, amma umma bata taba nuna ma Abba zmn da suke ba,shiko Abba a tunaninsa baya da wata matsala a gdns.</p><p><br /></p><p>Haka suka ci gaba da zama hr aka haifi yaya abdallah,qwarai hjy bintu tayi bqncki domin ita ko batan wata bata taba yi ba, sai gashi yaya nada shekara biyu aka hfne,tun daga wannan lokaci hjy bintu take kiran ummana da krwa ganin take a krwnci umma ta samo mu, tunda ita bata samu hfwr ba, ta manta hfw ta Allah ce.</p><p>Klmr krwnc tana ma umma zfi sosai amma hkn baisa ta fada ma Abba ba, kuma daga lkcn bata sake hfw ba.</p><p><br /></p><p>Hk rywa taci gaba har yaya abdallah ya qare scndry nikuma ina a SS2</p><p>Amma shi Yaya abdallah yana krt ne a Egypt kuma idan yazo ganin gd yakan dade sosai bai dawo ba.</p><p><br /></p><p>🌹1⃣7⃣🌹Bayan na qare scndry ne,muna zaune a harbar gida nida abbana, na ke ce ma abbana inaso nima nje krt a Egypt,a nan take naga ran abbana ya baci,kafin yake cewa,walidana, meyasa kike son kije krt a waje,Abba kawai ina sha'wan krt ne a waje kuma ai kaga yayana a can yake krt,Walida!na'am Abba am sry to say bazaki je ko'ina krt ba anan cikin garin Abuja zakiyi krt,domin bazn iya jure rashin ganin ki ba.</p><p>Da yake mun saba sosai nida Abbana tun ina yrnya yake zuwa da ni majalisar su,da na girma sai ya koma zuwa dani qasashen da yake zuwa hrkr kasuwanci shi, amma sai in muna hutu yake zuwa dani,sai dai bada ni kadai yake zuwa ba, ya kanje da matansa,amma abin duty by duty ne sbd yana dan jimawa kafin ya dawo,kuma ko ba umma ke da zuwa ba yaknje dani,amma hjy bintu abin baya yimata dadi, shiko Abba a yanda take nuna mai tana sona sosai sai yaga kamar ba komai bane,kuma gashi ba tauye haqqi a ciki tunda gdn da yake kama mana dakuna ne dashi.Roqonsa nake ina mai cewa,</p><p>"Abba pls kabanni inje don Allah,na gaya miki fa ba inda zakije kawai kiyi hkr!yayi mgnr ne a cikin kakkausar mry.</p><p><br /></p><p>🌹1⃣8⃣🌹Wanda hkn ne yasa na miqe da niyar na bar gun,ina isowa falon na hadu da hjy bintu, kallona kawai tayi ba tare da tace min komai ba ganin ina zubar da hawaye,ta fita,Abba ta samu a zaune tana tmbyr sa yau kuma meya hada ka da 'yar lelenka?me kika gani? gani nayi tana kuka koda ta shiga gdn,tashi muje na ganta.</p><p><br /></p><p>Ni kuma da shiga ta gdn, dakin umma na nufa,ina kuka na fada jknta,me yake frw ne symh, Abbana ne umma😪, yau kuma me kika masa,yace bzn je ko ina krt ba wai a nan xnyi, nikiuma umma a waje nake so nyi krtu na...pls umma ki roqa min Abba da ya banni nje, symh kinsan fa abbanki baya mgn biyu,hkr dai zky, haba umma wlh har mun tsara nida mami, a can zamu yi krtu kuma ita har Abbanta ya yarda, ni kadai take jira taji daga baki na,symh ki gaya mata abbanki bazai bri ba,wasu hwyen ne suka qara zubowa kafin take cewa "umma qawaye na fa duk a wje zasu yi krtu.....ki daina dubin abinda wani zaiyi ke dai ki bi abinda mhfnki yake so, kuma kiriqa tunawa a rywr ki ba duk abu zki nema ki samu ba,inkin samu ki gode Allah idan baki samu ba sai kiyi hkr, amma kar kice wai duk abinda wnce tyi sai nyi, shi yake kaimu ga halaka ki daina kinji, to umma nji zn daina.....amma ai shi Abba bafa don baya da hln kaini bane kawai bayaso nyi nisa dashi.....kuma naga dole yau da gobe zamu rbu ne, hkne symh, domin akwai mtwa.......Nooooo!😳🙊umma,wlh ba hk nake nufi ba,umma don Allah ki daina kira min Abbana zai mutu.....To me kike nufi? nasan zuwa gaba aure znyi, with out shame symh kike gaya min haka,Aaaaa umma🙈 to a daina mgnr nama hkr, na rungume ummana kenan nj Abba ncewa yauwa walidana ko ke fa,tashi nyi nadawo jkn Abbana,shiko yana cewa ummana, shiyasa nake sonki matata sbd kin iya shawo kan yara, murmushi kawai tyi domin ta fahimci ya manta da hjy bintu na bayansa,ga kuma dukkan alama ranta ya baci sbd wannan karon ta kasa boye hkn a gbnsa.</p><p><br /></p><p>🌹 1⃣9⃣🌹Bayan kwana biyu da frwr hkn,ina kwance a saman qafafun umma, tana tje min gashin kaina, take cemin symh wai kuwa kin kira Mami kin gaya mata abinda ake ciki? umma ban fada mata ba nafiso ke da kanki ki kira Maman Mami kiyi mata bayani zasu fi fhimta, to yayi zn kirata in Allah yaso.</p><p><br /></p><p>Ranar kwatsam ina zaune ina kallo ni kadai a falo, sai ga abbana yazo cike da murna,nikuma na tashi da gudu na rngumesa,Abbana sannu da zuwa, yauwa walidana,yau kuma Abba me kazomin dashi? da yake duk abbana ya fita sai ya sayomin wani abu.</p><p> Yau nazo miki da wani lbr wnda zkyi frn ciki da jinsa sosai,mene ne Abbana?na Samar muku admission keda Mami a Egypt a school dinda yayanki Abdallah ke krt,bansan lokacinda na daka tsalle tare da buga kuwa, na qara rungume abbana,ina mai cewa wayyo Allah abbana thank u very much, I love my dady, luv u too walidana,ina mamanki tana ciki,ya tafi zuwa dakinta nikuma na juya dmn na dauko wayata a samn kushin na kira Mami, dagowanda znyi nayi ido hudu da hjy bintu ta min wani mugun kallo Wanda ni na kasa gane laifin me nayi,hk dai ta koma bangarenta batare da ta cemin komai ba.</p><p><br /></p><p>Yau ne zamu je Egypt tun da safe na tashi domin sammako, amma sai ji nake gabana na faduwa,amma nakasa gane dalili,hk dai nje dakin Abbana domin naga ya yatashi........ Sai kawai kuka ya qwacewa symh waldah sosai take kuka hjy ce ta fara da cewa yadai symh wldh meye na kuka kuma, hjy a tun daga wannan ranar Abbana........ Kuka ya sake hanata qarasa zncen,ihsan ce tace me yasamu abbanki......rashin lfy ya same shi?A'a,ko ya rasu ne?a'a Abbana ba mutuwa yayi ba,har yau abbana yana raye.</p><p><br /></p><p>Tabdi muje zuwa kenan domin jin a ina abbanata yake,me kuma yasa yabar su a cikin wannan hali.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:29PM, 11/21/2016] Rynt: [8:54PM, 11/6/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDA🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p><br /></p><p>🌹2⃣6⃣🌹Hjy bintu wannan wace irin mgn ce wacce mai hnkl ba zai dauka ba,karfa kwadayin duniya yasa ki soma zautuwa,.....ba wani zaucewa kuma ba kwadayin duniya a ciki,tabbas mgnr da na fada miki gsky ce, sai dai bazaki gane ba sai nan zuwa gaba,..... Sai da ta nisa kafin take cewa,"toh Allah ya kaimu lokaci,tayi mgnr ne cike da rashin yadda da abin da hjy bintu tace,a game da abdallah ganin take kamar so take ta hanashi gadon mhfnsa,bayan duk wannan cutuwr da ta musu, bata barsu haka ba,har sai ta bullo ta </p><p>nan,anya ko hjy bintu naso ta gama lfy da duniya?....... Hjy larai yadai naga kin zurfafa, ba komai ni zan tafi,to yayi sai munyi waya kenan.</p><p><br /></p><p>Symh wldh ce a daki sai qoqarin kiran abdallah take amma,ta kasa tuna numba daya a cikin nmbrsa,cike da mamaki take sake danna nmbar amma bai sa ta tuna ba...... tana cikin hk ne sai ga ihsan ta shigo cike da mrna, tana mai cewa "symh wldh gobe yaya sa'eed zai dawo,.......Allah ihsan? Allah kuwa,kina fa ji da shi sosai wannan murna haka, hr kin tuna min da yaya abdallah, idan zai dawo barcin kirki ma bazn yi ba sbd duk na juya a cikin barcina sai na tuna gobe yayana zai dawo, na matsu sfy bata waye ba,hmmm aike bakiyi murna a banza ba, tunda kuna shiri dashi sosai, amma ni bamu shiri,yafi shiri da rqy,waini na fiye surutu, da dmw,Allah sarki shi baya son surutu kenan?baya so........kin sami yaya abdallah?bansame saba sbd wai na manta nmba daya,am very surprise, ace na manta nmbar yayana abin da kamar wuya, domin yana da wuya na riqe abu a kaina na manta shi......dama idan xaki kira shi da wyr hjy bintu sakawa kike? ko a seve take?eh anyi saving dinta Kira kawai nake, ba sai na sake sawa ba,to ai ba mamaki dn kin manta....but keep trying ko Allah zai sa kituna, to Allah yasa,Ameen.</p><p><br /></p><p> 🌹2⃣7⃣🌹Washe garin rnar,Hjy ce a daki tana waya bayan ta gama ne, ta fito, ta sami symh wldh a afalo,tana krnt wani littafi na addu'oi.</p><p> Symh waldh! Na'am hjy, so nake ki hada ma sa'eed abinci,domin wai hr ya shigo gari bayan yace sai da maraice zai dawo, ashe ya fasa,to me za'a dafa masa? ba wani abu bane face indomie ita ce yafi so, amma ki hada masa da dafaffen qwai,to hjy...symh wldh ki daina kira na da hjy, ki kirani da umma kamr yadda su ihsan ke kirana, domin kema 'ya ce a gareni, kinji,daga kanta tayi alamar tji tare da murmushi sannan ta nufi hnyr kici.</p><p> Tana cikin kici taji sallamar wani, daga jin mryr zakusan haddaden gaye ne,tana qokarin amsawane taji, umma ta amsa sallamr,.... cike da girmawa ya durqusa yana gaishe ta,ta amsa gaisuwr ne tare da yimasa ya hny, Alhmdlh umma... sai dai ayi hkr umma nace saida yamma amma sai kikaji waya hr na shigo gari,dama wani meeting zmyi sai aka fasa, shi ne na yanke shawarar dawo wa yanzu,.....ai ba komai, ta fadi hknne tare da barin gurin,ta dauko lemu da ruwa ta aje masà,sanan ta nufi hnyr kici, ta samu hr symh wldh ta kammala komai.</p><p> To jeki ki kai masa yana a falo, ni Zn shiga daga ciki, to umma.</p><p><br /></p><p>Tana fito wa daga kicin ta hango shi a samn kjra 1seater ya aza qafa akan dayar qafarsa, kamar wani sarki,ya dan jingina a jikn kjr yana waya sai dai a rufe idawnsa suke da alama a gjye yake yana bqtr bacci,fari ne tas dogo yana da faffadan qirji,da ganininsa anga cikakken nmj,fuskar sa tana dauke da,dan siririn saje ya kwanta sosai,gashi da dogon hnci da bakin sa ma daidaici mai kyau.</p><p><br /></p><p> 🌹2⃣8⃣🌹Sannu a hnkli ta iso inda yake tare da sallamrta, ta ajiye abinci kenan, daidai ya gama waya idonsa yakai kan kyawawan yatsunta,tana sanye da wani zobe na diamond, yayi matuqar yi ma yatsan kyau,riqo hannun yayi yana mai cewa,"wow this diamond ring look beauty, rqy where did u .....wani irin shock yaji har cikin tafin qafafunsa,da sauri ya dago idanuwansa,caraf sukayi ido hudu,yanayin kallonta ne ya qara rikitr da shi,sabida sexy eyes ne da ita,duk da haka ya kasa dauke idonsa a kanta,ta ido tayi masa alama da ya sake mata hannu, ba yanda ya iya dole ya sake, domin ji yayi kamar hannayensu, su tabbata a haka,....katse masa tunani tayi,tana mai cewa "Sannu da zuwa, yauwa sannu,tashi tayi zuwa dakinta, sai faman kallonta yake tfyr ta kmr 'Yar fashion,ya salm wannan yrnyr akwai kyau na fitar hnkli a tare da ita,cewar sa'eed.</p><p><br /></p><p>Yana cikin cin abinci ne,umma tazo,da isowr ta yake tmbyr umma wa ya dafa min indomie, me kagani? Allah umma tayi min dadi sosai,hmm symh wldh wacce ta kawo ma abincin, ita ce ta girka maka, ynyr ta iya girki sosai, domin ni a gsky duk iya grkina, dana ci nata sai da na raina nawa........hln daga ina take?kallonsa tayi tana mamaki sa'eed da bai cika sa kansa a hrkr mace ba amma yau hr yana tmbyr inda symh wldh ta fito....umma ya nji kinyi shiru?wato sa'eed lbrn symh wldh, da abin tausayi a ciki,... nan dai ta bashi lbrn tun daga farko hr qarshe.Sosai ya tausaya mata,sai dai bai ce komai ba,sai ma tmbyr umma da yayi,inda su rqy suke,yaga baigansu ba, a nan take cemasa suna school.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:29PM, 11/21/2016] Rynt: [8:52PM, 11/5/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹2⃣3⃣🌹</p><p>Bayan mun koma gd ne nake tunanin na tmbyi umma wace irin mgn ce tji hr hkn ta faru,kuma meyasa ta matsa a dawo gd, da jinya, tana qoqarin fada min ne sai ga hjy bintu ta shigo, ta kuma ce na basu guri zasuyi mgn,tashi nyi na fita, sai da hjy bintu ta fito sannan na koma,umma wai mene ne ke frw ne? bakomai symh kawai dai ina so ki sani cewa Abbanki yana raye bai mutu ba,kar kiyi tunanin rashin ganin sa da ba'a yiba ko ya mutu ne, ..... Cike da mamaki,na tmbyeta,anji lbrn sane umma?shiru tayi kafin take cewa, a'a ina dai jin hk ne a jikina, kuma inaso ki dage da addu'a in Allah ya yadda, da sannu Allah zai bayyana muna shi, Ameen umma, kuma inshaAllan Zn dage da addu'a, amma kuma umma,ina so nji shin mene ne kika ji a bangaren hjy bintu?.... symh kibar mgnr kawai,....umma meyasa?sbd bai kamata kiji mgnr ba, babu alhairi a cikinta face tashin hnkli, kuma inason kar ki qara tmby ta wannan mgnr,domin tuna mgnr yana qara haifar min da matsala,shiru nyi ina tunani,wai kodai tji wani lbr ne game da abbana ne wnda bai mata dadi ba, shi ne take boye min,ko kuma tji lbrn mtuwar sa ne, saurin kawadda tunanin nyi,ina mai cewa, "umma inshaAllah bzn qara tmyr ki ba, sbd bana so kici gba da samun matsala, sai dai muyi fatan Allah ya yayemuna ita,Ameen symh wldh,Allah yayi miki albarka,Ameen.</p><p><br /></p><p> Umma nji kince symh wldh? eh hka nace, ina so ko bayan raina sunayennan guda 2, a riqa krnki dasu,bana so ki ajiye ko guda a cikinsu,sbd abbanki yana kiranki da Walidah nikuma ina kiranki da siyamh,kuma dukannimu bama so a ajiye ko daya a cikin sunayennan,ina fata kinsan dalilin da yasa nake kiranki da symh,abbanki kuma wldh?eh umma kina kirana ne da symh sbd kin haifeni a cikin azumi,abba kuma yana kirana da walida,sbd sunan kaka ne dani wato maimunatu.</p><p><br /></p><p> 🌹2⃣4⃣🌹Umma mtsala ta daya itace yaya Abdallah bai san hlinda muke ciki ba,tunda ko ankira wyr sa baya dagawa,....... kiyi masa uzuri mana, wata qil wayr ta fadi ko kuma suna jrbw,kinsan Abdallah a yadda ya dauki krtnsa da muhimmnci,kawai dai umma abar mgnr amma dai da laifinsa a ciki, kusn wata biyu bai kira ba fa, hk ne hkr dai zamuyi hr ya dawo tunda ya kusa dawowa kinji, to umma Allah ya maidashi lfy Ameen,</p><p><br /></p><p>Tun daga wannan ranar,na qara ganin sauyin ryw, domin hjy bintu ta kori duka masu yimuna aiki,ta kuma canza mai gadi, ko meye dalili oho,ga kuma lalurar umma sai gaba takeyi, hr takai ga duk jknta baya motsi sai kanta kawai zuwa wuya,amma hkn baisa hjy bintu tyi min sassauci ba,hr kasuwa ma idan znje cefane, sai ta hada ni da wani domin kar nje ko'ina, kuma dama ni ba inda nake zwa face gidansu mami, sukuma basa nan.</p><p><br /></p><p>Hka dai ta cigaba da basu lbr, tun daga rasuwr mhfyrta, har zuwa ranar da suka taimaka mata,kuka take sosai ihsan ma haka,Ita ma hjy cike take da tausayin symh wlida,sai kuma tji son ta ya qara shiga a cikin ranta,jawo symh wldh tyi a jiknta ta rungume ta, tana mai lallashinta,"ki daina kuka symh wldh ki dauka nan tamkar gdn Ku ne, kuma inshaAllh sai nasa an kama hjy bintu.....hjy nasan hjy bintu bazata zauna a qasar nan ba, tunda taga na kubuta.....hk ne amma a duk inda tje ba a can zata tabbata ba, zata dawo Nigeria,inshaAllah,.....hjy ni ynz so nake kawai yaya abdallah ya dawo na sanar dashi abinda ake ciki, na tabbata yaya abdallah zai dauki mummunan mataki akanta, sbd dama can basu shiri da Ita, kuma shi tana shakkun gaya masa mgnr da taga dama, domin baya bata bashi,ai kamata yayi,ki Kira shi ko Allah zaisa wyr ta shiga,ina fata kina da nmbrsa akai? Eh ina da nmbr.</p><p><br /></p><p> 🌹2⃣5⃣🌹A bangaren hjy bintu kuwa, tun ranr da symh wldh ta gudu, ta yanke shawarar Barin gdn, wato ta kwashe duk wani abu da tasan tana buqata, ta koma a sabon gidanta, da zama wnda ba wanda yasan tana da gdn face hjy larai, qawa ce ga hjy bintu.</p><p><br /></p><p>Zaune take a babban falonta ita da hjy larai, hjy larai ke cewa, "nikuwa qawata banga alamun kina da niyyar barin qasar nan ba bayan kinsan hlin da ake ciki..... ba inda zani,sbd nsn a duk inda symh wldh taje , zasu yi tunanin zn bar qasa,kinga kenan baza suyi bncke a Nigeria ba,sai dai sukai rahota a filayen jirgi koda na dawo a cafkeni, to kinga ban fita ba, balle hr su kamani,sannan kuma na tabbata symh wldh jire take da dawowar yayanta,ta gaya mishi hlnd ake ciki,idan hr ma tayi tunanin kiransa a waya hkn ma yafi min dadi,sbd zanji inda take a gurin abdallah,kinga kenan,tamkar bata tsira bane muddin ta kira abdallah,domin duk yadda za'ayi,sai na maida symh wldh a hannu na,sai kuma na nuna mata kuskuren guduwanda tayi,ta yaya zaki maida symh wldh a hnnaunki? bayan kinsan cewa idan abdallah yaji bazaki tsira ba,ko kuma kina tunanin bazata fada masa abinda ya faru ba,hr sai ya dawo, hmmmm hjy larai kenan abu daya da baki sani ba shine, abdallah yasan komai.....bangane ba hjy bintu?kina nfn yasan bacewr mhfinsa da kuma mtwr mahaifiyar sa?da kakar sa?amma yaqi dawowa Nigeria,wani mgn murmushi tayi kafin take cewa, "hjy larai, inso kisani cewa, abdallah ba jinin su bane, ba kuma shine dansu na gaske ba, kwata kwata basu da alaqa dashi.</p><p><br /></p><p>Ina fatar kuna tare dani, domin jin, ya akayi Abdallah ya kasance ba shine dansu na gaske dasu ka haifa ba.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:29PM, 11/21/2016] Rynt: [8:11PM, 11/7/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹2⃣9⃣🌹Bayan sati daya da faruwr hkn.</p><p>Symh wldh ce zaune a samn gado, da alama kiran waya take amma bata samu,hkn yasa tji haushi hr tana qoqarin jifa da wyr, sai tji salamr sa'eed, kallon ta kawai yayi,yana mai kallon hannuta da take qoqarin jefar da wyr, ya fara da cewa, "me yake frw ne symh wldh, cikin sigar kuka ta fara mgn, yaya sa'eed kullum sai nayi qoqarin tuna nmbr yaya abdallh amma na kasa tunawa,kuma gashi ina so nyi waya dashi kafin ya dawo.</p><p><br /></p><p>kallon ta kawai yayi yanayin yanda take shagwaba abin sha'wa,sai wani qara shiga ransa da tayi, amma ita ga alama bata ko san a shagwabe tayi mgnr ba,yana cikin kallonta sai naga yayi 😊ya fita ko meye dalili oho.</p><p>Binsa tyi cike da mamaki, tana cewa "amma lallai gayen nan, wato ba wani taimako da zaimin ya tmbye ni,wata qil ma akan abincin sa ne yake tmby, me yake frw yaga ba'a dafa masa ba,niko kawai na fara suburbuda masa mtsalata, ashe ba Ita ce dmwr sa ba......shigowar umma ne yasa ta yin shiru,umma ta fara kirn sunan symh wldh kafin take cewa "ina fata dai baki fadamasa komai a lbrn kiba,kamar me kenan umma?kamar ki gaya masa,hjy bintu ce ta kashe miki iyaye ,ko sunan hjy bintu bana so sa'eed yji, sbd ba komai na fada masa ba, a game da lbrnki,meyasa umma, ina da babban dalili,duk da nsn bai zai sake tmbyr ki ba,ganin yadda yake shiri dake ne, yasa na fada miki Kar watarana kuna fira ki gaya masa,domin ko ynz nji kina mgn akan abdallah, inshaAllh umma bzn fada masa ba,yauwa symh wldh, na fiso sai abdallah ya dawo ko mene ne sai ayi kinji, daga kanta tayi alamar taji,amma tana dan mamaki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ashe fitar da sa'eed yayi kirn sa akayi a wya, da yake vibrate take yi ba'a jin ringing,wani babban abokin sa ne ya kira shi,yana so zai zo, zasuyi wata muhimmiyar mgn.</p><p><br /></p><p>Ba bata lokaci ya iso, yasamu sa'eed a dakinsa, doctor na gani wanda hjy bintu ta kai,lkcn da su symh wldh zasu yi tfy zuwa india,ita da umma,,,,,,zama yayi yana cewa "kai ko shi ne ka baro Oman, ban ko sani ba,.....kai dai kawai gaya min abinda ya kawo ka,kallon sa'eed yayi, yana mgn a cikin rans, shi dai hlnsa kenan baya son srtu marar amfani......katse tunanin yayi yana,cewa "wannan mgnr dana fara ai mai amfani ce naga baka so ayita......ina kuwa amfani tunda nadai riga da nadawo baka sanin ba.</p><p><br /></p><p> 🌹3⃣0⃣🌹To naji amma dawowr ka ne yasa nima na dawo, meyasa baka fada min zaka je ba? sannan kuma me ya kaika,? naso na fada maka,amma sai nji wayr ka bata shiga, nayi tunanin network ne, sai kawai na yanke shawarar nje, sbd muhimmancin abin,koda nje sai nayi rashin Sa'a ka dawo Nigeria, shi ne na biyoka, sannan kuma abin da ya kaini wata mata ce bata da lfy, sai hjyr gdn ta kira ni da nayi mata allurar da aka saba yi mata kullum,......dama kai ne ke mata allura kullum?No am not d one,but doctor dinda ke mata yayi tfy baya gari,gashi kuma ba'a so a qetare koda kwana daya, shi ne ta kirani domin na mata, to byn nyi mata ne,zn fita daga gidan, sai nji hjyr na waya, tana cewa"ai kedai bri hjy larai burina ya kusa cika na ganin bayan Zainab,domin yau nasa ammata allurar mutuwr jiki, hr ta kwana ukku ba tare da tà farka ba, kinga kenan za'ayi tunanin ta mutu,kawai sai a sakata arami kowa ma ya huta.,,,,,,,,, sai dai bana jin a dayan bangaren me ake cewa, sai amsa da nji ta bayr tana cewa"ai ke bayanzu ne allurar zata fara aiki ba sai gobe da safe,kafin suje India, kinga kenan na tura ta inda ma yafi indiya,........to kai ya ma akayi ka mata allura baga dubi ko wace iri bace, kana abu sai kace marar ilimi!.....ba fa hk bane sa'eed,tabbas allurar da ake ma mai irin ciwonta ne, bafa qaramin shiri tayi ba domin ruwan allurar suka canza......... Tabdi! wannan matr bata da imani wlh.....shin wai ma tukuna yanzu ina mtr take?tana Oman a asibitin da kake aiki,sai dai bata san inda take ba kwata kwata bata motsi numfshi kawai take yi,to kai ya akyi ka ceto mtr? byn an rufe ta, nikuma sai nje na cirota,,,,,da yke na koma da safe domin yimata allura,sai kawai na nuna kamr ban san komai a Kai ba,hr aka je dani maqabarta,naga inda a Ka saka ta,shi ne nadwo da dare na cire ta.....Gsky kayi babban taimako sàlmn.</p><p><br /></p><p> 🌹3⃣1⃣🌹To ynz ya kake so ayi? kulawr ka nake so a gareta sa'eed, sbd akan ka kadai na kaita Oman, domin nsn zaka iya, sannan matr sai an kashe mata kudi sosai........kudi ba matsala bane agareni salmn,sai dai ya kamata ace 'yan uwanta,ko 'ya'yanta, sun san hlinda ake ciki,hk ne gsky sai dai bansan kowa nata ba face 'yar ta, kuma nje gidan,domin na samu nagaya mata abin a asirce,sai na tarar sun tashi ba'asan inda suka koma da zama ba, amma tabbas idan naga yrnyr zan gane ta,..... Tunda abin yazo hk salmn,fatanmu Allah yasa matr ta tashi,kaga kenan sai muji komai daga gareta,to Allah yasa sa'eed, Ameen.</p><p>Gsky sa'eed yunwa nake ji,... nima injin yunwar bari nasa akawo muna abinci,,,,,,,,, symh wldh ya Kira awaya yace ta kawo musu abinci,ba jimawa ta iso da sallamar ta ta ajiye musu abinci ta fita, fitar ta keda wuya slmn ya fito daga toilet,,,, yana cewa hr ankawo abincin kenan? eh yanzun nan ma ta fita, shi ne baka bari mun gaisa ba,.......ai ba rqy bace,idan itace ai baxn bari ta tafi ba hr sai kun gaisa,,,,,, duk da hk ya kamata naganta kafin na tafi,rqy fa tana school, sai yamma ko zata dawo,sai dai idan Umma zaka gaida,to mugama cin abincin sai muje na gaida ta.</p><p><br /></p><p>Suna gamawa bada bata lokaci ba,suka shigo bangaren su umma.</p><p> Umma ce da symh wldh a falo, suka ji ana knocking, symh wldh ce ta miqe domin bude qofar.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:30PM, 11/21/2016] Rynt: [9:09PM, 11/8/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDA!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹3⃣2⃣🌹Miqewr ta ke da wuya sai aka kirata a waya,,,,,,,symh wldh wayanki na ringin a daki jeki kawai bari na bude, ta wuce zuwa dakinta,,,,,,,sai umma taje ta bude musu qofar suka shigo, suna gama gaisawa ne,, sai salmn yace "yana son zai tafi domin sauri yake,,,,,,,,fitar su keda wuya,sai ga symh wldh ta dawo tana mai cewa"umma ihsan ce ta kira ni ta manta da wani lecture guide dinta,tana so akaimata,,,,,,,,to a ina ta ajiye shi,cewa tyi na duba a smn gadonta domin hr ta dauko ta manta,,,ok to jeki ki dauko bari na kira sa'eed sai yaxo ya kaiki,,,,,ba jimaw yazo suka tafi, suna cikin mota shiru ba mai mgn a cikinsu,sa'ed ya katse shirun yana mai cewa, "dazu kinga na fita bance miki komai ba, ankira ni ne a waya,ai ba komai yaya sa'eed,,,,,, daga hkn ba wanda kuma ya sake cewa komai, sai str kallon juna da suke, hr suka isa mkrntr su ihsan.</p><p> A hnyr su ta dawowane aka gwapce da ruwan sama ,da yake dama koda suka fita akwai hadari, symh wldh ta matsu basu iso gd ba domin ta shiga rwa tayi wasa, hnnunta ta aza akan gls din gambun motr, sai kallon yanda rwn ke sauka a jikn gls din take, tana mai murmushi,sa'eed kuwa driving yake amma yana yi yana kallonta cike da sha'wa domin shidai a zahiri komai na symh wldh burgeshi yake,mgnarta,murmushinta,dryrta,shagwabrta,,yanyin jknta,kai komai ma,,,,,, kuma bai taba jin hk awata 'ya mace ba, face symh wldh,kuma yakasa gane dalilin hkn,</p><p><br /></p><p> Um um fa sa'eed kar kace min baka san so ba,duk waywrka da hdwr nan taka,,,,,,,koya kikace,my lovely Namesake(futuhatulkhair)😘</p><p><br /></p><p> 🌹3⃣3⃣🌹Suna isowa gida ,da sauri tayi yunqurin fita a cikin mortar,sai kawai taji yasa key wa motar,kallonsa tayi da niyr tayi mgn sai dai yananyin yanda ya dan fuske yasa ta fasa mgn,,,,,hr kusn minti biyr tji baxata iya hkrn rashin shiga rwn nan ba, ta fara da cewa,"yaya sa'eed ina so na fita pls,,,,kamr bazai yi mgn ba, can sai yace"ba kya ganin ruwa ake,to ai ni rwn nake son shiga,shiru kawai yayi kuma da alama baya da niyr sake yin mgn,,,,Ita ma dai bata sake cewa komai ba,iya bacin rai rnta ya baci domin taqi jinin taga ana ruwa a hana ta shiga,,,,bayanda ta iya dole ta dan kwantr da seat, ta kwanta hr ruwn su dauke,,,,,saida aka dauke tsaf ya juyo da nyr yace mata tana iya ta fita, sai yaga ashe hr bacci ya dauke ta,kallon ta yake yana mai cewa a cikin rnsa"wow sleeping beauty,wato yrnyr nan ta ma fi kyau idan tana bacci,,,,,,,yayi kusn minti 3 yana kallonta, yana kuma tunanin yanda za'ayi ya tashe ta,ya matsa daf da ita hr yana jin numfashinta hade da qamshin turaren ta mai dadi,,,,,,kamr wacce aka tsakara sai ta bude idanwnta da suke cike da jin bacci,dama idanun ya suke balle tana jin bacci,,,,,gashi kuma da bude su ta sauke su akan nashi, ba shiri ya runtse idonsa,hr tana ganin yanda yake fitr da numfashi sama sama kadan, sbd wani abu da yaji,tun daga smn kansa hr cikin tafin qafafunsa, hr saida tsikr jikinsa ta tashi,da qyar ya iya frta "zaki iya fita an dauke ruwan,</p><p> Kalonsa ta koma yi,shi ma hk yana mai murmushi akasin ita da tasha masa toka,domin ganin take ya hana ta jin dadi yau,,,,,binta yayi da kallo lokacin da take wucewa,shima daga bisani ya wuce nasa bangare.</p><p><br /></p><p> 🌹3⃣4⃣🌹Bayan kwana biyu da frwr haka.</p><p> Ihsan ce a bakin gate din gdnsu Ita da wani saurayi, tsaye a bakin motrsa suna fira,sai faman dry suke irin ta masoya,suna cikin hk sai ga motr sa'eed ta kunno kai,,,, ihsan ce ta fara hngoshi duk inda hknlinta yake ya tashi, nan take tace ma saurayin ya tafiya ga yayanta nan yazo,yana qoqarin tmbyr ta dalili....... ta katse shi da cewa"kai dai nace ma ka tafi, OK yayi sai munyi waya kenan.</p><p> Ya shiga motrsa ya tafi ita kuma tashige cikin gd,,,,,,Ashe sa'eed ya riga da ya hango su, ranshi yayi matuqar baci, wai ita 'yar ihsan din nan ta fara tsayi da samari, ko samari irin 'yan iskan samarin nan.</p><p> Yana gama parking bai zame ko ina ba sai bangaren su, kuma a dakinta direct ya tafi, tare da zare belt din wandonsa,,,,,ya bankin qofar dakin da qarfin tsiya, ba shiri ihsan ta juyo domin ganin wane ne,kafin tyi wani yunqiri ya fara dukanta baji ba gani,sai faman kuwa take tana bashi hkr,,,,,,</p><p> Symh wldh na fitowa daga wanka ta jiyo kuwan ihsan, a rikice ta tafi domin ganin me yake frw, gashi daga ita sai towel iya cinya,,,,,,, tana zuwa dakin ihsan ta samu sa'eed sai zabga ma ihsan belt yake ba qaqqautawa,,,,riqe belt din tayi tana mai cewa"haba yaya sa'eed me yayi zafi hk kake dukanta,😡symh wldh give me d belt pls,ko kuma wlh na hada har dake, No yaya gsky bazan bayar ba,ganin da gaske take yasa,ya damki hanunta ya amshi belt din da qarfi, sai da ta saki 'Yar qara, sbd zafin da taji,,,,, bai damu da hkn ba, komawa yayi gun ihsan da niyr ci gaba da dukanta,da sauri ta yo wurin symh wldh ta labe a bayan ta,ta rirriqe ta tana kuka,,,,"don Allah yaya kayi hkr wlh bazn sake ba,,,,,da wane dan iska ne kike tsaye,? yana mgn yana matsowa inda suke,tare da riqo hannun symh wldh yanaso ya jnye ta domin yaga ihsan din da kyau, ya jawota kenan ita kuma ihsan ta damqi towel din ta baya,ai kuwa sai towel ya zame a jkin symh wldh,saukin ta daya akwai pant a jkinta.</p><p>😳 Oh Nooo!🙈 cewar sa'eed da sauri ya bar dakin,yana mai cewa,a cikin ransa,"yrnyr nan sai da ta bani hkr naqi gashi na gano ma kaina abinda ya fi qarfi na, wanda zai sa na kasa yin bacci mai kyau a daren yau.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:30PM, 11/21/2016] Rynt: [9:24PM, 11/9/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDA!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹3⃣5⃣🌹Da sauri ta duqa ta dauko towel dinta ta daura, sannan ta juya gun ihsan, tana mai cewa"haba ishan meye hk don Allah,😔...... Please symh wldh don Allah kiyi hkr na tsorata da yawa ne shiyasa,..... amma ai mgn kawai yaso yayi dake, ba cigaba zai yi da dukanki ba, tunda kinga ya ma ajiye belt din,..... Hlin yaya sa'eed ne baki sani ba, zai yi kmn ya hkr amma ba hkr yayi ba,...amma am so sry pls,,,,,kallon ta kawai tyi ba tare da tace mata komai ba, ta tafi abinta,tana mai jin haushin ganin ta da sa'eed yayi,,, hr tana mgn a cikin ranta"ina ma ace mafarki nakeyi ba gske bane,ko kuma ace mace ce ta ganni ba nmji ba, yaya ma za'yi nakoma hada ido dashi,wannan abin kunyar hk.</p><p><br /></p><p>A ranar wuraren karfe 8:30pm</p><p> Umma ce da rqy a falo suna kallo a tashar MANARA TV,suna cikin kallo ne umma ta lura tnda ta dawo daga unguwa bata sa symh wldh a idonta ba,,,,sa kwn Kiran ihsan tayi"ihsan!ihsan,,,,,,,Na'am umma ina zuwa,koda tazo sai wni kame kame take, ta zata sa'eed ya fada ma umma abinda ake ciki,,,,,me yake frw na gnki sai kace mrar gsky,,,,uhm ba komai umma dama grin sauri ne na fsa turare na,,....to nji kira min symh wldh.</p><p> Koda taje ta same ta sai rwr dari take,ta qundundune a cikin bargo.,saurin yaye bargon tayi tana mai cewa.</p><p> "Me yake dmn ki ne symh wldh,,,nuna mata hannun ta tayi ya dan qabe sbd jinmwr da tayi dazu da Karfen belt, shi ne ya sako mata zazzabi,,,oh my God ashe hr haka yaya sa'eed yaji miki ciwo,,,,dama fa hk jiki na yake abu kadan sai kiga ya zama babba hr ya saka ni zazzabi,,,,na shiga uku! gashi kuma banaso umma tasan yadda akayi hr kika ji ciwo,pls symh wldh koda ta tmbye ki, kice mata yankewa kikàyi da wuqa.</p><p><br /></p><p>🌹3⃣6⃣🌹Bata tsaya jirn jin me zata ce ba,ta kirwo umma,,,, umma ke cewa ayya symh wldh, ashe yankewa kikayi a hannu,,ta duba hannun tana mai cewa bari na kira sa'eed yazo ya duba ki,..... A'a ba sai yaxo ba kawai a bani mgani nasha,.... A'a jkinki yayi zafi sosai ina ga ma hr allura sai an miki,bata fi mniti 5 da kiransa ba sai gashi yazo,yana duba hannu yace"oh my God ashe hk na......a'a fa yaya sa'eed wuqa ce.....ba na son rainin wayo ihsan,...girgiza kanta tayi alamar don Allah ya rufa mata asiri bata so umma ta gane,.....umma don Allah a ftr da yrnyr nan zata dameni ne kawai,....kai dai sa'eed na rasa gane me ihsan tamaka,kafiye ta kura mata, daga kawai ta gaya maka abinda ya same ta,.....kinga ihsan zo muje,,,,, dama shi sa'eed abinda yake so kenan su basu guri.</p><p> Hannunta ya riqa yana mai cewa"symh wldh, kiyi hqr bada niya na miki ba, rai na ne ya baci da yawa,am so sry pls kinji, shiru ta mishi kamr mai yin bacci,hr so biyu yana kirnta,bata tanka masa ba,kuma ya lura ba duk bacci takeyi ba,,,ya dan yi wani tunani kadan kafin yake cewa,,,"OK tunda bacci take bari kawai na mata allura na tafi,yafara da yaye bargo, yakai hannusa a gun zip din siket dinta,da niyr ya bude,,,,da sauri ta tashi zaune domin ta fhimci da gaske yake,,,, yayi murmushi kafin yake cewa"yadai hr kin tashi daga baccin,..... shiru ba amsa,,,, kinga symh wldh mgn fa nakeyi dake kin min shiru, ko baki hkra bane?</p><p><br /></p><p> 🌹3⃣7⃣🌹Tashi yayi ya dauko reza,,,oya gashi rama abinda na miki a hnnu,...nifa bashi bane, to mene ne?kallon sa kawai tayi ta gefen ido, ba tare da tace komai ba.....uw ko don naganki ba kaya a jkinki,nima bari ki ganni ba kaya kenan, ko?yayi mgnr ne tare da fara cire aninin rgrsa,sai dai bada gaske yake ba, yayi hkn ne domin yana so ta sake,,,,ita kuwa ta zaci da gaske yake yi,tayi saurin cewa "No yaya sa'eed wlh ba haka bane,yau bana ra'yin mgna ne, kuma idan bana da lpy bana so ana min srt, to nji yi hkr,.... zn miki allura sai ki gyara ko?yaya sa'eed pls ka bani mgni ni bana son allura😔,... Ita kuwa ya kamata ayi miki domin jkinki yayi zafi sosai,yayi mgnr ne tare da dauko allura,......tana ganin hk, Sai kawai ta fara kuka mrar sauti,</p><p>dago kansa yayi yana mai kallonta yanayin yanda take kuka,sai yaji ta bashi tausayi.</p><p> Ok ya isa hk tunda ba kya so shi kenan,,ya miqa mata magani tasha, shiko ya nufi hnyr fita,share hawayen ta tayi tana mai cewa "thank u yaya sa'eed.</p><p> Ya juyo ya kalleta kmr yayi mgn, ko me ya tuna sai kuma ya fasa, ya fita abinsa.</p><p> Bayan kwana hudu da frwr hkn.</p><p> Sa'eed na gani zuwa bangaren su umma,cikin shirin tafiya, da alama zai koma Oman ne,umma ya samu a falo zau ne ita kadai,sai da ya gaishe ta kafin yake cewa, "wai ina symh wldh take naga a 'yan kwanakinnan ke kadai nake gani,akasin da, dana ke samun ku a tare,,,,, nima na kasa gane kanta, sai muna zaune muna firar mu,da zrar tji zaka shigo sai kawai naga ta tashi,....... ko wani abu ya hada Ku ne? ba wani abu umma,...amma bari naje nji ta bakinta, ko akwai wani abunda na mata ban sani ba.</p><p> kwance ya same ta a smn gado,ya fara da cewa,"symh wldh ki tashi zaune ina so zamu yi mgn, cikin jin kunya ta zauna ba tare da ta kalle shi ba,..... Ya kamata ace kin daina jin knyr nan haka, tunda dai mistake ne fa,kiyi hkr kinji ki maida komai ba komai ba,domin idan kina min hk sai nayi ta tuna abun,.... Kalonsa tayi,....eh hk ne mana,....yanzu duk ma ba wannan ba,zan koma Oman,kuma ina so nayi wata magna dake, mai muhimmanci sosai.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:30PM, 11/21/2016] Rynt: [7:26PM, 11/13/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🎄🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊</p><p>4⃣5⃣YaYa sa'eed pls kar ka min hk😭.</p><p><br /></p><p>Firgigit,ta tashi daga mummunan mfrkin da take,,,,sa'eed ta gani a tsaye,aikuwa firgicn da take ciki ya qaru,.... ganin hk ne sa'eed yje gurin ta da sauri, yana mai cewa my lady what hapn to u?,,.....mene ne gayamin?,, komai ta kasa ce masa sbd tsananin rudanin da ta shiga a cikin mafarki,gashi kuma da tashinta sai ta ganshi,,,,rungume ta yayi anan yji jikinta har rawa yake,oh no my Lady,, wane irin mumnan mfrki ne kikayi hk da ya rktr min dake,?...No lovely kawai abr mgnr,tyi mgnr ne a cikin kuka,,,,,,my lady irin hk addu'a zakiyi ba kuka ba,amma me kike tunani ne akaina kafin kiyi bacci?me kaga ni lovely?koda nazo da nyr namiki sai da safe,na samu kinyi bacci, amma sai naga kin fiye motsi,hkn yasa na tsaya da niyr yi miki addu'a, sai kawai nji kina cewa"pls yaya sa'eed kr ka mn hk ,,,,sai gashi naga kin tashi a frgice,mene ne kike cewa kar na miki?kallonsa tayi tana mai cewa a cikin rnta,"ya zama dole na masa qarya,domin na fhmci rqy bata gaya masa ba,...tmbyr ki nake my lady, No jst i mean kar ka kusance ni,hln ba'a daura aure bane a mfrkn?an daura,... amma kike jin tsoro,...ko da yake kinaji ana fada da zafi shine yasa kike jin tsoro,kar ki damu ni a haaaankali zn miki,,, kallonsa tayi cike da jin kunya,,,,,my lady ba batun kny kwana fa biyu ne ya rage mu zama daya,don hk ki dai na jin kny ta kinji,,,,uhm nji😊</p><p><br /></p><p>Bashi ya fito dkn ba hr sai da ya tabbatar tyi bacci.</p><p><br /></p><p>Da safe rqy sai tunanin take yadda zata bullo ma sa'eed akn ya fsa auren symh wldh,gashi umma tayi rantsuwa akan kar ta fada masa zncn hjy bintu,hk ta yini tana tunani hr dare bata samu mafita ba, gashi gobe ne daurin aure,tana a cikin tunanin ne, sai kawai naga ta tashi tana mai frnciki,da alama ta samu mafita,,, bngaren sa'eed ta nufa, tayi sa'a bai fita ba domin da niyr fita yake hr ma ya rufe side dinsa,ganin ta da yayi ne yake cewa "ya akayi ne rqy,?yaya inaso zamu yi mgn dakai ne, ok to mu shiga daga ciki,,,,inajinki rqy,ta fara da cewa"nikuwa yaya me yasa kake so ka auri symh wldh bayn bamu san kowa nata ba?sbd ina sonta,,,amma yaya baka tunanin lbrn da ta fada ba gskya bane?uhm rqy kenan na ydda da symh wldh dari bisa dari,...to idan ka yadda da ita, me ya baka shawa'an auren yrnyr da wasu mzn suka sani kafin kai?</p><p>Ban gane zncen ki ba rqy😳,,,,yaya sa'eed inace umma ta gaya maka cewa biyo symh wldh akayi da nyr fyade?ta gaya min hk amma ai basuyi nasara aknta ba,,,,yaya sa'eed symh wldh qarya tayi ma umma, domin koda ta zo gdn nan ko tfy bata iya yi da kyau hr sai da umma ta kaita asibiti,,,dakata!✋rqy ni na yadda da ita bazata yi qry ba,don hk ki tashi ki bani guri,yaya gsky fa nake fada maka, nji zn kuma aureta a hkn,,,fita min daga daki,kuma kar ki qara tunanin dawo min da wani znce,domin bzn yadda ba indai akan symh wldh ne,ina sonta so na hr abada,koda kuwa ya ksnce sun mata fyaden, yaya......I said get out of my room😡</p><p>sum sum ta fita jki mace.</p><p><br /></p><p>Byn ta fita ne yake mgn a cikin ransa,,,kaddai ace abinda rqy ta fada gsky ne idan ba hk ba me zai sa my lady tasa tsoro a ranta na kar na kusnceta har ta kai ga yin mfrki,kenan gsky ne,.....No ba gsky bane, kai koma gsky ne zn aureki a hk,kuma znci gaba da sonki symh wldh so na hr abada.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro 💗</p><p>[10:30PM, 11/21/2016] Rynt: [9:03PM, 11/10/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDA!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹3⃣8⃣🌹Ina jinka yaya sa'eed,,, wato wata mata ce bata da lpy sosai hr ma bata san inda take ba,kuma ba'a sn su waye 'yan uwnta ba,gashi kuma ni ne zn kula da ita, shi ne nake so ki taya ni da addu'a,ko Allah zai sa ayi nasara ta farfado, kuma wlh ina so matr nan ta tashi ko don abinda aka mata,,,, me ya faru da ita ne?ko kade ta akayi da gayya ba'a tsaya ba?babu ko daya a ciki symh wldh,,</p><p> wani abokina ne slmn da ya taimaki mtr,shi ne yazo min da lbrnta, Allah akwai rashin imani da akayi wa mtr a cikin lbrin,,,, nikuwa yaya sa'eed ina so ka gaya min lbrn inji?kin gane shi slmn din doctor ne.......wayr sa ce tayi ringing, ya duba yana mai cewa,,,,,Oh my God kinga hr na manta fa da slmn yana jira na a waje,,,,tare zakuyi tfyr kenan? eh amma dawowa zai yi sbd ba'a can yake aiki ba,....taso ma muje ki ganshi daga nan ku gaisa,sbd shine babban amini na, kar watarana ku hdu baku san juna ba,,,,No yaya sa'eed abar shi hr wani lokaci tunda yanzu sauri kuke yi,Ok na tafi,,,,Allah ya kiyaye hnya, Amin symh wldh.</p><p><br /></p><p>Shiru tayi tana dan tunani kafin take cewa,"wannan mtr ko me aka mata na rashin imani......wata qil ma'yan asibiti ne suka wulaqnta ta ganin ba 'yan uwa,,,,,,shiko slmn ya taimaka mata,,,Allah ya biyaka slmn, ita kuma Allah ya bata lfy,Allah kuma kasa yaya sa'eed ya kula da ita yanda ya kamata. Ameen cewar Billy giro.</p><p> Ni kuma symh wldh nayi alqawari sai inda qarfi na ya qare a game da yi mata addu'a,inshaAllah.</p><p><br /></p><p> 🌹3⃣9⃣🌹Bayan sati biyu da faruwr hkn, zaune take akn kafet din sallah tana azkar,hr bacci yana so ya dan dauke ta,...ringing dinda taji ne yasa ta bude idonta domin taga wa yake kirant,, nmbr waje ta gani, ta tashi cikin zumudi tare da murmushi a fskrta,hr zata daga sai kuma tayi wani dan guntun tunani,da alama akwai abinda take cewa a cikin zcyr ta,can kuma sai ta fara mgn a fili, tana mai cewa,"to idan yaya abdallah ne a ina ya samu numba ta, amma bari na daga nji ko waye,tana aza wyr a kunnen ta sai tji ance symh wldh,,, a nan take ta gano mai mryr ,,,,la yaya sa'eed Kaine?eh nine symh wldh, ya kike?lfy kalau, su kayi shiru na 'yan sakwanni,sa'eed ne ya katse shirun yana mai cewa, ina ftr baki manta da alqawari na ba? No yaya bn manta ba, ina kuma ftr mtr ta fara jin sauqi, eh... to baza a ce komai ba sai dai nace Alhmdlh,to Allah ya qaro sauqi, Ameen my lady,....yau kuma nice ur lady yaya sa'eed? dama kullum kece my lady ba wata ba.</p><p>symh wldh, ina ftr na zama hawaye a idanunki, na zubo a kumatunki,hr zuwa lebenki amma ni bana fatan ki zama hawaye a idanuna,sbd zan rasa ki a duk lokacin da nayi kuka,my lady take care of ur self, yana gama fada sai kawai ya katse wyr, yana cike da jin frn ciki marar misaltuwa,,,,, symh wldh kuwa tunda ya katse wyr ta kasa wani qwaqqarn motsi, tana tunin anya kuwa yaya sa'eed yasan dawa yayi waya kuwa,,,,, to idan dani yake me yake nufi da waddanan kalamai nasa?bata da mai bata amsa don hk ci gaba kawai tayi da abinda take.</p><p><br /></p><p> 🌹4⃣0⃣🌹Haka yaci gaba da kiranta kullum yana fada mata kalamai masu dadi masu kuma daure mata kai,kuma yaqi ya fito fili yace sonta yake, balle ta fahimci inda kalamnsa suka nufa, sannu a hnkli hr ta daina mamaki, Wanda hkn yasa hr ta fada sonsa bata sani ba,kullum sai zuba soyayya suke abinsu,</p><p> Yau kamr kullum wyr suke,a cikin haka ne yake cemata in Allah ya yadda gobe zai dawo,,,,,,tji dadi sosai,sai dai bata nuna masa ba illa cewa da tayi to yaya sa'eed Allah ya maida kai lpy,,,, Ameen,..... Amma ki sani tare zani koma dake, sbd me yaya sa'eed.....no be yaya ki kirani da lovely,....ni bazn iya ba gsy na riga da na saba da yaya sa'eed, aiko dole ne ki kirani da abnda nake so,sbd kin kusa ksncwa mallakina, don hk abnda nake so shi zaki yi mn, Hmmm yaya sa'eed kenan,zncen ka da abin dry a ciki,....OK nji zn miki tambaya, tmbyr ita ce, a kwanakin nan umma tayi tafiya ko batayi? tayi tfya mana, to me tace miki zata je yi?siyen kayan auren dan yayr ta, gud kinga kenan zance na bai zama abin dry ba tunda hr kayan aure an siya,to bakai zakiyi aure ba ai,dan uwnka zai yi,nine dai znyi aure kuma kece mtr, inkuwa ba kya so nane sai inji,,,, haba yaya na taba ganin inda za'yi aure amma amryr bata sani ba? Sosai ma kuwa,idan ma ba'a taba ba to za'a fara a kanki,sai dai idan sona ne ba kya yi, yayi mgnr ne a cikin mareraicewa,,,,tabbas nsan ina sonka amma yazma raini idan na yadda ka aure ni ba tare da ka frta kana sona ba,shin ta yaya zn gane sona kake, ko kuwa tausayi ne kawai zai sa ka aure ni. tayi mgnr ne a cikin zcy,,,,shi ko kmr ya fhimci tunanin da take ya fara da cewa,"idan kina tmbyr ko ina sonki? amsar ita ce hr abada.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:30PM, 11/21/2016] Rynt: [2:45PM, 11/12/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>4⃣1⃣Idan kina tnbyr ko ina buqatr ki amsar itace qwarai kuwa,idan kuma kina tmbyr abinda nafi girmamawa amsar itace ke👉💃.</p><p> Ina sonki symh wldh,ina sonki sosai kuma so na haqiqa,wnda bana ftr mu rabu hr abada,,,, ta nisa kafin take cewa,"idan hr kana haqiqanin sona kamar yadda ka fadr min, to don Allah kayi a hnkali da zcyt,zaka iya daukar ta amma kar ka cutar da ita,in ba haka ba duniyata zata tarwatse.,,,,my lady kar ki damu inshaAllah bazn cutr da ke ba,kuma zan ci gaba da sonki a lokutta da baza su qirgu ba,a rayuwa bayan rayuwa,a shekara bayan shekaru har abada. </p><p> My lady inaji a jikna Allah ya halitta min kene wa ni kadai, kuma ya zaboki a cikin zababbu, sbd ina tsananin sonki,ina ftr kema zaki soni?......,,,,shiru tayi ba amsa,,,my lady inaso nji amsa daga bkinki,amma ta ksnce mai dadin ji ce,,,yaya sa'eed akwai watanni 12 a shekara,akwai kwanaki 30 a wata,n 24 hours in a day,60 minute in an hour........ But ni ina sonka hr tsawon rywt, kuma inshaAllah bazakayi nadamar ksncewa tare da niba,,,,nima hk my lady,,,,I luv u my lady💋,,, luv u too my lovely,sanan suka ajiye waya suna masu frnciki da jin kalamn juna.</p><p>Nima billy giro nace muna sonku💋 makaranta littafanmu😊</p><p><br /></p><p>Tsaye take a gabn madubi sai kallon kanta take yanda tayi matuqar kyau,wani farin ciki ne ya ziyarci zcyr ta da ta tuna yau zata ga lovely dinta,ta qara kallon kanta a madubi tana murmushi, tana kuma mai jin dadi irin wanda ta dade bata ji ba,tana kuma tuna rbnta da kwalliya irin hk tun bacewr Abbanta,Wanda hr yanzu bata ydda ya mutu ba,sbd tana ji a jknta cewa yana raye, duk da cewa taji hjy bintu ta furta,cewa ta kashe shi,amma hkn bai sa ta karaya da tunanin yana raye ba.</p><p><br /></p><p>🌹4⃣2⃣🌹</p><p>Umma ce a falo gurin firij ta bude kenan da niyr saka fruit salad a ciki,...sai taji sallamar sa'eed,ta amsa sallamar ne tare da saka fruit sld din a ciki,tana mai ce masa"sannu fa kasha hny,,yauwa umma na same Ku lpy? lpy lau,sunyi kusan 5 mnt suna firar yaushe gamo sama sama,,,, domin shi mgn kawai yake amma hklnsa na gun symh wldh sai kallon dakinta yake ko zata fito,,,,umma ta lura da hkn hr tana qoqarin yi masa mgn sai ya riga ta da cewa"umma bri nje gun symh na ganta,Ok to yayi,binsa tayi da kallo lkcn da ya tashi,murmushi tayi tana mai cewa, "lallai sa'eed na sn symh wldh da yawa,ubngji Allah ka tabbatar da alhairi.</p><p><br /></p><p> Ko da yashiga ya same ta agbn mirror tana qoqarin daurin dankwali, ya fara da cewa "No my lady bana son dankwali abr gashin hk yanda ya zubo a baya yayi min kyau,yayi mgnr ne tare da rungumeta ta baya, ya maida gashin a dyn bangaren kafadr ta, ya hade gefen fuskokin su,suna masu kallon juna ta jikn mirror,yana mai cewa,I hv rly miss u my lady, me too my lovely nayi missing dinka sosai wlh, tayi mgnr ne tare da jaye jknt daga nsa,,,,me kike nufi my lady?No ksn fa baikamata muyi hk ba,....waya gaya miki da fa sadakina a kanki,inace jiya byn mun gama waya, umma ta kiraki tayi miki mgn akn aurenmu kuma sai da kika yadda sannan aka bada sadaki,,,,hk ne amma duk da hk kabari hr a daura ko ma mene ne sai kayi,,,Allah? Eh mana,gashi kama kawo auren kusa,,,jawota yayi ya rungume yana mai cewa, wlh baki ji yanda nake sonki a raina ba ne, shiyasa kikaga na matsa ayi auren nan domin ji nake kmr wani zai kwace min ke,....inshaAllah lovely ba wanda zai qwace maka ni,domin ni takace kai kadai,kuma nima da kai kadai nake ftr ksncw har abada......sai dai baqnciki na daya ne su umma basa raye za'yi aurena..... Hba my lady inace umma ta maye miki grinbnsu ai ko?,shiru tayi bata ce komai ba, a nan ya fhimci kuka take domin yji alamr hkn, zaunawa yayi tare da ita a samn gado,,,,,,No my Lady ba kuka zakiyi ba, addu'a ya kamata kiyi musu, pls stop weeping kinji,,,, daga knta tayi alamr taji, sai kuma ta sake fsa wani kukn tmkr ynzu abin ya faru.,,,, qara rngumeta yayi yana mai bata hkri.</p><p><br /></p><p>🌹4⃣3⃣🌹My lady pls ki daina kukan nan sbd ba qaramin sosa min rai yake ba wlh, don Allah ki daina kinji my lady,,,,dagowa tayi tare da riqo hannayensa ta hade su da nata, ta fara da cewa "yaya sa'eed don Allah ina so kayimin alqawarin baza ka rabu dani ba duk wuya duk rintsi,kuma baza ka wulaqanta niba,domin yanzu ksn idn akayi auren nan,kaine zn fusknta a matsayin kowa nawa,,,symh wldh ni sa'eed nayi miki alqwarin kasncewa da ke duk wuya duk rintsi,kuma inshaAllah bzn taba koda tunanin walaqanta ki ba,,,,hannusa yasa yana mai share mata hawaye, tare da cewa,"duk kin bata min kwalliyr da kika min😔,,,,uhm sry.....no ni bzn hkra ba,sai dai idan cin hnci zaki bani,😉 name fa?bari ki gani, jawota yayi yana qoqarin kai mata kiss a kumatu sai suka ji an banki qofar dakin da karfi,,,rqy suka gani a tsaye,,, sa'eed ne ya fara mgn,,,,yana mai cewa"u are very stupid rqy! ta yaya zaki shigo muna daki ba sallama,,,,,am sry pls dama umma ce ke son ganin ka,,,tashi yayi yace ina zuwa my lady,,, cike da mamaki rqy ta kalle shi sai dai bata ce komai ba hr sai da ya fita........hmmm lallai ma yrnyr nan so kike ki lalata muna yaya ko, wato ya koma irinki kenan, tunda kinga yana shiri da ke hr ma yana zo miki fra,ynzu abin ma hr ya kaiga idan ya dawo da tfy ba lallai bane ya tmbye mu, amma ke hr da zuwa dakinki yake,abin da mamaki wlh yayanmu ba mai ywn srtu bane, amma yanzu akanki ya dawo mai srtu aknki ya fara kula mace amma sam ba hlns bane wlh,to bri kiji in gaya miki, ki kama kanki a game da yayanmu,ta buga wani ubn tsaki tare da cewa, "d snatcher brother kawai,symh wldh dake zaune kallon ta kawai tayi hr ta fita bata ce mata komai ba.</p><p><br /></p><p> 🌹4⃣4⃣🌹Bayan kwana biyu da frwr hka su umma,ihsan da rqy ne a falo suna kallon kayan lefen da aka kawo sai yaba wa suke,ihsan ke cewa "Allah umma kynnan sun dace da mai su, gsky yaya sa'eed ya kashi kudi sosai, hr dai yanda ya zuba gwalagwalai sai kace ba kudi aka sa aka siyaba,rqy da ke tsaye, tana qoqarin zuba juice a glass cup,,,take cewa, shin wai umma wace ce yaya zai aura? naso ganin ta domin nsn iya hdw ta hadu,,,,wace ce kuwa banda symh wldh,,, qarar fashewan cup suka ji, suka juyo domin ganin me ke frw,rqy suka gani cikin rudu da mamaki,,,, umma ke cewa meye hk rqy?umma😳symh wldh fa kika ce,..... umma ya akayi kika yadda zai aureta byn kinji lbrn ta, kuma kinsan ko wace ce hjy bintu a gurin mu,,,.... bri kij rqy koda bai ce yana sonta ba nyi niyr hada auren, sai gashi shi da kansa yace yana sonta, kuma nyi frn ciki sosai da hkn domin symh wldh yrnya ce mai hnkali da natsuwa,.....😭haba umma, wato shine kikace kar mu gayama yaya ainihin lbrn ta, domin wlh da yasani ba zata zauna a gdn nan ba,balle hr yakai ga cewa zai aureta, sbd kinsan yaya ya tsani koda mai sunan hjy bintu ne, balle makusncinta,umma pls don Allah ki jnye batun auren nan, domin idan ta shigo zuri'ar mu zamu sake shiga wani tashin hnkli ne kmr yadda mukayi a baya,umma meyasa kike so ki rasa danki nan kusa? kinfa san yadda ake bibiyr ynyr nan, kuma kinsan hlin hjy bintu duk tayi niyr yin abu to sai tayi shi ba makawa,...dakata rqy, bamu fa da tabbacin cewa, ita ce hjy bintu dinda kike tunani,.... InshaAllah ita ce,kuma ni gsky umma zanje ne in gayama yaya,nsn wlh idan yaji ba zai aure ta ba,......symh wldh dake labe tsaye,bata sn lokacinda tayi mtwn zaune ba.</p><p>Tana mai cewa "na shiga uku idan yaya sa'eed ya fasa aurena yaya znyi domin wlh ina sonsa sosai,,,,,nikuwa me hjy bintu ta musu wanda hatta na kusa da ita baya so,wayyo Allah hjy bintu kin cuceni, kin rabni da iyayena,ynz kuma wnda nake tunanin samun frn ciki a gareshi,za'a rabani da shi a dalilin ki😭😭😭,,, why rwt ta zamo hk ni symh wldh,,why!, tashi tayi ta koma smn gado tana tsananin kuka,hr bacci ya dauke ta,a cikin baccin ne taji sa'eed na kwala mata kira da alama rqy ta gaya masa komai,,,,da shigowr shi ya jawota da karfi,yana cewa "ashe dama ke kina da alaqa da hjy bintu,😡 to wlh kisani ni bzn aure kiba!, kuma baza mu cigaba da zama dake ba,ynz zaki bar mana gida ko kin shirya ko baki shirya ba,,......qiiii ya jata kmr ba 'yar mutum ba, tana kuka tana rqnsa akn yayi hkr hr da safe,,....Allah ya kiyaye ki qara kwanar muna a gda,,,,ci gaba yayi da janta hr wjen gdn,gashi daga ita sai rigr bacçi iya guiwa,ga tsananin duhu,,,ya ingiza ta hr sai da ta fadi,yana kuma mai cewa," ko a mafarki kar ki kuskura ki qara tunanin dawowa nan gdn,,,,, ya juya zai tafi kenan, take cewa a cikin kuka,"yaya sa'eed kar fa ka manta kayi min alqawari baza ka barni ba duk wuya duk rintsi,.....banda wannan rintsi symh wldh!banda wannan!,,,,yana gama fadar hk ya juya ya tafi, ya bar ta gun, tana kuka sosai.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:30PM, 11/21/2016] Rynt: [8:07PM, 11/21/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p><br /></p><p>4⃣6⃣Duk da yace hkn sai da yaji jkinsa ya mutu, hr yaji ba zai iya fita ba, sai tuna ne2 yake akn zncen rqy,sai dai baya jin zai iya ryw ba symh wldh balle hr yayi tunanin rbw da ita.</p><p><br /></p><p>Kwance take tana tunanin yau tun da safe rbnta da taga lovely, tana cikin hk ne umma ta shigo tana tmbyr ta,,,,,,shin symh wldh sa'eed ya ci abinci kuwa? Azumi yayi kuma dana kirasa na tmbyesa abinda za'a masa, sai cemin yayi"baya son komai yau",,,,, prblm din sa'eed kenan idan yana busy baya son cin komai, iya karsa ruwn Lipton,,, amma ace hr da azumin da yayi ba zai ci komai ba,bri nakirasa nji,,,ba jimawa sai gashi ya shigo,,, kallo daya tayi masa ta gane yana cikin dmw,,,me yake dmn Kane sa'eed? Ba komai kawai dai gjy ce da yunwa,,,anya kuwa sa'eed? da alama akwai dai dmw atare da kai,,.....No umma kinsn fa ango ne dole abubuwa suyi masa yawa,ihsan ce tayi mgnr tana saukowa kan bene,,,,Ita dai symh wldh dake tsaye,bata ce komai ba, amma tabbas tsn akwai dmw a tattare dashi,juywa tayi domin komawa dakinta, sai sa'eed ya tsaidata yana mai cewa,,"my lady pls kawo min abinci naci,,,hnyr kici ta nufa ta dauko masa abincin,tare da ruwa da lemu,,,....my lady bana shan lemu yau myr dashi,kallonsa tayi cike da mamaki, wanda baya iya cin abinci sai da lemu amma yau yace baya ra'ayinsa tabbas da akwai dmw a tare da shi,,,lovely wai me yake dmn ka ne?dan gntn murmshi yayi kafin yake cewa, ba komai my lady,,,,,,,,shiru tyi bata sake ce masa komai ba, tunda ta fhmci baya sn fadin abinda ke dmnsa.</p><p><br /></p><p>4⃣7⃣</p><p>🎈🌹🎈🌹🎈🌹🎈🌹🎈🌹</p><p>🌹🎈🌹🎈🌹🎈🌹🎈🌹🎈</p><p>Yau ne za'a daura aure,anyi mtuqar yin taro sai kace daurin auren dan wani govna,mtane maqil abin gawanin ban sha'awa.</p><p><br /></p><p>Sa'eed ne a daki sai faman sauri yake, domin lkcn daurin auren ya kusa bai shirya ba,,, yana dauko tufafin sa sai kawai yaga pic ya fado, dauko pic din yayi, yana mai dubwa, sai kawai naga yaja baya da qarfi, yana salati hwye na zuba a idonunsa,da kyr ya iya furta my...la...dy acikn tsanani firgici,zama yayi bisa gado dmn tsaywr ta gagare shi,sai kallon photn yake yana cewa "No my lady meyasa kika ksnce haka,,,, why my lady😭........knocking yaji ana masa da sauri ya share hwyensa tare da boye pic din sanan ya bada izinin shigowa,,,Slmn ne ya shigo yana mai cewa,,"sa'eed ina ganin daurin aure kawai za'ayi dani baxn samu dmr tsayi bukuwn da za'ayi anjima ba, meyasa slmn? znje oman ne domin ynz aka kirani cewa mtr da nakai,ta farfado sai dai bata iya mgn,shine ake son dynmu yaje......basu kira ka bane?tabbas ankira ni amma bn samu dmr rsvng ba,wai sa'eed lfyn ka kuwa duk kawani fada sai kace ba ango ba,,murmushi kawai yayi bai ce masa komai ba, domin ganin yake wannan matsalr tasa ce shi kadai ba zai iya fallasa sirinsa dana symh wldh ga wani ba.</p><p><br /></p><p>Bayan an daura aure ne, akayi wlma.</p><p><br /></p><p>za'ayi wnkin amarya, 4pm to 6pm,sannan 8pm to 10pm ayi Indian night,domin masu zuwa sai Ku suburbuda kuje dmn kar abrku baya, nidai ba za'a barni a baya ba😜</p><p> A gurin ko wane biki duk inda kaga symh wldh sa'eed na maqale da ita kmr ba abnda ke dmnsa sai nuna frn ciknsa yake sosai,,kuma sunyi bala'in yin kyau duk Wanda ya gansu yasn sun dace da juna,hr dai da aka zo gun Indian night, wnda bai sn su ba zai zaci indiyawan gske ne, hr dai symh wldh yanda tasa sarin yayi mata kyau sosai,shiyasa sa'eed ya matsu a qare domin ya lura wsau mzn sai kallonta suke.</p><p><br /></p><p> 🌹4⃣8⃣🌹Symh wldh ce cikin sbn shiri,tayi kyau sosai sai zuba qamshi take, tana durqushe agbn umma tana mata nasifa akan tabi mijnta sau da qafa,kuma shi zama na aure dole sai da hkr, kuma ki knsnce mai rufawa junan Ku asiri,domin ba komai ne zkyi da mjnki ba kizo kina fada sbd ba kyau,kuma koda kun samu sabani a tsakaninku kar ki kuskura kice zaki fada, Ku tsaya can tsakaninku, ku sa santa,sai dai idan abin ya gagare ki matuqa,sanan ne zaki iya zowa ki fadamin,,....hk dai tayi2 mata nasifa hr symh wldh takai ga yin kuka ba qaqqautwa,domin ji take kamr ace ummanta ce kemata nasifa,,, sa'eed ne ya shigo yana mai cewa,umma kukan me take hk?ai ksn su amare hk suke........... comn my lady, ki daina kuka mana,,,oya tashi mu tafi,,ganin bata da nyr tashi ne yasa ya tashe ta da kansa suka tafi,hr cikin mota kukan takeyi sosai, sai dai marar sauti, hkn ne yasa ya jawota ya rungume yana lallashinta,,da yake a baya suke sai kuma wasu abokanansa su 2 a gaban mota.</p><p> Hr kowa ya watse bata daina kuka ba,,,sa'eed da ke zaune akusa da ita sai tausayinta yake ji domn yasn kukn bai wuce na iyayenta da bsa raye ba,,,,gyalenta ya fara yayewa tare da dankwali, yana mai cewa "my lady ki daina kukan nan hk ya isa,kuma ki tashi mje muyi arwala,,, tashi tyi suka je sukayi arwala sukayi sallah hade da yin addu'a,,,.kallonta yake cike da tausayi akn hkn har manta cewa yaga wani pic,jawota yayi yana kaimata kiss ta ko'ina,tare da cire mata hjb,yana shafr ta ta ko'ina hr yazo gun cknta yaji ckn ya lafe sosai alamr tana jin yunwa, hkn ysa ya dauko musu gasashyr kaza da drnks yana ci yana bata,hr sai da ya tabbatar da ta qoshi sannan ya dauke ta cak suka koma bisa gado,ganin yana qoqarin cire tufafinsa ne yasa ta</p><p>rufe idanunta cike da jin Kunya,murmushi kawai yayi yaci gaba da aikin da yake yi, sannan ya dawo kanta, tana qoqrin yin mgn ne ya hde bknta da nsa, sunyi 5 mnt a haka,sanan ya fara cire mata tufafi,gaba ki daya ya rasa nastuwr sa ganin surar jknta, anan take yayi yunqurn kai bknsa a dkyr flninta,,wani abu tji kafin yakai bknsa, hkn yasata rungumeshi,sbd Kar yakai bknsa, batasn hkn da tyi ba yama fi riktr dashi, baji ba gani kuwa ya fara aika mata da saqonni sai abnda ya mnta,yana gab da shigarta sai kawai ya tuna da pic dinda ya gani, anan ya fasa abinda yayi niya.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:30PM, 11/21/2016] Rynt: [5:53PM, 11/16/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹 SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>Kuyi hkr masu krtu jiya nyi kuskuren numba,inaso nsa 48 sai nsa 50,amma na gyara yanzu zamu tashi a 49.Sry 4 that pls🙏🏻.</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹4⃣9⃣🌹Jawota yayi ya rungume domin baya son ta fhmci akwai abnda ke dmnsa.</p><p> Da asuba suka tashi sukayi sallah sannan suka koma bacci, basu suka tashi ba sai qarfe10am,ko shi symh wldh ta fara tashi,sannu a hnkli take jaye jknta daga nasa dmn bata so ya tashi, pillow ta dauko da nyr ta ajye masa a kusa dashi,,,,,,sai kawai tji ya riqo hannunta yana mai cewa"my lady ni kuma zkyi ma wayo, ki azmn pillow sai kace qarmn yaro,,.bhk bane lovely bana so ka tashi ne,,, hmmm to aini duk motsin da kikayi ina sane, domin ya zama wjibi a gareni na kula da duk wani motsinki, uhm to nji na kuma gde da klwr ka😊,,, bari naje nayi wanka,,,mudai je muyi wnka not only u,No ni a gsky lovely bzn iya yin wnka da kai ba kunya nakeji,amma kuma kikayi.....sai kawai ya fasa abinda yayi niyr fadi,,,,me nayi lovely?Ba komai my lady jeki kawai kiyi😔,a'a gsky muje muyi tunda kafi so muyi tare,,, a'a jeki kawai,cikin yanayi na bacin rai yayi mgnr,,pls lovely yi hqr tashi muje,,oh no my lady!nace miki ki tafi kawai bana yi,kallonsa kawai tyi sannan ta wuce zuwa toilet, shima kuma ya tafi nasa daki domin yin wanka. </p><p> Zaune take tana shafin mai,sa'eed ya shigo yana mai cewa "my lady umma ta aiko da abinci,idn kin gama injrnki a dining table.ya fita batare da yaji me zata ce ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🌹5⃣0⃣🌹zaune yake yana jrnta, sai gata ta fito cikin wani mayen less sky blue n pink tayi kyau sosai, sai dai ya lura da yanayin ta kamr tana cikin fushi,,,tana isowa wani kamshin turare mai dadin gske ya bugi hanncinsa, zama tayi akan kujera suna fskantr juna, sai dai bata yadda ta hada ido dashi ba,,,my lady zonan ki zauna,yace hkn ne tare da nuna cinyrsa,ba musa taje ta zauna akai,,,,,kallonta yayi yana mai cewa pls my lady am so sry, indai wnkane daga yau zamu riqa yi tare kinji,bzn qara cewa banayi ba,,,ni bama shi ba kmn tsawa kakuma yi fushi dani😒,ok to kiyi Hkr kinji,,,,,nima kayi hkr bzn sake yi maka musu ba,domin da banyi maka musu ba, da hkn ma bai faru ba,Ok let eat,,, ksn nifa sai nasha tea ko znci wani abu,oya to hada tea din ina jrnki,ta gama hada tea kenan ta kurba bata sn lokacin da ta furzadda shi ba sbd tsanin zafi,,saurin myrda ita yayi a kujerar da ke kusa dashi,tare da duba bknta in bata kone ba,,.Ita ko sai cewa take a cikin shagwaba" wsh lovely zfi sosai,,,oh sry sry my Lady bari na hura miki,,,,da iskn bknsa yake hura mata har ta samu relief,sannan sukayi lkcn cin abinci.</p><p> </p><p>Hjy bintu ce a bed room tana dialing number din hjy</p><p>Larai, ringn daya tayi aka dauka, ta fara da cewa"kedai albishirinki yau nagano inda symh wldh take,da gske kike hjy bintu? da gske kuwa,, tana a Kaduna hr tayi aure,kuma har gdn da aka kaita na sani.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:30PM, 11/21/2016] Rynt: [7:19AM, 11/18/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>5⃣1⃣Ke kuwa a ina kika samu lbrnta,, ke dai bari ranr kawai ina zaune ina kallon labarai sai nji ansa sanarwar aurensu,kuma ke abin baqin ciki wani mai kudi ne ta aura,domin nsn ko shi waye,yanzu abinda nake so dake hjy larai,'yar wjenki nake so tayi muna wani aiki,....... wane aiki kenan hjy bintu?wato so nake taje Kaduna duk yadda zata yi taje kidn symh wldh ta samo nmbr ta, in yaso sauran aiki ya rage nawa,,,,sai dai kash hjy bintu na aiki Sarah a dubai jiya jyn nan sai dai idan ta dawo,,,to yaushe ne zata dawo domin shi wanda ya auri symh wldh ba'a kasar nan yake aiki ba, kuma a kowane lokaci zasu iya tpy kinga plan dina zai watse kenan,,kar ki damu hjy bintu inshaAllah baza ta dade sosai ba,, to yayi sai ta dawo kenan, duk abinda ake ciki sai ki sanr dani.</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>A bangaren su sa'eed kuwa hk suka ci gaba da rywr su,cike da soyayya sai dai sa'eed bai yadda ya ksnceta taba iya karsa rmnce hr symh wldh ta saba da hkn, kuma a tunanin ta tausaya mata yake yi,,,,,,sai dai kuma shi sa'eed abn yana dmnsa sosai, yana kuma tunanin yadda za'ayi ya tunkari symh wldh da wannan zncen pic din,dmn baya son bcin ranta ya fiso ya br abin a ransa,sai dai fatansa Allah ysa auren nan da sukayi ysa ta daina abin da takeyi.</p><p><br /></p><p> 🌹5⃣2⃣🌹Symh wldh ce a daki tana ta bincike da alama akwai abinda take nema,.....me kike nema ne hk?kai tsaye taji tmbyr hr sai da ta dan razana,kafin take cewa "haba lovely ni hr ka bani tsoro wallahi,"OK sry my lady me kike nema ne haka? Ina nemn pad ne kuma na ganta,,,ammm pls lovely ka dan fita inaso inje toilet,...... da yake ba kaya ajiknta shine tke jin nauyin miqewa, wani kallon kinma rainani ya mata kafin yake cewa "a matsayina na mjnki zki ce na fita, wane dare ne jemage bai gani ba? uhm lovely duk fa ganin da kake min ba hske sosai kuma idn muna wanka tare, da pant nake yi, to waima me yasa kika fito hk ba towel?ina sauri ne shiyasa.... pls lovely ka fita.....😀Allah ba inda znje gara ma ki tafi,, lovely pls....my lady Allah da gske nake,,shaye da toka ta wuce shiko sai kallonta yake cike da sha'awa,,,amma kuma sai naga ransa ya baci, yana mai cewa a cikin ransa"my lady kenan to a tunain ki ban san komai bane kinzo kina nuna min knyr qarya, byn kinje kina nuna tsiraicinki ga wani,,Allah ka shirya min my lady,hawaye ne suka zubo masa sannan ya ci gaba da cewa,ina sonki my Lady ina sonki sosai amma why kika zamo min hk hr kika sa na kasa ksntrki,gashi a kullum sha'awrki nake qara ji.</p><p> Koda ta fito daga wanka ta sameshi kwance a smn gado yana dubin silin sai dai idanuwnsa a rufe suke, kwantawa tayi samn jiknsa tare da kai masa kiss a kumatu hade da shafo sajensa,,ya bude idanunsa da sukayi jwr yana mai cewa "my lady hr kinfto"?eh na fito.....amma yana nga launin idonka ya cnza zuwa ja, me yake damnka? Ko kana jin bcci ne?kallon qirjinta yake cike da sha'awa dmin yanda ta daura towel din rabin nononta a waje yake, kafin yake cewa"No my lady ina dai buqatr ki ne,haba lovely baka tashi buqata ta ba sai byn bani da tsarki,my Lady ganinki da nayi ba kaya shi ya jmn hkn,😀da kyau ai sai da nce ka fita kaqi,....kinga bafa zncn wasa bane a buqace nake wallahi,to ya kake so nyi lovely ksn fa hrmn ne ka kusnce ni a hk.....OK na tuna akwai yanda znyi maka hr kayi releasing ba tare da ka ksnce niba.</p><p>Nidai Billy giro fita nyi na bsu guri sbd bn kai wannan matsayin ba,,bani na koma ba har sai da na tabbatar sun gama sannan na dawo.</p><p> Na same ta hr ta shirya,sa'eed kuwa ya fito daga wanka yana cikin tsane rwn jiknsa da dan qrmn towel,yake cewa "my lady kmr inajin bell ringer jeki duba ko waye,koda taje ta bude ta ga wata mta ce da hjibnta hr qasa da kuma niqaf,tayi mata iso, ta nuna mata guri ta zauna tare da kawo mata drinks hade da abin motsa baki,kafin suke gaisawa,Baquwr ta fara da cewa "sunana Sarah yayanki abdallah ya aikoni gurinki"......yaya abdallah????😳😊😀.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:30PM, 11/21/2016] Rynt: [8:01PM, 11/26/2015] Billy giro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹6⃣4⃣🌹Dakinta yaje yin wnka yana a cikin wnka ne ya lura da ashe tean ya qona shi dmn hr wrin yayi ja sosai,byn ya fito ne ya koma gurnsu yana mai cewa"ni umma znje masallaci sallar magrib amma sai byn isha'i zn dawo",,,to yayi ba matsala idn ka dawo sai ka maida ni gida dai2 nima nagama sallar,,,,,,koda ya dwo ya samu umma tagama sallah,smyh wldh na bacci,, umma ke cewa "idn ka dawo ka tashe ta tayi sallah dmn magrib kawai tayi"</p><p> Koda ya dawo yaga hr ta tashi tana sallah sai dai a zaune take yin sallar,,duk sai ya qara jin bai kyauta ba,,,ba ita ta tashi daga kn sallaya ba sai qarfe tara,,,jan qafa take sannu a hnkli da nyr brn dakin,,,,"my lady ina zki tafi?,,,shiru ta masa tci gaba da jn qafrta....jin kawai tayi ya dauketa ya myr bisa gado, yana mai cewa "pls my lady kiyi hqr da abnda na miki, bawai ban yadda dake bane kinsan daga sama muka hadu bxn iya gane zk iya aikata hkn ko bxki iya ba,kuma koda ace kece kika ga hkn akaina ba kai tsaye zki ce bxn aikata hkn ba dole abn zai rikita ki kafin ki gano gsky......yaya sa'eed nji daga sama muka hadu kuma bamu dade da sanin junanmu sosai ba sbd kwata 2 ko wata uku bnyi a gdnku ba hr yin aure,,amma ya kamata kmn uzuri ko don rantse2n da namaka yafi a qirga amatsayina na musulma,kuma inaso ka tuna cewa zamana dakai ban taba yimaka rantsuwa irin hk ba sbd ba kyau yawn yinta ba kuma abr wasa bace, amma ka manta hkn kaci mtnci na ka kuma yi sex dani kmr wata dabba,sbd bani da gata ko😭kana ganin kmr daku kadai na dogara shine kake nemn illata ni,shin ko ka manta cewa akwai Allah kuma shine gatan kowa.....saurin rufe bkinta yayi😷da hannunsa dn ganin yayi kmr ma tayi sabo kfin yake cewa "my lady yazaki ce na manta Allah......</p><p><br /></p><p> 🌹6⃣5⃣🌹Eh haka znce mana tunda ba irin rqnka da bnyi ba akn kayi hqr kaqi,it's very shameful a matsayin ka na doctor kana qoqrin yimn illah,, my lady inaso ki gane cewa koda abin ya faru bana a cikn hayyacina,,,kmry ya?I mean haka nake idn na hrzqa bana jin kowa.....ashe kuwa idn naci gaba da rywa dakai nan gaba kashe ni kawai zkayi.....😳ya za'ayi na kasheki anya Kuwa kinsan abnda kike fada?....wlh bzn iya kasheki ba my lady, kwata2 ni ko kiyashi bxn iya kashewa ba.....sai dai ina rqnki da ki taya ni da addu'a ko xn rage zfn zcy sbd abn yana damuna sosai,ni kaina banson kaina da hkn. </p><p> Kwanciyr ta kawai tayi tare da juya masa baya,bata sake ce masa komai ba shima hk.</p><p> Byn kwana biyu da frwr hkn, kwance yake kn 3 seater duk abn dnya ya dameshi sbd rashin jituwr sa da symh wldh abn sai gaba yake dmn ynz ko yayi mata mgn bata kulashi, yana ckn haka ne sai kawai yaji qamshin turarenta zata wuce ta gbnsa,saurin riqo hannunta yayi yana mai cewa "pls symh don Allah yau ki tsaya ki saurareni"....qoqrn fizgr hannuta take,, sa'eed yace "haba my lady kefa musilma ce kuma ansn muslmi da hqr da kuma yfya"......fari da ido tayi, tace"ayya hk nefa to amma kai ya akayi kmnta hkn a lokacinda nake rqnka"Babu abinda yafi mn zfi kmr yadda na daddage ina maka rantsuwa amma ka qrytani ka kuma ksnceni kmr wata dabba da kuma qarfin tsiya wanda ba don Allah ya taimake ni ba da nyi rashin qafafu,gashi ma hr ynz bana iya tfya da kyau,,,,sai nji kmr ma ace alokcn da akayi yinqrn ymn fyade da na brsu sunyi, in sn cewa su basu sanni ba kuma mgye ne su, amma😭kai fa!ka sanni! kuma ni mtr ka ce! kuma wai anawa tunanin kaine mtmn da zn samu frnciki,kulawa,tausayi,soyayya mai dorewa ,Ashe ba hk bane dama ashe rashin ksnta ta da bakyi ba ba tausayi bane zargi ne,wai hr da krmn jarababbiya,'Yar iska, sannan kayi tunanin abn zai wuce a gurina anan take.....kae na tabbata da ace baka same ni a virgin ba, zaka yadda cewa ina alaqa da wannan mtmn koda kuwa ace banayi,wa fyade kadai na rasa budurci na ban qara kula wani ba,bxaka yadda ba tunda kai anaka tunani smna a virgin shine gskyr komai,,my lady pls am so sry n i know i made a big mistake,but i wnt u to forgive me pls n pls,,,yaya sa'eed tuni na yafe maka but bzn iya cigiba da ryw dakai kmr yaddai na saba a baya ba,dmn bana so na sake jin bqin ciki makamncin wannan......ni a gsky bxn iya ryw dake a haka ba......fine n gud sai ka sauwaqe min dmn ni a hk nake iya rywa dakai,,,saki fa kika ce my lady kin kuwa sn irin sonda nake miki? I don't know n I am not d parson u should ask,......all what i know is i love u but dole na nuna maka kuskurenka, ta fadi hkn ne a cikin zcyr ta byn ta bashi amsa.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: . [5:50PM, 11/20/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹 SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na BIlky giro😊08140674366</p><p>🌹5⃣3⃣🌹Huh wayyo Allah dadi!Sarah inajinki gaya mn,,,da farko dai ni course mate dissa ce,akwanakin baya yazo Nigeria ya samu lbrin abinda ya faru dake,shine ya shiga nemn ki ako'ina amma baisamu nasar ganinki ba, hk ya koma egypt ba a ckin jin dadi ba,to da yaji zn zo Nigeria shine ya bani photon ki da kuma maqudn kudi yace don Allah inqara sa abincika masa ke hr a gdn TV,ranar kwatsam ina zaune ina kallon labarai sai kawai aka sako sanarwar aurenku aka kuma saka pic dinku,to anan naga tabbas kece wacce abdallh ke nema,shine nazo domin in tabbatar ko kece, in kuma baki nmbrsa,,kae😊 amma wallahi nji dadi na kuma gde,😀wayyo yaya abdallah ashe yana nan yana nemana,,, to ga numbr shi ko,,to Sarah na gode sosai😊amma bari naje na kira mijna Ku gaisa,,,,,saurin dago kanta tayi tana mai cewa ackn zcy"wato ashe mijnta na nan shine mai gadi yace min baya nan ya zama dole na bar gidan nan ynzu ynz".....kinji sarah,,, uhm ok kiyi sauri fa dmn inaso na tafi.</p><p> Da gudu symh wldh taje ta sami sa'eed cikin tsananin murna tana mai cewa,"wooohoohooo lovely yau nasamu nmbr yaya abdallah,"😃wow my lady a ina kika samu?cewr nan da kayi na dubo ko waye ashe wata Sarah ce tazo.....Sarah!!😳,me ksnta ne?ina tunanin hk, yaya yanayin ta yake?gsky bxn iya ganewa ba sbd hjbnta har qasa kuma asanye da niqaf take,akwai matsala my lady.... muje na ganta amma idan Sarar da nake tunani ce baza mu sameta ba,,, koda kuwa suka je falo basu gnta ba,,,,,, kin gani ko my lady bata nan inshaAllhu itace,ke kuwa a ina kika santa.</p><p><br /></p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p><br /></p><p>🌹5⃣4⃣🌹No lovely ni gsky ban santa ba yau na fara ganin ta....kash my lady hr ki amshi numba amma baki ga fsknta ba,, amma ai kinga hannyenta, fara ce ita?eh fara ce, chabdi wato hjy bintu bata daina bibiyr mu ba kenan, amma sai na nuna mata tayi kuskuren aiko Sarah a gdna, kmrya ya lovely?kuma wacece hjy bintu? my lady akwai wani mumunan abu da ya faru damu a baya,kuma hjy bintu ce sila.</p><p> Wato hjy bintu ta ksnce tana son mhfin mu sosai tun tana budrwa, amma shi mhfnmu baya sonta sbd bata da kirki,babu yadda bata yi ba amma yaqi,gashi ta dade batayi aure ba sbd krtn da tayi mai tsawo,ganin hkne mhfnta yace ta amince da auren Abokin mhfina tunda shi ke sonta, amma taqi amincewa da auren,haka yayi ta matsa mata,sai da qyar ya samu ta yadda akayi aure,hr suka shekara 5 da aure bata taba jin sonsa ba,sai dai kullum qara jin son abbanmu take, hkn ysa ta matsa ma mijnta sai ya sake ta,ala dole ya saketa dmn wanda yake tunanin ysata tyi abu dole baya raye, wato mhfnta, balle hr yayi tunanin yakai qarar ta.</p><p> Byn tyi idda ne ta sake dawowa a gurin abbanmu akan tana so ya taimaka ya aure ta,amma yace shi sam bazai aureta ba, ko dn sonda aminiñsa ke mata, don hk gara ma ta koma ma mjnta,,,to da yake umma tsn da zncen shi ne ta bashi hqr akan ya auri hjy bintu tunda aknsa ne ta ksa zaman aure,Abba ya amince da zncn Umma ya kuma gayama hjy bintu cewr ya amnince,sai ce masa tayi tana da sharadi,...uhm my lady wai kinsan mene ne sharadin?sai ka fada lovely,,wai ce masa tayi sai idn zai saki mtr sa sannan ayi aure sbd ita bazata iya zama da kishiya ba,,,Abba yace sam shi bazai yadda da sharadin ta ba, na mrasa hnkali,ta yaya zai rabu da uwr 'ya'yansa byn suna zaune lfy,,,lallai kuwa idn baka amnce da hkn ba sai na rabaka da frin cikin ka kmr yadda ka rabani da nawa,,,ba abunda Abba yace mata domin ya dauka shirme take.</p><p> Ranar kwatsam muna zaune a falo sai gata ta shigo ita da qawr ta hjy larai da Sarah,ita Sarah 'yace ga yayar hjy larai amma hjy larai ke riqnta, ksn 'yan wari muke da ita,....budan bakin hjy bintu ke da wuya tace "waye yayi miki ciki a cikinsu dan ko uban, sai kawai Sarah ta fashe da kuka tana cewa,"Baban ne",, gaba ki dayn mu bamu san lokacin da muka miqe tsaye ba sbd tsananin mamaki,Abba ne ya fara da cewa Sarah ni kuma nayi miki ciki😳,qrya tayi ne?mtsw inspector azo atapi dashi da Allah,cewr hjy bintu,,,</p><p>Hk aka tafi da Abba muna ji muna gani,Abba hr aka fita dashi sai kallon hjy bintu yake sbd tsananin mamaki dmn shi baiyi tunanin abinda zata masa Kenan ba.</p><p> Har abin yakai kotu dmn sunyi duk yadda zasuyi Abba ya amsa cewa cikinsa ne shikuma yaqi, inbanda abinsu ta yaya Babban mutum irin Abba Wanda kowa ke ganin mutuncinsa ya amshi laifin da bana shi ba musamman ma irin</p><p> wannan😭......ya qarasa mgnr ne a cikin kuka yana mai cewa</p><p><br /></p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p><br /></p><p>🌹5⃣5⃣🌹"My lady kigaya mn ta yaya".......😭No lovely pls stop crying,...dole ne nyi kuka my lady dole ne!domin ancuce mu dawa duk wanda muke tunanin zai tamaika muna a gurin fitr da mhfinmu a zrgn da ake masa, sun koma abayn hjy bintu sbd kudi da kuma rashin tsoron Allah,gashi mu a wannan lokaci ba wasu kudi ne damu ba,my lady in taqaice miki hatta mqwaptanmu da suka san cewa abbanmu mutumen kirki ne bazai Iya aikata hkn ba amma da aka je kotu cewa skyi shiyayi,bayn sun san bashi bane,😭my lady kinsan me?sai ka fada lovely😭,wai fa hatta aminin mhfina wato tsohon mjin hjy bintu da aka kirasa akotu cewa yayi abban mu ne yayi ma Sarah ciki,,ai kuwa anan kawai abbah ya fadi jini na zuba ta hnci da baki,koda akaje asibiti,zcyr sa ce ta buga,kuma ya rasu.,,,tun daga wannan lokci my lady nji na tsani duk wani makusancin hjy bintu,hkn yasa muka baro garin abuja,muka dawo kaduna da zama.</p><p><br /></p><p> Hk nake zama wani lokci,nayi tunani wai kudi!kudi!kudi! wai duk don rashin kudi ne yja mana hka,domin na tabbata ba'a banza hjy bintu ta brsu ba dole da kudi,tun daga wannan lokaci nayi qudrin sai nanyi kudi amma ta hnyr alkairi,hkn yasa na qara dagewa akrtuna domin na samu ilimi na kuma duqufa da addu'a ba dare ba rana cikin ikon Allah yanzu nyi kudi,kuma inshaAllah sai na daukaka qara.</p><p><br /></p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p><br /></p><p> 🌹5⃣6⃣🌹Ni kuwa lovely abinda yafi daure min kai da lbrnka, shine shin shima aminin abbanku baya da kudi ne da hr hjy bintu ta saye shi, kuma ita ya akayi ta ksnce mai kudi haka?gadon mhfinta ne sbd shi mutum ne mai trn dukiya kafin ya rasu,</p><p> Aminin abbanmu kuma yana da kudi sosai,Sannan ko don son Abbanmu da take taqi shi zai sa yaji ya tsani Abba,,,,to lovely..... Oh my lady a daina mgnr bana son tuna baya dmn ji nake ina ma ace nine hjy bintu tayi ma wannan sharri ba Abbana ba.</p><p> My lady ni abinda nake so ynz shine,ita Sarah din daga wane gari tace miki take, bata fada min gari ba abnda tace min kawai shine Ita course mate din yaya abdallah ce,ok Allah yasa ba wacce nake tunani bace Ameen lovely,,,but my lady kira abdallah muji idn shi ne,OK lovely,,,ringin take kmr ba za'a daga ba, sai kawai tji an daga kuma mryr abdallah ce, wani tsalle ta daka sannan take cewa "yaya abdallah!!Na'am symna ya kike?.....yaya I'm really miss u alot😢,wlh nima nyi missing dinku sosai, wai amma koda nadwo na samu bqin lbrn da hr na mutu bzn manta ba,....ya qarasa mgnr ne a cikin kuka,sanan yci gaba da cewa sai dai inaso inji yadda ki ka kubuta daga hanunta.</p><p>sai da ta koma daki sannan ta bshi lbrn yadda komai ya faru hr zuwa ynzu ,tana mai zubr da qwallah,,,shima hk sannan yake cewa "kukan ya isa hk siymh mu gode Allah da ya kubutr dake lpy,"kuma ki kwantr da hnkli idn na dawo zn qwatomuna haqqin mu a gurin hjy bintu kuma inshaAllah sai tayi babbar nadamr aikata hkn a gare mu,kar ki damu kinji,to yaya yaushe zaka dawo?ba jimawa inshaAllah kuma ai zaki ji tunda muna waya......nifa yaya wynka baya da tabbas sai ayi ta kira baka dagawa kuma idn kaga missedcalls baka kira😔,...... ba hk bane symh alokcin wayata ta lalace komai bana gani kuma koda na sayi wata bana samnku ko na kira, amma inshaAllah hkn ba zai sake frw ba kinji,to yaya nji.</p><p> sannan suka ajiye waya, dagowan da zata yi kawai sai tyi ido biyu da sa'eed, hr ta dan rzana idn bai ji lbrn da taba yayanta ba,sai tyi saurin bsrwa, ganin alamun sa da tyi kmn bai ji ba.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [8:17PM, 11/24/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊</p><p>6⃣1⃣Da yake qarfin nmji dana mace ba daya bane, nan ta ke ya rabata da kyn jiknta ya kuma daddanneta sannan ya cire nashi tare da kashe wtr dakin.</p><p> Ba ko wani dan rmnce hk yake qoqarin saka babananr sa,tare da yin addu'ar saduwa da iyali,ya zira da frko bata shiga ba na biyu ma hk,Ita kuma sai rqnsa take cikin kuka akn yayi hqr Kar yayi forcing dinta........ Bai bi ta knta ba,sai kawai ya sake sakawa da qrfin tsiya hr saida tayi wata irin qara mai shiga kunne,,,,tundà ya fara moving sai yaji gabaki daya yarasa natsuwr sa sbd tsananin ni'imr da yaji a tare da ita hkn yasa yaci gaba da suburbudr ta, ita kuma akn kukan da tasha hr mryrta ta disashe hkn take rqnsa amma kwatkwata bayajinta, hr sai da yji he is totally satisfied sannan ne yayi lkcn kulata cike da tsananin mrnr ya sameta a virgin, hnklinsa yayi mtqr tashi ganin bata motsi,jijigata yake amma ina,.....tashi yayi dmn debo rw anan yaga irn dnyen aikin da yayi duk yayi mata kaca kaca, gdn duk ya baci da jini gashi bed sheet din fari ne,rwn snyi ya dauko ya yayyafa mata amma bata tashi ba,ya qra zba rwn hr sau byr, amma duk daya, sosai hnkli sa ya tashi ganin duk rwn da yake zbw bata tashi ba, sai yaji gabaki daya ya rikice ya rasa abnda zai mata a matsayin sa na doctor,,umma ce ta fado masa arai da sauri ya saka kynsa tare da daukn pic n key ya fita,bai zrce ko ina ba sai gida,dkin umma yje yana kirnta a rikice sai dai bai gntaba,ihsan ce ta shigo a rude dmn jin kirn da tji yana ma umma,,,"yaya sa'eed lpy?ina umma take? Umma ta fita.....Oh my God..... Yauwa bani ywrki,ta miqa masa wyr ya amsa jiki na rwa,gallery ya shiga yana duba pictures sai dai ntsuwr sa bata tare da shi hkn yasa ya miqa wyr yana cewa "ishan nuna min pic din da kukayi da my lady wnda take daure da towel, bajmw kuwa ta nemo ta nuna masa, ya gnshi exactly dana hnnusa banbnci daya shine, nan grdi can ihsan,, ba wadda ta fado masa arai sai rqy.</p><p><br /></p><p>🌹6⃣2⃣🌹Dakinta ya nufa yana qoqarin shiga yaji tana cewa "woooo ka kyauta wlh domin ynx na tabbatar dole ya saketa tunda yaqi yadda da photon ynz yagani a zhr ai saki dole a ynda nsn yaya da xcy"......jin tayi an damqo gashin kanta tare da buga kanta a bangon dakin, ya dauko wyn caji yana zubata da Ita baji ba gani,kmr wanda Allah ya aiko,,,.ihsan dake tsaye ba shiri ta kira umma ta gaya mata dmn tsn ko hqr ta basa bazaiyi ba inma bai hada hr da ita ba,ita Kuwa rqy kuka take tana bashi hqr akn bazata sake ba sharrin shaidan ne,ji yake kmr ma taqara masa qarfi,duknta yake kmr zai kasheta....... Kae! kae!! kae!!! Sa'eed lpyn ka kuwa so kake ka kashe ta ne.....umma ai gara na kasheta kowa ma yahuta, dmn wannan abnda tayi zuwa gaba fiye dashi zatayi,tun baki je ko ina ba kin fara qoqarin raba aure,........😳subhanallah auren wa take qoqarin rabawa?umma kalli pic din nan ki gani itace tasa aka hada shi dmn na saki smyh wldh, subhanallah rqy ashe baki da hnkli haka bnsani ba!</p><p>wato dana hana ki.....umma ba ma wannan kadai tayi ba.....ya kwashe tun zwnta dakinsa da lkcn da yaga pic da ftr su da symh wldh da kuma fdnshi shi da symh wldh da kuma abnda ya mata, har zuwa smn rqy da yayi tana waya duk ba abnda ya rage,ya qarasa znce cikin kuka yana cewa"ynz umma fisabilillah ta yaya zn kalli symh wldh na bata hqr, da wane ido Zn kalle ta,,,tabbas rqy bata kyauta ba kuma kayi mn dai dai da kamata dukn tsiya kuma wlh zaki hadu da fishina,... Ynz ma ba wannan ba muje inga symh wldh, koda suka je sun sameta a yadda yabarta wato rufe da bed sheet sai fuskrta da ya bari a bude.</p><p><br /></p><p>Sa'eed ne ya fara da cewa umma ina ganin dgwr sumace tayi,zata farfado ba jimawa inshaAllah,,,,to ynz ka tashi kaje kayi mata wnka ka kuma gasa mata jiki da rwn zafi da dettol, daukn ta yayi tare da bed sheet din da yarufe ta dashi ya wuce da ita toilet, umma na ganin jinin da ya zuba tace"ba makawa kajiwa ynyr nan ciwo da yawa wannan wane irin aikin rashin hnkli ne.....yaye znin gadn tayi ta znxa wani.</p><p><br /></p><p> 🌹6⃣3⃣🌹 a bahon wanka ya hada rwn, ya fara sakata sannu a hnkali, bai ida sakata ba sai kawai ta fara motsa babn yatsanta na qafa sannan ta fara motsa idanunta ba tare da ta bude ba,tsaye yayi yana kallonta hr ta fara bude idanwnta sannu a hnkali,tana hada ido dashi tayi saurin kaucewa tana mai zbr da qwalla,cike da tausayi yake kallonta kafin yake ida sakata a ckin bahon, aiko ba shiri ta qanqame shi tana cewa"wayyo Allah! lovely ruwan da zafi sosai! da sauri yacire ta ya rungume,can yaji umma na cewa idn rwn sunyi zafi ka surka kar ka qona ta,umma gsky rwn a yanda yakamata suke...."Nidai lovely gsky karka sake saka ni a ciki😢" my lady hqr zkyi dmn kinji rauni a gun dole sai anmiki gashi, yana gama fadin haka ya sakata sannu2 yanda baza taji zafi kai tsaye ba,wannan krn rirriqeshi kawai tayi hr aka zo gun tsalki, duk da</p><p>taji zafi hkn baisa ta nuna ba, shima ya fhmci dauriya kawai takeyi,,, sosai yji tausayin kmr ma yayi kuka yakeji,,,,byn ya gama yi mata wanka ne yake cewa "my lady yi wankan tsarki ko" a gbn idnsa tayi wnka dmn ya tabbatar da iyawr ta, kuma sosai ya gamsu da wankn.</p><p><br /></p><p>Don hka maza Ku kula da hkn,ba wai hk kawai ake kai muku mata dmn byn buqatr kuba, yana dakyau kuyi ma matyenku tambayoyi akn addinin musulunci kji idn basu da matsala dmn hakki ne ya rataya a wuynku,duk da nsn knsn da hkn ina muku tuni ne.</p><p><br /></p><p>Koda suka fito basu sami umma ba,ya ajiye ta bisa gado tare da shirya ta, sannan ya hada mata tea mai kauri ya bata, kallo daya ta masa ta kauda ido,yayi lallashi hr ya gaji taqi amsa,matsawa yayi kusa da ita tare da Kai cup a bknta,......"ah! cewr sa'eed sbd tsananin zfin da yaji,dmn bugo cup din tayi hr saida tean ya zuba a qirjin sa, kallon ta kawai yayi baice komai ba sai ma gyara wrin yake qoqarin yi, sai ga umma ta shigo dauke da tray na abnci ta kai agbn symh wldh ta aje sannan ta hada mata tea ta bata, ta kuwa karba tanasha,nan sa'eed ya fhimci nashi ne bata so....."to kai kyi wnkn ne?a'a umma,,,, oya maza kaje kayi dmn ba kyau zama da najasa.</p><p><br /></p><p> Mu kula 'yan uwa.</p><p> </p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [3:54PM, 11/21/2015] Billygiro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊</p><p>🌹5⃣7⃣🌹Bayan Sati daya da frwr hkn,kwance take tana bacci wuraren 3:30pm,sa'eed ne ya shigo yana mai cewa"my lady wai kina tufin tun sannan baki tashi ba",,,,,,,ya kaimata kiss yana mai kirn sunan ta a hnkli, wani irin juyi tayi mai daukan hnkli tare da miqa sannan ta fara bude idnunta sanu a hankli hr ta sauke su akan nasa, sai da yji tsikr jknsa ta tashi,,,ba shiri ya rungumeta yana shafr jknta ta ko'ina hr yakai ga ya rabasu da kyn jknsu sannan ya kashe wuta, tana qoqarin mgn ne ya saka bknsa anata yana tsutsa tare da shfr dkyr fulnin ta,can kuma ya koma yana sha bji ba gani sai kace jajirin da yayi kwanaki bai sha nonon mhfyr sa ba,hk ita ma take myr masa da mrtani,jin tayi yana qoqarin saka babananr sa a pp dinta, saurin cafko babananr tyi tana mai cewa "pls lovely kar min hk wlh ina jin tsoron jin zafn da ake fada" No my lady bxn iya hqr ba yau pls ki banni nyi ko xn samu sassaucin abnda nake ji,,, ansar babanr sa yayi a hannunta yana qoqarin saka ta a pp dinta,, sai kawai yji ta fashe mai da kuka hr da su hwye,,, OK my lady ya isa ki daina kuka na fasa,yana gama fdin hk ya sauka kan jknta ya kwanta kn gado yana maida nunfashi,kallonsa tyi taga ynda idanuwnsa sukyi jawr sai kawai tji ya bata tausayi,,,,lovely pls yi hqr kaji nyi ma alqawari anjima zn bar ka kayi,,,saurin tashi zaune yayi yana fadin da gske?Allah kuwa,, thank u my lady😘 to tashi myi wanka ko.</p><p> Byn sun fito daga wnkane take cewa "lovely pls ina so mu dan fita yau ksn tun lkcn da muka je gida ban qara fita ba" a ina kikeso muje ne? wurin shaqtawa,ok bri muyi sallah sannan mu tafi.</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p> 🌹5⃣8⃣🌹Koda ya dawo daga masallaci itama tyi sallah ta kuma shirya kama hnya kawai sukayi,wani wayeyyen wri ne sukaje yra da mnya duk suna zuwa dmn shaqatawa,zmnsu keda wuya hr yana qoqarin tmbyr ta abinda za'a kawo mata sai kawai aka kirasa a waya,koda ya duba slmn ne, sai dai ba'a ji sosai hkn yasa yace mata"my lady ina zuwa pls, dmn ba'aji anan inason in dan qara gaba ko znji" zaune take hr ksn 30mnt amma bai dawo ba, miqewa tyi tana dan yawatawa ko zata ganshi ganin bata ganshi ba, sai tayi tunanin kiransa a waya,hr yayi recvng sai kawai tji anyi hugging dinta ta baya,jin qamshin turaren da tayi ne yasa ta gane sa'eed ne dmn shi kadai takeji da wannan qamshin,,,,"haba lovely meye hk a gbn mutane" tana gama fdr hk sai kawai ta hngo sa'eed tafe, a razane ta juya dmn ganin ko waye</p><p> ya rungumeta, wani ta gani wnda bata taba ganin sa ba, ba shiri ta wanke shi da mari biyu masu kyau tana mai cewa "kae wane irin dabban mutum ne kai! ko kuma kai ba musulmi bane da zaka rungume ni hk kawai kuma a matsayina na mtr aure!,,dai dai nan Sa'eed ya iso sai gyn yake cewa "haba symh wldh me yasa zaki mn hk byn ke kika ce mu hadu anan ko kuma akan wannan garn mijin naki ne zaki........tas!tas! kakeji sa'eed ya wnke shi da mari hudu masu kyau sannan ya ja symh wldh cikin fushi, ita ko sai fadin take "wallahi lovely qarya yake mn bnko taba ganinshi ba"bai tsaya sauraren taba ya jefa ta cikin mota suka tafi,gudu yake kamr wanda zai tashi sama sbd tsananin hasalr da yayi,Allah ne yasa suka isa gd lpy,, janta yayi zuwa dakinsa tare da dauko photo ya jefa mata,koda ta duba sai da ta ja baya da qarfi hr tana qoqarin faduwa, sbd abinda tagani a jkn pic din, itace daga ita sai towel wnda ko dqwa tayi za'a iya hngo ta,gashinta kanta duk ajiqe yake gata rungume da gyen da ya rngumeta a dazu shima towel ne daure a jknsa da alama wnka sukayi,kallonsa tayi tare da girgiza kanta tana batun tayi mgn...... sai kawai ya dakatr da ita yana mai cewa"karki kuskura kice min shima wannana photo qarye ne".</p><p><br /></p><p>Masu krtu kuyi hkr na rashin samn ci gaba hr na 'yan kwanaki,sbd wata lalura data kifta min.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [8:04PM, 11/23/2015] Billygiro😊</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDA🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊</p><p>🌹5⃣9⃣🌹Lovely wlh wannan photon hadi ne kawai😭.....ai dama nsn abinda zaki ce kenan! dmn shi dan iska bazai taba cewa dan iska ne ba, sai idn ganin yayi anka mashi dumu 2,cike da mamaki tare da zbwr hwye😳😭 take cewa "me kake nufi ne lovely" duk abnda kika fmta hk nake nufi!😡...... Symh wldh a da nyi tunanin zama dake duk da nsn cewa qarya kikayiwa umma na cwr ba'ayi miki fyade ba byn anyi,sai nji sonda nake miki bzn iya hqr dake ba, kuma na duba cewa qaddara ce ta sameki ba yin knki bane, sai gashi ranr daurin aurenmu naga wannan pic, na rzana sosai da ganinsa amma hkn baisa na fasa auren ki ba, dmn a tunani na zaki daina idan kikayi aure,.....dafa kafadar ta yayi yana mai ci gaba da cewa,"my Lady meyasa baki daina ba?why my lady?.....ita gaba ki daya ma imani yayi mata yawa hr tarasa abin ce masa,illah hwyen da ke zuba a idanunta tayi tsaye kamr gunki,ganin haka ne yasa sa'eed ya jijjigata cikin kuka yana cewa</p><p>"tmbyr ki nake kibani amsa mana😭,wai ma wace irin jaraba ce dake daga yi miki fyade sai kawai ki zarce....my lady meyasa kika zabi ki cutr da rwt ne kin kuwa san irin sonda nake miki?qarya ne wlh,qary ne baka sona😭 dmn da kana sona da duk baka yrda da wannan baqr qryr da aka shirya ba,wai hr ma kana zrgina😭.....No my lady bana zrginki, sbd akoda yaushe muna tare dake kuma sau daya kika fita koshi a tare dani, kuma hr muka dawo muna tare,sai dai ganin ki dana yi dashi yau ya tabbtr mn kina so ki koma ma gdn jiya, sannan idn hr ba sonki nake ba da bxn aure ki ba, byn nsn qryr da kika yi,sai gashi naga wannan pic din kokuwa a cikin rashin so ne yasa na aureki,.... wlh my lady ba kowane nmji ne zai ga wannan photon ba ya aure ki.</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p> 🌹6⃣0⃣🌹Sannan kuma naganki da wani rungume hr kina masa murmushi, wai sai da kika ganni sannan kika wani juya kina masa fada,,, Lovely, wlh nazaci Kaine sbd qamshin turaren ka nji kuma ai idn ka lura ta baya ya rungumo ni, hkn yasa banga ko waye ba,hr sai da na ganka ne na fhmci ba kai bane,,,,,,OK nji,to me ya taso ki a inda na barki?sbd nga ka dade baka dawo ba, nyi tunanin na dan yawata ko xn ganka, danaga ban ganka ba, sai na kira ka a waya, kuma na tabbata ka gani tunda har kayi rcvng,....uhm shi ko photo fa yaya akayi kuka yi shi ko shima kin zaci nine?</p><p> Yaya sa'eed wallahi tallahi ni da ihsan nyi wannan ptn......ohooo kinaso kice min ishan ce tazama gardi kenan.... Cikin fushi ta daga masa hannu✋🏻 tana cewa "da Allah malam dakata! wai kai wane irin bagidaje ne😡da ka kasa gane cewa mqiyi knyi komai dmn yaga yara ba masoya,ni ashe kallon wayeyyen mutun kawai nake maka, ashe kai qaton baqauye ne bansani ba!....ke!! ni kike gaya ma hk,,.to ya kake so nace bayn ni nsn wlh duk abu buwannan guda uku qarye ce da kuma sharri ba gsky ba,ta yaya kike tunanin zn fhmci qarya ne da kuma sharri......Gud! jinki a virgin kadai zaisa na yrda da hkn, don hk Let's go to d bed,....tsaye kawai tayi tana mishi kallon baka ma yadda da abnda na fada ba Kenan......gnin hk yasa ya jawo hannunta da qrfi da niyr jefa ta abisa gado,,ta fizge hannun tana cewa"idn hr baka yadda dani ba da kuma rantse2n danayi ni kuma bzn taba yadda ka ksnceni ba,,,, bai tsaya bi ta kanta ba ya jowata ya jefa bisa gado yana qoqarin raba ta da kyn jknta, ita kuma tana qoqarin qwatr kanta.</p><p><br /></p><p>Writing by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [7:20PM, 11/28/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹7⃣0⃣🌹A bangaren Symh wldh kuwa tunda sa'eed ya fita,ta maida hnklinta akn SUNNAH TV tana sauraren wa'axi sai taji bell ringer,tashi tayi ta bude qofr, ihsan ta gani cikin frn ciki suka rungume juna,symh wldh ke cewa " ni nayi fishi tun shekarn jiya kika ce min zaki zo amma nji shiru,,, ayya to yi hqr kinsan ynx jrbwa muke shiyasa,,,OK to ya exam?alhmdlh,,yauwa to zauna naje na kawo maki rwa ki sha.</p><p><br /></p><p>Sa'eed kuwa tpy yake yaga basu daina binsa ba, hkn yasa yayi parking dmn yaga iya gudun rwnsu, ga mamakinsa sai yaga sun tafi abnsu don haka yayi tunanin ba byrshi suke ba, yaja motr sa ya tafi,gudu yake sosai dmn ya samu ya dauko symh wldh kafin dattijon ya tafiya,bai ankara ba sai kawai yaga qaton gundlin icce akn hnyrsa,da sauri yake qoqarin kaucewa amma ina! ya riga da ya makara,,,anan nji gwagwab ya bugi iccen nan take mtr tyi sama ta dawo sai juyi take dashi.</p><p><br /></p><p>Symh wldh dai2 ta dauko ma ihsan abinsha da na motsa baki a cikin plate,sai kawai tji gabanta na dukn uku2,,,shiko sa'eed motr bata daina juyi dashi ba saida ta bugi wani dutsi da qrfi hr saida kansa ya bugi strin mtr,hkn yasa gabn syhmh wldh yayi mugn faduwa sosai hr saida ta saki plate dinda ke hannuta tare da dafe qirjinta tana furta"innalillahi wa innaillahi raji'un!,,lpy symh wldh?huh!wallahi haka kawai nji fadwr gaba sosai,hr da jikina duk nji ya mutu.</p><p><br /></p><p> 🌹7⃣1⃣🌹umma ce ta fito daga wnka cikin sauri take qrasowa a gbn mirror sbd qarar wyrta da taji, ta dauki wyr ne hade da yin sallamah,sai dai bana jin me ake cewa a dyn bangaren sai ji nayi tace innalillahi wa innailaihir rajiun shi sa'eed din!,a wace asibiti?....OK to gani nan zuwa,,, rqy ce ta shigo ganin umma na shiri a rikice yasa take tmbyr ta"umma lpy?rqy bamu ga ta zama ba dauko key din mota mu tafi asibiti, umma waye baya da lpy?yayanku ne yayi hadari amma da sauqi sosai,.... tace mata hkne dmn kar ta tyr da hnklin ta,rqy ce ke driving hr suka isa asibiti,suna isa akayi ma umma byanin cewa dole sai anyi masa qarin jini dmn jininsa ya zuba sosai sanadyr fashewr da kansa yayi amma sauqin abn bai ji wani rauni ba byn nan,sai 'yan qana nan raunuka,,,, to doctor kaje kayi masa duk abnda y dace mudai fatn mu ya samu lpy.</p><p><br /></p><p> A bangaren su symh wldh sai hwye ke zb a idanunta ba qaqqautawa,ihsan ke cewa yau ni naga ikon Allah daga fdwr gaba sai kuma kuka Kuma kince baki san dalili ba, ko hkn ya taba frw dake ne?a Iya sani na hkn bai taba frw dani ba sai yau,kuma inson nyi controlling din abn amma na kasa😭pls ihsan yimin addau'a,rungume ta tayi tana tofa mata addu'a hr abn ya fara rage mata,,, ihsan kiramin lovely,,,,ta dauki wyr ta tana kira sai kawai sukji wyr na ringin akn dining table,,,,kash ashe bai fita da wyr sa ba,ya za'ayi ynz?kawai kibashshi nsn baya nesa da dawowa,amma don Allah ki zauna hr sai ya dawo kinji,, kar ki damu Zn zauna hr ya dawo.</p><p> Jrn dawowar sa suke hr byn isha'i basu ga alamr zai dawo ba, symh wldh ke cewa" nifa ihsan yaya sa'eed bai taba dade wa a waje irin haka ba, hr dai da ya mnta wyr nan da ynxu ya dawo,,,,kwantr da hnkalin mana......no hnkli na bazai kwanta ba har sai naga ya dawo.....kinga ihsan kira umma muji ko yana a can,, tana kira aka daga wyr sai dai ba umma bace rqy ce ta dauka tana cewa a cikin kuka.</p><p><br /></p><p>Sry masu krtu ba anan naso tsaya muku ba.</p><p> Ina dn jin jiki ne shiyasa.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [8:39PM, 11/29/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p> 🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p> Na Bilky giro😊</p><p>🌹7⃣2⃣🌹Hello ihsan ...... rqy me yake frw ne nji kina kuka?yaya sa'eed ne yayi hadri yanx hk muna asibiti,tana cikin fada mata a asibitin da suke sai kawai tji an fzgi wyr,......"kina da hnkli Kuwa rqy, da zaki fadamasu",,umma kiyi hqr amma fa ai dole ne su sani, amma ai kya bari hr muga yanayinsa ko, sbd ko mu dake nan basu bari mngansa ba, umma ihsan fa ce da symh wldh kinsa fa dole su sani,ko su ne fa, ai ba kai tsaye zki fada musu ba dmn ynx baki san irin tuqin da zsyi ba,idn akaje aka samu matsala fa,shiru rqy tayi bata sake cewa komai ba,suna cikin hk ne sai gasu ihsan gudu2 cikin tsananin rudu,suka qaraso inda suke.</p><p> Symh wldh ce ta fara magn tana mai cewa a cikin matsanancin kuka"umma ina yaya sa'eed yake....a wane hli yake....... Umma pls muje na gnshi.....😭umma,rqy, yana ganku a tsaye don Allah umma kuxo mu tafi mana, naga hln da yake ciki....rqy magana nake muku ku bani amsa mana....ko shima ya tafi ya barni ne😭....um...ma😭....rqy tace"ke da Allah dakata! muma abnda muke jira kenan mushi ga mu ganshi,sai kace ke kika fi kowa sonshi,kina mgn bako qaqqautawa,".....meye hk rqy?.....hjy zaku iya ganinsa ynz,,,yauwa doctor,,,koda suka shiga sun samu anyi rlng din kansa da bandage,sannan ana masa qarin jini,da kuma 'yan raunukn da yaji suma anyi plstng dinsu.</p><p><br /></p><p>🌹7⃣3⃣🌹Sai dai ba'a farke yake ba.</p><p><br /></p><p>symh wldh ce tayi saurin isa gurinshi,tana isa kuma sai ta tsaya tana kallonsa, tana kuma tuna kmn ba'a dazu2n nan suka rabu lpy ba,rwy kenan Allah mai yin yadda yaso,yanzu wai shine akwance,kafin take cewa"Allah na gode maka da kabr min shi a raye......mundai gode masa, sbd ta dalilinki ne haka ta faru dashi,dmn an tabbatr muna cewa abu aka gifta masa akn hnyr sa ta dawowa....shine sai da nace ma umma kar ta bari yaya ya aure ki, sbd hjy bintu bibiyr duk wani frn ciki naki take taga ta rabaki dashi,don haka mu a gsky.....ke rqy bna son shashanci, da jin hk kawai kice hjy bintu ce,umma nidai a iya sani na yaya sa'eed baya da wasu abkn gaba😔,,,sai aka ce maki tasn inda</p><p>Symh wldh take,..umma nan da abuja, kuma ai abn dny baya boyuwa, kuma ina ce a lbrn da symh wldh ta bamu, tace hjy bintu nada yara 'yan daba,kin koga kosu zata sa smta bincekn inda take, kuma ba mamaki ta gano hkn shiyasa hkn ya faru da yaya,,, kinga yi ma mtne shiru ko ki fita daga dakin nan, dmn ke na lura baki san qaddara ba,,, ai umma ba rashin sanin qaddara bane jahilci ne ke cnta,ke baki da aiki sai tsoron hjy bintu....Allah ihsan kimn shiru ko ynz nan na mareki..... Ai kuwa da kinsha dkn tsiya, haba umma😭ya kina biye mata ba kya ganin Ita ihsan bata san zfin komai ba tunda tana jinjira koda abin ya faru, kwata 2 ko abba bata sani ba,,nji na kuma biye mata,kuma kar in qara jin kin ambci hjy bintu,, sannan ta juyo gun symh wldh da tun dazu kuka kawai take dmn ganin take kmr kfn ta zo gdnsu zmn lpy suke,amma ynx sai fada suke aknta,...umma ce ta katse ta da cewa symh wldh zo nan,,fadawa tayi jkn umma tana kuka, tana ba umma hqr,umma ko sai lallashinta take.</p><p><br /></p><p> 🌹7⃣4⃣🌹Shigwr doctor ne yasa symh wldh ta tsagaita kuknta dmn tji me zai fada,,,,"hjy sa'eed ba zai samu farfadowa ba har sai nan da kwana biyu,kuma idn bai tashi a dai2 lkcn da muka dibar masa ba, to akwai matsala,yana gama fada ya fice,,umma kinji abnda doctor yace? Symh inshaAllah zai farfado zai kuma samu lpy.</p><p><br /></p><p>Byn kwana biyu symh wldh ce rungume da sa'eed sai zbr da kawalla take ganin lokaci ya kusa amma bata ga alamr wani abu a tare da shi ba,gashi umma tje gda su ihsan kuma suna grn jarabawa,,,,mgn take tana cewa"lovely pls ka tashi don Allah,kar ka tafi ka barni dmn bxn iya ryw ba kaiba,katashi kaji,girgz shi ta fara tana kiran lovely!lovely!!lovely!!!pls ur lady is calling u,,comon lovely ka tashi mana sai kace ba nmji ba,,,uhm sai kace wnda ke jinta,,,,hk taci gaba da yimashi srt amma shiru takeji gashi bata son dbn lkc kar taga lkci ya wuce,hkn yasa ta qara lpewa a jkns tana rera kuknta mrar sauti.....sai kawai taji ya motsa,tayi saurin kai dbnta gareshi,tana cewa"lovely ka tashi😀,sannu a hnkli yake bude idnsa hr ya bude gabadaya, sai dube2 yake almr baisan a ina yake ba,sannan yakai dbnsa a gunta kafin yake tashi zaune tare da taimokon ta,wato ta taima ka mishi ya tashi a zaune,...slmr umma tji cikin fara'a ta tarbe ta,,,tace"umma kinga ya tashi,,,😀Masha Allah,Allah mun gode ma,,bari na kira doctor,,byn</p><p> ta fita ne symh wldh ke cewa"sannu lovely ya jikin naka?shiru kawai yayi yana kallonta,,"wani abu kake buqata ne?nan ma haka, lovely kayi mn mgn mana,,....shin wai waye lovely? kuma wace ce ke?kmry ya😳 nice fa symh wldh, nifa ko sunan nan ban taba ji ba balle na sanki,girgza kanta tayi hade da 'yar gntwr dry sannan tace"don Allah lovely idn wasa kake ka daina ........kodai ke keyin wsa ba, dmn nidai wlh ban sanki ba ban kuma taba ganin kiba sai a yau,.....wani irin mirdawa marar ta tayi hr saida ta dafe wrin,ta dn ja baya kadan, dmn xncen nasa ya fara yi mata girma, tnda tji ya sako rantsuwa a ciki......sai ga umma,rqy,ihsan da kuma doctor sun shigo,,,,"yauwa su wadan nan fa ksn su ko? ta nuni su umma,,mtsw ha'a! yaki na min tmby kmr qramin yaro ni kuduka fa ba wnda na sani!</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [12:15PM, 12/1/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p> 🌹SIYAMAH WALIDAH!🌹</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹7⃣9⃣🌹Kamashi tayi suka shiga daki,cike da mamaki suke kallon juna,shi cikin da yagani ne yake bashi mamaki ita kuma mamaki take shin ya dawo nrmal ne?ta fara da cewa lovely!na'am my lady.... wannan cikin fa na wasa ne ko? buge hannusa tayi da ya dora akn ckin sannan ta rungumeshi cike da mrna,tana mai cewa "Alhmdllh Allah na gode ma" me yake frw ne my lady?kai dai bari a tsayadda wannan jinin zaka ji komai,first aid ta dauko ta fara masa dressing sai kawai tji ya matsa mata mara har sai da saki 'yar qara kafin take cewa, "haba lovely da ciwo fa",, shiko sai cewa yayi "surprise wai ashe ckn nan na gaske ne"sannan ya sake sa hanunsa a ckn rigr ta yana shafo cikin, har ya fara zuwa sama wato wrin nonnanta da yake ganin suma sun qara girma, wani shu'umin kallo ta masa kafin take cewa "ka fara ko"Allah abn ne da mamaki my lady,ya fadi hkn ne tare da zuge zip din rigr ta,ya cire rgr hr da bra sai binta yake da kallo tun daga kirjinta hr zw cki,ta katse shi da cewa "kana mamaki ne?sosai ma kuwa,bani lbrn yadda akayi,,, nan ta bashi lbrn abnda ya faru kaf,ya nisa kafin yake cewa "ayya my lady hr kin ban tausayi"....ina ce dai bana miki mgnta?, tab kai ko ke min mgnta,sbd bama yin bacci tare,wanka...kae duk komai ma da kasani kuma hr dukn tsiya kake mn😔da gaske my lady😳har saida ya bata dry yanayin mgnrsa da alamà ya rzna sosai.</p><p><br /></p><p> 🌹8⃣0⃣🌹Wasa nakeyi kaida ba rwnka a wannan lokaci,sai mu yini wata mgnr kirki bata hada mu ba,sai dai da kaji ynwa sai kace"symh wldh yunwa nake ji" sai da yayi dry sbd a yanda yake mgn tayi mgnr, kafin yake cewa "ashe kin iya mryr maza kuma sai ta miki kyau",...yauwa na taba ksntr ki?ko sau daya baka taba ba, ayya my lady hr wata shida ashe kinyi kewata sosai,?Allah kuwa🙈 to meyasa baki cmn kina buqata taba,, sai da ta hararesa da wasa kafin take cewa,"salon ka kirani jarababbiya,'yar iska....kallon ta yayi cike da jin kunya kmr wani qramin yaro,yace"haba my lady 😒ko wncn lkci ai kuskurene",,,rungumesa tayi tana dry sosai, yau taga abn nashi na ban dry ne,,,sai kawai tji yace, "zn biya ki duk ksntr ki da bnyi ba hr na tsawon wata shida,kuma yau din nan a ynx", kuma knsn fa a da, duk dàre sai nayi,don hk sai ki shirya😃kaddai ce yau mtw kawai xnyi😄rungumeta yayi yana dry sosai yace"ah haba my lady".</p><p> Nan dai suka fara rmncin din juna kmr su cinye kansu,da gni knsan snyi missing din juna sosai,hr suka lula dnyr ma'aurata, hr saida yayi sau uku sannan ya barta,rungume da juna suke sai maida numfashi suke,duk da hk hannunsa na akn cknta yana shafa,</p><p> Tace"wai kai baka gjy da shafr ckin nan ne"haba kin kuwa san irin frncikin da nake ciki, wlh frnckn da nakeje har bxn iya misalta miki shi ba,,, oya tashi mje muyi wnka,,bacci fa nakeje kuma ka gjry dani da yawa,,, uw yeah amma ai njyr dake dadi da yawa😉,,,🙈kae lovely wai meyasa bkijn knyr gaya min duk klmr da taxo maka,,au ynz hr kinji kny?sai da ta kai masa dk a qrjinsa ckn shagwaba kafin take cewa "Eh mana"kinga tashi mje muyi wnkn dmn akwai wani guri mai muhmnci da nake so mje,,, byn sun fito daga wnk ne, take cewa"af wlh sam na mnta yaya abdallah na falo,au haba saukr yaushe?yau2 din nan,kuma fa ko wani zama dashi bnyi ba fa,hasali ma abnci muke qoqarin ci sai mukaji fdwr ka,au haba, ba kece miji dadi ba, muna fita zn gaya masa abnda kika tsaya krba a gurina,lovely!😡my lady!😊yace hkn ne tare da lakuto hncinta,yana mai cewa</p><p>"My lady sauri fa zkyi mu tafi", wai ina ne zamu tafi hk", inda naso mu tafi kafin nayi hadri,ina ma kn hnyta ta dawowa ne na dauko ki mu tafi na samu hadarin,,,😔amma shine kuma kake so mutafi? ni gsky kr muje,,, dole ne fa my lady,,, kallonsa tayi da idanunta da suka cika taf da hwye kmr su xbo tace"pls yaya kar muje",meyasa?bana so wani abu ya sake frw da kai,,,jawota yayi ya rungume yana dan bubbuga bynta yace"pls my lady kibari mu tafi kinji,inshaAllah ba abinda zai faru damu,, to lovely Allah yakai mu lpy ya dawo damu lpy,,,amin my lady😊</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [7:28PM, 12/3/2015] Billy giro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹8⃣4⃣🌹Yanda ta rungumeshi kmr wacce aka ce qwace mata shi za'ayi,hk ko cikin mota mqale take da shi,basu zrce koina ba sai gd,gurinsu umma, ba qaramin murna sukayi ba,musamman ma umma tayi frn ciki sosai marar misaltuwa, symh wldh kuwa, yanayin fskr ta mrna fal hr bkinta baya rfuw amma kuma hwye ne ke zuba a idanunta,ta rasa wanne zata yi a ciki murna ko kuka,dmn daganin mhfinta tasan cewa ya samu tabin hnkali,sbd WALIDAH kadai yake iya fadi ,ita ko duk lokacin da ya kira ta sai tace"na'am abbana"tare da qara jawoshi jknta duk da daudar da ke jknsa hkn bai dameta ba,sa'eed ne yace"ya kamata abashi abnci yaci ya kuma yi wanka sai mutafi aski,yana gama fdr hk ya fita dmn sayo masa kyn da zai saka idn yayi wnka.</p><p>Byn sundawo ne daga aski sa'eed ne ya shiga ckn gida suka fito tare da symh wldh suka wuce nasu gida tare da babanta.</p><p><br /></p><p>Sa'eed ne kawnce a dàki shi kadai tunda suka shigo bai qara sa symh wldh a idonsa ba</p><p>tana can gurin abbanta,yayi jiranta ko zata shigo suyi wnka bata shigo ba hkn</p><p> yasa ya je yayi wnknsa dmn ganin dare nyi,da ya fito ne yaje dakin Abbanta, me zai gani,Abdallah ya gani da symh wldh sai kuka suke bana wasa ba,symh wldh ce ta fara ganinsa ta taso tare da cewa"lovely tunda yaya abdallah ya shigo na fada masà cewa angane</p><p><br /></p><p>🌹8⃣5⃣🌹 Abbanmu sai kuka yake sosai nàyi2 ya dainà yaqi"lovely pls kayi masa mgn ya daina kukn nan haka,zuwa yayi ya durqusa agbn abdallah ya fara da cewa"haba abdallah ina ce wannan abin frn ciki ne bana kuka ba,murna ya kamata kayi ba kuka ba,kodan yana dauke da lalura ne?a'a ba wai ina kuka ne sbd lalurar da nagani a tare da shi ba, dmn inshaAllah wannan lalurar da alama mai sauqin wrkewa ce,kuma sosai nyi frin ciki dajin cewa angane abbanmu ba zato ba tsammani,wlh sa'eed a halin da nake ciki ynx nama fi symh wldh farinciki,....amma yaya abdallah kukan da kake yi kmr da akwai dmw a tare dakai, sai kasa nayi tunanin ko Abba bazai taba wrkewa bane......ba hk bane qanwata,,,, yace hkn ne kafin yake cewa a ckin zcyr sa"ina kuka ne akn ya Abba zai ji idn yaji cewa ni ba dansa bane, ya kuma zai ji idn yji cewa har dani cikin ctrda su duk da cewa ba'a cikin hayacina na aikata hkn ba,sannan meyasa nakasa tmbyr su cewa ashe ni ba dansu bane?,dana tabbata hkn duk bai zai faru ba,ko da yake abu ne da Allah yariga da ya rbto cewa hkn zai faru, amma tabbas nyi frin ciki sosai, ko don hjy bintu dake qoqarin mallake masa dky,......symh wldh ce ta katse masa tunani da cewa yaya abdallah nsn kna jin yunwa sosai bari nje na kawo maka abnci,,.,tana isa kicin sai ga sa'eed yaxo yace"my lady bari naje na sayo masa abincin, ke kuma sai kije kiyi wnka ki huta.......no lovely gsky ni bana ra'ayin miji na yaje sayen abinci, tunda lpy ta qalau kabari kawai na dafa muna dmn muma muna jin yunwa ko? Eh hkn ne gsky,tare sukyi girkin,byn ya dafu ne ta kaima su abdallah nasu sannan su kuma suka je sukaci nasu.</p><p><br /></p><p>Kwance suke rungume da juna hannun sa'eed na kan cikinta sai shafa yake,symh wldh ke cewa"lovely ina so namaka wata tmby...qara rungumeta yayi kafin yake cewa "my lady pls kibr tmbyr nan har gobe dmn inaso ki yi bacci kinji,"ckin shagwaba take cewa "no lovely ni gsky ynz nake son yinta,"da yake yasn tmbyr bazata wuce ta Abbanta ba,kuma gashi shi bacci yakeji sosai kuma ya tabbata ita ma tanajin bacci,dmn hr 11:30 pm tayi,sai kawai yace "ok 1 mnt, bakinsa da nata ya hade yana tsutsa tare da shafr gashin kanta hr tayi bacci ba jimawa shima bacci ya daukesa.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [8:48PM, 11/27/2015] Billy giro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹6⃣6⃣🌹Tana qoqrin wcewa sai taga ya dn dafe gfn zcyr sa,kallonsa kawai tayi don anata tunani inda ya qone ne ke masa ciwo,,,,hkn yasa ta sa kai dmn zuwa dkinta....sallamr rqy ta juya da ita ckin mamaki,kafin tayi mgn sa'eed ya riga ta da cewa"me ya kawo ki gidana munafuka kawai ko kinzo ne ki sake qulla wani mnfrcin,,,,yaya sai'eed na..... Hey! Rqy i don't wnt hear anything from u,just get out of my house!,,,yaya don Allah ka tsaya ka saurare ni,nazo ne na baku hqr</p><p>akn abnda na muku.....mtsw sai ynzu kika ga dmr zuwa bamu hqr byn hr an kwana biyu,kawai ki fitamin daga gida..... haba yaya sa'eed kbrta ta shigo mana,,my lady wlh idn naganta wani bqn ciki nake ji a cikin zcy ta wai ace my blood sister.......sai kawai suka ga ya dafe qirji ya fadi...da sauri suka qaraso inda yake rqy ke cewa "na shigo ukku yaya pls dn Allah ka tashi ynz xn fita,,,"yana da cwn zcy ne rqy?eh cwn ya smo asali ne a dalilin rashin Abbanmu amma ya dade bai tashi ba,,, oh my God rqy kiramana doctor yazo,,, ba jimawa kuwa sai ga doctor yazo ya duba yace tabbas cwn zcyr sa ne ya tashi dmn akwai abnda ya nema ayi masa mai mhmmnci bai samu ba kuma ya hadu da bcn rai, don haka a kula a kuma kiyaye,OK doctor za'a kula inshaAllah. symh wldh ce tayi mgnr cikin kuka dmn tasn hqrn da ya nma ne tayi masa taqi yi, da kuma zwn rqy,,,,nan dai doctor yayi masa duk abnda ya kamata ya tafi ya kuma rbt musu magunguna yace asiyo ynx idn ya tashi daga bacci sai a bashi,,,rqy ce taje siyo mgni byn ta dawo ne take cema symh wldh"don Allah karki gaya ma umma cewa cwn yaya ya tashi dmn tkn sa dmwa a ranta sosai",,,sannan kuma don Allah symh wldh kiyi hqr da abnda na miki sharrin shaidn ne da kuma shakkar hjy bintu,,,babu komai rqy na hqr kuma na fmci abnda kike nufi kina da gsky,,rqy tayi mata gdy sannan ta fita.</p><p><br /></p><p> 🌹6⃣7⃣🌹kallonsa take ta lura ckn kwana biyun nan da sukyi fada,duk ya rame kmr wanda yayi sati bashi da lpy,,,zufn da taga yana yi ne yasa ta cire masa riga,a nan taga ashe ta dn qona shi daywa,hannuta tasa ta shafi wrn kadn,sai taji duk bata kyauta masa ba.</p><p><br /></p><p> Kwanansa biyu yaji sauqi sosai.</p><p><br /></p><p>Sa'eed ne ya dawo daga masallaci sallar isha'i ya shigo dakin symh wldh ya samu tana krtn qur'ani tsaye yayi yana sauraren yanda take ba kowane hrfi haqqinsa gashi ta iya qira'a sosai,yana tsaye hr ta gama krtn, sai yji gabakidaya ta qara shiga ranshi,ganin zatayi addu'a ne yasa shima yaje ya zauna a kusa da ita suka yi addu'ar tare,,,, byn sun gama ne ya dauke cak sai bisa gado, suka Lula dnyr rmnce.</p><p> </p><p>Hr wata daya kullum rmnce suke dmn shi yna jin nauyin cewa ya knsc ta, gashi a bqace yake sosai kullum ckin azumi yake akn hkn.</p><p> Ta fito daga wnka wraren qarfe 04:20pm daga ita sai towel, ta zauna kan mirror tana qoqarin shifin mai,, taji sllamr sa ta amsa sallamr ne tare da kallon yanayinsa yanda idawnsa sukayi jawr,tashi tayi ta rngumesa dmn tarbonsa, tana mai cewa,"lovely yadai na gnka suku2 yau me yake dmnka ne, a bqce nake my lady ya fadi hk ne tare da zame towel dinta, saurin qame jknta tayi tace ckin marairai cewa"lovely baza ka min da zafi ba,Allah bxn miki da zafi ba kinji ki banni nayi pls,tausayin sa taji sosai yanayin ynda yayi mgn tasn a bqce yake, dn hk ba musu ta amnce masa suka lula dnyr ma'aurata,sai dai ta wahala sosai dmn bashi ya brta ba sai da sukaji ana kirn sallar magrib, sai dai bata ji zafi irn na rnr ba.</p><p> Byn sallar isha'i.</p><p>Zaune suke suna cin abnci kn dining table,,symh wldh ke cewa "nikuwa yaya sa'eed,ya batun zwnka Oman naji shiru hr lkc mai tsawo,,, na manta ban gaya miki ba na br aiki a can...sbd me? sbd umma tace bata son nisn da nake musu gashi ni kadai ne mai kula dasu,shine tace na dawo na bude asibitin da na gina sai na cigaba da aiki na a ciki,, amma kar ki damu znje Oman bnda gobe kuma dake zn tafi dmn dauko mtr da bata da lpy,,,ba slmn na can ba why not bazai dawo da ita ba?sbd nasa hannu cewa kar abari kowa yazo daukr ta sai ni, kinga baza su bashi ita ba, kuma inaso na rbta tkdr brin aiki sbd a waya kadai na iza musu,,shi slmn ya yayi da gurin da yake aiki?wai kinga ya dade bai dawo ba?Eh,,yana aiki a asibitin qanin mhfnsa ne,,,,to ynx yaya idn ka dauko ta ya zkayi da ita tunda ba'a san 'yan uwnta ba,,,my lady sai kace 'yar jarida😉 gashi muna cin abnci muna srt ba kyau fa😊,,, to Allah ya yafe mana, Ameen my lady.</p><p><br /></p><p> 🌹6⃣8⃣🌹Byn sun gama cin abnci ne suka koma daki,kwance take tana game da wyr ta,, sa'eed ya amshi wyr tare da cewa " my lady kinsan wani abu? sai ka fada,,,,insn idn muka dauko mtr ta zauna anan gdn hr a gane 'yan uwanta dmn ynzu ta warke komai tana iyayi amma hr ynx bata yi mgn ba,, zaki iya my lady?qawarai ma kuwa😀lovely wlh zn iya,, yauwa my lady shiyasa nake qara sonki,ya kaimata kiss tare da cewa"ai da ganin mtr mutuniyr kirki ce bata da matsala inshaAllah,,,tashi ma ki duba a cikin wardrobe dita ki dauko photon ta ki gani,yauwa kmn kuwa ksn ina son ganinta kafin muje,tana cikin dubawa bata ga na mtr ba taga nata dinda sukayi fada aknshi,,,"mtsw ni wannan kadai nga ni, tace hkn ne tare da nuna masa pic din,,,kawo minshi na yaga,yana cikin yagashi ne yake cewa,"nikuwa my lady</p><p> abnda yafi daure mn kai shi ne wai ya akayi rqy tasan cewa zmu fita a wannan ranr"? ina ganin a gurin ihsan taji dmn byn munje nayi waya da ita a lokacinda nake jrnka....nidai lovely tashi ka duba min pic din,, ya tashi ya duba duk inda yake tunanin ganinsa bai ganshi ba,,,"gsky ina ganin bnzo dashi ba, OK ba matsala.</p><p> Da safe wrarn 11am,byn suyi wnka sunyi break fast,sa'eed sai damn symh wldh yake da tabe 2,itako sai cewa take"Oh no lovely bacci fa nake ji kbrni nayi mana,,,,idn kin barni nayi ba,mene ne?abnda mukayi jiya.... Oh pls lovely wai baka gjy ne,jiya fa kamin muyi bacci sai da kayi, ai jiya da yau ba daya bane, kuma kin kuwa san irin ni'imr da Allah yayi miki,tab ai ina ma hqr wlh,Ok nji amma fa kar kmn da zafi dmn ko jiya nji zafi,... nji kuma ai zaki saba ne a nan gaba,nan dai suka lula dnyr ma'aurata. </p><p> 2:30pm</p><p>Symh wldh ce ke waya da abdallah tana fadasa cewa "zasu tafi omn gobe,"shi kuma yace "yaushe zaku dawo,"sai cemasa tayi"gsky yaya ban sn lokacin da zamu dawo ba,OK to yayi ba matsala znje can mu hadu ko,,yauwa yaya abdallah idn zaka zo sai ka gaya min,jin kawai tyi ya katse wyr,sai dai bata dauka ko wani abu bane.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🌹6⃣9⃣🌹Shiko abdallah ya katse wyr ne dmn ya kira hjy bintu,,, byn ta daga ne yake fada mata btn tafyr su symh wldh,,, anan ta ke ce masa "kar ka damu tuni mtanena na Kaduna dmn su klr mn da shiga da ftrsu",,, matsala daya ita ce idn mijnta bai fito ba hr gobe to bazamuyi nsra ba sbd kace tunda safe ne tfyrsu,,, kmrya kenan mama? Ina nufin ya fito daga cikin gdnsa yau zuwa wani guri, to komai zai zo a yadda muke so, don ynz xnsa a kula mn da ftrsa hr zuwa dare komai ake ciki xn Kira ka.</p><p> 5pm</p><p> Kwance take kn cinyrsa shikuma yana wasa da gashin kanta,sai kawai ya zbra yana sauke ta daga kn cinyr sa,kallonsa tayi kafin take cewa"lovely lpy?my lady sam na mnta da ina so na fita,..... bai tsaya jin me zata ce ba ya dauki key din mota yana batun fita....."lovely kmnta wani abu,juyowa yayi tare da cewa"mene ne"? baka yima mtr ka kiss ba😊,,,,ya mnna mta kiss hr zai fita,ta riqo shi ckn shagwaba tana cewa baka cemin ba,,,,ok i love u,yauwa luv u too,bye.....oh dakata yana tsayawa,ta tafi da gudu ta manna masa kiss,sannan ya tafi.</p><p><br /></p><p> Yana ckin tafiya ne sai mnsa ya qare da yake akwai gdn mai anan kusa dashi sai ya tafi aka sa masa,,,,hr zai tafi ya tuna yau duk baiyi sadaka ba, can ya tsinkayo wani dattijo zaune yje ya bashi dari byr guda biyu yace masa"daya tawa daya ta symh wldh",,, zmbr dattijon nan ya miqe yace"symh wldh 'yata ce,,,kmry ya bwn Allah...... kaga malam tafi abnka dama hk yake cewa kullum baya da isashshen hnkli ne,sa'eed ya kalli yrn da yayi mgnr bai ce masa komai ba, amma tabbas yaga kama ta jini a tare da dattijon nan da kuma symh wldh, kuma a lbrn da umma ta bashi cemasa tayi abban symh wldh ya bata ne,,,sake kallon dattijon yayi yana cewa a cikin zcyr sa"lallai yazama dole naje nazo da my lady dmn ta ganshi,tpy yake ya lura da wasu tun dazu da ya fito gida suke byrsa,hr ynx kuma binshi suke.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [9:02PM, 11/30/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p> 🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊</p><p>🌹7⃣5⃣🌹Umma ce ta fara da cewa"wai meya ke frw ne symh wldh?umma wai cewa yayi bai sanni ba, shine hr Ku ma yace bai san Ku ba,,doctor yace"OK hjy to Ku dn bàni guri na nyi masa bincike,,,duk wani bincike da tambayoyi da suka kamata doctor yayi masa yayi, ya kuma gane cewa sa'eed yayi loosing memory dinsa ne,, hkn yasa ya kira su umma ya gaya musu,,, ba qaramin rzana sukayi da jin wannana xnce ba musamman ma symh wldh,,,ta fara da cewa na "shiga uku ni symh wldh shin ko nayi ma ubngiji na wani laifi ne da yake hknta tani da irin wanan hknci mafi muni a gurina.......ke!ke!!symh wldh kinsàn me kike fadà kuwà?...yi sauri kiyi istigifari wa ubngiji........😭umma ganin nake kàmr akwai abñda nàyi màsa,shine yake hkn tani da mtanen da nafi ji dàsu, ki duba fa narasa Abbbana,narasa umma ta,na kuma rasa kakata, sannan kuma ynx mijna wnda nake tunanin zai maye mn grbnsu su,yayi loosing memory,ynx kwatà2 baisan da wata soyayya da muka gina nida shibà😭,,,,to shikuma yaya abdallah ko mai zai faru dashi 🙊umma ce tayi saurin rufe mata baki tana cewa "subhannallah,meye haka symh wldh keda nace kiyi istigifari,maxa kiyi,, kuka take sosai kafin take cewa"astagfirullah3 Allah ka yafe min,3 amma umma ganin nake dole na tafi na barku kar kuma wani abu ya shafe Ku,,,symh wldh ina so kisani, shi ubngaji ba wai sai kayi masa laifi yake jarabtarka ba,dmn wanna jarabawace, yake maki yagani shin zaki iya jure cinta ko bazaki iya ba, don hk inaso kiyi hqr ki kuma dage da addu'a akn Allah yà baki ikon cin jrbwrsa,dmn dole sai da iknsa ne zakiyi nsara akn komai na dñy da kuma lpr.</p><p><br /></p><p> 🌹7⃣6⃣🌹umma nji kuma insahaAllah znci gaba da hqr da kuma addu'a,,mashaAllah,hk a ke so,shiru tayi tana kallon sa'eed da ryw ta cnx masa cikn qanqanin lkci kuma shikenan ya manta soyayyarsu da komai ma,sai kawai ta sake fashewa da kuka tana cewa" wayyo Allah ni symh wldh nazamo abin tausayi shike nan duk wani mai bani kulaw, soyyaya ta gsky tafiya suke suna barina😭",,umma wlh yazama dole na tafi na barku dmn kuuma bxn so wani abu ya faru daku ba,,,ihsan ce tazo ta rungume ta cikin kuka take cewa"no. Symh wldh ba inda zaki tafi,muna son ksncewa tare dake duk rintsi duk wuya",,,a'a ihsan gsky dole na tafi dmn banaso wani abu ya qara frw daku a ta dalilina,, haba symh wai ina hnklin ki ya tafi da kuma ilmnki,inace dake da bake idn Allah ya rbto frwr abu aknmu dole zai faru damu,,,kuma ki gode Allah a duk hlinda kika sami knki a ciki,sbd idn kika ga rwr wasu wlh sai kiga ashe ke ba baqramin jin dadi kike ba,,,kuma ki ksnce mai hqr domin Allah yana tare da mai hqr,inshaAllah wata rana zaki ci rbr hkn,,,ngde sosai ihsan,,,ita dai rqy dake gefe ba abnda tace amma ga alama ta tausaya ma symh wldh,,,umma ce ta kai dbn ta ga sa'eed dake zaune yana kallonsu ko shi da alama ya tausaya mata,tafara</p><p>da cewa "nsn kana so ksn komu su waye, nice mhfyr ka, wannan kuma qanwrka ce mai bi maka sunanta rqy sai kuma wannan ihsan Ita ma qnwr kace ta biyu,sannan ta nuni symh wldh tace"wannan kuma mtr ka ce, sunanta symh wldh,ina ftn ka fhmceni? Ya nisa kfin yake cewa na gane amma nikuma meye suna na?gabadaynsu sai da hwye suka zubo musu kafin umma ke cewa"kae sunanka sa'eed"to meya sameni ne dana samu rauni?hdrn mota kayi knka ya bugu hkn yasa kmnta komai,sannan ta juyo gun symh wldh tana cewa"kin fada ma yayanki abdallah?eh umma na fada masa wai amma yace nyi hqri bazai samu dmr zuwa ba sbd ynz suke gab da qarewa,saura wata nawa su qare,hr wata shida fa umma,wai amma bazai xo ba, sai naga kmn akwai rashin kulawa a cki,....a'a symh kar kiyi wannan tunanin, ya danganta daga yananyin krtnsa ne,, Allah dai ya kaimu lokacin,ameen umma.</p><p><br /></p><p> 🌹7⃣7⃣🌹Byn sati biyu aka sallami sa'eed suka koma gida,zaune suke shida symh wldh a dakinta tana qara koya masa abubuwan addini dmn tun a asibiti ta fara kowa masa,krtn Qur'ani suka koma yi,hr ksn 40mnt sannan ne sa'eed yce"symh wldh,bacci nake ji ina ne dakina?tashi tayi taje ta nuna masa dakinsa sanann ta dawo tayi wnka tayi shirin kwanciya.</p><p> Da safe zaune suke kan dining table suna break fast,hr tayi tsaka da cin abincin sai taji amai da sauri ta haura sama zuwa toilet tana kwarara amai hr sai da ta amaye abinda taci kaf sannan ya tsaya mata, ta kuskure bkinta tafito kenan ta ganshi a bkin toilet, yace"sannu",,tace"yauwa,"hln baki da lpy ne? lpy ta qalau hka dai kawai naji injin amai.</p><p> HK aman ke dmnta kullum bata da hln cin abinci sai tayi amai,hr tsawon sati biyu tana fama da hk,rnr dai sa'eed yaga whlr tayi yawa shine yake cewa "symh wldh yakamta muje asibiti",dayake Ita tuni ta gano cewa ciki ne da Ita,sai cemasa tayi"no ba sai munje ba ai namaji sauqi, da hk bai sake cemata komai ya haura sama,binsa da kallo tyi,tana tuna cewa"da sa'eed din da ne zata samu kulawa sosai,amma shi wannan ganin sa take kmr yakasa sakewa da ita,,ada tare suke bacci,wnka,kwanciya,cin abinci a plate daya,su kuma yi wasa da dry,amma ynx ba ko daya,share hwyn da suka xbo mata tayi kafin take cewa"ina ma ace sa'eed bai sami wannan mtsala ba,dana fada masa qrwr da muka samu,da kuwa yayi frn ciki marar misaltuwa,ya kuma bamu kulawa sosai nida bebina amma ynx ina baza mu sami hk daga gareshi ba sbd ynx zai iya yini bmuyi wata mgn sosai ba,,,"ya Allah na roqeka daka yaye ma yaya sa'eed wannan lalura,mu dawo kmn ynda muke a da cikin,soyayya,shaquwa,kulawa, Allah don girmn ka Allah ka amshi roqana,Allah Amin.</p><p><br /></p><p> 🌹7⃣8⃣🌹Byn wata shida da frwr hkn, symh wldh ce cikin shiga ta alfarma tayi kyau sosai ga kuma cikin ta ya fito sai dai ba sosai ba yayi bala'in yimata kyau,sai fara'a take yau yayan ta abdallah zai dawo,, ta shirya komai tsaf na abinci shi kadai take jira dmn tayi masa kwatencen gidn, zaune take hr ksn minti 30 sannan tji qarar bude gate, saurin duba window tayi, dai2 shikuma ya fito daga cikin mota, bata san lokacin da ta saki kuwr jin dadi ba,ta fito da gudu ta fada jiknsa, tare da fashewa da kukan jin dadi, bubbuga bynta yake yana bata hqr,ya fara da cewa"qanwata yau gani gaki dn hk ki daina kuka kuma mugode Allah da ya sada mu cikin qoshin lpy,"share hyenta tayi taja hannusa suka shiga daga ciki,ta nuna masa guri ya zauna,suka fara firar yaushe gamo,....af yaya abdallah zo mje kaci abnci na manta sai srt nake maka, zuwa sukyi kn dining table ta zuba masa abnci, Ita ma ta zuba ma kanta hr zata ci,abdallah ya katse ta da cewa,"qanwat wai ina mjinki?yana ciki baya jin dadin jknsa ne,amma bari na kira maka shi Ku gaisa,,sai da ya tabbatar ta shige,sai kàwai naga ya ftr da wata 'yar qaramr kwalba da alama poison ne,zuba mata shi yayi a drink dinda ke gbnta cikin wani glass cup,yana gama sawa sai gata ta fito.</p><p> Kallon ta yake yana cewa "ba zài iya fitowa bane?ai gashi nan zuwa,zama tayi tare da daukn drink din tana qoqarin kafawa a bkinta,shi kuma sa'eed yana ckn saukowa,sai kawai yayi missing stape, ya fadi knsa ya bugi grin hr sai da yayi qara,,ba shiri symh</p><p>wldh tayi jifa da cup din ta haura sama,tana mai cewa"oh my God"sannan ta tallafo knsa da taga jini na zb, kafin tace wani abu sa'eed ya riga ta da cewa"wash Allah,my lady ya akayi nzo nan hr na fadi,,kallonsa tayi da sauri sbd sunan da taji ya fada,rbn da tji ya kira ta hk tun kafin yayi hdari,.....ya katse mata tunani da cewa my Lady pls kamani na tashi mana.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [11:44AM, 12/2/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p> 🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊</p><p>🌹8⃣1⃣🌹Shiko Abdallah tun lokacin da su symh wldh suka shiga daga ciki, yaji ko abncin bazai iya ci ba,tashi yayi ya fita cike da nadama da kuma jin hushin kansa, ko meye dalili oho.</p><p> Bai zarce ko ina ba sai abuja gdn hjy bintu,koda yaje falon ba kowa,hkn yasa ya tafi bedroom dinta dmn ya qwanqwasa,yana qoqarin knocking ne yayi saurin dakatawa dmn abnda yaji hjy bintu na cewa"ai ko shi abdallah bai san cewa suna da wani da ba,nuna masa nayi symh wldh ce kadai 'yarsu,,,to shi yakayi ya yadda cewa shi ba dansu bane?hm kedai bari hjy larai da qyar fa,koshi saida bokana ya bani wani mgni na sa masa a abnci,amma fa duk da hk bai yadda ba, kuma kinsn boka na cewa yayi sai ya yadda aiki zai yi kyau, au haba byn yace sai kin cnx dan sannan zaki samu dmr mallake dkyr? eh kuma knsn cewa yayi da an haihu in tabbatar ko gd kar a shiga da dan kuma hk nayi tun asibiti na cnza dan,sannan kuma yace idn abdallah ya girma in nuna msa cewa shi ba dansu bane, idn kuma bai yadda ba aiki bazai yi kyauba dmn yaddarsa kadai xai sa a mallake dkyr,heee amma bokn nan fa yayi,kedai bari abnda cewa yayi, ko sunan da suke son sama dan kar na bari su sashi,kuma nice zn fadi sunan da za'a saka, hk akayi kuwa nayi kisisinar da aka yadda na bada sunan da nakeso wato abdallah,hk Zainab tayi hqr da sunan da take so asa wato muhseen.</p><p> Nikuma sai na Samu kaina da son danta da kuma sunan hkn yasa nasa masa sunan wato muhseen,ynx hk yana gurin wata qawata, da yake ita bata taba haihuwa ba,shine na kai mata shi a cewr gdn mrayu na dauko mata shi,da yake mun taba mgn akn xn samo mata,.... kinga pic dinsa ynx hk suna maleshiya can mijnta ke aiki....la gyen fa ashe sak mamansa zainab,,eh suna da kama gsky......yauwa shin ya akayi abdallah ya yadda?wai cewa yayi sai anyi gwajin jini,shine yayi qrya wa baban akn cewa mkrntr su ance kowa ya kawo grp din jininsa da na babansa, to da yaga result din nan fa.</p><p><br /></p><p> 🌹8⃣2⃣🌹ya yadda cewa ba dnsu bane, to ya akyi ya yadda zai cucesu dmn nsn abdallah a ynda ykeji dasu,da wuya ya iya ctrwsu kai tsaye,.... bokana mana ya bani mgani mai qarfin,koshi da qyar yayi masa aiki, da yake yrn akwai ibada kmr uwrsa ko ince mriqyrsa,,ynx shi kadai nake jira yazo nji abnda ake ciki, dmn yñx hk nasa ya saka ma symh wldh poison a abn sha, in yaso ta mutu kowa ma ya huta, kinga dky ta zama tawa ni kadai,kmry? ba sai abadallah yayi signing ba ko zaki mallaki dkyr?au kin manta cewa komai nace yayi,zai yi ne ba tantama,amma zaki 'yammasa wani abu daga ciki ko......wa! cabdi ai rbrsa ita ce rywr da yayi a ckin daula ya kuma yi krt mai kyau,,ynx ya kike son yayi?,yako sai ya koma gdn mryu dmn can na daukosa kuma na fada masacewa gdn mryu suka daukoshi kafin su haifi symh wldh,.....heeee kinyi daidai wato bai ko san ke kika dauko sa a gdn mryu ba,bai sani ba duk daukr shi sune,kuma dana gaya masa sosai yaga sun kyauta masa dmn ganin basa nuna banbanci a tsaka ninshi da symh wldh,bai san cewa su sun dauka ko dansu ne shi,saidai yayi baqin ciki qwarai da jin cewa basu ne iyayensa ba,,,,hmm hjy bintu ai a lokcin da kika fara fada min ba dansu bane ca nake ba gske bane,Hmm hjy larai kenan, kisani cewa ke kadai kika san da wannan znce don hk ki kama bknki,,, tafawa sukayi sannan hjy larai tace"kar ki damu bwnda zaiji wannan mgnr.</p><p><br /></p><p> Abdallah dake labe gaba ki daya zufa sai kryo masa take hr wani jiri ke dibnsa yana kuma tunanin mfita....qarar wyrsa ce ta katse shi da tunanin da yake, saurin fita yayi tare da sata a silent</p><p><br /></p><p>🌹8⃣3⃣🌹 kfin suji, saida ya shiga mota sannan ya duba mai kirn, symh wldh ce, kuma hr ta katse yana qoqarin kirn tane,sai ta sake kirn sa,ya dauki wyr ne tare da boye dmwrsa, sai dai banjin me take cewa,sai yace "eh na fita amma zn dawo anjima,"Allah ba komai, sannan ya ajiye wyr tare da buga strin mtr hadi da jingina kansa yana matsanancin kuka.</p><p> Symh wldh na ajye wyr ta juyo gun sa'eed tace"amma lovely sai mun biya gida koza mutafi ko?Eh dama nyi tunanin hkn,da suka biya gida ba qaramin murna sukayi ba da ganin sa'eed ya dawo normal, basu wani jima ba suka hau hny sai gdn mai,yana gama parking suka fito,sa'eed sai dube2 yake ko zàiga mutumen da yagañi rñr, symh wldh ko sai kallonsa take ganin ya kawo su gdn mai kuma ba mai zai sha ba,,,.da yaga bai gansa ba sai ya tmbyi wasu mutane, a nan suke ce masa "ynx2 nan ya daga amma zai dawo"jiran dawowrsa suke hr ksn 30mnt bai dawo ba,Sa'eed ne ya juyo gun symh wldh cike da dmw tare da kallon cikin da ke jknta yace"my lady am so sorry nsn kin gaji ko,muje mota ki zauna kinji,suna cikin tpy sai kawai sa'eed ya hango shi tafe yana qoqarin tsallake titi,ba shiri ya damqo hannun symh wldh yace"kalli mutumen can kigani kin sanshi?tana kai dbnta gareshi sai kawai tji komai nata ya tsaya cak sbd tsananin mamaki,bakinta na rawa ta furta Ab...ba,sannan ta murza idonta ko mafarki take,, my lady bafa mafarki kike......tabbas kuwa idn ba mafrki nake ba wallahi Abbana ne,qoqarin zuwa take grinsa da gudu,da sauri ya riqo hannuta yace"my lady ki dakata kinji ai zai tsallako ne,sai da hawaye suka zbo mata jin an tsaidata kafin take cewa "meye haka ne lovely,don Allah kabarni naje kafin ya bace min,"bazai bace miki ba my lady,nidai kabrni naje pls🙏🏻😭wallahi abbana ne,cike da tausayi yake share mata hwye kafin yake cewa"naga zakiyi gudu ne kuma kina dauke da lalura shiyasa, amma muje a hnkli mu tarbo shi kinji yi hqr,shikuma baban ya tsalloko titi riqe da dankali da qosài a cikin</p><p> jarida ko leda ma ba'a sa masa ba,amma hkn bai dami symh wldh ba Ita dai kawai taji sa a jknta ta tabbatar shine, saura kadan su isa gurinsa amma sai taji bazata iya hqrn tpyr da suke ba, hkn ysa ta fizgi hannuta tare da kiran Daddy!!!juyowa yayi da sauri dmn idn ya manta komai banda mryr symh wldh,,cike da mamaki yace"Walida!tana jin haka ta sheqa da gudu ta fada jknsa tana kuka sosai.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [3:07PM, 12/9/2015] Billy giro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹9⃣8⃣🌹Bayan sati uku da frwr hakn.</p><p> Suka koma Nigeria basu zarce ko ina ba sai Abuja a sabon gidn Abban symh wldh.</p><p>Byn kwana daya da zwnsu ne su umma,ihsan,rqy suka zo,,....nan suka ynke shawarar zuwa gdn hajiya bintu,gaba dayansu,</p><p>Koda suka tafi nan ake shaida musu cewa ai tayi hadarin mota zuwa wani qauye yau sati uku kenan da frwr hkn ynx hk tana asibiti.</p><p> </p><p>Hkn yasa suka dunguma zuwa asibiti,koda suka je dakin da akace nan hjy bintu take,sai basu ganta ba face wata mata da take fama da rashin qafafu wato an gundule su ba kuma hannu daya fskrta kuma ta qabe sosai hkn yasa kamanninta suka cnxa, dyn idon yana ftr da wasu irin ruwa masu wari, gaba ki daya dakin ma wari yake na ftr hnkli dole idn zaka shiga sai kà rufe hancin ka.</p><p> Ba shiri suka juya dmn barin dakin sai kawai mtr ta kira Umman symh wldh(hjy Zainab)cike da mamaki,mryr ta na rawa,</p><p>umma ta juyo sai</p><p>Kallonta take amma ta kasa gane ko wacece, kfn tayi mgn mtr ta riga ta da cewa,baku gane ni ba ko?.......nice hjy bintu,HYJ BINTU😳!!!su duka suka frta hkn,tace eh nice😭kunga yadda Allah ya maida ni ko,....tace Zainab dama kina raye?.....Sa'eed yace qwarai Kuwa dmn mgun nufinki bai faru aknta ba,ya nuna slmn yace kinga wannan Doctor shine ya ceceta dmn yaji komai a lokacin da kike waya,.....sallamr wsu mutane sukaji ksn su hudu,wani mayen kallo Sa'eed yayi ma mtm byu daga cknsu har saida hntr cikinsu ta kada da suka ganshi,mtanen sune Sarah da hjy larai sai kuma wata mata da mijnta tana dauke da tsohon ciki,Sa'eed ne ya kalli Abban symh wldh yace Abba muyi abnda ya kawo mu, mutafi,dmn nan gurin ba grn tsayi bane,,,Abba ya ciro wasu tkrdu guda biyu</p><p>Ya miqa ma hjy bintu yace dyn tkrdr ta sakin ki ce na sake ki saki uku daya kuma tkrdr shaidar kotu tana son ganin ki, suka juya zasu tafi tace don Allah kayi hkr basai anje kotu ba,ka dubi fa ynda nake kuma hasali ma aknka ne hkn ta faru dani dmn ji nayi cewa anganka kuma kunyi tfy har da Abdallah hkn ysa na kama hny da nyr zuwa grin boka sai kawai nayi hadarin mota....wannan ke ya Shafa bani ba,kuma nagode ma Allah da ya maida ki haka dmn shine dai2 dake!.....kuka take sosai kafin take cewa</p><p> Don Allah ku yafe min laifin da nyi muku kuma danka muhseen in ynx kake so za'a baka shi,dmn na fada musu abnda ake ciki,</p><p> ta kalli mtr da mjinta tace inaso kubani muhseen na maida shi ga iyayensa,mjn mtr ne ya miqe tsaye yace da Abban symh don Allah kayi hqr dmn mu bamusan cewa ba'a gdn marayu ta dauko shi ba.... sallamr wani matashin saurayi sukaji hadadden gaye sai dai fskr sa na cike da dmw.... Hjy bntu ta nuna shi tace wannan shine danku muhseen,</p><p><br /></p><p>[7:42PM, 12/9/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹9⃣9⃣🌹Muhseen ya dubi Abba nan take yaji wani farin ciki ya zyrc xcyr shi, Abba ya kira shi ba musu yaje ya fada jkns cike da murna,sannan ya juya gun umman symh wldh, da yake tunanin ita ce mhfyr sa sbd yaga kama, ita ma zuwa yayi ya rungumeta ya hngo symh wldh sai murmushi take masa sannan suka rungumi juna cike da murna, sannan daga bisani. Ya gaisa dasu umman su rqy da kuma su sa'eed.</p><p><br /></p><p>Kafin su bar asibiti saida Sa'eed yasa aka kama su hjy larai da Sarah aka tafi dasu,muhseen kuma kuka yake kmr qaramin yaro zai rabu da iyayensa na maleshiya suma haka kukan suke,duk da cewa yayi musu alqawrin zai riqa zuwa kai musu zyra,akai2.</p><p><br /></p><p>A cikin mota Abdallah sai str kallon ihsan yake kamr yadda slmn ke ta famn kallon rqy da yake dama su masoya ne.</p><p><br /></p><p>Byn kwana biyar da frwr hkn symh wldh ce a falo da ita da muhseen suna fira tana ba baby boy nono,sai suka ji sallamr mami ai ko ba shiri symh wldh ta aje shi,ta sheqa da gudu ta fada jknta har tana qoqarin kadata, cike da mamaki symh tace mami saukr yaushe?jiya jiyan nan.....kinga ni boye nazo gani, ta dauke shi kenan suka hada ido da muhseen sai da suka ji wani abu ya tsargu a jknsu, saurin jaye idnta tayi tare da gaishe shi,ya amsa gaisuwr tare da barin falon,mami ke cewa shine real brother dinki?eh shine,wow gayen nada kyau but mijn ki fa?yana a Kaduna amma gobe zasu zo shida su umma da qannan shi da yake gobe ne bikin suna..... mami ina su umma?tare muke dasu suna a main falo suna ma umma da abbanki barka akn abnd yasa meku,ai nji ance hjy bintu tayi hadarin mota abn ba kyn gani,Allah kuwa baza maki so ki qara ganin ta ba idn kika gnta da frko,....kinga ikon Allah taso na walaqnta amma sai Allah ya juya abn aknta shine bahaushe yace idn zaka gina ramin mgnta to ka gina shi kadan dmn watarana zaka iya fadawa cknsa,,,symh kika ce gobe biki?Eh...to ya naga gdn ya cika haka kmr yau ake biki? Hmmm duk barka ne abbukn Abba ke zo masa,da kuma maqotanmu,kinsan da ya bata anyi ta nmnsa ako ina hr jaridu aka buga to shine ynx yaya Abdallah da mijina suka sa aka buga jarida, daxun2 nan nagama krn tata ashe har da yrn hjy bintu aka kama da su hjy larai da Sarah ke har wadanda sukayi shedr zur wa Abbn mijina sai da aka ynke musu hknci ciki har da abokin mahaifinsa,ke kowa bai ragawa ba kuma aka fadawa dny cewa Abbanshi bai aikata laifin da aka tuhume shi dashi ba,duk da cewa ya rasu....ai mjnki yayi dadai dmn gobe bazasu sake tunanin yin shaidar zur ba,kuma ya cika cikakken da,danda ko mahaifinsa basa raye yakn cika burin iyayenshi,,,uhm shifa har son yayi in hjy bintu ta warke a ynke mata nata hknci ,sai da na bashi hqr akn ya barta da abinda Allah yayi mata ba hannu ba ido sannan kuma ba qafafu,,,ina ce dai an saka photon ta a jarida kowa yagnta su kuma san abnda tayi, an saka photon ta, tana akan gadon asibiti,da kuma sanda tana lpyr ta qalau,,,hmmm ikon Allah ai ni jiya nakejin lbr agrn ummana byn ta gama waya da ummanki,Allah dai ya shirya, Amin.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [7:01PM, 12/7/2015] Billy giro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹9⃣3⃣🌹Ya dawo da dubansa gun symh wldh da yake dauke da ita,wasu zafafan hwye ne ke zubo masa har suna sauka kan pink lips dinta, umma ce ta katse shi da cewa,ai ba kuka zakayi ba sa'eed kaje da ita a bata taimakon gaggawa,ba mamaki ta tashi,,.nan take Kuwa yaji qwarin guiwa ya fita da ita da sauri,emergency ward ya fara zuwa da ita ajima kadan kuma sai naga za'a shiga da ita theater room,tare da Sa'eed sai faman sauri yake.</p><p><br /></p><p>Umma na gani sai sàfa da marwa take tana jiran ftwrsu, sai ga su abdallah sunxo,suke tmbyr ta abnda ake ciki nan ta fada musu komai, su kuma sukà cemata Allah yasa ayi nasara,tace Amin kafin take cewa abban symh fa? slmn yace "Dnt worry umma dmn ynx hk doctors na a kanshi,kuma in Allah ya yadda zai samu sauqi,sanan yace toni xn tafi bngrn Abbah duk abinda ake ciki xnxo in fada muku,kai abdallah sai ka zauna tare da umma kujira ftwr su Sa'eed,OK to, cewr abdallah.</p><p><br /></p><p>Zaune suke har ksn 2hrs ba lbrn ko guda daga cikinsu,can ksn 30 mnt sai ga Sa'eed ya fito a gajiye ya nufo inda suke cike da dmw.</p><p><br /></p><p>Ba shiri suka miqe tsaye suji me zai ce, yana isowa yace wlh umma Alhmdlh amma fa da qyar muka ciwo nasara sai dai, da Dan da uwar duk sun wahala sosai har dai symh.......me kake nufi Sa'eed?umma ina nufin symh wldh ta haifu kuma da kanta wato ba'ayi mata aiki ba,an samu qrwr da nmji amma bai isa haifuwa ba ynx haka yana a cikin incubator,symh fa?Abdallah symh tana bacci ynx sbd koda ta haifu bata a cikin hayyacinta, shine aka mata allurar bacci amma bata nesa da tashi,,,,Alhamdlh cwr umma,Sa'eed yana qoqarin tmbyr su a game da Abbah sai ga Slmn tafe cikin murna yace"Alhamdlh an shawo kan matsalar but sun ce a samu mutuñe ko biyu hk wadanda ya sani su zauna a kusa dashi.</p><p><br /></p><p>[8:25PM, 12/7/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹9⃣4⃣🌹Koda ya farka, dmn ynx yana bacci but ko da wane lokaci xai iya tashi,gaba dayansu suka dunguma suka je dmn dubnshi,ksn 10 mnt,Sa'eed yace shi zai tafi kar symh wldh ta farka ba kowa kusa,yana gama fada suka fita shida slmn,koda suka je tana bacci abnta sa'eed ya shafi fskr ta yace,huh! wlh slmn my lady ta wahala sosai har saida namata kuka,, ynx na matsu ta tashi naga yanayin ta,, Allah sarki cwr slmn kafin yake cewa ni zn dan fita na dawo, ya fita shi kuma Sa'eed ya samu guri ya zauna sai kallonta yake cike da tausayi,tare da shafr gashin kanta,wyrsa ce tayi qara, ya tashi yaje gun window yana waya, tashinsa keda wuya symh ta fara motsi hade da kiran,umma!umma!!umma!!!ta tashi zaune a rikice,da sauri Sa'eed ya qaraso inda take ya zauna kan gadon,saurin</p><p> qanqameshi tayi tare da boye fskr ta a qirjinsa kmr mai jin tsoro,jkn ta har rawa yake, kafin take cewa lovely ina ne nan?sai da ya jaye mata gashin knta da ya rufe mata fska kafin yake cewa my lady kina a SULTAN QABOOS UNIVERSITY HOSPITAL,a wane gari?OMAN my lady,me ya kawo mu asibiti?kinmnta mnxo dbn wannan mataar,,kallonsa tayi kmr wata tababbiya,tace eh amma kafin mu iso bacci nayi ko?a'a.....No bacci nayi mana tunda har mafarki nayi wai naga umma,my lady da gaske ne fa kinga umma,Itace mtr da muka zo dubi, ashe umnki ce,mtsw lovely meye haka pls ka daina min irin wannan wsn,Wallahi my lady ba wasa nake miki ba,to ina umn take tana gurin Abba shima baya da lpy,me ya faru dashi?,,,,nan ya bata lbrn komai a game da Abba,tana qoqrn tayi magana ne sai mararta tayi wani irin tsinkawa,qara rungumeshi tayi tana wani marayen kuka sbd tsananin ciwo,,,lovely ciwo,ina ne yake maki ciwo?hannuta tasa da nyr ta tabi wurn amma sai taji bazata iya ba ganin take in ta aza hannun ciwn zai qaru,Sa'eed yace marar ki? daga knta tayi tare da cije lebe tana yarfi da hannu,,,hannunsa yasa a cikin rgrta zai shafi marar,,.riqe hannun tayi tana kuka tace lovely kar ka taba ciwo,,,ba ciwo my lady,Allah akwai😭rungumo ta yayi ta baya yace"oya to musa hannun a tare,sannu a hankali ta aza hannunsa akn mararta, koshi saida ta dauke cknta,har ksn mnt 5 yana shafa wurin,yana mata addu'a sai kuwa ta rage jin zafi, tace cikin marairaicewa lovely ina so na tafi gurin su umma,kallon ta yayi dmn ya zaci babyn ta xata tmby, anan ya fhmci har ynx kenan bata ma san ba baby a jiknta ba,kafin yake cewa "No my lady ba kya ganin yanayin da kike ciki,kibari ai zatazo,,fashe masa da kuka tayi tace ni ka banni in tafi inaso naga Abba,,,ok to nji amma sai kin sha tea, tashi yayi ya hada mata tea mai kauri ya bata.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [6:00PM, 12/5/2015] Billy giro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹8⃣9⃣🌹"Don Allah lovely kayi hqr bxn sake ba,ki matsa daga gurina nace,ba musu ta matsa nesa dashi,,Sa'eed yace then kije ki duba packing dinda nayi inda akwai wani abu da kike son qarawa sai ki qara amma bada ywa ba sbd in mnje can xn saya miki wasu kyn, just the must important things ne nake so ki qara,har sai da tji jknt ya mutu jin cewa har packing yayi musu,sai ta qara jin bata kyauta ba,dmn Ita ya kamata ace tayi packing din,tashi tayi jiki sanyaye ta duba abnda babu ta qara ta dawo dmn kwanciya ganin tayi ya linka blanket din biyu ya lullube da abnsa, da alama baya so su lulluba tare yau, gashi ba wani sai a dakinta hkn yasa taje dkinta tayi kwancyr ta acan.</p><p> Koda ya tashi cikin dare dmn yin nafila bai ganta ba ya duba toilet bata can,dakinta ya nufa ya sameta ta qudundune a ckn bargo ta rufe har kanta sbd ita bata da jimirin sanyi ko kadan,matsawa yayi kusa da ita tare da yaye bargon,ya jaye filon da take rungume dashi ya shafi cikinta yayi masa addu'a ita ma yayi mata sannan ya gyara mata kwanciyr ta ya fita.</p><p><br /></p><p> Da asuba ma ya shiga dakinta dmn ya tashe ta ya samu har ta tashi taje toilet, ya fice abnsa zuwa masallaci.</p><p><br /></p><p>Zaune yake smn gado yana danne2 da laptop,sai sallamr symh wldh yaji ya amsa sallamar ba tare da ya kalleta ba,ta gaishe shi ya amsa ba yabo ba fallasa,ksn minti 3 tana tsaye knta a kasa sai wasa take da zoben hannunta kmr mai son cewa wani abu.</p><p><br /></p><p>[9:13PM, 12/5/2015] Billy giro😊:</p><p><br /></p><p> 🌹9⃣0⃣🌹Gashi kuma da alama ta fara gjy da tsaywr,kallonta yayi yace lpy kin wani zo kinmin tsaye,ko akwai wani abu ne?kallonsa tayi da jajjaye idanunta da suka sha kuka har ma sun dan kumbura, kmr tace wani abu sai kuma ta fasa,juya wa tayi da nyr barin dakin yace zo nan,kuka kikayi ne?shiru ba amsa,ko bakyaji nane?kasa cemasa komai tayi sai hawayen da suka fara zbo mata,tashi yayi ya jawota ya zaunar da ita bisa gado gab dashi hr jknsu na gugan juna, yace my lady nji nayi hqr don hk ki daina kuka amma kisani cewa ba kyau mijnki ya kira ki kiqi zuwa dmn Allah yana fushi da maiyin haka kinji,cikin mryr kuka tace inshaAllah bxn sake ba, Oya to tashi kije ki hada break fast sai ki dawo muyi wnka ko,,,,,cike da jin knya ta kalle shi tace to baxa kayi bane,mene ne?uhm🙈abun mana,dan guntun murmushi yayi kafin yake cewa there's no time my cwt lady sai dai idn mun tafi Oman sai muyi ko,to yayi Allah ya kaimu lpy, Ameen my lady yace hkn ne tare da yi mata kiss.</p><p><br /></p><p>Cikin qan qanin lokaci suka gama komai suka shiga mota zuwa abuja ba jimawa jrginsu ya tashi sai DUBAI, sauqin su daya basu kwana a dubai ba, suka wuce, dmn sun sami jirgin zuwa OMAN a wannan ranr.</p><p><br /></p><p> OMAN</p><p> da Isar su,suka sauka a gdn da slmn ya kama musu,basu samu zuwa asibiti ba sai da safe, suna shiga asibitn sai kawai symh wldh ta samu kanta da fdwr gaba, hkn dai ta daure har suka isa daga cikin asibitin slmn suka fara gani ya fito a dakin da zasu shiga,Sa'eed ne ya fara yimasa magana amma shi slmn bai ko jinsa sbd kallon symh wldh da yake cike da mamaki da kuma tmby,Sa'eed ya lura da hkn yace kae lpy? Mata tace fa,matr ka😳to ai na.....to ai me? baka santa ba ko,kmnta tpy kayi a lokacin auren mu kuma jiya baku hadu ba.....kaga nidai mu shiga daga ciki,bai tsaya jin me zai ce ba kawai yaja su symh wldh suka shiga dakin.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [12:34PM, 12/4/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p> 🌹SIYAMAH WALIDAH!!!🌹</p><p> 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊</p><p>🌹8⃣6⃣🌹Koda na koma da safe na samu har snyi wanka.</p><p> Symh wldh na zaune kan gado tana shafin mai daga ita sai towel,shi kuma Sa'eed na a bakin madubi yana taje smr kanshi shima towel ne a jknsa iya kunkuru,Sa'eed ne yace"my lady jiya me kike son tmby tane?yauwa dama znce ne hln ya akayi kasn cewa shi Abbana ne kuma har kasn inda yake za?kinsan rnr nace inaso nje wani guri,ina a cikin tpy sai kawai man mota ta ya qare,shine na je gdn mai nasha mai, hr zn tafi na tuna bnyi sadaka ba a wannan ranr,to sai kawai na gansa zaune na bashi dri biyr guda biyu nace gatawa gata symh wldh, nan fa kawai yace "symh wldh 'yata ce",......... nan dai ya ci gaba da bata lbr har hatsarin sa,saida tayi ajyr zcy kafin take cewa "lovely na gode sosai wlh, da hr kayi tunanin mutafi nganshi dmn da wani ne basr wa kawai zaiyi tunda ance masa baya da hnkli,ni hr ma na rasa ta ynda xn maka gdy, sai dai nace Allah yasaka maka da mafificin alhairinsa,...no my lady ni ba sai kinmin gdy ba ai mn riga mun zama daya,murmushi tayi hadi da bugo ciknta da yake ta famn yi màta motsi"tace "hey! baby wannan motsin fa",...jin kawai tayi Sa'eed ya matse hannunta hr saida tayi qara,yace"tun babyn bai fito bà kika fara dknsa, gsky bxn dauka miki hkn ba,,, ahaaahaahaaa😩to bashi ne yake tamin motsi, yake tamin motsi har inajin ciwo ba😭au wai kuka kike da gaske😄to shi babyn yace me?to ai ni kadn na dakesa fa,kai kuma kamin da zafi😥ynz hr kinji zfin 'yar màtsar da namiki"ai kàsn</p><p> wannan period da muke ciki abu kadan ya isa mutm yaji ciwonsa,eyya sory....... ya fadi hkn ne tare da share mata hwye hadi da bata kiss.</p><p><br /></p><p> 🌹8⃣7⃣🌹Cire towel dinta yayi wai zai ba bbynsa hkr ne,shafr cikin yake kafin yake cewa amma wannan cikin yafi six mnth? Eh ynx yana seven mnth ne,Yace lallai kam,nan yaci gaba da shafr cikin har ya fara wuce guri har yana qoqarin saka bakinsa a mamanta ne sai kawai ta daktr dashi da cewa "ina ce ka yafe ma babynka baxa ka qara Shava,wannan ji da kake dashi ai ya kamata kabr masa tun ynx,,,,tayi mgnr ne a cikin tsokana,kallonta yayi kafin yake cewa"my lady tsokana ko😊sai kuma yayi shiru yana ta kalon kirjin ta,yace kinsan me? Sai ka fada,kinga na daya nononki yana da fadi sosai,.....sai ya zagayi nonon da frcen sa yace ba zai yi saurin fdw ba, na biyu ga taushi kmr auduga .....sai kuma ya matsa nonon yace na uku gashi tsayayye....yakai hannunsa yaja kan.....😊baxn fada ba injin kunya🙈....symh wldh kuwa cewa tayi"kae!kae!Allah sai na rama,da sauri ya bar</p><p> gun yana mata dry hadi da jifa da towel dinsa ya nufi wardrobe dmn saka kynsa, ita kuma sai kukan shagwaba take,tana fadin sai ta rama,yace ni meye dani na ramawa?Allah kaima kanada,,,,,ware hannayensa yayi yace oya zoki rama,tana fadawa jknsa kawai ta rama har sai da tsikr jknsa ta tashi,yace hey 'Yar baby kinjama kanki yau,fadawa yayi da ita samn gado yana rmncing dinta ta ko ina,da qyr ta samu ta dktr dashi tana cewa "meye hk lovely?ksn fa ko break fast ban dora ba,ba ruwana sai nayi, no lovely kaga bamu kadai bane kabri pls nje nyi kaga inyaso after sai kayi,no badai da kika tyr min da sha'awa ta ba,cigaba yayi da aikinsa baji ba gani,ita ko ganin da gaske yake sai kawai tace "Abba!yaya abdallah!,yace au kirnsu kike bari na kama maki,Abba!!!Abdallah!!!da sauri ta rufe masa baki gam sai rarraba ido take kmr mai sauraren wani abu, kafin take cewa,kae lovely qwarai fa ka kira su idn suka jifa?inace so kike suxo su ceceki,kuma ko sunzo kinsan bazasu hanani amsar haqqina ba,sai dai ma su qaramin qarfin guiwa.....yauwa my lady dama inaso na fada maki cewa gobe zamu tafi Oman tare da ke, Abba n abdallah sbd inaso ne aje da Abbah asibiti a duba shi ko Allah zaisa a dace.</p><p> 🌹8⃣8⃣🌹Amazing! am very happy to hair this am very very happy😀tanks a lot my lovely husband n i really Luv u yeah💋hadi da kaimasa kiss,shiko Sa'eed ba qaramin jin dadi yayi ba dajin klmnta sai murmushi yake kafin yake cewa,"wai kinsan har yanxu mtr nan tana asibiti but ashe shi slmn wata balaraba ya samo mata dmn ta riqa kula da ita shi kuma ya dawo ma aikinsa amma yana danyi yana zuwa dmn ynx hk ma yana can, jiya ma nayi waya dashi na fada masa cewa zamu zo,shine yake cemin ya mayi nyr yazo yaja ni mtafi a san yadda za'ayi adawo da mtr sai kawai yji ance na warke......oh my lady 8:30am tashi kije ki hada break fast Allah ma yaso mu yau bamuyi bacciñ safe ba da shiritr tafi hkn,to ai lovely duk kaine,ko?😊eh mana.</p><p><br /></p><p> Byn sungama break fast ne sa'eed ya fita,symh wldh kuwa tabi su abdallah a bangarensu su suna ta fira, lokaci 2 taknji wani frn ciki ya zyrci zcyr ta wai yau ace gata ga Abbanta da kuma yayanta abdallah,zaune guri daya.</p><p><br /></p><p> 9:00pm Sa'eed ne shi kadai a daki yana yi musu parking din kynsu da zasu tafi dasu,byn ya gama ne ya tafi gurin su abdallah shima aka shiga yin fira dashi dmn aikin kenan,tashi yayi yana mai kallon symh wldh ko zata biyoshi dmn shi tun da safe hqr kawai yake amma a matse yake sai dai ya lura hnklinta na gun abbanta, hkn yasa ya fita yaje ya kwanta hr bacci ya daukeshi da dadewa, sannan ta dawo sai da tayi wnk hadi da shirin bacci sannan ta hau gado tare da rungumo Sa'eed ta sa harshenta a kunnesa tana yawo dashi ga alama tashe shi take sonyi, bude idonsa yayi shaye da toka yana mata kallon takaici kafin yake cewa sai ynx kika ga dmr zowa,koshi da baki ji bacci ba da bazki zoba ko,pls lovely kayi hqr.....qarfe nawa ynx?10:30,gud ina ce tun 9:40 na tura maki text akn kixo inason ganin ki,ko kuwa baki ga text din bane?na ganshi, yayi kyau rainin wayo ne yasa kika yi zmnki ko,,,no lovely ba......mtsw! yi min shiru dmn baki da abin cewa,kin fa san cewa a matse nake symh,fisabilillah meyasa kika barni tun dazu ina jirnki wai said a nayi bacci sannan xaki xo ki tashe ni, bayn kisn na gaya miki cewa ba'a tashe ni idn nayi bacci, amma shine kika tasheni, laipi biyu kenan,,,kwanciyr sa kawai yayi tare da juya mata baya,rungumoshi tayi ta baya,tana qoqarin bashi hqr,sai kawai taga ya tashi zaune a hasale tare da cewa "u are very stupid😡matsa daga gurina kuma kar ki kuskura ki sake gigin tabani, kallonso tayi da idanuwnta da suka cika tap da hawaye sai dai basu zubo ba bakin ta na rawa take qoqarin cewa.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [7:01PM, 12/7/2015] Billy giro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹9⃣3⃣🌹Ya dawo da dubansa gun symh wldh da yake dauke da ita,wasu zafafan hwye ne ke zubo masa har suna sauka kan pink lips dinta, umma ce ta katse shi da cewa,ai ba kuka zakayi ba sa'eed kaje da ita a bata taimakon gaggawa,ba mamaki ta tashi,,.nan take Kuwa yaji qwarin guiwa ya fita da ita da sauri,emergency ward ya fara zuwa da ita ajima kadan kuma sai naga za'a shiga da ita theater room,tare da Sa'eed sai faman sauri yake.</p><p><br /></p><p>Umma na gani sai sàfa da marwa take tana jiran ftwrsu, sai ga su abdallah sunxo,suke tmbyr ta abnda ake ciki nan ta fada musu komai, su kuma sukà cemata Allah yasa ayi nasara,tace Amin kafin take cewa abban symh fa? slmn yace "Dnt worry umma dmn ynx hk doctors na a kanshi,kuma in Allah ya yadda zai samu sauqi,sanan yace toni xn tafi bngrn Abbah duk abinda ake ciki xnxo in fada muku,kai abdallah sai ka zauna tare da umma kujira ftwr su Sa'eed,OK to, cewr abdallah.</p><p><br /></p><p>Zaune suke har ksn 2hrs ba lbrn ko guda daga cikinsu,can ksn 30 mnt sai ga Sa'eed ya fito a gajiye ya nufo inda suke cike da dmw.</p><p><br /></p><p>Ba shiri suka miqe tsaye suji me zai ce, yana isowa yace wlh umma Alhmdlh amma fa da qyar muka ciwo nasara sai dai, da Dan da uwar duk sun wahala sosai har dai symh.......me kake nufi Sa'eed?umma ina nufin symh wldh ta haifu kuma da kanta wato ba'ayi mata aiki ba,an samu qrwr da nmji amma bai isa haifuwa ba ynx haka yana a cikin incubator,symh fa?Abdallah symh tana bacci ynx sbd koda ta haifu bata a cikin hayyacinta, shine aka mata allurar bacci amma bata nesa da tashi,,,,Alhamdlh cwr umma,Sa'eed yana qoqarin tmbyr su a game da Abbah sai ga Slmn tafe cikin murna yace"Alhamdlh an shawo kan matsalar but sun ce a samu mutuñe ko biyu hk wadanda ya sani su zauna a kusa dashi.</p><p><br /></p><p>[8:25PM, 12/7/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹9⃣4⃣🌹Koda ya farka, dmn ynx yana bacci but ko da wane lokaci xai iya tashi,gaba dayansu suka dunguma suka je dmn dubnshi,ksn 10 mnt,Sa'eed yace shi zai tafi kar symh wldh ta farka ba kowa kusa,yana gama fada suka fita shida slmn,koda suka je tana bacci abnta sa'eed ya shafi fskr ta yace,huh! wlh slmn my lady ta wahala sosai har saida namata kuka,, ynx na matsu ta tashi naga yanayin ta,, Allah sarki cwr slmn kafin yake cewa ni zn dan fita na dawo, ya fita shi kuma Sa'eed ya samu guri ya zauna sai kallonta yake cike da tausayi,tare da shafr gashin kanta,wyrsa ce tayi qara, ya tashi yaje gun window yana waya, tashinsa keda wuya symh ta fara motsi hade da kiran,umma!umma!!umma!!!ta tashi zaune a rikice,da sauri Sa'eed ya qaraso inda take ya zauna kan gadon,saurin</p><p> qanqameshi tayi tare da boye fskr ta a qirjinsa kmr mai jin tsoro,jkn ta har rawa yake, kafin take cewa lovely ina ne nan?sai da ya jaye mata gashin knta da ya rufe mata fska kafin yake cewa my lady kina a SULTAN QABOOS UNIVERSITY HOSPITAL,a wane gari?OMAN my lady,me ya kawo mu asibiti?kinmnta mnxo dbn wannan mataar,,kallonsa tayi kmr wata tababbiya,tace eh amma kafin mu iso bacci nayi ko?a'a.....No bacci nayi mana tunda har mafarki nayi wai naga umma,my lady da gaske ne fa kinga umma,Itace mtr da muka zo dubi, ashe umnki ce,mtsw lovely meye haka pls ka daina min irin wannan wsn,Wallahi my lady ba wasa nake miki ba,to ina umn take tana gurin Abba shima baya da lpy,me ya faru dashi?,,,,nan ya bata lbrn komai a game da Abba,tana qoqrn tayi magana ne sai mararta tayi wani irin tsinkawa,qara rungumeshi tayi tana wani marayen kuka sbd tsananin ciwo,,,lovely ciwo,ina ne yake maki ciwo?hannuta tasa da nyr ta tabi wurn amma sai taji bazata iya ba ganin take in ta aza hannun ciwn zai qaru,Sa'eed yace marar ki? daga knta tayi tare da cije lebe tana yarfi da hannu,,,hannunsa yasa a cikin rgrta zai shafi marar,,.riqe hannun tayi tana kuka tace lovely kar ka taba ciwo,,,ba ciwo my lady,Allah akwai😭rungumo ta yayi ta baya yace"oya to musa hannun a tare,sannu a hankali ta aza hannunsa akn mararta, koshi saida ta dauke cknta,har ksn mnt 5 yana shafa wurin,yana mata addu'a sai kuwa ta rage jin zafi, tace cikin marairaicewa lovely ina so na tafi gurin su umma,kallon ta yayi dmn ya zaci babyn ta xata tmby, anan ya fhmci har ynx kenan bata ma san ba baby a jiknta ba,kafin yake cewa "No my lady ba kya ganin yanayin da kike ciki,kibari ai zatazo,,fashe masa da kuka tayi tace ni ka banni in tafi inaso naga Abba,,,ok to nji amma sai kin sha tea, tashi yayi ya hada mata tea mai kauri ya bata.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [1:21PM, 12/8/2015] Billy giro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊0814064366</p><p>🌹9⃣5⃣🌹Ta karba tana sha har saida ta shanye kaf sannan ta ajiye cup,tana mai cewa wow, lovely wai meyasa ciki kesa ci haka,tyi mgnr ne tana shafa cikin sai taji wayam,wani irin fdwr gaba taji tana ci gaba da Shafar cikin, kmr ta duba sai kuma tafasa dmn tana shakkun taga ba cikin, hkn yasa ta kalli Sa'eed a tsora ce, tace lovely ina babyna?ya danji dry ganin ynda ta rude amma ya sha tokà yace,wane babyn?Babyn da ke cikina mana, Allah ba komai a ciki😢taba ma kaji, dry yake sosai kafin yake bata lbrn yanda akayi,pillow ta jefa masa a cikin shagwaba, ya capke pillown sannan yace kinji ki har da kuka ba baby,,,to ai dole ne ksn ynda na wahala da renon shi hln😔,hancin ta yaja yana murmushi yace oya muje kiga babyn.</p><p><br /></p><p>Byn sun dawo ne take cewa ashe babyn ma yana dan da girmnshi,Eh ina ga ai bazai ma dauki lokaci mai tsayo ba,za'a ftr dashi a incubator.</p><p><br /></p><p>Kallonshi tayi tace Lovely bacci nake ji sosai, to yi baccin,yce hkn ne tare da rungumeta yana Shafa bynta har bacci ya fara dauknta, sai kawai ta zbra kmr wacce aka tsakara tace,lovely muje naga umma da Abbah,suna qoqarin tashi sai sukaji sallamar su Abbah.</p><p><br /></p><p>Da sauri symh wldh ta sauko kan bed,sai kuma ta dakata tana kallon umma tana tunanin shin wai da gaske ummanta ce kodai mai kama da ita ce dmn a iya sanin ta Ummanta ta rasu...kmr Umma taji me take cewa tace symh zo nidai ce ummanki,tare da ware hannayenta da gudu symh wldh ta fada jknta tana kuka ta dago knta ta qara kallon umma ta sake fadawa jknta ta rungumeta sosai sannan kuma ta koma jkn Abbanta shiko sai lallashinta yake sañnan sukà zauna.</p><p> </p><p>Umma ta kalli slmn tace inaso ka basu lbrn yadda akayi,ka kbtr dani.</p><p> Nan take slmn ya basu lbrn yadda akayi,..... symh wldh,Abbah, Abdallah,sai da suka nisa dajin abn al'ajabi,</p><p>Sannan Abba ya fara da cewa nikuma a rànr da zamu tafi Egypt na gama shiri kenan sai aka kirani a waya ana son gani na a waje,</p><p>ina fita naga wasu mutane ckin shiga ta mtnc kmr mtnen kirki,</p><p>da isa ta ko gaisawa bamuyi ba suka fesa mn wani abu a hanci,</p><p>Ya ksnce komai bana iya yi amma ina ganin abnda ke frw,</p><p>Sani a mota sukayi suka tafi dani wrn wasu ruwa masu ywn gske,</p><p>sai da suka min dukn tsiya kafin suka jefani a cikin rwn(Rafi) suka tafi abnsu,inaji ina gani amma bana iya taimakon kaina,</p><p>Nayi ksn mnt goma a rwn,sai kawai rwn sukà banka doni waje da qarfi,tun daga wannan lokaci ban qara sanin inda nake ba sai a yau.</p><p><br /></p><p>[2:37PM, 12/8/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹9⃣6⃣🌹Sai kuma yace, na rasa gane wanda yasa ayi min wannan aiki,.....bakowa bane face hjy bintu, cewar umma....Abba yace hjy bintu😳?... Koda yake ba mamaki tunda tasa ayi miki haka, to ni kuwa meye dalilinta nasa a kasheni, tunda ke kishi ne a tsaka ninku? Dalili kuwa shine dkyr ka take so ta mallake ita kadai,</p><p>dmn akwai wata rana da na tafi bngrn ta, ina batun shiga falonta sai nji tana fadn abnda tasa ayi maka,</p><p>Sai dai tji haushin mutanen da tasa su kashe ka,</p><p>Sbd sunce mata basu da tabbacin ko ka mutu ko baka mutu ba,</p><p>amma sun tabbata bazaka rayu ba</p><p>sbd baka iya tabuka komai</p><p>Duk da hk sai taji hkn baiyi matà ba,na rashin tabbacin mtwr ka</p><p>Dn hk tace su koma su nemo mata gwrk</p><p>Koda sukje basu ga gwr kaba, amma sukace mata tabbas bazaka rayu ba,dole kana a mace a duk inda Kake,</p><p>ni kuma anan nji jiki na yabani cewa kana raye</p><p>sai dai kuma kafin na bar gun na qara jin wani mummunan lbr wanda ya tyr min da hnkli matuqa har na ynke jiki na fadi</p><p>wato lbrn shine....sai kuma ta kalli Abdallah,cike da tuhuma wanda hkn yasa abdallah hntr ckin sa ta kada</p><p>Sannan tace Ashe Abdallah ba jinin mu bane!gabaki dayansu suka miqe tsaye suna masu kallon umma sannan suka kalli Abdallah,</p><p>Abba yace kmry😳mamn symh? </p><p>Ina nufin shi ba danmu bane a gdn marayu hjy bintu ta daukoshi</p><p>ta dauki dnmu ta aje muna abdallah</p><p>Sbd boknta ya fada mata cewa sai ta cnz muna da, zata mallaki dkyr ka</p><p> Innalillahi wa inna'illahir rajiun!!, cewr su dknsu</p><p>Sannan taci gaba da cewa ada har naso naga laifin Abdallah</p><p>na qin fada muna shi ba danmu bane,ko kuma ya tmbye mu,kafin yaje asbti,</p><p>Sai na tuna cewa akwai boka a cikin hrkr hkn yasa na masa uzuri</p><p>Sai kuma nayi tunanin na fada ma symh akn kr ta sakanknce cewa Abdallah yayanta ne,</p><p>dmn Ita ma nji ta na son hada mata wani mgntr kuma har da sa hannunsa a ciki,</p><p>Byn an sallamoni da asibiti nyi qoqarin fada mata</p><p>Sai ga hjy bintu tashigo tace min idn na kuskura na fada ma</p><p>Symh abnda nji zata sa a kashe ta </p><p>amma idn ban fada mata ba to tyi mn alqawrin xata qyale symh wato baxata kasheta ba kuma abnda tasa ayi nyr yi mata shima ta fasa</p><p>ni kuma nsn tabbas xata iya kasheta,hkn yasa na fasa fada ma symh </p><p>.........Ba abinda ta fasa akaina umma😭dmn wlh umma byn kin rasu tasa ayi min fyade, </p><p>nan ta basu lbrn abnda ya faru da ita hr zuwa rywr ta dasu Sa'eed.</p><p><br /></p><p>Sannan ta juya gun Sa'eed tace yaya sa'eed nsn cewa xaka dauke ni a matsayin mayaudry na boye maka da nyi akn alaqata da hjy bintu </p><p>Wlh umma ce tace kar na fada maka</p><p>kuma danaji ynda ka tsani hjy bintu zaka iya rbw dani hkn yasa naci gaba da boye maka </p><p>Sbd bana so na rabu dakai😭</p><p><br /></p><p>Kallonta yayi idanuwnsa cike da qwalla,yace No my lady ni a gsky bxn iya.......</p><p><br /></p><p><br /></p><p>[7:32PM, 12/8/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹9⃣7⃣🌹Bazaka iya rayuwa dani ba ko😭</p><p>girgiza knsa yayi </p><p>yana ji kmr ya rungumeta</p><p>Ko zai samu sassaucin</p><p>abnda yake ji</p><p>sai dai ba hali,kafin yake cewa</p><p>ba hk nake nufi ba my lady ina nfn bxn iya ryw bake ba</p><p>domin ke ta dbnce hr abada muna tare my lady ina sonki so na</p><p>haqiqa dn hk kar ki taba tunanin zn iya rbw</p><p>dake,qara rungume Abba tayi sbd tsananin farin cikin da ta samu kanta a ciki.....Abba yace kai kuwa Sa'eed meyasa ka tsani hjy bintu?kallonsa yayi kafin yake bashi lbrn abnda ta musu,</p><p><br /></p><p>In taqai ce muku anan suka taya junansu jimami, sannan suka ynke hknci idn suka koma Nigeria zasu sa akamata dmn Abdallah yagaya musu inda take da kuma cewa tasan inda muhseen yake,</p><p><br /></p><p>Sannan ya roqe su dasu su yafe mishi abnda ya musu,nan Abba ke cewa babu komai Abdallah mun yafe maka dny da lfr dmn na tabbata da akn hayyacinka kake da bakayi muna haka ba, kuma har ko yaushe kai danmu ne,kar ka taba tunanin zamu rabu.</p><p><br /></p><p>Kuka yake sosai kmr qaramin yaro tashi yayi ya rungume Abba yana gdy sanan ya rungumi umma ya tafi da hnxarin sa zai rungumi symh wldh sai kawai ya tuna cewa ynx fa ba qanwarsa bace,dn hk hrmn ne ya rngmeta, gata kuma mtr aure,</p><p>Symh wldh dake tsaye tana kallonsa sai rusar kuka take sbd tausayinsa da taji, bata san lokacin da ta fada jiknsa ba tana kuka sosai shima haka,ksn 5 mnt suna a haka,</p><p>can ta tsinkayo Sa'eed sai dallah mata harara yake ba shiri ta janye jknt daga na abdallah,nan Sa'eed ya fita ba tare da yace komai ba.</p><p><br /></p><p>Ba shi ya dawo ba sai byn 2hrs tana zaune ita kadai a daki ya shigo, da sauri ta fada jknsa tace lovely duk kishin ne tun dazu kaqi ka dawo,my lady am so sry hk kawai nji wani irin kishi da kika rungumeshi, eyya yaya abdallah ne fa, ni wlh duk ya bani tausayi😭shi ke nan ba'a san iyayensa ba,share mata hawaye yayi yana bata hqr, ksn 20 mnt, amma ta kasa daina kuka hkn yasa ya hade bknsa da nata ksn 10 mnt suna a hk sannan ta samu natsuwa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: [2:36PM, 12/6/2015] Billy giro😊: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>🌹SIYAMAH WALIDAH🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p>🌹9⃣1⃣🌹Symh wldh na sa qafarta, taji bugn zcyr ta ya qaru har saida abinda ke ckn cikinta ya juya, hkn yasa tayi saurin riqo hannun sa'eed ta jimqe sosai,tare da rintse idnta tana numfashi sama2 hr yana hngo hkn, yace yadai my lady?no ba komai,are u sure?surely,,,,sannan suka qarasa daga ciki,sun sami mtr a kwance ta juya bynta,sbd hk bayanta kadai suke iya gani, sallamar su ne yasa take qoqarin tashi zaune, suma su Sa'eed suna qoqarin zama akn kjrun da ke gefe,tare da kallon mtr da take qoqarin gyara zmnta da kyau,gabadaynsu saida suka shiga wani yanayi kmr haka:</p><p><br /></p><p>Abdallah: 😳mamaki,tsoro da kuma tmbya.</p><p><br /></p><p>Abbah: kallonta yake ya dafe Kansa, yana so ya tuna wani abu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Symh wldh:Tsananin mamaki da tsoro na qarshe, da kuma tambaya gashi kuma ita bata zauna ba, bata kuma tashi a tsaye ba, tana riqe da hannyen kurjera.</p><p><br /></p><p> Umma:kallonsu take su duka uku,wato Abbah,abdallah,symh wldh,fskr ta tana cike da tsananin mamaki,da kuma tambaya.</p><p><br /></p><p>Salman:Murmushi ko murna ko mgna yake son yi ko kuma jiran yake yaji me zasu ce,na rasa ganewa.</p><p><br /></p><p>Sa'eed:👀kallonsu yake fskr sa cike da alamar tambaya.</p><p><br /></p><p>Umma ce ta fara da cewa"Abban Symh wldh!!😳</p><p>wanda hkn ne yasa slmn da sa'eed suka shiga mamaki ganin cewa tayi magana.</p><p><br /></p><p> 🌹9⃣2⃣🌹Miqewa tsaye symh wldh tayi ta nufi gurin umma tana son tace wani abu sai kawai ta fara jin juwa, hkn yasa ta dan dafi gefen kanta,sai kuma ta saki jiki zata fadi, Sa'eed ne ya lura da hkn yayi saurin tarbo ta, ta fada jiknsa, abin mamaki kuma sai yaga abinda ke cikin ckinta yana motsi haniqm kmr wanda zai burme ftr ciknta ya fito.</p><p><br /></p><p>Da sauri Sa'eed ya dafi cikin ya kuma kalli symh wldh nan ya fahimci bata sheda, hkn yasa cikin ke motsi sosai,cikin tsananin rudu yake jijjigata yana cewa"my Lady don Allah ki tashi!kar abunda ke ciki ya mutu,my lady pls!kitashi,bakinsa yasa akan hancinta yana jawo sheda amma ina tayi nisa,slmn ne ya miqo masa ruwa, ya yayyafa mata amma ko alamar motsi batayi ba.</p><p><br /></p><p>Ana cikin hk ne shima Abba abinda yake ji ckn kansa sai qaruwa yake, kmr mai son tuna wani abu amma ya kasa, sai dai ba wanda ya lura da hkn domin hankalinsu na gun symh wldh.</p><p><br /></p><p>Tib!suka ji faduwr mutum, slmn da adallah ne suka je gurinsa cikin sauri suka kamashi.</p><p><br /></p><p>Sa'eed da umma kuwa,na kan symh wldh suna nasu qoqarin ganin ta farfado, amma abin ya ci tira gashi kuma har abinda ke cikinta ya fara rage motsi.</p><p> </p><p>Sa'eed ne yaga abin ba mai yi bane yace kaga slmn kira doctor a tafi da Abba a duba shi nikuma zn tafi da symh wldh na duba ta.</p><p><br /></p><p>Suna fita shima ya dauketa zai fita da ita sai kawai yaji ta motsa tare da sakin yr qara kadan ta dafe qasn cikinta, da qyr ta iya furta lovely ciwo nakeji sosai a marata, lovely pls help me,aza ta yayi a bisa gadon da umma ta tashi, yace ok to bari inazuwa,yace hakn ne a rikice da alama bai ma san Inda zai je ba, saurin riqo hannusa tayi har saida yaji zafin riqon,tare da cewa wayyo Allah,lovely marata, mutuwa znyi don Allah ka taimaka min,No my lady bazaki muta ba,sai kawai yaji tace innalillahi wa innailaihir rajiun! da qarfi ta furta hkn tare da sake masa hannu, sai komai nata ya tsaya cak, bata motsi cikin baya motsi,yana ganin haka ya dauke ta da sauri zai bar dakin sai ya hangi gadon duk jini ne cak ya tsaya yana kallon gadon, nan take yaji hnkalinsa ya qara tashi jknsa kuma ya mutu. </p><p><br /></p><p> Nima nji nawa jkn ya mutu dole na tsaya.</p><p><br /></p><p>Written by Bilkeesu giro💗</p><p>[10:31PM, 11/21/2016] Rynt: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p> 🌹SIYAMAH WALIDAH!!!🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Na Bilky giro😊08140674366</p><p> 🌹1⃣0⃣0⃣🌹Symh wldh ce dauke da tray da kuloli akai, zata je masaukin Sa'eed cikin qayatacciyar kwalliya tayi kyau na ftr hankali,tana cikin tapiya sai kawai taji an bankade ta har saida trayn hannu ta ya fadi ita knta ma batun faduwa take,sai jin tayi ta fada hannun mutum koda ta duba taga Sa'eed ne ajyr zcy tayi tare da qura masa idanunta masu kashe mishi jki ko yaushe sannu a hnkali yake ida tallabota ya manna ta a qirjinsa yana mata murmushi, lumshe ido tayi hade da sake mishi murmushi har saida fararen hqrn ta tas suka bayyana masu dauke da yr siririyr wushiryr,hade goshinsu yayi har hanccinsu na shafr juna, sun jima a haka suna kallon juna,qoqarin hade bknsa da nata yake hr ma lips dinsu sun hadu,sai kawai slmn yayi gyaran mrya da sauri symh wldh ta jaye jknta, kanta qasa tana gyara mayafinta,slmn da rqy sai dry suke musu,</p><p><br /></p><p> Sa'eed yace au knya kikaji ai sune zasu ji knya, bamu ba kuda akn gujen2 soyayyr kune kuka bangaje min mata, kuma kukayi tsaye kuna kallon mnya na soyewa,bai tsaya jin me zasu ce ba ya dauketa cak tare da kallon slmn da ya saki baki, Sa'eed yace inkayi zcy kayi aure😜 sannan ya shiga da ita cikin dakin ya aje ta bisa gado yana yawo da hànnunsa akn qirjinta, daya ke rabin mamanta,duk a wàje yake, sa hannunsa yayi a cikn</p><p>rgr yana yawo dashi tare da hade bakinsu lokaci mai tsayo sannan ya cire bkns yana mai da numfashi ya kalleta da idanunsa da suka cnx kala yace my lady pls I need ur help kuma don Allah kar kice a'a,No lovely baza ayi haka ba kayi hqr har na koma pls,kuma ksn fa biki ake,kmr yayi mata kuka yace my Lady knsn fa rabona dake tun kafin muje omn,kuma don ana biki sai akace baxaki bani haqqina ba,gsky ni bxn iya hqr ba, jawota yayi yana rmncng dinta ba ji ba gani nan take ta fita hayyacin ta dmn har ya rabasu da kyn jknsu,yana qoqarin kashe wuta ne ta jaye shi daga jknta da qarfi tana maida numfashi shima hk kallonta yayi yaga har idanunta sun cnxa kala da qyar yace kinga kibari muyi mana tunda muna bqce da junanmu,lovely znje nayi feeding din Asim kaga har nonon ya fara zba,Asim sunan da aka sama yrn kenan,,binta kawai yayi da kallo har ta shirya ta fita, yana nan kwance jiki mace yaji anyi knocking, sa kynsa yayi sannan ya bude,abnci ne ta aiko masa dashi sbd wncan ya zube.</p><p><br /></p><p>[6:58PM, 12/10/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹1⃣0⃣1⃣🌹</p><p> 🌹🌹🌹🌹</p><p>Byn wata biyu da frwr hakn symh wldh ce ke shayarda Asim sai kallonsa take cike da so, yayi tubul2, gashi sak da mhfnsa, mai kyau dashi,harma yaso yafi mhfnsa kyau,</p><p><br /></p><p> Sa'eed ne yazo yana cewa na kamaki sai kallona kike ashe ina miki kyau haka har da wani murmushi,,,kallonsa tayi tace waye ya kalle ka?ai idn kika kalli Asim tmkr kin kalle ni,kinga mun miki wayo baki da mai kama dake, au haba lallai kuwa xnyi zcy na haifo 'yata mai kama dani sak,daukr Asim yayi ya shimfide a kn bed dinsa,yana mai cewa gamu gani sannan ya dawo grn ta ya dauke ta cak sai kn bed yace yau xn nuna miki rashin tausayi kmr yadda kika nuna min,....ni kuwa me nayi na rashin tausayi?2month da kikayi a gd yau xn debe su a jkn ki, dry kawai tayi tace to muje dai muyi wnka dare nayi,</p><p><br /></p><p>Suna fitowa daga wnka ko mai bai bari suka Shafa ba ya dire ta bisa gado yana shfr jknta ta ko ina harshensa yasa kn wynta yana lasa kafin yake zuwa gun qirjinta ya fara zame towel dinta a hnkali harshensa yasa yana lasar qirjinta ta koina sannu a hnkali yake zuwa da harshensa qasa har gun cibiyr ta yana wasa dashi a cikin ramin cbyr har yakai gun qasan marar ta Ita kuma sai numfashi take sama2 kafin take fara maida masa martani har suka lula dnyr ma'aurata bashi ya barta ba har saida yaji tana kukan wahala sauka yayi kan jknta ya rungume ta yana ta lallashinta sannan sukayi wanka suka kwanta bacci.</p><p><br /></p><p>Haka rywr su taci gaba cike da so da qauna, wanda suma su rqy da slmn,ihsan da abdallah,mami da muhseen soyayyar su tayi qarfi har iyaye sun sani hkn yasa aka sa ranr aure. </p><p><br /></p><p>Yaune aka daura aure, ko wacce aka kaita gdn mijinta amma mami da muhseen zasu wuce Egypt sbd karatun ta shima muhseen akwai course dinda yake son yi a can.</p><p><br /></p><p>Sa'eed ne a falo yana kallon labarai sai kawai yaji kukan Asim sosai, da Sauri ya haura sama zuwa dakin symh wldh. kallon ta yayi cike da mamaki kwance take abnta daga ita sai dan wani gntn wndo iya cinya rgr kuma baxata wuce cibi ba ta pake gashin kanta guri daya.</p><p>Daukar Asim yayi da yake ta famn kuka kafin yake cewa my lady bakyajin yrn nan nata fmn kuka?,, inajinsa sai akayi yaya,bai ce komai ba,da yake ysn fushi take dashi,</p><p>miqa mata Asim yayi yace yi hqr ki shayadda shi kinji, bxn shayar dashi ba,sry pls my lady.... ka daina ma whlr da kanka dmn ni bxn qara bashi nono na yasha ba mudin baka bari na zbr da wannan cikin ba.</p><p><br /></p><p>[9:23PM, 12/10/2015] Billy giro😊:</p><p> 🌹1⃣0⃣2⃣🌹</p><p>🌹🌹🌹🌹🌹</p><p>Sosai rnsa ya baci sbd abnda tace amma ya matse yace pls kinga yrn nan watansa bakwai bai isa yaye ba kiyi hqr ki qara masa ko wata daya ne kinji,wani ubn tsaki ta buga ta gyara kwnciyar ta, tace naqi in byr din,iya hasala ya hasala ga Asim sai kuka yake bai san lokacin da yaja gashin kanta ya daka mata tsawar da saida ta tashi zaune bata shirya ba,Asim kuwa kuuwa yayi, ya qanqame sa'eed,sannan yace kitashi ki bashi ko kuma wlh ki gane krn ki,jiknta na rawa ta amshi Asim tana bashi nono, hwye sai zry suke a kncnta tana gama bashi ta shinfide shi sbd yayi bacci, ta fada ruf da ciki kn gado tana kuka sosai,Sa'eed ya kalle ta cike da tausayi kafin yake rungumo ta yana Shafa bynta yace my lady ya isa hk,cikin kuka sosai har magana na katse mata tace ya...ya sa'eed don Allah kbri na cire cikin nan, meyasa my lady?sbd kaga nayi saurin samu pls😭kabri na cire,qara matse ta yayi a jknsa yace my Lady ki gode Allah dmn wasu ncn nason Allah ya basu amma basu Samu ba,ke har ma ya baki,ko kina so ki nuna ma Allah ba kya son kyautr da yabaki ko kuma kina so ki nuna yayi saurin baki, saurin girgiza kanta tayi tace a'a ba haka nake nufi ba ina duba ma Asim ne,indan Asim ne karki damu kinji,sannan kika sani ko ki samu baby girl dinda kikeso, ko bakya so?tace inaso tare da share hawayenta ta qara rungume shi,,,yauwa my lady ya dauke ta cak yana juyi da ita kmr yr baby yace that's y I Luv u,bata san lokacin da ta fashe da dry ba,daga nan kuma salo ya znxa suka Lula dnyr ma'aurata.</p><p><br /></p><p>Byn shekara daya da wata 5 da frwr hkn symh wldh na gani da yr baby mai kama da Ita sak sai wasa take mata tana bata kiss ta koina tana kuma daga ta sama, </p><p><br /></p><p>Sa'eed da ke zaune yace um um sai kace bakiyi kukan samn cikin ta ba,ta hararesa da wasa tace lovely😡a daina tuna baya,dry yake sosai yace kinga yadda kika fuske kuwa har nji na qara sonki sosai,kallonsa tayi dmn ta zaci wani abu dbn zaice tayi murmushi tace nima ina sonka lovely.</p><p><br /></p><p>Asim ne yazo da gdnsa yace daddy muje yawon da kace, OK kira ummnka mutafi.</p><p> Zasu shiga motane Asim yace mommy nida ilham zamu zauna a baya, kallonsa tayi tace um um fa kar ka kada mn 'ya wlh,...a'aah mamn ilham dai😄Abban Asim bana so😀hk suka shiga mota suna dry</p><p> Kan hnyr su ta dawowa ne symh wldh ta tsinkayi wata mata tana bara bisa keken guragu, da sauri tace pls lovely stop d car,yana tsayi tace my God! hjy bintu ce fa cike da mamaki da tausayi tayi mgnr kallonta yayi yace tabbas itace,ya akayi haka lovely?oho may be kudin ta sun qare kan jinya kinga ynx ma wasu quraje ne da ita har quda na byr ta,,,, kudi masu yawa ya debo zai fita ya bata, symh wldh tace tsaya min muje, suna zuwa ta gane su nan take ta fara kuka,kudin suka miqa mata tana kuka tayi gdy suka shiga mota cike da tausayi,sa'eed yace na tabbata hjy bintu bata taba tunanin rywr ta zata ksnce haka ba,shine ake son mutum ya ksncr mutumen kirki a rywrsa to inshaAllah baxaka walaqanta ba.</p><p><br /></p><p>Ya kalli symh wldh da hawaye ke qaqrin zubo mata ya rungume ta yana bata hkr tare da bubbuga bynta, daga nan kuma suka hade bkinsu suna rywr masoya.</p><p> Nidai billy giro nace ba ruwana in yara suka ganku dmn fa suna a seat din baya. </p><p><br /></p><p>ALHAMDULILLAH</p><p>Na gode ma Allah da yabani ikon qare wannan littafi lpy. MASHA ALLAH</p><p><br /></p><p>Godiya ga masoyana.</p><p> Ayi hqr da kura kuran da nayi.</p><p><br /></p><p>Godiya ta musamman ga my lovely sister Zainab(zee giro)the Siyamah WalIdah's Mother N MUHSEEN.</p><p><br /></p><p>Love u my niece SIYAMAH WALIDA💋</p><p> N</p><p>Luv u my family n my frnds.</p><p><br /></p><p>Written By Bilkeesu giro💗</p><div><br /></div>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-68202251312978172332021-01-24T06:37:00.002-08:002021-01-24T06:55:59.709-08:00DA SANNU COMPLETE SABBIN HAUSA NOVELS<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-GQjOqPfiq1Y/YA2FwOg5E-I/AAAAAAAAJgo/T_Jovz1DqV4eO-paWwYWMJY47LT4RUS-ACLcBGAsYHQ/s2048/DA-SANNU.jpg" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="DA SANNU COMPLETE SABBIN HAUSA NOVELS" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-GQjOqPfiq1Y/YA2FwOg5E-I/AAAAAAAAJgo/T_Jovz1DqV4eO-paWwYWMJY47LT4RUS-ACLcBGAsYHQ/w320-h248/DA-SANNU.jpg" title="DA SANNU COMPLETE SABBIN HAUSA NOVELS" width="320" /></a></div><br /><p> GODIYA</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Godiya ta tabbata ga Allah ubangijin halitta daya bani damar Rubuta wannan littafi, tsirada aminci su tabbata ga Shugaban'mu Annabi Muhammadu (S.A.W)</p><p>Da iyalan gidan sa Da Sahabbansa, da wayanda suka bashi gaskiya har zuwa Ranan Alkiyama Amin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p> SADAUKARWA</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Na sadaukar da wannan littafin ga iyayena "Alh Umar Muhammad da "Hajiya Lauratu nagode kwarai da tarbiyar da kukai Mani ubangiji yasa kugama da duniya Lafia Amin.</p><p><br /></p><p>Wannan labarin kagaggene bawai yafaru da gaske bane, saidai nayi shine akan irin "mutanan nan masu saurin yanke hukunci batare da bincikeba, nasama wannan labarin Nawa suna DA SANNU dafatan zaya fadakar.</p><p><br /></p><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p>Sannan wannan labarin ina kirane ga masu kudi dasuyi koyi da halin irin Na Alh Ya'u Na KaKa, suka sance masu taimakama talakawa kamar yanda wannan bawan ALLAH yayi acikin wannan littafin</p><p>Wannan shine littafina' nafarko inafata zaya fadakar daku,kuma ban rubuta shi doncin zarafin wani ko wata KO kuma wasuba, saboda haka duk Wanda yaga halayya ko kuma suna sundace dashi to arashine ba dashi akeba nagode.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_edited by Zainuddeen Zain_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>-------------------------------------------</p><p>® *~PEN WRITERS ASSOCIATION~*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PEN: THE STRONGEST WEAPON_</p><p>-------------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bismillahirramanirhim</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mama! Mama!! Mama!!! Ina mama kam tayi nisa domin kuwa ko motsi batayi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tafdijam! Babbar magana... wai Dan sanda ya ga gawar soja. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ai kuwa tuni Abdul-jabbar ya yi kukan kura ya chakumi wuyan Dan siririn nurse da sai rabon idanu yakeyi a firgice, yana cewa "ai wallahi tun da Kayi sanadiyar mutuwar maihaifiyata, to kai ma sai nayi Ajalinka. Dan iska kawai sai na kashe ka".</p><p><br /></p><p><br /></p><p>ko kafin jama'a su kawoma Dan siririn nurse dinnan agaji, tuni ya fara jin kamshin mutuwa, domin kuwa bakaramin, shake sa Abdul-jabbar ya yi ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dakyar wasu nurses su hudu suka kwache shi daga hannunsa, daya daga cikinsu ne yace "lafia me ke faruwa ne cayode?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dan siririn nurse da aka kira da suna Cayode bai samu damar bayar da amsa ba kasancewar yanachan yana kokarin nemo numfashinsa da yake Neman kubucewa daga gareshi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar ne cikin tsananin bacin rai yace "ka duba abun da ya yi Mani", ya nuna musu in da Mama take kwance magashiyyatan</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Da sauri suka hada baki suka ce "subhanallahi! Ai mu bamu kula ba sam, ya akayi haka ta faru?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p>Gaba dayansu suka nufi in da take kwance. Abdul-jabbar cikin kidimewa bayan ya daga hannunta ya juyo ya kalle wadanda sukayiwo ca a kanta, yace "ta mutu"</p><p>💞💞💐💐💞NU"</p><p>💐💐💞💞N</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐SA</p><p>💞DA 💞</p><p> Page💐2</p><p>💞DA" 💞</p><p>💐💐SA</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐💞💞N</p><p>💞💞💐💐💞NU"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐 *MEENAT UMAR FARUQ* 💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>```Dedicated to my lovely sisters may aljannah be your final destination with other Muslims ummah, Ameen.```</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_edited by Zainuddeen Zain_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>-------------------------------------------</p><p>*~PEN WRITERS ASSOCIATION~*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PEN: THE STRONGEST WEAPON_</p><p>------------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar ya zabura tareda cewa "ta mutu KO"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya nufi Cayode yace ba fa zan yardaba, har ya fara cakumar wuyansa da niyyar ya kai masa wawan naushi, sai wani yace "Kai Ina fa ganin kamar bata mutu ba".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Musa yi sauri ka kira doctor" daya daga cikinsu ya fada.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sauri Musa ya nufi office din har da sassarfa, sai ga su tareda doctor, da sauri yace "A'uzubillahi! Me yasa me ta"? Sukace "wallahi bamusani ba", daya daga cikinsu yace ina ganin kamar ta mutu fa", doctor yace "what"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Da sauri ya tsuguna gabanta tareda daga hannunta, yai shiru, cen ya mike yace "Musa Kai maza ka dauko(stretcher) ayi maza a kaita emergency room, oya please hurry up"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yace "OK sir", da sauri yaje ya dauko, har da hadawa da gudu suka nufi emergency room da ita, doctor na bin su a baya shima Abdul-jabbar yana biye da su, yace "don Allah doctor hide nothing from me, is she dea"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ba tareda doctor ya kalleshiba yace "no bata mutu ba", a dai dai lokacin da suka isa emergency room din, har doctor zaya shige room din sai ya juyo, ya dafa kafadar Abdul-jabbar yace "don't worry we will do the best we can to see her alive" yace "OK", da sauri doctor ya shige room din.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yabar Abdul-jabbar tsaye cikin tsananin tashin hankali da tunani, a ransa kuwa cewa yake "shin idan har Mama ta mutu yaya zaiyi"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ji yayi gabansa ya fadi, da sauri ya furta "innalillahi wa'inailaihi raji'un!", yace "ya ubangiji ka ba Mamata lafiya Ameen".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ji yake kirjinsa yana mashi zafi kansa sai sarawa yake, abubuwa sunyi mashi yawa zucci-zucci sai kai da komowa sukeyi a kansa. Ya kasa me ke yi masa dadi,ga matsalar Humaira Wacce kanta ne ya dawo Nigeria, Ga shi tun bai je ga warware matsar ba sai kuma ga wata ta bullo, duk ya rame yayi fayau dashi kamar yayi shekara yanayin jinya,</p><p>Shiru tsawon wani lokaci yana tunani, a ransa sai ya saka wannan ya kulla wanchan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cen sai ga doctor ya fito,</p><p>kafin doctor ya karaso gurin, Abdul-jabbar ya kare mishi kallo, Dogo ne yanada kiba kadan Wanda takarama tsayinsa kyau, wankan tarwada ne bai cika dariya ba yana saye da farar T-shirt me dogon hannu da bakin wando hannun sa yana rike da lab court, Yai ma Abdul-jabbar nuni da hannu alamar ya biyo shi da sauri, yabi bayanshi zuwa office din, mai girima ne an shinfide shi da carpet, akwai Kujeru masu laushi guda biyar da suka kewaye office din, sai wasu kananan kujeru dake gefe, table din me girmane cike yake da takardu,</p><p>Akwai laptop akai sai kuma wani Dan karamin katako me dauke da sunan shi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya kalli Abdul-jabbar tareda zare dan karamin glass din dake manne a ldonshi yace "Bissimilla have a sit,"</p><p>Abdul-jabbar yazauna a hankali, tareda karanta Dan Karamin katakon Da akayima rubuta da manyan baki kamar haka, DOCTOR I. S. G. Ya tsurama Abdul-jabbar ido yace "munsamu ta farfado saidai nayi Mata alluran bacci saboda tadan samu Hutu, nan da awa daya zata farfado normal insha Allahu kar ka samu damuwa kaji KO, Saidai wane irin abu ne kai mata Wanda ya sa ta tsananin firgici, har ya sa ta tayi dogon suma haka?" </p><p>A dai-dai wannan lokacin ne aka turo kofa aka shigo office din, Dan siririn nurse din nan ne, hannunshi rike da (files) suka juya gaba daya suna kallonshi.</p><p>Yayin da Abdul-jabbar yake yi masa kallon tsana, shi kuma doctor kallon tambaya yakeyi masa, Cikin bacin rai Abdul-jabbar yace "wannan Dan iskan shi ne sanadin faruwar komai", doctor yace "kamar ya fa"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Muna tsaye muna jiran Result sai ga shi ya kawo yace sai sakamako yanuna cewa ina dauke da kwayoyin cutar nan me karya garkuwan jiki,</p><p>wai kanjamau shi ne ta fadi ta suma".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Doctor yace "what"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Eh! Haka ya fada,</p><p>Yakalli Cayode da yai tsuru-tsuru da idanu kamar makaryaci.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin tsananin takaici doctor yace "are you stupid </p><p>Shi ne joy chukuma"? Yayi tsuru da ido ba tareda ya bada amsar tambayar da akai masa ba, </p><p>Yadaka masa tsawa "Ina magana kayi mini shuru". Ya kalli Abdul-jabbar yace "kai ba sunan ka Abdul-jabbar </p><p>Ahmed ba"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya ce "eh! Sunana kenan", ya kara kallon Cayode yace "ba nace ne ka kira shi ba Shi ne kaje Kai abun da ban sa ka ba ko? Saboda tsabar iskanci salon kabatawa mutane aiki ko"? Cayode zai yi magana doctor yace "shut up you stupid, and give me the files"ya mika masa hannu alamar ya bashi files din, Cayode ya mika masa ya karba yace "oya get out of my office, mahaukaci kawai", cikin sauri ya fita tareda cewa "sorry sir".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar ya bishi da harara yace "banza kawai Wanda baisan Aikinsa ba",</p><p>Doctor ya maida hankalinsa ga Abdul-jabbar yace "don Allah Kayi hakuri, wannan ba shi ne result din ka ba sakarci ne kawai irin Na Cayode, nace masa ne fa ya kiraka, Sha-sha-sha ne aikin da aka sashi daban Wanda yaje yayi daban, please sorry".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yace "it's OK, dama dai Mamana nake ji", "kar ka damu zata farfado ai very soon inshaa Allahu ba tareda wata matsala ba, then, sai abu na biyu, abokina, damuwarka tayi yawa matuka, har tana barazanar haifar maka da ciwon zuciya, Wanda inhar zaka cigaba da sa damuwa acikin ranka to komai yana iya faruwa. Saboda haka ya kamata ka cire komai daga cikin ranka, Yanzu haka ma dole sai na rubuta maka wadan su magunguna Wadanda za ka samu Relief, saboda condition din da ka ke ciki yanzu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ko kadan Abdul-jabbar bai yi mamakin abin da doctor I .s. g. yace ba, dama yasan za'ai haka donmin shi a zaton shi ma doctor zaice masa Abdul-jabbar ai zuciyarka ta kumbura sosai saura kiris ta fashe,</p><p>Saboda tsananin tunani da damuwa to kuma sai aka samu akasin haka. </p><p>Ya kalli doctor yace "to nagode doctor kwarai da gaske, kuma in Allah ya yarda zan yi kokari nai aiki da abin da kace", yace "OK to Bari na rubuta maka maganin".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yayi rubutu a takarda ya bashi, ya karba yace "nagode sosai fa, sai kudin Mama nawa zan bayar"?</p><p>Doctor I.s.g yayi murmushi yace "ba abin da za a bayar", "a ah doctor ayi haka"? "Eh! ka bar shi kawai ba komai," Abdul-jabbar ya sake yin godiya, A hankali aka turo koda aka shigo doctor ya kalli Wanda ya shigo yace musa ya akayi ne"? "Sir matan nan ce ta farfado", "OK to gani nan zuwa" yace "OK sir" tare sukafita da Abdul-jabbar.</p><p>💞💞💐💐💞NU</p><p>💐💐💞💞N</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐SA</p><p>💞DA"</p><p> 💞</p><p> Page💐3</p><p> 💞</p><p><br /></p><p>💞"NU</p><p>💐💐N</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐💞💞SA</p><p>💞💞💐💐💞DA"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> 💞 *MEENAT UMAR FARUQ* 💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>```This page belongs to my Aunty khadeeja lbrahim Godabe A b u Zaria, pls come back soon we miss youuu```</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_edited by Zainudeen Zain_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>-------------------------------------------</p><p>*~PEN WRITERS ASSOCIATION~*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PEN: THE STRONGEST WEAPON_</p><p>-------------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p>Tana zaune ta zabga uban tagumi sai kace wadda akayiwa mutuwa, gaba dayan su suka karasa wurin doctor, yace "Hajiya kin tashi" tace "umm!"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yace "sannu Mama bata amsaba, saidai tsuramasa idanu da tayi kamar bata taba ganin sa ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya sake "cewa sannu Mama ya jiki"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tayi ajiyar zuciya tareda cire tagumin da tayi, tace "sannu Ina ciwo ne? Ai kai ya kamata Ayiwa sannu ba ni ba, domin kuwa Kai ke dauke da cuta. Yanzu saboda Allah abin da ya kai ka America ke nan"? Nan ta fashe da kuka tana cewa "nikam wallahi da nasan abin da za kaje kayi kenan, tovda ban yar da ka tafi ba, ga shi yanzu ka dauko wa kanka cutar da batada magani. kuma ka sani sarai ita wannan cutar in har takama Mutum to lahira ne direct ba tsayawa, amma shi ne ka kwasowa kanka saboda kasan koka Mutu ba kada hasara KO"? ta sake fashewa da wani sabon kukan"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Doctor yace "kwantar da hankali Hajiya", tace "kyaleni Likita, ai ni wannan yaron ya chuceni", yace "Hajiya da kin saurareni kiji abin da zamfada miki"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta fyace majina da gefen zani tareda share hawaye, tace "Ina saurarenka". Cikin shesshekar kuka.</p><p>Yace "kina ji ko"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta kada Kai, yaci gaba da cewa wannan ba result din shi ba ne.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Akasi aka samu amma shi baya daukeda wannan cutar". </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta daga Kai da sauri ta kalli doctor tace "a ah Likita kar fa ka yaudareni kar ka kuskura Kayimani karya"</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>Yace "Allah Hajiya da gaske nakeyi ai ba zanyi miki karya ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tace "to ya akayi ya rame yayi baki? Na tabbata domin ba kasan shi ba ne kafin ya tafi shi yasa, amma ai ba haka yake ba".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yace "zazzabi ke damun sa da ciwon Kai shi ne ya sashi ya rame" (ya fada Mata haka ne saboda hankalinta ya kwanta domin idan ya fada Mata gaskiya zata koma rikicewa ne).</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da kyar ya samu ta yarda sannan ta sauko daga kan gado, ta kalli Abdul-jabbar tace "Allah ya rufa maka asiri da yanzu sunan ka gawa".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta mayar da dubanta ga doctor tace "to ka bashi magani"? Yace "eh! Na rubuta masa ya siya", tace "to madallah Likita mun gode kwarai DA gaske".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shikam Abdul-jabbar bai ce komai ba saboda tsananin mamaki, aranshi kuma fadi yake "Ashe Mama tana sonshi haka?</p><p>Ah! tana sonka mana ga shi ta nuna damuwarta a kanka,</p><p>Daga ance kana dauke da cutar H.I.V duk ta rikice".</p><p>Yayi ajiyar zuciya a hankali, hakan yasa yaji sanyi a ranshi yau Mama ta nuna masa kulawa ya saki sanyayyan murmushi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tace "to ai sai mu tafi ko"? Yace "to", suka fito doctor ya kara jaddadawa Abdul-jabbar kan yayi kokari ya sayi magunguna, yace "ai zan siya insha Allahu".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mama tace "Ya sunan Likita ne"? Yayi murmushi yace "sunana Ibrahim", tace "A ah Ashe sunan Babana ne to mungode sosai Dattijon kirki".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yace "Lah! ai ba komai sukayi musabaha da Abdul-jabbar yace sai anjima, mun gode fa doctor" yace "nima nagode", suka tafi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sunkusan fita daga harabar asibitin sai ga Cayode, Abdul-jabbar ya watsa masa harara.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sauri Cayode ya matsa gudun kada Abdul-jabbar ya sake shakesa, ita kam Mama bata kula ba har sukafita.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yabi bayansu da kallo yace "Kai Ka ga Mutum sai karfin tsiya kamar Zaki?, yanzu ba domin su Musa ba ai da tuni na zama Dan gida a barzahu".</p><p>Yayi kwaf "Kai wannan guy din akwai shegen karfi,</p><p>a tafi dai Allah ya raka taki gona"</p><p>(Su Cayode anji Hausa har da su karin magana).</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mama tace "to yanzu sai mubiya Kasayi maganin KO"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yace "Mama ni fa akan sauri KO wallet dina ban dauko ba, tun da kika matsamank sai natashi muntafi"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tace "to ai kai dinne wallahi kamar Wanda bai san ciwon kansa ba, ba kaga yadda kadawo ba ne shi yasa".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yayi murmushi yace "to mu tafi idan naje nayi wanka da sallah sai naje (LUFHAT PHARMACY) na siyo tunda suna kawo magunguna masu kyau", tace "to Ai shikenan".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya tare musu Dan a-dai-dai-ta sahu yace ya kaisu kurmin mashi me adai-dai-ta yaja suka tafi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda suka isa gida Abdul-jabbar dakinsa ya nufa, ita kuma Mama ta shiga cikin gida, "assalamu'alaikum", "a ah! Baba Lami Ashe kin zo"? "Wa'alaikumussalamu", eh! Hajiya kun tafi kenan"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Baba mai gadi ne yace mani maigidana ya dawo, amma Kuma kumfita tareda shi nace to KO lafia"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wallahi maigidan naki ne ya dawo ba lafia, shi ne nace yatashi mutafi asibi".</p><p>💞💞💐💐💞NU"</p><p>💐💐💞💞N</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐SA</p><p>💞DA"</p><p> 💞</p><p> Page 💐 4</p><p> 💞</p><p><br /></p><p>💞DA"</p><p>💐💐SA</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐💞💞N</p><p>💞💞💐💐💞NU"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞 *MEENAT UMAR FARUQ* 💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>```This page belong to my best friends, Maryam Aliyu Bala Mrs Shehu Maigishiri Minna and Maryam Muhammad Mrs Mamman gas knt```</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_edited by Zainuddeen Zain_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> "Tun da na ga alama ba hankali ya ishe shi ba", Baba Lami tace " rashin isasshen hankali fa, me ya faru ne"? Likita yace "zazzabi ne da ciwon Kai ke damunsa ya ma rubuta ma shi magunguna"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Allah sarki maigidana yana ina ne yanzu"? Yana dakinsa zai yi wanka ne", "to Allah ya kara sauki" tace "amin".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ko da ya shiga dakin sai ya gan shi tastas ko'ina an share an goge sai kamshi ke tashi, kamar kantin turare, yayi murmushi yace "Baba Lami kenan Allah dai ya biya ki"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya shiga wanka ya dauki tsawon lokaci kafin ya fito, sai da ya gama shirinsa tsaf sannan ya nufi cikin gida, sai faman kamshin turare yake.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana zaune tana kallon tashar MBC 2 duk da cewa ba jin abin da ake fada take yi ba, hakan bai hanata maida hankali ga kallon film din da ake yi ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Jin kamshin turarensa ya sa ta dago Kai ta kalleshi tareda amsa mishi sallama.</p><p>Tace "sannu maigidana ka fita Ashe kuma baka ji dadi ba, to yajiki"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yayi murmushi yace "Baba Lami kenan uwargida sarautar Mata ko ankiya bale an yarda, ba fa wani rashin lafia ba ne sosai, zazzabi ne da ciwon Kai, kuma da zarar na sha magani insha Allahu zansami sauki".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tace "Kai maigidana ai shi ciwo komai kan-kantar shi to ciwo ne, ba ga shi nan ya sa duk ka rame kayi duhu ba? Kaidai Allah ya raba mu da cuta kowane iri ne". Yac "Amin".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"To ai ke baki sanibane", tace "me kenan fa"? </p><p>Yace "tunaninki naketayi achen shi yasa kika ga na rame" yakai karshen maganar shi da dariya, ita ma dariyar take yi tace "kaidai fadi gaskiyarka na daure"? </p><p>Yace "a sakeni". </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kodai kana tunanin Humaira"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A ransa yace "kamar KO kinsani", amma a fili kuma cewa yayi "ga uwargida wake ta amarya"?</p><p>Tace "umm-umm! kodai anata amarya wa ya ke ta uwargida", yace "a ah! Tun da ba a kama amarya ba ai kin ga dole a rike uwargida da kyau KO ya kika ce?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tace "hmmm! To na yarda kadan amma fa kasan halinku maza, da kunyi amarya to kuma shikenan uwargida ta zama kwandon shara".</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya kyalkyace da dariya yace "Kai Baba Lami harda wani kwandon shara"? Tace "eh! Haka kuke yi sai kaga anatayiwa uwargida wulakanci".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yace "a ah! Ni kam ba zanyi haka ba", tace "umh-umh! Fa", Yace "insha Allahu", "to shikenan Allah yasa haka amin".</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka nan sukaci gaba da barkwanci har Mama ta fito. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yace "ni zamfita zambiya gidan Y.Y.K, saboda bai san na dawo ba, (abokinsa ne Y.Y.k wato Yusuf Ya'u Na kaka)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mama tace "au! Dama ba kuyi waya ba"?</p><p>Yace "eh! Nayi ta neman line nasa ban samu ba", "to ka gaishe mini da Ummi ai duk bayan kwana biyu-biyu yakan kawota ta yini,</p><p>(Ummi diyar Y.Y.K ce sunan mahaifiyarsa ne wato Hajiya Karima) yai murmushi yace "to za ta ji, ya kallo Baba Lami yace "uwargidasss na tafi", A dawo lafia Ina gaida amarya domin dai yau nasan Chan za'ayini ko"?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yai murmushi yace kin Amince in naje na yini a chan kenan"? "Na Amince tun da dai an dade ba a ga juna ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"To kin kyauta an gode miki, zamfada Mata cewa uwargidanta na gaisheta, sannan kuma tace ta bar miki ni, duk yafada yana dariya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da Sauri tace "ni"? to bamfadi haka ba nikam ba zambar Mata kai duka ba", </p><p>Ya fita yana dariya Itama dariyan takeyi hada Mama na taya su.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da misalin karfe 3:30pm na rana, Humaira ce ke yin wanke-wanke abakin fanfo jikinta ya bata kamar ana kallonta cikin sauri ta kalli bakin kofa, aikuwa sukai ido hudu da mutumin da batai tsammanin ganinshi a wannan lokacin ba, batasan lokacin da ta saki kwanan da ke hannunta ba ta nufi in da yake tsaye, har ta kusa kaiwa gurinsa, ko me ta tuna sai kuma ta ja ta tsaya tayi shuru Chan kuma sai ta fashe da kuka.</p><p>💐💐💞💞NU</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐SA</p><p>💞"DA 💞</p><p> page6&8 💐</p><p> 💞 </p><p>💞"DA</p><p>💐💐SA</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐💞💞NU</p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞MEENAT💐 UMAR💐 FARUQ💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> this page belong to All people of kontagora.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>---------------------------------------</p><p>PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>T"ace dakatafi kabarni mana yau shekara kusan hudu sannan kadawo ,</p><p><br /></p><p> yakada Kai yace OK shine yabaki damar kibarmani yarinya tafada tarkon wani kato KO? </p><p><br /></p><p>To aigashinan ya yaudareta ya cuceta DA sauri ta katseshi dacewa cuta kuma? Yace eh cuta mana idan ba cuta da kuma yaudareba, yaza'ai saida yabari tafara sonshi sannan zaya gudu yabar da gyanbo acikin zuciya, </p><p><br /></p><p>domin Na tabbatar haryanzu baza'arasa sauran son shi acikin zuciyartaba.</p><p><br /></p><p>Yanzu kiduba kiga yadda yarinya takoma duk tarame sobada Allah,</p><p>Kuma dakike cewa natafi nabarku shekara hudu, aisanin kankine saida na shekara biyu agidan yari.</p><p><br /></p><p> Yace nibaki kyauta maniba wallahi yarinyar daya kamata ace antakura Mata tayi karatu, amma Sam ba'ayi hakaba saikawai kuka barta tana soyayya kuka hada,</p><p><br /></p><p> takatseshi</p><p> D"a sauri tace muka hadata dame? Yace da abunda yafi kafin kwakwalwarta mana, tace a ah muba ruwanmu tahada kanta dashidai.</p><p><br /></p><p> Yace Kuka hadata dashidai dabaku yardaba aibazata tsaya tasaurari saurayiba, Ita kam umma sai tayi shuru tana saurarenshi batareda tasake cewa komaiba, yanatayi can saiyaja tsaki mtsww.</p><p><br /></p><p>Ta kalleshi aranta tace wanzami kenan bakaso ajikinka, saikuma tai murmushi abayyane tace daga dawowa kuma saifada? </p><p><br /></p><p>Yace haba umman yara yabazanyi fadaba saboda Allah. tace wato kar'abarta sake tsayawa da saurayi kenan KO?</p><p><br /></p><p> Yace eh kusan hakadin nakenufi. Au zubamata ido zamuyi muna kallonta bazamu yimata aureba ka kenufi? </p><p><br /></p><p>Nagaya miki baza aimata aureba? Aure kam tunda shiya haifeta aidolenta itama tayishi amma aisai'ajira hartakai munzalinyi ko? </p><p><br /></p><p> A"to Inbaka fadiba hakaba to yaza'ai kamar Humaira amatsayinta Na ya mace acekuma baza A"barta ta tsaya DA saurayiba,</p><p><br /></p><p>Y"a kalleta ya girgiza Kai Yace Asma'u wai maiyasa ki keyimini hakane nadawo zamufara</p><p> sa'insa dake kenan? kinga indamuke samun matsala dake Inna ce ga yadda za'ayi saikice maniba hakaba, </p><p><br /></p><p> Yacigaba da cewa yaza'ayi ace kamar Humaira tahada Dan taura biyu abaki akema kinsan bazaiyi yuba. Tace kamar yaya Dan </p><p> taura biyu abaki? </p><p><br /></p><p> Yace yazata hada karatu da kuma soyayya shin karatu</p><p> zatayi KO soyayya? Saiki zaba Mata daya domin kuwa kece kika kamata Da hartasamu damar kula samari, saboda haka nan Ina sauraranki zabar Mata daya daga cikin biyu kinjiko? </p><p><br /></p><p>Ta"kallesa saitaga kamar ransa yabaci, tayi murmushi tace Abban yara kenan to yaizafi? Yabata amsa dacewa aibazafi acikin magana ta sai, tace akwai mana ba gashi nan kabata raiba.</p><p><br /></p><p>Ya" tsura Mata ido cikin bacin rai Yace ya bazan bata raiba Asma'u meyasa zakiyi Mani haka?</p><p>Kinsan halinmu sarai bawai bakisaniba,</p><p><br /></p><p> baikamata ace kamar Humaira tafara daukar matsalar da namiji ba, common fifteen years fatake tama Kai shabiyar dinma kuwa? </p><p><br /></p><p>Tace batakaiba tukun na saura wata hudu, yace to kinjiba amma kika barta tadauki abunda KO yar shakara talatin saitayi da gaske zata iyamasa,</p><p><br /></p><p> To ballan tana Humaira yar sha hudu dawani abu yaja tsaki mtsww, yaci gaba dacewa nidai Asma'u baki kyauta miniba wallahi KO kadan,</p><p><br /></p><p>Yayi shuru Na tsawon wani lakaci batare daya sakecewa komaiba. Tace to kayi hakuri Abba Humaira nayi kuskure amma insha Allahu haka bazata karafa ruwaba kaji? </p><p><br /></p><p> Aima tundaga wannan yaron bata Kara kula kowani saurayiba, har lokaci baice komaiba, tace naji kayi shuru ko haryanzu fushin kakeyi?</p><p><br /></p><p>Y"ace a ah bafushi nakeyiba kinsan nibanason abunda zaibatama Addana rai duk sai naji rayuwana yabaci,</p><p><br /></p><p>T"ace ato kariga kasan halin kayanka da sa'abu cikin rai, Kaga gakawa zuccinka gana karatu sannan kuma gawan nan yaron datasashi arai, gajarabawa badole tarameba, </p><p><br /></p><p>dama jibi zasu gama jarabawa idan Allah yakaimu narai lafia. </p><p>Yayi murmushi Yace Amin Allah sarki Adda Humaira na hakana me sunanta kedason karatu, inaganinma idan jarabawarsu tafito D"a kyau America zankaita tayi karatuta achan I hope dai tarubu jamb?</p><p><br /></p><p>Tace eh tarubuta Amma duk makarantun dake kasarnan Najeriya basuyiba, </p><p><br /></p><p>meyasa zakakaita America kasar masu jajayen kunne kasar dabasuda tarbiyya, meyabaka sha'awa dazaka kaita Chan taikaratu?</p><p><br /></p><p>Yace saboda inas on tayi karatunta me kyau cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, </p><p><br /></p><p>kuma insha Allahu nasan tarbiyyar damukai Mata bazata zubarba dayardan Allah,</p><p>Sannan kuma aigidan ubangidana zata zauna bawai waniguriba, </p><p><br /></p><p>kuma bawanda zayata kuramata akwai yarinya agidan tsarartace don Itama natafi shabiyar dinba, zataji dadin zamadasu kwarai da gaske domin basuda matsala wallahi kedai kawai</p><p> kiyimata addu'a. </p><p><br /></p><p>T"ace audama Chan katafi Kai zamanka hankalinka akwance Mukuma muna nan duk hankalinmu atashe, Kai kuma babu abunda yadameka?</p><p><br /></p><p>Yace umman Adda Humaira meyasa kikemaida hannun agogo bayane? angaya miki nima danake Chan hankalin nawa akwance take? To barina fadamiki hankali na ba'akwanche yakeba, akoda yaushe hankali na atasheyake saboda bansan halinda kuke cikiba, bantaba kwana nashi batareda nai tunanin kuba, </p><p><br /></p><p> kuma cikin raina akoda yaushe, nima bantaba zatan tafia wata kasa nabarkuba, Bari kinji nagaya mini yadda akai harnatsin kainan America agidan yari nahadu da wani Mutum da matsalasa tai kusan daya datawa,</p><p>Yakece mini shikam najiriya kasarsace amma wallahi yagaji da ita, saina tambayesa saboda meyasa yafadi haka? </p><p><br /></p><p>Sai"yacemun saboda yawancin mutanan dake cikin ta macutane azzalumai.</p><p>Don haka shikam idan har Allah yasa yafito daga gidan yari lafia, to zayayima kanin mahaifinsa magana yahadasa dawani abokinsa, datake can America dazama. Hakanan kawai naji nasamu kaina iname cemasa nima inhar dahali to nimazan bishi mutafi tare, domin kuwa nima,</p><p><br /></p><p>Alokacin naji kasar Tafitamun arai. Harmadai idan natuna cewa ba'asan inda yar'uwata takeba duk sai naji hankali na yakara tashi, domin kuwa nasan banida kowa sai Allah saikuma ku,</p><p><br /></p><p> don haka sai kawai nayanke shawarar nabishi mutafi tare saboda nayi imani Allah zaikulamun daku kuma inada tabbacin cewa Malam zaya kuladaku,</p><p><br /></p><p>Koda muka isa mutumin mesuna Alh jamilu yakarbemu DA mutunci, yakuma Samar mana Aiki munkuma samu alkhairi aciknsa sosai, </p><p><br /></p><p>Wanda harna keta aiko sako ta gurinta Alh musa kusan sonawa, Amma sai akoma mundashi waibasu ganeshiba, sai sakon karshene sannan akaganeshi saidai kuma baiyimun yanda naceba, </p><p><br /></p><p>domin kuwa cewa nayi yasaimun fili atudun wada yaimun gini amma wai duk fadin garin Kaduna babu filin daza asaimun saida akatafi garin yola saboda tsabar walakanci irin Na Alh musa,</p><p><br /></p><p> Yaja tsaki mtsww ainasan da yola nace agina akaduna. Tace menene laifin Alh musa anan ? </p><p><br /></p><p> hakanan dayayi shine dai-dai haka akeson abokina kwarai yasa abokinsa hanyar gaskiya bata karyaba, </p><p><br /></p><p>Abban Humaira lokaci yayi daya kamata kakoma mahaifarka hakanan, komai yaizafi maganinsa Allah yar'uwarka inhartana Raye aduniya Koda shekara nawane inhar Allah yakaddara zaku gamu, tofa bamakawa sai kun gamu idan kuma Allah bai kaddara kugamuba tofa bawanda ya'isa yahadaku.</p><p><br /></p><p>Y"a kalleta yace nasan da haka Umman Humaira tun bayanzuba, saidai zanzauna ayolane bawai don inasoba, </p><p><br /></p><p>domin kuwa sam bazatai mun dadin zamaba Tace hakuri zakai ka kuma daure kazauna hakanan tunda mahaifarkace,</p><p><br /></p><p>Yace to yana iya tunda shima Malam yace dole saina koma candin dazama, yanzu kifito muje kofar gida kiga motar Dana siya Tana nan waje gurin Malam,</p><p><br /></p><p>Sannan kuma gobe KO jibi in Allah yasa munaciki masu yawancin rai zantafi Zaria Nagano babana, </p><p><br /></p><p> "Malam kuma yace dole za'asamu wasu daga cikin almajiransa atafidasu Chan yola don susauke Alkur'ani maigirma agidan,</p><p><br /></p><p> domin kuwa yace bai kamata ashiga gidan hakanan ba Humaira ce tashiga dakin tareDa sallama suka asma,</p><p><br /></p><p>Yai murmushi yace zonan Adda Humaira ta harkingama wanke-wanken kenan? Tazo gefensa tazauna tareda cewa eh nagama, </p><p><br /></p><p>Yace to yaya jarabawa ummanku tace jibine zaku gamako? Tace eh to me'ake karantawa? tace Abba medicine nake karantawa, </p><p><br /></p><p>Ban mantaba domin kace abunda kakeson nakaranta kenan, Yace Karatunda kikeyi mewuyane sannan kuma kika hadashi dawani abun maiwuya sosai meyasa kikai haka Humaira? </p><p><br /></p><p>Da sauri ta kalleshi tareda cewa Abba wani iri abune nahada dashi mewuya sosai? Yau murmushi yace nifana Fara tambayarki, </p><p><br /></p><p>Amma bakibani amsaba sai kema kika tambayeni? To nibari nabaki Amsan taki tambayar inanufin soyayya,Dasauri ta kalli inda umma take, ita kam umma harara tawatsa Mata ahankali ta sunkuyarda Kai kasa batare datake komai ba. Yace Na tambayeki? </p><p><br /></p><p>Tace eh zaki'iya tauna Dan taura biyu abaki? A ah bazan iyaba? yace why? Tace Abba gaskiya is two big, Yace good, ummanku tafadamun abunda duk yafaru. Saboda haka,</p><p><br /></p><p>A"bunda nakeso dake yanzu shine kirabuda dukan wasu samarin dakikasani,kimaida hankalinki akaratu kinsan inda zankaiki kicigaba da karatunki?</p><p><br /></p><p> T"ace a ah to America zankaiki tai murmushi harsaida wushiryarta yabaiyana , Abba nice zantafi America karatu? Eh ko bakison zuwa ne?</p><p><br /></p><p> Lah Abba wallahi inason zuwa, yauwa toshike nan kinga inhar Allah yakaiki lafia to kimaida hankalinki kan karatu kiyi shi sosai. Inharki kayi yadda nakeso to nima zanyi miki duk abundanc kema kikeso kinajiko? Addan Abba. </p><p><br /></p><p>T"ace eh Abba insha Allahu zakasameni maibiyayya akan dukan abunda kace, Yace yauwa Adda Humaira Allah yai muku Albarka yabaku abunda kuke nema Na alkhairi tace Amin, Abba amma zakudinga zuwa kaida umma Da yah Himu KO?</p><p><br /></p><p> Yai murmushi yace karkidamu agidan ubangidana Zaki zauna, akwai yarinya agidan kusan sa'arkice batada matsalar sannan kuma duk lokacinda kikeson ganina zanzo kinjiko ? </p><p><br /></p><p>Tace to Abba, to katashi muje kuga motar suka ce to, Sukafita dukansu don ganin motar.</p><p><br /></p><p>koda Abdul-jabbar ya'isa gidan Y Y k afalo yatarar dashi zaune shida matarsa Jamila,</p><p><br /></p><p> yanaduba wasu takardu ita kuma Tana kallon wani India film, ita kuma ummita kuma Tana kan dan kekenta tana wasa, Yai sallama suka asma Y Y K ya kallesa fuskasa cikeda mamaki, Jamila tace a ah.</p><p>?💐💞💞NU</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐SA</p><p>💞DA"</p><p> 💞 </p><p> Page💐5</p><p> 💞</p><p>💞DA"</p><p>💐💐SA</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐💞💞NU</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐MEENAT💞 UMAR💞 FARUQ💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>This page belong to my best friend LARAI IBRAHIM RIBAH Dan Fodio university of sokoto.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>-------------------------------------</p><p>PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN: THE STRONGEST WEAPO</p><p>-------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>only the exquisite and whizkid writers are opportune to be writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>D"a sauri yakarasa wajanta yaca a ah haba Adda ta yahaka kuma bakiyi murnada dawowata bane? </p><p>Ta girgiza Kai alamar a ah,</p><p><br /></p><p>Yadago kanta tareda share Mata hawaye yace to menene kuma abun kuka? bagani nadawoba,</p><p><br /></p><p> Pls stop crying, kinsan banason ganin hawayanki ko?</p><p>Cikin kukan sha'gwaba tace pls Abba karka Kara tafia kabarmu Allah daka tafi munsha wahala sosai.</p><p><br /></p><p>Y"ace ainadawo kenan babu inda zankara tafia nabarku Ina nan taredaku insha Allahu kinjiko? Tadaga Kai alamar to,</p><p><br /></p><p>Yace to ya isa hakanan yasake cewa to kiyi dariya mana naga open teeth din nan dana Dade banganiba,</p><p><br /></p><p>Aiko ta Saki dariya harsaida wushiryarta din yabaiyana, </p><p>Yace yauwa Humaira Addan Abba kokefa Ina umman kune bangantaba? tace tana nan cikin dakin gwaggo,</p><p><br /></p><p>To ita gwaggon kumafa? Taje unguwa OK to Bari nashiga wajan umman taku tace to.</p><p><br /></p><p>T"ana zaune bakin gado, yayi sallama yashiga sanin muhimmancin sallama yasata amsa, amma inbadan hakaba dako sallamarsa bazata amsaba. </p><p><br /></p><p>A"hankali yakarasa wajanta yacire Mata tagumin zabga, yace umman yara tagumi bayada kyau.</p><p><br /></p><p>Batace masa komaiba yasake cewa umman yara yanasa meku inafata nasameku lafia?</p><p><br /></p><p>Malam yafada mini cewa Himu Na yana A. b. u Zaria KO? </p><p><br /></p><p>Aini ba abinda zancewa Malam saidai nace Allah yabiyasa ubangiji yasa Aljannar fiddausice makomarrr, maganar ta tsaya masa sakamakon hawayen daya gani suna sauka afuskarta,</p><p><br /></p><p>Yace a ah umman yarakuma yahaka kuma?</p><p>Yanzu Adda Humaira ta tareni da kuka sannan kuma kema dashi zakitareni? Inagadai ga dukkan alama bakuyi farin cikin dawowa taba kenan KO?</p><p><br /></p><p>T"ashare hawaye dagefen zaninta, tace yanzu saboda Allah da Annabi abunda kayi ka kyauta maiyasa zakai mana haka?</p><p> </p><p>A" lokacin da muke bukatarka akusadamu, A"sannan ne Kai kuma kayi tafiyarka kabarmu,</p><p>Haba Abban yara shekara hudu kenan fa,</p><p><br /></p><p>Sannan kuma don munyi kuka kakecewa bamuyi farin cikin dawowar kaba?</p><p><br /></p><p>To munji bamuyi farin cikinba Kaga Kai kuma ba saika komaiba, tunda kaima ga dukkan alama ba kayi ninyar dawowabako?</p><p><br /></p><p>Y"ayi murmushi tareda Kama hannunta yace haba umman yara meyai zafi haka shiba wutaba?</p><p><br /></p><p>Shin bazakiyi mini uziriba saboda Allah? Kisa nima ba'ason raina natafi nabarkuba dolece tasani yinhaka,</p><p>Ya kuma yin murmushi yace habawa uwar yayana bansanki</p><p> dafishiba,</p><p><br /></p><p>Kinsa meye? Fishin baiyimiki kyau saikika fito MA'U yafada cikin zolaya yana dariya, </p><p>Cikin jin haushi tace karyayi kyaudin aibawai nayi bane don yayi mini kyau,</p><p>Kayi saika ce Kaine mutumin nafarko da kaddara ta taba fadamawa,</p><p><br /></p><p>Y"ace to naji amma yanzu dai kiyi hakuri nasan nayi laifi ayafemini kaina bisa wuya, bazan Kara tafia mainisa irin hakaba insha Allahu kinji?</p><p>Asma'ul'Husna uwargidan Alh mahamud umman Ibrahim da Aishatul'Humaira, </p><p><br /></p><p>T"ayi murmushi tace aifa za'akin baki agurinku maza kamar ganga,</p><p><br /></p><p>Badole nayi hakuri tunda kasan bayadda zanyi dakai,</p><p><br /></p><p>Ni'abinda mayake bani mamaki kai kasani sarai dacewa, kowani bawa da irin kaddaran da Allah kedora masa, </p><p>Allah baitaba dorama bawa abunda yafi karfisaba,</p><p><br /></p><p>Duk abunda Kaga ubangiji yadorama bawonsa to yasan zaya'iyane shiyasa masa,</p><p>Amma kai duk sai kamanta da haka KO?</p><p><br /></p><p>Yace amma dai kinsa tunda ban taba shiga irin wannan haliba aidolene najigata KO?</p><p><br /></p><p>Tace eh yadda baka taba shiga ba hakanan wanima baitaba tunani KO kwatan kwacin shiga irin nakaba,</p><p>Amma Allah mai iko dayatashi sai no yasakashi cikin wani halin Wanda yafinakama nesa bakusaba ya kumayi hakuri,</p><p><br /></p><p>Saboda yasan akwana atashi Allah zayafitar dashi daga cikin wannan halin.</p><p><br /></p><p>Y"ace to shikenan naji mubar wannan maganar, ubangiji ya yayemana matsalolin Rayuwa, tace to Amin don Darajar Annabi.</p><p><br /></p><p>Y"ace naca miki Malam yafada mini ankai Himu A.B.U Zaria bakice mini komai ba kinata fishi, </p><p><br /></p><p>Sannan naga Adda Humaira tarame shinwa haryanzu mutanan basubarta bane?</p><p>Wai shin me mutanan nan suke sone da bazasu barmini yata tahutaba?</p><p><br /></p><p>(Yananufin mutanan boye)</p><p><br /></p><p>T"ayi murmushi tace a ah baruwan mutane</p><p>Indai wayan mutanan ne, dataimakon Allah dana malam sukarabu da'ita, </p><p> I tace dai dasa Abu cikin rai.</p><p>Yace menene yasaka acikin ranta dayasa tarame haka? </p><p><br /></p><p>Tace</p><p>Komai maimata sashi cikin rai,</p><p>Kasanta da kawazucinka gakuma tadason karatu, </p><p>Sannan kuma gawani yaro dayazo yanasonta itama Tana sonshi sunyi nisa dason juna, tosaikuma dagabaya tagane yanada Mata,</p><p><br /></p><p>Yace matar tashi I tace zata hanasu cigaba da son junansu?</p><p><br /></p><p> Ta"ce eh to kusan hakadin ne tunda had gida tazo tacimini mutunci, takumace Humaira tafita Mata harkar mijinta inba hakaba kuma zata nakasata.</p><p><br /></p><p>Dasauri yace me Tana haukane? saboda mijinta yace yana son Adda Humaira shine zata nakasata, </p><p><br /></p><p>tace eh hatafada,</p><p>Yaja tsaki mtss yace saboda yana aurenta shikenan kuma sai akace karya kula wata ya mace ko,</p><p><br /></p><p>To afadamata namiji mijin mace daya ne?</p><p>Waima yar gidan waye datake ikirarin zatanakasa mini Adda Humaira ta,</p><p><br /></p><p>T"atce wallahi bansan KO yar wayaba, Amma dai daga ganita ba gidan mutunci tafitoba, domin shigarta baikama da yar mutunciba ,</p><p><br /></p><p> kamar ba matar aureba wallahi yarinyar tacimun mutunci sosai Wanda tunda nake ba'ataba yimini irinsaba, </p><p><br /></p><p>Toni kuma danaga haka sai nace tafita Mata harkar mijinta tunda bashi kadai bane DA namiji, saboda dai nibanason ta shin hankali, </p><p><br /></p><p>toshinefa tasama kanta tunani DA"damuwa harda zazzabi tayi, aimayanzu tadanyi dama-dama.</p><p>Yana tsaki mts tareda cewa Ai wallahi duk laifinkune dagake har Abba Himu,</p><p>Kema kinfi Himu laifi sosai saboda Allah Humaira gudanawa take da harza'abarta ta tsaya da saurayi, (class 2) fanabarta ya kuma cewa ke haryanzu bakisan halinmu bako?</p><p>D"asauri tace halinkufa kace hmmm nikuwa nasanshi domin kuwa kayimin nagani. </p><p> Cikin bacin rai yace me nayi miki?</p><p>?💐💞💞NU</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐SA</p><p>💞DA 💞</p><p> Page9-12💐</p><p> 💞</p><p>💞DA</p><p>💐💐SA</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐💞💞NU</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞MEENAT💐 💐UMAR💞 FARUQ💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p>dedicated to my Aunty Hajja from Maiduguri live in Saudi Arabia we miss you so muchhh i greet my little sister's fatima zahra and lsrah</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zanuddeen zain</p><p><br /></p><p><br /></p><p>---------------------------------------</p><p>PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p> </p><p>PEN THE STRONGEST WEAPO</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>only the exquisite and whizkid writers are opportune to be writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Jamila tace a ah mutanan America saukar yaushe? Yace dazu nadawo wallahi ya maida hankalisa ga ummita datake daga masa hannun alamar ya dauketa,</p><p><br /></p><p>Yai dariya yace ummita kinsani ne? Jamila tai dariya tareda cewa bata ganka tsaye ba mai daukar ta sutafi yawo.</p><p>Ya dauke yana murmushi yace baby ummita yawo kikeso atafi?</p><p>Yadagata sama yana mata wasa Tana bangale baki Tana dariya, Yace mutafi yawo tadaga Kai alamar eh,</p><p><br /></p><p>Y Y k Yace kajita harda saurin cewa eh KO? to babu inda Zaki yarinya sai danbanzan yawo sai kace taci kafar kare.</p><p>Abdul-jabbar yace Mutum da kafarsa sai ahanasa yawo, ah gaskiya abar Mutum yawala.</p><p><br /></p><p>Y Y K Yace Ai wannan yawon tane yawuce misali in yanzu kabarta tafita tosai kafita nemanta,</p><p>Shiyasa nace Mamanta tadaina barinta tanafita tunda kafafunta kaikayi suke mata.</p><p>Hakanan ran nan tafita ba Wanda yasani saboda baba maigadi yakewaya bayi, </p><p><br /></p><p>kuma yamanta bairufe kofaba kawai tafita ingayamaka mukaita nemanta, bamu gantaba Kai ranan hankalinmu yatashi wallahi sosai hartsawon wani lokacifa bamu gantaba, sai chan mukaganta abayan layinmu taci kuka takoshi Tana zaune akofar wani gida hartafara gyangyadi sannan muka daukota ,</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yace kai! Kai!! Kai!!! ummita Ashe kintaba bachewa tace eh suka kyalkyace DA dariya, Jamila tace aiwajan nan duk jinta take atakure,</p><p><br /></p><p>Yace ummita kidaina yawo kinji? tace to idan kinayawo sai anyanke kafafunki kuma shikenan bazaki sake ganin mom and Dad ba ko kinason kidaina ganinsu? </p><p><br /></p><p>Tace a ah Daddy Adena KO? Sukai dariya Yace yauwa my gud gal, Jamila takawo masa Ruwa da lemon juice tareda soyayyen nama ta'ajiye kan table din dake gabanshi, </p><p><br /></p><p>T"areda cewa muntsaya sauraran wannan me surutun bankawo maka ruwa ba, </p><p><br /></p><p>Y Y K yace kai ni surutunta har mamaki yakeban yarinya sai sai dankaran surutu saikace parrot,Yai murmushi yace aifira mukeyi KO ummita?</p><p><br /></p><p>Tace eh aje gidan Ajiya ko? tananufin Hajiya "karima , Jamila tace aifa haryanzu yawon dai yana nan Oya tashi muje muyi karatu ki kyale daddy yasha ruwa tace to,</p><p><br /></p><p>Y"asauketa ta kalleshi tace daddy anyi kalatu yace to my gud gal kiyi dayawa kinjiko?</p><p><br /></p><p> Yace to Daddy ankalanta inji Yace eh, domin kuwa duk yagane gwarancin datakeyi tace ABCDE ta kuma cewa 12345 hartana nunamasa yan yatsunta alamar 5 kenan,</p><p>Yatafa Mata tareda cewa eyye gud gal kin iya amma kikarayi sosai, zamuje gidan Hajiya kuma musiyo sweet aizakisha KO? tace eh , to kiyi karatu dayawa kinji KO? Tace to,Jamila tace nidai mutafi Sarkin surutu</p><p><br /></p><p>Y"a tsiyaye lemon yasha Y Y K Yace Ina dalta boy? Yace afilin jirgi muka rabu dashi nace ya tsaya kwana gobe sai yatafi Yace a ah shi bazai tsaya ba.</p><p>Ya'ajiye cup din yayi murmushi tareda cewa yah akayine Nawa naga kanata kallona kodai nasake makane?</p><p><br /></p><p> Y Y K Yace kwarai kuwa da gaske kasake mun, naga duk karame kayi duhu meya farune kodai kayi rashin lafia ne achan? </p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar ya girgiza Kai alamar a ah Cikin tsananin mamaki Y Y K Yace yazakace a ah? Alhalin kowa yaganka yaga Wanda bashi da lafia,</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yace daga dawowana KO ruwaban shaba "mama tace waibani DA lafia, don karnace mata a ah tace nai Mata karya sai kawai nace Mata eh,</p><p>Amma ni lafia ta qalau,</p><p><br /></p><p>Y Y K Yace OK naji lafiyarka qalau to amma menene yasaka kayi wannan ramewa da duhu haka?</p><p>Kamar Wanda yatashi jinya Kaga kanka kuwa a mirror?</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar ya tsurama Y Y k ido Na tsawon wani lokacin batareda Yace komaiba,</p><p><br /></p><p>Chan Yace Nawa narasa gane awani matsayi nake a gurin my cool, domin kuwa yanzu nasan tana daukata mayaudari ko maciyi Amana tunda banfada Mata cewa nayi aure bako?</p><p>Nikam babu abunda zancema wannan yar iskar yarinyar itada uwarta saidai Allah ya'isa tsakanina dazu,</p><p>Saboda duk wani abunda yafaru tsakanina DA my cool to sune silar komai,</p><p>Nibansan ma ya'akai tasan ina neman my cool ba, ban kuma San ubanda yanuna Mata gidan suba DA hartasamu damar zuwa taci musu mutunci,</p><p>Saboda haka don Allah katashi muje karakani nabata hakuri,</p><p><br /></p><p>Domin Nikam Ina Matukar son mesanyina inayimata son Dani kaina basan iyakarsaba,</p><p>Wanda inaji ajikina muddun narasata to bansan yadda Rayuwata zata kasanceba.</p><p>Don haka katashi mutafi kajiko Nawa? Yafada fuskarshi cike DA tausayin kansa,</p><p><br /></p><p>Shikam Y Y K tunda Abdul-jabbar yafara magana gabansa kefaduwa, (Aransa kuwa fadi yake wato angudu ba'atsiraba kenan abunda yake gudu shine keshirin faruwa,)</p><p><br /></p><p>A hankali ya kalli Abdul-jabbar din duk sai yabashi tausayi, aransa yake cewa Yace lafiar sa qalau Alhalin kuma yana dauke DA babbar cuta maiwuyar magani,</p><p><br /></p><p>Domin kuwa SO babbar cuta ne tabbas SON "Humaira Yai masa mugun kamu, yaki fadamasa ne don karya shiga wani hali, amma kuma duk dahaka saida yashiga.</p><p>Ya katsemasa zanchan zuci datakeyi dacewa Nawa tashi mana mutafi,</p><p><br /></p><p>A"hankali Y Y K Yatashi jikinsa asanyaye hannun shi rikeda takardu yanufi ciki,</p><p>Akangado yajefa takardun yafara safa DA marwa,</p><p><br /></p><p> Jamila kallesa tace baban ummita meke faruwa meyasami "Abdul-jabbar din naga yarame ko bashida lafia ne? </p><p>Y"a tsura masa ido tareda cewa maman ummita Nawa baida lafia, tace maiyake damunsa? </p><p><br /></p><p>Yace abunda yake damunsa yanada wuyar magani,</p><p>Tazaro ido alamar tsoro tace wace irin cuta ce haka mewuyar magani? </p><p><br /></p><p> Yace "SO"yanada wuyar magani matukar bakasamu abunda kake Soba</p><p>Maganinsa daya shine hakuri,</p><p><br /></p><p>Amma narasa ta yadda zanfahimtar DA Nawa" yagane cewar "Humaira kam tai masa nisa saidai Yai hakuri,</p><p>Saboda haka fadamun maiye abunyi maman ummita Ina mafuta?</p><p>Domin kuwa Yace saina tashi munje natayashi bata hakuri,</p><p><br /></p><p>Kinsan abunda Yace min kuwa? Tace a ah Yace muddun yarasata "Humaira to shikam baisan ya rayuwarsa zata kasanceba,</p><p>D"on haka fadamun yazanyi?</p><p><br /></p><p>Jamila tadafe kirji tareda cewa munshiga uku yanzu kafada masa ne cewa Humaira suntashi kaikuma ba kasan inda sukako mana?</p><p>Yace banfada masa komaiba,</p><p><br /></p><p> tace toh"</p><p> yanzu kaje kutafi in kuka aikai- yaro yakirata akace muku bata nan suntashi, nasan zai tambayeka mai yasa baka fadama saba, Kaga sai kace kayi hakane saboda karya shiga wani hali, saikaji maizai cemaka,</p><p><br /></p><p>Y"ai ajiyar zuciya Yace kinaganin hakan shine mafita?</p><p><br /></p><p>T"ace kwarai kuwa saboda masu Karin magana sunche zuwada Kai yafi sako, Kaga idanyagani da ido sa zaifi yarda akan kafada masa, duk dadai nasan bazai karyata kana koya kagani?</p><p><br /></p><p>Yace to shikenan Bari mutafi sai mundawo kenan tace to adawo lafia Yace Allah yasa yafita.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞💐LUFHAT ce 💞💐</p><p>💐💐💞💞NU</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐SA </p><p> 💞DA</p><p> 💞</p><p> Page13-15💐</p><p> 💞</p><p>💞DA</p><p>💐💐SA</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐💞💞NU</p><p><br /></p><p> NA </p><p><br /></p><p>💞MEENAT💐 💐UMAR💞 FARUQ💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>-----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION </p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>only the exquisite</p><p>and whizkid writers are opportune to be pen writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Y Y K ne yake Jan motar yayida Abdul-jabbar kegefensa, Yace aika Nawa baka sani ba? </p><p><br /></p><p>Yace inasondai nasani yanzu, Yace Mama takwasheni zuwa wani private hospital adubani tunda wai nibansan ciwon Kainaba,</p><p>Infadamaka koda mukaje munsamu ganin doctor munajiran Result, nan yasanar dashi abunda yafaru tsakanisa DA Nurse kayode.</p><p><br /></p><p>Y Y K Yace amma dai wannan baisan kan aikinsa bako? Abdul-jabbar yaja tsaki mtsww tareda cewa yaushe fa sai iskanci kawai yasani,</p><p><br /></p><p>Y Y k kalleshi Yace aikama iskan cinka yawane dashi ba yanzu Na tambaye cewa bakada lafia ne, amma sai kace waikai lafiyarka qalau. </p><p><br /></p><p>Yai murmushi yace Nawa kenan karka samu damuwa bawani rashin lafia bane sosai, zazzabi ne da kuma ciwon Kai aima doctor yarubuta mun magani danasha Zan warware in sha Allahu, </p><p>Kuma danaga my cool zakaga nakoma normal maisanyina aikagane KO? yafada yadaga masa gira tareda yin dariya.</p><p><br /></p><p>Y Y k ya hararesa Yace abunda zakace kenan tunanin "Humaira ne yasaka duk karame kayi duhu, karka wani lakawa zazzabi da ciwon kai, kaibaka kankabane shiyasa wallahi duk kayi wani iri sai kace bakai ba, </p><p>Nidai abunda nakeso dakai karinga daukar komai dasauki kadaina daukar abuda zafi.</p><p>Abdul-jabbar ya kada Kai Yace Nawa kenan bazaka ganeba neshiyasa amma bakomai mutafi kawai,</p><p><br /></p><p>T"saye suke suna jiran yaron dasuka aika</p><p>Chan sai gashi yafito daga gidan, yana yarwakarsa.</p><p>Koda yakarasa gurinsu sai Yace ance waibabu "Humaira anan gidan,</p><p> </p><p>Abdul-jabbar ya watsama yaron harara Yace kufa yaran nan wani lokacin kiwiyar tsiyane gareku,</p><p>Yaza kace nan gidan babu "Humaira? Yace Allah kuwa haka akacemun,</p><p>Yace toh" munji yimaza katafi mungode,</p><p><br /></p><p> Shikam yaro yai tafiyarsa.</p><p>Yaja tsaki mtsww Yace Nawa Kai kaji wannan yaronko? kilama a zaure ya tsaya yadawo yacewa mutane wai babu "Humaira agidan,</p><p>Ya kuma cewa shegiyar kiwiyace kedamun wasu yaran wallahi, Shidai Y Y k ummh kawai Yace</p><p><br /></p><p>Kai! Kai!! Kai!!! Yakira wani yaro dayake kokari wucewa tagabasu, yaron Yace gani, Yace don Allah kashiga gidan Chan kace ana sallama da "Humaira kaji KO? Yace to.</p><p><br /></p><p>Shuru Chan saiga yaron yafito wani saurayi Dan kimanin shekara shabiyar yana biyedashi abaya, suna karasowa gurinsu sai kawai wannan saurayin Yace habawa malamai wannan wani irin abune haka saboda Allah da Annnbi?</p><p>Saunawa za'afada muku cewa babu wata "Humaira anan gidan iye? </p><p>Ance babu ankuma cewa babu amma bakuyar daba, shi in akwai za'aboye tane? </p><p><br /></p><p>Ya kalli Y Y k Yace tareda nunasa da yatsa Yace kaidai mutumin nan kacika dan banzan naci, saunawa zanfada maka? kazo ka kuma zuwa Kai kanama tazuwa, </p><p>N"ace maka maigidan yatadasu tunda basubiyan kudin haya ka kuma tambayeni cewa ina suka koma nace maka bansaniba! bansaniba!! Tunda ban sansuba, </p><p>Amma kuma bakajiba shine yaukuma kasake zuwako? </p><p> Toh" yakake San nayi maka saboda Allah iye?</p><p><br /></p><p>Shikam Abdul-jabbar tunda wannan saurayin yafara magana yayi mutuwar tsaye, tareda zubamasa idanu tamkar yaga wata sabuwar halitta wace babil Adamuba domin kuwa bai fahinci abunda saurayin yake fadaba,</p><p><br /></p><p>Y Y K ya katseshi dacewa toh" Malam ya isahaka nan munji mun kuma gode Karka dokemu, domin naga kiris yarage kado kemu saboda munzo gidanku Neman "Humaira KO?</p><p><br /></p><p>To kasa ido kagani daga yau daga Rana irin ta yau bazamu kuma zuwa Neman "Humaira gidan kuba insha Allahu, ballan Tana kasamu damar fadamana maganar DA taimaka dadi kaji KO?.</p><p><br /></p><p> Saurayin zai kumayin magana sai Y Y k Yace Jinan Malam don Allah kayi tafiyar NA nace munji kodole ne saika kasake maimai tawa iye?</p><p>Saurayi yatafi yana gunguni tareda cewa kada Allah yasa kujimana, kawai kunwani damun mutane dawata "Humaira Humaira sai kace wata yar gwal, ba "Humaira ba kodai Harawace kune kukasanta bamuba.</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yadawo DA dubanshi kanY Y K Wanda shima idonsa nakan Abdul-jabbar din,</p><p><br /></p><p>D"akyar ya iyabude bakinsa Yace Nawa wai meke faruwa ne?</p><p>Saboda Ban fahimci abunda wannan guy din yakefadaba, </p><p><br /></p><p> Y Y K Yace mushiga daga cikin mota zanfada maka abunda kefaruwa.</p><p>Baiyi musuba yabude mota daker ya'iyadaga kafafunsa yashiga saboda nauyin DA sukai masa, </p><p><br /></p><p>Y Y K Yasanar dashi duk abunda yafaru harzuwan dayake tayi ancewa batanan, yaci gaba dacewa ninasan Tana nan tadai kifito wane kawai zuwan kashe danyi shine akace Wanda akacemun wai ai "Humaira suntashi,</p><p>NA" girgiza kwarai da gaske domin kuwa bantaba tunani cewa gidan dasuke ciki nahaya neba, sai a wannan Rana nayi iya bincikena don nagane inda suka koma amma Allah baisana ganeba,</p><p><br /></p><p> Nayi tunanin nasanar dakai abunda kefaruwa.</p><p>To kuma sai natuna in harna nafada maka abunda kenan to kana iya shiga wani hali, domin kuwa nasan halinka sarai dasaka abu Cikin rai, don haka sai kawai nace Bari in barshi harka dawo sai musan abunyi.</p><p><br /></p><p>T"urkashi babbar magana wai dansanda yaga gawar soja, tashin hankali Wanda ba'asamashi Rana,</p><p>To shine yafaru da Abdul-jabbar domin</p><p> kuwa jiyayi kansa yana sarawa gawani daci dayaji bakinsa yayi,</p><p>Y Y k yadafa kafadarsa yace Nawa I hope kafahimci abunda nafada kuwa?</p><p>Ya kallesa DA idanuwansa dasuka kada sukai jajir kamar anwatsa masa barkono,</p><p><br /></p><p>Y"ace lallai nayi zurfi Cikin SON abunda narasa, saudayawa RAI yakan kwadaitu dawani BURI wanda yake ganin shine hanya daya TAK da rayuwa zata gudana Cikin kwanciyar hankali da NUTSUWA, amma sai Kaga Cikin Dan kankanin taki Mutum yarasa wannan abun to yaya kenan ZAIYI?</p><p><br /></p><p>Y Y K Yace sai yayi hakuri yabarma Allah komai domin kuwa shike maganin kowani irin matsala a rayuwa,</p><p>Ya girgiza Kai Yace gaskiya ne yanzu shikenan narasa "Humaira maisanyina kenan? Yace a ah wayafa damaka cewa karasa ta?</p><p>Insha Allahu indai "Humaira rabon kace to zamusan inda suka koma, aishi bawa bayataba cire tsammani Daga Rahamar ubangiji,</p><p>Saboda haka nan abunda nakeso dakai yanzu shine ka kwantar DA hankalinka kacire komai a zuciyarka,</p><p><br /></p><p>Don Allah kada kajama kanka wata cuta, dubi dai yanzu yanda kakoma sai kace Wanda ya shekara yana jinya, please kamai da komai ba komai ba kuma zamuci gabada binciken in da suka kuma dayardan Allah za muganta kajiko?</p><p>B"atare daya kalli Y Y K Yace muje kawai, </p><p>Yace ok yanzu LUFHAT PHARMACY mukanufa don kasayi maganin KO? Yace a ah gida zaka kaini, </p><p><br /></p><p>Yace bangane gida zankai kaba to shi maganin kumafa? Yace nafasa siya, Cikin matsananci mamaki Yace a ah nifa banganeba kanabufi baza kasha maganin ba kenan? Yace eh haka Na kenufi,</p><p><br /></p><p> Cikin bacin rai Y Y K Yace wai mai yasa kake yin hakane? Kana nufin zaka zauna daciwo ajikin ka? shin wai anfadamaka SO" haukane?</p><p>Ko kuma Kai kadai ne mutumin dayafara soyayya a duniya dazaka wani rikicewa mutane,</p><p>Toh" Bari kaji ingaya maka kafin Kai dubunka sunyi dabasu samu abunda suke soba sukai hakuri toh" ballantana Kai, </p><p><br /></p><p>Tsaya nan ka kashe kanka abanza awofi "Tana can kilama tamanta dawani Abdul-jabbar, tasamu wani Kai kana nan kana tunanin banza DA wofi don hak!</p><p><br /></p><p>Yadoka masa wani uban lhun daya sashi Yai shuru, yace Yusuf kakaini gida inzaka kaini idan kuma baza kakainiba to sai nafita maka daga mota,</p><p><br /></p><p>Y Y K yaja tsaki mtsww tareda cewa a ah tsaya don Allah Malam kar kafasa mun dodon kunne , yaja motar suka tafi yana Dada cewa oho dai Kai kasani niba abunda ya dameni,</p><p> </p><p>Y Y K baigama yin parking ba Abdul-jabbar, yabude Marfin motar yafita yamaida marfin dakarfi yarufe jikake gaffff!!!</p><p><br /></p><p>Y Y K yabi bayansa DA kallo daker yakedaga kafafunsa Yana tafita yana hada hanya, yatabe baki tareda cewa Allah Yai maka sauki yaja motar shi Yai gaba.</p><p>Ta kofar baya yashiga daki batareda kowa yasan shigarsaba, yazube kangado jabar tamkar anzubar dakayan wanki, yadafe kansa sakamakon sarawar dayaji Yai masa,</p><p><br /></p><p>Hakanan kuma yaji kirjinsa yana harbawa DA Sauri DA Sauri, yasa hannu da Sauri yadafe kirjin tareda cewa washhhhh. Saikuma yaga dakin yana juya masa A"hankali yarufe idosa daga nan kuma baisake sanin inda yakeba.</p><p><br /></p><p>To adai-dai wannan lokacin ne kuma Humaira tadauki ruwa abokiti daniyar tayi wanka, shigarta bayike dawuya sai kaji kwachauuuu!! </p><p>Bokitin yakucche ruwan yazube,</p><p><br /></p><p> gaba daya jikinta yadauki Rawa yayinda gabanta kedakan uku-uku , </p><p> umma dake tsaye bakin fanfo tace Lafia meke faruwa?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞LUFHAT CE💐</p><p>💞💞💐💐NU</p><p>💐💐💞N</p><p>💞💞SA</p><p>💐DA 💞</p><p> Page16-19💐</p><p> 💞</p><p>💐DA</p><p>💞💞SA</p><p>💐💐💞N</p><p>💞💞💐💐NU</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💐 MEENAT💞 💞UMAR💐 FARUQ💞</p><p><br /></p><p> </p><p>Dedicated to my Family Allah yakara mana k'aunar juna Amin,</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION </p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN: THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are opportune to be writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>T"ana tsaye jikinta sai rawa yake yayin da kirjita yaci gaba da bugawa, </p><p><br /></p><p> umma ta leka bayin tana cewa lafia? Cikin rawar murya tace ruuh wanh !! yaah zu beeeee!!!</p><p>Umma ta tsura Mata ido saka makon ganin datai jikinta sairawa yakeyi, tace wai Humaira saunawa zanfada miki inzaki shiga bayi kidinga yin Add'du'a? </p><p><br /></p><p>Da sauri tace umma wallahi inayi ko yanzuma nayi basan ya'akaiba kawai naji bokitin ya kubuche mun, </p><p>Tace toh" Allah yakwauta ni miko mun bokitin nazubo miki wani ruwan, ta dauko Tamika Mata har A"lokacin jikinta rawa yake, ta rintse ido tareda dafa kirjinta aranta take fadin innalillahi'wa'inna'ilaihir'raju'un,</p><p><br /></p><p>Umma tace gashi tabode ido da Sauri tace toh" tareda karban ruwan, tana wanka tana maimaita Kalmar innalillahi acikin ranta,.</p><p><br /></p><p>Umma tace toh"Abba "Humaira munga mota Allah yasa Albarka ya kuma kade tsautsayi da hasara, Yace to Amin kuma gobe insha zantafi Zaria yau yakamata natafi toh"amma naga yamma tayi, sannan kuma Malam Yace saidai nabari DA sassafe natafi, idan kuma nadawo mutafi yola akan maganar saukar daza'ayi domin kuwa Malam Yace dawuri zamu koma Chan yola din.</p><p>Tace yanzu duk agobe kakaje Zaria kuma kadawo katafi yola? Yace insha Allahu duk a gobe za'ayi ai Zaria kusane saidai ko yola, KO shima aiba'amota zamu tafiba jirgi zamushiga in Allah ya yarda, tace to Allah ya yardan mana ya kuma kaimu goben lafia to Amin, ya mike tsaye tareda cewa Bari na fita waje gurin Malam tace toh"</p><p><br /></p><p>D"a Sauri tashiga dakin fitowarta daga kwanka kenan, don haka da Sauri DA Sauri tagama shiryawa tana kokarin saka hijab. Umma tace waishin wannan saurin duk nazuwa Ina ne? Ta kalle ta tareda cewa umma banace miki zanje gidan su HANAH da HALEEH bah,</p><p><br /></p><p> Tace yanzu da yamman nan zakije gida jansu? Cikin sha'gwaba tace umma to aida gidan su Hanah dana Haleeh banisa, tace to Ai shikenan saikiyi sauriki dawo tunda kinsan bason fitar yamma nikeyiba, to umma Ai bazan dadeba yanzu zakiga nadawo natafi toh" kidawo lafia ki gaishe da Hajiya Hafsatu da Mariya toh" zasuji ungo kudi mota, umma inadashi, to karadai tace toh" nagode tafice tareda cewa sai nadawo adawo lafia Allah yasa,</p><p><br /></p><p>A ah budurwar kauye sai Ina kuma? tace Allah Malam indai baka daina ce mun budurwar kauye ba to zance nafasa auran, Yace au toh"kice kinfasa kigani yarinya idan ban hau buzunaba, saikinzo kina cewa don Allah Malam ka aureni yafadi Cikin zolaya yana dariya, tace wah nicezan rokeka saika aureni? yace eh Saikin Rokeni, tace a haka zanrokeka Kai duk furfura sai kace narasa maisona? </p><p><br /></p><p> Yace sosai ma kuwa yoh ke aibaki saniba ingaya miki irinmu masu furfura yan matan yanzu sukeso, saikiji suna cewa aini yan tsofaffun nan sun iya rukon aure Dan haka irinsu yansamu Na aura</p><p>Ta kyakyale da dariya tace Kayyah!</p><p><br /></p><p> Amma duk budurwar data auri tsoho kamar ka gaskiya taci baya,</p><p>T"abdijam nikam ina budurwa kamarta bazan auri tsoho ba, tab wane Mutum aini nan dakagan ni saurayi gal aleda Zan aura ba tsohoba irinka Kai duk furfura, </p><p><br /></p><p>Abba Yai gyarar murya da Sauri Humaira ta waiga Aikuwa sukai four eyes dashi , da gudu taruga hanyar kofar gida domin kuwa bata luradashi agurin ba Sam, </p><p><br /></p><p>ya kwala Mata Kira Adda! Adda!! Adda!!!, tace na'am zonan, tazo tanarufe fuska da hijab saboda kunya Abba yaji a firarsu da Malam, </p><p>Malam yace yar,nemakai, </p><p><br /></p><p>Abba Yace inazakije yanzu da yamma nan Cikin inda-inda tace um- umh dama- dama Malam yai dariya Yace zataje fadamusu kadawo, dariya Abba yayi shima Yace toh" shine za'aje yanzu DA yamma, why note dabaza abari har gobe ba? cikin shagwaba tace Abba please let me go I come back soon, Yace OK amma fakidawo dawuri, tace to tareda cewa Malam Dan tsoho bye saina dawo Yace Allah ya kiyaye tafice da sauri,</p><p><br /></p><p>Malam Yai murmushi yace shakiyiya yau bazatayi karatun yamma ba kenan, Abba yace a ah waidama tanayin Karatu shine tafita unguwa da yamman nan? </p><p><br /></p><p>Yace eh ta nayi, toh" barina kirata tadawo yamike da Sauri, Malam ya dakatar dashi tareda cewa a ah kyale ta kawai aibata wasa da karatu, Bari ka gani bayan sallah isha'i zakaga tazo tauka kasan yanzu hadda takeyi tana kokari sosai, saidai yau kam baza'agane kantaba tunda kadawo to sai tafadama wayannan kawayan Nata, wadan da kullun suna tare sai kace Aluf da Lam sannan hankalinta zai kanta,</p><p><br /></p><p> Abba yakoma ya zauna Yai murmushi domin kuwa yaji dadin Abinda Malam yafada, tabbas yasani tanada kokari karatu tunbata Kai hakaba Yace to shikenan Malam tunda kace a kyaleta, sukaci gabada tattaunawa akan al'amuran duniya me cike da abun mamaki da al'ajabi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A"kofar gidan su Hanah mai'adai-daita yasauketa bayan tabiyasa kudi, saita shiga cikin gidan tareda sallama Hajiya Hafsatu maihaifiyar Hanah ta amsa Mata dacewa maraba da Humaira tace yauwa sannu Hajiya inayini? Lafia qalau yasu "ummaki da "gwaggo Da "Malam? duk suna lafia sunce a gaisheki to madallah ina amsawa, yayanki" dai yana makaranta koh"? tace eh yana can toh Allah yabada sa'a </p><p>tace Amin,</p><p><br /></p><p>Hajiya "Hanah tana nan kuwa? Tace ta nan Cikin hausama kisameta yanzuta tashi nan wurin, tace to tareda hayewa sama.</p><p><br /></p><p>A hankali ta lallaba tarufe Mata ido, tafara laluben KO wane amma bata ganeba Can sai tajawo hijab dinta takai hancinta D"a Sauri tace Humeeh tasakar Mata ido suka fada kangado suna kyalkyala dariya Humaira tace yah akai kika ganeni? Tace kamshinki kawai naji naganeki,</p><p><br /></p><p> Tazaro ido alamar mamaki hada wani kamshi nakeyi daban Wanda yasa'ake saurin ganeni dashi? Cikin zolaya Hanah tace. "eh mana" (kasan cewar sarar dasuke fadakenan in sukai magana) kinsan special dinki yariga ya bataki da kamshinsa me shiga rai takai karshan maganar dayin dariya,</p><p><br /></p><p> Harara ta watsa mata tare da cewa banso iskanci zakifara KO? Cikin dariya kasa- kasa tace sorry me wasafa nake miki, Amma kinsan Allah bazancan wasa ba kamshinki yasa naganeki, tacigaba da cewa toh ya'akayine? Naganki da yamman nan kuma nasandai bamuda buki yau ko? Domin dai jiya munje munyi karatu balle ince ko school zamutafi, don haka yanzu Ina muka dosa kuma?</p><p><br /></p><p> Tayi dariya tace gidan Doctor muka dosa Hanah tace kin Rama kenan KO? tace "eh mana" toh" ya kikaji? tace very cool don haka indai gidan "D" nane am ready to go oya tashi mutafi,</p><p><br /></p><p> Humaira tace Toh" zakin mazallako wai da daga ciki rokon uban kwabo, inke kinshirya toh"mu bamu shiryaba yar gidan doctor, tace aini nayi zaton kunshirya ne danaji kince can muka dosa, toh" yar iska bamu shiryaba toh" wallahi gara kuyi kushirya inba hakaba kuma intafi nikadai , a haba dai kina iya Kai kanki kenan? Me zaihana tace eh nasanza ki'iya, yanzu kinsan me ne ne? </p><p><br /></p><p> Tace sai kinfada, saka hijab mutafi gidan su Haleeh nazo muku D"a albishir maidadi, tace DA gaske? tace Allah kuwa toh" tashi mutafi tasaka hijab suka fice,</p><p><br /></p><p>Haleeh tace yana ganku yanzu badai karatu zamuje bako? Hanah tace a ah kinga wacce tace inzo muzo gurinki waitazo mana da albishir mai dadi, tace ah Haba dai? Allah kuwa toh" feso mana muji man ta special tafada Tana Mata dariya Humaira tace nagane abun'naku iskanci ne to nafasa fadin albishir din,</p><p><br /></p><p> Haleeh tace tuba mukeyi Addan "Abba A"utan "Umma beben "yah Himu ta Hanah DA Haleeh Dan fadamana kinji? Suka kyalkyale da D"ariya tareda cewa "eh mana" tace albishirinku? sukace goro fari kalkal, </p><p><br /></p><p>Tace "Abba yadawo dazu wani irin ihu su kayi tareda rungumeta suna dariya, tace kadaku karyanifa kuyi ma umma ahasara, Hanah tace wayyo dadi jibi zamuyi Candy "Abba ya dawo yau kice zamu balle bishasha KO mai kikace? Haleeh tace kwarai kuwa da gaske tace kunsan abunda Abba Yace?</p><p><br /></p><p> Sukace saikin fada, cewa yayi idan jarabawar mutayi kyau to America zaikaini nayi karatu Na me kyau acan. Suka kuma saika ihu sukace wow ammafa zakifasa taro gaskiya Humeeh kin hadu wallahi , Abba ya birgeki sosai tace nikuma tawani bangaran abunbai birgeniba, </p><p><br /></p><p>Hanah tazaro ido alamar mamaki tace ke koh" saboda menene? tace saboda zanyi miss dinku dayawa fa kuma zamu koma yola dazama, dasauri suka hada baki sukace yoh meh? </p><p><br /></p><p>tace yola , Cikin sanyin jiki sukace gaskiya zamuyi miss juna sosai amma kuma dasauki tunda akwai Waya mun dinga communicaty ,Halee tace saukinta kenan ma, tasake cewa kunsan Allah ni mamaki nake wai zamuyi candy Sainaga kamar munyi kanana ,Hanah tace me wallahi bamuyi kananaba gawasu nan basuko kaimuba sunayin candy, </p><p><br /></p><p>Humeeh tace ah basai mugama karatunmu da sauri ba Haleeh tace eh kumafa hakane, sukaci gaba da tattaunawa akan yanda candy zaya kasance,</p><p><br /></p><p>Humeeh tace kubari natafi gida Cikin zolaya tace Haleeh su O oh fatace muyi Sauri mukaita gidan doctor inba hakaba kuma she take herself to him"</p><p><br /></p><p> Haleeh tace au hakane? Hanah tace eh dole naje gidan "D" dina kunsan inaji dashi sukace "eh mana" ta "D D" tareda tafawa tace ni kadaice bawata sukai dariya tareda mikewa suka raka Humeeh ta hau adai-daita sahu, sannan kowa tanufi gida tunda tsakanisu banisa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞💐LUFHAT CE💞💐</p><p>💞💞💐💐"NU</p><p>💐💐💞N</p><p>💞💞SA</p><p>💐"DA 💞</p><p> page20-24💐</p><p> 💞</p><p>💞"DA</p><p>💐💐SA</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐💞💞"NU</p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞MEENAT💐 💐UMAR💞 FARUQ💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p>This page belong to charming boy Muhammad Bangee's yola, Hey boy where are you? I have bee looking for you since kasan meh ?nayi miss shirmenka sosaifa 😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜missssSsss boyyyyyyy onceeeee againnnnn.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>-----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN: THE STRONGEST WEAPON</p><p>-----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are opportune to be writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da misalin 6:00 pm na yamma suna zaune kallo suke suna kuma Dan taba fira kadan kadan, sai Baba Lami tace Hajiya wai shin maigidana yadawo kuwa? tace aibakidade tafita sai naji motsin shigarsa daki kodana leka haryayi bacci, nace to kila hada maganin bacci suka bashi to koshifa? aiyasamu yadan huta tunda kila achan basu samun lokacin bacci, </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Baba Lami tace yoh inazasu samu lokacin bacci wanna aiki nasu kullum suna tsaye kamar hakori, Ai yanzu zasusamu damar hutawa da kyau tunda </p><p>aisungama KO?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tace yoh inafa sukagama sundai samu Hutu nadan wani lokacin lallai kam aisuna kokari sosai Mama ta tabe baki tace aiyaga zaya'iyane shiyasa yadau karma kansa wannan Aiki yaro sai shegiyar kafiya, kodayake ai barewa bata gudu danta Yai Rarrafe ko? Baba Lami tace wannan magana haka take, toh" Ai shikenan Allah yakyau tai murmushi tace Hajiya kenan kedai kamar bakison wannan aiki na megidana, to kuma Ai naga aikin nasu yanada kyau sosai, </p><p>tace to Allah yabashi sa'a akan dukan abunda yasa gaba tace toh Ameen Addu'ar dayaka Mata kiringayi masa kenan A"matsayinki Na UWA, tace hmmm baba Lami kenan toh" ai kullum inayimasa toh" Allah ya amsa tace Ameen, hakanan suka cigaba dafira har'akakira sallah magrib suka tashi don suyi sallah.</p><p><br /></p><p>Da misalin 10:30 pm 5nadare Suna Cikin kallo T.V atashar MBC 2 baba Lami hartafara hamma alamar tafara jin bacci, tace Hajiya maigidana baizo yadauki abincinsa bafa kodai saina Kai masane? gashi hartafara gyangyadi, Tace toh" nima bansan abinda yahana sa zuwa yaci abincinba, baba Lami tace kila duk gajiyarce tahanasa zuwa toh barina tashi nakai masa can dakin nasai,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Assalamu'alaikum maigidana? shuru maigidana shuru babu asma tace a ah maigidana yau wani irin bacci ne haka, shin wai kamayi sallah kuwa? ta kuma kiransa haryanzu shuru bai amsaba tace a ah wannan bacci Na lafia ne kuwa? </p><p><br /></p><p> Saita ajiye abincin takoma Cikin gida tana cewa Hajiya wanga bacci DA maigidana yakeyi yau nalafiya ne kuwa? Ina ta tadashi bai tashi ba wanda dakakira sa saudaya yatashi amma yau nakirashi yafi akirga bai tashi ba, </p><p><br /></p><p>Mama tace a toh" kirabu dashi mana idan yagaji DA baccin yatashi, tace a ah Hajiya wannan bacci bana akyalesa bane domin ni nagama kamar baya motsi fa,</p><p><br /></p><p> Da sauri tace baya motsifa kikace? tace Allah Kuwa zomuje kigansa Cikin hanzari tamike jikinta haryana Rawa tanufi dakinsa,</p><p> </p><p>Tace Kai! Kai!! kai!! harsau uku tunda dama bakiran sunan sa takeyiba, wani irin bacci kakeyi haka ne yau? ta bubbugasa akafa amma ko motsawa baiyiba tadafe kirji tare da cewa nashiga uku baya motsi kodai ya Mutu ne? I tama baba Lami duk tarikice tace a ah Hajiya bai mutu ba KO kikira abokinsa "yusufa yazo akaisa asibiti, amma kafin nan barina debo ruwa azuba masa KO suma yayi? dasauri taje tadauko ruwa mesanyi acikin fridge suka yayyafa masa, </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Amma har alokacin kodan yatsansa bai motsaba, tace Hajiya kira "yusufa yazo akaisa asibiti da Sauri tace toh takoma Cikin gida tadauko wayarta jikinta sai rawa yakeyi, Da kyar tasamu Y Y K yana zaune yana kallon labarai saiyaji wayarsa tana ringing kodaya daga saiyaga Ashe Mamace, </p><p><br /></p><p>Da Sauri yarage volume T.V ya amsa wayar Cikin ladabi haryana dukawa tamkar yana'agabanta, </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yai sallama tare da cewa sannu mama inayini? Da Sauri tace lafia qalau don Allah Kai maza kazo Dan"uwanka bayada lafia, Zumbur yamike tare Da cewa ya salam! mama gani nan zuwa yanzun nan, </p><p><br /></p><p>Koda ya isa gidan yatarar dasu tsaye chirko -chirko baba Lami sai kuka takeyi, I takam mama karfihali kawai takeyi yayin da sai salati take tafamayi, aranta kuwa saifadi take Allah dai yasa bamutuwa yayiba,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana ganinsa yace lnnalillahi'wa'inna'ilaihir raju'u Allahumma'ajirni'fimusibati'wa'aKlifni'khairan minah,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mama maiyasa meshi ne? tace toh wallahi bamusa niba, baikuma tsayawa dogon bincike ba kawai yasun gumesa yafece sukabi bayan sa yasashi mota yace mama kishiga mutafi tace a ah baiyajeba kutafi tare Da baba Lami kawai, yace shiga muje baba Lami tace toh bari nadauko hijab, da Sauri yashiga mota yatayar sukanufi asibiti,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda suka isa asibiti Da Sauri akateresu, suka nufi emergency room dashi,</p><p>Doctor I S G ne akansa yanata kokarin ceto Rayuwarsa, ankwashi awoyi kafin doctor yasamu yafar fado KO shima saida taimakon oxygen numfashin sa ketafiya dai dai </p><p>Doctor yazaro hand kacif daga Aljihun labcot dinsa yashare gumin daya tsatsufo agoshinsa, </p><p>Yaduba agogon hannun sa yaga karfe uku da rabi nadare ya girgiza Kai tare da kallon inda "Abdul-jabbar yake kwance lallai yadafe rabonda yaci karoda matsala irin ta "Abdul-jabbar.</p><p><br /></p><p>Baba Lami tuntana kuka haryayi shuru bacci nemaya dauketa, shikam Y Y K bai'iya runtsawaba saboda baiga fitowar doctor ba,domin kuwa baisan awani hali amininsa yakeba.</p><p>Da Sauri doctor yafito yanufi office din,Cikin sauri Y Y K yabi bayan sa zuwa office, yace doctor wai meyasami Dan uwana ne? yace gaskiya Y Y K bazan boyema kaba datake yasan Y Y K din, Abokinka yakamu da ciwon zuciya ,</p><p> Zumbur ya mike tare da cewa ciwon zuciya kacefa? yace kwarai da gaske domin kuwa hartafara kumbura,</p><p><br /></p><p>Sannan DA alama</p><p> abokin nan naka yabada taurin kai saboda yazo nan nafada masa abunda kedamusa harda magunguna masu kyau narubuta masa yasiya yasha before ciwon Yai worst Amma baiyiba, I don't know why?</p><p><br /></p><p>Shikam Y Y K mutuwar tsaye yayi ahankali ya zauna meye abunyi yanzu? </p><p>Yace abinyi kenan mubari yadawo hayyacisa tukun Kaga sai'asan yaza'yi,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yace some times "Abdul-jabbar yanada kafiya wallahi saida nacemasa muje asai maganin Amma yace shi Sam a ah, </p><p><br /></p><p>Please doctor don girman Allah katai makenu yanda Allah ya taimake ka,wallahi shikadai ne agurin maihaifiyarsa, karkabari yarasa rayuwarsa don Allah kaji? </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Doctor yace Y Y k ka kwantar da hankalisa insha Allahu zaisamu lafia,</p><p>Kasan cewa darayuwa D"amutuwa duk suna hannun Allah idan yazo saiya tashi idan kuma baiso hakaba toh" fabawanda ya'isa yatadashi kanaji ko? </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Y Y k ya kada Kai alamar gamsuwa,</p><p>D"domin shikam duk ya rikice yaja Dogon numfashi yace toh" shikenan ubangiji yabasa lafia, yace to Ameen addu'ar daza aimasake nan.</p><p><br /></p><p>Baba Lami baba Lami Y Y K yakira sunannta tai figigit tafara tare dacewa sannu yusufa ni har bacci yafada daukata, </p><p><br /></p><p>Toh" ya jikin maigidan Nawa dasuki daiko? Eh dasuki saidai doctor yamasa alluran bacci, insha Allahu zai farko normal tace toh Allah ya bashi lafia, yace Ameen mutafi nakaiki gida kiyi sallah tunda naga asuba takusa,</p><p>tace asubafa kace nadabo ? Yace eh baba Lamin tunda Hudu darabi yanzu aikiga kuwa asuba takusa KO?</p><p><br /></p><p>Tada gaKai Cikin tsananin mamaki yanzu har sukai asuba,</p><p><br /></p><p>Sun iske mama tsuru tsuru domin kuwa tunda sukatafi bata rintsaba, tana tarokon Allah yabasa lafia,</p><p><br /></p><p>Yai Mata bayayin komai saidai yabiye Mata abinda kedamusa gudun karta daga hankalita, tace to shikenan Allah yabar zumunci, katafi gida Kaga iyalinka shikuma ubangijit yabasa lafia Yace Ameen idan nayi sallah zuwa karfe shida sainakoma tace tace toh nagode kwarai DA gaske, bakomai mama aidani dashi duk dayane, toh ka gaishe dasu Jamila Yace zasuji yafice daga gidan,</p><p><br /></p><p> WASHE GARI</p><p>D"amisalin 8:15 Am nasafe , Alh mahamud ne yafito Cikin shirinsa natafi ya Zaria, </p><p>Sungama magana da Malam kenan yana kokarin bude mota saiga Humaira dagudu tafito Cikin gida Cikin shirinta tsaf,</p><p><br /></p><p>Malam ya kalleta yace su budurwar kauye sai'ina kuma DA sassafan nan haka? Tace Malam kadainafa nibanaso ,Yai dariya Yace a ah nikam bazan dainaba,</p><p><br /></p><p>T"ace to shikenan Cikin sha'gwaba tace Abba nima zanije Zaria naga "yah Himu nadade bangasaba,</p><p><br /></p><p>Malam Yai murmushi yace aukema Zaria kikeson kije,? </p><p>Tace eh kaima zakajene? Yace a ah kedai kisamu atafida ke,tace aidani Abba zaune KO? Cikin wasa Yace a ah ni bazanje dakeba,</p><p><br /></p><p>Tafara bugakafa Cikin sha'gwaba tace don Allah Abba katafi Dani nayi miss "yah Himu sosai, yamakale kafada alamar a ah tace please Abba kaji?</p><p><br /></p><p>Yace toh zagaya kishiga mota tace yauwa Abba Na thanks ta kalli Malam tayi dariya sannan tace Kaga Abba Na zaya tafidani kaiko baza'a tafida kaiba, yai dariya Yace basai nace afasa tafiyar dakeba tace Ai Abba Na bazaifasa tafiya Dani ba KO?</p><p><br /></p><p>Yai murmushi batare Da Yace komai ba sukai sallama da Malam yaimusu fatan Allah yakiyaye hanya a dawo lafia kuma agaida masa da Abokinsan, Abba Yace zaiji insha Allahu yaja mota suka tafi.</p><p><br /></p><p>💞💐LUFHAT Luv yours all FANS 💞💐</p><p>💞💞💐💐NU</p><p>💐💐💞N</p><p>💞💞SA</p><p>💐"DA. 💞</p><p> Page25-28💐</p><p> 💞</p><p>💐"DA</p><p>💞💞SA</p><p>💐💐💞N</p><p>💞💞💐💐NU</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞MEENAT💐 💐UMAR💞 FARUQ💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wannan page nakune ADUK INDAKUKE AFADIN DUNIYA NAN,inafata gaisuwata zata iskeku 2006 graduated from GIRLS DAY SECONDARY SCHOOL kontagora Niger state, AMEENAN kuce l'm really miss yours LOVE ALLLLLL💞💞💐💐💞💞💐💐💞💞💐💐💞💞💐💐💞💞💐💐💞💞💐💐💞💞💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>------------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>------------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are opportune to be writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tafiyar awa dayace takaisu garin Zaria Cikin A.B.U Abba yaifaki agefen wata bishiya me yawan ganye bayan yakashe motar, sai ya kalli gefenda "Humaira take baccinta kawai take kwasa ba abinda yadameta,</p><p><br /></p><p>Dama" tun ahanya suna Cikin fira yaga tafara gyangyadi Yai murmushi tare da kada Kai Yace Adda! Adda!!,</p><p><br /></p><p>Ta bude ido ahakali tayi mika tare da salati sai kuma tace washhh Abba nagaji,</p><p><br /></p><p>Ya bude ido alamar mamaki Yace keh! Adda banason laziness saikace keki Kai driving dinmu? </p><p><br /></p><p> Tace Abba Allah idan mutum yadade zaune duk saiyaji yagaji,</p><p><br /></p><p>Yai dariya Yace Adda Humaira tawa Haryanzu dai Ragwancin nan baira geba? </p><p>Cikin sha'gwaba tace ummh Abba ah yakatseta dacewa Adda kenan, </p><p><br /></p><p>Yanzu dai kalli can kiga "gawani saurayi Can yaza shiga Hostel kirasa saimu basa sako yakira mana "Yah Himu dinko? </p><p>Ta kalli Abba tare da cewa a ah Abba kakirasa awaya mana, ya girgiza Kai alamar A ah, tace why? "Yace bcos I want to give him a surprise, ta kyalkyace da dariya tace yes Abba, barina kirasa tafada tare da fita daga motar. "Saurayin yace ma Abba ina kwana? Yace Lafia qalau ya sunan malamin ? Saurayin Yai murmushi tare da cewa sunana saminu, Abba yace Malam saminu ya karatu? Yace Alhamdullah, toh" masha'Allah, "dama don Allah munason ne kakira mana wanine a Hostal din nan idan kashiga. </p><p>Saminu yace hala kuna tane man sa a waya Baku samuba ko? ya Yamutsa fuska tare da jan tsaki kadan mtsww Yace wlh matsalar net work ne, </p><p>Abba Yai murmushi Yace bamu kirasa ba just we want to give him surprise, </p><p><br /></p><p>Saminu Yai dariya Yace ah lallai zaku basa mamaki tunda baisan dazuwan kuba, toh" ya sunan sa? Humaira tafada masa Yace ok nagane sa yanzu zaku gansa in Sha Allahu, Abba Yace toh" mun gode sosai, ya Nufi hostal ita kuma Humaira ta koma Cikin Mota ta zauna.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A" hostal saurayin nan me suna Saminu shine yake tafan ihun kiran "IBRAHIM MAHMOUD IBRAHIM YOLA.</p><p>Saida saminu yakusa zowa dai dai bakin wata kofa An rubuta Room 13 sannan Ya tsaya ya Kara kiran sunan.</p><p>"Yana kwance yana karatu saiyaji kamar Ana kiran sunan sa Yai shiru yana saurare tabbas shi din ake Kira don haka sai yai zumbur yamike yafito yayi tsaye abakin kofar Room dinsu,</p><p>A dai dai lokaci da Saminu ya iso</p><p>Suka hada ido sukai ma juna murmushi Yace ya akaine "saminu Naji kanata kiran sunana ne?</p><p>Yace"kanada baki Awaje,</p><p>Da Sauri yace suwane ne? yace wani ne shida wata yarinya, Yace OK saminu thanks bari naje nagani kila "Malam ne shida "Ashaty.</p><p><br /></p><p>Tunda'ga nisa ta hango sa ya nufo gurinsu, da Sauri tafito daga motar tanufi gurinshi, yace oyoyo esha bebeh tare da Rungumeta aka fadarsa, ya kalleta yana murmushi I tama tanayi yace keda wane? </p><p>Domin naga ba "Malam bane I hope dai ba Wannan "Abdul-jabbar din nan bane yadawo da munanan kalamansa na yaudara?</p><p><br /></p><p>Ta bata rai sannan tace kai yah Himu ni' inaruwa "dashi Aini tun'tuni na manta dashi, yace eh dama Aini sonake kimanta dashi" domin nagane shi din mayaudari ne, saboda haka nan bake bashi kinji KO?</p><p>(A ranta tace sorry yah Himu I can't forget him)</p><p><br /></p><p>A fili kuma sai ta dan Taturo baki tare da cewa toh" aini dama narabu "dashi, yace yauwa my little sister shiyasa nake Kara sonki saboda kina jin maganata,</p><p>Sukai dariya tare da karasawa gurin motar. </p><p><br /></p><p>Ya juya baya"yana amsawa waya don haka ne yah Himu baigane shiba,</p><p>A hankali yajuyo dai dai lokacin da ya gama amsa wayar, yaje fata Aljihu yai murmushi i tama Humaira murmushi take.</p><p><br /></p><p> Shi"kam yah Himu mutuwar tsaye yayi saboda tsananin mamakin ganin Abban su,</p><p><br /></p><p>Ya"runtse ido yabude ya kuma runtsewa yabude sannan ya kalli Humaira yace sister mafarki nake KO da gaske ne? </p><p><br /></p><p>Tai dariya tace yah Himu kenan you are not a Dreaming oh Na reality fa,</p><p>Yace No! No!!No!!sister pinch me now saina tabbar l am dream or not,</p><p>Dariya tayi tare da kaima sa tsunkuli a hannun sa</p><p>Da Sauri yace yesss....lallai da gaske ne ba mafarki nake ba, sai kuma yasa hannun sa dai dai inda ta tsunkule sa Yace washhhh...</p><p>Gaskiya sister kin pinch nisosai fa,</p><p>Tai dariya tare Da cewa sorry yah Himu toh" aikai ne kace Na tsunkule ka" Yai dariya tare da kallon inda</p><p>Abba yake tsaye yana murmushi, Abba yabude hannu tare dacewa zonan baba Na nidin ne da gaske ba mafarki kake ba,</p><p>A hankali ya karasa gurin shi yafada kirjin sai tare da sauke ajiyar zuciya yace Abba meyasa katafi kabarmu tsawon wani lokacin ba kadawa garemuba?</p><p>Abba ya Dan bubbugi bayan sa kadan yace insha 'Allahu nadawo kenan bazan Kara tafia maitsawo irin haka nabar kuba kaji KO? Yace toh" Abba.</p><p><br /></p><p>Abba Yace Adda bude mota kidauko mana dadduma sai muzauna, tace toh</p><p>Ta ciro ta shinfida suka zazzauna.</p><p><br /></p><p>Bayan sungaisa sai Abba yake tambayan sa ya karatu? Yace lafia lau, komai Na tafiya dai dai ko ? Yace eh Alhamdullah bah matsala, toh" ai haka nan a keso.</p><p>Sukaci gaba da hirarsu akan lamarin karatu Abba ya mika mishi key mota yace ka bude but akwai provisions Dana kawo maka da kuma tsarabar ka ta America, nace adebo maka sauran kuma sai kadawo.</p><p>Ya karbi key yana dariya yace nagode Abba yabude but din cike yake da kayan provisions, yace Abba duk nawa ne wannan nikadai? yace eh duk nakane KO sunyi kadan Ne akaro maka wasu?</p><p>Ya bude baki Cikin mamaki yai dariya sannan yace a ah ni sunyi Mani yawa, yace A ah basuyi yawaba tunda kanada friends sai kuyi amfani dashi duk.</p><p><br /></p><p>Yace toh" mun gode sosai Allah yakara budi Yace ameen.</p><p>Humaira ta tayasa fitoda kayan a Cikin kayan ne yaga wata yar karamar cooler me kyau ya dauka yana juyata yace Abba wannan kumafa me ke Ciki? Yace af harna manta sakone "daga "gwaggo tace akawo maka.</p><p><br /></p><p>Yace Allah sarki "gwaggo kaka tawa nagode sosai ya zauna tare da bude cooler sai yaga soyayyen naman kaza da miyar tumatur, Yace Kai! tsohuwar nan ta'iya cin dadi fa ya yagi naman yakai baki ya tauna tare da lumshe ido sannan yace Kai! wannan aisai yasa kunnan Mutum ya tsinke saboda dadi,</p><p><br /></p><p>Humaira tana dariya tace yah Himu nima Dan bani inci inji, Yace a ah nikam bazani bakiba tace please yah Himu Kaga raina yabiya, Yace toh" ungo ya gutsuro Dan karami Yace kada kici dayawa Cikin kiyayi ciwon KO Abba?</p><p>Dariya yake masu tace Dan wanga zaka bani? nikam bazan Ciba Yace Allah kici akwai dadifa bude baki inbaki, tabude yasa mata ta tauna tareda cewa ummh! ummh!! gaskiya akwai dadi toh" Dan karamun kadan, yace nakiya tace don Allah kaji my bros?</p><p>Ya harareta Cikin wasa Yace naki wayon naki wato kicinye mun abina sannan kitafi kibarni Ko? tace Ai bazan cinye ba, yace toh shikenan ya'aje sukaci gabada ci suna fira.</p><p><br /></p><p>Sunyi nisa da cin naman sai ya kalli Abba Yace abba idan yarinyar nan tacinye Mani nama toh" fa bazatabar school din nan ba saita biyani abina.</p><p>Abba yai murmushi Yace aizata biyaka ne shiyasa take taci ,yace toh" da dai yafi kam.</p><p><br /></p><p>Can Yace af aina manta sister ya jaravawa?</p><p>Ta kalle sa tace aina zata bazaka tambaye niba ne shiyasa Na kyale ka, Yace sorry Allah murnan ganin Abba ne yasa namanta toh"yaya? </p><p><br /></p><p>Tace Alhamdullah gobe Nema ai zamu rubuta last paper, yace toh" Allah yabada sa'a tace Ameen.</p><p><br /></p><p>Can kuma sai ya kalli Abba Cikin tsokana Yace Abba yarinyar nan tayi karama da yin candy, kamata yayi amaida ita J s s two,</p><p>Kadan yarage ta kware saboda jin abinda yah Himu yafada ,dariya yake mata sosai sannan ya mika mata eve water (dayake hada su Cikin provisions din)yace ungo kisha don naga kin kusan kwarewa toh" ni dawasa nake miki,Saidai tasha ruwan tukun sannan tace yauwa yanzu naji magana dakam banjiba.</p><p>Wane keson Allah yakai sa gaba sannan kuma yadawo baya? Aiba wanda yakeson haka KO</p><p>Abba? </p><p><br /></p><p>Yace eh tareda kallon agogon hannun sa lallai innabi tanaku" toh' KO yau bazani tafi yola ba, yah Himu Yace Abba tun yanzu zaku tafi? Yace eh duba agogo kagani, yaduba da Sauri yamike yace Abba 11:30am yanzu kuma inada test around 12:00pm </p><p>Yace toh" aisai ka hanzarta katafi muma yanzu zamu tafi. yace toh" Ku "gaida su "umma da "Malam ita kuma "gwaggo kaKa ace mata nagode sosai sannan Ina gaida lta da kyau DA kyau waidaga ita bakari yakara she maganar dayin dariya suma dariyan sukai,</p><p>Abba Yace kaga gawasu" samari nan zuwa kace su tayaka daukan kayan yace toh" Abba Yace kafa maidai hankali akan karatu banda shiririta kajiko? yace toh" Abba insha'Allahu,</p><p>Samarin nan suka tayasa daukan kaya sukanufi Hostel su kuma suka shiga mota abba yaja suka tafi.</p><p> </p><p>**********************</p><p>Yanzu 12:00pm narana amma harzuwa wannan lokacin "Abdul-jabbar baifar fadoba, hankalin Y Y K yatashi sosai yarasa abinda kemasa dadi Doctor yafada kafadar shi tareda cewa l am sorry to say bincikena tanuna Mani cewa "Abokinka yataba irin wannan ciwon</p><p>Sannan kuma yakai kusan awa biyar asume Wanda ta dalilin hakane yahaifar masa Da shiga koman Wanda bazance maka ga lokacin da zaya farfadoba,</p><p>Yana iya kaiwa gobe jibi one week two weeks three weeks Kai Harnan da one month yana iya kaiwa batare da ya farfado ba Koma yawuce fiyeda wayan kwana kin Dana lissafa maka, domin kuwa babu yanda baya zuwawa Mutum</p><p>Saboda haka saidai kawai muci gaba da yimasa addu'a Allah ya basa lafia.</p><p><br /></p><p>Cikin tsananin tashin hankali Y Y K yadora hannu akai Yace yah salam!!! Sai kuma yafita Da Sauri daga office din,</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> 💞💐LUFHAT Ce Love friendssssss💞💐</p><p>💞💞💐💐NU</p><p>💐💐💞N</p><p>💞💞SA</p><p>💐DA 💞</p><p> page29-32💐</p><p> 💞</p><p>💐"DA</p><p>💞💞SA</p><p>💐💐💞N</p><p>💞💞💐💐NU</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💐MEENAT💞 💞UMAR💐 FARUQ</p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p>-----------------------------------------</p><p>PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN: THE STRONGEST WEAPON</p><p>--------------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are opportune to be writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tsaye yai abakin kofar office din tare da fitoda wayar sa daga Aljihu, yafara neman lambar "M.B daya daga Cikin abokansu wato Muktar Bello, don yasanar dashi abinda kefaruwa domin shikam yarasa abinyi gashi "Alh sa baya kasar, Kira daya M.B yadauki wayar Bayan sun gaisa yake sanar dashi cewa "Abdul-jabbar fa bayada lafia yanzu hakama suna asibiti saboda haka yazo yasa meshi,</p><p>Daga can M.b yace gashi nan zuwa yanzu insha'Allahu wani Asibiti ne? Y Y K yafada mishi yace gashi nan zuwa yace toh saikazo din,</p><p>Bayan yagama Waya da M.b sai kuma yafara neman number dayan abokin nasu (Wato "Abdul-ganiyu Delta boy kamar yanda suke kiran sa kasan cewarshi mutumi Niger delta)bayan sun gaisa yakefada masa rashin lafiyar "Abdul-jabbar.</p><p>Shikam delta boy tambaya yake meyasa "mesa kuma? jiyafa muka dawo lafia kalau koda yake tuncan naga "yana ramewa idan na tambaye sa me ke damunsa sai yace bakomai,</p><p><br /></p><p>Nan Y Y K kesanar dashi Abinda "doctor yafada, Delta boy yai salati tare da cewa lnsha'Allahu yana nan zuwa jibi Da sassafe Allah "yabashi lafia Y Y K yace toh" ameen sai kazo din sukai sallama yakashe wayar.</p><p><br /></p><p>Yayi shuru yana tunanin ta yadda zai bulloma wannan lamarin ,</p><p>Ahaka M.b yasa mesa bayan sukara gaisawa sai Y Y K yajasa zuwa dakin da Aka kwantar Da "Abdul-jabbar din, M.b ya tsorata daganin yanda "Abdul-jabbar yakoma Cikin lokaci kankani</p><p>M.b yace nifa ban san'ma yadawo ba?</p><p>Y Y K yace hmmm kaidai bari jiyafa "yadawo dasafe nan yasanar dashi abinda "doctor yafada, M.b ya numfasa yace toh yanzu meye abinyi?</p><p>Y Y K yace abinyi kenan mu tsaya muga hukuncin ubangiji, M.b yace hakane toh Allah "yabashi lafia yace toh Ameen, </p><p>Sukaci gaba da tattaunawa akan ciwon "Abdul-jabbar din.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau asabar kuma a yau ne su "Humaira ke graduated, don haka gabada basu samu nutsuwa ba saboda zirgazirgr dasuke tayi sai yanzu,</p><p><br /></p><p>Zaune suke su uku Adakin "gwaggo Hanah Haleeh da ita Humeeh kasan cewar Anan suka tsara zasuyi shirinsu tuda daganan gidan "Malam zuwa school din banisa,</p><p>Sanye suke Cikin wayansu tsararrun dogayan Rigunan yadin materia ne pink colour yanada ratsin marun colour dinki Rigar daga sama tadan matse kadan sai kuma daga kasa tabude sosai gaskiya dinkin yai kyau sosai, "Aunty Habeeh ce ta dinka masu material "Aunty Habeeh ta kasance yaya ga Haleeh, </p><p><br /></p><p>Kai! yam'matan dai acan'acan abinsu gwanin sha'awa ko wacce tayi ruling da mayafi marun colour, fuskar nan "tasu koh hmmm tasha make up harta gaji sai zuba daddadan kamshi suke Kai!! yam'matan dai kam tubara kallah masha'Allah kamar kadaukesu ka gudu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yah Himu yadaga labulen dakin tare da cewa toh malamai sarakan kwalliya in kungama sai kufito mutafi, shima cikin shiri sa tsaf (kasan cewar yazo tunjiya Friday shida wani friend din sa me suna "Idris Shehu Dan Zaria ne, yarako shine sunzo saboda grdt din idan angama su koma gobe lahadi kasan cewar "Humeeh ta damesa akan Dole sai yazo)</p><p><br /></p><p>Ga badaya suka amsa da cewa mungama "yah Himu yace toh aisa kufito suka ce toh" gamu nan zuwa,</p><p><br /></p><p>Da Sauri Humeeh tabi bayanshi tace yah Himu yace yap tare da juyowa ya kalleta yadai? tace wane zai kaimu school din? ni yabata amsa, yah Himu yaushe ka'iya mota? yace yau tadan zaro ido kadan alamar mamaki tace yaufa kace? Yace Yesss kuma ka'iya sosai? Ya harareta sannan ya dungure mata kai tareda cewa toh" malama idan zaku fito nakaiku toh" kufito saboda inason nadawo nakai Abba, idan kuma zaki tsaya dogon question" toh oya bismillah, yafita yabarta nan tsaye itakam bin bayansa tayi da kallo Cikin mamaki takama haba tare da cewa tabdi yanzu "yah Himu zayi driving dinmu? hmmm toh" Allah yakaimu Lafia nima danake gefe nace to Ameen.</p><p><br /></p><p> Tace hey bebes kufito mutafi "yah Himu nachan yana jiranmu, sukace toh tare da mikewa tsaye KO wacce nakara kallon kanta amudubi taga inda beyiba ta gyara,</p><p>"Gwaggo dake tsaye tana kallonsu tai dariya tace kai yam'matan nan aiba sai kun sake duban kankuba kun hadu sosai, suka kyalkyace da dariya sukace " eh mana" sauran hadu warmu Da Allah Ko? tace toh lallai sauran shikam,</p><p><br /></p><p> Amma dai yanzu kam wajan Hadu warku da samari yayi dai dai,</p><p><br /></p><p>Sukace ahhhh gwaggo tace eh wannan kalliya yau haka aisai ba samari, sukace Kai! gwaggo mudai kinga tabiyar mu,</p><p>Sukafita suna dariya itama dariya take.</p><p><br /></p><p>Tafe suke Cikin motar "Abba parado jeep yah Himu ke driving dinsu ldris nagefen sa sukuma suna baya, fira suke shida ldris yayinda su Haleeh kesa baki jefi jefi itakam "Humeeh gum tayi Da baking ta domin kuwa gaba daya a tsorace take kodama ita din matsoraciya ce ta gaske, don haka take gani kamar "yah Himu zaije yawatsar dasune kawai tunda dai ita batasan ya'iya mota ba,</p><p><br /></p><p>Saidai tasha mamaki lokacin da suka hau kan titi saboda yadda taga yana sarrafa sitiyar motar, domin kuwa kallo daya zakai masa ka tabbatar dacewa yadade da kwarewa atuki.</p><p><br /></p><p>A hankali tai ajiyar zuciyar da harsaida yajita kasan cewar ta gefenshi take,</p><p>yai dariya tareda juyoda mudubi ta dai dai saitinta dama yana kula da ita tunda suka shiga dayake yariga yasanta Sarkin tsoroce, yace yadai sister? ta kalleshi tareda turo baki Cikin sha'gwaba tace nothing,</p><p>Ya kyalkyace dariya dai dai lokacin da yake kokari shiga school din yace matsoraciyar yarinya kawai, ni narasa "inda kika samo wannan tsoro yarinya sai shegen tsoro sai kace farar kura, sai kace ba bafillataba,</p><p><br /></p><p>Dai dai lokacin dayai parking su fito Hanah Da Haleeh sai dariya suke mata hada Idris,</p><p><br /></p><p>Yah Himu ne yazo kusada ita saida yalalubi kunnanta sannan yadan murda kadan yace keh wai Afada miki fulani sunada tsoro ne?</p><p><br /></p><p>Tace washhhh yah Himu you hot me fa,</p><p>Yai dariya tareda cewa sorry yadan rungumeta A kafada yace kina mamaki ne na'iya driving? "Idris ya koya mani tun lokacin danaje school farko farko gashi yanzu na'iya sosai,</p><p><br /></p><p>Yace bari mukoma mudauko " Abba tace toh" suka shiga mota sukatafi su kuma suka nufi inda inda za'a gudanar da programs.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A hanya Abba yace ma yah Himu su tsaya wani shop complex yanason ya sayi Waya, Yace toh" "Abba nizaka saima Waya?</p><p><br /></p><p>Abba yace no I want to buy to my "doughtes yace Abba toh" mu kumafa? yace a ah,</p><p><br /></p><p>Dasuka shiga shop din Abba yace Waya yakeso yasiya akawawo masa yazabi iPhone7 guda uku masu kyau, afada masa kudin yabiya,</p><p><br /></p><p>Yah Himu yace Abba remains us Abb yace no! yah Himu yace why? saboda you're too Young's to carry the phone,</p><p>Yai dariya yace Abba toh" idan mu kanana ne to sukumafa? Abba Yace ah "sukam ai big girls ne bakada yau suke candy bah,</p><p><br /></p><p>Dariya suke sosai dagashi har ldris saboda jin abunda Abba yafada,</p><p><br /></p><p>Shima Abban dariya yai cikin wasa Yace ko ba haka bane? ldris Kai yakada yana dariya yace hakace Abba,yah Himu yace toh" shikenan tunda "su yan candy ansiya musu toh muma yan high sai asaya mana,</p><p><br /></p><p>Yace a ah nakiya! yace please Abba buy us, Yace toh kudauka,</p><p>Suma suka zabi manya manya masu kyau yabi kudi sutaka tafi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda suka isa school din har anfar gudanar Da programs din don haka suma sukabi layi A hankali Cikin tsari da nitsuwa ake tafiyar da komai har akagama, yayinda su Humeeh "suka karbi kyaututtuka masu yawa kasan cewar su dalibai masu hazaka da kuma tsafta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan agama ne suka koma gefen wata bishiya suna daukan photo hada Abba da kuma Aunty "Habeeh dayake tazo itama da kannan Hanah da kuma wayansu kawayan su.</p><p><br /></p><p>Bayan sun gama daukan photos sai Abba yabasu Waya yace ganasa kyautar nan aiko sukasa ihun murna tareda rungu meshi dariya yake yace toh yanzu idan Ku ka kada Abban naku Cikin mutanefa? </p><p><br /></p><p>Suka sake sa suna dariya tareda tsugunnawa sukace Abba mun gode Allah yakara budi, yadafa kawunasu Yace kutashi-kutashi Allah yaraya manaku yasa maku Albarka ya kuma Baku ilimi mai amfanin Al'umma suna dariya sukace Ameen Abban mu.</p><p><br /></p><p> Saida yah Himu yakai "Abba gida sannan yadawo ya kwashesu yakai su "Hanah da "Haleeh gida jansu sannan suka tafi gida</p><p><br /></p><p>******************</p><p>Bayan kwana biyu da misalin 4:00pm su uku ne tsaye ajikin window dakin Da aka kwantar Da "Abdul-jabbar Y Y K M.b Delta boy, saboda yanzu doctor ya Hana kowa shiga dakin saidai kowa yazo tsaya ta window "ya gansa.</p><p><br /></p><p>Delta boy Yace ni gaskiya ciwon "nasa yana bani tsoro yaufa satinsa daya kenan ahaka? watoma tunda nakoma gida haryanzu baya moving?</p><p><br /></p><p>Y Y K yace kaidai bari one week kenan Amma hattada dan yatsan sa bata working, hmmm kaidai lamarin saidai gyaran Allah kawai.</p><p>M.b yace ni wallahi "Mama kebani tausayi Acikin yan kwana kin'nan duk tarame saboda tsabar zullumi Da fargaba Y Y K yace nima tausayi take bani sosai wallahi,</p><p><br /></p><p> Delta boy Yace Hmmm aidole atausaya Mata" domin kuwa shikadai ne mata gaba da baya kagako dole tayi fargaba da zullume,</p><p>Gashi kuma bata" fada masa kowa ne mahaifinsa ba, inaga harda tunnanin haka yasata zullumen halin dayake Cikin,</p><p><br /></p><p>M.b yace hakane kumafa toh" yanzu dai mucigaba dayi masa" Addu'a kamar yadda muka saba Allah yabasa" Lafia sukace Ameen.</p><p><br /></p><p>💐LUFHAT ce Luv Fanssss💞</p><p>💐💐💞💞NU</p><p>💞💞💐N</p><p>💐💐SA</p><p>💞DA 💞</p><p> page33-35💐</p><p> 💞</p><p>💐DA</p><p>💞💞SA</p><p>💐💐💞N</p><p>💞💞💐💐NU</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞MEENAT 💐U. MAR 💐FARUQ💞</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>This page belong to All people of PEN WRITERS ASSOCIATION ✍🏾 ANA TARE kugane GUYS irin Very tied din nan Faaaaaa!!!😀😀😀</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen Zain</p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS -ASSOCIATION</p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN :THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Y Y K yace nifa Ina ganin harda san "yarinyar nan daya kwallafa A zuciyar saha dashi keda munsa,</p><p><br /></p><p>Delta boy yace hmmm tabbas harda shi domin kuwa nizan fada maka kaga "yanda yatada hankalisa saboda yakira number ta baijeba? yiyayi kamar wani zararre naita lalla "shinsa inabashi hakuri akan cewa yabari mana harmu dawo gida tunda kadan yarege mukarasa amma ko "ya saurareni sai abun yafara bani haushi ni kuma kawai saina kyale shi tunda yaki ya saurareni Kai tun "yanabani haushi har yako mabani tausayi, Dana gane cewa bayin kasa bane Allah ne ya jarabeshi da San "Humaira Dan haka saina farayi mashi Addu'an Allah ya yaye mishi,</p><p><br /></p><p>Ameen sukace Nan shima Y Y K kesanar dasu abinda yafaru tun kafin "sudawa har zuwanda sukai gidan su Humaira.</p><p><br /></p><p>M.b yanisa yace gaskiya "Abdul-jabbar yana San yarinyar dayawa, kuma har yanzu bakuji inda "suka komaba?</p><p><br /></p><p>Y Y K yace inafa muka sani Delta boy yace inafa zasu sani kaidai bari kawai koda cewa akai za'aje "nemanta Toh ta'inama za'afara? tunda garin Kaduna ba kadan bane, hmmm kaidai Allah yai mana maganin dabazamu yiwa kan'muba shi kuma Allah yabashi lafia sukace Toh Ameen,</p><p> Y Y K yace Mujenku sai zuwa anjima kuma sukace Toh.</p><p>Nasan dai me karatu yaso yasan wace wannan "Humaira da soyayyar ta keta wujujuwa da Abdul-jabbar hartana KO Karin Kai sa barzahu.</p><p>yakamata kam muji KO,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>WACECE HUMAIRA?</p><p> Aishatul Humaira shine cikakken sunanta ta kasace ya ga Alh Mahamud Da Hajia Asma'u wadda suke kirada Umma, su biyu ne agurin iyayensu ita da yayanta lbrahim wato yah Himu,</p><p><br /></p><p>"Alh Mahamud asalinshi mutumin Adamawa ne aikine yakawo shi garin kaduna inda yake aikin bank yana zaune A unguwar malali,</p><p>Alh Mahamud yahadu da "Asma'u ne akan hanyar shi tazuwa aiki Asma'u diyace ga Malam Garba me Almajirai, Cikin hukunci Allah soyayya me karfi tashiga tsakanin Mahamud DA Asma'u har Allah ya kaddara Aure tsakanisu, suna zaune Cikin aminci da yardan juna, inda yaci gaba dazuwa aikinshi Cikin hakane,</p><p><br /></p><p> Allah ya'azurtasu da yara biyu wato lbrahim da Aishatul Humaira lbrahim yaci sunan kakanshi ne nagurin Abba itama taci sunan yayar Abba shiyasa "yake kiran ta Adda.</p><p><br /></p><p>" su Humaira suntaso Cikin soda kaunar iyayensu itada lbrahim wato "yah Himu Wanda itane ke kiran shi da yah Himu din,</p><p><br /></p><p>Iyayansu Na matukar kaunar su musamman dasu kaga tunda gasu Allah bai Kara basu haihuwaba,</p><p><br /></p><p>Don hakane "suka dauki so DA kauna suka Dora musu duk abunda Abba yamu Toh Na yah Himu ne da Humaira don haka Cikin gata suka tashi fache! fache!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yah Himu yana aji biyar Na secondary ita kuma Humeeh tana jss two,</p><p><br /></p><p>Kwatsem wani bakon lamari yasa mesu bank din da Abba yake aiki wasu makudan miliyoyi suka nace,</p><p><br /></p><p>A lokacin kuma Abba shi ne manager Bank din don haka yashiga matsanaci tashin hankali, KO kuma nace sun shiga shida iyalinshi.</p><p><br /></p><p>Wasa'wasa saida bank ta kwace duk wani Abuda ya mallakah hatta gidan da yake saidai suka kwance.</p><p><br /></p><p>Kuma duk wannan abun "Alh Mahamud yana tsare a prison, "Abokin shi Alh Musa ke tsaye akan lamarin ko lokacin da akabasu notice cewa su tashi Alh Musa ne "yakama masu gidan haya a unguwar tudun wada suka koma chanda zama,</p><p><br /></p><p>A haka "suka cigaba da Rayuwa cikin wani irin yanayi mara dadi,</p><p><br /></p><p>Ana cikin haka akayen kema "Abban nasu zama agidan prison Na tsawon shekara biyu, saka makon makudan kudin da'aka biyoshi,</p><p><br /></p><p>"Shikam bayada wayan kudi don haka dole ya Amince da hukunci da Alkali ya yanke mishi Na zama gidan yari Cikin tsananin bakin ciki Da bacin rai.</p><p><br /></p><p>Domin shikam yasan baici sisin kwabo acikin makudan kudin da suka salwanta ba, saidai kam yana zaton "mataima kinshi, koda yake ance zaton zunubi koda ya kasance gaskiya Amma dai kam yana zarginshi dasa hannun shi acikin lamarin,</p><p><br /></p><p>Tunda "yanuna baya kaunarshi, tun lokacin Da akarbi matsayin shina manager akaba "Abban su Humaira,toh shikenan ya dauki karanta tsana yadore mishi</p><p><br /></p><p>shiyasa Abba yayi tunnan KO shine toh kaidai wanene yake da sa hannu acikin wannan lamarin Toh yabarshi DA Allah.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A haka su "Humaira suke Rayuwar Cikin matsananci hali inda hartakai aka kiresu daga school din dasuke, tunda basu biyan kudi dayake su private school baruwan su dazar time yayi Toh abasu kudi.</p><p><br /></p><p>Dama "Alh Musa kedan taimaka musu toh shima iyalin shi sun'isheshi mata biyu dayara bakwai gashi shima karayar Arziki yasame shi, don hane maya Ko mai yakara jagulewa,</p><p><br /></p><p>Dole badan sunaso ba suka koma wata government school tunda shi bawani kudi ake biyaba,</p><p> </p><p>A haka har yah Himu ya kammala S.S three din shi da taimakon Malam wato mahaifin Umman su dayake yah Himu yasamu result me kyau, Don haka Malam yasamar mishi Admission a A b u Zaria don yaci gabada karatun shi inda yake level one yanzu haka sunyi hune yana gida ita kuma Humeeh tana S.S two yanzu,</p><p><br /></p><p>A yau ranace datake sance ranan aiki ga kowani ma'aikacin government Kai harda students wato yan makaranta, ranace wadda Malam bahaushe keyima kirari da cewa KO bature na tsoronki wato Monday.</p><p><br /></p><p>" Wata yar kyakkyawar matashiyar buduurwace yar kimani shekara goma sha hudu zuwa sha biyar farace Itaba doguwaba ita kuma bagajera ba fuskarta Dan dai dai tana dauke Da manyan idanu Amma ba sosai ba, tanada Dogon hanci da Dan karamin baki Wanda idan tayi dariya kamar kada tarife bakin, badan komai ba saidan open teeth din datake dashi sama Da kasa wanda ya karama fuskarta kyau Da kwarjini, ga kirjinan Nata Kam hmmm! ba'acewa komai domin koh cike yake Da dukiyar Fulani zaka fahimci hakane ta yadda suka dago hijab dinta,</p><p><br /></p><p> Sanye take Da school uniform riga Da wando Da hijab, rigar da hijab din fararene shikuma wandon me ruwan kasane, Tara taya irin jakarnan da yammatan yanzu suke yiwa lakani da swaga bag ko kuma suce wankan gefe Humaira kenan yamma tan "Umma.</p><p><br /></p><p>Kallo daya zakai ma kyakkyawar fuskarta kagane cewa da'alama yau bata jin zuwa school din, zakafahimci hakane daga ya nayi yanda take tafiya Ahankali tamkar bata son taka kasa,</p><p><br /></p><p>A hankali take kokarin shiga kwarda zatafita Da ita bakin titin dazata hau adai dai ta sahu,</p><p><br /></p><p>Toh kuma a wannan lokacin ne hanci wata mota kiran Honda civic yar karama new model takunno cikin tsautsayi kaji fachauuu daruwan kwataaaa!</p><p><br /></p><p>Tunda ga kasanta har saman gaba daya school uniform din jikinta yabaci Da ruwan kwata, Allah yasota bada beauty fice din tabah a hankali tadago dakai don taga "waye kedai wannan Aikai- akan?</p><p><br /></p><p>Dai Dai lokacin da "yafito Cikin mota domin tuni yayi parking gefe yanufo gurinta,</p><p><br /></p><p>Ta tsura masa ido farine Dogone kuma mikakke yanada tsayayyu kafada masu birgewa ma'abucin faffadan kirji da kakkauran jiki, sai kuma yadan Rankwafa kadan ta yadda zubin halittar shiya bada kirar wani Mutum mai tsararren tsayi mai ban sha'awa, </p><p><br /></p><p> Kai kace wani bako ne daga karasar Lebanon, gawani saje daya aje wadda takarawa kyakkyawar fuskarshi me dauke da eye balls da Dogon hanci kyau da kwarjini, </p><p><br /></p><p>shekarun shi bazasu wuce Ashirin da takwas zuwa da taraba yana sanye da Riga t-shart white and wandon jeams black. Abdul-jabbar Ahmed kenan</p><p>Mashi saurayi me jini ajika,</p><p><br /></p><p> Cikin lokaci kankani takare masa kallo Ahankali tadukar Da kanta kasa, A dai dai lokacin da yakarasa gurinta,</p><p>Cikin muryarsa me dadin saurare Yace eyya please Am so sorry ban kula dakeba wallahi, ahankali tadaga Kai ta kallesa aiko suka hada ido at the same time jitai gabanta ya fadi shima Abdul-jabbar hakata kasance agaresa, Da sauri ta dukarda kanta kasa tareda cewa it's ok,</p><p>Sannan tajuya da sauri</p><p> tafara tafia,</p><p>Yayi Dan taki kadan ya isa gareta badon komai ba saidan yasake jin daddadan muryanta, ahankali ciki rada yace sorry once again,</p><p>Batare Da ta juyoba tace I say it's ok sannan tacigaba da tafiya ya tsurama bayanta ido duk Da cewa tana sanye da hijab hakan be hanashi hango kugunta yana motsawa ba,</p><p><br /></p><p>Yana tsaye harta shiga wani gida me dakali biyu ahankali yasauke nauyayyan ajiyar zuciya sannan yajuya yanufi inda yai parking motar sa.</p><p><br /></p><p>Itakam Humeeh kallo daya zakai mata kagane cewa kiris take jira tafashe da kuka,</p><p><br /></p><p>Aikam tana shiga cikin zauren tafashe Da kuka Wanda kanajisa kasan Na sha'gwaba ne,</p><p>"Yah Himu da dakin shi yake cikin zauren yanaji kukanta yafito da Sauri haryana buga tuntube da bakin kofa,domin kuwa idan akwai abunda yatsana to baiwuce kukan Humeeh ba,</p><p><br /></p><p>Lokaci guda yajero mata tambayoyi kamar haka meyasa meki? me'akai miki? kedaw! Maganar ta tsaya saka makon yadda yaganta, </p><p> </p><p>Da Sauri ya karasa gurinta tareda cewa kut! "wani Dan renin Hankali ne yai miki wannan wulakanci?</p><p>Cikin sha'gwaba tace "wani ne yanhhh aibai jira takara Saba ya shuri takalma da sauri yai waje</p><p><br /></p><p>Cikin zafin nama yah Himu yakara sa gurin Abdul-jabbar dake ko Karin shiga mota sai yaji ance dakata Malam,</p><p><br /></p><p>Da sauri yajuyo suka hada ido cikin daurewar fuska yah Himu yace haba don Allah Malam wannan wani irin abune haka meyasa idan kuna driving Baku kallon hanya da kyau ne?</p><p><br /></p><p>Dubi yadda kabata mata school uniform yanzu shikenan Kai mata hasarar zuwa school yau,</p><p><br /></p><p>Mtsww yaja tsaki sannan yaci gabada dacewa kudama ya yan masu kudin nan haka kuke some time sai kurika daukan yayan talaka abanza,</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar dayake sauraran shi tunda yafara baice komaiba saida yaga yakai ayah sannan,</p><p>Yace Toh" kuyi hakuri bansan tana tahowo ba nikuma nariga nakawo shiyasa,</p><p>Yace toh idan bamuyi hakuri ba yaza muyi tunda kariga kagama, yajuya yanufi gida yana gunguni fada.</p><p><br /></p><p>Shikam Abdul-jabbar bin bayan sayai da kallo harsaida yashiga gida,</p><p> sannan ya bude mota yashiga yaja yai tafiyar sa</p><p>Wannan shine silar haduwar Abdul-jabbar DA Humaira.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐LUFHAT ce I Love all FANssss💞</p><p>💞💐💞💐 </p><p> 💐💞💐💞💞 </p><p> DA SANNU</p><p><br /></p><p> 💞💐💞💐💐</p><p> 💞💐💞💞</p><p><br /></p><p> 💐page36-40💞</p><p><br /></p><p> </p><p> NA</p><p><br /></p><p>💐MEENAT 💞UMAR FARUQ💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Assalamu'alaikum</p><p>Masaoya wannan littafi kuyimun hakuri narashin ganin posting din na jiya saboda banajin dadin jikina, Amma yanzu Alhamdullah. sannan kuyi hakuri </p><p>Na chanja tsarin littafin hakan yafaru ne saboda wasu basugane sunan littafin ba, so dafatan hakan bamatsala NAGODE SOSAI.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wannan page NA sadaukar DA shiga duk Wanda yagane SUNAN WANNAN LITTAFIN nagode kwarai dako karinku nagane sunan book din wato DA SANNU.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda Humeeh tashiga cikin gida Umma tana duke bakin fanfo tana wankin kayansu, </p><p><br /></p><p>saijin sallamar Humeeh tayi" ta amsa tare da mikewa tsaye tace ke kuma lafiya ki kadawo baki tsoron ki Makara?</p><p><br /></p><p>Tajuya ta kalle ta ganin yadda take ne yasa tace A ah ya'akai kuma hakata faru? </p><p><br /></p><p>Cikin kukan Sha'gwaba tace bawani" ne yawatsa Mani ruwan kwata ba?</p><p><br /></p><p>Umma tai murmushi tareda girgiza Kai tace Toh" shine kuma abun kuka?</p><p><br /></p><p>Ta turo baki tace Umma kalli fa "yanda duk yabada Mani school uniform dina,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Umma tace hmmm "Humaira kenan "toh" yazakiyi da kaddarar Ubangiji?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tasake turo baki kadan tace "toh" shikenan fa yau barani school ba,</p><p><br /></p><p>Umma tadan ja tsaki mtsww tareda cewa toh" sai meh? Dama yau bakiyi niyar zuwa makaranta ba ai ina kula dake tunda kika tashi,</p><p>Saboda haka sai kicire kayan Na wanke.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dai dai lokacin da yah Himu ya shigo yana fada, Umma ta kallesa tace Kai kuma fa Kai dawa ne?</p><p><br /></p><p>Yace Umma nida wannan "guy din nan mana daya watsama Humeeh ruwan kwata Dan renin hankali kawai, yai kwaf"</p><p><br /></p><p>Umma data zuba masa ido saida yakai Aya, sannan tace yanzu zuwa kayi kukai tashin hankali ko? banasan haka fa</p><p><br /></p><p>Yace Umma nifa ba tashin hankali natafi mukayi ba, kawai da nafada masa" irin haka dasuke be dace ba ya kamata surika kula.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya kalli Humeeh yace tafi kitube kayan kikawo Na wanke maki kinji my sister?</p><p><br /></p><p>Tace toh tanufi daki don ta tufe,</p><p><br /></p><p>Shikuma yanufi wurin Umma yana cewa "Umma wanki ki kikeyi Ina daki baki kirani nayi makiba?</p><p><br /></p><p>Tace eh ai bansan kana nanba, yace Ina nan banfi taba, dai dai lokacin da ya tattare hannun Rikarsa yaduka yafara wankin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin nitsuwa yake driving zuciyar sa cike da tunani "Humeeh Ahankali ya furta is beauty "she have a Sweet voice sai kuma yasaki lallausan Murmushi tareda Shafa suman kansa sannan yace ko meye </p><p>sunan ta?</p><p><br /></p><p>(Nikam dake gefe nace oho "kaji shi daga ganin Sarkin fawa sai meya tai zaki.?)</p><p>Chan kuma sai ya hade fuska sannan yai tsaki mtsww" saboda tuno kalaman "yah Himu,</p><p><br /></p><p>Yace kai kaji "guy din nan fa? Don yaga wannan motar shine hada wani cewa yayan masu kudi,? toh" nima Arzikinta naci akabani Ni din'ma aidan talaka ne, yai kwaf."</p><p><br /></p><p>"Yana tafe yana surutu harya karasa unguwar su Y.Y.K yai hon mai gadi "yabude masa get yashiga bayan sun gaisa da "baba maigadi sannan yakarasa ciki,</p><p><br /></p><p>Bayan yayi parking sai yakashe "motar sannan yanufi cikin gida,</p><p><br /></p><p>Yai sallama yashiga Y.Y.K suna zaune shida Jamila matar sa ya amsa tareda daga Kai ya kalle sa, </p><p><br /></p><p>Magani yake ba "Jamila dayake tana dauke da tsohon ciki Haihuwa KO yau KO gobe."</p><p><br /></p><p>Saida ya zauna a daya daga cikin kushin din falon sannan ya kalli "Jamila cikin sigar zolaya yace sannu tsohuwa!</p><p><br /></p><p>Ta Dan harare sa kadan tace "wace tsohuwa?</p><p><br /></p><p>Yace ah "kemana, tace koh dai Kaine tsohon ba?</p><p><br /></p><p>Yai murmushi yace ah haba</p><p> dai ki kalle nifa da kyau yaro dallele Dani kice mani tsoho,</p><p><br /></p><p>Tace tabdi lallai kam A haka kake kiran "kanka yaro hada wani dallele bayan kakusa zama baba,</p><p><br /></p><p>Saida yai dariya sannan yace gaskiya kam toh barina Dena kiran kaina yaro tunda yanzu Na kusa zama baba KO?</p><p><br /></p><p>Tace a"toh da dai yafi kam,</p><p><br /></p><p>Saidai gaskiya kidena kirana tsoho domin ni aiba tsoho bane,</p><p><br /></p><p> Wanda zaya kwanke yammatan uku nan gaba shine za'akira da tsoho? yakai karshen maganar dayin dariya"</p><p><br /></p><p>Tace oho Ashe babu dadi "ni aka kirani da tsohuwa?</p><p><br /></p><p>Sannan ba "yammata uku zaka wanke ba ko goma ne ba abunda ya dame ni" kuma nima adena kirana tsohuwa,</p><p><br /></p><p>Yace ah ke "kam ai tsohuwa ce ke bakiga yadda kike zama dakyar tashi dakyar ba,</p><p><br /></p><p> Sannan karki damu da</p><p> "matan daza'a karo Asalima ba'akanki fa zasu zaune ba"</p><p><br /></p><p> Harara ta watsa masa cikin wasa sannan tace dama ya za'ai "su zauna akaina saidai kam "su zauna kan Wanda "ya daukosu"</p><p><br /></p><p>Dariya yai yace "toh shikenan tunda kan Wanda ya daukosu zasu zauna,</p><p><br /></p><p>Itama dariya take tace yasu "Mama da baba Lami?</p><p><br /></p><p>Yace suna Lafia tace "toh madallah dai dai lokacin datake Ko Karin tashi dakyar,</p><p><br /></p><p>Yace kin gani ba?</p><p>Ance ke tsohuwa ce kince "a ah,</p><p><br /></p><p> Tai murmushi tace kaidai kasani "Abdul-jabbar nikam nashiga daga cikin in kakoma ina gaidasu "mama.</p><p><br /></p><p>murmushi yai yace "toh" Uwan biyu zasuji azauna Lafia."</p><p><br /></p><p>Y.Y.K dariya yake masu sannan ya "kalli Abdul-jabbar yace Nawa kenan</p><p>Kadai ya'iya zolayar my "Dear har kagaji,</p><p><br /></p><p>"Toh ya akai ne"? naganka tunda sassafe I hope dai lafia ko kayi mafarkin My "Dear ta haihune? yakai karshen maganar sa da yin dariya"</p><p><br /></p><p>Shima Abdul-jabbar dariya yai yace kaidai bari Nawa narasa yadda aikai yau nafito Tunda sassafe haka,</p><p><br /></p><p>Saidai ga dukkan alama fitowar mai sa'ace domin ko nayi babbar tsintuwa,</p><p><br /></p><p>Y.Y.k yace babbar tsintuwa ta me kenan?</p><p><br /></p><p>Nan "yabashi labarin abunda yafaru tsakaninsa da "Humaira,</p><p><br /></p><p>Yaci gabada dacewa Kai "Nawa gaskiya beben "ta hadu sosai wallahi ya Kai karshen maganar da yin murmushi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shikam Y.Y.K ido ya zubama "Abdul-jabbar saboda ganin yadda ya takarkare sai koda "yarinyar yake,</p><p><br /></p><p>Hannu yasa ya girgiza Y.Y.k yace Nawa Ina ta magana Amma bakace komai ba,</p><p><br /></p><p>Yai firgigi tareda cewa hmmm Nawa kaine kuwa?</p><p><br /></p><p>Yace yes I am you Abdul-jabbar Amma me yasa kace ni ne kuwa?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mamaki nake wai Kane ke koda mace hmmm Amma dai kam gaskiya this girl is Lucky ko wacece domin ga dukkan alama ta tafi da lmanin ka koh? </p><p><br /></p><p>Dariya yai tareda shafa kyakkyawan sajen yace Kai nawa baka "ganta bane,</p><p><br /></p><p>Shima dariya yake yace ai zanso kam naganta ko wacece ita,</p><p><br /></p><p>Yace saidai gaskiya bajin dadin yadda nabata mata school uniform ba" shikenan yau Na "hanata zuwa school kamar yadda yayanta yafada,</p><p><br /></p><p>Y.Y.k yadan bubbuga kafadar sa tareda cewa kada kadamu</p><p>Anjima zamu je mukara "bata hakuri daga nan sai mu kafa gwamnatin mu ko?</p><p>Ya kai karshen maganar da yin dariya.</p><p><br /></p><p>Shima Abdul-jabbar dariya yake,"</p><p><br /></p><p>Hakan sukaci gabada firarsu har lokacin da Abdul-jabbar ya mike tareda cewa nizan tafi,</p><p><br /></p><p>Shima Y.Y.K mikewa yai yace tunyanzu?</p><p><br /></p><p>Yace eh zanbiya ta wurin "M .B daga Chan saina tafi gida,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Har wurin motar sa yaraka sa bayan yatafi sai shikuma yakoma cikin gida don yai shirin tafiya office.</p><p><br /></p><p>**************</p><p><br /></p><p> Wanene Y.Y.K?</p><p><br /></p><p>"Yusuf ya'u Na kaka Dane ga Alh "ya'u Na kaka da Matar sa daya Hajiya karima da yaran su uku</p><p><br /></p><p> Mata biyu Aunty "Naja'atu Da Aunty "Murjanatu sai namiji daya shine "Yusuf matan duk sun girmi "Yusuf ko wace tana zaune gidan mijinta lafia tare da yaranta"</p><p><br /></p><p>Alh "ya'u Na kaka hamshaki mai kudi ne kuma dan kasuwa yana zaune a unguwar sarki, yakasance Mutum ne mai tausayin talaka,</p><p><br /></p><p>Dazaran ya kula kana bukatar taimako "Toh KO baka tambaye saba zai tai makeka,</p><p><br /></p><p>"Toh balle kaje ka tambaye sa to fa sai inda karfinsa yakare,</p><p><br /></p><p>Wanda shine yadauki yauyin karatun "Abdul-jabbar tundaga primary secondary har zuwa N.D.A,</p><p><br /></p><p> yanzu haka ma "Abdul-jabbar yagama N.D.A din sa Zasu tafi America akwai wani kwas da zasuyi Na shekara daya, kuma Alh "ya'u Na kaka ne yadauki nauyin tafiyar",</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A hankali Abdul-jabbar yake driving har ya isa gidansu dake unguwar kurmin mashi,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Inda suke zaune shida mahaifiyarsa Hajiya "Aisha wanda shima Alh "ya'u na kaka ne ya mallaka masu kuma shine ya kaita makka,</p><p><br /></p><p>"Toh wai duk sanadin Abotan dake tsakanin Yusuf DA Abdul-jabbar ne?</p><p>A ah shidin dai mai taimakone kawai Toh madallah da kyakkyawar zuciya irin ta "Alh ya'u Na Kaka."</p><p><br /></p><p><br /></p><p>DA sallamar sa yashiga cikin gidan tana zaune afalo kallo take ta amsa masa sallamar tare da daga Kai ta kalle sa,</p><p><br /></p><p>Dai dai lokacin daya zauna kan kafet tare da cewa ya Allahu, sannun "mama ya gida?</p><p><br /></p><p>Tace yauwa sannu da zuwa, ina kaje ne tunda sassafe haka? Yace yace naje gidan Y.Y.k tace aw "toh suna lafiya ? yace lafia kalau sunce suna gaida ke, tace Ina amsawa,</p><p>Sun Dan taba fira kadan yamike tare da yace cewa Mama "baba Lami bata iso ba tukun ? tace eh wallah bata iso ba" yace toh Allah ya kawota Lafia tace Amin", ni Zan shiga Na kwana,</p><p> tace Toh shikenan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar Sai juyi yake a gado shida ya tafi daniyar yai bacci Amma yakasa,tunanin "Humeeh ya addabi kwakwalwar sa,</p><p>Daya yarufe idon fuskarta yake gani tareda kyakkyawar surarta, Chan kuma kunnu wansa yana tuna masa daddadan voice nata,</p><p><br /></p><p>A hankali ya jawo filo ya matsesa a kirjin sa tareda rintse ido wani irin yanayi yakeji Wanda be taba jin irin</p><p> Saba,</p><p><br /></p><p>Dakyar! dakyar!! Abdul-jabbar ya gaya dare saboda tsabar tunanin "Humeeh burinsa kawai yasake gani beauty fice dinta tareda jin sweet voice Nata,</p><p><br /></p><p>Bayan yai sallar magrib sai yai bude baki kasan cewa yana yin azumin Litinin Da Alhami",</p><p><br /></p><p>Key motar sa kawai yadauka ya fita,</p><p>Ya kokarin shiga mota sai yaji wayar sa tana ringing, koda yaduba saiya ga "NAWA kamar yadda yai save, yai murmushi tareda dagawa,yace ya akai ne?</p><p><br /></p><p>Daga Chan yace Lafia lau kana Ina ne? Yace gani nan zanzo wurinka, yace bana gida muna asibiti DA Sauri Abdul-jabbar yace Lafia meya faru?</p><p>My Dear ce zata haihu,</p><p>Kuma wani asibiti ne? Y.Y.K ya fada masa sunan asibiti yace OK gashi nan zuwa,</p><p><br /></p><p>Don haka dole Abdul-jabbar ya hakura da maganar zuwa wurin Humeeh, ya nufi asibiti,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda ya isa asibiti Jamila ta haihu ta haifi yarta mace kyakkyawa DA ita tubara kalla masha'Allah,</p><p><br /></p><p>Sai misalin karfe10:30pm nadare sannan Yakoma gida saida yashiga cikin gida yafadawa Mama cewa "Jamila ta haihu,</p><p><br /></p><p>Mama tai murna sosan ta kumayi addu'ar Allah yaraya Bebe yace Amin tareda juyawa yanufi dakin sai.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>**********</p><p>Washegari da misalin 2:30pm Abdul-jabbar ya isa gidan Y. Y.K ,</p><p><br /></p><p>Bayan sun gaisa sai Abdul-jabbar yace Ina maijego? Y.Y.K yace tana ciki bacci take,</p><p><br /></p><p>Y.Y.K yace ya akai ne nawa,?</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yace Dan safa kwata miliyon dinsa, yace gaskiya Nawa ina cikin wani yanayi fa,</p><p><br /></p><p>Y.Y.K Idon yazaro alamar tsoro yace Nawa meya faru? Yace gaskiya tunanin yarinyar nan ya hanani sakat fa, dariya yake masa sosai,</p><p><br /></p><p> yayinda shi kuma ido yazuba masa sai kuma ya Dan hade fuska tareda cewa bansan fa iskaci wannan wani irin dariya ne haka?</p><p><br /></p><p>Y.Y.K ya Dan tsaya dayin dariya yace toh aikai Nawa daganinka Ansan cewa you're a new come din Na,yanzu dai tashi mutafi yafada yana mikewa tsaye, shima Abdul-jabbar din mikewa yai suka fita</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞LUFHAT CE💐</p><p>💞💞💐💐 💐💐💞💞</p><p> </p><p> DA SANNU </p><p>💞💞💐💐</p><p>💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> 💞Page41-45💐</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐MEENAT </p><p>💞UMAR FARUQ💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p>-----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN: THE STRONGEST WEAPON</p><p>-----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tsaye suke suna duban suga ta inda "yaro zaya bullo su'aikesa yakira masu "Humaira,</p><p>Y.Y.K ne ya hango wani yaro yanufosu sai yace yauwa gawani yaro zaya biyo tanan bari saimu aikesa yakirata,</p><p><br /></p><p>Ya sunanta? Abdul-jabbar yai masa kallon nima bansa niba,</p><p><br /></p><p>Dariya Y.Y.K yai a dai dai lokacin da yaron ya iso wurin su har zaya wuce su,</p><p>Da sauri Y.Y.K yace salamu'alaikum, tareda meka masa hannun shima yaro Hannun yamika masa tareda amsa"sallaman,</p><p><br /></p><p>Dan Allah abokina kashiga gidan Chan kace ana sallama da "maigidan yace toh" yanufi gidan</p><p><br /></p><p>Da Sauri Abdul-jabbar yamatso wurin Y.Y.K yace Kai Nawa maigidan fa kace?</p><p>Yace eh toh" tunda bakasan sunan sabuwar budurwar takaba basai muyi maigaba daya ba?</p><p><br /></p><p>Yace Nawa banfa ganeba kamar ya maigaba daya?</p><p><br /></p><p>Yace dadina dakai kenan wallahi sai Kai tayin abu kamar dan fari,</p><p><br /></p><p>Yace toh ai shidin ne, yai murmushi yace toh" sannu Sarkin yan wauta, abunda Nake nufi shine mufara kamun kafa da Babanta,</p><p><br /></p><p>Yace da fatan kagane ai Dan fari gilashi? yakarasa maganar da yin dariya.</p><p>Shima Abdul-jabbar dariya yai yace eh nagane kanin mata,</p><p><br /></p><p> Ya watsa masa harara yace waikai baza kadena kirana kanin mata ba ko?</p><p><br /></p><p>Dariya Abdul-jabbar yake sosai yace baza A denaba din, kaima baka cemani Dan fari ba?</p><p><br /></p><p>Yace toh"kai badan farin bane? yace ni ne,</p><p>Toh kaima ba kanin matan bane? ya langabe Kai tareda cewa toh" yazanyi tunda sun'rigani zuwa ni ne" dariya sukai gaba daya tareda tafawa.</p><p><br /></p><p>Dai dai lokacin da yaron yadawa yace ace "maigidan baya nan waisu wane ke nemansa? Kodaya kema naji ace wata tazo tagani Kusu wanene? tana nan zuwa.</p><p><br /></p><p>Y.Y.K yace yauwa abokina mungode ya zaro naira Dari biyu Aljihu sa yami kama yaron,</p><p><br /></p><p>Yaro yadan russuna tareda sa hannun biyu ya karba yace Nagode yajuya yatafi.</p><p><br /></p><p>Tunda ga nesa "Abdul-jabbar ya zuba mata ido hankali take tafiya kamar bataso taka kasa sanye take da atamfa brown me ratsin ash Riga da zani ne dinkin tasa hijab mai hannu Ashe colour,</p><p><br /></p><p> Ta isa wurin su tareda sallama "Y.Y.K ne ya amsa mata fuskarsa dauke da murmushi, tadan russuna kadan ta gaida su Y.Y.K ya amsa mata </p><p><br /></p><p>Shikam "Abdul-jabbar be amsa ba saidai ido daya zuba "mata ganin yadda take komai cikin sanyi hakanan yasa yaji takara shiga cikin Ransa,</p><p> </p><p>A hankali ya sauke ajiyar zuciya tareda maida hankalin sa wurin su,</p><p><br /></p><p>Cikin Dan siririn muryarta mai dadin saurare tace kuke Neman maigidan Chan?</p><p><br /></p><p>Yace eh mune saidai ba "maigidan muke nema ba yar maigidan muke nema"</p><p><br /></p><p>Da sauri tace kalle sa yai murmushi yace eh wurinki mukazo" ni sunana Yusuf kina iyakirana Y.Y.K shi kuma dan 'uwana sunan sa Abdul-jabbar,</p><p><br /></p><p> tace Lafiya dai KO? Yace Lafiya lau saidai bamu San sunan Malamar ba?</p><p><br /></p><p>A hankali ta dukar dakai kasa tana murza zoben dake Dan yatsanta, </p><p><br /></p><p>Shikam "Abdul-jabbar ido ya zubama zarazaran yatsunta masu kyau da sha'awa sabada adon Jan lalle da bakin da akai masu,</p><p><br /></p><p>Cikin sanyi tace sunana Aisha Amma Humaira ake kirana yace nice name toh malama Humaira ya "mutanan gida ya kuma school? Tace Lafiya Lau yace toh" madallah,</p><p><br /></p><p>Yace Malama Humaira nasan dai kingane wannan KO?</p><p>Ta kalli wurin da "Abdul-jabbar yake wanda shima din ita yake kallo,</p><p><br /></p><p> ido suka hada at the same time Abunda taji jiya shita karaji yau saboda haka saitai saurin dukar dakai kasa tareda cewa eh nagane sa,</p><p><br /></p><p>Yace toh" dama munzo ne mu karabaki hakuri Akan abunda yafaru jiya don Allah a muna afuwa,</p><p>Sannan kuma idan ba damuwa munason kulla alaka tsakanin mu dake,</p><p>Wato Dan uwana ne yaji kin kwanta masa Arai tun lokacin daya ganki ma'ana yana sonki, saboda haka ne mukazo da kokon bararmu gareki dafatan za'a</p><p> Amunta damu.?</p><p><br /></p><p>Shuru tai ba tareda tace komai ba, Yace mlm Humaira kinyi shuru bakice komai ba?</p><p><br /></p><p>Tace toh ni mezan ce? yai dariya yace keko keda abuncewa, gaskiya bazan boye makiba dan'uwana yakamu da sonki lokaci daya don haka kinga dole zaiso yasan matsayinsa awurinki KO?</p><p><br /></p><p>Tace toh kudan bani lokaci nai shawara, Yace kamar yaushe kenan? tace nanda sati biyu, Da sauri yace two weeks fa ki kace!?</p><p><br /></p><p>Ta kada Kai Wanda ita kanta bata San lokacin da tace two weeks din ba, </p><p>Shikam Abdul-jabbar cikin tsoron jin abunda tafada yasahi Kara zaro big eyes dinsa waje, Y.Y.K yace haba Humaira sati biya ai yai yawa A yadda dan'uwana yakejinki aransa ai baza ya'iyayin sati biyu be gankiba,</p><p>Tace toh sati daya, Yace a ah inama dai laifin muzo gobe? ya fada yana mirgina kai, a ah ba gobe ba, toh" sai yaushe? tace jibi, yace beyi yawaba? tace a ah beyiba,</p><p><br /></p><p>Yace toh shikenan ba komai hakama da akai mana mungode kwaraida gaske,</p><p>Tace sai anjima Y.Y.K Yace toh a gaida su "Umma da yayan mu yafada yana murmushi itama murmushi tai tace to zasuji tajuya ta tafi.</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yabi bayanta da kallo,</p><p><br /></p><p>Y.Y.K ya zungure sa tareda cewa Kai wannan wani irin kallo ne haka? sai kace Wanda yawarke makanta</p><p>Wannan aisai kasa ta buga tuntube tafadi, tun dazu kake kallo ta da wannan kwala-kwalan idon naka kamar na mage kilama Shiya takasa sakin jiki tai magana, yakai karshen maganar dayin dariya.</p><p><br /></p><p>Shima Abdul-jabbar dariya yake yace Amma dai Nawa da sharri kake, yanzu saboda Allah idona ne kwala- kwala kamar Na mage?</p><p><br /></p><p>Cikin zayala Yace eh koba haka sukeba? barima Allah yasa idan muka dawo jibin tace bakai mataba, saboda kafaye kato sannan kuma idanun ka kwala-kwala.</p><p><br /></p><p>Aikam me Abdul-jabbar zaiyi inba dariya ba hada rike ciki yadan tsaya dayin dariya yace ba Amin ba,aizata soni da yaddan Allah kuma "DA SANNU" kuma zata gane irin kaunar danake mata.</p><p><br /></p><p>Y.Y.K yace bani key kagani najamu kai kam yau naga Happy yacika maka ciki so ba lallai bane ka'iya driving din'mu.</p><p><br /></p><p>Yajefa masa key tareda cewa ai kaidin ne Wallahi ko mutun beyi niyar dariya ba sai kasa sa,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yai dariya yace Nawa kenan duk kawani rikicewa datace two weeks,yace aidole Na rikice ba kasan yadda nakejinta araina bane shiyasa.</p><p><br /></p><p>Yace Hmmm ni mamaki kake bani ban taba zaton zaka mato akan san ya mace ba wallahi, a yadda naga mace bata gabanka kuma komai kyanta Amma sai gashi naga wannan kanata rawar jiki a kanta,</p><p><br /></p><p>Koda yake gaskiya nayaba da "Humaira kyakkyawar ce gatada nutsuwa da alama tarbiya yaratsata, gata Da sanyin murya kawai dai ka'iya zabe konace kayi dace saidai ace Allah ya tabbatar Da Alkhairi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar dadi yaji aransa Yace amin, Amma afili kuma sai yace Kai Nawa tun bata yai accept dinba tukun idan tace banyi mataba fa?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yace Ah' haba dai wane ita santalelen saurayi kamar ka zatace bakai mata ba? Ai banga wannan macen ba tukun, haka sukaci gaba da tattaunawa akan "Humaira.</p><p><br /></p><p>**************</p><p><br /></p><p>Koda "Humaira tashiga gida da ta iske "Umma zaune akan tabarma ta, karasa kusada ita ta zauna tareda cewa sannu Umma.</p><p><br /></p><p>Ta amsa da yauwa sannu najiki shuru Lafiya dai KO?</p><p><br /></p><p>Humaira tace Lafiya lau toh suwaye kene man "Abban Ku?</p><p><br /></p><p>Takauda Kai gefe sannan tace aiba wurin "Abba suka zoba, </p><p><br /></p><p>Toh" wurin wasu kazo? batare data kalli Umman tace wai wurina sukazo,</p><p><br /></p><p>Da saurii Umma tace toh Lafiya dasukazo wurin ki?</p><p><br /></p><p>Tace Mutumin nan ne fa najiya daya watsa mun kwata,</p><p><br /></p><p>Oho toh mai kuma yakawosa? wai yazune yasake bani Hakuri,(ba tafada mata daya abunda ya kawo sunaba saboda tanajin kunya) </p><p><br /></p><p>Umma tace toh ke meki kace masu? ta Dan tabe baki kadan tace ainace masu ba komai na Hakura.</p><p><br /></p><p>Umma tace ai haka yana Da kyau duk abunda mutun yai maka kayi hakuri kada karikesa a zuciyar ka, saboda Riko ba kyau ko zalintarka akai to kayi hakuri "DA SANNU" Allah yai maka sakayya.</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu.</p><p>************</p><p>Da misalin karfe 8:30 nadare Abdul-jabbar yai parking motar sa akofar gidan su "Humaira</p><p><br /></p><p>Shika daya ne batare Da "Y.Y.K yana Zane acikin mota be fitoba saidai yabude kofar motar ya fitoda kada daya waje dayar kuma tana daga ciki, hannun wansa duk suna kan sitiyarin motar.</p><p><br /></p><p>Wani yaro ne yazo ta kusada shi zai wuce da sauri yace salamu'alaikum abokina yakake?</p><p>Yaron yanarike da Allo ahannun sa Da Alama daka makaranta yake, ya Amsa salamar tareda tsayawa.</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yace abokina zaka tafi makaranta ne ko katasone? Yaro yace eh natasone, toh ya karatu? yace Lafia qalau toh" madallah, don Allah shiga gidan nan kace Abdul-jabbar yana sallama da "Humaira kaji? Yace toh.</p><p><br /></p><p>Salama'alaikum wa'alaikassalamu, Umma ta amsa masa yace wai ana sallama Da "Humaira inji "Abdul-jabbar tace toh" gashi kuma bata ta tafi islamiyya Amma dai tabar sako tace idan yazo Abasa bari Na dauko maka adai dai lokacin da take shiga daki, jimawa kadan tafito hannun ta dauke da takarda tace ungo kakai masa yaron yakarba tareda cewa toh"</p><p><br /></p><p>Koda yaron yafito yace masa ance ta tafi islamiyya Amma gashi tace idan kazo abaka yafada tareda mika masa takarda,</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar ya karba yace nagode abokina ungo wannan yaciro kudi Daga ajihusa yamika masa yaron yarba yace nagode yatafi.</p><p><br /></p><p>Shikam Abdul-jabbar bayan yaron yatafi sai yakoma cikin mota ya zauna tareda bude takarda yafara karatawa kamar haka.?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐💞LUFHAT Luv your FANS ALL💞💐</p><p>💐💐💞💞 💞💞💐💐 </p><p>DA SANNU</p><p>💐💐💞💞</p><p>💞💞💐💐</p><p><br /></p><p> 💞Page46-50💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐MEENAT 💞UMAR FARUQ💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p><br /></p><p>-----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>-----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>ABDUL-JABBAR</p><p> Kana Lafiya ya gida da abokinka? nayi tunani kuma Na Amince Allah ya tabbatar DA Alkhairi tsakanimu, saidai Na tsani abu biyu cin Amana da yaudara so please don't try to inter it our relationship between u and me please,</p><p> daga "Aisha Mahmoud (Humaira).</p><p><br /></p><p>Ya karanta takarda yafi akirga yai murmushi tareda girgiza Kai yace "Humaira kenan insha'Allahu bazaki taba samuna da daya daga cikin abunda kika fadaba saboda nima natsani cin Amana da yaudara, yajuya yashiga mota yatayar yatafi zuciyar sa cike fari ciki da kuma kaunar "Humaira ziryan Ahankali yake driving harya isa gida.</p><p><br /></p><p>Washe gari da misalin 10:15am suna zaune a karkashi bishiyar mangoro basu dade dafitowa break fast ba su uku ne "Humaira ce tareda best friends dinta "Haleema Abubakar da "Hannatu Umar,</p><p><br /></p><p>"wayanda batada kamarsu, kamar yanda Humaira take batada rigima suma haka suke, Toh" dama malam ba haushe yace sai hali yazo daya ake abota toh" haka ne yakasace tsakanin Humaira da kawayanta,(saidai wani Lokacin sunada tsokar fada especially Hanah) sunshaku da juna sosai saboda tsananin shakuwarsu yasa tunbayan da "Humaira takoma government school,</p><p><br /></p><p> Sai suma suka matsawa "iyayansu da amaidasu government school din da aka maida "Humaira saboda bazasu iya cigabada zuwa school din batareda "Humaira ba kasan cewa dama tare suke achan private school din wannan shine dalilin dawo warsu wannan school din,</p><p><br /></p><p>Kawancen nasu yasamo asaline tun suna primary school gashi yanzu suna secondary s s two,kuma iyayan suma sunsan da zaman wannan kawance nasu mai tsafta wace ba gulma ba ha'inci duk dasun kasan ce su uku Amma hakan baisa suna munafurtan junansu ba, </p><p><br /></p><p>Kusan komai tare sukeyi ko abincin school matare sukeci Wanda suka tsaraayisa idan yau "Humaira takawo gobe "Haleema takawo jibi kuma "Hannatu takawo, toh kamar yauma "Humaira ce takawo.</p><p><br /></p><p>Wani kula ne dan madai-dai ci mai kyau A gabansu soyayyen Dankalin Hausa ne da miyar tumatur(stew) aciki,</p><p>Hannah tace Humeeh (kasan cewa haka suke kiran junansu Hannah; Humeeh; Haleeh;).</p><p><br /></p><p>Gaskiya miyar dankalin nan is too sweet inji cewar Hannah, Haleeh tace Ai "Umma ta iya miya sosai wallahi Humeeh tai murmushi tace kudai kun cika santi wallahi sai kace yau kukafara cin girkin "Umma,</p><p><br /></p><p>Haleeh tadan harare ta kadan cikin wasa tace toh" munji muncika santi din toh" ai miyar tayi dadin daza ai santi ne koh meh kikace ne Miss "D"?</p><p>("Doctor I S G saurayin Hanah ne da suhadu Asibitin sa lokacin da Hajiya "Hafsat mahaifiyar Hannah batada Lafiya "Toh" Cikin Ikon Allah soyayya tashiga tsakanin Hanah da "Doctor I S G" Wanda hartakai ga manya sunsan da soyayyan tasu yanzu hakama anajirane dasun gama school asha biki,Ita da "D" din Nata.</p><p><br /></p><p>Hannah tai dariya tareda daga babban yatsanta alamar jinjina tace godiya nake</p><p>kinsan tukuicin ki? </p><p><br /></p><p> Haleeh tace A ah' saikin fada tace zance my "D"yai maki Allura talatin takara she maganar Da kanne mata ido daya,</p><p>Humeeh tace Wanda bature bai'iyaba,</p><p><br /></p><p>Haleeh taro ido tace wayyo Allah Na! yadai yimaki keda zaki zama matarsa,</p><p><br /></p><p> Humeeh tai dariya tace kinji tsorone?</p><p><br /></p><p> Haleeh tace ke ya bazanji tsoro! ba 30 injection wasa ne</p><p>tabdi badani ba wallah</p><p><br /></p><p>Hannah tana dariya tace wai kuturun gada arama bah</p><p><br /></p><p>Sukai dariya gaba dayansu tareda hada baki sukace "eh mana",</p><p><br /></p><p>Humeeh tace Hmmm kunsan mai yafaru? sukace sai kin fada" tace ina mutumin nan daya watsa mun kwata shekaran jiya har banzo school ranan bah?</p><p>(Kasan cewa tafada masu abunda yafaru tsakanin ta da "Abdul-jabbar)</p><p><br /></p><p>Nan dai tasake basu Labarin zuwansu "Abdul-jabbar jiya gidansu tareda abokinsa Y Y k,</p><p><br /></p><p>Sukam mamakin ta suke saboda yadda ta takarkare tanata koda mutumin da ta hadudashi jiya-jiya Hmmm lallai da Alama dai wannan mutumin yasamu babba matsayi azuciyarta.</p><p><br /></p><p>Haleeh "ta zungurin Hanah suka hada ido sukai Dariya sannan sukace eyeeeeeh lallai da Alama wannan guy din yasamu shiga Toh" ya sunansa? </p><p> </p><p>Humeeh tai fari da'ido sannan tace sunansa Abdul-jabbar abokinsa kuma "Yusuf Amma yace Y Y K ake kiransa,</p><p><br /></p><p>Sukace "eh mana" gaba dayansu, Humeeh tace Ku gaskiya guy din yahadu sosai,</p><p><br /></p><p>Sukace ah"! haba dai ? tace Allah Kuwa bakugan sabane bafa kyakkyawa dashi ga hanci kamar karas shidin Ai special ne wallahi, sukace Au Allah ? tace sosai makuwa, nan dai tafara wassafa masu kaman ninsa,</p><p><br /></p><p>Hakanan sukaci gabada fira wadda Rabin firar duk ta "Abdul-jabbar ce har zuwa lokacin da aka buga komawa class sannan suka tashi suka nufi class dinsu.</p><p><br /></p><p>*****************</p><p>Cikin lokaci kankani Soyayya mai tsanani tashiga tsakanin "Abdul-jabbar da "Humaira son junansu suke sosai hartakai daya baya iya yini batareda yaga daya ba abun nasu gwanin sha'awa, idan kagansu sai karantse sun shekara tare, yanzu bafada tsakanisa da Yah Himu saidai mutunci.</p><p><br /></p><p>Tun'wani Rana dayazo week ya iskosu </p><p>Suna zaune akan dakali suna fira a lokacin ma tuni sundade dasha kuwa dajuna,</p><p><br /></p><p> sai ga yah Himu zaya shiga gida da sauri Abdul-jabbar yamike tsaye yai masa sallama tareda mikamsa Hunnu shima yah Himu hannun yamika masa suka gaisa fuskarta nan ba walwala sannan yashiga gida.</p><p><br /></p><p>Daga zaure ya kwalama Humaira" Kira dasauri ta tashi tashiga zaure yana tsaye ransa abace yace ke me yakawo wanga guy din nan</p><p>gurinki?</p><p> </p><p>Cikin jin tsoro tace ayya ! yazo sake bani Hakuri ne,</p><p><br /></p><p>Cikin hade fusta yace toh" sai me kuma?</p><p><br /></p><p>Tai shiru kanta nakasa tana wasada yatsun hannunta batare da tace komai ba,</p><p><br /></p><p>Yadaka mata tsawa yace Ina magana kinyi mun shiru ko bakiji abunda nafada bane?</p><p><br /></p><p>Cikin tsoro da ha'gwaba tareda turo baki tace wayyo ! yace nefa yana sona, </p><p><br /></p><p>DA sauri yace what?</p><p>tace eh kuma fa yanada kirki sosai</p><p><br /></p><p>Ido yah Himu yazaro</p><p>Cikin mamaki! yace keh Ashanty har yaushe kika sanshi daki kagane cewa yanada kirki?</p><p><br /></p><p>Ta turo baki tace toh" ai yadade yana zuwa tunfa lokacin daka koma school </p><p><br /></p><p>Ido yasake zarowa yace yadade fa kikace?</p><p>Tace eh, sai ya sassauta murya Yace toh ke kina son sa?</p><p>Fuskarta tarufe datafin Hannun ta sannan tadaga Kai alama eh,</p><p>Yai shiru yana kallon ta kawai sai yaji tabasa tausayi ganin Cikin lokaci kankani takamu dason guy din, (aransa kam fadi yake Allah yasa ba'irin mayaudaran samarin nan bane) sai Yace toh" shikenan Amma fa kikula bana son Abunda zaya cuta makine shiyasa bakomai kije yana jiranki.</p><p><br /></p><p> tace toh yah Himu nagode.</p><p><br /></p><p>***************</p><p>Ahankali yake driving yana sararon kira'ar sheikh Ahmed Sulaiman cikin suratu Kahf kasan cewar yau jumma'a (toh dama yasaba duk ranan jumma'a bayan ya karanta suratul kahf toh" sai kuma ya wuni yana sauraren kira'ar yana kuma bi)Abdul-jabbar kenan, cikin nutsuwa ya kalli agogon hannun sa yaga 5:00pm yai murmushi a dai dai lokacin dayake kokarin shiga layin gidan su "Humaira.</p><p><br /></p><p>Karar Hon din sane ya tabbatar mata dacewa (specia dinta yazo kamar yanda take kiransa).</p><p>Lallausan murmushi tasaki tareda daukan Hijab dinta fari toh" dama already ashirye take tana sanye da jallabiya ne baka mai dogon hannu rigar tasama ta matse saikuma tabude takasa saboda haka sai kawai ta sake kallon kanta a mirror ta gyara zaman hijab dinta sannan tafito daga dakin.</p><p><br /></p><p> ta kalli "Umma dake zaune akan tabarma tana tsintar shinkafa yar Hausa, Ahankali tace sannu Umma da Aiki?</p><p><br /></p><p>Umma tadago dakai ta kalleta tareda cewa yau sannu Umma tace sai Ina haka kuma?</p><p><br /></p><p>Humaira cikin jin kunya tagukar da Kai kasa tana murza yatsunta ahankali tace um! um!! um!!! Da! Dam!!</p><p><br /></p><p>Umma ta katseta dacewa dama "Abdul-jabbar ne yazo KO?</p><p>Humaira da kanta ke kasa tace eh,</p><p>Murmushi Umma tai sannan tace sai kindawo Amma fa ki kulada kanki sannan kada kidade kinji ko? </p><p>Tace toh Umma tafita, girgiza Kai Umma tai tareda bin bayan ta da kallo, ita kam mamaki take yanda Humaira take son wannan yaro haka, wadda ko sauraren samari batayi Amma sai gashi ta saurari wannan,</p><p>Tace hmm toh Allah ya zaba mana abunda yafi zama Alkhairi.</p><p><br /></p><p>Labewa tai abayan kofar zauren gidan ta kusurwar kofar take hangen sa,</p><p><br /></p><p>Zaune yake a kan dakali ya juyo bayan sa yana sanye da tsararriyar shadda fara kasan ba hula, gashin kansa sai kyalli yake gwanin sha'awa saida ta gama karemasa kallo sannan tafito tanufi gurinsa.</p><p><br /></p><p>Kamshi turarenta yasanar dashi isowar ta Ahankali yadaga Kai ya kallo ta,</p><p><br /></p><p>Hannuwan ta biyu tasa tarufe fuska cikin jin kunyarsa tace Assalamu'alaikum, my special one,</p><p><br /></p><p>Ya Saki lallausan murmushi yace wa'alaikassalamu my cool heart, yace barkada fitowa sarauniyar zuciya ta ya nuna mata kusada shi alamar ta zauna,</p><p><br /></p><p>bamusu ta zauna kusa dashi kadan,</p><p><br /></p><p>Kamshin turaren sa Dana ta yahadu saboda haka sai yabada wani daddadan kamshi mai dadi,</p><p><br /></p><p>Ahankali yace yaki ke" ya "Umma ta? </p><p>Tace tana nan Lafiya lau toh" ya school din? Tace Alhamdullah yace yayi kyau,</p><p><br /></p><p>Yace ko kunji motsin Yah "Himu? tace eh yana nan Lafiya Yace is good, toh" meye Labari? tai murmushi Cikin jin kunya tace umh! ba wani labari, shima murmushi yai yace Ah haba dai? tace Allah kuwa, yace toh"bani labarin Hanah da Haleeh (yasan batada wani magana datawuce nasu Hanah DA Haleeh, wani abun kuma shine har yanzu basu hadu da "Hanah Da "Haleeh da Abdul-jabbar ba).</p><p><br /></p><p>Aikam nan tashiga bashi labarin "Hanah Da "Haleeh.</p><p><br /></p><p>Dariya yake sosai sakama konjin sunan Da "Hannah tasa ma wata senior (saboda waita aiki Hanah tasawo mata yoghurt toh kadata je yoghurt din yakara shine tai ma Hanah bulala biyar wai aita tsaya wasane shiyasa ba tasawo mata yoghurt din ba).</p><p><br /></p><p>Toh" fa shikenan Hanah tasa mata suna wai mai tafiyar agwagwa,</p><p><br /></p><p>Ya tsaya dayin dariya yace my cool Hanah bataji tsoro kada wata Rana tajita tasake yimata bulalar datafi wadda tai mata abaya?</p><p><br /></p><p>Tace oho mata nibasan Irin Hanah ba ita batada tsoro Sam,</p><p><br /></p><p>Hakanan sukaci gabada firarsu Cikin soda kaunar juna Wanda Rabin firar duk a kan Haleeh da Hanah ( A hankali yafa himmci cewa Hanah da Haleeh sunada matsayi mai girma a zuciyar ta) har misalin karfe shida na yamma.</p><p><br /></p><p>Ya tashi yace ina zuwa yanufi motar sa jim kadan sai gashi yadawo hannun sa rike da wata firar leda saida ya zauna sannan yamika mata ledar,</p><p><br /></p><p>Mamaki ne yakamasa saboda kin karban ledan datai ya kalleta yace A ah ungo mana,</p><p><br /></p><p>Ahankali tasa hannun biyu ta karba tace na meye? batareda ya kalleta ba yace kiduba mana,</p><p><br /></p><p>Koda "taduba sai taga kwalin Waya Tecno yace kiduba akwai Sim card aciki nasa number ta saida gaskiya banyarda kisaka number kowa acikin ba musamman ma ta namiji saidai ta yah "Himu kawai sai kuma nasu "Hanah da "Haleeh,</p><p><br /></p><p>Ya kalli agogon hannunsa yaga 60:30pm yamike tsaye tare da cewa zantafi itama tamike tsaye tace nagode Allah yasaka da Alkhairi ina gaida "Mama da baba "Lami yace OK zasuji,</p><p><br /></p><p>Saida taga tafiyar sa sannan tashiga gida zuciyar ta cike Da kaunar special dinta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐LUFHAT Luv your All FAN💞</p><p>💞💞💐💐 💐💐💞💞</p><p>DA SANNU</p><p>💐💐💞💞</p><p>💞💞💐💐</p><p><br /></p><p> Page46-50 </p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐MEENAT 💞UMAR FARUQ💐</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p><br /></p><p>-----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>-----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>ABDUL-JABBAR</p><p> Kana Lafiya ya gida da abokinka? nayi tunani kuma Na Amince Allah ya tabbatar DA Alkhairi tsakanimu, saidai Na tsani abu biyu cin Amana da yaudara so please don't try to inter it our relationship between u and me please,</p><p> daga "Aisha Mahmoud (Humaira).</p><p><br /></p><p>Ya karanta takarda yafi akirga yai murmushi tareda girgiza Kai yace "Humaira kenan insha'Allahu bazaki taba samuna da daya daga cikin abunda kika fadaba saboda nima natsani cin Amana da yaudara, yajuya yashiga mota yatayar yatafi zuciyar sa cike fari ciki da kuma kaunar "Humaira ziryan Ahankali yake driving harya isa gida.</p><p><br /></p><p>Washe gari da misalin 10:15am suna zaune a karkashi bishiyar mangoro basu dade dafitowa break fast ba su uku ne "Humaira ce tareda best friends dinta "Haleema Abubakar da "Hannatu Umar,</p><p><br /></p><p>"wayanda batada kamarsu, kamar yanda Humaira take batada rigima suma haka suke, Toh" dama malam ba haushe yace sai hali yazo daya ake abota toh" haka ne yakasace tsakanin Humaira da kawayanta,(saidai wani Lokacin sunada tsokar fada especially Hanah) sunshaku da juna sosai saboda tsananin shakuwarsu yasa tunbayan da "Humaira takoma government school,</p><p><br /></p><p> Sai suma suka matsawa "iyayansu da amaidasu government school din da aka maida "Humaira saboda bazasu iya cigabada zuwa school din batareda "Humaira ba kasan cewa dama tare suke achan private school din wannan shine dalilin dawo warsu wannan school din,</p><p><br /></p><p>Kawancen nasu yasamo asaline tun suna primary school gashi yanzu suna secondary s s two,kuma iyayan suma sunsan da zaman wannan kawance nasu mai tsafta wace ba gulma ba ha'inci duk dasun kasan ce su uku Amma hakan baisa suna munafurtan junansu ba, </p><p><br /></p><p>Kusan komai tare sukeyi ko abincin school matare sukeci Wanda suka tsaraayisa idan yau "Humaira takawo gobe "Haleema takawo jibi kuma "Hannatu takawo, toh kamar yauma "Humaira ce takawo.</p><p><br /></p><p>Wani kula ne dan madai-dai ci mai kyau A gabansu soyayyen Dankalin Hausa ne da miyar tumatur(stew) aciki,</p><p>Hannah tace Humeeh (kasan cewa haka suke kiran junansu Hannah; Humeeh; Haleeh;).</p><p><br /></p><p>Gaskiya miyar dankalin nan is too sweet inji cewar Hannah, Haleeh tace Ai "Umma ta iya miya sosai wallahi Humeeh tai murmushi tace kudai kun cika santi wallahi sai kace yau kukafara cin girkin "Umma,</p><p><br /></p><p>Haleeh tadan harare ta kadan cikin wasa tace toh" munji muncika santi din toh" ai miyar tayi dadin daza ai santi ne koh meh kikace ne Miss "D"?</p><p>("Doctor I S G saurayin Hanah ne da suhadu Asibitin sa lokacin da Hajiya "Hafsat mahaifiyar Hannah batada Lafiya "Toh" Cikin Ikon Allah soyayya tashiga tsakanin Hanah da "Doctor I S G" Wanda hartakai ga manya sunsan da soyayyan tasu yanzu hakama anajirane dasun gama school asha biki,Ita da "D" din Nata.</p><p><br /></p><p>Hannah tai dariya tareda daga babban yatsanta alamar jinjina tace godiya nake</p><p>kinsan tukuicin ki? </p><p><br /></p><p> Haleeh tace A ah' saikin fada tace zance my "D"yai maki Allura talatin takara she maganar Da kanne mata ido daya,</p><p>Humeeh tace Wanda bature bai'iyaba,</p><p><br /></p><p>Haleeh taro ido tace wayyo Allah Na! yadai yimaki keda zaki zama matarsa,</p><p><br /></p><p> Humeeh tai dariya tace kinji tsorone?</p><p><br /></p><p> Haleeh tace ke ya bazanji tsoro! ba 30 injection wasa ne</p><p>tabdi badani ba wallah</p><p><br /></p><p>Hannah tana dariya tace wai kuturun gada arama bah</p><p><br /></p><p>Sukai dariya gaba dayansu tareda hada baki sukace "eh mana",</p><p><br /></p><p>Humeeh tace Hmmm kunsan mai yafaru? sukace sai kin fada" tace ina mutumin nan daya watsa mun kwata shekaran jiya har banzo school ranan bah?</p><p>(Kasan cewa tafada masu abunda yafaru tsakanin ta da "Abdul-jabbar)</p><p><br /></p><p>Nan dai tasake basu Labarin zuwansu "Abdul-jabbar jiya gidansu tareda abokinsa Y Y k,</p><p><br /></p><p>Sukam mamakin ta suke saboda yadda ta takarkare tanata koda mutumin da ta hadudashi jiya-jiya Hmmm lallai da Alama dai wannan mutumin yasamu babba matsayi azuciyarta.</p><p><br /></p><p>Haleeh "ta zungurin Hanah suka hada ido sukai Dariya sannan sukace eyeeeeeh lallai da Alama wannan guy din yasamu shiga Toh" ya sunansa? </p><p> </p><p>Humeeh tai fari da'ido sannan tace sunansa Abdul-jabbar abokinsa kuma "Yusuf Amma yace Y Y K ake kiransa,</p><p><br /></p><p>Sukace "eh mana" gaba dayansu, Humeeh tace Ku gaskiya guy din yahadu sosai,</p><p><br /></p><p>Sukace ah"! haba dai ? tace Allah Kuwa bakugan sabane bafa kyakkyawa dashi ga hanci kamar karas shidin Ai special ne wallahi, sukace Au Allah ? tace sosai makuwa, nan dai tafara wassafa masu kaman ninsa,</p><p><br /></p><p>Hakanan sukaci gabada fira wadda Rabin firar duk ta "Abdul-jabbar ce har zuwa lokacin da aka buga komawa class sannan suka tashi suka nufi class dinsu.</p><p><br /></p><p>*****************</p><p>Cikin lokaci kankani Soyayya mai tsanani tashiga tsakanin "Abdul-jabbar da "Humaira son junansu suke sosai hartakai daya baya iya yini batareda yaga daya ba abun nasu gwanin sha'awa, idan kagansu sai karantse sun shekara tare, yanzu bafada tsakanisa da Yah Himu saidai mutunci.</p><p><br /></p><p>Tun'wani Rana dayazo week ya iskosu </p><p>Suna zaune akan dakali suna fira a lokacin ma tuni sundade dasha kuwa dajuna,</p><p><br /></p><p> sai ga yah Himu zaya shiga gida da sauri Abdul-jabbar yamike tsaye yai masa sallama tareda mikamsa Hunnu shima yah Himu hannun yamika masa suka gaisa fuskarta nan ba walwala sannan yashiga gida.</p><p><br /></p><p>Daga zaure ya kwalama Humaira" Kira dasauri ta tashi tashiga zaure yana tsaye ransa abace yace ke me yakawo wanga guy din nan</p><p>gurinki?</p><p> </p><p>Cikin jin tsoro tace eyya ! yazo sake bani Hakuri ne fa.</p><p><br /></p><p>Cikin hade fusta yace toh" sai me kuma?</p><p><br /></p><p>Tai shiru kanta nakasa tana wasada yatsun hannunta batare da tace komai ba,</p><p><br /></p><p>Yadaka mata tsawa yace Ina magana kinyi mun shiru ko bakiji abunda nafada bane?</p><p><br /></p><p>Cikin tsoro da ha'gwaba tareda turo baki tace wayyo ! yace nefa yana sona, </p><p><br /></p><p>DA sauri yace what?</p><p>tace eh kuma fa yanada kirki so sai</p><p><br /></p><p>Ido yah Himu yazaro</p><p>Cikin mamaki! yace keh Ashanty har yaushe kika sanshi daki kagane cewa yanada kirki?</p><p><br /></p><p>Ta turo baki tace toh" ai yadade yana zuwa tunfa lokacin daka koma school </p><p><br /></p><p>Ido yasake zarowa yace yadade fa kikace?</p><p>Tace eh, sai ya sassauta murya Yace toh ke kina son sa?</p><p>Fuskarta tarufe datafin Hannun ta sannan tadaga Kai alama eh,</p><p>Yai shiru yana kallon ta kawai sai yaji tabasa tausayi ganin Cikin lokaci kankani takamu dason guy din, (aransa kam fadi yake Allah yasa ba'irin mayaudaran samarin nan bane) sai Yace toh" shikenan Amma fa kikula bana son Abunda zaya cuta makine shiyasa bakomai kije yana jiranki.</p><p><br /></p><p> tace toh yah Himu nagode.</p><p><br /></p><p>***************</p><p>Ahankali yake driving yana sararon kira'ar sheikh Ahmed Sulaiman cikin suratu Kahf kasan cewar yau jumma'a (toh dama yasaba duk ranan jumma'a bayan ya karanta suratul kahf toh" sai kuma ya wuni yana sauraren kira'ar yana kuma bi)Abdul-jabbar kenan, cikin nutsuwa ya kalli agogon hannun sa yaga 5:00pm yai murmushi a dai dai lokacin dayake kokarin shiga layin gidan su "Humaira.</p><p><br /></p><p>Karar Hon din sane ya tabbatar mata dacewa (specia dinta yazo kamar yanda take kiransa).</p><p>Lallausan murmushi tasaki tareda daukan Hijab dinta fari toh" dama already ashirye take tana sanye da jallabiya ne baka mai dogon hannu rigar tasama ta matse saikuma tabude takasa saboda haka sai kawai ta sake kallon kanta a mirror ta gyara zaman hijab dinta sannan tafito daga dakin.</p><p><br /></p><p> ta kalli "Umma dake zaune akan tabarma tana tsintar shinkafa yar Hausa, Ahankali tace sannu Umma da Aiki?</p><p><br /></p><p>Umma tadago dakai ta kalleta tareda cewa yau sannu Umma tace sai Ina haka kuma?</p><p><br /></p><p>Humaira cikin jin kunya tagukar da Kai kasa tana murza yatsunta ahankali tace um! um!! um!!! Da! Dam!!</p><p><br /></p><p>Umma ta katseta dacewa dama "Abdul-jabbar ne yazo KO?</p><p>Humaira da kanta ke kasa tace eh,</p><p>Murmushi Umma tai sannan tace sai kindawo Amma fa ki kulada kanki sannan kada kidade kinji ko? </p><p>Tace toh Umma tafita, girgiza Kai Umma tai tareda bin bayan ta da kallo, ita kam mamaki take yanda Humaira take son wannan yaro haka, wadda ko sauraren samari batayi Amma sai gashi ta saurari wannan,</p><p>Tace hmm toh Allah ya zaba mana abunda yafi zama Alkhairi.</p><p><br /></p><p>Labewa tai abayan kofar zauren gidan ta kusurwar kofar take hangen sa,</p><p><br /></p><p>Zaune yake a kan dakali ya juyo bayan sa yana sanye da tsararriyar shadda fara kasan ba hula, gashin kansa sai kyalli yake gwanin sha'awa saida ta gama karemasa kallo sannan tafito tanufi gurinsa.</p><p><br /></p><p>Kamshi turarenta yasanar dashi isowar ta Ahankali yadaga Kai ya kallo ta,</p><p><br /></p><p>Hannuwan ta biyu tasa tarufe fuska cikin jin kunyarsa tace Assalamu'alaikum, my special one,</p><p><br /></p><p>Ya Saki lallausan murmushi yace wa'alaikassalamu my cool heart, yace barkada fitowa sarauniyar zuciya ta ya nuna mata kusada shi alamar ta zauna,</p><p><br /></p><p>bamusu ta zauna kusa dashi kadan,</p><p><br /></p><p>Kamshin turaren sa Dana ta yahadu saboda haka sai yabada wani daddadan kamshi mai dadi,</p><p><br /></p><p>Ahankali yace yaki ke" ya "Umma ta? </p><p>Tace tana nan Lafiya lau toh" ya school din? Tace Alhamdullah yace yayi kyau,</p><p><br /></p><p>Yace ko kunji motsin Yah "Himu? tace eh yana nan Lafiya Yace is good, toh" meye Labari? tai murmushi Cikin jin kunya tace umh! ba wani labari, shima murmushi yai yace Ah haba dai? tace Allah kuwa, yace toh"bani labarin Hanah da Haleeh (yasan batada wani magana datawuce nasu Hanah DA Haleeh, wani abun kuma shine har yanzu basu hadu da "Hanah Da "Haleeh da Abdul-jabbar ba).</p><p><br /></p><p>Aikam nan tashiga bashi labarin "Hanah Da "Haleeh.</p><p><br /></p><p>Dariya yake sosai sakama konjin sunan Da "Hannah tasa ma wata senior (saboda waita aiki Hanah tasawo mata yoghurt toh kadata je yoghurt din yakara shine tai ma Hanah bulala biyar wai aita tsaya wasane shiyasa ba tasawo mata yoghurt din ba).</p><p><br /></p><p>Toh" fa shikenan Hanah tasa mata suna wai mai tafiyar agwagwa,</p><p><br /></p><p>Ya tsaya dayin dariya yace my cool Hanah bataji tsoro kada wata Rana tajita tasake yimata bulalar datafi wadda tai mata abaya?</p><p><br /></p><p>Tace oho mata nibasan Irin Hanah ba ita batada tsoro Sam,</p><p><br /></p><p>Hakanan sukaci gabada firarsu Cikin soda kaunar juna Wanda Rabin firar duk a kan Haleeh da Hanah ( A hankali yafa himmci cewa Hanah da Haleeh sunada matsayi mai girma a zuciyar ta) har misalin karfe shida na yamma.</p><p><br /></p><p>Ya tashi yace ina zuwa yanufi motar sa jim kadan sai gashi yadawo hannun sa rike da wata firar leda saida ya zauna sannan yamika mata ledar,</p><p><br /></p><p>Mamaki ne yakamasa saboda kin karban ledan datai ya kalleta yace A ah ungo mana,</p><p><br /></p><p>Ahankali tasa hannun biyu ta karba tace na meye? batareda ya kalleta ba yace kiduba mana,</p><p><br /></p><p>Koda "taduba sai taga kwalin Waya Tecno yace kiduba akwai Sim card aciki nasa number ta saida gaskiya banyarda kisaka number kowa acikin ba musamman ma ta namiji saidai ta yah "Himu kawai sai kuma nasu "Hanah da "Haleeh,</p><p><br /></p><p>Ya kalli agogon hannunsa yaga 60:30pm yamike tsaye tare da cewa zantafi itama tamike tsaye tace nagode Allah yasaka da Alkhairi ina gaida "Mama da baba "Lami yace OK zasuji,</p><p><br /></p><p>Saida taga tafiyar sa sannan tashiga gida zuciyar ta cike Da kaunar special dinta....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐LUFHAT Luv your All FAN💞</p><p>💐💐💞💞</p><p>💞💞💐💐</p><p>DA SANNU</p><p>💞💞💐💐</p><p>💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> Page51-55</p><p><br /></p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p><br /></p><p>------------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>------------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda Humeeh tashiga gida ta iske Umma bakin murhu ta nayi masu girkin dare,</p><p>Dakin tashiga tacire hijab dinta tareda ajiye wayar sannan tafito don ta taya Umma Aiki.</p><p> </p><p>Bayan sallah magrib suna zaune abinci sukeci akwano guda Humeeh itada Ummanta, bayan sungama ne sai Humeeh ta tattara kwanoni takai su kicin ta'ajiye. bayan tadawo sai tashiga daki tadauko wayar da "Abdul-jabbar yabata bayan ta zauna ne saita mikawa Umma wayar tareda yimata bayani....</p><p><br /></p><p>Shuru Umma tai tareda jujjuwa wayar sannan tace toh" Humaira nifa bana san karbe-kaben kayan samari, tsayama dai tukun na inafata dai ba rokon sa ki kayiba?</p><p><br /></p><p> Da sauri Humaira tace a ah Umma niban rokesa" ba, Umma tace ah toh" domin ni gaskiya banason roko saboda yana zubarda kima da darajar ya'mace a idon samari.</p><p>Allah Umma ni barokonsa naiba shi yabani dakansa,</p><p>Toh" shikenan yanzu abinda nakeso dake shine kibari yayan kin" yazo saimusan yadda za'ai kinji KO?</p><p><br /></p><p> Murmushi Humeeh tayi tace toh" Ummana yanda duk kikace haka za'ai,</p><p><br /></p><p> haka suka cigaba da hira har aka kira sallar isha'i suka tafi yin sallah.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*****************</p><p>Koda yah Himu yazo week Umma tayi masa bayanin kan wayar Da "Abdul-jabbar yaba Humeeh, baice komai ba... saidai yace abata tayi amfani dashi saidai takula dakainta tatsare mutuncinta.</p><p><br /></p><p>Toh tunda ga wannan lokacin kuma sai soyayyar su itada "Abdul-jabbar yakara karfi,</p><p> </p><p>Koda yaushe suna makale awaya KO Abdul-jabbar baige gidansu Humeeh toh" za'asha soyayya tawaya,</p><p>Sun shakuda juna sosai har sunajin idan daya yarasa daya tofa sai a slow,</p><p><br /></p><p>Ah soyayya sukeyi kamar bagobe suna tsaka da Soyayyarsu kwatsan sai wani lamari ya shiga masu.</p><p><br /></p><p>Wata Rana Abdul-jabbar yaje gurin Humeeh bayan sun sha hirarsu Wanda aran nan hada Hanah akayi hirar kasan cewar sunzo, saida ita Haleeh ta tafi gida dawuri saboda Hajiyar ta tace takoma gida dawuri zatayi mata aiki saboda haka sai bata dadeba ta tafi don hakane ma bataga Abdul-jabbar din ba. sai Hanah ce kawai tagansa"</p><p>Suna cikin hira sai Hannah tace zata tafi gida bayan tafiyar "Hannah da dan mituna kadan sai shima Abdul-jabbar yatafi,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana kulle kofar mota sai yaji wata murya abayansa tamkar ta mashaya tace ya kake? Bai juyaba saboda a tunanin sa ba dashi akeba,</p><p><br /></p><p>Jiyayi ansake fadar ya kake? saboda haka sai yajuya don yaga wakeda wannan murya haka irin ta mayashaya,</p><p><br /></p><p>Aikam yayi arbada wata yarinya tana sanye da wata Riga body hook da kuma minin siket kafarta sanye Da wani high shoe tarataya kwankan gefe, kanta yaci uban atterch jiki shaya belicin yagaji ga farce zaro-zaro sun sha janfarce fuskar nanko tasha makeup ba kyan kallo. Amma ita kam agurin ta tahadu batada wani fasali sai kace sandar sunuka.</p><p><br /></p><p>Bayan yakare mata kallo sai kuma yafara tunani aransa wannan kuma wacece haka?</p><p><br /></p><p>Katse masa tunanin tayi dacewa baka ganeni bane?</p><p><br /></p><p>Ya kalleta fuskarsa ayamutse yace inafa naganeki,</p><p> keh' nibanma taba ganin ki ba sai yau,</p><p><br /></p><p>Tace Lah kodai kamanta dani? yace eh toh' da alama Na manta dake kam.</p><p><br /></p><p>Tayi wani yake wanshi dariya tace yoh nice fa Lariya,</p><p><br /></p><p>Ya tabe baki tareda kauda kai gefe yace toh" Lariya ta'ina kenan?</p><p><br /></p><p>Dariya tasake yin tace Lah! Kai Abdul-jabbar haryanzu baka tunaniba ?</p><p><br /></p><p>(Aransa yace ai mutanan kwarar ake tunawa ba'irin kuba), afilikuma cikin kosawa da maganar Yace Ayyah ban tunakiba?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tace yoh nice" fa Lariya yar Hajiya "Jumma.</p><p><br /></p><p>Yace oh! Allah sarki toh"sannu fa ya Hajiyar taki take?</p><p><br /></p><p>Tace Lafiya lau i tacema tace nazo nagaida Hajiya A'i,</p><p><br /></p><p>Yace toh" Sannu da kokari ki gaisheta, yafada yana kokarin shiga cikin gida.</p><p><br /></p><p>tace Abdul-jabbar yajuyo batare da ya" amsa, takarasa wurin sa har jikinta yana kokarin gogar nasa jikin.</p><p><br /></p><p>Dasauri yaja baya domin kuwa wani irin Kari yaji tanayi, </p><p><br /></p><p>Dariya tayi tareda cewa Abdul-jabbar kanada kyau fa, hannun ta mika danufin shafo kyakkyawan shajansa tace Inason irin wannan abun yanada kya!</p><p><br /></p><p>Wani uban tsawa yadaka mata Wanda yasatai sauri sauke hannun ta, harara ya watsa mata cikin takaici Yace keh! dalla gafara meye haka? </p><p>Batace komai ba saidai ido data tsura masa. </p><p><br /></p><p>Harara yasake watsa mata tareada jan dogon tsaki mtsww.</p><p><br /></p><p> sannan ya juyawa yanufi gida cikin takaici domin gaba daya tabasa haushi,cikin rai sakuma yace dafa da wannan kazamin Hannun nata" zata tabani Kai! Amma da tacuceni, yayi kwaf dai-dai lokacin yake bude kofar dakin sa.</p><p><br /></p><p>Wayarsa ce tayi kara dasauri yaduba sunan daya ganine yasa yai lallausan murmushi. bariyai saida ta katse sannan yakira tareda bude sifika A hankali ya lumshe ido yace my cool yakike?</p><p>Cikin zazzakar voice dinta tace Lafiya lau dama Inason naji yaka isa gida?</p><p><br /></p><p>Yace Lafiya lau Na isa kingama yanzu Na shiga daki.</p><p>Tace toh ka huta lafiya ka kuma gaida "Mama da baba "Lami,</p><p>Yace ai bazan fadaba. dasuri tace why?</p><p>yace kullun fa cewa kike Na gaida su" ya sassauta murya yace please My cool kizo kidai dasu mana dakanki kinji?</p><p><br /></p><p>A hankali tace nifa kunya nakeji Amma dai zanzo.</p><p>Da sauri yace yaushe zakizo?</p><p><br /></p><p> Tace zanzo very soon Amma dai yanzu kace in gaida su.</p><p> yace toh" zasuji tunda kin kizuwa nima kigaidamun da "Ummata tace toh" zataji, sanna sukai sallama ya kashe wayar tareda jefata saman gado sannan yanufi Cikin gida.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tundaga zaure Lariya take kukan Sangarta tana shiga Cikin gida sai tafara jifa da jakarta da kuma takalmanta, sannan tayi zaman yan'bori a tsakar gida sai kuma tasaki wani kuka Mara dadin saurare.</p><p><br /></p><p>Da sauri Mahaifiyarta Hajiya jumma tafito daga daki, hartana buga tun-tube da bakin kofa zani a hannun dankwali a hannun. </p><p><br /></p><p> Da sauri tanufi gurin yartata tadafa kafadarta Cikin tashi hankali tace Lariri ta maiyasa meki? mai akai maki ?</p><p>Taya mutsa fuska tareda tura hannun ta Cikin wannan danbanzan gashin dokin tana yamutawa (nabakin tsofaffi ) sannan tace Hajiya ni aure nakeso.</p><p><br /></p><p>Ajiyar Zuciya Hajiya Jumma tasauke, tace haba Lariri aini Na dauka wani abun akai maki.</p><p><br /></p><p> Sai kuma</p><p> tawashe dafaffun hakoranta wai ita adole dariya take tace A ah abu mai sauki aini nan daki kagan'ni kullum fatana baiwuce naga auran kiba.</p><p><br /></p><p>Taso zonan kafada Mani kinsamu Wanda kikesone?</p><p><br /></p><p>Saman wani banci suka zauna Hajiya jumma ido ta tsurama yartata tana neman Karin bayani, Lariya tace eh nasamu.</p><p><br /></p><p>Tace toh"- toh" wanene shi? tace Abdul ne, tace wani Abdul din? tace Abdul-jabbar Dan wajan Hajiya A'i.</p><p><br /></p><p>Aikam tasake washe bakin tace A ah kice tuwona maina za'ai kenan KO? </p><p>ta daga Kai alamar eh, tace toh" shiyace yana sanki? tace eh Ai mun kwana biyu muna Soyayya bandai fada maki bane saboda inajin kunya.</p><p><br /></p><p>Nikam saboda Tsabar mamakin jin Abunda Lariya tafada harsaida birona yakusa fadiwa kasa, DA sauri narike tareda tsura mata ido ganin yadda take kauda kai gefe ita adole kunyar takeji</p><p> </p><p>Tabdi sunan wani waishi "zubairu(ah ita" kam wannan zubairace)</p><p> </p><p> Hajiya Jumma ta washe baki tareada dukanta" kadan akafada tace yar'nema kunyar me? shakuru minki indai "Abdul-jabbar ne kamar kin auresa' gobe zanje nasamu Hajiya A'i sai mutsara yadda za'ai kinji KO? tace toh"</p><p> </p><p><br /></p><p>Nasan dai mai karatu zayaso yasan WACECE Hajiya Jumma tare DA yarta LARIYA, Hajiya Jumma mutumiyar Buruku ce tanan Cikin garin Kaduna Hajiya Jumma macece mai zaman kanta saboda San abun duniya yasa tabaro garin iyayanta Buruku tadawo nan Cikin kaduna dazama.</p><p><br /></p><p>Hajiya Jumma irin matan nan ne masu auren Mutum badan Allah ba saidan Abun hannun shi batada wani kyau, asalima bakace sosai gata batada hanci saidai kam tanada dirin Allah yaimata Kira mai kyau. </p><p><br /></p><p>Wanda dashi take cutar duk Wanda yace yana sonta dazar kace kana sonta toh" shikenan saitabi boka DA Malam ta aure ka bayan ta aure ka idan kanada iyali sai tarabaka DA iyalinka, sannan ta mallakeka ta kuma rabaka da Abunda ka mallaka daga karshe kuma taraba ka da rainka Hajiya Jumma kenan muguwar mace ce ta iya shiga bokaye da Malamai sosai </p><p><br /></p><p>A hakanan ta mallaki dukiya mai tarin yawa tasayi gida tasayi adai-dai tasahu har guda uku take bada haya ana kawo mata kudi,</p><p><br /></p><p> kuma tana zuwa kano saro kaya su atanfofi dasu lesissika dadai sauransu. </p><p><br /></p><p>don haka Cikin lokacin kankani tayi kudi hartaje makka inda acan'ne suka hadu da Hajiya A'i mahaifiyar Abdul-jabbar suka kulla aminta.</p><p><br /></p><p> bayan sun dawo makka ne sai Hajiya Jumma taci gabada kasuwancin ta inda Allah ya hadata dawani Mutum mai suna Labaran, yanuna yana santa wani abun mamaki shine itama Allah ya jarabe tada navigate sanshi cikin lokaci kankanidon haka ba'adauki wani lokaci ba aka saura masu aure.</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu da yin aure sai Labara yazoma Hajiya Jumma da Labarin cewa anche Lagos tafi kano saukin kaya, saboda haka takawo kudi yaje yaraso mata kaya acan aikam saikace wadda yaima asiri(dayake yafahimci cewa itadin gurin kudi batada sauki) </p><p><br /></p><p>aikon tawashi kudin ta tabashi harda sayarda adai-dai sahunta guda biyu duk tahada kudin tabashi yatafi.</p><p><br /></p><p>Aure da Albarka</p><p>Bayan tafiya Labaran da sati uku sai Hajiya Jumma tafamci cewa tanada Ciki, </p><p>Saboda haka murna kamar ya kasheta.</p><p><br /></p><p> Tunda duk aure-auren datayi bata taba haihuwa ba sai wannan, saboda haka saita maida hankalin ta gurin kulada Cikin ta.</p><p><br /></p><p>Har Cikin ta yakai wata hudu ba Labaran ba labarinsa,</p><p>(Hmmm Abunda Hajiya Jumma bata saniba shine Labaran rikakken Dan cacane kuma mane min matane,</p><p> don haka koda yaje Legos Abunda yai tayi kenan da kudin.</p><p><br /></p><p>Saida Cikin ta yakai wata biyar sannan sai gashi yadawo, dawasu yankaya wayanda KO Rabin-rabin kudin daya yaje dasu basu Kai ba.</p><p><br /></p><p>Aikam sun kwashi yan'Kallo domin kuwa mutane ta tara masa tana taimashi masifa akan sai yafito mata da kudin ta tunda bai saro mata kayan ba, sai faman masifa take bata kodamu DA Cikin dake jikinta ba.</p><p><br /></p><p>Shikam dayake tantirin Dan duniya ne sai ya kalalla meta dace mata aikayan yana siya yana sayar wane acan kuma anasamun riba sosai.</p><p><br /></p><p>yanzu hakama yasiya yabarma abokinsa yakula masa dashi. yanzu ma Abunda yasa yazo saboda yanata tunanin ta dakuma mafarkinta shiyasa yazo don yaganta shine acikin kayan yataho mata da wannan.</p><p><br /></p><p>Aikom sai tashiga washe baki ita adole miji yadamu da'ita, bayan kwana biyu yakoma.</p><p><br /></p><p>Besake dawowa ba harta haihu inda tasamu ya"mace mai Kama DA babanta tasamata suna LARIYA" tasha wahala sosai godiyan ta guda adai- dai sahun da'akeyi mata haya Ana kawo mata kudi.</p><p><br /></p><p>Saidai Lariya tashe Kara biyar sannan Labaran yadawo batare dakomai ba DA gashi sai kayan jikinsa, duk yacinye mata dukiya.Hajiya Jumma taimasa tarba mai kyau kamar babu komai aranta abun yabashi mamaki sosai.</p><p><br /></p><p>A wannan lokacin kuma tuni Hajiya Jumma tasangarta Lariya sosai</p><p>Ta dauki San duniya tadora akan Lariya tareda wani buri marar amfani tana kula da'ita sosai irin kulawan nan Wanda bakomai acikin sa sai zallar rashin tarbiyya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tunda ko makaranta taje idan tai badai-daiba akai mata fada sai Hajiya Jumma take har makaranta tai ta masifa wai saboda meza'a takurama yarta,</p><p><br /></p><p>Su kam malamai dasu kagaji sai suka koreta a makaranta.</p><p>Hajiya Jumma tace yoh sai me don sun koreki yi zaman ki nima uwarki ai banyi karatu ba kuma gashi Ina rayuwa ta kamar kowa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu da dawowan Labaran sai Hajiya Jumma ta fahimci Labaran yana matukar kaunar yar tashi duk Abunda yasamo toh" Na Lariya, ne kuma har zuwa wannan lokacin batace masa komai ba akan dukiyar ta da yacinye.</p><p><br /></p><p>Akwai wata Rana yadawo sai yakira Lariya bayan ta zauna sai yamika mata kunshin Laida Ashe tsirene aciki aikom sai tabude tafaraci,</p><p>tana Cikinci sai Hajiya Jumma ta kallesu sai tayi murmushi tace Laririta zonan,</p><p>Aiko sai ta tashi yanufi gurinta,ta dorata acinyarta tare da daukar guda tasaka abakinta sannan ta kalli Labaran Wanda shima suyake kallo ita DA yarta ta.</p><p>Hajiya Jumma tahade girar sama da kasa ma'ana tabata fuska kamar bata tabayin dariya ba,</p><p>Cikin daga murya tace...?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞Lufhat Ce💐</p><p>💞💞💐💐💐</p><p>💐💐💞💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page 56-60</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p><br /></p><p>------------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>------------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>LABARAN! wai kana nufin dukiya ta dakaje kacinye kaci banza kenan? bai bata amsa tambayer taba, saidai jajayeb idosa daya tsurama ta yayida yaji kirjinsa yafara dakan Uku-uku, Ahankali yace Ashe ranan zatazo?</p><p><br /></p><p>Nikam dake gefe nace tabdi Labaran ai dole wannan ranan tazo domin kuwa KO kudin Uwarka kacinye sai tayi maka magana toh" ballantana matarka.</p><p><br /></p><p>Wani killer smile Hajiya Jumma tayi Wanda yasa kirjin Labaran ya cigaba da matsananci bugawa, domin tunda yake da ita bai taba ganin tayi irin wannan murmushi ba,</p><p>Saikuma yagata daure fuska tace nasan bakada amsar bani tunda kana ganin kacinye Mani kudi kaci banza kana nufin nadauki hakuri ko? tabdi </p><p>Toh wallahi baka'isaba bazan dauki hakuri ba "Ai Hajiya Jumma ba'ai mata Abu tayefe Ina Labaran kayi kuskure idan har kayi tunani cewa zan yafe maka a ah, bana yafiya, kowa yaimani kankara toh" ni sainai masa Na itace yanzu kam nasan konace kabiyani kudi Na nasan baka dasu, saboda haka kaga wannan? tanuna Lariya dake kanciyarta sai cin nama take ba Abunda yada meta,</p><p>tace yarka ita ne madadin kudina da kacinye,</p><p>Cikin karfin hali yace aikema yarkice tunda ke keka haifeta, tayi dariya tace tabbas ya'tace saidai kabar tunani cewa Nina haifeta, saboda ninan daka ganni gurin KUDI banida mutunci saboda haka babu Abunda bazan iyayi ba indai akan kudi ne.</p><p>Cikin tsoro dajin kalamanta yace toh"Zaki siyar da'itane KO" me zakiyi da'ita?</p><p>Tai shewa tare da dariyar mugunta tace Allah nadawo inji Dan cirani Labaran Uban Lariya mai kakeci nabaka nazuba Bini Ahankali DA SANNU zakaga Abunda zanyi da yarta ka,</p><p><br /></p><p> Ta tashi tare da tajan Hannu Lariya suka nufi daki tabarshi nan cike da tsoro da kuma tunani Abunda zata'aikata da Lariya din.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>SANNU ahankali rayuwa tai ta tafiya Lariya tazama cikakkiya Budurwa a wannan lokacin kuma tuni tazama tantiriya yar'iska bin maza take bihakki DA gaskiya Wanda hakan ya farune Da taimakon Uwarta,</p><p> Wanda Labaran yayi fada yayi zagi hada su duka Amma duk abanza.</p><p>(Allah yasa wake Amin).</p><p><br /></p><p>Nikam nace toh"ai dama Kama titdina tidan duk abunda Kai sai Anyi maka</p><p>(Allah yasa</p><p><br /></p><p>Sanadiyar hakane yasa Labaran kwantawa mummunan rashin Lafiya Wanda har saida yakai shi dabarin duniya,</p><p><br /></p><p>ko" bayan mutuwar sa baisa Hajiya Jumma itada yarta Lariya sun saduda ba, saima Abunda yai gaba sai azo har gida adauki Lariya saitayi kwana DA kwanaki sannan, tadawo ma Hajiya Jumma da kudi sosai, shikam ciki gurin zubar dashi tuni ta zama customer.</p><p>Wannan shine takai tattace tarihin Hajiya Jumma da yarta Lariya, </p><p><br /></p><p> Yanzu gama yawace-yawacen ta aure takeso kuma ba wanda take so sai Abdul-jabbar, tabdijam toh" bari mugani abun zayayuyu kuwa?</p><p><br /></p><p>Washegari tun misalin karfe goma Na safe Hajiya Jumma ta isa gidan Hajiya A'i,da sallamar ta tashiga parlor Mama na zaune ta kallo atashar MBC Bollywood, </p><p><br /></p><p>Sai jin sallama tayi Ahankali ta amsa tare da dagakai sai taga Hajiya jumma, hakanan kawai sai Mama ta tsinci kanta dajin faduwar gaba saka makon ganin Hajiya jumma, Amma kuma sai bata nuna mata ba,</p><p><br /></p><p>Saidai tace a a" yau Hajiya Jumma ce agidan namu? yayi dariya tace kedai nice fa, dai-dai Lokacin data zauna</p><p> Bayan sun gaisa sai Hajiya Jumma tace "ke dai kinganni tunda sassafe "KO? Mama tayi murmushi tace "eh "ai jiyama Lariya tazo tai gaida ni aina gode Allah dai yabar zumunci,</p><p><br /></p><p>Hajiya Jumma tayi murmushi tace "ai kedai bari gawani zumunci ma zaya kara kulluwa,</p><p>Mama tace toh" daga ina kuma?</p><p><br /></p><p>Tace Hmm Ashe yaran nan Suna San junan su bamu saniba"?</p><p>Cikin rashin fahimta Mama tace wasu yara "kenan fa?</p><p>Dariya tayi tace Abdul-jabbar mana shida Lariya,</p><p>ita kam Mama jin maganar tayi tamkar Almara sai tace toh" lallai kam nibansani ba,</p><p><br /></p><p>Ta washe baki tace "eh KO" nima bansaniba sai yau Ashe ma hada alkawarin aure sukai ma junansu", Mama tace toh" kice magana ta girma? </p><p>Tace Hmmm kedai bari "ai abun yayi dadi kinga shikenan sai "ai tuwona maina,</p><p><br /></p><p>Mama tace kinga nikuma banga alamar faruwar hakan ba,</p><p><br /></p><p>Da sauri Haj jumma tace saboda me? yasa ki kace haka Haj A'i?</p><p><br /></p><p>Saboda tarbiyyarsu tasha ban-ban ke kanki kinsa cewa " "Lariya batada ce da shiba, ba wannan ba kinsani sarai cewa "Lariya batada tarbiyya duk kin bata yarinya Sam ba kiyi mata tarbiyyan kwarai, ba jifa jiya yadda tazo gidan nan kamar ba diyar muslmai ba, gaskiya Yaron nan bazaya auri Lariya ba.</p><p><br /></p><p>Ita kam Haj Jumma idan ranta yakai dubu toh"yabaci DA jin kalaman Mama,</p><p><br /></p><p> Sai ta kalleta rai abace tace Haj A'i yanzu Abunda zakice Mani kenan? tace " aike kinsa abunda nafada gaskiya ne,</p><p><br /></p><p>Tace toh" "ai shikenan bakomai nagode nizan tafi tafada ranta bace tare da mikewa tsaye,</p><p><br /></p><p>Itama" Mama mikewa tsaye tayi tareda cewa a a" har Zaki tafi kenan?</p><p>Tace Ummh dai-dai Lokacin da takai bakin kofar fita,</p><p><br /></p><p>Mama tace toh"sai anjima ki" gaida gida, bayan ta" koma tazauna sai tace "ai "shikum zata shigo yasameni idan bayada ahankali ne toh" "ai nagani,</p><p><br /></p><p>Duk yan'matan cikin garin nan yarasa wadda zayayi Soyayya da ita sai "Lariya, ko"me yagani ajikinta" daya birgesa Rashin tarbiyya? ko" kuma rashin Kamun kai? "oho masa.</p><p><br /></p><p>Sai misalin karfe 11:15 Am sannan Abdul-jabbar yashiga cikin gida, yana sanye da Riga T.shat white da wandon jeans black hannun rige da key mata sai zuba kamshin yake,</p><p><br /></p><p>Saida ya zauna ya Lankwashe kafafu sannan yace Mama Ina kwana?</p><p>Ta amsa rai bace da Lafiya lau,</p><p>idanu tsura mata domin yaga ranta kamar abace,</p><p>Saboda haka sai yace Mama meya faru naga kamar ranki yabaci?</p><p><br /></p><p>Tace "ai ba Kama bane raina abace yake sosai, yanzu saboda Allah duk yan'matan garin nan karasa wadda zakai Soyayya sai "Lariya </p><p>Kai KO" mekagani ajinta" daya birgeka?</p><p> </p><p>Big eyes dinsa yazaro,Wanda har saida yasa taji faduwar gaba saka makon tuno mata wani Abunda idanun sa yayi, ga kuma wani irin kwarjini da sukai mata.</p><p><br /></p><p>Don haka DA sauri takauda idonta daga barin kallon sa,</p><p><br /></p><p>yace Mama "Lariya fa ki kace? Cikin jin haushi tace wannan wani irin abune haka Ina tambayar "ka kana tambaya ta?</p><p>Ko" baka game "Lariya yar gurin Haj "Jumma ba?</p><p>ba harda alkawarin aure Kai mata ba?</p><p><br /></p><p>Yace kiyi hakuri Mama nagane ta" jin abun'nayi kamar Almara, niko" me zaya birgeni ajikin "Lariya da zayasa nayi Soyayya DA ita,"har nayi mata alkawarin aure?</p><p><br /></p><p>Hmmm Mama ke dagajin wannan Magana kinsan ba gaskiya ba ne,</p><p>Haba dai tabdi</p><p>God for forbid nayi Soyayya da "Lariya har nai mata Alkawarin aure,</p><p><br /></p><p>Yarinya DA batada kamun Kai kowa yatashi sai yakwashe ta, sai Dan banzan yawo wato</p><p>Yanzu tagama yawace-yawacen ta zatai aure sai nikuma nakwasa, tunda banida kowa KO"? toh" bawai hakan yana nufin nakai kaina ga halaka bane,</p><p>Yaja dogon tsaki mtsww</p><p>Kai amma dai yarinyar nan taraina ma kanta"hankali</p><p>Toh"nima ida baji dana ganta ba a kofar gida nan harna manta dawata "Lariya yai kwaf,</p><p><br /></p><p>itakam mamaki abun yabata don haka,sai tace kana nufin kace Kai bakata ba zuwa gurinta ba?</p><p><br /></p><p>Cikin takaici Yace haba Mama me zanjeyi gurinta? ke kanji kinsan bata dace Dani ba ,ya kuma Jan tsaki mtsww sannan yace Allah Maya hadani da'ita sai naci mutuncinta.</p><p><br /></p><p>Tace a a" karabu dasu duk abinda suke nufi ya kare Kansu, ya mike tare da cewa nizan fita, tace toh" sai kadawo.</p><p><br /></p><p>Shuru Mama tayi tana nazarin maganar da Haj "Jumma tazo mata dashi,</p><p>Jitayi gabanta yafadi saka makon tunawa da tayi kowacece Haj "Jumma,</p><p><br /></p><p>Ahankali tafara tunani wani lokaci da "Haj Jumma tazo gidan ta bayan sun gaisa, </p><p>Sai tace ke KO" Haj A'i meyasa bazaki auri Alh ya'u nakaka ba? gashi acikin Bari anata maganar yana sanki sosai,</p><p><br /></p><p>Mama tace saboda bana ra'ayin aure,</p><p>Haj Jumma tace</p><p>Kinga idanice ke KO"? wallahi auransa zanyi, Mutum mai kudi irin "Alh ya'u nakaka tabdi "ai bazan barsaba, kinga idan kina tsoron matarsa ne toh" kisha kuruminki", ninan daki kagani nasan bokaye da malamai Kala-Kala saboda haka kizo muje nakai ki" gurin boka yan miki maganin ta",</p><p>ke" bama ita kadai ba har dashi" Alh ya'u Na kakan sai boka ya asirce mikisu, Ke koma kashesu" kikeso ayi boka zata iya.</p><p><br /></p><p>Da sauri Haj A'i tace "a ah Haj Jumma kisafa kikace?</p><p><br /></p><p>Tace eyi "yoh toh" meye? tace gaskiya nibana zan iya kashe mutum ba,shiko" harka Da boka Da malam ban iyasaba kuma banason Na iyashi har abada, bama haka ba ni aure ma baya gabana saboda hakanan mubar wannan maganan.</p><p><br /></p><p>ajiyar zuciya tayi tareda dawowa daga dogon tunani datake,</p><p>tace toh" ni bansa Abunda "Haj Jumma take nufiba da tace "Lariya suna Soyayya DA wannan yaron ba toh" me hakan yake nufi?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Itako Haj Jumma rai abace ta isa gida Lariya ta tambaye ta yadda sukai da Haj "A'i ? nan tafada mata komai "aiko Lariya sai tasaki kukan sangarta tace itakam wallahi idan ba "Abdul-jabbar bazata auri kowa ba,</p><p><br /></p><p>Haj Jumma tace kwantar da Hankalin ki indai "Abdul-jabbar ne sai kin aure sa kota halin kaka, badai Abunda Haj A'i tace Mani kenan ba? toh" sai tazo gidan nan daka farta taro keni ki auri danta, da alama ta tamanta KO" wacece Haj Jumma toh" Amma zantuna mata,</p><p>tashi kitafi abunki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>****************</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu</p><p>Abdul-jabbar ne zaune Shida Humeeh firarsu suke ta masoya, sai ya kalleta Cikin So da kauna Yace my cool idan muka tafi zanyi kewarki sosai fa.</p><p><br /></p><p>DA sauri ta kallesa tace Ina kuma zaka tafi? yace kin manta nafada miki cewa zamuje America yin wani cos? tace "eh natuna yaushe zaku tafi? yace nanda three weeks,</p><p>tace Amma dai baza kodade ba KO"? ummh one year ne kawai, DA sauri tace shekara daya ne kawai? tafadi haka ne kamar zatai kuka.</p><p><br /></p><p>Ahankali yace my cool idan akwai raida lafiya shekara daya a gurin Allah kamar yaune,</p><p>saboda haka karki damu very soon Zaki ga mundawo insha'Allahu,</p><p><br /></p><p>Ke nimafa don tafiyar tazama dole ne, idan badan haka ba dasai nayi zamana muyita Soyayyar mu KO"? yakai karshen maganar sa dayi murmushi, </p><p><br /></p><p>itama murmushi tayi tare Da rufe fuskarta Da hannun alamar kunya, hakan sukaci gabada fira har tsawon wani lokaci sannan yatafi gida.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mama ce keta faman safa da marwa a tsakiyar parlor, kallo daya zakai mata kafahimci cewa hankalin ta atashe yake,</p><p><br /></p><p>Koda Abdul-jabbar yashiga ya isketa Cikin wannan halin,</p><p><br /></p><p>Ya kalleta tare da cewa Mama Lafiya?</p><p>Cikin tashin hankali tace sonake yanzun nan Kai maza-maza katafi gidan "Haj Jumma kudai-daita juna kaida "Lariya,</p><p><br /></p><p>DA karfi Abdul-jabbar yace eyeeee? </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞Lufhat ce💐</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU </p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> Page61-66</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p> ------------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE</p><p> STRONGEST WEAPON</p><p>------------------------------------------</p><p><br /></p><p>only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shidin ne" bayada Uba? Haj Jumma tade fuska tace "eh "shidin mana, yoh yanada ubane idan kuma kince yana dashi toh" yana ina" Uban NASA"?</p><p><br /></p><p>Mama tace haba Hajiya yazakice bayada Uba wallahi yanada uban sa kamar KO wani da dakikasani,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tace Hmmm Haj A'i kenan inada labarin kifa kaf, tunda kikazo garin nan yau kimani shekaru kusan talati Amma baki taba zuwa gida ba, </p><p>sannan kuma wani dan'uwan ki be taba zuwa gurin ki ba kinga hakan yana nufin kinyi abun kunya ne, shiyasa ki kabaro garinku ki kadawo nan dazama KO?</p><p><br /></p><p>Itakam Mama komai ya kwance mata saboda haka sai tarasa abunda zatace,</p><p>tabbas a Cikin ranta taji zafin kalaman Haj jumma musamman Na San shegan ta mata DA datake shirin yi saidai babu yadda zatai da'ita, </p><p>ita dai yanzu burinta kawai shine Haj Jumma ta amince yarta ta auri danta,</p><p><br /></p><p>Ahankali tace Haj Jumma wallahi dukkan abunda kike fada ba haka bane,</p><p> ni banyi abun kunyaba </p><p>kuma bana tunanin "aikata sa a rayuwa ta,</p><p><br /></p><p>kuma kamar yanda nafada miki abaya cewa shi ba shege bane toh"ba shege bane yanada uba,</p><p>Saboda haka mu daina wannan maganar,</p><p><br /></p><p>Mufuskanci wannan maganar danazo muyin, nidan Don Allah Haj Jumma ki yarda da maganar auren yaran nan,</p><p><br /></p><p>Wallahi idan ba auran nan akayi ba hankali Na bazai taba kwanciya ba,</p><p><br /></p><p>Haj Jumma tace Hmmm Haj A'i manya toh shikenan,</p><p> Amma dai kije tukun Na sainayi shawara</p><p><br /></p><p>Mama haba Haj jumma wani irin shawara kuma?</p><p><br /></p><p>Tace "eh idan mukai shawara da ita Laririn tawa kinga koda nan da kwana biyu ne ke" dawo kiji abunda kenan,</p><p><br /></p><p>Itakam Mama ba haka nan taso ba toh" Amma ya ta'iya dole ta tafi gida har zuwa bayan kwanan biyun,</p><p><br /></p><p>ta mike tsaye tareda cewa</p><p>Toh"shikenan nagode Haj jumma nizan tafi toh" ki gaida gida toh" tafita,</p><p>yayin da Haj Jumma tabi bayanta</p><p>da harara a ranta tace Zaki gane naje gidanki" kinyi Mani walakanci saboda haka sai narama abunda kikai mani domin nibana yafiya",</p><p><br /></p><p>taja wani dogon tsaki mtswwwww sannan ta mike tashiga daki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Washa gari da misali karfe 10:15 Am,</p><p>Zaune suke su uku suna break fast suna Dan fira kadan- kadan kamar yanda suka saba, Amma kuma sai sukaga yau Humeeh tayi shuru,</p><p><br /></p><p> Humeeh kam tunanin halin dataga special dinta jiya takeyi, itakam tunda take dashi bata taba ganin sa Cikin wani yanayi irin najiya ba</p><p>Ahankali tayi ajiyar zuciya,</p><p><br /></p><p>Haleeh ce tadan taba Hannah tareda yimata nuni da Humeeh, tambayan ta tayi da ido alamar meyasa mi Humeeh din? amsa tabata alamar itama bata sani ba,</p><p><br /></p><p>Hannah ce tace Hey Miss special what is happen?</p><p>Haleeh tace yes tell us" meyasa meki ?</p><p><br /></p><p>Murmushi tayi tace nothing, baki suka hada sukace Ahhhh!</p><p>Shine mukaga kinyi shuru?</p><p><br /></p><p>Dataga sun dameta saita fada masu abunda yasa tai shuru</p><p>Suma shurun sukai,</p><p><br /></p><p>can sai Haleeh tace kila kansa ke ciwon kamar yadda yafada maki,</p><p>Hakan nan sukaci gabada fira har lokacin komawa class yayi suka tashi sukanufi class.</p><p><br /></p><p>*******************</p><p>Kwana biyu nan Mama tayishi ne Cikin matsananci wahala domin kuwa hankalin ta atashe yake natsuwarta ta gushe, hada wata yar ramewa tai tunanin ta yatsaya a guri daya shine Abdul-jabbar ya auri "Lariya yar gidan "Haj Jumma,</p><p><br /></p><p> shikasan Abdul-jabbar baya cikin nutsuwa badama yashiga cikin gida sai Mama tace masa kaje gidan su "Lariya kuwa? wani lokaci yace mata "eh wani lokaci kuma yace mata "a ah dayagane idan yace mata "a ah sai tayi tafada, saboda haka saiya daina ce mata " a ah idan ta tambaye sa sai yace mata "eh kawai.</p><p><br /></p><p>Kamar yanzu ma yashiga Cikin gida Don yafada mata zai fita,yana sanye Cikin kananan kaya sai kamshi yake zubawa,</p><p><br /></p><p>Bayan ya gaida ita kafin duk yace wani abu, sai tace zakaje gidansu "Lariya ne? yace "eh tace toh" nima Ina nan zuwa saboda yaune mukai da ita zanje sai mutsara yadda auren zaya kasance,</p><p><br /></p><p>Jiyai kirjinsa" ya buga ya kalleta" cikin tausayin kansa yace Mama Dan Allah kiyi Hakuri da maganar auren na da "yarinya nan Wallahi bana Santa,</p><p><br /></p><p>Nafada miki Mama</p><p>Inada wacce nake So itama tana sona" kuma wallahi yar gidan mutunci ce, kinga yau saura sati biyu mutafi kinga Dana dawo sai "ai maganar aurenmu da Humai</p><p><br /></p><p>Katse shi tai da cewa dalla rufe mani baki, ni"basan wata "Humaira ba "Lariya nasani, maganar aure kuwa idan kaga na barshi toh" bana numfashi ne "aini idan ba auren nan akai ba toh" hankalina bazaya taba kwantawa ba, saboda haka kawai katashi katafi nima gani nan zuwa</p><p>Haka yatashi jiki ba kwari yafita.</p><p><br /></p><p>Shikam Abdul-jabbar daya fita</p><p>Bai tsaya ko'ina ba sai gidan "Alh ya'u Na kaka, domin yasanar dashi abunda ke faruwa, saboda yasan "Alh ya'u Na kaka ne kadai mutumin da "Mama take jin maganar sa", </p><p><br /></p><p>Ya yinda ita kuma tafito tanufi gidan Haj Jumma,</p><p><br /></p><p>Da sallamar ta tashiga gidan yayinda Haj jumma ke zune a tsakar gida taji sallaman Amma bata amsa mata ba, toh" itama Mama bata damu darashin amsa matan ba,</p><p><br /></p><p>Kujera ta dauka ta zauna bayan sun gai sai sannan Mama tace Haj Jumma nazo ne akan maganar auren yaran nan, </p><p><br /></p><p>"aikam nanta ke sai Haj Jumma ta daure fuskarta tafara surfa masifa tana cewa "aidama nace sai narama walakanci daki Kai Mani lokacin da naje gidanki, </p><p><br /></p><p>kuma maganar aure tsakani danki da yata babu saboda ta tace bazata auri Abdul-jabbar din ba tunda kince batada tarbiyya</p><p><br /></p><p> saboda haka sai kije kisamo masa mai tarbiyya ki aura masa,</p><p><br /></p><p>Itakam Mama jikinta sai rawa yake saboda tsanani tashin hakali, </p><p><br /></p><p>tace Don Haj Jumma kitai makeni kirufa Mani aisiri wallahi idan ba auran nan akai ba hankalin bazaya taba kwanta waba, Oh Allah sarki Mama baiwai Allah,</p><p><br /></p><p> (Kai jama'a Allah Kai mana tsari da Aminai irin su Haj Jumma Amin)</p><p><br /></p><p> Saida Haj jumma ta tabbatar dacewa Mama ta galabaita sannan, tunda harda guntun hawayen tareda zube guywuyunta akasa tana rokon ta akan ta aminci da auren yaran nan sannan,</p><p><br /></p><p>Da karfi Haj Jumma tace Na amince Amma da sharadin?</p><p><br /></p><p>Da sauri Mama tace na amince da KO" wani irin sharadi ne</p><p><br /></p><p>Tace inason da daurin aure da komai karya wuce sati daya, Don wallahi idan ya wuce sati daya toh" saidai afasa,</p><p><br /></p><p>Mama tace na amince, Haj Jumma ta mike tanufi daki tareda yima Mama dariyar mugunta, tace Oho nadai fada maki" dai dai lokacin da tashiga daki,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mama ta mike tana cewa nagode sosai sai anjima.</p><p><br /></p><p>Koda Mama tafita batai tunanin zuwa ko'ina ba sai gida "Alh ya'u Na kaka,</p><p><br /></p><p> domin tasan shine kadai ne mutumin" da zaya tsaya mata akan maganar aure nan Don haka direct cen tanufa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sallamar ta tashiga parlor zaune suke su uku, Alh ya'u Na kaka Y Y k Da Kuma Abdul-jabbar domin tun-tuni ya isa gidan,</p><p><br /></p><p>Suka amsa sallaman tareda daga Kai suka kalleta, Alh ya'u Na kaka Dattijon kirki mai cikar kamala, </p><p><br /></p><p>Yace ah Haj A'isha ne sannu da zuwa, tace yauwa sannu Alh adai-dai lokacin data zauna a daya daga Cikin kushin din parlor,</p><p><br /></p><p>Bayan sun gaisa ne sai Alh ya'u yace Haj A'isha dama KO" yanzu nake cewa Na Dabo" yaje ya daukoki"saboda Ina San magana dake",</p><p><br /></p><p>Tayi murmushi tare da cewa Allah sarki nima dama nazone naiman wata alfarma,</p><p><br /></p><p>Alh yace toh" Haj A'isha wani irin alfarma kenan fa?</p><p>Nan tafada masa abunda yake tafeda ita,</p><p><br /></p><p>Shuru Alh ya'u yayi yana nazarin maganar ta, cen yanisa yace Naji abunda ketafe dake Amma Haj A'isha meyasa like San Abdul-jabbar ya auri "yarinyar nan? Shin meyasa bazaki bari ya nemi yar gidan mutunci me tarbiyya yaura ba?</p><p><br /></p><p>Tayi dariya tace Alh wannan ma "ai yar gidan mutunci ce "Lariya ce fa yar gurin Aminiyata ce "Haj Jumma,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yace yanzu nidai abunda nake soda ke shine kiyi Hakuri abar maganar auren nan Don Allah kinji KO?</p><p><br /></p><p>Aikam tuni jikinta ya dauki rawa tace Don Allah Alh ka taimaka mani wallahi idan ba auren nan akayi ba, bazani taba samun nutsuwa Da kwanciyar hankali ba a rayuwa ta,</p><p><br /></p><p>Tanuna Abdul-jabbar tareda cewa wannan yaron Sam bayajin magana ta,</p><p><br /></p><p>Tun-tuni nake masa maganar aure nan Amma yaki saurarena,</p><p>Wai "ace ka haifi yaro da Cikin ka kasayai maka abu sai yaki yimaka toh" "ashikenan, kawai sai tafashe da kuka,</p><p><br /></p><p>Shikam Abdul-jabbar kirjinsa" ne yabuga yayinda jikinsa" yadauki rawa,</p><p><br /></p><p>Da sauri yamatsa kusada kafarta cikin tsoro yace Mama kuka kike yimani?</p><p><br /></p><p>Hannun sa yadora duk akai yace kaichona ni" Abdul-jabbar mahaifiyata kemani kuka? Wayyo Allah Na,</p><p><br /></p><p>ya kalleta da idanusa dasuka kada sukayi jajir yace ki taimakeni Mama kidaina kukan nan, kinsa cewa kukanki" agareni babbar masifane? </p><p><br /></p><p>Cikin kuka tace toh" idan banyi kuka ba meka keson nayi? tunda bakajin magana ta,</p><p><br /></p><p>Wani irin Yasu Abdul-jabbar ya hadiya mai daci sannan yace toh"Mama kidaina kukan hakanan,</p><p> kifadi abunda kikeso nayi miki" koda hakan yana nufin daukewar numfashi nane zanyi miki shi insha'Allahu,</p><p><br /></p><p>Tashare hawayen dagefen zaninta tareda fece majina, sannan tace toh"aini dama "Lariya kawai nakeso ka aura,</p><p><br /></p><p> wallahi jinake idan har baka aure taba "Lariya ba zuciya ta bugawa zatai,</p><p><br /></p><p>Da sauri Abdul-jabbar yace.....?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞Lufhat ce💐</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page67-70</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dan Allah kuyi hakuri narashin ganin posting din kwata biyu wallahi aikine yai mun yawa nagode,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Innalillahi'wa'inna'ilaihinraju'una, Mama Zuciyar ki bazata bugaba insha'Allahu badai "Lariya ki kesan Na aura ba?</p><p><br /></p><p> Da sauri tace "eh yace toh" Zan aure ta tace toh"Allah yai maka Albarka ya kare mani Kai yace Amin Mama,</p><p><br /></p><p>Alh ya'u nakaka shida Y Y K kallon su" suke cike da tausayin su ,</p><p>Musamman ma Y Y K dayake tsanani tausaya ma Amin'ninsa akan wannan aure daba yada tsari,</p><p><br /></p><p>Alh ya'u shuru yai nazarin yake aransa tabbas abun'nan Na Haj A'i akai sihiri Cikin sa,</p><p><br /></p><p>Yai nauyayyan ajiyar zuciya yace Haj Aisha ki kwantar da hankalin ki, inda Abdul-jabbar ne zai auri "Laria take KO wa?</p><p> </p><p>murmushi tayi tareda cewa "Lariya ne sunanta yace toh" indai hakan shine farin Cikin ki toh" zaya aureta,</p><p><br /></p><p> Amma dai sai yadawo daga kos tunda saura sati biyu sutafi,kuma ba wani dadewa zasu yiba tunda duk bai wuce suyi shekara daya ba, </p><p><br /></p><p> kinga dasun dawo sai "ai maganar auren KO?</p><p><br /></p><p>DA sauri tace a ah Alh "ai mun'riga munsa rana nan da sati daya muke San "ayi bukin,</p><p><br /></p><p> Y Y k baisan lokacin da yace what ba?</p><p><br /></p><p>Shikam Abdul-jabbar daya zaune tunda zu kamar butun-butumi jiyayi kirjinsa yaci gaba da matsananci bugawa,</p><p><br /></p><p>Alh ya'u Na kaka kam yanzu takara tabbatar da zargin sa na cewa Haj A'isha akwai sihiri atareda "ita</p><p><br /></p><p>Saboda hahabsai yace haba Haj A'isha wannan wani irin aure haka,</p><p><br /></p><p> daza'ace za'a yi shi nan da sati daya batare da anshirya komai ba?</p><p><br /></p><p>tace "eh nidai don Allah Alh ka yaimaka mani nasan kanada halin yin mani wannan alfarma nan,</p><p><br /></p><p>Yace Haj A'isha bawai Ina maganar cewa banida halin yi maki bane,</p><p><br /></p><p>Kuma bawai Ina alfahari bane, Abdul-jabbar kadai ba idan sunkai Mutum Dari insha'Allahu inada abunda Zan aurar dasu Rana daya,</p><p><br /></p><p>Ni Ina magana ne akan gaggawar abun,kin gaggawa " "aikin shedan ne fa?</p><p><br /></p><p>Kuka ta fashi dashi tace don Allah Alh Ka taimaka mani wlh bakaji yadda nake jibane aran'na,</p><p><br /></p><p>Da suri Alh ya'u nakaka Yace a ah Haj A'isha kidai Na kukan nan,</p><p><br /></p><p>Indai auren Abdul-jabbar da wannan "yarinyar ne ki kwantar da hankalin ki insha'Allahu za'ai shi, yanzu ma Zan tafi ne mar masa auren ta" kinji KO"</p><p><br /></p><p>tace toh" Na gode Allah yakara budi ta mike tareda cewa ni Zan tafi, </p><p><br /></p><p>yace toh" kijira su agurin Haj zasu zo sumai da ke gida, tace toh" adai- dai lokacin da tafita daga parlor,</p><p><br /></p><p>Shuru parlor tsawon wani lokaci ba wanda yace komai,</p><p><br /></p><p>Alh ya"u na ne ya mike ahankali yanufi gurin da Abdul-jabbar yake zaune kan"sa yadafa tareda cewa kiyi hakuri Abdul-jabbar kadauki wannan abun a matsayin kaddara, </p><p><br /></p><p>saidai Ina gani kamar akwai sihiri ajikin "Haj A'isha' toh" kodai ma mene muciga ba dayi mata Addu'a insha'Allahu Komai zaiyi dai-dai ne kaji ko?</p><p><br /></p><p>Ahankali yadaga Kai alamar "eh, sannan yace kuje kudau keta Ku kaita gida,</p><p><br /></p><p> yafadi haka ne dai- dai lokacin da yafita daga parlor,</p><p><br /></p><p>Da sauri Y Y K ya matsa kusada Abdul-jabbar yafada kafadar sa" yace kayi hakuri Nawa komai yai farko toh" insha'Allahu zaiyi kashi ne kaji KO?</p><p><br /></p><p>Shikam Abdul-jabbar sai Kai yaketa gyadawa sai kace kadan gare,</p><p><br /></p><p>tsabar tashin hakalin daya ke ciki yasa shi, yakasa furta koda kalmar a ne,</p><p>Y Y k yace tashi muje mukai ta,</p><p><br /></p><p>Haka suka mike jiki ba kwari suka nufi hanyar fita,</p><p><br /></p><p>***************</p><p>Cikin lokaci kankani baka fara shirin bukin Abdul-jabbar Da Lariya,</p><p>Wanda tuni Alh ya'u nakaka yadauki nauyin yin komai,</p><p> </p><p>Abagaren Haj Jumma ma haka shiri takeyi sosai domin taci buri wa bukin Lariya don haka da kare da biri duk ta gayyacesu,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Y Y k da M B suke tsaye akan sha'anin bukin shikam ango ko" ajikinsa domin KO ya dauki auren ne tamkar wasan yara,</p><p><br /></p><p>Ana saura kwana uku bukin suna zaune su uku suna" fira sai Y Y K yace kai M B bari nakira Dalter boy na yafada masa, </p><p>M B yace gaskiya ya kamata,</p><p><br /></p><p>Shikam Abdul-ganiyyun wato dalter boy mamaki yake haryana tambayar Y Y K wai dama Abdul-jabbar yanada budurwar ne? </p><p><br /></p><p>shi kam Y Y k dariya yayi yace sai dai kazo tukun na,yace OK yana nan zuwa ana gobe daurin aure, yace toh" sai kazo sukai sallama.</p><p><br /></p><p> Abdul-jabbar sai faman masifa yake wa Y Y K wai akan wani dalili zayai tafadawa mutane wannan auren da bashi da tsari,</p><p><br /></p><p>Yace malam idan kanaso ne kaburge ni toh" ka tsaya aure Na da my cool yazo,</p><p><br /></p><p> Sannan kafadawa duk Wanda zaka fadawa Amma ba wannan auren ba,</p><p><br /></p><p> Wanda kai daganin sa kasan bana Allah da Añnabi bane abu haka ko"tsari babu yaja tsaki mtswwwww.</p><p><br /></p><p>**************</p><p>Yaune aka daura Abdul-jabbar da Lariya da misalin karfe goma naran Asabar,</p><p><br /></p><p>Kira'ar sheikh Ahmad Sulaiman ke tashi acikin motar,</p><p><br /></p><p>Ahankali Dalter boy ke driving dinsu Abdul-jabbar yana kusa dashi, yayin da Y Y k da M B suke zaune abaya suna kan hanyar sune ta koma wa gida,</p><p> </p><p> Y Y k ne ya katse shuru da cewa cikin zolaya oh! shikenan yau wani yazama ango,</p><p>yakara she maganar dayin gwalo ga Abdul-jabbar,</p><p><br /></p><p>Da sauri yace a ah ba ango ba ankwa Mtsww yaja tsaki,</p><p><br /></p><p>Yace don Allah Dalter boy kabi hanyar cen muje naga my cool ko" zuciya ta nayi fari,</p><p><br /></p><p>Bamusu Dalter boy yajuya kan motar tareda cewa wacece hakan kuma?</p><p>M B yace budurwar sa ce</p><p>Yace oh KO" "Humaira da Y Y K ya bani Labarin ta jiya?</p><p>M B yace ita fa kaidai, Yace "ai KO" zanso naganta,</p><p><br /></p><p>Da sauri</p><p>Abdul-jabbar yace "ai ko zaka ganta very cute baby, </p><p><br /></p><p>Y Y yace kajishi saikace wata yar jaririn, ya bashi amsa dacewa "ai jariri yar,ce</p><p><br /></p><p>da kwatance da Abdul-jabbar yake ma dalter boy har suka karasa unguwar su "Humeeh.</p><p><br /></p><p>Cikin zolaya Y Y k yace zumuje mufada mata" andauran aure ka ne da "Lariya?</p><p><br /></p><p>Yace ban saniba Nawa bafa nason walakanci daka ke mun,</p><p><br /></p><p>M B yace "au dama baifada mata" zayayi aure ba?</p><p><br /></p><p>Y Y k inafa yafada mata" nayi nayi dashi yafada mata" Amma yaki fada mata",</p><p><br /></p><p>Dalte boy yace "au haka ne toh" Ku kyalesa ni zanfada mata" yau din'nan,</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yace tunda kashe kwaya basai kafada mata" ba din ba, dalter boy yace "aiKo zaka gani,</p><p><br /></p><p>dai-dai lokacin da Humeeh ta karasa gurinsu ,</p><p>Lokaci daya suka fito daga cikin mota,</p><p><br /></p><p> Cikin jin kunya Humeeh ta gaida su,</p><p>Suka amsa fuskarsu dauke da murmushi </p><p>gogan'nata,</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar ne yagaba tarda dalter boy Humeeh ta sake gaida shi, ya amsa tareda tambayan ta ya school? tace lafiya lau,</p><p><br /></p><p>Shikam Dalter boy aransa sai yaba kyawau Humeeh yake, </p><p><br /></p><p>yayinda yake mamaki abunda yasa "Mama tace sai Abdul-jabbar ya auri wannan yarinya mai Kama da one,</p><p><br /></p><p>Maganar Humeeh ce ta katse masa tunanin sa" inda yaji tana cewa Ina zakuje yanzu KO" dama gurina kawai mukazo?</p><p><br /></p><p>Dalter boy yace "eh dama munzo ne mufada miki,</p><p><br /></p><p>DA sauri Abdul-jabbar yace....?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat ce💞</p><p>💞💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page76-80</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Umma tana zaune ita kadai atsakar gida tana linkewa "Humeeh school uniform dints kasan cewar "Humeeh bata nan ta tafi islamiyya,</p><p><br /></p><p>kawai sai taga anshigo mata gida bako sallama,</p><p>Ahankali tadaga Kai ta kalleta tace "a ah haba baiwar Allah yazaki shigo Mani gida haka bako sallama?,</p><p><br /></p><p>Lariya datake sanye da wani matsiyaci dressing ta kalli Umma sama da kasa, ta yamutsa fuska tace sallama tabdi" aini ban sannan ya'akeyin taba, Umma gyada Kai tace tabbas naga alamar bakisan yadda akeyin taba,</p><p><br /></p><p>Toh" bismillah ga wurin nan ki zauna tanuna mata shimfidar datake zaune akai,</p><p><br /></p><p>Lariya tace zama? Umma tace eh, taja wani uban tsaki mtswwwww... tace "ah bashi yakawo niba Kuma, Umma tace toh' keh! ko" yarnan meya kawoki toh"?</p><p><br /></p><p>Tace kinga Malama badon zance yakawo niba nazone infada miki kijawa yar iskar "yarki kune takiyayi "mijina,</p><p><br /></p><p>Idan Kuma bata" kiyaye "shiba wlh sainai mata" mummunan illa,</p><p>Da sauri Umma tace subhanallahi! Nidai ban haifi yar iskaba sannan kuma wanene "mijin naki? tace "Abdul-jabbar idan bata fita harkar Saba tabbas saina nakasa mata rayuwa eheee!</p><p> </p><p>tajuya danufin tafiya Da sauri Umma tace yi hakuri kinji indai "Humaira ce za tarabu da mijiki insha'Allahu kinji KO? fiyuuuu tafice tana cewa oho indai bata rabuda shi" duk abunda yasa meta ita tazajo makan ta domin ninan daki kagan'ni banida mutunci wlh DA SANNU Zan maida "yarki abun kwatance eheeee,</p><p><br /></p><p>Tun bayan fitar "Lariya Umma take zaune shuru nazari take aranta tabbas wannan "yarinya duk inda tafito toh" ba gidan mutunci tafita ba,</p><p><br /></p><p>Umma kam jitayi kirjinta yabuga saka makon tuno kalaman "Lariya ga "yarta, ahankali tasaki sanyayyan ajiyar zuciya tareda cewa inda Abdul-jabbar ne toh" Humaira tabarsa tunda bashi kadai ne da namiji ba,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin bacin rai Mama tace keh! Lariya nafa gaji da wannan abunda kikeyi mun haka, KO" agidan ku ankafada miki"haka ake zaman aure, "mijinki bayanan amma ke" kullum cikin yawon bin gari kike toh" wlh bazan cigaba da daukar wannan abun ba,</p><p><br /></p><p>Lariya ta kalli Mama sama da kasa irin kallon nan Na walakanci mai dauke da harara sannan taja wani uban tsaki mtswwww...tace hmmm wai bazaki cigaba da daukan wannan abunba, yoh Ina abun yake? hmmmm "ai ba'ai komai ba toh" barima kiji in fada miki Haj A'i kike nema kowa? gwanda cigaba da dauka domin ninan dakika ganin yanzu ne zanfara tsulamiki rashin mutunci badai kinci banida tarbiyya ba KO"?</p><p>toh" ko" zakiga zallar rashin tarbiyya damani bason wannan shegen "danki nake ba, dama wata muguwar sha'awar sace takamani toh" kuma dayake "shidin Dan bakin Cikine sai yaki yarda naji kalarsa, don haka ke kuma baki'isa ki hanani sha katawa ba eheeeee tafice daga gida, </p><p><br /></p><p>ita kam Mama kuka tafashe dashi tareda cewa "Oh ni A'isha wannan wata irin matsiface haka waima ya'akai wannan yaron ya auri wannan "yarinyar ne marar mutunci,? Nikam nace toh,</p><p><br /></p><p> baba Lami ce tafito daga kitchen tace Haj Lafiya kike kuka? Mama tace "aidole nayi kuka saboda Lamarin "yarinyar nan ya'isheni, ni basan ya "akai "ya auri wannan "yarin ba wlh,</p><p><br /></p><p>itakam baba Lami hakuri kawai take bata, sannan tace "ah Haj aure kam ke kikace dole sai maigida Na ya aure ta,</p><p>Mama ta face majina da gefen zaninta" tace toh" dole Kuma yarabuda itaba, domin ni wlh bazan iyaba, haka kawai bakin Cikin Dana bai kasheni basai Na wata yar banza "aizan kirasa nafada masa yara bani da wannan marar tarbiyya "yarinyar,</p><p><br /></p><p>***************</p><p>Da misalin 9:00pm suna zaune Humeeh itada Umma fira suke kadan kadan sai Humeeh ta fahimci kamar wani abu nadamun Ummanta, don haka sai ta kalleta tace Umma tunda nadawo daga islamiyya sainaga kamar wani abuna damunki KO"?</p><p><br /></p><p>Umma tace Hmmm tabbas Ko" akwai abunda yake damuna, nan dai Umma tafada mata abuda yafaru ta karashe maganar ta dacewa saboda haka kirabu mata da miji tunda ba "shi kadai bane dan namiji a duniya atoh" nibana San tashin hankali kinji KO?</p><p><br /></p><p>Kai kawa Humeeh ta gyada domin kuwa takasa cewa komai asalima tunda Umma tafara magana kirjinta ke bugawa, aranta ko" fadi take Allah yasa ba "Abdul-jabbar dinta Umma ke magana akai ba,</p><p><br /></p><p>Umma tace waiko kinji abunda nace kuwa? "eh Umma najiki saidai Ina ganin ba "Abdul-jabbar din'na bane shi "Abdul-jabbar din'na bayada mata bai taba aure bafa shi,</p><p><br /></p><p>Harara Umma ta watsa mata tace "au shi "Abdul-jabbar din'ne naki da yaushi yazama Naki ban saniba? Ciki Dan jin kunya Humeeh ta sunku yarda Kai kasa,</p><p>Umma ta cigaba dacewa ke kinsa waye namiji kuwa? idan yanada mata zaya fada miki ne KO"Kuma idan zaiyi auren sa yafada miki?</p><p><br /></p><p>tabbas wannan "yarinyar datazo gidan matar "sace Kuma abuda tafada lallai zata iya aikata shi don banga alamar digon mutunci a idanun "taba saboda haka idan Zaki rabu "mata da "mijinta toh" Kira budashi" idan Kuma bazaki rabuda "shiba toh" bismillah tana kaiwa nan, tashi ta shige daki tabar Humeeh zaune kamar anshu kata agurin,</p><p><br /></p><p>Itakam Humeeh ido ta rintse sosai Ahankali tafurta Allah katadani daga wannan mummunan mafarkin tsawon wani lokaci sannan tabude idanun tana nan inda take zaune hakane yasa tagane tabbas ba mafarki takeba,</p><p><br /></p><p>Ahankali tace haba my special meyasa zakai Mani haka? can Kuma saita mike kamar wadda aka tsikarama allura, daki tashiga Umma Na kallon ta wayar ta dauko tafito waje ta kunna wayar tayi kasan cewar tundazu daza taje islamiyya take kashita number Abdul-jabbar tayi dialing</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Shikam Abdul-jabbar suna zaune shida Dalter boy suna fira saiyaga calling din Mama, yana dauka saiji yai tafashe masada kuka da sauri ya mike tareda cewa ya Salam, Mama meyasa meki kike kuka Allah yasa bani ne sanadin zubar hawayen kiba?</p><p><br /></p><p>Cikin sheshekar kuka tace toh" idan ba "Kai bane sanadi toh" waye? da </p><p> sauri yace oh kaicho na ni Abdul-jabbar shikenan nikuma zamana kenan sa mahaifinyata kuka? lallai kam banji dadin rayuwa ta ba,</p><p>kiyi hakuri Mama kifada Mani abuda nakeyi Wanda yasaki kike kuka nikuma insha'Allahu daga yau Na daina kinji?</p><p><br /></p><p>tace toh" sonake kasaki "Lariya, idanu ya ritse aransa kuma fadi yake Allah kasa mafarkin dana keyine kullum yau zaya zama gaskiya,</p><p><br /></p><p>Daga can Mama taca kajina kuwa? Dasauri yace "eh Mama meki kace?</p><p>tace cewa nai ka Saki Lariya, wani irin sanyine yaji yakwarara Cikin zuciyar sai, Amma don ya tabbatar da cewa da gaske takeyi, saiyai gyaran murya tareda daure fuska kamar yana gabanta yace haba Mama yazakice nasaki "Lariya matata cefa kuma kinsa muna San juna, tace "au abuda zakace Mani kenan KO saboda baka san irin rashin mutunci datake mun bako? toh" wlh idan baka sake taba toh" saidai kanemi wata Uwar Amma bani ba,</p><p><br /></p><p>DA sauri yace yi Hakuri Mamata "ai duk duniya nan ba wata Uwa dazanje nema bayan ke, indai "Lariya ce yanzu nan Zan saketa bama sai anjima ba Mama ina "Lariyan take? tace barina kirata Yanajin Mama tana kwalawa "Lariya kira "yajin Lariya na cewa Malama Lafiya ki ke mani irin wannan kira haka saikace kin warke makanta?</p><p><br /></p><p>itadai Mama ba tace komai ba saida kawai tamika mata Waya, "Lariya ta yamutsa fuska tace meye zanyi da waya,? Mama tace anason ayi magana dake takar ba tareda cewa waye? Cikin daka tsawa Abdul-jabbar Yace Uban ki ne Ashe bakida mutunci Maman tawa kike fadawa magana haka? </p><p><br /></p><p>toh" dama ita ce tasana aure ki" yanzu Kuma tace nasake ki saboda haka ki tattara komatsan kije nasakeki Saki biyu, tsaki tayi mtsww tace toh" donka sakeni saime? Dariya yayi yace sai narabuda jaraba, tsaki mtsww tasakeyi tareda jefawa Mama wayar ta akan ciya tace don kinsa yasake ni toh saime? Mama tace Saina rabuda bakar kadara, tafeta fuuuuu daga falon</p><p>Mama tace Allah yaraka taki gona,</p><p><br /></p><p>baba Lami dake zaune tana sauraren duk abunda ake, batace komai ba sai yanzu tace Hmmm nidama nasan DA SANNU Allah zaya baiyana gaskiya, asauka lafiya dama shi duk abunda akayisa badan Allah ba toh" dama karshan sa kenan,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sauri Mama tadauki wayar tace Kai! yace na'am Mama yanzu shikenan hankalin ki ya kwanta? tace "eh Allah yai maka Albarka ya baka abunda kake nema na' alkhairi duniya da lahira kuma Allah yadawo daku Lafiya yace Ameen Mama ta, yace taba baba Lami su gaisa itakam baba Lami hada murnata tayasa narabuwa da "Lariya sukai sallama,</p><p><br /></p><p>Shikam Abdul-jabbar jiyayi kamar ansauke masa wani katon dutse akai,</p><p>don haka yana gama Waya dasu Mama sai yai dialing din Humeeh kasan cewar yaji shigowar calling dinta lokacin dayake Waya da Mama,</p><p><br /></p><p>A abangaren Humeeh kuwa tana takiran Abdul-jabbar acemata number busy, tana KO" karin sake yin dailing dinsa kenan sai gashi calling dinsa ya shigo,</p><p><br /></p><p>Da sauri ta dauka tai sallama ya amsa tareda cewa sorry my cool naga kiranki lokaci Ina Waya da Mama ne, toh" yakike ya Umma ta? tace Lafiya lau yace gud than where is my Soyayya?</p><p>Shuru tai bata bashi amsa ba yayinda takeji sonshi yan ratsa jikinta,</p><p>A hankali tace tambayar ka" nake sanyi Kuma inasan don Allah "kafada Mani gaskiya banasan ka" boye Mani komai,</p><p><br /></p><p> Murmushi yayi har saida taji sautin sa akun'nanta ta rintsa ido, yace my cool ki tambaye ni KO" mene shi indai nasani zanfada miki gaskiya kinji?</p><p><br /></p><p>tace OK Abdul-jabbar kanada MATA? Jiyayi kirjinsa" yabuga zaune yake Amma saboda tsabar razana dajin tambayan datai masa" saida "yamike tsaye, </p><p> tace ina nufin kataba AURE NE?</p><p>gaba daya Abdul-jabbar ya daburce Cikin Karfi hali yace.....?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page81-85</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ah! Eh! Da sauri Humeeh ta katsesa da cewa just amsa my question yes or no? Saida ya tattara natsuwar sannan yace "eh nataba aure Amma! </p><p><br /></p><p>da sauri ta katse sa dacewa OK nagode kwarai DA abinda Kai Mani sai anjim, Da sauri Abdul-jabbar ya katse ta da cewa my cool ki saurareni, tace no I don't want to hearing anything from you, da sauri ta katse wayar,</p><p><br /></p><p> tabarsa yanata fadin Hello! hello!! hello!!! gaba daya Abdul-jabbar ya birkice sai fadin yake pls my cool ki saurare ni mana sai faman neman line din "ta yake Amma switch off,</p><p><br /></p><p>itakam Humaira tana katse wayar sai ta tsugun'na tareda sakin wani irin kuka Mara sauti fadi take meyasa zakai" Mani haka Kasan yadda nake sonka" kuwa? "my special Ina sonka dayawa shiyasa nake matsananci KISHIN Ka" har Ina tunanin babu wata ya mace dazata rabeka sai ni" Ashe bansani ba tuni wata mace tadade da rabarka?</p><p><br /></p><p>Wani kuka tasake Saki mai ban tausayi, daga can Umma ta kwala mata kira, da sauri ta amsa tareda mikewa tsaye tana goge hawaye, </p><p><br /></p><p>tace Umma gani' kallon ta Umma tayi tace meki keyi awaje? Ciki rawar murya tace bakomai da sauri Umma tace kuka kikeyi? tace a ah, tace hmmm yaro man kaza yanzu saboda Da namiji kike kuka? tun yanzu Zaki farasa damuwa da namiji a zuciyar ki? lallai kinada "aiki dalla wuce kitafi ki kwanta, sum-sum tawuce ta kwanta.</p><p><br /></p><p>A bangaren Abdul-jabbar kuwa abun ba'acewa komai, domin kuwa gaba daya ya birkice yatada hankalin sa" yatada Na Dalter boy" yakira Waya har yagaji Amma amsar dai guda ce wato switch off, kusan kwana yai yana abu daya, dayaga abun yanason birkita masa kwakwalwa sai kawai yaje ya dauro alwala, yafar gabatar da lafila tareda rokon All akan duk abinda yaza faru tsakanin sa da my Cool dinsa toh" Allah yasa yazo cikin sauki, yanda yaga Rana haka yaga dare,</p><p><br /></p><p>Itama Humeee hanne Ya kasance agareta yadda taga Rana haka taga dare ko kadain bata runtsa ba,don haka kids gariyawa sai ta tashi da matsananci Zazzabi mai zafi da kyar ta'iyayin sallar asuba sannan takoma ta kwanta</p><p><br /></p><p>Tunda Umma taga takoma ta" kwanta tasan cewa yau ba Lafiya tunda bata saba komawa bacci ba idan tayi sallah,</p><p> </p><p>Su Lariya kam sunzo da safe suka kwashi kayansu Amma fa "an rabu kare jini biri jini, itakam Baba Lami sai basu Hakuri takeyi, </p><p><br /></p><p>inda Haj Jumma tace Haj A'i "ai zamu hadune wlh, da suri Mama tace insha'Allahu Allah baya sake hadani dake ba daga nan duniya har lahira muguwar Aminiya kawai,</p><p><br /></p><p>Yayinda Baba Lami take fadin "ai duk abida ba'ayisa domin Allah ba toh" dama karshen sa kenan Allah dai Ya kyauta, nima nace Amin</p><p>Haka dai aka rabu bada dadi.</p><p><br /></p><p>A yau jumma@</p><p>Wanda yayi dai-dai da kwana biyu kenan da zazzabi ya kwantar da Humeeh, hankalin Umma yatashi sosai Ana cikin haka sai gaya Yah Himu yazo weekend kamar yadda yasaba,</p><p><br /></p><p>Hankalin sa yatashi sosai da yadda ya ga Humeeh, Umma ke fada masa dalili zazzabin Nata "aikam yanata fada ya Kuma ce karta sake kiransa awaya dama shi bawai ya yarda da wannan Abdul-jabbar din bane,</p><p><br /></p><p>Ana cikin wanna hali Kuma saiga notis anbasu sutashi gidan tunda wai basu biyan kudin haya, hankalisu yatashi sosai basuda gurin zuwa dole suka tattara suka koma gidan Malam mahaifin Umma, </p><p><br /></p><p>wanda bai sannan halin dasuke cikiba saida yagansu, aikam yayi fada kamar ya ari baki, musamman dayaga halin da Humeeh take ciki nadai, Umma tayi ta ba shi Hakuri har ya Hakuri amma yace tarege wanna zurfin cikin Nata,</p><p><br /></p><p>Wasa wasa saida Humeeh ta kwanta gadon Asibiti ahakadai akai tafama" har tasamu Lafiya taci gabada harko kinta" Amma fa son "Abdul-jabbar yana nan makale acikin zuciyarta,tawani bangane Kuma jin haushi sa take sosai akan abunda yai mata,</p><p><br /></p><p> Abdul-jabbar kuwa kullum yana cikin Neman line "Humeeh Amma shuru baya samu, Dalter boy yayi magana akan yayi hakuri harsu koma gida Amma yaki sauraren sa" saboda haka sai ya kyale sa,</p><p><br /></p><p>wanna shine abinda ya faru da Abdul-jabbar Da Humeeh, toh" wai Soyayyar Humaira ce ke faman wujujuwa da Abdul-jabbar kodai akwai wani abun ne? toh bari mugani,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>CIGAGAN LABARIN</p><p>------------------------------</p><p>Wurjan-jan yashi ga parlor tareda yin sallama,</p><p>Alh ya'u nakaka Dattijon kirki mai cikar kamala, ya amsa Sallama tareda kallon Dan nasa"</p><p><br /></p><p>Dayake ta faman zuba gumi kamar yahadiyi Karin kuna ma, sai duk yabashi tausayi gashi duk yarame yayi duhu, alamar dai tare suke yin jiya Da abokin'nasa,</p><p><br /></p><p>Yasamu gurin ya zauna tareda cewa sannu, Baba,"</p><p><br /></p><p>Batare daya amsa ba yace "any-anya nadabo ciwon nan Na "abokinka Ana samun cigaba kuwa?</p><p><br /></p><p>yau kimanin sati hudu kenan fa Amma ace har yanzu "Mutum baisan duniyar dayake ba, balle yasan Wanda ke kanshi ,</p><p><br /></p><p>Nifa 'ni abin'nan yaki toh" fa Zan fita da "yaron, Germany tunda suna da kwararru likitoci,</p><p><br /></p><p> domin nidai tausayi mahaifiyar sa" yakaini makura gaskiya,</p><p>DA sauri Y Y K yace...?</p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page86-90</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ansamu cigaba' </p><p><br /></p><p>Alh ya'u yace ta ina aka samu cigaba? "Mutum kashiga har kafito Amma bai sani ba,</p><p><br /></p><p>Y Y k yace daga asibiti nake yanzu shine nazo nafada maka cewa "Abdul-jabbar din ya farfado, saidai haryanzu baiyi magana ba,</p><p><br /></p><p>Sai "yanata wasu surutai alamar baya cikin hayyacinsa,</p><p> Sannan Kuma yanata kiran Mama,</p><p><br /></p><p>Shine nace toh" bari inzo nafada maka, abinda ke faruwa,</p><p>Alh yace toh" masha'allah Allah mun gode maka,</p><p><br /></p><p>Yanzu abida nakeso dakai" shine Kai" maza- maza,</p><p>Kaje kataho Mani da "Haj A'isha,</p><p>Sai Ku iskemu can asibitin kaji KO"?</p><p>Yamike tareda cewa toh" yafita dasauri,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asibiti Abdul-jabbar yana zauna ya jingina da filo, Alh ya'u yashiga dakin da sallama sa ya kalli Abdul-jabbar,</p><p><br /></p><p>Yace sannu Abdul-jabbar yaya jikin naka,Ina fata kasamu Lafiya?</p><p><br /></p><p>Bai amsa ba saidai ya zubawa Alh ya'u idanu, kamar bai taba ganin shi ba,</p><p>Ya sake tambayar sa still shuru ba amsa,</p><p><br /></p><p>Sai ga Doctor I S G yashio dakin, yace sannu Alh kaga Abdul-jabbar ya farfado ko?</p><p><br /></p><p>Alh yace kwarai nagansa", ya farfado saidai Kuma banji dadin ganinsa" hakaba gaskiya,</p><p><br /></p><p>Doctor shiyasa nace kabari nafita dashi Germany, amma kace nabarsa ,</p><p><br /></p><p>Yanzu haka zaya zauna babu magana, hakanan zayayu kuwa doctor?</p><p><br /></p><p>Doctor I S G yace a ah Alh insha'Allahu dazaran ya" warware zakaji yai magana,</p><p> sannan Kuma yana bukatar ganin "mahaifiyar sa" </p><p><br /></p><p>yace "eh natura nadabo ya daukota" docto yace OK shikenan,</p><p><br /></p><p>Alh yayi shuru yana tunanin, abinda Doctor ya fada masa tun kwankin baya dasuka wuce,</p><p><br /></p><p>Aransa yake fadin shiko "Abdul-jabbar meya keso haka, wanda yasaka shi acikin rai haryana baraza nan salwantar masa"da rayuwa?</p><p><br /></p><p>Ahankali aka turo kofa aka shigo,</p><p> Y Y K yana gaba Mama tabiya dashi abaya,</p><p><br /></p><p>Wannan shine Karo nafarko Da Mama tazo asibitin, domin KO" da'akace tazo taga jikin Abdul-jabbar din sai tace "aibasai tazoba,</p><p><br /></p><p>Tunda ga abokanan" sa nan suna zuwa, sannan Kuma ga "</p><p>Haj karima ga kuma "Baba lami kullun idan taje da safe sai dare take komawa gida,</p><p><br /></p><p>Don haka ba dole sai tajeba, saboda haka bata taba zuwaba sai yau,</p><p><br /></p><p> Mama ta tsurama dan tilon dan'nata idanu tana kallon sa,</p><p>ta firgita kwarai daganin yadda ya koma,</p><p><br /></p><p>A ranta take fadin ashe haka "yaron nan ya koma? tabbas duk abinda</p><p> yasa meshi nice sila,</p><p><br /></p><p>Domin kuwa naki fada masa" ko wane mahaifinsa", sannan nasa shi ya auri "yarinyar da bayaso,</p><p><br /></p><p>Alh ya'u nakaka' neya katse mata tunanin da takeyi", dacewa Haj A'isha matsa kusa da dan'ki,</p><p><br /></p><p>Yana bukatar ki kusa dashi, sannan Kuma "akwai abinda yakeso" Wanda muba musani ba, Amma babu mamaki ke kinsanshi,</p><p><br /></p><p>Tunda kinzo don haka matsa gareshi KO" yaji sanyi aranshi,</p><p><br /></p><p>Batayi musu ba ahankali ta matsa kusada gadon dayake, sai kallon ta yake kamar bai taba ganin taba,</p><p>ita din'ma shita ke kallon,</p><p><br /></p><p>A hankali ta zauna a gefen gadon tace sannu ya jinkin ka?,</p><p>Haryanzu kallon ta yake batare Da yace komai ba,</p><p><br /></p><p>Ta Kuma cewa meka keso yanzu? nan'ma babu amsa saidai hawaye daya wanke masa fuska,</p><p><br /></p><p>Jitayi ga banta yafadi aranta Kuma fadin take tabdijam, lallai abu yayi abu tunda harya keyin kuka, domin ba karamin abu ne kesashi" kuka ba,</p><p><br /></p><p>A hankali ya matso kusada ita ya kwantar da kansa akan ciyarta, hakanan taji ta tsinci kanta da Dora hannun ta saman kamshi, ahankali tafara shafa masa" cukur kudeddan sumanshi irin Na fulanin asali,</p><p><br /></p><p>Tace Na tambaye ka' meka keso? baka bani amsa ba,</p><p>Koda yake nasan abinda ka keso, tana' maganar ne Amma idanun ta Na zubar da hawaye,</p><p><br /></p><p>ta cigaba da cewa nasan kana" san kasan wanene mahaifinka KO?</p><p><br /></p><p>Sannan kana san kasa dalilin da ya rabu dashi KO?</p><p>toh" zanfada maka komai,</p><p><br /></p><p>Amma kafin nan inasan kayafe abinda nai maka,nasaka' dole ka aurin "Lariya wanda nidai basan ya akai haka tafaru Dani ba,</p><p><br /></p><p> Nasan Na kunta tamaka' a rayuwa saboda kayi hakuri, Na Kuma gode da biyayyar da Kai mun, </p><p>Ina rokon Allah kaima yabaka mai yi maka biyayya fiye da yadda Kai Mani </p><p><br /></p><p>A yau zanfada maka KO" wanene mahaifinka' sannan Kuma zanfada maka dalilin daya rabani dashi, </p><p>A hankali tace....?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>don Allah kuyi hakuri DA wannan </p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page91-95</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Assalamu'alaikum, friends dan Allah kuyi hakuri narashin gani post din Na akan lokacin abubuwan ne sai Ahankali nagode* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asalinmu mutanan" Adamawa ne kamar yadda kasani sunana A'ishatu, Amma ana kirana lndo, mahaifina Kuma sunan sa Ibrahim amma ana kiransa Malam lro,</p><p>mukuma bappa muke kiranshi,</p><p>ita Kuma mahaifiya ta sunan ta Hajara Amma hajjo ake kiranta mukuma Inna muke kiranta,</p><p><br /></p><p>Mu biyu iyayan mu suka haifa nida kanina Mahmud amma mado muke kiransa,</p><p><br /></p><p>Mu fulanine gaba da baya masu zama a wannan ruggar zuwa waccan ruggar, a takai ce dai mu fulanin tashine,</p><p><br /></p><p>Amma dai asalin ruggar mu idan muke zaune shine Husirin bombe,</p><p>nakance yar fari a gurin Inna ta' don haka take nuna Mani kunya Da kawaici irin tamu ta Fulani, saboda haka ban faye sakin jikina da ita ba domin bata bani damar yin haka ba,</p><p><br /></p><p>Idan ma kaga "tasaki jiki Dani toh" sai idan bappa" da Mado basanan, kamar wata rana basanan su tafi kiwo kasan cewar bappa" baya barina, natafi kiwo,</p><p>saidai yace Na zauna Na taya Inna "aikin gida kamar su tatsar nonon shanu, da Kuma dafa madara, da dai sauran aika-aikacen gida Wanda baza'a rasaba sai shi' kuma bappa da Mado su tafi kiwo,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A wannan lokacin kuwa munkai kimanin wata goma, rabanmu da ruggar mu, muna zaune nida Inna' Ina tankadan Karin tuwo ita Kuma tana kada zaren kadi (audiga),</p><p><br /></p><p>Saina kalleta tareda jefa mata tambaya kamar haka, Inna meyasa bamu zama a ruggar mu saidai muje mudawo?</p><p>sai tace "aidaga bappan' kune yafi gaye ma haka shiyasa,</p><p> saina Kuma cewa Inna kice ma bappan" idan muka koma kawai muyi Zan,mu a ruggar mu, karmu Kuma zuwa KO" wacce rugga,</p><p><br /></p><p>Harara Na tayi tareda cewa toh" Sannu uwata sai kisani dole nafada masa", tunda duk maganar Dana kemasa' bata isaba sataki daki ka kawo yanzu kam "ai zaiji sosai KO"? </p><p> Kin wani tasani agaba da tambaya sai kace wata tsarar ki KO"? da sauri Na kalleta sai naga ta tsuke fuska tareda harara ta, </p><p><br /></p><p>toh" daganan nafahimci cewa firata tafara isarta, dama baka safai take zama Dani muke firar ba,</p><p>wani lokaci sai su bappa"da mado" basan nan KO" Kuma idan naganta cikin nishadi,</p><p><br /></p><p> toh" inda muke batawa da ita shine gurin tambaya, domin kuwa haka nake da dankaran tambaya kamar yar jarida, toh" ita kuma bata san yawan tambaya don haka dagan nan firar ke tsayawa domin kuwa tashi taka tabarni agurin, kamar lokacin danai mata wannan tambayar tashi tayi ta barni agurin,</p><p><br /></p><p>Bin bayanta da kallo nai har saida tashiga daki sannan nayi ajiyar zuciya, domin kuwa mamakin Inna' take bani araina nace oni indo, wai Danna kasance yar' fari shikenan Kuma banida yanci daza "azauna Dani ayi fira?</p><p><br /></p><p>Ina Cikin wanna tunani sai ga bappa shida mado sun dawo kiwo, nayi musu sannu da wowa tareda karban sandar hannun bappa Na agiye,</p><p> yace Sannu Da gida nace yauwa,</p><p><br /></p><p>tareda kawo masa ruwa atulo mai sanyi, ya karba yana cewa "an gaisheki' yace Ina ita lnnar tatu take bangan taba? nace tana daki, muna cikin magana saigata tafita tanayi masu Sannu, ya amsa tasamu guri ta zauna sai suka fara fira har aka kira sallar magriba,</p><p>bappa yai alwala shida mado suka tafi mallaci, nikuma mukai tama nida Inna,</p><p><br /></p><p>*********</p><p>Bayan sati biyu da misalin karfe biyar Na yammacin ran alhamis, lokaci har mungama girkin dare nida inna bayan naci abinci sai nafita waje, Dan nisada bukkar mu kadan ta gefen wata bishiya na daura lilo,</p><p><br /></p><p>Tunani ruggar mu kawai nakeyi Da Kuma kawayena, gaskiya a lokacin Na matsu mukoma ruggar mu,</p><p><br /></p><p>Can nahango mado yana daga mani hannun yana dariya, nima nayi dariya tareda saukowa daga kan lilon,</p><p><br /></p><p>A hanya muka hadu muka Kuma yiwa juna dariya, na ce har kundawo kiwon? yace tundazu muka dawo bappa yana Kiranki, nace lafiya dai KO"? yace lafiya lau,</p><p><br /></p><p>Muka jera muna tafiya muna fira sai Mado ya kalleni yace Adda Albishiri ki?, (kasan cewar haka yake kirana wato yaya kenan da fullanci), nayi murmushi tareda cewa goro madona Kuma fari tas- tas,</p><p><br /></p><p> Yace kinsan abokina nan Na bappa dayake bamu labarin raban dasuga juna tun suna kana nan?</p><p><br /></p><p>Nace "eh bansan shiba Amma Kuma ban manta DA labarin sa ba,</p><p>Mado yace toh" yau mungan shi agurin kiwo, Kuma bappa yace masa" yadubi hanyar mu yau din nan zamu kawo masa ziyara,</p><p><br /></p><p>Nace ahaba dai? yace aradun, a dai- dai lokacin da muka karasa bukkar mu, muka isko bappa yana yiwa Inna bayani harnaji yana fadin sunan ruggar wato yolde kohe,</p><p><br /></p><p>bayan na gaida bappa sai Na kalli Inna nace, nace Inna wata rugace yolde kohe Amma dai bamu taba zuwa can bako?</p><p>batare da takalle niba tace nima ban saniba, amma idan ki kayi hakuri "ai can zamu tafi yanzu KO?</p><p><br /></p><p>Dajin haka Sai naja bakina natsuke munshirya tsaf, muka fito zamu tafi sai bappa yace yana zuwa mujirasa kadan,</p><p><br /></p><p>can sa gashi' yadawo yana cewa nafada wa "Malam jauro zamuje ruggar yolde kohe, yajimani motsin shanu tunda bazamu dawo yauba sai gobe,</p><p><br /></p><p>"Malam jauro magocin mune, tunda muka sauka agurin sa" mike daukar karatun kasan cewar sa Malamin makaranta kallo,</p><p><br /></p><p>haka muka Kama hanya da yamma nan, domin kuwa a lokacin rana tayija ta tafi yamma zatafadi, kunsan Fulani basuda tsoron dare, haka nan muka cigaba da tafiya, su bappa" suna gaba mu Kuma muna binsu abaya</p><p>munyi tafiya sosai,</p><p><br /></p><p>Ta! ta!! ta!!! haka naji karan abu da sauri Na waiga bayana "aiko nai arangama dawani katon Mutum", bakikirin dashi' hannun shi yana rikeda wani abu, Wanda koba afada maniba nasan bindiga ce"</p><p><br /></p><p>gabana yafadi tsoro yakamani domin kuwa ban taba ganin Mutum irin shiba, "azato nama KO" aljani ne</p><p><br /></p><p>Sai naji yai magana Cikin kakkausar murya, yana cewa duk Wanda ya motsi koyai yankurin gudu saina harbemashi Kai, Cikin firgici muka cukuikuye juna nida Mado, bappa Kuma yayi tsaye yayinda Inna ta boye bayan bappa, daga bayan mu Kuma mukaji wata murya mai Kama da irin wancan yace komotsai Mutum yai ka harbeshi,</p><p><br /></p><p> Muka Kuma rike juna nida mado, ashe su biyu ne </p><p>Kuma kowan'ne hannun sa da bindiga, gudan yace kudi zaku bamu KO" muka she ku' yanzun nan,</p><p>bamusu bappa yafito da kudi Cikin aljihunsa ya mika masu da sauri gudan ya warce kudin yasa aljihun wandon,</p><p> </p><p>Sannan ya kalli Inna yace ke Kuma fa? bamu kudi, Da sauri bappa yace "aisune duk Na baku' tsawa mutumin' ya bugawa bappa yace yimana shuru makaryaci</p><p><br /></p><p> keh! bamu kudi ? Jikinta yanarawa tace handin boni bani da kudi, yadaka mata tsawa tareda cewa karya kikeyi kina dasu, Cikin tsoro tace "aradu banidas,</p><p><br /></p><p>Bai bari "taka rasaba yana karanta harbi agoshi, aikon take tafada kasa,</p><p>Cikin matsananci firgici muka saki juna nida Mado, muka nufi inda take kwance da sauri gudan yarike Mado,</p><p><br /></p><p> ni' kuma na karasa inda Inna take bappa Na kiran ta nima Ina kiran sunan ta'amma bata amsa kiranan kowa daga Cikin muba', da'alama ta amsa kiran Ubangijinmu,</p><p><br /></p><p>Kuka nasaki domin kuwa tuni jini ya wanke mata' fuska, da sauri bappa ya dauki sandarsa yarafkawa dayan, ya Kuma rafka masa take yafadi sumamme,</p><p> </p><p>Da gudan yaga haka saiya harbi bappa akafa, tuni bappa yafadi hannun sa rike da kafarsa dake zubar jini,</p><p><br /></p><p>wani sabon kuka Na Kuma Saki, domin kuwa naga wayan nan mutanan suna kikarin nakasa mana rayuwa, shiko Mado yanata ihu mutumin nan yasake shi amma yaki yasake shi,</p><p>don haka sai Mado ya Kama hannun mutumin ya gantsara masa cizo, da sauri yasake shi da gudu "yataho muka hadu muka rungume Inna muna kuka hada bappa,</p><p><br /></p><p>Domin kuwa mungane cewa Inna tarigamu gida gaskiya, da sauri mutumin yabiyo Mado zai Kuma rikesa Ciki zafin nama bappa ya dauki sandarsa ya rafka masa akafa,</p><p>yafadi tareda rike sandar da hannun suka fara komawa da bappa, Ciki fullanci bappa yace mu tashi mugudu</p><p>da sauri na kalleshi nace bappa Ina zamu tafi? tsawa yadaka mani yace nace kutafi KO?</p><p><br /></p><p>Zumbur Na mike nafinciki hannun Mado nukanufi Cikin duhun daji da gudu,</p><p>gudu muke ba tsayawa munyi gudu sosai sannan muka tsaya agefen wata bishiya mai yawan ganye,</p><p><br /></p><p>muka hada Kai nida Mado muna kuka sosai ba me lallashin wani, saida mukai mai isarmu tukun sannan mukai</p><p>shuru, can sainaji tsoro yaka mani tunani nafara yi kar wani Abu yasame mu Cikin dajin nan,</p><p><br /></p><p>Don haka sai Na Kuma Jan hannun Mado" muka koma gurin su bappa, atunanina zamu iskosu koda muka isa gurin bamu iske kowaba , "aiko basan lokacin da Na Dora hannu akai Na kurma ihu kiran sunan "bappa da "Inna, shima Mado' kukan yakeyi haka mukayi tsaye agurin muna tafan kuka, ga garin sai duhu yake karayi don haka sai Na Kuma fincikar hannun Mado,</p><p><br /></p><p>Muka nausa Cikin dajin dagudu, gudu mukeyi batare da mun San ida muka dosaba Cikin ikon Allah sai gamu abaki titi,</p><p>nakali gabas da yamma kudu da arewa ba alamar mota KO" mashi balls keke,</p><p>Mukai tsaye Ciki jiran tsammani domin kuwa bamu Santa Ina mota KO mashin zaya bullo ba,</p><p><br /></p><p>Can sai muka hango hasken fitilla mota daga gabas tanufo Inda muke tsaye, sai Kuma muka ga ta tsaya sai hasken fitillar ya dauke alamar ankashe,</p><p>sai Kuma mukaji shuru Na tsawan lokaci ba "akaraso inda muke ba, ni Kuma ganin haka sai naja a hannun Mado muka nufi gurin motar dagudu,</p><p><br /></p><p> saida mukai gudu sosai sannan muka iske motar ashe ma akori kurace, bamu tsaya bata lokaci ba muka hau motar daba musan ida tadosa ba, mudai burin mu mubar wannan dajin, saida muka shiga muka zauna sannan ne muka fahimci ashe rake tadauko,</p><p><br /></p><p>can sai mukaji anfisgi motar da karfi da sauri muka rike juna, Cikin tsoro domin kuwa ba mutaba shiga mota ba sai a wannan lokaci,</p><p> Bansan KO" awa Nawa muka dauka muna tafiya ba, saidai kam mun dauki lokaci mai tsawo muna tafiya,</p><p><br /></p><p>Can saigamu aciki birni muna tabaza idanu muna kalle- kalle, ahaka yashiga wata anguwa ya tsaya DA alama salla zayayi tunda munga mutane natayin alwala,</p><p><br /></p><p>Sai bayan daya shiga masallaci ne sannan muka sauko daga motar, naja hannun Mado muka Fara tafiya ba tareda munsan inda zamu ba,</p><p><br /></p><p>Tafiya mukeyi batareda mun hadu dako dabba ba balle ba bil'adamu, tsit gurin bakajin motsin komai sai Na tafiyar mu, sai KO"bukun zuciyoyin mu domin kuwa tsoro yafara kama mu'</p><p><br /></p><p>Ko"Kuma nace yakama mu' har,madai ni domin kuwa Allah yayini Da matsananci tsoro,</p><p><br /></p><p>Saboda haka sai nakara sauri tareda Kuma damke hannun Mado, muka cigaba da tafiya har muka isa wata anguwa wanda tafi inda muka baro kyau,</p><p><br /></p><p>Domin kuwa manya- manyan gidajene masu dauke da manyan kofofi, sai Kuma manya- manyan fitilu dasuka haske anguwar, saika rantse DA Allah badare bane rana ce,</p><p><br /></p><p>A kofar wasu gidaje masu kamada tagwaye kuma tsaya, domin kuwa komai nasu irin guda ne, hatta da fantin kofar irin guda ne wato kore, kowani kofar da karami da babba,</p><p><br /></p><p>abakin karamar kofar muka zauna, kuka ne ya kwace wa Mama saida tayi mai isarta sannan taci gaba da cewa...?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞Lufhat ce💐</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page91-95</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Assalamu'alaikum, friends dan Allah kuyi hakuri narashin gani post din Na akan lokacin abubuwan ne sai Ahankali nagode* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asalinmu mutanan" Adamawa ne kamar yadda kasani sunana A'ishatu, Amma ana kirana lndo, mahaifina Kuma sunan sa Ibrahim amma ana kiransa Malam lro,</p><p>mukuma bappa muke kiranshi,</p><p>ita Kuma mahaifiya ta sunan ta Hajara Amma hajjo ake kiranta mukuma Inna muke kiranta,</p><p><br /></p><p>Mu biyu iyayan mu suka haifa nida kanina Mahmud amma mado muke kiransa,</p><p><br /></p><p>Mu fulanine gaba da baya masu zama a wannan ruggar zuwa waccan ruggar, a takai ce dai mu fulanin tashine,</p><p><br /></p><p>Amma dai asalin ruggar mu idan muke zaune shine Husirin bombe,</p><p>nakance yar fari a gurin Inna ta' don haka take nuna Mani kunya Da kawaici irin tamu ta Fulani, saboda haka ban faye sakin jikina da ita ba domin bata bani damar yin haka ba,</p><p><br /></p><p>Idan ma kaga "tasaki jiki Dani toh" sai idan bappa" da Mado basanan, kamar wata rana basanan su tafi kiwo kasan cewar bappa" baya barina, natafi kiwo,</p><p>saidai yace Na zauna Na taya Inna "aikin gida kamar su tatsar nonon shanu, da Kuma dafa madara, da dai sauran aika-aikacen gida Wanda baza'a rasaba sai shi' kuma bappa da Mado su tafi kiwo,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A wannan lokacin kuwa munkai kimanin wata goma, rabanmu da ruggar mu, muna zaune nida Inna' Ina tankadan Karin tuwo ita Kuma tana kada zaren kadi (audiga),</p><p><br /></p><p>Saina kalleta tareda jefa mata tambaya kamar haka, Inna meyasa bamu zama a ruggar mu saidai muje mudawo?</p><p>sai tace "aidaga bappan' kune yafi gaye ma haka shiyasa,</p><p> saina Kuma cewa Inna kice ma bappan" idan muka koma kawai muyi Zan,mu a ruggar mu, karmu Kuma zuwa KO" wacce rugga,</p><p><br /></p><p>Harara Na tayi tareda cewa toh" Sannu uwata sai kisani dole nafada masa", tunda duk maganar Dana kemasa' bata isaba sataki daki ka kawo yanzu kam "ai zaiji sosai KO"? </p><p> Kin wani tasani agaba da tambaya sai kace wata tsarar ki KO"? da sauri Na kalleta sai naga ta tsuke fuska tareda harara ta, </p><p><br /></p><p>toh" daganan nafahimci cewa firata tafara isarta, dama baka safai take zama Dani muke firar ba,</p><p>wani lokaci sai su bappa"da mado" basan nan KO" Kuma idan naganta cikin nishadi,</p><p><br /></p><p> toh" inda muke batawa da ita shine gurin tambaya, domin kuwa haka nake da dankaran tambaya kamar yar jarida, toh" ita kuma bata san yawan tambaya don haka dagan nan firar ke tsayawa domin kuwa tashi taka tabarni agurin, kamar lokacin danai mata wannan tambayar tashi tayi ta barni agurin,</p><p><br /></p><p>Bin bayanta da kallo nai har saida tashiga daki sannan nayi ajiyar zuciya, domin kuwa mamakin Inna' take bani araina nace oni indo, wai Danna kasance yar' fari shikenan Kuma banida yanci daza "azauna Dani ayi fira?</p><p><br /></p><p>Ina Cikin wanna tunani sai ga bappa shida mado sun dawo kiwo, nayi musu sannu da wowa tareda karban sandar hannun bappa Na agiye,</p><p> yace Sannu Da gida nace yauwa,</p><p><br /></p><p>tareda kawo masa ruwa atulo mai sanyi, ya karba yana cewa "an gaisheki' yace Ina ita lnnar tatu take bangan taba? nace tana daki, muna cikin magana saigata tafita tanayi masu Sannu, ya amsa tasamu guri ta zauna sai suka fara fira har aka kira sallar magriba,</p><p>bappa yai alwala shida mado suka tafi mallaci, nikuma mukai tama nida Inna,</p><p><br /></p><p>*********</p><p>Bayan sati biyu da misalin karfe biyar Na yammacin ran alhamis, lokaci har mungama girkin dare nida inna bayan naci abinci sai nafita waje, Dan nisada bukkar mu kadan ta gefen wata bishiya na daura lilo,</p><p><br /></p><p>Tunani ruggar mu kawai nakeyi Da Kuma kawayena, gaskiya a lokacin Na matsu mukoma ruggar mu,</p><p><br /></p><p>Can nahango mado yana daga mani hannun yana dariya, nima nayi dariya tareda saukowa daga kan lilon,</p><p><br /></p><p>A hanya muka hadu muka Kuma yiwa juna dariya, na ce har kundawo kiwon? yace tundazu muka dawo bappa yana Kiranki, nace lafiya dai KO"? yace lafiya lau,</p><p><br /></p><p>Muka jera muna tafiya muna fira sai Mado ya kalleni yace Adda Albishiri ki?, (kasan cewar haka yake kirana wato yaya kenan da fullanci), nayi murmushi tareda cewa goro madona Kuma fari tas- tas,</p><p><br /></p><p> Yace kinsan abokina nan Na bappa dayake bamu labarin raban dasuga juna tun suna kana nan?</p><p><br /></p><p>Nace "eh bansan shiba Amma Kuma ban manta DA labarin sa ba,</p><p>Mado yace toh" yau mungan shi agurin kiwo, Kuma bappa yace masa" yadubi hanyar mu yau din nan zamu kawo masa ziyara,</p><p><br /></p><p>Nace ahaba dai? yace aradun, a dai- dai lokacin da muka karasa bukkar mu, muka isko bappa yana yiwa Inna bayani harnaji yana fadin sunan ruggar wato yolde kohe,</p><p><br /></p><p>bayan na gaida bappa sai Na kalli Inna nace, nace Inna wata rugace yolde kohe Amma dai bamu taba zuwa can bako?</p><p>batare da takalle niba tace nima ban saniba, amma idan ki kayi hakuri "ai can zamu tafi yanzu KO?</p><p><br /></p><p>Dajin haka Sai naja bakina natsuke munshirya tsaf, muka fito zamu tafi sai bappa yace yana zuwa mujirasa kadan,</p><p><br /></p><p>can sa gashi' yadawo yana cewa nafada wa "Malam jauro zamuje ruggar yolde kohe, yajimani motsin shanu tunda bazamu dawo yauba sai gobe,</p><p><br /></p><p>"Malam jauro magocin mune, tunda muka sauka agurin sa" mike daukar karatun kasan cewar sa Malamin makaranta kallo,</p><p><br /></p><p>haka muka Kama hanya da yamma nan, domin kuwa a lokacin rana tayija ta tafi yamma zatafadi, kunsan Fulani basuda tsoron dare, haka nan muka cigaba da tafiya, su bappa" suna gaba mu Kuma muna binsu abaya</p><p>munyi tafiya sosai,</p><p><br /></p><p>Ta! ta!! ta!!! haka naji karan abu da sauri Na waiga bayana "aiko nai arangama dawani katon Mutum", bakikirin dashi' hannun shi yana rikeda wani abu, Wanda koba afada maniba nasan bindiga ce"</p><p><br /></p><p>gabana yafadi tsoro yakamani domin kuwa ban taba ganin Mutum irin shiba, "azato nama KO" aljani ne</p><p><br /></p><p>Sai naji yai magana Cikin kakkausar murya, yana cewa duk Wanda ya motsi koyai yankurin gudu saina harbemashi Kai, Cikin firgici muka cukuikuye juna nida Mado, bappa Kuma yayi tsaye yayinda Inna ta boye bayan bappa, daga bayan mu Kuma mukaji wata murya mai Kama da irin wancan yace komotsai Mutum yai ka harbeshi,</p><p><br /></p><p> Muka Kuma rike juna nida mado, ashe su biyu ne </p><p>Kuma kowan'ne hannun sa da bindiga, gudan yace kudi zaku bamu KO" muka she ku' yanzun nan,</p><p>bamusu bappa yafito da kudi Cikin aljihunsa ya mika masu da sauri gudan ya warce kudin yasa aljihun wandon,</p><p> </p><p>Sannan ya kalli Inna yace ke Kuma fa? bamu kudi, Da sauri bappa yace "aisune duk Na baku' tsawa mutumin' ya bugawa bappa yace yimana shuru makaryaci</p><p><br /></p><p> keh! bamu kudi ? Jikinta yanarawa tace handin boni bani da kudi, yadaka mata tsawa tareda cewa karya kikeyi kina dasu, Cikin tsoro tace "aradu banidas,</p><p><br /></p><p>Bai bari "taka rasaba yana karanta harbi agoshi, aikon take tafada kasa,</p><p>Cikin matsananci firgici muka saki juna nida Mado, muka nufi inda take kwance da sauri gudan yarike Mado,</p><p><br /></p><p> ni' kuma na karasa inda Inna take bappa Na kiran ta nima Ina kiran sunan ta'amma bata amsa kiranan kowa daga Cikin muba', da'alama ta amsa kiran Ubangijinmu,</p><p><br /></p><p>Kuka nasaki domin kuwa tuni jini ya wanke mata' fuska, da sauri bappa ya dauki sandarsa yarafkawa dayan, ya Kuma rafka masa take yafadi sumamme,</p><p> </p><p>Da gudan yaga haka saiya harbi bappa akafa, tuni bappa yafadi hannun sa rike da kafarsa dake zubar jini,</p><p><br /></p><p>wani sabon kuka Na Kuma Saki, domin kuwa naga wayan nan mutanan suna kikarin nakasa mana rayuwa, shiko Mado yanata ihu mutumin nan yasake shi amma yaki yasake shi,</p><p>don haka sai Mado ya Kama hannun mutumin ya gantsara masa cizo, da sauri yasake shi da gudu "yataho muka hadu muka rungume Inna muna kuka hada bappa,</p><p><br /></p><p>Domin kuwa mungane cewa Inna tarigamu gida gaskiya, da sauri mutumin yabiyo Mado zai Kuma rikesa Ciki zafin nama bappa ya dauki sandarsa ya rafka masa akafa,</p><p>yafadi tareda rike sandar da hannun suka fara komawa da bappa, Ciki fullanci bappa yace mu tashi mugudu</p><p>da sauri na kalleshi nace bappa Ina zamu tafi? tsawa yadaka mani yace nace kutafi KO?</p><p><br /></p><p>Zumbur Na mike nafinciki hannun Mado nukanufi Cikin duhun daji da gudu,</p><p>gudu muke ba tsayawa munyi gudu sosai sannan muka tsaya agefen wata bishiya mai yawan ganye,</p><p><br /></p><p>muka hada Kai nida Mado muna kuka sosai ba me lallashin wani, saida mukai mai isarmu tukun sannan mukai</p><p>shuru, can sainaji tsoro yaka mani tunani nafara yi kar wani Abu yasame mu Cikin dajin nan,</p><p><br /></p><p>Don haka sai Na Kuma Jan hannun Mado" muka koma gurin su bappa, atunanina zamu iskosu koda muka isa gurin bamu iske kowaba , "aiko basan lokacin da Na Dora hannu akai Na kurma ihu kiran sunan "bappa da "Inna, shima Mado' kukan yakeyi haka mukayi tsaye agurin muna tafan kuka, ga garin sai duhu yake karayi don haka sai Na Kuma fincikar hannun Mado,</p><p><br /></p><p>Muka nausa Cikin dajin dagudu, gudu mukeyi batare da mun San ida muka dosaba Cikin ikon Allah sai gamu abaki titi,</p><p>nakali gabas da yamma kudu da arewa ba alamar mota KO" mashi balls keke,</p><p>Mukai tsaye Ciki jiran tsammani domin kuwa bamu Santa Ina mota KO mashin zaya bullo ba,</p><p><br /></p><p>Can sai muka hango hasken fitilla mota daga gabas tanufo Inda muke tsaye, sai Kuma muka ga ta tsaya sai hasken fitillar ya dauke alamar ankashe,</p><p>sai Kuma mukaji shuru Na tsawan lokaci ba "akaraso inda muke ba, ni Kuma ganin haka sai naja a hannun Mado muka nufi gurin motar dagudu,</p><p><br /></p><p> saida mukai gudu sosai sannan muka iske motar ashe ma akori kurace, bamu tsaya bata lokaci ba muka hau motar daba musan ida tadosa ba, mudai burin mu mubar wannan dajin, saida muka shiga muka zauna sannan ne muka fahimci ashe rake tadauko,</p><p><br /></p><p>can sai mukaji anfisgi motar da karfi da sauri muka rike juna, Cikin tsoro domin kuwa ba mutaba shiga mota ba sai a wannan lokaci,</p><p> Bansan KO" awa Nawa muka dauka muna tafiya ba, saidai kam mun dauki lokaci mai tsawo muna tafiya,</p><p><br /></p><p>Can saigamu aciki birni muna tabaza idanu muna kalle- kalle, ahaka yashiga wata anguwa ya tsaya DA alama salla zayayi tunda munga mutane natayin alwala,</p><p><br /></p><p>Sai bayan daya shiga masallaci ne sannan muka sauko daga motar, naja hannun Mado muka Fara tafiya ba tareda munsan inda zamu ba,</p><p><br /></p><p>Tafiya mukeyi batareda mun hadu dako dabba ba balle ba bil'adamu, tsit gurin bakajin motsin komai sai Na tafiyar mu, sai KO"bukun zuciyoyin mu domin kuwa tsoro yafara kama mu'</p><p><br /></p><p>Ko"Kuma nace yakama mu' har,madai ni domin kuwa Allah yayini Da matsananci tsoro,</p><p><br /></p><p>Saboda haka sai nakara sauri tareda Kuma damke hannun Mado, muka cigaba da tafiya har muka isa wata anguwa wanda tafi inda muka baro kyau,</p><p><br /></p><p>Domin kuwa manya- manyan gidajene masu dauke da manyan kofofi, sai Kuma manya- manyan fitilu dasuka haske anguwar, saika rantse DA Allah badare bane rana ce,</p><p><br /></p><p>A kofar wasu gidaje masu kamada tagwaye kuma tsaya, domin kuwa komai nasu irin guda ne, hatta da fantin kofar irin guda ne wato kore, kowani kofar da karami da babba,</p><p><br /></p><p>abakin karamar kofar muka zauna, kuka ne ya kwace wa Mama saida tayi mai isarta sannan taci gaba da cewa...?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞Lufhat ce💐</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page96-100</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>Slm don Allah kuyi hakuri da rashin ganin posting din Na akan lokaci, banida Lafiya ne kwana biyu shiyasa, Amma yanzu Alhamdullah nagode,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wannan page nakane kai *DAYA*wato *ZAINUDDEEN JIBRIN ZAIN* Ina tayaka murna zagayowar ranan haihuwar ka, *ALLAH* yakara maka tsawon rai mai *ALBARKA*</p><p>*Happy* *Birthday* once again Dan 🕺🏻 *Zainunu*😜 *ALLAH* yakara shekara masu yawa muga diyanka da jikoki harda tattaba kunne, Ameee, Yeeeeee 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼Dan *YARO*</p><p>Cut the *CAKE* 🔪🎂🎂🎂😀</p><p><br /></p><p> </p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mado yace Adda inajin bacci, kallon sa nai Cikin tsananin mamaki na kalle sa wato shi har yaga gurin bacci,?</p><p><br /></p><p>Arai na kuwa fadi nake Hodijam lallai yaro yarone "inbanda abin Madon toh" mu har wani bacci zamuti yanzu, "wayanda suke Cikin wannan tashin hankali, narashin iyaye da rashin sanin takamai man inda zamu mado sa,</p><p><br /></p><p> Mado ne ya katse Mani zancen zucin danake, da yasake mai-mai tamani abinda yafada,</p><p><br /></p><p>Kallon sa nai duk sainaji yabani tausayi, domin KO" dani dashi duk munyi wurjan-wurjan, ahankali Na mike kafa-funa nace ya kwana yayi bacci, nikuma sai najingina Da kofar sai Kuma nafara tunanin, tayaya rayuwar mu zata kasance? taya kuma zamu fara rayuwar ba tareda "Inna da bappa ba? </p><p><br /></p><p>Can Kuma saina tuna " ashefa "Inna tarigamu gidan gaskiya, bansan lokacin da Na fashe Da kuka ba da sauri Na toshe bakina saboda kadana tayar da Mado daga bacci, domin naga yana jin dadin baccin,</p><p><br /></p><p>Hakana cigaba da kukana ina tunanin kila shima bappa" sun kashe sa, can wata zuciya tace toh" insun kashe sa ina gawarsu" take shida Inna"? can Kuma naji wata zuciya tace kura sun cinye,</p><p><br /></p><p>Da karfi Na Kuma sakin wani sabon kuka, nace shikenan munrasa Inna" da bappa" bamu da kowa" sai Allah, ni kadai nake ta faman surutu sai kace wata tababbiya, </p><p>Shi KO" Mado yanata bacci sa ba bu abinda ya damesa',</p><p><br /></p><p>************</p><p> Bansan rana tayiba sannan Kuma banji karar bude kofa ba, hakalizika banji karar fitowar mota ba,domin kuwa nayi matukar nisa a tunani Wanda yahana Mani rintsawa,</p><p>Saidai naji da karfi ance "ku Lafiya me kukeyi anan gurin?</p><p><br /></p><p>Nasan zakai mamakin yadda "akai mukejin hausa, tunda mu fulani ne kuma "arugga muke zama, sanna kuma bamu taba zuwa birniba maka toh" ba abin mamaki ba,</p><p><br /></p><p>Domin kuwa min koyi Hausa ne abakin wani Mutum mai suna mlm Mudi" da matarsa hassu," adalilin zaman daya kawosu ruggar mu toh" saboda haka agurin su muka koyi Hausa,</p><p><br /></p><p> Na daga Kai don naga me wannan maganar,</p><p>"aiko nai aranga da wani kyakkawan "Mutum acikin wata, zukekiyar mota baka wulik har sheki takeyi Saboda tsananin bakinta,</p><p><br /></p><p>Da sauri Na duki Mado Ina cewa tashi Kai ga aljaninan yazo yakama mu, domin KO" azatona ba Mutum bane Saboda kyawunsa ya muce tunanina,</p><p><br /></p><p>wani tunani ne yafado Mani inda Malamin mu Na makarantan allo, yataba fada mana cewa mutanan boye sunada matukar kyau, don haka saina Kama hannun Mado narike tareda yin duk wata Addu'a datazo bakina,</p><p><br /></p><p>Mado KO" dama tuni ya watseke daga baccin dayakeyi, sai mukayi tsaye tareda tsurama wannan Mutum idanu,</p><p><br /></p><p>Sai yafito daga Cikin motar yanufo inda muke tsaye, da saurin muka jada baya sai yayi tsaye Cikin murya sa mai dadi, yace nace Lafiya me kuke nema anan gurin? da sauri nace bakomai , toh" wakuke nema acikin gidan, nan na Kuma cewa bakowa,</p><p><br /></p><p>Jinai yace Peter sai gawani Mutum yafito yana KO" karin rufe kofa, sai bayan da yarufe kofar ne sannan yanufo inda muke tsaye, saiji suna wani irin yare shi ba fullanci ba shi Kuma ba Hausa ba, </p><p><br /></p><p>Domin KO" su kadai muka iya, Saboda haka sai kawai muka tsura masu idanu, tunda bamajin abinda sunke fadi, kallon mu yasake yi yace wai kudaga Ina ku" kafito? da sauri nace daga ruggar husiri bombe,</p><p><br /></p><p>Yace' "Ina kika ce? Na Kuma mai-mai tawa, sai naga yai shuru can Kuma yace toh" Ina iyayan Ku! sai nasaki kuka mai karfin gaske tareda cewa "ankashe su, da karfi yace suwane ne suka kashe su? Cikin kuka nace wasu mutane ne suka kwace kudin bappan" mu, suka harbeshi akafa sannan Kuma suka harbi Inna"</p><p><br /></p><p>Da sauri naji yace innalillahi sannan yace kubiyoni, bamu tsaya bata lokaci ba muka bisa domin KO" mungane Mutum ne ba aljaniba, Cikin wannan gidan muka shiga gidan kato ne sosai gawasu shuke- shuke Na bishiyoyi, da Kuma fulawoyi masu kamshi farfajiyar gidan Kuma, wayansu duwatsune kanana-kanana masu ban sha'awa,</p><p><br /></p><p>Munata kalle-kalle can sai idanun mu suka kallo mana, wayan su mutane manya-manya masu bakaken kaya, dakuma dogayen bindigogi a hannun su sunkai kimanin "Mutum goma sha biyar koma fiyeda haka,</p><p><br /></p><p>Gashin duk sunyi saranda fuskokin nan babu annuri ko" kadan, da alama jirasuke abasu dama sukashe mutanan gari gaba daya, </p><p><br /></p><p>Wani irin ihu nasaki mai karfi tareda rungume Mado, da sauri ya waigo inda muke yace Lafiya,? Nace mu baza mu shiga wannan gidan ba yace Saboda me? nace masu irin wannan abin'ne suka kashi mana Inna" Da bappa" Na nuna mashi, mutanan nan,</p><p><br /></p><p>Yace "aisu wayan nan bamasu kashin mutane ba ne, masu tsaron Lafiya Mutum ne, nace a ah mudai bazamu shiga ba, yayi yayi damu mu shiga nace a ah, dadai yagada gaske bazau shiga ba sainaga ya kallesu tareda irin wannan yaren nadazu, duk sai naga sunjuya baya "a lokacin guda,</p><p><br /></p><p>Sai yakalle mu yace toh" kuzo mu shiga babu abinda zasuyi maku, sai muka bishi munata waigen wayan mutanan har muka shiga ba tareda sunjuyo ba,</p><p><br /></p><p>Wani guri muka shiga mai girman sosai da kujeru manya, sannan Kuma ga wasu irin abuda aka manna ajikin bango mai dauke da sunan Allah, kasan Kuma wani abune mai taushi domin kuwa jimukai kamar kafaunmu zasunutse aciki,</p><p><br /></p><p>ga Kuma wani katon hoto "aman'ne "ajikin bango, kallo guda zakaima mutanan Cikin hoton ka tabbatar tagwayene, badon komai ba sai don tsananin kamar da sukai da juna,</p><p><br /></p><p>Ya juyo ya kallemu yace kujirani anan inazuwa,ga guri nan kuzauna mukace toh", sai yabita wata kofa yashiga cikin,</p><p><br /></p><p>Saida muka gama kalle kallon mu sannan muka nufi kujera Dani yar zama, "aimuna zama sai muka mike zumbur kamar </p><p>wayanda suka zauna akan "allura,</p><p>Nida Mado sai muka tsurama juna idanu domin KO" munga "aniyar hadiyemu, </p><p><br /></p><p>Mado yace Adda "aradun Allah idan muka zauna zata hadiye mune,</p><p>Nace eh toh" kadamu zauna,</p><p>Don haka sai mukai tsaye cirko-cieko sai kace zakarun dasuka shafada suka gaji,</p><p><br /></p><p>Can sai gashi yafito shida wata mata kyakkyawa mai cikar kamala, tana sanye da doguwar Riga baka ta Kuma lullube kanta tada mayafi baki, kasan cewar farace sai kayan sukai mata kyau, Dana kalleta' sainaga suna Kama da wannan mutumin daya shigoda mu gidan,</p><p><br /></p><p>Cikin sakin fuska ta kalle mu tace toh" baku zauna ba? Mado yace aradu "in muka zauna nan gurin yana hasiyemu, sainaga sun kalli juna sunyi murmushi, tace bazai hadiye kuba nace "a ah tayi dariya tareda cewa toh" shikenan ku zauna anan tanu banana kasa,</p><p><br /></p><p>Muka zauna sannan suma suka zauna,muna kallo bai hadiye Suba kamar yadda muka zato, araina nace kila Dan sun saba ne, ahankali tafara tambaya ta "Ina bata amsa kamar yadda naba wannan mutumin, Wanda nake kyauta ta zaton danta ne,</p><p><br /></p><p>Sai naga ta kallesa tace kasan ruggar dasuka fadi yace baisani ba,</p><p>tace yanzu idan akasaku amota zaku iyagane ruggar taku?</p><p><br /></p><p>Nace "aiba amota muje zuwaba akafa muke zuwa, KO" yanzu ma wani" mai motar rake mukabiyo yakawomu nan cikin birni Amma muba mutaba zuwaba sai yau,</p><p><br /></p><p>Sai ta girgiza kai tace ya sunan ki' nace lndo shi Kumaz Mado, tace indo A'isha kenan KO" nace "eh toh" shi kuma Mado fa? Nace Mahamud,</p><p><br /></p><p>Tace masa kaje ka Kira Mani lya Asabe yace toh", can saiga shi yadawo tareda wata yar dattijiyar mata sai matar tace Haj baki mukai, tace "eh wannan sunan ta A'isha shi Kuma sunan sa Mahamud,</p><p><br /></p><p>Don Allah Inna Asabe akaita dakin anan nakusa danawa, tayi wanka akwai kaya wadurof abata tasa sannan abaya abinci tayi karin kumallo,</p><p>ta kalli mutumin nan tace Kai Kuma kai Mahamud dakin nan Na hanyar boy's quarter, shima yai wanka akwai kaya a cikin wadurof kabashi yasa sannan yazo yai Karin kumallo,</p><p><br /></p><p>Tamike tana cewa Bari "inje nasami general kila bazaya rasa sanin ruggar tasu ba, suka amsa da toh" dukkan su" Nina bi wannan mata Da akakira Inna Asabe, shi Kuma Mado yabi wannan mutumin da bansan sunan sa ba,</p><p><br /></p><p>Gaskiya dakin ya kayatu matukar kayatuwa, "ainan nasaki baki Ina kallo dama gani yardaji Dan haka sai nakara zama yardaji sosai,</p><p><br /></p><p>Tanuna Mani bayi nashiga nai wanka nafito tabani mai nashafa, sannan tabani kaya nasaka sannan muka koma falo, anan muka isko Mado shima haryana shirya, aka bamu abinci banyan mun gama sai ga,</p><p><br /></p><p>Hajiya tafito bayanta wani mutum yana biyeda ita kyakkyawa dashi managarci, mai cikar kwarjini yasamu guri ya zauna adaya daga Cikin kujerin falon, tace</p><p>Hajiya general kaga yaran nan Kai ya girgiza Cikin tausayi mu,</p><p><br /></p><p>Sai yace gaskiya doctor bansan ruggar nan ba Amma insha'Allahu zansa abincika Mani,</p><p> dajin haka sai kawai nasaki kuka "Ina fadin shikenan mun banu, ahankaki ta karaso gurin na tace haba A'isha yace maki kunbanu,?</p><p><br /></p><p>Insha'Allahu za'a gane ruggar kinji " aiyace zaya sa "abinci ka ki ba?</p><p>Nace "eh tace toh" kidaina kuka haka nace toh" tare da share hawayan, </p><p><br /></p><p>Wasa-wasa saida mukayi satin uku agidan nan batare da angane ruggar mu ba, a lokacin Kuma idan kaganmu saika rantse da Allah bamu bane fulanin nan yan daji, mun goge munyi kyau abinbu, </p><p>Sai ranan damuka cika sati hudu sannan aka samu Wanda yadan ruggar mu, </p><p><br /></p><p>"aikam dadi kamar ya kashemu don murya, munsan dai KO" bakomai idan aka kaimu husiri bombe ruggar mu, akwai kannan bappa" da Kuma Na Inna"</p><p><br /></p><p>Don haka sai mukayi ta murna muna hada kayan mu,Wanda mu kasan anbamu Hajiya natayi mana dariya,</p><p><br /></p><p>Saida muka gama shiryawa tsaf sannan muka fito afalo muka isko Hajiya,</p><p><br /></p><p>Sai muka ajiye kayan mu muka zauna tareda tsurama Hajiya idanu, ta kallemu sai tayi dariya,</p><p><br /></p><p> tace karfe Tara darabi na dare zamubi hanyar ruggar husiri bombe? Nace "eh toh" aimu da daddare muke tafiya, sai tace...?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞Lufha ce💐</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page96-100</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>Slm don Allah kuyi hakuri da rashin ganin posting din Na akan lokaci, banida Lafiya ne kwana biyu shiyasa, Amma yanzu Alhamdullah nagode,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wannan page nakane kai *DAYA*wato *ZAINUDDEEN JIBRIN ZAIN* Ina tayaka murna zagayowar ranan haihuwar ka, *ALLAH* yakara maka tsawon rai mai *ALBARKA*</p><p>*Happy* *Birthday* once again Dan 🕺🏻 *Zainunu*😜 *ALLAH* yakara shekara masu yawa muga diyanka da jikoki harda tattaba kunne, Ameee, Yeeeeee 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼Dan *YARO*</p><p>Cut the *CAKE* 🔪🎂🎂🎂😀</p><p><br /></p><p> </p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mado yace Adda inajin bacci, kallon sa nai Cikin tsananin mamaki na kalle sa wato shi har yaga gurin bacci,?</p><p><br /></p><p>Arai na kuwa fadi nake Hodijam lallai yaro yarone "inbanda abin Madon toh" mu har wani bacci zamuti yanzu, "wayanda suke Cikin wannan tashin hankali, narashin iyaye da rashin sanin takamai man inda zamu mado sa,</p><p><br /></p><p> Mado ne ya katse Mani zancen zucin danake, da yasake mai-mai tamani abinda yafada,</p><p><br /></p><p>Kallon sa nai duk sainaji yabani tausayi, domin KO" dani dashi duk munyi wurjan-wurjan, ahankali Na mike kafa-funa nace ya kwana yayi bacci, nikuma sai najingina Da kofar sai Kuma nafara tunanin, tayaya rayuwar mu zata kasance? taya kuma zamu fara rayuwar ba tareda "Inna da bappa ba? </p><p><br /></p><p>Can Kuma saina tuna " ashefa "Inna tarigamu gidan gaskiya, bansan lokacin da Na fashe Da kuka ba da sauri Na toshe bakina saboda kadana tayar da Mado daga bacci, domin naga yana jin dadin baccin,</p><p><br /></p><p>Hakana cigaba da kukana ina tunanin kila shima bappa" sun kashe sa, can wata zuciya tace toh" insun kashe sa ina gawarsu" take shida Inna"? can Kuma naji wata zuciya tace kura sun cinye,</p><p><br /></p><p>Da karfi Na Kuma sakin wani sabon kuka, nace shikenan munrasa Inna" da bappa" bamu da kowa" sai Allah, ni kadai nake ta faman surutu sai kace wata tababbiya, </p><p>Shi KO" Mado yanata bacci sa ba bu abinda ya damesa',</p><p><br /></p><p>************</p><p> Bansan rana tayiba sannan Kuma banji karar bude kofa ba, hakalizika banji karar fitowar mota ba,domin kuwa nayi matukar nisa a tunani Wanda yahana Mani rintsawa,</p><p>Saidai naji da karfi ance "ku Lafiya me kukeyi anan gurin?</p><p><br /></p><p>Nasan zakai mamakin yadda "akai mukejin hausa, tunda mu fulani ne kuma "arugga muke zama, sanna kuma bamu taba zuwa birniba maka toh" ba abin mamaki ba,</p><p><br /></p><p>Domin kuwa min koyi Hausa ne abakin wani Mutum mai suna mlm Mudi" da matarsa hassu," adalilin zaman daya kawosu ruggar mu toh" saboda haka agurin su muka koyi Hausa,</p><p><br /></p><p> Na daga Kai don naga me wannan maganar,</p><p>"aiko nai aranga da wani kyakkawan "Mutum acikin wata, zukekiyar mota baka wulik har sheki takeyi Saboda tsananin bakinta,</p><p><br /></p><p>Da sauri Na duki Mado Ina cewa tashi Kai ga aljaninan yazo yakama mu, domin KO" azatona ba Mutum bane Saboda kyawunsa ya muce tunanina,</p><p><br /></p><p>wani tunani ne yafado Mani inda Malamin mu Na makarantan allo, yataba fada mana cewa mutanan boye sunada matukar kyau, don haka saina Kama hannun Mado narike tareda yin duk wata Addu'a datazo bakina,</p><p><br /></p><p>Mado KO" dama tuni ya watseke daga baccin dayakeyi, sai mukayi tsaye tareda tsurama wannan Mutum idanu,</p><p><br /></p><p>Sai yafito daga Cikin motar yanufo inda muke tsaye, da saurin muka jada baya sai yayi tsaye Cikin murya sa mai dadi, yace nace Lafiya me kuke nema anan gurin? da sauri nace bakomai , toh" wakuke nema acikin gidan, nan na Kuma cewa bakowa,</p><p><br /></p><p>Jinai yace Peter sai gawani Mutum yafito yana KO" karin rufe kofa, sai bayan da yarufe kofar ne sannan yanufo inda muke tsaye, saiji suna wani irin yare shi ba fullanci ba shi Kuma ba Hausa ba, </p><p><br /></p><p>Domin KO" su kadai muka iya, Saboda haka sai kawai muka tsura masu idanu, tunda bamajin abinda sunke fadi, kallon mu yasake yi yace wai kudaga Ina ku" kafito? da sauri nace daga ruggar husiri bombe,</p><p><br /></p><p>Yace' "Ina kika ce? Na Kuma mai-mai tawa, sai naga yai shuru can Kuma yace toh" Ina iyayan Ku! sai nasaki kuka mai karfin gaske tareda cewa "ankashe su, da karfi yace suwane ne suka kashe su? Cikin kuka nace wasu mutane ne suka kwace kudin bappan" mu, suka harbeshi akafa sannan Kuma suka harbi Inna"</p><p><br /></p><p>Da sauri naji yace innalillahi sannan yace kubiyoni, bamu tsaya bata lokaci ba muka bisa domin KO" mungane Mutum ne ba aljaniba, Cikin wannan gidan muka shiga gidan kato ne sosai gawasu shuke- shuke Na bishiyoyi, da Kuma fulawoyi masu kamshi farfajiyar gidan Kuma, wayansu duwatsune kanana-kanana masu ban sha'awa,</p><p><br /></p><p>Munata kalle-kalle can sai idanun mu suka kallo mana, wayan su mutane manya-manya masu bakaken kaya, dakuma dogayen bindigogi a hannun su sunkai kimanin "Mutum goma sha biyar koma fiyeda haka,</p><p><br /></p><p>Gashin duk sunyi saranda fuskokin nan babu annuri ko" kadan, da alama jirasuke abasu dama sukashe mutanan gari gaba daya, </p><p><br /></p><p>Wani irin ihu nasaki mai karfi tareda rungume Mado, da sauri ya waigo inda muke yace Lafiya,? Nace mu baza mu shiga wannan gidan ba yace Saboda me? nace masu irin wannan abin'ne suka kashi mana Inna" Da bappa" Na nuna mashi, mutanan nan,</p><p><br /></p><p>Yace "aisu wayan nan bamasu kashin mutane ba ne, masu tsaron Lafiya Mutum ne, nace a ah mudai bazamu shiga ba, yayi yayi damu mu shiga nace a ah, dadai yagada gaske bazau shiga ba sainaga ya kallesu tareda irin wannan yaren nadazu, duk sai naga sunjuya baya "a lokacin guda,</p><p><br /></p><p>Sai yakalle mu yace toh" kuzo mu shiga babu abinda zasuyi maku, sai muka bishi munata waigen wayan mutanan har muka shiga ba tareda sunjuyo ba,</p><p><br /></p><p>Wani guri muka shiga mai girman sosai da kujeru manya, sannan Kuma ga wasu irin abuda aka manna ajikin bango mai dauke da sunan Allah, kasan Kuma wani abune mai taushi domin kuwa jimukai kamar kafaunmu zasunutse aciki,</p><p><br /></p><p>ga Kuma wani katon hoto "aman'ne "ajikin bango, kallo guda zakaima mutanan Cikin hoton ka tabbatar tagwayene, badon komai ba sai don tsananin kamar da sukai da juna,</p><p><br /></p><p>Ya juyo ya kallemu yace kujirani anan inazuwa,ga guri nan kuzauna mukace toh", sai yabita wata kofa yashiga cikin,</p><p><br /></p><p>Saida muka gama kalle kallon mu sannan muka nufi kujera Dani yar zama, "aimuna zama sai muka mike zumbur kamar </p><p>wayanda suka zauna akan "allura,</p><p>Nida Mado sai muka tsurama juna idanu domin KO" munga "aniyar hadiyemu, </p><p><br /></p><p>Mado yace Adda "aradun Allah idan muka zauna zata hadiye mune,</p><p>Nace eh toh" kadamu zauna,</p><p>Don haka sai mukai tsaye cirko-cieko sai kace zakarun dasuka shafada suka gaji,</p><p><br /></p><p>Can sai gashi yafito shida wata mata kyakkyawa mai cikar kamala, tana sanye da doguwar Riga baka ta Kuma lullube kanta tada mayafi baki, kasan cewar farace sai kayan sukai mata kyau, Dana kalleta' sainaga suna Kama da wannan mutumin daya shigoda mu gidan,</p><p><br /></p><p>Cikin sakin fuska ta kalle mu tace toh" baku zauna ba? Mado yace aradu "in muka zauna nan gurin yana hasiyemu, sainaga sun kalli juna sunyi murmushi, tace bazai hadiye kuba nace "a ah tayi dariya tareda cewa toh" shikenan ku zauna anan tanu banana kasa,</p><p><br /></p><p>Muka zauna sannan suma suka zauna,muna kallo bai hadiye Suba kamar yadda muka zato, araina nace kila Dan sun saba ne, ahankali tafara tambaya ta "Ina bata amsa kamar yadda naba wannan mutumin, Wanda nake kyauta ta zaton danta ne,</p><p><br /></p><p>Sai naga ta kallesa tace kasan ruggar dasuka fadi yace baisani ba,</p><p>tace yanzu idan akasaku amota zaku iyagane ruggar taku?</p><p><br /></p><p>Nace "aiba amota muje zuwaba akafa muke zuwa, KO" yanzu ma wani" mai motar rake mukabiyo yakawomu nan cikin birni Amma muba mutaba zuwaba sai yau,</p><p><br /></p><p>Sai ta girgiza kai tace ya sunan ki' nace lndo shi Kumaz Mado, tace indo A'isha kenan KO" nace "eh toh" shi kuma Mado fa? Nace Mahamud,</p><p><br /></p><p>Tace masa kaje ka Kira Mani lya Asabe yace toh", can saiga shi yadawo tareda wata yar dattijiyar mata sai matar tace Haj baki mukai, tace "eh wannan sunan ta A'isha shi Kuma sunan sa Mahamud,</p><p><br /></p><p>Don Allah Inna Asabe akaita dakin anan nakusa danawa, tayi wanka akwai kaya wadurof abata tasa sannan abaya abinci tayi karin kumallo,</p><p>ta kalli mutumin nan tace Kai Kuma kai Mahamud dakin nan Na hanyar boy's quarter, shima yai wanka akwai kaya a cikin wadurof kabashi yasa sannan yazo yai Karin kumallo,</p><p><br /></p><p>Tamike tana cewa Bari "inje nasami general kila bazaya rasa sanin ruggar tasu ba, suka amsa da toh" dukkan su" Nina bi wannan mata Da akakira Inna Asabe, shi Kuma Mado yabi wannan mutumin da bansan sunan sa ba,</p><p><br /></p><p>Gaskiya dakin ya kayatu matukar kayatuwa, "ainan nasaki baki Ina kallo dama gani yardaji Dan haka sai nakara zama yardaji sosai,</p><p><br /></p><p>Tanuna Mani bayi nashiga nai wanka nafito tabani mai nashafa, sannan tabani kaya nasaka sannan muka koma falo, anan muka isko Mado shima haryana shirya, aka bamu abinci banyan mun gama sai ga,</p><p><br /></p><p>Hajiya tafito bayanta wani mutum yana biyeda ita kyakkyawa dashi managarci, mai cikar kwarjini yasamu guri ya zauna adaya daga Cikin kujerin falon, tace</p><p>Hajiya general kaga yaran nan Kai ya girgiza Cikin tausayi mu,</p><p><br /></p><p>Sai yace gaskiya doctor bansan ruggar nan ba Amma insha'Allahu zansa abincika Mani,</p><p> dajin haka sai kawai nasaki kuka "Ina fadin shikenan mun banu, ahankaki ta karaso gurin na tace haba A'isha yace maki kunbanu,?</p><p><br /></p><p>Insha'Allahu za'a gane ruggar kinji " aiyace zaya sa "abinci ka ki ba?</p><p>Nace "eh tace toh" kidaina kuka haka nace toh" tare da share hawayan, </p><p><br /></p><p>Wasa-wasa saida mukayi satin uku agidan nan batare da angane ruggar mu ba, a lokacin Kuma idan kaganmu saika rantse da Allah bamu bane fulanin nan yan daji, mun goge munyi kyau abinbu, </p><p>Sai ranan damuka cika sati hudu sannan aka samu Wanda yadan ruggar mu, </p><p><br /></p><p>"aikam dadi kamar ya kashemu don murya, munsan dai KO" bakomai idan aka kaimu husiri bombe ruggar mu, akwai kannan bappa" da Kuma Na Inna"</p><p><br /></p><p>Don haka sai mukayi ta murna muna hada kayan mu,Wanda mu kasan anbamu Hajiya natayi mana dariya,</p><p><br /></p><p>Saida muka gama shiryawa tsaf sannan muka fito afalo muka isko Hajiya,</p><p><br /></p><p>Sai muka ajiye kayan mu muka zauna tareda tsurama Hajiya idanu, ta kallemu sai tayi dariya,</p><p><br /></p><p> tace karfe Tara darabi na dare zamubi hanyar ruggar husiri bombe? Nace "eh toh" aimu da daddare muke tafiya, sai tace...?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞Lufha ce💐</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page101-105</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A ah nikam bazanyi tafiyar dare ba, kunga yanzu abinda nakeso daku shine Ku kwashi kayan nan Ku maidasu daki, gobe da safe Ina Allah ya kaimu sai mufi dawuri,b</p><p><br /></p><p>Kunga dama gobe Lahadi ba "aiki sai mutafi harda, Magaji domin yace Mani yana hanyar dawowa gida, tunda shima nagane yakoyi tafiyar dare irin ku,</p><p><br /></p><p>Ta kallemu tana murmushi taciga ba dacewa basai mutafi harda shi ba? Cikin zoyaya tace kodai kungaji DA Hajiyar takune, shine yasa ku kamatsu Ku tafi kubarni?</p><p>Na dukar dakai kasa tareda cewa "a ah, </p><p><br /></p><p>Tace toh" Ku mayar da kayan daki sai kuzo muyi fira, mukace toh' kowa yanufi daki don ya ajiye kayan,</p><p><br /></p><p>Ni KO" arai Na tambaya nake wanene kuma Magaji? domin inajin wani lokaci Inna Asabe Na fadin Magajin gida Amma ban taba gani shi ba,</p><p><br /></p><p>Sannan wani abin mamaki shine tun ranan da wannan "mutumin, yashiga damu wannan gidan haryau ban sake ganinsa ba,</p><p>Wata kila "Mado ya ganshi Amma nidai kam banganshi ba,</p><p><br /></p><p>Muna kallon wani film nayaki Wanda nalura Hajiya Na matukar San kallo, da idan muna kallo tsoro mukeji amma damuka saba sai muka daina jin tsoro,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Muna kallo tana dan janmu dafira muna mayar mata,</p><p>Sai "akai sallama muka amsa tareda kallon maiyin sallama,</p><p><br /></p><p>Zumbur namike tareda boyewa bayan Hajiya, Saboda tsananin tsoro domin kuwa saye yake da kaya irin na mutanan da muke kallon acikin </p><p>harda wata yar karamar bindiga "asake akugun sa,</p><p><br /></p><p>Da sauri nace SOJA kasan cewar Hajiya tafada mana sunan wayan damuke kallo acikin t.v,</p><p><br /></p><p>Murmushi yai Wanda yakara mashi kyau da kwarjini yace Na'am,</p><p>Sai Na kalli Hajiya Cikin sanyin jiki nace "au Hajiya itama SOJA takeyi? tace "eh a hankali Na zauna tareda fashewa da kuka,</p><p><br /></p><p>Da sauri Hajiya tada fani tace A'isha Lafiya meya faru? Nace itama tana kashin mutane tunda gatan da bindiga, shikenan muna zata kashe mu KO?</p><p><br /></p><p>Zama yayi dirshan yana dariya saina daina kuka Na tsaye kallon sa, yanada kyau kwarai da gaske sai Kuma dariya shi takara masa kwarjini,</p><p><br /></p><p>Dana kalli Hajiya sainaga tana murmushi, sai nace Hajiya "ai itama tana kashin mutane KO?</p><p>tace "a ah sai mace toh" me takeyi dawan nan bindiga? </p><p><br /></p><p>Saiya tsaya dayin dariya sannan yazaro yar bindigar, da saurayi Na matsa kusada Hajiya, sai ya Kuma yin dariya sannan yace kinga wannan ko ? Nace "eh yace toh" da irinta ake kashe mutanan nan dasuka tareku "ahanya,</p><p><br /></p><p>Da sauri nace yauwa irin su zakirika kashe wa tunda, din azzalumai ne masu raba yaya da iyayansu nafada kamar zanyin kuka,</p><p><br /></p><p>Hajiya tace banasan kukan nan daki keyi share hawayen nan, da sauri Na share domin Na fahimci Hajiya Na san mu ya maida bindigar "agurin zamanta</p><p><br /></p><p> Sannan ya gaida Hajiya sai nida Mado muka gaidashi, Sai naji tana tambaya sa "ina Aina'u"?,</p><p>Sainaga ya yamutsa fuska sannan yace tareda "ita muka fito tace' Na sauke ta agidan gwaggo Rakiya,</p><p>tace" tana gaidake' wai sai gobe zata zota gaida Ku,</p><p><br /></p><p>itama ta amsa fuska bafara'a tace toh" aishikenan, Amma dai kotazo gobe bazata iskoni ba,tunda asamu wanda ya san ruggar su A'isha,</p><p><br /></p><p>Yace masha'allah yanzu gobe-gobe zasu tafi, tace "eh suda sukace da yau zasu tafi ni nace su bari sai gobe, </p><p><br /></p><p>Ya kalleni' yace "au da tafiya zakuyi ba tareda muyi sallama ba? nace " a ah dama "ai Hajiya tace abari sai Magaji yadawo, sannan mutafi gobe,</p><p>gashi kaima kadawo ba sai atafi harda Kai ba</p><p><br /></p><p>Sai naga sunyi murmushi yace toh" Allah ya kaimu goben Lafiya, nace Amin, saidai tunani nakeyi araina wacece Aina'u,? kaina nake tambaya wanda nasani banida amsarta, gadai masu bani amsar nan,saidai kuma kash! bazan iya tambayar suba domin kuwa sudin mutane ne masu girma wayan da kokaso tambayar su" abu kwarjini su da haibarsu bazata barka ka tambaye su" abuba, sundan taba fira kadan sannan yai mata sallama ya tafi,</p><p><br /></p><p> *********</p><p> Washe gari da misalin karfe takwas na safiyar Lahadi, bayan mungama karya kumallo, muna tsaye afalo nida Mado muna rikeda kayan mu, Hajiya muke jira tafito,</p><p><br /></p><p> Sai gasu itada maigidan ta Wanda take kirasa Da general, suka kalli juna sukai dariya, saina gaida su shima Mado ya gaida su, suka amsa fuskarsu cike da fara'a,</p><p><br /></p><p>Cikin zolaya yace doctor "aini har "Ina cewa mun samu yaya,tayi murmushi tace wlh nima Da haka nace saidai</p><p> Kuma naga yayan, sai sauri suke sugudu subar uwartasu KO" A'isha?</p><p><br /></p><p>Nace "a ah Hajiya "aiko muntafi zamu dinga zuwa muna ganin ki ko Mado? yace " eh, ta kalli maigidanta tace kaji abinda "sukace KO? yace naji ta kuma cewa kunyi Alkawari zakudiga zuwa? nace "eh tace toh shikenan Allah yasa kutashi mutafi,</p><p><br /></p><p> Muna zaune acikin mota ni' da Hajiya da Mado muna abayan, Shi Kuma Soja (nikan soja nake kiransa tunda bansan sunan sa ba)yana zaune agurin maituki da alama shi zaya kaimu , sai kuma Mutumin dazaya rakamu akusa da Soja mai suna Malam Habu,</p><p><br /></p><p>Har Soja' zaya tada mota sainai saurin cewa Hajiya gashi har za'a tafi ita "Magaji batazo ba?</p><p><br /></p><p>Murmushi tayi tace A'isha kenan toh "ai shine' yaza jamu zuwa ruggar taku,</p><p><br /></p><p>Da sauri Na kalli Soja sai naga shima' yana kallo Na', mai hade Da murmushi yace yanzu ke' da har Zaku tafi ba tareda kinsan 'suna Na ba?</p><p> Dai-dai lokacin da maigadi" yabude mana kofa muka fito muka dauki hanya,</p><p><br /></p><p>Da sauri nace "a ah toh" aike nasan sunan ki Soja mana ko"?</p><p><br /></p><p>Yace "a ah ni basuna na Soja ba Soja sunan "aikina ne, amma ni suna Na AHMED su Hajiya ne suke kirana' Magaji, kema Zaki iya kirana Magaji KO" ki kirani Ahamed dina,</p><p><br /></p><p>Ahankali Na gukar da kaina kasa cikin jin nauyinsa' nace toh" kiyi hakuri ni bansan sunanki kenan ba,</p><p>Sannan Kuma kiyi hakuri bazan iya kiran sunan kiba,</p><p><br /></p><p>Da sauri naji yace Saboda me? Kaina' nakasa Nace shaboda sunan ki yanada girma saidai zani cigaba da kiran ki SOJA,</p><p><br /></p><p>Yace toh" shikenan Amma dai kidaina kirana mace,"aikece mace Amma ni' "aina mijine ko"? Nace toh" Hajiya itada mlm Habu sai dariya suke yimana, harda shima Sojan dariya yake,</p><p><br /></p><p>Can Kuma sai kaji motar "anyi shuru yayinda Soja yaketa sharara gudu akan titi, tum muna tafiya akan titi har mukafara tafiya cikin Dani, yayida mlm Habu yake muna masa' hanya munyi tafiya mai tsawon sosai, Wanda har saidai Hajiya tace mlm Habu' Amma dai ruggar akwai nisa? yace sosai ma kuwa, tace toh" Allah yakaimu Lafiya, yace amin. ahaka har Allah yasa muka isa ruggar husiri bombe Lafiya.</p><p><br /></p><p>bayan yai fakin sai muka firfito daga motar, kallo guda naima ruggar araina Nace ayya wannan mlm Habun yasan ruggar mu kuwa?</p><p> </p><p>Domin kuwa banga bukko kinmu ba wanda suke sunkai guda goma sha,toh" amma kuma yanzu bukka guda nagani kol,</p><p><br /></p><p>Mlm Habu ne ya katse Mani zancan zucin danake, jinai yace naga ruggar tasake mun ne amma dai bari Na tambayi mutumin can,</p><p>dayake alwala suka nufi gurin shida Soja, mu kuma sai mukatsa jiransu.</p><p><br /></p><p>Shikam Mado yakasa hakuri saida yace Adda amma dai wannan ba ruggar mu bane KO"?</p><p>Jikina asanyaye Nace Mado nan ne, bakaga "inda ku keyin gardo gardo ba kaida su jauro ba, </p><p>Yace' eh Adda nan ne toh "Inasu Kawu dasu jauro hadasu Dija kawayanki,' kum...</p><p>Yayi shuru Saboda ganin su Soja sun dawo, gabana yafadi saka makon ganin fuskokin su ba bara'a,</p><p><br /></p><p>Hajiya tace yadai mlm Habu meya faru ne? ya girgiza Kai yace wai "a tun lokacin da yanfashi suka kashe matarsa, sai yan'uwana suka dawo dashi wannan ruggar don suyi jinyarsa,</p><p><br /></p><p> Kasan cewar sun harbesa" akafa toh" bayan kwana biyu Kuma, sai suka tashi gaba daya daga wannan ruggar, Kuma mun tambaye shi KO" yasan "inda suka koma yace shi wallahi baisan "inda suka koma ba,</p><p><br /></p><p>Kuka nasaki "Ina fadin mu kam mu shiga uku shikenan banida kowa, da sauri Hajiya ta rungumeni tace "akul nasa kejin wannan Kalmar tafito daga bakin ki',</p><p><br /></p><p>Sannan Kuma kiyi maza ki gaggauta yin istigifari, domin KO" kin sabi ALLAH,</p><p>ta Kuma cewa shin ke kika halicci kanji? Nace "a ah Waya halicce ki' Nace ALLAH, tace yauwa toh" aiduk Wanda yakeda ALLAH toh" "aiyana da kowa,</p><p><br /></p><p>Saboda haka share hawayen ki' domin nagane cewa kudin amanace ALLAH ya bani, don haka nikuma zanrike amana Kuma "Ina rokon Ubangijinmu, yata yani riko, </p><p><br /></p><p>Saboda haka kwantar da hankalin ki' nizan rike Ku tamkar yayan Dana haifada da cikina, sai "a lokacin naji hankali ya kwanta,</p><p><br /></p><p>Ta' kalli Soja tace maidamu gida, yace toh" Amma Hajiya da mun tsaya munyi sallah tunda naga lokaci yayi, tace' "eh yaja mata muyi kar mutafi da ita akai, tunda bamusan lokacin da zamu isa gida ba.</p><p><br /></p><p>Bayan munyi sallah "agidan wannan mutumin sannan muka Kama hanyar komawa gida,</p><p>sai kusan sallar magrib sannan muka isa gida.</p><p><br /></p><p> Bayan munyi sallah munci abinci muna zaune afalo muna kallo, saiga general yafito ya zauna kusada Hajiya tace sannu da fitowa yace yauwa,sannan muka gaida shi ya amsa tareda cewa A'isha nace na'am yace Doctor tayi Mani bayani komai, Saboda haka Ku kwantar da hankalin Ku" Ku dauka cewa nan gidaku ne kinji KO? Nace toh"</p><p><br /></p><p>Cikin wasa yace Doctor "ashe maganta tazama gaskiya danace mun samu yaya? yakara sa maganar dayin dariya itama dariya tayi tace takam zama, yace toh" Allah yata yamu riko tace amin,</p><p><br /></p><p>***********</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu da misalin karfe goma nasafiyar litini "Ina zaune afalo nikada "Ina kallo kasan cewar Hajiya" ta tafi gurin "aiki Mado" Kuma yafita, Inna " Asabe Kuma tan kichin tana "akinta, Saboda haka sai Na kasance ni' kadai,</p><p><br /></p><p>Azahiri "inkagani zakace "eh kallo nake, toh" Amma Kuma ba kallon nakeyi ba domin kuwa nayi nisa "atunani,Wanda ba lallai bane nafahimci "abinda akeyi a" T.V</p><p><br /></p><p>Don haka banji shigo warsa ba ballan tana "insan zaman sa, saidai kawai naga mutun zaune kusada ni' KO" Kuma Nace naji kamshin turaren sa'</p><p><br /></p><p>Da sauri Na waiga Sojane ya tsura Mani idanu, nadukar DA kaina kasa Nace "Ina kwana? bai "amsa ba saidai yayi Dan guntu tsaki mtsww.... da sauri na dagoda Kai Na kallesa,</p><p><br /></p><p>Batare da ya kalleni ba yace "inacan office jikina yabani cewa kina nan kina "aikin tunani, narasa "abinda yasa haryanzu kin kasa sakin jikin ki' damu, kiduba kiga Mahamud tuni yasaki jikinsa yanata harkokin sa ba'abinda yada mesa,</p><p><br /></p><p>Yace A'isha Nace na'am, ko" har yanzu baki yarda samu bane kina ganin kamar zamu cuceku ne? da sauri Nace "a ah,</p><p><br /></p><p>Yace toh" meyasa bazaki Zaki jikin ki' kiyi harkokin ki' kamar yanda kowa yakeyi ba,? bance komai ba sai ya girgiza Kai tareda mikewa,</p><p> Yaje ya dauko wanna babban Hoton dayake manne "ajikin bango,</p><p>sannan yadawo ya zauna ya kalleni yace....?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page101-105</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A ah nikam bazanyi tafiyar dare ba, kunga yanzu abinda nakeso daku shine Ku kwashi kayan nan Ku maidasu daki, gobe da safe Ina Allah ya kaimu sai mufi dawuri,b</p><p><br /></p><p>Kunga dama gobe Lahadi ba "aiki sai mutafi harda, Magaji domin yace Mani yana hanyar dawowa gida, tunda shima nagane yakoyi tafiyar dare irin ku,</p><p><br /></p><p>Ta kallemu tana murmushi taciga ba dacewa basai mutafi harda shi ba? Cikin zoyaya tace kodai kungaji DA Hajiyar takune, shine yasa ku kamatsu Ku tafi kubarni?</p><p>Na dukar dakai kasa tareda cewa "a ah, </p><p><br /></p><p>Tace toh" Ku mayar da kayan daki sai kuzo muyi fira, mukace toh' kowa yanufi daki don ya ajiye kayan,</p><p><br /></p><p>Ni KO" arai Na tambaya nake wanene kuma Magaji? domin inajin wani lokaci Inna Asabe Na fadin Magajin gida Amma ban taba gani shi ba,</p><p><br /></p><p>Sannan wani abin mamaki shine tun ranan da wannan "mutumin, yashiga damu wannan gidan haryau ban sake ganinsa ba,</p><p>Wata kila "Mado ya ganshi Amma nidai kam banganshi ba,</p><p><br /></p><p>Muna kallon wani film nayaki Wanda nalura Hajiya Na matukar San kallo, da idan muna kallo tsoro mukeji amma damuka saba sai muka daina jin tsoro,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Muna kallo tana dan janmu dafira muna mayar mata,</p><p>Sai "akai sallama muka amsa tareda kallon maiyin sallama,</p><p><br /></p><p>Zumbur namike tareda boyewa bayan Hajiya, Saboda tsananin tsoro domin kuwa saye yake da kaya irin na mutanan da muke kallon acikin </p><p>harda wata yar karamar bindiga "asake akugun sa,</p><p><br /></p><p>Da sauri nace SOJA kasan cewar Hajiya tafada mana sunan wayan damuke kallo acikin t.v,</p><p><br /></p><p>Murmushi yai Wanda yakara mashi kyau da kwarjini yace Na'am,</p><p>Sai Na kalli Hajiya Cikin sanyin jiki nace "au Hajiya itama SOJA takeyi? tace "eh a hankali Na zauna tareda fashewa da kuka,</p><p><br /></p><p>Da sauri Hajiya tada fani tace A'isha Lafiya meya faru? Nace itama tana kashin mutane tunda gatan da bindiga, shikenan muna zata kashe mu KO?</p><p><br /></p><p>Zama yayi dirshan yana dariya saina daina kuka Na tsaye kallon sa, yanada kyau kwarai da gaske sai Kuma dariya shi takara masa kwarjini,</p><p><br /></p><p>Dana kalli Hajiya sainaga tana murmushi, sai nace Hajiya "ai itama tana kashin mutane KO?</p><p>tace "a ah sai mace toh" me takeyi dawan nan bindiga? </p><p><br /></p><p>Saiya tsaya dayin dariya sannan yazaro yar bindigar, da saurayi Na matsa kusada Hajiya, sai ya Kuma yin dariya sannan yace kinga wannan ko ? Nace "eh yace toh" da irinta ake kashe mutanan nan dasuka tareku "ahanya,</p><p><br /></p><p>Da sauri nace yauwa irin su zakirika kashe wa tunda, din azzalumai ne masu raba yaya da iyayansu nafada kamar zanyin kuka,</p><p><br /></p><p>Hajiya tace banasan kukan nan daki keyi share hawayen nan, da sauri Na share domin Na fahimci Hajiya Na san mu ya maida bindigar "agurin zamanta</p><p><br /></p><p> Sannan ya gaida Hajiya sai nida Mado muka gaidashi, Sai naji tana tambaya sa "ina Aina'u"?,</p><p>Sainaga ya yamutsa fuska sannan yace tareda "ita muka fito tace' Na sauke ta agidan gwaggo Rakiya,</p><p>tace" tana gaidake' wai sai gobe zata zota gaida Ku,</p><p><br /></p><p>itama ta amsa fuska bafara'a tace toh" aishikenan, Amma dai kotazo gobe bazata iskoni ba,tunda asamu wanda ya san ruggar su A'isha,</p><p><br /></p><p>Yace masha'allah yanzu gobe-gobe zasu tafi, tace "eh suda sukace da yau zasu tafi ni nace su bari sai gobe, </p><p><br /></p><p>Ya kalleni' yace "au da tafiya zakuyi ba tareda muyi sallama ba? nace " a ah dama "ai Hajiya tace abari sai Magaji yadawo, sannan mutafi gobe,</p><p>gashi kaima kadawo ba sai atafi harda Kai ba</p><p><br /></p><p>Sai naga sunyi murmushi yace toh" Allah ya kaimu goben Lafiya, nace Amin, saidai tunani nakeyi araina wacece Aina'u,? kaina nake tambaya wanda nasani banida amsarta, gadai masu bani amsar nan,saidai kuma kash! bazan iya tambayar suba domin kuwa sudin mutane ne masu girma wayan da kokaso tambayar su" abu kwarjini su da haibarsu bazata barka ka tambaye su" abuba, sundan taba fira kadan sannan yai mata sallama ya tafi,</p><p><br /></p><p> *********</p><p> Washe gari da misalin karfe takwas na safiyar Lahadi, bayan mungama karya kumallo, muna tsaye afalo nida Mado muna rikeda kayan mu, Hajiya muke jira tafito,</p><p><br /></p><p> Sai gasu itada maigidan ta Wanda take kirasa Da general, suka kalli juna sukai dariya, saina gaida su shima Mado ya gaida su, suka amsa fuskarsu cike da fara'a,</p><p><br /></p><p>Cikin zolaya yace doctor "aini har "Ina cewa mun samu yaya,tayi murmushi tace wlh nima Da haka nace saidai</p><p> Kuma naga yayan, sai sauri suke sugudu subar uwartasu KO" A'isha?</p><p><br /></p><p>Nace "a ah Hajiya "aiko muntafi zamu dinga zuwa muna ganin ki ko Mado? yace " eh, ta kalli maigidanta tace kaji abinda "sukace KO? yace naji ta kuma cewa kunyi Alkawari zakudiga zuwa? nace "eh tace toh shikenan Allah yasa kutashi mutafi,</p><p><br /></p><p> Muna zaune acikin mota ni' da Hajiya da Mado muna abayan, Shi Kuma Soja (nikan soja nake kiransa tunda bansan sunan sa ba)yana zaune agurin maituki da alama shi zaya kaimu , sai kuma Mutumin dazaya rakamu akusa da Soja mai suna Malam Habu,</p><p><br /></p><p>Har Soja' zaya tada mota sainai saurin cewa Hajiya gashi har za'a tafi ita "Magaji batazo ba?</p><p><br /></p><p>Murmushi tayi tace A'isha kenan toh "ai shine' yaza jamu zuwa ruggar taku,</p><p><br /></p><p>Da sauri Na kalli Soja sai naga shima' yana kallo Na', mai hade Da murmushi yace yanzu ke' da har Zaku tafi ba tareda kinsan 'suna Na ba?</p><p> Dai-dai lokacin da maigadi" yabude mana kofa muka fito muka dauki hanya,</p><p><br /></p><p>Da sauri nace "a ah toh" aike nasan sunan ki Soja mana ko"?</p><p><br /></p><p>Yace "a ah ni basuna na Soja ba Soja sunan "aikina ne, amma ni suna Na AHMED su Hajiya ne suke kirana' Magaji, kema Zaki iya kirana Magaji KO" ki kirani Ahamed dina,</p><p><br /></p><p>Ahankali Na gukar da kaina kasa cikin jin nauyinsa' nace toh" kiyi hakuri ni bansan sunanki kenan ba,</p><p>Sannan Kuma kiyi hakuri bazan iya kiran sunan kiba,</p><p><br /></p><p>Da sauri naji yace Saboda me? Kaina' nakasa Nace shaboda sunan ki yanada girma saidai zani cigaba da kiran ki SOJA,</p><p><br /></p><p>Yace toh" shikenan Amma dai kidaina kirana mace,"aikece mace Amma ni' "aina mijine ko"? Nace toh" Hajiya itada mlm Habu sai dariya suke yimana, harda shima Sojan dariya yake,</p><p><br /></p><p>Can Kuma sai kaji motar "anyi shuru yayinda Soja yaketa sharara gudu akan titi, tum muna tafiya akan titi har mukafara tafiya cikin Dani, yayida mlm Habu yake muna masa' hanya munyi tafiya mai tsawon sosai, Wanda har saidai Hajiya tace mlm Habu' Amma dai ruggar akwai nisa? yace sosai ma kuwa, tace toh" Allah yakaimu Lafiya, yace amin. ahaka har Allah yasa muka isa ruggar husiri bombe Lafiya.</p><p><br /></p><p>bayan yai fakin sai muka firfito daga motar, kallo guda naima ruggar araina Nace ayya wannan mlm Habun yasan ruggar mu kuwa?</p><p> </p><p>Domin kuwa banga bukko kinmu ba wanda suke sunkai guda goma sha,toh" amma kuma yanzu bukka guda nagani kol,</p><p><br /></p><p>Mlm Habu ne ya katse Mani zancan zucin danake, jinai yace naga ruggar tasake mun ne amma dai bari Na tambayi mutumin can,</p><p>dayake alwala suka nufi gurin shida Soja, mu kuma sai mukatsa jiransu.</p><p><br /></p><p>Shikam Mado yakasa hakuri saida yace Adda amma dai wannan ba ruggar mu bane KO"?</p><p>Jikina asanyaye Nace Mado nan ne, bakaga "inda ku keyin gardo gardo ba kaida su jauro ba, </p><p>Yace' eh Adda nan ne toh "Inasu Kawu dasu jauro hadasu Dija kawayanki,' kum...</p><p>Yayi shuru Saboda ganin su Soja sun dawo, gabana yafadi saka makon ganin fuskokin su ba bara'a,</p><p><br /></p><p>Hajiya tace yadai mlm Habu meya faru ne? ya girgiza Kai yace wai "a tun lokacin da yanfashi suka kashe matarsa, sai yan'uwana suka dawo dashi wannan ruggar don suyi jinyarsa,</p><p><br /></p><p> Kasan cewar sun harbesa" akafa toh" bayan kwana biyu Kuma, sai suka tashi gaba daya daga wannan ruggar, Kuma mun tambaye shi KO" yasan "inda suka koma yace shi wallahi baisan "inda suka koma ba,</p><p><br /></p><p>Kuka nasaki "Ina fadin mu kam mu shiga uku shikenan banida kowa, da sauri Hajiya ta rungumeni tace "akul nasa kejin wannan Kalmar tafito daga bakin ki',</p><p><br /></p><p>Sannan Kuma kiyi maza ki gaggauta yin istigifari, domin KO" kin sabi ALLAH,</p><p>ta Kuma cewa shin ke kika halicci kanji? Nace "a ah Waya halicce ki' Nace ALLAH, tace yauwa toh" aiduk Wanda yakeda ALLAH toh" "aiyana da kowa,</p><p><br /></p><p>Saboda haka share hawayen ki' domin nagane cewa kudin amanace ALLAH ya bani, don haka nikuma zanrike amana Kuma "Ina rokon Ubangijinmu, yata yani riko, </p><p><br /></p><p>Saboda haka kwantar da hankalin ki' nizan rike Ku tamkar yayan Dana haifada da cikina, sai "a lokacin naji hankali ya kwanta,</p><p><br /></p><p>Ta' kalli Soja tace maidamu gida, yace toh" Amma Hajiya da mun tsaya munyi sallah tunda naga lokaci yayi, tace' "eh yaja mata muyi kar mutafi da ita akai, tunda bamusan lokacin da zamu isa gida ba.</p><p><br /></p><p>Bayan munyi sallah "agidan wannan mutumin sannan muka Kama hanyar komawa gida,</p><p>sai kusan sallar magrib sannan muka isa gida.</p><p><br /></p><p> Bayan munyi sallah munci abinci muna zaune afalo muna kallo, saiga general yafito ya zauna kusada Hajiya tace sannu da fitowa yace yauwa,sannan muka gaida shi ya amsa tareda cewa A'isha nace na'am yace Doctor tayi Mani bayani komai, Saboda haka Ku kwantar da hankalin Ku" Ku dauka cewa nan gidaku ne kinji KO? Nace toh"</p><p><br /></p><p>Cikin wasa yace Doctor "ashe maganta tazama gaskiya danace mun samu yaya? yakara sa maganar dayin dariya itama dariya tayi tace takam zama, yace toh" Allah yata yamu riko tace amin,</p><p><br /></p><p>***********</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu da misalin karfe goma nasafiyar litini "Ina zaune afalo nikada "Ina kallo kasan cewar Hajiya" ta tafi gurin "aiki Mado" Kuma yafita, Inna " Asabe Kuma tan kichin tana "akinta, Saboda haka sai Na kasance ni' kadai,</p><p><br /></p><p>Azahiri "inkagani zakace "eh kallo nake, toh" Amma Kuma ba kallon nakeyi ba domin kuwa nayi nisa "atunani,Wanda ba lallai bane nafahimci "abinda akeyi a" T.V</p><p><br /></p><p>Don haka banji shigo warsa ba ballan tana "insan zaman sa, saidai kawai naga mutun zaune kusada ni' KO" Kuma Nace naji kamshin turaren sa'</p><p><br /></p><p>Da sauri Na waiga Sojane ya tsura Mani idanu, nadukar DA kaina kasa Nace "Ina kwana? bai "amsa ba saidai yayi Dan guntu tsaki mtsww.... da sauri na dagoda Kai Na kallesa,</p><p><br /></p><p>Batare da ya kalleni ba yace "inacan office jikina yabani cewa kina nan kina "aikin tunani, narasa "abinda yasa haryanzu kin kasa sakin jikin ki' damu, kiduba kiga Mahamud tuni yasaki jikinsa yanata harkokin sa ba'abinda yada mesa,</p><p><br /></p><p>Yace A'isha Nace na'am, ko" har yanzu baki yarda samu bane kina ganin kamar zamu cuceku ne? da sauri Nace "a ah,</p><p><br /></p><p>Yace toh" meyasa bazaki Zaki jikin ki' kiyi harkokin ki' kamar yanda kowa yakeyi ba,? bance komai ba sai ya girgiza Kai tareda mikewa,</p><p> Yaje ya dauko wanna babban Hoton dayake manne "ajikin bango,</p><p>sannan yadawo ya zauna ya kalleni yace....?</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page106-1010</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yanzu idan "aka tambaye ki "mutanan cikin Hotan nan, dawa sukai Kama meza kice? Da sauri Nace tagwaye,</p><p><br /></p><p>Yai murmushi yace hakane tagwaye nesu," wannan shine babba general ABDUL-JALAL" kenan shene mai gidan nan sai muna kiransa baba general,</p><p><br /></p><p>Wannan Kuma shine karami engineer ABDULl-JABBAR" kenan, shine kuma baba engr muke kiransa,</p><p><br /></p><p>Gidan sane na kusa da wannan "aikin gashi KO"? Nace "eh, yace su uku ne iyayansu" suka haifa da kanwarsu wacce takasan ce' Gambon su' mai suna goggo "Rakiya,</p><p><br /></p><p>Kuma dukkan iyayansu" sun rasu da sauri Na kallesa yace "eh kwarai da gaske sun rasu ba wanda yarage daga ya"ya sai abokan arziki,</p><p><br /></p><p>Kinga mahaifinsu "Alh Ahmed Dan kwangila, tsohon Dan kwangilane Kuma ma'aikacin gwamnati ne, yarasu ne " asana diyar hatsarin jirgin sama, daga London zuwa gida Najeriya, kasan cewar yana taba kasuwancin "acan ,</p><p><br /></p><p>Mutuwar sa" ta taba iyayansa DA Kuma matarsa kasan cewar sun shakuda shi sosai, hakana sukayi hakuri suka rungumi mahaifiyar su" saidai Kuma kash!, ALLAH maiyadda yasa a lokacin da yaga dama, bayan mutuwar mahaifinsu" da shekara guda sai ALLAH yaima Hajiya Hajara rasuwa, wato mahaifiyar su" sun girgiza kwarai da gaske da rashin iyayansu" dasu kayi "a kusan lokacin guda,</p><p><br /></p><p>Hakan su kayi hakuri suka rungumi junansu', suka Kuma rike maraicinsu domin sun'san iyayansu" sunyi masu nisa,</p><p><br /></p><p>Bawani mai taimakon su sai ALLAH suka cigaba da gudanar da harkokin su" har suka kammala karatun su", suka cigaba Da kulada dukiyar da mahaifinsu" yabari ,</p><p>ga Kuma "aikinsu dasu keyi sukai "auransu a lokaci guda,</p><p><br /></p><p>Saida ALLAH bai ba Baba gen haihuwa ba, shikam Baba engr ALLAH yabasa domin "a lokacin shekaransu" goma shabiyar dayin "aure ya"yansa biyar duk yanmata,</p><p>"Baba engr yana tausayama dan'uwansa" da rashin haihuwar DA ALLAH bai basaba,</p><p><br /></p><p>Don haka sai yabashi babbar yarsa wadda taci sunan mahaifiyar su' wato Hajara Amma sai anakiran ta da "Uwa baba gen yaji dadin abinda dan'uwansa yai masa, don haka sai suka dauki son duniya suka dorawa Adda "Uwa,</p><p><br /></p><p>Kwatsam sai ga Hajiya Binta tasamu Ciki wato matar Baba gen, kenan zokiga murna agurin wayan bayin ALLAH, cikin yana wata biyar suka tafi Saudiyya, saida ta haihu sannan suka dawo tahaifi DA namiji, akasa masa suna AHMED wato sunan mahaifinsu"</p><p><br /></p><p>"Baba engr ne yasa masa wannan suna domin kuwa yace shine MAGAJIN gida, DA saurin Na kallesa sai naga shima niyake kallo, yai murmushi yace "eh dalilin dayasa akekirana magaji kenan, </p><p><br /></p><p>Amma fa "anan gida ne kawai suke kirana da Magaji, awaje kam Ahmed dina "ake kirana,</p><p>Tun "inajariri "baba engr yake sawa anakai nasani', har nai wayo nake zuwa da kaina Saboda haka nafi sabawa dashi, </p><p><br /></p><p>Yanayi Mani duk abinda nakeso KO" kadan bayasan bacin raina, yadda nake ganin "Baba gen acikin kakin SOJA shine yake bani sha'awa, sai nacewa "Baba engr nima SOJA zanyi sai yayi dariya yace Magiji kenan toh", kadage da karatu saikaga kazama Soja,</p><p><br /></p><p>Dan haka saina dage da karatu wanda rabinayi sane akasar waje, har Na kammala tafito Soja, bayan nafara "aikine sai Baba engr yace' saura aure sainace masa niban samu yarinyar da nakeso ba, sai yace "aisu yanke shawara zasu hadamu aure nida " "Aina'u yar gurin goggo "Rakiya,</p><p><br /></p><p>Duk dacewa bana Santa, hakan baisa nayimasa" musu ba domin kuwa bazan iya jayyada shiba, sai kawai Na amsa masa da toh" ba'adauki wani lokaci mai tsawon ba akai auran mu,</p><p><br /></p><p>Yau shekara daya kenan da wata biyar dayin auren mu, yaushe zakuje gidana keda Mahamud? koda yake haryanzu bakisaki jikin kiba balle Hajiya tasa drive yakai ku,</p><p><br /></p><p>Yace A'isha don Allah kisaki jikin ki kinga kamar ranan da babu "aiki sai nazo nakaiku gidan "Adda Uwa da "Adda murja "Adda Safiya "Adda Sa'adatu" da Kuma gidan Jamila autar "Baba engr ita ba adade dayin auren ta ba, azaku jeko?</p><p><br /></p><p>Yafada 'yana murmushi nima murmushi nayi tareda sun kuyar Da</p><p> kaina kasa Nace "eh, yace yauwa A'isha haka nakeso,</p><p>Dai-dai lokacin da yamayar da hoton gurin zaman sa,</p><p><br /></p><p>Mado ne yashigo da sauri yana cewa Adda zoki gani, nace mezan gani? yace zodai muje kigani, tareda Soja muka fita koda muka fita sai mukaga yara" suna sayeda wani irin kaya, duk da dai bansan ko kayan meye ba, amma dai ga dukkan alama kayan makaranta,</p><p><br /></p><p>Lallai kuwa wai kayan makaranta Boko ne, Mado yace Hamman Soja nima inasan irin wannan kayan, yai murmushi yace ashe kana San kazama Dan makaranta Boko kenan? </p><p><br /></p><p>yace "eh yana so, sai Ya kalleni yace kefa A'isha kina so? Nace "eh, yace toh" Ku bari sai gobe insha'Allahu saina Kai Ku mukace toh"</p><p>Koda Hajiya da baba gen suka dawo muka fada musu sunyi murna sosai,</p><p><br /></p><p>**************</p><p> Washe gari tun karfe bakwai Soja yazo yadaukemu muka isa makaranta,</p><p> Ciki lokacin kadan aka gama komai wani sati muka fara zuwa makaranta boko,</p><p>Dama tuni muna zuwa makaranta allo,</p><p><br /></p><p>Saida gabaya nafahimci cewa ashe awan can lokaci karatun Boko sai Dan wane' dawane keyin sa, hakan mukaci gabada zuwa makaranta Boko, data data allo Cikin nutsuwa Da kwanciyar hankali,</p><p><br /></p><p>Saboda haka Cikin lokacin kankani muka rikida muka zama zuriyan Alh Ahmed Dan kwangila, idan kaganmu sai karantse da Allah Cewa mu yayan "Baba gen ne, Saboda yadda muka saje da su "Adda Uwa,</p><p><br /></p><p>Muna yima kowa biyayya, haka zalika muna bin kowa sauda kafa, Saboda </p><p>Bamuda matsala da kowa kaf zuriyan nan kowan yana sanmu, idan kacire Mutum biyu wato "goggo Rakiya da yarta' "Aina'u sunan kam nasara abida mukai masu ba basu sanmu,</p><p>tsakanin mu dasu sai zagi da hantara ga "goggo Rakiya irin mutanan nan ne masifaffu,</p><p><br /></p><p>Daga ita har "yarta gashi nikuma Allah yasaka mun tsoron su"shiko "Mado baya tsoron su' KO" kadan, yayinda Na lura ita Kuma Aina'u tana shakkar "Mado sosai, don KO" idan yana gida kota zo batayi Mani rashin mutunci Wanda sai takula "Hajiya bata kusa sannan takeyi mun,</p><p><br /></p><p>Cikin haka har muka gama mataki nafarko karatun Boko, munajiran mutafi mataki nagaba sai kuma samari suka fara neman aure na domin KO" nazama budurwa tunda a lokacin shekara ta goma sha hudu,</p><p><br /></p><p>Shikam "Hamman Soja baya so "Ina kula samari saiyai tafada idan yazo yasameni Ina fira, aciki samarin Nawa yafijin haushi Abubakar Saboda yaga nafi kula shi,</p><p><br /></p><p>**************</p><p>Akwai wata rana yazo sai ya iskemu muna fira, sai yace nashiga gida bace komai ba Na nufi cikin gida nabar su' nan tsaye shida "Abubakar,</p><p><br /></p><p>"lna daga daki naji yace wa Hajiya wai tadaina barina "Ina fita yin firada samari barkatai harda mawan "Abubakar din wallahi Hajiya ni haushi sa nakeji, Hajiya tace "ah samari kam "ai dole takulasu' tunda ba'ajiye ta zamuyi "agida muna kallon taba dole gidan wani zata,</p><p><br /></p><p> "aima tunda naga tafi kula shi Abubakar din zan fadawa gen yace masa ya turo iyayansa, da karfi naji yace haba Hajiya "ai gida bai koshi ba baza'akai waje bako"? (sai tayi kamar bata fahimci abinda yake nufi ba) </p><p><br /></p><p>Sai tace kamar ya gida bai KO shiba? sai yace Hajiya wallahi nadade nima "lna San "A'isha don Allah ki yardan mun Na aureta, tace "a ah nibazan yardan maka ba har sai tace tana sanka, Saboda haka sai kaje kanemi so dayar danta.</p><p><br /></p><p>Niko "lnajin haka saida gabana yafadi "araina ko" fadi nake ni A'isha Hamman Soja keso? "Ina cikin wannan zancen zucin sai naga Hamman Soja yashigo dakina,</p><p>"aiko sai naji gabana Ya cigaba Da faduwa,</p><p><br /></p><p>Zama yayi kusada ni kadan yace A'isha nasan kinji maganar da mukai da Hajiya KO"? Nace "eh yace toh" meki kace? shuru nai bance komai ba, yace A'isha wallahi "Ina sanki Kuma "Ina san Na aure ki, kema kina sona? </p><p><br /></p><p>nai shuru domin jinai kunya duk tarufe ni, yasake cewa don haka A'isha kina so na Zaki aureni,? Kai nadaga alamar "eh ko" da bana san Hamman Soja, bazan iya cewa "a ah ba balle "Ina San sa, kodan halaccin dasukai mana a rayuwa,</p><p> </p><p> "ako gaba daya zuriyan "Alh Ahmed Dan kwangila sunyi murna da jin haka, idan kadauki mutun biyu wato goggo "Rakiya DA yarta "Aina'u,</p><p>Oho! Ba wanda kula</p><p> lamarin su, don haka Cikin lokaci kankani "Baba engr yasa ranan auren wata biyu,</p><p><br /></p><p>Wanda tundaga ranan nafara fuskantar kalubale a rayuwa ta daga gurin "goggo Rakiya DA "Aina'u </p><p><br /></p><p>haka naci gabada fuskarta abubuwa kala-kal daga gurinsu" Wanda sai sun tabbatar da Hajiya bata nan sannan sai suzo suyi Mani zagi ta Uwa ta Uba,</p><p><br /></p><p>tsoron su" yashige ni sosai da Kuma gargadin su", dauke cewa duk ranan dana kuskura nafadawa "Hajiya sai sunyi Mani dukan tsiya don haka bantaba tunani fada mata ba,</p><p><br /></p><p>Ana saura sati biyu auren, a wannan lokacin Kuma tuni Mado "aikai shi karatu can kasar waje, wai bazaya dawoba sai yagama karatun sa duka, </p><p><br /></p><p>Don sai nakasan ce' ni kadai "a gida "Ina zaune a falo "Ina kallo, kasan cewar aranan "Hajiya taje unguwa, sai kawai naji saukar duka "abaya na,</p><p>tareda cewa yauwa gashegiyar nan'</p><p><br /></p><p>Zumbur namike goggo Rakiya nagani "itada Aina'u, jinayi gabana yafadi yayinda suka Hauni da zagi da dunguri,</p><p><br /></p><p>Cin mutunci su" kayi mani nakarshe Kuma suka ce Mani muddun nayarda Na AURI "SOJA sai sun kasheni fuuu....</p><p>Suka fice daga falon...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tab turkashi babban magana,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞Lufhat CE💐</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page116-120</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*😭KULLU'NAFSI'ZA'EKATUL'MAUT*😭</p><p>*DUKKAN RAI* saita dandani *DACIN* *MUTUWA*</p><p>Wannan page din NASA daukar dashi ga yayata *HAJIYA LARAI GODABE wadda tarigamu gidan *GASKIYA* Ina rokon *ALLAH* yaji kanta da *RAHAMA* yasa Aljanan'nar *FIDDAUSI* makomar ta tarada yan' uwa *MUSLIMAN* baki daya Amin, 😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭</p><p>*WE MISS YOU MORE AUNTY LARAI* Allah yajikan kida *RAHAMAR SA* </p><p> </p><p>*DAN ALLAH KUYI MATA ADDU'A*</p><p>Please Don Allah Ina rokon Duk Wanda </p><p>Karanta wannan page din nan yaima *AUNTY NA HAJIYA LARAI GODABE ADDU'A*</p><p>----------------------------------------</p><p>®PEN WRITERS ASSOCIATION</p><p><br /></p><p>PEN:THE STRONGEST WEAPON</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p>"Meh ? "eh Nace masa duk dacewa ban fahimci "abinda yake nufi da hakan ba, amma dai tunani na yabani cewa farin ciki ne yasa shi yace haka, don haka sai nima naji farin cikin yaka Mani, duk dacewa "Ina danjin faduwar gaba kadan, Saidai Kash! "Ashe bansa niba farin cikin nai shine zaizama mani bakin ciki mara musaltuwa arayuwata zuwa gaba bansa niba...</p><p><br /></p><p>Domin kuwa wani irin harara yai Mani Wanda yasa, naji gabata ya cigaba da matsananci bugawan dayake yi, yace toh" wannan takardan kam ba naki bane, </p><p>Na zaro idanu Ciki tsoro tareda cewa eye! ? da sauri nakarbi takardan "a hannun sa nace' nawane mana ga sunana nan "an'rubuta A'isha Ahmed,</p><p><br /></p><p>Yace' "eh sunanki nagani A'isha Ahmed, saidai Wanda ya baki takardan baisan "aikinsa bako...? Cikin matsananci kosawa dajin zancen Hamman Soja, wayan dasuke kokari tarwatsa Mani kwakwalwa,</p><p>Nace masa "Hajiya ce fa ta tadu bani' Kuma itane tayi rubuta Kuma ma "aikasan "aikin tane tadade tanayi ballan tana "ace bata iyab.... </p><p><br /></p><p>Da daga murya yakatseni dacewa ke! rufe Mani baki, "aikam da sauri nayi shuru, yace kinsan abinda takardan ta kunsa kuwa? DA saurin Nace "eh Ciki "akace "ina dauke dashi, yace "eh hakane wato ke' din kina dauke da cikin kenan KO? Nace masa "eh "ai wannan watan daya kare banga "al'adata ba Kuma kasan farkon wata nake gani, gashi wannan harya kwanan sa" hudu amma ban gani ba, kaga kenan "Ina' dauke dashi KO? Wani wawan tsawa Hamman Soja yadoka Mani, tareda cewa Ke! banasan maganar banza DA wofi kinji KO"</p><p><br /></p><p>"An fada maki Ciki "abun wasa ne da kike kokarin kiyi wasa dashi? Kodaya ke' naga "alama Nema kikeyi kiyi Mani wasa da hankali, "inba haka ba "a "Ina kike da Ciki eye? yakarasa fada Cikin daga murya, Cikin matsananci tsoro Nace wallahi "Ina dashi nafada tareda kallon sa' gabana ne ya cigaba DA matsananci bugawa lokacin danaga idanun shi sun can a Kala daga fari zuwa JA,</p><p><br /></p><p>Sainaga yafito mani SOJA SAK Don haka sai naji tsoro yasake kamani, sai ya girgiza Kai tareda watsa Mani JAJAYEN idanu sa masu bani TSORO, yace lallai A'isha baki Cikin hankalin ki dan'naga alama bakisan "abinda kike fadaba, kodai CIWON KI' yatashi ne? nace wallahi "Ina Cikin hankali Na Kuma bawani ciwon danakeji ajikina "idan ba zazzabin Cikin nan ba, kaduba kagani da gaskene Hamman Soja wallahi "Ina DA ciki,</p><p><br /></p><p>Dakarfi yace "indai harda gaske ne "kina' da Ciki toh" tabbas dashi kika zo, amma kam ba'agidan nan kika same shiba, Domin kuwa ni' bana haihuwa Dan haka taya za'ai kisamu Ciki tareda ni'?</p><p>Jinai gabana yayi mummunan faduwa harsaida naji "antar Ciki Na yakada dajin kalaman Hamman Soja, bangama fita daga cikin wannan tashin hankali ba, Hamman Soja yasake sakani "cikin wani,</p><p><br /></p><p>Domin kuwa cewa yayi' barina kawo maki takardan dasuke nuna cewa' nidin bazan taba haihuwa ba, Saboda nasamu matsala tun lokacin Da nayi hatsari, da sauri yanufi dakin shi,</p><p><br /></p><p>Can sai gashi yafito hannun sa' rikeda takardu, yana zuwa girina sai watsa matani takardan "ajikin tareda cewa gashi nan Kiduba kigani DA kyau saida naga likitoci har mutun uku Kuma sun tabbatar Mani da cewa bazan taba Haihuwa ba Saboda kwayoyin Na sun mutu,</p><p><br /></p><p>Toh" tayaya zakice Mani wai kinada ciki, yanada kyau kije kinemi Wanda yakeda Cikin nan, amma bani ba ransa "abace yafita,</p><p>"Ahankali nabi bayan sa DA kallo har yashiga Cikin daki, sannan nadawo da kallo Na kan takardan tareda dauka "Ina dubawa,</p><p><br /></p><p>Tabbas rubutun "irin guda ne, wato hakan yana nufi da gaske Hamman Soja bazaya taba haihuwa ba...? Idanu na rinte fatana wannan abun yazama mafarki, rokona kuma shine ALLAH yatasheni daga wannan nauyayyan baccin mai dauke da mummunan mafarki, Saidai ba mafarki nakeyi ba domin kuwa "Ina bude idanu Na takardun magani, "Ahankali nasa hannuna nakwashe su' sai kallon su nake daya bayan daya, naima takardun kallon da ni kaina bansan "iya "adadin sa ba,</p><p><br /></p><p>Yayin da gabana yaci gabada faduwa zuciyata kuwa wani irin matsnanci harbawa takeyi, "araina Kuma fadin nake Na shiga uku ni A'isha mene yake shirin faruwa Dani...? "Ahankali Na mike Hannun na dauke da takardun JIKINA "asanyaye, Na nufi dakin Hamman Soja domin Na Kai masa, saidai ga Bamako na ko" da na'isa kofar dakin kod nasa hannun natura kofar sai najita GAM,</p><p><br /></p><p>Kirjina najiya Kuma bugawa yayinda kaina yasara "Ahankali naja nafara zuwa bakin table dakin dayake tsakiyar falon, Na'aje mashi takardu domin nasan idan yafito zaya ganinsu,</p><p>Na nufi dakina ba tareda "Ina ganin hanya ba domin kuwa wani irin duhu nake gani, rabona dashiga tashi hankali irin haka tun lokacin da, yan'fashi sukai sanadin rabamu da iyayen mu'</p><p><br /></p><p>"Ahankali Na kwanta "agado yayinda wani matsananci zazzabi yarufe ni, da kyar nasha magani Na koma na kwanta,yadda naga rana haka naga dare domin kuwa ko" bacci ya kaura cewa iduna,</p><p><br /></p><p>*******************</p><p>Washegari tunda nai sallah "asubu nashiga kicin Nawa Hamman Soja abun Karin kumallo, kamar yadda nasa ba duk ranan danake da girki, saidai wani abun mamaki shine koda naje dakin sa Don nagaida shin "in, Kuma fada masa ga Karin kumallo shi" saina "iske har yafita, JIKINA "asanyaye najuya DA nufin nakoma dakina, tsaye nayi turus saka makon ganin Adda Aina'u tsaye abakin kofar dakina,</p><p><br /></p><p>Tana doka mani wani irin murmushi Wanda narasa gane kona mene?... , cikin faduwan gaba Nace mata "Ina kwana? tace lafiya lau mai CIKI, sai Kuma ta fasheda dariya Wanda kana jin sa kasan ta mugun ta ce', </p><p><br /></p><p>Saida tayi mai "isarta sannan tsaya tace su"ciki manya ke' yanzu kina nufin ciki gareki?..., tab lallai taya ki ke tunani samun ciki da mutumin da bazaya taba haihuwa ba?..., toh" bari kiji "nafada maki muddun kika yarda kika haihu "agidan nan toh" KO" DA SANNU...Zaki gane kin tabka babban kuskuren "arayuwan ki', domin kuwa kisani cewa duk "Abinda kika Haifa "agidan nan toh" KO" dashi da shege basuda bambanci,</p><p><br /></p><p>Saboda "Hamman Magaji bazaya taba daukar miki shege ko" shegiya ba "ehee, don haka gwanda kisan yadda Zaki yi DA wannan cikin , ta harareni sama da kasa ta watsar sannan taja tsaki mtsww...., tareda tureni tawuce.</p><p><br /></p><p> Da" sauri nadafa bango badan haka ba dana fadi, gaba daya maganganun ta" sun Kuma birkita Mani kwakwalwa,</p><p>yayin da gabana ya cigaba da faduwa DA kyar Na "iyajan kafa zuwa daki,</p><p><br /></p><p>Koda nashiga dak... kukane yakwa cewa Mama' mai tsuma zuciyan mai sauraro gaba daya dakin sunyi tsit suna sauraran Mama' tareda tausayi ta Y Y k shima kukan yake na tausayin ta,' saida tayi kuka sosai sannan taci gabada Shafa kam Abdul-jabbar Wanda shima kukan yakeyi, Na tausayi mahaifiyar sa,</p><p><br /></p><p>taci gabada da cewa" kuka nayi sosai dana shiga daki, Na tausayin kaina da " abida Zan Haifa, tun baizo duniya ba "anfara shegan tasa?... nikam nasan shi ba shege bane tabbas "Hamman Soja shine UBAN shi tunda ni' dai bantaba tarayya dawani DA namiji "idan ba Hamman Soja ba, </p><p><br /></p><p> Shikenan Kuma tundaga wannan lokaci, nake fuskarta matsaloli Kala Kala banayin bacci kullum da zazzabin nake kwana, dashi nake tashi gashi bana "iyacin "abinci sosai saboda laulayin ciki, kullum "ina cikin daki duk narame nayi baki "Hamman Soja kuwa dama tuni yadaina kulani, bana ganisa Kuma bana sanin lokacin fitarsa" haka kum banasanin dawowar sa" </p><p><br /></p><p>"Wani abin mamaki Kuma shine ban taba fadawa kowa halin danake ciki ba, "idan "Hajiya takirani ta tambaye ni' yanake "ina shan magani kuwa?... saidai nace mata "eh kawai, "a haka har Ciki Na yakai wata biyar "a lokacin Kuma rabona da Hamman Soja harna manta rana, </p><p><br /></p><p>Ran wata Lahadi da bazan taba manta da ita ba "arayuwa ta, nafito daki kenan sainaji telephone nakara saina dauka, gabana ne yafadi saka makon jin murya Hamman Soja,</p><p><br /></p><p>"A hanka Nace "Ina yini bai amsa cikin fada yace A'isha wai zaman meki keyi "agidana har yanzu dauke DA wanna cikin Daba Nawa ba?...</p><p> toh" Bari kinji nafada miki karki kuskura nadawo nasa meki gidan nan kina dauke DA wannan cikin, Saboda haka duk yadda zakiyi da shi kiyi dashi kinji nagaya miki, Domin ni bazan dauki abinda bana waba zanyi magana kenan sainaji ta katse,</p><p><br /></p><p>Don haka sai namayar Da telephone din na'jiye, yayin da"idanu Na sai tsiyayar hawaye suke jiki "asanyaye Na nufi daki,kayan jikina nacire nasa wasu tareda daukan wasu kudi da wasu yan kayana guda biyu, sannan nafito, yahuza drive nagani zaune yana ganina sai yataso,</p><p><br /></p><p>Bayan mun gaisa saiya tambaye ni' ta "Inazaya kaini'?.... saina ce' masa " "asibiti zaya Kaine, yace toh" kodaya kaini "asibiti sai yace zaya jirani nagama ne?.. sai Nace "a ah yatafi sai "anjima yadawo ya daukeni yace toh", "Ina gani yawuce, sai kawai nafita daga </p><p>"asibi ,</p><p><br /></p><p>domin banajin Zan' iya fadawa "Hajiya komai toh" mizan ce mata?... Saboda haka "koda na fita asibitin motar haya Na hau sai nace yakai ni' tasha, yace toh" sai kallon gari nake tunda bana fita koda muka "isa nabi yashi kudinshi sai naji "Ana fadin Kaduna mutun daya, basan kaduna ban taba zuwa ba, amma kawai sai nashiga mota nan da "akace kuduna ba'dauki wani lokaci ba motar ta tashi zuwa Kaduna.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"tafiya sosai mukayi tunda sai daddare muka "isa, Kaduna fasinja suna tafita amma ni' "Ina zaune ban fita ba saboda nayi nisa "a tunani sai jinai mai mota yace?....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞Lufhat Ce💐</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page121-125</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*WANNAN page*</p><p>*GARGADI NE GA MASU SATAR FAHIMTAR WASU SU MAYAR TA SU*</p><p>*Hmmm Abun DA mamaki gaskiya NI BAN TABA tunani SATAR FAHIMTAR KOWA Ba hmmm dazan fada maka/ maki TUNLOKACI DANA KE RUBUTA WANNAN LITTAFI SAI KAYI MAMAKI saboda haka WALAHI duk wacce KO Wanda I mean MACE' KO NAMIJI" ta Ya JUYA Mani LITTAFI NA azuwan SHIYA RUBUTA TO BANYA FEBA! BANYA FEBA!! BANYA FEBA!!!*</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*®PEN WRITERS ASSOCIATION*</p><p><br /></p><p>*PEN:THE STRONGEST WEAPON*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Haba Baiwar ALLAH wannan wani irin "abune haka tun dazu muka "iso mutane duk sun fita "amma ke' baki fito ba KO" bakisan dare yayi bane? </p><p>"Ahankali Nace kayi hakuri sannan nafito, gefe nakoma Na tsaya sainaji tsoro yaka mani ' Saboda ganin tashar ba buwasu mutane sosai, sai kadan kadan, shikam drive tuni yaja motar sa" yatafi,</p><p><br /></p><p>"Ahankali nakoma jikin wata runfa nazauna tsawon wani lokaci, sainaga mutanan sunata tafiya " saida Na tabbatar mutane sungama tafiya, dare yayi sosai, saina shinfida zani Na, na kwanta duk Dana sai dacewa ba baccin zanyi ba, saboda dama nasaba sai kusan sallah "asuba bacci mai nauyi yake dauka ta,</p><p><br /></p><p> "A hankali nabude "idanu na saka makon Jinda nai "ana bubbu gamani kafa, tareda cewa ke! baiwar Allah lafiya ki kazo nan Ciki tasha kika kwanta,?...</p><p><br /></p><p> "A hankali na juyawa dan'naga mai magana, wata dattijiyar mata nagani tareda mutane ne dayawa suna kallon Na, Da sauri natashi nazauna matar ne tace baiwar Allah lafiya meya same ki'?....</p><p><br /></p><p>Kuka kawai nafashe dashi batare da nace" mata komai ba, da sauri tace' "subhanallahi! mai yafaru taso! taso!! takama hannuna muka shiga shagon dake cikin wanna runfar,</p><p><br /></p><p>Babu wani tarkace "acikin shagon daga bancina nazama ne sai table "inda "ake dora abinci, "abanci ta zaunar Dani sannan "itama ta zauna, sannan tace yishuru kinji ya'ta share hawayen ki fada Mani meya faru dake?</p><p><br /></p><p>"Ahankali nafada mata "abinda yafaru ban boye komai ba, tayi shuru Na Dan wani lokaci tana nazari, can tace tabbas "ayanda nafa himci labarin ki' lallai akwai sihiri "aciki tareda sharrin kishiya, sannan mijin ki baiyi kwakkwar bincike "akan cikin kiba,</p><p><br /></p><p>Saidai karki damu "DA SANNU" Allah zai bayyanar da gaskiya, saboda haka yanzu "abida nakeso dake shine kikwan tarda hankali ki' kinga ba'asan mai juna biyu" tana yawan tunani dasa damuwa "aranta tashi muge nakai ki' gidana kiyi wanka ciki Abinci kinji ko?</p><p>Nace toh" tareda mikewa muka fito,</p><p><br /></p><p>Bayan mun fitone sai naji tana kiran maryam, saiga wata yarinya yar kimani shekara goma , tafito daga dayan shagon dayake kusa Da "inda mukafi to, hannun ta rige da tsintiya da "alama shara zatayi,</p><p>tace gani' matar tace yauwa kikula sosai bari nakai wannan gida yanzu zan dawo, Maryam tace toh" </p><p><br /></p><p>taxi muka shiga tace masa' sabangari zaya kaimu, yace toh' "adai-dai wani Dan matsakaicin gida aka saukemu bayan tafiya shi" kudi, sai muka shiga gidan yana dauke da dakuna uku,da kuma kicin da bayi tsakar gidan yana da fadi kadan, ga wasu manya-manyan tukwane Dana hango "acikin kicin din,</p><p><br /></p><p>Daya daga cikin dakin muka shiga yana dauke da, gado biyu da Kuma tarkacen kaya tace bari Na kai miki ruwa kiyi wanka, Nace toh"</p><p><br /></p><p>Bayan nayi wakan da ruwan zafi, tunda "a lokacin (hunturu ne) wato sanyi takawo Mani abinci, naci, sai take fada Mani sunan ta Hajiya Hafsatu amma Hajiya Magajiya ake kiranta', sannan gidan nan nata ne' "itada yarta, da mijinta yarasu aka raba gado aka bata sai tasiya, tana Kuma yin abinci takaiwa tasha, bayan tagama fada Mani sai tace toh" nahau gado Na kwanta nahuta "ita zata koma Tasha gurin sana'arta Nace sai tadawo ALLAH ya bada sa'a tace' Ameen tareda fita,</p><p><br /></p><p>Haka naci gabada zama agidan Hajiya Magajiya, cikin kwanciyar hankali tana kula Dani sosai bata barina nayi "aikin wahala, saidai Dan motsa jiki kawai, ranan wata litini natashi Dana kuda Hajiya takira mai taxi yakaimu "asibiti,</p><p><br /></p><p> Ciki "ikon Allah Na haifeka lafiya bayan "angama komai, "aka salla memu muka dawo gida, nikam ba "abida zancewa Hajiya saidai nace Allah yajikan ta', da rahama yasa Aljannar Fiddausi ce mako marta, domin tayi mani abubuwa dayawa arayuwa, bayan kwana biyu saita tambaye ni"wani suna nakeso asakama?,nafada mata akai maka huduba dashi, komai "ita ce tai mani kayan sawata DA naka da ragon suna duk itace' tayi da sati yaza gayo "akai suna,</p><p><br /></p><p>Bayan suna saita cigaba da kula mu ni' dakai, da dafarko Da "Madona kake kama "amma daga baya saika rikida ka koma "Hamman Soja, kamar yanda"akace jarirai rikida suke" toh" haka yake,</p><p><br /></p><p> domin kuwa rikida ka keyi naban mamaki, kullum kaman'nika sake fitowa yake Dana "Hamman Soja komai naka irin Na shine', hattada kunban kafarka irin nashi ne, hankali ya kwanta ganin yadda kayi Kama Da "Hamman Soja Wanda KO makaho yalalibeka yasan kaidin DAN SANE", "ahaka dai Na cigaba da goyonka harna yayeka,</p><p><br /></p><p> lokacin da ka shekara hudu Hajiya tasaka "a makaranta islamiyya data boko "awanna lokacim Kuma tadade tanayi Mani maganar komawa gida, "amma saina ce' mata "a ah, bazani kowa ba wani lokaci idan tayi maganar komawa gida saina farayi kuka, dan'haka sai ta kyaleni tunda taga bana so",</p><p><br /></p><p> ************</p><p>Ranan Wata jumma'a daga makaranta aka kawo ka', baka da lafiya hankali mu yatashi sosai muka tafi "asibiti, bayan Likita yaduba ka' yace kana fama da ciwon zuciya, dan haka sai "aguji bata maka rai,nikam mamaki nayi tareda tambayar kaine cewa dama yara suna ciwon zuciya,?</p><p><br /></p><p>"Ahaka dai mukai jinyarka' har kaji sauki, saidai Kuma tun bayan Da kaji saukin sai Na kula dawani bakon "al'amari daga gareka, shine sai ka zauna kayi shuru "abin Nada muna'</p><p>Duk da cewa dama Kai din bamai yawan magana bane,</p><p><br /></p><p> "Amma Kuma wannan din yayi yawa sosai, ran saina tambaye ka mai kakeso sai kace Mani bakomai, can Kuma sai kace Mani Mama "ina BABA NA? gabana yafadi tareda jin wani irin tashin hankali, "amma Kuma sai ban bari kagane ba,</p><p><br /></p><p> murmushi nayi Nace babanka bayanan, sai bakace komai toh" shikenan kuma</p><p>tundaga wannan lokacin sai ka cigaba da tambaya ta, "amsar daya ce nake baka shi BABAN Ka bayanan, ran sai kace yaushe baban ka zaya dawo? shuru Nai "Ina tunani "abida zanba ka? saboda karka cigaba da tambaya ta, sai Nace maka ba "Ai BABAN Ka yace bazaya dawowa ba,</p><p><br /></p><p>toh" fa shikenan sai kadaina tambaya Na, duk da cewa bakasan BABAN ka ba Amma Ina ganin SON shi akwayar idanu ka, </p><p><br /></p><p>Kanada shekara bakwa, ALLAH yaima Hajiya rasuwa, saka makon rashin lafiyar kwana biyu, nayi kuka sosai bayan tayi kwana arba'in, hankali Na yatashi lokacin da yan' uwanta "sukazo, Dan asiyar Da gidan, su" Kuma tafida "Maryam za'ai mata aure can garinsu sokoto,</p><p><br /></p><p>Haka kuwa akai bayan ansiyar dagida, sai suka tafi da maryam, amma kafin su tafi saida Maryam takama mini gidan haya tabiya kudi, sannan Kuma tabani wasu kudin tace' narike,</p><p><br /></p><p>A haka Na cigaba Da kula da Kai' gashi Allah yasa maka san karatu "aranka', Dan haka nasha wahala sosai gurin Neman kudin Da zakai karatu, ba abinda banyi ba nasiyar wa kosai, waina, wankau, aikatau, harda surfe da daka duk nayi, kai komai nasamu yinake, don kawai naga na'inganta rayuwar ka, nafara samun saukine lokacin da karfinka yakawo, sai kafar dako da Na baro, Wanda nasan duk baka manta da hakan ba,</p><p><br /></p><p> Har lokacin DA ALLAH ya hadamu DA Alh ya'u Na Kaka, yatallafi rayuwan mu" wannan shine abinda yafaru arayuwa ta da Kuma Kai, takarashe maganar tareda share hawaye.</p><p><br /></p><p>"Tabbas Abdul-jabbar bai manta wahalar dasu kasha ba shida Mama, Ahankali Abdul-jabbar yakejin wani irin tausayi Mama na ratsashi, tareda Sonta da Kaunar ta yana ratsa jini da bargon shi, yayinda yakejin wani iri. haushi babansa" musamman daya kasance mutun Mara BINCIKE, "acikin lamari sa domin inda yayi bincike tabbas da Mama bata shiga wani haliba, "ahankali ya dagoda kansa, ya kalli Mama fuskarsa shabe-shabe Da hawaye, hannun yasa yana share mata hawayen fuskarta tareda cewa, kiyi hakuri Mama na kidaina Kuka tabbas "anzalin ceki tareda yimaki mummunan fahimta, saidai kisani DA SANNU gaskiya zatayi halinta, kinji KO?</p><p>tace haka ne musamman ma "akan mahaifiyaka" Wanda "Naji LABARIN cewa yanzu shine Governor Adamaw! da sauri yace " a ah! a ah!! a ah!!! Mama basonjin koshi" wanene yanzu, tunda yace niba Dansa bane toh" shikenan, nima shi" ba babana bane' kece MAMA Na Kuma kece BABA na, dakarfi yake fadar maganar Wanda kanaji kasan baya cikin hayyacinsa, yace</p><p> saboda haka abinda nakeso shine kidaina kuka, saboda bana san ganin hawayenki kinji, sannan "ina Son duk Wanda ya kyautata maki a rayuwa, saidai kam Na tsani Wanda duk ya cuta maki, Mama ina Sonki! "Ina Sonki!! Ina Sonki!!! Mama Na!!!!!!! </p><p><br /></p><p>A hankali jikinsa yasaki, saka makon alluran bacci da Doctor I s g yai masa, aikam cikin lokaci kankani nauyayyan bacci ya dauke sa, da sauri Y Y k yazo yadaga kasan daga kafar Mama, yayin da Doctor yai sauri jawo filo suka dorasa tareda gyaramasa kwanciyar,</p><p><br /></p><p>Alh ya'u nakaka ya suke nauyayyan ajiyar zuciya, yace kiyi hakuri Hajiya A'isha kisani kowani bawa DA irin jarabawar da Allah keyi masa, Amma idan yayi Hakuri toh" "DA SANNU" zayaga kyakkyawa saka mako, yamaida dubansa ga Doctor yace Doctor Ina fata babu wani sauran matsala tareda Abdul-jabbar din KO?.... yace eh Alh bakomai darazan yasamu isassaa bacci toh insha Allahu sai tashi normal, saidai game DA ciwon zuciyansa sai andinga yin taka tsantsan da gudun bacin ransa, Alh yace toh " shikenan ALLAH yabashi lafiya gada suka "amsa DA Ameen, yace nadabo kamaida Hajiya A'isha gida yace to, "alokaci guda suka fita daga dakin gaba dayansu.</p><p><br /></p><p>**************</p><p>Abdul-jabbar yaji sauki sosai,jikinsa yamarje yakara wani irin kyau idan kagashi baka taba cewa shine yai wannan rashin lafiya, sai wani Kuma shine tun bayanda "Mama tabashi labarin ta,</p><p><br /></p><p>Shikenan Kuma sai yake jin haushi mutane Abinda bayayi da toh" shiyakeyi yanzu wato fada, abu kadan sai yafara, yayinda yake ba Mama kulawa ta musamman fiye da tunani mai karatu, data motsa sai yace Mama mekike son, hakan itama tace kula dashi sosai musamman dataji abida likita yafada dan haka batasan "abida zaya bata masa rai,</p><p><br /></p><p>Ranan wata laraba Abdul-jabbar yafito zayaje gida su Y Y K dakuma yawan da yasaba Na Neman Humaira *nikam Nace tabdi Humeeh kam tana yola*</p><p>yana sanye da t shat baka da wandon jims fari kalkal, hannun sa rike Da key" mota tareda wayar sa,' sai kamshi yake zubawa cikin nutsuwa yake tafiya har ya isa bakin mota, zaya bude motar kenan sai yaji wayarsa Na Kara koda yaduba saiyaga sunan Dalter boy, yana dauka sainaji DA karfi yace?.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufha Ce💞</p><p>💐💐💞💞💞 💞💞💞💐💐 </p><p> DA SANNU</p><p>💐💐💐💞💞 💞💞💞💐💐</p><p><br /></p><p> page126-130</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT 💐UMAR 💐FARUQ</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>------------------------------</p><p>------- </p><p><br /></p><p>*®PEN WRITERS ASSOCIATION*</p><p><br /></p><p>*PEN:THE STRONGEST WEAPON*</p><p>--------------------------------------</p><p><br /></p><p>*only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏽</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Meh kace? sai kuma yacire wayar da sauri daga kunsan shi', sannan yakara volume din wayar, don yaji maganar da kyau, yace banji da kyau ba fa meh kace? Delter boy yace Dan "iska nasan kaji, kanaso ne nasake maimai tawa, toh" nace ne" "anyi posting din mu yola nan da two months zamu tafi,</p><p><br /></p><p>Cikin karaji Abdul-jabbar yalallayo wani Uban ashar yakwada wa Delter boy, tareda cewa Kai! Uban wanene yai posting dina Wannan garin? Delter boy yace a ah to menene "aiba Shame bane, Dan "anyi posting dinmu Adamawa inace garin kune? </p><p><br /></p><p>Cikin masifa Abdul-jabbar yace toh" nibana San wannan gari kaji KO"? Cikin mamaki Delter boy yece toh" ikon Allah tunda nake bantaba jin Wanda yake gudun garinsa ba saikai' </p><p><br /></p><p>yace "eh naji Dalla malam kafada mun Uban wanene yace ayi posting dina wannan garin? cikin jin haushi Delter boy yace Ubana ne, Dan iska tunda idan zasuyi posting din suna tambayan Mutum ne, Kuma wlh saikaje yola nan saboda haka kazauna cikin shiri nan Da wata biyu zamu tafi , yana kainan yakashe wayarsa kit!!!</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar kam ranshi yabaci fadi yakeyi Don me za'ai posting dinsa wannan garin daya tsana,awani gefen Kuma yafijin haushi Delter boy *nikam nace Toh" aibashi yace ai posting dinka can ba*</p><p><br /></p><p>Cikin bacin rai Abdul-jabbar yajuya yakoma cikin gida, don "ayanda yakejin bacin rai bazaya "iya driving ba,</p><p>Mama kam gaban tane yafadi saka makon gani shi datayi a hargitse, saboda yanzu batason abinda zaya bata masa rai, shiyasa ma take taka tsantsan DA abinda "Doctor yace',</p><p> don bata son tarasa Dan tilon DANTA</p><p><br /></p><p>Da sauri tace meya faru? cikin bacin rai yace mama wai "arasa inda za'ai posting Dina sai YOLA? "Ajiyar zuciya tayi "aranta tace Masha'allah Anzo gurin, lokacin Dana kejira yazo kenan?</p><p>Kallon sa tayi tareda cewa zonan,</p><p>"Ahankali yazo kusa Da "ita yazauna tareda kwantar Da kansa saman cinyar ta,domin yanzu ya sangarce dayin haka, yayin "ita Kuma saita Dora hannun ta saman kanshi, tana shafa lallausan sumanshi irin na fulanin asali,</p><p><br /></p><p>tace kwantar DA hankalin ka, aiko" bakaje Adamawa Dan kowa ba kaje Dan Dan'uwana, KO" kamanta dashi' ne?, yace "a ah tace Saboda haka kadaina bata ranka kafa Doctor yace ba'asan kana bata ranka, Saboda bacin ranka tashin ciwon kan Kuma kaga ciwon ka,' ciwone mai hatsari tashin sa komai Na iya faruwa, </p><p><br /></p><p>Wanda tasanadin haka "Ana "iyarasa ran Mutum KO" kana san' narasa kane?, da sauri yace a ah tace toh" kadai bata ranka kaji KO"? yace toh" saboda haka kar kadamu kataje kayi "aikinka, kawai kaji ko"?</p><p><br /></p><p> yace toh" Mama "amma dai gaskiya "idan naje "iyakata barikin daza'a "ajiyemu (nasojoji) kawai, tace "ah baza katafi gurin "Mado na ba? shi kadai nefa dan'uwana, "a duniya,</p><p><br /></p><p> yace toh" gurin sa"kawai zanje ni' baruwana dakowa, tunda basa sanki' toh nima banasan su" ,yakara she maganar Cikin jin haushi, tace "ah suna sona mana "Hajiya tana sona' "Baba genr Da "Baba engr Da su Adda "Uwa duk suna" sona',</p><p><br /></p><p> yanajin tana tafadan sunayen mutane "amma baiji tafadi sunan "Baban sa da na wannan "Adda Aina'u ba, wato haka yana nufin sune mutanan dasuka fi kuntata mata arayuwa kenan ko?, Mtsww yaja tsaki, "ahankali shiyasa yake jin haushi su" duk dacewa yanajin kaunar "Baban shi acikin zuciyarsa, Amma hakan bai hanashi jin'hau shin abinda ya "aika tawa Mama shin ba, "Ahankali ya mike tareda cewa Mama Bari natafi gidan Y Y k, tace toh" yaushe ne tafiyar naku"? </p><p>yace nan da wata biyu ne tace toh " ALLAH yakai mu Lafiya, yace Amin tareda fita</p><p> </p><p>*******************</p><p> YOLA</p><p>Wani katafare gida Na hango awata hadadde yar unguwa me suna KAREWA GRA ginin gidan upstear ne anyi mashi paint ashes and White colour,</p><p><br /></p><p>"Tana kwance awani tanfareren gado tana sanye da wani sleeping gown milk colour ce, Rigar tanada dan sirin hannun batada tsawon sosai domin KO iyakarta kwauri, Humaira kenan mutanan YOLA.</p><p><br /></p><p> A hankali tafurta sorry "yah Himu I can't forget "Him bcos l Love "him so much "where are you my special?....,</p><p>Chan kuma saita fashe da kuka me ban tausayi, sai kuma tafara surutai barkatai tankar zararriya, "acikin surutu natane take cewa "yah Himu yace waikai mayaudari ne? Ni' Kuma zuciya ta taki yarda dacewa "kaidin mayaudari, ne Amma kuma meyasa kai Mani haka? Why are you doing this to me (meyasa!!)why!! (meyasa!!)why!!! "Abdul-jabbarrrrrrr?</p><p><br /></p><p>Haka tacigaba da kuka dakuma surutai har tsawon wani lokaci, saida tayi mai'sarta tukun sannan ta mike Ahankali tanufi (toilet) bayi,</p><p><br /></p><p>Ko" a toilet dinma tana wanka tana kuka kadan kadan, "ahaka harta gama tadauro towel tafito, agaban mirror ta tsaya tana kallon kanta saida taka rema kanta kallo tukun, sannan tafara Shafa mai kamar bataso harda tagama, tabude wedrof tadauko Riga da siket na'atamfa tanada ratsi ja da fari ajinta, bayan tasane sai tayafa Dan karami mayafi fari, sannan tasa wani flat shoe fari sannan tanufi waje "A hankali take taka steps din tamkar bataso.</p><p> </p><p>Ta "kuntane yasa Umma datake falo tana kallo T.v tadaga Kai ta kalleta, </p><p><br /></p><p>Sannan tadubi agogon dake manne "afalon yanuna 1:00pm, sannan tamaida dubanta kan Humeeh data zauna kusada ita, fiska ba walwala tace Umma Ina kwana?</p><p><br /></p><p>Umma tace dayake yanzu kika tashi kam dole kice Ina kwana, kalli "agogo yanzu kafe Nawa?</p><p><br /></p><p>"A hankali ta kalla tareda dukar dakai kasa sannan tace karfe daya Na Rana,</p><p><br /></p><p>Umma tace ace" tunda kikai sallar asuba sai yanzu kike fitowa haba "Humaira, nalura dake duk kwana kin nan haka kike, wai me ke damunki ne?</p><p><br /></p><p>Me makon taba "Umma Amsar tambayar datai mata sai kawai tafashe da kuka,</p><p><br /></p><p>Umma kam baki tasaki tana kallon ta Cikin matsanancin mamaki tace a ah lafia?</p><p><br /></p><p>Cikin kuka tace "Umma nima bansan "abunda keda munaba saidai banajin dadi araina,</p><p><br /></p><p>Umma tai murmushi tace shikenan kuma Dan bakijin dadi aranki saiki zauna kina kuka?...Haba autata, matso kiji,</p><p><br /></p><p> "A hankali Humeeh tamatsa tareda kwantar da kanta akafadar "Umma,</p><p>Umma tasa hannu tana Shafa bayanta tace' idan Mutum yatsici kamshi Cikin wani yanayi dabai sabajiba toh" addu'a yakama tayayi ba kuka ba habah,sai kace ba matar "Malam?... ba tafadi tana murmushi.</p><p><br /></p><p> itama Humeeh murmushi, tayi tareda turo baki tace toh" Umma "ai "inayi, tace yauwa toh kikara "DA SANNU" komai zaiyi dai dai ne kinjiko? tace Toh" Umma Ina "Abba Na?..., tace Abbanki kam tundazu yafita tunda yayi zaman jiranki baki fitoba, baki ta turo kadan tace toh" Umma shine baki tadani ba?.... baki Umma ta tabe tareda cewa taya Zan tadake" bayan 'kinsan "Abbanki yace "adaina tadake idan kina bacci, abari harsai kin tashi dakanki " Saboda ciwon Kain nan naki nafama, murmushi tayi tareda cewa toh Umma yaushe yace zai dawo?,,,, tace "a ah ni bai fada Mani ba, yanzu dai kitashi kaje kicin kidebo abinci Ciki. toh" tace tareda mikewa tanufi kicin.</p><p><br /></p><p>***********</p><p>*DA MISALIN KARFE 12:30PM*</p><p>Yana zaune akatafarin office dinsa" gaba daya attention (hankali) dinsa, yanaga wani babban photo dayake manne ajikin bango, wato irin window size din nan duba guda zakai wa photo kane cewa bana yanzu bane, irin photo nan ne nada wato fari da baki, photo akalla zaikai kimani shekara ashirin da takwas zuwa talatin, macece ajikin photo tana sanye da kayan Fulani hannun reke da kwarya tana dariya,</p><p><br /></p><p>"Ahankali aka turo kofar office din aka shiga tareda sallama, duba guda zakaiwa mai sallama kagane cewa shi security guard ne (maigadi) "aciki ya "amsa sallamar ba tareda yajuya ba, yace Jabeer sonawa zanfada maka cewa bana San damuwa?....</p><p>idan wani Abune aje gurin Dept mana KO" dole saini?</p><p><br /></p><p>Ahankali Wanda akakira da Jabeer ya russuna tareda cewa, Allah ya huci zuciyar excellecy" bawani Abu bane, damai wani Mutum ne yake son ganin </p><p>ka, toh kuma "ace masa yatafi sai anjima yadawo yace "a ah shi yanzu yake san ganin ka,</p><p><br /></p><p>Cikin daga murya yace wanene shi?...., Jabeer yace "eh toh ranka yadake bansan shi ba,</p><p>Saidai yace "ace Alh Mahmoud wai idan baka gane ba "ace maka MADO n! da </p><p>sauri yajuyo yace *what*?... (Meh) MADO kace yace?...</p><p><br /></p><p> Jabeer cikin jin tsoro yace "eh ranka yadade haka yace,'</p><p>Da sauri yace OK" jeka shigo dashi yanzun nan, da sauri Jabeer yace toh" tareda fita,</p><p><br /></p><p>"A hankali aka tura kafar Da sallama aka shiga, ya'amsa sallama tareda zuba masa idanu shima Wanda yashiga kallon sa yake, Ciki sanyi murya yace Mahmoud Ashe Zan sake gani. Ka?... wato hankan yana nufi "DA SANNU" ALLAH zaya baiya nar mun da A'ISHA ta kamar yanda ALLAH ya baiyanar dakai,</p><p><br /></p><p>"A Hankali Yace kana nufin kace mani har yanzu ba' asan inda Adda A'isha Na take ba kenan?....</p><p> Cikin sanyin murya yace have a sit first, bamusu yasamu kujera guda ya zauna, yana duban sa Wanda shidin ma duban nasayeke, </p><p>A hankali excellancy</p><p>Yace?......</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐LUFHA CE💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page131-35</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*®PEN WRITERS ASSOCIATION*</p><p><br /></p><p>*PEN:THE STRONGEST WEAPON*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>*only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mene ne yasa tun bayan, da kadawo "aka fada maka abinda yafaru tsakanin Nada "A'isha shine ka tafi, tsawon shekaru masu yawa baka dawowa ba sai yau,</p><p><br /></p><p> "Anya Mahamud abinda kayi ka kyauta mana kenan,?...kako San "irin tashin hankali da "aka shiga lokaci da "aka nemeka ba'agan kaba?...., muna Cikin jima min rashin A'isha sai Kai kuma katafi, Shin meyasa baka yarda da kaddara ba?.. meyasa bakayi tunani cewa duk abinda yasami bawa da sanin UBANGIJI ba?..., Mahmoud ba baka kyauta ba, Sam, "ahankali yadukar da kai cikin nadama, yace kayi hakuri Hamman Soja, nazauna nayi tunani nage cewa haka danayi sam kyauta ba, shiyasa nakasa tunkarar "Baba gen Da "Hajiya domin "Ina matukar jin kunyarsu, </p><p><br /></p><p>wani "irin kaya tattace murmushi yayi yace tsawon shekaru masu yawa, nake san naji wannan "sunan musamman daga bakin wacce "tasa mun sunan' Amma banji ba saiyau, Hmmmm...</p><p><br /></p><p> ya ALLAH Kaine masani abinda yake boye DA baiyane ya UBANGIJINMU "ina rokonka' ka" banyanar mana da wannan baiwa taka "A'isha, tareda abida ta Haifa,"ahankali yace Ameen tareda kwantawa sosai a "irin kujerar nan mai juyawa, idanu yarufe tareda.....jin wani irin kauranar ta yana ratsashi.</p><p><br /></p><p> *TUNA BAYA*</p><p>***********""""********</p><p>"Tun Lokacin da Hamman Soja sukai magana da A'isha bai saike kiran taba, "asalima bai dawo gidan ba, saida yayi wata daya sannan yadawo kuma bai isake A'isha agidan ba wani abin mamaki kuma shine Sam baidamu ba, don "a tunanin sa' gida taje domin yasan batada gurin zuwa daya wuce can, </p><p><br /></p><p>" Tunda A'isha tabar gidan "Aina'u takecin karanta babu babbaka,gida yazama Nata sai yadda taso takeyi KO" dayake tace dama gidanta ne', "akacin Amanarta' Dan haka nema yasa taci alwashin cewa duk Wanda yashiga hurumin ta toh" "DA SANNU" zata fitarda dashi,</p><p><br /></p><p>********</p><p>"A bangaran Hajiya kam hankalin ta yafara tashi,Saboda takira telephone din gidan su A'isha saidai Aina'u ce" ke' dagawa, kuma idan ta tambaye ta "Ina "A'isha sai tace mata "aitana bacci,</p><p>toh" itakuma Hajiya Saboda ganin tana dauke da juna biyu</p><p>Shiyasa bata cewa "atashe da "ita toh ganin cewa cikin ta yashiga wata Na biyu, </p><p><br /></p><p>ya kamata tafara zuwa "ana dubata "itada "abinda ke ciki ta, saidan kuma da gabaya "idan ta kira telephone din ba'a dauka, toh shine kuma "abin yafara bata tsoro, gashi shima Magajin kota kira shi bata sabu.</p><p><br /></p><p>Tana zaune afalo tana tunanin A'isha, sai ga Hamman Soja yashiga da sallama, ajiyar zuciya tayi tareda amsa sallama saida yazauna nesa da'ita kadan sannan yagaida ita, bayan ta amsa sai take tambayar sa ya'u shi yadawo?...</p><p><br /></p><p>yace dazu, tace yasu A'isha da Aina'u ?.... yai shuerun sannan yace lafiya lau, nan dai tafar yimasa Malabar A'isha har tana cewa yaka mata </p><p>tafara zuwa "ana </p><p>dubata "inafata dai cikin baya bata" wahala sosai, kasan cikin fari wani saiyai tabashi matsala Saboda rashin sabo,</p><p><br /></p><p>shikam Hamman Soja gaban sane yake faduwa, saka makon jin abinda Hajiya take fadi, "ahankali yadago dakai yace batana nan ba?.. cikin rashin fahimar abinda yake nufi, tace wakenan fa?...cikin daure fuska yace ita Aishan mana gaskiya Hajiya A'isha bata kyauta Mani ba ni Sam basan haka take ba,</p><p><br /></p><p>Da sauri tace me "A'isha tayi maka sannan Kuma tana "Ina,?... Don niba tazo nan ba,asalima rabona da ita tunda taje asibiti Na dubata nace tanada juna biyu, Kuma nakira telephone din gidan Kuma sai "Aina'u ce ke dau sai tace mun tana bacci</p><p>nan data fada mashi, </p><p><br /></p><p>Mtsww yaja tsaki yace yafi "mata dama nace", karta kuskura nadawo Na isaketa agidan nan,</p><p>Da sauri Hajiya ta mike tareda cewa me kake nufi da hakan?... Cikin bacin rai Yace Hajiya wannan cikin dayake jikin Aisha banawa bane', alima ni bazan tabaq haihuwa ba tunda nasamu matsala lokacin, danai hatsari saboda haka shiyasa nace taje tanemi wan...</p><p><br /></p><p>Da sauri Hajiya tadafe kirji tareda cewa Na shiga uku ni FATIMA, kace Ciki dake jikin A'isha banaka bane toh" nawaye?.... sannan Kuma bazaka taba haihuwa ba meyasa meka,?....</p><p>Yace "eh sabo...maganar ta tsaya saka makon gani Hajiya tafadi Sumammiya...</p><p><br /></p><p> Da gudu Baba gen ya karasa gurinta'wanda dama tuni yafito daga daki yana tsaye yana sauraran su, daga kanta Baba gen yayi tadora akafar shi yayinda yakata fadin Subhanallahi, Hajiya gabada hankalin sa yatashi ganin KO" motsi batayi,</p><p><br /></p><p>Da sauri Hamman Soja zaya gurinta,wani mahaukacin tsawa Baba gen yadaka masa, tareda cewa kana zuwa gurin nan zanyi shooting din ka Da wanna bindigan najikin ka,' (nace tab lallai ran tsohon soja ya baci) yace zaka bani ruwa KO sai nayi mugun Saba maka, da saurin Hamman Soja yadauko ruwa, baba gen ya yayyafa mata, wani irin ajiyar zuciya tayi tareda bude idanun, da sauri ta tashi ta dubi Baba gen cikin gigita,</p><p><br /></p><p> Tace general mafarki nakeyi KO" da gaske ne abinda yaron nan yafada?... Cikin bacin rai tareda duban Hamman Soja Wanda ya dukar da Kai kasa, yace ba mafarki kikeyi ba Docter yakori matarsa daga gidan shi, Saboda yana zargin cewa cikin jikinta bana shiba ne, saboda wai baza taba haihuwa ba,</p><p><br /></p><p>Cikin daka tsawa Baba gen yace' Dan Ubanka,' waye yace maka bazaka taba haihuwa ba?... </p><p>Da saurin yace naje gurin Likita har sau uku, shine yafada min,Hajiya kam kuka tasaki mai ban tausayi, cikin tashin hakali take fadi shikenan yanzu baza ka taba haihuwa ba....?</p><p>yace "eh Baba ger Yace toh Maine ne hujjar ka?.. yace takardun suna nan, </p><p>Shuru Baba gen yayi yana nazari, </p><p><br /></p><p> Cikin kuka natashin hankali tace toh yanzu Ina A'isha ta tafi,?....yace niban saniba, tace oh" ni Fatima KO Ina A'isha ta shi ga?..</p><p><br /></p><p>oho yafada aran shi koma dai inataje ita' tasani, nikam bazan iya zama Da itaba tana cin amanata ba, </p><p><br /></p><p>Cikin kuka Hajiya tace "a yadda nayima A'isha tarbiyya Sam bazata iya aikata wanna mummunan Aikin ba, haba Magaji zina da aure fa kake nufi?...., general nikam banyarda da "abinda wannan yaron yafada ba, kilama karya yakeyi,</p><p><br /></p><p>Da sauriyace' ba karya nakeyi ba takardun suna nan, Baba gen yace' jeka dauko Mani takardu nagani toh" yace tareda mikewa yafita.</p><p><br /></p><p>Cikin minti talatin sai gashi yadawo koda Baba gen yaduba takardun, jikinsa yai sanyi yayinda wani irin zufa ke karyo masa,</p><p> Da sauri Hajiya ta karba itama taduba, wani sabon kuka tasaki tana fadin,</p><p><br /></p><p> shikenan mu kuma haka ALLAH ya kaddara mana, Kai guda muka Haifa Kai kuma bazaka taba haihuwa ba ikon sai ALLAH, toh meyasa ka kori A'isha meyasa baka kawo Mani ita ba nikam, Dana taya ta rungumar kaddara,</p><p> Koda yake dama kila kana Neman hayyar dazaya rabuda ita, haka Hajiya taciga da fada tareda surutai, Wanda kai daga jikasan bata Cikin hayyacinta,</p><p>Yayin DA Baba gen meta faman lallashinta Wanda shima karfin hali kawai yake.</p><p><br /></p><p>***************</p><p>Cikin lokacin kankani magana takarade family cewa "A'isha tabace' sannan Kuma Hamman Soja bazaya taba haihuwa ba,</p><p><br /></p><p> hankalin zuriyan Alh Ahmed Dan kwangila yatashi sosai, dajin cewa Magajin family baya haihuba, Cikin lokaci kankani aka baza Neman A'isha tareda abinda ke Cikin ta, saida kome kama Da ita basu gani ba balle ita kanta toh" ballanta Na su saran ganin abinda ke Cikin ta,</p><p><br /></p><p>Tun "ana saran ganin A'isha har "aka fidda rai, yayinda kwana ki suka tafi tareda satittika da watan'ni shekaru, sunja Sosai yayinda Hamman Soja yaci gabada gudarar Da "aikin sa, ganin shekaru sun tafi sunja amma har awannan lokaci, Hamman Soja da Aina'u shuru ba haihuwar, saboda haka nan sai su Baba gen suka yanke shawara cewa" Hamman Soja yasaki Aina'u sai ta "auri wani KO" ALLAH yasa tasamu rabonta, tunda shi bazai haihuwa duk dacewa basu debe tsammani ba daga RAHAMAR ungijiba "aikam Aina'u ta tuma kasa tace ita "abarta da mijinta zata zauna dashi "a haka, don haka sai "aka kyale ta, saidai Kuma hakan yabata daman yin abidan duk tagadama takeyi, sannan duk "abinda tace dashi Hamman Soja yake "aiki ,</p><p><br /></p><p>itakam Hajiya idanu tasa musu yanzu tsakanin tada Hamman Soja sai gaisuwa, yayin kullum Addu'a takeyi ALLAH ya tsare A'isha aduk inda take tareda abinda ke jikinta, don tanaji ajikin ta cewa wannan cikin najikin Aisha Na halal ne yayinda shikuma </p><p>Hamman Soja take rokon ALLAH ya yaye masa "abinda keda mashi, domin tabbas kwai wani abun da'akai masa wanda yake damusa Amma KO" meyene "DA SANNU" Allah zaibaiya narai dashi,</p><p><br /></p><p>Kwatsam Aina'u tace Hamman Soja ya ajiye aiki wai tunda yasamu kudi yafara business, aikam baiyi shawara dakowa ba ya ajiye aiki, yafa business, ranada Baba gen yaji yaimasa fada sosai Baba engr yace' ya kyale shi dama shi yace yanasan Soja toh Dan yanzu yace bayayi aiba dole,</p><p><br /></p><p>Don haka sai yaci gabada da Business dinsa din sa, kwatsam, wata rana sai ya hadu dawata yarinya yar wani tsohon kwamishi Na ilimi Na nan Yola, sunanta Maryam yanu yansan ta DA aure itama haka, yafada mata baya haihuwa tace "eh zata aure sa haka saboda tana son shi,</p><p><br /></p><p>"Aiko ba "adauki lokaci ba "akai bikin duk da rashin sanda Aina'u tanuna, wanda saida aka Kai ruwa Rana tukun na, watan Amarya Maryam biya da tarewa sai tafara rashin lafiya zazzabi sosai a lokacin tuni Hajiya tadaina aiki, don haka Hamman Soja ya dauki Maryam dakan shi yakata asibiti, bayan Doctor ya dubata tareda yan tambayoyi ya tabbatar musu da cewa Maryam tana dauke da Ciki Na wata daya da sari biyu,</p><p><br /></p><p> Da sauri Hamman Soja yace Sam Maryam batada Ciki Doctor, ya kalleni shi yace haba yallabai kamar yabata daciki?... nifa nadu bata, Kuma kaganni Na Kai kusan shekaru goma sha biyar Ina aikin balle kace KO" ban iyaba ne </p><p><br /></p><p>itakam Maryam hankalin ta yatashi, yayinda Hamman Soja ya kurawa Doctor idanu tabbas baza taba mantawa da wanannan fuskaba, yace eh haka ne "ainata bazuwa gurin ka shekarun baya dasuka wuce, kadubani' Ka kuma tabbatar Mani dacewa bazan Baba haihuwa ba, ka Kuma hadani da wasu Doctors suka dubani suma Kuma sunka tabbatar Mani dacewa bazan haihuwa, toh yanzu kuma ya'akai matata tasamu ciki?...,</p><p><br /></p><p>Wani irin faduwa gaban Doctor yayi yayinda yaji zufana karyo masa "ahankali yace?...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufha ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page141-145</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*®PEN WRITERS ASSOCIATION*</p><p><br /></p><p>*PEN:THE STRONGEST WEAPON*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p> _only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Lokacin danayi wani zazzabi tareda wani irin ciwon ciki mai tsanani, ga kuma jini yana tazuba mani saina shirya natafi asibiti saboda naga Likita, </p><p><br /></p><p>don "atunani Na ciki nasamu yake rawa, don haka saidai kashhh Ashe ba haka bane, bayan likita yadubani don harda sikainin yace' najena yi bayan nakwo masa takardan sikaini din,</p><p><br /></p><p>Sai yace Mani banida ciki "asalima mahaifata talalaci tayi guntu-guntu bazata iya daukar daba, saka makon sham magunguna barka tai dankeyi,</p><p><br /></p><p>Yanzu haka masai yayi Mani aiki yacire domin batada amfani, "idan ba "acire ta ba toh" zantayin zubar jini ne, hankali Na yatashi sosai sai nace masa toh" zanje nayi shawara da mijina zandawo yace Mani toh", nikuma atunani Na bazan dawoba,</p><p><br /></p><p>Sai abun mamaki tundaga wannan lokacin jini yake tazubo mani sosai, dole muka tafi nida gwaggo don "acire Mani mahaifa, tunda duk abinda yake faruwa ba wanda yasani dagani sai ita, Kuma "a lokacin Hamman Magaji yana can gurin aiki sa, don haka mukai tayin komai batareda yasani ba,</p><p><br /></p><p>Bayan Doctor yacire mani mahaifa yace Mani shikenan banza taba haihuwa ba, muka dawo gida toh" tundaga ran muka fara shirya yadda zamuyi, tunda "a lokacin ansaka ranan auren Hamman Magaji da A'isha, bamu samu mafitaba saida "ana gobe sauri aure.</p><p><br /></p><p>Sai muka shirya muka tafi Wani kauye, mukaje gurin wani mugun boka bayan mun fada masa, bukatar mu, yace karmu damu dai mubiya kudin aiki, basai anbarta da Lafiya sannan zata samu Cikin ta haihuba.</p><p><br /></p><p>Toh shine ran da'aka kaita akuma dawo Da ita ba Lafiya, Wanda tadauki tsawon lokacin tana fama darashin Lafiya, bayan taji sauki ta tare saina fara tunanin yadda Zan hanata samun Cikin, nadauki alwashin cewa tunda bazan haihuba toh" itama bazan taba Bari tahaihuba,</p><p><br /></p><p>Nayi ta tunani yadda zansamu mafita amma ban samu ba, watan "A'isha biyu da tareda sai nafahimci cewa tasamu ciki, saboda haka shine nai amfani da lokacin da Hamman Magaji yai hatsari, sai nacewa Hamman Magaji yakamata yaje yafara ganin Doctor saboda matsalan rashin haihuwar,</p><p><br /></p><p> Wani abin mamaki shine baiyi mani musuba, sai yace mani toh" yauwa zayaje amma saita fara biyawa tagida tukun Na sannan yaje asibiti, yana fita, sai nikuma nashirya nadauki bindigar Hamman Magaji naje guri Doctor nace masa baya idan yazo tafada masa cewa bazaya taba haihuwa ba,</p><p><br /></p><p> Toh Kuma bayan nayi nasara yakori A'isha, na kuma jegurin boka nace yayimata asirin da bazata dawo ba, sannan Kuma muka ce mashi muna San yaima Hamman Magaji asirin dazamu mallakesa,</p><p><br /></p><p>Bayan yayi mani aiki sai yace toh" saidai muddun muka Bari Hamman Magaji, yai aure har yayi tarayya da matar har tasamu ciki, toh" daganan asirin zaya karye, mukace' ba matsala mu'a tunanin mu tunda baya haihuwa aiba zaya taba yin aure ba,</p><p><br /></p><p>Kwatsam sai naji Hamman Magaji zaiyi aure, naso nahana amma hankan baiyu ba, tun bayan DA Maryam ta tare Saina fara tunanin, yadda Zan hanata samun ciki, Ashe bansani ba tuni tasamu ciki.</p><p><br /></p><p>Wannan shine abinda na'aikata don Allah Baba engr kuyi hakuri, kace kar Hamman Magaji yasakeni' son shine yasa na'aikata haka saboda bana San wata ta haihu dashi yazo yana fifitata akaina, takarshe maganar tada sheshshekar kuka.</p><p><br /></p><p>Hamman Soja ya harareta tareda cewa karya ki ke' munafuka bakya sona, asalima kedin makiyiya tace Kuma Saki "ainariga nayi shi, (kasan cewa lokackn dayai sakin batasani ba)saboda ni bazan Kara zama da azzaluma macuciya irin ki ba,</p><p><br /></p><p>yayinda falon yakaure da surutu yan'iwa sai Allah wadai da halin irin ta sukeyi, dama dayansu sunajin haushin ta tunda kirikiri saita hana Hamman Magaji yai musu Alkhairi,</p><p>Baba general da Hajiya Binta kam Kala basuce ba,</p><p><br /></p><p> Baba engr ne yace ya isa haka</p><p>Cikin bacin rai yafara fada sosai, yace nasan duk abinda Aina'u takeyi dasa hannun ki, Rakiya Kuma baki kyautawa kanki ba "ace yarki zakisa "amugun hanya da za'a cuci Dan dan'uwanki, tareda baiwar Allah "A'isha mai tayi muku haka dakuka rabata da mijinta, kunata kulla mugun aiki bawanda yasani toh" aigashi nan dayake batada Hakkiku "DA SANNU" Allah ya bayyana Ku,</p><p><br /></p><p>Cikin bacin rai Baba general yace aidama duk abinda Mutum yake aikata wa aboye sharri ko hairan toh" fa DA SANN wata rana Allah zaya baiyya nashi mutane kowa yaganshi, ALLAH ya shirya Ku, sannan yatashi bar falon.</p><p><br /></p><p>Baba engr yabi bayan shida kallo tabbas yasan ran dan'uwansa ya baci, ahankali itama Hajiya tabi bayan mijinta,</p><p><br /></p><p> Sai falon yaitsit, shima Baba engr ransa yabaci sosai, sai yadubi gwaggo Rakiya data dukar dakai kasa, yace Rakiya ki dauki Aina'u kutafin gida domin Magaji yariga yasake ta Saki biyu,</p><p><br /></p><p> zatayi magana yace banasan jinkomai, kawai kidauke ta kutafi duk shawarar damuka yanke zanfada maki, yace ku kuma kowa wacce ta tashi tatafi gida saboda haka sai ko" yatafi gida,</p><p><br /></p><p>************* </p><p>Saida Aina'u ta kai wata viyar sannan takoma gidan Hamman Magaji, koshi saida Baba engr yanuna mashi bacin rai tukun, Amma dayace shi Sam bazaya baida "ita ba,</p><p><br /></p><p>Kulawa sosai Hamman Soja yakeba Maryam, har Cikin ta ya'isa haihuwa ta haifi diya Mace, ranan suna taci suna Hajiya Saratu matar Baba engr, fadin shagalin da'akayi ranan suna ban baki ne saidai mai karatu yasani shagali 'akayi bana wasa ba,</p><p><br /></p><p>A haka yaci gabada kulada Maryam da AMA haka suke kiran ta, tare Kuma da son A'isha Wanda yakasa boyeshi "agaban kowa nuna begenta yake, Wanda har hakan yafara damun Maryam, musamman dataga duk yabi falon su yaman'na photo A'isha saboda haka sai tafara nuna kishi, </p><p><br /></p><p>Yayinda shi kuma tuni yaja mata burki dacewa tabari, baiyi matar dazata fi A'isha azuciyar shi ba, tasani cewa Aina'u hadasu akayi A'isha kuwa itace macen daya fara so", saboda haka "amatsayin tada ban'ne "a zuciyar shi,</p><p><br /></p><p>Saboda haka idan har tana son farin Cikin sa toh" taso A'isha, batada yadda zatayi don haka dole tabi "abinda yace' amma kasan zuciyar ta tanajin haushi A'isha,</p><p><br /></p><p>Amah nada shekara daya Maryam tasake haihuwar diya Mace, akasa mata A'isha Wanda Hajiya ce tace asa mata A'ishan ta, "aikam Hamman Magaji kamar yayi hauka don farinciki, yayinda yadauki so yadora akan Little esha wacce yake kirada Honey, itama shekarar tadaya Maryam tasake haihuwar diya Mace, sai "akasa mata Fatima wato sunan Hajiya kenan sai suna kiranta Zarah mama</p><p><br /></p><p>Toh" Kuma tundaga kan Zarah mama Hajiya Maryam bata sake haihuwa ba, saboda haka sai suka cigaba da kulada yaransu, tareda yi musu tarbiyya mai kyau,</p><p><br /></p><p>Aina'u kam da'ita da banza agidan Hamman Magaji duk daya, kilama har gara banza yafita daraja, domin kuwa kwata-kwata yafita harkarta baya shiga sha'anin ta,</p><p><br /></p><p> bakin ciki ya isheta don haka sai ta iske shi daki tace itaka tagaji da'bakin cikin dayake mata saboda haka ya </p><p>bata takardan Saki,</p><p>ba musu ya rubuta Saki daya yabata,</p><p>yace gashi nan rabuwarki Dani shine Abu mafi sauki garayuwai ki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> shukaru sunja arziki ya bunkasa ga Hamman Magaji, yayinda kaunar A'isha ke karuwa "azuciyar shi saboda haka ya dukufa Addu'a Allah ya baiyyana A'isha tareda abinda tahaifa.</p><p><br /></p><p>********"******</p><p>Kamar wasa,Abokan Hamman Magaji sukace yafito "takarar gwamna, aikam yafito, da lokacin zabe yayi Cikin sa'a yalashe zabe "inda yahaye kujerar gwamnan jahar Adamawa yola, yayinda yazama gwamna mai adalci wannan kenan.</p><p><br /></p><p>A hankali ya sauke ajiyar zuciya tareda bude idanun shi ya zubawa Alh Mahamud, yace?.... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat Ce 💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page136-140</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>edited by Zainuddeen zain</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*®PEN WRITERS ASSOCIATION*</p><p><br /></p><p>*PEN:THE STRONGEST WEAPON*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pe writers_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"eh tabbas "anyi haka shekarun baya dasuka wuce nafada maka, saidai kasani' nima bada San raina na rubuta maka, cewa bazaka taba haihuwa ba, tilasta Mani "akayi, da sauri Hamman Soja yace ban fahimce kaba waye ya tilasta maka ka' rubuta Mani bazan taba haihuwa ba?... yafadi haka yayinda yakejin wani irin matsananci faduwar gaba,</p><p><br /></p><p>Doctor yace shekurun baya dasuka wuce, "Ina zaune "a office din Na sai ga wata tashigo bako sallama, saidai kawai tanuna Mani bindiga, mamaki yakamani tareda tsoro Cikin karfin hali nace baiwar Allah Lafiya?...</p><p><br /></p><p>tace Lafiya lau "aiki takeso nayi "mata "idan kuma bazanyi ba, toh" zata kasheni tafita batareda kowa yasani ba, Dan yanzu ma ba wanda yaga sanda tashigo,</p><p><br /></p><p>"Idan Kuma kana ganin, bazan iya kashe' kaba toh" "aizan "iya kulla maka sharrin da Harka mutu bazaka manta dashiba,</p><p><br /></p><p> Tabbas zata iya "aikata abinda tafada domin naga fuskarta" ba "imani, don haka Cikin faduwar gaba nace wani irin Aiki kenan fa?... </p><p><br /></p><p> Sai tace Mani wani mutun" zayazo nadu bashi,' "idan nadu bashi nafada masa cewa bazaya taba haihuwa ba, sannan Kuma nayi masa" hayyar zuwa gurin wasu "Doctor's din "idan yaje "suma sufada masa cewa bazaya taba haihuwa ba,</p><p> </p><p>Banida yadda zanyi don haka sai nace mata toh" sannan tafita tareda cewa sai nado, batafi minti talatin da fitaba sai gaka kashe go,</p><p><br /></p><p>Don Allah Kayi' hakuri wallah koda nadubaka, lafiyar ka kalau ba abida yasame ka, saidai narasa abida yasa wannan matar tace nafada maka haka kagafarc.....Hamman Soja ne yakatse shi ta hanyar daga masa hannun, </p><p><br /></p><p>gaba daya jikin sa rawayake yayinda yakejin kafafunshi kamar baza su'iya daukar saba, don haka sai yadafa table din Doctor tareda dukar da kashi kasa, domin kuwa wani irin nauyi yaji yai masa,Wanda tunda yake bai tabajin nauyi irin wannan ba,</p><p><br /></p><p>Cikin tashin hankali yadaga Kai ya watsawa ma Doctor jajayan idanun sa, yace kana nufin "a wannan lokaci duk macen danayi tarayya da ita zata iya samun ciki?...., Doctor yace sosa kuwa tunda lafiyar ka kalau, saidai idan itace batada Lafiya,</p><p><br /></p><p>Wani irin Kara Hamman Soja yayi tareda faduwa kasa Sumamme, ihu Maryam tayi Cikin matsananci tashin hankali, taduka tana jijjiga shi tana kiran sunan shi Amma baitashi ba, hannun ta Dora akai ta tace Na shiga uku shikenan Doctor ka kashe Mani mijina,</p><p><br /></p><p>Doctor da shima jikinsa rawa yake da sauri, yazo ya taba Hamman Soja yaji bai mutuba sumadai yayi, yace kiyi hakuri ba mutuwa yayi ba sumace Ina zuwa ruwa ya dauko, yayyafa mashi, can saiya farfado da sauri ya mike tareda rike kwalar rigan Doctor, Cikin tashi hakali yace yasunan matar?...</p><p><br /></p><p>Cikin matsananci tsoro yace bansan suna ta ba, Amma dai bazan taba matawa Da kaman'nin ta, Farace tanada kina ba sann... Hamman Soja ne yakatse shi da cewa nagode kasan cewar yagane wadda yake nufi, sannan yakama hannun Maryam wacce keta faman kuka suka fita da sauri daga office din.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tun bayan fitar Hamman Soja DA Maryam, hankali Aina'u yatashi don haka saita kasa zaune takasa tsaye, sai faman safa DA marwa takeyi "atsakiyar falo, sai tunanin take tareda tambayar kanta "Ina Hamman Soja sukaje shida Maryam,</p><p>Kasan cewar tana bacci suka tafi,</p><p> </p><p> tana Cikin wannan halin sai kawai taji sallama Maryam, dauri tajuya tana kallon su gabanta ne yafadi saka makon gani Hamman Soja, yanufe ta fuskashi ba'an'nuri don haka da sauri tajuya zata nufi daki,yayinda Hamman Soja yafinciko tada karfi ya yarda ita kasa timmm sai kace kayan wanki sannan yajata kiiiii yanufi dakinshi da ita,</p><p><br /></p><p>wata irin katuwar bulala yadauko irin tasuce ta SOJOJi, aikam tuni idanun Aina'u suka fito waje saboda tsoro zatai magana kenan, saitaji saukar bulala dukan ta yake DA iyakacin karfi sa' "itako sai ihu takeyi tana fadin menayi maka?....Magaji, yana dukanta yana fadin "au tambaya ta kike abinda kikai Mani ko?....Hmmm "DA SANNU" idan jikinki yaci duka Zaki ba kanki amsar tambayar ki',</p><p><br /></p><p>Maryam kam tana tsaye abakin kofar dakin sai kuka takeyi, takasa shiga kasan cewar itakam tana bala'in tsoron bulala, Amma dai sai faman bashi hakuri takeyi, cikin tsoro tace Ahmed kar kayi kisan Kai fa! yace Maryam "aiyau rai kadan zan ragewa yar iska, "idan Kuma nayi Na sarar rabata daran' nata toh" shikenan ta huna, nima nahuta domin idan muka cigaba da rayuwa tare toh" tabbas zan dauwama Cikin bakin Cikin abinda ta'aikata Mani yayinda, ita Kuma zata gwanmaci gara muguwar ta da bakin cikin dazan guma mata arayuwa, duk wannan maganar yanayin tane ya dukan Aina'u wadda tuni tagala baita, jikinta kuwa duk yafarfashe abu ga farar mace harjini nafita,</p><p><br /></p><p>Itakam Maryam tuni takara tsorata ganin jini yafita ajikin Aina'u, hakan ne yasa take ganin da gaske Hamman Soja kisan Kai zayayi, </p><p><br /></p><p>don haka da sauri taje takira layin gidan Baba engr ciki sa'a shida kansa' Baba engr yada wayar, aikam tana kuka tana fada masa abinda kefaruwa, Cikin tashin hankali yace toh" gashi nan zuwa shida Hajiya Saratu matar shi,</p><p><br /></p><p>Cikin abinda baifi miti talatin ba suka iso gidan, dai-dai lokacin da Hamman Soja yace nasake ki Saki daya Aina'u Nasake ki Saki biyu nas.... DA sauri Baba engr yace Kul! kana karasa fada sainayi mummunan Saba maka, ashe bakada hankali Magaji?.....,</p><p><br /></p><p>Da sauri yasaki bulalan yaje yafada jikin Baba engr yasaki wani irin kuka maiban tausayi, kuka yakeyi sai kace karamin yaro "ahankali Baba engr ya zauna dashi, yayinda yake Shafa masa baya yana cewa ya'isa haka.</p><p><br /></p><p>Yace haba Magaji "idan rai yabaci "aibai kamata hankali ya gushe ba, kanasan kayi kisan kaine?.... sannan ya kalli Hajiya Saratu yace dake DA Maryam ku kama Aina'u kuje mukai ta asibiti, tace toh" dakyar suka iyafita da ita saboda nauyi tunda KO" motsi batayi, </p><p><br /></p><p>Sanna ya dubi Hamman Soja yace Magaji meya faru ne haka?...Cikin kuka yace Baba Aina'u ta cuce rayuwa ta' ta ha'inceni taraba nida matata A'isha, don haka ni ba'abunda zance mata saidai Na bartada ALLAH "DA SANNU" kuma zata gane kurenta, Baba engr yace fada mun abinda tayi maka?....</p><p><br /></p><p>Nan yafada mashi abinda Doctor yafada masu, rai Baba engr sosai yace tashi mutafi bamu Hamman Soja tashi suka fita,</p><p><br /></p><p>A can asibiti Kuma da taimakon ALLAH dana likitoci Aina'u tafarar fado, yayinda Maryam taci gabada kula da ita harta jisauki Wanda bada San rain Hamman Soja haken tafaru ba, saidan tirsasawar da Baba engr yai mashi.</p><p><br /></p><p>Gaba daya family an'hadu gidan Baba gen, Baba engr yadubi Aina'u yace Aina'u menene dalilin daya sakika ce sai Doctor ya rubuta wa Magaji cewa bazaya taba haihuwa?...</p><p>Cikin kukan nadama tace.?..</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page146-150</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*</p><p><br /></p><p>*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>~Don Allah kuyi hakuri narashin ganin posting Dina akan lokaci~ </p><p><br /></p><p><br /></p><p>_*only exquisite and whizkid writers are opportune to be pe writers*_ .</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mahamud "Ina son ganin A'isha tareda "abinda tahaifa narokesu" gafara saboda, nasan nine silar shigan su duk wani kunci dasuka fuskanta arayuwa, saidai kashhh! ban San "inda zangansu" ba, don ALLAH katayani Addu'a Allah ya bayyana su "a duk "inda suke Afadin duniya nan, wlh Mahamud "Ina matukar bukatar su" kusada ni.</p><p><br /></p><p>A" hankali yece Hamman Soja ka kwantar DA hankalin Ka, insha'Allahu " DA SANNU " ALLAH zaya baiyyanar dasu," kullum Addu'ar Dana keyi kenan Kuma inajin "Ajikina da yarda Allah sun kusa baiyana garemu.</p><p><br /></p><p>Yace Hmmm! Mahamud na tabka babban kuskure "Arayuwata Wanda gashin nan har yanzu "Ina Da nasani yisa, Mahamud meyasa ban saurari A'isha ba lokacin da take fadin Hamman Soja ka saurareni ba?..., meyasa bankasan ce Cikin mutane masu _"BINCIKE"_?.... ba, farin Cikina guda "idan Na tuna cewa ban furta kalmar _SAKI"_ga A'isha ba,</p><p><br /></p><p>Yace Hmmm! Mahamud kokasan cewa duk abinda yafaru dasa hannun Aina'u, Dasauri Abba Yace kamar ya?...nan yafada masa abinda yafaru, Cikin takaici </p><p>Abba yace "aikanta tayiwa,</p><p><br /></p><p>"A hakali ya sauke Ajiyar zuciya tareda Mikewa yazo kusada Shi, kafadar shi yadafa yace Kayi hakuri Mahamud nine Silar rabaka Da yar'uwarka, Wanda ta dalilin haka ne yasa katafi kabarmu tsawon shekaru, baka dawoba sai yau daka zama babban Mutum,</p><p>Yafada yana murmushi,</p><p><br /></p><p>Shima Murmushi yai yace Kai Hamman Soja, yace Allah you're a big Man nasan dai by now kanada iyali KO?...,</p><p>Yace eh inada Mata daya Asma'u" da yara biyu Baba na "Ibrahim da "Adda A'isha Yace masha'allah naji dadi da kasa A'isha Allah ya Albarkacesu"</p><p>Yace Ameen.</p><p><br /></p><p>Toh yanzu kabani Labarin bayan rabuwa, murmushi yai yace "ai lokacin dana barnan Kaduna natafi, nan dai yabashi labari "abubuwa dasuka faru dashi,"agarin Kaduna da masu" dadi da marasa dadi,</p><p><br /></p><p>Nan dai Hamman Magaji ya jajanta mashi marasa dadi, yayinda yai mashi farin Ciki ga masu dadi, yace toh" yanzu "Ina iyalin Ka suna can Kaduna nan ne?...,yace "a ah tareda su nazo saidai shi Baba Na "lbrahim yana can Abu Zaria yace ita Kuma A'isha tagama Secondary school din ta, yace madallah Ashe dai yaran Nawa Sungirma?.. Murmushi yai yace bafa wani babba bane saurin girma ne kawai _he just nineteen years go to twenty_ ita kuma A'isha _yanzu tashiga fiftieth years_ kasan yaran yanzu saikace "Ana zuba masu taki saboda saurin girma, Murmushi yai yace haka fa yanzu fa "Amah itama _fifteen years_ My "Esha Honey _fouteen_ itakuma "Zarah Mama _thiree teen_ kasan cewar basu dawani tseyarya tsakanin su" sosai, toh" kajiba toh" Allah dai yaraya manasu" yace toh Ameen , toh" yanzu "Ina su "A'isha da "Mamanta kace tare Ku kazo KO"?...., </p><p><br /></p><p>"Eh "ai gidana yana nan "a Karewa GRA watan'mu daya kenan da tarewa agidan, da sauri Yace _one month_kana garin nan Amma bakaje family House ba haba Mahamud toh' kana "Ina?...., yace "aikamar yau muka tare toh" Kuma washe gari sai natafi America kasan cewar Ina gudanar da Business "acan toh" shine fa sai jiya nadawo, yace "OK</p><p><br /></p><p>" Ashe muna tare kenan, kasan nimafa Business din nakeyi, shine fa su ALH NASIR JIMETA(abokinsa ne) sukasa nafito takarar gwamna, toh sai gashi kuma Cikin lkon ALLAH nazama Governor of Adamawa state, Abunfa</p><p> very Surpersi wai l'm a Governor Hmmm l can't believe saida nagan'ni a office din nan sannan fa nayarda.</p><p><br /></p><p> yace Masha'allah A"iba "a Mamaki Da hukunci UBANGIJI kasan Mulki nashine kuma sai wanda yagadama yake ba, Addu'armu dai shine Allah yatayaka riko ya Kuma baka lkon" yimana Adalci, yace Ameen, yakai karshen maganar dayin dariya, shima dariyar yace toh" Ameen, </p><p><br /></p><p>Sannan Ciki Zoyala yace' yanzu tashi mutafi family House, Ka karbi bulala gurin Baba general da Hajiya Kai harda Baba engr, shima sai yatsala maka nashi bulalan saboda tafiya dakayi kabar su', tsawon shekaru kaga daka can sai mutafi gidana kaga iyalina,</p><p><br /></p><p>Dai-dai lokacin da suka fita office din Hannun su rike da juna suna dariya.</p><p><br /></p><p>**********</p><p>Wani Kyakkyawan Dattijo nagani zaune "Akan lallausan kushin, yana karanta Jarinda idanusa man'ne Da _medicate glass_ Baba general kenan dottijon kirki managarci mai cikar kamala, Sallaman da'akayine yasa shi dagoda Kai,</p><p>tareda amsa sallama Cikin Matsananci Mamaki Yace Mahamud Kai ne?....Yace nine Baba.</p><p><br /></p><p>Dai-dai lokacin da naga wata kyakkyawar Dattijiyar tana saukowa daga _steps_Hajiya Binta kenan, yayi danaji tana fadin "a ah wanake gani haka kamar Mahamud ?....,</p><p><br /></p><p>"A dai-dai lokacin Da ta zauna, sukuma suka zauna "akasan kafet,</p><p>Tace general shin gizon da idanuna suka sabayi munne, kodai da gaske ne Mahamud Din'mu ne yau "agabana ?...</p><p>Murmushi Baba general yayi Yace Doctor tabbas Mahamud din'mu ne, sai kawai tafashe da kuka tace ashe zan sake ganinka Haba Mahamud me yasa kayi mana haka?...,</p><p>"Ahankali yamatso kusada ita cikin matsananci tausayita, yayinda yaji wani irin haushin kashi yaka mashi waima meyasa yatafi ya barsu?...,</p><p><br /></p><p> Sai shima yafara kukan yana cewa kuyi hakuri Hajiya</p><p>nasan ban kyauta ba, amma insha'Allahu bazan sake ba kinji?...Baba General yace "a ah Doctor farinciki zakiyi kin gansa "araye Kuma Lafiya lau, Amma bawai kixauna kina Kuka ba, "Ahankali tasa hannu tashare hawaye shima yashare nashi,</p><p><br /></p><p>Bayansu nutsu sai Kuma "a kafara gaisuwar yaushe gamo, toh" dagan nain kuma sai ya basu labari kamar yanda yaba Hamman Soja,</p><p>Baba general yace toh" _Alhamdullah_ ALLAH mungode maka, dama shi duk abida kaga yasamu BAWA toh" dama can rubutacce "Al'amarine daga ALLAH,</p><p><br /></p><p>Ya UBANGIJINMU don tsarkin Mulkinka Ka "idan har A'isha tanareye itada abinda ta haifa toh" ka baiyyana mana da dasu" kamar yanda Ka baiyyana mana Mahamud </p><p> Dukkan su suka "amsa Da Ameen.</p><p><br /></p><p>**********</p><p>Wani hadaddan folane mai dauke da kayan more rayuwa, wasu _3 beautiful flowers girls_nagani dukkan su suna sanye Cikin kayan _sports_, da "alama sun dawo daga motsa jikine. duk da cewa sunyi kama da juna domin idan kagansu zakace ko Hassana Da Husaina Da Gambo ne toh" biyu sunfi dakyar tsawon, babban Cikin su tana rike da Waya da " alama chatting takeyi, mai bimata Kuma ear piece ne makale akunnen ta tan,karamar Kuma tana t.v game, gaba daya hankalin su yatafi ga abida sukeyi, gaskiya yamma ta kyakkyawai ne sai kace yayan larabawa.</p><p><br /></p><p>Can sai karamar ta "Ajiye remote din ta mike tana tsalle tareda fadi yeeeeehhh! "Dad is back, babban ta Dan harareta tace dalla yiwa mutane shuru me karya Dad ne zaya dawo ya zu?.... Ganin suna magana ne yasa tacire earpiece din "A hankali ta kalle su tace _what's happen?...._karamar tace Dad is back, dasauri tace ur liar "Dad ne zaya dawo yanzu?...tace Allah l'm not a liar, ku tsaya kuji karar jiniya mana, "aikam tana rufe bakinta sai sukajiyo karar jiniya,</p><p><br /></p><p>Da sauri sukaje gurin _Window_dakin suka leka, dai-dai lokacin da motoci kimanin guda goma suke shigowa harabar gidan, wasuma har sunfa Rayin _parking_ "aikam Da gudu suka sheka, don suyo mashi" oyoyo har suna rigerigen shiga babban falo,</p><p><br /></p><p>Dai-dai lokacin da yashiga falon da Sallama shi, da gudu sukaje suka rungume shi suna murna sukace barkada dawowa Dad, Cikin farin yace yauwa _My lovely Daughters yakuke ?_ suka ce Lafiya lau,</p><p>Dad yau meyasa ka dawo dawuri?...</p><p>yace "Ina tareda bako ne,</p><p><br /></p><p>Shikam Abba kallon su yake cike da sha'awa "aranshi Kuma yace oh! Da yanzu wannan yaran diyan Adda A'isha ne, oh! ALLAH mai lko", gaisuwar sune takatsa mashi Zan can zucin dayake, ya Amsa fuskar shi cike da fara'.</p><p><br /></p><p>Bayan sun zauna sai Dad yace Mahamud this is my Doughters, yana Nuna su shi yace wannan itace Saratu Amah, sai Kuma A'isha My Honey esha and last born Fatima Zarah Mama, Abba yace masha'allah ALLAH yara yasu yasa musu Albarka yace Yace Ameen,</p><p><br /></p><p>Dad ya kalli _beautiful Daughters dinsa_ Yace kunsan wannan?... yanuna Abba dayake ta Murmushi, Amah tayi shuru tana tunani itama Zarah Mama haka tayi, "Itakam esha datake can makale jikin Dad kamar zata shige Cikin babban rigarsa, dayake "itadin Sarkin son jiki ce kamar Mage,</p><p><br /></p><p>"A hankali tace Dad yayi kamada Na cikin picture din can, daka ke bamu labari harma kace sunan shi Uncle Mahamud,</p><p>Dad yace yes My Honey shine, da sauri Amah tace Lah Dad Allah bangane shiba, dariya sukeyi shida Abba Dad Yace toh" shine, Yace Zarah Mama jeki kira "Mom dinku tazo yau munada babban bako agidan mu,</p><p> tace toh" tareda mikewa tanufi Ciki.</p><p><br /></p><p> </p><p> *KADUNA*</p><p>*BAYAN WATA DAYA*</p><p>**********************</p><p>Kamar koda yaushe yana zaune "a office dinsa' kanshi "aduke sai faman rubutu yake Doctor I S G kenan, A hankali Abdul-jabbar yaturo kofar yashiga bakinsa "adauke da sallama, </p><p><br /></p><p>"A hankalin yadaga Kai ya kalleshi suka hada idanu sukai wa Juna Murmushi, biron hannun shi ya'ajiye yana cewa ni wannan _patient_ din Nawa koda yaushe "amakare yake zuwa _Check up why?_ yace saboda banasan na isko kada mutane sosai dai-dai lokacin da yazauna, nasan _by this time_ karage duba _patient_</p><p><br /></p><p> Shiyasa nake zuwa wannan lokacin, Doctor I S G yace hakane fa Kuma "aikai kyauta mun aikin ne yake yawa "inada maka abinfa sai "a Slow Abdul-jabbar yace "aikuna kokari Sosai wlh Yace toh yaza'ayi,</p><p><br /></p><p>Bayan Doctor yagama duba shi yace abokina munkusa cin nasara "akan ciwon nakafa, Bakin Abdul-jabbar yadan tabe kadan tareda cewa toh" Allah yasa yace Ameen, sun Dan taba fira kadan sannan Abdul-jabbar ya mike yana cewa toh" nizan tafi, shima Doctor din mikewa yayi yace OK" toh" muje nataka maka, harsun Kai bakin kofar fita office din,</p><p><br /></p><p> Sai Doctor yace af "aina manta barina baka naka _I.V_ dai-dai lokacin daya ke mika masa katin yace gashi kaga nahuta zuwa kasan saura _one week ne fa_ </p><p>Abdul-jabbar yakarba yace?...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat Ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page151-155</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*</p><p><br /></p><p>*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>~*Don Allah kuyi Mani Hakuri narashin ganin posting Dina akan lokaci*~</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers._*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haba Doctor yanzu Saboda ALLAH yau saura _one week_ bikinka sannan zakayi "invited din'na,?... toh" yanzu dabanzo Check up din bafa?... Doctor</p><p> Yace yi hakuri "Aiyukane suyin mun yawa shiyasa, </p><p><br /></p><p> Dama yanzu danatashi daga office zantafi nakai maku kaga hada manasu Y Y K shida M.B, Cikin zolaya Abdul-jabbar yace toh" nidai bazan zoba, Da sauri Doctor ya rungumo kafadar sa tareda cewa yi hakuri taimaka mun kazo Don ALLAH kaji?..yakarshi maganar yana langabe kai irin nayara din'nan,</p><p><br /></p><p> Dariya Sukayi gaba daya tareda tafawa Abdul-jabbar yace karka damu Doctor zanzo insha'Allahu, nima saura _two weeks "intafi Yola kasan can sukai posting Dina,_ kaga bayan bukinka da _one week_ Zan tafi yace masha'allah toh ALLAH yakaima narai Lafiya, </p><p><br /></p><p>Yace Ameen nagode, yace kai habadai "Ana tare nima nagode Allah ya bar zumunci ya kuma bayyana mana da "Humaira, Da sauri Abdul-jabbar yace ya'akai kasan zancan Humaira?... yace karkadamu "Ai yanzu mun zama daya, naji komai "agurinsu Y Y K mu cigaba da Addu'a Allah zaisa kaganta "indai tana garin nan, yace nagoda Doctor kawo nasu Y Y K nakai masu, yadauko yana cewa yauwa my _My friend_kaga kahutar sheni dai-dai lokacin da yamika Abdul-jabbar l .V card din, </p><p>Har bakin Motarsa yara kashi sannan yakoma office dinsa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*********</p><p>Hannah DA Haleeh ne Zaune afaton gidan su Hannah, kasan cewar sufara shirye shiryen bikin Hannah din, yayinda ta keta faman kiran wayar Humeeh, sai kara take Amma bata dagaba, Haleeh tace "Ah toh" wai "Ina "ta'ajiye wayar ne haka?... kasan cewar takirata yafi sau goma sha biyar, Don haka Cikin Haushi Hannah tace oh mata ace _Handset_ita tamaida Nata _Roomset_ Domin daga jin wayar nan "adaki tabar ta,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sauri Humeeh ta daga wayar da harta kusa katsewa, daga can Hannah zata farayi mata masifa ta katseta dacewa _Sorry My Hannah ta D D bada kanji asare kije gida kice ma Hajiya yafadi_dariya Hannah tayi tace Kai _My Humeeh kin kashe bakin dazanyi maki masifa kenan KO?..._ tace "ah wace ni DA kashe wannan baki naki wannan aikin "aisai Darling Doctor din.</p><p><br /></p><p>Tace "aibazai iyaba tace Hmmm yarinya "aibaza ki'iya ganewa ba tukun sai kinje, dariya Hannah tayi tace nida kyaleni, yanzu Saboda ALLAH "Ina kika "ajiyar Waya tundazu nake ta faman Kiranki Amma _no respond?..._ tace kedai bari "Ina kicin "Ina tanaya "Umma aikine, tace "OK shiyasa, toh" ya kike _where is my Haleeh_?... Haleeh tace _hello My Humeeh l'm here, (dayake Hannah tabude volume din) yakike?..._ tace Lafiya lau ya kuke ya Kuma shirye-shiryen?... sukace Lafiya lau, Hannah tace yaushe zakijo? </p><p><br /></p><p>Tace Ranan _Friday_ Da sauri Hannah tace wani irin Friday Kuma?..abinda za'afara events gobe, tace abinda yasa nace Friday Saboda shirye-shiryen School kinsa ranan Monday zanfara zuwa School din,</p><p><br /></p><p> (kasan cewar Malam yasoke maganar zuwa School America din Shiyasa Abba yanema mata, "Admission "a American University dakenan cikin Yola) Hannah tace "eh hakane Kuma fa "aini walh naji dadi da da "Malam ya yahana tafiyar nan,</p><p><br /></p><p> Da yanzu fa badake za'ai bukin nan ba, Humeeh tace kedai Bari dama inata tunani taya zanfara Rayuwa ba tareda "Ummata ba, tace toh" yar gidan "Umma "aigwara kifara koyo tunda "idan ba School akwai aure, tace hakane Kuma fa ke! "aidana tuna zaya rabani Da "Umma sai naji gabana yafadi _My Hannah yaki keji yanzu Don ALLAH? Dariya tayi tace My Humeeh kyaleni yanzu pls kizo jibi mana?,...tace au baza kifada mani ba?...tace zan fada maki Amma sai kinzo zakizo jibin?... tace toh" bari "Abba ya shigo saina fada mashi najima yana cewa zaya tafi Kaduna jibi sai mutaho tare shikenan ko?..., sukace "eh Mana" ta Special_da sauri tace sai "anjiman ku tareda katse wayar.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>***********</p><p>Masha'allah _Dinner ya kayatar_Amarya Hannah Da Angonta Doctor Ibrahim saimuce ALLAH yabada Zaman Lafiya, _Alhamdullah! Alhamdullah!! Alhamdullah!!!_injicewar Humeeh data ke kokari rufe taro da Addu'a, gabanta ne yafadi yayinda ta hango Abdul-jabbar Zaune yana Cikin wani dakakken Shadda _Sky blue yasa hula mai ratsi blue,_ya goge yayi kyau abinshi kamar bashene yaiwann tashin Lafiya ba, ita Humeeh gani tayi kamar yakara kiba, da sauri tarufe taron Da Addu'a tabar gurin,</p><p><br /></p><p>Zumbur Abdul-jabbar ya mike sai kace antsira masa "Allura, Ku tsawa yafara yi Cikin mutane da sauri Y Y k ya bishi yana cewa Nawa me yafaru?... batareda ya kalleni shi ba yace _My Cool_ ce gatacen zata fita Da Sauri Y Y K yajawo shi daga cikin mutane, yana cewa Haba Nawa wannan wani irin "Abune haka pls kanutu kadawo hayyacinka mana,</p><p><br /></p><p>Tun' dazu fa nake maka magana Amma kana can kana tafaman tunani, toh" waima Ta'ina kaga Humaira?....da Sauri Abdul-jabbar yace naganta" tacan tabi pls Nawa kasa keni naje gareta karta sake kubce cemani,</p><p><br /></p><p>Shikam Y Y K sai sake rike shi yake yana cewa ni bazan sake kana, Saboda bansan inda zakaje ba Don naga alama baka Cikin Hayyacinka,</p><p><br /></p><p> Abdul-jabbar yarasa yadda zayayi, Y Y K yasake shi Amma yakiya, Don hakane yaji wani irin bacin rai yaziyarce shi, Saboda haka sai ya tattaro gabada karfinsa ya ture Y Y K "aikam yatafi taka-taka zaifadi sai yai saurin dafe wata bishiya dake kusa dashi,</p><p><br /></p><p>Cikin matsananci Mamaki Y Y K yadaga Kai ya kalli Abdul-jabbar, Wanda yake faman huci saikace kumurcin maciji, Cikin bacin rai yace Dalla gafara Malan wannan wani irin abune haka?... duk kabi karirrikeni saikace wani Mahaukaci, nace kasa keni gashi nan harta" tafi Saboda tsabar iskanci da walakanci irina ka, yakai karshen maganar dayin wani irin tsaki mtswwwww, yana gyara rigarsa adai-dai lokaci da M.B yakara so gurunsu,</p><p><br /></p><p>Shikam Y Y K cikin matsanacin "al'ajabi yabude baki da hanci yana kallon Abdul-jabbar, yayinda ya hango wani irin matsananci bacin rai "afuskar shi Wanda tunda yake dashi bai taba gani irin shi ba.</p><p><br /></p><p>M B yace kai Amma dai gaskiya ana Kama duniya, yanzun nan nagawa Kamar Humaira, Da sauri Abdul-jabbar yarike mashi hannun tareda cewa "itace ba Kama bace kagani wlh KO"?.. Nawa nafada maka _l see My Cool_ Amma kace wai _l'm not ln My Sense,_ pls muje Karta tafi banaso narasa "ta "akaro Na biyu Ina Sonta" sosai, gaba daya Abdul-jabbar ya birkice masu saijan hannun M.B yake,</p><p><br /></p><p>M.B yace Pls Abdul-jabbar Ka nutsu Kama fa nace kaga banida tabbacin itace" KO ba ita bace, Da sauri yace wlh itace _see her ln my eyes_</p><p>Yace toh" mutafinku muduba kila itace' da sauri Abdul-jabbar yace "eh, Sai kutsewa suke Cikin mutane suna duban Humaira har mutane sun Fara watsewa Amma KO mai kanada "ita basu ganiba,</p><p><br /></p><p>Cikin bacin rai Abdul-jabbar yace saida nafada mashi Naganta" Amma yaki yarda, "Ahankali Y Y k yakarasa gurin shi saboda wani irin tausayin shine yaji ya kamashi, "aran kuwa fadi ya Kai ALLAH yaraba muda *MASIFAR SO* rungume shi yayi yace kayi hakuri, banyi zaton da gaske kaganta" ba Amma Ka kwantar Da Hankali Ka idan tana ciki garin nan "DA SANNU" Allah yaza bayyanar Da ita,</p><p><br /></p><p>M.B yadafa kafadar shi yace haka ne Ka kwantar Da hankalin ka insha'allahu zamu ganta", Amma kafin nan _why not_ mu tambayi "Ango shikuma ya tambayar mana "Amarya kila kawarta ce'KO?,...da sauri Abdul-jabbar yace "eh hakane mukarasa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Doctor ya Dan hararesu Cikin sigar wasa yace saboda Allah sai yanzu kuke zuwa?...Y Y K yace "a ah tundazu mukazo saboda jama'a sunyi yawane shiyasa bamuyi maka magana ba, yace OK Shikam Abdul-jabbar wani sanyi ne yaziyarci zuciyansa saboda gani KO" wacece "Amarya hakan ya tabbatar masa Da cewa _you Cool dinsa tana nan gurin_.... nadai suka gaggaisa yayinda "Ango yagaba tardasu gurin Amarya Hannah, tagaida Y Y k Da M.B Amma sai taki gaida Abdul-jabbar "asalima hararan shita tareda Jan tsaki mtswwwww! sannan ta kauda kai tanuna irin bama ta San kallon sa.</p><p><br /></p><p>Mamaki ne yakama "Ango kai bashi kadai ba harda Su Y Y K, Shikam Abdul-jabbar Jikinsa ne yai sanyi ganin yadda Hannah tayi masa, Da sauri Ango ya kallesu yace?.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat Ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page156-160</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*</p><p><br /></p><p>*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>~dafatan readers zasuyi Mani afuwa narashin ganin posting Dina akan lokaci~</p><p><br /></p><p>*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kuyi hakuri Don ALLAH "Ina zuwa Hannun Hannah yaja suka yufi bayan wata mota, suka tsaya hannun shi yaka dai-dai gefen Cikin ta ya _pinch ce ta sosai yanda zataji zafi,_ "aikam taji domin kuwa kara tasaki mai hadeda Shagwaba, tafada jikinshi yariketa sannan yadago da'ita yadan tureta kadan ya kalle ta Cikin bacin rai yace My D "abokina nefa tun yanzu irin kalar tarban dazaki ringayiwa abokanai Na kenan?</p><p><br /></p><p>Meyai maki baki gaida shiba" sannan kika masa wannan _bad look_? baki ta turo tareda zuba masa fararan "idanunta, sannan tace tabdi shi wannan mayaudarin ne abokinka?... lallai kam bakayi abokin kwarai ba.</p><p><br /></p><p>"Idanu yazaro Cikin Mamaki yace ke! "Inaki kasan shi?... sannan kuma yaudarai meyayi maki?....,tace ah! ba Abdul-jabbar bane? Da sauri ya matso kusa da'ita yarike mata hannun da karfi, da sauri tadaga kai takalle shi gaban tane yafadi, saboda yadda taga idanun shi sunyi jajir lokaci daya alamar kishi karara "afuskar sa, sai abunya bata dariya Amma saita gintse gudun kartasha Mari lol,</p><p><br /></p><p>yace "eh shine fada Mani inda kika sanshi?...,</p><p>Tace shine" fa saurayin My "Humeeh Wanda ya yaudareta, wani irin sanyayyan "ajiyar zuciya yayi tareda sakin hannun ta, dariya tasaki hararanta yayi Cikin sigar Soyayya yace _what are you laugh?.._ tana rurrufe baki tace nothing,</p><p><br /></p><p>Tsaki yayi mtswwwww tareda cewa Allah My D kinrai nani fa, Amma kwanan nan zanyi maganin wannan bakin meyiwa mutane tsiwa, </p><p><br /></p><p>Ya kalle ta yace fada mani yaudarain meyaiwa Humeeh?...., nan Hannah tafada Masa komai, yace wai yanzu dama Humeeh ce yarinyar da My friend yake nema acikin garin nan?....tace nema kuma toh" neman me yake mata "OK nagane yana Neman "tane yajidadin Kara yaudaranta KO?...,</p><p><br /></p><p>Hararar tayati tareda cewa ban sani ba, Allah idan kika sake fadar Kalmar yaudaran saina bige maki baki, waiku mata meyasa tunani Ku kusan duk daya ne?...., keda "indakin San halinda Abdul-jabbar yashiga akan Son Humaira da kowani kikaji yakira shi da mayaudari sai "inda karfinki yakara, mutumin da Har COMA yashiga kusan wata daya yayi batareda yasan "inda yake ba, ga ciwon zuciya dake damushi yanzu haka yanazuwa gurina _Check up_, "idanu ta zaro tareda cewa what?... yace yes nine Doctor shi, kuma duk "a dalilin Sonta" Amma sai faman kiransa" mayaudari kike'</p><p>Nan yafada mata duk abinda yasani dakuma </p><p>Wanda Y Y K yafada masa,</p><p>Toh yaudaran meyayi mata?....</p><p><br /></p><p>Jikin Hannah yai sanyi dajin "abida Doctor yafada, tadan tabe baki tace Hmmm toh" aida saiyafata mata gaskiya, "Amma meyena boye mata toh" aigashi nan "DA SANNU" Allah ya baiyyana gaskiya, yace "eh toh" nan kam bai kyauta ba yanada kyau duk "abinda mutun zayayi "arayuwa toh" kafadi gaskiya, toh" "Ai mashi" afuwa yanzu mutafi kigaida shi"sannan kibashi hakuri, Don gaskiya banji dadin "abinda kikai mashi ba, sannan kikira masa Humaira tace toh"</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Doctor yace kuyi hakuri Don Allah munbar Ku tsaye, Y Y k yace "ah bakomai Hannah tace Abdul-jabbar "Inayini yajiki "Ashe kayi rashin Lafiya?.... da saurin Yace " eh Lafiya lau Hannah jiki aiyayi sauki ya jama'a?.... tace Lafiya lau toh" Allah yasanya Alkhairi yabada zaman Lafiya, </p><p><br /></p><p>Tace' Amin mun gode fa Don Allah kafayi hakuri dazu nayi maka mummunan fahimta, dariya yayi yace Lah bakomai "ai rashin sanine, </p><p><br /></p><p>Tace kaga "Humeeh kuwa?....da Sauri yace "eh naga kamar "itace" tayi Closed prayer KO?... tace "eh itace yace toh" yanzu kuma banganta, tace "OK Bari nakirata "awaya yace toh"</p><p><br /></p><p>"Abun mamaki kuwa shine Hannah sai kiran number Humaira take Amma is Switch off, ta kalli Abdul-jabbar wanda shima ita yake kallo tace' kaga wai wayar Nata akashe yake,</p><p><br /></p><p>Amma Bari nakira "Haleeh kila suna tare, tana kokarin kiranta" sai ta hangota zuwa gurin su" Don haka sai tace yauwa gatanan mazuwa,</p><p><br /></p><p>Assalamu'alaikum sannun Ku, shine abinda Haleeh tace' suka amsa, tace Miss D D kokin ganar Mani Humeeh?... l have be looking for her "Amma bangan taba, nakira wayar ta wai "akashe take" Hannah tace nimafa "ita nake nema ainayi zaton KO kuna tarene"?... tace "a ah tace toh" Ina Humeeh tashiga ne?..., toh" KO ta tafi gida ne?… Haleeh tace Anya kuwa?...toh" idan KO" ta tafi toh" KO tabbas "Aleeyu ne yatafi kaita gida, domin inajin yana cewa "idan antashi shizaya maida ita gida,</p><p><br /></p><p>Dammm! Abdul-jabbar yaji kirjinsa yabuga, wani irin kishine yaturni kesa" nan DA nan idanun sa sukaru fe, Don haka Cikin zafin nama yafin ciki hannun Haleeh yace wanene "Aleeyu neye hadinta" dashi?....ina yakai Mani My Cool?... Cikin tsoro tareda zaro ido tace "ah Saurayinta ne" mana, Kai kumafa waye?... dakake kokarin tsinka Mani Hannu,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Pls readers kar kumanta Haleeh bata taba ganin Abdul-jabbar_</p><p><br /></p><p>Yace pls Sorry call me Abdul-jabbar. da sauri ta nunashi da yatsa tana cewa Oho" dama Kaine' ka, yaudari my besty "Humeeh saida kadasa Sonka "acikin zuciyar ta sannan kagudu kabarta", saboda tsabar yaudara shine yanzu ka kuma dawowa toh" kasani cewa yanzu My besty "Humeeh tafi karfin ka domin tasamu me" Sonta da gaskiya Wanda yafik.....</p><p><br /></p><p>shuru tayi saka makon wani irin Uban tsawa da Abdul-jabbar yadaka mata, Cikin matsananci bacin rai yace' karyane babu wanda yafini "SONTA" kum.... yakasa karasa wa, saboda jindayai Zuciyar shi tanai masa zafi, da saurin yasa hannun shi dai-dai saiti zuciyar shi yace wahhhhhhh!</p><p><br /></p><p>Yayi da Hannah taja Haleeh gefe tana cewa gaba Haleeh meye haka?... bashi Da lafiya fa, nan dai tafada mata komai jikinta yai Sanyi, "ahankali tajuya tana kallon shi saitaji yabata tausayi su" Doctor ta hango suna mashi magana da "alama suna lallashin sane'</p><p><br /></p><p>"Ahankali suka karasa gurin su" nandai "aka fahimci juna tareda bajuna hakuri, sannan suka kwashi jiki zuwa gidan su Hannah "Amarya Dan suna kyauta ta zaton Humeeh tana can.</p><p><br /></p><p>**********************</p><p><br /></p><p>"Abinda yafaru kuwa shine Lokacin Da "Humeeh tagama " Addu'a jikinta yana tarawa tabar harabar Hotel, saboda kar Abdul-jabbar yaganta Don haka tana fita sai ta tare "adai-dai tahau Sai gidan malam,</p><p>Bayan tabiya me adai-dai kusan kudin sanna </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sai tanufi cikin gida "A zaure ta iske Malam shida Abba suna fira, Malam yace "a ah su budurwar Kauye yan biki mashaya gara, "ai yanzu nake cewa Abban ki yatafi kawai yabarki', idan kun gama bikin sai kiringa taya matana Aiki,</p><p><br /></p><p>Tace wani?.... tab... kafata kafar Abba na, Bari ma kagani nashiga Nai Sallama da yar tsohuwar </p><p>matar taka, tareda dauko kayana nazo mutafi KO" Abbana....? shidai Abba baice komai Sai dariya dayake yi, Cikin wasa Malam yace aisaikin sati biyu anan tukun na, tace me?... aibazan iya sati biyu banga "Umma ta ba tafada tana dariya shima dariya yake yace ja'ira sannan tashiga Cikin gida.</p><p><br /></p><p>**********</p><p>Zaune suke' Cikin kayatattacen falon gidan Hannah dayaji kayan more rayuwa, _(tunda dama anriga ana kai ta daga can aka tafi Dinner)_ Abdul-jabbar Y Y K, M B Doctor S I G Haleeh and Hannah, ga badaya hankalin su atashe yake especially Abdul-jabbar, tunanin Su "Ina wannan Aleeyun yakai "Humeeh?....</p><p><br /></p><p>Kasan cewar suje gidansu Hannah hada gidansu Haleeh amma bata can, sannan har Lokacin wayar ta "Akashe gashi tun karfe takwas har yanzu karfe goma darabi nadare, Hannah tace toh" wai Ina My "Humeeh tashiga ne?... </p><p><br /></p><p>Haleeh tace' kashhhh! ai mun matan kodai tana gidan Malam ne?...Hannah tace' tabbas tana can da sauri Abdul-jabbar yace "Ina ne?... tace gidan kakanta Doctor yace lallai kuwa toh" mujenku can gidan ko?... Abdul-jabbar yace eh muje, Doctor yace My D kubarimu muje KO?,... tace toh" .</p><p><br /></p><p>Har zasu fita sai Wayar Hannah tayi Kara, kodata duba saita ga sunan Humeeh" da sauri tace Lah!... Kunga taka kira, da Sauri suka dawo, Wayar tadauka tareda bude Volume din yaka sance duk sunajin magana kenan.</p><p><br /></p><p>Saidai Hannah shuru tayi ba tareda tace' komai ba, daga can "Humeeh tasaki kayatattacen Murmushin Da harsada saurin shi yafito ta cikin wayar,</p><p>Yayinda Abdul-jabbar yaji Wani irin yarrrrrr! "ajikinshi "Aranshi KO fadi yake yaushe rabonda yaji wannan tsadaddan Murmushi.</p><p><br /></p><p>Sannan Cikin siririyar muryarta mai dadi tace _Sorry My Hannah I know U angry with me ba,?_... Hannah tace haba My Humeeh "aikema kinsan dole nayi fushi kin kosan irin tashin hankalin damuka shiga, saboda rashin ganin ki'?...tace toh kuyi nan "Ina my Haleeh?.. tace gatan kusa dani tanajinki,</p><p><br /></p><p>Hannah tace toh" munyi Amma dai yanzu where are you?... Dariya Humeeh tayi me sauti, sannan tace am ln my "Umma bed What?.... shine abinda Hannah DA Haleeh suka fada "alokaci guda, da Sauri Hannah tace kina nufin yola?...tace yap...tace pls my Humeeh talk true fa?... tace Allah kuwa gani nan "akan gadon "Ummana, "inata juye-juye saboda kewar Kuta dameni, Hannah tace Amma meyasa zakiyi mana haka?.., tace shiyasa nace kuyi hakuri, bansan yadda zanyi na fada maku ba ne, tunda saida Abba yariga yayi bokin jirgin sannan yakira yace idan mun gama nataho mutafi.</p><p><br /></p><p>Pls kiyi hakuri kinji My besty kicewa my Haleeh itama tayi Hakuri, Allah har nayi miss dinkufa Haleeh tace muma muyi miss dinki. Hannah tace toh" yanzu kice Ina gaida "Abba DA "Umma sannan kifada mana Address dinku, DA Sauri Humeeh tace Zaku zone?.. tace "eh tace toh" kibari idan kunzo sai muzonida driver mu dauke Ku' Hannah tace kedai fada mana saboda zuwan bazata zamuyi maki',</p><p><br /></p><p>Tace "au hakane? sukace "eh mana" tace toh" shikenan rubuta nandai tafada, Haleeh ta rubuta sukai tace toh " wai yaushe zakuzo keda kike "Amarya?... tace kedai baruwankin, tace "au hakane?... sukace "eh mana" sannan sukai Sallama. ta kashe wayar. tareda kallon Abdul-jabbar tace my Haleeh bashi Address din, idan harda gaske yana Son our "Humeeh toh" yasa meta Yola Kome kikace?...</p><p><br /></p><p> Haleeh tace kwarai DA gaske, dai-dai Lokacin da tamika masa takardan medauke DA Address din,</p><p>Ya karba fuskarta shi cikeda farinciki yace?...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat💞💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page161-165</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_*.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Insha'Allahu zani Yola Saboda Na tabbatar maku dacewa Son "My Cool "acikin jinina yake, yanzu saura Number ta zakubani saidai don ALLAH kar kufada mata, komai gameda Address dinta dakuma number tada kuka bani, Saboda "Inason ne nai mata zuwan bazata. So dama nest week zamu tafi kasan cewar Chan "akai posting din'mu, So kunga da yardan Allah zuwa Yola bama kawa KO?.. Me kukace friend's dai-dai lokacin daya ke kallon su Y Y K fuskarsa cike tada farin Ciki da an'nashuwa,</p><p><br /></p><p>Suka hada baki gaba daya sukace" yesssss "angon A'isha Humaira, tareda tafawa sukai dariya harda shi yace in ALLAH yayarda, very soon zakusha bikin kamar yadda mukasha Na Doctor yau. Sukace Allah yasa Ameen suka amsa gaba DAYA. nan dai Hannah tabashi number Humeeh sannan sukayi Addu'a Allah yaba Amarya da Ango zaman lafiya da zuri'a tagari, sannan sukai musu Sallama zasu tafi sai Haleeh tace ummh Bari nazo kusaukeni gida. </p><p><br /></p><p>DA sauri Hannah tarike ta tareda fata fuska tace haba my Haleeh ki kwana "anan mana? "Idanu Haleeh ta zaro tace kwana kuma my?... Hannah. suma baki suka hada guri fadin kwana kuma?...</p><p><br /></p><p>Cikin shagwaba Hannah tace "eh tunda dare yayi basai takwana ba gobe ta tafi KO? My D D tafada tana kallon Doctor Wanda yaketa watsa mata harara cikin gatse yace mata "eh dariya tayi tace yau shikenan kinga my D D yace "eh ki kwana nan,</p><p><br /></p><p>Su Abdul-jabbar kam suma dariya suke najin wannan "Almara DA Hannah takeyi, itama Haleeh "abin dariya ya bata. tace toh" zomu koma sai My D D yaraka su KO?...tafadi tana Jan hannun Haleeh, da Sauri Kuma Ciki daure fuska Doctor yace ke! Haleema wuce muje su' sauke ki "agida,</p><p><br /></p><p>Tace toh" Hannah kam rike Haleeh tayi sosai tana cewa haba my D D bakace ta kwana ba?...</p><p> Doctor Bai saurare taba yace wuce mutafi yafada yana kallon Haleeh, saida Kuma takasa tafiya Saboda rikentan da Hannah tayi.</p><p><br /></p><p>Kallon Hannah yayi tareda cewa my D saketa sutafi, kafada tama kale tareda rungume Haleeh sai Kuma tasaki kuka, tana cewa pls my Haleeh Karki tafi kinji?... "itama Haleeh rungumeta tayi sai kuma tafashe da kuka, sukam</p><p>Su Abdul-jabbar shuru sukai suna kallon cikin Mamaki. Yayinda sukuma suke kuka sosai narabo dajuna, Wanda sunsan "inbadan aure ba toh",sunsan babu abinda zaya rabasu saidai mutuwa tunda wani lokacin taresuke kwana, KO" gidan su' Hannah KO" gidan su Haleeh, toh" sai gashi yau zasu kwana da ban Da ban.</p><p><br /></p><p>Ganin cewa da gaske kuka suke sosai sunki sakin juna, sai Kuma suka basu Abdul-jabbar tausayi. Ahankali Doctor ya isa gurinsu cikin sigar lallashi yace haba _Lovely friends_kukan mekuke?... </p><p><br /></p><p>OK" nagane kuna kukan rabuwa da junane KO?...da Sauri suka daga Kai alamar "eh yace toh" "anfada Ku "idan daya "yayi aure shikenan "an'rabu?...</p><p>toh" ba'arabu ba "ai wannan lokacin ne zaku Kara dankon zuminci ku, bawai Ku tsaya kuna kuka kamar irin little-little childrens din'nan ba.</p><p><br /></p><p> Kuba kusan cewa yanzu they're bigs girls ba?... cikin zolaya yace bani wayarki nakira Humaira ko dariya tayi maku</p><p><br /></p><p>Cikin shagwaba Hannah tace gashi, yace "au nakira tadin?... tace "eh. nan danan yayi Dialling number Humeeh tareda sa Wayar "ahandsfree, saiko tadaga, saidai cikin sheshshakar kuka zukaji tace Hello waye?...kasan cewar bata tsaya duba waba, cikin matsananci Mamaki Doctor yace Humeeh tace na'am yace meyasa meki naji kamar kina kuka ko?..</p><p><br /></p><p>_*Allah sarki Humeeh" tana can tana kuka mai kunshe da Abu biyu", daya kewar su Hannah da Haleeh daya Kuma na SON Abdul-jabbar, wanda ganishi yatayar mata da tsohon mikin dake zuciyar ta. domin kuwa jitayi SON Abdul-jabbar yadawo mata sabo fil "ayanda takeji yanzuma haryafi Nada saidai tunawa datayi cewa yanzu Abdul-jabbar banata bane yasa take kukan tausayin kanta*._</p><p><br /></p><p>"Don haka cikin cikin kukan Shagwaba tace ummh! I Miss my Hannah and Haleeh I lot.</p><p> </p><p>Dariya ce takwace wa Doctor shidasu Abdul-jabbar, da sauri Humeeh tace waye Kai?... yace l am Doctor Ibrahim "Angon Hannatun Humeeh DA Haleeh, hakane?... Tace eh, yace ayya</p><p> No wonder ashe kema kina can kina kukan'ne, shiyasa suma suke nan sunayi.</p><p>"ALLAH sarki three heart's in one place,</p><p><br /></p><p>Toh ku "Inbanda "abunku ai "idan kaji kewar dan'uwanka bazama zakayi kana kuka ba, just dauki Waya kakira shi saikaji lafiyarsa' Shima sai yaji taka za'a</p><p>Ko?....</p><p>Bahaka bane friends suka ce" hakane.</p><p> </p><p>Yayinda sukaji tausayinsu" yaka masu" tawani bangaren kuma kawancansu yana birgesu. Haleeh tace Doctor "Ina Hannah DA Haleeh yace gasunan sai kuka suke faman yi,</p><p>Humeeh tace My Hannah,</p><p>Cikin Shagwaba Hannah tace Na'ma</p><p>toh" my Humeeh Shinefa yace my Haleeh ta tafi ba,</p><p><br /></p><p> yace toh" ai abinda yasa nace ta tafi Saboda kinga gida ba'asan zata kwana ba shiyasa,</p><p><br /></p><p>Humeeh tace pls Doctor kabari my Haleeh ta kwana mana?...kaga saita taya my Hannah hira. yace Humeeh bai Kamata Haleeh ta kwana ba tunda gida ba'asan zata kwana ba, kinga kwanan ta anan zaya'iyazama damuwa "azo ana nemanta "amma kunsame ?.. girgiza Kai sukayi alamar "a ah yace l promise yours gobe dakaina Zanje har gidana dauko maki Haleeh tazo tawuni maki hardare, wani "abinda Mamaki shine DA Sauri suka hada baki harda Humeeh, sukace da gaske?... yace insha'allahu</p><p><br /></p><p>Dariya sukayi gaba dayan su" tareda cewa "eh mana", nandan Doctor cikin hikima irin ta maza ya lallashesu", sannan suka tafi "akasauke Haleeh gida sannan Y Y k yakai M B gida yakai Kuma Abdul-jabbar sannan shima yanufi gida, dayake da motar shi Y Y k din sukaje gurin Dinner.</p><p><br /></p><p>*American university Yola*</p><p>*****************</p><p>Da misalin karfe goma Na safe, Humeeh ce' zaune saman wani dotse "akarkashin wata bishiyar fulawa, sanye take cikin rigada siket na'atamfa mairuwan toka, tanada ratsin ja tasaka hijab shima ja.</p><p>tana rataye da jaka mairuwan toka shima takalmin kalarshi kenan.</p><p><br /></p><p> fuskarta bawani kwalliya saidai powder kawai data Shafa, sai Kuma man baki kadan data shafa alebenta. Gaskiya dress din yai mata kyau musamman data man'na wani Dan siririn glass "afuskarta. </p><p><br /></p><p>Wasu littafiai naga tana dubawa, can Kuma sai naga tabude Jakarta tafito da wayarta, Dailling Number Hannah naga tayi tareda bude hands free din wayar sannan ta ajiyeta "akan littafai.</p><p>Daga can Hannah tadauka tareda yin Sallama, cikin zalaya Humeeh ta amsa dacewa Amarya kinsha mai yamike?</p><p><br /></p><p>Dan tsaki mtsww! tayi tareda cewa nasha mai kona sha wahala,</p><p>Dariya Humeeh tayi, yayinda Hannah tace "au dariya ma kike Mani?... tace toh" kedince' wlh "inbanda abinki meya hada Amarya Da shan wahala?... Wadda akace' yar'sha galice "ita komai a kasamu ita "akaba ta karashe maganar tana dariya. tsaki mtsww tayi tace "aiko meye idan kikayi "aure zakisani yar'rainin sense kawai.</p><p><br /></p><p> DA Sauri tace wani?... tab.. nikam bazanyi aure nabar Umma taba. tace "au Allah?... tace ummh, (Murmushi tayi data tuna cewa Abdul-jabbar yana nan zuwa gareta Wanda Kuma tabbas da maganar aure zaije) Dan haka sai tace toh "ashikena saiki zauna kiyi tayiwa "Umma gadin daki, </p><p>tace "aidama yarinya kobaki fadaba, tace toh "Aisaiki tattake nidai yakike?.. </p><p><br /></p><p>Tace lafiya lau toh" ya school din?... tace lafiya toh" Allah ya bada sa'a Ameen, nan dai suka Dan taba fira sannan ta kashe wayar, yayinda tacigaba DA duba littafai.</p><p><br /></p><p>Assalamu'alaikum shine Abunda taji amfada cikin wata siririyar murya,</p><p>A hankali ta "amsa tareda daga Kai ta kalli maiyin Sallamar wata budurwar tagani yar kimani shekara goma sha biyar, kyakkyawa tana sanye da "Abaya baka.</p><p> tayaye kanta da mayafin abayar fuskarta tasha kwalliya, yayinda ta man'nawa idonta irin glass din'nan DA "akekira no respect.</p><p><br /></p><p>Cikin yar siririr murya tace Don Allah zan'iya zama nan wurin?...tana Nina kusada Humeeh, yayinda Humeeh tace Lah! bakomai kizauna mana. tace OK ta zauna tareda cewa thanks, Humeeh tace no problem. Can sai tace sunana *SARAH "AHMED ABDUL-JABBAR* kefe?...,wani irin yarrrrrr! Humeeh taji "ajikinta saka makon jin sunan "Abdul-jabbar, Murmushi tayi sannan tace *A'ISHA "MAHAMUD IBRAHIM,* tace OK wani department kike?.. tace Medicine. Da sauri tace Wow! nice to meet you wlh, dai-dai lokacin datake mika mata hannu tace nima can nake.</p><p><br /></p><p>"Itama hannun ta mika mata tana dariya tace Allah sarki, tace kinga nifa banyi copying times table ba koda yake "ance sai 12:00 mukeda lecturer KO?... Humeeh tace "eh hakane toh" ganawa basai kiyi copy din ba, tace "OK toh" nagode takarba tana rubutawa. bayan tagama sai kuma sukafara fira kamar sun dade dasanin juna, har zuwa Lokacin lecture yayi suka nufi Class din.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*BAYAN SATI DAYA*</p><p>*****************</p><p>Da misalin karfe 2:30 pm Humeeh ce" kwance tana Waya da Sarah sabuwar kawarta. kasan cewar yau tun 2:00pm suka tashi daga school. Dan haka take hutawar ta'abinta, wadda Kuma "acikin sati dayan nan sun shaku sosai dajuna itada SARAH "idan kagansu" sai karantse dama can tare suke" wanda har tasan "Haleeh DA "Hannah kasan cewar Humeeh tabata Labarin su harsun gaisa "AWaya"</p><p><br /></p><p>Hira suke tazu bawa kamar bayanzu suka rabu makaranta ba, Sarah ce' keyiwa Humeeh korafi cewa ya kamata tazo gidansu. Kasan cewar "ita Sarah taje gidansu" Humeeh har sau biyu, dariya Humeeh tayi sannan cikin zolaya tace </p><p>Sorry my Saratutu aizanzo.</p><p><br /></p><p>_(Dayake tasan bata son akirata Saratu saidai_*SARAH*)</p><p><br /></p><p>Da sauri tace Kut! Amma dai my Humeeh kinci abinci hada wani Saratutu KO?... kuma kinsa I don't like it faaa! Cikin dariya tace Sorry nadaina. tace "OK toh" fada Mani yaushe zakizo?... kinga sisters Dina sun'matsu suganki.</p><p><br /></p><p>Tace Ummh! dama "Abunda yasa kikaga banzo ba saboda "Abba baya nan ne shiyasa toh" Amma kinsan me?.. tace "a ah saikin fada, tace "Abba yadawo da sauri tace da gaske yaushe?... tace Allah koda nadawo gida Na iske shi' dama shizan fada miki, So kinga gobe zanzo insha'Allahu. tace toh Allah ya kaimu tace Ameen, "Ina gaida "Umma shima "Abba ina gaida shida dawowa sukai Sallama.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana cikin chatting Da mutanan ta "Hannah da "Haleeh sai bacci ya kwashi ta, cikin baccin taji Wayar Na Kara, dauka tayi tasa "akun'ne batareda taduba ba. cikin murya bacci tace Assalamu'alaikum,</p><p><br /></p><p>Zumbur naga tamike tamkar wadda "aka tsikarawa Allura tareda zaro beauty eyes dinta waje cikin hada kalmomi naji tana cewa?...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat Ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page166-170</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*</p><p><br /></p><p>*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_*Pls masoya wannan littafin kuyi Mani afuwa narashin ganin posting Dina, akan lokaci. abubuwa wanne sai a slowly Amma insha'Allahu komai zayazo normal nagode.*_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"W..a..n..e..ne..?.. Sai Kuma naga tasauke wayar tareda tsura wa number idanu, yayinda jikinta yaketa rawa "a handsfreen tasa wayar, da'alama tanaso ne' ta tabbatar da gaske muryar shi" din'ne, KO kuwa kunnan tane yake mata gizo kamar yanda yasaba.</p><p><br /></p><p> Saidai ga Mamakin ta saitaji Cikin Zazzakar muryarshi dabaza ta taba mantawa da'ita ba, yace Hello my Cool kenan, nasan kinajina sannan kuma kamar yadda *SONKI da KAUNAR KI' kE DA KOMAI NAKI*bazaya taba gushewa acikin Kwakwalwa taba, toh" kema nasan haka *KOMAI NAWA* bazaya taba gushewa acikin Kwakwalwarki ba.</p><p><br /></p><p> Domin *SO DAYA NE* saboda haka gani "A harabar gidanku, kizo kiyi Mani jagora domin kinsan bai dace Na shiga gidan mutane, batareda *IZINI* ba so l am wanting for *U my Cool*" sannan yakashe wayar.</p><p><br /></p><p>"Idanu nagata tsurama wayar tabbas shine jitayi kirjinta yaci gaba da bugawa, saka makon tunawa datayi yace' yana harabar gidan. don haka da sauri tamike tareda jawo mayafin "abayarta dama shike jikinta Dan haka saita yafashi,</p><p><br /></p><p> Tareda shuran flat shoes dinta tasaka sannan tafito waje, da sauri take saukowa daga matattakalar benan, Da sauri tawuce Umma dake zaune "afalo, yayinda Umma tabi bayan ta Da kallo Cikin mamakin "aranta tace toh "ina kuma wannan lafiya "inazata haka Da sauri?..</p><p><br /></p><p>Humeeh kam tana fita Sai tafara waige-waige aikam saita hango shi, tsaye ya jingina ajikin wata dan kareriyar mota ya rungume hannu akirji, yana sanye da uniform din,su" na SOJOJI.</p><p><br /></p><p>_*Kut shine abinda nace saka makon ganin ABDUL-JABBAR turkashi toh faaaa*!_</p><p><br /></p><p>Tsaye tayi Chak! tana kallon shi fuskarta cike da mamaki, yayinda shima yake kallon ta yana takowa "Ahankali Cikin tafiyar kasaita, irin Nasu" na Sojojin masuji da'isa da takama.</p><p><br /></p><p>Sai Murmushi yake sakar mata ganin yakusa isketa yasa tafara tafiya, "ahankali da baya da ba yayinda shikuma yake binta ahankali-"Ahakali, </p><p><br /></p><p>Harsuka isa bakin kofar falon tadaga kafa daniyar zata shiga falon kenan, Saita tafisuuuuu! zata fadi tabaya.</p><p><br /></p><p>Cikin Zafin nama irin Na SOJOJI yarike mata hannun, tareda tallabo kugunta. yayinda hannun ta guda Cikin nashi hannun, gudan Kuma tadafa kafadar shi yaza mana suna jiyo bugun zuciyar su tareda jin'numfashi </p><p>Juna.</p><p><br /></p><p>Kallon juna suke sosai yayinda kamshin turaransa yahadu danata, Sai yabada wani irin ni'imantaccen kamshi mai dadin gaske, yayinda sukaji wani irin kasala yaka masu "alokaci guda.</p><p><br /></p><p>"A hankali yakai bakin sa gurin kun'nanta Cikin rada yace wayace maki ana tafiya da baya da baya bakisan hakan bayada kyau Ummh?..</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Itakam Umma dataji Humeeh shiru bata shigoba, Saita tashi tanufo hanyar waje don taga KO lafiya,</p><p>Saidai abinda tahango talabulen yasata tsayawa, kasan cewar labulen falon irin mai ragan'nan ne </p><p>Don haka da sauri tace Humaira...</p><p><br /></p><p>Cikin tsoro tareda rawar murya Humeeh tace N..a.n.a na'am Um..mah gani, "Ahankali Abdul-jabbar yadaga ta yayinda yaketa sakar mata lallausan Murmushin sa mai kashe mata jiki.</p><p><br /></p><p>Da sauri tajuya tanufi Cikin falon jikinta Sai rawa yake, bin bayanta yayi yana dariya bakinsa dauke da Sallama yashiga cikin falo, Umma ta amsa yayinda ya tsugun'na har kasa yace sannu Umma "Inayini da fatan munsa meku lafiya?.. cikin jin kunya tace lafiya ya Aiki yakuma mutane nan gida?...yace lafiya, tace toh" madallah sannan tanufi kitchen kasan cewar dama tana girkin'ne,</p><p><br /></p><p>Humeeh tana ganin "Umma tanufi kitchen Sai ita Kuma tanufi dakinta, yayin da Abdul-jabbar yabi bayanta da kallo, da dan gudu-gudu take taka steps din tana shiga dakin tarufo kofa. tareda jingina bayanta "a kofar idanun ta rufe, sai sauke nufashi take sai kace wacce tayi gudun tsere.</p><p><br /></p><p>"A hankali Abdul-jabbar yamike' daga tsugun'nin,yayinda yatura hannun wanshi dukka biyu 'acikin aljihun, tunani yake arashi kuma fadi yake meyasa my "Cool ta tafi kodai batayi farin Cikin ganinsa bane?...</p><p><br /></p><p>Zama yayi "a daya daga Cikin kushindin falon yafara kallon t.v, kusan 30 mints shuru ba Humeeh ba dalilin ta. Yayinda kallo daya zakaiwa Abdul-jabbar ka' fahimci cewa kallon kawai yake ba tareda yana fahimtar abinda "akeyi acikin t.v ba.</p><p><br /></p><p>Domin kusan duk hankalin sa yanaga hanyar da Humeeh tabi, yayinda jafi-jafi yana kallon agogon hannun shi ki'la yanada wani uzirine.</p><p><br /></p><p>Umma ce' tafito daga kitchen zata hausama sai taga Abdul-jabbar zaune shikadai. Kallon sa tayi tace "a ah Kai kadai ne ina ita "Humaira take'? Cikin jin kunya tareda Sosa Kai yace "eh tunda tashiga Ciki bata fitoba,</p><p><br /></p><p>Tace" a ah toh" inazuwa, yace toh" dai-dai Lokacin datake hawa steps din.</p><p><br /></p><p>"Abangaren Humeeh kuwa bayan tagama tsayuwa, saita koma gefen gado ta zauna tareda zuba Uban tagumi, sai kace wadda akayiwa mutuwa.</p><p><br /></p><p>Sai kuma tafara tambayar kanta take Waya ba Abdul-jabbar number ta?.. sannan Kuma Waya fada mashi cewan tadawo Yola bayan haka Kuma me yazo yi gurinta?...</p><p><br /></p><p>_domin batayi tunanin cewa Hannah KO Haleeh zasu bashi no taba_ </p><p><br /></p><p>Toh Waya bashi no ta?..toh kodai wanene tabbas agurin bikin Hannah yasamu toh" kodai Doc... turo kofar Umma ne' yakatse mata tunani.</p><p><br /></p><p>'Da sauri tamike tana kallon Umma, itama Umman kallon ta take', cikin mamakin domin taga tsoro karara 'afuskar ta. saboda haka sai tace "a ah waike yau Lafiyar ki' kalau kuwa?... Humeeh tace Lafiya lau. </p><p><br /></p><p>Umma Tace toh" Lafiya lau kike shine kika bar "mututum, shikadai "afalo ko' ruwa baki'kai masaba. baki ta turo tareda cewa Umma *ABDUL-JABBAR* nefa.. Da sauri Umma tace' "Abdul-jabbar fakikace'?.. tace "eh Umma shine, tace "ikon Allah nikam 'aiban'ma ganeshi" ba dama nan garin yake aiki?. </p><p><br /></p><p>Humeeh tace "Oho niban saniba, toh" yanzu Kuma meya zoyi gurin ki?. toh" waima Waya fadamasa mundawo nan garin?.</p><p><br /></p><p> tace Umma nimafa "abinda nake tunayi kenan, kawai nidai yakira ni yace wai "infito gashi nan "aharabar gidan mu, toh" shinefa kikaga nafita da sauri toh" Kuma kodanaje sai kawai naganshi'. </p><p><br /></p><p>Umma tace toh" aisai kije kiji da meyazo Kuma, tace Umma nidai gaskiya ba.. Umma ta katse ta dacewa wuce kitafi nace' kije kiji da meyazo, hakan Humeeh tawuce' tana gun-guni.</p><p><br /></p><p>_Nikam nace um-umhum su Humeeh anaso ana kawai market (kasuwa)_</p><p><br /></p><p>Kitchen tanufa tire Da Cup tadauka, tareda bude fridge taciro lemon juice da ever water masu sanyi, tajera "afarantin sannan tanufi gurinsa fuskarta ba walwala</p><p>yayinda kirjinta keta dukan uku-uku.</p><p><br /></p><p>"A hankali tayi sallama Cikin yar siririyar murya ta, idanunshi na'akanta ya amsa sallaman, a hankali tajawo Dan karamin table gabanshi tadora faranti, sannan takoma nesada shi kadan ta zauna.</p><p><br /></p><p>Batareda ta kalleshi' ba tace inawuni, shuru bai amsa ba tasake cewa inawuni nan ma shuru bai amsa ba, Dan haka sai tajuyo dasaurin do taga meyasa yaki amsa bai suwarta.</p><p><br /></p><p>Caraf suka hada idanu dashi' tsawon yan mintoci suna kallon juna, can sai ta kauda Kai gefe tace bismillah kasha ruwa.</p><p><br /></p><p>Cikin sanyin yace pls ataimaka azuba mani, "ahankali ta tashi tajeta zuba mashi Lemon juice din ta miki masa batareda ta kalle shiba,yayinda shi Kuma idanu shi suna kanta. </p><p><br /></p><p>Bayan tamika mashi saita komawa ta zauna, yayinda taketa cika tana batsewa fuskar nan nata babu walwala, ganin hakane yasa gaba daya Abdul-jabbar yadaburce yarasa ta iyazai fara..</p><p><br /></p><p>Har yagama shan lemon idanu shi nakanta' yayinda ita Kuma KO kallon inda yake batayi ba.</p><p><br /></p><p>Wata dabarace tafado mashi wayar shi naga yaciro, yayi dailling number Mama tareda sata a handsfreen, yayi Sallama Mata amsa yace Mama nakira wayar ki' dazu Amma baki dagaba Lafiya?.. </p><p><br /></p><p>Tace" eh Lafiya lau bana kusada wayar ne,"ainagani toh" Kuma Dana kirana sai ban sameka ba, yace</p><p>Kila "inata gurin da ba</p><p>Network. tace Oho" toh" yanzu ankaiku gurin daza kuyi "aiki?.. yace eh ankaimu Gibson jalo Barrack, shuru tayi batace' komai ba, (da'alama ta tuna wani abune) yace hello Mama naji kinyi shuru l hope dai Lafiya?..</p><p><br /></p><p> Tace' a ah bakomai nadai tuna wani "Abune,' Da sauri yace' inafata dai abinda kika tuna baisa kinji ranki yabaci ba?.. kinsa bana</p><p>san bacin ranki yanasa naji duk hankali Na yatashi.</p><p><br /></p><p>Tace a ah bakomai don haka ka kwantar DA hankalika, ALLAH yabada sa'an abuda "akaje nema, yace Ameen tace yaushe zakaje kidansu takwara ta?..</p><p><br /></p><p>_*kasan cewar tasan DA maganar zuwa wansa gurin Humaira*_</p><p><br /></p><p>Yace Mama gani "agidansu"My Cool, tace masha'allah kasa mesu lafiya?..</p><p>yace Lafiya lau suke", saidai kinsan wani abu?.. tace "a ah sai kafada yace' Mama My Cool tana fushi dani sosai ko" magana batayi maniba, saboda hakane yasa narasa ta "ina zanfara bata Hakuri. Kingani ma hada hararana takeyi pls Mama kiyi wani abun kinji?</p><p>Yakara she maganar cikeda shagwaba.</p><p><br /></p><p>Cikin Mamaki jin 'abunda yafada Humeeh take kallon shi, yayinda shidin'ma idanun sa suna "akanta yana sakar mata Murmushi, aranta kuma take fadin ji yadda yake' magana kamar wani karamin yaro.</p><p><br /></p><p>Murmushi Mama tayi har saida sauti shi yafito tacikin wayar, (Allah sarki Mama yanzu kam tuni tasaba da shangartar Abdul-jabbar, domin kuwa tun bayada yaji sauki shikenan sai yake zuba mata shagwaba "iya san ranshi yayinda ita Kuma take biye mashi)</p><p><br /></p><p>Tace toh" yanzu kaba takwarar tawa wayar,yace toh" tareda mikawa Humeeh wayar, idon shi cikin Nata takarba, yayinda take sakar masa' harara Wanda narasa gane kona meye..</p><p><br /></p><p>"A hankali tace Mama 'inayi, Tace Lafiya lau takwarata ya "Ummanki' da yayanki" ya kuma karatu?..tace duk Lafiya lau, tace toh" madallah. nan dai Mama tafada mata duk Abunda yafaru, tun daga yanda akai "aurenshi Da Lariya har zuwa rashin Lafiyar dayayi. </p><p><br /></p><p>Takara da cewa don ALLAH kiyi Hakuri kinji takwarata, duk wannan abun da yafaru nice' natilasta mashi Wanda ni kaina bansan yadda akai hakan tafaru ba</p><p><br /></p><p> Saidaga baya nagane cewa harda makircin Haj Jumma, kinga dayake "abun ba Saboda ALLAH akayi shiba sai gashi "DA SANNU" Allah yawarware komai.</p><p><br /></p><p>Don haka "inasan kimance Da duk "abunda yafaru "abaya, domin nasan dake dashi kuna SON junanku" saboda haka Ku manta da baya Kufuskanci gaba, Allah ya tabbatar Da Alkhairi tsakanin ku'</p><p>Kinji KO"?.. </p><p><br /></p><p>tace toh" Mama Insha'Allahu komai yawuce, tace toh" nagode ALLAH yaimuku Albarka</p><p>tace' ameen sai anjima sannan tamika mashi wayar.</p><p><br /></p><p>Yakarba tareda cewa Mama "Ina SONKI' sosai ga kewarki tada meni dayawa, dariya tayi tace Kai kam shiriri tarka tayi yawa, daga jiya zuwa yau shine kayi kewata dayawa?..</p><p><br /></p><p> Yace' Allah kuwa Mama sainaji kamar nashekara bana kusa dake", shiyasa nake rokon Allah yabarni da Mamanta, Murmushi tayi tace' ka kulada kanka sannan Karin ga shan maganin ka'</p><p>"Akan lokaci, saboda nasan halinka sarai baka San shan magani.</p><p><br /></p><p>Yace zanyi yadda kikace insha'allahu kice" ina gaida Baba Lami Tace toh" sai anjima ka gaida abokinka yace toh tareda kashe wayar.</p><p><br /></p><p>Ya kalli Humeeh itama shi take kallo, sannan tace' kaci *DARAJAR* Mama, Amma badan hakaba hmmm?... Yace ainasan dayau sunana SORRY KO?.. Kilama KO wannan ruwan da juice Umma ce' tasa kika kawo Mani Ko?..</p><p><br /></p><p> Bata bashi amsa ba saidai tace' Waya baka number Wayata, Waya fada maka mun dawo nan Yola than Waya baka Address Dina?..</p><p><br /></p><p>Murmushi yayi yace duk wannan questions din ni kadai?.. Kai tadaga alamar "eh, yace "aikam yanzu kuwa zanbaki "amsar tambayar ki'.</p><p>Nan dai yafada mata duk abunda yafaru, harda gani ta dayayi yakara da cewa Dr I S g</p><p>"Abokina ne Kuma shine Dr na.</p><p><br /></p><p>Murmushi tayi tace'</p><p>Nima ainagan ka, idanu yazaro Cikin Mamaki yace' shine kika kyaleni?.. tace' toh" mezance' maka?.. yace hmm My cool "inda kinsan halin Dana shiga adalilin SONKI' dabaki guje maniba.</p><p><br /></p><p>Tace toh" aikain...da sauri ya katseta dacewa Shhhh! don't say anything, just we do what Mama say.</p><p>Aikam Cikin lokaci kankani suka balle Da firar Soyayya, tareda tambayar bayan rabuwa nan dai kowa yafadi wa Dan uwansa, halin da yashiga dalilin rashin dan'uwan sa.</p><p><br /></p><p> Sun'nutsun sosai acikin firar Soyayya harbasu" San lokaci yajasosai ba, saidai kawai sukaji "ana kiran sallar La'asar</p><p>Kallon juna sukai suna dariya.</p><p><br /></p><p>Ya mike tareda kallon agogon hannun shi yace", kinga har lokaci yaja bansaniba bari natafi kar'anemeni </p><p><br /></p><p>Itama tamike tareda cewa toh" ya kalleta Cikin So da kauna yace' Kai my Cool bako cewa sai anjima KO sai yaushe?.. kodai kindai SO Na sosai ne?..</p><p><br /></p><p>Fuska tarufe da hannun ta tace' ah nikam aibanki kazauna muyita firaba, ya matsa kusada ita kadan yace' da gaske My Cool?. kaita daga alamar eh.</p><p><br /></p><p>Murmushi yayi yayinda yakejin Sonta yan karuwa acikin Zuciyar shi, yace nima zanso haka saidai yanayi aikin'mune sai a Slow, amma karki damu insha'Allahu "DA SANNU" </p><p>zamu kasance tare, har abada kedai kiyi mana Addu'a kinji me SANYI TA?.. </p><p><br /></p><p>tace toh" insha'Allahu zanyi. yace' yauwa toh"muje kirakani,</p><p>Har gurin mata tarakashi sannan takoma Cikin gida,</p><p>Zuciyar ta cike DA farin Ciki yaugata ga Special dinta.</p><p><br /></p><p>Umma ta kalleta tace' sai yanzu yatafi?. Cikin farin Ciki tace' "eh yatafi yace" yana gaida ke' tace' "Ina 'amsawa toh" meke tafedashi kuma?..</p><p><br /></p><p>Nan tafada mata duk yanda sukai harda wayan Da sukai Da Mama, tace' Umma Bari naje nayi sallah,</p><p>batajira amsar Umma ba tanufi hanyar toilet.</p><p><br /></p><p>Yayinda Umma tabi bayan "tada kallo tace Hmmm yaro" mankaza, Humaira ainasan haryanzu kinsan Yaron nan toh" Allah ya tabbatar Da Alkhairi tsakanin nace' </p><p>Toh Ameen.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dai-dai lokacin da Abdul-jabbar yake kokari fitadaga harabar gidan, toh" Kuma alokaci ne Abba ya kun'no hancin motar shi.</p><p><br /></p><p>Da sauri Abdul-jabbar yasauke glass din motar shi, domin KO Ba'a fada masaba yasan cewa Abban' su" Humeeh Saboda Kama daya hango.</p><p><br /></p><p>Shima Abba yasauke glass din motar yayi tareda tsurama Abdul-jabbar idanu, Cikin ladabi ya gaida Abba ya'amsa tareda cewa?..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat Ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page178-182</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*GAREKI MASOYIYAR "DA SANNU"*</p><p>*Wannan page naki ne ke kadai kiyi yadda kikeso dashi, MY HABITY SALMA USMAN gital group novel, inayi dake kamar yadda kikeyi Dani NAGODE SOSAI DA KAUNARKI AGARENI ALLAH YABAR ZUMINCI "DA SANNU" ALLAH ZAYA HADA FUSKOKIN MU LOVE U SO MUCH*💋💋💋</p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*</p><p><br /></p><p>*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wanene wannan?. SARAH tayi Murmushi tareda cewa Lah my besty shinefa "Daddy mu,</p><p><br /></p><p>Tace sorry My besty ban fada maki koni wacece bako?. toh kamar yadda kika sani sunana SARAH AHMED ABDUL-JABBAR, </p><p><br /></p><p>wayan nan najikin picture din sune' mahaifana wannan itace Mom dina Hajiya Maryam, wannan mahaifina Kuma shine governor jahar nan ayanzu dai nice babba agidan nan sai kan'nan Na gasunan,</p><p>wannan itace Esha baby wannan Kuma Zarah Mama,</p><p><br /></p><p> SARAH tayi dariya tace besty I hope kin gamsu, Cikin karfin hali Humeeh tace "eh Amma kinsan ban taba sanin cewa Dad dinku shine governor jahar nan ba?</p><p><br /></p><p>Idanu SARAH tarazo Cikin mamaki tace Kai besty kina Cikin garin Yola kice bakisan governor kuba?.. Humeeh tace Allah ban sanshi ba saiyau dana ganshi ahoton, kinsan nafada maki bamu Dade Da dawowa nan garin ba,</p><p><br /></p><p>SARAH tace' eh haka nefa, nan dai suka Esha baby da Zarah Mama suka gaida ita, dagan kuma suka nufi danning don cin Delusions din Da aka hadawa Humeeh,</p><p><br /></p><p>Bayan su gama sai suka koma falo suka baje kolin fira, yayinda rabin ahankali ta yana kan wannan hoton, suna cikin fira sai Mom tafito Humeeh ta gaida ita harta tambaye ta ya Umman ta da Abban ta tace Lafiya lau suke,</p><p> Sai bayan tayi sallah azahar sannan tayi shirin tafiya gida, </p><p><br /></p><p>Mom tayi mata kwatar abaya da turaruka DA mansha fawa masu asalin kyau da tsada, ta Kuma bata wasu turare da lifaya takaiwa Ummanta, tace toh ta godiya.</p><p><br /></p><p>Har gurin mota suka rakata saida sukaga fitarsu sannan suka koma Cikin gida. </p><p><br /></p><p>"A cikin mota kam Humeeh Sai tunani take tareda mamakin hoton datagani agidan su "Sarah, Wanda Sarah tace shine Daddy su"</p><p><br /></p><p>Caf aida badan da "Sarah tace' Daddy su ba tabbas datace' shidin Special dinta ne,</p><p><br /></p><p>Hakadai take ta tunani DA Kuma mamaki, can dai wata zuciya tace toh waike mamakin mekike shin kin manta dacewa "anakama?</p><p><br /></p><p>Da karfi tace' "eh hakane Kuma fa,</p><p>har saida Bala drive yajuyo yace ranki yadade kina magana ne? dasauri tace' a ah,</p><p><br /></p><p>A ranta kuwa take fadino "Oh ni A'isha tunda nake aduniya bantaba ganin Kama irin haka ba, irin wannan kama haka sai kace irin identical twins, haka take tasake sake harsuka isa gida.</p><p><br /></p><p>Suna shiga motar su Abdul-jabbar tana shigowa, Bayan Bala drive yayi parking sannan tafito tanufi cikin gida Cikin nutsuwa take takawa, har takusan shiga falon sataji ance Aminci Allah ya tabbata ga mai sanyin ZUCIYA ta.</p><p><br /></p><p>Ahankali tajuyo suka hada idanu tareda sakarwa juna Murmushi, yauma sanye yake da kakinsu Na SOJOJI, ahankali yakaraso gurinta saikuma yadan hade fuska yace' yawo kigaje ko?</p><p><br /></p><p>Kai ta girgiza alamar "a ah, yace toh' idan bayawo kikaje ba toh Ina kikaje saida ta turo Dan mitsitsin bakinta sannan tace Kai Special gidansu my besty Sarah fanaje shine naje yawo?</p><p><br /></p><p>Dariya tabashi ganin yadda ta turo Dan bakin hada wani bata fuska, sai yace toh" shine Kuma hada su fushi? bakin takara turowa tareda cewa toh" bakai bane kace naje yawo,</p><p><br /></p><p>Yace toh' yi hakuri aibasan gidan su new besty mu kikaje ba, Kuma ni aiwasa mana nakeyi nasan my Cool bazata ringa zuwa yawoba, kodan kar wasu surinka kalle Mani beautiful face dinta KO? toh" Dan Saki fuskar mana yafadi yana Murmushi, itama Murmushi tayi Wanda har saida wushiryar ta tabaiyyana.</p><p><br /></p><p> A dai dai lokacin da Dalter boy yakaraso kasan cewar taresu kazo, nan dai tashiga gaba suka bita abaya zuwa falo Bayan sun zazzauna sannan suka gaisa,</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yace Abba fa?.. tace' yafita yece OK aikilan kafin mutafi yadawo tace "eh Ina sa ran haka insha'allahu,</p><p>Dalter boy yace wa Abdul-jabbar shi Sam bagane Humaira ba wai yaga takara kyau da kiba, ita kam kunya yaka mata, don haka ta tashi tareda cewa tana zuwa tanufi sama.</p><p><br /></p><p>Bayan tafita sai Dalter boy ya kalli Abdul-jabbar yace J boy, dama suma Humaira mutanan Yola ne kamar ka?.. Kafada yadaga yace I think KO" Kuma aiki yakawo Abbansu nan ba,</p><p><br /></p><p>Dalter boy yace may be haka ne KO, aiki ya kwoshi KO Kuma "asalin kararsu kenan, dai-dai lokacin da Humeeh tadawo itada Umma,</p><p><br /></p><p>Da sauri suka sauka daga kan kushin suka tsuguna suka gaida Umma, ta amsa fuskarta sake har tana tambayar su ya Aiki?. sukace' Lafiya lau tace toh madallah sannan ta koma sama,</p><p><br /></p><p>Yayin Da Humeeh tashiga jera masu Delusion's din data shirya masa, bayan ta zuzzu bamasu', sai ta mike zata tafi da sauri Abdul-jabbar yace inazaki Kuma?</p><p><br /></p><p>Cikin jin kunya tace Zan shiga daga cikine har kugama, yace "ah 'ai idan baki kusa Dani abincin bazaya tafiba, amma Idan ina kallon beautiful face dinki sai nakusan ciyen wannan garar batareda nasani ba KO bahaka ba?.. Dalter boy?.. yace ummh dai-dai lokacin daya Cika bakin sa, da farfesun kayan ciki daya sha kayan yaji sai kamshi katashi.</p><p><br /></p><p>Yace yauwa toh kinji so come and sit here yanuna mata kusada shi, kasan cewar a three site suka zauna Dan haka sai ta zauna dan'nisa dashi kadan,</p><p><br /></p><p>Sunacin abinci suna zuba santi daga Abdul-jabbar din har Dalter boy, tana tayimusu dariya harsuka gama sannan ta kwashe kayan takai kicin,</p><p> </p><p>Bayan tadawo sannan Kuma suka cigaba da fira harda Dalter boy din, sundan taba fira sannan Dalter boy ya kalli agogon hannun sa, sannan yamike</p><p><br /></p><p> yace' </p><p>J boy yakamata mutafi haka nan yanzu fa 3:40Pm kasan akwai aiki agaban mu, Humaira mun gode sai kuma gani Na biyu tace nikeda godiya, sai anjima yace OK sannan yafita yabarsu.</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yace my Cool gashi har yanzu Abba baidawo ba gashi Kuma muza mutafi Saboda akwai Abunda zamuyi tace toh shikenan, yace ba damuwa kinfa San yace' yana San magana dani..</p><p><br /></p><p>Tace "eh haka yace so kutafi kawai idan yadawo sai nafada mashi kazo, yace toh' idan yadawo kitambayar mani shi lokacin dayake gida ya free sainazo KO?</p><p>tace toh" shikenan.</p><p><br /></p><p> Suna tafiya zata rakashi, tace' af my Special aina mata nafada maka, yace" me kenan fa?.. tace yau agidan su my besty Sarah kasan mena gani?.. yace "a ah saikin 'fada, my Cool, </p><p><br /></p><p>Tace wlh Daddy su my besty kamar kudaya dashi, jiyayi gabansa yafadi amma saiya basar yace' ah habadai?</p><p><br /></p><p>Da sauri tace ALLAH dakai dashi kamar irin identical twins din'nan saida shi yafika kiba kadan, yace ikon Allah, tace ai inata mamaki harnace kilama Dan' uwanka ne shi? yace' a ah bansan shiba nida nake bako agarin, ke Kama ce ba kawai, tace haka nefa,Kuma fa shine governor garin nan, </p><p><br /></p><p>Yace ALLAH sarki dai-dai Lokacin Da suka isa gurin motar, saida taga tafiyar su sannan takoma Cikin gida.</p><p><br /></p><p>Daga yadda yake Driving zaka fahimci gaba daya ransa abace yake, Saboda wani irin mugun gudu yakeyi akan titin kamar zaya tashi sama,</p><p><br /></p><p>Ganin hakane yasa</p><p>Dalter boy yawaiga ya kalleshi tareda cewa master duk wannan gudun dakakeyi iyakarmu fa Gibson barrack,</p><p><br /></p><p>Juyowa yayin shima ya watsa mashi idanun sa dasuka kada sunayi jajir, yace I know sannan yamaida hakalinsa ga driving, Cikin bacin rai yace' kajiko yanada mata dayara hakan yana nufin wato gaba daya yamanta damu",</p><p> yashafemu "ababin RAYUWAR SA" Saboda baya kaunarmu ko? saidai kuma "DA SANNU" zayayi NADAMAR "Abunda ya'aikata agaremu,</p><p><br /></p><p>Dalter boy yace' master nifa ban fahimce kaba domin gaba daya maganar adunkule kayita, don haka bansan inda kado saba, batareda daya kalleshi ba yace' aiba zaka gane ba ahaka harsuka isa barrack din.</p><p><br /></p><p>*************</p><p>Yau Monday don haka Humeeh yau sai 4:00pm zasu dada makaranta Saboda sunada lectures kuma zasuyi practical, zaune suke itada Sarah fitiwarsu kenan daga masallaci sunyi sallah azahar,</p><p><br /></p><p>Sarah tace Kai! Kai!! kai!!! besty tashi mutafi ga mutunki nan Chan ya iso, muyi sauri kafin yashiga kinsan shiba sauki, Humeeh tace hakane fa dai-dai lokacin da suka nufi cikin holl din'da zasuyi lecture din,</p><p><br /></p><p> Sarah tace I hopo kinyi switch off din phone naki? Kinsan shi Dan ka'idane, Humeeh tace tundazu, dai-dai lokacin da suka shige cikin holl din.</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar ne agaban Abba kasan cewar sunyi wayada Humeeh tace" masa Abba yana gida don hakane yaje,</p><p><br /></p><p>Tun bayan dasuka gaisa da Abba kanshi ke kasa Saboda wani irin kunyar Abba yakeji, shikam Abba kallon Abdul-jabbar yake yayinda yake mamakin irin wannan Kama komai irin guda haka, hatta da kunbar hannun irin dayane.</p><p><br /></p><p>Saida yagama nazarin sannan yace samari ya sunanka kace'?...Cikin jin nauyi yace Abdul-jabbar, "ance daga Kaduna akaturoka nan kayi kos KO? yace "eh,</p><p><br /></p><p>Abba yace "Ok shin wanene mahaifinka "a Kaduna?.. Abdul-jabbar jiyayi gabana yafadi yayinda yaji nutsuwar shi tana Neman kubce masa,</p><p><br /></p><p> Shi Sam baiyi tsammani wannan tambayar Abba zayayi masa ba, saida ya tattara natsuwarsa sannan yaba Abba amsa da cewa?..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat Ce💞</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page183-187</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*</p><p><br /></p><p>*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Alh ya'u nakaka shine mahaifina, kuri Abba yayiwa Abdul-jabbar da idanu yana kallon shi cikin matsananci mamaki, yace' kace' sunan ka Abdul-jabbar KO?.</p><p><br /></p><p>Cikin jin nauyi yace "eh Abba sunana kenan, Abba yace toh" Abdul-jabbar "Inaso kafada Mani ainihin gaskiya wanene mahaifinka "a cikin Kaduna?..</p><p><br /></p><p>"A hankali Abdul-jabbar yasake cewa Alh ya'u nakaka shine mahaifina, Abba yace bashi bane mahaifika, gaban Abdul-jabbar ne yafadi yayi da yaji zufa tana karyomasa kai yadukar batareda yace' komai ba, Abba yace nasan Alh ya'u nakaka dan'shi daya ne Yusuf, Amma meyasa zakayi mani karya Abdul-jabbar?.</p><p><br /></p><p>Cikin sanyi murya yace Abba kayi hakuri wlh duk fadin Kaduna banida Ubanda yawuce Alh ya'u nakaka domin shi nasani,</p><p><br /></p><p>Abba yace OK" toh" wacece Mahaifiyar ka?.. yace sunanta Hajiya A'isha, yace' bata fada maka ko wanene mahaifin kaba?.. Da sauri yadago dakai yakalli Abba Wanda shima din kallon shi yake, dukar dakai kasa yayi batareda cewa komai ba,</p><p><br /></p><p> Abba yace shin Abdul-jabbar baka San "mahaifinka bane?.., sannan Kuma "mahaifiyar ka' bata fadamaka kowane shiba?.., Cikin karfin hali Abdul-jabbar yace Abba tafada mani saidai banasan nasan shi dama can bansan shiba don haka ko yanzu ma banasan nasanshi </p><p><br /></p><p>Shuru Abba yayi domin yanzu kam zargin dayakeyi akanshi yazama gaskiya, dama Abba tun ranan farko daya ga Abdul-jabbar yagane kosha waye, jiyayi wani irin Sanshi tareda matsananci tausayi shi, yaka mashi,</p><p><br /></p><p>"A hankali Abba yace Abdul-jabbar meyasa baka San kasan shi waishin bakasan cewa kowani Da' da' uba yake adoba?.. shi bakasan cewa duk matsayin mutun duk mulkinsa dazan akace yau bashida UBA toh" darajarshi fa ragewa take a gurin mutane ,</p><p><br /></p><p>Shin meyasa bakanan kasa kowaney mahaifinka?</p><p>"A hankali Abdul-jabbar yabude baki daniyar yayi magana, saikuma yakasa saka makon wani irin zafi dayaji ZUCIYAR shi nayi,</p><p>Kai yadago tareda yazubawa Abba idanu shi dasuka kada sukayi jajir,</p><p><br /></p><p>Sai Kuma yasaki kuka tamkar karamin yaro kamar kuma ba SOJA ba, SOJAN ma wanda yake sanye uniform ajikinsa kuka yake mai ban tausayi, Wanda kanajinshi kasan 'andade "anasan ayishi ba'asamu damaba sai wannan lokaci,</p><p><br /></p><p>Cikin kuku yace Abba tunban San kainaba nake san ganinshi, ZUCIYATA tarayu da KAUNAR shi saboda tunani nasan shi harsaida nakamuda CIWON ZUCIYA, wanda haryanzu inashan magani, Amma meyasa shi baya sona meyasa tun Ina cikin mahaifiya ta yatsaneni? </p><p><br /></p><p>Abba shiyasa nima yanzu bana San ganin shi tunda shima baya sona, pls Abba Ina son Humaira kar kace bazaka bani auren ta ba Saboda naka sance banida mahaifi sai Uban riko,</p><p><br /></p><p>"Ahankali Abba tadaga hannu sama yanatafan kwarara Addu'a, saida yayi Addu'a sosan sannan yasauke hannu tareda karasa dafadin ALLAH Kaine maji rokon bayinka ALLAH mun gode maka daka amsa Addu'a mu,</p><p> </p><p>Cikin sanyi murya yace zonan kusa dani Abdul-jabbar "aikam da sassarfa Abdul-jabbar yakarasa gurin sa, Abba yace haba SOJA sukutun yake kuka haka kamar MACE ayya kuwa SOJAN NE?.. Kai SOJAN NEFA tunda gashinan harda kakinsu Ajikin shi,</p><p><br /></p><p>Cikin zalaya Abba yaci gaba da cewa</p><p>Kai Kuma fa shi din JARUMI NE KO sunan shi kawai abun kallo ne, toh" koya manta da hakan ne"?.hmm Lallai nasan "DA SANNU" zaya gane cewa shinefa</p><p> ABDUL-JABBAR jikan "ABDUL-JABBAR Da "ABDUL-JALAL Daga "AHMED DA A'ISHA" Addan MAHAMUD Angon "AISHA HUMAIRA insha'allahu,</p><p><br /></p><p>Cikin mamaki Abdul-jabbar yasaki bakida hanci yana kallon Abba, dayake tafaman doka masa murmushi, cikin rada Abba yace kayi sauri kashare hawayen nan kafin Humaira tazo tagani,</p><p><br /></p><p>tace tafasa auran tunda kaidin RAggo ne kana sanye da kakin SOJA amma kana kuka kamar mace, Abba yakarashe maganar tareda rike haba,</p><p><br /></p><p>Da sauri yashare hawayen tareda yin murmushi sannan ya dagoda Kai yatsurawa Abba idanu, shisai yanzu ma yagano kamar DA sukeyi DA Mama wani irin dadine yaji yaratsashi,</p><p><br /></p><p>"Ahankali Abdul-jabbar yace KAWU NA Mahamud Abba yace na'am ABDUL-JABBAR da sauri yamike ya rungume Abba shima rungume shi yayi cikin tsananin farin cikin Abdul-jabbar yace Abba ya'aikai kaganeni?..</p><p><br /></p><p>Abba yace' haba Abdul-jabber "ai tun ranan farko danaganka gane cewa Kaidin jinina ne, balle kuma ko makaho yalalubaka zaya gane kokai Dan waye, baki Abdul-jabber yaturo kamar karamin yaro yace Abba toh" nidin Dan waye?..</p><p><br /></p><p> Dariya Abba yayi yace' Abdul-jabbar kenan "ai kobaka taba sanin shiba nasan kaji Labarin shi gurin Maman ka Kuma aikaji dazu nafadi sunan shi akirarin danai maka KO?.. </p><p><br /></p><p>yace Abba toh nikam bashi bane "Babana, DA sauri yace kul naji kasake jin kalman nan tafito daga bakin ka, toh" idan bashi bane "Babanka toh" wanene Baban Ka?.. cikin sanyin murya yace' Abba toh" Ai shidin ne baya SONA Abba yace Waya fada maka baya son ko?.</p><p><br /></p><p> Nan dai Abba yafada masa duk "abinda yafaru Wanda "Aina'u ce duk keda sahannu 'afaruwar komai, jiyayi SON mahaifinsa yasake kamashi amma fa duk da hakanan yanajin Dan haushin Sa kadan, narashin BIN CIKEN da baiyi ba kawai ya yanke hukunci.</p><p><br /></p><p>Abba ya kalli Abdul-jabbar yace toh" yanzu fada mani Address "inda Adda ta take dama yau zantafi Kaduna Saboda wasu kayana dasuka fito tacan, Saboda haka yau agidan Adda ta Zan sauka insha'allahu, </p><p><br /></p><p>dariya Abdul-jabbar yayi yace Abba Ka tsaya mana nakara ganinka da kyau,</p><p>Shima dariya yayi yace "a ah aikai kagan'ni Adda ta yarage tagani, naganta Kuma yaudin nan zamu haduda izinin Allah,</p><p><br /></p><p>Yamike yana cewa Bari nakira Umman taku kugaisa KO?... Abdul-jabbar yace toh" Abba yana gaba Umma tabiye da shi'abaya, tana fadin ikon Allah Ashema shin din Dan gida ne nan dai suka gaisa Da Umma, yayida Abdul-jabbar yasaki jikin shi da sun har suka danyi fira kadan,</p><p><br /></p><p>Sannan yace zaya koma gurin aiki Abba yace toh" shikenan, shima kamar yadda yafada masa insha'Allahu idan ma yasamu yadda yakeso zaya taho da Addan, yace toh" shikenan sai yadawo nan dai sukai Sallama yatafi.</p><p><br /></p><p>Yau sai karfe 4:00Pm su Humeeh suka tashi daga school don haka agajiye ta isa gida, koda taleka dakin Umma tana Sallah don haka itama sai tashiga wanka tayi sallah sannan tanufi kichin don wata irin yinwa takeji,</p><p><br /></p><p>Saida taci abinci tayi nak sannan tanufi dakin Umma tana cewa sannu da gida Ummata, tace yauwa ake za'ayiwa sannu sai yanzu kuka tashi? Tace' Hmm kedai Umma sai yanzu fa, toh" Sannun Ku' yauwa Umma Ina Abba Na?</p><p><br /></p><p>Abbanki kam yana Kaduna da sauri Tace' Kaduna Kuma? Umma Lafiya tace' Lafiya lau nan dai tafada mata komai gameda Abdul-jabbar, cikin mamaki tace Umma yanzu Abdul-jabbar Dan Uwanane?.. tace' najini kuwa,</p><p><br /></p><p>Wani irin dadi taji yaratsata da sauri ta tashi tanufi dakin ta, yayinda Umma tabi bayan ta DA kallo tana murmushi, koda ta isa daki wayar ta taciro ajaka takunna wadda ta kasheta tun lokacin da zasu shiga lecture,</p><p><br /></p><p>Kiran Abdul-jabbar ne first Da yafara shigowa dariya tayi Sannan tadaga tareda sa wayar a handsfreen, jinai yace' haba my cool wannan wani irin "abune haka yaza'ai ki kashi waya tun dazu inata faman nema layinki wai switch off Lafiya?..</p><p><br /></p><p>tace ah Malam aikai Zan tambaya Lafiya kakirani sai faman yimani ihu kakeyi, alhalin ni bansan komai wanene ba Kai wannan number warron number ce', don niban mataba ganinta ba sai yau Saboda haka sai anjim, </p><p><br /></p><p>Da sauri yakatse tada cewa ke! Ninefa Abdul-jabbar fuska tayamutse kamar yana ganinta tace' waye Kuma haka nan?.. jitayi Ciki sarkewar murya yace' Special dinki nefa, harza tace Oho sai tafasa sai Kuma ta kyalkyace da dariya,</p><p><br /></p><p>"Ahankali yasake ajiyar zuciya tareda cewa haba my Cool wannan aisaikisa ZUCIYAR ta tarwatse, ke bakisan haryanzu akwai sauran gyanbo acikinta ba?.. cikin dariya tace Sorry my Special one banyi niyar bata maka rai ba,</p><p><br /></p><p>tace kasa meye yace a ah saikin fada tace' wannan shine karona farka arayuwata danai wasada abokin wasana, yace "OK toh" ni abokin wasanki ne? tace "eh mana, yace eyyee lallai ma yarinyar nan waya fada maki?.. tace' ah tun yaushe naji komai, yace haka ne Abunda kikaji, Kai no wonder nafaye Son ki dayawa Ashe kedin jininace,</p><p><br /></p><p>Tace toh" ainima "inason kadayawa harfada zazzabi saida nayi,</p><p>yace Hmmm Son Danake yimuku kedai Daddy yayi yawa sosai tunda har saida ya haifarmani DA ciwon ZUCIYA,</p><p><br /></p><p>tace toh" Amma meyasa danace ko kasan Daddy su my besty sai kace Kai baka sanshi ba, yace toh" mezan ce maki my Cool bakisan Abunda mutumin nan yai mana bane shiyasa,</p><p><br /></p><p>Da sauri tace kodai meyayi maka shi din dai ne mahaifinka </p><p>Don haka Ka gyara kalaman ka, so fadin munanan kalamai ga iyaye badabi'abace me kyau ga mutumin kirki irin ka, shi lamari duniya DA kagani idan Mutum yabi ahankali toh" "DA SANNU" Allah zaya warware masa komai,</p><p><br /></p><p>Nan dai tayi tamasa magana gani masu ratsa zuciya Wanda yaji kaunarta takarashiga aranshi, Daga nan Kuma sai sukacigaba da tsokanar junansu me cikeda Soyayya.</p><p><br /></p><p>*Kaduna*</p><p>*************</p><p>Alh ya'u nakaka ya kalli Abba bayan sun gama gaisawa sai yace" bawan Allah ban bangane kaba fa, Abba yai murmushi tareda cewa ainasan baka ganeni ba Amma dai aikasan Haj A'isha Mahaifiyar Abdul-jabbar KO?</p><p>Cikin mamaki yace'</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞Lufhat Ce💐</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page188-192</p><p><br /></p><p>Second to the last</p><p>page</p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>_*Slm Masoya wannan littafin kuyi hakuri da sunan shi za yakare Ina nufin "DA SANNU" zamuga karshen shi Lafiya Dani daku insha'Allahu nagode sosai da kawar Ku*._</p><p><br /></p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*</p><p><br /></p><p>*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Niko nasan ta inafata dai lafiya?.. Abba yace'l lafiya lau, sunana Alh Mahamud ni mutumin Yola ne "amma na taba zama agarin nan idan tabayin manager Bank a G T ada, amma yanzu banayi nakoma can Yola,</p><p><br /></p><p>kuma ni kanine "agurin Hajiya "A'isha mundade muna Neman ta, Allah baisa mungan taba sai yaune cikin gudurar ubangiji mukasamu Labarin inda take agurin danta, Abdul-jabbar toh" shine nazo natafi da ita idan bada muwa?..</p><p><br /></p><p>Tunda Abba yafara magana Alh ya'u nakaka yake Murmushi farin ciki najin wannan daddadan labari, yace ikon Allah dama duk abunda kaga yayi farko toh" idan akayi hakuri "DA SANNU" za'aga karshen shi,</p><p><br /></p><p>Abba yace'wannan haka yake nan dai Abba yabashi labari "abunda yafito da Mama gida, Alh ya'u yace kai wasu matan sai "ahankali kaji irin wannan makirci haka, kai Allah kayi mana tsari da shaidanun mata, ameen</p><p><br /></p><p> Abba yace Ameen nan dai shima Alh ya'un yabashi Labarin tun lokacin daya hadu dasu har zuwa yanzu, Abba yaita godiya Alh ya'u yace bakomai aiyiwa kai sannan yakira Hajiya karima matar shi suka gaisa,</p><p><br /></p><p>Bayan komai yalafa sai Alh ya'u yakira Y Y K awaya yace' masa yajeya dauko masa "Mama yakawo ta nan gidan shi yanasan ganin da, Y Y k yace' toh".</p><p><br /></p><p>Dagan suka cigaba cigaba da fira har lokacin da Y Y k shida Mama suka iso da Sallama suka shiga falon, bayan sun gaisa sai Mama tace" Alh gani yusufa yace kana son ganina nace toh" Allah yasa Lafiya?..</p><p><br /></p><p>Yace" lafiya lau dama wannan bawan ALLAH ne yazo gurin ki, yafada yananu namata inda Abba yake zaune yana tafaman doka Murmushi, kuri tayi mashi da idanu tabbas baza taba manta wa da wannan kyakkyawa Murmushi ga fuskar dan'uwanta duk dadai yanzu yazama babban Mutum. </p><p><br /></p><p>da sauri ta tanufi inda yake dai-dai shima yataso Hannun shi tareke tareda cewa wannan MADO name, yace" nine ADDA rungume juna sukayi suna farin cikin ganin juna, Mama kam harda kuka tayi najin dadin ganin dan'uwanta, yace' Adda na ashe Zan sake ganin ki?..</p><p><br /></p><p>Tace mado Na gashi Allah ya hada mu yace' haka ne toh" Allah mungode maka, tace Allah "abun godiya kallon shi take cike da mamaki tace madona kazama babban Mutum, </p><p><br /></p><p>dariya yayi yace' Addana kenan niko sainaga kamar bake kika haifi wannan santalelen saurayin nan Abdul-jabbar ba,</p><p>tace hmmm kana nandai yadda nasanka da tsokana bakasan yanzu kagirma bako?..</p><p><br /></p><p>Dariya yayi tareda sake rike Hannun ta yace" a ah idan Ina kusadake nidin yarone harma dai idan kince MADO na, yakara she magana yana dariya itama dariyar takeyi, nan dai sukan taba fira yaushe gamo sannan Abba yace yanason yatafida Mama gidan Malam su gaisa.</p><p><br /></p><p>Alh ya'u yace idan bada muwa shima zayaje sugai sa, Abba yace badamuwa, nandai suka dunguma sai gidan Malam, bayan "angama gaggaiwa sai Abba yaiwa Mlm bayanin komai tareda nunamasa Mama,</p><p><br /></p><p>Sosai Mlm yayi Fari Ciki tareda sawa Alh ya'u nakaka Albarka dagan kuma sai aka ajiye maganar lafiya Yola gobe insha'Allahu.</p><p><br /></p><p> ********""""*********</p><p>Washe gari karfe goma nasafe jirgin su yatashi zuwa Yola, Abba Alh ya'u nakaka Mlm Hajiya karima gwaggo da Y Y k, Abba da Alh ya'u nakaka sune suka dauki nauyin lafiyar , dan Kari kaji masu abida abunsu kurada kallabin kitse,</p><p><br /></p><p>_*To mukan saidai muce "asauka Lafiya*._</p><p><br /></p><p>💐💐💞💞💐💐</p><p>Sun isa Yola lafiya Abba ne yakira bala direba yazo yadauke su, direct gidan Baba gen yace" bala yakaisu, bayan yasauke su sai yace yaje yadauko Umma da Humeeh kasan cewar yau basuda lecture,</p><p><br /></p><p>Labari Abdul-jabbar dan"uwanta kuwa ne tuni ta fadawa mutanan ta, watoh Hannah da Haleeh</p><p>Sarah kuwa tace sai sun hadu gidan baba gen,</p><p><br /></p><p>*GIDAN BABA GENR*</p><p> Baba gen da Hajiya Binta suna zaune a tamfareren falonsu" suna fira sai jin Sallama sukai,</p><p><br /></p><p>Abba yana rikeda hannun Mama suka shiga falon ahankali ya karasa gurinsu gaba daya dashida Mama suka tsugunna gabansu, yayinda sukuma kallon sukawai suke fukarsu cikeda mamaki, Abba yace' Baba Hajiya yau ga Adda A'isha Allah ya baiyyana mana ita,</p><p><br /></p><p>Da sauri Baba gen yace Masha'allah Allah mungode maka, yayinda ita kuma Hajiya Binta ta rungume ta tareda sakin kukan farin Cikin tana cewa Allah nagode maka, daka baiyyana Mani Amanar daka bani dama "ance mahakurci mawadaci, gashi damukayi hakuri muka barwa Allah komai gashi "DA SANNU" Allah ya baiyyana ta.</p><p><br /></p><p>Nan dai akai ta farin Ciki harda Baba engr da Matarsa kasan cewar Baba gen yace akira shi, sai da</p><p> komai yalafa sannan Abba yagabatar da Alh ya'u nakaka da matar sa tareda dan shi Yusuf, sune suka taimakawa Mama tareda danta Abdul-jabbar, sannan yagatarda Malam Garba da gwaggo sune sarakan shi.</p><p><br /></p><p>Aikam nan su Baba engr sukai tazuba godiya tareda samashi Albarka, Alh ya'u wlh bakomai ai anzama daya, bayan komai yalafa sai matar Baba engr tace' A'isha toh" Inashi maigidan nawa banga shiba?..</p><p><br /></p><p>shuru tayi tareda dukarda kai kasa Saboda kunya irin ta fulani, Abba yayi dariya tareda cewa Hajiya aikam Santalelen maigida yana nan SOJA amma sai kin bada toshi Zaki ganshi, tace au haka ne?.. Cikin wasa yace' "eh Saboda haka kawo nikuma yanzu naje nataho dashi.</p><p><br /></p><p>Da sauri Baba engr yace Masha'allah Mahamud yimaza kaje kataho Mani da ABOKINA, Abba yace toh" yayinda matar Baba engr ta sake cewa yauwa jeka tahodashi, idan naga yayi Mani kagasai nabada toshi dakyau idan kuma baiyimaniba sai akai kasuwa, tafada tana dariya gabadaya falonma dariya akayi, yayinda Abba yamike tanufi hanyar fita yana cewa sosai kuwa zayayi maki kilama kibar Baba engr ki dauke shi.</p><p><br /></p><p>Yana fita sai gasu Humeeh sun iso key ya amsa Hannun bala direban yace' su shiga Ciki zayaje yatahoda Abdul-jabbar, sukace toh tareda shiga Cikin gidan.</p><p><br /></p><p>Abba bai tsaya ko'inaba sai Gibson barrack, bai samu matsalaba gurin tahowada Abdul-jabbar, suna tafiya suna fira yayinda Abdul-jabbar kejansu Abba kuma yana gefen shi yayinda Dalter boy yake baya kasan cewar harda shi.</p><p><br /></p><p>Abba yana fadawa Abdul-jabbar cewa?.. tareda su "Alh ya'u nakaka suka zo, harda abokin shi "Y Y K, Abdul-jabbar yaji dadin cewa harda Y Y k akazo, yace Abba duk family sun hadune?..</p><p><br /></p><p>Basu naduba tukun amma zasu hadun idan ka'isa, yace shi kam nasan yazo KO?.. Abba yace waye shikuma?...baki yaturo tareda cewa shi din mana Daddy su" bata rai Abba yayi yace ayya Abdul-jabbar yanzu Daddy nakane shi Ku.a Daddy wasu, Ai kafin yazama Daddy wasu" Daddy ka yafara zama, yace' Abba toh" aisu" yakeso nibaya sona shiyasa nace sh....</p><p><br /></p><p>Kasa karasa wa yayi saka makon kallon Da Abba ya watsa masa tareda cewa baza kadaina bako?.. da sauri yace' yi hakuri Abba na daina, kyale shi Abba yayi baice komai, can sai yace Abba kafada Mani yadda "Baba gen da "Baba eng suka banbanta,</p><p><br /></p><p> Saboda "Mama tace mun "sunyi Kama dajuna sosai wai harkaya irin daya suke sakawa, Saboda tsananin kamar su bakowa yake gane su ba, haryanzu mada suka tsufa kaya iri daya suke sakawa.?..</p><p><br /></p><p>Gaskiya nikuma sona ke nagane su", dakaina batareda "annuna munsu ba.</p><p>Dariya Abba yayi tareda cewa?...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💞Lufhat ce💐</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p> DA SANNU</p><p>💞💞💞💐💐</p><p>💐💐💐💞💞</p><p><br /></p><p> page193-200</p><p><br /></p><p> END</p><p><br /></p><p> NA</p><p><br /></p><p>💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ</p><p> OR</p><p> (MEENAT)</p><p><br /></p><p>Alhamdullah!</p><p>Alhamdullah!!</p><p>Alhamdullah!!! nagode ALLAH daya bani ikon fara littafin nan lafiya, ya kuma bani ikon gamashi lafiya Allah kabani Ladan Abunda Na rubuta,tareda wayanda suka karanta inda kumanayi kuskure kayafe Mani, tareda wayanda suka karanta Ameen.</p><p><br /></p><p>----------------------------------------</p><p>*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*</p><p><br /></p><p>*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*</p><p>----------------------------------------</p><p><br /></p><p>*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>✍🏾</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tabbas har yanzu ma kaya iri daya su" kesawa, don haka Bari nafada maka yadda zaka gane su kaga "Baba gen baya dariya saidai yanada yawan murmushi, kuma bayada yawan magana,</p><p><br /></p><p>Shikuma Baba engr yanada magana sosai sannan yanada yawan dariya, nan dai Abba yai tafada mashi yadda suke har suka isa gidan da taimakon Abba tunda baisa gida ba.</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yanata Mamaki wannan tangamemen gida haka kusan unguwa guda, haka dai suka shiga Cikin gidan security kuwa gasu nan birjek, bai tashi tsinkewa ba saida suka shiga tamfatsetsen falon dayaji kayan more rayuwa wai ran kashi aljannar duniya kenan.</p><p><br /></p><p>Cike falon yake Da mutane kasan cewar bayan tafiyar Abba sai Baba engr yasa Waya, yana takiran ya'ya'da jikoki suzo akwai family mitin Saboda haka falon cike yake wasu mabasu isoba tukun,</p><p><br /></p><p>Abun Mamaki shine saida Baba engr yagama kiran kowa Sannan yakira Daddy, yace yazo shida iyalinsa yanason ganin su yanzu-yanzu.</p><p><br /></p><p>Shikam Abdul-jabbar gaba daya daburcewa yayi Saboda ganin yawan mutane haka, gashi kuma duk ahankalin su' yana gurinshi.</p><p><br /></p><p>gurin Y Y k yanufa ya zauna tareda cewa Kai Nawa irin wannan kollo "aisaina buga tuntube nafadi, kallesu fa duk nikadai suke kallo, Cikin rada yace' ka kallesu" da kyau mana meka gani acikin kwayar idanun su?...</p><p><br /></p><p>"Ahankali ya kalle su" ba'abunda yagani akwayar idanunsu" sai zallar kaunarshi gawani lallausan Murmushi dayake tashi "a fuskokinsu", jikin shi ne yai sanyi "aranshi kuwa fadi yake duk wayannan di yan'uwana ne?.. Oh ashe ni Abdul-jabbar dandangine haka, jiyayi wani irin kaunarsu yadarsu a zuciyar shi Cikin kan-kai lokaci.</p><p><br /></p><p>"Ahankali yamaida kallon shi gasu" Baba engr aikam sai yaga Baba gen yanata Murmushi fuskarsa cikeda farinciki naganin wannan santalele Saurayi wai jikansa ne, kuma magajin shi kai aidole yai farinciki tareda godiya da wannan kyauta da Allah yabasu.</p><p><br /></p><p> Shima Baba engr dayake amsa waya Murmushi yake tareda yiwa Abdul-jabbar nuni da hannu alamar yazo garesu', "aikam da sauri Abdul-jabbar yatashi jikin shi har yana rawa yanufi gurinsu domin jin kaunar su yakeyi har cikin jininshi, tsakiyarsu yazauna ya kalli Baba gen haryanzu Murmushi yake sai ya kalli Baba engr shima Murmushi yake amma sai yamika wa Abdul-jabbar hannun shi yakama ya kalli Baba gen shima hannun yamika masa yakama yahada hannu Baba engr dan baba gen ya rungume "akirjinshi wani irin kaunar su yaji har cikin jinshi.</p><p><br /></p><p> Sai kuma yasaki kuka Wanda Ina kyauta ta zaton nafarinciki ne, dai-dai lokacin da Baba engr yagama amsa wayar tareda dora hannushi guda saman kafadar Abdul-jabbar Sannan Cikin zoyala yace kai "ashema wannan SOJAN raggo ne ban saniba, Cikin kuka yace "eh din "aikam gabada ya falon "akasa dariya, juyawa yayi yakalli Baba gen Cikin kuka me kunshe da farin Ciki yace toh Kai kuma baba gen mekace?.. Cikin Murmushi yace toh" ni mezan ce' tunda Na gashi magajin Nawa raggo ne, yace' au haka neko?.. to shikenan dama bakusanmu shiyasa Ku kabarmu munata faman shan wahala badan Allah yasa Baban abokin Na yataimake muba dashikenan hakaza kubarmu mukare rayuwar mu acikin wahala nida mama Na KO?... </p><p><br /></p><p>da sauri suka rungume shi suna cewa kayi hakuri duk abunda kaga yasamu bawa toh dama can Allah yatsara hakan sai yasa meshi kuma wani lokaci jaraba mutun ubangiji yakeyi idan ka kwantar Da hankalin ka saikaga "DA SANNU kacinye jarabawar kuma dakace bamusan ka waya fada maka bama sonka?.. Baba engr yace' kalli can ahankali yadaga Kai yakalli tulin jama'ar dake falon Cikin sanyi murya yace' nagansu, yace toh dukkan sun masoyan Kane wasu" mabasu zoba tukun saboda haka duk muna sonka, yace nima Ina sonku.</p><p><br /></p><p>Nan Dai Baba engr yayi tafada masa irin yadda suke sanshi daga nan kuma yakira Adda Uwa yace tayita nuna masa kowa da kuma yadda suke", "ahankali Abdul-jabbar yagane kowa yawancinsu duk abokan wasa shine aikam sunata zolayar shi bayan komai yalafa sai yakoma kusada Y Y k yanzu. dai-dai lokacin da Daddy yashiga falon da Sallama iyalansa nabiye dashi, gurin su baba yanufa yazube tareda gaidasu suma iyalain shi haka sukayi, Sarah ce itada Esha baby da Zarah Mama suka nufi kusada Humeeh suka zauna Sarah cikin rada tace ke! my besty lafiya naga all family here?..</p><p><br /></p><p>tace Lafiya lau za'yi mitin ne tace OK dai-dai lokacin da idanun ta yasauka akan Abdul-jabbar, Cikin tsoro tace' my besty waye wancan din mai kamada Daddy mu?.. Esha baby tace' eh fa, Cikin rada tace you brother Abdul-jabbar da sauri tace' don Allah?.. tace Allah kuwa aikam da sauri suka tashi dukkan su Esha baby da Zarah Mama suka nufi guri Abdul-jabbar suka bufe gaban shi tareda Kama hannun shi sukace da gaske Kai Hamman mune?.. inaka shiga munata son ganin ka amma bamu ganka bai sai kuma suka fashe da kuka sukace Hamman mu muna sonka. </p><p><br /></p><p>kallon su yake yayinda yaji kaunar su" takamashi rungume su yayi shima kukan yake yace, nima inasanku sosai inata neman inda yan'uwana suke amma bansan inda suke ba sai yau Allah yahadani rabin jikina Ina sonku sosai, Sarah tace pls Hamman karka sake tafiya kabarmu kaji?.. yace "a ah ba'inda zayi Ina nan tareda Ku duk dacewa Daddy Ku baya sona, Cikin tsoro esha tace kai! Hamman mu Waya fada maka cewar Dadd'mu baya sonka?..Cikin Dan jin haushi yace ba shine yakori Mama Na tun'ina Cikin Ciki kinga hakan yana nufi baya son muke nanko?.. Kai take girgizawa alamar a ah.</p><p><br /></p><p>dai-dai lokacin da Daddy yakaraso gurinsu ya zauna idanu suka hada shida Abdul-jabbar Daddy jiyayi son Dan'nashi yana ratsashi shima Abdul-jabbar din haka yaji kaunar Daddy yana shi garshi, Abdul-jabbar ne yakauda Kai gefe hannun Daddy yasa yajujo da fuskar shi tareda cewa my Son baka son ganina ne?...Cikin kuka yace' Daddy toh' aikaine bakas....bai bari ya karasa ba yajawo shi ya rungume shi yana kuka tareda cewa Ina Sonka my son kuyafe Mani abunda nayi maku duk sharri makirci Aina'une, nan dai Daddy yabashi hakuri tareda zuwa gurin mama itama yabata hakuri tace bakomai dama haka Allah yatsara hakan sai yafaru,</p><p>harda Aina'uma tabasu hakuri sai kukan nadama takeyi, gatadai Cikin dauka amma duk tare me ta lalace, nikam nace alhakine.</p><p><br /></p><p>Bayan komai yalafa sai Mlm yayitayi nasiha mai kashe jiki musamman ma "akan mata dabasu San zama da kishiyoyin su Lafiya,</p><p>har Mlm zaya rufe taronda Addu'a sai Daddy yace yanane man alfarma da amayar da auren shi da A'isha aikam bawani bata lokaci mlm yafadi sadaki Daddy yabayar aka daura aure,</p><p><br /></p><p>bayan "angama daurin auren sai Abdul-jabbar yace Daddy wani abunake so kayi Mani...yace fadi abunda ka keso indai baifi karfina toh" zanyi maka shi ko mene ne?... yace aure nakeso dariya akayi falon Daddy yace Abu me sauki fadi komata Nawa nakeso, yace biyu ne gasu can yanuna inda Hajiyar Baba gen Da Hajiyar Baba engr, dariya akasakeyi yayinda Daddy yakama kun'nan shi yace my Son iyayan Nawa zaka aura?.. yace ahhhh Daddy wasa nake sudin aitsofine kaga wanda nakeso can yanuna inda Humeeh take zaune aikam da sauri taboye fuskarta "abayan Sarah,</p><p><br /></p><p>Daddy yace Kai masha'allah "aikam ba'abar gurinba saida da "akasa ranan bukin Abdul-jabbar da Humeeh wata daya, sannan Mlm yarufe taro DA Addu'a</p><p>Washegari tunda safe jirgin su mlm yatashi zuwa Kaduna.</p><p><br /></p><p>💐💐💐</p><p>Bayan kwana biyu Mama tare agidan Daddy "aranan ne kuma Daddy yahada gagarumar walima na farin cikin baiyyanar Danshi, walimar kam manyamayan mutane sun halatta sosai "ankuma gama lafiya inda Abdul-jabbar yasamu kyau gudu ka sosai.</p><p><br /></p><p>Haka rayuwa yaitatafiya Abdul-jabbar da Mama basuda sauran matsala yanzu duk yasan gidajen yan'uwansa yana kuma cigaba da aikin sa, Soyayya kuma shida Humeeh sai abunda yai gaba, "akwana antashi bawuya "agurin Allah gashi yausauran sati daya bukinsu.</p><p><br /></p><p>Su Sarah "ankasa zaune "ankasa tsaye bukin nasu da kawa da yaya yaune suka fara event, zaune suke afalon gidan Baba gen kasan cewar nan za'a sa Amarya lalle Humeeh Sarah Esha Zarah da kuma, Haleeh da Hannah dayake duk sunzo saikuma sauran wasu yammata daga Cikin family din fira suke tayi irin na'amare.</p><p><br /></p><p>"A yaune dubun mutane suka shaida auren ABDUL-JABBAR AHMED ABDUL-JABBAR DA amaryarshi A'ISHA HUMAIRA MAHAMUD, masha'allah Allah yabada zaman Lafiya.</p><p><br /></p><p>"Anhada lafiyayyan dinner awani kayatacce gurin mesuna komesment dinar tahadu iyakar haduwa angoda Amarya sunyi kyau harsun gaji, abokan angodana Amarya ma sunyi kyau sosai kasan cewar sunyi ankonsu mai asalin kyau, haka nandai aka gama dinner lafiya.</p><p><br /></p><p>Zaune suke sai faman shakiyanci suke irin na kawayan "amarya saijin Sallama angon'nai sukaji "aikam sai sukayi shuru, Humeeh kam da sauri tarufe fukada mayafi Bayan sun shigo "angaisa akataba Dan barkwanci Sannan M B yayimusu nasiha Y Y k yai Addu'a Sannan sukayi masu Sallam</p><p><br /></p><p>"aikam da sauri Humeeh tarike Hannah da Haleeh sai tafara kuka wai karsu tafi suma kukan suke, Doctor S I g ne yakallesu yai dariya yace wato tarihi zaya maimaita kanshi kenan KO?.. kallon shi Haleeh tayi tareda turo baki Dalter boy yace a ah Barau sunyi kukan rabuwa kasa yanzu idan suka rabu kafin su gajuna sai andade..</p><p><br /></p><p>Abdul-jabbar yace' eh fa haka ne Nan dai Sukai talallashi su har sukayi shuru sannan sukayi masu Sallama suka tafi, suka bar Amarya da Ango don yace bazaya rakasu ba tunda suna dayawa, suma sukace "eh sunyafe yazauna yaci amarcisa.</p><p><br /></p><p>_*toh" ainima barin Amarya DA Ango zanyi suci amarcisu lafiya*_</p><p><br /></p><p>**********</p><p>"DA SANNU" rayuwa tacigabada tafiya Abdul-jabbar yagama kos dinshi Cikin sa'a kuma su kabar shi nan Yola din don haka Soyayyar su sukeyi shida Humeeh, yayida itama tacigaba dazuwa makaranta abunta.</p><p><br /></p><p>*********</p><p>*BAYAN WATA TARA*</p><p>Humeeh ce" nahango sanye da doguwar rigar shadda me ruwan toka, dinkin aikin wutane gaskiya shaddan yamata kyau sosai idanba kasanta ba toh" balallai bane kallo guda kagane ta, kasan cewar tayi kiba tabude saka makon Cikin da take dauke dashi.</p><p><br /></p><p> "ahankali take saukowa daga bene da koma "ace kyar Da kyar, kasan cewar cikin yashiga watan haihu steps biyu ta taka zata ta kana uku kenan, saiga Abdul-jabbar yashigo sanyeda uniform din SOJOJI,</p><p>da sauri najiyace tsaya daganan aikam cak tatsaya dasassarfa yahau benan yace bakijiko?..my Cool.</p><p><br /></p><p>Baki ta turo tareda cewa toh" nina ganijene yace' toh" basai kikiraniba?..tace toh" Sorry, daukanta yayi cak yasauke takasa tareda Doratasaman kushin yafara manmatsa mata kafafunta dasuka dan kunbura.</p><p><br /></p><p>Can saitaji matar yaya daure dakuma ba harda kunkuru da sauri tace Innalillahi, yace mene?.dai-dai lokacin da taji wani irin ciwo aikam tuni tasaki kuka tareda cewa wayyo Umma,Cikin tsoro yace me yafaru tace marata da sauri ya dauke ta sai mota "asibiti Cikin ikon Allah tahaifi tagwaye duk mata, kyakkyawai dasu masu kamada Babansu"</p><p><br /></p><p>Zokaga murna gurin Abdul-jabbar nanda nan yafarakiran mutane yanafada musu Cikin lokaci kankani akacika asibiti.</p><p><br /></p><p>***********</p><p>Rana yara sukaci sunan su" wato Hassana DA Hussaina, suna yakayatu mature kayatuwa mutanan ta sunzo Hannah da goyon danta, namiji Haleeh kuma da Cikin tana "aure wani laccara haka nan akaci suna akawatse taro lafiya alamar megego da yaranta toh" mu masaimuce ALLAH yaraya HASSANA DA HUSSAINA.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Masha'allah_</p><p><br /></p><p>Anan </p><p><br /></p><p>Nakawo karshen wannan littafi me suna DA SANNU.</p><p>kuskuren DA nayi ALLAH kayafe Mani.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>💐Lufhat ce💐</p><div><br /></div>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-71270233625274805672021-01-24T06:29:00.000-08:002021-01-24T06:29:11.316-08:00DAN HAKIN DA KA RAINA COMPLETE HAUSA NOVELS<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-GTUu9XSgoFE/YA2CwcYelNI/AAAAAAAAJgc/YLnuxWN562YDid051nqxbhsDLtdrrNnXwCLcBGAsYHQ/s2048/DAN-HAKIN-DA-KA-RAINA.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="DAN HAKIN DA KA RAINA COMPLETE HAUSA NOVELS" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-GTUu9XSgoFE/YA2CwcYelNI/AAAAAAAAJgc/YLnuxWN562YDid051nqxbhsDLtdrrNnXwCLcBGAsYHQ/w320-h248/DAN-HAKIN-DA-KA-RAINA.jpg" title="DAN HAKIN DA KA RAINA COMPLETE HAUSA NOVELS" width="320" /></a></div><br /> [12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...*<p></p><p><br /></p><p>_PURE MOMEN OF LIFE WRITER'S_</p><p><br /></p><p>_Story/written by_</p><p> 🌸 ~biebie dee~🌸</p><p><br /></p><p>_dedicated 2 amazing sister Afrah bhai_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN KAI_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 1-2_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>""""Banko k'ofar akayi batare DA sallama bah,a tsorace Afrah ta juyo Dan ta tsorata sosai, ajiye book din hannunta tayi gami DA kallan Farty, harara mai lafiya Farty tabata sanan tace" kije Mommy na k'ira" jawo k'ofar takumayi da k'arfin gske Afrah ta bita da ido,</p><p> Azuciyarta tana addu'ar Allah yashiryar da sister'n Nata.<span></span></p><a name='more'></a><p></p><p> Hula ta asanya akanta sanan tatafi k'iran mommy'n</p><p> Kitchen tanufa direct Dan tasan mommyn tana Chan,tashiga DA sallama batagama kaiwa bah mommy" tace yauwa so nake Ki haddamin abinci mai lafiya coz yanzo Daddy'n Ku yayi waya yana hanya da Baki"smiling Afrah tayi sanan tace oky mar" shafa kanta mommy tayi Dan mummy irin matananne masu son a daukakasu anuna sunfi kowa a waje.</p><p> Babu bata lokaci tafara aikinta cikin nutsuwa bawani abu Mai wahala takeyi bah jelof rice ne da salad sai Pepe soup na kaza, batafi 2hrs ba tagama komai kamshi sai tashi yakeyi</p><p><br /></p><p> duk tajeresu a food flask masu kyaun gske, tana k'ara kintsa kitchen dinne Farty tashigo smiling tama Afrah ta jawo plate nan tashiga zuba abincin Afrace tayi magana tace"Daddy ney fa zaixo da ba'ki" tabe baki Farty tayi sanan tace toh sukadai zasuci duk kayanan"bata gama rufe ba'ki bah mommy tashigo kallan Farty tayi sanan tace"wanan wani sabon iskancinne?, nasa ayi abinci keba da aiki bah ke da farkon D'ibah" turo baki Farty tayi Sannan tace" Kai gidan nan dabun fada DA bana fa'da ba, fa'da" fuuuu tabar kitchen din.</p><p> Fita Afran tayi itama Dan anfara k'iran sallan magrab.</p><p> Tana idar da sallah note book dinta na economics ta dauko kasancewar sunada test gobe karatu taitayi har akayi k'iran sallan Isha, ajiye book din tayi ta tada sallah, bayan ta idar da sallah kitchen tanufa d'an tasa wani Abu a cikinta.</p><p> A palo duk ta gansu Daddy, Mommy, Sulaiman,Farty sai Afifah daketa buga game cikin tap dinta, k'arasawa cikin palo'n tayi sai da ta zauna sanan tafara gaida Daddy" ina yini Daddy</p><p>Ya hanya"?</p><p> Smiling Daddy yayi sanan ya amsa da" lafyalau,Alhmdulillah,ya sch? Kina dai karatu ko"?</p><p>Smiling Afrah tayi sanan tace inayi sosai"</p><p> Daddy yace"good"</p><p>Nan tajuwo tace Yaa Sulaiman ina wuni"</p><p>Hararan tayi kadan sanan yace" bani amsawa sai yanzo kika ganni"? Sorry Afra tace" Sulaiman yayi murmushi yace yawuce" phone din Daddy ne yafara ringing tashi yayi yafifa side dinshi, Afra na k'okarin tashi ne Mommy ta tsaida ita da cewa"sai dai kidafa indomie Dan Abincin kaf ya k'are, kuma food flask dinan da kikasa abinci dazo please ki wankesu dan kisan halin su salamatu basu aiki DA natsuwa"(Mai akinta kenan) Afrah ta amsa da toh tayi hanyan kitchen</p><p> Hafiz ne yashigo d'akin bako sallama Sulaiman ne yalalleshi yaja tsaki sanan yace"Kai kuma meye haka kashigo waje babu KO sallama" </p><p>Bai ko lalle yayan nashi bah yace mommy abinci please" Farty ce tayi magana Hafiz Ina promise dina"? Yace kibari mana" shuru Farty tayi taci gaba ta tapping phone dinta.</p><p> Mikamashi wani d'an food flack Mommy tayi Amsa kawai yayi gami da mikewa yayi waje.</p><p> Kallan Mommy Sulaiman yayi yace" meye haka mommy? Kin hana wanda tayi abincin taci Amma Hafiz da baisan anyi abincin ba shi kin ajemai,wanan halin baiyi bah sam kuma bai kamata ba"</p><p>Harara tabashi sanan tace" toh sannu masani wanda yasan yakamata, naga Alaman yanda kakesan Abdulrahm da Afrah a gidan ko k'ananka na jini baka so,toh wlhy kakiyayeni kashiga hankalinka" katse mummy yayi dacewa" ni kowa inaso a gidan duk d'aya na daukeso" Mommy cikin fa'da tace" toh ni bandauka d'ayan bah, saikayi abinda zakayi" mtssw taka tsaki tabar palon.</p><p> Tabe baki Farty tayi sanan itama tabi bayan Mommy tsaki Sulaiman yayi sanan yace da Afifah taje ta kwanta" kallenshi tayi sanan tace" am not sleepy" hannu ya d'aga kaman zai daketa nan tatashi a guje tayi d'akin Mommy...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>~biebie Dee cee~</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAINA...*</p><p><br /></p><p>_PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S_</p><p> </p><p>_we don't just_ _entertain and_ _educate, we also_</p><p>_touch heart of the_ _readers_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_story/written by_</p><p>~Biebie dee~🌸</p><p><br /></p><p>_Ina mai ba duk wani makaracin littafinan hakuri da jina shuru dakukayi,hakan yafaru ne sanadiyan dauke mun phone da akayi amma yanxo komai ya daidaita zakurika jina akai akai da yaddan Allah_</p><p> *wanan page din sadaukarwa ne da duk wani masoyin bie-bie dee nagode sosai da kaunarku agare ni,ina maku fatan Alkhari a duk inda kuke*</p><p><br /></p><p>_page5-6_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>""""Wunin wanan ranar Farty da mommy basu ko kalle Afrah ba,itama batabi ta kansu bah aikin gabanta kawai takeyi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mommy ce zaune a palo tana kallan wani series film sai Afifah a gefenta tana home work, Fartyce ta shigo palo'n bako sallama gaban mommy ta tsaya kallanta mommy tayi gami dacewa "lfiya? Kin tsayamin a gaba" baki Farty ta turo gaba sanan tace "kud'in mana mommy su Zee nikadai suke jira" jeki dauka mana a bedroom dina" cewar mommy Farty tace" pls ki karamin mommy wlhy 7k baxai isa bah, dan ko Zee 12k tace xatafitoh dashi yau hafsah 10k sai ni 7k haba mana" kallanta mommy tayi tace "je ki dauka 5k cikin handbag dina danaje gidan anty maijidda dashi jiya kuma wlhy in daddy'n ku yadawo ki ansamin ku'dina nafada maki" da sauri farty takoma bedroom ta dauki kud'in tafitoh tana waya hannu ta d'agama mommy tayi gaba(yaran manya..lol)</p><p><br /></p><p>Tanafita takira Zee </p><p>"Baby tafito fa yanxo gidansu hafcy zan k'arasa" Zee tace " oky bea ganin soon"</p><p> Takai babu dadewa sai ga Zee ta iso nan suka dau motan gidan su Hafsah sukai gaba </p><p> Yawo dai a wanan ranan sun shata haka ciyeciye ma akarshe dai syd resort suka je nan dai suka zauna sukai ta hira.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> A gida kuwa bayan Afrah ta gama aiyukanta tsaf, shiryawa tayi cikin riga da skirt na atanpa da red a jiki d'inkin sunyi mata kyau sosai sai dan simple makeup da tayi a face dinta sai tayi kyau sosai,mayafita ta dauko sleek veil red colour sai black side bag da black flat shoe ta sanya tayi kyau sosai😘 side din mommy ta nufa bata ganta ba, a babban palo ta hangota tana kallo, k'arasawa tayi da sallama kallanta mommy tayi gami da "cewa sai kuma ina da wanan yamman"</p><p>Smilling Afrah tayi tace"mommy 4 nefa yanzo, kinmanta yaune waliman sister'n Aysha da nafada maki tin lastweek" baki mommy ta tabe tace"ohh haka faa, kin hadamin salad din dai ko?" aa Afrah tace" aiko sai ki koma ki hada dan zanyi anfani da shi ne" hakan Afrah ta cire mayafinta ta aje jakanta tashiga kitchn ta hada salad dinan </p><p> Mommy ko sai fad'a takeyi sai kace wani babban laifi Afran tayi cewa take" magana karinka nanatawa kenan ni kam gaskiya na gaji haba"</p><p> Bata dade sosai ba ta gaba (kundai san Afrah wajen harkan abinci) palo ta dawo ta dauki mayafinta da jakarta tama mommy sallama tohh kawai mommy tace batare da tabata ko 200 bah(kai mommy😡 )</p><p> </p><p>Tafitoh palo kenan yaa Sulaiman na shigo da mota gidan, fitowa yayi yace"sis sai ina wanan kwalliya dariya Afrah tayi tace" kinkinau gidansu Aysha sis d'inta ke walima"bari nashiga wajen mommy na fitoh na sai na kaiki ko?" dariya Afrah tayi gami dacewa nakogode yayana" wajen da ya aje motan ta tsaya shikuma ya shiga palo,banza da shi mommy tayi har yagama fadamata sakon ya juya zai bar palon ne tace" sai ina?"</p><p>" Afrah zan sauke gidan k'awar ta"</p><p>Dogon tsaki tajaa dan ita abinda ta tsana taga mutanan kirki na kula Afra Amma abin haushi harda d'anta ke kulata, tsaki takuma jaa tace mune dai, a haka dai murmushi tayi ganin duk cikin family mijinta babu wanda ya kaisu ku'di da haduwa kowa ganin girmansu yakeyi shiyasa mommy keganin babu wanda zai kamosu har abada dan bama a haifi wanda zai fisu da ita da yaranta haka dai mommy taita zancen zuci har wajen 5 wata zuciyar ne tace daita why not kije gidan hajiya Aina'u yanzo(Ummu_abdulnaseer) zubur ta tashi tayi bedrood,shiyawa tayi cikin lace dan ubansu mayafi,jaka, takalmi duk masu tsada ne kuna ganinta kunga matar manya turaruka tafesa iri iri sanan ta dau car key, sai da ta kulle bedroom dinta sanan ta fitoh babban palo salamatu ta kira" ni zan fita, a daura tuwon shinkafa Afrah ta dawo zatayi miyya" Salamatu ta amsa da toh adawo lfya nan mommy ta tasa Afifah gaba suka fita sai malali</p><p><br /></p><p> Hajiya Aina konace Ummu-abdulnaser k'awar mommyce a aikin hajji suka hadu shekara 2 dasuka wuce, tinda mommy taga Ummu masu kudine shikenan amintan k'arfi da yaji ya kullu da yake Ummu akwai sanan darajan d'an adam(rufaida omar)shiyasa suka saba sosai</p><p> Yaran UmmuAbdulnaser duk maza ne Abdul_naserr ne babba sai mubarak,muhammad </p><p> Mommy Mubarak da muhammad kawai tasani batasan nasir ba coz yana schooling a turky.</p><p> Tashiga da sallama y'an aikinta tagani"hajiya ko nanan?"</p><p>"Ehh tanan"inji nafee kai tsaye tasa kai side hajiyan Afifa nabiye da ita</p><p>"Muryan wanakeji kaman hajiya Bilki inji Ummu murmushi kawai mommy keyi nan Ummu ta amsa handbag din hannun mommy sukai ciki,</p><p>Bayan sunzauna ne Afifah tace"ina wuni Aunty"</p><p>"Lafiyalau babyna zonan" nan Ummu tashiga tanbayanta sch Afifah tace fine"</p><p> Babu bata lokaci aka cika gaban mommy da kayan mutsa baki nandai sukaita hira saida mommy tayi sallan nagrib suka dawo gida Ummu-Abdunasir tahadama Afifah kayan zaki sai murna takeyi.</p><p> Bayan Mommy ta chanza kaya zuwa marasa nauyi d'akunsu Farty tashiga, bata ganta ba sai jakan Afrah da mayafinta kan bed tsaki tayi tanufa kitchen nan taga Afran na k'olarin daura biyan oyun nan Mommy tashiga masifa"haba tintini bakiga daman daura miyan ba sai yanzo, kwana biyunan naga kina fitoh da sabin iskanci ne nikam wlhy ba zan iya ba, daka zuwa walima kiyi dare kuma kinsan zakiyi miya ai na k'iraki" hakuri kawai Afrah ke bata dan ita mommy mamaki take bata yaranta zasuyi laifi bata ganin laifinsu amma ita Abu k'adan sai mommy ta hau fad'a, </p><p> Babban palo mommy takoma phone dinta ta d'auka tashiga kiran layin Farty ringing 2 ta dauka</p><p>"Hello mommy ganin pls" bata tsaya jiran abinda mommy'n zatace bah ta kashe wayan tsaki mommy tayi gami da "cewa zakidswo ai"</p><p> Babu dadewa sai ga Farty ta shigo, kujeran da mommy take Farty ta zauna gami da cewa" kai mommy nagaji wlhy"</p><p> hararanta mommy tayi sai yanzo kikaga daman dawowa dan kinga daddy'n ku bayanan ko, wlhy ki shiga hankalinki banasan shashanci" </p><p>"Sorry toh mommy bazan k'ara bah" cewar Farty</p><p>" dalla rufamin baki kinfita tin 3 sai yanzo akeganin ki"</p><p>Baki Farty ta turo tace" ni matsalana da ke kenan naci mommy wlh, ance sorry sai yii kikeyi haba" barin palon tayi fuuuu.</p><p><br /></p><p>_toh readers ya zata kasance kenan su din ne koko ba su bane??_</p><p><br /></p><p><br /></p><p> ~BIEBIE DEE~</p><p><br /></p><p>.</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAINA...*</p><p> </p><p><br /></p><p>_PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S_</p><p><br /></p><p> _Story/Written by_</p><p> ~Biebie dee~🌸</p><p><br /></p><p>_Dedicated 2 amazing sister Afrah bhai_</p><p><br /></p><p>_page 3-4_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>""""Afifah ce ta fad'a jikin Farty,tureta tayi"dallah malama ke dawa"?</p><p> Murgud'a baki tayi sanan tace" ba Yaa Sulaiman bane wai naje nayi bacci"</p><p> Kallan Mommy Farty tayi gami da cewa" ai nasani,mutum sai shegen iyayi wai shi masanin adalci"mtws taja tsaki</p><p>Mommy tace" har banaso na ganshi a gida komai kayi baka iya bah ne, barin ma akace Abu akan way'anan yaran ne yarinka zak'ewa kenan" </p><p> Afifah ce ta kalle mommy gami dace wa" wasu yara wai"?</p><p> Hararan ta Farty tayi dallah malama kiyi bacci"</p><p> "Bazanyi bah" inji Afifah</p><p> Anshe tap din hannun ta Farty tayi " in kika sake magana sai na mareki, yariya sai shegen gulma"</p><p> Hararan ta Afifah tayi gami dacewa" kema ai y'ar gulman ce" mommy wlhy kiyima yariyar ki magana, ni sai naci k'aniyan ta" tashi mommy tayi zatashi ga toilet ai sai kutayi" tsaki Farty tayi ta dauki phone dinta tabar bedroom din.</p><p> Bayan fitarta kwanciya Afifah ta gyara da kulle eyes Dinta sai bacci.</p><p> </p><p><br /></p><p>Afrah nak'okarin barin kitchen d'inne Farty ta shigo, "please in indomie d'inan yarage kibani inajin yunwa"</p><p> "D'aya kawai nadafa bansan zakici ba ai" tsaki Farty tayi tabar kitchen din, bedroom din mommy takoma kallanta Mommy tayi sanan tace" d'auki Afifah kikaita d'akinku"</p><p> B'ata fuska tayi gami dace wa gaskiya ni mommy nagaji,ba daman kinga mutum kedai sai kinsa shi aiki" </p><p>"Wai badake nake magana bane"?</p><p> "Bari dai na Kira Afrah ta d'auketa dann ni na d'auki yariyanan ai sai nayi ciwan kirji" Mommy batace komai ba har Farty ta fita ta dawo.</p><p>Chan sai ga Afrah tashigo da Sallama ko amsawa basuyi ba mommy tace" tin d'azu na aiko kizo ki dauketa sai yanzu kikaga daman zuwa ko? kin kyauta"</p><p>"yi hakuri mommy wlhy Ina toilet ne Afrah tace"</p><p>"Okay,d'auketa kutafi sai da safe" </p><p>Afrah tace toh, Allah bamu Alkhari"</p><p> Nan mommy tayi ma Farty sai da safe tayi side d'in Daddy "okay" kawai Farty tace </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Wayanta tashiga yi sai after 1 tagama tea ta ha'da tasha sanan ta kwanta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asuban fari Afrah ta tashi, bayan ta idar da Sallah sai da tad'an yi karatun Qur'ani sanan sukai wanka ita da Afifah, bedroom d'insu ta fara ygrawa tsaf, sanan tayo hanyan kitchen Arish tafere Dan Afifah tace dashi zata sch" </p><p> Nan da nan ta gama kafin 6:20 tagama arish da source dinta da tafasa egg aciki, tahada ma Afifah lunch box d'inta Sauran tajuyeshi a d'an wani wermr, ruwan tea ta d'aura yana tafasa ta hada masu tea ita da Affifah sauran ruwa ta juye a flacks, suna gamawa tashirya cikn uniform dinta long slip riga da flirting skirt sai hula Afifah kam gown ne Nata sunyi kyau cikin uniform d'in.</p><p> K'arfe 6:47 Mommy tafitoh daka side Daddy tana Shiga bedroom dinta Farty tagani a kwance sai shan baccin ta takeyi blanket din ta yaye gami da cewa"tashi joo time yatafi kinan ko wanka maybe ma bakiyi sallah ba"</p><p> Mik'a Farty tayi gami da murje idunta agogo ta kalla taga 6:50 toilet tayi da sauri mommy taja tsaki tabar d'akin kitchen tayi bu'de bu'de tarinka yi har taga ragowar arish d'inda Afrah tayi tsaki taja gami da cewa" wanan yaushe zai wani isa?, dan iskanci anyi Abu kad'an sai kace babu, bari naje naga Afrah'n" </p><p> Tashigo d'akin Afrah na sakama Afifah sucks </p><p>"Ina kwana mommy" Afrah tace</p><p> </p><p>"Lafiya, naga kinyi abinci k'adan ne"</p><p><br /></p><p>"Naga Daddy yananan ne, nasha sai anjima zakuyi"</p><p><br /></p><p>"Yanzo mai kikeso Fartyma taci, kinsan dai wannan ba isan ta zaiyi ba"</p><p><br /></p><p>Afifah tace" toh mommy ta ha'da da tea mana, ko kuma itama tayi Nata da kanta" wayasa bakinki? mommy tace" ba kowa" Afifah tace tana daria juyawa mommy tayi tako ma kitchen inda ta tadda Farty ta sa kulan d'ankalin ta gaba sai ci takeyi tana korawa da tea ga phone a hannunta </p><p> Kallanta Farty tayi sanan tace" kai gskiya mommy Afrah ta iya girki" harara mommy ta watsa mata tabar kitchen din d'an in akwai abinda ta tsana baiwuce a yabi wasu 'yayan da ba Nata bah</p><p>Duk da tasan gskiya Farty ta fa'da</p><p><br /></p><p> K'arfi 7:30 duk suka fitoh already Aminu direba yazo nan duk sukayi ma mommy sallama sukayi sch.</p><p> Sai da akafara sauke Afifah anasu sch din *future leaders* sanan aka ajiye Farty a nata sch d'in *JAMAL SCH*</p><p> AFRAH ce karshen saukewa d'an ita *Standerd foundation*take zuwa da ke cikin gari. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dukkansu ss3 suke bambacin sch ne kawai DA class kuma 3moths ne kawai Farty tabama Afrah.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> babu wanda bai san Farty bah a sch d'insu saboda ita akwai biye ma friends, friends gare ta hadda na tsiya ga shegen iyayi da nuna fa akwai.</p><p> </p><p> Afrah kam babu ruwanta abinda ya kaita Kawai takeyi indai wajen karatu ne sune a gaba ita da k'awarta Aysha shiyasa akeji da su a sch d'in nasu daka principal har teaches. </p><p> </p><p> K'arfe 3:30 aka tashi su Afrah, school d'in su Farty sukazo dan yau ba'a bata na napep bah mommy tace su dawo tare da Farty yau.</p><p> d'an tsaki tayi k'adan gami da kallan agogon hannun ta 4:12 tagani gashi tana so taje hadda Amma ba Farty babu kuma alamarta ga dai Students nata fito wa amma banda Farty, cikin sch din Affah tashiga har class d'in su Farty'n amma bata ganta ba dole tafito ga time sai tafiya yakeyi Already Afifah na gida d'an ita 2:30 take tashi haka sukai tajiran Farty har 4:30 babu alamanta ganin haka ne Aminu yace" tinda ke zaki hadda bari na ajeki sai nadawo na dauketa, kan lokacin kila ta fitoh"</p><p> Afrah ta amsa da "toh"</p><p> nan suka kama hanya suna isa gida Afrah ta fitoh, mommy da ke palo zaune a 3siter tin shigowar mota take lekansu ta window fitowan Afrah kawai tagani bataga Fartyma ba, sai kuma taga yana ko'karin fita babu shiri ta fito da k'arfi ta k'ira Aminu Afrah na ko'karin shiga d'aki mommy tace " tsaya"</p><p><br /></p><p> Bayan Aminu yazo nan mommy ke tanbayansa Fartyma bayani yamata yanda zata gane Ai bai gama k'arasawa ba tafara masifa ta inda take shiga ba tanan take fita ba shi dai Aminu sai bata hakuri yakeyi sanan ya koma d'an dauko Faryma'n.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> nan Afrah ma tafara bata hakuri ita ma hararan ta mommy tayi gami da cewa ita" bata san mutin mai san kai da wasu maganganu wanda ita Afrah'an bata gane ba jin mommy Nata fad'a ne yasa Sulaiman futowa ko da yafito masifan dai taketayi ta bai tsaya neman sanin dalili ba d'an yasan halin mommy hakuri ya shiga bata Kawai takoma ciki.</p><p><br /></p><p> Afrah na shiga d'aki wasu hawaye ya zubo mata nan da nan tashare su da ta tuna da nasihar ummin ta smiling tayi nan tacire uniform sanan ta dauro Alwala dan gabatar da sallan la'asar ko da ta idar da sallh phone d'inta ta dauka ta kira yayanta Abdulrahm.</p><p><br /></p><p> Ko da Aminu direba yadawo da Farty Mommy sai habaici takeyi, Afrah tayi kaman bata san metakeyi Ba,aikin gabanta kawai takeyi...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*muje zuwa dai*🚶♀🚶♀🚶♀</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAINA...*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S (We don't just entertain and educate,we also touch heart of the readers_)</p><p><br /></p><p>*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p>*#IG PML WRITERS*</p><p>*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p>*#http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Story/written by_</p><p>~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p>_Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p>_page 9-10_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Bansan Mai zance bah wlh,kuyi hakuri da jina shuru dakukayi, Insha Allah zakuriqa jina akai2 da yadda Allah, nagode sosai*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ASALIN LABARIN*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"""""Malam Abubakar da matarsa Hadiza, y'an Asalin Katsina ne.</p><p> iyaye ne ga Alhaji Shu'ibu watau mahaifin su Sulaiman,su biyu ne Kawai wajen iyayen nasu shiyasa sukasamu kula sosai wajen iyayen Nasu,d'an Malam Abubakar yana matuk'ar k'okari a gidan shi, d'an yanada rufin asiri</p><p> Shu'ibu ne Babba sanan k'aninshi Salis( maihifinsu Afrah) </p><p>sai dai yanada wani Hali Wanda matarsa ta tsana watau bambaci,dan cikin yaran nashi yafisan Salis,</p><p>Hadiza batajin d'adin halin mijin Nata Sam ko Dan shi Salis din yafi maida hankali kan karatu ne oho. </p><p><br /></p><p> Haka dai rayuwa tai ta tafiya har shu'ibu ya kammala secondary school d'insa a lokacin Salis yana ss1, babu yanda Malam Abubakar baiyi da shu'ibu ya ci gaba da karatu bah amma firr ya k'i sai kawai yasamai ido. </p><p> Shiko shu'ibu dama tin kafin yagama school yana d'an bugabubuganshi d'an haka koda yayi WAEC sai yadage sosai da zuwa kasuwa,cikin ikon Allah kuma yasamu ci gaba sosai ganin haka ne yasa Malam Abubakar ya k'aramai jali iya k'arfishi,shu'ibu yayi murna sosai </p><p> Himma ya k'ara d'an yana matukar san kula da iyayen nasu.</p><p> Lokacin da Salis ya gama nashi secondary ba b'ata lokaci yacigaba,yafara poly inda yake karanta accounting a wanan lokacin shu'ibu yak'ara samun cigaba sosai d'an shiyake kula da gidansu da k'aninshi iyayenshi najin d'adi sosai.</p><p> Haka rayuwa yaita tafiya har shu'ibu yafara zuwa gari gari cigaba da bud'i kuwa Allah yabashi kayan abinci sosai suke kaiwa garigari,har yakai bayayin sati a garin katsina ganin haka yasa malam Abubakar yamai maganan aure a wanan lokacin shu'ibu "yace a Dan bash lokaci"babu d'adewa yafidda Mata Bilkisu a Zaria take da iyayenta ba dadewa akayi biki kasancewar da ku'di a k'asa, a kaduna ya Ajeta d'an Bilki firr tace"bazatai zaman Katsina bah,</p><p> Yayi aure da watanni yagama gininshi d'an haka sukatare sabon gida Bilki sai hura hanci takeyi d'an akwai isgili Dan ita batasa talakawa Sam da y'an kauye kuma kalan datakema dagin mijin nata kenan bataso ko k'adan a rabesu amma bayanda ta iya d'an mijin nata mai sanyin Alheri ne.</p><p> Koda Salis yadawa gidan da zama ba haka taso bah amma bayanda ta iya tasamai ido.</p><p> Salis yadawo kaduna babu dadewa yasamu aiki da sky bank yayanshi yasu yayi aiki tare dashi amma shi Salis din yanuna yanasan aikin banki bayanda shu'ibu zaiyi yabarshi but still yana temaka ma yayanashi da wasu aiyika sosai. </p><p> Ganin haka yasa Bilki(mommy) d'anko k'anuwarta Azeezah daka Zaria ko Allah zaisa Salis yace yanasanta,amma shi tinda Azeezan tazo ma gaisawa kawai sukeyi d'anshi yanada Wanda yakeso </p><p> Ana haka Bilki ta haihu D'a namiji watou Sulaiman malam Abubakar ne ya zabar ma yaro suna Bilki ba sunan taso ba amma ba yadda ta iya, y'an katsina sunzo sosai dan duk k'anan Inna Hadizaa sunzo haka wasu daka cikin dagin Malam ma,anyi suna da kwana 2 duk y'an katsina suka koma yarage ina Rakiya kawai,da wata k'annuwar maman Bilkin,</p><p>shu'ibu yah'ada masu shatara na arziki sai samai Albarka suke.</p><p> Haka zaman Salis yakasance gidan komai yakeyi Bilki da kanuwarta suna samai ido har yakai inna Rakiya tafahimta amma tasa masu ido.</p><p> Saidai Bilki tayi arba'in Sanan suka shiga katsina siyaya sosai duk yaran sukama iyayensu ido kawai Bilki tasa takuma sa a ranta insunje katsinan Zaata fadama inna cewar Azeezah nasan Salis tinda talura surukan Nata masu saukin kai ne su.</p><p> Sun isa lfya sunkuma samu tarba Mai kyau amma duk da haka Bilki sai yamotsa fuska takeyi d'an ita aganinta duk dan anga mijinta nadashi ne yasa sukemasu haka.</p><p> Ana saura kwana d'aya Subar katsina tasamu inna da zanchen Salis da Azeezah Daria Inna tayi sanan tace"toh ai shi Salis d'in yakusa aure,y'ar gidan aminin malam zai Aura Rabi'atu" murmushi Bilki ta k'akalo amma dai na ciki na ciki k'ar dai wanan yaron bai fada maki ba" ina tace </p><p>"aikuwa dai bamuyi maganan bah" cewar Bilki cigaba da cewa tayi da Allah sanya Alheri yasa kuma ayi da mu"inna ta amsa da ameen..</p><p> Tindaka wanna lokacin Bilki ta k'ara tsanar duk dagin mijinta ta r'ikesu a rai. </p><p> Koda da bikin Salis din yazo bani abun arziki ta tsinana bah kasancewanta mai rowa ce ita,haka dai ayi biki lfya aka kawo amarya Rabi'atu gidanta side din da Salis d'in yake aka k'ara gyrawa sanan akasa kayan Amarya.</p><p> Haka rayuwa tai ta tafiya dai zaman gidan dai gashinan ne Dan Bilki ta k'aro wulacanci.</p><p> Rabiatu nada wata 6 Bilki ta k'ara haihuwar da namiji watau Hafiz nan fa kanta yak'ara girma wai ita maman maza d'anginta na k'ara zugata.</p><p> Tahaihu da wata 8 itama Rabiatu ta haifo d'anta d'a namiji watou Abdulrahman ita katsina tako MA saida tayi wata2 chuff tadawo kaduna.</p><p> Yara dai sunyi wayo sosai Masha Allah,Sulaiman nasan anty Rabi haka itama,Bilki ko batasan wanan Abu da Suleiman keyi Sam </p><p> Ana haka Malam Abubakar yafara rashin lfya yaran nashi duk hankalinsu yatashi masu kaduna basu Katsina,asibiti Mai kyau aka kaishi,amma ciwan na Malam sai addu'a kwananshi 12 a hospital ya rasu Inalillahiwa'ina'ilaihirajiun duk sunji rasuwa mahaifin nasu sosai amma bayanda suka iya Wanda yafisu sanshi yadaukeshi sai muce Allah jikansa ameen . </p><p> Bayan rasuwan Malam yaran sunso inna tadawo kaduna amma tace a'a sam d'an haka suka barta saidai suna kula sosai da ita kuma suna zuwa a kai akai.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Haka rayuwa yaita tafiya shu'ibu nata k'ara samun bud'i haka Salis ma.</p><p> Saida Hafiz yayi shakara 3 sanan Bilki ta sake haiwuwa, wanan karan Mace tasamu watau Farty, watanni tsakani Rabi'atu ma tasake haiwuwa sunan inna Hadiza taci suke k'iranta da Afrah.</p><p> School d'aya duk suke zuwa yaran Suleiman, Hafiz, sai Abdulrahm iyayan na k'okari sosai a kansu sai dai wani lokacin Bilki na b'atawa d'an ita bata d'auka yara d'aya ba bata had'a yaranta da kowa ba.</p><p> Su Afrah Nada shekara 4 Daddy yashirya masu birthday na gani kuma na fad'a sosai ya kashe kud'i a Birthday'n haka a kaci aka sha akasha pictures y'an Uwa da abokan arziki sanan akatashi.</p><p> Afrah nada shekara 6 Daddysu ya rasu wayyo yaran sunsha kuka haka inna ma shu'ibu ko ba'acewa komai d'an sai dayayi kwanciyan asibiti na kwanaki, hakadai sukayi hakuri sukabi marigayin da addua d'an shine mafita </p><p> Rabiatu nagama takabanta takoma Katina d'an Daddy yace babu inda yara zasu abarsu a hannunshi haka inna taita samai albarka. </p><p> Mafarinda kik'on su Afrah yakoma hannun Mommy Kenan.</p><p> Daddy yanzo bayazama abubuwa sunmai yawa Dan ta hannushi duk wani shikafa dake shigowa kaduna a hanshi yake </p><p>sanan Bilkin bata barshi haka ba D'an haka Abubuwa dayawa sukafara chanzawa sai addua kawai</p><p><br /></p><p> Shu'ibu yarage zuwa Katsina sosai Inna na magana zaice abubuwa sunyi yawa Addu'a kawai takemai kaman yanda tasaba.</p><p> Abubuwa dayawa sunfaru ciki hadda tafiyan Suleiman school Dubai Bilki kuwa bako wace mace take bi ba d'an acewarta ita matar manyace.</p><p> Batasa Zata sake haihuwa ba babu shiri sai ga Afifah tazo🤣 akwai tazara sosai tsakaninta da Farty </p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*BACK TO STORY*</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAINA...*</p><p> </p><p> _PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S_</p><p>( _we don't just entertain and educate, we also touch heart of the readers_)</p><p><br /></p><p>_story/written by_</p><p>~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p>_dedicated 2 amazing sister Afrah bhai_</p><p>_I also dedicated dis page 2 all members of biebie dee novels group,thanks for d love n support,MUCH LOVE_❤❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 7-8_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>""""Farty na shiga d'aki kayan hannunta ta zube a kan bed ta shiga toilet, wanka tayi gami da alwala rigan tasa mara nauyi sanan ta tada sallah, bata bar kan sallayan bah sai datayi har isha,babban palo ta fito direct nan taga mommy da Hafiz suna hira, Xamatayi kusa da mommy k'adan sanan tace" mommy wai me aka dafa yau ne?"</p><p>" kee dallah tuwo ne" Hafiz yace Farty tace" Salamatu tayi ko Afrah?" Mommy tace Afrah ce" tashi Farty tayi tabi hanyan kicin, Mommy ta bita da harara</p><p> </p><p>Ta zubu tuwan kusa da Hafiz ta zauna tana danna waya,ajiye plate din tayi ta matso kusa da Hafiz shima phone yake dannawa" Hafiz plz kalla wanan guy din, kasanshi?"</p><p>ansan phone din yayi yana k'ara kallan pic din gyrawa yayi yace" kee ina kika san Ahmad Muhammad Yakasai?"</p><p>Smiling tayi sanan tace" wlhy a instagram muka hadu,jiyama munhadu a syd resort naga kai kasan mutane shine nakeson san sanin suna da ku'di ne sosai ko yaa d'an ni banasan wahala" kee yi shuru pls kinsan kud'in family din Yakasai kuwa wlhy bakida hankali" duk wanan maganganun da sukeyi Mommy na jinsu batace komai bah sai ma gyra kwanciya datayi.</p><p> Plate din tuwan Farty ta jawo tacigaba da cewa" Hafiz plx da gske kakeyi? Toh wlhy ina san shi yau d'akin Afrah ma zan kwana dan nabata labari tasan ni babban yarinyace ba k'arama ba wlh"dariya taitayi tanacin tuwanta tashi Hafiz yayi yana tsaki</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kusa da Mommy tadawo tana nuna mata pics din Ahmad Muhammad Yakasai murmushi Mommy tayi gami da cewa"Allah mana zabin Alkhari Farty tace" Amiin dai Mommy,dan Allah Mommy ya zakiyi da biki na ne? Mommy tace" ai dubai zamuwuce da ni da kee da anty Maijiddah ki zaba irin kayan da kikeso da kanki" nan Farty tafara rawa voice din Afifa sukaji tana cewa"Mommy toh anty Afrah ma za kikaita dubai d'in?"</p><p>Farty ta anshe dacewa" Dallah kimana shuru, manya na magana kina sa banzan bakin ki wajen" hararan ta Afifa tayi gami da murguda mata baki tace"gidaki d'in banxa da hufi bazan taba zuwa ba" mtwss taja tsaki, da ido Farty ta bita chan tace wlhy Mommy sai kinfara gayama yarinyanki gskiya d'an inaga haryanxo batasan ni bace asalin yayarta,jifa cewa takeyi bazatazo gidana ba kenan fa gidan Afrah zata zanga irin banzan miji da Afrah zata aura inan ai" tabe baki Mommy tayi sanan tace" bana tunan tanada saurayi ma wanan, in batasamu bah ai sai Daddy'n ku ya bincika mata a cikin dangin nasu" dariya Farty tayi sanan tace wayaga ba cigaba, ta taso a k'asa mu zakuma tak'are a k'asanmu" wani dariyan takuma bushewa dashi, Mommy zatayi magana kenan Ya Sulaiman ya shigo ashe tinda Farty tafara magana yana jinta shigowa cikin palon ne baiyi ba </p><p> K'arasowa cikin palo'n yayi,harara ya zabgama Fartyn sanan ya kale Mommy gami da cewa"wlhy Mommy kirika ma yariyanan fad'a,batada hali sam wlhy" Mommy ba tace komai bah sai ma tashi datayi tabar palon, mik'ewa itama Farty tayi zatabar palon "tsaya kee" Yaa Sulaiman yace, tsayawa tayi gami da turo baki gaba " kee haka'acemaki kud' in zakiyi kokuwa ancemaki mai kud'in zaki aurah?"da kike wani maganganun banzanki a wajen?"</p><p>Baki ta turo gaba "toh toh ni Yaa Sulaiman ba magana na keyi ba ai ba da kowa nakeyi bah" na lura da duk y'an gidanan sun raina Afrah da Abdul a gidan,ku ganinku bazasu zama komai ba ko? Tin da iyayansu basu zamaba komai bah ko? Toh ba abin mamaki bane su temakemu wata rana wlh, babu wanda yasan gobe sai Allah" Allah yakiyaye ya karemu da ganin wanan b'akin ranan" Farty tace tana murguda baki </p><p> Hannu ya kai zai duketa tayi d'akin Mommy a guje, binta d'akin shima yayi </p><p> "Keekuma lafyanki kinfadomin d'aki bako sallama?"Mommy tace </p><p> " wlhy Ya Sulaiman ne zai dukeni" </p><p> "Akan wani dalili"Mommy ta tanbaya</p><p> Farty bata kai da magana ba Sulaiman ya shigo d'akin gami da cewa" wlhy Mommy kirika fad'adama yarinyan nan gaskiya, batasan life bah sam wlh"</p><p>Kallanshi Mommy tayi a kaikaice tace metayi kuma sarkin anyi laifi?"</p><p>"Abubuwanan da takema Afrah a gidan mana gaba d'aya ta raina ta *D'an hakkin da ka raina*dai shi ke tsolema ido wlhy"</p><p> cewazakayi kaxo kamin wa'azi ba Farty bah naji toh sarkin sanin gaskiya,sai kayi gaba haka" juyawa yayi zai fita Mommy tace" saura 3weeks kakoma sch ko?" </p><p>"Ehh Sulaiman yace"</p><p>"Kafada ma Daddy'n ku dai ko?"</p><p>"Sai yadawo zamuyi magana" yana gama fadan haka yayi gaba Farty tabishi da harara</p><p> "Allah kiyaye wasu chan su temakemu a rayuwa,mu bamuyi anfani ba kenan?" fartyce ke wanan maganan </p><p> Kallanta Mommy tayi gami dacewa " waye yace za'atemakeku wataran?" </p><p>" Ya Sulaiman mana, duk a kan su Afrah yake wanan bayanin banzan" Farty tacema Mommy</p><p> Tabe baki Mommy tayi sanan tace" bazanga wanan ranan ba kuwa, inshi baimin ba Hafiz yanan gaki kuma duk nasan sai kunzama wasu a duniya, sai yaje chan ya k'arata dasu Afra da Abdul din" </p><p>" Wlhy kuwa " inji Farty haka dai sukaita hiransu da Mommy..</p><p> </p><p><br /></p><p>Afrah ta maida hankalinta sosai a kan karatunta kasancewan sukusa fara exams din su na waec da neco</p><p> Farty kuwa babu abunda yadameta sai waya da chating.</p><p> Ya Sulaiman yakoma sch gida daka Hafiz, Farty,Afrah, Afifah Mommy sai Daddy inyana gari.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Asalin LABARIN....</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...*</p><p> </p><p> _PURE MOMENT OF LIFE WRITERS(We don't just entertain and educate, we also touch ♥ of the readers)_</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Story/written by_</p><p> ~Biebie Dee(Ss very)~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p>_Also dedicate 2 you sweetheart,darling Ummu-Abdulnasee Thank you so much for d love,support n care I really appreciate n I love you very very much sweetheart, wishing you Allah's blessings always_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Kema b'an manta da ke bah Munirah nagode sosai da sadaukar da littafinki a gare ni, Biebie dee nagodiya mai yawan gske sosai da sosai Allah yasa kigama lfya kamar yanda kikafara Lfya Ameen stay blessed babe*💕💕</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 11-12</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p>*#IG PML WRITERS*</p><p>*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p>*#http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"""""Sosai Afarh ta Maida hankali k'an karatun ta bata wasa da lesson da suke a school Sam, Alhmdulilhi kuma Tana fahimta. </p><p> Yau Friday tin da Mommy ta tashi take tsaki komeye dalili oho,Afrah ce tashigo d'akin da sallama amsawa Mommy tayi ciki ciki(y'an iskan suna kanta kenan🤣🤣) kallanta mommy tayi sanan tace</p><p>" ya naganki da uniform kuma inace bazaki ba"</p><p>"a'a zanje akwai abinda zanyi school ne"</p><p>Tsaki Mommy tayi gami da cewa "Allah tsare Allazi karatu" Ameen Afrah tace tabar d'akin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>A Palo ta tadda Afifah na jiranta "baby Tasha Muje kinji" Afifah a gaba Afarh a baya, sai da suka shiga mota Afifah tace</p><p>"anty Afrah anty Fartyy bata fitoh bah zata jamana latti wlhy" tana magana tana wani b'ata fuska, murmushi Afrah tayi sanan tace "wai bazata ba" juya ido Afifah tayi gami dacewa better" </p><p> Da kikaga batan kow?,babu ruwana wlhy"</p><p>"wanna basket d'in ai ni wlhy anty bana tsoranta, kotanan ma bata isa tamin komai bah"</p><p> Haka Afifah taita zuba surutu har aka sauketa school din su,kafin itama aka Sauke ta nasu school d'in.</p><p> </p><p><br /></p><p> A gida kam Fatty bata Tasha bah sai after 11 shima Mommyce ta isheta da naci,mik'a tayi gami da hamma,hanyan toilet tayi, tabar Mommy zaune bak'in gado, harara Mommy Tabita da shi gami da tsaki dawa da baya Fatty tayi</p><p>"Mommy mekuma nayi da ka tashi Nani? "</p><p>"ni dallah maza kifitoh wanka ki daura mana wani abu"Fatyy bata kuma magana ba tashige toilet </p><p> Sanda tafitoh Mommy bata d'akin D'an tsaki tayi sanan tashiga shiryawa, gown tasa mai armless hand,phone d'inta tadauka gami da d'anna earpiece a kunne tabar bedroom d'in</p><p><br /></p><p> Kitchen tayi Salamatu tagani tana gogegoge kunne d'aya na earpiece d'in tacire "ke ina Afrah tadawo? "</p><p>" a'a" Salamatu tace da ita</p><p>"mai Mommy tace ki dafa yau?"</p><p>"jolof na macaroni" tsaki Fatty taja sai kace kin wani iyane ma" Dariya Salamatu tayi gami dacewa" anty ko na barmaki kiyi NE? " harara mai lafiya Fatty ta dallamata ai Salamatu batasake magana bah har Fatty tagama dafa indomie d'inta tabar kitchen din Tana bin sorry na Justin Bieber</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Palo ta zauna taci tana bin wak'an, ya Suleiman ne yashigo side d'in Mommy zaije yaji voice ana wak'a juyowa yayi yaga Fatty "Kee"yace da k'arfin gske, cire earpiece d'in tayi gami da cewa</p><p> " ina kwana ya Suleiman"</p><p>"lafiya" yace da ita ya shige side d'in mommy </p><p> Tsaki Fatty tayi Kai kasani masifaffe" wak'anta tacigaba da ji tana chatting.</p><p><br /></p><p> Bayan Sun gaisa da Mommy ne yakefada mata yanasan zuwa Katsina, baki ta tabe sanan tace "yin me a katsina"</p><p>" zanje nama su inna sallama dakanan zan biya gidan anty Rabi na gaidata" </p><p>" da kyau, amma naga bak'a dad'e sosai da kaje bah ko?, gaisuwa da sallama kuma naga ko ta waya anayi ai ba sai anje bah"</p><p>Rage murya Suleiman yayi sanan yace "hakane mommy kawai inaso naga inna ne, amma ai ba dadewa zanyi bah is just 2days"</p><p> "Hmmmm kai dai kawai kafisan dagin Daddy'n ku, ko Zaria da ke nan kusa bacika zuwa kakeeyi ba amma kulin kai kana hanyan Katsina kai ko tsoro bakaji, kuma yaushe rabonka da kiran su anty Azeezah da sauran aunties d'inka? Amma kana min zanjen wata Rabi chan da bamu hada komai da ita bah" duk wanan maganan da mommy keyi tanayi ne Tana tapping phone d'in tah.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Murmushi Suleiman yayi sanan yace " ai mun riga munzama d'aya da anty Rabi tinda dai ga Abdul da Afrah kuma kowa yasan we cousins" </p><p><br /></p><p>Harara mommy ta watsa mai "bakada wani magana sai nasu, dama nasan abin da zakace kenan, me su Afrah suka zama in ba wahala bah? D'an riko har wani abin alfahari NE a duniya?"</p><p> " wlhy Mommy ki bar cewa haka, babu wanda yasan gobe mai zata haifar, kawai mubar ma Allah komai kawai"</p><p><br /></p><p>"Yauwa tashi kaje ni, Allah tsare na biyema haka zamutayi ai na t'abo gudan jininka su Afrah ba" murmushi Suleiman yayi yanacewa" mommy kenan ai ba yau bane tafiyan sai gobe insha Allah D'an ni da Abdul xamu anjima zaidawo"</p><p><br /></p><p> Allah kaimu kawai tace tana danna phone d'inta, har yakusa barin d'akin mommy ta tsadashi </p><p>"in ka idar da sallan juma'a ga sak'o kabiya gidan anty maijiddah ka kai mata zan kirata" amsa yayi yafita, waya tashigayi da Ummu Abdulnaseer tana kan wayan ne Fatyy ta shigo d'akin, xama tayi kusa da mommy, nata zaune har mommy tayi sallama da Ummu-Abdulnaser zama Fatyy ta gyara sanan race "wai mai yaya Suleiman ke cewa ne?"</p><p><br /></p><p>"mekuwa inbanda dai zanchan su Afrah"</p><p>Tsaki Fatyy tayi gami dacewa" banziya ba ta dage wai ina y'ar karatu Insha Allah babu wani abin arzikin da zata d'auko"</p><p> "inma ta d'auko a banxa tinda dai komai sai da hanya, shima Abdul d'in sa'a yaci yasamu ABU d'in D'an kawai naji daddy'n ku zai turasu kairo tare da Hafiz ne yasa nabari ya fara ABU dashima yana gida, shegu gayyar tsiya"</p><p> "mommy Hafiz za'akai kairo wlhy babu karatun da zaiyi wanan" harara mommy ta watsa mata sanan tace" har yaje ma da yadda Allah, naga dama kema sai na hana wlhy" dariya Fatyy tayi Sanan tace" haba dai wasa ne wanan, ni wlhy har na hangoni nan da 4year wayyo time d'in duk mugama school muyi kud'i, hoo wayaga mommy yaranta duk ansansu a nigeria,nasan su Afrah lokacin anata *zaman aure*" Dariya Fatyy ta bushe da shi</p><p>Mommy tace "Allah kaimu dai" Fatyy ta amsa da Amen dai.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sai 12:45 Afrah tashigo gida kasancewar yau Friday sai da tash wahala tasamu abin Hawa. </p><p> Tama dawowa mommy taje ta gaisar sanan tayi Hayan d'akinsu,Afifah tagani kwance sai waya takeyi da anty Nana da tablet d'inta, school bag d'inta ta aje sanan tashiga wanka gami da Alwala,tana fitowa shiryawa cikin black jallabiya sanan ta tayar da sallh Bayan ta idar da sallah ne tad'anyi apply simple makeup amma sai tayi kyau sosai </p><p> Kitchen tayi d'an sa wani abu a cikinta, Tana gaba Afifah na bayanta har suka isa kitchen d'in, abin tazuba masu sanan suka zauna Palo.</p><p> Suna k'an cin Abincin ya Suleiman da ya Abdul suka shigo nan suka shiga yimasu oyoyo, </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan ya Abdul yaje ya gaida mommy polo yadawo nan yasamu har afrah takawo masu abinci sunaci anata hira,duk wanan abu daketayi Fatyy na kwance tin bayan gaida ya Abdul datayi batasake magana bah.</p><p> Mommy ne tashigo Palo'n bayan tazauna ne take cewa "please kubar hiranan Daddy'n ku hanya girki za'ayi" tana magana tana kallan Afrah, nan da nan Afrah'n tayi hanyan kitchen Fatyy ko nan a kwance ko motsawa batayi ba, sai da ya Suleiman yayi mata magana sanan ta tashi tana turo baki...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>#toh Readers yakukaji ya kuma kuka gani </p><p># ya kuma kuke ganin za'ayi </p><p> Duk baku sani bah sai kun biyoni </p><p><br /></p><p><br /></p><p>~BIEBIE DEE CE~🌸</p><p>07039732859</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p>*Much love*❤❤❤❤❤</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> *gaisuwa ga dukkan masoya nah masu bibiyan labari na,nagode sosai Biebie dee na k'aunarku har cikin ranta a duk inda kuke a fad'in dunia*❤❤❤❤❤</p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 13-14_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"""""Koda Fatty tashiga Kitchen d'in ba aikin da tayi Afarah da Salamatu ne ketafaman aikin,wak'anta Kaiwai taketaji minti minti tana tsaki</p><p> Sai da taga sungama tass tabar kitchen d'in Salamatu na k'ara gyara wajen,Mommy tashigo kitchen da fara'arta shirye take ciki lace mai shegen kyau da tsada takoyi kyau abinta 😝 bude wamars d'in tashigayi babu ko d'an sannu da aiki sai da ta gama bud'esu tas sanan tace" yayi, sai a jeresu a dining ko, nan da nan Afrah tagama komai yadda mommy'n tace</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> K'arfe 6 daidai Daddy yadawo direct side d'insa na nufa, sai da yayi wanka sanan yaran duk suka shigo yimai sannu da hanya cikin Mirna duk ya amsa, sunan duk zaune akayi k'iran sallah nan duk suka Tashi, masjid su daddy suka tafi yayi da su mommy duk suka wace bedroom d'an gabatar danasu sallan</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Su daddy basu shigo gidan bah sai da sukayi sallan isha </p><p> Babban Palo duk suka zauna nan mommy tayi saving Daddy yayi da Afrah tayi saving sauran mutanan Palo'n nan ko wa yamaida hankalinsa kan plate d'insa baka jin k'aran komai sai na spoons</p><p> </p><p> Bayan Sun kammala Afrah tashiga kwace kayan ganin Daddy da su yaa Suleiman yasa Fatyy ma kwace wasu kayan, Salamatu ne ta k'arasa sauran aikin</p><p><br /></p><p> Sunan zune Afifah tasasu gaba sai Zuba surutu takeyi Anita dariya Hafiz da Fatyy kam tsaki suketayi </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya Suleiman ne yakalle Daddy sanan yace " daddy ina san shiga Katsina gobe Insha Allah ni da Abdul"</p><p><br /></p><p>"Allah kaimu da rai da lafiya nima dama Sunday nakeson naje,tinda zaku gobe duk sai a shirya gaba d'aya muje"</p><p><br /></p><p>K'aramin tsaki Hafiz yayi sanan yace" nikam bazan samu zuwa bah d'an ina da abinyi gskia"</p><p><br /></p><p>" menene abinyin naka ko kana da sana'a ne? " daddy yatan bayeshi </p><p><br /></p><p>"a'a, kawai dai" kamin shuru kowa yashirya kawai"</p><p><br /></p><p>Suleiman bak'aramin dad'an maganan daddy yayi bah smiling kawai yaketayi </p><p><br /></p><p>Duk wanan abu dakeyi Mommy najinsu sai da ta gyara zama sanan tace </p><p>"toh Alhaji tin da bazashi ba a barshi mana, ai Hafiz ba yaro bane ? "</p><p> Shuru kowa yayi babu wanda ya k'ara magana a Palo'n Mommy ce ta fara barin Polo'n Fatyy ma tabita Chan phone d'in Hafiz yashiga ringing tashin shima yayi</p><p><br /></p><p> Yarage daka Daddy,ya Suleiman, ya Abdul sai Afarh da Afifah hira suka d'an tab'a da Daddy sanan shima yayi masu sai da safe </p><p> Nan suka shiga hira Afrah sai zuba takeyi ya Suleiman ya Zuba mata ido yana jin wani farin cikin a ransa wanda baisan Dalila bah </p><p><br /></p><p>Afifah kam tini tayi bacci</p><p>Sai 12 suka ma juna sallama, sai da Afrah ta kashe duk kayan wutan sanan ta dauki Afifah sukai nasu bedroom d'in.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da asuban fara ta tashi sai da suka idar da sallah sanan Afarh tayima Afifah wanka d'an itama yau Afifan asubancin tashi tayi sabida taji zajen xuwa KT </p><p><br /></p><p> Kitchen nufa abu mai sauki tayi duk tazuba a warmers tazuba nata da na Afifah a plate,</p><p> Bayan Sun gama Afifah tafara shiryawa sanan itama tashiya cikin lace Riga da skirt d'inkin yayi masifar kyau, kwaliya tayi amma ba sosai ba amma zokuga kyan da tayi, face d'inta ta kalla a mirrow sai Kawai ta fara dariya </p><p><br /></p><p>"Darian mekikeyi anty" Affifah tace da ita </p><p><br /></p><p>"coz zanga inna da mami yau da su Arfat da fahad(Arfat da Fahad k'anan Afrah ne, bayan rasuwan Salis da shekaru 4 Rabi tayi aure shine ta aifesu) </p><p><br /></p><p>K'arfe 6:30 dai dai su Afrah har sungama shirun su d'akin su yaa Suleiman tayi bayan Sun gaisa tace" yaya wai baku Gama bane, time na tafiya fan, ina ma yaa Abdul ne?" ta k'arashe maganan tana D'an dube dube </p><p><br /></p><p>"yanzo zamushigo muyi breakfast sai mu dau hanya Insha Allah "</p><p><br /></p><p>"Kai nasamaku a takeaway sai kuci a mota kasan lokaci na tafiya fa"</p><p><br /></p><p>Dariya yayi sanan yace kedai jeki gamunan yanzo,aje a k'arasa yima Mami makeup " dariya kawai tayi ba Tate da tace komai bah</p><p><br /></p><p>Tana komawa side d'insu bedroom d'in Mommy tayi, gaisheta tayi mommy ta amsa fuskanan kaman dare😂😂 ita dai tayi gaba Abinta</p><p> A Palo ta tadda Daddy har yashirya kaidashi tayi ya amsa gami da tsokanar ta</p><p>"mamana har kinrigani shiri,lallai Kuwa anya ma kinyi bacci?"</p><p><br /></p><p>"nayi sosai ma Daddy "</p><p>Mommy ne tashigo Palo'n sai yatsina fuska takeyi nan Afrah tabasu waje kitchen tashiga D'an sama su ya breakfast d'insu a takeaway </p><p><br /></p><p><br /></p><p>K'afe 7:30 duk Sun gama shiri kowa yafitoh yayi kyau abinshi,Afarah sai washe baki takeyi</p><p><br /></p><p>Ya Suleiman yanufo wajen da car key Hannun shi kallan Afrah yayi gami dacewa </p><p>"my sisi kiyi kyau sosai"</p><p> Dogon tsaki Fatyy ta jaa mommy kam harara mai lafya ta jefama Suleiman </p><p> </p><p>Daddy mommy saiAfifah motor su da ban</p><p> Yaa Suleiman ya Abdul su biyu a nasu Motan sai Hafiz,Fatty sai Afrah nasu motan da ban suma wanan duk tsarin mommy ne kuma sabida Afrah tayi hakan....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Toh masu karatu kubiyo ni dai muje zuwa*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Amma ya kukejin labarin ???</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>~BIEBIE DEE CE~🌸🌸</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> *gaisuwa ga dukkan masoya nah masu bibiyan labari na,nagode sosai Biebie dee na k'aunarku har cikin ranta a duk inda kuke a fad'in dunia*❤❤❤❤❤</p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_15-16_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>""""""Su isah katsina lafiya duk daa dai Afrah tasha maganganun banza da rainin wayo wajen Hafiz da Fatyy,har D'an kuka sai da tayi, Amma suna parking k'ofar gidan inna duk tanema damuwan tarasa</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tinkafin motan ya tsaya Afrah ta bud'e tayi cikin gidan a guje tsaki Hafiz da Fatty sukayi gami dacewa" stupid girl "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hugging d'in Inna tayi Tana daria "kedawaye? " inna ta tanbayeta "ni kadai ce" inna bata Kai da magana bah Su daddy suka shigo, murna sosai inna tayi d'an taji dad'in ganunsu matuka </p><p><br /></p><p>"barkanku da zuwa mutan kaduna,kusha hanya" waje tasamu ta zauna nan aka shiga gaisuwa,kafin kace Mai inna tasa Zainab ta cika masu gaba da kayan motsa Baku,</p><p><br /></p><p>Hafiz da Fatty tinda suka gaida inna basukuma magana bah phone kawai suketa latsawa </p><p><br /></p><p>Suleiman,Abdul, Afrah da Afifah kam sunsaka inna gaba sai tsokanar ta sukeyi Mata</p><p><br /></p><p>Inna na lura da Mommy tinda sukazo takewani cin magani kallonta kawai inna keyi tana mamakin bak'in Hali irin na Bilki </p><p><br /></p><p>"Inan bari mushaga daka ciki mommy tace"</p><p><br /></p><p>"toh ai gara a huta gajiya" nan Faaty tabi bayan mommy'n</p><p><br /></p><p>Tashi Hafiz yayi " sai ina kuma d'an nema" k'aramin tsaki yayi sanan yace iska zansha"</p><p><br /></p><p>"tohh yau inajin salon salo d'akin nawa ba iska kenan"</p><p><br /></p><p>"nifa bance ba k'arki Kai ni gaba yanxo kisa Daddy yafara.." bai k'arasa bah yayi shuru</p><p><br /></p><p>Musrmushi tayi sanan "tace sai kaje gidan malam duk ka gaidasu nasan dai Kai ba kwana zakayi bah"</p><p><br /></p><p>" toh" kawai yace yafita yana k'ara Jan tsaki</p><p><br /></p><p>Daddy ne ya kalle su Suleiman yace " anko shigo da kayayyakin nan?"</p><p><br /></p><p>"a'a daddy, ai ni na manta da wasu kaya, buri na naga tsohuwa mai ran k'arfe" daria duk sukayi sanan suka Tashi dan shigo da kayan </p><p><br /></p><p>A waje suka ga ySafiyanu yaron mak'okin Inna, sai da suka gaisa sanan yatayasu shigo da kayan</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kayan abinci ne iri iri babu abinda babu a ciki sai atanfofi da hijabai da takalman sakawa godia inna tayi gami da samai Albarka</p><p><br /></p><p>"Bari na d'an fita mugaisa da jama'a" daddy yace</p><p><br /></p><p>"adawo lfya"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hira da barkonci aketayi da inna da jikokin nata Afifah sai zuba zance takeyi ana ta faman daria </p><p><br /></p><p>A cikin d'aki ko mommy ne da Fartty ke k'ananun maganganun su wanda suka Saba </p><p><br /></p><p>"mommy wlhy inna tafisan su Afrah "</p><p><br /></p><p>"ai nad'ade da sanin wanna sai dai na baki labari"</p><p><br /></p><p>"Allah bamu rai da lfya wallahi zan bama inna mamaki, D'an wlhy ni sai nafi daddy kud'i, ke mommy kinsan dai yanda Loyers kesamun kud'i, ki bar su kawai wlhy zan bada mamaki "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"kibar y'an rainin hankali, kallan kowa nakeyi a tafin hannu na wlhy"</p><p><br /></p><p>" yauww sweet mum shiyasa nake sanki wllahi, ai insha Allah daka Abdul d'in har banzan Afran babu wanda zaicigaba "</p><p><br /></p><p>"ki daina wahalar da kanki ,abune gashi a baiyane k'iri k'iri, ba class d'inku daya da Afrah ba Sam, kinfita haduwa da sanin yaran Manya,sch dinku yafi nasu kan me zaki hada kanki da ita? ai da babbanci a lamari"</p><p><br /></p><p>Hakadai sukai ta hiransu har akai k'iran sallan azahar </p><p> Kuma a wanan lokacin ne Afrah da Zainab jikan inna Rakiya suka gama shirya abincin su mai rai da lafiya, sallah duk suka tafi gabatarwa yayinda mazan duk sukayi masjid </p><p><br /></p><p><br /></p><p>A Palo'n inna duk a ka baje ina kwasan girki gami da kunun aya mai shegen dad'i a na ci ana wasa da dariya </p><p><br /></p><p>Bayan Sun gama gami da gyara wajen sabon shafin hira a ka bude, kowa zuba Kawai yake inkacire Fatty da ita sama sama take maganan</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sai da su Daddy sukai sallan la'asar sanan suka fara haraman tafiya,</p><p><br /></p><p>Sallama inna tamasu gami da k'ara samasu Albarka, tsaraba iri iri ta hada masu nanan suka masu rakiya waje </p><p><br /></p><p>Inna ce tayi manana " ke Fatima bazaki kwana wajena ba ko? Kina Abu kaman yarinya k'arama, ke kikasa ai"</p><p><br /></p><p>Su daddy ne suka fara shiga mota deriver ya jasu sanan Hafiz da Fatyy suka shiga nasu motan, sai Hannu inna ke d'aga masu har suka b'ace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"bar hannun haka har ya tsinke" Abdul yace ma inna </p><p><br /></p><p>Dariya Suleiman yayi sanan yace" daka barta ai in ya tsnke anamata na robber "</p><p><br /></p><p>Wani mahaukacin dariya Afifa tayi sanan tace " waya ga inna da hannun kutare"</p><p><br /></p><p>Duk dariya sukayi gaba dayansu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kaman a mafarki Aunty Rabi taji sallanman Afrah </p><p>Bata yadda ba sai da ta gansu ita da Afifah</p><p><br /></p><p>, kallonta kawai anty Rabi keyi rungume ta Afrah tayi gami dacewa"i miss you so much mami"</p><p><br /></p><p>"ke da waye wai?" mami ta tanbayeta</p><p><br /></p><p>"ni da su yaa Suleiman ne"</p><p><br /></p><p>"shine kika barsu waje?"</p><p><br /></p><p>Afrah bata kai ga bama Mami answer ba sai gasu </p><p><br /></p><p>"bana murna zakuzo ko notice babu a shirya maku wani Abu"</p><p><br /></p><p>"haba mamin mu surprise ne kawai wlhy ko Abdul?"</p><p><br /></p><p>"ehh wllahi mami kiyi hakuri kawai,next time bazamu k'ara bah"</p><p><br /></p><p>" yamaku kyau mushiga ciki"</p><p><br /></p><p>Bayan Sun zauna aka k'ara gaisawa mami tacika gabansu da kaya iri iri </p><p><br /></p><p>"wai ina su Arfat ne mami, ina uncle ?"</p><p><br /></p><p>"ba mamaki ki gansu yanxo Sundawo, d'an fita sukayi"</p><p><br /></p><p>"Okay"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"ina Hafiz ne da Fatima,ko basu bane"mami ta tanbaya </p><p><br /></p><p>"ai mami wayanan tun jiya suka juya wai bazasu kwana ba"</p><p><br /></p><p>"au lallai tin jiya kuka shiga banda ko labari, ko ta waya ai asanar dani"</p><p><br /></p><p>Abdul yace"mami surprise ne fa ba'a fada"</p><p><br /></p><p>Basufi minti talatin da zuwa bah sai gasu ko sundawo </p><p><br /></p><p>Nan duk sukamai sannu da dawowa,zama yayi suka gaisa cikin sakin fuska </p><p><br /></p><p>Hira akaitayi Afifa tasiga cikin su Arfat sai maiyance take kamar Babba🤣</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nan suka wuni sai dare Abdul da Suleiman suka masu sallahma suka koma gidan inna Afifah da Afrah kam kwana zasuyi....</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_this page is for you AUNTY SIS💞 thank you so much for the du'a i really appreciate, may Allah protect you n your family 👪 always n forever Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 19-20_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*KADUNA STATE*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>""""""""""""Zaune take kan sallaya da ta idar da sallan magrib dugon tsaki taja phone d'inta ta jawo number'n Suleiman ta shiga dialing amma still a kashe jefar da phone din tayi saman godo gami da jan wani dugon tsaki</p><p><br /></p><p>"Wai menene mommy"Fatyy ta tanbaya</p><p><br /></p><p>"Mekuwa in banda y'an iskan yaranan sunki dawowa, duk nawkiran number'n su switch off "</p><p><br /></p><p>"Yanzo haka munafukanan ne sukace abari gobe, barinma wanan shegir Afran jitakeyi kaman family d'inta ne ita kadai"</p><p><br /></p><p>"Zata aika wllahi"</p><p><br /></p><p>"Dama kawai sukoma katsinan wajen inna, da yafi masu duk muhuta"</p><p><br /></p><p>"Bakida hankali wallahi sam, sukoma fa kikace, saboda duk abinda Daddyn ku yasamu yaje can ya sauke masu kenan, bakisan mai kike fada ba wlhy, ko ance maki inna zaitai ta kallansu ne batare da tace aymasu wasu abubuwan ba?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ke mommy daka magana sai masifa, ni menene nawa? Kedama haka kike ba'a maganar arziki dake, saikace nine na bata maki ran habaa" ta k'arasa maganan tana barin bedroom d'in</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hijab d'inta ta cire ita tayi palon (niko nachai hmmm). </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Duk sunan zaune a palon babu mai magana kowa da abinda yakesak'awa a ranshi, minti-minti mommy na tsaki, kallan side d'inda Fatyy take tayi sanan tace" wai ina wanan shegen yaron ne?" </p><p><br /></p><p>"Wakenan?" Fatyy ta ce</p><p><br /></p><p>" dan ubanki Hafiz nake magana"</p><p><br /></p><p>"Ohhhh, toh ni ina zansani, ke da yaron ki call him now "</p><p><br /></p><p>"Duk zanci ubanku wllahi, na lura duk kun rai nani a gidanan"</p><p><br /></p><p>"Toh wai memukayi ne mu? Kawai sai wani masifa kikeyi, nifa shiyasa sometimes banasan zama inda kike wllahi d'anni bancika san matsala ba, ke kanki kinsani, kawai kijira wayanda suka bat'a maki rai su dawo sai kiyi masu masifar da jaraban"</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Shuru mommy tayi d'an takasa magana, sunan zaune dai mommy taji kaman ana bud'e gate,window ta laka d'an ganin mai shigowa motan Sulaiman ne ya shigo, waje tayi da saurinta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sulaiman ne yafara fitowa sai Afrah da Afifah, Abdul kam yana k'ara ygara parking motan </p><p><br /></p><p> Karasowa wajen ta Afrah da Afifah sukayi gami da cewa" sannu da gida moomy"</p><p><br /></p><p>" dallah ku matsamin na bar ganinku"</p><p><br /></p><p>Babu musu sukawuce ciki Afrah a ran ta tace "masifar na kusa kenan"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kai Sulaiman"ta kirashi da k'arfi </p><p><br /></p><p>K'arasowa yayi gami da cewa " am sorry mommy, munyi dawowan dar... "</p><p><br /></p><p>Bata bari ya k'arasa bah ta fara masifa, hannun ta yaja suka shiga palo </p><p><br /></p><p>"Haba mommy, daka dawowa na sai fad'a, indan wani laifin nayi ai sai ki bari na huta kafin ki sanar da ni"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Abdul ne yashigo yana gaishe ta, ko kallanshi batayi ba bare ma ta amsa sai dag'a mai hannu da tayi, ficiwa yayi side d'insu</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kallonta ta maida kan Sulaiman sanan tace</p><p><br /></p><p>" bakada asara shiyasa zaka zubu marasa afani cikin mota kudauko hanyan kaduna, inda kamutu ni keda asara basu ba"</p><p><br /></p><p>"Nifa mommy banasan k'anan magana, daka wanan sai wanan haba d'an Allah, kuma waye yace maki su marasa anfani ne? Kowa dakika gani duniya da anfaninsa tinda Allah ne yayi su"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Toh dukeni, nace kadukeni yaro babu damar a fad'a gskia"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>" Allah kare ni da dukanki, babu wani gskia a nan kema kinsani"</p><p><br /></p><p>" fita kabani waje shasha kawai"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" tafiya ma zanyi na bar gidan duk mu huta"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" wllahi mommy yaa sulaman d'inan yarai naki"Fatyy tace</p><p><br /></p><p>"Kibarni dashi zanyi maganinshi"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Afifah ce tashigo palon da gudu, kusa da mommy ta zauna </p><p><br /></p><p>" mommy kalle abinda anty Rabi tabani, tache kar nabud'e sai nazo gida, please budemin"</p><p><br /></p><p>Wurgi da bag din mommy tayi gami da cewa " Rabi har tana da abinda zatabama yarana, lallai ma"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da gudu Afifah tabi bag d'in sanan tace" ke da ma mommy haka kike komai masifa, daka dawowa na yau" </p><p><br /></p><p> Daukan bag d'inta tayi tawuce bedroom d'insu</p><p>Abakin k'ofa suka hadu da Afrah zata fitoh duk abinda mommy tace duk taji kallan Afifah tayi sanan tace </p><p>" baby banace in anamaki fad'a kidena magana ba? "</p><p>"Aunty ke bakiji abinda mommy kecewa bane? "</p><p><br /></p><p>"Naji amma babu kyau, kidena kinji"</p><p><br /></p><p>"Toh insha Allah, wallahi mommy ta batamin rai"</p><p><br /></p><p>"Amma nace kiyi shuru ko"</p><p><br /></p><p>"Sorry, sorry nayi"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda Sulaiman yadawo d'akinsu hakury yaita bama Abdul, Abdull yace ba komai wlhy "</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yau wensday Fatyy, Afrah da Afifah duk sun wuce school, Abdul ma tin ran Monday da safe koma Hafiz kam yafita yawanshi na fama </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Turo k'ofan akayi kanshi yad'aga dan ganin wanene mommy ce, abinda yakeyi yacigaba dayi batare da kalleta ba </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Haba big brother, har yanxo baka huce bane wai? Saura Fa 1day murabu" mommy tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kallanta Sulaiman yayi sanan yace " noo kinsan ni bani da rik'o, kawai ina dan wani aiki ne"</p><p><br /></p><p>"Okay toh adai yi hakuri"</p><p><br /></p><p>"Yawuce fa mommy, kawai dai kicanza wasu halin"</p><p><br /></p><p>"Insha Allah zan gyara"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hira suka d'an yi sanan tafitah</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mommy kenan akwai san nata.....</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 21-22_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"""""""""""""""Thursday yau ne tafiyan ya Sulaiman, Amma sai Abuja zai je sai Friday zasu tashi</p><p><br /></p><p> Zaune suke dukkansu a babban palo, kasan cewan yau duk basu je sch ba, wai sai kunga tafiyan Sulaiman d'in daddy, Mommy da dukkan ya ran gidan </p><p><br /></p><p>"Kai Hafiz kagama research d'in sch dinkuwa? " Daddy ya tanbaya</p><p><br /></p><p>"Noo, nafasa kairon ma Daddy"</p><p><br /></p><p>" sai ina? "</p><p><br /></p><p>"Ghana nakeso"</p><p><br /></p><p>Tsaki Daddy yayi gami dacewa nidai zanga randa zakai hankali, kaidai kawai kadauki mota kaje yawo shine matsakanka, ghana kuma bazakaje ba duk nayi canceling, jamb zaka sake da sisters dinka sai ka fara sch din anan"</p><p><br /></p><p>Magana Hafiz yashiga yi k'asa-k'asa wanda ni kai na bansan mai yake cewa ba nadai ga bakinshi nata motsi</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>Kallan Mommy yayi, itama shi d'in take kallo</p><p><br /></p><p>Side d'in da Daddy nasu yake ta kallah sanan tace</p><p><br /></p><p>"Haba Alhaji kai fa kasamai rai fita dashi waje karatu, sai yanzo da rana tsaka kace wai kafasa, wanan bai kamata bah gskia dawasu ne jiki na rawa zakamasu"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kallanta Daddy yayi da kyau sanan yace</p><p><br /></p><p>"Mai kedamunci wai? Indai ina magana kedena samin baki"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tinda Mommy ta fara maga duk yaran suka bar palon</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sulaiman ne yashigo da sallama</p><p><br /></p><p>"Daddy tinda kai ma Abujan kayi mufita tare kawai" Sulaiman yace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mikewa Mommy tayi gami da cewa "aa, kai da sai 4"</p><p><br /></p><p>"Yes, yanzo nakesan natafi kawai, zamuyi waya ai"</p><p><br /></p><p>"Oky bari nashiga na fito" Daddy yace</p><p><br /></p><p>Bedroom d'in su Afrah Sulaiman yayi, zaune yaganta saman gado da wani book hannunta da alama katu takeyi Afifih na kwance game takeyi cikin tab d'inta</p><p><br /></p><p>"Sisters" yakira sunansu</p><p><br /></p><p>"Ni zan wuce, sai kumin Addu'a"</p><p><br /></p><p>"Ahh yaa ba sai d'an Anjima ba" Afrah tace</p><p><br /></p><p>Kai ya girgizamata alaman a'a</p><p><br /></p><p>"Toh Allah tsare, yakai ku lafya, ya bada sa'an karatu"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen thanks </p><p><br /></p><p> "Yaa Allah kai ka lfya, Amma please inzaka dawo next year d'in kazo min da iPad d'in" Afifah tace</p><p><br /></p><p>"Matsalanki kenan ai, kedai a saimaki abu"</p><p><br /></p><p>"Tap, wallahi gara ni da wanan Anty Fattyn nifa har addu'a nayi ita kokasan dai baxatayi ba ko? "</p><p><br /></p><p>"Kinciki magana lil-lil"</p><p><br /></p><p>"Ai munfi wayo irinmu ko anty Afrah? "</p><p><br /></p><p>Dariya duk sukayi </p><p><br /></p><p>"Jeeki kitchen ki amso min ruwa Afifah"</p><p> Nan Afifih tayi kitchen ta barsu</p><p><br /></p><p>"Toh sis zamurika waya, chatting ko"? Sulaiman yayi maganan yana kallanta</p><p><br /></p><p>"Yes insha Allah "</p><p><br /></p><p>"Toh kuta hakuri kinji, wata rana sai labari"</p><p><br /></p><p>"Hakane babu komai insha Allah"</p><p><br /></p><p>" ga ruwan yaya" Afifah tace tana daria</p><p><br /></p><p>"Kee mekikema daria ne?, ina Fatty wai? "</p><p><br /></p><p>"Ahh ni yaya ba komai, taba d'akin Mommy i think "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Har bakin mota duk suka rakoshi</p><p><br /></p><p>Fatty tace "please yaya kabarmin laptop d'in? "</p><p><br /></p><p>"Yes kidauka ba d'an halinki ba"</p><p><br /></p><p>"Thank you "kawai tace</p><p><br /></p><p>"Toh Afrah Jinki abinda nafada maki ko? "</p><p><br /></p><p>"Ehhh"tace a hankali</p><p><br /></p><p>Tsaki Fatty tayi gami da watsama Afran harara</p><p><br /></p><p>Duk wanan abu dakeyi Mommy bata sani ba tana side d'in Alhaji suna magana</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka dai suka tafi suna dagama suna hannu har suka bar gidan</p><p><br /></p><p>Afrah duk sai taji babu dad'i wunin ranan a d'aki ta wuni ko Hadda bata je ba</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya Sulaiman yatafi da sati d'aya Fatty da Afrah suka fara exams d'in su</p><p><br /></p><p>Banbanci da saankai iri iri babu wanda Afrah bata gani wajen mommy, gidan baya mata dad'i sam d'anma tana waya dasu Inna, Mami, yaa Abdul da ya Sulaiman sai kuma in Afifah na gida suta labari</p><p> Fatty kuwa in bataga dama ba ko magana batayi mata kanta k'ara girma yayi</p><p><br /></p><p>Cikin nasala da kwanciyan hankali duk suka kammala exams d'insu WAEC, NECO da JAMB</p><p>Inda Afrah keda 210 Fatty kuma 167</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*YANZO A KA FARA*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_kuyi hakuri da wanan kai na ke ciwa_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>fans yakukejin labarin???? </p><p><br /></p><p>Shin Mommy zata bari Afra ta fara school bayan Fatty nataci jamb ba??? </p><p><br /></p><p>Ya kuke ganin zata kasance??? </p><p><br /></p><p>Inajiran comments d'inku</p><p><br /></p><p><br /></p><p>~biebie dee~🌸</p><p>07039732859</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Page17-18_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"""""""""Afrah da Mami kwana sukayi suna hira, Mimi taji dad'in zuwansu sosai sai kusan 3 na dare suka kwanta </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan Afrah tayi sallah kitchen ta nufa ta shirya masu brkfast Mai lfya, sai da ta gama ta yi wanka sanan ta sa su Arfat ma duk sukayi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sai After 9 Mimi tafitoh, a Palo duk ta gansu kallo sukeyi </p><p><br /></p><p>"woyyo babies d'ina kuyi hakari yanzo za a shirya Brkfst kuji" Mami tace da rayan </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"AI duk na gama mami jeki shiya kawai"</p><p><br /></p><p>"thank you sweetheart, Allah maki albarka"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ameen ameen mami nah"</p><p><br /></p><p>Nan mami ta shige d'an shiryawa </p><p><br /></p><p>Murmushi Afrah tayi a ranta tace" zama da uwar da banaka bah sai hakuri,dan aikin da nayi tana godia abinda mommy bata t'aba cewa ba"</p><p><br /></p><p>Sunan zaune su yaa Abdul suka shigo nan uncle junaid ya fitoh hiran aka shiga yi dashi, Mami nafitowa akashiga cin abinci bayan Sun gama Arfat ta kwashe kayan dan wankewa hira sukai tayi har kusan 1 yayinda mami da Afrah ke kitchen dan shirya abincin rana</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan duk sundawo da ka masjid matan ma duk sunyi sallah nan aka shiga cin abinci, ko da suka gama hira suka d'anyi kadan sanan aka Fara haraman tafiya, tin da Afrah tashiga bedroom dauko side bag d'inta ba ta fito ba</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bin bayanta mami tayi a bakin gado ta ganta zaune </p><p><br /></p><p>"haba Afrah keda zaku Fara exams menene na damuwa, IN kungama ba sai ki dawo bah"</p><p><br /></p><p>Kallanta Afrah tayi sanan tace "ba sai mommy ta yadda ba"</p><p><br /></p><p>"noo don't worry, sai nasa babansu Arfah yakira daddy'n naku, abinda nakeso dake shine ki kara hakuri kan wanda kikeyi komai da kika gani time ne, nafi sannin kowacece anty Bilki kiyi hakuri kinji ki tsaya a yanda na sanki"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Insha Allah mami zan cigaba da zama da su da zuciya d'aya kaman yanda na Saba Insha Allah "</p><p><br /></p><p>"yauwa princess Allah maku albarka"</p><p><br /></p><p>"Ameen yaa Allah" Afrah tace, nan ta dauki bag d'in tayi Palo </p><p><br /></p><p>Ya Suleiman ne yayi magana " haba sis kin wani shige kin barmu, yau fa zamu koma kd"</p><p><br /></p><p>Beautiful eyes d'inta ta zero sanan tace " yau kuma yaa tafiyan dare zamuyi kenan"</p><p><br /></p><p>"eh mana mommy ce tace wai mudawo yau, gashi Abdul ma zaikoma school gobe da sassafe"</p><p><br /></p><p>"toh Allah kaimu lfya, amma zamukai dare fa"</p><p><br /></p><p>Abdul da tunda suka Fara magana bai ce komai bah sai yanzo " kisa ma aranki har mun kai kaduna da yadda Allah "</p><p><br /></p><p>Mami ce tafito da wani d'an jaka hannunta wajen Afifa ta nufa </p><p><br /></p><p>"baby gashi ko, inkinje gida sai ki nude thank you so much ki gaidamin mommy sosai"</p><p><br /></p><p>Dariya Afifah tayi sanan tace" Thank you so much anty Rabi Insha Allah mommy zataji"</p><p><br /></p><p>Wajen Suleiman ta juyo "toh d'an turai Allah tsare, Allah kaika lafiya, banda wasa ayi abin da akajeyi kawai, Allah bada sa'a thanks alot"</p><p><br /></p><p>Shima Abdul d'in addu'an tayi mashi sanan uncle junaid ya hada masu sha tara na har ziki sai Godiya sukeyi, har waje duk suka rakosu Arfah hadda hawayenta </p><p><br /></p><p>Ya please don't forget kaji" Fahad yace </p><p><br /></p><p>"ah don't worry bro, yaa Abdul zai kawo ma har gida"</p><p><br /></p><p>Har suka fitoh Arfah bata bar kuka ba ta rike Afrah gam 2k yaa Abdul ya zaro ya bata gami da cewa" je kisha ice cream, ranki zaiyi sanyi"</p><p><br /></p><p>Kawo kud'inan mami" tace ai a guje ta shige gida dariya duk sukayi, mota duk suka shiga suna d'aga masu hannu </p><p>Ba subar wajen bah sai da suka daina ganin motan Nasu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ko da suka koma gidan inna basu wani dade bah suka fitoh, kaya iri iri ta hada masu gami da masu addu'a da sa masu Albarka</p><p><br /></p><p>Sun kusa waje Afifah tace" Inna ina d'an waken da kikace zakimin yau"</p><p><br /></p><p>"auu yanan ai angama na zubashi a roba Mai murfi,maza kije kitchen ki dauko" da gudu tayi cikin gidan babu jumawa ta dawo </p><p><br /></p><p>"Kai gskiya nagode tsohuwa wanna Abu haka"</p><p><br /></p><p>"kedai wanna y'a akwai shegen manyace" dariya Afifah tayi sanan tace ai wajenki na gado"</p><p><br /></p><p>Duka Inna taso Kai mata, gocewa tayi sanan tashige mota "zaki sani" inna tace </p><p><br /></p><p>Bayan duk sun shiga motan Suleiman a mazaunin driver Abdul a jefanshi sai Afrah da Afifah a gidan baya </p><p><br /></p><p>Kallan Suleiman Inna tayi sanan tace" saura IN ka koma bokon kak'i Kira na, na hanaka matar Allah shi Abdulrahm ban da Marsala da shi, kai ko ka bini a hankali"</p><p><br /></p><p>Dariya Abdul yayi sanan yace" k'arma kidamu zaikira"</p><p><br /></p><p>" k'arma yakira yaga aiki da cikawa"</p><p><br /></p><p>"toh ke Inna ki Fara chatting mana" Afrah tace tana daria</p><p><br /></p><p>"zanyi maganin ku, kutafi Allah tsare ya kai min ku lafiya,duk a k'ara gaida mutan gidan Allah yayi Albarka"</p><p><br /></p><p>Duk suka amsa da Amin, suna d'aga mata hannu itama hannun take d'aga masu Tanana tsaye har tabar ganansu sanan tashiga gida..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"wlhy kowa y'all kashe phone d'inshi kafin mommy ta k'ira" Afifa tace</p><p><br /></p><p>" good idea lil-lil" Suleiman yace </p><p><br /></p><p>Nan duk suka kashe phones d'insu, aka ciga ba da tafiya....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>(Allah tsare hanya nace)</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Thais page is for you Aunty Maijiddah musa thank you so much for d love n care Biebie dee na godia*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PAGE 23-24_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"""""""Mommy ce zaune gaban mirror ta sha kwalliya, Fatty tashigo d'akin babu ko sallama, kallanta Mommy tayi sanan tace "wai bazaki je bikin bane? Fuska ta b'ata sanan tace</p><p><br /></p><p>" noo bazani ba, coz yau Afrah zataje"</p><p><br /></p><p>"Mesuka hada da Muniran da har zataje bikin? "</p><p><br /></p><p>"Wai Mommy kin manta islamiyya d'aya mukayi ne, abinda yasa nake kula Muniran ma sabida naga suna da kud'i ne kuma she's classy ba laifi Amma tin da zataje yau ni bazani ba d'an she's not my mate "</p><p><br /></p><p>"Okay ki shirya sai muje gidan Ummu-Abdulnaseer tare, inna san zuwa gidan Aunty Maijiddah ma d'an tak'ira ni kayanta daka dubai sunzo so duk saimuje"</p><p><br /></p><p>"Yauwa Mommy, bari na shirya toh"</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sai da Fatyy ta bat'a moren 1 hour wajen shiryawa, tasha kwalliya cikin atanpa pink n blue d'inkin riga da skirt, d'inkin yayi kyau sosai, wani d'an yalolon mayafi tasa blue sai wani takalmi mai shegen tsowo kasanwar Fatty bata da tsowo (uwarta ta gado🤣) wani side bag ta sa sai earpiece da ta danna a kunne</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mommy toh muje" cewar faty </p><p> Sai da Mommy takalle ta sanan tace "kiramin Afrah"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kizo inji Mommy " Fatyy tacema Afrah</p><p> Batare da tace komai ba tabi bayan Fatyy'n </p><p><br /></p><p>Da sallama ta k'araso wajen Mommy'n, babu wanda ya amsa cikisu, kallanta Mommy tayi da kyau sanan tace" zakije biki yau shine ban isah kifadamin ba ko Afrah?"</p><p><br /></p><p> Ware beautiful eyes d'in tatayi gami da cewa</p><p><br /></p><p>"Nooo Mommy babu inda zanje ni, da zan fita da zan fada maki tin shekaranjiya ai"</p><p><br /></p><p>Baki Mommy ta tabe sanan tace" ke kika sani, indai zaki fida ki kulemin duk inda yakamata, fita zamuyi sanan a daura ko jolof ne kan nadawo sai salat"</p><p><br /></p><p>"Okay sai kundawo, sis bye"</p><p> Hannu kawai Fatty ta dag'amata sukai gaba tabisu da eyes a zuciyan ta tace " mata sai chanxa magana, Allah dai ya ganar daku" d'akinsu ta koma tacigaba da abinda takeyi.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Agidan Ummu-Abdulnasir kam Ummun tayi farin cikin ganinsu sosai kayan motsa baki babu irin wanda bata kawo masu ba, sai hira sukeyi yayinda Fatty ke palo wajen Humaira itama yarinyan Ummunce , hiran school suketayi chan phone d'in Fatty yafara ringing sai da taja tsaki sanan ta dauka </p><p><br /></p><p>"Hafiz wai meye ne?" Daka chan bangaran yace "kefa bakida mutinci, ya maganinmu ne? "</p><p><br /></p><p>"Kabari nadawo sai kazo" bata bari yakara magana ta katse wayan tana kuma jan tsaki</p><p><br /></p><p>Humairah ce tayi magana </p><p>"Gskiya kin rai na gayanan da yawa" ta karasa maganan tana dariya</p><p><br /></p><p>"Kee brother nane fa"</p><p><br /></p><p>"Au amma k'aninki ko? "</p><p><br /></p><p>"Noo yayana, dakashi sai ni"</p><p><br /></p><p>Sai da tad'an ware eyes d'inta sanan tace "lallai yarinya, wayaganni inama bro magana haka, ai sai Ummie tacimin k'aniya"</p><p><br /></p><p>"Waye kuma bro" Fatty ta tanbaya </p><p><br /></p><p>"Yaya Abdul-naseer mana"</p><p><br /></p><p>"Bayana school ba"</p><p><br /></p><p>"Noo, yanan sai December zai koma, kuma 6 months kawai zaiyi yadawo yagama"</p><p><br /></p><p>"Ohhh ai ni ban taba ganinshi ba ma, nashama bayan ne"</p><p><br /></p><p>"Noo, muje garden naduba maybe yanan, sai kiganshi, zakiga ba wasa" dariya Fatty tayi suka fitah</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Nan sukayi garden ikon Allah kuwa yanan, tinda Fatty taga yanayinshi ta d'an saita tafiyan ta da d'an mayafi ta ( ni biebie nach Hmmmm) </p><p> Sallama sukayi gami da zaunawa a kujerun da ke wajen </p><p> Amsawa yayi cikin voice d'insa mai dad'in sauraro</p><p><br /></p><p>"Yaa ga Fatima daughter'n Aunty Bilkisu tazo gaisheka"</p><p> Sai da ya harari Humaira ta gefen ido, sanan ya kalle Fatty'n</p><p><br /></p><p>"Ina wuni, yakake? "Tayi maganan cikin muryan iyayi</p><p><br /></p><p>"Lafiya, ya school? "</p><p><br /></p><p>"School fine, mumata jiran admission ne"</p><p><br /></p><p>"Best of luck " </p><p><br /></p><p>Tinda kanan bai sake cewa komai ba, phone d'inshi kawai yake dannawa Hajia Fatty kam sai labari takebama Humairah da muryan iyayi da yagaji dajin maganan nata barin wajen yayi a ranshi yace "dis girl rawan kai"🤣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sai , wajen 6 su Mommy sukafara haraman barin gidan, inada Ummu ta had'ama Fatyy kayan kwalliya masu yawan gaske, godia sosai mommy da Fatyy sukayi, rakosu tayi har bakin mota</p><p><br /></p><p>"Toh hajia nagode sosai, insha Allah inanan zuwa"</p><p><br /></p><p>"Ahh babu komai, Allah kawoki lfya"</p><p><br /></p><p> </p><p>Kallan Mommy faty tayi sanan tace " wai sai muje gidan antyMaijiddah? "</p><p><br /></p><p>"Nan ma zamu"</p><p><br /></p><p>Kafin 6:20 sun isah gidan Aunty Maijiddan Fatyy sai kunbure-kunbure takeyi</p><p><br /></p><p>Bayan sun gaisa kayan motsa baki Aunty Maijidda tasa aka kawo masu, juice kadai mommy tasha Fatty kam tin gaisuwa bata k'ara cewa komai ba saima danna waya da taitayi</p><p><br /></p><p>"Kai gskia kayan suyi kyau"cewar Mommy</p><p><br /></p><p>Murmushi Aunty Maijiddah tayi sanan tace " banga wayanda kika zaba ba ai"</p><p><br /></p><p>"Gasunan laces d'inan yan 70k guda biyu, sai mayafi danakeso naji kinchai sai nan da 3days zasuzo"</p><p><br /></p><p>"Okay toh kinkoyi zaben masu kyau, ita Fatima batasan ko jallabiya ne?, akawaisu masu kyau da su side bags na y'an mata"</p><p><br /></p><p>Kallanta Mommy tayi sanan tace" kinaji bakiso ne? "</p><p><br /></p><p>"Noooo barshi kawai Mommy"</p><p><br /></p><p>"Ke kika sani bakisan abin arziki ba ke"</p><p><br /></p><p>Kallansu anty Maidddah tayi sanan tace" ai sai a daukan ma Afrah da Afifah tinda ita bataso"</p><p><br /></p><p>"Okay yanxo dai zantafi dawayanan, zan aiko nan da 3days a amsamin mayafin da sauran kayan, lissafi kuwa sai muyi waya kawai"</p><p><br /></p><p>"Toh yayi sai kin aiko d'in, amma Afrahce zatazo ko? d'an ta dauki irin wanda takeso"</p><p><br /></p><p>"Toh, saidai munyi waya"</p><p><br /></p><p>Nan sukayi sallama da Aunty maijiddah sukayi gida. </p><p><br /></p><p>Sun isa ana k'iran sallan magrab, bedroom suka wuce direct bayan suyi sallah ne Fatyy ta kalle Mommy sanan tace" ita anty Maididda nan yau tabani haushe, daka kince na dauka abu d'an nace banso shine hada k'iran sunan Afrah, sai kace Afran yarinyar kice, toh ma ina ruwanta"</p><p><br /></p><p>"Ni dallah jeki kiramin Afrah"</p><p> Fita tayi tana turo baki, d'akinsu tayi kan bed taga Afrah da littafi hannunta</p><p><br /></p><p>"Kekam baki gajiya da kallan littafi, sai kinmakace wlhy, kije mommy nak'ira"</p><p><br /></p><p>Murmushi Afrah tayi kawai ta tafi k'iran Mommyn</p><p><br /></p><p>"Ashe kundawo bama muji ba" Afrah tace</p><p><br /></p><p>"Ehhh, munshigo anakiran sallah shiyasa, anko gama girkin? "</p><p><br /></p><p>"Ehhh duk angama komai"</p><p><br /></p><p>"Okay shikenan"</p><p><br /></p><p> D'akinsu takoma still Fatty nan, book d'inta ta dauka d'an cigaba da karatunta</p><p><br /></p><p>"Please kibar karatunan nabaki wani labari, kekuma Afifah kifita"</p><p><br /></p><p>"Tap wallah babu inda zani, ai anan kikazo kikasameni"Afifah tace</p><p><br /></p><p>"Sai na mareki stupid girl"</p><p> </p><p>"Am not stupid, sai dai kifasa bada labarin mu bai damemu ba"</p><p><br /></p><p>"Ke Baby bakiji ko? "Afrah tacema Afifah</p><p><br /></p><p>Barin d'akin Afifah tayi tana hararan Faty, tsaki Fatty tayi sanan tace" yaushe ma Daddy zai dawo? "</p><p><br /></p><p>"Friday ne insha Allah"</p><p><br /></p><p>"Ohh gara yadawo acigaba da maganan sch d'anni bazanje wani poly ba, labari kam kibari anjima wanan mara kunyan tabatamin rai"ta karasa magana tana barin d'akin</p><p><br /></p><p> Da ido Afrah tabita gami dacewa "ke kika sa kankin ai bawani ba, school kam kitafi London ni inan a KASU"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>Yau Daddy yadawo bayan yayi Sallah yakuma ci abinci,duk zaune suke a palo gyran murya yayi sanan yace"ku yaushe ne za'afara screening d'in ne? </p><p><br /></p><p>"Daddy Afrah zaka tanbaya d'an itace zatayi, ni banci jamb bah bandani"</p><p><br /></p><p>"Okey tin dahakane kema mamana harkiyi screening d'in, private university zannema maku konan Al-hikma ne, Amma ke Fatima ba degree xasu baki ba, kinsandai komai basai namaki bayani ba, inkuka kikaje kika tsaya wasa koranki zasuyi inkuma kinsamu yanda sukeso subaki 200lvl gara ki natsu"</p><p><br /></p><p>"Toh Daddy ta amsa kaman zatayi kuka, barin palon tayi mommy kam shuru tayi a ranta race "abinda bazai taba yuwuba kenan wallahi"</p><p><br /></p><p> Itama Afrah barin palon tayin d'an gaba d'aya bataji dad'in maganan da Daddy yayi kan sch d'insu ba ita tafisan KASU bawani Al-hikma ba nisan duniya</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hakadai kowa ya kwana da tunani </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Afrah ta yanke wukuncin samun Daddy tace tafisan KASU kawai, Fatyy kam tace dataje school d'aya da Afrah gara ta fasa gaba d'aya... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_TOH FAH READERS KUNAJI, MAI KUKE GANIN YAKAMATA DUK SUYI???_</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PAGE 25-26_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>""""""""""Koda Afrah ta tashi sallan subh Addu'a taitayi Allah sa Daddy ya yadda da nata choice d'in bayan ta idar k'atun Qur'ani tayi sai da gari yafara haske sanan tayi kitchen, nan taga Salamatu na goge-goge bayan sun gaisa ne Afrah tafara abinda yakawota, arish n source with egg tayi sai pepper soup na kayan ciki sai kuma ruwan tea dayaji kayan kamshi nan duk sukajere su a dinning ita da Salamatu, dakanta taje takai ma Baba Haruna(mai gadinsu) nashi, bayan sun gama duk abinda zasuyi d'akinsu ta koma dan yin wanka yayinda itama Salamatu ta dauki nata abincin tayi nata d'akin. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda takoma d'in Afifih bata tashi bacci ba, wanka tayi tashiya cikin gown na material red n black sai veil red da ta daura kanta, powder kawai ta shafa buh still she look cute😇 tashin Afifah tashiga tashi " baby tashi, Afifatuh kitashi"</p><p><br /></p><p>Mik'a Afifah tayi gami dacewa aunty baccin yau d'adi wallahi"</p><p><br /></p><p>"Ni kimin shuru babu salati bale addu'an tashi daka bacci zaki faramin surutunki, haka da subh nace kitsaya muyi karatu kikak'i"</p><p><br /></p><p>K'ara kwanciya Afifah tayi,salati tayi gami da Addu'a sanan ta tashi " sorry sweetheart gobe insha Allah zanyi bazan koma baccin ba"</p><p><br /></p><p>"Good girl that's why i love you Always"</p><p><br /></p><p>"I you more sislove, dama haka anty Fatyy take da yaa Hafiz, da duk sunji dad'i Wallahi kinfiso kirki"</p><p> </p><p><br /></p><p>Smiling Afrah tayi sanan tace"naji toh jekiyi wanka" bata wani jima sosai ba tafitoh shiryawa tayi cikin gown itama amma nata pink color sai wula da tasa a kanta palo duk sukayi kasan cewan indai Daddy na gari a duk tare suke cin Abinci</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dinning area sukaga Mommy sai bud'e bud'e takeyi k'arasa wasu sukayi </p><p> Afrah ce tafara gaisheta sanan Afifih Mommy ta amsa cikin fara'a(Mommy haka take wata rana taita fara'a wataran kuwa ta had'e fuska kaman dare batare da anmata komai bah) </p><p><br /></p><p>"Ahh Afrah nasha ma kunun gyada zaki mana"</p><p><br /></p><p>Smiling Afrah tayi sanan tace"ban san shikike san sha ba ai da anyi, kuma dan baki fada da dare bane"</p><p><br /></p><p>"Ehh kinsan jiya duk da wuri mukai bacci shiyasa"</p><p><br /></p><p>"Nifa yunwa nakeji" cewar Afifah</p><p><br /></p><p>"Afrah jeki kira Hafiz, nakira phone dinsa kashe"</p><p><br /></p><p>"Toh"ta amsa</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sallahma tayi a bak'in k'ofar batare da ya Amma ba yace "waye wai? "</p><p> </p><p>Voice d'inta na rawa tace "Mommy tace kazo" juyawa tayi da sauri d'an batasan masifan Hafiz, d'anshi abu baikai abu ba masifa ne, kafin takai polon har ya kamota kallanta yayi gami da jan tsaki sanan yace" kinwani ci kaya red n black kamar yar mafiya" banza dashi tayi d'an ita Hafiz yafi k'arfinta Fatyyce dai dai da shii. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nan suka fara breakfast dukkansu Daddy ne yafara gamawa, kallan Fatyy yayi sanan yace" wanne kika dafa acin abincin? "</p><p><br /></p><p>"Ahhh ni Daddy banyi kokai ba duk Afrah tayisu"ta k'arasa maganan tasa arish a baki</p><p> </p><p>"Ahhh Ahhh Mamana kodai gidan girki zan bude ma kine? "</p><p><br /></p><p>Smiling Afrah tayi sanan tace" Daddy ai bangama iyawa ba"</p><p><br /></p><p>"Wayace? Dan kinfi wanan yanuna Fatyy, baka taba ganin tana aiki kowani abu sai d'anna waya"</p><p><br /></p><p>"Ehh wallahi Daddy ai karkakuma chanza mata phone ne"Afifah tace</p><p><br /></p><p>Harara Fatyy ta watsa mata itama Afifan Hararanta tayi amma bata bari Daddy yagani ba</p><p><br /></p><p>Dariya Daddy yayi gami dacewa" kinganki nan, ke kin iya girkin? "</p><p><br /></p><p>"Ehh mana tanbaya Mommy ko anty Afrah"</p><p><br /></p><p>"Toh masha Allah, kema Fatima sai ki daure ki koya in Mamana nayi kirika kallo"</p><p><br /></p><p>Wani haushi yakama Fatty da Mommy kai kaawai ta d'aka batare da ta amsa bah</p><p><br /></p><p>"Mommy kina jina da yaranki kinyi shuru" Daddy yacema Mommy </p><p><br /></p><p>"Hmmmm mai zance? Ai kunfi kusa" tashi tayi tabar wajen, nan Hafiz yafara k'oran tashi shima Daddy ne ya tsaidashi " kai ya maganin karatu? Kanema sch d'in? "</p><p><br /></p><p>"Ehhhh, wani ne a turkey"</p><p><br /></p><p>"Okay shine sai da na tanbaya sabida nixanyi karatun ko? "</p><p><br /></p><p>Kai Hafiz ya sosa gami dacewa "aa dama dama."</p><p><br /></p><p> "Dama mai? kaci sa'a me inna da Sulaiman sunsa baki game da karatunka da saide nasama ido kokuma kayi anan"</p><p><br /></p><p>"Ya hakuri Daddy"</p><p><br /></p><p>" dole ai nayi hakurin, duk yanda akeciki kasanar dani"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah saka da Alkhari". </p><p><br /></p><p>"Ameen duk suka amsa</p><p><br /></p><p>Nan Fatyy tashiga kwashe kayan kan dinning din ( niko biebie nace su fatty anji gori👅)</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Daddy nanan zaune har Faty tagama kwashe kayan, waya aketayi da abokan kasuwancin sa, bayan yagama kallan cikin palon yayi baiga kowa ba sai Afrah tashi yayi daka dinning area d'in yanufi cikin palon, zama yayi nesa k'adan da ita, sai da ya kalleta da kyau sanan yace" Mamana"</p><p><br /></p><p>"Na'am Daddy"ta amsa</p><p><br /></p><p>"Fad'amin damuwanki, anamaki wani abune da bakiso a gidan? "</p><p>. </p><p><br /></p><p>Girgiza kai tayi alamun a'a</p><p><br /></p><p>"Toh Fad'amin menene matsalan?"</p><p><br /></p><p>Sai da tayi k'asa da kanta sanan tace" dama k'an maganan school d'in da kayi manane jiya" sai kuma tayi shuru</p><p><br /></p><p>"Ikon Allah Mamana hala dai banine babanki ba shiyasa kikemin haka ko?"</p><p><br /></p><p>"A'a Daddy"</p><p><br /></p><p>"Maxa gayamin"</p><p><br /></p><p>"Daddy dama school d'inne yayi nisa, ni hanka- lina bai kwanta ba, koma ba waje d'aya xamu zauna da Fatyy ba tinda ita ba degree zatafara ba"</p><p><br /></p><p>"Duk na gane, yanzo wanne kikeso? "</p><p><br /></p><p>"Ni nafisan nan garin KASU koma POLY nasamu duk inaso Daddy"</p><p><br /></p><p>"Shikenan matsalan" </p><p><br /></p><p>"Ehh shikenan Daddy"</p><p><br /></p><p>"Toh shikenan Mamana angama" ya karasa maganan yana daria</p><p><br /></p><p>"Yauwa Daddy Allah saka da Alkhari, yakara budi da wadata yasa afi haka"</p><p><br /></p><p>"Ameen Ameen Mamana, makarantar girkinfa kina so? "</p><p><br /></p><p>"Ehh inaso Daddy"</p><p><br /></p><p>"Da kyau Mamana, sai kinemo wanda kikeso, duk yanda akeciki kisanar da ni zanyi magana da Mommynku ma kan makarantar Fatiman"</p><p><br /></p><p>"Toh Daddy"</p><p><br /></p><p>"Bari nashiga daka ciki"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana ganin Daddy zai bar palon tayi side Mommy da gudu, Fattyce wanke ke lab'e tinda su Afran na magana</p><p> Da k'arfi tabugo k'ofar d'akin Mommyn kawai tasa babu ko sallama</p><p><br /></p><p>"Kee bakida hankaline kinturomin k'ofa da k'arfi"</p><p><br /></p><p>Fuska Fatyy tabat'a sanan tace" matsalanki kenan Mommy masifa, inda kinsan news d'in da nazo maki da shi bazaki ce haka ba"</p><p><br /></p><p>"News d'in uban mee"</p><p><br /></p><p>"Please Mommy kitsaya kiji, Daddy nagani da Afrah a n palo suna magana"</p><p><br /></p><p>"Maganar uban mai? " tayi ma Faty tanbaya tana gyara zama</p><p><br /></p><p>"Toh kinata masifa inafa zakiji kan maganan"</p><p><br /></p><p>"Ke d'an ubanki fad'amin inaji"</p><p><br /></p><p>Nan Fatty tashiga zubo ma Mommy zance hadda k'arya a ciki, sai da mommy tagama ji tass sanan tace" tama kanta adalci"</p><p><br /></p><p>"Kaman ya Mommy"</p><p><br /></p><p>"Keda kina tunanin zan ba rta taje private university ne tana degree ke kina wani abun chan daban wanda ba degree ba? Taiki kenan, sai kace bana raye, ta kyauta ma kanta da tayi wanan tunan, makarantar girki kuwa taje taitayi duk wahala ne kee baza kiyi irin karatunan ba"</p><p><br /></p><p>"Auuuu hakane ashe, ai tama kanta adalci kuwa, yanxo Mommy ki cema daddy sai next year zan fara school kafin time d'in nasake duba wani school d'in dan Al-hikkimanan bai min ba"</p><p><br /></p><p>"Kar ki damu ko nan Abuja ne sai kije akwai private university masu kyau dai dai ke, buna na dai kiyi passing jamb"</p><p><br /></p><p>"Insha Allah akwai inda ake biya ma akecin jamb Lailah friend d'ina kefadamin"</p><p><br /></p><p>"Ai shinenan sai kisake kawai, ita kam chan ta k'arata a KASU"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Koda Daddy kemata zancen sch d'in Mommy cewa tayi Afran tafara kawai Fatyy zatasake jamb next year tafara nata. </p><p><br /></p><p>AFRAH tayi duk abubuwan da yadace tayi na school daka university d'in har polyn, dan Saura 2weeks afara screening Hafiz ma sai shirye shiryen tafiya yakeyi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p>Zaune suke ita da Afifah, karatu take koyama Afifahn Fatyyce tashigo d'akin babu ko sallama phone d'inta tamik'amata "gashi yaa Sulaiman zai kiraki inkingama Afifah takawo min d'akin Mommy" batajira amsa ba tayi gaba</p><p><br /></p><p>"Wanan anty Fatty masifa"Afifah tace</p><p><br /></p><p>"Kimin shuru"</p><p><br /></p><p>"Wai maye ne kindawo kinamin kunbura anan" Mommy tacema Fatty </p><p><br /></p><p>"Ba yaa Sulaiman bane yakirani wai na kai ma Afrah phone d'an"</p><p><br /></p><p>"Kan wani dalilin? "</p><p><br /></p><p>"Oho mai, su suka sani"</p><p><br /></p><p>"Tapdijam bazai taba faruwa ba wallahi, ina bazan taba yadda ba sam"</p><p><br /></p><p>"Wai menene Mommy "</p><p><br /></p><p>"Dallah fita kibarni na san abinyi tukunna"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*muje zuwa*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Gaisuwa mai yawa gadukkan masoyina koma masu bin labarina BIEBIE DEE na k'aunarku har cikin ranta, ALLAH BARMU TARE_❤❤💞❣💞💕💖💘</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>~Biebie dee~🌸🌸</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 27-28_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"""""""""""""B'angaran Afrah kam waya sosai sukayi da yaa Sulaiman d'an har mantawa tayi da phone d'in banata bane, ganin Fatyy a gabanta ne yasa ta tuna(lol) </p><p><br /></p><p>"Okay bruh za muyi magana anjima" sallama sukayi tamik'ama Fatty wayanta, amsa tayi gami da jan wani dogon tsaki, banza da ita Afrah tayi d'an tariga ta saba da halin Fatyy'n</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mommy kam kaiwa dakomo wa tai tayi a cikin bedroom tama rasa abinyi, zama tayi bakin gado tana cewa " wallahi Sai nayi maganin Sulaiman, yaro tin yana k'arami ya mak'ale ma Rabi, yanzo yakoma jininta, toh wallahi bazan yadda ba, bakar aniyar ta tabita d'an duk yarana sunfi k'arfinta"haka dai tai ta surotainta mara kan gado da lissafi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gaba d'ayan ranan Mommy sai cika take tana batsewa, ita dai Afrah Aikin gabanta kawai takeyi d'an tariga ta saba da halinsu, duk yanda sukazo ta nan take bidasu. </p><p><br /></p><p>_2 WEEKS LATER_</p><p><br /></p><p>Anata screening, Afrah nasa ran admission d'an Daddy nada hanya bata da problem, Hafiz ma nata shirin tafiya nashi sch d'in dan duk wani abu da yakamata anyi, Fatty kam bata sa komai a gaba ba, sai yawo duk wani joint dake garin kaduna tasan dashi, gayu kawai tasa a gaba babu aikin fari bare na bak'i yawo kawai sai siyan kaya a online. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gaba d'aya yanzo bata cika zama a gida ba, sabida zirga-zirgan school,tashigo gida a gajiye, side Mommy tayi direct bayan ta gaisheta bedroom d'insu tayi, tsaki tayi gami da cewa" Fatty da tashigo waje sai ta birkitashi hankalinta ke kwanciya" kawar da kayan duk tayi saban ta shiga toilet, wanka tayi gami da Alwala, gown tasaka sanan tayi sallan la'asar d'in kwanciya tayi tana duba wani girki a online, tanan kwance har Afifah ta dawo daka islamiya, da sallama ta shigo d'akin gami da gaida Afran</p><p>"Aunty Mommy tace wai bake zaki mana dinner ba yau"</p><p><br /></p><p>"Yes sweetheart, kai na yana ciwo kad'an"</p><p><br /></p><p>"Sorry Allah sawake, bari naje wajen yaa Abdul yakoyamin wani assignment tinda kanki na ciwo yau"</p><p><br /></p><p>"Yaa Abdul ya dawo ne? "</p><p><br /></p><p>"Ehhh, nima na dawo school na ganshi, maybe daddy zai gani, yace gobe zai koma wai"</p><p><br /></p><p>"Lallai ma, shine ko yagayamin kuma muyi waya da safe"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> "Shine ko kafadamin zakazo" Afrah tace ma Abdul </p><p>" ni bansan zanzo bah"</p><p><br /></p><p>"Kai dai kawai yaya Magana na baka wahala, da yaa Sulaiman ne ai wlhy bazaiyi haka ba"</p><p><br /></p><p>Daria Abdul yayi sanan yace" ai dole kice haka yarinya"</p><p><br /></p><p>"Hmmmm naji, ya karatu, ya school? "</p><p><br /></p><p>"Alhmdulillahi, muna fafatawa, ya naki"? </p><p><br /></p><p>"Tap ai tinkafin mufara ma wahala mukesha, gashi inaso naje katsina Inna tasa min Albarka"</p><p><br /></p><p>"Ah lallai yarinya sai kibi Daddy zai dawo yau da dare, gobe insha Allah kuma katsina zaije daka can zai wuce Abuja"</p><p><br /></p><p>"Na bishi wazai dawo dani? "</p><p><br /></p><p>" see you bai da drives ne, kawai ki bishi ko Bala ma ai zai iya dawo dake"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah dawo dashi lafya"</p><p><br /></p><p>"Ameen" duk sukace</p><p>. </p><p>"Ni gaskiya a jidani" Afifah tace</p><p><br /></p><p>"Lil-lil wats your problem? "Andul ya tanbaye tah</p><p><br /></p><p>Sai da ta d'an bata rai sanan tace" bayan nazo ka koyamin assignment sai magana kuke tayi kun share ni, kuka ni kubar cemin lil-lil"</p><p><br /></p><p>"Ahh haba sorry babban k'awa"yaa Abdul yace</p><p><br /></p><p>"Toh naji yaushe za a koyamin? "</p><p><br /></p><p>Kallan agogonshi yayi sanan yace " kinga saura mintoci k'adan ayi magrib, in nadawo daka masjid kema kinyi sallah sai kixo muyi ko? "</p><p><br /></p><p>"Toh Allah kaimu" </p><p><br /></p><p>Fatty ce tashigo su biyu da k'awarta Asiya, anci sa'a tayi sallama, amsawa duk sukayi, ko kanlansu barayi tashige ciki sai Asiya tace tasu "ya kuke? "Suka amsa da lafya lau"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Babe waye wanan handsome d'in? Wai ku bakuda munana a gidan ne" Asiya ta tanbaya</p><p><br /></p><p>"Kee ina kikaga handsome d'in? </p><p><br /></p><p>"Wanda na gansu tare da Afifah da Afrah"</p><p><br /></p><p>Mtswww taja tsaki" brother d'in Afran ne n don't ask me anything"</p><p><br /></p><p>"Matsala dake kenan rashin mutunci"</p><p><br /></p><p>"Ke kika sani, </p><p><br /></p><p>"Ni dallah Suraj d'in zaizo picking dinki ko nama driver magana ya maidaki? "</p><p><br /></p><p>"Yana hanya"Asiya tace</p><p><br /></p><p>Sai bayan magrib sanan akazo daukan Asiyan, A palo taga Mommy </p><p><br /></p><p>"Ina wuni Mommy"</p><p><br /></p><p>"Lafiya lau, ya mamanku"ta amsa cikin sakin fuska</p><p><br /></p><p>"Lfyalau mommy, sai da safe"</p><p><br /></p><p>"Ahh harkinfitoh? Allah bamu alheri"</p><p><br /></p><p>Ko datazo fita ma taga su Afrah, sai da safe ta masu sanan ta wuce, tsaki Fatty tayi game dace wa"babe ni zan koma, sai munyi chatting"</p><p><br /></p><p>"Okay bye"</p><p><br /></p><p>Palo ta dawo ta zube kusa da Mommy </p><p>"Wallahi nagaji"</p><p><br /></p><p>"Da kikayi uban me?" Mommy tace</p><p><br /></p><p>"Matsala dake kenan, Mommy kin ga mutananki a wajen gida hadda Afifah? "</p><p><br /></p><p>"Bar sakarkarun, wahalanlu,marasa anfani"</p><p><br /></p><p>"Wai mema Abdul yadawo yine"</p><p><br /></p><p>"Waya sani ma munafikin, ganinshi kawai nayi"</p><p><br /></p><p>"Aifa, toh ita uwar girkinan bata samu sch d'in abincin bane? ". </p><p><br /></p><p>"Ina nasani ma yar wahalan"</p><p>Haka dai sukata hiransu, a zaki wanan a tsine ma wanchan</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Daddy bai samu dawowa ba sai washe garin ranan, girki kala-kala Afrah tayi mai Afifah da salamatu suka tayata, ko da yadawo Albarka yaita sa ma Afran d'an yaji dad'i sosai</p><p><br /></p><p>Duk zaune suke a babban Palo dawo wanshi daka masjid sallahn isha babu dadewa, Afrah ce ta kalle Daddyn sanan tace"Daddy xan bika Katsina gobe insha Allah sai Bala yadawo dani jibi"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah kaimu goben lafiya"</p><p><br /></p><p>"Nima zanje Daddy" Afifah tace</p><p><br /></p><p>"Babu inda zakije cewar mommy, wani tafiya ni da nake zaune daku bansani ba sai yanzo? Ita dai Afran da banda iko da ita sai taje, ke kam Afifah babu inda zakije"</p><p><br /></p><p>Banza da ita Daddy yayi bayasan hayaniya, haushi sosai Mommy taji d'an taso ya tanka ko sata samu k'arasa fad'an abunda ke ranta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shiryawa sukayi tsaf sanan suka shiga side d'in Mommyn, banyan sun gaisheta, ta amsa a banxache</p><p>"Mommy sai mundawo insha Allah gobe zamu dawo"</p><p><br /></p><p>"Hmmmmmm, ina Daddyn naku? </p><p><br /></p><p>"Yana palo", Afifah tace</p><p> Hakanan tabiyo su har palon amma a ranta Allah ne kadai yasan irn haushin da Afrah take bata. </p><p><br /></p><p>"Har kunfitoh?"</p><p><br /></p><p>"Da yaddan Allah"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah tsare, Allah bada sa'a"</p><p><br /></p><p>"Ameen Ameen, acigaba damana addu'a akwai wani business ta muke san farawa in komai ya kankama zanyi maki bayani, insha Akwai ciga ba"</p><p><br /></p><p>Baki Mommy ta washe gami dace wa"toh Allah tabbatar mana da Alkhari"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen"</p><p><br /></p><p>Har gaban Mota ta rakosu tana k'ara masu addu'a</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sun isah katsina lfya, Inna taji dad'in ganinsu sosai, kaya iri irin Daddy yakawo mata Inna sai Albarka takesa mai, nan yake fada mata game da business d'in dakesan yafara, Albarka sosai tasa mai gami da fatan Alheri, sai da duk ya lak'a dangi gami da masu alheri kaman yanda yasa ba sanan yamasu sallama yawuce Abuja, su Afrah kam Haruna ne zai dawo dasu(yaron Daddy ne) </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p>Tinda su Daddy suka tafi Mommy ke masifa na babu gari babu dalili kowa haushi yake bata Allah kasai yasan irin tsar da tama Afrah d'an aganinta tafi zak'ewa bata kawai Abdul bah</p><p><br /></p><p>"Fatty mekike ganin zanyi ne? Gaba daya labarin Afrah hauhawa yakeyi, idanuwanta k'ara budewa sukeyi" Mommy ta tanbaya Fatty </p><p><br /></p><p>"Haka ne Mommy ni kaina yanxo Afrah bata wani cika shiga harka na ba, kawai kuyi magana da aunty Azeezah ko anty Nana"</p><p><br /></p><p>"Toh su yanxo ina fara fad'a masu zasuce bana nemansu sai ina da damuwa"</p><p><br /></p><p>"Ehhh, kije zaria ne d'an shopping kayan yara dai dai sauransu, kinsan zasu baki mafita insha Allah"</p><p><br /></p><p>"Toh hakan zanyi zan fara k'iransu a waya ma"</p><p><br /></p><p>"Toh mommy Daddy ya turo da kud'inan kuwa?"</p><p><br /></p><p>"Ehh mai yafaru? "</p><p><br /></p><p>"20k zaki bani a ciki akwai abunda zan siya"</p><p><br /></p><p>"Matsalanki kenan kedai"</p><p><br /></p><p>"Haba Mommy yanxonan fa na gama baki mafita, ko kud'in naki ne ai sai ki bani bare ma ba naki bane"</p><p><br /></p><p>"Zanci ubanki wallahi"</p><p><br /></p><p>"Hmmmm nidai kibani kawai Mommy" tak'arasa maganan tana barin dak'in. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p>Kwanansu d'aya a katsina suka dawo kasan cewar Afifah na school, Addu'a sosai Mami, Uncle junaid, Inna da sauran d'angi sukayi mata gami sa samasu Albarka kamar yanda suka sabah</p><p> Da misalin k'arfe 2 narana Haruna iso daukansu har jikin mota Inna sa Zainab jikar Inna Rakiya suka rakosu, Zainab ce tace" toh yar uwa Allah bamu sa'a yasa kuma mudace, Allah tsare duk agaida kowa"</p><p><br /></p><p>"Toh Ameen Ameen, insha Allah duk zasuji, duk wahalan da kikasha wajen registration ki labarta min a online "</p><p><br /></p><p>Dariya Zainab tayi sanan tace"karkidamu ai har da pictures ma"</p><p><br /></p><p>"Kee dallah shiga kuje kubar bawan Allah najira"Inna tace</p><p><br /></p><p>Juya idanu Afifah tayi game da cewa"ke tsohuwa me naki? Ki lallaba ki ware gida kawai sai mun hadu a waya"</p><p><br /></p><p>"Kinganki kifita idona fa"</p><p><br /></p><p>"Ni dama wallahi banshi gaba, indai kinaso nashiga bari nazo"</p><p><br /></p><p>" na tsaya biye maki kwana zamuyi a wajenan, kule Allah tsare"</p><p><br /></p><p>Haka suka shige mota suna ta dagama juna hannu..</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> *gaisuwa ga dukkan masoya nah masu bibiyan labari na,nagode sosai Biebie dee na k'aunarku har cikin ranta a duk inda kuke a fad'in dunia*❤❤❤❤❤</p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 29-30_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"""""" *S*un isah kaduna lafiya, wajen Mommy suka fara shiga kafin sukawoce d'akinsu, sama sama ta amsa gaisuwan d'an Allah ne kadai yasan irin tsanar da tama Afrah</p><p><br /></p><p> Suko Afrah suna shiga bedroom d'innasu wanka sukayi gami da Alwala, salla sukayi sanan suka ci abinci, wajen k'arfe 9:30 Innah ta kira taji ya suka iso, hira suka d'an yi sanan sukayi sallama, ta aje phone d'in babu dad'ewa Mami ma takira itama dai taji yasuka saukane sanan sukayi sallama, whatsapp ta shiga tafada ma yaa Sulaiman ma sundawo, batawani dade online d'in ba ta sauka, alwala tasakeyi sai addu'an bacci ta kwanta Afifah kam tinda taci abinci rayi baccinta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> "Haba Mommy naga dai kud'inan bafa kece kike nemowa ba, da anyi magana kice kina manege duk kudaden da Daddy ke baki ina kike kaisu? " Fatyy tace ma Mommy </p><p><br /></p><p>"Kinsan Allah zanci ubanki"</p><p><br /></p><p>"Kedai yau Mommy kin hau litter🚮 zaki sauke a kai na, Afara ke baki haushe, kijey ki cimata qaniya bani bah"</p><p><br /></p><p>"Fitamin a d'aki dan ubanki"</p><p><br /></p><p>"Wallah mommy Daddy yace kibani 5k kud'in subscription"</p><p><br /></p><p>"20k d'in ranan fa? "</p><p><br /></p><p>"Babu ruwanki kawai nidai yace kibani, ai muyi waya dashi"</p><p><br /></p><p>"Kude kenan keda Hafiz sani magana ko? Duk k'okarin da nakeyi kanku baku gani ko? "</p><p><br /></p><p>"Toh ai kece Mommy komai masifa, inbanda haka wazaiji kanmu nida mommy nah"ta k'arasa mafanan tana daria</p><p><br /></p><p>"Hmmmm jeki sai da safe"</p><p><br /></p><p>"Zaki bani kud'in? "</p><p><br /></p><p>"amma nace kije ko"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah bamu Alheri"</p><p><br /></p><p>Da ido Mommy tabita. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Koda tashi d'insu, taga duk suyi bacci tsaki tayi sanan ta aje phone dinta toilet ta shiga tayi wanka da alwala, sai datasa kayan bacci sanan tashiga yin sallan isha, nan da nan ta idar, yadda hijab d'in tayi anan tahaye gadonta, phone dinta ta dauka 11:45 tagani, Data tabude tashiga Snapchat, tana kallo tana daria hayani yarta ya farkar da Afrah kasancewar batada hauyin bacci, juwowa tayi sukayi ido hud'i da Fatty, tsaki Fatty tayi tacigaba da abinda takeyi, haka tai kalle kallenta a Instagram, Snapchat da status d'in mutane ko ta rage k'aran, juyawa Afrah tayi kawai badan tana bacci ba d'an Fatty tadameta amma babu yanda zatayi, haka taita kalle-kallen ta sai kusan 2 na dare ta gama, chaji tajona phone d'in sanan ta kwanta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Duk da rashin baccin da batayi sosai ba, hakan bai hanata tashi sallahn subh bah, Sai da tayi Alwala sanan tashiga tashin Fatty, Amma inna mutumiyar taku batasan anayi ba, gajiya da tashin ta tayi ta barta, wajen Afifah ta nufa, bata dade sosai tana tashinta ba ta tashi gami da Addu'a kaman yanda Afran ta cemata, sai dataga tayi hanyan toilet ta tayar da sallanta, har duk suka idar Farty ko motsawa batayi ba, har suka gama Azkar na safe Fatty bata tashi ba, wajenta Afrah takoma tana tashinta amma dai still, toilet Afifah tashiga, ruwa tadebo bata bari Afrah tagani ba tace</p><p>"Ai aunty ki barta kawai, kisan halin masifan ta, ba'ayi mata abin arziki"</p><p><br /></p><p>"Wai ke baki da kunyan ko baby, sunawa kikeso namaki magana? "</p><p><br /></p><p>"Allah baki hakuri, kawai kije kiyi abinda zakiyi ni banasan afara ihune tinkan gari yayi haske sosai"</p><p><br /></p><p>"Lallai ma yarinya, keda zaki sch kina cewa naje nayi abunda zanyi? Kece mai abinyi ai"</p><p><br /></p><p>"Hahahaha, ai kema dai zaki anty, ni yanzo banda case sch kinsan nakusa graduating "</p><p><br /></p><p>"Ita ina"</p><p><br /></p><p>"Wallah kuwa, kin manta primary5 going ss1 kuma am 9</p><p><br /></p><p>"Ohhhhhh hakane pa, baby ankusa zama big girls "</p><p><br /></p><p>"Hahaha Aunty kenan, kije bari natasheta"</p><p><br /></p><p>"Okay vari naje kitchen, kishiga wanka inkintasheta"</p><p><br /></p><p>"Tohhh" Afifah tace </p><p> Sai data k'ara kulu k'ofar dakin gam sanan tadawo cup d'in da ta debo ruwa ta jawa, gadon Fatty tanufa, sai da ta k'arema Fatty kallo tas gami da kecewa da dariyan muguta"ba dai chatting ba, yanzo zan maki aiki nima chatting ce"daria takuma yii sanan ta antayama fatty ruwan a face d'inta</p><p> </p><p> Azabure ta tashi tana xare eyes, Afifah tagani agabanta tana daria, goge fuskan ta tayi sanan tayunkura zata tashi a 360 Afifah tashige toilet gami da murja key</p><p><br /></p><p>"Dan ubanki, uban wa yasaki zubamin ruwa? "</p><p><br /></p><p>Daka cikin toilet Afifah tace"ubanmu sabo da kinqi tashi kiyi ibada, har ni k'anuwar bayanki nayi keko kina bacin asara"</p><p><br /></p><p>"Wallahi zaki fitoh zakiga abinda zanmaki, wawiya kawai stupid "</p><p><br /></p><p>"Naji dai aje ayi sallah iyayen chatting"takarasa maganan tana daria</p><p><br /></p><p>"Zaki fitoh ai"</p><p><br /></p><p>"Ohoo dai, aje sallah mama guntu"</p><p><br /></p><p>Fita a d'akin tayi d'an takasa magana, ita kadai tasan abinda zatama Afifah yau, D'akin Mommy tashiga ko sallama, toilet tanufa direct ta dauro alwala, tana fitowa ta tayar da sallah, babu dadewa ta idar(yar baki bayawa sai lada😂😂) hayewa bed d'in mommy tayi ta kwanta amma sai buga tsaki takeyi</p><p><br /></p><p>"Wai wanan wani iskanci ne kinshigo min waje sai tsaki kikeyi, bansan iskanci fa"mommy tace</p><p><br /></p><p>"Wanan wawiyar yarinyance, nan Fatty tabama Mommy labari</p><p><br /></p><p>"Karki sake kiduketa wallah, inba haka ba sai naci maki mutunci, ai maganinki kenan ba dai wayn dare ba"</p><p><br /></p><p>"Allah sai na duketa"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sai ki duketan nagani, shegiya mai b'akin ran tsiya"</p><p><br /></p><p>Magana qasaqasa Fatty takeyi wanda nakasan jin ko mai takecewa</p><p><br /></p><p>"Fitarmin a d'aki"Mommy tace</p><p><br /></p><p>"Toh ni bacci zanyi"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A kitchen kam Afrah da Salamatu sun gama kammala komai da ya gamata tazu bama Afifah na sch dinta, d'akin Mommy naufa d'an gaidata, rashiga da Sallah Mommy ta amsa yau fuskanta sake "har kin gama kenan"?</p><p><br /></p><p>"Eh Mommy duk nagama, yau har kunnun gyada namaki"</p><p><br /></p><p>Ahhhhh kin kyauta"tayi maganan tana d'an murmushi</p><p><br /></p><p>"Bari naje nayi wanka"</p><p><br /></p><p>"Tohhh, Allah sa y'ar tsokanan tayi dai"</p><p>. </p><p>"Aikam bari na dubuta naga"</p><p> </p><p> Kan Bed ta ganta har tasa uniform, kallanta Affrah tayi sanan tace</p><p><br /></p><p>"Ya bakije kin gaida Mommy bah? "</p><p><br /></p><p>"Wallah anty Fattynan nazuba ma ruwa, dafita duka na zarayi"</p><p><br /></p><p>"Wayace ki zuba mata toh? Tashi kije ni " tashi yayi tafita, a hankali tai ta tafiya har ta iso d'akin Mommyn sallahma tayi sai da Mommy ta amsa sanan tashiga, Fatty najin Voice d'inta ta rashi, bayan Mommy Afifah taboye "wawiya uban wayace kizuba min ruwa"</p><p><br /></p><p>"Ni ba wawiya bace"</p><p><br /></p><p>"Wai ke Fatty mai nagaya mak? Zan cimaki mitunci fa" matsawa mommy tayi gami da jawo Afifan kusa da fattyn "oga gata daketa dan ubanki nabaki mamaki, kebakin san halina ba wallahi, ganina kawai kikeyi"</p><p><br /></p><p>Banza da Mommy Fatty tayi, batace k'ala ba phone d"inta ta dauka kan bed d'in Mommy rabar bedroom d'in gami da jan wani wawan taki qala Mommy batace ba sai ma kallan Afifah datayi gami dacewa" ki bar shiga harkan Fatima, kindai san hakinta"</p><p><br /></p><p>Baki Afifah ta turo sanan tace" Sallah fa na tasheta ni"</p><p><br /></p><p>"Nidai na fad'a maki"</p><p><br /></p><p>"Tohhhh, ina kwana? "</p><p><br /></p><p>"Lafiyalau autana, yakikatashi? </p><p><br /></p><p>"Qalau, gani kinganni ma"</p><p><br /></p><p>"Uwar mantace maza jeyi brkfast, bari na shiga wanka"</p><p> Tashi Afifah tayi tabar d'akin, kafin 7:30 tagama kimai, bubu b'ata lokaci tama Mommy da Afrah Sallahma tawuce.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sai datagama duk abinda ya kamata, sanye take cikin arebiyan gown black da toch d'in milk,mayafin ma black ne sai daka gefe akasa milk simple makeup ne afuskanta Amma sai tayi kyau sosai. </p><p> D'akin Mommy tashiga da Sallamanta, sai da Mommy ta amsa sanan Afrah ta shiga cikin dakin</p><p> Tunda ta shigi Mommy ke binta da ido, waje tasamu zauna sanan tace" Mommy naso na je cafe akwai abinda zanyi"</p><p><br /></p><p>"Ban gane akwai abinda zakiyi ba, kina nufin kulin sai kin fita kenan ko yaya? "</p><p><br /></p><p>"Mommy ba dad'ewa zanyi ba insha Allah "</p><p><br /></p><p>"Ahhh lallai, naga alama yanxo so kike kifi k'arfina, inbanda iskanci zama ki fita ne ban isa kifadamin tin jiya da dare ba sai da kika shirya tsaf, kanki na rawa kuwa"</p><p><br /></p><p>"Kiyi hakuri Mommy "</p><p><br /></p><p>"Duk naji, sanan ma abincin ranan uban wa zaiyi kinsan sai banasan girkin Salamatu nikuka ba dad'i nakeji ba bare nayi"</p><p><br /></p><p>"Ai insha Allahu ba dadewa zanyi ba"</p><p><br /></p><p>"Kedai kika sani, tashi ki bani waje"</p><p><br /></p><p>Tashi Afrah tayi gami da yima Mommy sallama tafita, banza da ita mommy tayi kaman bata jiiba</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Itakam Afrah d'akinsu takoma tasa takalmi da side bag d'inta tayi gaba, a zuciyan ta tana mamakin halin san kai irin na Mommy, taga dai Fattyma shiryawan ta takeyi sanan ta fitoh kuma Mommy bata isa ta hanata ba, sai ita dazatayi abu mai mahimmanci da anfani tana neman hanata Allah dai ya kyauta san kai, dawanan tunanin tabar gidan. </p><p><br /></p><p> Bakin titi tanufa kasancewar gidansu bai da nisa da titi, babu dadewa tasami abin hawa yaja sukayi gaba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>A gida kam Fattyce ta shirya tsaf cikin material pick sai mayafi back, tayi kyau babu laifi kallan Mommy tayi gami dacewa "bani kud'in zan wuce"</p><p><br /></p><p>"Gidan ubanwa? "Mommyn ta tanbaya</p><p><br /></p><p>"Haaaaa gidansu Aseya zani ai ba dadewa xanyi ba"</p><p><br /></p><p>"Babu inda zaki"</p><p><br /></p><p>"Wanan wasa ne, bayan muyi waya tana jirana sanan kice babu inda zani, kawai ni kibani kud'in na tafii"</p><p><br /></p><p>"Inkuma ban bada bah fa? "</p><p><br /></p><p>"Ai zaki badama"</p><p><br /></p><p>"Kije bedroom dina kiduba wanan red bag d'in ki dauka, karkidauki abinda yafi 5k kinji na fada maki"</p><p><br /></p><p>Tana dauko kud'in ko sallaman kirki bata ma Mommy ba tayi gaba abinta</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tana fita tsakar gida tashiga kiran driver su cikin d'aka murya, aguje yazo gami dacewa "ranki ya dad'e" wani wawan harara ta watsamai sanan tace "ni dallah gyara mota, gidansu Asiya zamuje" gyara mota yayi sanan tashiga gidan gaba tana tsina fuska, jan motan yayi sukayi gaba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>K'arfe 1 Afrah tadawo, ko kallo bata isa Mommy ba, itama sallah tayi sanan tafara abinda zatayi a cikin gidan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p>Yau saura 2days Hafiz yatafi school d'an haka sai shirye-shirye yakeyi, musanman Mommy tasa Afrah tamai dabon nama mai yawan gske,duk abinda yake buk'ata Daddy yayi haka shima duk shirinshi ya gama tas rananr tafiya kawai duk suke jira. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ranan tafiyan Hafiz yakama Thursday har Abuja duk suka rakashi, har airport fad'a sosai Daddy yama Hafiz Mommy ma rayi iya daidai nata, matan Alkhairi Afrah tama Hafiz ya amsa babu laifi, Addu'a Afifah tana tamai Fatty kam da fad'a suka rabu dan yaqi bata wani laptop dinshi taba k'awarta, basu bar airport din bah sai da jirgunsu ya tashi(su Hafizu asauka lfya) </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sai da suka kwana A abuja Friday kafin Sallan juma'a suka shigi kaduna. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Bayan Daddy yadawo saka salar juma'a a babban palo daddy ya tsaya, yaransa ne sukai ta kawo mai gaisuwa da k'anan yan kasuwa shikam sai Alheri yake masu, cikin gida kam Mommy taci tayi fam, d'an ita tsana taga Daddy na kyauta gani take duk dukiyan su sai kwashe ya kyautar. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Bai samu shigowa cikin gida ba sai bayan Sallahn isha, sai da yayi wanka yaci abinci sanan yashiga sanar dasu cigaba da duk suka samu game da Business din da zasufara nashigo da kaya iri daban daban ta jigin ruwa, daka kayan abinci, kayan gine-gine, kayan sakawa da kaya dai duk na anfanin rayuwa</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Murna sosai duk sukayi gami da fatan Alkhari, Aduu'a sosai sukayi na qarin haske da cigaba</p><p><br /></p><p>Daddy ya amsa da Ameen gami da samasu Albarka, sai k'arfe goma Afrah da Afifah sukamasu sai dasafe sukabar palon, Fatty kam bedroom din Mommy tawuce, k'an gadon Mommy ta zube tana wani ihun murna, can kuma tace"nasan kafin next year munfi haka kud'i insha Allah, dole natafi NEIL UNIVERSITY abuja sanan dole asaimin mota mai zafi su Afrah kam time d'in nasan anata pama a KASU da qazamen k'awayenta"dariya ta bushe da shi... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_kuyi hakuri readers laifin NEPA ne, amma ga wanan shafin har jibi da gata_🤸🏻♀🤸🏻♀🤸🏻♀🤸🏻♀🤣🤣</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *ayi comment nasan halin da kuke ciki, da dad'i kokuwa babu??? Ya kukejin labarin ne?? Wai*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*MUCH LOVE FOR YOU ALL SWEETHEARTS*❤❣💞💞💕💖💘</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>~BIEBIE DEE~🌸</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*wanan page d'in nakune Aunty Billyn Abdul n Rabi'atu sk mashi(mommyna💘) thanks for everything, Allah qara karemin ku*❤❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Page 31-32_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"""" *H*aka dai Fatty taita lissafinta har Mommy ta shigo d'akin</p><p><br /></p><p>"Kekuma wanan wani sabon iskancin ne? "Mommy tace ma Fatty </p><p><br /></p><p>"Ahh Mommy dole fa nayi murna, wanan babban cigaba haka damuka samu"</p><p><br /></p><p>Murmushi Mommy tayi sanan tace"ki dai bari kud'in sufara shigowa, zan baki mamaki"</p><p><br /></p><p>"Dats why i love Mommyna kinsan yakamata"</p><p><br /></p><p>Haka dai sukata d'an hiransu, sai da Mommy tagama duk abinda zatayi a d'akin tayima Fatty goodnight ta nufi side daddy. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> *D*uk abin da Afrah zata buk'ata na makaranta Daddy yama Afrah, kayan sawa masu yawan gaske yasa Aunty Maijiddah takawo ma Afrah d'an zuwa school, godia sosai Afrah rayi gami da addu'a</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mommy da Fatty sunji haushin wanan siyyyan da Daddy yayi mata sosai, dan wunan wanan ranan habaici iri iri babu kalan wanda Mommy da Faty basu mata ba, share su tayi, ikaman bata san yaranda sukeyi ba, </p><p><br /></p><p>"Wallahi mommy sai kiyi da gske kan wanan shegir Afran" cewar Fatty </p><p><br /></p><p>"Ki barni da su kawai, har shi kanshi Daddy"</p><p><br /></p><p>"Ai Daddy kina ganin shi Wallahi sai a hankali, shi dai Abdul yama kanshi adalci da baya zuwa every weekend"</p><p><br /></p><p>"Hmmmmm wanan banda case dashi d'an ban gama alaman cigaba tare dashi ba, Daddyn ku kuwa ido zan qara samai da kyau, naga lamarin nasu nasan wuce gona da iri"</p><p><br /></p><p>"Yauwwa Mommy, kiqarasa ido sosai, nima kai na ba barinsu zanyi ba shegiya munafuka, gashi duk ta chanzama Afifah hali bata ganin laifinta ko k'adan"</p><p><br /></p><p>"Ita kuma wanan zanci ubanta"</p><p><br /></p><p>Haka dai Mommy tai ta zancen marasa anfani kan Daddy da Afrah.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Afrah da Sulaiman kuwa yanxo sunyi wani irin sabo wanda su kansu suna mamaki, suna manne a waya ko da yaushe, sai dai in yatafi sch ko zaiyi karatu haka itama, sosai suke chatting, yanzo hakan ma chatting d'in sukeyi, kwance take phone hannunta sai smiling takeyi Fatty ce tashigo d'akin babu sallama kamar yanda tasaba, kallan Afrah tayi sanan tace "niko kinga red kimona na dakikazo gyra d'akinan? "</p><p><br /></p><p>Batare da ta kalleta ba tace"nooo, bangani bah nikam"</p><p><br /></p><p>Tsaki Fatty tayi gami da barin d'akin, da ido Afrah ta bita chan kuma tace "ikon Allah sai kallo"</p><p><br /></p><p> A palo ta tadda Mommy turo baki gaba tayi gami da cewa "naje. Ina tanbayanta ko kallo ban isheta ba danna phone kawai takeyi, innaga ita da saurayinta ne" Faty tace ma mommyn</p><p><br /></p><p>"Urauban saurayin, dan ubansu" d'akin nasu tayi da izza</p><p><br /></p><p>Koda tashigo Afrah bata ji ba tana chan tana zuba zance a online 😂</p><p><br /></p><p>"Wanan wani sabon iskanci ne Afrah, kice kike gyra d'akinan antanbayeki abu kuma kina bada amsar banza, na lura kwanan kanki rawa yakeyi toh kisani duk abinda ke kanki zan sauke maki shi, gida dai nawa ne, babu wani shegen da zai kawomin sabon salon iskance"</p><p><br /></p><p>Afrah da tunda taji voice d'in Mommy ta aje phone din tayi shuru. </p><p><br /></p><p>"Badake nake magana bane ko? Allah dai yakaremu da gadon mugun hali"</p><p><br /></p><p>"Yihakuri Mommy, in Afifah tadawo islamiyyah xan tanbayeta ko ta gani"</p><p><br /></p><p>"Da kyau, anjima inason kimin fruit salad "</p><p><br /></p><p>"Oky"kawai Afrah tace</p><p><br /></p><p>Ita yanzo tadena mamakin sankai irin na Mommy da mugun hakinta, kallansu kawai takeyi tabar ma Allah komai a hannunshi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> *K*wana biyunan bata cika zaman gida ba, sabida registration aketayi, Daddy yaso yasa ayimata komai sai dai tafara zuwa lectures kawai, amma Afrah taqi tafisan komai tashiga ayi da ita taji yanda akeji kuma taqara wayewa da qara karantar jama'a</p><p><br /></p><p> Duk abinda zatayi yau a sch d'in ta gama, tafito kenan d'an tafiya gida sukayi karo da wata buduruwa wanda bazata wuce age mate d'in Afran bah, doguwace batada jiki sosai, moderate (kamar ni Biebie dee🤸🏻♀) fara ce amma ba sosai ba d'an Afrah tafita haske sosai tanada kyau dai dai ita, she's just pretty </p><p><br /></p><p> "Am so sorry please, wallahu sauri nakeyi ana jirana shiyasa ko ganin gabana banayi"buduruwan tacema Afrah</p><p><br /></p><p>"Never mind, lamarin sch ne sai a hankali"</p><p><br /></p><p>Dariya tayi sanan tace" by the way am Zarah Maktar, You? "</p><p><br /></p><p>"Khadija Afrah Salis"</p><p><br /></p><p>"Wow kaji sunan gayu har guda 2"</p><p><br /></p><p>"Wani gayu Fa, keda kikace ana jiranki na tsaidake"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hmmmm just forget about them, bani number ki inkinzo gobe Allah ya kai mu sai na nemeki"</p><p><br /></p><p>Mika ma Afrah phone d'inta tayi qiran Samsung s7,ansa atayi tasa mata number'n, </p><p><br /></p><p>"Insha gobe i'll call u, Allah sa ma department d'aya muke" ta k'ara maganan tana tafiya cikin hanzari</p><p><br /></p><p>Daria Afrah tayi sanan tace"ikon Allah ji yanda rake sauri kaman zata tashi sama"😂</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Da tunanin Zarah ta iso gida, sai dataje tama Mommy sannu da gida kana tawuce d'akinsu</p><p><br /></p><p>Fatty da friends d'inta su 5 ne suke zaune d'akin, da sallama tashigo, suka amsa sama sama, "sannunku tace daso, babu wanda ya amsa sai Aseeya, itama Afran Batabi ta kansu ba, bag da mayafi tacire tashiga toilet ta d'auro Alwala, tana idar da Sallah tabar masu d'akin</p><p> Hiran su sukai tayi na abu d'aya wanan babanshi nada kud'i, wanan handsome ne, wanan classy ne wanan ba classy ba, haka dai sukai ta hiransu har 5 sanan sukayi make-up duk sukafitoh, masha Allah duk suyi kyau, a palo sukaga Mommy, sai a lokacin suka gaisheta, ta amsa cikin sakin fuska fiye da yanda kuke tunani</p><p><br /></p><p>"Toh Mommy sai na dawo"Fatty tace</p><p><br /></p><p>"Okay tohm k'arki kai dare" (nikam BIEBIE nace hmmmm Mommy kenan) </p><p><br /></p><p> _NEXT DAY_</p><p><br /></p><p>Afrah ta shirya cikin black jallabiyya tayi kyau sosai, d'an har red💄tasaka sanan tasaka sunglasses 🕶 black tayi kyau kaman menene, shigowa tayi tama Mommy sallah, ta amsa mata a dak'ile kamar dole"duk kin gama shiya abincin da komai da kimai ko? dan su Umme-Abdulnaseer d'in tana hanya"</p><p><br /></p><p>"Duk nagama komai"</p><p><br /></p><p>"Da kyau, ai nasan Daddynku yabaki kud'i ba sai nabaki ba"</p><p><br /></p><p>"Ehhh ina dashii"</p><p><br /></p><p>Sallama tayi mata tabar d'akin, agogon hannunta takalla 1:43 tagani, d'an tsaki tayi sanan tacigaba da tafiya, bata kai da isa bakin gate ba phone d'inta yafara ringing, tsayawa tayi ta fiddo da phone d'in da side bag d'inta, Zarah Muktar ce(sunyi waya tin jiyan hadda chatting ma) </p><p><br /></p><p>Murmushi tayi gami da sa phone din a kunanta</p><p><br /></p><p>"Haba khadeeAff, nifa nafitoh ina yanya"Zarah tace</p><p><br /></p><p>"Nma ganin da yaddan Allah"</p><p><br /></p><p>Katse wayan duk sukayi, tana kokarin barin gidane taga baba mai gadi na bud'e gate, tsayawa tayi motar tashigo sanan tafita. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gaba da ita k'adan akayi parking motan, ta gyra zaman side bag d'inta zata bar wajen taji anacewa"hajiya ko naciki? "</p><p><br /></p><p>Juyowa tayi d'an ganan wanene, ido hud'u sukayin da Ummu_Abdulnasir, k'arasawa wajen tayi a kunyace,"Ummu kiyi hakuri wallahi ina sauri, sam ban ganeki ba"</p><p><br /></p><p>Murmushi Ummu tayi sanan tace"babu komai, ina zaki wanan kwalliya? "</p><p><br /></p><p>Sai da ta gaisheta sanan tace"KASU zani munata registration ne"</p><p><br /></p><p>Ehh hakane Allah temaka"duk wanan magan dasukeyi Ummu-Abdulnasir narike da hannunta, har zasu bar wajen sai Ummu taleka motan"kai Abdulnaseer fitoh mushiga, kana abu kaman mara lafiya"</p><p><br /></p><p>Ido hud'u sukayi da Afrah, juya big n beautiful eyes d'inta tayi sanan tacemai"ina wuni"</p><p><br /></p><p>"Lafiyalau"yace da ita, bata k'ara magana ba sukayo cikin gida, murna sosai Mommy tayi da ganinsu amma bata ji dad'in ganan Ummun da Afrah ba, shiru kawai tayi. </p><p><br /></p><p> Abdulnaseer ne ya gaida Mommy cikin girmamawa da fara'a itama fuska sake ta amsa, tashi yayi gami da cewa"bari naje Mota"</p><p><br /></p><p>"Nooo Afrah kaishi d'akin Sulaiman, gyare yake tas kaman nasan tare zakuzo nasa aka gyra jiya"Mommy tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nooo Mommy bari nazauna a motan kawai"yaqarasa maganan yana barin palon</p><p><br /></p><p>"Shiyasani" cewar Ummu</p><p><br /></p><p>"Toh Afrah samai abinci sai ki miqa mai inzaki tafi"</p><p><br /></p><p>Nan Afrah ta zubamai komai tajere a tray, Sallama tamasu tafita da tray'n </p><p><br /></p><p> Tana isa wajen motan, k'onkusa window motan tayi, bud'e murfin motan yayi d'an ya ganta da tray </p><p> Mik'amai kawai tayi batare da ta ko kalleshi ba, amsa yayi gami dacewa "thank you "kaman bataji ba tayi gaba abita, sunglasses 🕶 d'inta ta fiddo ta maida wanda tacireshi tin sanda suka Fara magana da Ummu-Abdulnaseer, sai dayaga tabar gidan yamai da hankalinshi kan trayn da takawo, smiling yayi sanan yafara cin abincin.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A bakin gate suka hade Afrah zatashiga Zarah zata fita, Afrance ta ganta hannunta tajawo a tsorace ta d'aga kai dan ganin wanene, ganan Afrah datayi yasata sauke ajiyan zuciya "kekam meyasa in kina tafiya baki kallan gabanki kai kawai kikesawa"Afrah tace</p><p><br /></p><p>"Hmmmmm wallahi kibari kawai haka nake, jiya ma haka nayi" ta k'arasa maganan tana daria</p><p><br /></p><p>"Naga alama ai, muk'arasa ciki"</p><p><br /></p><p>"OMG KhadeeAff wanan dressing din haka fa? Nifa sai yanxo na ganki da kyau"</p><p><br /></p><p>Dariya Afrah tayi sanan tace"ina zaki ganni inkikasa kai a gaba ke shikenan"</p><p><br /></p><p>Itama dariya sanan tace"kingane ni da yawa, wai mai ya tsaida ke ne? "</p><p><br /></p><p>"Kibari kawai wallahi baqi mukayi kuma sai dafitoh sukazo dole nakoma"ita qarasa maganan tana jan tsaki</p><p><br /></p><p>Tsayawa da tafiya Zarah tayi sanan tace"tell me meyafaru"ta qarasa maganan tana d'aga mata gira😉</p><p><br /></p><p>"Kedai wallahi kincikasa mutun dariya, babu wani komai"</p><p><br /></p><p>"Yeahh nasani just tell me"</p><p><br /></p><p>"Kawai wanda zukazo da friend d'in Mommy ne kallo, duk sai yaqara bat'amin rai"</p><p><br /></p><p>Bat'a face Zarah tayi sanan tace"wai shi tohh?"</p><p><br /></p><p>"Ohooo i think yaronta ne, naga suna kama sosai"</p><p><br /></p><p>"Ohhhhh kodai"sai kuma tayi shuru bata qarasa maganan ba tana daria</p><p><br /></p><p>"Kodai mene?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A'a kedai kika sani, muje muyi abinda zamuyi time is going" nan suka qarasa ciki suka kiyi duk abinda zasuyi. </p><p><br /></p><p> Kafin 3 duk sun gama abin da zasuyi a sch din, tsaye suke, suna sallama wata buduruwace y'ar gayu ta tsaya gabansu, kallon ta Zarah Muktar tayi, smiling buduwan tayi masu sanan tace"d'an Allah ku sister ne naga kuna kama, tin dazo naketa kallanku"</p><p><br /></p><p>Kallan juna Afrah da Zarah sukayi sanan sukai daria, Zarah'n ce tace" yes we are cousins"murmushi Afrah tayi sanan tace "yes "</p><p><br /></p><p>"Wow shiyasa kukai kama, by the way am Husna Mansur, anan Marafa nake "</p><p><br /></p><p>"Ohhhh nice, wani course kikai applying ne" Zarah ta tan bayeta</p><p><br /></p><p>"Micro biology"Hunsna tace</p><p><br /></p><p>"Wow duk muna tare kenan"cewan Afrah</p><p><br /></p><p>Ex changing numbers sukayi, Zarah taso suqara sa gidansu suyi sallan la'asar amma sukaqi, sallama sukayi kowacensu tayi nasu gidan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A gida kam Mommy da Ummu-Abdulnasir hira suka sha sosai "ni kam ina Fatima tinda nazo bam ganta ba"</p><p><br /></p><p>"Eh na d'an aiketa ne malali, Amma nasan maybe tana hanya"</p><p><br /></p><p>"Okay gara da bamuzo da Humairah bah, gashi duk yan matan gidan basunan hadda autanki"</p><p><br /></p><p>"Aikuwa dai, auta kam tanan hanyan dawowa nasani" hira dai suketayi kayan motsa baki iri iri gaban Ummu, Fattyce ta shiga(, yau anyi sallama) k'araso wa tayi d'an ganin ko wanene d'an tin a waje dataga motan da baba gidansu ba take san sanin wanda yazo</p><p> K'arawa tayi wajen su Mommy'n tana ganin Ummu tasaki wani smiling, gaisheta Fatty tayi cikin girmamawa da sakin fuska, Ummu ta amsa da fara'arta kamar yanda tasa ba</p><p><br /></p><p>"Ummie ina Humaira, bakuzo tare ba? "</p><p><br /></p><p>"Ehh humaira taje gidan anty Murja sister na, jin zancen sch d'inta da mijin k'arwar tawa ke nema mata, amma da tare zamuzo, danaga duk bakunan har inacema Mommy ku gara da bata zoba"</p><p><br /></p><p>Smiling Fatty tayi gida cewa"aikuwa, wani school ne? "</p><p><br /></p><p>"ABU zaria ne"</p><p><br /></p><p>Fuska Fatty ta bat'a sanan tace "ohhhh Allah sa su fara a sa'a"</p><p><br /></p><p>"Ameen daughter, ke sai next year ko? Mommynku kefadamin bakiyi passing ba"</p><p><br /></p><p>"Insha Allah Ummie"</p><p><br /></p><p>"Allah temaka, kije Abdulnasir nan cikin mota kuyi hiran dashi, nasan yagaji"</p><p><br /></p><p>"Okay toh"Fatty ta tashi tayi wajen da saurinta</p><p><br /></p><p> Mommy da tunda suka fara magana take murmushi, qarowa murmushin nata yayi dataji Ummu tace Fatty taje tasamu Abdulnasir suyi hira, wani abu tashiga kitsawa a ranta ita kadai, Ummu ko tace hakanne bawai da wani manufa ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Haka Fatty taje taita damunshi, banza da ita yayi sai time to time yake kulata, itadai sai zuba takeyi, sai bayan la'asar sanan suka bar gidan, kayan kwalliya masu yawa Mommy tabada akaima Humaira, Abdulnaseer agogo tabashi mai kyau, godia sosai Ummu tayi ita da Abdulnasir,Ummu na shirin shiga mota Afrah tashigo, motsowa tayi sujayi sallama sanan tashige ciki, da ido Abdulnasir yabita, itakam batasan ma yanayi bah... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_ina gaisuwa masoya, ina sanku sosai, lodi lodi_❣💋❤❣❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_kai gaskiya ina jiran comments in ba, nayi shuru sai, amma ya xata kasance?? Ga Sulaiman gakuma Abdulnaseer ga Fatty classy😂 ga kuma Afrar, ina Mommy??? Ita mezatayi nee?, duk sai naji comments zancigaba_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*MUCH LOVE ❤️ FOR U ALL*</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Wanan page d'in naku ne Mutanan kirki*</p><p><br /></p><p>*Ummu-Abdulnaseer*</p><p>*Aunty Barakah*</p><p>*Bakhitey(k'awalli)*</p><p>*~jiddah*</p><p>*princess Nusy*</p><p>*Ummu safeeya*</p><p>*Husnah Mansur*</p><p>*Oum Abdulkhaliq*</p><p>*maman heeshmer*</p><p>*Fatima Ibrahim Muneerah*</p><p><br /></p><p>*thank you so much for d love n support, Allah barmu tare har gidan Aljannah. Ameen Ameen*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 33-34_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"""""" *Abdulnaseer*a palo kwance saman doguwar kujera, Ummu ce ta fitoh, zama tayi a kujeran da ke kollonshi</p><p><br /></p><p>"Ni kam kaci abinci? "Ummu ta tan bayeshi</p><p><br /></p><p>Tashi zaune yayi sanan yace"ni Ko Ummie wanan Afrah'n ma yariyan Mommy ne?"</p><p><br /></p><p>Smiling Ummu tayi sanan tace"ehh toh, yariyar kanin mijinta ne da yarasu, kaga kenan ai y'ar tace ko"</p><p><br /></p><p>"Ehh hakane gskiya"ya k'arasa maganan yana wani smiling </p><p><br /></p><p>"Meyafuce kake tanbaya?"</p><p><br /></p><p>"Nooo, kawai dai na tanbaya ne fa Ummie"yayi maganan yana shafa kanshi</p><p><br /></p><p>Murmushi kawai Ummie tayi sai kuma tace"ko mai dai Mainene kai kasani"</p><p><br /></p><p>"Hmmmm, Ummie banfa cii bah"tashi yayi yanufa dinning </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kai dai kasani, komai ake ciki inan zakazo kasameni, dama bansanka da surutu bane"</p><p><br /></p><p>"Kikace mene Ummie? " *Abdulnaser* yace daka can dinning </p><p><br /></p><p>"Kai bada kai nakeyi ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>Alhamdulillahi su *Afrah* sun kammala komai na registration har sufara lectures, </p><p>Kamar kulin, yauma *Afrah*ta kammala duk wani aikinta da takeyi cikin gidan, cornflakes tasha sanan ta k'arasa shiryawa, tana gyra zakan mayafinta ne Afifah tace "Aunty yau Saturday zaki school?</p><p><br /></p><p>"Yes baby, muna karatu ne"</p><p><br /></p><p>"Okay best of luck"</p><p><br /></p><p>"Thank you lil_lil"</p><p><br /></p><p>Face Afifah ta bat'a sanan tace" ni banasan wanan sunan ki bari anty"</p><p><br /></p><p>Dariya *Afrah*tayi sanan tace bakin yaa Sulaiman naji ai"</p><p><br /></p><p>"Ehh ai shima daka baya yabar cemin"</p><p><br /></p><p>"Toh shiken nima na bari"</p><p><br /></p><p>"Yauwa, aunty please inkindawo xaki aramin phone d'inki xan gayama yaya wani abu ne"</p><p><br /></p><p>"Tohh Baby sai nadawo"takarasa maganan tana barin d'akin nasu</p><p><br /></p><p> Side d'in Mommy tayi, tashiga bedroom d'in nata da sallama, sai da Mommy ta amsa sanan tashiga, gaisheta tafarayi sanan tace"mommy sai nadawo"</p><p><br /></p><p>Kallanta Mommy tayi sanan tace"sai kindawo daka ina fa? "</p><p><br /></p><p>"Mommy school zani, akwai karatun da yan 3lvl da 4lvl sukeyimana yau"</p><p><br /></p><p>"Tohh yayi kyau alhudahuda"</p><p><br /></p><p>Tashi tayi tabar d'akin dan tasan ko shekara zatayi Mommy ba addu'a zata mata ma, bama tama yaranta ba ne sai ita, dawanan tunanin ta bar gida.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tana isah school d'in babu dad'ewa su Zarah da Husnah suka iso da duk wani mai buk'atan karatun da yazo, babu bat'a lokaci akafara karatu suna jotting, haka akai ta karatu har 12:45.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Bayan sun idar da Sallah suna zaune,Zarah Muktar ne tayi magana" ni fa yunwa nakejii"</p><p><br /></p><p>"Toh mezamuci? "Cewar Husnah</p><p><br /></p><p>"Ku ni dai banjin wani yunwa" *Afrah*tace tana duba wani book da ke hannunta</p><p><br /></p><p>"Ke mufa ba dan karatu mukaxo duniya bah" cewar Zahrah </p><p><br /></p><p>"Toh mamarciki muje muci ko snacks ne mu daura"</p><p><br /></p><p>Dariya Husnah tayi sanan tace"kuna da abin dariya wallah"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan sunci abincin, hall suka koma aka cigaba da karatu sai 3 dai dai suka fitoh. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Suna fitowa *Afrah*phone d'inta ta fiddo daka cikin bag d'inta wanta tun suna karatu takejin vibrating d'inshi, missed calls na Mommy tagani har 12,babu bat'a lokaci *Afrah*tashiga k'iran Mommy'n ringing 2 Mommy ta dauka</p><p><br /></p><p>" *Afrah*kina ina ne? "</p><p><br /></p><p>"Ina school Mommy, amma yanxo zandawo"</p><p><br /></p><p>"Oky toh please kiyi sauri, Daddy'n ku yayi waya yana hanya, girki za'ayi masa"</p><p><br /></p><p>"Tohm ganin soon da yaddan Allah"</p><p><br /></p><p>"Yauwa toh adawo lfya, kiyi sauri please"</p><p><br /></p><p>Kafin *Afrah*tace wani abu har Mommy ta kashe kiran, da ido *Afrah*tabi phone d'in, a xuciyan ta tace"Ai na san k'ira sai da dalili, meye anfanin Fatty dake gida toh? Wata zuciyan tace da ita" ke ma inna ruwanki da Fatty'n komai zakiyi dai toh kiyishi d'an Allah". </p><p><br /></p><p><br /></p><p>K'arasawa wajen su Zarah tayi, sai da ta kallesu sanan tace"Ni zan wuce gida"</p><p><br /></p><p>Hararanta Husnah tayi cikin wasa gami dacewa"kin manta ne"</p><p><br /></p><p>"Bangane gida zaki bah"cewar Zarah</p><p><br /></p><p>"Wallahi Mommy ce tak'irani Daddy na hanya"</p><p><br /></p><p>"Ohhh toh ke Husnah kiyi hakuri next time sai muje gidan naku, ai muna tare insha Allah"Zarah tace</p><p><br /></p><p>"Toh shikenan no problem Allah kaimu"</p><p><br /></p><p>"Ameen "duk suka amsa</p><p><br /></p><p>Sai da sukazo gate sanan sukai sallama kowanne su yayii hanyan gidansu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A gida kam bayan Mommy ta gama waya da *Afrah* harara ta watsama Fatty gami dacewa</p><p><br /></p><p> "Kedai badai bakida mutunci ba, ban isa nasaki kiyi ba"</p><p><br /></p><p>"Toh wai Mommy ni na iya irin kallan girkin da kike magana ne, kinfa san daka indomie sai soya kwai na iya, Amma sai wani harara kikemin sai kace nayi wani babban laifi haba"tak'arasa maganan tana danna phone d'inta</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wawiya ita *Afran* kanta ba ta waya takoya ba, ke sai tsinannen danna wayan baki tsinana uwar komai, kinfi so komai tawuce ki"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tab'e baki tayi sanan tace"ita duk zata iya wanan wahalan,ni kam baxan iya ba wallahi"</p><p><br /></p><p>"Kar kikoya d'an ubanki, kikayi aura mijin yakoro ki"</p><p><br /></p><p>Dariya Fatty tayi sanan tace" zamanin ku ma Daddy bai koreki ba sai namu zamanin? Kema fa Mommy girkin naki sai aslow"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Zanci mutuncinki fa, baki dakunya"</p><p><br /></p><p>Dariya takuma yi sanan tace" Wallahi mommy gaskiya na fad'a, ko su Aunty Azeezah girkinsu babu dad'i, gaskiya kawai nake fad'a"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kallanta kawai Mommy keyi takasa magana. Ganin kallon yayi yawa ne yasa Fatty cewa" kawai mommy k'ar kiwani damu d'an ban iya girki ba, dan gidana masu min abinci ma sai mai degree wallahi, dan nasan akwai cash"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah sa, inna fatan haka"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yauwa mommy, kicire wata banzan *Afrah*a rainki d'an ita ba komai bane daka ita har Abdul d'in"</p><p><br /></p><p>"Toh shikenan naji, jeki shiryamin kaya cikin drower"</p><p><br /></p><p>"Toh"Faty tace kawai tayi hanyan bedroom din, da ido Mommy tabita. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_kuyi hakuri please_ 🙏</p><p>_bubu yawa MUCH LOVE_</p><p>[12/18, 09:03] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*congratulations sis SADNAD INA taya murnar kammala book dinki SANADIN GROUP, Allah saka da Alkhari yakuma qara basira, Allah ya bamu ikon aiki da saqon da kika isar, Allah tsaremu ya karemu da ka dukkan sharri AMEEN*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 35-36_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"""" *Afrah*nadawo wa sallah tafarayi sanan ta shiga kitchen, tuwan shinkafa takeyi miyan ogu, sai pepper soup na kayan ciki, sai wani shegen zobo dayaji kayan kamshi da flavors iri iri, kafin kace mai gida yadau kamshi,Mommy sai kaiwa da komuwa takeyi, taci kwalliya cikin atanpa super Holland mai zanen red n yellow rayi kyau sosai😇</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yauwa sannu Afrah, nace ko zaki d'an dafa maku wani abu tinda basan tuwa kukeyi ba"</p><p><br /></p><p>"Oky toh bari nayi mana mcroni"</p><p><br /></p><p>"Yauwa toh"</p><p><br /></p><p>Bayan sun gama gyara kitchen din Salamatu tayi, sanan duk suka nufa bedroom dinsu. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sai gab da magrab Daddy ya dawo, da murna duk suka tarbeshi, drink kawai yasha yanufi side dinshi, wanka yayi gami da Alwala, yana fitoh parlor aka fara k'iran sallah, dan haka babu bat'a lokaci yayi massallaci, kamar yanda yasaba bai shigo gida ba sai da yayi har isha.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A parlor duk ya gansu zaune, duk anjere kulolinn abicin da jugs da dai sauran kayan bukata. </p><p><br /></p><p> Zama yayi duk yaran suka sake gaisheshi gami da sannu da zuwa, amsawa yayi cikin sakin fuska, nan Mommy tazuba mai abinci, itama tazuba nata, Afrah ce tazuba ma Fatty da Afifah sanan itama tasa nata. </p><p><br /></p><p> Parlon yayi shuru kowa ya maida hankalinshi kan 🍽 plate dinsa, Daddy ne yafara gamawa, bakinshi yagoge gami dayima Allah godia, kallan Mommy yayi kana yace"Abdulraham yadawo weekend kuwa? "</p><p><br /></p><p>"A'a, tinn wanan dawo wan dakayi dai"Mommy tace</p><p><br /></p><p>"Toh meyasa? "</p><p><br /></p><p>"Tanbayeshi, tinda da mutun yanuna bakai ne ka haifeshi ba yazakayi dashi? "</p><p><br /></p><p>Daddy baice kimai bah, phone dinshi ya dauka yashiga kiran layan Abdul, ringing 2 ya dauka</p><p><br /></p><p>"Meke hanaka hawowa gida weekend? "Daddy yamai tanbayan batare da ya amsa gasuwanshi ba</p><p><br /></p><p>Daka chan bangaran Abdul yace" babu komai daddy "</p><p><br /></p><p>"Good kadawo gida gobe gobenan"</p><p><br /></p><p>Baijirah amsashi ba ya kashe phone d'in, d'an tsaki Mommy tayi gana tace"Allah dai ya kyauta"</p><p><br /></p><p>"AMEEN" daddy yace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sunan zaune a parlorn Afifah sai zubo surutu takeyi, daddy na biye mata chan tace "Daddy dazo nak'ira yaya Hafiz ta phone din anty Afrah nace yasiwomin gown d'inda zansa ran birthday na, wai nace ma kuturo kud'i"</p><p><br /></p><p>Tsaki Daddy yayi gana yace"matsalanshi kenan ai"</p><p><br /></p><p>"Toh dinda akwai ai sai atura ma"cewar Mommy </p><p><br /></p><p>"Alhmdulillahi kam, amma baxan tura ba, d'an last week natura mai kud'i kuka masu yawa, meyakeyi da kud'i yana student? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ai wallahi karkatura mai komai Daddy"Fatty tace</p><p><br /></p><p>Hararanta Mommy tayi ta kana tace"sai kihana tinda kud'in naki ne"</p><p><br /></p><p>"Daddy ai kace bazaka tura ba ko? Amma ni ma kace zaka bani 50k nasiya kaya time d'in da kasai ma Afrah"</p><p><br /></p><p>"Toh kaji, ai duk d'aya kuke da Hafiz din, koyaushe kunada matsala, basan mekuke da kud'i haka ba"</p><p><br /></p><p>Naki Fatty ta turo kaga gami dacewa "please daddy, kaifa kace</p><p><br /></p><p>"Naji Fatima zan baki insha Allah"</p><p><br /></p><p>"Yauwa daddy'n mu Allah kara maka bud'i"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Amen, kee mama kiyi shuru keda kanuwar taki baku buk'atan wani abu ne? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A'a Daddy bana bukatan komai, Allah saka da Alheri"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Toh kintan bayo makarantar girkin"</p><p><br /></p><p>"A'a Daddy indai ta binciken mai kyaunne"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Da kyau, in kinbinciko sai kuhiga keda Fatty tinda ita batama samu sch ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A'a Daddy ni wallahi banaso"tayi maga tana tashi tsaye</p><p><br /></p><p>"Zauna abinki babu dole ai"daddy yace yana daria. </p><p><br /></p><p>Mommy na kallonsu tinda yafara ma Afrah magana tawani bat'a fuska, k'arfe 10:30 yaran suka masu sai da safe suka bar parlon. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kallon Mommy yayi da kyau da gyara Zama, itama gyaran zaman tayi kana tace "Daddynsu lfya kuwa? "</p><p><br /></p><p>"Lfyalau zance tinda bawani tashin hankali bane"</p><p><br /></p><p>"Toh toh mash Allah "</p><p><br /></p><p>Gyaran Murya Daddy yayi sanan yace"dama bbawani abu bane, abokin kasunci na Alhaji Yusuf ne yace mu ci bashin banki muk'ara kan wanan sana'ar da na sanar daku kwanaki tinda kudad'enmu baza su dauko mana irin kayan da mukeso bah, sai nace yabari xanyi shawara da iyali na tukunna, insha gobe ma zan sanarma Sulaiman da sauran yaran naji nasu shawaran"</p><p><br /></p><p>"Masha Allah, aiko dai shi Alhaji yusuf din yakawo shawara, kuma bakacemin ya tab'a irin sana'ar bah"</p><p><br /></p><p>"Ehh hakane"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Toh ni ina ganin shawara mai kyau yakawo, yana hango maka bud'i dakuma daukakan dazaka samu ne nan gaba insha Allah, tin da dai shi sana'arshi ne, yasan cigaban da ketare da abun"</p><p><br /></p><p>"Hakane kuwa"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kagani? Maganan zakafada ma yara kuwa duk bai taso ba, ka barsu kawai, kiransu dai zakayi kace sucigaba dama addu'a kamar yanda suka saba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Toh shikenan, Allah maki albarka da dukann yara gaba daya"</p><p><br /></p><p>"Ameenn Mommy tace tana wani murmushi wanda ita kadai tasan ma'anar yinshii.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_DUBAI_</p><p>Sanye yake cikin wado 3 quoter sai riga armless mara hannu, dawanshi daka sch kenan yayi wanka yashirya, yayi kyau abinshi weather garin ya amshe shi ba kadan ba, dan yanda skin disa yaqara gogewa zaka dauka dan sudan ne ba Nigeria ba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zama tayi bakin gado da cup hannunshi</p><p><br /></p><p>"Friend please tell me, what the u want me to do nw"yace ma wani handsome guy da ke xaune a kujera yana danna waya</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"I really donno" handsome din yace tashi</p><p><br /></p><p>Cup d'in hannunshi ya aje gana yace"haba Muhammad please"</p><p><br /></p><p>"Naji, ni mekakeso nayi yanzo? Nafadama duk abinda yadace, kaqi yi, u are telling me she's still young, toh kabarta sai ta girma"ya k'ara maganan yana tashi</p><p><br /></p><p>"Haba momoh ina xaka muna magana"</p><p><br /></p><p>"You asking me inna zani? Toh zanyi magana da sunshine dinane, na tsaya biyema sai ka kiramin ruwa"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Please now, just 10mns"</p><p><br /></p><p>"Okay, okay naji"zama Muhammad din yayi </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Inajinka friend "</p><p><br /></p><p>"Hmmm kana abu kaman wani dan kauyen katsina"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Just tell me wat to do, ba wanan surutan ba"</p><p><br /></p><p>Dariya Muhammad yayi tayi, sai da yagaji dan kanshi sanan yace"kanaji na"</p><p><br /></p><p>"Yes inaji"</p><p><br /></p><p>"Toh just call her, tell her that you love her so much"</p><p><br /></p><p>Zama Sulaiman ya gyra sanan yace"how? "</p><p><br /></p><p>"Kai i don't know, ina advice dinda naita baka da, duk kanemuso kahada, inkuma bakayi yiba, left to you dats is your wahala" yak'ara maganin yana barin dakin, da ido Sulaiman yabishi har yabar d'akin. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Phone dinshi k'iran iPhone7+ yakalla dake bedside drwer, jawo phone din yayi 6:30 gogon Dubai yace inda Nigeria yanzo 3:30 kenan</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yakai minti10 batare dayasan abinyi ba phone din na hannunshin sai juyashi yakeyi, wata zuciya tana yakira yayin da wani side na zuciyar shi yana kar ya kira, maganan Muhammad ne yafad'o mai a rai inada yake cewa" ka tsaya anan kanan zata fara baka labarin boyfriend din ta wallahi" ai kaman an ingixashi nan yashiga dialing numbern nata. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_NIGERIA_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zaune take tana kara duna wani littafii, yau tin 2:30 tadawo giida, sai Afifah a gefanta tana nata assignment din, phone d'inta ne yafara ringing </p><p><br /></p><p>"Afifah mikomin "</p><p><br /></p><p>Batare da takalla mai kiran ba tamiqama Afran wayan, sunan Sulaiman tagani, ware idonta tayi da kyau sanan tace " iyyah bai ganni online ba" </p><p><br /></p><p>Phone din ta kara a kunnanta gami da cewa Am sorry big brother "</p><p><br /></p><p>Daka chan bangaran Kwanciya yayi gami da lumshe eyes dinshi sanan yace" babu wani sorry kinwani banta da ni"</p><p><br /></p><p>Tashi tayin daka inda take tahaye gado " noo wallhy ina karatune, kasan new student"</p><p><br /></p><p>"Naji ya sch ya friends dinki? "</p><p><br /></p><p>"Duk suna lfya"</p><p><br /></p><p>"Afrah " yakira sunanta cikin wani irin voice da bata sanshi da shi ba</p><p><br /></p><p>"Na'am ta amsa"</p><p><br /></p><p>"Kina jina?"</p><p><br /></p><p>"Ehhhh"</p><p><br /></p><p>"Magana nakeso muyi ta fahimta, kuma please k'ar kimin k'arya"</p><p><br /></p><p>"Toh insha Allah"</p><p><br /></p><p>"Kina da boyfriend? "Shuru tamai batace komai ba, a zuciyar ta tace toh kai meye naka, jiwani tanbaya</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kinyin shuru, zakice ni menene nawa ba??"</p><p><br /></p><p>"Noooo"</p><p><br /></p><p>" toh answer my question"</p><p><br /></p><p>Bakinta narawa tace "noo Am single"</p><p><br /></p><p>Ajiyan zuciya ya sauke sanan yace "toh baki taba saurayi ba? </p><p><br /></p><p>Nashiga uk'unAfrah tace a zuciya, axahirinkam cewa tayi" na tabayi kawai bana accepting dinsu ne"</p><p><br /></p><p>"Alhmdulillahi, nasan sakinso kiji reasons dinda yasa nake tamaki wanan tan bayan ko? "</p><p><br /></p><p>"Ehhhhh" Afrah tace </p><p><br /></p><p>"Because i do love you, Afrah I love you very much, i love you with all my heart n u knw it," nan Sulaiman yashiga fad'amata duk anbinda ke ranshi</p><p><br /></p><p>Shuru tayi batace komai ba, kirjinta sai harbawa yakeyi</p><p><br /></p><p>"Zan baki time kiyi tunani, kawai don't forget that I love you"</p><p><br /></p><p>"Tohh" tace kawai ta katse wayan</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Shiko Sulaiman jiyayi kaman an sauke mai katan dutse, smiling kawai yakeyi abinshi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zaune take kamar andasata, magananta da shi kawai taketa tunowa, muyar Afifah ne yadawo da ita ka duniyar tunanin da ta tafi, "anty natafi islamiyya"ta bar dakin bare da ta tsaya jin mai Afran zatace bah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Afrah kam Mami ta k'ira ta fad'a mata, yanda sukayi da yaya Sulaiman, murna Mimi tayi gami da cewa "Allah tabbar da Alkari, "</p><p> Bayan sun gama waya da Mimi best friend din ta ta kira Aysha(tana Alhikkma university) ta fada mata itama cemata tayi tayi accepting kawai, wunin wanan ranan, cikin sanyi jiki tayi shi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> batayi wani baccin kirki ba, hiranta da yaya Sulaiman taketa tunowa, Allah Allah take gari ya waye taje school tabama su Zarah labari. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Next day_</p><p><br /></p><p>Bayan sun fitoh daka lectures ne, Husna ce ta kalle Afrah kana tace"babe wai mekedamun ki yau ne? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Suyi fad'a da Sweetheart dinta ne"Zarah tace tana dag'amata gira😉</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kallanta Afrah tayi kana tace"wayace? "</p><p><br /></p><p>" ke kifada mana kawai"Husna tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nan Afrah ta zayyano masu duk yanda sukayi Da Sulaiman tana kallansu</p><p><br /></p><p>"Toh ke kinada wani ne dakike dating ne? "Husna ta tanbayeta</p><p><br /></p><p>"No, am single"</p><p><br /></p><p>"What are waiting for? Just accept him kawai, tinda kinsan good person ne"Zarah tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Okay thank you babies, Allah barmu tare"</p><p><br /></p><p>"Ameen baby" duk sukace, haka dai sukaita tsokanan Afrah daka k'ashe sukace ta gaisheshi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Side'n Sulaiman ya damu sosai dan 2days kenan dasukayi waya da Afrah, kuma tin ranan phone d'inta kashe yake,"Friend wallahi tin ranan phone dinta kashe"Sulaiman yacema Muhammad </p><p><br /></p><p>Dariya Muhammad d'in yayi kana yace"zata kunna jan class ne irin na mata"</p><p><br /></p><p>"Allah sa toh"</p><p><br /></p><p> Sai da Afrah tayi 3days sanan takuna phone dinta, messages din tagani masu yawan gske, haka WhatsApp data shiga, messages dinshi ne kaman na group, smiling tayi sanan itama damai reply masu dad'in gske, alamun tayi accepting dinshi, wanan ranan murna wajen Sulaiman kamar mai, Muhammad sai dariya yakemai, tin daka wanan ranan Sulaiman da Afrah suka bud'e sabon safin soyayya batare da Mommy kowani a gidan yasani bah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p>Zaune yake a d'aya daka cikin kujeran bedroom d'in, Ummiece tashigo d'akin, zamanshi ya gyara, zama tayi bakin gado tana kallanshi kana yace"Ummie" saikuma yayi shuru</p><p><br /></p><p>"Abdulnaseer Nasha fad'ama inkana da damuwa kafad'amin,amma dai kai kasani" Ummu tace</p><p><br /></p><p>"Noo Ummie kisan dai inna fad'a maki komai, wanan maganan ina d'anjin kuya ne"yayi magana yana shafa kanshi</p><p><br /></p><p>"Kasan ai ni surukar kace, sai kaitajin kunyan ai"tayi maganan tana qokarin tashi daka zaune</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hannunta ya riko gami da zaunar da ita kusa dashi kana yace" Ummie wallahi inna san Afrah, yarinyan Mommy and i want to Marry her, tin randa muje gidansu da mukadawo nakesan fad'amaki na kasa"</p><p><br /></p><p>Smiling kawai Ummu takeyi tana sauraranshi, sai da yagama duk magananshi sanan Ummie tace"menene abin kunya anan? Kasan dai banasan nuqunuqu ko? "</p><p><br /></p><p>"Am sorry Ummie nah, bazan sake bah"</p><p><br /></p><p>"Good yanzo Zan kira ita hajiyan nafad'a mata, dan tasani"</p><p><br /></p><p>"Nooo Ummie, banfayi magana da Afrah ba, bare ki fad'ama Mommy, kawai taji magana daka sama sai kace y'an zamanin daa, Addu'a kawai zakiyi, inkomai ya kan kama sai ki fad'a ma Mommy da kowa ma"</p><p><br /></p><p>"Allah shiryeka Abdulnaseer"Ummie tace tana dariya</p><p><br /></p><p>"Wallahi Ummie Addu'a zakiyi Allah sa karta bani ciwan kai"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah tabbatar da alkhairi yasa ayi da mu"</p><p><br /></p><p>"Amen Ameen"</p><p> Abdulnaseer yace</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Nima biebie dee nace Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_fans yakukaji na yau??_</p><p>_comments zakuyi nasan halin da ake ciki, love you all lodi lodi_❤❤❤</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*wanan page d'in kyau ne ga duk wani masoyin biebie dee, sanan da duk wani makarancin D'AN HAKKIN DA KA RAINA... Ina godiya mai yawa Allah bar qauna*😻😻</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Bazan tab'a mantawa da kuba y'an BIEBIE DEE NVLS GROUP hakika ina jin dadin comments d'in ku, d'an yana sani nishad'i, ina sanku lodi lodi*❤❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 37-38_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*""""""" Abdulnaseer* yabar bedroom d'in Ummie cikin farin ciki, d'akin shi yayi direct, kan bed ya zube yana daria, chan kuma yatashi zaune, phone d'inshi ya jawo da ke kan bed number'n Hasheem friend nashi yashiga dialing, ringing biyu ya dauka, daka chan bangaran Hasheem yace" ya'akayi ne? "</p><p><br /></p><p>Smiling Abdulnaseer yayi kana yace" dai dai fa, kana gida ne na shigo? "</p><p><br /></p><p>"Nooo, ina hanya zan je naga Nusy"</p><p><br /></p><p>"Toh kajirani nazo sai naraka ka mana"</p><p><br /></p><p>"Yi zamanka bamasan surutu"</p><p><br /></p><p>Dariya Abdulnaseer yayi kana yace" kai d'an iska ne, amma kasan dai ba kowa nake ma surutun ba ko? "</p><p><br /></p><p>"Kai da sauki dai, ai matar ka zatasha zuba"ya karasa maganan yana daria</p><p><br /></p><p>"Katunamin ma"</p><p><br /></p><p>"Mekenan fa? "</p><p><br /></p><p>"wallahi wata yarinyan Friend d'in Ummie nagani inaso, bansan ma ta ina zan fara ba, coz yarinyan na ganta bakamar sauran bane"</p><p><br /></p><p>Daka can b'angaran dariya Hasheem yayi kana yace"kar ka bani kunya mana, kai da ke temaka mana,Ta wanan side d'in mezai baka tsoro kuma? "</p><p><br /></p><p>"Baxa ka gane ba, batada rawan kai ne, basan ma ya zance maka ba"</p><p><br /></p><p>"Bakana da number'n ta ba? "</p><p><br /></p><p>"Yes, ai tin randa na fara ganinta nasamu number'n"</p><p><br /></p><p>"Good, k'iranta kawai zakayi, kai ba sai na maka bayani ba, bakin ka ya temake ka kawai"</p><p><br /></p><p>"Hahahaha, insha Allah kuwa, Dan ko tana da wani ma koreshi zanyi"</p><p><br /></p><p>"Hhhh da ka temaki kanka, zanzo dai kafin nakoma gida"</p><p><br /></p><p>"Okay ka gaida Nusy"</p><p><br /></p><p>"Zataji "sallama suka gama duk suka katse kiran.</p><p><br /></p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p>Soyyan Sulaiman da Afrah yana tafiya yanda ya kamata, amma Har yanzu babu wanda ya sani a gidan, su biyu suke kid'ansu da rawansu. Suna bama junansu kulawa yanda yakamata. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_BAYAN KWANA BIYU_</p><p><br /></p><p> Zaunee suke dukkan su a parlor, Mommy, Fatty, Afrah sai Afifah da keta buga game a new iPad dinta da Daddy yasiya mata, parlor'n shuru babu mai magana kowa yana abinda ya fiye mai. </p><p><br /></p><p> Phone d'in Afrah ne ya shiga ringing, Daga kanta tayi daka karatun da takeyi ta kalla phone d'in, new number da tagani ne yasata share kiran taciga ba da abinda takeyi, haka wayan ya k'arata ringing d'inshi ya katse batayi picking ba, kiran ne ya k'ara shigo wa, shima batayi picking ba, sai ma silent data sa a wayan, taci gaba da karatunta, a takaice dai sai da akakira sau 6 duk bata dauka ba. </p><p><br /></p><p> Tunda k'iran yafara shigowa wayan nata Mommy ta kasa ta tsare tana jiran taji mai k'in Amma taji gum, kallan Afran tayi kana tace" wai ba phone d'inki ke ringing ba ne? "</p><p><br /></p><p>"Shine Mommy, basan mekiran bane"baki Mommy ta tab'e, Fartty kam wani dogon tsaki tayi taci gaba da sana'ar danna wayan nata. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wayan ta dauka d'an duba wani abu ciki, bata kai da dubawa taga alamar message yashigo wayan, shiga cikin inbox d'in tayi, new number tagani, shiga tayi d'an ganin me'aka turo</p><p> _please pick d call, am one_ abinda tagani kenan, a zuciyarta tace" u are d one? Who? " tashi tayi gami da tattara duk wani kayan ta tayi d'akinsu da kallo Mommy ta bita. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Afrah na shiga d'aki call din na k'ara shigowa, number dazo ne dai da'aka mata 6 missed calls da next,kallan Number ta tsaya yi kaman ta sanshi, sai dayakusa tsikewa ta dauka gami da karawa a kunnanta, shuru tayi batare da tace k'ala ba, daka chan bangaran kam tana picking "Alhamdulillahi"akace kana yadaura da cewa" kina jina? "</p><p><br /></p><p>"Inaji, how are you? N wat d u want from me?" Afrah tace</p><p><br /></p><p>Sai da ya d'anyi shuru kana yace" how U, ya su Mommy n all? </p><p><br /></p><p>"Fine, who are you please"</p><p><br /></p><p>" am mrs right, don't worry zaki sanni soon" yayi maganan yana daria</p><p><br /></p><p>"Wrong number, i don't know what you are talking about"</p><p><br /></p><p>"AFRAH! "</p><p><br /></p><p>taji ya kira sunanta, samun waje tayi ta zauna kana tace" please tell me who are you?"</p><p><br /></p><p>"Oky, okay, it's *Abdulnaseer*</p><p><br /></p><p>*Abdulnaseer! ** ta maimaita sunan</p><p><br /></p><p>"Yes" yace da ita</p><p><br /></p><p>" gaskia ban ganeka ba"</p><p><br /></p><p>Smiling yayi kana tace" nasani ai, buh zakisanni yanzo"</p><p><br /></p><p>"Okay " tace kawai</p><p><br /></p><p>" kaman yanda kika sani am Abdunaseer Abdullahi Yalwa,tarihin kanshi yabata a takaice</p><p><br /></p><p>"Good, wani course" ta tan bayeshi</p><p><br /></p><p>" in mun had'u i'll tell everything"</p><p><br /></p><p>" okay good "</p><p><br /></p><p>"Yes, when zamu had'u? Coz i have something to tell you, n it's important"</p><p><br /></p><p>"What is it " ta tanbaya</p><p><br /></p><p>"In munhad'u den asking anything, so dai yaushe zanzo? "</p><p><br /></p><p>Shuru tayi sai kuma chan tace" i'll think about it"</p><p><br /></p><p>Sallama yayi mata ya kashe wayan, da kallo da bi wayan a zuciyan ta tanasan sanin maganan da yace zasuyi, toh wani magana, ta kai minti 15 tana tan bayan kanta, dataga bata da answer phone d'inta tajawo tashiga dialing numbern Mimi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A parlor kam tinda Afrah ta tashi Fatty ta kalle Mommy kana tace" inaga fa wani, Munafurcin wanan shegiyar ke hadawa fa " tak'arasa maganan tana kallaan Mommy da kyau</p><p><br /></p><p>"Ina tunanin haka" Mommy tace</p><p><br /></p><p>"Kigafa kiranta akairayi raqi dauka a gabanmu sai sai da tabar parlorn, wanan ai rashin gaskiya ne, yanzo haka wani mana qisar suke shukawa da Inna"</p><p><br /></p><p>Zama Mommy ta gyra sanan tace"Aniyarsu ta bisu, kurwana kur, nama na da yarana da d'aci, munafinsu zai qare masu wallahi"</p><p>.</p><p><br /></p><p>"Mommy wai waye munafuki"Afifah ta tanbaya dan tinda suka fara maganan batasan sunayi ba hankalinta na kan game</p><p><br /></p><p>"Dallah tashi kibar wajenan wawiya kawai" Farty tace</p><p><br /></p><p>Baki tamurgusa sanan tace" bazan bari ba, ai ba parlorn ki bane"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tasha Fatty tayi zata kai mata duka"ni zan mareki ne, indai ina magana kinasamin banzan bakin ki"</p><p><br /></p><p>Bayan Mommy Afifah ta boye, tana magana kasa kasa wanada bansan metake cewa ba</p><p><br /></p><p>" wallahi Mommy kiyi mata warning "</p><p><br /></p><p>"Kee oya wace d'aki"mommy tacema Afifah</p><p><br /></p><p>Sai da tagama harare hararen ta sanan tabar parlorn fuuuuu</p><p><br /></p><p>Kudai bakuda aiki sai na fad'a sai kace kuna ganin hanjin juna" Mommy tace ta qoqarin tashi</p><p><br /></p><p>Tsaki Fatty taja</p><p><br /></p><p>Juwowa Mommy tayi kana tace" uban wa kike ma tsaki dan Ubanki? "</p><p><br /></p><p>" ni banyi da kee ba, mutun baida aiki sai zagi da masifa"</p><p><br /></p><p>Mommy batace komai ba tawuce. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> B'angaran Abdulnaseer kam yana gama waya da Affrah Hasheem ya kalla sanan yace" Allah temake ni dai"</p><p><br /></p><p>Dariya Hasheem yayi kana yace " please kar kabani kunya mana NASS, i know you n i trust you, kai dai kaita Addu'a inhar da alkhari komai cikin sauki zaizo"</p><p><br /></p><p>" Allah sa kam, Amma kaman she have someone else"</p><p><br /></p><p>"See you, kana nufin haka zataizama kenan saboda zakazo ka aure ta ko?yan da kaban labarinta ai irin wayanan yammata sufi yawan samari"</p><p><br /></p><p>Kallanshi Abdulnaseer yayi kana yace" da gske? Toh gaskiya wajen Ummie zanje ta bani shawara coz i don't want to lose her"</p><p><br /></p><p>" kai ko kunya bazakaji ba zakace kasamu Mommy da wanan maganan? "</p><p><br /></p><p>"Kunya? Ummien nawa zanji kunya? For wat reason ma? Ai ko Abbane zan iya zuwa mashi da maganan balanta na Ummie"</p><p><br /></p><p>"Toh yaran Ummie muje naraka neman sawaran"</p><p><br /></p><p>Hararanshi Abdulnaseer yayi cikin wasa kana sukayi siden Ummien. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sunshiga da Sallah, zaune suka sameta tana waya, waje suka samu suka zauna harta gama wayan, gaisheta Hasheem yayi ta amsa cikin sakin fuska, zamanta ta gyara kana tace" inma yunwa kukeji kuje kudafa kayanku d'an babu wanda zansa yimaku girki"</p><p><br /></p><p>"A'a Ummie bawanan bane problem d'in" Hashem yace</p><p><br /></p><p>"Toh mene problem din?"</p><p><br /></p><p>Sai da Hasheem ya kalle Abdulnseer sanan yace" wanan narako, kibashi shawara kan Afrah"</p><p><br /></p><p>"Shawara kan mene fa"Ummie ta tanbaya</p><p><br /></p><p>Ummi na wallahi Afrah nada boyfriend" Abdulnaseer yace kaman k'aramin yaro</p><p><br /></p><p>"How d u knw that? Ko kataba ganinshi ne? "</p><p><br /></p><p>"Noo, ban tantaba ganinshi ba, kawai yanda taketamin magana ne Ummie"</p><p><br /></p><p>"Good, ai sai danace kabari nayi ma Mommysu magana, buh u said no, yanzo what d u want me to do? "</p><p><br /></p><p>"Addu'a kawai Ummie"</p><p><br /></p><p>Smiling tayi kana tace" Addu'a ai tin da kukazo duniya mukeyi maku, kuma zamuyita maku har illa masha Allah"</p><p><br /></p><p>"Shima wallahi Ummie duk bakinshi na qarya ne, d'an tanada saurayi har wani tsoro zaiji, sai kace ba *Abdulnaseer* dana sani ba"Hasheem yace</p><p><br /></p><p>"Nima abinda nagani kenan, abinda yace zaiyi kenan Amma yanzo yazo yana wani tunani, fitumata kawai zakayi a asalinka babu k'arya, kafitu mata yanda kake, inhar da alkhari komai zaizo cikin sauki"</p><p><br /></p><p>Dariya kadan *Abdulnaseer* yayi kana yace" xanbaku mamaki"</p><p><br /></p><p>"Kaba kanka dai" cewar Hasheem</p><p><br /></p><p>"Zan fad'ama Abbanku ma kasamu girlfriend" Ummie tace</p><p><br /></p><p>Sosa kai *ABDULNASEER*yayi sanan yace" Ummie please ki tsaya bayanzo ba"</p><p><br /></p><p>" toh shikenan, Allah tabbatar mana da Alkhari, musha bikin samari"</p><p><br /></p><p>"Ameen " duk sukace suna smiling, hira suka d'anyi kana Hasheem yama Ummie sai da safe tafito. </p><p><br /></p><p> Har jikin motan shi *Abdulnaseer* yarakoshi, sai da Hasheem din yashiga motan yazauna gana yace" friend don't worry pls, yanda nama Nusy kawai zakaita mata"</p><p><br /></p><p>Smiling *Abdulnaseer* yayi kaga yace"okay duk yanda ake cikin xakaji"</p><p><br /></p><p>"Oky, good night, Allah bamu Alkhari"</p><p><br /></p><p>"Ameen" *Abdulnaseer* yace, baibar wajen sai dataga fitar Hasheem daka gidan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kamar kulin tagama duk wani aikin datakeyi cikin gidan, shirye take cikin black abaya, simple makeup tayi applying amma sai tayi kyau sosai kamar ka gudu da ita</p><p><br /></p><p> Kallan ta Afifah tayi kana tace "wow gaskia Anty kinyi kyau sosai"</p><p><br /></p><p>"Thank you sweet sister, inkin gama shiryawa muje"</p><p><br /></p><p>"Okay toh" nan suka nufi wajen Mommy, sallama sukayi, sai da mommy ta amsa kana suka shiga cikin d'akin, gaisheta sukayi ta amsa, nan dai suka yimata sallama suka miqe</p><p> " *Afrah* Mommy takira sunanta, dawowa tayi ta zauna" gani Mommy"</p><p><br /></p><p>" kibi driver ya saukeki tunda kingana shiryawa"</p><p><br /></p><p>"Oky tohm, sai mundawo"</p><p><br /></p><p>" toh"kawai Mommy tace (dan mommy bata Addu'a... 😂) </p><p><br /></p><p>Hartakusa barin parlor ta tuno da phone dinta danke dakunsu jikin chaji, komawa tayi cikin sauri d'an daukan watan, missed calls tagani duk na *Abdulnseer* sai text daya turo mata, cire phone d'in tayi jiki chaji tabar dakin cikin sauri</p><p><br /></p><p> Sai da taciga mota ta bud'e message din kamar haka _smile can open heart faster than a key can open a door... So brighter the world with smile. GOOD MORNING BEAUTIFUL_ smiling *Afrah* tayi kana tasa phone d'in cikin jaka.</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Page 39-40_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Z*aune suke dukka su ukun a kapteria, phone din *Afrah* ne yai ta ringing batayi picking bah</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> Husnah ce ta kalle *Afrah* kana tace " babe kiyi picking mana"</p><p><br /></p><p>"Mayb Mtn ne" Zarah tace</p><p><br /></p><p>"Ba wani Mtn, tun kafin mu k'araso wajen phone din ke ringing, wulak'anci ne dai kawai irin namu na mata" Husna tayi magan tana daria</p><p><br /></p><p>Itadai *Afrah* duk bata tanka masu bah, call d'in ne ya k'ara shigowa, sauri Zarah tayi ta jawo phone din, yana gab da tsikewa tayi picking </p><p><br /></p><p>"Beautiful how are you?"abinda taji ance kenan, sai da ta kalla *Afrah* kana tace " hmmmm, ba ita bace, buh kakira anjima kad'an" Zarah tace, smiling *Abdulnaseer* kana yace " okay, thank you" ya katse kiran, Kallanta Zarah tayi kana tace" babe wai waye ne?" Nida nasani tinda naga batasan picking nasan wulak'ancin ne, kawai dan kinada wani Sulaiman sai akace kiyima kowa wulak'anci ,? ko kuwa shi Sulaiman d'in ansamaku rana ne?Ni na tsana wulak'anci wallahi" Husnah tace, ta k'arasa maganan tana jan tsaki</p><p><br /></p><p>"Ke bakisan reason d'inta ba" Zarah tace</p><p><br /></p><p>"Babu wani reason, yanzo mu in brothers d'in mu sukaje suna san wasu 'yanmata a nayi masu wulakanci zakuji dad'i? Koma dai menene yakamata taji mai zaice, in baiyi mata ba tamai explaining yanda zai gane"</p><p><br /></p><p>" ahhh kuma gaskiya ne, so babe kiyi magana kinyi shuru"</p><p><br /></p><p>Ajiyan zuciya *Afrah* ta sauke kana tace "wai fa shi so yake muhad'u kuma ni, bansan mai zance mai ba, besides inada boyfriend kuma duk kunsani"</p><p><br /></p><p>Ya mutsa fuska Husnah tayi kana tace" dan kina da boyfriend sai me? , ankawo gaisuwa ne, ko ansa rana? </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"OMG ina ganin drama a wajen nan ke Husnah dakike ta hura hanci menene naki, kodai yayanki ne? " Zarah tayi maganan tana daria</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" baki da kai, in brother ki a kama haka zakiji dad'i? Kawai yakamata taji dai mai zai cee ne"</p><p><br /></p><p>"Hakane, yakama kibashi chance yazo kuyi magana kiji mai zaice, in bai maki ba sai kiyi mai magana cikin, natsuwa, amma irin haka duk babu kyau kuma ke kanki kinsani"</p><p><br /></p><p>" toh shikenan, Amma ina zamu had'u? Dan ni banso yazo gidan mu gskia"</p><p><br /></p><p>Zaro eyes Husnah tayi sanan tace " wai duk kan Sulaiman kikewanan abu? "</p><p><br /></p><p>Hararanta *Afrah*tayi sanan tace" toh ina ruwanki? "</p><p><br /></p><p>"Da ruwana hadda tsakina ma"</p><p><br /></p><p>Dariya Zarah taitayi, ana cikin haka call d'in yakara shigowa, sai da *Afrah*ta kallesu kana ta kara wayan a kunnenta</p><p><br /></p><p>Daka can b'angaran *Abdulnaseer* yace " beautiful kina lfya? "</p><p><br /></p><p>"Alhamdulillahi" *Afrah* tace</p><p><br /></p><p>" masha Allah, kiyi hakuri na kiraki kina school"</p><p><br /></p><p>" Nooo, ba komai"</p><p><br /></p><p>Smiling yayi kana yace" when zamu had'u ko har yanzu baki sani ba? Yayi maganan cikin sanyin murya</p><p><br /></p><p>Kallansu Zarah tayi kana tace" kunji wai yaushe zamu had'u" tace a hankali yanda bazai jiba</p><p><br /></p><p>"Kice yau, Husnah tace</p><p><br /></p><p>Sai da tayi gyaran murya sanan tace" yau yayi? "</p><p><br /></p><p>Gyara kwanciyanshi yayi sanan yace" sosai ma, toh a ina? Wani time? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kallansu Husnah tayi tafad'amasu abinda yace a hankali</p><p><br /></p><p>" kice gidanmu" Zarah tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" hmmmm, gidan friend d'ina a marafa"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Okay, wani time? "</p><p><br /></p><p>"In muntashi school i'll call you"</p><p><br /></p><p>"Okay thank you so much princess, bari na barki sai zuwa anjiman"</p><p><br /></p><p>"Oky" tace ta katse kiran</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ko kefa dan Allah " Husna tace tana kai meat pie bakinta</p><p><br /></p><p>" dalla ni kibarni,Zarah yanzo gidanku xamu? Kina ganin Mama bazatayi magana ba? "</p><p><br /></p><p>"Ke karki damu ina mata explaining shikenan"</p><p><br /></p><p>"Allah dai ya kaimu nima sai naga *Abdunaseer* din" Husna tayi maganan tana yima *Afrah* daria</p><p><br /></p><p>"Kedai kikasani" *Afrah* tace. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Abdulnaseer* kam yana gama waya da *Afrah* side d'in Ummie yawuce, a parlor ya gansu zaune ita da Abbansu,k'ara gaidasu yayi kana ya zauna ya daria</p><p><br /></p><p>"Ikon Allah son kai kadai kana daria" Abba yace</p><p><br /></p><p>Smiling *Abdulnaseer* yayi mai kyau sanan yace" ai dole ne</p><p><br /></p><p>Zama Abba ya gyara kana yace" fad'amin naji"</p><p><br /></p><p>"Duk dai bazai wuce kan *Afrah* ba" Ummie tace</p><p><br /></p><p>" waye ita" Abba ya tanbaya</p><p><br /></p><p>"Girlfriend d'inshi"</p><p><br /></p><p>Murmushi mai kyau Abba tayi kana yace" masha Allah, yaron nawa ya girma har yafara neman aure, madallah, kun sasanta kenan? "</p><p><br /></p><p>"Ehh toh, yau dai zamufara had'uwa" yayi magan yana sosa kai</p><p><br /></p><p>"Ah ah dole kaita dariya kai kadai kuwa" Ummie tace</p><p><br /></p><p>Smiling kawai *Abdulnaseer* yayi</p><p><br /></p><p>" toh Allah tabbatar da Alkhairi, yasa ayi damu Allah kuma ya bada sa'a"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen Abbanmu"</p><p><br /></p><p>"Yauwa Allah maku Albarka ku dukka"</p><p><br /></p><p>"Ameen Abbah"</p><p><br /></p><p>"Kaje bedroom dina ka dauki 30k kad'an siyama surukan tawa chocolate" Abba yace yana daria</p><p><br /></p><p>" toh Allah saka da Alkhari"</p><p><br /></p><p>"Ameen, jeka kayi shiri da kyau" Ummie tace</p><p><br /></p><p>Fita yayi side d'in yana smiling yana k'ara jin san iyyayensu a ranshi, babu ruwansu yaransu kaman friends d'insu.</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 42-42_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shirye yake cikin milk color shadda dinkin irin na wayayin sanari da keji da kansu</p><p> Kasan cewarsa baki ne sai kalan kayan yamai kyau sosai, car Key din motan Ummie ya dauka yayi gaba, Ummie na binshi da Addu'a murmushi yake yana amsawa yafice</p><p><br /></p><p> Sai da ya tsaya a wani super market</p><p> yasiya mata uban chocolates da kayan kwadayi iri iri sanan ya dauki hanyan marafan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Su *Afrah*kam bayan sun tashi a school gidan su Zarah sukayi direct, a nape Husna sai kara karfafaa *Afrah*takeyi</p><p><br /></p><p>" wai kee hala dai kinsan *Abdulnaseer* dinan ne, sai wani zuga kikeyi a kanshi" Zarah tace</p><p><br /></p><p>Dariya sosai husnah tayi kana tace " ina fa kawai dai ina san shi da k'awata ne"</p><p><br /></p><p>Hararanta *Afrah* tayi sanan tace" kila ma 'yan uwa ne, wayasani"</p><p><br /></p><p>" zadai muzama 'yan uwan inkika aureshi"</p><p><br /></p><p>Haka dai Husna taita tsokanan, *Afrah* har suka iso gidan</p><p><br /></p><p> Da sallama duk suka shiga, a parlor suka tadda Mama da sisters din Zarah Khadija da Zeezee</p><p> Gaisheta duk suka ta amsa cikin sakin fuska</p><p><br /></p><p>" ya karatun? "Mama ta tanbayesu</p><p><br /></p><p>" Alhmdulillahi" duk sukace</p><p><br /></p><p>"Masha Allah, yau nan za ayi min wuni kenan"</p><p><br /></p><p>"Toh a'a gaskia" Zarah tace</p><p><br /></p><p>Kallanta mama tayi kana tace badake nake ba"</p><p><br /></p><p>" Mama saurayin Afrah ne zaizo tanan shiyasa mukazo"</p><p><br /></p><p>" ohhh madallah Allah kawo shi lfya, sai kuje ku shirya ai kan yazo din"</p><p><br /></p><p>Tashi sukayi duk kansu sulayi bedroom din Zarahn</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zama sukayi bakin gado yayin da Zarah tashiga toilet, bayan tafito Afrah ta kalla kana tace" babe kije kiyi wanka"</p><p><br /></p><p>" ni dan Allah karku dameni, kunbi kun isheni daka jin mutum yace zaizo, bazan yii bah" ta karasa maganan ta kwanciya</p><p><br /></p><p>"Haba babe, nifa bance kiyi kwalliya ba, wanka kawai nace"</p><p><br /></p><p>Haka Husna da Zarah sukai ta lallabata sanan tayi wankan, wani black abaya Zarah ta bata tasa, aiko kaman dan ita kayi yayi mata kyau sosai</p><p><br /></p><p>Husna da Zarah sai yaba kyauwun da tayi suke ita dai tayi banza da su</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ta kama shiryawa babu dadewa ABDULNASEER yakira yana wace(zarah tamai kwatance dama) </p><p><br /></p><p>" toh babe Allah tsare"Husna tace tana dariya</p><p><br /></p><p>" dallah ni kutashi kurakani" </p><p><br /></p><p>Babu yanda suka iya hakanan suka fitoh dan rakata</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana cikin mota, yana ganin fitowan su shima yafitoh, a hankali AFRAH ta 'dago beautiful eyes dinta ta kalleshi, baki ne amma ba sosai ba, yana da tsawo dan yafita sosai, fuskan shi tasha gyara iri na samari masuji da gayu da kuma naira, a gaskia ABDULNASEER yafi Sulaiman kyau sosai sai Sulaiman yafi shi haske</p><p><br /></p><p> Sai da ta matso kusa taga lafiyyan dimple dinshi wanda ko ita bata samu kamarshi ba, gawani irin eyes da yakedashi komai dai masha Allah </p><p><br /></p><p>Smiling yaketayi itama shidin takeyi, gaisawa sukayi da Husna da Zarah, cikin sakin fuska kamar ya dade da sanunsu, haka suka rakosu har parlorn saukar bak'i sanan suka basu waje</p><p><br /></p><p> Drinks da snacks AFRAH ta kawo mai kana suka faragai suwa, ya amsa yana kallon ta, batare da yasha ko yaci wani abu ba yashiga yi mata cewa</p><p><br /></p><p>" kaman yanda na fad'amaki sunana ABDULNASEER ABDULLAHI YALWA, mu biyu ne wajen parents dinmu ni da sister na Humairah, i think age mate dinkice tana ABU zaria inda take karanta mass. Communication, ni kam nagama degree na a Ghana sai nakoma turkey ina masters yanzo, nadawo hutu, buh soon zan koma"</p><p><br /></p><p>"Masha Allah Allah temaka"AFRAH tace</p><p><br /></p><p>"Ameen" ya amsa</p><p><br /></p><p>AFRAH! yakira sunanta</p><p><br /></p><p>Kallanshi tayi batare da ta amsa ba</p><p><br /></p><p>Shima shuru yayi kana yace" na ganki ina so, kuma da aure, ba da wasa nazo ba ko Allah yasani, har Ummie da Abbah duk sun sani, inaso kafin na koma mu daidai ta kanmu sosai, inyaso da nadawo many a su shiga ciki, amma yakika gani? "</p><p><br /></p><p>Tin da yafarra magana tayi shuru batace komai ba, batada kuma niyan magana wasa kawai da hannunta takeyi</p><p><br /></p><p>"AFRAH answer please, in kinada wanda zaki aura ne just tell me, answer me please "</p><p><br /></p><p>" Allah tabbatar mana da Alkhari" tace</p><p><br /></p><p>"Ameen Ameen wify, thank you so much, thank you very much" haka yaringa fada yana daria a hankali</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sai lokacin AFRAH tasan abunda tace ma'ana ta amince kenan, haushin kanta tafara ji wani side na zuciyan ta tace" yaron yanada kwarjini, baza ki iyacewa baki sanshi ba, toh ina laifin wanda yace yana sanka? Ai wuce komai a wajenka, kiyi Addu'a ne, Allah tabbatar da Alkhari dan Allah Allah zai zab'a maki mafi Alkhari cikinsu. Zuciyanta taji yai sanyi</p><p><br /></p><p>Kallanshi kanatace " zan tafi"</p><p><br /></p><p>Tashi shima yayi, kalan kayan da takawo mai tayi sanan tace"baka sha komai ba"</p><p><br /></p><p>" don't worry beautiful, akwai next time ai insha Allah"</p><p><br /></p><p>Batace komai ba sukafita</p><p><br /></p><p>Har jikin mota tarakoshi, sai da yashi yaga ledojin da yamata siyayya</p><p><br /></p><p>"Ohhh ga sakon Abbah tace nakawo maki"</p><p><br /></p><p>Kallan ledojin tayi kana tace" kabarsu na gode"</p><p><br /></p><p>"Banene na baki ba ai"</p><p>Sai da yaita bata hakuri sanan ta amsa gami da godiya tayi gida</p><p> Sai da yaga shigewarta sanan yaja mota.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A gida kam ganan lokacin da AFRAH ta saba dawowa yawuce yasa Mommy taitai masifa</p><p><br /></p><p>" wanan wani irin jarababen karatu ne? A tafi tin safe, amma haryanzu bubu ko alamar mutum"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wai ke Mommy toh mai zatamaki intadawo, bai sai taita zama a school din ba ita tasani ai"fatty tace</p><p><br /></p><p>"Girkin da nakeso ayi kee zakiyi? Tasani sarai nace zatayi girki yau shine ta tayi zamanta, toh ubanta zanci ai zata dawo gidan"</p><p><br /></p><p>"Hmmmm dan taga kina damuwa da girkinta neyasa take hakan, ki aika kawai wani restaurant a siyo maki"</p><p><br /></p><p>"Girkinta na manza da hofi, girkin banza, abinci kam ba zansiya ba tinda nada duk wani kayan girkin saitayi dan ubanta"Mommy tace tana hura hanci da baki😆😂😂</p><p><br /></p><p>" mommy ni natafi gidansu Aseeya"Faty tace tana gyara mayafin da ke kanta</p><p><br /></p><p>" babu gidan su Asiyan da zaki, baki da aiki sai yawo, bari Daddyku yadawo zan fad'a mai nagaji da halinki"</p><p><br /></p><p>"Nifa Mommy sai naje dan nariga nayi mata waya kuma tana jira na"</p><p><br /></p><p>" nace bazaki ba ko"</p><p><br /></p><p>"Ni fa Mommy bani nasa ranki yayi zafi ba, kawai kibari AFRAH ta dawo sai kimata, sai nadawo" tak'arasa maganan tana barin parlon. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Da ido Mommy tabita har tafita, tsaki taja Allah kadai yasan kalan hukuncin da zata ma AFRAH inta dawo. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>😂😂😂😂😂😂😂😂</p><p>Mommy kenan kima y'arki hukuncin kafin AFRAH</p><p><br /></p><p> Hoooooooooo san kai😏😏😏😏</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_PAGE 43-44_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>B'angaran AFRAH kan tana shiga ciki parlor duk ta taddasu hadda Mama, ledojin hannunta duk suka amshe gami dacewa "Ahh ba sauki</p><p> hadda tsaraba"</p><p><br /></p><p>"Kudai Allah yashiryeku wallahi daka ganin ledoji duk kunwani rud'e wallahi kar kutashi da shegen san abun duniya d'an baya kai mutun ko ina sai halaka da danasani"Mama tace</p><p><br /></p><p>"A'a Mama ba san abin duniya bane, kawai so nake naga komai" cewar Husna tana k'ara bude ledan</p><p><br /></p><p>" OMG kai gskiya angonmu yasan kan chocolates, Allah dai yabarku tare wallahi Mama shine wanda zata aura fa insha Allah"Zarah tace tana kai chocolate 🍫 d'aya bakinta</p><p><br /></p><p>"Masha Allah, Allah nuna mana lokacin yasa anyi damu" Mama tace</p><p><br /></p><p>AFRAH kam tinda zarah ta fara magana tashige bedroom din Zarahn d'an wani irin kunyan Mama taji. </p><p><br /></p><p>Dariya duk sukayi kana Zarah tace " Mama AFRAH fa kunya taji"</p><p><br /></p><p>"Lallai kina tare da wahala kuwa ni har uwarku ce kuma aminiyarku, kunya menene kuma tsakani? "</p><p><br /></p><p>" wallahi kuwa Mama ai mu babu ruwanmu" cewar Husna da ke bud'e wani sweet</p><p><br /></p><p>" wai bazaku bar kayanan haka ba? Ko nakune? Sai kace ku aka kawoma wa"</p><p><br /></p><p>Tashi sukayi sayi hanyan bedroom suna daria, bakin gado suka tadda ita har ta kaida kayanta da tazo dasu, harara ta watsa masu kana tace" wallahi ku dai kuncika magana, ba a tab'ayin sirri gabanku"</p><p><br /></p><p>"Haka muke amaryan ABDULNASEER" Husna tace</p><p><br /></p><p>Zarah kam dariya a boye can tace" babe yakika canza kaya kuma? "</p><p><br /></p><p>"Coz badasu nazo ba, yanzo sai wasu su zargi wani abu, ni muje kuraka ni, AFRAH tace</p><p><br /></p><p>" yes hakane kuma, toh wacan kayan fa? "</p><p><br /></p><p>" kuraba mana, nawa kikawo min school gobe indan Allah ya kaimu"</p><p><br /></p><p>"Oky Amarsu" Husnah tace tana daria</p><p><br /></p><p>Banza da ita AFRAH tayi d'an talura Husnah shegen tsokana ney da ita. </p><p><br /></p><p>Sunfito Mama bata parlor bedroom dinta suka shiga AFRAH da Husnah sukayi mata sallama,nasiha ta d'anyi masu gami da samasu Allah barka, sanan suka fitoh</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Dayake gidan su Zarahn babu nisa da titi bata jima ba tasami abin hawa, Husna sai tsokanar ta takeyi ita dai AFRAH hararanta kawai taketayi. </p><p><br /></p><p> Sai da AFRAH ta tafi sanan itama Hushan ta samu na uguwarsu tayi gaba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> K'arfe 5:46 AFRAH tashigo gidan nasu, tashiga parlorn da sallama zaune taga Mommy sai karkad'a kafafu takeyi</p><p> </p><p>" sannu da Gida Mommy"AFRAH tace tana kok'arin wucewa</p><p><br /></p><p>"Kee AFRAH! " MOMMY takirata</p><p><br /></p><p>"Na'am gani Mommy"</p><p><br /></p><p>" wai uban me kika tsaya yi a school ne? ni tin da nake ban taba ganin mayya kamarki ba, kina sane nace zakiyi min girki shine kikaje kikai zamanki watou ka banza ko? Toh wallahi ni na fi k'arfin ki kirani banza d'an arzikina da yarana kikeci a gidanan ke kanki kinsani gara ki bud'e idanuwanki da kyau kisan ke wacece kafin kice zayi fiddo da sabon salo, wanan ma ai rai ni ne duk abinda nake maki cikin gidanan bakigani ba ki daukeni a matsayin uwarki ba har ni zance zakimin abu kije kiyi zamanki saboda rai ni da wulak'anci watou na damu da girkinki bari ki wanani ko? Toh ko uwarki ta buga dani ta barni wallahi d'an ni nafi k'arfin duk wani munafiki wallahi, haka kawai ina bazan d'auka ba sam, gara ki canza inhar kinaso mu shirya dake" duk wanan maganan Mommy nayinsu ne cikin masifa da d'aga murya</p><p> </p><p> AFRAH kam tin da Mommy ta fara masifan take hawaye, shuru tayi tana sauraranta</p><p><br /></p><p>" wai badake nakeyi bane kinmin wani gum"</p><p><br /></p><p>Hawayen fuskarta ta share kana tace" kiyi hakuri Mommy insha Allah zan kiyaye kiyi hakuri"</p><p><br /></p><p>Baki Mommy ta tab'e kaga tace" nidai na fad'a maki, karatu kamar d'an kekadai akayi shii haba mutane nawane sukayi karatun kuma basuci gajiyan karantun ba? In ma da wani manufa kikeyi Allah sai yak'i baki saunawa akayi wanan muka gani da idanunmu"</p><p><br /></p><p>Ita dai Afrah batace komai ba tayi d'ankinsu. </p><p><br /></p><p> </p><p> Kaya ta canza zuwa mara nauyi kana tashiga kitchen,tana aiki tanajin karatun qur'ani Salamatu na tayata sai bayan magrab ta kammala duk sukajere a dinning hadda AFIFAH. </p><p><br /></p><p> Kasancewar ba sallah zatayi ba tad'an zauna a kitchen tana cin wani samosa da Afifah ta soya</p><p><br /></p><p>Kallanta Sallamatu tayi kana tace" auntymu nayi sallah naxo ki biya min karatun? </p><p><br /></p><p>"Ehh jekiyi sallan zanzo ma nasameki"</p><p><br /></p><p>Washe baki Salamatu tayi" kana tace Allah barmana ke antynmu"</p><p><br /></p><p>"Meyafaru naji ana magana ne" cewar Mommy da tashigo kitchen d'in</p><p><br /></p><p>"A'a Mommy AFRAH ce tace zata koyamin karatu, shine nake godia"harara Mommy ta watsa ma Salamatun, aikuwa sumsum tabar kitchen d'in kamar munafuka</p><p><br /></p><p> Sai dai Mommy tagama bud'e bud'e da rufe rufe da tsakinta kana tabar kitchen d'in, idanuwa AFRAH tabita tana mamakin sabon hali da Mommy ta fiddo dashi na zargi parlor takoma tana bin k'aratunta FATTY ce tashigo parlon babu sallama kamar dai yanda ta saba kashe karatun AFRAH tayi tana kallonta zubewa tayi saman kujera gami da cewa" wasss nagajii"</p><p><br /></p><p>"Sorry "AFRAH tace</p><p><br /></p><p>"Mommy fa d'an Allah?</p><p><br /></p><p>"Tana d'akinta tana sallah inaga"</p><p><br /></p><p> tazo yau akwai labari sister Aseeya dake India ne zatayi aure kalle pre_wedding pictures dinsu d'an Allah" Fatty tace tana nunama AFRAH</p><p><br /></p><p>"WOW masha Allah gaskia sunyi kyau sosai, amma mijin yafita kyau"</p><p><br /></p><p>"Wallahi kuwa ai ji nayi dama miji nane, Amma nasan ni mijina sai yafi wanan kyau da kud'i"</p><p><br /></p><p>Smiling AFRAH tayi kana tace "Allah sa haka"</p><p><br /></p><p>"Ai dole ne ma na aura mai kud'i d'an samari na duk masu kud'i ne"</p><p><br /></p><p>" toh Allah kaimu bikin musha rawan wooo" AFRAH tace tana daria</p><p><br /></p><p>"Ameen dai sisi, aike zakiyi mana abinci tinda zaki shiga catering school" tayi maganan tana dariya</p><p><br /></p><p>"Ai ba damuwa kafin Time d'in ai nima na bud'e na hab'aka d'an har sch zan bud'e nima nan gaba"</p><p><br /></p><p>"Lallai fa toh abincin fa yinin biki zakiyi bafa na dinner ba"</p><p><br /></p><p>Smiling kawai Afrah tayi kana tace bari naje d'akin salamatu zan koyamata karatu"</p><p> </p><p> AFRAH na k'okarin tace Afifah ta k'araso cikin farlon tana cewa" aunty Fatty kin siyomin shawarman"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ban siyo ba"</p><p><br /></p><p>Dama ai nasan basiyowa zakiyi ba, aunty Afrah d'an a ramin phone d'inki na tura pictures"</p><p><br /></p><p>Mik'amata phone d'intayi kana ta nufa d'an Salamatun</p><p><br /></p><p>Bedroom d'in Mommy Afifah tayi Fatty ma tabi bayanta. </p><p><br /></p><p> Dukkansu gan gado suka haye Afifah tashiga tura pictures yayin da Fatty keta zuba ma Mommy labari na bikin da za a na sister Aseeya</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Phone d'in Afrah ne yashiga ringing " laaaa yaya Sulaiman ne" Afifih tace gaban Mommy ne ya bada rasssss Afifah kam aguje tabar d'akin dan kaima Aftah phone d'in. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ke Fatima kina ganan babu komai tsakanin Sulaiman da Afrah kuwa?" Mommy tace</p><p><br /></p><p>"Mekika gani Mommy? "</p><p><br /></p><p>"Bakiga yanzo shine ya kirata ba kwanaki can ma ba k'iranta yayi da phone dinki ba? Sanan meyasa indai ana kiranta a gabanmu bata picking?"</p><p><br /></p><p>"Hakane kuwa wallahi, amma mai yaya Sulaiman zaimayi da ita? Ai yawuce da class dinta"</p><p><br /></p><p>"Kece kikasan wanan ai shiyasa kuke birgeni keda Hafiz kuna fahimtan abubuwa"</p><p><br /></p><p>"Ai toh haka kawai, AFRAH kam sai kin tashi tsaye a kanta"</p><p><br /></p><p>"Ina Wallahi ba zai tab'a faruwa ba sai duk tsiyar da za a sai dai ayi bazan tab'a yadda ba d'an yarona yafi k'arfinta wallahi, d'an ubanshi zan kirashi gobe naji"</p><p><br /></p><p>" eh wallahi karki sake ki yadda mommy"</p><p><br /></p><p>"Ki barni dasu zan fito masu a true color dina"</p><p><br /></p><p> Ranan Mommy ko baccin kirki barayi ba, wani tsanar AFRAH ne sabo fil ya shigeta wanda yafi na uwarta.</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 47-48_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*wanan shafin naku ney BIEBIE DEE NVL GROUP hakika bani da kamarku, ina sannku har cikin rai nah❤❤, Comments din ku nasani nishadi*💃💃💃💃💃💃💃💃💃</p><p><br /></p><p> *gaisuwa mai yawa gare ki second admin AUNTY BARAKA nagode Allah bar zuminci*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*N*umbern UmmuAbdulnaseer tashiga dialing ringing 2 ta dauka " Assalamu'alaykum" Ummu tace daka chan b'angaran</p><p><br /></p><p>"Wa'alaykissalam, gaisuwa sukayi kana Ummu tace" kina raina wallahi inataso inzo Allah bai banini iko ba"</p><p><br /></p><p>"Hakane dama komai sai Allah yayi ai, ina nan zuwa gobe insha Allah gobe zan shigo akwai maganan da nakeso muyi"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah kaimu da rai da lfya"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen"</p><p><br /></p><p>"Yarona bai dad'e da yabar nan ba ai yazo sallama, ashe har zai koma"</p><p><br /></p><p>"Ehh ya fada min zaizo dama"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah ya basu sa'a dukka, duk a gama karatun asha biki"</p><p><br /></p><p>"Aikuw dai Ameen" cewar Ummu, hira suka d'an tab'a kadan kana sukayi sallama. </p><p><br /></p><p>"Mommy wai dawa kike ta waya tinda na shigo?"Fatty tayi maganan tana k'okarin zama kusa da Mommy </p><p><br /></p><p>Gyara zama Mommy tayi kana tace" da Ummu Abdulnaseer ne, waman 'yar banzan yarinyan tana neman tadamin hankali ina zaman lfya"</p><p><br /></p><p>"Wakenan?"</p><p><br /></p><p>"Akwai wata y'ar ne bayan AFRAH? "</p><p><br /></p><p>"mommy please meye faru ne? "</p><p><br /></p><p>"ABDULNASEER yazu bakinan, wallahi ki rage wanan yawan naki Fatima inba haka ba kina can abubuwa zaita wuce ki"</p><p><br /></p><p>"Ohh Allah wajena yazo Mommy? Mai yace? Kai dama ban fita ba wallahi" </p><p><br /></p><p>Hararanta Mommy tayi kana tace" wajen ki? Kina hauka wallhy"</p><p><br /></p><p>"Mommy bangane ba please kimin bayani kince fa yazo wajen wa yazo inna niba? "</p><p><br /></p><p>"Wajen Munafukar gidanan AFRAH mana"</p><p><br /></p><p>Tashi tsaye FATTY tayi gami da cewa " wajenta? A ina yasanta tohh da har zaizo wajenta? Ai ita ba kalanshi bace ma"</p><p><br /></p><p>" dallah zauna" Mommy tace tana jan hannun Fatty</p><p><br /></p><p>Zama tayi tana wani kwalo idanu </p><p><br /></p><p>"Zuwa fa tayi har bedroom tacemin wai ABDULNASEER yazo, bata fad'amin tare suke bah sabida ita Munafuka ce sai shine yake fad'amin"</p><p><br /></p><p>Sauke ajiyan zuciya Fatty tayi kana tace" yanxo haka ganinshi tayi a hanya tace yadawo da ita, kinsan dai bazaice yana santa ba, inma ita sanshi takeyi bah kulata zaiyi ba dan koni ma bawani sakemin yake sosai bah kin dai san komai Mommy "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hakane zata aika taga batada saurayi shine wanda kike mu'amula da shi watou ta shige masa"</p><p><br /></p><p>"Ehh mana ai manufar ta kenan"</p><p><br /></p><p>"Toh k'aryanta gobe gobe zani gidan Ummun nasanar da ita nabama yarona kee, d'an nafiso kiyi aure inda zaki huta kaman ni ke harma kifini"</p><p><br /></p><p>Wani smiling Fatty tayi wanda har saida dimple d'in dole yafito wanda ban t'abaganinta da shii ba, rugume mommy tayi sosai kana tace"mommy insha Allah ai munyi kud'u mungama tin daka kan yaya Sulaiman har Afifah Wallahi nan gama ma sai kinfi haka, kin san dai yanda akeji engineers suke ai sa a ranki kawai ma muyi kud'i sosai, ita kuma Munafukar tana ganin tayi abinci sai ta k'are a shago"</p><p><br /></p><p>"Yauwa aini nasan duk yarana mai haifi fak'iri ba, ita kuma AFRAH ai gadon tsiya tayi d'an har ubansu yamutu yana k'arkashin Ubanku ne, so a haka zasu k'are daka ita har Abdulrahim din, aniyarsu tabisu munrika mayi masu nisa"</p><p><br /></p><p>"Yanzu sai gobe zakije wajen Ummun ko Mommy? "</p><p><br /></p><p>"Insha Allahu za'ayita ta k'are ba"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah kaimu goben lfya"</p><p><br /></p><p>"Ameenn Ameen"</p><p><br /></p><p>"Mommy dakika kira yaya Sulaiman maiyace maki wai? "</p><p><br /></p><p>"Bai ce suna soyayya ba, nidai nayi warning d'inshii d'an bazan yadda da wani Auran zumicin iskanci ba, yaro ba yafi k'arfinta wallahi"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dama Mommy ina wata AFRAH ina yaya Sulaiman ma?? AFRAH mai abinci da aiki a LAB wai zata bud'e restaurant nan gaba injita"ta k'arasa maganan tana wani d'an iskan dariya</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Da kud'in Uban wa zata bud'e restaurant d'in?"mommy tace tana b'ata fuska </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ina zansani mata, mommy keda kikesan girkinta sai kita siya"ta karasa maganan tana daria sosai</p><p><br /></p><p>"Ohhhh ni Bilkisu Allah kareni, nan da shekara 3 ai duk muyi nisa"</p><p><br /></p><p>"Wallahi kuwa, sai aita fama da shagon abinci"</p><p><br /></p><p><br /></p><p> hira sukaitayi duk dai zagin AFARAH da duk wani masoyinta sukeyi gajiya nayi na basu waje. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> AFRAH kam waya suka sha da ABDULNASEER abinta a bedroom d'insu batasan ma su Mommy nayi ba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Bayan ta gama wayan karatu tayi kasancewar sunada test gobe, ko a porlor ma itada AFIFAH keta hiransu Mommy da Fatty tsaki da harare harare suketayi ganin haka yasa tayi ma Mommy sai da safe tayi bedroom d'insu da harara Farty tabita har tabar parlorn. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mommy taso zuwa wajen Ummu yau amma kuma babu hali d'an Daddy yayi waya yana hanya babu yanda ta iya hakanan ta hakura da zuwa sai k"in Ummun tayi ta saidamata indai Daddynsu ya koma zatazo</p><p><br /></p><p> Babu yanda ta ita hakanan ta k'ira AFRAH tadawo gida da wuri Daddynsu zai dawo tazo tayi girki, d'an tasan ko sama da k'asa xata had'e Fatty bazatayi ba, toh mai ma ta iya? Daka taci sai nayi kallo taje gidan friends sufita yawo sai kuma bacci da chatting. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yauma ABDULNASEER ne yadawo da ita buh bai shiga ciki ba, masu gadi kuma babu ruwansu d'ansu ganin Mutuncin AFRAH sukeyi sosai Mommy da Fatty kam basu san halinda ake ciki ba. </p><p><br /></p><p> Tana shiga gidan a parlor taga Mommy gaishe ta tayi sanan tayi d'akinsu, mayafi da jaka ta aje kan bed tayi hanyan kitchen kasancewan ba sallah xatayi ba</p><p> Tana shiiga kitchen din cikin hanzari da kwarewa tafara shirya abubuwan da zatayi ai kafin 6 har tagama komai ta jeresu inda ya dace Sallamatu ta gyara kitchen d'in kaman ba ayi aiki a ciki ba, bedroom d'isu wuce tayi waka ta shiya cikn wani simple gown black color phone d'inta ta jawo tashoga chtn da yaya Sulaiman tana cikin chatting din ABDULNASEER yakira haka sukai ta waya har saida aka kira magrib sanan sukai sallama. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sai bayan Magrib Daddy yadawo har side d'inshi duk suka shi ga sukamai sannu da zuwa ya amsa masu cikin kulawa da sakin fuska, wanka yayi ya shirya cikin farar jallabiya fita yake shirin yi Mommy tace"inace a gida zakayi sallan isha'in"</p><p><br /></p><p>"A'a masjid xani"Daddy yace</p><p><br /></p><p>"Ba dawowan yanzu ba kenan? Nasan sai tunda yan koranan sunan kadawo bazasu barka kadawo da wuri ba"</p><p><br /></p><p>Murmushi Daddy yayi kana yace" Ai arziki ne"</p><p><br /></p><p>"Nidai dan Allah kashigo dawuri abincinka najiranka"</p><p><br /></p><p>"Toh insha Allahu indai basuzo da yawa ba ai ba jumawa zanyi ba"</p><p><br /></p><p>"Toh inma su dayawanne ai sai kabasu wani lokacin sudawo"</p><p><br /></p><p>"Hmmmmm Bilkisu kenan, ba ayima *D'AN ADAM* haka dankowa da anfaninsa, saina dawo" ya k'arasa maganan yana barin d'akin</p><p><br /></p><p>Wani kululun b'akin ciki ne ya tsaya ma mommy ta tsana masu neman temakonan ta tsana taka Daddynsu na kyauta tafiso komai yasamu ita da yaranta ko y'an uwa kar ya tuna dasu, haka dai mommy taita maganganunta da zage zage gajiya tayi da magana ita kadai tabar siden din takoma parlor. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sai 8:45 Daddy ya shigo</p><p><br /></p><p>"Sannu da dawowa Daddy" duk sukace Fatty, AFRAH da Afifah</p><p><br /></p><p>"Yauwa yaran Daddy sannunku" zama yayi nan Mommy tashiga zuba mai abinci already su duk sunci nasu sai wani b'ata fuska yakeyi tana gama zubawa yayi bismala yayi yafara kai loma tuwan semo miyan ogu da yaji nama da busheshen kifi, side din da AFRAH take ya kalla kana yace" wow my daughter naji dadin tuwanan dole Daddy ya bada kyauta"</p><p><br /></p><p>"Ehh mana wallahi Daddy Aunty Afrah ta iya abinci tafi kowa iyawa"Afifah tace</p><p><br /></p><p>"Shiyasa zan bata kyauta ai, hope kema kina zuwa kina kallan yanda takeyi?". </p><p><br /></p><p>"Ina zuwa Daddy sosai sai dai innaje islamiya"</p><p><br /></p><p>"Good kema za'a baki"</p><p>Afrah kam Murmushi taketayi tinda Daddy ya fara magana, mommy da Fatty kam wani haushen Daddy ne ya kamasu kan mai xai yabi AFRAH? </p><p><br /></p><p>"my daughter kindubu catering school din kuwa"Daddy ya tanbaya</p><p><br /></p><p>"Ehhh dama ina jiran saikadawo ne sai na fada maka"</p><p><br /></p><p>"Ai da kin kirani da ko transfer nayi maki kinyi registration din, amma zuwa gobe zanyi maki transfer"</p><p>. </p><p><br /></p><p>"Toh Daddy, nagode Allah saka da alkhari"</p><p><br /></p><p>"Ameen, ke Fatima bazakiyi ba kikace? "</p><p><br /></p><p>Turo baki tayi gaba kana tace" Ehhhhh Daddy ". </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Toh ai shikenan"</p><p><br /></p><p>"Daddy ni zanyi toh"Afifah tace</p><p><br /></p><p>"Nooo baby kibari sai zakije ss1"</p><p><br /></p><p>"Allah kaimu, Daddy naga kazo da sabon driver ne, waye shi? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Auu sai yanzu natuna, malam bukar ne, mota zai koyama Afrah tinda ita ke zuwa sch"</p><p><br /></p><p>Sai yanzu Mommy tasamuyin magana " magane ba, itama Fatiman kwanan nawa ne zata fara makarantan? Tare dai zasu koya"</p><p><br /></p><p>"Toh hakkan yayi" Daddy yace</p><p><br /></p><p>Haka dai sukai ta hira har 10:30 sanan yara duk sukayi masu sai da safe sukabar parlorn. </p><p><br /></p><p>Bedroom din Mommy Fatty tayi, Mommy na shigowa ta ganta kwance </p><p><br /></p><p>"Bakiyi bacci ba?"mommy tace</p><p><br /></p><p>"Inna zanyi bacci Mommy kina ganin banbancin da daddy yaso yayi"</p><p><br /></p><p>"Kar wanan ya dameki, zanyi maganin komai ai Azeezah da Maryam nanan shugowa kaduna nan da kwana 10(sisters din Mommy dake zaria) mota kuma babu abinda zata koya, ita har takai matsayin jan mota sai kace gidan Ubanta"</p><p><br /></p><p>"Yauwa Mommy gara kiyi maganin abun"</p><p><br /></p><p>"Karkidamu kiyi kallo kawai"</p><p><br /></p><p>Mommy na gama yin abinda zatayi a d'akin nata tayima Faty sai da safe tayi side din Daddy</p><p><br /></p><p>Sai da Mommy tayi mata wanan bayanin ranta yayi sanyi, sai da tayi chatting dinta san sanranta sanan ta aje phone din ta kwanta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kasan cewan yau Friday da wuri AFRAH tadawo da ka sch,zaune take a baranda waya takeyi da ABDULNASEER yanaso yazo tace yabari sai Sunday sai kaiwa da komowa Fatty keyi tanaso taji dawa AFRAH ke waya amma har tagama tsayuwarta bata gane ba.</p><p><br /></p><p> Bubu yanda ta iya hakanan ta hakura ta koma ciki, bedroom din mommy tasa kai babu ko sallama</p><p><br /></p><p>"Lafiyanki zaki shigomin daki haka? "</p><p><br /></p><p>"Mommy lfya mana, AFRAH nagani a baranda tana ta waya mayb da saurayinta ne"</p><p><br /></p><p>"Toh sai mai saurayinta d'in banxa da wufi,menene abin damuwa anan kuma? Keda zaki aura santalelen yazo ABDULNASEER ga kyau ga kud'i"</p><p><br /></p><p>"Hakane toh naga har yanzo bakije bane, bansan madafar da nake ba"</p><p><br /></p><p>"Dawowan Daddynku ne ya hanani zuwa itama Ummun nasan sabida Daddynku na gari yasa bata zoba, amma ai Satuday daddynku zai koma dan zaije benin"</p><p><br /></p><p>"Oky randa ya koma zakije kenan? "</p><p><br /></p><p> " insha Allahu"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah kaymu"Fatima tace</p><p> </p><p>" Daddynku fa?"</p><p><br /></p><p>"Yana can side dinshi y'an koro da y'an neman k'arin jali suncika gida"</p><p><br /></p><p>Tsaki Mommy tayi kana tace"nagaji da wanan masifa babu da ma yashigo gari duk a cika ma mutum gida da marak'a kala kala"</p><p><br /></p><p>"Wallahi nima haushi suke bani, nafiso naga manya mutane mazuwa wajen Daddy ba wanan masu uban yawan ba, dan munafunci har gaidasu Afrah keyi Afifah ma na tayata" </p><p><br /></p><p>"Suna ina ne ma? "</p><p><br /></p><p>"Baranda" Faty tace tana danna wayarta</p><p><br /></p><p>Tashi Mommy tayi dan zuwa wajensu,kafin takai bakin k'ofa tahad'u da Abdull zai shigo, k'arasu inda take gasheta yayi cikin girmamawa babu laifi Mommy ta amsa d'an shii bata cika jij haushin shii ba kaman AFRAH</p><p> Tashi yayi na nufa side su"ka kiramin su AFRAH " tace da shii Abdull ya amsa da toh, sai da yafad'ama AFRAh da Afifah kana ya shiga siden nasu. </p><p><br /></p><p> Suna shiga Mommy tafara masifa mara dalili mara lissafi ita dai AFRAH batace komai ba tayi kitchen dan had'o ma yaya Abdul Abinci, tana zuba komai ta jere a tray tayi d'ankin Yayan nata da shii Afifah na biye da ita. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Daddy bai natsu ba sai bayan sallahn isah'i zaune sune dukkan su a Parlor suna cin abi ci bayan su gama gyara wajen AFRAH tayi tas </p><p><br /></p><p>sai Daddy yasan duk aninda yaran zasu buk'ata yabasu sanan aka daura da hira, 11:00 duk suka ma iyayen nasu saida safe kowa ya wuce d'an kwanciya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da sassafe Daddy yabar gidan d'an zai fara biyawa katsina ya gaida Inna daka can jirginsu zai tashi, addu'a duk suka mai ya amsa gami da samasu albarka. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kafin 12 na rana Mommy ta gama shirin ta tsaf cikin wani arnan lace kalan milk n pink tayi kyau sosai komai na jikinta mai tsada ne da kaganta kaga matan manya, car key d'inta ta dauka tama Fatty sallama tayi gaba, sai addu'a Fatiy ketayi mata.. (Basaban ba😂😂) </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana isa gidan Ummu ta amsheta da murna da sakin fuska nan da nan aka ciga gaban Mommy da kayan Motsa baki iri iri</p><p><br /></p><p>"Ina daughter na ne bata dawo weekend bane? Mommy ta tan baya</p><p><br /></p><p>"Ta dawo amma tana gidan *Aunty Baraka*sistern Abbansu"</p><p><br /></p><p>"Oky yarona ma bayanan?"</p><p><br /></p><p>"Yaronki yaje gidan Aminin shi Hasheem, mayb yadawo kan kitafi"</p><p><br /></p><p>"Oky ai wajen shi nazu dama, albishir zanmai"</p><p><br /></p><p>Daria Ummu tayi kana tace "tinda bai nan ai sai ni a fad'amin"</p><p><br /></p><p>Daria itama Mommy tayi kana tace"mata na mai a gida na tazo yabani tukwici"</p><p><br /></p><p>"A'a tsohun zance tin yaushe yaje suka dai daita da AFRAHN, babu yanda banyi da shi ba yabari naxo na sameki amma fir yak'i wai sai sun daidai ta kan su, yanzu daya dawo zamuxo neman aure"Ummu ta k'arasa maganan tana murmushi</p><p><br /></p><p>Wani irin juyi kan Mommy yayi wanda bata tab'a jin irinshii ba....duhu take gani gawani zufa data fara duk da Ac dake aiki</p><p><br /></p><p>"Hajiya yakikayi shuru? Ko bakisan zancen bane?"</p><p><br /></p><p>Natsuwarta na nemu gami da gyran murya kana tace" Basan Wanan zance ba ni, ina maki maganan y'ar wajena Fatima ne"</p><p><br /></p><p>"Ohhh Allah sarki, toh ai shi yaron Naki sun dai daita da AFRAH ai duk d'ata ne tunda duk ta wajenki suke kuma duk yaranki ne ai"</p><p><br /></p><p>Gyaran Murya Mommy ta sake sanan tace " wallahi har ga Allah da Fatima na so shi coz ita ma ABDULNASEER din ya kwanta mata"</p><p><br /></p><p>"Ikon Allah duk wanan bai taso ba tinda shi ya zaba da kanshi, ai Alhmdulillahi Da yadawo za'a zo ayi magana d'an yakusa kammala wa"Ummu tace</p><p><br /></p><p>Gaba d'aya Mommy tafara jin haushin ta, tagaji da jin duk wani maganan ta kuma tasan Ummu ta fahinceta na san a maida neman kan Fatima, amma sai wani daliyewa takeyi wai ita wayayyiya, tashi Mommy tayi gami da cewa "bari naje hajiya"</p><p><br /></p><p>", tun tanzu muna hiran abin arziki" </p><p><br /></p><p>Musmushin dole Mommy tayi kana tace" dama ba dad'ewa xanyi ba, zancen nan ya kawo ni tinda har sun dai daita kansu ai sai muje mufara shiri" ta k'arasa magnan tana daria</p><p><br /></p><p> Kallanta kawai Ummu keyi d'an maganar dabtayi fad'a kawai tayi bawai yakai zuci ba, har mota Ummu ta rakota kana takoma tana mamakin hakin hajiya Bilki na san kai da banbanci..... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_bye wallahi nagaji_</p><p>_insha Allahu zan cigaba gobe, amma sai Allah yabani sa'a_</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 45-46_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka kawai yau bata sake jiki suyi waya kamar yanda suka saba ba, da ta tuno yanda sukayi da Mommy sai taji gabanta ya fad'i bayan sungama wayan Mami ta kira sallama tayi cinkin sanyin murya take magana</p><p><br /></p><p>" yanaji voice d'iki haka? Meke faruwa? Mami ta tanbaye ta</p><p><br /></p><p>"Babu komai Mamina"</p><p><br /></p><p>"Oky koma dai menene kiyi hakuri *wata rana*(asmy b aliyu) sai labari"</p><p><br /></p><p>"Toh Mami insha Allah" nan AFRAH ta kwashe duk yanda sukayi da ABDULNASEER ta sanar da ita</p><p><br /></p><p>Shuru Mami tayi sai can tace " ya zakiyi accepting mutane biyu a lokaci d'aya? Baki san babu kyau ba"</p><p><br /></p><p>" Mami wallahi na kasa cema ABDULNASEER d'in a'a ne ni kai na bansan dalili ba Mami sai da nace naga ban kyauta ma kai na ba"</p><p><br /></p><p>"Kar kidamu addu'a kawai shine abinyi. Nima zan k'ara kan wanda nakeyi"</p><p><br /></p><p>"Kuma inga Mommy... " sai tayi shuru </p><p><br /></p><p>"Na sani, aina sane da ita sarai ai ita bata isa ta hana abin da Allah ya dad'e da shiryawa ba inhar baki aura Sulaiman ba dama ba mijinki ba ne, kingane"</p><p><br /></p><p>"Eehh Mimi"</p><p><br /></p><p>"Yauwa ki cire wanan tunanin a ranki kidai dage da addu'a kawai"</p><p><br /></p><p>"Insha Allahu" sallama sukayi da Mamin tacigaba da wayan da su Fahad d Arfah sai labari suke bata tana daria</p><p><br /></p><p> </p><p> ABDULNASEER kam kiran ta yaketayi amma sai call waiting yakeji hakanan ya gaji da kira sai text ya tura mata kana ya kwanta</p><p> Ko da suka gama wayan da su Arfah data karanta text d'in smiling kawai tayi a k'asan zuciyan ta tanajin wani dad'i. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kamar kulin ta shirya tsaf cikin riga da skirt na atanfa tayi kyau sosai, d'ankin Mommy tayi d'an yimata sallama</p><p> Da sallama ta shiga d'akin gaisheta tayi Mommy ta amsa a dak'ile</p><p><br /></p><p>"Tanbaayan ki zanyi,kuma ki fad'amin gaskia "</p><p><br /></p><p>"Tohh Mommy Afrah tace</p><p><br /></p><p>"Sulaiman yace yana sanki ne?" Ta k'arasa maganan tana zuba mata idanu</p><p><br /></p><p>Xaro big n beautiful eyes d'inta tayi kana tace " niii kuma Mommy? "</p><p><br /></p><p>"Jeki kawai sai kindawo"</p><p><br /></p><p>Barin d'akin AFRAH tayi da sauri tana sauke nunfani da sauri da sauri, girgiza kai tayi kana tace " zan iya kuwa?" Hakadai taita tunani har tazo titi</p><p> Agogon hannun ta ta duba ganin kamar zatayi latti gashi bata samu abun hawa ba, kamar daka sama taji yace" beautiful" kallanshi tayi sanan ta dauke ido smiling tayi sanan yafito. </p><p> Bud'e mata gidan gaba yayi sai da yayta lallashi sanan tashiga. </p><p><br /></p><p> Tinda ta gaisheshi bata k'ara magana ba har yayi parking, kallanta yayi kana yace" wani time zaku tashi?"</p><p><br /></p><p>"Basai kazo bah zan koma da kaina"</p><p><br /></p><p>"Please sweetheart" ABDULNASEER yace kaman zaiyi kuka</p><p><br /></p><p>Smiling tayi mai kyau kana tace " don't worry inna koma gida i'll call you "</p><p><br /></p><p>"Are you sure? "</p><p><br /></p><p>"Yes sure"</p><p><br /></p><p>"Oky take good care of yourself"</p><p><br /></p><p>"I''ll" tace gami da barin motan</p><p> ABDUMNASEER bai bar bakin gate d'in ba sai da yadena gananta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Dubai_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zaune yake yana cin pizza🍕 yana kallan wani movie phone d'inshi ne yashiga ringing ganin mai kiran yasa shi wani irin murmushi </p><p><br /></p><p>"My Mommy i miss you" Sulaiman yace</p><p><br /></p><p>Daka can b'angaran zama Mommy ta gyara kana tace " i miss you more my son"</p><p><br /></p><p>Smiling Sulaiman yayi sanan ya gaidata, batare da ta amsa ba tace" tanbayanka zanyi kana jina"</p><p><br /></p><p>Gabanshi ne ya d'an fad'i can kuma yace" ehh ina jinki Mommy nah"</p><p><br /></p><p>" menene tsakaninka kai da AFRAH!? "</p><p><br /></p><p>Faduwa wayan takusa yi saboda wani faduwa da gabanshi yayi</p><p><br /></p><p>"Ba da kai nake magana ba ne"</p><p>.</p><p><br /></p><p>"Da ina ne, kee Mommy mai kika gani? "</p><p><br /></p><p>" ina ganin wasu abubuwa ne da ban tabbatar ba, toh kasani inma akwai alama santa a zuciyar ka to kacire shii d'an bazan taba yadda ba kai kafi kowa sanan halina"</p><p><br /></p><p>"Ajiyan zuciya yasauke kana yace " toh Mommy duk meye yakawo maganan nan kuma? "</p><p><br /></p><p>"Oho nidai na fada in bahaka ba ran kowa zai baci wallahi" kittttt ta kashe wayan</p><p> Da ido yabi wayan yarasa wani irin uwa Allah yabasu, wanda bata san darajan y'ayan wani bah sai nata wanda bata sai mezai faru nan gaba bah, wanda batasan ba'ayima Allah shishigi ba wani tausayin AFRAH ne ya k'ara kamashi numbern Inna yashiga dialing ringing 3 Inna ta dauka " Allah k'ara maki tsawan rai yaaa hajjahu" Sulaiman yace</p><p><br /></p><p>Dariya Inna tayi anata b'angaran kana tace" tare da kai babban mai gida, ya karatun? Ya larabawa da turawa? "</p><p><br /></p><p>" duk lfyalau Alhamdulillahi" yace yana daria</p><p><br /></p><p>"Madallah Allah temaka ya kuma bada sa'a"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen Innarmu ta kanmu"</p><p><br /></p><p>Shuru Sulaiman yayi bace komai ba Innace ta katse shurun dacewa" maigida akwai magana bakinka fa, gara kayi magana kafin na kashe wayana"</p><p><br /></p><p>"Matsalana dake kenan sababi, mekikeci na baka na zuba? Inkinsa hakuri ai zan fada maki ne"</p><p><br /></p><p>"Tohh inajii ka"</p><p><br /></p><p>Nan Sulaiman ya kwashe duk yanda sukayi da Mommy yafad'a mata shuru Inna tayi na minti1 kana tace" kadai cigana da Addu'a in ita AFRAH matarkace babu makawa dole ka aure ta duk yanda taso da k'in aure a tsakaninku indai Allah yaso batada yanda zatayi d'an haka kacigaba da addu'a Allah yamana jagora Allah kuma ya tabbatar mana da duk abinda yafi alkhari"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen Innah nagode hajjajuwa"</p><p><br /></p><p>"Yauwa aita hakuri dai *wata rana* sai labari lamarin Bilki sai addu'a"</p><p><br /></p><p>"Hakane Insha Allahu Inna"</p><p><br /></p><p>"Yauwa Allah yamaku albarka dukkanku"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen" sallama sukayi Inna nata samasu albarka, smiling yayi sosai wani sanyi yaji a ranshi ko babu magana mai dad'i ma wani abu ne pizzan shi yacigaba daci yana kallan movie Muhammad ne yashigo nan zama yayi shima yana kallan movien.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>B'angaran AFRAH da ABDULNASEER kam Alhamdulillahi kula yake bata bana wasa bah duk wani al'amurorinta sa kanshi yakeyi, itama yanxu ta saba dashi d'an ABDULNASER is a very friendy person gashi wayayye da shi duk ya saba da su Zarah muktar haka suma. </p><p><br /></p><p> Sulaiman ma yana iya nashi amma ko kad'an bai taka k'afar ABDULNASEER ba yana daidai nashi, ita kam AFRAH addu'a take sosai Allah zaba mata mafi alkhari cikinsu. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Abu buwa nata faruwa time nata tafiya toh dama haka rayuwar take.</p><p> Haka takasance da Mommy na baza murki cikin gidanta, sai fitoh sa sababin hali takeyi na yau da ban na gobe da ban d'an cikin watanin nan DADDY yasamu cigaba fiye da yanda kuke zato buri mai girma ta d'aura kan yaranta Farty ma hakance takasance da ita k'awaye iri iri mulki babu irin wanda basuyi a cikin gidan shiyasa AFRAH ta yanke hukuncin ansan kudi taje tayi registration na catering sch ta huta da zaman gidan gaba d'aya.</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>Kallanta ABDULNASEER yayi kana yace " yau zanzo daukanki school"</p><p><br /></p><p>"Ni kabarshi basai kazo bah fa" Afrah tace</p><p><br /></p><p>"Meyasa toh? Ko bakiso Mummy tasan muna datting ne? "</p><p><br /></p><p>"Noooo ni haka kawai"</p><p><br /></p><p>"A'a dole da reason"</p><p><br /></p><p>"Toh nidai babu" AFRAH tace tana turo baki</p><p><br /></p><p>"Toh naji, inaso innakai ki na shiga nama Mommy sallama ne, kinsan saura 5days na koma sch, kuma akwai wuraran da zani shiyasa nakesan shiga yau, amma inbakiso yau sai nafasa"ya k'arasa maganan yana kallanta</p><p><br /></p><p>"Ohhh shikenan Allah kyaumu anjiman"</p><p><br /></p><p>"Ameen sweetheart " sallama sukayi kana tashiga school </p><p>Sai da yaga shigarta school ya juya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p> Ai kam suna gama lectures AFRAH ta k'irashi ta sanar dashi bai wani jima sosai ba ya k'araso, sai da suka sauke Husnah da Zarah gidanjensu kana sukayi gidansu AFRAH hira sukai tayi harsuka iso, horn yayi maigadi ya bud'e gate yashigo ko gama parking baiyi ba AFRAH tafice da idanu yabita, sai da ya k'ara kin tsawa sanan yafitoh</p><p><br /></p><p> AFRAH kam tana shiga Bedroom mommy tashiga dayasha uban gyara kamar ta sabuwar amarya, amaryanma masu hali d'an ankashe ma bedroom d'in kud'i bana wasa ba. sannu da gida taiyi mata kana ta bar d'akin. </p><p><br /></p><p> Jinta shuru har na tsawan minti15 yasa shi k'iranta</p><p><br /></p><p>"Sweetheart kinbarni waje kizo kishiga da ni mana"</p><p><br /></p><p>Dariya tayi k'adan kana tace" am sorry ganinan"</p><p><br /></p><p>Wajen Mommy takoma tasanar mata cewan ABDULNASEER yazo yana compound(bata fad'a mata tare suke ba... Ko mai yasa?) </p><p><br /></p><p>"Jeki shigo dashi bari nafito parlorn yanzu"</p><p><br /></p><p>Kafin sun shigo har Mommy ta fitoh parlorn </p><p> Da sallama duk suka shiga " ahh lalelale da son d'ina zauna mana ka tsaya" Mommy tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kitchen AFRAH tayi da kawo mai kayan motsa baki, babu jumawa kuwa tashiga parlorn da tray hannunta ajewa tayi gabanshi tayi d'akinsu</p><p><br /></p><p> Gaisheta ABDULNASEER yayi Mommy ta amsa cikin fara'a da sakin fuska " ashe har tafiyan ta matso" mommy tace</p><p><br /></p><p>"Ehh Mommy " ABDULNASEER yace yana murmushi</p><p><br /></p><p>"Toh Allah ubangiji ya bada sa'a yasa agama lfya"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen Mommy"</p><p><br /></p><p>"Ya Ummu take da daughterna Humairah? "</p><p><br /></p><p>"Duk lafiyalau, Humairah na school Ummie tana gaidaki sosai"</p><p><br /></p><p>"Masha Allah ina amsawa, ai munyi waya jiya ma"</p><p><br /></p><p>"Okay Mommy bari nawuce, dama nace bari nazo gaisheki kuna maki sallama tin yau dan inada inda zani da yawa"</p><p><br /></p><p>"Ahh nagode sosai sosai my son, bakaci komai ba"</p><p><br /></p><p>Smiling ABDULNASEER yayi kana ya d'auki cake guda d'aya sai ruwa da yasha k'adan bayan yagama ne yace" mommy bari na wuce"</p><p><br /></p><p>"Wai har ya isheka my son? "</p><p><br /></p><p>"Ehh mommy Alhamdulillahi"</p><p><br /></p><p>"Toh gashi har zakawuce baku had'u da mutuniyar taka ba batanan"</p><p><br /></p><p>Smiling yayi d'an shi har ga Allah baisan wa take magana ba kuma yasan maida wata mutuniya inba AFRAH ba "ai tare da AFRAHN muke, tare mukazo ai Mommy "</p><p><br /></p><p>Wani abu Mommy taji duumm a ranta wani bak'in ciki da haushe duk ya kamata a lokaci d'aya, </p><p><br /></p><p><br /></p><p> daurewa tayi ta k'akalo murmushi sanan tace "Fatty nake magana"</p><p><br /></p><p>"Ohh kigaisheta inta dawo" yayi maganan yana sosa kai</p><p><br /></p><p> Har jikin motanshi ta rakoshi kana takoma ciki da tunani barkatai. </p><p><br /></p><p> koda ABDULNASEER zai tafi bai nemi AFRAH ba tafiyanshi yayi da niyar inyakoma zai kirata, haka dai ABDULNASEER yabar gidan cikin farin ciki. </p><p><br /></p><p> Mommy kam tana shiga parlor ta zauna jabar a kujera tanbayoyi taketayi ma kanta marasa lissafi wanda batada amsarsu "toh ma a ina shi yaga AFRAN? </p><p> Yaushe da yaushe suka saba da har zai kawota gida? </p><p> Ko dai santa yakeyi ne? </p><p> A'a Mommy tace a fili, wani dabara ne ya fad'o mata na k'iran Ummu Abdulnaseer din na sanar mata nata k'urin game da yaran nasu. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_toh sweethearts!!_</p><p><br /></p><p>_Kuna ganin UMMU ABDULNASEER din zata yadda?????_</p><p><br /></p><p>_ina jiran amsarku_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Much love for u all sweethearts*❤❤❤❤ *sai an d'an kwana 2*</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Thank you so much for d preys i really appreciate_ </p><p> _Much love for you all_💋❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 49-50_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A wahalce Mommy ta iso gida wani irin haushin Ummun takeji wanda batasan iyakarsa ba, ganin zaman cikin motan bazai fisheta ba yasa ta fitowa jiki a mace ko band bag dinta bata dauka ba tabar motan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bedroom din ta tayi direct kan bed taga Fatty kasancewar yau bata je ko ina ba, ta tsaya jiran yanda sukayi da Ummu(lol) ganin Mommy tashigo a jigace yasata tashi zaune matsowa kusa da Mommyn tayi sosai kana tace" Mommy meyafaru? Ya naganki haka? "</p><p><br /></p><p>Wani wawan tsaki Mommy taja kana tace" yayaa nema baza kiganni ba, yarinya tazamemin annoba da masifa a gida duk wani hanya da nabi nasa k'afa sai tasa wanan wani irin masifa ne? "</p><p><br /></p><p>"Mommy wai meyafaru ne? Kimin bayani yadda zan gane"</p><p><br /></p><p>Kallan ta Mommy tayi sosai kana tace" toh ABDULNASEER da AFRAH sun dai dai ta kansu"</p><p><br /></p><p>A haukace Fatty ta tashi bakinta na rawa tace" Wai da gske kikeyi Mommy kodai wasa ne? "</p><p><br /></p><p>" dan ubanki zan maki wasa ne? Inma wasan zanyi sai insaka AFRAH ciki? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wani kuka Fatty tasaka gami da zubewa a k'asa</p><p><br /></p><p>"Kibin shuru karki k'ara b'atamin rai wallahi"</p><p><br /></p><p>"Dole bayi kuka mommy AFRAH da bata kama k'afata a kan komai ba har zanso abu tasamu ni narasa, wai Mommy maiyasa baki ma Ummun bayani sosai ba, kuma a ina suka had'u sa AFRAH ma"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Rugumuta Mommy tayi gami da share hawayan fuskanta" kiyi hakuri kinji, ni kai na bansan ina suka had'u ba, zancen bayani kuma duk nayima Ummun kawai batasan laifin yaron ta ne"</p><p><br /></p><p>"Toh shii yama rasa wa zai so sai AFRAH? Itama Ummu dan batada Mutunci ta kalle tsabaragen idanunki tace wai sun daidaita da AFRAH wanan ai cin fuska ne"</p><p><br /></p><p>" hmmmm ke da baki wajen kenan Fatima, bazan iya fad'amaki irin tashin hankalin da na shiga ba, nayi bak'in ciki ba d'an kadan ba wallahi ban tab'a tunanin wani Mutumin arziki mai abin duniya da asali zai so wanan yarinyan ba"</p><p><br /></p><p>"Nafiki bakin ciki Mommy wallahi inasan ABDULNASEER ina sanshi sosai wallahi kuma dani ya dace ba wanan banziyan Afran ba wallahi" tak'asa maganan tana kuka mai cin zuciya</p><p><br /></p><p>"Kiyi hakuri Fatty nima cikin bak'in cikin nake wallahi, insha Allahu yanda tasaki kuka nikuma tasani cikin bakin ciki da yaddan Allah itama sai tayi kuka, Auransu da ABDULNASEER bazai zame masu komai ba sai masifa da bala'e insha Allah"(Mommy da Father kenan wayace maku Allah na amsan muguwar addu'a?? 🤣🤣😂😂) </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Jan majina Fatty tayi kana tace " toh menene abinyi yanxo Mommy? Dole ni ki dakatar da auranan duk murasa gaba d'aya, taya ma AFRAH Zatayi aure ina kallo bayan na girmeta? Kuma sanan ta aura mai kud'i? Ai wanan rayuwa bai dace da ita ba sam gaskiya kisan abinyi"</p><p><br /></p><p>Shuru mommy tayi tana nazarin maganganun fattyn can tace" kiyi magana mai kyau dole kuwa na tsayar da zancen auranan yanzo dai mubari Azeezah da Nana Suzo duk sai musan abinyi, ko madai zaki shirya muje zarian ne gobe? "</p><p><br /></p><p>"A'a nikam bazani wani zaria ba kaje kaita wahala wanan gari da shegen zafi ga yan sa ido"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ai ke bakida mutunci, kice kawai bazakije ba, basai kin zage mahaifata ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Allah baki hakuri, naga dai kaman yau ne su auntyn zasu zo basai mujira subah"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Toh ai shikenan dama naga kindamu ne shiyasa nace haka, tinda kince haka Allah kawosu lfya"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ameen, bari naje nacima Munafukarnan mutunci"Fatty tace taba barin bedroom d'in. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>" ehhh jeki kimata naki kafin nazo nayi nawa, yarinya tazamar mana masifa kamar uwar ta"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>B'agaran Ummu kuwa mamaki ne fal a zuciyanan bayan ta dawo daka raka Mommy parlor ta zauna har yanxo mamaki takeyi, Sallam Humaira da *Aunty Baraka*ne ya dawo da ita daka duniya tunanin da ta wuce</p><p><br /></p><p>"Ummie tunanin mekikeyi haka? "Aunty baraka ta tanbaya</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hmm kibari kawai Auntynsu, indai kana duniya bazakadena ganin abin al'ajabi ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hakane kuwa wallah" gaisawa sukayi cikin mutunci da girmama juna, Humairah ma ta gaida Ummie</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ina yaya ne? "Humairah tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yacemin xaije gidansu Hasheem, maybe yakusa dawowa</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"D'an nema ai har gida yazo yasameni wai yayi mata"Aunty Baraka tace tana smiling </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Aikuwa yasamu AFRAH yarinyan wata kawata hajiya Bilki"</p><p><br /></p><p>"Masha Allah Allah tabatar mana da alkhari"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ameen hajiyan bata dad'e da barin nan bama"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ikon Allah babu rabun zamu had'u"</p><p><br /></p><p>"Ummie wai Mommy? "Humaira tace</p><p><br /></p><p>"Ehhh maza kije bedroom dina kik'arasa jeremin kaya a drawer"</p><p><br /></p><p>Bayan Humaira ta wuce ne Ummie ta labartama Aunty Baraka yanda sukayi da Mommy</p><p><br /></p><p>"Hooooooo mu mata munsha uku, kiga sankai a baiyane in banda abita abinda yayi AFRAH ai shine yayi Fatiman"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ke kikasan wanan ai ita a san ranta tafiso nace toh zan sashi ya janye neman AFRAh sai yakoma ma yarta kuma ni ace ma na zaba acikin su biyun ai AFRAH xance d'an tafi natsuwa da kamun kai ga girki iri iri da ta ita Fatiman kam kusan kulin naje batanan inkuwa tanan bantaba ganinta tana wani aikin ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Allah kyauta kam mudai abida yaronmu yakeso shi mukeso, tun suna yara mukemusu Addu'an samu mace ta gari cikin yaddan Allah gashi yakawo sai dai mujira lokaci"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Allah kaimu lokacin lafiya ita kuma Allah shiryeta da masu irin halinta, Amma ban taba </p><p> Zaton haka take ba wallahi tabani mamaki sosai"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ameen toh Amma su matan ma kikaji halinsu ai ko kare baxai ci ba, kawai dai Allah k'ara shiryar damu"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Amern dai"hakadai sukaita hiransu da al'ajabin Mommy. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sa kai kawai tayi a cikin d'akin babu ko sallama kamar yanda ta saba</p><p><br /></p><p>"Wai ke anty Fatty nan ba Daddy yace kirika sallama a waje ba"Afifah tace tana murguda baki</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Toh banga damar yi ba wawiya wanda bata san ciwan y'ar uwarta ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wanan kuma kekika sani"</p><p><br /></p><p>AFRAH dake waya tana jinsu tayi banxa dasu</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ke kuma AFRAH wajenki nazo"katse wayan tayi kana tace "toh ina jinki hajiya"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wani wawan tsaki tayi kana tace" wallahi kinji kunya kiyi hasaran Halinki a haka kamar mai mutunci nan ko kinfi kowa iya tsiya"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ni bansan mekike fad'a ba kimin bayani yanda zan gane"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dama haka zakice ma k'aryaci ya kawai, ni zaki rai na ma hankali? Wai har ni zakiyi ma snatching saurayi n you are telling me baki san menake cewa ba" (leaders kuji Faty ta k'arya😂🤣🤣🤣) </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wanne da ka ciki na maki snatching d'in? ai samarin naki da yawa"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kin fini sani ai sabida kisan abinda kikayi baki kyauta ba shiyasa da ya yadawo da ke daka school baki fada ma Mommy tere kuke bah, kina bakin ciki baki da saurayi masu kud'i shi ne kikayi kutun kutun kika shiga tsaka ni to walhy ko kink'i ko kinso dole na aura mai kud'i d'an ko makawo ya shafa yan ni ba level d'inki bace nariga na dad'e da mayi nisa wallahi"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ai saurayin ki ne kikace ko? Zuwa zakiyi ki tan baye shi wani mugun halin kikayi ya gujeki ya dawo min bawai kizo kai na kina min ihu ba, kike cewa dole ki aura mai kud'i ai dama fatan da nake maki kenan"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Duk borin kunya kikeyi wallahi AFRAH shiyasa kike cewa haka"</p><p><br /></p><p>", toh nayi hajiya"</p><p><br /></p><p>"Madam masifa tinda kin gama ai sai kije ni assignment za ayimin"Afifah tace</p><p><br /></p><p>"Zan ci ubanki stupid girl" </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ni ji d'in da anyi magana kin iya cewa u are classy, wanan abin da kikeyi halin classy girls dinne? </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Fuuuuuuu Fatty ta bar d'akin bata tsaya ko ina ba sai Bedroom din Mommy kan bed ta zube ta kuka</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Menene? Ya kukayi da ita? "Mommy ta tanbaya</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Face dinta ta share kana tace wanan shegir AFRAH ta karo iskanci ina maga tana magana fa kuma AFIFAH har da shigar mata kuma sai da tafara banxan KASU dinan har ta ita maida ma mutun martani kawai d'an takusa shiga 2lvl? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"KASU din banxa da wofi kwana nawa ya rage kema zaki tafi Abuja karatun makatan da yaran masu dashi sukeyi, kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki sai kin aura wanda yafi ABDULNASEER ni na fada maki su inma sunga masu kud'i zasu sa kansu a ciki ne? Maza goge fukan ki wata wawiya chain bata isa tasaki kuka bah ita kuma Afifah zanci ubanta"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Gara kuwa d'an yariyan nan san AFRAH take na masifa"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Zanyi maganin abun bari dai su Azeezah suzo"haka dai sukai ta zancen su kwance wanan warware wanan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Su Mommy basu k'ara tsikewa bah sai da suka ga uban shopping da ABDULNASEER ya kawo mata ranan saura 1day yawuce, shopping yayi bana wasa kud'i sosai suyi kuka kaya ne masu kyau da kuma tsada AFRAH kasa magana tayi sabida yawan kayan "wai meyasa zaka siyomin abubuwa haka? "</p><p><br /></p><p>"In ban siya maki ba wa zan siyan mawa sweetheart Humairah ma haka nasiya mata, inkuma baki so ne sai nasan position din da nake"</p><p><br /></p><p>"Nooo ni ban ce bah"</p><p><br /></p><p>"Toh sai kiyi addu'a kawai"</p><p><br /></p><p>"Toh thank you so much, Allah kai kaika lfya ya kuma dawo da kai lfya, Allah ya bada sa'an karatu"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen sweetheart ai basai kiyi godiya ba Addu'an ma yayi, da nadawo za'azo ayi kagana naso a ce Daddy ma yanan na shiga na gaishe shii"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Allah dai ya tabbatar mana da alkhari"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen" hira sukayi sosai sai da zai tafi ya shiga ya gaida Mommy ta amsa babu babu fallasa " kai kuma haka a keyi wanan uban shopping haka ai sunyi yawa gaskiya ka tafi da su"</p><p><br /></p><p>"A'a Mommy please Ummie ce ta ce nakawo ai ba ni bane ayi hakuri"</p><p><br /></p><p>"Kai amma baku kyau tamin bah, angode, Allah tsare ya bada sa'an karatu"</p><p><br /></p><p>"Amen Mommy nagode"</p><p><br /></p><p>Har mota AFRAH ta raka shi, sai da taga fitar motan shi daka gidan nasu sanan ta koma ciki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ta shigo Mommy na kara duddu ba kayayyakin</p><p><br /></p><p>"Ya tafi kenan? "</p><p><br /></p><p>"Ehhh ya wuce"</p><p><br /></p><p>"Toh kwashe min wayanan kayan da suka cika min parlor, abinda ki kayi kin ji dadi ai ko? Ina rabaku da halin san kai amma sam baki dauka wai ina ma kika san ABDULNASEER din ne? Wanan yaro bazai ce yana san ki bah kedai kikasan abin da kikayi FATIMA kuwa Allah zai bata mafiyin shii" tana gama fadan haka ta tashi ta shige d'aki</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kwashe kayan tas AFRAH tayi ta kai dakin su, ita gaba daya tsoron Mommy ma takeji sai ta tsinta kanta da Addu'an Allah ya nisan ta ta da Sulaiman, wanan da ba yaron ta bama tace yana santa duk sun sata a gaba ina ga kuma tasan Sulaiman din ma santa yakeyi, Allah kar ka nunamin wanan rana AFRAH tace da karfi </p><p><br /></p><p>Tunane tunane tai tayi dataga bamai k'arewa bane phone d'inta ta jawo tashiga dialing number Inna ringing 3 ta dauka</p><p>" yar nema sai yau kika ga daman kirana? "</p><p><br /></p><p>"Ni Inna kiyi hakuri kisan karatu"</p><p><br /></p><p>"Sannu al huda huda uwar karatu"</p><p><br /></p><p>Gaiswa sukayi cikin bar kwanci kana Inna tace "yaya angon naki? "</p><p><br /></p><p>"Wani ango na kuma? "</p><p><br /></p><p>"Ke kiji har duniya"</p><p><br /></p><p>Dariya AFRAH tayi kana tace" duniyan cin mene? "</p><p><br /></p><p>"Ehh mana Sulaiman din ne baki sani ba? "</p><p><br /></p><p>"Ohhh Innar mu kenan"</p><p><br /></p><p>Hira sukayi sosai bayan sunyi sallama Maminta ta kira sukai hira. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>Gaba d'aya yanxo bata cika zaman gida ba, ga sch ga kuma catering sch da take zuwa ko tana gida ma aikin gaban ta wai rakeyi sai kuma karatun exams da zasu fara next month na second semester, har Mommy da Fatty su karaci habaicinsu tana jinsu sai ta nuna kaman bata gane wa, hamar kuli yau ma zaune take tana karatun Alqar'ani Fatty ce tashigo dakin babu sallama kamar koda yaushe " Mommy na kira" abinda tace kenan ta juya</p><p><br /></p><p>Sai da takai karshen aya sanan ta rufe qur'an ta wuce kiran Mommy </p><p><br /></p><p> sallama tayi a bakin k'ofan sai da aka amsa tashiga " ke kam baza a taba k'iranki kizo a kan time ba sai kinga dama"</p><p><br /></p><p>"Ina karatune sai da nakai karshen aya sanan nazo"</p><p><br /></p><p>"Yayi dai dai, dama su Azeezah ne zasuzo shine nakeso ki shirya masu abinci, ki fara yanxo kinsan dai babu wani nisan tsakan zaria da kaduna"</p><p><br /></p><p>"Oky tohm" bayan ta fita kitchen tayi direct babu bata lokaci tafara aikin da zatayi girki tayi sosai bana wasa ba fried rice da arebiyan salat tayi sai Pepe soup na kaza sai wani Pepe soup na kayan ciki da tama daddy daya dawo shekaran jiya(ya k'ara tafiya jiya) sai tayi warming sai kuma fruit salad da dai kayan mak'ulashe. Kafin 1 har ta gama ta jeresu inda yakamata d'anki su ta koma tayi salla sanan tacigaba da karatunta</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Karfe 2 daidai su Anty Azezah suka shigo gidan Mommy da Fatima sunyi marnan ganinsu sosai sallah suka fara yi kana aka zauna cin abinci har Bedroom din Mommy AFRAH tashigo ta gaishe su a dak'ile suka amsa</p><p><br /></p><p>"Yaya wai har yanzo kece kike rike yaran Rabi? "Azeezah tace</p><p><br /></p><p>"Gashi kuwa kingani" cewar Nana </p><p><br /></p><p>" tap ashe kina fama zama da wanda ba naka ba ai da wahala"</p><p><br /></p><p>"Mema kuka sani aunty " cewar fatty </p><p><br /></p><p>"Fadamin Dan Allah Fatty" nan Fatty tashiga jero zance hadda karya</p><p><br /></p><p>Dukkan su biyun salati suka dauka sai da suka dire Azexah tace" wallahi ko ki yadda ko kar ki yadda Rabi da y'arta na asiri kuma kisan nasha fada maki ba tin yanzo bah"</p><p><br /></p><p>"Sosai ma, inbanda aikin asiri taya za'ace saurayin Fatty yakoma ma wata AFRAH "Aunty Nana tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dole ki tashi tsaye inkuwa ba haka ba wallahi sai dai kiji zancen auranta da Suleiman tinda tama kina zargi irin muna fukan yaranan ba gane kansu akeyi ba"</p><p><br /></p><p>"Yanzo menene abinyi? " Mommy tace</p><p><br /></p><p>" Abinyi shine kinemi temako "</p><p><br /></p><p>"Wani irin temako? "</p><p><br /></p><p>"Na farko dai acire san AFRAH a Zuciyan Sulaiman inma akwai shi na biyu dole kirika juya gidanan yanda kikeso"</p><p><br /></p><p>"Kai Azezah babu matsala kuwa? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Babu wani matsala ai bawani kikai ma mugun abu ba ai Allah ma ya sani"</p><p><br /></p><p>_Dan Allah d'an girman Allah mukula MATA shirka ko wani iri ne haramum ne kwana 40 ba'a amsan sallah bare wasu aiyukan kar wata/wani ya zugaka wai kayi makamancin Abinda Mommy kesan yi kace wai baza kasamu zunubi ba, wanda yace ma babban mak'aryaci ne, Dan Allah mukula mubar komai a hannun Allah dan shine ke tsara komai yanda yaso, Allah shiryar damu yakuma sa mu dace AMEEN_</p><p><br /></p><p>Hakadai sukai ta zuga Mommy har ta yadda da maganansu. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Nagode sosai da kulawanku a gare ni naga kira naga next wasu ban samu dauka ba, Dan Allah kuyi hakuri,jikin ne ya matsa min Amma Alhamdulillahi da sauki yanxo nagode nagode Allah saka da alheri_</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 51-52_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Duk shawarwarin da Azeezah da Nana suka ba Mommy tayi na'am dashi, shiyasa babu b'ata lokaci duk ta aiwatar da abinda yakamata. </p><p> </p><p> A halin yanzo gaba d'aya Suleiman yadena shiga harkan AFRAH babu ruwan shii da ita. Basu waya basu chatting. Muhammad kanshi yana mamaki yanda gaba d'aya yadena kiran ko sunan AFRAH. zaune suke dukkan su biyun a Suleiman na aiki da laptop yayin da Muhammad ke waya bayan ya gama wayan Suleiman ya kalla kana yace "friend wai kunyi fad'a da AFRAH ne? "</p><p><br /></p><p>"Mekagani? "Yayi maganan ba tare da ya 'daga kanshi ba</p><p><br /></p><p>"Nothing naga dai baku waya ne"</p><p><br /></p><p>Sai da ya kalla Muhammad sanann yace" yes am just waiting for d perpect time ne"</p><p><br /></p><p>"What d u mean? perfect time how? "</p><p><br /></p><p>"Yes, i don't know "</p><p><br /></p><p>Kallanshi kawai Muhammad yakeyi chan yace "Allah tabbatar mana da alkhari"</p><p><br /></p><p>"Ameen" Suleiman yace yaci gaba daba da aikin shi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Side din AFRAH ma hakan ko kadan bai dameta ba dad'i ma taji coz ita gaba daya tsoron Mommy takeji shiyasa ko takan yaya Suleiman batayi ba ko dayadena kiranta shareshi tayi taciga va da harkan gabanta ga ABDULNASER dinta na kula da ita always san shi take sosai har Ummu kiran ta take suna gaisawa haka aunty Baraka Humairah kam tazama kawarta shiyasa take mugun respecting dinsu sosai. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shirye shirye exams suketayi shiyasa gaba daya kwananan ta maida hankali sosai kan karatun ta duk da dama ita kulin cikin karatun take, yawan karatun ta yasa Fatty da Mommy ke jin haushin ta su rinka habaici kenan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yau Sunday zaune take tana karatu dan Monday exams Fatty ce tazo wucewa naga AFRAH na karatu tsaki tajaa kana tace" shi mutun bai da wani aiki sai karatu duk ya damemu a gida kaman wasu yaree"</p><p><br /></p><p>Daria AFRAH tayi sanan tace" kee ma soon zaki fara ai zaki ji yanda akejii"</p><p><br /></p><p>" zan fara kuwa soon amma ni ba irin wanan masifar naki zanyi ba, naki yana neman yazama masifa ne ai ke"</p><p><br /></p><p>Smiling kawai AFRAH tayi taci gaba da karatunta yayin da Fatty tayi gaba. Bayan fitar fatty gidan Mommy ce ta fitoh tana shan kamshii tana cika tana batsewa dan har yanzo haushin AFRAH takeyi kuma haushin Ummu ma takeji shiyasa tin ranan bata kuma zuwa gidan baa</p><p> Kwaliya sosai tayi kaman mai shirin zuwa wani liyafa zama tayi a parlor numbern Hafiz tayi dialing waya suka shiga yii duk AFRAH najinsu bayan ta gama wayan ne ta kalla AFRAH sanan tace " toh Alhuda huda tashi zaiyi ki hadamin fruit salad yanzo sanan zuwa anjima inaso ki shirya min lunch mai kyau dan matan Alhaji Yusuf zatazo(kar ku manta alhaji Yusuf abokin business na Daddy) abinci mai kyau nekeso ki shirya" </p><p><br /></p><p>Babu yanda AFRAH ta iya haka ta aje karatunta ta shiga kitchen.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>AFRAH bata wani sha wahala ba kasan cewar Mommy ta karo masu yan aiki so duk su suka taya ta sai kuma AFIFAH daketa zuba surutun taa abinci kara 2 masu lafiya tashirya sai pepe chicken da juice masu dadin gske tin kafin ta gama Mommy tazo sai hura hanci takeyi tana wani isaa da mulki itam AFRAH tabata waje su sajida ne suk suka karasa jere abincin AFRAH kam daki ta koma </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan duk anjere komai yanda ya kamata parlor Mommy ta dawo tashiga kiran Number Fatty sai da yakusa tsikewa ta dauka</p><p><br /></p><p>"Wai dan uban ki bazaki dawo ba har sai suzo koo"</p><p><br /></p><p>Daka dayan bangaran Fatty tace" Mommy ganin kara sowa ina isa kaita" kittt ta kashe wayan </p><p><br /></p><p>Sai bayan minti20 Fatty ta dawo gidan nan da nan ta shiga ta shiya itama cikin kwaliy sai bayan la'asar bakin Na mommy suka iso watau hajia Hauwa ta iso ita da yarinyarta Haifa itama kamar Fatty take yar gayuce itama sosai </p><p><br /></p><p> Sosai mommy tayi murna da zuwansu tarba mai kyau tayi masu nan da nan yan aikin Mommy suka cika masu gaba da kayan motsa baki iri iri da kuma girke girken da AFRAH tayi Fatty da Haifa kam tuni suka ware kansu(hali yaxo daya... 😂) jin alamun mutane sun shigo gidan ne yasa AFRAH fitowa daka dakin su, bakuwa ta hango ita da Mommy a parlor karasawa parlor tayi ta gaida hajia Hauwa cikin ladabi da girmamawa hajian ta amsa cikin sakin fuska bayan AFRAH ta wuce kallan Mommy hajia tayi sanann tace" dama 'yan mata Uku gare ki ashe"? </p><p><br /></p><p>Murmushi mommy tayi kana tace" AFRAH yariyan kaninshi ce da yarasu"</p><p><br /></p><p>"Allah sarki AFRAH mai kyau da ita ga natsuwa"</p><p><br /></p><p>Wani haushi da bakin ciki ne ya tsaya Mommy danne wa kawai tayi dan bataso hajian tagane, murmushi ta k'akalo kana tace "hajia sako kici abinci tin dazo juice kawai kikasha" bata jira amsanta ba tashiga zuba mata fried rice da coslow tasa mata sai perpe chicken </p><p> Tinda hajia Hauwa tafaraci take santi" ni kam hajia Bilki kinada kuku a gidanan"</p><p><br /></p><p>"Ah'a AFRAH ne tayi shi dayake tana zuwa catering school"</p><p><br /></p><p>"Ikon Allah aikuwa dai ta iya dan ko abincin restaurant bai kaiwa haka"</p><p><br /></p><p>"Ehhh tana kokari ba laifi"cewar mommy </p><p><br /></p><p>"Gaskiya kokari sosai wanan girkin da Suraj zai samu ai dadi zai ji dan shi yana san girki mai dad'i"</p><p><br /></p><p>"Allah sarki my son ai sai duk kutafi dasu dama dan ku akayi shii ai"</p><p><br /></p><p>"Ai kuwa kin kyauta hajia kuma nagode sosai"</p><p><br /></p><p>Duk abun nan da Mommy keyi daurewa kawai takeyi amma Allah kadai yasan haushin AFRAH datakeji kowa sai ya yabeta kowa sai yanuna yana santa haushi kawai takeji na AFRAH sosai sai taji dama batace itace tayi girkin ba, haka dai hajia Hauwa tai ta yaba abincin AFRAH mommy dai sai murmushin karya takeyi</p><p><br /></p><p> Ko da su Hajia Hauwa suka tashi tafiya sai datasa aka kira mata AFRAH </p><p>"Toh AFRAH mu zamuwuce"cewar hajia hauwa</p><p><br /></p><p>Smiling AFRAH tayi kana tace " toh Allah kaiku gida lfya</p><p><br /></p><p>"Ga wanan ladan iya girki naji dadin abinciki sosai"</p><p><br /></p><p>"Nooo wallahi bazan amsa ba hajia nagode"</p><p><br /></p><p>Kamo hannunta hajia Hauwa tayi sanan tasama ta kudi gami da cewa "kisiya jan baki da powder"</p><p><br /></p><p>Babu yanda AFRAH ta iya haka ta amsa tayi mata godia</p><p><br /></p><p>Kallan Haifa hajia tayi kana tace bakuyi exchanging digit da AFRAH ba, da yake itama Haifan babu ruwanta kaman mamanta take yasa sukayi exchanging numbers abinsu</p><p> Tinda aka fara drama din Mommy taci kam wani mugun haushin AFRAH da tsanar ta takeyi wanda takasa gane irinshi ma</p><p><br /></p><p>Haka dai hajia ta tarkata duk abincin da su juice suyima juna sallama sukai gaba, aka bar Mommy da Faty cikin bakin ciki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tinda suka shiga ciki Mommy ke sauke buhun masifa sai masifa takeyi kuma AFRAH tagane sarai da ita takeyi amma sai ta fuske tayi kaman batasan metakeyi ba, dakinsu ma tashige tabarsu anan</p><p><br /></p><p>"Mommy please kibar damun kanki"cewar Fatty </p><p><br /></p><p>"Amma baki ganan duk wanda yazo gidanan sai dai yace AFRAH! AFRAH kowa wanan abun haushi yake bani faa"</p><p><br /></p><p>Daria Fatty tayi sanan tace" kan girki nefa ba wani abu baa, besides lokacinta nema, muma haka ake kiran sunayenmu a wajaje masu matsayi wai wai kan girki bah" haka dai sukai ta xancensu kamar yanda suka saba.</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 52-53_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*C*igaba bud'i, daukaka da kuma haske duk Daddy yasame su kud'i yayi fiye da tunanin kai karatu business ta ansheshi, yana k'okarin kyautatama mahaifiyarshi danginsa dakuma iyalinsa sosai dakuma marasa k'arfi shiyasa kulin cikin ganin cigaba yakeyi a rayuwansa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Al'amarin Mommy yayi gaba dan yanzo mulki sosai take zabgawa a sabon gidan ta san ranta sai abinda taga dama takeyi gashi yanzo Daddy sai ayi abu d'ari bayyi magana ba Mommyce take ruling komai na gidan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Fatty ma na baza tsiyarta d'an yanzo liyafa yacigaba mota takeja da kanta, duk inda zataje AFRAH kam k'ememe Mommy tahana a koya mata wai motan zai lalalace indai ana yawan hawa acewar mommy(Allah tsaremu da san kai... ameen) friends kuwa ga sunan lodi lodi yaran manya yan gayu suke mutanan Fatty. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>AFRAH kam ko kadan san kan da Mommy keyi kirikiri baya damunta d'an tasan komai lokaci ne indai kanada rai toh baka cire rai da rahman Allah, shiyasa tasa masu idanu insun sata cikin labarinsu ta shiga in basu sataba tanuna kaman batasan mesukeyi ba, soyayyansu da ABDULNASEER yanan sai abinda yayi gaba d'an duk family dinshi sunsan AFRAH haka itama, Suleiman kan tuni ya manta da ita a rayuwanshi ita hakanma dadi yayi mata d'an duk abinda zai sadata da Mommy tsoranshi takeyi shiyasa ko kadan Suleiman bai bata haushi ba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Fad'an irin girke girken da AFRAH ta iya bata lokaci ne abinci iri iri ta iya hadda na outside haka snacks ma babu irin wanda bata yiii ita kanta mamakin hanta takeyi intayi irin birthday cake dinan gashi har popular tayi sabida su Zarah da Husnah da sauran friends dakesa abubuwanta a Snapchat da sauran social network. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau Saturday girke girke taketayi kasan cewar yau Humairah zatazo gaisheta sai Zarah da Husnah da zasuzo suma, Mommy ce tashigo kicin d'in cikin isa take magana</p><p><br /></p><p>"Suwa kekema girki haka? "</p><p><br /></p><p>"Mommy kin manta yau Humairah zatazo?inaso na bata takaima Ummie ne, kuma su Zarah ma zasuzo"</p><p><br /></p><p>Tsaki Mommy tayi kadan kana tachai " in banda neman suna da iyayi menene na wani yima Ummie abinci? Inkuma dan su Zarah ne ai su ba bak'i bane, ita kanta Humairan drinks da snacks ai ya isheta amma dan neman wajen zama hadda girki, inkin gama duk ki zuba ki ajemin"ta karasa maganan tana ya tsina fuska</p><p><br /></p><p>Itadai AFRAH shuru tayi batace komai ba har mommy tagama yatsinar ta tabar cikin din. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tana kan hada salad Zarah da Husnah suka shigo cikin din cikin murna hugging juna duk sukayi kana AFRAH tace" kungaisa da Mommy ne?"</p><p><br /></p><p>"Noooo bamuganeta a parlor kasa ba"cewar Husna dake kokarin daukan part din pepper chicken, Zarah kam abincin da AFRAH tayi decorating takema video ta Snapchat </p><p><br /></p><p>" please muje ku gaida ta sai mudawo kucigaba da sana'ar taku" cewar AFRAH dan inhar Mommy tasan sunzo basu shigo gaisheta kan time ba ranann tarinka tsine masu kenann dan duk wani mai san AFFRAH Mommy ta tsaneshi haushisa takeji kawai batada yanda zatayi ne</p><p><br /></p><p>Phone da bags dinsu duk a cikin din suka barshi suka nufi bedroom din Mommy da fadan irin kyaunsa da dukiyan da ke cikinsa b'ata lokaci ne, sallama sukayi baki kofar sai da suka tabbatar an amsa sanan suka sa kansu cikin dakin, kwance Mommy take saman bed tana shann fruit salad, karasowa ZARAH da HUSNAH sukayi har bakin gadon suka gaidata cikin ladabi, sai da Mommy takaremasu kallo tass sanan ta amsa a dak'ile kamar yanda tasaba</p><p><br /></p><p>" yaa mamanku?"Mommyn tace</p><p> duk suka ansa da lfyalau, nan dai suka tashi suka bar bedroom din suna mamakin halin Mommy dan yanzo sunsan ba ita bace real Mother na AFRAH halin Mommy wasu sai su rubuce shi cikin takarda dan tana yimasu insunzo gidan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kicin din suka koma gaba dayansu har sai da AFRAH tagama aikin ta duk tazubama Mommy sanan tajere sauran</p><p><br /></p><p> Tana shirin barin kicin din Lantana tashigo(mai ma yan cikin gida abinci) </p><p><br /></p><p>"Ahhhh kecemin ameenan arziki sunzo"Lantana tace tana washe baki</p><p><br /></p><p>Dariya Husna da Zarah sukayi dukkansu sanan Husnah tace" gamu kuwa kinganmu mutu karaba insha Allah"</p><p>. </p><p><br /></p><p>Dariya Lantana tayi sanan tace" ai kawai miji guda yadace ku aura sai kuta zuminci"</p><p><br /></p><p>" lallai ma Lantana Kanki ba d'aya yake ba, muyi k'iyayya badai zuminci ba" Husnah tace</p><p><br /></p><p>"Allah dai ya karemu wallahi da wanan aiki, wani zai ci amanan wani kenan fa kike nufi" Zarah tace</p><p><br /></p><p>Daria Lantana tayi kana tace" ashe aneentarr kar..... " bata karasa ba AFRAH ta tsaidata da tun sazo ma takasa magana</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wai ke baki gajiya da magana ne? Wai mema kikesan cewa ne?kinzo sai magana mara anfani kikeyi"</p><p><br /></p><p>"Antyn AFIFAH kenan dama cewa zanyi kicema Hajiya nagama abincin"</p><p>. </p><p>D'an tsaki kadan AFRAH tayi sanan tace " ai kinsan dakinta sai kije ai" dabi'ar Mommy ne inhar Lantana tagama abincin yan tsakar gida sai tazo ta fadima Mommyn, a gabanta ake rabo wai dan kar yan aikin su diba a buye(kai Mommy badai rowa ba😆) </p><p><br /></p><p> Nan Lantana tawuce sum sum kamar Munafuka dan tasan shiga dakin Mommy sai da k'a'ida, da ido duk suka bita suba dariya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dakin ta suka nufa dan wanan sabon gidan kowa da bedroom dinsa Afifah ne kawai taki yadda ita dole sai da AFRAH lokacin Mommy taji haushin Afifah amma dayake batasan ran yaran ta ya baci yasa ta barta tare da AFRAHn da babu yanda zatayi</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kwance sukaga Afifan tana game cikin iPad din ta gaba daya hankalinta ya tafi ga game batasan ma sun shigo ba, Zarah ne ta amshe iPad din tana cewa" haba kawa wani irin game ne haka kikeyi? "</p><p><br /></p><p>Smiling Afifah tayi kana tace "anty yaushe kukazo? "</p><p><br /></p><p>" tini mukazo bamu ganki a cikin ba yau har antynki tagama girki" Zarah tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" wallahi saboda new game din nan danayi downloadig ne, amma naso muyi aikin tare" Takarasa maganan tana tashi zaune</p><p><br /></p><p><br /></p><p>" baby wai ma kiyi haddan ki? Kina sane yau Saturday ko"AFRAH tace</p><p><br /></p><p>Eyes dinta tazaro waje kana tace" ina fa tun wanda mukayi tare da subh"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Za kimasu explaining ni inanan wallahi"</p><p><br /></p><p>Qur'ani ta dauka kana tace dasu Husnah" ina zuwa naje nayi haddan nadawo yau akwai gist muyi waya da Yaya ABDULNASERR" sai da takai karshij maganan sanan tabar bedroom din</p><p><br /></p><p>Dariya Zarah da Husna suka saka</p><p><br /></p><p>"Babe wallahi Afifah kamar babba shegen manyance" Husnah tace tana daria</p><p><br /></p><p>" ai baki ga komai ba indai Afifah ce haka tace wallahi" AFRAH tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zarah na shirin magana phone dinta yashiga ringing,smiling mai kyau tayi kana tayi picking, nan ta shiga magana da Mahmud saurayinta wanda ko Husna da Afra basajin mai take cewa bare ni </p><p> Tsaki Husnah Da AFRAH sukayi, Afrah tace " mutun sai munafunci wayan ma sai anyi munafunci" toilet tashige tanajan tsaki</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan tafitoh daka wakan Zarah da Husnah tagani suna cin abinci bata bita kansu bah tashiga shirinta, shiyawa tayi cikin atanfa gown sai dan simple make-up datayi applying amma sai tayi kyau, bayan tagama shiryawa sallan la'asar ta gabatar sai lokacin su Husnah suka gama cin aninci suma salan sukayi</p><p> Sun idar kenan Afifah tashigo tasa kayan islamiyanta sallama tayi masu tawuce, Afifah tafice baifi da minti 10 suna dan hira Humairah takira Afrah ta iso tana kasa, nan duk suka fitoh dan tarbota </p><p> Wajen Mommy Afrah tafara kai ta ta gaidata</p><p>Mommy ta amsa cikin fara'a da sakin fuska... Amma dai naci na ciki sanan AFRAH tayo da ita bedroom dinta already duk su Zarah sun jere mata komai drinks snacks girke girke fruit da kayan motsa baki iri iri, abinci kadan taci amma sai santi takeyi gami dacewa yayanta yamore</p><p> Hira sukayi sosai da sosai abinka da wayayyu kuma yan gayu sai 6pm Humairah rakira drivernsu dan yazo ya dauketa , turaruka da mayafai masu kyau Afrah ta bata, godiya sosai Humairah ketayi kamar anbata duniya, goda Humaira taje yima Mommy sallama mommy komai bata bataba sai cewa tayi" ki gaida Ummu, kice mata inan zuwa"suna fita taja tsaki. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Har bakin Mommy suka rakota da girke girke da snacks takaima UmmieAFRAH sai godiya takeyi itama Humairan na godiya, nan Humairah tazaro phone dinta tashiga daukansu selfie, suna cikin daukan pics din Fatty tazo wucewa kallansu tayi taja tsaki kana tashiga ciki</p><p><br /></p><p>Sai da Humairah tashiga cikin mota idanunta suka ganemata sakon da Ummie da Aunty Baraka suka bada akawo mata, nan da nan Humairah tafitoh da ledojin ta aje gabanta sanan takoma cikin motan, kallanta Afrah takeyi sosai smiling Humairah tayi kana tace" inji Ummie da Aunty baraka"itama smiling din tayi, haka dai sukai ta dakama juna hannu har sai da tagama motan nasu yabar haraban gidan sanan su Zarah suka tayata kwashe kayan sukai ciki</p><p><br /></p><p>Farty dake hangansu ta balcony kaman tayi kuka ranta zafi yakeyi mata wani haushin AFRAH takeji sabo fil na shiganta</p><p>Bedroom din mommy tayi cikin bakinn ciki kamar hadin baki sai ga AFRAH ma tashigo da uban kayan da Humairah takawo mana</p><p><br /></p><p>"Mommy kinga kaya wai Ummie da Aunty Baraka sukace a kawo min" AFRAH tace</p><p><br /></p><p>Yamutsa fuska Mommy tayi kana ta shiga duba kayan, cosmetics ne iri iri, sai abayas, veils, shoes, sidebags hadda sunglasses masu shegen kyau duk product din kayan babu na banza ciki duk masu tsada ne, d'ayan ledan kuwa chocolate ne da kayan zaki iri iri kala daban daban sai da Mommy ta gama kallan kayan tas sanan tace" rok'o dai babu kyau bakida tabbacin auran yaron su, amma kina amshe masu kaya kedai kika sani kwashe kayan kije"</p><p><br /></p><p>AFRAH batace komai ba ta kwashe kayan tana mamakin halin Mommy na lauya yanzo yanzo sai ta juyama mutum fassara</p><p> Bedroom dinta tanufa da kayan nan su Husnah sukai ta santin kayan da yaba irin sanda familyn ABDULNASER kemata ita dai AFRAH smiling kawai takeyi, abaya, mayafi da turarikan duk ta basu a cikin kayan chocolate kam tin a wajen suka diran mai suka fara sha, sai da sukayi sallahn Magrib Mahmoud wanda Zarah zata aura yazo daukansu, koda suka shiga yima Mommy sallama a wulakance ta amsa basu bi ta kanta ba sukai gaba</p><p><br /></p><p>Har bakin mota AFRAH da Afifah suka rakosu, gaisuwa sosai gami da barkonci AFRAH da Mahmoud sukayi Afifah ma ta gaidashi ya amsa cikin sakin fuska</p><p><br /></p><p>"Toh babies nagode sosai.. Sai munyi waya" AFRAH tace</p><p><br /></p><p>"No worries, sis baki bamu labarin ba"Zarah tace</p><p><br /></p><p>Smiling Afifah tayi kana tace" ai dan naje islamiyya ne, amma ai akwai next time "</p><p><br /></p><p>Dariya husnah tayi kana tace" toh tafara manyancen"</p><p><br /></p><p>Dariya duk sukayi hadda Mahmoud, 5k yazaro yaba Afifah wai tasha chocolate godia tayi sosai kamar wata babba daria sukai ta yimata, sallama suka karayi sanan ya jasu suka tafi. </p><p><br /></p><p>A guje Afifah ta shiga gida bata tsaya ko ina ba sai bedroom din Mommy, zaune ta gansu jugum jugum</p><p><br /></p><p>" dama ke nake nama aunty Farty"Afifah tace</p><p><br /></p><p>"Ai gani kin ganni ko? Sai kifada abinda zakice"</p><p><br /></p><p>5k din da Mahmoud yabata nuno kana tace"kin gansu nan saurayin Aunty Zarah friend din Anty AFRAH yabani su, ke kam saurayin ki bai iya bada sisi sai k'aryan hawa motoci da tafiye tafiyen tsiya, ko sau daya banga shopping din shi ba, ko yaya ABDULNASEER da baya gari yana aiko da shi ke kam gum... " ta karasa maganan tana dariya</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Daka Mommy har Fatty rasa abin cewa sukayi sai kallanta da suketayi tana rawa Mommy ce tayi k'arfin halin cewa" fita kibar dakinan dan ubanki" a guuje kuwa ta fice</p><p><br /></p><p>"Mommy wallahi nagaji komai kowa AFRAH haba kiga abinda Afifah yanxo kecewa"</p><p><br /></p><p>"Kar kisake wanan ya dameki da duk abin da zai samu AFRAH yanzo mai kud'i kam kema dole ki aura tinda har ita iya samun ABDULNASER dole ki samu mafiyin shi kisa wanan ki aje a zuciyan ki" haka Mommy taita lallashin Fatty har ta hakura.</p><p> Wani tsanar AFRAH ke kara shigan Mommy haushin ta takeji sosai kani takeyi komai AFRAH tasamu shishigi tayi dan ita bata kai matsayin da zata sameshi hakanan ba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p><br /></p><p>Rayuwa na ta tafiya haka a bubuwa nata faruwa lamarin Mommy gaba gaba yaketayi ita dai AFRAH nata ido ne</p><p> Halin yanzo Fatty ta k'ara jamb inda tayi registration da wani center amma kudi sosai suka biya aikam score har 220 ta samu nan Fatty tai ta hura hanci ita a dole tayi kokari a jamb, BAZE university tayi applying Fatty sai iya yii takeyi sch dinta yafi na AFRAH ita dai AFRAH ko a jikinta bai dameta ba abubuwan gabanta kawai takeyi</p><p><br /></p><p> Ko da time din registration yayi kud'i sosai Daddy ya sake masu, tin kafin Fatty ta fara sch din tayi friends yan ABUJA Mommy sai habaici takeyi itama yarta xata tafi school na ma yaran manya</p><p><br /></p><p>Saura kwana biyu Fatty ta wuce sch ta shigo bedroom din AFRAH zama tayi kana tace</p><p><br /></p><p>"Allazi karatu nima dai nakusa tafi school dinan"</p><p><br /></p><p>Daria Afrah tayi kana tace" ai ni boss dinki ce 200lvl ba wasa ba ne"</p><p><br /></p><p>Tsaki Fatty tayi kana tace" ohooo dai" hira suka dan yii rabi dai duk habaici Fatty keyi mata ita dai Afrah Smiling kawai takeyi</p><p><br /></p><p>Ranan da Fatty zata wuce dukkansu har ABUJA suka rakata shopping sosai Fatty tayi bana wasa ba sai iya yii takeyi daka ita har Mommy kwanasu daya a Abuja suka juwo kaduna Daddy kam turkey yayi dan duba HAFIZ. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin kwanciyan hankali AFRAH ke karatun ta, game da snacks din da ta iya kuwa AFRAH tayi fice sosai an santa a wanan harkan manyan yaran masu kudu haka suke birthday cake, cups cake wajen ta da snacks iri iri kudi sosai take samu a wanan business din mommy haushin wanan sana'ar na AFRAH takeyi wai tana jawo masu talaucii da fatara ita dai AFRAH bata cewa komai... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_kuyi hakuri readers, sweethearts please, amma kuyi comments, much love for you all_❤❤❤❤❤❤❤❤❤</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 56-57_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*kuyi ta hakury dani please sweethearts*😇</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*wallahi wasu na bani mamaki, naga dai rubuta Novel sa kai ne, bawai salary ake biya ba bare mutum yama iko ko ya zageka wai d'anbakayi typing bah, kawai kai kaga zaka iya kakeyi, ni bazan zageki bah kamar yanda kika zageni amma ina so ki sani Biebie Dee bata saki dole kibi labarinta ba bare har rashin typing yasa ki zageni, akwai masoya da yawa wanda ko zanyi shekara ne banyi typing ba zasumin uzuri kuma duk randa nayi xasu karanta,so kidena bin labari na babu dole, zagi dakikamin kuma nagode Allah saka da alkhari, fatan Alkhari nakebin kowa da shi ba sharri bah*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*R*anan babu irin kula da Suleiman bay samu ba daka wajen Mommy da Daddy, sai sa suka dawo daka sallan magrab kowa ya hallara a dining dan cin abinci Sulaiman sai santi Abinci yakeyi minti minti yana kallan AFRAH duk abin da yakeyi Mommy na noticing dunsa sai tsaki takeyi ita kam AFRAH bata masan halin da suke ciki ba. </p><p><br /></p><p>Basu bar kan dining din ba sai da akayi kiran sallan isha'a Daddy, Suleiman da Abdull masjid sukayi yayin da sukuma su AFRAH da Mommy suka shiga ciki dan gabatar da nasu Sallan. </p><p><br /></p><p> Bayan su dawo daka masjid din dakin shi yawuce da hutawa wanda yasha gyara sosai bedroom din ya tsaru sosai ba a cewa komai abin sai wanda ya gani, Abdul ma nashi dakin yawuce dan shima ya gaji. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Su AFRAH kam bayan su idar da sallah Parlorn k'asa suyo inada suke ta hira da Daddy mommy kam sama sama take sa masu baki cikin maganan kuma d'an ganin AFRAH ne, kallan Mommy daddy yayi kana yace" jibi nakesan tafiya zuwa Ghana d'an akwai wani kayan mu da zasu zo tanan, kuma sanan ku samu cikin addu'a wasu kayan namu suna hanyan zuwa ta jirgir ruwa kuma kaya ne masu yawan gske, indai Allah ya kawo kayan lafiya kuma muka sai da su toh zan maida ma banki duk wani bashin su dasuke bina" ya kara sa maganan yana k'ara gyara zaman shii</p><p><br /></p><p>Mommy ma zaman ta gyara kana tace" haba Alhaji zasuyi magana bamu da sirri sai gaban mutane? Kamata yayi kabari in munshiga d'aki muyi magana ba nan ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wani kallo Daddy ya watsa mata sanan tace" su wanene Mutanan a nan?AFRAH ko? na riga na lura da duk wani take takenki kan Yaranan toh wallahilazim ki shiga taitayin ki, kalle su chan farkon parlor suna kallo basu san ma memukeyi bah amma kince gaban mutane, ina da right d'in da zanyi magana da koma gaban wanene wanan ba matsalanki bace in baza kiyi addu'a ba kiyi gum"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tin da yan da ka fassara ni kenan ai shikenan hakan ma yayi dai dai"</p><p><br /></p><p>"Da kyau kowa ya shirya gobe insha Allahu zamu shiga katsina" </p><p><br /></p><p>"Ni kam bazan samu zuwa bah d'an zani wajen Aunty Maijiddah dubuma Fatima Bedsheets,musan man ta kirana tachai ta dawo daka Dubai"</p><p><br /></p><p>"Yayi dai dai" Daddy yache yana kokarin tashi bin bayan shi Mommy tayi tabar AFRAH da AFIFAH a parlon. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kaman yana jira Mommy na barin Parlorn ABDULNASEER ya k'irata nan yake sanan da ita insha Allahu nan da 1week zay iso Nigeria, dad'i sosai AFRAH taji wanda har takasa boyewa hiran su suka sha na masoya kana sukai sallama, tana kama wayan kayan kallon da da wuta ta kashe ta tada AFIFAH sukayi bedroom dinsu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da asubah Daddy ke sanar dasu zuwan su katsina a yau, har bedroom dinsu AFRAH daddy ya shigo ya sanar dasu suma, shiyasa ko da suka dawo daka masjid babu wanda ya koma bacci kowa shiri ya shiga yii, AFRAH ma tin da sukayi sallah suka shiga shiri ita da Afifah, kasancewar AFRAH da hanzari nan da nan ta kammala duk abin da zatayi har d'an breakfast tayi nasu 7am dai dai duk sungama shiri Suleiman da Abdul shadda ce sukasaka d'inkin zamani sunyi kyau abinsu AFRAH kam atanpa tasa mai color din red n black dinkin gown ne simple make-up tayi amma sai tayi kyau sosai black mayafi tasa sai wani d'an brown jaka ta tarike tayi kyau sosai Afifah ma gown tasa na atanpa amma Make-up tayi sosai kaman babba in kun ganta sai ta birgeku</p><p><br /></p><p> Ko da Sulaima yaga AFRAH kallan ta ya tsayayi bai sani bah d'an tayi mai kyau sosai fiskewa tayi ta gaidashi shida yaya Abdul nan tasa kayansu cikin both </p><p> Sai da suka shiga dukkansu sukayi ma Mommy sallama sanan suka shiga Mota suna jiran fitowan Daddy babu dadewa yafitoh nan driver yajasu sai da suka tsaya tawani super market suyi siyayya sosai kana suka dau haanya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sun iso lfya Inna tayi Murna sosai da ganin su haka yan uwa da abokan Arziki bayan gaishe gaishe sallah suka farayi kana Inna ta gabatar masu da abinci mai rai da lfya. Inan Daddyya sanar da su game da kayan su masu zuwa da kuma business din da zasuyi a Ghana da kuma bashin banki da yakesan biya, Addu'a dukkan su sukayi gami da Fatan Alkhari. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> bayan sun gama ne aka shiga shigo da shatara na arzikin da Daddy ya kawo Inna sai Albarka take sai mai gami da mai Addu'a bayan angama shiga da kayayyankin Dagi suka suka shiga dan gaishesu shima abin arzikin Daddy yayi kaman yanda yasa</p><p><br /></p><p> Har gidan Aunty Rabi sai dasukaje tarba mai kyau suka samu wajen aunty Rabi da uncle junaid komai a mutunci sikayi shi koda Daddy xai wuce kud'i masu yawan gske yabama Fahad d Arfah </p><p> Tare da su Suleiman suka dawo gidan Inna inda Kabar AFRAH da Afifah a gidan Mami</p><p><br /></p><p>Daddy nadawo wa yama Inna sallama ya juwa Kaduna Inna Inna taita samai Albarka, su ko yaran sai suyi kwana 2 zasudawo</p><p><br /></p><p> Ranan Da AFRAH ta kwana gidan Mami har waya Mami sukayi da ABDULNASER kuma ta yaba da hankalinshi tinda ka yanda taji maganan shi a natse, Addu'a sosai Mami tayi masu, ranan dai basu wani baccin kirki ba sunsha fira. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Washegari ma gidanta Suleiman da Abdul suka wuni haka aka baje a parlor anata hira hadda uncle Junaid, Afifah ma ba a bar ta abaya bah sai zuba surutu takeyi haka Fahad d Arfah ma. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>A gidan Inna kam da ta kalla Sulaiman ta kallan AFRAH sai tace" wayyo kama kanka wallahi" </p><p><br /></p><p>Abdul yayta daria shi da Afifah shi dai Sulaiman sai dai ya kallesu kawai</p><p><br /></p><p>Haka dai suka gama wanan kwana biyun cikin farin ciki da kwanciyan hankali kana suna kawo kaduna.... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ranan da suka dawo the next Abdul yakoma school da sassafe AFRAH da Afifah ma suka nasu makaranta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka dai kwanaki sukai ta tafiya kowa abinda ke gabanshi yakeyi, AFRAH na karunta sosai afanin business dinta kuwa kulin kara pupular takeyi abin gwanin sha'awa</p><p> </p><p><br /></p><p>Yau haushe duk ya ishe AFRAH sai tsaki takeyi ADULNASEER yace sai wani week d'in zai dawo ga Daddy ma tin da ya tafi ghana yau satin shi d'aya amma bai dawo ba tsaki takumayi sanan ta yafa mayafin jallabiyanta ta dau bag dinta tafice daka bedroom din</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Parlor taga Mommy nan take sanar da ita zataje gidansu HUSNA da Zarah nan Mommy ta fara masifa wai bata fada mata kan lokaci ba, ita dai AFRAH batace mata komai bah har tagama masifanta kana tachai taje, a compound taga yaya Suleiman na waya kirr ya kafeta da idanu bata bita kanshi ba tayi gaba abinta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Side Daddy kam kud'i sosai ya narka a wanan business din ba na wasa bah, kaya ney dai za'arika turomai dashi daka chan Ghanan wanan business nashi ney shi kadai bakaman wanchan ba da suka hada hannu da Alhaji Yusuf, kwanan shi tara yau yagama duk wani abu da zai yi duk wani kudi yagama bayarwa, yau yake shirin dawowa sai kuma ya jira isowan kayan Nigeria</p><p><br /></p><p><br /></p><p> K'arfe 11 dai dai girjinsu ya sauka a malan Aminu kano, babu bata kolaci ya kira deriver shi take kano suka sauki hanyan Kaduna</p><p> Lafiya suka iso kowa yayi Murna da dawowan Daddy d'an bay taba dadewa haka a tafiya ba sai wanan, nan da nan AFRAH ta shiya mai tuwon semo miyan kubewa sai zobo, sai da Daddy yayi sallah da wanka sanan ya zauna zaman cin abincin, duk suna zaune a parlorn bayan ya gama ya labarta masu komai Addu'a duk sukayi kana aka cigaba da hira. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Side UMMUabdulnaser shir suketayi na dawowan shi side dinshi tasa a kara gyarawa duk da a gyre yake duk wani abu da zai buk'ata sun tanadeshi dawo wanshi kawai suke jira</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ba su kadai suketa shirin dawowan shi ba Hadda AFRAH dan zan iya cewa ma tafisu </p><p> Yau Thursday kuma a yau dinne suke sa ran dawo wanan ABDULNASEER su Ummie sai Shiri suke tayi abinci kala kala suka shirya masa aunty Baraka ma shiri sosai tayi d'an lelensu zai dawo </p><p><br /></p><p> AFRAH ma a kitchen ta wuni yau d'an ko school bata shiga ba girke girke da snacks masu rai da lfya ta shirya mai da temakon y'an aikinsu ko da Mommy tashigo cikin din taga irin girkin da AFRAH keyi fad'a tafarayi wai tacika kankanba da iyaya ita dai bata ce komai ba</p><p> Tana gama kammala komai tabama drivernsu ya kai gidan kasan cewar tasan gidan Mommy takan aike shii</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ko da Ummie, Abbah da Anty baraka da Ameen yaron Anty baraka sukaga irin garan da AFRAH takawo sunji dadi sosai sunkuma k'ara yabawa da hankalinta</p><p><br /></p><p> 12 dai dai jirgin su ya sauka a Abuja, fad'an irin haduwan ABDULNASIR wallahi bata lokaci ney karshe ne wajen iya sa kaya sai wani smiling yakeyi wanda ke kara fidda kyauwunsa sosai ga wani dimple na musanman da yakeda wanda ko taya ne dole dimple din ya baiyana kanshi. </p><p><br /></p><p> Already dama ana jiran shi a airport din so yana sauka Mamuda yasamai kayan shi cikin both sanan suka dauko hanyan Kaduna. </p><p><br /></p><p> Lafiya lau suka iso kaduna kowa ya shirya cikin kwalliya, Ummie tayi kyau sosai haka Abbansu, Aunty Baraka da Ameen(last week shima yadawo daka China) su Humairah da Aisha ney kawai basunan sai gobe Friday zasu shigo suma. </p><p><br /></p><p>Cikin farin ciki ABDULNASEER ya had'a Ummie da Abbabsu yayi hugging suma hugging dinsa suka suna samai albarka, bayan ya sakesu wajen Aunty baraka yanufa itama yayi hugging dinta ita hugging dinsa tayi tana samai albarka shida Ameen ma hugging din suka suna yima juna Smiling nan duk suka shiga cikin Parlon gidan cikin farin ciki sallah suka farayi sanan aka zauna cin abinci</p><p><br /></p><p> Anci an sha cikin barkonci familyn nasu abin sha'awa abincin AFRAH sosai ABDULNASEER yaci shii sai dariya da tsokanan shi sukeyi shidai sai smiling din jin dadi yakeyi</p><p><br /></p><p> Bayan sun gama side dunsa yanufa shi da Ameen Sim din shi na Nigeria yasa ya kira Habibiyanr shi AFRAH hira sosai sukayi sanan sukayi sallama</p><p><br /></p><p> Wanka yayi sanan ya kwanta dan hutawa, washe gari suka shirya shida AMEEN suka nufa gidan su AFRAH da uban tsaraba bana wasa ba har ciki suka shiga suka gaida Mommy itama suka diremata nata tsara ban, ranan hira sosai sukayi da ABDULNASEER da AMEEN cousin dinsa kuma sunsamu tarba mai kyau dakawa wajen AFRAHN</p><p> sanda Suleiman ya hanga AFrah Da su Abdulnaseer Jiyakeyi kamar yayi hauka gaba daya hankalin shi a tashe yake ya kasa zaune ya kasa tsaye suko bama su ma lura da shi bah, haka suka sha hiransu cikin kwanciyan hankali.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A wanan satin Daddy kesa ran zuwan kayan shi na Ghana amma shuru kakeji babu wani bayani duk wani hanya da zaisamu wani information babu sun kule shi, ga kayansu da alhaji Yusuf ma shuru har yanzo babu labari Daddy baima kowa zancen ba yana dai ta Addu'an kawai</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau Wednesday Daddy zaune a parlornshi yana tunani AFRAH ce tashigo parlorn da sallama, waje tasamu ta zauna kana ta k'ara gaisheshi ya amsawa yayi cikin sakin fuska da fara'a nan take sanar da shi zuwan familyn ABDULNASEER daddy yayi mamaki saboda Mommy tachai babu wani tsayayen da ke zuwa wajen AFRAH daddy bai nuna ma AFRAH komai ba yachai Allah kawo su lfya sai sanar da yan kstsina, AFRAH na barin Parlon side Mommy yayi bata parlornta direct bedroom dinta yayi xaune ya ganta kan bed tana waya zama yayi yana jiran tagama wayan, nan da nan kuwa Mommy ta sallama da kawarta kallan Daddy tayi kana tachai" Lafiya kuwa na ganka haka? "</p><p><br /></p><p>"Lafiyan kenan, mekika ce dani game da zancen AFRAH? "</p><p><br /></p><p>"bangane ba, mekake nufiney? Mekefaruwa? "</p><p><br /></p><p>Wani wawan kallo Daddy ya watsa mata kana yace" kin ce dani bata da wani tsayayye, toh yanzo tazo take sanar dani Saturday yan uwan yaron zasuzo, amma kince ke baki sani ba wallahi Bilki kiyi hankali da duniya wlhy kuwa"</p><p><br /></p><p>"Kaman ya nayi hankali da Duniya?nifa ban gane kanka ba komai in kan yaranan ne karinka zakewa kenan abinda ko yaran ka na cikinka baza kayi hakan ba"</p><p><br /></p><p>"Yara dai duk nawa ney ni keda iko dasu bawani ba, kuma yaro ko ma na wanene ba d'an uwanka ba bakasan mai zai zama nan gaba bah d'an haka duk abinda kikayi dai dai ne, sai kikassnce cikin shiri dan ran Saturday xasu zo" Daddy ya karasa maganan yana barin bedroom d'in</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wani wawan tsaki Mommy taja kana tace wanan" mstsalan kune tinda yara naka ney ai" </p><p><br /></p><p>Daddy ko yana fita daka bedroom din side dinsa yakoma phone din shi ya jawo ya shiga k'ran yan uwansa ya fad'i masu cikin hadda Uncle Junaid dukkansu fatan Alkhari sukayi gami da Addu'an kaiwa lokacin lfya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Suleiman yashigo bedroom din yaga Mommy sai masifa takeyi ta inda take shiga ba tanan take fita bah, zama yayi bakin bed dinta kana yace "please mommy kiyi hakuri koma menene"</p><p><br /></p><p>"Har ni Daddynku zai fad'a ma bakar magana kan Auran wata AFRAH chan mainene nawa ciki? Wanan ai damuwarsu ce ba tawa bah"</p><p><br /></p><p>Tinda Suleiman yaji Mommy tachai Auran AFRAH gaban shi ya fad'i kallan Mommy yayi bakin sa na rawa yace" au.. ran AF.. RAH kaman... Yaya? "</p><p><br /></p><p>"Duk kawanu rud'e bakayi interview d'in bane ko yaya? "</p><p><br /></p><p>"Naji kaman kince AFRAH aure zatayi"</p><p><br /></p><p>"Ehhhh aure zatayi menene naka a ciki? "</p><p><br /></p><p>Sulaiman bai bata amsa bah yabar bedroom d'in cikin sauri kaman mahaukaci itama Mommy a haukacan ta tashi daka kan bed d'in tabi bayan shi kamar mahaukaciya....</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 54-55_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*wanan page din naku ney BIEBIE DEE NVLS GROUP I LOVE YOU All with all my heart* 💞 💞 </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*F*atyy na karatu babu laifi sai dai matsalan ta tara friends, friends gare ta hadda na tashin hankali kashi tanaso a ce da ita she's classy shiyasa kulin cikin siyan kaya take da kwalliya kulin cikin requesting kud'i take waje Daddy. </p><p><br /></p><p> Wasu shegun friends tayi Haneefa da Fa'izah yan gayu ne na masifa dan sunfi Fatty nesa ba kusa ba shiyasa take masifar san su problem din su basa san karatu d'an yaran masu kud'i sosai ita kuwa duk abinda sukeyi birgeta sukeyi shiyasa take shishige masu ko kadan Fatty bata duba irin karatun LAW natsuwa yakeso da mai da hankali burinta ita dai tafita da dasu Haneefa </p><p> Yanzo haka makeup suke tayi zasu shiga 2lip cin abinci</p><p><br /></p><p>"Babes i don't understand naga kuna shiri ne kuma kunsan munada test fa" Fatty tace</p><p><br /></p><p>Kallan ta Haneefa tayi kana tace" i don't zan shiga lecture yau coz i have something to do"</p><p><br /></p><p>" wat u mean? Bazamuyi test din ba kenan? "</p><p><br /></p><p>" babe in zakije just go n dress up, akwai important person da zamu had'u a chan ne, da kike maganan rest nariga nayima lecturer magana bamuda case da wanan" Fa'izah tace tana sa eye maskara</p><p><br /></p><p>" oky tohm bari na shirya" Faty tace </p><p><br /></p><p>Duk sun shiya tsaf cikin gown na material ku na kunga dressing nasu kasan manyan yara ne dan sun had'u babu karya bag n shoe duk gucci ne kasan newan su Haneefa a garin abuja suke amma gida sosai da mota iyayansu suka samasu a gidan </p><p> Nan suka nufa 2lip Fa'iza ce ke driving, suna ina suka samu waje suka zauna abinci mai rai da lfya sukayi Oder sunan zaune wasu hadad'un maza masu jii da gayu da kuma kud'i suka iso nan da nan Haneefa taje tayi hugging d'aya cikin su ita dai Fatty tana kallan ikon Allah</p><p> Gaiswa sukayi da samarin Fa'izah ce ta kalle Haneefa kana tace" baby zan wuce Najeeb na jirana"</p><p><br /></p><p>"Oky take care"</p><p><br /></p><p>Kallan Fatty tayi sanan tace" sai mu had'u a gida" nan Fa'izah ta wuce</p><p> Hira sosai akai tayi tsakan saurayin Haneefa Majid da Fatty sai kuma friend din Majid din Musty ganin irin haduwar su yasa Fatty sake jiki da su, kafin su bar wajen sai da Musty ya amsa Number Fatty wai yana santa dadi wajen Fatty ba a cewa komai tasa mu mai kudi, sai da su Musty suka kaisu shopping a wani shegen super market na yariyan Indimi </p><p> Sai dare suka dawo gida, abakin Fa'izah takeji wai Musty babanshi tsohun minister ne, wani dadi ke ziyartar zuciyan Fartyy sai yanzo tafara yadda da zancen Mommy ashe dole ta aura mai kudi ashe mijinta zaifi ABDULNASEER saurayin AFRAH, ai cikin dare takira Mommy take labarta mata tasamu Musty murna sosai Mommy tayi bana wasa ba habaici tai tayi a gida</p><p><br /></p><p> Haka dai rayuwan Fatty ya kasance a school kwalliya da gayu da bin friends kawai tasa a gaba karatun sama sama ney dai, dating dinta da Musty na tafi yanda yakamata kud'i sosai yake kashe kata kuma yachai wai zai aureta ita dai Fatty dadi kawai takeji. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>AFRAH kam maida hankali tayi sosai kan karatun ta kuma fahimta rakeyi sosai dan duk department din microbiology ansanta, haka a fannin snacks tayi fice dan ansan ta sosai a wanan fannin </p><p> Ko kadan bata jira sai anyi mata abu tinda ta lura Mommy basu take ana yimata abin arziki ba </p><p> Tanada kudunta a account in Daddy ya bata tayi godia in bai bada bah tayi ma kanta mommy kanta mamakin irin kudin da AFRAH kesamu takeyi sau da yawa wasu daka side Mommy zasu nuna sunasan cake ko wani abun amma sai Mommy ta kushe abun tachai ai gara suje dalema ko frch cafe sunfi iyawa kuma hakan da takeyi bashi kesa mutane kin zuwa bah kulin qaruwa ma sukeyi mutane</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> </p><p>Lamarin Hafiz a Turkey kan sai dai addu'a babu karatun da yake tsinanawa sai yawo da bin friends ga danfaran mutane ta online school din da yake zuwa ma sun korashi amma ko fada bayyi a gida ba sai da daddy yazo duba shi ne yaji wanan lamari ranshi ya baci sosai amma babu yanda ya iya sai addu'a bai bar k'asan bah sai da ya nemamai wani school din ya gama mai duk wani abu da zai bukata fada da nasiha sosai Daddy yayi mai sanan yabaro k'asan ko HAFIZ yaji ohoooo</p><p><br /></p><p>Kafin Daddy ya dawo Nigeria Hafiz yakira Mommy ya shirya mata k'arya da gaskia ya fadi mata sai zage zage takeyi wai an cuceshii</p><p><br /></p><p> Ko da Daddy ya dawo yake sanar da Mommy halin da Hafiz yasa kanshi ciki firrr Mommy tace wai manak'isa akayi mai wasu friends dinsa wai saboda sunga yafisu kud'i "kee a rayuwan ki baki san gskia barin ma kan yaranki, sam baki nuna masu rayuwa baki ganin yanda ABDULRAHIM ke tafiyar da rayuwan sa inace sa'an Hafiz ne? Amma shi kulin cikin matsala ake da shii" daddy yace</p><p><br /></p><p>"A'a walhy kar kayi ma yarana baki insha Allah kanan zakaga cigaban da zasu samu, kuma da kake xacen Abdulrhm shi kaje makarantar tasu kaga yana karatun ne? Kawai ni banasan haka "</p><p><br /></p><p>Idanu kawai Daddy ya zuba mata chan yace" Allah shirya mana yakuma sa mudace" </p><p><br /></p><p>"Ameen " tace tana bat'a fuka. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p>Yau Fatty zata dawo hutu kasan cewa anyi exam na first semester amma bana tunanin Fatty zata fido wani result mai shegen xafi, AFRAH tayi mata fried rice da salad sai farfesun fresh fish sai kuma cup cakes datayi mata Mommy sai dadi takeji anyi ma yar lelenta girki </p><p> Sai 2 Fatty ta iso gidan Murna sosai Mommy tayi Afifah kam ko a jikinta masifa takeyi ma wai masifaffiya zata dawo</p><p> Bayan Fatty tayi wanka taci abunci labarin Musty taita bama Mommy haka har bedroom tasa mu Afrah taita bata labarin Musty addu'a AFRAH tayi masu na ALLAH yabar su tare</p><p> Tadawo da kwana 3 Musty yace zai zo rokon AFRAH tayi kan dan Allah tayi mai girki dayake Afrah nada pure heart haka ta fidda ta kunya tayi Musty girki masu rai da lfya bayan Afrah tagama komai da temakon Afifah da Salamatu Fatty ce tashigo kicin din kan warmers din abin cin tayi da yanda AFRAH tayi decorating wasu tayi smilling"kai gaskia sis nagode dole na bada 10k"</p><p><br /></p><p>"Wa zakibama 10k din? "AFRAH tayi tanbayan tana kallanta da kyau</p><p><br /></p><p>"Kee mana Mommy tace ai business kikeyi"</p><p><br /></p><p>"Allah kiyaye na amsa kud'in ki wallahi"</p><p><br /></p><p>"Ai kuwa dole ki amsa tinda sana'ar ki ney"</p><p><br /></p><p>"In da kinsan zaki biya kud'i ai dawa wani restaurant din kikaje kika siyo abincin sai ki biyasu da kayau, nidai baki da abinda zaki bani coz kin wuce haka a wajena so kirike kudin kii"</p><p><br /></p><p>Maganan AFRAH na karshe ya bata mata rai, a zuciyan ta tace bani da abinda zan bata? Niko keda abubuwan bata sai ma nan gaba dandai sana'ar girke girke bazai kai ta ko ina ba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Musty yaji dadin tarban da Fatty tayi mai Mommy har parlorn baki tazo suka gaisa da Musty(niko biebie nace Hmmmmm) </p><p> Shoppin sosai yayi ma Fatty tunda ya lura abinda tafi so kenan sanan kud'i 100k wai a bama Mommy </p><p> </p><p>Ko da Mommy taga uban shopping gode ma Allah tafarayi gakuma kud'i</p><p><br /></p><p>"Kinga abinda nake fad'a maki kow Fatima? Da zaki wani sa ABDULNASIR a rai yaushe zai iya irin wanan shopping din shi? Naji labarin ma su UmmuAbdulnaser din arzikin baka man daa ba"</p><p><br /></p><p>"Ohoooo wanan kuma matsalan Afrah ce dama a wahala zata kare"</p><p><br /></p><p>"Aifa ai sai kirika temaka mata,tinda nasan daya dawo za'azo neman auranta"</p><p><br /></p><p>"Chan su kara ta kuwa"</p><p><br /></p><p> Kwanan Musty 5 a kaduna amma kulin zaizo sai yazo da uban shopping ita dai AFRAH nata ido, randa zai koma ne yake cemai Fatty yanasan ganin Daddyn ta dan shi auranta yakesan yayi, Fatty tachai yayi tafiya amma yadawo zata sanar dashii, koda Mommy taji wanan labari har rawa tayi da buda</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A wanan hutun ne AFRAH taje katsina kwanan ta 5 sukaka dawo, suna dawo wa suka fara shirye shiryen komawa school randa akayi resuming Affrah takoma FATTY kam saida takara kwana 3 sanan takoma abujan</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ta koma da kwana 2 Daddy ya dawo tarba mai kyau yasamu bayan yaci abinci ya huta mommy ta shiga bashi labarin Musty Addu'a yayi kana yace" sai kisanar da ita nadawo ai" </p><p><br /></p><p>"In dai zancen bikin ya kankama dubai nakeso muje siyo kaya daka nan sai naduba Suleiman duk da yakusa dawowa"mommy tace</p><p><br /></p><p>"Sai kiyi addu'an kaiwa lfya kafin kifara wani burin" Daddy yace</p><p><br /></p><p>"Toh Allah tabbatar mana da Alkhari"</p><p><br /></p><p>"Ameen ita AFRAH babu wani tsayayyen ney? "Daddy yace yana kallonta</p><p><br /></p><p>Wani miyau Mommy ta hadiye kana tace" ni gaskia ban sani ba dan bata fadamin damuwanta bata dauke ni matsayin uwa ba sam"</p><p><br /></p><p>Shuru Daddy yayi baichai komai ba ya lura indai lafin yaran wasu ne Mommy ta rinka zakewa kenan</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kwanan Daddy 4 yawuce Lagos Snacks masu dadi AFRAH tayi Daddy ya tafi tasu 20k ya bata kudin da zatasa mai a mota dan shi bai san Mommy ta hana a koya mata Motan bah, godia tayi gami da Addua Albarka ya sa mata kana yawuce</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sai da yafara zuwa zaria dan duba Abdulrahm, Alhamdulillahi yasamu Abdul lfya kuma yana karatu sosai dan sune yan 400lvl kanshin Abdul yayi mamakin zuwan Daddy amma sai bai kawo komai bah ya nuna jin dadin shi kan ziyaran da yakawo mai, bai bar zarian bah sai da yabiya ta gidan surukan sa dan kwasan gaisuwa aikuwa Alkhari sosai Daddy yayi masu sai godia da sa mai albarka sukeyi dan Mommy ba cika zuwa takeyi ba bare ma tamasu wani abin arzikin(dama Mommy da rowa.. 🤣🤣) sai da ya cikasu da abin arziki sanan yabaro xarian, katsina yayi nan ma sha tara na arziki yayi ma yan uwansan daka nan yabi jirgin Lagos yawuce. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Soyayyan Fatty da Musty yana tafiya yanda ya kamata dan duk wani abu da yasan tanaso yana kokarin yimata kulin cikin yimata shopping yakeyi ga uban kud'i dake cusa mata abinda takeso dama kenan</p><p> Karatu kuwa tanayi babu laifi gayu kuwa sai abinda yayi gaba dan in kunga Fatty bazaku ganeta ba sabida hud'uwarta classy ce ta karshe ni kaina na sara mata wajen iya dressings(kundai san yan ABUJA.. LOL) </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>AFRAH ma da ABDULNASEER suna tafiyar da soyayyan su cikin natsuwa da kwanciyan hankali babu karya ko kadan a tsakaninsu tsakani da Allah suke zaune da junansu, duk family ansan AFRAH dayadawo za'azo ayi magana.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>ABUJA</p><p><br /></p><p>Farty da Musty ne zaune a parlornsu kasan cewar ta dade databar hostel tadawo gidansu Haneefah kallanta Musty yayi kana yace"baby next week fa uncles dina zasuje gidanku kinsan nakosa na aureki i love you so much"</p><p><br /></p><p>Sai datawa juya eyes kana tace " i love you more n u knw dat, nariga nafama Daddy so don't worry babu wani problem"</p><p><br /></p><p>"Oky Allah kaimu baby"</p><p><br /></p><p>"Ameen sweetheart" Farty tace</p><p><br /></p><p>Hiran soyayya suka cigaba dayi sai 11 yatashi dan tafiya, har gaban motan shi tarako shi hugging dinta yaya sosai kana yashiga fada mata kalaman soyayya" i love you so much baby u ar my everything" sun dade a haka kana yasaketa smiling kawai Fatty keyi dan a ganinta irin wanan ba komai bane, ko da yashi mota blowing kiss yaita mata itama tana yimai sai dataka yabar gidan sanan takoma ciki</p><p><br /></p><p> Kwanciya tayi sama kujera tunanin irin daulan da zata shiga takeyi smiling mai kyau tayi da tanuna wai su ABDULNASEER basuda kud'i kamar da, dataga tunanin ba mai karewa bane tashi tayi tanufa bedroom inda taga su Haneefa nata waya, wani book ta dauka tafice a bedroom din.</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mommy tinda taji zancen Musty zai turo rasa inda zata sa kanta tayi y'arta zata aura mai kud'i </p><p> Musanman taje har gidan UmmuAbdulnaseer ta labar tamata smiling Ummie tayi kana tace" abu yayi kyau Allah ayi damu, muma ai Abdulnaseer Na dawowa zamuzo neman auran saura wata d'aya yadawo ai"</p><p><br /></p><p>Ameen ameen Ummie Allah dawo mana dasu lafiya Suleiman shi nan da 2weeks zaidawo"</p><p><br /></p><p>"Allah dawo dasu lfya" Ummu tace</p><p><br /></p><p>Hiran yanda bikin na yaran nasu zai kasance sukai tayi Ummie na saka zancen AFRAH sai Mommy ta dauke wuta ko ta chanza maganan Ummu dai tana kanin ikon Allah haka dai sukaita hira sai 5 Mommy tayi haraman tafiya, har bakin mota ta rakota sai dataga Mommy tabar gidan takoma ciki tana mamakin hali irin na hajiya Bilki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ranan da family da Musty sukace xasuzo Saturday ney, ranan Mommy babu zama tahana AFRAH sakat girki kala kala kala da iri iri ta sata tayi masu ga uban zama'a da Mommy ta gayyato wai suzo yau za'akawo gaisuwan Fatima gida fam da mutane dan ma akwai su salamatu, Atika, safiya da Lantana da da k'ara man wahala zata sha bah sabida uban aikin da tayi ranan ba na wasa bane haka dai suka shirya girke girkenan a babban parlor na bak'i ga uban snacks da juice iri iri sabida samun waje hadda wanda zasu tafi dashi Mommy tasa ayii duk a ka jeresu a parlorn baki </p><p><br /></p><p> Da misalin k'arfe karfe 4 bayan salan la'asar uncles Musty suka iso su 4 ney sai Aunties dinsa su 3 Daddy ma su 3 ne shii sai yaron Inna Rakiya uncle Isma'i da uncle Musa duk Isma'l yayane a wajen Daddy Musa kan k'ani ne </p><p> Tarba na mutunci sukayi masu nan uncles din Na Musty suka gaba tar da abinda yakawo su nan dai su Uncle Isma'l suka ce sunbasu nan aka saka ranan biki nan da wata 2 Addu'a sukayi Allah ya kai su lokacin lfya, su Uncles Umar basu iya cin komai ba sai drinks da snacks </p><p><br /></p><p> Side din Mommy ma hakan ne ya kasan ce tarba mai kyau su anty Lailah suka samu wajen Mommy haka dai a ka rabu cikin girma da mutunci </p><p><br /></p><p> Fad'an irin kayan sa ranan Fatty bat'a lokaci ne kaya ney hadda na hauka da mara sa anfani ga kuma akwatuna 3 wai kayan NAGANI INA SO abun dai sai wanda ya gani </p><p> Tanan rawa da babu irin wanda Mommy batayi ba yarinyan ta tayi goshii ranan saura 2weeks Suleiman yadawo ita dai AFRAH nan taga ikon Allah</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bangaran familyn Musty kuwa mamakin inda yasamu y'ar mutunci sukeyi kasan cewar sun san halinshi, Baban shii yafi kowa Murna da wanan auran da Musty xaiyi(nidai nace Hmmmmm) wasu daka cikin familyn Addu'a suke Allah sa auran yazama sanadiyan shiryuwan saa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Rayuwa nata tafiya haka lokacin nata k'aratowa haka abubuwa nata faruwa</p><p> Yau ko gobe ne suke sa ran dawowan Sulaiman Murna wajen Mommy ba a magana ita AFRAH ke lissafe ABDULNASEER dinta ma nan da 10days ko 1weeks zai dawo shiima, girki dai sukayi masa dai dai ba wani mai wahala ba sai cupscaks masu kyau, kowa ya hallara a gida Abdul ma yadawo cikin ikon Allah kuwa ranan Sulaiman ya iso Nigeria da nan da nan Bala driver, Abdul da Afifah suka nufa kano dan dauko shi kasan cewar nan ya sauka </p><p><br /></p><p> Sai 6 Na yamma suka iso kaduna cikin koshin lfya, inkunga Suleiman baza kugane shi ba yayi wani fresh ga kyau da ya kara abundai sai wanda ya gani(nii baxan iya bayani ba) hugging dinsa Mommy tayi gami da cewa "welcome home my son" </p><p><br /></p><p>Smiling yayi yayi hugging dinta sosai kana yace" i miss u Mommy"</p><p><br /></p><p>"I miss you more sweetheart" mommy tace tana wani Murmushi nan suka isa ciki Sulaiman sai kallan gidan yakeyi ashe haka Daddynsu yasamu cigaba</p><p><br /></p><p>Daddy ma hugging dinsa yayi yana samai Albarka shima kara rungume Daddyn yayi yana amsawa da Ameen</p><p><br /></p><p>"Saura Muu" yaji maganan daka sama yana juyawa yaga AFRAH da Afifah a tsaye Afifah sai wani murguda baki takeyi</p><p> Kasowa wajen yayi yayi hugging Afifah yana cewa" i miss you so much lil-lil"</p><p><br /></p><p>" bawani bayan na shiga jss1 ma baka sani ba"</p><p><br /></p><p>"Gashi yanzo nasani"</p><p><br /></p><p>Jin sweet voice din Afrah yaji tana gaidashi tana wanan smiling din nata, kallanta ya tsaya yii for some second kaman yana san tuno wani abu Mommy da ke jefe kaman ta dauke AFRAH da Mari dan haushi dafashi da mommy tayi ne yadawo daka duniyar sunanin da yatafi jan hannunshi tayi suka shiga ciki, Abdul, AFRAH da Afifah suka mara masu baya Daddy dama tuni ya shige ciki. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_sweetheart mekuke ganan zai faru?? Suleiman yadawo, Abdulnasser xay dawo soon, ga Fatty zatayi aure da Musty duk ya zata kasancee neeeeey wai??????_</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 58-59_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*wanan Page din naku ney AUNTY MAIJIDDAH MUSA & A'ISHA MUH'D(AUNTY) thank you so much for d love, care and support, thank you so so Much may Allah guide and protect you Always ALLAH barmu tare,Thanks alot sweethearts*❤❣❤❣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*S*ide din shi direct yayi bai tsaya ko ina bah sai a bedroom dinsa, yana shigowa itama Mommy ta shiga" wai lafiyan ka kuwa?daka magana duk kabi ka rud'e" Mommy tace tana kallan shii</p><p><br /></p><p>"Lfyalau" yace yana k'okarin shiga toilet </p><p><br /></p><p>Takai tsawan mintin5 a bedroom din kana tabar dakin tana wasu tunani haka har takai side dinta </p><p> Zama tayi bakin bed miss called na FATY tagani har 5 nan da nan tashiga dialing number nata ringing 3 ta dauka hira suka danyi nan Mommy ke sanar da zacen zuwan familyn ABDULNASER neman auran AFRAH Fatty cewa tayi su suka sani ita bai dameta ba hakadai sukai ta hiran yan da biki zai kasan ce dan lokaci nata matsowa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> B'angaran AFRAH kuwa ranan hiran su suka sha da Adulnaseer sosai, haka AFRAH takasan ce cikin farin ciki ranan d'an ita kanta tasan tana san ABDULNASEER kaman yanda yake santa sosai</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A katsina ma Mami tayi murna sosai da jin zancan auran AFRAH ya tasu nan ta sanar da k'anuwarta anty Safiya(maman Heeshmer) zancan babu b'ata lokaci Maman Heeshmer ta baza a d'angi kasancewar Familyn aunty Rabi duk mata ne, dan da nan suka kira meeting d'an susan abinyi tun da wuri(niko Biebie nachai AFRAH yar gata... Hmm) </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Inna ma sosai tayi murna takuma sa Albarka a k'asan zuciyanta tana taya Sulaiman bakin ciki Amma babu yanda ta iya sai hakuri haka Allah ya tsara </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Side din su UMMUABDULNASEER ma shir sukeyi sosai d'an basu tab'a aurar da kowani yaro cikin family ba kancewar bawani yawa suke dashi chan ba so fadan irin shirin da sukeyi ma b'ata lokaci ne gskia. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tin ran Friday Zainab yarinyan uncle Isma'i ta diro kaduna haka ZARAH da Husna da Aysha gidan suka wuni dan taya AFRAH aikin yin wasu snacks, AFIFAH cikin su tashige ta zauna kaman friends dinta sai manyance takeyi wanan ranan Mommy ko fitowa batayi bah tana bedroom, amma duk hayani yaniyansu a kunnen ta mamakin inda AFRAH tasan mutane haka takeyi wanda ko Fatty da bata aiki sai bin Friends bata da irin friends na AFRAH gasu duk masu hankali da natsuwa ga wayewa da iya kwalliya </p><p><br /></p><p> AFRAH na zaune saman freezer tana waya da ABDULNASER Lantana tashigo kikcin din kallan AFRAH tayi kana tace" Antyn Afifah hajia na kiranki" sallama tayi da ABDULNASEER sanan tawuce kiran Mommyn</p><p><br /></p><p> Sallama tayi bakin k'ofan sai da Mommy ta amsa sanan tasa kanta cikin bedroom din" gani Mommy"AFRAH tace tana gyra zamanta</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sai da Mommy ta kalleta da kyau sanan tace" kee yanzo d'an bakida kunya d'an za'azo neman auranki shine duk zaki baza magana a gari kin tara mutane fam a gida babu ko kawaici"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mommy wallahi ni ban kirasu bah, Zainab ce takira Husna Da Zarah wai suzo sutayamu wani aikin cakes da zanyi shine kuma sukazo tare da sulXee bako, jiddah,hafsah, da Hawee, aysha kam zuwa kawai tayi duk basu san zancen bah ma sai dasukazo Zainab kefada masu"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hmmmmm kedai kika sani, kunya dai abu ney mai kyau d'an bata zuwa sai da alkhari"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kiyi hakuri Mommy"</p><p><br /></p><p>"A'a nemene nawa ciki? fata ma zanyi sai asha shagali lafiya" handbag d'an ta tadauka gami da gyara mayafinta tana shirin fita, bin hayanta AFRAH tayi har suka sauko k'asa "sai kindawo Allah tsare"AFRAH tace</p><p><br /></p><p>"Ameen" Mommy tace, da idanu AFRAH tabita tana mamakin halin Mommy na juya abu yanzo yanzo ta juyama fassara da ma'ana dataga tsayuwan bamai k'arewa bane yasa tayi cikin, haka dai sukai ta aikin su har suka kamma duk abinda zasuyi yau, Husnah sai sana'arta takeyi watou daukan selfie haka Xee bako ma san camera kaman mee... 😂 bayan sungama bedroom din AFRAH sukayi AFIFAH nabiye dasu sallah suka farayi sanan AFIFAH tajuyo masu indomie din da tadafa a babban tray wanda yasa vegetables ga eggs da ta yayyaka a kai decorating sosai tayi ma wanan indomie(rainon AFRAH) nan ma kafin a fara ci sai da HUSNAH ta dauki indomie dinan picture, haka suka zauna suka ci abinsu ga juice mai sanyi suka kora da shii, bayan sun gama kwashe kayan Afifiah tayi sanan ta gyara wajen tass dawowa tayi tazauna kusa da zarah, kallanta AFRAH tayi sanan tace" oya madam tashi ki dauki qur'aninki kije kiyi hadda gobe Saturday" babu yanda tayi haka ta dau Qur'anin tayi gaba, nan aka bud'e chapter na hira kowa nata bada labari nan Husnah Kebasu labarin nata saurayin hanci da baki Afrah da zarah suka sake suna kallanta d'ansu basu tabajin labarinshi ba</p><p><br /></p><p>"Amma ke kam baki da hali, yaa ma akayi bamu sanshi ba wai" AFRAH tace tana watsama Husnah wani kallo Zarah kow taguma tasa d'an takasa magana</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Babes dama zan fad'a maku ai, kawai da bama tare bai dade sosai damuka dawo dating ba, shiyasa inyazo daukana anjima sai duk nakaiku kugaisa"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ohhh toh Allah tabbatar mana da alkhari"Zarah tace</p><p><br /></p><p>Duk suka amsa da ameen, haka dai kowa yaita bada labari saurayin shi( kun dai san emmata insun had'u hiran kenan) k'afe 5 saurayin Husna IMRAN yazo gaba d'ayansu suka fita a kagaisa takuma gabartarmai dasu sanan sukayi ma juna sallma suka wuce, basu kai ga shiga ciki bah Mahmoud na Zarah shima ya k'arasu gida ta koma ta dauko bag dinta yayinda su AFRAH suka k'ara wajensa dan gaisawa, tana fitawo itama tayi masu sallama tayi gaba, aysha, Xee bako,jiddah kam da kansu suka wuce dan nasu fiance's din basunan sunyi tafiya, haka dai suka rabu AFRAH sai godia takeyi masu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_washegari_</p><p> K'arfe 12 a garin kaduna yayi ma su uncle Isma'l, uncle musa, uncle Junaida da Uncle Umar brother din Mami, tarba mai kyauwan gaske suka samu dakawajen Daddy ga abinci mai dadi da AFRAH da zainab sukayi masu, Mommy ma har side d'in bak'i taje tagaidasu babu yabu babu fallasa, bayan sundawo daka masjid zama sukayi suna tattauna maganan auran yaran Uncle Junaid ya yaba sosai da hakin mutunci da karamci irin na daddy, sai bayan sallan la'asar bak'in nasu suka iso dai dai lokacin da akazo neman auran Fatty, ganin irin Motocin da keshigowa gidan suna parking yasa Mommy dake tsaye ta sama sakin baki da hanci tana ganin ikon Allah, sai da motoci 6 suka shigo gidankuma duk babu na banxa ciki, maza uku ne suka fara fitowa nan da nan su Daddy suka taresu cikin fara'a jagora sukayi masu har parlorn b'aki, kaman Amafarki ta hangi _Aunty maijiddah_cikin wani arnan lace wanda ak'alla kudin lace dinan yayi 150k gawani mayafi da handbag duk zafafa, chan kuma ta hango wasu mata su 3 *aunty Baraka* ce a gaba itama cikin wani masifafan material wanda nakasa kane kanshi ga mayafi, talalmi da handbag duk masu shegen zafi sai sauran mata Biyun Atanpace jikinsu super Holland suma sunyi kyau sosai duk Mommy na kallansu takasa motsi babu abinda yafi bata mamaki kaman ganin aunty Maijiddah cikinsu, cikin sauri Mommy takoma bedroom chanza kayan jikinta tayi zuwa wani lace(😂😂😂 Mommy kenan...) Toh babu laifi tadanyi kyau</p><p><br /></p><p> Su Aunty Baraka kuwa parlorn k'asa suka ja birki, zama duk sukayi nan da nan Zainab da su Lanta, Salamatu, Atika da sauran y'an aikin gidan suka shiga jere masu kayan motsa baki iri iri da kala kala, kafin kuce mai sun cikasu a girke girke, snacks, drinks kala da ban da ban, (dan kansu yan akin gidan sunci burin wanan ranan dole su fidda Afrah kunya kaman yanda take darajasu da mutuntasu) bayan sungama gere duk abinda yakamata tsawa sukayi suka gaishesu sosai cikin ladabi duk suka amsa cikin Fara'a suna godia</p><p> Dai dai nan Mommy ta sakko tana smiling gami da cewa"sannunku sannunku, sannunku dazuwa, Latana ya kika barsu nan baku hauro dasu ba? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A'a nan ma yayi mungode sosai" inji Anty baraka</p><p><br /></p><p>Smiling Mommy tayi kace" duk dahaka banji dadi ba wallahi"</p><p><br /></p><p>"Babu komai" Ummu Safeey tace tana smiling ita ma, gaisuwa sukayi sosai cikin barkonci nan Aunty Maijiddah ke sanar da ita ai ita kawar auntyn angoce watou Aunty baraka, smiling Mommy tayi kana tace" kawai dai aunty ango" daria duk sukayi nan mommy ta k'ara gabatar masu da abinci, basuci abincin ba sai drinks da snacks, su Ummu Safeeya da aunty A'isha suka bukaci ganin Amaryan tasu, wani haushin Suka ba Mommy talura y'an boko ne iyayinsu yayi yawa, babu yanda ta iya smiling tayi masu gami da cewa "bari na kira maku ita"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>B'angaran su Daddy Ma Komai cikin Mutunci Da haramci sukayi komai d'an Familyn ABDULNASEER sosai suka yaba da halin girma irin Nasu Daddy da yan uwansa, haka suma su Daddyn sunyaba da halin mutunci irin nasu, Daddy yaso a had'a bikin gaba d'aya hadda na Fatima toh sai Uncle Umar yace yayi hakuri ba dan Daddy yaso bah hakka yahakura tsakani dai Wata daya da sati d'aya ne daidai, godiya sosai su Uncle Muhammad sukayi nan dai sukayi duk abinda yakamata kaman bada kud'in gaisuwa da na sara rana, godia suka kara yima junansu kana suka tashi Dan tafiya, kayan abincin tas drinks da snacks su Sunusi(yan aikin gidan) suka kwasu suka samasu cikin mota kasancewar basu tab'a komai ciki ba, godia suka k'arayi ka duk suka shiga mutocinsu, sai da Su Daddy sukaga fitan su gidan suka koma ciki da fara'a kunshe a fuskarsu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Side din su Mommy kam. Bayan Zuwan AFRAH gaishesu tayi ciikin ladabi da biyyah dakuma fara'a fuskanta, duk suka amsa cikin sakin fuska nan suka sa AFRAH tsakiya Aunty A'aisha(aunty) tace a daukesu pictures haka kuwan akayi Picturs suka dauka sosai ita dai Mommy tana ganin ikon Allah da sabon salo, _Aunty Maijiddah_ taceh" baki shigo bah pictures din namu ba Mommy" tana murmushi</p><p><br /></p><p>"Ai barin ku nayi kuyi da Amaryan taku sosai" tace hakan ne kawai amma ita tagaji da ganin sabon iskancin su, sai kace sunzo neman suran diamond ko gold </p><p><br /></p><p>Voice din Ummusafeeya ya katse mata tunani inda take cewa" kuma Amaryan namu mai kyau ABDULNASEER yayi dace ga hankali" daria duk suka kana sukace "Aikuwa dai Alhmdulillahi" gaba daya Mommy ta gaji dasu haushe suke bata iyayinsu yayi yawa hakan dai babu yanda Mommy ta iya haka tasha picturen nasu badan taso ba tawani had'e fuska babu ko d'an smiling babu(sai kace wata gunki😂) </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hmmmmmm fad'an irin kayan sa ranan da su ANTY BARAKA suka kawo bat'a lokaci ney wallahi ku kanku inda zaku ga irin kayan kuda kanku zakuce sun shiryama bikinan(toh abinda ba a tabayi ba) kayana sosai bana wasa ba, d'an komai buhu 2 suka sauke NAGANI INA SO kuwa yanda kukasan kayan lefen wata amaryan Mommy tuni tafara jin wani zafi zufa har zubu mata tacikin kaya yakeyi(yiriri nanayi injini💃😂) haka dai su aunty bakara suka bar gidan cikin farin ciki, bayan duk girke girken sun sashi cikin mota, Mommy dai bacikin kwanciyan Hankali ta rakasu ba, sai dataga fitansu gidan sanan tadawo ciki, k'ara hangan kayan kawai datayi yasa gabanta dad'uwa, bedroom dinta tayi cikin sauri watsar da mayafin jikinta tayi sanan tajawo phone d'inta Numbern Fatty tashiga dialing amma har yagama ringing batayi picking bah, sai datayi mata miss calls 8 amma duk no answer Mommy jitayi kaman zatayi hauka tarasa yanda zatayi, shawara ta chanza Numbern k'awarta Hajia Amina tashiga dialing ringing 2 kuwa ta dauka</p><p><br /></p><p>Wani dugon ajiyan zuciya Mommy ta sauke</p><p><br /></p><p>"Lafiya kuwa? " hajiya Ameenah tace daka can bangaran</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Toh da Sauki dai, yau akazo neman auran AFRAH da sa rana" Mommy tace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Toh sai maiyafaru? </p><p><br /></p><p>"Wai fa duk d'an kar abin yayi kyau yasa ban kiraku bah, kuma kinsan babu wata matan da zatazo min gida daka katsina ta zauna lfya wai d'an kawi xa'azo neman aure"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ni har yanzo baki fadamin komai ba, wani mugun abun yafaru ne? </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hmmmm hajiya wallahi inkinga irin kayan arzikin da suka kawo abin sai yabaki mamaki yanda kikasan wasu shahararrun masu kud'in Nigeria, rawan kan da sukarinka yi kuwa kaman sunzo neman auran diamond d'an bama zance gold ba, ko Familyn mijin da Fatty zata aura sun fisu kud'i amma basuyi irin abu haka kaman na wanan ba, wallah abun duk ya dameni" tak'arasa maganan kaman zatayi kuka</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Iko Allah amma Hajia nasha fad'a maki cewa AFRAH y'ar baiwa ce Allah ney duk yake bata wanan ba mutun bah, yakamata kigane haka mana, tin yarinyan na k'arama takeda wanan baiwar kike dakusheta amma hakan duk bai t'aba cigabanta ba, gaba d'aya kin raina ma yarinyan gashi tin ba a je ko ina ba cigabanta sai baiyana kanshi yakeyi kawai ido zakisa ki kalle ikon Allah"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tin da Hajiya Ameena tafara magana bak'in cikin Mommy ya k'aru gawani zafi da zuciyan takeyi mata, sai datayi gyaran Murya kana tace" sannu da k'okari dama kina zaune da ni ne bada zuciya d'aya ba shiyasa duk zakice haka, amma ba laifinki bane nawa da har na sanar dake damuwata, biki kuwa duka biyun babu wanda zaki halarta dan nanyi canceling naki daka cikin yan gayya" tana gama fadan haka ta kashe kiran</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Side din Hajiya Ameena kuwa daria tayi kana tace" sai bak'in ciki yayi ajalinki kuwa zancen kinyi cancel dina cikin yan biki ai inanan za'akawo mana I.V mayb ma muna meeting da uwar angon ko auntyn angon d'an haka sai yak'are maki chan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> FATTY takira mommy nan Mommy ta zayyano mata komai da irin kayan da suka kawo mamaki sosai Fatty tayi nan sai tace ma mommy zatashiga kadunan gobe kodan tazo taga kayan, tin 11 na safe Fatty ta iso kaduna, sosai kayan suka bata tsoro da kuma mamaki ranan dai wuni sukayi cikin bedroom suna maganganunsu dasuka saba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> AFRAH kam bata masan sunayi bah, hakan gabanta kawai taitayii, AFIFAH kuwa rawa tasha ranan hadda na ban mamaki saboda Murna, a rananne yan katsina sukayi masu sallama suka koma Sunday kenan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sulaiman yashiga tashi hankali sosai kasa hakura yayi har sai dayaje yasamu Daddy ya sanar da shii kallanshii da kyau daddy yayi kana yace" Meyasa toh tin tini baka sanar da ni ba sai yanzo da lokaci ya wuce? "</p><p><br /></p><p>"Daddy wallahi bansani ba ni kaina"</p><p><br /></p><p>"Yanzo dai lokaci ya kure sai dan kayyi hakuri Allah sa hakan ne mafi Alkhari duk da da hakan yafaru zanfi kowa Murna da farinci amma kayi Hakuri Allah zai musanyama da Alkhari kaji ko? Allah yayi ma Albarka ya kuma kawo ma tagari"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ameen ameen Daddy nagode sosai Allah kara girma"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ameen Sulaiman, yaushe ney tafiyankan naka? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nan da 3 days ne insha Allah"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah temaka yakuma bada sa'a, kila matar tachan bauchin inda zakayi bautan k'asan"</p><p><br /></p><p>Smiling kawai Suleiman yayi baice komai ba, nan daddy yake sanar dashi game da rashin isowan kayansu, kwantar mai da hankali Sulaiman sosai gami da Addu'a sosai Daddy yaji dad'i yaita samai Albarka, hira suka d'an yi kana Suleiman yabar side Daddyn. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Suleiman nafita Mommy nashigowa zama tayi tana karema daddy kallo, shima zaman shi ya gyara sanan yace" ashe wai Suleiman san AFRAH yakeyi sai yanzo yake sanar dani"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Bangane ba kamar yaa? Mommy tace tana zare idanu</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wai san AFRAH yakeyi amma baiyi magana da wuri ba sai yanzu, amma da hakan yafaru da nafi kowa murna wallahi"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Tabdi gam, gara da Allah yasa hakan takasance d'an bazaitaba yuwu ba wallahi, haa kawai yarinya duk tabi ta addabi rayuwa ta"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Amma ke bakida hankali, dama abinda na dade inason ji kenan gashi kuma yau kinfada, bak'in halinki da bak'ar zuciyar ki yasa Allah ya chanza mata da ABDULNASEER ba Sulaiman ba, kinbi kinsama yara ido kin rai nasu kina ganin baza suzama komai ba ko?toh ai sai ki hana in Allah yabasu kuma so nawa yaron da ba naka ba yatemake ka d'anka na cikin ka baima ba?" Ya karasa maganan yana watsama Mommy harara</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wai duk kan wayanan banzayen yaran ne yasa kake jifana da munanan kalamai? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"An jefeki da munanan kalaman ai baki da tunanin ne, kuma karki kuskura ki kuma kiran yarana da banzaye d'an ba banzaye bane su"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nice banziyar kenan ko alhaji?kan wasu yara chan kana cimin mutunci" takarasa maganan tana kuka</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Duk yanda kika dauka hakan ne, kuma ko a titi na tsinto su baici ki kalle idona kice masu yara chan ba, bare yaran d'an uwa na d'an haka ki kula sosai" Yak'arasa maganan yana shiga toilet </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mommy kuwa ranan kuka sosai tayi zuciyanta na zafi kamar zanfito waje haka dai Fatty taita lallashinta, AFRAH kam batama san sunayi ba d'an tun ran Saturday Mommy batayi mata magana haka koda Fatty tadawo ma ko magana batayi mata ba, sai AFRAHN ce keyi masu. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yaya Suleiman har bedroom yashigo yayi Afrah Allah sanya Alkhari gami da Addu'a kaiwa lokacin lfya, sosai AFRAH tayi mai godia gami da Addu'a bashi wata ta gari, tindaka ranan Sukadawo kamar daa suna respecting junan su sosai koda ABDULNASEER yazo har inda suke Suleiman yazo suka gaisa, ashema rana d'aya zasutafi camp sai dai shi ABDULNASEER sokoto zaije ranan dai hira sosai sukayi kaman sun dad'e da sanan juna. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mommy kam gaba d'aya tasama kanta damuwa kulin cikin ciwan kai take, Suleiman yana mamakin halin Mommy na bak'in ciki kiri kiri Addu'a dai yakeyi mata Allah ya ganar da ita. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ana gobe ABDULNASEER sai wuce shopping sosai yayi ma AFRAH yakawo koda Mommy tagani ko magana takasa, haka dai abubuwa yaita tafiya ko da Suleiman yazo tafi bai samu wani addu'an kirki daka wajen Mommy ba d'an batacikin hayyacinta Daddy kam Addu'a sosai tayi mai gami sa samai albarka. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka abubuwa keta tafiya bikin Fatty nata matsowa d'an baifi saura kwana 20 bah, randa Mommy tayi ma Daddy zancan zuwa Dubai cewa yayi babu inda za'aje ya riga yasa amai order kayan gado da kujeru daka China na FATYY DA AFRAH ranan Mommy tayi kuka kamar menene d'an tariga tagama yad'awa zataje Dubai...</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Happy birthday sweet sis(Afrah bhai)wishing long life and prosperity, may Allah bless your new age much love n stay blessed* ❤️ ❤❤❤❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 60-61_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*H*aka rayuwa taita tafiya abubuwa nata faruwa mommy kulin cikin k'unci take da bak'in rai, gaba d'aya Daddy baya shiga al'amarinta hakan gaban shi kawai yakeyi, kayansu dai haryanzo babu labari kabarma Allah komai a hannunsa duk yanda ya tsara mai kyaune a gare shii. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Duk wani haushe da Mommy keji sai tanemi saukewa a kan AFRAH amma sam bata nuna ma tadamu hakan datakeyi yana k'ara b'ata ran Mommy, haka dai lokacin Bikin Fatty keta matsowa Mommy ta k'ara d'aga hankalinta coz duk yanda taso tsara bikin bahaka yazo ba, biki taso tayi nagarari na bugawa a jarida amma kuma sai kokai yazo mata a juye hakadai tai ta dauriya amma da kamata kallon tsaf xakagane tana cikin damuwa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yau ne Aunties na Musty zasu kawo lefe dan haka gidan cike yake da jama'a d'an tarban su, as usual abinci mai lafiya da snacks AFRAH tayi da taimakon y'an aikin gidan komai ya kammala, fita duk sukayi a kicin din da gabatar da sallah, bayan duk sun idar k'ara gyara ko ina akayi waje dai yayi kyau masha Allah, mommy da mutananta sunyi kyau babu laifi haka ma Anty Ramlat matar uncle Isma'l, zaune suke anata hira, k'arfe 2:5pm daidai y'an kawo kaya suka iso, suna dayawa d'an zasukai su 10 sanan yan mata 4 da alama dai familyn Musty sunada yawa, y'an gayune sosai </p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tarba mai kyau suka samu daka wajensu Mommyn da sauran Mutanan, sun zauna kaman da minti 3 wasu mata su suka fara shigo da akwatuna da alama dai musaman akazo da matan da shigo da kayan d'an daganinsu ba wasu bane cikin familyn haka sukai ta shigowa da akwanunan wani mutun daya ya dauko wani kuma sai su biyu sai da suka shiga da guda goma sha biyu sai wasu 2 na Mamman Amarya da babanta kowa akwati 1 a gefe nan fa dangin Mommy suka hau guda da shewa nan aka shiga bude kaya wata y'ar dattijuwa ne Inna Asabe(kanuwar Maman Mommy) tashiga bubbude kayan, aiko kayane bana wasa ba d'an an ruba januwa komai 12 ne a ciki kud'i yayi kuka a wajen kayane masu kyau da tsada ga ku'din dinki 250k ni basan ta ina zan maku bayan kan kayan kugane ba, English gold gasu nan har iri 5,kawai dai sai kun gani (ni kaina *Biebie dee* ware eyes nayi ina kallo d'an kayan sun wuce dani gskia) kowa sai san barka yake da sa Albarka 100k suka bada tukwaci sanan uban girke girke da snacks kala kala Su Aunty Lailah sai godia suke haka su Anty Azizeema sai da suka rakasu har bakin motocinsu kana suka juyo ciki, nan fa suka bud'e sabon chapter na ihu da guda AFRAH da Anty Ramlat dai naganin ikon Allah, AFRAH sosai tayaba da kyan tasa albarka gami da Addu'an Allah basu zaman lfya haka Anty Ramlat ma, ganin irin kayan da kayi ma Fatty ne yasa Mommy tad'an ji dad'i cikin ranta damuwanta yadan rage ko babu komai yarinyanta tayi goshi, wunan wanan ranan gidan cikin shewa yake sai bayan sallan Isa'l Daddy yaga kayan Albarka sosai yasaka gami da masu Addu'a. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ranan Wednesday Fatty da friends dinta yan Baze suka iso kaduna, tarba mai kyau suka samu daka wajen Mommy har ma da Daddy batada case da Friends dinta na kd coz duk Aseeya duk takai masu invitation card, amarya Fatty ce kawai tayi lalle sai AFRAH da friends nata Aseeya da Hayfah sauran kam wai bazasuyi ba, a ranan ne zasuyi *bridal shower* a syd resort duk wanda ke kaduna dai yasan tsadan hall na syd resort, *ILAURAH*itace zatama ta make-up a duk ka events din friends kuma *LAYYAJEY* cezatayi masu wanan abu duk Anty Musty ta dau nauyin yi wato Anty Lailah, Fatty Amarya tashirya cikin pink color weeding gown kanta yasha fixsing a xubu da gashin har gadon bayanta sai wani crown 👑 a saman kanta sai wani abu da ta aza saman gown a rubuta *bride to be* sosai *ILAURA* ta fitoh da ita cikin make-up dinta, kai kai gaskia Fatty tayi kyau ba karya wallah friends kam da su AFRAH white gown duk suka saka wasu daka cikin su sunyi daurin turban wasu kuwa irinsu HANEEFAH komai basu sa bah suma haka *layya jey* ta masu makeup kyau sosai sukayi gskia sunyi kyau masha Allah AFRAH tayi kyau sosai haka su Zarah sukai tacewa dawasu daka cikin friends na Fatty amarya, abindai sai wanda yagani haka dai suka dunguma sai syd resort haka amarya Fatty da friends da yan uwanta yamata suka ci Bridal shower depphotos ya kashe masu picture duk abinda kukadan anayi a nakuma ci a had'edan bridal shower na yaran masu kudi kuma yan gayu toh anyi a na fatty haka dai suka k'are bridal shower, sun dawo suntadda yan katsina sun iso, bedroom mai kyau da girma a kaware ma Inna, haka ma sauran jama'un, anty Rabi MA tazo mahaifiyar AFRAH y'an Zaria ma dam da gida, washe gari *KAMU* wanda za'ayi a holiday conference ranan ma kwalliya duk suka sha amarya fatty ma tayi kyau ba na wasa ba da friends dinta AFRAH, Zarah, husnah ma duk sunyi kyau haka Mommy da mutananta ma, haka aunty Rabi da sauran yan katsina,Inna ma kwalliya tayi sosai tana sa kaya tana masifa wai kawai zataje sabida ubanta amma d'an uwarta da ita kanta amaryan ba, haka akaita bata hakuri yan uwan Mommy ma sunyi kyau ba laifi. a ranan ne ya sulaiman ya dawo gida, babu bata lokaci suka hau shiri shida ABDUL da Muhammad bayan duk sun je sun gaida mutan gidan, Abdulnaseer ma yadawo shima shiryawo yayi shi da su Ummie, aunty baraka, Humairah da Aisha suka dau hanyan holiday conference </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Biki yayi biki haka waje yayi waje Amarya da ango sunyi kyau sosai haka friends dinsu, familyn Musty ma sunyi kyau cikin nasu anko masha Allah kowa yayi kyau, biki yayi kyau anci ankuma sha ankuma dauku pictures anyi rabon abubuwa iri iri mai dauke da pics na ango da amarya</p><p><br /></p><p> Abdulnaseer har wajen da aunty Rabi(Mami) da Inna yaje ya kwashe gaisuwa haka su Ummie da aunty baraka wannensu ya yadda da junansu, wajen bikin Muhammad friend din Suleiman yaga Zainab din Uncle Isma'l nan dai suka dai daita kansu bayan tagama yanganta</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Wajen *kamu* akayi sa lalle, haka dai taro yatashi kowa yana san barka da sa albarka y'an *biebie dee nvls group* ma sunzo suma duk sunyi kyau amma babu wanda yayi rawa cikinsu zaune dai suke, sai kashe pic's sukeyi da AFRAH da ABDULNASEER da Afifah data likemasu dan sunyi masu kyau. 😂 Lol </p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yau Friday kuma yaune jama'a suka saida daurin Auran Mustapha Ahmad D'anbatta da Fatima Shu'aib Mani a masalacin Al-manar dake kaduna, jama'a da dama sun halata aurin auran kamar manyan yan siyasa dakuma manyan yan kasuwa, ango Musty yayi kyau sosai sai smilling yakeyi haka friend dinsa sai daukan Pics sukeyi da friends, y'anuwa da kuma abokanar arziki </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A gida ma amarya tayi kyau sosai ita da friends dinta haka mommy da friends dinta da yan uwanta haka yan katsina ma AFRAH tayi kyau cikin ankonta dass gown din ya zauna a jikinta, Afifah ma tayi kyau sosai masha Allah, nan dai ango da friends dinsa suka iso anata pics, haka dai akayi yinin biki komai Alhamdulillhi duk da Mommy ba haka taso bikin yakasance bah, addu'anta kulin shine Allah sa na AFRAH yakai na Fatty data nuna irin kayan sa ranan AFrah sai gabanta yafadi amma kuma tana cewa su Musty sunfisu kud'i sai taji sanyi a ranta, gaba d'aya ta manta zuciya ne abin ba dukiya ba( Nidai nachai Hmmm, za dai mugani) </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kafin magarib akazo daukan Amarya wajen Daddy akafara kaita fad'a da nasiha mai ratsa jiki yayi mata wanda yasata zubda hawaye, haka Inna ma da sauran yan katsina nasiha sosai sukayi mata mommy ko babu wani nasiha bare wani addu'a gani kawai take y'arta ta gana dacewa da miji tinda akwai kud'i nan dai Anty Ramlat da Anty Azeezah da ina da wasu yan uwan Mommy suka wuce dan raka amarya Fatima. </p><p> Friends kuwa ga mota nan sai wanda suka so shiga AFRAH da Afifah kam ABDULNASER yakaisu Zaynab kuma Muhammad, Zarah, Husna, Haneefa da Fa'izah ma duk samarinsu suka kaisu, sun iso gidan Lfya tarba mai kyau suka samu saka wajen dagin Musty nan dai akayi abinda yakama side Fatty na nan kaduna yayi kyau babu karya daddy yayi k'okari sosai suna shirin tafiyane akace su tsaya dan uwar angon sun shirya dinner a cikin garden din gidan kasancewar duk da kwalliyansu yasa basu damu ba nan Aunty Azeeza tashiga kiran wayan wai suzo akwai dinner a family house na ango Mommy taso taje amma Daddy ya hanata zuba bubu yanda zatayi haka ta zauna badan taso bah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Nan aka kara shiya amarya da ango sunyi kyau haka Friends ma duk kowa yayi kyau masha haka aka yi dinner, anci kuma ansha anyi pictures sosai, 12 dare su Anty Ramlat da sauran yan kawo amarya suka wuce tare da sha tara na arziki yayin da aka bar familyn ango da friends sunata shan shagali sai 2 akatashi kasancewar su Mustyy yan bidi'a ne sosai amarya da ango sukayi rawa haka dai taro ya tashi, suna dawowa ciki kowa kwanciya yayi dan sungaji. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Washe gari da safe bayan sunyi brkfst duk friend da yan uwan Amarya emmata suka fara shirin tafiya abin arziki su aunty lailah suka hada masu da kud'i 300k godia sukayi, Haneefa tace" toh Amarya sai mun had'e a school dan yau zamu juya abuja"</p><p><br /></p><p>Smiling Fatty tayi kana tace " toh Babe muma nan da next week zamu shigo abujan ai"</p><p><br /></p><p>Hugging duk dinsu daya bayan daya Fatty tana yimasu godia tana zuwa kan AFRAH tace "toh Amaryan Next Month saduwan alkhari sai munzo biki"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Smiling AFRAH sanan tace " toh Amaryan Musty Allah daku zaman lafiya"duk suka amsa da ameen exchanging numbers sukayi da wasu daka friends din Fatty wai in bikinta tazo zasuzo, haka dai suka rabu cikin Farin ciki</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Nann dai akasa driver ya maidasu gidan su Fatty dan duk kayansu na chan, nan Abin arziki Mommy da daddy suka hada masu Inna sai Albarka take samasu da Addu'an suma Allah basu na gari, nan duk suka kama gabansu yan Abuja suka wuce yan kaduna kuwa kowa tayi gidan su, a ran wasu daka cikin yan zaria suma suka wuce, washegari ma duk yan katsina suka wuce da sauran yan zaria tare da sha tare na arziki, Inna kam Daddy yace tayi zamanta sai bayan bikin Afrah dama haka ta shirya shiyasa koda Daddy yace haka ta amince nan takira Aunty Zulaiha yariyan inna Rakiya ce watou kanuwar uncle Isma'l mijinta yarasu shekara daya dawuce dan so take ya gyara AFRAH sosai dan tasan a irin bakin halin Mommy babu gyaran da zatayi mata tinda ba itace uwarta ba, kwana biyu tsakani anty Zulaiha tazo nan fa aka fara gyara AFRAH ba dare babu rana, Mommy bata so zamansu ba amma babu yanda ta iya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Washegarin ranan ne Fatty da Musty suka dan yimasu Sallama zasu koma Abuja, albarka gami da Addu'a Daddy da inna keta samasu Mommy kam sai washe baki takeyi y'ar zata abuja zaman aure Hmmmmm nan taja Farty jefe gami da damka mata wasu maganin kallanta Fatty tayi kana tachai"gskia Mommy nifa nagaji"d'an ubanki ke bakida hankali wanan shi zai gyara maki aure yakuma sa mijinki ya kara sanki, Ko AFRAH bazan ma wanan gatan ba, kidai sani"jin haka yasa Fatty sa ledan cikin handbag dinta sanan suka fito daka bedroom din, har waje suka rakosu mommy, aunty Zulaiha, Afrah da Afifah sai da sukaga Moransu yabar gidan sanan suka juyo ciki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka Abubuwa keta tafiya lokacin biki nata matsowa Afrah nata shan gyara families kowa nata shiri dangin Mami da ita Mamin kanta da uncle Junaid ga dagin Ubanta dan sunce dole suyima AFRAH gata kaman yanda marigayi Salis ya girmamasu yakuma mutinta su haka Familyn ADULNASIR ma shiri sukeyi sosai,haka side Daddy ma kowa shiri yakeyi bana wasa ba(AFRAH y'ar gata) ga kuma abokan arziki su Zarah da Husna ba zama y'an *Biebie Dee nvls group* ji sukeyi kaman sujawo 22days din da yarage anko tini sun dade da siyan shi 😂 lol </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haki yaita matsowa dagi ta kowani side anata shiri pre wedding pics nasu mai Gaskiya ne yayi masu pictures da akayi a natse kuma a mutunce pics ne wanda da kungansu kusan yan gayune kuma wayyu simple make-up a face dinta dan Jiddah ce tayi mata amma kyau tayi sosai haka Abdulnaseer ma abindai sai wanda yagani</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Pictures din sun zagaye social network, Snapchat, Instagram, WhatsApp da dai sauransu friends da abokan arziki keta sakawa kowa ya gani sai yachai masha Allah.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Fatty tinda tawuce Abuja tarage kiran Mommy inkuma Mommy takira yawancin lokuta bata dauka inkuma ta dauka Mommy ta tanbayeta dalilin dake hanata picking calls sai tace karatu, yauma ta k'irata ya kai sau 20 amma no answer sosai hankalin Mommy yatashi nan tashiga dialing numbern Haneefah ringing 3 tadauka bayan sungaisa Mommy ke tanbayanta Fatty nan Haneefah kesanar da ai Fatty bata dawo sch bah sosai hankalin Mommy ya tashii tana sallma da Haneefa tashiga dialing numbern Musty haka tai takira amma no answer haka ta hakura side din Daddy tayi hankali tashe, zama tayi sanan tashiga yimasu Daddy da Suleiman bayani kallanta sosai Daddy yayi kana yace" hukuncin Mijinta kenan ko ina da abinyi ne? " kuka Mommy ta fashe dashi gami da cewa" yanzo Suleiman abinda Daddynku yachi kaga ya dace?"</p><p><br /></p><p>"Mommy hakuri zakiyi bamusan reason dinsa na hana taba, dole mubi komae a hankali"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ni gaskia gobe zan shiya naje abuja na ganota sanan Muyi magana"mommy tace</p><p><br /></p><p>"Babu inda zakije, inma hanata karatun yayi mayb hakan yaga yadace da ita, d'an kai na na dade da sanin Fatima nada rawan kai, soo komai a hankali zamubi coz shikeda iko da ita yanzo"</p><p><br /></p><p>Haka Mommy ta bar side zuciyanta na zafi sosai tunani iri iri haka taitayi haka dai tawuni wanan ranan babu walwala sam.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yaune yan uwan Abdulnaseer zasu kawo lefe...</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 62-63_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*A* yau ne y'an uwan Abdulseer zau kawo lefe so gidan cike dake da mutane babu laife d'an aunty Safiya maman Heeshmer tace sai tazo tarban kaya itama dan haka cikin shirinta take haka su Inna da aunty Zukaiha, gashi tin da inna tazo gidan sai yayibu jama'u takeyi wai y'an uwanta nan fa su maman Musa, Maman Fauxeey, Anty fatuu da dai sauran mutanan Inna duk suka cika gida kowa cikin shiga ta alfarma mommy kuwa b'akin ciki da haushi duk sun hana ta fitowa ga damuwa da halin da Fatty ke ciki, haka suko sukai ta shagali a cikin gida sai girke girke akeyi, a d'aura wanan a sauke wanan, a jere wanan a kulle wanan gida sai kamshi yakeyi, wanan karan komai Afrah batayi sai cupcake da cookies shima su Zarah duk sun tayata, y'an aikin gidan ma su Lantana sai kaud'i akeyi AFIFAH kam k'in zuwa islamiyya tayi babu yanda ba ayi da ita ba amma fir tak'i taje hakanan suka rabu da ita. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> An shirya komai yanda ya kamata Sallah duk sukatafi gafa tarwa, bayan sun idar kowa k'ara gyara kanshi yayi ana jiran isowan b'aki AFRAH da Friends dinta duk suna bedroom duk wanan abu da ketayi sai yanzo Mommy ta sakko</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> Aikuwa kaman anajiran sakko wanta, dai dai wanan lokacin Motaci sukai ta shigowa cikin gidan suna parking sai da motoci 8 suka shigo cikin gidan daka baze, banzer, rang robber, golf8 dai sauran manyan motoci keta parking cikin gidan</p><p><br /></p><p><br /></p><p> firfitowa duk matan sukayi Aunty Baraka ce a gaba ita da Aunty Rabielah (autansu Ummie ce, amma tana zama ne a america ita da mijinta da yaranta Ahmad da Hajara- Iman sai k'aramarsu Rabi'a ancemata pretty) sanan Aunty Murja, Aunty Maijidda, sai Aunty Aisha Muh'd(aunty) su Ummu safeeya da Mom. Ameer, aunty Binta, Aunty Billy duk suna baya sai Humairah da Aisha suma da wasu emmata suma a baya sai wasu Mata 3 a ka hari suna jawo akwatunan nan yan aikin gidan Maza suka nufesu d'an tayasu shiga dashi ciki. </p><p><br /></p><p>Kowanne a cikin su cikin shiga ta alfarma yake da kun gansu kunga wayayyu kuma y'an gayu jii da illimi</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>tin kafin Su kai da shiga ciki aka fara tarbansu cikin Murna da sakin fuska suna cikin fara'a sosai suke, anan Parlorn k'asa duk suka zauna basu kai ga fara gaisuwa ba su Haruna da Yakubu suka fara shigo da akwati a tsakiyan Parlorn suka dire suka juwa d'an dauko sauran tin da su Yakubu suka fara shiga da akwatin Inna ke gud'a ga gaskon turaran wuta hannunta tana bin parlorn dashi sakin baki da hanci Mommy tayi tana ganin sabuwar al'adan da *Uwar mijinta* ta fito dashii yau yau,Haka akai ta shigo da akwatuna sai da aka shigo da sha d'aya(11) tara(9) irin su da ban sai 2 suma irinsu daban </p><p><br /></p><p> Gaisuwa aka farayi cikin fara'a da kuma barkonci nan dai Wata nan dai wata Saratu tashiga zuge zip din akwatunan ta fara fiddo kayan eyes sosai Mommy ta ware tana san ganin irin kayan da keciki Designs ne ko kuwa dau dauki bisu ne da laces taga anfara da irin na 400k dinan laces masu azaban zafi sai da kafito da kala 9 k'amin cikin su ne na 50k Super Holland 6 ne sai Ghana English 6 atanpan Aura 5, shaddoji masu azaban zafi shima 9,material masu kyau da tsada 8,sai k'anun Atanfofi irin na 7k kala 10 sai jallabiya 10 duk masu shegen kyau _hmmmm wasu kayan ma dai ni ban gane irin su ba, kawai bud'e idanu nayi da kyau ina ganin kayan arziki_ Mayafai guda 12, shoes n bags suma 9 pieces Amma duk Designs ney d'an babu vinci da wasu vine kai babu k'anan designs gskia, kayan inner kam wanne 24 pieces be, cosmetics kam ba'a magana gskia sabida kyaunsu da kuma tsadansu _ina tunanin ma Aunty Rabielah ce ta had'o su daka america d'an kyaunsu yayi over_gold set 2 d'aya mai d'an kunne da sarka, zobe da warwaro d'ayan kuma sark'a ne da d'an kunne sai English gold shima set 2 sauran kuma fashion ne masu shegen tsada da kyau har kala 7 sai kud'in dinki 200k</p><p><br /></p><p> Akwati biyun kuwa na Maman amarya da Babanta ney, shi kaya kala 6 ko wane a ciki amma duk masu kyau da tsada ne kaka saka </p><p><br /></p><p> K'arya ne kachai kayan lefa AFRAH baiyi ba wallahi sai mak'iyi kaya suyi 100% na Fatty yawa kawai yafi na AFRAH duk da dai itama an zuba mata kaya amma na AFRAH wasu irin kyau ne da su na musanman komai a tsare sukayi a natse babu hargowa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ganan uban kayan da Inna tayi sanan ga kuna na Uwa da na Uba kawai sai tasa kuka gami da cewa" Allah sarki Salisu Allah ya jikanka babu rabon kaga auran y'arka, Allah sarki" ta k'arasa maganan cikin kuka sosai</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hakuri aka shiga bata gami da yima Daddyn Afrah Addu'a Inna na amsawa da Ameen </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mommy gaba d'aya zaune take kamar wata picture tinda aka fara fiddo da laces dinan miyaun bakin ta ya k'afe zufa yafara keto mata smiling na dole kawai takeyi, bata tunanin zasu iya irin wanan kayan ba na masifa, kaya ba wani yawan kirki bah amma sai shegen tsada babu abida yafi bata tsoro kanan lace din farko na 400k dinan wanda ko Fatty iyakan na 250k lace dinta a lefa Amma ita sai ta nanka abun, Mommy ta kula duniyan tunani sosai bata san mai akaitayi bah, sai jitayi ana addu'a 100k tamik'o ma su Aunty Baraka tukwaici nan Inna ta karkace ta k'ara 50k kan 100k da Mommy ta bada sai snacks, girke girke da drinks iri iri, Godia sosai suka yi suma su Manan Heeshmer da Anty Zulaiha da sauran mutane nata godia, har jikin Motocin su suka rakosu, sai da suka bar haraban gidan duk suka koma ciki. </p><p><br /></p><p>Kafin sutafi sai aunty Rabilah,Humairah da Aisha suka shiga waje AFRAH dan an aika ta fito sugaisa kuma Aunty Rabilah ta ganta amma AFRAH takasa fita sabida kuya, sosai Aunty Rabilah ta yaba da Afrah haka itama Afrah ta taba da girkin Aunty Rabilahn babu ruwanta she's nice, simple n unique. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Wanan ranan wuni akayi shigowa kallon Kayan Afrah, ita kam takasa fitowa d'an kunya su Husnah da Xarah da sauran friends kuwa suna a gaba sai daukan pics din kayan sukeyi ana posting a Snapchat Afifah kam tasha kamar zata balle sabodi murna </p><p><br /></p><p> AFRAH kam na bedroom tana ta waya angonta anata soyewa a haka Friends dinta suka shigo suka sameta, sallama tayi da ABDULNASEER tamai da hankalin wajen hiransu hiran kayan lefanta suketayi kowa na yaba irin kyau su da tsadansu, nan Husnah ta shiga nuna mata pics din kaman zata tura kan Afrah cikin screen wayan</p><p>" kee barni haka ko nafasa wayan" cewar Afrah</p><p><br /></p><p>"Hehehehe gashi Fasa yarinya angonki sai yasiyamin iPhone 7+ d'an nayi ban kwana da 6s walh" Husnah tace</p><p><br /></p><p>"A'a iPhone-X zai siyamaki bah 7+ ba barauniya"</p><p><br /></p><p>"Ahhhh khadee har anfara shiganmai fad'a? " cewar Jiddah tana daria</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Bansani bah" Afrah tayi maganan tana hararanta</p><p><br /></p><p>"Please manta da wanan banzayen amarya" Zarah tace ta daria</p><p><br /></p><p> Hadai akaita zuwa ganin kaya sai yamma mutanan Gidan suka ragu friends na Afrah duk suntafisuma nan Inna tasa a jere duk akwatunan a d'akinta Mommy na taganin kayan haushi dai, Daddy da yaya Suleiman sai bayan salan isha'i suka shigo gidan bedroom na Inna sukayi gaisheta suka k'arayi kana aunty Zulaiha tafa fiddo kayan suna gani Albarka sosai Daddy ketayi gami da Addu'a haka Suleiman ma, a nan d'akin Inna duk sukayi Dinner amma banda Afrah da Mommy bayan sun kammala dinner dinne Inna tace Afifah ta kira Afrah su Daddy kam kowa siden su sukawuce. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Da sallama tashigo bedroom din, zama tayi a bakin gadonn sanan tafa gaidasu, Inna bata amsa bah sai cewa tayi" gidan Bubu kowa kuma wani sabon salon xama a d'aki ke dai yatashi? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ina wani abune" Afrah tace</p><p><br /></p><p>Baki Inna ta tabe kana tacha" ga kayan nakin nan sai kije kiduba"</p><p><br /></p><p>"Ba sai naduba ba, ai nagani"</p><p><br /></p><p>"Karki duba din keka sani ai, naga dai ko a karkara amare na ganin kayansu"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Gani tayi ai itace zatasaka kayan, kuma gidan zasu shiyasa" Aunty Zulaiha tace tana dariya maman Heeshmer ma dariyan tayi nan suka chanza chapter sunata hira.</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> Mommy kam dama tanan tana lura da shigan daddy so yana bar d'akin tabi bayanshii, yana shigo sai gata kaman tare suke, kallonta Daddy yayi da kyau kana yace" lafiya kin shigo babu ko sallama? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Magana nakeso muyi" Mommy tace cikin sanyi Murya</p><p><br /></p><p>Zama Daddy yayi gami da maida hankalinshi gareta" Ina jinki"</p><p><br /></p><p>" yanzo sabida Allah da darajan Manzonsa Abinda y'an uwanka sukeyi ya dace kenan?"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Toh toh meme kuma ya faru? " Daddy yace yana gyara zamansa</p><p><br /></p><p>" tsakani da Allah sai banbanci suke nunawa tsakan Afrah Fatty duk abinda basuyi bikin Fatty amma wanan Bikin kuwa rawan kan yayi yawa wai har Inna nak'ara 50k kan 100k dana bada tukwaici wanan ai duk nuna san kai nw da banbanci ai baikamata ba wanan tinda yara duk daya suke"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tinda ta fara magana yazuba mata eyes yana kallonta shi gaba d'aya mamaki matake bashii</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Kayi shuru bakace komai"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ai ina mamaki ne nima sabida dai duk wani mai sanka toh ai sai dai yabi bayanki, ke kindauki yaran a matsaye d'ayan ne? Kuma zancen suna sankai kam ai ce shuga ba kece kika nuna masu shiyasa"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yanzo dai kanaso kachai sunyi dai dai kenan? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ehhhh kusan hakan ne, ai dayake laifi tudu ne kin take naki kina kallan nawasu, AFRAH dai kinsan ubanta yarasu dole ne kowa yataka rawar gani kanta"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yayi dai dai kaima ai sankai kakeyi ba tun yanzo ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ni bana neman tashin hankali kibarni naji da abinda ke damuna kar kik'aramin damuwa" yayi maganan cikin kwanciyan Hankali</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Fita Mommy tayi cikin fushi, ko da takoma side dunta Fatty tashiga kira amma no answer wanan sabon hali na Fatty na k'ona mata zuciya na kin picking calls gajiya tayi da kira tashiga dialing number Mommyn Musty aikuwa ringing 3 tadauka gaisuwa sukayi cikin Mutunci nan Mommy keyimata complaining rashin picking calls da basu yi dukka su buyun, kasancewar Mommyn musty tasan halin takesuke ciki tas yasa ta yi murmushi mai sauti kana tace" ai karki damu lafiya suke phones dinsune ta fad'i wai kar kidamu"</p><p><br /></p><p>"Toh shikenan dana bikin y'ar uwartace ya taso yau saura 2kweeks"</p><p><br /></p><p>"Masha Allah Allah sa alkhari ya basu zaman lfya yakuma kaimu lokacin lafiya insha zamuzo ai itama Fatty nasan duk suna sane"</p><p><br /></p><p>Godia Mommy tayi kana sukayi sallama, ajiyan zuciya Mommyn Musty ta sauke kana ta shiga dialing numbern AuntyLailah ringing 2 ta dauka Mommy bata bari sun gaisa ta shiga karanto anty Lailh yanda sukayi Da mommy daka chan b'an garan sauke nufashi Aunty Lailah sanan tace" yanzo menene abinyi? "</p><p><br /></p><p>"Toh ni ina ma nasa ni Lailah ai Mustapha yafi ganin girmanki a kai na, ke kanki kinsan ban isa nafad'a mai abu yaji ba bare kuma Daddyn shii gashi kinga tunda yayi auran munsa ran gyaruwanshi amma kuma lamarin nashi gaba yayi"</p><p><br /></p><p>"Hakane Aunty insha zan daure naje gobe ko zaiga dama ya bud'e min k'ofa"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah sa amma gskia bai kamata iyayen yariyan susan halin da y'arsu ke ciki ba da kuna irin halin Mijinta"</p><p><br /></p><p>"Hakane amma inyazama dole ai dole suji karya kashemasu yarinya"</p><p><br /></p><p>"Haka ne Allah dai ya shirya" </p><p><br /></p><p>"Amen ameen" Aunty Lailah tace hira suka d'anyi kana sukayi sallama</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tun Zuwansu Abuja kwanciyan hankali na 10days kawai Fatty tasamu ita da Musty coz Musty mugun d'an shaye-shaye ne ga zuwa club na masifa da Farko Fatty tasha zata iya hanashi ranan tahana shi fita tanata masifa amma mari masu lafiya ya bata har 3 gami da cewa tafita harkanshi kulin sai cikin dare ko subhi yake dawowa gashi ya amshe phone dinta inkuma tayi bak'i y'an uwanshi ya kule door din ya boye key sai dai sukaji sukoma school ya hanata zuwa wai sabida zataje taita yawo dasu Haneefa kuma yassn ba yaran kirki bane wajen kud'i kuwa batada problem sam d'an haka yake zube mata su coz shima Daddy haka yakemai transfer kawai wai d'an ya shiryu Amma Fatty bata komai da kud'in d'an ba barinta fita yakeyi ba kuma baya fita da ita inkuwa yana gida toh babu sauki girki xaice tamai ranan farko datafara girki tayi kuka kaman mai coz girki babu taste sam zagi da masifa har da jaraba babu irin wanda bata shaba kaman zaimata dukka aranan ney tayi bak'in cikin rashin shiga catering sch dabatiyi ba a zuciyan takuwa cewa takeyi AFRAH taji dad'in dan tayi imani inda itace cikin condition dinta bazata sha wahala haka ba d'an tafita experience sosai, duk wanan iskancin na Musty yana sallah amma a gida danshi bai cika fita da safe ko rana bah sai dare. </p><p><br /></p><p> Yaunzu haka zaune suke a parlorn su da yasha kayan More yaruwa iri iri tsaf yake d'an babu y'ar aiki ko 1 a gidan(ina Musty zai bari) Farty kecin aikinta tun batasa bah gashi yanzu har tad'an saba</p><p><br /></p><p> Jugum suke babu mai magana cikinsu wani series film suke kallo phone d'inta ya wurgo mata kana yace" gashinan baby kuma bada kowa nace kiyi waya ba, in kuma kinyi zan sani" _jin sunanda Musty ta kirata dashi yasani wani kwashewa da mugun dariya ganin Musty na wurga idanuwa yasani natsuwa d'an kar yakamani nima yaci gidanmu yasa nayi gum_😂😂</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Oky thank you alot"</p><p><br /></p><p>"Kin dai ji abinda nace ko? "</p><p><br /></p><p>"Yes insha Allah zan kiyaye"</p><p><br /></p><p>"Good to here dat, yau fried rice, salad n pper chicken nakeso yi da coconut drink, ko baki iya ba? </p><p><br /></p><p><br /></p><p>" yes ban iya ba gskia kuma aiki yayi yawa"</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Hararanta yayi sanan yace" sai kiyi browsing, mene anfanin baki phone din da nayi? Inkuma bazakiyi ba bani phone din"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Nooo zanyi zanyi sorry" nan ta tashi tayi kicin yabita da kallo</p><p><br /></p><p> Tana shigewa cikin din aka fara knocking door din parlorn Musty naji amma yayi kaman baijiba haka akaita bugu amma yayi banza</p><p><br /></p><p> A waje kam aunty lailah phone dinta ta fiddo cikin handbag tashiga dialing number Musty, sai da yakusa tsikewa ya sauka gami dace " yes aunt"</p><p><br /></p><p>"Open d door, ina waje"</p><p><br /></p><p>Katse kiran yayi sanan yanufu kofar, yana budewa batare da yace da Aunty Lailah komai ba ya koma ya zauna, ita zama tayi kana tace" son how u? "</p><p><br /></p><p>"Am good" Mustie yace</p><p><br /></p><p>"Masha Allah Ina Fatima?"</p><p><br /></p><p>"Tana kicin"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Okay amma son kasan da bikin Sister dinta nan da 13days ko? And i hope zaka barta taje"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Shuru yayi sai chan yace" i'll think about it, buh i don't even know if she's going"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Okay amma please kabar ta taje inba haka ba familyn ta zasu iya suspecting wani abu"</p><p><br /></p><p>"I don't care, ni keda right kan matata basu ba, and please duk complain da zasuyi you, Mom n Dad ya tsaya kai na kawai" yayi maganan ya juya kanshii</p><p> Dai dai Faty ta fito karaso cikin parlon tayi cikin smiling gai da aunty Lailah tayi ta amsa cikin sakin fuska nan da nan Fatty tawuce da kawo mata soft drinks da snacks, tana kawo ta aje a gaban aunty godia anty yayinda Fatty ta koma cikin dan cigaba da aikinta</p><p><br /></p><p> Aunty Lailah ta dade sosai tana bama Musty hakuri har ya yadda nan suka cigaba da hira kaman ba su ba, ko da Fatty tagama girki anan parlon tajere masu ita kuma ta wuce bedroom </p><p><br /></p><p> Numbern Mommy tashiga dialing, ringing 2 Mommy ta dauka" lafiyanki kuwa Fatty ina kika shiga? "</p><p><br /></p><p>"Lafiya lau Mommy ya gida da kowa? "</p><p><br /></p><p>"Lafiya lau, ankawo lafe AFRAH bakida labari, ina fada maki kaya sunyi baxata dan anzubs kaya"</p><p><br /></p><p>"Mommy duk ba wanan problem dina, zan maki transfer anjima in muka fita sai a saimin anko dukka sanan akaimin dinkinsu"</p><p><br /></p><p>"Yar banza ina fada maki Affrah tayi gaba kina bashine damuwarki ba, toh menene damuwar? "</p><p><br /></p><p>"Please Mommy kibari sai nazo ni fa bansan ihu" Fatty naga fadan haka ta katse wayan, friends dinta ta duga kira daya bayan daya kafin takoma parlor aka cigaba da hiran da ita, yau Fatty taji dadin gidan sosai ba kadan ba dan tasake ba kamar kulun bah</p><p><br /></p><p> Ko da aunty Lailah zata wuce tare suka fitoh, ita tawuce gidanta sukuma suka wuce shopping. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>Haka biki yaita matsowa ko wani side shirye-sheye kawai ake tayi yau saura kwana 5 biki kuma tin a yau din ne wasu yan katsina suka fara zuwa Mommy kaman ta mutu d'an ta haushi gashi yanzo Daddy baya shiga harkanta shiga suke cikin dangi aita hira, Sulaiman, Abdul, Afrah da Afifah in dare tayi hadda Daddy Mommy kaman ta mutu dan bakin ciki. </p><p><br /></p><p> Gyara ko sosai AFRAH ke samu d'an in kun ganta bazaku gane ta ba sabida kyau datayi. </p><p><br /></p><p> Innah da Aunty Zulaiha suna mamakin bakin zuciya irin na Mommy ko mutun d'aya babu wanda yazo daka side dinta sune suna ganin ikon Allah. </p><p><br /></p><p> Saura kwana 3 biki PATTY ta shigo kaduna bayan Musty yayi jamata kunne sosai dan kafin tazo dinan ita kadai tasan bala'i da masifan da tashiga amma tana zuwa ta manta da duk wani magananshi. </p><p><br /></p><p> Haka aka fara gudanar da shagalin biki cikin farin ciki da kuma kwanciyan hankali side na musanman aka warema Mami da y'an uwanta fad'an irin goshi da Afrah tayi sai na kwana anan ban gama fada ba kowa yayi rawar gani sosai, Mommy kuwa kaman tayi hauka d'an abin ya wuce da tunanunta da kuma hankalinta haka Fattyma mamaki kawai takeyi irin shatara na arzikin da akebama AFRAH yafara basu tsoro. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yau Wednesday yaune kunshii, amma gidan dam yake da mutane kaman yaune akai daurin aure, Friends na Afrah gasunan kamar tsako kowa cikin gayu ba raini anata pictures wanda kema Amarya lalle daban haka wanda kema friends ma ga abinci iri iri kaman ana wani babban walima, haka akaita lalle har bayan magrab, Mommy gaba daya tarasa abinyi ita da Fatty zafi kawai zuciyan sukeyi masu, nanan zaune A parlorn sama wata Fadela daka side ango tazo bayan tagaida kowa ne ta mikama Afrah sakon da aka bata takawa gown da komai da zatayi anfani dashi gobe na *Bridal shower* (wata aunty shuwa family friends suke da Abban su Abdulnaseer tazo daka London tabada akawo kuma itace ta dauki nauyi yima AFRAH amarya make-up) </p><p><br /></p><p> Mommy Da Fatty suma ne kawai basu yii baa sosai suka shiga tashin hankali.</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Congratulations for d compilation of your sweet n Mazing Novel ITACE 'KADDARA TA!!! Allah bamu ikon aiki da da abinda ke cikin littafin Ameen, more grs to your shining elbow, much love n stay blessed d whole page is yours@Zee Yabour_❤❣❤</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_Page 64-65_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau ne *Bridal shower* so gidan cike yake dam da mutane babu sauki, tin daka wajen Inna, Mami wajen Amarya ko Friends ne gasunan ba'a cewa komai Mommy kam daka ina sai sisters dinta biyu anty Azeezah da Nana </p><p><br /></p><p> Abinci kuwa gashin duk wanda kakeso k'arfe 2pm dai wanda wanda zatama AFRAH make-up ta iso ita da yaranta watou *TARA* duk wani wanda yasan manya-manyan make-up artist toh yasan *tara* d'an tayi fice sosai ba k'adan bah zan iya cewa duk wani wanda yafara make-up toh bayanta yake. Taty ce tashigo room din da Amarya take da friends nata nan takeji wai *TARE*ce zatama AFRAH make-up friends kuma *laiyajey*suman tsaye tayi d'an ita sam batama sa TARA ciki bah sauri tayi takoma wajen su mommy dan sanar dasu</p><p><br /></p><p>"Toh sukuwa wanan wani irin kud'i garesu? " cewai Anty Azezah </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Hmmmm ba wani shwgun kud'i garesu bah, kawai dai sunsan manyan mutane ne, toh sune ke daukan nauyi" Mommy tace</p><p><br /></p><p>" amma ni bantaba kawowa ita wanda ta daunauyin make-up din zata iya dauko TARA ba" Cewar Fatty </p><p><br /></p><p>"Toh aiko tunda hakane ashe bamugama ganin abun mamaki ba" Anty Nana tace</p><p><br /></p><p>" ah'a insha Allah babu wani abin mamakin da zamuji kuma" Fatty tace tana yatsina fuska Mommy ko harara ta kaima Anty Nanan. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>AFRAH tayi kyau har tagaji coz make-up mai lafiya akayi mata, kai bazNn iya bayanin irin kyau da AFRAH tayi ba gskia, gashi gown din yayi mugun ansan jikinta dass ya zauna a jikinta</p><p> white color ney sai stones din jikin gown din pink, crown 👑 ta daura kanta pink color wanda yasha mugun ygara gashin ya sauka har gadon baynta AFRAH taso ta ayi mata dauri ne amma su Husna sukai ta zugata ita da *Mee* da sauran friends har ta yadda da crown 👑 din... kai ni wallahi bazan iya yimaku bayanin kyaun da AFRAH tayi ba tayi kyau sosai Husnah, Xarah da sauran friends sunyi kyau sosai cikin gown pink color Husnah, Mee da Xarah komai basu sa kansu ba wai su gayu😂😂 Husnah ansha kyau ba'acewa komai sai selfie akeyi, a nan *syd resort* za'ayi d'an friends na Afrah da kansu suka zaba hall coz basunan babban nan dai suka wuce cikin Motoci na alfarma</p><p> Fadan irin haduwan da *bridal shower* Na Afrah yayi bata lokaci ne duk wani abu da kuka san anayi toh anyi shii hakama duk abinda akeci da sha toh anci kuma ansha, Humairah da friends dinta ma sunzo da Aisha da wasu emmata yaran aunties dinsu sai yarinyan anty Shuwa Leemah duk sunzo suma cikin kwalliya irin ta wayyanyun emmata, haka wasu daka cikin emmatan da ke cikin *biebie dee nvls group*ma sunzo suma sunyi kyau sosai AFRAH tasamu gifts sosai bana wasa bah, Husnah uwar pix tayi har tagaji coz ga masu hoto har guda biyu nan dipphotos da Fox photos nan, haka dai taro yatashi kowa cikin farin ciki. </p><p> Fatty mamakin irin Uban gifts da AFRAH ta samu dan ita dake masifaar bin k'awaye ko ita bata samu irin gifts din da AFRAH tasamu ba, da Fatty ta kaima Mommy ruhuto kam kasa cewa komai tayi da Al'amarin AFRAH komai a bazata yake zuwa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🌸🌸🌸</p><p> Anty Baraka ce tashigo bedroom din Ummie, zama tayi gami da kallan Ummie kana tace" kai Ummie Abulnaseer yayi goshi komai sai ace za'ayi mai"</p><p> "Aifa gashinan kunata gatalashi da Amaryansa"</p><p><br /></p><p>"Kinsan jiya dai hajiya Umma tazo sai fada takeyi wai sai da muka gama hada lefe sanan ake sanar da ita"</p><p><br /></p><p>"In banda abinta ai abinda hajia Shuwa tayi ya wadatar ma bayan daukan nauyin yima Amarya make-up hadda fa wasu kudin ta bayar, sanan kuma itama tace wai zatayi? "</p><p><br /></p><p>"Nima dai abinda nagani kenan"</p><p><br /></p><p>"Aiko bari nama hajia Ummam magana kinsan dai ba k'aramin aikin ta bane na fiddo da wani event kuma kinga mungama tsara komai kinsan su kud'i ba matsalansu bace"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Dama kiyi zamanki d'an har takira wata make-up artist wai LVB wai itace zatama amaeya Make-up ran daurin aure"</p><p><br /></p><p>"toh ita wanda hajia shuwa ta kira fa? "</p><p><br /></p><p>"Wai dama na event 2 kawai zayi jiya da yau kenan coz zarayi"</p><p><br /></p><p>"Lallai sudai basu da dama duk wani abin gayu sune a gaba"</p><p><br /></p><p>Daria Aunty baraka tayi kana tace" toh tashin turai</p><p><br /></p><p>"Lallai toh duk Allah saka da Alkhari, komai muna zaune akeyi"</p><p><br /></p><p>Haka akai ta gudanar da biki a side ango kuma suna shirin kuwa *Kamu* daza'a a ceremonical canopies, emmatan na da iyayyen kowa shiri yakeyi</p><p> Hance takasan ce a side na amarya ma, Amarya da mai mata makeup suna daki daban anata shiri haka friends ma side Mami da sisters dita da abokan arziki ma hakanne Inna da Mutanan ta ma sunata shiri, Mommy da sisters di tama shirn suketayi</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Amarya AFRAH tayi kyau cikin wani arnan race purple color da touch din silver,hand ma silver haka y'ar Purse ma silver sai wani shegen high heels tasa kyau iya kyau toh AFRAH tayi shii haka make-up dinta ma yayi sosai</p><p> Friends ma duk sunyi kyau cikin Ankonsu wanan na wane wanan Fatty sosai tayi kyau itama cikin nata ankon AFIFAH kam ba'a cewa komai tayi kyau sosai sunan zaune ana k'ara gyara make-up phone din Fatty yafara ringing picking tayi kana tace"okay am coming" kallan Duk emmatan tayi sanan tace" mari ni nawuce mijina ne zaikai ni"</p><p><br /></p><p>"Okay sis sai munhade" Husna tace</p><p><br /></p><p>Babu dad'awa Motoci suka iso irin ta alfarma nan friend aka fara wucewa da yan uwa Zarah da Husna kam kowa saurayinta ne zaikaisu</p><p> Da Mami wai bazataje ba nan yan uwanta sukayi chaa a kanta babu shiri ta hau shiryawa, Inna kanta tsaf take nan tafara masifa Wai Suleiman zai jamata latti tana kan masifan ne sai gashi ya shigo cikin kwalliyansa yayi kyau sosai nan dai yakama hannun inna yasata gaban Mota sauran suka shiga baya sukawuce</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mami kam a motan ABDUL take ita da aunties dinsu su uku sauran k'anan Mami kam tuni suka wuce</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mommyma ita da sisters dinta cikin shiga alfarma Mommy take dan sosai tayi kyau haka su Azeezah ma babu laifi sunyi kyau, suna shirin shiga mota phone dinta yafara ringing picking tayi daka chan side din akace " hajia gamunan karasowa" </p><p><br /></p><p>"Okay Allah kawoku lfya" nan tashiga cikin motan Bala driver yajasu sai *ceremonial canopies* hall dinda yasha decoration mai shegen kyau, iya tsaruwa kuwa hall yasha shii naina yayi kuka, mommy ai tuni tafara nemo yawun bakinta d'an gaba d'aya tanema tarasa *kamu* sai kacewani dinner haka dai akafara shan KAMU familyn ango sunyi kyau sosai cikin ankonsu mommy dai na kallan ikon Allah coz duk uban gayun da take ganin tayi amma dataga wasu sai da ta raina kanta, inada Amarya da ango ke zaunema sosai yasha decoration ABDULNASEER sai washe baki yakeyi, chan nahango yan * *Biebie Dee nvls*cikin nasu ankon sunyi shegen kyau suna picture da Aunty Baraka, anci ankuma sha komai a waye kuma a natse akayishi y'an Musty ma sunzo suma sosai bikin ya birgesu haka friends din Mommy ma</p><p><br /></p><p> Husnah pictures da tayi Allah kadai yasan yawan shii tayi pics hadda na masifa, tayi da amarya da ango,MaMi, Mommy, inna hada su aunty baraka banda wanda aketayi da friends abundai sai wanda yagani. </p><p><br /></p><p> Fili akabama ango da amarya dan suyi rawa ABDULNASEE ne kawai ke kayanshi babu kuya AFRAH kama tsaye kawai take takasa rawa, dai dai friends na ango suka shigo cikin gayunsu nan fa akafara lik'e photographs nata aikun su, nan kasama Amarya lalle, Babuwa Masu kyau da tsari aka rarraba haka dai taro yatashi kowa yana san barka.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ran Friday aka daura Auran ABUDULNASER ABDULLAHI YELWA DA KHADEEJA SALIS MANI(AFRAH) Bayan ansakko dake sallahn juma'a masalacin al-manar dake kaduna, manyan mutane da dama sun samu hakarrta daurin auran tunda kan masu kudi da tan yan kasuwa mango ABDULNASIER yasa kwalliya cikin farar shadda yayi kyau har yagajii baki yaki rufuwa sai smiling yakeyi, gaisuwa yarikayi da yan uwa da kuma abokan arziki anata daukan pictures abundai masha Allah, chan gidama Amarya AFRAH tayi kyau sosai duk da wani make-up ne a face dinta ba amma tayi kyau sosai haka friends ma da yan uwa da abikan arziki duk suyi kyau kowa ciki atanpan ankonshi,su Husna babu sauki tayi kyau sosai anata pics, Mommy, Mami, inna kowa yayi kyau masha Allah nan dai ABDULNASEER da friends dinsa suka iso ana ta daukan pictures kowa yayi kyau, inkun ga mommy kamar mara lfya ita komai ta baibai yazo mata gadai kwalliya tasha amma babu walwala sam a fuskanta ita kadai tasan halin da take ciki ABDULNASEER yareke AFRAH gam wajen pics babu ko d'an kunya nan sai smiling yakeyi da ance Allah sanya Alkhari yace ameen... Haka dai aka gama pics sukawuce a gidan angoma Ummu-Abdulnaseer, aunty Murya, Aunty Rabila, aunty baraka, aunty shuwa, aunty Ummah da sauran yan uwa da abokan arziiki duk sunyi kyau abin sha'awa da birgewa su HUmairah kam gidan su AFRAH sukawuce cin nasu yinin bikin, Mami da yan uwanta yinin biki mai kyau da tsari suka shirya babu wani kida da akayi amma abinci gashin big city rentals services suka dauko suke keta rabon abinci kana da zaune</p><p><br /></p><p> Mommy ita mamakin inda su MAMI suka iya irin wanan abu takeyi, abunda taso yi kenan a bikin Fatty amma komai yazo mata a karkace, _lol Mommy kenan_ haka akaita cikin yinin bikin cikin kwanciyan hankali anci ankuma shaa Alhamdulillahi, chan nahango y'an *biebie dee nvls group da biebie dee fans club* cikin anko sunyi masifar kyau kowa yaxo hadda wanda basa hawa online da yan labe. Lol kowa yaci gayu sun ci sunkuma sha ankuma yi pics da AFRAH kaman mai Afiface tazo taita raba abubuwa nan wasu suka fara tafiya yyayin da wasu sukace sai sunraka amarya gidanta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>K'arfe 6:00 akazo daukan Amarya wajen Daddy aka fara kaita nasiha sosai yayi maya mata gami da sa mata albarka nan akayi wajen Mami da ita nan ma nasiha mai tsara jiki tayi mata ita da yan uwanta sosai AFRAH ke kuka dakanan akayi wajen Mommy da ita, sunkai Minti 3 amma mommy babu abinda tace sai wani cika da batsewa takeyi mman Heeshmer da Anty Bee ne suce" sallama fa tazo yyimaki anty Bilki"</p><p><br /></p><p>Mommy da tacika tayi kam, so take kawai ta amayar da wasu abubuwa da ranta kozata samu sauki cikin zuciyanta takuma chusa masu haushi kaman yanda takeji chan tace" sai yanzo ne za'a wani kawomin ita nayi mata nasiha sabida ku butulu ne, na raina yarinya tin tana k'ara sanan nice za'akawo nayi mata nasiha a k'arshe? Toh bazanyi ba duk abinda taga dama tayi wanan matsalanta" tinda Mommy ke kan kika da batsewa aunty zulaiha taje tafada ma inna so Mommy nagama fadan haka inna tashigo side, jikawai sukayi ance" in baki sa Albarkan ba samai ja'ira? Yarki ta cikin ki ma baki sa mata ba re kuma ta wasu inkinsa ba sunanki Bilki ba" nan Inna ta shiga sauke kwandon masifa wanda Mommy batasan ta iya ba, nan kaita ba inna hakuri amma sai k'ara hawa takeyi da inna ta hakura sanan suka fice a side din. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mommy jin zuciyarta tayi na tafasa a fili tace insha auranan bazai taba albarka ba sakota za'ayi kuma wlhy bazata zaunamin a gida ba, tayi haka dan tabasu haushi takuma b'ata shirinsu sai gashi ita cema ranta ya k'ara baci </p><p> Su Axexah ne suka zauna jefanta Nana tace" sai da nace karkiyi komai amma baki jiba gashinan da girmanki an zageki abansu"</p><p><br /></p><p>"Bazaku gane ba Nana, haushi nakeji naga abubuwa haka nafaruwa Da AFRAH d'an bansata lissafin wanda zasu cigaba haka ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Mtsww toh Ai sai kiyi abinda zakiyi, yarinya dai tayi goshi na lura komai ke kan yaranki ki kikeso yafaru, da ni na Haifa Aftahn ma ashe haka zakimin" Azezah tace </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ni kikema Magana Haka azezah d'an kinganni cikin damuwa? "</p><p><br /></p><p>"A'a Yaya bakida wani damuwa fa, ji gidanki kedai da yaranki mubamuce muna da damuwa ba sai ke? Wanan dai sa ma kai ne"Nana tachai</p><p><br /></p><p>"Ohhh haka ma zakuce mai kuke nufi ne? "</p><p><br /></p><p>"Kawai kibar maAllah komai a hannunsa"</p><p><br /></p><p>"Ni zakice nabar ma Allah komai kun manta ku irin mugun halin da kukeyi"</p><p><br /></p><p>"Wanan Da ne banda yanzo, mun riga mungane gskia kema kum ya kamata kigane hakan"</p><p><br /></p><p>Xaginsu Mommy tashiga yi hadda yimasu gori iri iri </p><p><br /></p><p>"Mai da wukar gobe gobe zamu bar maki gidanki, Amma kisani akwai ranan nadama"barin Parlor sukayi Mommy ta rakasu da harara.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sun Mman Heeshmer kuwa suna fita moto duk suka shiga dan kai AFRAH gidanta, amarya da Inna, maman Heeshmer mota d'aya suka shiga yayin da su mom fauza, aunty zulaiha da sauran yan kai amarya duk suka shigiga mota</p><p> Friends ma duk sun shiga mota wanda keda samari kuwa sune zasu kaisu. </p><p><br /></p><p> Sun isa gidan amarya Lafiya da ke u/rimi jaaa Abdulkadir road, gida ne maidaidaice mai kyau compound din gidan za'ayi parking motoci 4 nan duk aka shiga ciki 4 bedrooms ne sai side na ABDULNASEER parlor ne da bedroom sai toilet a ciki. </p><p> Gidan AFRAH yayi kyau, yayi kyau sosai kaya masu kyau akayi mata bedrooms din duk an zuba gadaje 2 dai Daddy ne yayi kamar yanda yama Faty sauran Biyun kuwa wanan duk Aikin su Mami sunyi kokari matuwa sunkuma ba makiya mamaki Fatty gaba daya tarasa abinyii mamaki wai takeyi abinda bata taba zata ba. </p><p> Haka Mutane sukai ta san barka da sa albarka akafara wucewa, mutane sun d'an ragu nan su aunty Shuwa da aunty baraka da mai make-up sukazo, nan akasa Afrah tashiga wanka nan mai make-up tashiga yimata kwalliya tayi kyau sosai cikin material lace fited gown tayi kyau har tagaji. </p><p> Nan friends suma suka dau nasu wanka duk da basu san za'ayi dinner ba amma da kayansu in case nan suka dau walwali kowa yayi kyau su Mman Heeshmer da sauran k'anne duk anyi kyau nan aunty baraka ta aika mota a dauko maman Amarya Da sauran jama'a</p><p> Nan motan da Amarya zato aunty barakce tarakota har motan sanan ta rufe</p><p><br /></p><p> Nashiga cikin motan wani sanyi gami da kamshi ya ratsata juyowa tayi nan sukayi 4 eyed da angon tana yayi kyau cikin shadda fara tass... Kai baxan iya bayani ba sun kyau da yawa kawai</p><p> A cin kin silversand motan tayi parking da da sauran motoci nan AMARYA DA ANGO suka fitoh hannun su cikin na juna nan pa photographs suka shiga kashe masu pictures. </p><p><br /></p><p> Biki yayi baki waje yayi waje wanan event na manya ne coz friends na Abban Abdulnaseer ne suka had'a dinnern Husana da sweetheart dinta sunyi kyau sosai haka Zarah da Mahmoud dinta, Zainab da Muhammad dinta Suleiman da Abdul ma sunsha gayu, kowa yayi kyau familyn Abdulnaseer kuwa gayun su yayi yawa Anty maijidda, aunty aisha moh'd, Anty Baraka da sauran anties na ango duk sun sha kyau har sun gaji. </p><p><br /></p><p> Abdulnaseer yayi rawa kaman babu gobe shida amaryansa lik'i kuwa sun shata haka akaita gudanar da Dinner cikin farin ciki anci ansha har anba uku lada ga abubuwa masu da su aunty shuwa da aunty baraka suka raba tap da jaka haka dai taro ya tashi lafiya kowa na san barka, maman Zarah da husna duk sunzo haka sukaita san barka haka musty da yan uwanshi ma, Fatty kamar gunki</p><p><br /></p><p> 12:00 aka tashi kowa yana tasan barka Mommy ko d'an bakin cikin k'in zuwa tayi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Washegari bud'an kai ranan duk akazo ganin gidan amarya both family da abokan arziki sosai kowa ya yaba da tsarin gidan da kuma irin kayan da akayi mata, wa'azi malama Hassana tayi mai ratsa jiki sai kusan magrib aka gama k'are akayi addu'an Basu zaman lafiya hijabai aka raba sanan mutane suka kama gabansu, sai da a ka k'ara gyarama Amarya gidanta sanan kowa yawuce gida ya rage daka Afrah sai friends nata.</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 66-67_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*D*uk abinda yakamata ayi anyi nan friends aka a basu abinda za'abasu, kud'i masu yawa suka samu kana AMARYA da ANGO sukaita godia, haka duk suka tafi kowa na farinciki. </p><p><br /></p><p> Washegari duk y'an biki sukaita shirin tafiya sisters na Mommy kuwa tin 6:30 na safe suka bar gidan sabida ba k'aramin rashin Mutunci Mommy tayi masu ba ita da Farty su aunty Azeezah sunyi alkawarin bata k'ara ganinsu a gidanta, haka dai suka rabu a baran baran. </p><p><br /></p><p> Y'an katsina ma duk sun wuce a haka y'an uwan Mami ma da mamin kanta d'an babu abin da zata tsaya yii kuma, haka dai kowa ya tafi cikin farin ciki ga bun arziki</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gida duk yan biki sun wuce Inna da aunty zulaiha ne suka rage sai Fatty itama gobe zata wuce su Inna ko sai nan da 1week</p><p> </p><p> Wunin wanan ran a bedroom Fatty da Mommy suka kule suna maganganun su</p><p><br /></p><p>"Wai maganan meye Daddyn ku kemaki dazo?" Mommy tace tana kallan Faty </p><p><br /></p><p>"Hmmmm wai bana shigowa gaidashi"</p><p><br /></p><p>"Toh ta inda ya bullo kuma kenan"</p><p><br /></p><p>"Nima abinda nace kenan, kawai dai nace yayi hakuri"</p><p><br /></p><p>"Ai koma mekikayi shine yaja"</p><p><br /></p><p>"Wallahi kuwa"</p><p><br /></p><p>Haka sukai ta hiran Daddy suna kushe duk wani abu da yakeyi d'an Mommy tariga ta chusama Fatty wanan dabi'ar, kaka bisani kuma suka koma shirin bikin AFRAH suna tsine ma duk wani wanda yayi rawar gani abin dakuma kushe duk wani abu da a kayii</p><p><br /></p><p>"Ni wallahi Mommy dama a sake ta naga k'arshin rawan kai"</p><p><br /></p><p>"Hmmm wallahi da anga ruwan bala'i dan bazatamin zawarci a gida ba"</p><p><br /></p><p>Daria Fatty ta sosai kana tace "kai Mommy wai zawarci" </p><p><br /></p><p>"Ehh mana haa kawai, ai nima lokacin zanma Inna rashin mutunci kaman yanda rayi min" </p><p><br /></p><p>"Me tamaki Mommy? </p><p> Faty yace tana zare ido"</p><p><br /></p><p>Nan Mommy ta jayyane mata komai, nan suka shiga xaginsu gami da tsine masu haka dai sukai ta hiransu. </p><p><br /></p><p> Washe gari bayan sallan la'asar Musty yazo daukan Fatty, har wajen Inna yaje ya gaidata kana yadawo parlor ya zauna, mommy ce ta shigo parlorn cikin Fara'a gaisheta yayi mommy ta amsa cikin sakin fuska sanan tace " dama Mustapha akwai maganan da nakeso muyi da kai"</p><p><br /></p><p>"Oky Mommy inajii, Allah sa kafiya"</p><p><br /></p><p>"Ahhh lfyalau" mommy tayi magana tana smiling </p><p><br /></p><p>"Toh inajinki Mommy "</p><p><br /></p><p>"Dama inasan jin dalilinka na hana Fatima zuwa school ne"</p><p><br /></p><p>Kallan Fatty yayi da shigowanta kenan parlorn, gaban ta ne ya fad'i wani tsoron Mommy ya shigeta</p><p><br /></p><p>"Babu komai Mommy coz nan da 1 month zamuwu ce Turkey, inmuje chan sai ta cigaba"</p><p><br /></p><p>Washe baki Mommy tayi sosai cikin farin cikin tace"Fatty da *Gajen hakuri*(Afrah bhai) kike shine duk kinbi kin damu kanki" tayi maganan tana kallan Fatty, smiling dinda bai kai ciki ba Fatty tayi </p><p><br /></p><p>"Toh kutashi kuwuce kar kuyi dare"</p><p><br /></p><p>"Daddy bayanan ne? "</p><p><br /></p><p>"Ehh ya d'an fita ne"</p><p><br /></p><p>"Okay inyadawo a gaidashi sosai, sai munzo maku sallama"</p><p><br /></p><p>"Toh insha Allah zaijii, Allah tsare hanya yakuka kai ku lfya"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen mommy"</p><p><br /></p><p> Har bakin Mota ta rakosu ita dai Fatty gaba d'aya jikinta yayi sanyi faduwa gabanta kawai yakeyi, haka dai suka wuce mommy sai d'aga masu hannu takeyi har suka bar cikin gidan ita kuma Mommy ta koma ciki. </p><p><br /></p><p> A hanya kuwa tinda Musty ya kalla Fatty bai kuma kallanta bah driving kawai yakeyi gashi sai uban gudu yake shararawa Fatty duk a tsorace take, haka har suka iso abuja</p><p><br /></p><p> yayi horn mai gadi ya wangale mai gate yashige, inda aka tanada d'an adana motoci anan yayi parking, batare da da ya kalleta baya fita yabarta cikin moton Fatty dai gabanta sai faduwa yakeyi hata tafitoh a motan jikita sanyi qlau</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sallah duk suka farayi kana Musty yace" yayi maki kyau, kinje kinkai k'arana wajen Mommy ko? yayi maki kyau school kuma wallahi inhar kina gidanan baki sake zuwanshii har abada wallahi, kuma ko wa zakije kifadamawa a familyna kiyi aikin banza d'an babu abinda zasuyi"yana gama fad'an haka yatashi yawuce bedroom dinshi</p><p><br /></p><p>Xubewa Fatty tayi awajen tashiga rere kuka tanacewa"mommy meyasa xakimin haka, meyasa, why why" haka taita kuka</p><p><br /></p><p>" kibar kukanan kije kumin girki"</p><p><br /></p><p>Nan Fatty ta tashi tayi cikin, bawani abu mai wahala tayi amma sai bayan sallan magrab tagama, kadan Musty yaci sai da yayi sallah isha'i sanan yashi ga wanka bayan ya fito shiryawa yayi cikin gayun na masifa Fatty na ganin haka tasan hau zai shiga club kenan sai kusan 9pm yabar gidan bayan ya kule Farty ta baya sanan ya amshe phone d'inta ranan tasha kuka. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>, haka dai Fatty tai ta rayuwa gadai kud'i amma babu kwanciyan hankali ga Musty da saurin hannu in abunshi ya motso gashi baya tsoran kowa a familyn shi ta lura ma su lallabashi sukeyi bata zuwa ko ina sanan baya bari taje ko ina, sai inyana jin mutunci shine zai kaita gidan Anty lailah</p><p>Shima batawani dadewa gaba d'aya bata jin dadin xamanta da Musty sam gashi da san girkin masifa bai da aiki sai cin abinci. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> AFRAH da ABDULNASEER kuwa sunci amarcinsu cikin farin ciki da kuma kwanciyan Hankali, sosai ABDULNSEER ke kuda da ita da duk wani abu da takeso haka itama tana k'okari sosai irin soyayyan da suke zubawa a gidan nasu abin sha'awa ne da birgewa gashi duk y'an uwanshi na santa da k'unarta shiyasa itama take kyautata masu sosao, tin sanda sukayi wata d'aya da aure suka shirya sukaje katsina d'an gaida Mami da sauran y'an uwa</p><p> Sosai kuwa duk sukai murna da ganinsu, sosai Abdulnaseer yayi masu alheri daka gagin Mami har na Daddy kwanansu 2 suka dawo tare da tsaraba iri iri. </p><p><br /></p><p> Gida kuwa kotaje Mommy a dakile take amsa mata gaisuwa ita dai AFRAH mamakin kawai takeyi kawai ita dai tasan bata mata komai ba, haka zatawuce wajen Inna d'an har yanzo Inna bata koma katsina ba. Sai dai su sha hiransu da Afifah da y'an aikin gidan Mommy ko babu ruwan ta da ita. </p><p><br /></p><p> Haka lokaci yaita tafiya abubuwa sukai ta faruwa ciki hadda rasa Fatty a waya ko da yaushe k'ashe Musty da hanshi yakira mommy yace ta dena k'ira ranan Mommy tayi masifa da bala'i kiran Mommyn Musty tayi amma sai mommyn nashi ta koyi bayanshii kaca kaca sukayi da Mommy shidai Daddy ya zuba mata ido (dama Fatty bakin maganshi takeyi ba) ikon Allah kawai yake kallo, haka abu buwa sukai ta faruwa Mommy ko da yaushe cikin zafi zuciyar tayake, Inna ma ba shiga harkanta takeyi ba yaka inta gaisheta ta amsa duk abinda takeso batada damuwa coz ga y'an aikin gidanan gakuma anty zulaiha. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>🌸🌸🌸🌸</p><p>Har yanzo kayan su Daddy babu wani labari tun bayasa abin a rai har ya vara damushi d'an yanzo banki sun fara bukatar kudadansu da yaci, toh kayan sune Hope dinsa amma suru vabu wani labari</p><p> Yauma zauna yake shin kadai parlon shi yayi nisa sosai cikin tunani har daida Suleiman ya dafa shii kana yace" Daddy tunani irin haka babu kyau"</p><p><br /></p><p>"Nasani Sulaiman amma kuma dole ne, sabida bashin bakinan kulun da su nake kwana da shi nake tashi Suleiman wallahi Inna *Danasanin*, cin wanan bashii"</p><p><br /></p><p>"Kar kadamu Daddy insha Allahu kayanku zasu fitoh kuma da yaddan Allah zaka biya banshi"</p><p><br /></p><p>"Allah sa haka, kana ko samun Hafiz ta waya? "</p><p><br /></p><p>"A'a nima maganan da nazo muyi kenan"</p><p><br /></p><p>"Allah Dai ya shiryeshi yasa kuma yanayin karatun"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen"</p><p><br /></p><p> AFRAH tanan cikin kwanciyan Hankali ita da mijinta ga sch tana juwa haka kuma har yanzo bata dena yin cake da sauran abubuwa ba ka d'an Abdulnaseer bai hanata yana da burin tallafamata nema sosai k'an sana'ar nata. </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> 'Yan banki sun fara sa Daddy a gaba d'an lokacin da yayi masu alkawarin biya yakusa yacika, sosai hankalin Daddy ya tashi nan da nan yakira Sulaiman ya saida mai mishi babu abinda Daddy ke tsoro kaman tijaran y'an bakinnki, babu dad'ewa Suleiman ya iso d'an anan kaduna yake service dinshi</p><p> Kwantar ma Daddy hankali, yayi kana suka fara neman mafita nan daddy ya yanke shawaran sai da gidanshi da ke Kabala sai shaguna guda biyu, sosai Suleiman ya kalleshi kana yace" Daddy kadai sai bazai su wuce 20million ko"</p><p><br /></p><p>"Nasani Sulaiman"</p><p><br /></p><p>"Toh nasan ai wanan kudaden zasu isa ko? </p><p><br /></p><p>"Hmmm Sulaiman kenan bakaji nace ina danasanan cin bashin danayi bane? "</p><p><br /></p><p>"Naji Daddy"</p><p><br /></p><p>"Toh wallahi inhar zan had'a duk wani abinda na manlaka banda gidanan toh ba xasu biya bashinan ba, d'an bashi ne masu yawan gske kuma sanan kanka ne ni ban kasan ce mai siyan k'addara ba, dama basa hannu cikin business na Ghana ba da abin zai zo da sauki d'an kud'in da na zuba yafi 70 million"</p><p><br /></p><p>Ido Sulaiman yazaro sanan tace "Daddy waya baka shawaran yin wanan Business din? "</p><p> </p><p><br /></p><p>"Babu kowa Suleiman, inaga k'addarata kenan kuma a shirye na ke na amsa koma wani iri ne"</p><p><br /></p><p>Sosai Sulaiman yaji tausayin mahaifinsa ya kamashi yaji dama ace yana da kud'i ya sharema Daddynsu hawaye</p><p><br /></p><p>Nanan Daddy yayi waya da wani yaron su Hamisu ya sanar da shi kan sai da gidan da kuma shagunan, bayan kwana Hamisu yagama komai yakawo kud'i Ihsani Daddy yayi mai Hamisu nata godia</p><p><br /></p><p> A ranan ya turama bakin 15milion din nan dai suka k'ara mai 2 moths, addu'a Dady da Sulaiman sukai tayi kan Allah temakesu k'ansu yazo kafin lokacin. </p><p><br /></p><p> Alhaji Yunsuf Ma Hankalinshi sosai ya tashi d'an nashi bashin yafi na Daddy yawa nan dai shi ya bada milin25 ya rage 2 months shima suka k'ara mashi nan duk suka dukufa da rokon Allah babu dare babu rana. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Afra sosai tayi fice wajen yin snacks madu dad'i da kuma kyau, irin ficen snacks dinta yayi ne yasa Ummie da aunty baraka bama Abdulnaseer yawara kan ya bud'emata join na saida snacks ai kuwa cikin lokaci d'an ya gama komai tare da ya aikin wajen sancewar akwai kudi, sosai Affrah tayi murna hadda yima Abdulnaseer kuka d'an yafara cika buri da takeda shi cikin ranta ranan wuni tayi tana k'iran yan uwa da abokan arziki tana sanar dasu ciki Hadda Fatty (d'an sometimes akan sameta a waya) Mami, Uncle Junaid, Daddy, Inna da sauran yan uwa na kusa musaman suka kira Abdulnaseer sukai mai godia gami da samai albarka Mommy kam yi tayi kaman batajii ba</p><p><br /></p><p> Haka aka fara gudanar da aiki a Bakery na Afrah cikin kwanciyan hankali da natsuwa, in AFRAH ta tashi a school ta kan lek'a sai yamma ta dawo, bata samun matsa da ma aikatan sam coz duk sun iya aiki kaman ita sometimes kuma takanyi da kanta, cikin lokaci kad'an wajen yayi suna sosai. </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>Ansa Ranan Bikin Zarah da Mahmoud d'an yau nema aka kawo lefanta, masha Allah kaya sunyi kyau sosai anata san barka, su Afrah ne Gaba suke komai, koda mutane yan kallon lefe suka tafi, Su Husnah duk sunwuce sai ita kasala takeji sosai gawani irin gajiya kaman ta kwana ta wuni tana aiki tanan </p><p><br /></p><p>kwance a bedroom na Zarah, Zarah ce tashigo dakin da cup hannunta zamatayi bakin bed kana tace" ta nass wai kodai yau nan zaki kwane"</p><p><br /></p><p>"Ke walhy bazan iya driving ba, sweetheart xan kira ya zo ya daukeni"</p><p><br /></p><p>"Motarki kuma fa? "</p><p><br /></p><p>"Pakamin ita kawai a compound "</p><p><br /></p><p>Nan dai ta kira ango na ta fadamain yaxo ya dauketa bazata iya driving ba, hankali tashe Abdulnaseer yazo duk ya damu, koda suka koma gida tattalinta yaitayi kaman kwai, amma duk da haka da zazzabi ta kwana, da sassafe ya sata tashiya ya kaita hospital, babu irin rokon shi dabatayi kan ya barta ta warke amma sam yace shi bayyada ba, ba d'an taso bah haka ta shirya suka wuce hospital din...</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 68-69_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*S*una isa hospital din, office din doctor Jamilah direct sukayi bayan sun gaisa da doctor ne Abdulnasir da kanshi ya fidi abinda ke damun Afrahn, aune aune da gyaje gyaje a kayi mata bayan d'an wani lokaci result ya fitoh kallan shi doctor Jamilah tayi sosai kana tace" congratulations"</p><p><br /></p><p>Kallanta yayi irin naneman k'aran bayanin nan</p><p><br /></p><p>Kai ta dagamai kana tace" matar ka na dauke da ciki na 6weeks"</p><p><br /></p><p>Hamdala yafarayi kana yabama AfrahTight hug sosai nan yashiga sa mata albarka gami da kara godema Allah da kyautan Da yabasun gaba daya ya manta da doctor Jamilah gyaran murya tayi yasa yatuna da inda yake nan da basu shawarwari kana suka wuce. </p><p><br /></p><p> Gidan su direct yayi da ita bai bari ko gaisuwa sunyi da Ummie ba ya jayyano mata komai, nan Ummie tashi ga hamdala gami da godema Allah ita dai Afrah kunya duk ya cika ta Abdulnasir kam babu ruwanshi sai kiran yakeyi yana sanar ma jama'a haka Ummie ma ita abin nasu kamar a film. </p><p><br /></p><p> Sosai Afrah kesamun kula tin daka kan y'an uwan Abdulnaser ummie da Anty Baraka kuwa ba'a magana haka Inna da Mami ma sosai sukayi murna sunkuma yi Addu'an Allah yaraba lfya. </p><p> Musanman Inna kesawa tindaka katsina kawoma Afrah abubuwa iri iri na kwadayi wanan abu na bakanta ran Mommy addu'a tafata yi Allah sa cikin ya bare taga k'arshin rawan kai d'an har Daddy murna yakeyi d'an yanzo Mommy bakin cikinta a fili yake babu wani boye boye kaman da komai free takeyi shii yanzo bawani ginman Daddy take gani bah coz baya sake mata kud'i kaman da, Sulaima kuwa kulun cikin yima Mommy Addu'an Allah ya shiryeta yakeyi babu dare babu rana. </p><p><br /></p><p> Zaune take a parlor sai masifa takeyi tana zage-zage Suleiman ne yashigo da sallaman shi amma Mommy ko amsawa bata yii ba, kallaanta yayi sosai kafin yace" Mommy lafiya? meya b'ata maki rai haka?"</p><p><br /></p><p>" wai hanni Hajia Zaituna sata ma wulakanci kan dubu 100 shine takirani wai tanasan kudin nan da 3days, nama Daddy dinku magana amma har yanzo kudi sunki fitowa"</p><p><br /></p><p>"Abubuwa ne suka ma Daddy yawa amma ai da ya biya kema kin sani Mommy"</p><p><br /></p><p>"Naji masoyin Uba, inda kafi akwaiki kenan wajen kare Ubanka da su Afrah"</p><p><br /></p><p>"Allah huci zuciyarki, zan baki 40k ki bata sai ki rage"</p><p><br /></p><p>"Toh wai saura wata nawa ne kagama wanan bautar k'an? Shi Daddy ku ba company ba da yanada shi duk da kana chan kana aikin ka "</p><p><br /></p><p>Smiling Suleiman yayi kana ce" nan da lokaci kadan zan gama, aiki kuma insha bazai yi wahala ba"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Toh yaushe zaka kawo min kud'in dan so nake na tura mata yau, bari ma nayi trying number Fatima ma nace ta turomin yanzo Daddynku yazama abinda ya zama"</p><p><br /></p><p>"Anjima insha Allah" nan yafita yabar mommy na kokarin kiran Faty</p><p><br /></p><p> Cikin sa'a kuwa tasameta ringing 3 ta dauka bayan sun gaisa ne Mommy tace wai tayimata transfer din 100k daka b'agaran Fatty wani bacin rai taji tsaki tayi kadan kana tace" wai mommy sau nawa zan cemaki bana fita hum? Ko ta wayan zan maki transfer din ne? "</p><p><br /></p><p>" d'an ubanki ni kike fadama magana?"</p><p><br /></p><p>"Toh mekikeso nace maki baga AFRAH ba ki kirata kice tayi maki transfer mana ni kibar ni naji da abunda ke da muna please"</p><p><br /></p><p>"Lallai ma baki da hankali nice zan kira Afrah nace ta turomin kud'i? Allah kiyaye wallahi gara na mutu babu har yanzo bata da abinda zata bani ai d'an bata kai bah kuma bata isah ba"</p><p><br /></p><p>"Toh naji Mommy d'an Allah kin barni toh danni banda abinda zanyi maki" tana gama fadin haka ta gashe wayan tana kuka sosai sai yanzo da ta aure Musty ke koya mata hankali tafara nadamar abun da tayi da, kallon bedroom dinta tayi sosai komai najin dadi da more rayuwa a kwai shi a cikin d'akin ga kud'i ga komai amma babu kwanciyan hankali ko kadan ko da yaushe cikin tashin hankali take ga zaman kadaici sau biyu Musty na zubarmata da ciki wai bai shirya haihuwa ba kuka sosai Fatty tasha duk wannan masifar da take ciki AFRAH tayi ma fatan shiga irin wanan halin sai gashii ita ga dai kudin amma babu school babu farin ciki babu kwanciya hankali wanda ta RAINA tana ganin ita ba kobai bace kuma ita ba kowa bace ita duk tasamu cigaba dakuma farin cikin rayuwa, fuskarta na goge kana tajawo phone d'inta tashiga dialing number AFRAH har yagama ringing batayi picking ba chan sai ga call din AFRAH yashigo cikin farin ciki Fatty tayi picking gami da cewa" Sis ya k'arfin jiki? "</p><p><br /></p><p>Dariya Afrah tayi daka chan bangaran sanan tace" lafiya lau, alhamdulillahi"</p><p><br /></p><p>"Masha Allah haka mukeso, ya Baban baby?"Fatty tace tana daria</p><p><br /></p><p>"Lfyanshi lau, ai munan shigowa abuja next week insha Allah"</p><p><br /></p><p>"Allah kawoku lfya gskia nayi murna sosai"</p><p><br /></p><p>"Ameen amern sis ina yayana yake ne? "</p><p><br /></p><p>Sai da fatty ta kalle side dinda bedroom din Musty yake kana tace "yanan lfyalau"</p><p><br /></p><p>"Ah gaidamin shi acemai munan zuwa"</p><p><br /></p><p>"Toh zayji" jira suka d'anyi sanan sukayi sallama</p><p><br /></p><p>Kallan phone din Fatty tayi sai kawai taji hawaye na zubomata amma kuma taji dadin wayan da sukayi da AFRAHN, nan dai takira yaya Suleiman, yaya Abdull, Daddy da Inna albarkan da Daddy da inna keta samata ne yaita sata farin ciki sai smiling takeyi</p><p> Musty ne yafito daka bedroom dunsa sanye yake da 3quarter da T-shirt, zama yayi a 1 sitter kana yace" Baby kin gama abincin kuwa? "</p><p><br /></p><p>"Ehh nagama"Fatty tace a natse</p><p><br /></p><p>"Good kedawa kiketa waya? "</p><p><br /></p><p>"Su Daddy ne da su Yaya Suleiman na kira"</p><p><br /></p><p>"Ohhh sunan lfya ko? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ehh lafiya lau, AFRAH tace zasuzo next week"</p><p><br /></p><p>Shuru Musty yayi na minti 3 chan yace" ohhh wanan cousin naki mai kirki da akayi bikin ta bayan namu ko? "</p><p><br /></p><p>Baki Faty ta washe gami da cewa" yes ita"</p><p><br /></p><p>"That's nice Allah kawota lafiya"</p><p><br /></p><p>Mamaki Fatty tayi ganin Musty yayi saurin yadda Da zuwan Afrah, wanan ranan dai Musty da sauki bai birkice mata ba kuma bai fita ko ina bah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Mommy yanxo babu wahala anyi fad'a da ita duk friends dinta basayi da ita yanxo sabida rashin san gaskianta y'an uwanta ma duk sunfita harkansu sabida kawai sun fada mata gskia, Suleiman dake kokari sosai a kanta amma Mommy bata gani sai rainuwa abu k'adan tace ta k'osa Hafiz ya dawo(hafiz din da ko a phone ba'a samunshii) </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kula sosai Afrah ke samu ta wurare da dama kowa santa da tattalinta yakeyi abin dai gunin sha'awa. </p><p><br /></p><p> Bakery dinta kuwa Allah ya samai albarka sosai take samun alkhari gashi yayi fice sosai ita har mamaki takeyi, kudad'en da take samu kuwa sai dai ta temaki wanda bayida shi koda bata sanshi ba ita dai bata komai da shii d'an Abdulnaseer ya tsare mata komai, in taje katsina gaida su Mami haka takeyi ma mami da yan uwanta alkhari Abdulnasir ma yayi masu duk da basu nemi komai sun rasa ba, haka ta side babanta sai dai in bata ji abu ba, inko taji ko ta bank ne sai ta tura Afrah bata da rowa sam abunta bai rufe mata ido ba ko kadan abunda na jama'ane ko da bata sanka ba bakuma tasan da inda kafitoh bah shiyasa kowa kesama ta albarka. </p><p><br /></p><p> Sunje Abuja tarba mai kyau suka samu da ka wajen Fatty da Musty, sosai Afrah taga changi wajen Fatty d'an hira suka sha sosai daka Abdulnadir, musty Afrah dakuma Fatty sai dare suka tafi side din bak'i da yasha gyara, kwanan su biyu suka bar abuja suka dawo kaduna, wani ikon Allah tin da su Afrah sukazo Musty bai yi wani halin banxan shi ba Fatty taji dad'in juwan su Affrah sosai dan sosai ta ragemata damuwa da take ciki, musty kaman yana jira suna wucewa takoma gidan jiya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Suna dawowa aka fara gudanar da sha'anin bikin Zarah da Mahmoud bikin yayi kyau sosai Amarya da angonta sunsha kyau har sun gajii haka su Afrah da husna da sauran k'awaye duk suka sha shagali, Inna, anti Zulaiha sunje Daddy da su yaya Suleiman ma sunje daurin aure haka aka gama shagalin biki kowa na san barka</p><p> Ankai Zarah doctor's quarters gidanta yayi kyau sosai masha Afrah tasha girga girga hadda Abdulnasir din kanshii. </p><p> Yanzo bikin Husna ne a gaba kafin sufara exam's ne.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yau Sunday ranan Afrah a gidan su take yini zaune take a d'akin Inna tana cin d'an wake wanda Afifah tayi mata Daddy da yaya Suleiman da yaya Abdul ne suka shigo d'akin k'ara gaisu su Afrah tayi sanan ta ciga da cin d'an wakenta Afifah na manta zance, hira sukerayi cikin farin ciki phone Suleiman ne dake hannun Afifah ya shiga ringing "laa wallahi Anty Basma ce" cewar Afifah tana daria</p><p><br /></p><p>"Kee bani wayana" yaya Suleiman yace</p><p><br /></p><p>"Wacece kuma Basmah"/Inna ta tanbaya</p><p><br /></p><p>"Walhy girlfriend din yaya ce ai muna waya da ita"</p><p><br /></p><p>"Bani wayanan ni zan dauka"inna tace</p><p><br /></p><p>Suleiman da ke tsaye duk Afifah tabashi kunya sbida Daddy shi baiyi picking call din ba kuma shii bai ba Inna tayi picking ba " Allah sanya tabbatar da alkhari je kayi wayan ka" Daddy yace </p><p>Sosa k'eya Suleiman yayi kana yafice daka d'akin</p><p><br /></p><p>"Kai kuma dungum yaushe zaka kawo matar taka? "Inna tace tana kallan Abdull</p><p><br /></p><p>"Kai Inna D'an Allah ki barni"</p><p><br /></p><p>"Auuu babu farin jini kenan? "</p><p><br /></p><p>Daria sosai Afifah ta bushe da shii hadda rike ciki Abdul na kokarin yin magana Phone din Daddy ya hau ringing shuru duk sukayi kana Daddy yayi picking call din</p><p> Basan mai akacema Daddy bah nadai ji yana cewa"Alhamdulillahi, Alhamdulillahi Allah iso da su lafiya"</p><p><br /></p><p> Bayan ya gama wayan Kallan dukkan su yayi cikin fara'a da kuma farin ciki kana tace" kayan mudai da zasu zo ta jirgin ruwa ne suke hanya insha Allah " Nan suka dau kabbara gami da yima Allah godia haka Suleiman ya shigo ya samesu ko da aka fadamai hamdala yayi gami da yima Allah godia duk wanan abu da akeyi Mommy bata sani ba dan bata shiga cikin su Inna wai mak'iyanta ne, haka suka wuni farin ciki sai bayan sallan magrib Abdulnaseer yazo daukanta amma basu bar gidan bah sai da sukayi Dinner. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> *Bayan Sati d'aya*</p><p><br /></p><p>Zaune suke dukkan su a babban Parlor Daddy, Mommy, Inna, Anty Zulaiha, yaya Suleiman sai Afifah d, wani series film na Philippines suke kallo Inna duk ta isha Afifah wai ta fassara mata, phone din Daddy ne ya shiga ringing ganin mai k'iran nashi yasa shi washe baki sallama yayi daka chan b'an garan aka amsa a wahalce </p><p><br /></p><p>"Lafiya? " Daddy ya tanbata</p><p><br /></p><p>Daka chan ban garan akace"alhaji jirgin kayanku ne keta nitsewa munyi duk iya k'okarin mu amma abin yaci tura"</p><p><br /></p><p>"Inalillahi'wainnah'ilaihinraji'un" shine kalman da Daddy keta nanatawa</p><p><br /></p><p> Tashi duk sukayi suna kallon sa</p><p>"Lafiya? Meyafaru?" Mommy' tace</p><p><br /></p><p>"Shu'aibu meyafaru? kasanar damu" cewar Inna da duk ta rud'e</p><p><br /></p><p>Sulaiman da Afifah kam kasa cewa komai sukayi haka anty zulaiha</p><p><br /></p><p>" nii Shu'aibu ina zan kai bashin banki? Kayan mu ta jirgin Ruwa ya tsine bashin Banki ya zan yi dashiii? Ins tsoran tirajan banki, kayanmu sun nit..."bai k'arasa ba ya fad'i k'asa.... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_wallahi ban da bakin da xan godemaku masoyana nagode sosai Allah saka da alkhari ina maku fatan alkhari a duk inda kuke a fadin duniya kuma ina k'aunarku har cikin raina_</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*PAGE*7⃣0⃣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*S*ulaiman ne yayi kan shi cikin sauri, baiyi wata wata ba ya dauke shii sai mota, mommy, Inna da anti Zulaiha duk sun rude Afifah kam sosai take kuka </p><p> Suleiman ba tsaya jiran suba ya jaa motan cikin sauri gaskee, gudu ya ringa shararawa kaman zai tashi sama, minti minti yana juyawa ya kalle Daddy, cikin ikon Allah suka iso hospital, nan da nan ayi kan Daddy nan Reception Suleiman ya zauna tausayin Daddysa sosai ya kaama shii hawaye ne ya fara zubowa daka idanuwan shii gogewa yayi cikin sauri nan ya shiga karanto addu'a daban daban. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> A gida kuwa su Mommy na ganin haka Suma duk suka shiga cikin mota bala ya jasu sai hospital din, a reception suka ga Suleiman nan suka shiga tan bayan shii amma Suleiman kasa basu amsa yayi sai chan yace " ba'a fitoh da shii ba tukunan" Inna Addu'a kawai takeyi haka Afifah da Anty Zulaiha mommy kuwa kuka takeyi tana cewa" Yaya zamuyi da banki ni Bilki? Ga kaya sun nitse " abubuwan da taita fada kenan </p><p> Wani irin tsawa Suleiman yayi " haba Mommy muna ta rayuwa kina ta wani kaya da banki, ki barmu muji da abinda ya damemu please" idanshi jajur yakeyin maganan </p><p> Shuru kuwa Mommy tayi bata kuma cewa komai ba,aunty Zulaiha ne ta koma gida d'an danko wasu kayayyakin da za'a bukata Bala ne ya kaita. </p><p><br /></p><p> ganan shurun tayi yawa ne yasa Afifah ta shi ta matsa chan gefe</p><p> Number Afrah tashiga dialing da Phone din Inna dake hannunta,</p><p> Afrah da ke kwance jikin Abdulnasir taji wayan ta na ringing " mik'omin sweetheart" tace ma Abdulnasir</p><p> Washe baki Afrah tayi kana tayi picking gami da cewa" tsohuwa mai ran karfe"</p><p><br /></p><p> Daka chan b'angaran Afifah tace" ba ita bace" cikin muryan kuka</p><p><br /></p><p>Tashi zaune Afrah tayi kana tace" Baby wht happen? Meyasa ki kuka kuma"</p><p><br /></p><p>"Daddy baida lafiya muna hospital dinda muke xuwa"</p><p><br /></p><p>"Meyafaru? Daka waya sai kuka" Abdulnaseer ya tanbaye taa</p><p><br /></p><p>"Daddy ne ba lfya, yana hospital " Afrah tayi maganan cikin kuka sosai</p><p><br /></p><p> "Kibar kuka insha Allah Daddy zai samu lafiya, insha Allah bari na sa kaya muje" </p><p> Farar jallabiya Abdulnaser ya sanya Afrah ma gown tasa ta dauki hijab dinta sukayi hospital d'in.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Duk sunan zaunen tsaye kusa da d"akin da Daddy ke ciki doctor Khalid ne ya fito nan duk suka shiga tanbayan jikin Daddy " kar kuda mu muje office please" bayan shi duk suka, kallansu dukkan su doctor Khalid yayi kana yace" bawani abu bane kawai tsorata yayi, amma insha Yana tashi daka bacci zai dawo normal yanan a room 21"</p><p><br /></p><p>"Oky mungode sosai doctor" Sulaiman da Abdulnaseer suka ce Inna kuwa Albarka taita sama doctor Khalid. </p><p><br /></p><p> Kwance yake yana baccin sa peaceful, matsawa kusa Afrah tayi tashiga tofamai addu'a</p><p><br /></p><p>" please ki barshi kar ki tashe shii" cewar Mommy da ke matsowa</p><p><br /></p><p>"Mommy kema please kitashi" Suleiman tace</p><p> Inna dai kallon Mommy kawai takeyi, tsawa kuwa tayi chan naji tana cewa" ai sai ki daure kizo sarkin Miji ya hana fita, Daddy kune babu lafya" tana gama fad'an haka ta katse wayan tana naganganu kasa kasa</p><p><br /></p><p> Fatty kam kuka tasha gami da salati</p><p><br /></p><p>"Wai Lafiya da ka waya sai kiwani fara kuka"Musty yace</p><p><br /></p><p>"D'an Allah d'an girman Allah da darajan manzon Allah SAW kabarni naje kaduna gobe wallah Daddynmu ba lafya" ta k'arasa maganan cikin kuka</p><p><br /></p><p>Tausayi taba Musty sosai dawowa kusa da ita yayi kana ya jata zuwa jikinsa sosai " sorry kinjii, insha Allah Daddy zai samu lafiya"</p><p><br /></p><p>Janye jikinta tayi daka nashi, kkallanshi tayi sanan tace" toh zaka barni naje? "</p><p><br /></p><p>"Shhhhhhhh kibar kukan haka, zamuje insha" </p><p><br /></p><p>"Nagode" </p><p><br /></p><p>"Amma nace kibar kuka ko? "</p><p><br /></p><p>Haka yaita lallashinta hattabar kukan.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A hospital kam sunan zaune har wajen 10pm Inna ne ta kalle Abdulnaser kana tace" maxa kuwuce gida gobe da safe in Allah ya kaimu sai kudawo"</p><p><br /></p><p>"Ah'a Inna inan har Daddy ya tashi" Afrah tace </p><p><br /></p><p>"A'ah Affrah kinsan dai yanzo bake kadai bane ko? Sabida haka kije gida insha lafiya zai tashii"</p><p><br /></p><p>"Zan bita Inna"Afifah tace</p><p><br /></p><p>"Toh kuje, sai Allah ya kaimu"</p><p> Sai da Afrah ta matsa ta k'ayima Daddy Addu'a kana sukayi masu sai da safe suka wuce. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Suna wucewa kuwa Daddy ya farka da salati a bakin shii, Suleiman ne ya taima kamai ya tashi zaune ya jingina da pillow, Sannu duk sukai tamai yana amsawa a hankali, 🍵 tea Mommy ta had'a mashi ya amsa yana sha a hankali shigowa doctor yayi yace babu wani problem </p><p><br /></p><p>Nan Suleiman yakira Bala driver yazo ya mai da Mommy da su Inna gida shikuma zai kwana da Daddy. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>Washe gari da sassafe Afrah da Abdulnaseer suka iso hospital din da brkfst mai rai da lafiya gai da Daddy sukayi ya amsa cikin sakin fuska basu d'ade ba suka wuce kasan cewar Afrah nada test a school, Afifah kuwa bata samu taje ba, sun wuce babu dadewa su mommy suka iso, sunan zaune Doctor Khalid ya shigo nan ya k'ara duba jikin Daddy yace komai yayi normal.nan Daddy ya bukata sallama aikuwa doctor Khalid ya mashi tarkato komansu sukayi suka dawo gida, shigowansu babu dad'ewa Fatty da Musty suka iso, side Daddy sukayi Direct daka shii sai yaya Suleiman a d'akin cikin Ladabi Musty ya gaida Daddy gami da mashi ya jiki Daddy ya amsa cikin sakin Fusaka, cikin sakin fuska ma suka gaisa da yaya Suleiman shima itama Fatty cikin ladabi ta gaidasu nan tama Daddy ya jiki, sai Musty ya gaida Mommy da Inna kana yacema Fatty zaije gidan su nanan malali da yamma xaidawo.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sai 2:30 Afrah suka fitoh lecture direct gidasu tayi nan ta tadda Fatty tazo murna sosai sukayi na ganin junarsu nan suka bod'e shafin hira mommy na d'aki bakin ciki duk ya isheta da da yamma Affrah da Fatty tare suka shiga cikn suka shirya abincin Dare suna saune a parlor ana gab da magrib Mommy ce ta aiko Atika tazo ta kira Fatty, Atika na bari parlor Fatty tayi bedroom din mommy </p><p><br /></p><p>"Mommy gani" Farty tace tana daria</p><p><br /></p><p>"Mahaukaciya cikin mak'iyanki zaki shiga ki zauna kina washe baki kina zance ko? "</p><p><br /></p><p>"Haa kajimin mommy nifa shiyasa bana kin haushe in Musty ya hanani zuwa wlhy ko dan ke, ke kin cika masifa da k'anan maganganu walhy muna zaman lafitanmu zaki fiddo da wani salo kuma ni gskia ban san haka" Fatty ta k'arasa magan tana turo baki gaba</p><p><br /></p><p>"Ahh lallai kema din kinbi sahun Afrah ko? Ni kike kallo ki kefada min magana haka ko? "</p><p><br /></p><p>"A'a ni kar kimin wani muryan tausayi ke dama Haka kikeyi abu hakan gskia ba sai kiwani fara fuskan tausayi"</p><p><br /></p><p>"Yayi kyau"</p><p><br /></p><p>"Tohh ni nawuce parlor" </p><p><br /></p><p>Mommy jii tayi kaman tayi hauka sabida bakin ciki da takaici zuciyarta wani zafi takeyi d'an takaici da bakin ciki wani haushin mutan gidanne duk ya kamata haka dai ta wuni cikin kunci wanan ranan. </p><p><br /></p><p> Kwanan su Fatty 3 suka koma Abuja shipping sosai Muty yayi yakawo gidansu Fatty taji dad'in karan da Musty yayi mata rakuma ji dadin zuwanta d'an sosai Affrah tabata shawara takumayi alkawarin tayata da addu'a. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yau kwanan Daddy 5 kenan da faruwan wanan lamari koda yaushe Daddy cikin tunanin inda kudi zasu fitoh yakee, yanzo ma zaune yake a parlor yana nunani, Suleiman ne yashigo sai da ya gaida Daddy sanan yache" Daddy Please ka rage damuwanan haka, Allah na sane damu"</p><p><br /></p><p>Ajiyan zuciya Daddy ya sauke kana yace" hakane, kasan dai yau saura 3weeks lokacin da banki ya dinbanrmin ya cika ko? "</p><p><br /></p><p>"Ehh nasani Daddy"</p><p><br /></p><p>"Yanzo abinda nakeso da kai akwashe duk motocin gidanan banda naka a saidasu sanan ina da milin 6 da alhaji Sunisi biyani bashi na duk sai a hada da shii"</p><p><br /></p><p>"Daddy aka saida Motocin gidan duka am sure zasu isa abiya abinki bashin su ai"</p><p><br /></p><p>"Hmmm Sulaiman Kenan ai inkaga kud'inan sunkai toh sai dai asaida gidanan"</p><p><br /></p><p>Eyes Suleiman ya zaro kana yace" Gidanan kuma? Mai zai hana musai da motacin mubasu kudin Mocin kawai milin 6/kuma sai ka far wani business din? </p><p><br /></p><p>"A'a na fara wani? Bayan bani da tanbacin zan samu kud'in biyan ko bazan samu ba, kuma kai kanka kasan milin 6 bazaimin business ba"</p><p><br /></p><p>"Toh yanzo ya xa'ayi Daddy? "</p><p><br /></p><p>Ciki dakiya daddy yace" final decision shine zan sai da gidanan"</p><p><br /></p><p>"Daddy g.. i.. d.. a faa kace" Suleiman yayi maganan bakinsa na rawa</p><p><br /></p><p>" Ehh Suleiman gidanan zan siyar, nasan zaiyi 70 million ko ma fii, tinda Baaban gida ne sosai kuma a G R A kaga na siyar cikon kikon 30 milion kawai zanyi, shikuma in aka saida motacin nasan milin 30 zasu fitoh 6milion dinan da ke gida kuwa sai musamu wani gidan da shii ko hayane a marafa, yanxo kaje gidan Hamisu ka fadama shi komai nasan shi zaiyi komai" yana gama fadan haka ya jingina da kujera isanshi rufe</p><p><br /></p><p>"Daddy amm.. " bai karasa ba Daddy ya katse shi" Na riga na dad'e na amsan k'adda mai kyau da mara kyau, haka Allah yaso kuma haka Allah ya tsara kuma Alhmdulillahi nagode mashi sosai dan nafi mutane dubu a duniya so kai ma ina soka *YADDA DA K'ADDARA MAI KYAU DA MARA KTAU* da ai bamu kai haka ba, Allah ya buda mana sai yanzo muce zamuyi mai butulci? Ai ko dad'in jin babu so baso kace komai sai Addu'an Allah sa hakan ne alkhari"</p><p><br /></p><p>"Shiken Daddy Allah sa hakanne Alkhari yakuma zaba mana abinda yafi zama alkhari"</p><p><br /></p><p>"Yauwa tashi kaje Allah ma albarka"</p><p><br /></p><p>"Ameen Daddy"</p><p><br /></p><p>"Yauwa inkaje ka gaidashii"</p><p><br /></p><p>"Toh zaijii" nan Suleiman yabar parlorn Daddy ya bishi da ido yana tausayamai a hankali yace" kai kuma Hafiz in kaga kud'i basa shigowa zaka dawo da k'afarka".</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>7⃣1⃣_7⃣2⃣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*S*ulaiman na fita direct gidan Malam Hamisu yayi, bayan sun gaisa ne Suleiman ya fad'a mai duk abinda Daddynsu yace sosai Malan Hamisu ya tausaya ma Daddy har yakejin dama ace yana da kud'i da bazai taba bari ya sai da gidan shii ba d'an Daddy mutum ne ya temake shi ta wajeje da dama toh Amma babu yanda ya iya sai dai ya tayashi da addu'a. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A gida kuwa Suleiman nafita Daddy yayi siden mommy, zaune ya sameta tana danna waya ganin shi yasa ta aje phone ne a jefenta sanan tace" lafiya dai alhaji? "</p><p><br /></p><p>"Lafiya lau, Alhandulillahi"</p><p><br /></p><p>"Toh naganka wani iri ne ai"</p><p><br /></p><p>"Hakane, game da bashin banki dasuke bina ne"</p><p><br /></p><p>"Ehhh" mommy tace tana gyara zama</p><p><br /></p><p>"Toh shine na yanke shawaran sayar da gidan hadda motoci ma"</p><p><br /></p><p>Zubur Mommy ta mik'e tana bin Daddy da wani irin kallo," bangane zaka siyar da gidan baa Shu'aibu"</p><p><br /></p><p>"Yanda kika fada toh hakanne gskiyan magana, gidan zan siyar d'an na biya su kud'in suu"</p><p><br /></p><p>"Amma ai bai kamata ka saida gidanan bah motoci kawai kasiyar a ya isa kabiya su kud'insuu"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Lallaima Bilki watoh kin manta ma adadin yawan kud'in kenan ko? Da har kike cewa kud'in motoci ya isa na biya kud'in"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin muryan kuka mommy tace "yanzo yakake so muyi kenan d'an gidan da muke tak'ama dashii xaka saida, wai zakasamu cikin masifa da bala'i"</p><p><br /></p><p>"Bashi dai Allah ne yabani ikon cinshii kuma sanan hadda goyan bayankii, daki ke zancan masifa kuwa ai da na mutu lokacin zakuga masifu, jarabu, har da jafa'i ma d'an yan banki basu da sauki, tinda Allah yasa daka suma ban k'arasa ba dole na sauke wanan bashin da ke kaina ko d'an gudun tashin hankalin da yarana zasu shiga in bana raye"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ehhhh amma gashi xaka jefa yaran naka cikin talauci da wahala bahh"</p><p><br /></p><p>"Ki fad'a duk abinda zaki fada gida dai nawa ne bana kowa ba, ni ne natara kud'ina na gina shii batare da temakon kowa ba, so duk mai san jin dad'i sai ya dage yanema, nayi masu mai wahalan tunda na basu good foundation"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Wallahi ka cucemu, ka cucemu" mommy tace tana kuka sosai</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Sai ki fara shiiri d'an yau za'afara nema mana sabon gida kuma ba abin mamaki bane kiga masu siyan gida sunzo dubawa anjima gobe ko anjima ma so sai kikasance cikin shii, inkuma baki iya zama duk d'aya nee kuma bance asanar ma Fatima ko Mamana bah" yana gama fadar haka ya wuce kamar bayi da matsala, mommy kam da kyar ta iya jan k'afafuwanta zuwa bedroom sabida nauyin da sukayi mataa, zubewa tayi a kan bed tana kuka bin hakk'i da gskia kuka takeyi sosai chan tace" ni Bilki na shiga uku sai danagama juyama mutane baya duk abubuwa suka fara faruwa danii? Ko d'an wulakancin da nakeyi ne? Dama su Azeezah sunyimin baki wai zan ganii koshine na fara gani yanzoo? Na shiga uwa ga kud'in y'an meeting da naci 350k ina zan samosuu? Wanan nake sa ran samu daka wajenshi yayi k'asa ga Sulaiman bai fara aiki baa ga Fatty ita kuma bata fita bare tamin transfer, Hafiz basan halin da yake ciki bama" wani kuka Mommy ta sake da ta tuno da tijaran y'an Meeting oga hajia Adama babu mutunci ba sani ba sabo ai duk sai taji sai da gida ma bai dameta ba yanzo inda zata samu kud'in hajia Adama kawai takeyi, dayan wayan ta tajawo dake kan bedside drawer tashiga dialing number Hafiz amma switch off, mommy ji tayi kaman ta kurma ihu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ko da Daddy ke sanar na Inna hukuncin da yanke na siyar da gida, kwantar mai da hankali tayi sosai gami da Addu'an Allah sa haka ne yafi zama alkhari ya kuma bashi ikon ansan k'addaran da hannu biyu, yabashi ikon ciye jarabawan Da Allah ya d'auro mai a k'arshi ta samai albarka sosai gami da k'ara tausasan zuciyan shii. </p><p><br /></p><p> Daddy yaji dad'i sosai yakuma jii sanyi cikin zuciyan shii, d'an sosai damuwar shii yarage a xuciyan shii yak'ara daukan ma kanshii alkawarin kyautata ma mahaifiyarshi har k'arshin rayuwan shii *Uwa mai dad'i, Allah ka k'ara karemana iyayenmu,ka tsare mana su, yaa Allah ka saka masu da mafificin Alkhari Allah kabamu ikon yimasu biyyah da kyauta tamasu har k'arshin rayuwanmu, yakuma sa Aljanna ce makoma AMEEN*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Inna taso komawa katsina amma sam Daddy yak'i yadda dole ta zauna ba d'an taso bah. </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Cikin sata d'aya Hamisu ya nema masu wani gida haya a Marafa 4bedrooms ne da babban parlor sai B. Q yakuma kawo masu siyan gidan, anyi ciniki angama komai yanzo nan da kwana 4 ko biyar zasu bar gidan.75 million aka siya gidan, sai motoci uku da aka siyar 100 million chiff na banki suka fitoh, babu bata lokaci aka kaima banki kudinsu suna ta godia.washe gari kuma sukayi parking a sabon gidansu da ke marafa Mommy sai kwashe baki takeyi Inna ta lura da ita, Inna na mamakin halin Mommy na rainuwa da girman kai uwa uba bakin ciki da hassada,</p><p><br /></p><p> Mai daidacin Parlor ne, sai bedroom, cikin bedroom din da toilet a ciki sai k'ofa,na Daddy kenan inkafitoh da ka nan wani parlorn babba babu Laifi sai d'an corridor sanan bedrooms guda uku kowanne da toilet a ciki sai kitchen da chan k'arshin parlor banyan kawuce wani corridor shima, mommy ce ta dauka wanda yayi nesa k'adan da guda biyun sai Inna da Aunty Xulaiha suka dauki daya sai dayan Afifah da Salamatu(sauran yan aikin kuwa duk an sallamesu) tsaf Aunty xulaiha da mutanan Inna Su maman Ishaq da mom Fauxy suka shirya gida aikuwa sosai yayi kyau B. Q kuwa bedrooms ne guda uku sai toilet a waje sai kicin na tsakar gida, gida dai yayi kyau masha Allah amma Mommy sai kushewa takeyi wai gida a matse suna jinta duk sukayi banza da ita. Sai maman Ishaq suka taya anti zulaiha girkin dare kana sukayi masu sallama sukawuce Inna nata godia gami da samasu albarka. </p><p><br /></p><p>Duk wanan abu da aketayi Afrah batada labari kuma duk tana waya da y'an gidan amma basu fada mata ba Afifah ma duk surutunta bata fadamata ba. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Afrah ce cikin gown na atanpa tayi kyau sosai, skin d'inta kawai zaka kalla kasan tana cikin kwanciyan hankali kuma tana samun kula bana wasa ba, fitowa tayi daka *Freey delicious* bkry dinta kenan hannunta reke da kwalin cake, sai da ta aje cake din gaban mota sanan ta dawo ta zauna a mazaunin driver, phone dinta ta dauka number yaaSulaiman tashiga dialing ringing 2 ya dauka</p><p><br /></p><p>"Yadai sis" Suleiman yace daka chan mangaran</p><p><br /></p><p>"Lafiyalau, gani a hanya zankawo ma cake d'in yau zancika alkawari"</p><p><br /></p><p>"Am grateful, amma kinsan mun chanza gida"</p><p><br /></p><p>Eyes Afrah ta zaro sanan tace" chanxa gida? When? Baby bata fadamin bah"</p><p><br /></p><p>"Aikuwa an chanza" nan ya kwanta mata, sallama sukayi kana ta aje phone din taja motan tana mamakin canza gida babu ko sanarwa haka dai harta isa uguwan Inna ta kira aikuwa Afifah tayi picking " toh waje na ganki" Afrah nagama Fadan haka takashe wayan, daka nesa kadan ta hanga Afifah k'ara sawatayina bakin gate din gidan tayi parking ta fitoh hugging dinta Afifah tayi tana cewa"i Miss u so much sweet sis"</p><p><br /></p><p>"Dallah sakeni shine ko kifadamin kow"</p><p><br /></p><p>"Am so sorry sweet sis, wlhy Daddy ne yachai kar nafada" tayi maganan kaman zatayi kuka</p><p><br /></p><p>"Najii zagaya ki daukan ma yaa Suleiman cake dinsa"</p><p><br /></p><p>"Nawa fa anty Afrah? "Afifah tace nana zagayawa gaban motan</p><p><br /></p><p>"Next time, kee sai zakiyi birthday ma"</p><p><br /></p><p>"Kai aunty Affrah saura fa 5 months"</p><p><br /></p><p>"Nasani ai kaman yau ne" Tayi maganan daidai da suke shigowa parlor </p><p><br /></p><p>D'akin Inna Afifah ta jata</p><p><br /></p><p>"Lalelale da Amaryan Abdulnasir" Inna tace tana washe baki</p><p><br /></p><p>"Ni barni kun chanza gida ko musa ni"Afrah tace</p><p><br /></p><p>"Ohhh na zakima lalata ja'ira sai kije kisamu ubanki shiyace kar a fada maku ai"</p><p><br /></p><p>"Au Allah sarki Daddynmu"</p><p><br /></p><p>"Auu daa nii za'ayima diban albarka kenan ni da aka raina koo? "</p><p><br /></p><p>"Hmmmm ni bari naje na gaida Mommy "Afrah tace tana mik'ewa tsaye</p><p><br /></p><p>"Mommy batanan faa"Afifah dake lasan icing tace</p><p><br /></p><p>"Inna wai meyasa aka tashi a chan gidan ne? " Afrah tace tana kallan Inna</p><p><br /></p><p>"Kee jeki kai wanan abun cikin" Inna tace ma Afifah, nan ko ta dauki cake din ta fita, tana fita Inna ta sanar da Afrah komai sosai Afrah ta sausaya ma Dad dinsu hadda kukan ta </p><p><br /></p><p>"Ke dallah bakisan kaddara bane? "</p><p><br /></p><p>"Nasani Inna"</p><p><br /></p><p>"Toh hakuri zakiyi kuma Daddyn naku addu'a haka Allah yayi ai godia zamuyi ma Allah inda yanzo kuma ya mutu fa ai tashin hankalin da zamushiga sai yafi wanan ke kanki kinsani gana rasuwa gakuma tijaran yan banki"</p><p><br /></p><p>"Hakane Innah"</p><p><br /></p><p>"Yauwa ko kefa? Addu'a shine kawai abinyi"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Insha Allah zamu k'ara kan wanda mukeyi, bari naje kawai tunda Daddyn ma yayi tafiya"</p><p><br /></p><p>"Tun yanzo? "</p><p><br /></p><p>"Ehh Inna bari nake kawai"</p><p><br /></p><p>"MAdallah ki gaida angon naki"</p><p><br /></p><p>"Toh zaijii" nan Afrah ta tashi tawuce, hanyan kicin suka hadu da Afifah tace mata gobe insha Allah zata dawo. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Afrah na shiga Mota ATM tayi, kud'i masu yawan gske tacira sanan tawuce wani super market, shopping sosai Afrah tayi tundaka kan kayan abinci da kayan da duk tasan Daddy na siya da wanda Mommy keso da Afifah duk sai da tasiya haka aka cika mota dadi tarinkaji yau zatasa Daddy farin ciki. </p><p><br /></p><p> Sai 5:30 ta dawo gidan nasu, har cikin gida tayi parking nan ta kwala ma salamatu da Afifah kira suka fara firfitoh da kayan, Afifah nata murna hadda rawa haka Inna ma, sai da wani mai gidan makwabtan su yatayasu shiga da kayan dan bazasu iya bah, ana gama sauke kayayyakin Affrah taja mota tayi gidanta, Inna dai sai albarka take samata. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ana kan shiga da kayayyakin ne Mommy ta shigo gidan, bin kayan takeyi da Ido shopping ne taga ba na wasa ba, tanbayan kanta tayi"ina Suleiman yasamu kud'i haka? " </p><p><br /></p><p> Afifah ce ta katse mata tunani da cewa"mommy ki ga shopping dinda aunty Affrah tayi?"</p><p><br /></p><p>"Afrah kuma"Mommy tace tana kallon kayan da kyau</p><p><br /></p><p>"Ehh mommy bai dad'e da tawuce bama"</p><p><br /></p><p>Shuru Mommy tayi bata ce komai bah, mamaki irin shopping din takeyi, wai Afrah, Ina tasamu kud'i haka? Ta tanbaye kanta, ohoo _biebie dee tace_haka har ta isa bedroom dintaa, xama tayi bakin bed babu ehhh babu a'a chan ta dauko phone dinta a cikin jaka, number Hafiz tayi dialing buh still switch off tsaki tayi sanan tashiga dialing Number Fatty har yagama ringing batayi picking ba wani wawan tsaki Mommy takuma ja gami da wugar da phone din, chan taji yana ringing kaman baza ta dauka ba chan kuma ta tashi ta dauka phone din ganin Fatty ne yasa tayi picking da sauri</p><p><br /></p><p>Gaishe ta Fatty tayi Mommy ta amsa cikin sanyi Murya</p><p><br /></p><p>"Mommy ta muryan ki haka? "</p><p><br /></p><p>Nan Mommy ta kwashe komai ta sanar da Ita hadda shopping dinda Afrah tayi yanzo, sauke nunfashi Fatty tayi kana tace"Allah sa hakane mafi alkhari, Afrah ai dama bata rowa"</p><p><br /></p><p>"Hmmmmmm Fatima, Ni yanzo problem Dina kud'in hajia Adama ne kawai duk da nasan akwai bashin Mutane a raina amma nata duk yafi damuna" </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Yanzo yakike so ayii Mommy? "</p><p><br /></p><p>"Kud'i nakeso Fatima"</p><p><br /></p><p>"Mommy gskia tawaje na babu d'an yanzo ya nena bani kud'i na wajena kuma baifi 30k"</p><p><br /></p><p>"Toh ki turomin 30k din"</p><p><br /></p><p>"Toh Mommy sai ki jira sai randa Allah yasa na fita"</p><p><br /></p><p>"Bangane ba sai ki fitah"</p><p><br /></p><p>"Ehh mana, mommy toh ki tanbaya Afrah mana Am sure zata baki ko nawa kike so inhar tana da shii" kat Mommy ta kashe wayan zuciyan na zafi, ina ta ina zata fara tan bayan Afrah kudi? Zama ta ina makuwa? Tagumi Mommy tasa tama rasa abinyi.</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 75-56_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_this page is for sweetheart A'ISHA A MOH'D(K'arshin wahala) thank you so much for the love and support may Allah guide, bless n protect you always n forever Ana mugun tare_🤝🏻💯💖❤😁</p><p><br /></p><p> _gaisuwa mai yawan gske masoyana, thank you all Allah barmu tare har gidan Dadi Aljannah AMEEN_👏🏻👏🏻👏🏻</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ya labarin Hafiz? </p><p><br /></p><p> Hafiz dai a koda Daddy ya chanza mai school a turkey ba natsuwa yayi bah, baya zuwa sai yaga dama kasancewa karatun k'asar akwai wahala sosai shiyasa shidai gashinan bayyi gaba bah bayyi baya yanan inda yake dakashii har wasu friends dinshi</p><p> Tare da taimakin wasu friends dinsa y'an Nigeria suka cigaba da danfaran mutane ta online, dama wayanda ba y'an online ba, kud'i suke samu ba nawa sa ba, shiyasa duk wani kaya na celebrity Hafiz na sakawa phone kowa Saide ba'ayi lunchin dinshi ba da anyi zaysiya, dama kanshii kawai ya sani baydamu da kowa bah shiyasa ma y'an gida duk basu sani bah, bashi da complaining da requesting kudad'e duk uban kudin da yake samu baya is an shii, </p><p> Kulin cikin dan faran mutane suke, kodawani lokaci suna kan computer kawai d'an danfara da cuta(Allah karemu) ga shaye shaye sunayi duk da dai Hafiz ba sosai yakeyi ba amma yana tabawa, suna cikin wanan hakin d'aya daka cikin abokinsu Aliiii ya samu masu wani amshakin mai kud'i a online wanda dan faranshi yazamemasu masifa da bala'i dakuma danasanii babba, d'an ko wanan Alhaji baiyi da wasaba sai da yasa amai bincike sosai kansu babu zato babu tsanmani hukuman chan sukayi ram dasuu, kuma mutumin da suka danfara yace shi bayaso a cisu tare ko iyayensuu su fanshesu kawai yanasu ne a yankemasu hukunci a kullesu had sukoyi hankali, sosai suka shiga tashin hankali, nan duk aka amshe duk wani abu dasuka mallaka kana akayi da su prison sai bayan 4 months za'a fiddo suu.... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yau Wednesday Gidan Shuru Sulaiman har yanzo baydawo ba, Afifah tana gidanan Afrah daka chan ake kaita school,Salamatu nata aikace aikacenta Inna da aunty Zulaiha suna parlor suna kallan Sunna TV, Mommy ce tayi sallama duk suka amsa mata gaishesu tayi Inna ta amsa tana yin kai sama d'an talura kwana biyu wasu chaji take gani tare da ita dayake mommy bata gabanta shiyasa ko bi takanta Inna bata yii ba, AntyZulaiha ma mamakin chanxawa mommy yakeyi d'an Dai Mommy bata zama cikin suu, chan Inna tace" maza jeki cikin d'aki ki daukomin maganin ciwan k'afanan" Inna tacema Anty Zulaiha </p><p><br /></p><p>"Ahh Inna inada ko wani magani daka Niger aka amsomin shii, na ciwan k'afa ne bari na dauko maki" Mommy tace ta kokarin tashi</p><p><br /></p><p>"Oo oo, barshi kawai nafi gane kan nawa, ke maza daukomin" Inna tace tana bai da hankalinta kan tafsir in marigayi shirk JA'afar Adam kaman batman Allah yayi ruwan Mommy ba har Aunty Zulaiha tadawo tashiga shafema Inna Kafa da maganan, tafsir ne yakeyi kan irin Iyayen da kerike yaran da banasu ba, sai surika nuna bambanci da sanka da isgilin ai yaran da banasu ba ba isah yazama komai ba sai Wanda su suka haifa har yake bada misali da wani bawan Allah yanda marikiyanshii da yaranta suka rainashii da kyar yayi karatu a wahale yake, yaranta ne kawai kejin dadi suke kuma karatu a makaranta mai kyau a karshe yace ynzo haka shii Wanda suka raina din Yakuma tashi a wahale shine ya dau nauyinsu gabaki d'aya dan yaran nata dasuka samu gatan a sankarce suka tashi babu karatun kirki dasukayi shii wanda akeganan ba komai bane shine ya tallafi yaruwarsu gaba dd'aya sukuma datake ganan sune aishe basu bane, ai Inna wani kabbara tayi"Allah Akbar Allah mai girma watou *D'AN HAKKIN DA KARAI NA*shine zai tsolema ido, wayace masu anayi da Allah? Wanan ai yima Allah katsalandan ne kuma kaso naka duniya ta k'ishi kaki naka kuma Duniya ta soshii inji malan bahaushe"Inna ta karasa maganan taba d'an murmushii</p><p><br /></p><p>"Wanan Haka yake Inna Allah sa dai mudacee yabamu ikon zama da kowa tsakani da Allah kuma mubi yaran kowa da fatan alkhari bada mugun nufi bah"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ameen Ameen Zulai, Ameen kema Allah kawo miji na gari"</p><p><br /></p><p>Shuru Aunty Zulaiha tayi amma ta amsa a xuciya</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ameen Mommy tace a hankali, jitake kaman d'an Inna akayi tafsir Din dan duk wanan mugun hali ta ne, ga habaicin da Inna taitayi tasan da ita yakeyi, gashinan tunba aje ko ina Ba tafara ganin abinta, Allah kadai yasan irin burin da taci kan y'aran ta sai gashi dayake Allah Allah gashi yana nuna mata komai dalla Dallah, Sulaiman ma tasan mugun hali ta ne yajamai haryanxo bai samu aiki ba, Hafiz babu labarinsa rayuwan aure mai dad'i 💯Fatty bata sameshii ba, wanda takema mugun Fata itace tasamu kwanciyan💯k'aruwan Arxiki💯 da cigaba komai da komai tasamu samu, Abdull ma k'iri k'iri ta hana afita dashi karatu gashi har zaikama d'annata datama gata batasan babin dayake ciki ba, wasu hawaye ne masu zafi suka zubo mata d'an gskia sosai wa'azin yabi jinin jikinta wanda ta manta one last rabonta da jin tafsir sai yau, goge hawayen tayi da sauri gami da mik'ewa</p><p><br /></p><p>"Innah bari na d'an shiga ciki" Mommy tace</p><p><br /></p><p>"Madallah "Inna tace batare da ta Kalle ta ba.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mommy na shiga bedroom dinta zubewa tayi kan bed ta rinka Rusa kuka jitake kaman dan ita akai tafsir din nadama ne fal zuciyanta amma girman kai irin nata yahanata neman gafara, sai datayi mai isarta tashiga toilet ta wanko face dinta bayan tafitoh daka toilet kwanciyan tayi tana sauka ajiyan zuciya aikuwa babu dadewa bacci yayi gaba da ita, ta dad'e tana bacci sai 2 dai dai ta tashii, toilet dashiga ta dauro alwala tafito, sallaya ta shinfida ta tada sallah, ta dade sosai tana addu'a cikin sujjada kan Allah sa su Afrah suyafe mata kuma Allah bayyanar da Hafiz kafin ta idar tana zaune tana lazimi phone dinta yashiga ringing tashi tayi ta dauko ganin mai kiran yasa taji wani faduwar gaba daurewa tayi ta sallama cikin sanyin murya daka d'an bangaran aka amsa kana tace " Hajiya najiki shuru ne kinsan cikin satinan mukayi da ke, kuma banji wani bayani ba"Hajia Adama tace</p><p><br /></p><p>"Wallahi ina sane Hajia akwai wasu kudin da nake jira ne, dan Allah kikaramin lokaci"</p><p><br /></p><p>"Hehehehehe lallai Hajia Bilki innaga kin manta k'aidar mu kenan ko? Dakike cewa na k'ara lokaci, bayan tun last month yakamata ki bata amma sabida kece yasa nadaga k'afa sai ynzo kichai nakuma dagawa impossible kenan, dokarmu nan kaman yanda kika sani inka kasa biya kotuce zatashiga tsakani ko hukuma kinsan dai nii meting dina babu fitina cikinsa yanda kikaci kudi dolene kiyi kashin saa, ki saurari xuwani Nida su Hannatuu gobe ko jibi, inkuma kudin sunqi samuwa sai mu matsa gaba watou kotu" Tana gaman bayanan ta kashe phone din, mommy ji tayi kaman ta kurma ihu dan tashin hankali, kallan bedroom din tashiga yii gami da bude drawers din dakin koxata samu wani k'addaran amma duk babu duk tagama saidasu daxatabi ya bashii bata taba tunanin rayuwa zay chanza masu bah sai gashii duk wani fariya da tak'ama datakeyi yazama na banxa da hoofii da iska tan bayan kanta tashiga yii wai ya aiketa daukan rayuwan k'ara ta kasa ajiye kanta inda Allah ya ajetaa? Ta wukakanta d'anginta da yan uwanta na jini dan kawai basuda kudi ta manta Asalinta da kuma tushinta ta manta wacece ita da har tai ta wulakanta mutane tana isgilancii, yanzo wajen wa zata neman kudi? Wama zaibata cikin yan uwa? Bayan duk tagama yimasu tijara, gashii mijinnata datake tinkawo dashii baida Sulaiman kuma tashan ba Aiki yakeba bare yasamu 350k itakuma baza ta iya tanbayan Afrah ko mijinta ba dawani idoma zatakallesu? Ta inama zata fara? Wanan ranan mommy tayi shii cikin tashin hankali ko da Daddy ya dawo ya ganta wani iri tanbatan yayi amma tace babu komai tasan kota fadamai ba kudin zata samu ba wajenshii, kilama saidai yayi mata fad'a ita kuma mafita kawai take nema yanzo. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kwana biyunan duk Mommy tayi shi cikin matsanancin Tashin hankali, duk wanda ya ganta sai yaga alama amma ko ka tanbaya zatace babu komai, ko Sulaiman yakira ma inya tanbayeta zatacemai babu komai d'an tasan baida su, Fatty takuma tasan damuwan Mommy amma batada kudin kuma takasa fadama Afrah ma dan itama kunyan takejii</p><p> Yau Saturday Afrah daka Afifah sunzo gidan tinda sukaje suka gaida Mommy dake bedroom suka dawo parlor sunata hira, Afitah sai juba takeyi Afrah kam tana zaune a k'asa ga fruit a gabanta sanan da su ice cream da sauran kayan kwadayi tasa a gaba tana shas ta basu kabari, sallamn wasu mata uku ne suka katsemasu hira, d'agowa dukkansu sukayi gami da amsa sallaman,gaishe su duk sukayi kana suka tanbaya tanbaya ko Mommy nan " ehh tanan, baby jeki kaisu wajen Mommy "Afrah tace tana dan smiling </p><p><br /></p><p>"Toh aunty" Afifah ta shi sukabi bayanta</p><p><br /></p><p>Ashe tun shigowansu gidan Mommy taji amma fargaba da tsoro ya hanata fitowa, tanan zaune bakin bed suka shiga" Mommy ka bak'i" Afifah tace tana juyawa</p><p><br /></p><p>"Jekikawo masu wani abu" Mommy tace a daburce</p><p><br /></p><p>"A'a Baby basai kinkawo mana komao ba" wata tace wanda nake tunanin itace Hajiya Adama, aiko ko second 1 Afifah bata k'ara ba tayi gaba abinta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Xama sukayi a 2sitter dinsa ke bedroom din suna kallan Mommy Hajiya Hannatu tace" toh madam ashe haka Allah ya maidaku? *Karayan Arziki* zakice kunsamu ba wai kitsa mana nuk'unuku ba" ta karasa maganan tana kallan bedroom din da kyau </p><p><br /></p><p>"A'a Hajiya kuyi abinda ya kawoku kawai basai kuncima iyalina mutunci ba"Mommy tace</p><p><br /></p><p>"Hajiya Maryam tace". Please kuyi abinda yakawo mu"tayi maganan tana yatsina fuska</p><p><br /></p><p>"Toh Bilki kawo kud'ada den mutane" hajiya Adama tace ta mik'o hannu</p><p><br /></p><p>Shuru Mommy tayi coz batada bakin bayani, ai suna ganin haka sukasan babu kudi kwanan Masifa da bala'i gami da tijara suka shiga saukewa</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> A parlor kam tun suna jin magana da fada kadan kadan har sukaji abin yayi yawa Daddy ne yafito daka d'akin shii dan yaji hayaniyar tayi yawa, ganinsu duk yayi suna k'okarin karasawa bedroom din Afrah da Afifah ne gaba su Inna na baya shima Daddy bayansu yabi</p><p> Dai dai lokacin da suke isa bakin k'ofan ne Hajia Adama kecewa" wlhy kan kudinan sai munshiga kotu, zakiga tijara kuma kudi dole ki biya shii makaryaciya"</p><p><br /></p><p>Kaman daka sama dukaji Afrah nacewa"ba ku isah kutijara kowa bah Wallahi, ko nawa ne kud'in naku za'abiya ku..."</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 73-34_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_am so sorry sweethearts, kunjini shuru 2days, by God willing zakuna jina always ynzo, thank you so much for d love, care n support I love you all with all my heart_ 💞 ❤❣💋💖</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*H* aka Mommy tai ta tunani ynda zata samu kudin amma ta rasa, hakura wai tayi ta barma Allah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Koda Daddy yadawo yaga uban shopping da Afrah tayi sosai yaji dadi gami da saka mata albarka, yayi farin ciki sosai wanda har yakasa boyewa, bedroom din mommy yayi bayan yadawo daka masjid, samunta yayi ta idar da Sallah tana nike hijab, zama yayi a 1 sitter kallanshii mommy tayi kana tace "lafiya dai" tayi magana tana zama bakin fado</p><p><br /></p><p>"Lfyalau, Alhamdulillahi"</p><p><br /></p><p>"Toh hakan mukeso"</p><p><br /></p><p>"Naje wajen alhaji muntari ne kan maganan d'an business dinne kinsan zama haka bazai yuwu ba"</p><p><br /></p><p>"Hakane "</p><p><br /></p><p>"Naga shopping Mamana tayi naji dad'i sosai Allah ya masu albarka dukkansu"</p><p><br /></p><p>"Aikuwa tayi shopping fa basu chan, wai kai ma baka samun Hafiz a waya KO kuwa ni kadai ce bansamun sa? "</p><p><br /></p><p>"Hmmm nima bansamu, Suleiman baya samu ranan ma Abdull yakirani yakemin complain baya samu shima"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah sa dai lfiya d'an kasan fararan fatanan sai addu'a"</p><p><br /></p><p>"Hmmm Hafiz kenan,lfyanshii lau, inyaji bayajin alert nan da 2 months ko 3 zaidawo da k'afarshii"</p><p><br /></p><p>"Haba alhaji ai baikama ta kace haka bah"</p><p><br /></p><p>"Tohh ya ya kamata nace? " daddy yace yana zuba mata idanu</p><p><br /></p><p>"Kamata yayi ko kai ko Suleiman wani yayi bincike a kan lamari ba wai a zuba idanu ba"</p><p><br /></p><p>"Tohh ai Kama zaki iya binciken inni banyi ba, ke sam ba'ayin maganan arziki dakee sai kin nemo wani matsalan" ya karasa magaban tana barin Dakin, takumi Mommy ta zuba d'an damuwa yafara mata yawa, Daddy kam Dakin Inna ya shiga yanan zaune Sulaiman ya shigo, nan sukaci abinci sanan Daddy yayi masu sai dasafe yawuce dakinshii, Sulaiman, Afifah da Anty Xulaiha ko suka shiga hira. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ko dawasa Afrah bata bada ma Abdulnaseer komai bah, kawai dai tace sun tashi a wanachan gidan amma bata warwaremai maganan bah. </p><p> Ta sauki alkharin taimaka ma Daddy da duk k'arfin taa takuma k'ara girmamashi d'an shine yabata good foundation har nazama haka,shiyasa takesan kyautata mashi har illa masha Allahu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Rayuwa nata tafiya, sosai AFRAH ke kesamun kula wajen dangin mijunta da nata d'angin ga so da kaunar da mijinta ke nuna mata,jitakeyi tafi kowace mace dace da miji na gari mai Santa kuma mai kaunartaa, shiyasa itama take iyaka kokari a kanshi ganin ta kyautatamai ta kuma so shii ta kaunaceshii kamar yanda shima yake kaunarta, mazan su abin sha'awa ne da birgewa komai nasu cikin tsata da gskia sukeyin shii, shiyasa suke kuli cikin farin ciki da</p><p> kwanciyan Hankali. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Fatty ma Alhmdulillahi Musty babu laifi ya gyaru d'an halinshii cikin kashi Dari 50 sun ragu, baya shaye2 da yawan dare dawasu sauran mugayen halinsa sai dai rashin hakuri da shegen bakin kishii ga zafin zuciya ga birkicewa amma Fatty a haka tayi murna sosai takuma k'ara godema Allah, zakuma taciga ba da addu'a har Allah ya shirya mata shii gaba d'aya</p><p> Sometimes Farty bata jin haushin Musty in yana mata wasu abubuwan gani yakeyi alhakin AFRAHne mugun fatan da taketa yimata ne Allah yasa ya kare kantaa, kuma bata taba regretting auran shii ba coz auranshi ne ya chanza rayuwanta, auran shi ne yasa tasan darajan d'an Adam, auran shine yasa yadena bin mutane da mugun nufi dakuma yimasu mugun fata, auran shine yasa tsaya waje d'aya yadena hange hange dakuma kai kanta inda Allah bai kaita bah, sosai life d'inta ya gyaru ta kuma chanza har ga Allah tana bin kowa da fatan alkhari, shiyasa bazata taba gajiya da</p><p> yimai addu'a bah har Allah ya shiryeshi( Allah sarki Fatima)</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Brkry na AFRAH sai godian Allah sosai akesamun alkharii a cikinsa, d'an brkry din yayi fice kowa Afreey delious d'an sosai suka iya snacks bana wasa ba. </p><p><br /></p><p> Shiyasa bata wasa takema iyayenta alkhari da kyautata masu koda yaushii kuma tada burin bud'e restaurant. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yaa Abdul yafara final exams shima sosai yake temaka Daddy d'an yaron Akwai neman na jai tin kan ya kai haka yake u'ar business shi da friends dinsa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Afrah ma sun fara exams na shiga 300lvl cikinta yayi girma babu laifii kuma cikin yayi mata kyau</p><p> Yaya Sulaiman kuma yaje Abuja yin wani interview a wani company na baban abokinshi, sai da yabama Daddy da Mommy kud'i kafin ya wuce amma mommy tarasa inda kudin sukayi sabida uban bashi dake kanta</p><p> Mommy sosai ta damu d'an Hajia Adama tafara mata waya kan kudin da taci bashi 30k din da Fatty ta bata ma wani bashin tabiya kuma ta kasa tan bayan Afrah d'an kunya takeji sosai, bama tasan ta inda zata fara ba, gashii Hafiz har yanzo shuru duk banyan nemanshii sunbi amma babu labari sheyasa suka duk'ufa da addu'a ba dare babu rana.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zaune take a parlor tasa tagumi tunanin inda zata samu kud'i kawai yakeyi, gashii kaman yimata baki duk wani kayan gold dinta ta saida kuma batasan inda kudin sukayi bah komai bai albarka awajenta, nanan zaune Afrah ta shigo parlon da sallama Mommy ta amsa cikin sanyi murya, zama Afrah tayi a hankalina sanan ta shiga gaida mommy, mommy ta amsa cikin sakin fuska amma muryanta sanyi k'alau</p><p><br /></p><p>"Wai Afrah zakije gida ki hutata bah kulin kina hanyan ko? Last week ma naji har katsina kukaje"</p><p><br /></p><p>Smiling Afrah tayi sanan tace"mommy wai meki damunki? naji muryanki wani iri"</p><p><br /></p><p>"Ohh ina maki magana kina tan bayanane ko? "</p><p><br /></p><p>"Ya hakuri Mommy ai bani ke driving ba yanzo ma driver yakawoni katsina kuma tare da Abulnaser mukaje"</p><p><br /></p><p>"Duk da haka kirika hutawa"</p><p><br /></p><p>"Toh Mommy, meke damunki mommy? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"BabU komai Afrah kawai yanayin rayuwa ne"</p><p><br /></p><p>"Toh bari bashiga wajen Inna"</p><p><br /></p><p>Toh Mommy tace gami da binta da idanu sai taji dama Afrah y'arta ce d'an gskia she's very loving and caring, kulan da take bata ko Farty bata mata kamanshii duk da itama tana k'okari yanzo</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_please kuyi hakuri da wanna, nayi typing yarinyata tayi deleting , kuma har read more 6_😰😰😰 _insha Allah zakujini gove_</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 77-78_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*K*aman daka sama sukaji muryan AFRAH nacewa" baku isah kutijara kowa bah wallah, ko nawane kudin naku za'abiya kuu yanzo ba sai anjima bah"Afrah tace tana kallansuu</p><p><br /></p><p> Wani kallan banza Hajia Adama tayi kana tachai" ai ban ganki da kudin ba da kikazo kina shirgarma uwarki makaryaciya"</p><p><br /></p><p>Wani irin tsawa AFRAH tayima hajia Adaman wanda basu tabasanin Afrah ta iya ba tace" kar kikuskura kik'ara zagin uwata inkuma kinqi jii wallahi wallahi wallahi zakiyi nadama walhy so bani account number yanzo nayi maki transfer" </p><p> Su Daddy da Inna na gane kan rikicin kowa ya kama gabanshii yana jimami halin Mommy</p><p><br /></p><p> Hajia Hannatuce ta karanto ma AFRAH account number din, kallansuu Afrah tayi kana tace nawane kud'in? "</p><p><br /></p><p>"350k nee, taci takuma kass... " </p><p><br /></p><p>Ban tan baya wani bayani ba kuma kudi kawai nace" tayi maganan tana watsamasu harara, babu b'ata lokaci tayi masu transfer din kid'in su gami da madu warning mai kyau, binsu da ido Afrah tayi har suka fice. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mommy kam tinda taji muryan AFRAH nacewa zata biya kud'i wani zafafan hawaye ne suke gangaro mata, wani danasanii ne da NADAMA duk suka k'ara shigarta</p><p>Kuka tashiga yii nil hak'i da gskia kuka takeyi sosai gami dacewa" Allah na tuba Allah na tuba Allah ka yafenii" tana f'ada ne cikin muryan kuka sosai, Tanan zaune tana Aikin kuka Daddy ya shiga bedroom din, kallanta tayi sosai kana yace"dama kibar kukanan d'an bayda anfani yau kin yadda da maganata ko? Ba'ayima Allah shisshigi sam, san kai, banbanci duk basuda anfani "</p><p><br /></p><p>"Wlhy nayi nadama nakumayi danasani, wallhy Naduba Kaima ksyafeni, kayafeni d'an girman Allah kuma" </p><p><br /></p><p>"Bubu komai Bilki dama addu'an da mukaitayi kenan AFRAH da ABDULL kuwa karkidamu d'an basuda rik'o sam kinan a matsayin uwarsu har yanzu baki chanza ba" haka daddy yaita lallashin Mommy gami da k'arayima nasiha mai ratsa jiki kana yabar bedroom innata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Afrah kam su hajia Adama nawucewa babu dadewa ita da Afifah suka wuce sunje yima Mommy sallama suka tarar tana sallah sai suka wuce. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mommy bata Fitoh bah sai 5:21 a parlor taga Inna tana kallan tafsir, zama tayi a hankali kana tace" Inna d'an Allah atayani yima Afrah godia d'an ta fitar dani kunya ba k'arami ba" tayi maganan cikin sanyin murya</p><p><br /></p><p> Inna dama abinda takejira kenan, ranan da taita add'an Allah sa tana raye zaifaru, Allah kuwa ya amsa mata tinda gashii tagani, volume din TV tarage gami da gyaran Murya sanan tace" ai Bilki ni dana ranan da naita jira kenan gashi kuma Allah ya nunamin, inga ikon Allah KO? Kingani ko? Kin zagesu, kin hantaresu, kin masu mugun fata, kin masu bakin ciki da hassada kinyi masu, kinyi masu, kinyi masu Bilki sai gashii a cikin su dinne suka taimakeki yau, d'an dai inbatan Allah da kuma AFRAH wlhy muna kallo zasuyi gaba dake dan bamuda kudin ke kanki kinsani" Inna ta k'arasa maganan tana share y'an kwalla</p><p><br /></p><p>Cikin muryan kuka Mommy tace" nasani Inna wallahi nayi nadama, nayi nadaman da Nakasa h'ada idanu da Afrah, Inna kina da ikon yimin komai a wajenan d'an a irin mugun halina na chanchanta kowani hukunci, amma bazan taba gajiya da cewa kuyafe min ba, kuyafemin d'an Allah da daranan manzon Allah" tak'arasa maganan cikin kuka</p><p><br /></p><p>Jikin Inna ne yayi sanyi sosai, nasiha tariga yima mommy sosai mai ratsa jiki Mommy na ta hawaye" kar kisamu Bilki Indai su Abdul ne baduda matsala sam ninasan basu rikeki a zuciya bah, da sun rikeki Afrah baxa ta taba iya biya bashi baa, kar kidamu Allah yafemana gaba d'aya"</p><p><br /></p><p>"Nagode Inna Allah k'ara girma da tsawan rai mai anfani"</p><p><br /></p><p>"Ameen Allah k'ara shiryaku da yaran ku gaba daya Allah kuma ya bayyanar mana da Hafiz"</p><p><br /></p><p>"Ameen ya Allah " Mommy tace a hankali, ranan sai Mommy haka take wani iri _kai Mommy anyi nadama_🤣🤣💯 </p><p> Da dare takira Afrah a waya ta rinka samata albarka gami da godia amma Aftah tace babu godia tsakaninsu dan ita uwa ce a wajensu, ai mommy albarka taitasamata gami damasu addu'a gaba d'ayansu" wani hawaye ne ke xubima Mommy mamKin kyauwun halin Aftarh takeyi nakika tayi gadon arziki d'an halinsu daya da mahaifiyyarta Rabi'atu, tuno da irin rashin mutuncin da tama Rabi'atun tayi wani hawayenne yakuma gangarowa, alkawari ta daukanma kanta zata bi kowa ta nemi gafararsa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sai ran Mommy Sulaiman ya dawo gida, a company biyu yayi interview kuma yana sa ran samu aiki very soon da yaddan Allah. </p><p><br /></p><p> Mommy da kanta take fadama Sulaiman irin taimakon da Afrah tayi mata dakuma hakin arziki da Afrah keda shii</p><p><br /></p><p>"Alhmdulillahi "abinda Sulaiman yafRa cewa kenan kana ya daura dacewa" da in ina yaba kyawawan halin Afrah kina jin haushi na, gashinan kingani da idanuwanki, kuma nasha fad'amaki cewa ba d'an da kahaifa kawai zai taimakeka ba d'a a titima sai ya temakeka D'AN ka baima ba duk da ba'a fatan hakan, amma nuna sankai da bambamta yara tsakanin naka sam bai da anfani sai Allah yanunama iyakanka, tinda shi ke shirya komai kuma ya ke tsara komai yanda yaso in har kana cewa yaron da banaka ba bai isah yazama komai ba kaman kanama Allah kankanba ne, Allah bai san haka sam"</p><p><br /></p><p>"Hakane Sulaiman hakika da ina cikin dubu wanda Nakasa gane chaiwa D'A NAKOWA NE, nayi sankai nayi bambamci nabisu da mugun nufi da nuna su ba komai bah, ashe nice ba komai ba Sulaiman yarana ba komai ba, kana ganin Hafiz babu labarin sa, Faty zaman auran sai ah hankali kai da Afifah ne kawai baku dauki muguwar d'abi'a na bah, kai ma gashi har ynzo Aikin baisamu bah, Afifah kam bana tantama kanta d'an ita rainon Afrah ce"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A'a Mommy kar kichai haka, rashin samun aiki daka Allah ne badan komai ba, Fatty kuma insha komai zayyi normal Hafiz shima Da yaddan Allah zay bayyana". </p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Allah yasa, Allah yayi maka Albarka Allah yayi maku albarka ku duka"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ameen ameen Mommy Allah sa mudace"</p><p><br /></p><p>"Ameen Sulaiman ameen yaaa Allah "</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Abdul da Afrah sun k'are Exams Dinsu lafiya Alhmdulillahi, yadawo gida suna jiran fitowan result kafin sukuma fara Service, lafiyalau suke xaune a gidan sosai mommy ke kula da shii gani take kaman Hafiz shima sosai yake dawauniya da gidan coz yana D'an Business dinshi, Sulaiman kuwa haryanxo ba'a kirashi bah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sanda Abdulnasir yaji irin Abubuwan da Afrah keyi batare da tafada mai sosai ranshi ya baci" nii ban isah ki gayamin problem din ki ba ko? Sabida ni ba family inki bane ko? "</p><p><br /></p><p>"Nooo sweetheart, wallahi ba haka bane, kawai bansan daura ma dawaini yane, amma kayi hakuri mijina"tayi maganan tana hugging dinshi sosai</p><p><br /></p><p>Shima Hugging dinta yayi kamar zai maidata ciki kana yace" baby kintaba ganin inta yaron kirki ya Gaji da parents dinshii? "</p><p><br /></p><p>"Nooo sweetheart, am so sorry please"</p><p><br /></p><p>"Shikenan it's okay, buh kar kikuskura kisake"</p><p><br /></p><p>"I promise you love love"</p><p><br /></p><p>" yauwa babyna I love you"</p><p><br /></p><p>"I love you more sunshine "Afrah tace tana k'ara shigewa jikinshii. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Washegari baatare da sanan Afrah bah Abdulnaseer yayi sopping na tashin hankali da ban mamakii yakai gidan su Afrah,Inna, Daddy da Mommy sai Albarka sukesamai gami da masu Addu'a sanan kuma yama Afrah transfer din 350k dinta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_please kuyi hakuri da wanan kaina ke CIO_</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*page*7⃣9⃣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> *A*abinda Abdulnaser yayi sosai Afrah taji dad'i, ita kanta tasan tayi dace da miji na gari mai halin kirki kuma mai Santa da k'aunarta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Number Mami Mommy ta amsa wajen Inna d'an tanason tafara kiranta kafin taje katsina nan. </p><p><br /></p><p> Mami na zaune a parlornta banyan su Arfah da Fahad sun wuce islamiya, phone din tane yashiga ringing, bakuwan number tagani sai da yakusa katsewa sanan tayi picking amma batare datace komai baa, daka chan b'angaran kam Mami na Picking Mommy tayi sallama, Mami taso gane voice din, amma garin irin halin wanda take nunani yasa ta kawarda Mommyn ce</p><p><br /></p><p>"Rabi'atu kina lafiya? Ya gida da yarana dukka?"mommy tace a hankali</p><p><br /></p><p>"Lafiya lau Alhmdulillahi"</p><p><br /></p><p>"Masha Allah, Allah kara tsaremana su yakuma shirya mana su baki d'aya"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen yaaa Allah" Mami tace sai tayi shuru</p><p><br /></p><p>"Nasan kingane mai magana Rabi'atu sai dai kikasa yadda ko ni dince, nice kuwa Bilki mahaifiyar Sulaiman"</p><p><br /></p><p>"Alhmdulillahi "abinda Mami tace kenan</p><p><br /></p><p>"Hmm komai naki natse yake kanar y'arki AFRAH, hakika AFRAH tayi sa'an uwa tagari kamar yanda kema kikayi sa'an y'a tagari wanda kowa zaiyi alfahari da samun irinta"</p><p><br /></p><p>Shuru Mami tayi batace komai bah illa mamaki datakeyii </p><p><br /></p><p>"Dole Kiyi mamaki Rabi'atu d'an ni kaina nasan nadade ina binki da sharri am... "</p><p><br /></p><p>Mommy bata k'arasa bah Mami ta tsayar da ita"Wallhy Mommy bakimin komai ba, d'anni banda ba rike ki a raina bah"</p><p><br /></p><p>"Allahu Akbar Nasani, nasan haka zakice Rabi'atu amma d'an Allah ki yafemin dan Allah duk abinda nayi maki"</p><p><br /></p><p>"Wallahi nii tuni nayafe maki Allah ma yasani"</p><p><br /></p><p>D'an hawayene suka zoboma Mommy sharesu tayi kana tace" wallahi nayi nadana Rabi'atu nakumayi dana sani Wanda har nakejin kunya, mungun nufin da nataita bin wasu dashi da nuna su ba komai bane Ashe nice bakomai bah ga Hafiz tun tafiya karatu babu labarinsa"</p><p><br /></p><p>"A'a Mmn Sulaiman karkice haka wanan K'addarace daka Allah Amma Bawai d'an wani dalili ba, kar ma ki dangantashi da wanan, Hafiz kuma insha Allahu zaybaiyana ba da dadewa ba insha Allah, AFRAH tafadamin nasa a tayamu da Addu'a"</p><p><br /></p><p>"Allah sarki, nagode, nagode sosai Allah bar zuminci"</p><p><br /></p><p>"Ameen, Amma ai babu godia tsakaninmu dan D'AA NAKOWA NE barema Hafiz ai yaro nane"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nayi shuru amma d'an Allah kitayani yima AFRAH godia d'an tamin abun daako... "</p><p><br /></p><p>Tsayar da ita Mami tayi dacewa" ai AFRAH Y'AR ki ce babu godia tsakaninku sai dai albarka, kuma ni basai nasan tsakanin kubah, maganarku da ban namu ma da ban"</p><p><br /></p><p>"Toh nayi shuru yau nak'ara godema Allah, Da Allah yasa nagane gaskia gskia ne nakuma watsar da karya"</p><p><br /></p><p>"D'an ALLAH kibar maganganunan sun wuce, Allah tsaremu yakuma shirya mana zuriyya baki d'aya"</p><p><br /></p><p>"Amen amen yaa Rabbi, insha Allahu munan shigowa katsinan"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah kawoku lafiya, muna jiranku"</p><p><br /></p><p>"Bada dadewa zaku ganmu a gaidamin yarana"</p><p><br /></p><p>"Duk zasuji Agaidamin Alhaji da mutan gidan dukka"</p><p><br /></p><p>"Zasuji da yaddan Allah" nan kowa ya katse kiran yanamin wayan nashi da murmushi, Mami sosai taji dad'i d'an batasan fitinah tun bayanzo ba taso su shirya amma mommy ta k'i, yau da hakan ta faru sosai taji dad'i har ranta. </p><p><br /></p><p> Mommy ma dad'in taji sosai d,an sai taji kaman an ragemata nauyinda ke kantaa, yanzo y'an zariya ne problem inta d'an ko takirasu babu masu picking, Daddy ta fad'amawa yakumace cikin weekend d'an nan duk zasu je gaba d'ayansu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> Mommy dama duk tasanar ma Fatty duk wani abun alkhari da AFRAH tayi mata, natsuwa ne yak'ara shigarta sosai tayi da nasanin duk abinda tayi daa yanzo fatan alkhari kawai takebin kowa shii, every Monday n Thursday tana azumi sosai takema mijinta addu'a, iyayeta, yan uwanta dakuma ita kanta, alhamdulillahi ALLAH kam ya amsa d'an yanzo lafiya suke zaune da Musty sai dai fa har yanzo bayasan yawan fita da kuma bin k'awaye kuma yanada saurin fushi shiyasa takebin kayan ta a hankali, dan bayasan muso ko Yana magana kaima kayi yanada san girma sosai itadai Fatty haka takebinshi d'an Ance zama lfya yafi zama d'an sarki, Musty ya natsu yafara aiki a company din Uncle dinsa a nan abuja family shi nasan Fatty sosai d'an suna ganin sanadin auranta yasa yaronsu ya gyaru, kuma Farty na girmanasu sosai shiyasa Suma suke Santa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Zaune suke a parlor bayan sun kammala dinner dinsu, kwashe kayan Faty tayi gami da k'ara gyara wajen d'an yanzo Fatty tasaba da aiki, bayan ta gama dawowa Parlorn tayi ta zauna gami da daukan remote tana playing film din da take kallo wani series film ne na Philippines on till the end of my life, musty kam aikinshi yakeyi a laptop 💻 tanan zaune tana kallo sai kwallah takeyi sabida sausayi film din gareshi sosai tin musty bai dauki abin serious ba chan ya ganta sai share hawaye takeyi wasu hawayen na gangarowa, Tashi yayi daka inda yake zaune yakoma 2 sitter d'in da take, jawata yayi zuwa jikinshii kana a hankali yace" wat wrong with ma bby?" Yayi maganan yana kallanta</p><p><br /></p><p>"Nothing sweetheart"</p><p><br /></p><p>"Den what's make you cry hum? </p><p><br /></p><p>"I said nothing kawai film dinan tausayi wallah"</p><p><br /></p><p>"Mtsww yayi tsaki film kikema kuka? Lallai u ar not serious" Tashi yayi ya kashe TV in yadawo ya zauna, "Oga ki Tashi muje muyi bacci, coz gobe zamu kd"</p><p><br /></p><p>Tsashi zaune tayi da sauri sanan tace" kd? Sweetheart gobe Friday fa office fah? "</p><p><br /></p><p>"Nasa ai, if you ar not going good n fine, banasan magana"yana gama cewa haka yayi banyan bedroom dinshii, cikin sauri Farty ta tashi tayi bedroom dinta, wanka tayi shap shap tasa night gown dita gami da fesa turaroka masu kanshi tayi bedroom dinsa d'an tasan yayi fushi sai tayi lallashi sosai.. Lol🤣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> Washe gari 12 a kaduna tayima su Fatty,gidansu Musty na naduna suka fara zuwa sai 3 suka iso gidansu, har ciki Musty ya shiga ya gaida Inna, Daddy da mommy kana yace zaydawo da dare, hutun minti k'adan Faty tayi tashiga kiran AFRAH </p><p><br /></p><p>"Ai da kibarta gobe gidan zata wuni" cewar Mommy </p><p><br /></p><p>"A'a nidai mommy I Miss ha, kuma Kinga na manta bantanbaye Musty ya ajeni gidanta ba"</p><p><br /></p><p>"Daa hakan kikayi ai da yafii, yanzo ki kirashii ki tan bayeshii ko yayanku sai ya ajeki"</p><p><br /></p><p>"Mommy wallahi Musty bazai yadda bah, maybe ma ina cewa haka yaji haushi yace gobe na shirya muwuce"</p><p><br /></p><p>"Toh ALLAH kyauta, amma dakin barta ta huta gskia"</p><p><br /></p><p>"Ameen Mommy ai sirikin naki sai a slow, nidai bari nakira ai Abdulnaser baida problem" nanan tashiga k'iran AFRAH, Afrah dake zaune a parlor tana san ice cream tace "baby mikomin phone dina"</p><p><br /></p><p>"Laaa anty Faty ce" Afifah tace tana kokarin picking call din</p><p><br /></p><p>"Hello aunty yayane"Afifah tace tana daria </p><p><br /></p><p>"Kee dalla bata waya" Fatty tace</p><p><br /></p><p>"A'a ai batanan hira zamuyi, sun fita strolling da Yaa Abdulnaser"</p><p><br /></p><p>"Waye ya tafi strolling din? "AFRAH tace tana Dariya</p><p><br /></p><p>A Hans Free Afifah tasa phone din </p><p><br /></p><p>"Kibarni da shegiyar" Fatty tace tana Daria</p><p><br /></p><p>Dariya AFRAH dakuma yii"Autan ce shegiya? Wallahi babu ruwana" </p><p><br /></p><p>"Hmmm ni barni da wata auta chan, sis ina kd fa yanzo haka ina gida ma, ban tanbaye Musty ba har ya wuce ai danazo kuma sai dare zaidawo"</p><p><br /></p><p>"Don't worry gamunan zuwa" AFRAH na gama fadan haka tashe kiran, number sweetheart dinta tashiga dialing ringing 2 ya dauka" ma princess hw u? "</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Good sweetheartttt"</p><p><br /></p><p>"Aa ban yadda bah baby daka jin yanda kikace sweetheart dinan u need something"</p><p><br /></p><p>"Toh ni I wan to see u" tayi maganan a shagobe</p><p><br /></p><p>"Oky okay on ma way babe"</p><p><br /></p><p>"Je ki shirya baby" tace da Afifah, baifi 20mins ba ya iso gidan tana ganinshi tayi sauri ta tashi tayi hugging dinsa game da dacewa"I miss you sweetheart"</p><p><br /></p><p>Kallanta yayi sosai kana yace" really? "</p><p><br /></p><p>"Yes sweetheart"tayi maganan tana jan hannunsa zuwa bedroom dinsa " love love " Afrah ta kirashi cikin voice inta mai dadi</p><p><br /></p><p>"Yes baby"</p><p><br /></p><p>"Please zakayi dropping dinmu a gida Fatty ce tazo" tayi maganan kaman xatayi kuka</p><p><br /></p><p>"Noooo, ai nace baza kije ko ina bah dis week, kuma ai yau Friday"</p><p><br /></p><p>"Please sweetheart please wallahi I miss ha I wan to see ha, please" tayi maganan tana rik'e hannunshii</p><p><br /></p><p>"Ni fa Bawai banso kije bane kawai inaso ki huta ne, ita basai tazo ba"</p><p><br /></p><p>"Ai ni a huce nake, kuma bata fadama Musty zatazo nan bane shiyasa faa" ta karasa maganan tana kallanshii gami da turo baki" kuma har wani magani ma Inna tachai nazo na amsa yau, kawai van fada ma bane"</p><p><br /></p><p>"Hoooo baby shirya na kaiku"</p><p><br /></p><p>"Yeeeeeee, toh daukomin gown cikin kayana DA ke d'akin nan ina zuwa" tayi kasara maganan tana yin banyan toilet </p><p><br /></p><p>Bayan ta Fitoh Abdulnaser ne yatemaka mata tasa shirya tsaf a parlor suka tadda Afifah na jiransu, nan suka Fitoh Abdulnaseer ya kulle Gidan sanan suka nufi mota. </p><p><br /></p><p> Suna isa Afrah bata jira Abdulnaser yabude mata mota bah kamar yanda yasama tayi gaba cikin sauri shima cikin saurin yakashe motan yabi bayanta sai daria Afifa kemasu d'an ko a gida haka sukeyi taita daria ita kam. </p><p><br /></p><p>"Siss gani nazo"Afrah tace da KARAI</p><p><br /></p><p>Aguje Fatty ta tashi xatayi kan Afrah "ke ke baki da hankali ko, baki ganin ba ita kadai bace wai" mommy tace tana rike AFRAH </p><p><br /></p><p>"Ke kuma kita abu kamar wata Afifah" tace tana kallan Afrah </p><p><br /></p><p>"Wallahi Mommy haka takeyi ko a gida tanbaye Afifah kiji"Abdulnaser dake k'arasowa yace</p><p><br /></p><p>"Toh Allah shiryeki"</p><p><br /></p><p>Nan fatty ta ja hannuntaa suka shige ciki, nan Abdulnaser shiga gaida Mommy, cikin sakin fuska ta amsa tana tan bayanshi Ummie, yace duk lfya suke, "masha Allah ai munyi waya jia"</p><p><br /></p><p>"Ja'iri watou ko bakuda kawaici ko, sirikar zamani da d'an zamani" Inna tace tana kallan Abdulnaser </p><p><br /></p><p>"Ina yini Inna" </p><p><br /></p><p>"Ban amsawa mara kunya, ai duk ina jinku, ita kuma sirikar taka duk daya kuke"</p><p><br /></p><p>Daria kawai mommy da anty Zulaiha keyi Abdulnaser kam smiling kawai nakeyi</p><p><br /></p><p> Sai bayan Sallan isha Musty yadawo, anan babban parlor suka zauna suna ta hira bayan sun gama dinner, hira sukeyi gaba dayansu, Inna, Aunty Zulaiha, Fatty, Afrah, Afifah, Sulaiman, Abdul sai Musty DA Abdulnaser sunata hira gwanin sha'awa, kafin Daddy ya tashi Yake sanar dasu zuwansu zaria gobe insha Allah. </p><p><br /></p><p> Sai 10 na dare sukayimasu sallama kowa yayi gidansa, Faty da Musty ma sukawoce, Afifah kuma gida zata kwana sabida Afrah ta shiryo da wuri.</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>_page 80-83_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> *T*in 8 na safe su Abdulnaser suka fitoh gida, sai da suka fara biyawa ta gidansu suka gaida Abba da Ummie kana suka nufi gidansu AFRAH, su Afrah sun iso babu jimawa Fatty da Musty suka iso, su daddy, mommy da Sauran ma duk sun shirya sun gama komai, kulle gidan kawai sukayi gami da addu'a kowa ya shiga mota "Inna wani mota zaki shiga hum ?" Afifah tayi tanbayan a hankali tana kallan Innah</p><p><br /></p><p>"Haa ina ruwan kii, Nida keda jikoki gasu anan"</p><p><br /></p><p>"Left to you dama I gav something to give you ne, amma tinda baki shiga namu dats yur on cup of tea" Afifah nagama fadar haka tawuce fuuu ta nufi motan Yaa Abdulnaser </p><p><br /></p><p>"Yar arziki ba tsiya ke kika sani, yarinya sai shegen manyance sai kace wata uwar mata,ji wanan aiki? Sai lan kwasa hannaye da harshe takeyi wai dat noo tiiii, ina nasan abinda kikecewa tinda banyi boko ba"</p><p><br /></p><p>"Ahh Inna lafiya? Naga baki shiga motan bane"</p><p><br /></p><p>"Kai nii budemin na shiga d'an ba mutunci ne daku ba sai ka bode ma matar ka yanzo ta shige ni Inanan tsaye, nasan ku sarai"</p><p><br /></p><p>Smiling Musty yayi sanan yace"ahh haba dai Inna ai kema u ar special" yayi maganan yana bud'e mata motan</p><p><br /></p><p>"Kai nii banni dawani yare chan dama ynxo wanchan mai maganan kaman uwar mata tagama turanceni kaima kazo kanayimin"</p><p><br /></p><p>"Allah barmana ke kakus" Fatty dake gaban mota tace</p><p><br /></p><p>"Ni dan Allah ku rabu dani, kunanan kuna zance gasu chan su sun dau hanya"</p><p><br /></p><p>"Muma yanzo zamu dau tamu hanyan"Musty yace yana daria kadan</p><p><br /></p><p>"Toh Allah saukemu lfya"</p><p><br /></p><p>"Amren ameen"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p> Kowa yasan tafiya zuwa kaduna 2 zaria ba wani tafiya bace cikin yaddan Allah, dan wasu ko 1hr basayi hanyan zaria, Suma dai haura 1hr din sukayi kadan sabida basa gudu sam a hankali sukai ta tafiya har suka iso</p><p><br /></p><p> A wani k'ofar gida sukayi parking dake JUSHII anan zaria,sun fitoh kenan, wani k'anin mahaifin Mommy na kokarin fitowa daka cikin gida, cikin fara'a da girmamawa Daddy da sauran mazan da ke bayanshi suka sufeshii suna gaidaidashii, gaba da yansu suka shiga cikin gidan, amma inda su Mommy suka shiga daban inda su Daddy ma sukayi da ban, dan DA alama gidan family house ne mai dauke da sa-sa da ban da ban. </p><p> An basu tarba mai kyau masha Allah, sai fa da kyar marik'irar Mommy ta sauko daka fushin datayi d'an har kuka sai da tayii, su AFRAH ne sukai ta bata hakuri da Inna kafin ta hakura ta sauka, taita samasu albarka. </p><p><br /></p><p> Inna Safiya itace ta raini su mommy bayan rasuwan mahaifiyarsu, kanwan mamansu ce uwa daya uba daya,bayan rasuwan mahaifiyar Mommy ne akabashi kanuwarta safiya Kuma 'yaya maxa suke DA ita da mijin nata malan Sulaiman watou mahaifin su mommy kenan, Inna safiya tsakani da Allah ta rainesu batare da nuna sankai ko banbanci ba, har ta aurar da Mommy dan itace babba, da farko mommy na kokari a kansu amma daka baya ta bari tinda taga ba itace ta haifetaba, tadena masu komai takuma dena zuwa ma baki daya, sai Daddy in daddy yaje shii yake komai tare da masu alkhari mai yawan gske, tinda su Nana suka bama Inna Safiya labarin rashin mutuncin da Mommy yayi masu Inna Safiya tace surabu da ita ai duniyace, sukuma ta kara yimasu fada gami da nasiha mai shiga jinin jiki. </p><p><br /></p><p> *Duk wani wanda ake rik'eshii inhar da zuciya d'aya aka xauna da shii, babu banbanci ko sankai, tsangoma, aka daurashii a hanya mai kyau aka kawar da shii a hanya mara kyau, aka tsayamai tsayin daka kan karatunshii da dai duk wani alkhari toh yasani inhar ya juya masu baya ko yaqi yayi masu biyayyah wai dan vasune suka haifeshi ba toh inhar sukai fushii sai ya tab'ashii ko tsinemai sukayi sai ya tab'ashii, d'an haka gyara ko sharri akayima Kai kayi alkhari dan kafiso ko wajen Allah, Allah yasa mu dace ameen*</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> An sasanta komai su Nana da sauran k'anan Mommy duk sunzo anata raha, sai bayan la'asar suka dauki hanya kafin su wuce Abdulnaser ya sauke masu shatara na arziki da suka zubo a both batare da sanin kowa bah, Afrah ma 20k ta daura akai haka Musty 50k a ajiye masu, daddy, ya Suleiman da ya Abdul duk sunyi masu alkhari sai godia dai sa albarka kawai sukeyii. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mommy taji dadi sosai abinda Abdulnaser da AFRAH sukayi, yarda tak'arayi dan Afrah Yar baiwa ce, batada san Kai da banbanci Yan zaria da ba yan uwanta amma ta kyauta masu ita da mijinta, godema Allah tak'ayi da ya fargar da ita yafiddo ta daka bik'in duhuu, Nitsuwa yakara shiganta sosai, haka dai suka dawo lafiya cikin farin ciki. Mommy taji kaman ansaukemata babban dutse a Kai sai washe baki take tana jin Dadi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gidan AFRAH sukayi dan chan Fatty zata kwana, shi Kuma Musty ya wuce gidansu, ranan su Afrah ba suyi bacci ba sabida labari dasuketayi, ga zaman Abdulnaser da Afrah sosai ya birgeta komai tare sukeyi kaman friends , ga Abdulnaser ko gaban waye kula da AFRAH takeyi itama tin tana kunya yanzo har tasaba dan su Ummie babu ruwan su Suma 'yan gayune wayyeyu Kuma. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Da safe bayan sun kammala komai gidan su Abdulnaser sukawuce dan gaida Ummie, nan suka had'u da Humairah anta labari sai 2 deriver din Ummie ya kaisu gidannasu. </p><p><br /></p><p> Zaune suke a d'akin Inna Afrah na cin zogale sai Inna, Anty Zulaiha da Faty Afifah Kuma tawuce islamiya </p><p>"Sis wai ina friends dinki Xarah da Husnah ne" Farty tace tana sama Afrah hannu cikin bowl din xogalen</p><p><br /></p><p>Smiling Afrah tayi sanan tace "duk sunan lafiya, Husnah ma bikinta Saura 22 days, Dan ma an d'aga ne da next week ne"</p><p><br /></p><p>"Allah sarki, ai naso nazo bikin Zarah wallahi amma kinsan halin Musty yahanani fir, amma wanan insha Allah zanzo"</p><p><br /></p><p>"Allah ya yadda, nii sai na mai magana ma da kaina"</p><p><br /></p><p>"Wallahi Kiyi nasan zai yadda naga kuna 'dasawa ai"</p><p><br /></p><p>"ALLAH dai ya kaimu lfya, bari na kirasu"</p><p><br /></p><p>"Ameen"Afrah tace tana dialing Number Zarah, tana picking AFRAH tafara yimata iskanci wai ko tanada ciki ne, Kira a waya ma wahala yake bata, daria Zarah takeyi dan hira sukayi sanan Fartyta ansa itama suka gaisa, k'arshi takira Husnah ma suka sha labari</p><p> " kuu kun isheni kubarmin d'aki" innah da ke fitowa a toilet tace</p><p><br /></p><p>"Muje Ina kenan? Fatty tace tana kallan Inna</p><p><br /></p><p>"Chan maku, watou kun had'e kuna ta zance babu mai bi ta kaina bah"</p><p><br /></p><p>Dariya duk sukayi sanan Afrah tace" da girman kujerarki ba haka bane fa"</p><p><br /></p><p>"Ni tafi chan, ai zakixo ki same nine har mazauni na, Fatima ai banan takeba"</p><p><br /></p><p>"Haba tawaan"AFRAH tace tana rungumo Inna</p><p><br /></p><p>"Kee Sakeni karki ma Shu'ibu a sarar Uwa, ni kuficemin a daki"</p><p><br /></p><p>Dariya kawai sukayi suka fice daka d'akin parlor suka sauna suna hiransu hadda anty Zulaiha </p><p><br /></p><p> Ya Suleiman da Abdul ne suka shigo parlorn chan Sai mommy da Daddy ma sun shigo, suna zaune suna hira sai ga Inna nacewa"watou Family, ahhh lallai ba'aso naji shiyasa ni ba kirani bah kow" ta k'arasa maganan tana kallan su Afrah </p><p> Daddy na k'okarin magana ne phone nashi yashiga ringing shuru yayi yana kokarin picking din call din sai Fatiyy tace" ba a d'akin ki ake meting din bah kika koramu" Inna na shirin Yin magana sukaji Daddy nacewa" HAFIZZZZ!!! " duk kan su mik'ewa sukayi suma suna cewa HAFIZZZZ! A rud'e, </p><p> Daka chan b'an garan Hafiz kam hawaye ni ke zuba daka idanunhii</p><p>"Kayi magana Inajinka" Daddy yace</p><p><br /></p><p>"Dan Allah Dan girman Allah da Darajan mazon Allah SAW Daddy kazo ka fiddo ni, wallahi na tuba kayafeni Daddy sharrin shedan ne" ya karasa maganan cikin kuka</p><p><br /></p><p>" najii yanzo ka fadamin abinda ya faro da Kai, ina ka shiga Hafiz? Ka tadamana hankali" ganin yanda kowa dake parlorn yanasan jin muryan Hafiz yasa Daddy yasa phone din a has free, duk suna jin bayanin Hafiz, komai ya gayamasu bai boye komai baa, shuru Daddy yayi bai iya cewa komai bah dan wani zafi zuciyanshii yakeyii tsabar bakin ciki, mommy kam Kuka takeyi sosai, tasa itace ta b'ata Hafiz har yazama haka, ta san itace bah kowa ba, tinda take duk abinda Hafiz keyi bata taba tsawar mai KO hanashii abu bah kuma tasan ba mai kyau yakeyi ba, ita a ganinta gatane Ashe wuk'a ta dauka ta chakama kanta bata sani ba, antura shii yayi karatu chan dan yafi Abdul sai ga Abdul har yagama shii bai tsira da komai bah sai zaman person da asaran kudi yasa akayii. </p><p> Sulaiman ne yayi k'arfin Halin ansan phone din, gyran murya yayi sanan yace" kanaji kow hafiz? "</p><p>"Ehh inajinka yaya Sulaiman" Hafiz yace cikin muryansa da ke rawa</p><p><br /></p><p>"Yauwa, don't worry kaji, insha za'anema kud'in jirgin dakuma kud'in da za'abasu insha, xakadawo gida soon insha kaji"</p><p>" insha ALLAH danadawo," Abdul, Afrah da Fatty suma sukace</p><p><br /></p><p>"Okay OK , I miss you so much All, nasan duk su Daddy sunyi fishii dani amma please kutayani roqansu please " yayi maganan cikin muryan kula</p><p><br /></p><p>"Okay insha Allah, dont worry brush"</p><p><br /></p><p>"We Miss more, vry much"</p><p><br /></p><p> Katse kiran HAFIZ yayi sabida kukanda kezuwa mai</p><p><br /></p><p> kowa na parlorn shuru kawai yayi mommy sai hawaye takeyii, "yanzo Hafiz yayakeso nayi sabida ALLAH? Daddy yayi maganan cikin damuwa</p><p>"Kayi hakuri daddy"Abdul yace</p><p>"Nabashii duk wani farin ciki, nabashii duk wani gata daidai karfina, na daurashi hanya mai kyau, amma duk Hafiz bai gani ba,yaya yakeso nayi mai ne? Amma... "</p><p><br /></p><p>AFRAH ta tare nunfashin Daddy da sauri tana cewa" please Daddy, Dan Allah karkama yaya Hafiz baki, insha Allah za'asan abinyii, please daddy kace kayafemai" takarasa maganan hawaye na gangarowa daka idanunta, Sulaiman, Abdul da Fati ma hakuri suke ta bashii</p><p>"Shikenan Allah yayi maku albarka"Ameen duk sunaamsa, Inna kamar an kafata dan tsavaraken mamaki</p><p>"Amma tsakani da Allah abinda Hafiz yamin ya kyauta? "</p><p><br /></p><p>"Bai kyauta ba sam, sukaji mommy nacewa, sai ta daura da cewa, Amma ku kanku kunsani sai dai kuki fada, kowa yasan ban daura yarana kan hali mai kyau ba, na fifitasu, na banbanta su, na nunah su na dabanne su fi kowa, nayi sankai nayi zalumci, nayi baki ciki, nayi mugun hali da Duk wani abu da kuka sani, ni yadace kafarayi ma hukunci kafin Hafiz alhaji ni yadace kafara yima baki kafin kayima Hafiz"Mommy ta k'arasa maganan cikin mryar kuka</p><p>Rungomota Afrah tayi cikin sauri gami da cewa" please mommy kibar kuka, please kibar kukanan"</p><p><br /></p><p>"Nabari AFRAH amma dan ALLAH keda Abdul ku yafeni"</p><p><br /></p><p>"Nidai bakimin komai bah, tini nayafe maki walhy"</p><p><br /></p><p>Abdul ma matsowa kusa da Mommy yayi sosai kana yace " wallahi mommy ban taba rikeki a zuciyataba, kulin cikin yimaku addu'a nake DA fatan alkhari, nima baki min komai ba walhy"Dady, Inna da Anty Zulaiha, Sulaiman drama kawai suke kallo, Sulaiman wani dadi yakeji har cikin ranshii mommy ta shiryu abinda ya dade yana fata, sai yaga su Abdul DA AFRAH sun kara birgeshi, sabida dadi har dan hawaye sai dayayi, haka Anty Zulaiha da innah sosai su AFRAH suka birketa albarka kawai take SA masu Daddy kam wani side na zuciyarshii ne yabar zafi </p><p> </p><p>Itama Fatty dukar da kai kasa tayi tashiga neman gafararsu" please Sis stop it, Bakiyi komai ba" Abdul da AFRAH sukace</p><p><br /></p><p>"Nidai kuyafemin"</p><p><br /></p><p>"Shikenan please komai yawuce please "</p><p><br /></p><p>"Allah maku albarka duka"Mommy tace tana smiling</p><p><br /></p><p>Innah ma Albarkan tasa masu haka Daddy ma aunty Zulaiha nacikin Addu'a Afifah tadawo daka islamiya zama tayi itama aka karasa da ita. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sai bayan sallan isha kowancensu mijinta yazo daukanta Fatty kuma gobe zasukoma Abuja. </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> </p><p> Kwance take a jikinshii yana wasa da gashin kanta, nan AFRAH ke fadamai kiran Hafiz yayi da Duk labarin da yabasu, Addu'a sosai Abdulnaser yayi gami da cewa karta damu zasuyi magana da Sulaiman da ABDULL</p><p><br /></p><p> "Kai amma nagode, thank you so much for everything's sweetheart, u ar so so sweet, Kai am speechless, than... " bata ida fadan thanks inbah yakaima bakinta wani wawan kiss,kissing inta yayi sosai sai da yagaji dan kanshii ya saketa yana kallan cikin eyes inta sanan yace"I love you princess"</p><p>"I love you more ma prince"</p><p>"D u nkw smthn? "</p><p>" bana san jin komai jst slp, bbyna yahuta" ya karasa maganan yana shafa cikinta</p><p>"Iyye wani yaro zaizama father"</p><p>"Yh call me watevr, i'll soon bi a Father insha Allah"</p><p>"Kuma ai.."</p><p>"Kuma ai me? Ya katseta</p><p>"Toh kabari nafada mana"</p><p>"Noo jst slp"</p><p>O'o ni am hungry"</p><p>Zaro ido Abdulnaser yayi sanan yace" wat d want?"</p><p>" cornflakes"</p><p>"Oky wait fr me am coming "yayi maganan yana sauka saman bed din kan kace mai har yafice daka bedroom din dan hadomata cornflakes in. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Fatty ma tafada ma Musty shima yace zayyi wani abu a Kai, k'arfe 11 suka iso gidan nasu bayan sungaisa da Mutan gidan daki mommy tawuce Faty tabi bayanta</p><p>Gyara zama Mommy tayi kana tace" toh Fatty naji kina complaining kan mijinki, toh wallahi ki rekeshi da kyau, duk wani mugun abu dayakeyi addu'a kawai shine abinyi, kita hakuri, dan nima shii Daddynku da family sa sukaitayi danii, kinga inda baiyi hakuri da halina bah da kila bakin hali da mugun halina sunfi haka, sabida haka hakuri da juria shizaki kinayi, kuma kidage sosai da addu'a abinda baki ganeba wanda ni bazaki iya fadamin bah toh ga Yar uwarki nan AFRAH sai ki sarmata dan zata baki shawara maikyau Afrah nada basira, natsuwa da kuma hankali, kinji ko? "</p><p><br /></p><p>"Ehh mommy naji, insha Allah zanyi ynda kikace, insha Allah" yauwa Allah maku albarka"</p><p><br /></p><p>"Ameen ameen mommy"</p><p><br /></p><p>Musty sunyi magana da Sulaiman yace indai sunkoma ko transfer ne saiyyi, sanan ya roka Sulaiman daka yasarda su Daddy( Ashe dai su Musty anada mutunci.. Lol) </p><p> Gidan Afrah suka wuce dan yimasu sallama, nan Musty kesanar da AFRAH zasudawo nan ba da dadewa ba. </p><p>Sai da sukayi sallan azahar, sanan wani Hussain a gidansu Musty na nan kaduna yakaisu train station, dan train zasubi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Cikin kwana 3 su Abdulnaser suka gama shiya komai suka gama, kud'in jirgin mutum biyu Musty yabada, watou na Hafiz da yaya Sulaiman, Abdulnaser kam shine wanda zai biya kud'in da prison ke buk'ata, kafin su wuce yasar da Abba da Ummie komai goyan baya suka bashii gami da yimashi add'an fatan alkhari a k'arshe sukai ta samai albarka </p><p><br /></p><p> Sun isa Lafiya, taxi suka tare ya kaisu har masaukin suu, bayan sunyi sallah, wanka, sunci abin gami da dan hutawa, Numbern da Hafiz ke kiransu da shii suka kira nasani security, security ya hadasuu da Hafiz nan suke sanar dashi isowansu, Hafiz yaji dadi sosai nan dai suka sanar dashii gobe insha Allahu zasu iso. Hafiz yaji Dadi sosai addu'a kawai yaketamasu</p><p><br /></p><p> Washe Gari da sassafe suka isa wajen, sunyi duk abinda yakama ta, mamaki yakama hafiz mijin Afrah ne wai yakemai mutunci haka, kasu Afrah na Kira sosai suna gaisawa haka Faty da Musty DA su Daddy, cikin kwana 2 sun gama duk wani abu da'ake bukatan Hafiz yayi, sai da suka k'ara 3days dan Abdulnaser yayi shopping sosai a k'asar sanan suka dauko hanya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ranan Afrah gayyato Husnah, salamatu tayi da Afifah suka shirya lafiyyan abinci mai rai da lfya da drinks iri iri. </p><p> Gidan su Abdulnaser suka fara tsaya suka bah Ummie nata kana sukawuce nasu gidan, yaya Abdul ne zai dauko d'an ta kano suka sauka</p><p>K'arfe 4 na yamma suna garin kaduna lafiyalau suka ISO </p><p> Tin kafin mota yagama tsayawa Hafiz yafitoh, wajen Mommy yayi direct yayi hugging dinta gami dacwa " mommy please ina Daddy " ya k'arasa maganan yana kallan Inna da su AFRAH, Afifah DA ke tsaye a wajen, mommy bata iya cewa komai bah, ganin haka yasa Hafiz yasaketa yanufi wajen Innah, "kayi shuru Hafizu kaji Daddy din naku yanan lafiyalau " Inna tace tana shafa kanshii, smiling kawai yaketa masu, hama hannunsa Abdul yayi suka shiga cikin parlon, shi Hafiz sam bai lura da gidan bah, burinshi kawai yayi ido hud'u da Daddyn su. </p><p> A zaune kuwa ya ganshi, a nan parlorn, karasowa Hafiz yayi cikin sauri ya kama kafar Daddy yana cewa"kamin rai Daddy natuba wallahi, dan Allah ka yafemin walhy duk abinda kace dani yanzo shi zanyi dan Allah Daddy kayafemin" Hafiz ya karasa maganan yana kuka yana rike Daddy gam, duk wanda ke parlorn sai da Hafiz yabashi tausayi Inna kam hadda hawaye, Sulaiman, Abdul da AFRAH kam Daddy ne ta rufesu</p><p>"Shu'ibu kayafema yaronan yatuba" Inna tace cikin muryan ta daka rawa</p><p><br /></p><p>Shafa sumar kanshi Daddy ya shiga yii, yana cewa" Wallahi nayafema Hafiz, na yafemai duniya da lahira, kawai inaso naga wani abu ne, nakuma gani, tashi kazauna Allah maka Albarka" </p><p>Ameen ameen yaaa " Hafiz yace tana hugging din Daddy, shina Daddyn run gumeshi yayi yaba bubbuga bayansa</p><p> Bayan yasaki Daddy wajen mommy yaje itama ya rungumeta, haka Abdul Afifah sai pictures take sauka tana wani jin Dadi. </p><p><br /></p><p> Bayan anci ansha nasiha Sosai Daddy ya karayima su haka Inna ma, gami da samasu albarka, Daddy nagamawa su Afrah daka Abdulnaser suka wuce gida cikin farin ciki. </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> Sai da Hafiz yadawo yayyacinsa yake tanbayan gidansu nadaa nan Sulaiman da ABDULL sukabashi labarin abinda ya faru sosai ya ji tausayin Daddy yakuma yii alkawarin barin duk wani hali dayakeyi. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kwanan Hafiz biyu da Dawowa har yayi dan kiba daka ramar da ya d'anyi dan abinci yakeci sosai, a ranar ne Fatty sukazo, sunan zaune a parlor suna dan Hira Yaya Sulaiman ya shigo sai da ya gaida duk yan parlorn sanan yashiga sanar dasu duk company dayayi Interview sun daukeshi aiki,kabbara duk sukayi gami da yima ALLAH godia.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_wanan page din NAKOWA ne kyauta ga mai karanta book din nan, kusa biebie dee na sanku har cikin ranta wallahi_</p><p><br /></p><p> _Maryam da Haneefa naji sakonku, kawai kuta hakuri nidince sai a slow wlhy_🤣🤣😅🤸🏻♀</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*page 84*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*C*ikin kwanakin nan kowa yana cikin farin ciki dakuma walwal da jindadi, 1 week Musty yabar Faty tayi a kaduna sai shine yakoma abujan, tin Thursday suka wuce katsina, ziyara sosai sukayi gidan 'yan uwa da abokanan arziki Mommy nata neman yafiyar jama'a kasan cewar mutanan katsina masu mutunci da karammci ne yasa suka yafe mata kaman komai bay faru ba, ko da sukaje gidan Mami mommy sosai ta roketa kafara, amma dayake masu suba Rabi'atu na musanmanne daban suke yasa Mami tace subar zancen komai ya wuce, haka wanan zuwa katsina yayi dadi sosai akayi zuminci, ranan Sunday daka nan katsina Sulaiman yayi abuja dan Monday da yardan Allah zai shiga office( toh Sulaiman Allah afara a sa"a) su Mommy kam sai Wednesday suka dawo kaduna tare da tsaraba iri iri, tare da Fahad DA Arfah suka zo d'an anyi hutu Afifah ba sauki ansamu abokan surutu. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Innah ma taso ta zauna nan katsina amma sam jikojinta suka k'i dole suka dawo tare. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sai yamma suka iso kaduna duk a gajiye suke fatty kam fever ne mai zafin gske ya rufeta, bata samu komawa gidanta ba, Afrah DA su Afifah ne Abdulnaser yazo yawuce dasu bayan yagaida su Daddy, kwana Fatty tayi da wanan fevern sai da safe cikin yaddan Allah taji sauki, suyi waya Musty nan yake sanar da ita ta zauna kawai zai shiga kaduna ran Friday Dadi Fatty taji sosai. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau Su Afifah tin safe suka wuce gida ita kadai ne bayan tagama duk abinda xatayi a gida brkry dinta ta leka Alhamdulillahi komai dai dai yake tafiya, tana dawowa sallan laasar, tayi kana tashiga duba wani book har 5:00 na yamma, tana ganin 5:30yayi kuma ba'adawo dasu Afifah bah tasan yau bazasu kwana wajen taba, shiyasa komai bata daura ba, Tana zaune taji shigowan motan Abdulnaser gidan tashi tayi a hankali dan tarboshi, jakan laptop din taso amsa sai yakibata sai wasu I. V da yamikamata tareke" sweetheart waye zayyi aure ne I. V masu kyau wallah</p><p>" ajesu kawai sai nadawo masjid nabaki labari,</p><p> naga tinda kikaga invitation card duk kin rud'e" yayi maganan suna shigowa bedroom dishi,ajiye cards din tayi kan bedside drawer, tafice daka bedroom din, cikin tanufa, ruwa mai sanyi a Dan tray AFRAH ta dauko tare da cup ta dawo d'akin, cikin sauri Abdulnaseer ya amsa tray din yana yimata smiling yana cewa" nifa banaso kina wahala"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"A'a kawai cewa zakayi kana min bakin cikin ladan da zansamu"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>"Ahh haba wane ni, ai ko zaman nan dakikayi a gida yau ladace"</p><p><br /></p><p>"Aa nidai bani nazubama ruwan"</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bottle din ruwan Abdulnaser ya d'aga yana sha batare da yazuba a cup dinba, AFRAH na ganin haka tayi toilet dan hadamai ruwan wanka, " ai sai kaje kayi wanka"</p><p><br /></p><p>" toh hajjaju"</p><p><br /></p><p>"Karka kuma kirana hajjaju, sai kace wata uwar mata"</p><p><br /></p><p>Dariya yayi sanan yace" uwar yayana ba" </p><p> </p><p> Smiling kawai Afrah tayi, kafin ya fitoh har ta fiddo mai da kayan da zaisa ta fesa turare, ya shiyar tsaf zai tafi masjid Afrah na k'ara tsamsa bedroom tace" sweetheart nifa banyi girki ba yau"</p><p><br /></p><p>"No wahala in mun idar da isha'i zan samu mana wani abu, Abincin Ina ma kikeso? "</p><p><br /></p><p>"Na big treat, yafi kusa"</p><p><br /></p><p>"Tohh, sai nadawo"</p><p><br /></p><p>"Adawo lfya Allah tsare"ya mansa da ameen yana bari bedroom din, tana gamawa alwala tayi itama ta shinfida preying mat, ta zauna har a ka Kira magrb, bata bar sallayan ba sai datayi isha gami da azkar na sallah, nike hijab da abin sallan tayi tashiga wanka, tana fitowa tasa duguwar rigar bacci har kasa Sure kawai tashafa dan tinda tasamu ciki bata san kanshi sosai, parlor ta dawo ta zauna tana jin karatun Al'Qur'ani mai girma sai 8:45 Abdulnaser yadawo, bayan sunci sunsha sunyi dam Abdulnaser ya kalleta sanan yace" baby ina cards dinnan? "</p><p><br /></p><p>"Yan bedside drawer na bedroom dinka"</p><p><br /></p><p>Da kanshi ya dauko ya dawo yaxauna" kinga na bikin Hashem ne da Nussy"</p><p><br /></p><p>"Ah masha Allah abin ya matso" Afrah tace tana bude card din, ikon Allah tsakaninsu da Husna 1 week ne, lallai munada sha'ani"</p><p><br /></p><p>"Ke baki gajiya da yawo ne wai? Shekaran jiya kuka dawo daka katsina fah, haba baby"</p><p><br /></p><p>"Wai kana nufin bazan je bikin Husnah ba? "</p><p><br /></p><p>"Zakije ko sau daya ne kawai dan mutincinta, gashi zakukoma sch ma, ni wallahi basan fitanan yanzo" shuru kawai Afrah tayi dan tasan bada wani problem da mijinta</p><p>"</p><p>" gobe ne zamuje hospital ko? "</p><p><br /></p><p>"Ehh insha Allahu"</p><p><br /></p><p>"Allah kaimu, </p><p><br /></p><p>"Ameen"</p><p><br /></p><p> Afrah cikinta yashiga 7 moths, anyi mata awo ita da baby sunan lfyalau.</p><p><br /></p><p> </p><p> </p><p>Ran Friday da yamma Musty ya shigo kaduna yazo Fatiyy ba lafiya bayan ya gaisa da mutan gida, Hospital direct yayi da ita, suna isa akayima Fatty duk abinda yadace, angano tana da shigan ciki na 2moths, wanan karan Musty yayi murna sosai Fatty ko hamdala tayi ma Allah daya shirya mata mijinta, da suka dawo gida haka Musty ya Kira mommyshii da aunty Lailah da sauran Family yafada masu sai murna sukeyi da addu'an Allah raba lfya.</p><p><br /></p><p>Fatty takira Afrah tagaya mata, sosai tayi murna yakuma yimasu addu'a baki dayansu na Allah ya rabasu Lafiya. </p><p><br /></p><p> Haka Musty DA y'an uwansa nan kaduna suketa kula da Fatty, ko da zai koma abuja wanan karan ma Fatty bata bishii ba, gidanta nan kaduna take, AFRAH da kanta ta gayama Musty bikin Husna da zasuje ya yadda Fatty taje amma sai da ya damka amanarta wajen Abdulnaser.</p><p> Da Musty zai wuce gidansu ya aje Faty dan gidan nata yayi Shuru babu kowa sai dare deriver zaiso ya dauketa</p><p><br /></p><p> Suna zaune a parlor suna hira Kaman daka sama sukaga AFRAH d Abdulnaser sun shigo da sallama, bayan gaishe gaishe hira akai tayi, Abdul, Hafiz, Abdulnaser Faty DA AFRAH cikin farin ciki da kwanciyan hankali sai 5pm su Afrah suka wuce shima Inna da mommy ne sukai musu tsiyan wai su kulin yawa suna hanya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> An fara bikin Husnah, komai cikin kwanciyan hankali akeyin shii, biki yayi kyau sosai anci ankuma sha, ango DA Amarya Husnah anyi kyau kamar babu gobe, anyi pictures sosai, event 1 kawai Su AFRAH sukaje KAMU shima da kyar sai yinin Biki watou ran daurin aure, shima duk Ba wani zama sukayi ba, Zarah ita batama zobah sai sisters dinta dan ciki ne da ita mai bata wahala sosai, Ita Husnah ma taso AFRAH ta huta dan tasan inda Afrah qalau take ita da Zarah su na daban ne, a hakama tagode sosai da abinda suka bata familynsu da mazajensu, haka akayi biki aka gama duk babu AFRAH sai Afifah dan hadda friends din ta tayi inviting, Mommy Inna Afifah su suka sha biki dan har Gidan amarya da dinner duk sunje, Daddy, Hafiz da Abdulma sunje daurin aure yaya Sulaiman ne kawai baije ba Dan ran Friday bai shigo kaduna da wuri ba, Haka Mamin Xarah da sisters dinta duk dasu akayi komai. </p><p><br /></p><p> Uguwan dusa aka Kai Husnah, gidanta mai kyau haka kayan da a ka zuba mata ma, addu'a kowa yaytayi na neman zama lfya da samun xuriya nagari *toh Husnah Allah bada zaman lfya Amern*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yau Sunday Sulaiman ne zaune shi da Daddy suna dan hira vaYan sun gaisa, kallan Sulaiman Daddy yayi sanan yace"Sulaiman ya zancen yarinyar da kake nema ne? "</p><p><br /></p><p>Dan sosa Kai Sulaiman yayi san yace" Daddy bamu sasanta da ita ba gskia, last 2 weeks ma tayi aure"</p><p><br /></p><p>"Tohh ALLAH kawo ta gari"</p><p><br /></p><p>"Amern Daddy"Sulaiman yace a hankali </p><p><br /></p><p>"Naga kasamu aiki ne, kuma mai tsoka shiyasa na tanbaye ka ko kuna tare sai aje ayi magana manya sushiga ciki"</p><p><br /></p><p>"Haka ne very soon zan samu wata insha"</p><p><br /></p><p>"Toh Allah temaka" Daddy yace yana daukan wayanshii yana duba abu chan yace " kaga dubamin message dinan nidai ban gane kanshi ba" Amsan wayan Sulaiman yayi yana duba text din, Daddy ya cigaba da cewa tin last 3weeks ago suke turowa ni bangane ba"</p><p><br /></p><p>Zama Sulaiman ya gyara sanan yace" Daddy wanan ai sunan association din da kasa Business dasu ne a Ghana "</p><p><br /></p><p>"Ehh nagani ai bansan inda suka dosa bane ai"</p><p><br /></p><p>"Ina zuwa " Sulaiman ya fita da sauri </p><p><br /></p><p>Laptop dinsa ya dauko daka dakinshi yadawo ya zauna nan ya shiga link na association din sosai yayi bincike har ya gano bakin zaran, Ashe problems sosai aka samu sai last month suka daidai ta komai, duk wanda yasa business dasu sun sai damai kayanshi shine suke turo text kayi bincike zakaga zabi inkana san cigaba da business dasu profit kawai zasu turoma ta bank tndaa kan kasa hannu a business din akwai duk wani information a kanka inkuma kadena Business dasu zasu turona uwar kud'in ka da kuma profits(riba) da ka samu a yin Bussine dasu na farko, ai Sulaiman bai jira tan bayan ra'ayin Daddy ba yatura Daddy ya bar business da suu, kancewar phone din Daddy na hannun Sulaiman baifi minti 8 ba alert yashigo wayan, uwar kudi da profit din Daddy na kayan da suka saida masu daka chan, sujjada Sulaiman yayi yana cewa Allahu Akbar ganin haka yasa Daddy shima yayi sujjada tare da cewa "Alhmdulillahi" batare da yasan dalilin da yasa Sulaiman yayi sujjadan bah, dagowa Sulaiman yayi yana wani irin Smiling sanan yace" Daddy kaga ikon Allah SA mu'ujizan sa, Daddy kaga anfanin ansan Kaddara mai kyau ko mara kyau da hannu biyu, Allahu Akbar, ALLAH mai girma da daukaka mai juya al'amura a Duk sanda yaso kuma yaga dama"</p><p><br /></p><p>"Wanan Haka yake Sulaiman hak'ika duk wani wanda ya kauce hanyan Allah yana cin masifa da bala'i"</p><p><br /></p><p>"Sosai Daddy kaga dai kudinka da kasa...... " Sulaiman yayima Daddy bayanin komai </p><p><br /></p><p>"Kagani har kudadenka sun fitoh hadda riban kayan da suka siyarma" wani kabbaran Daddy yasa gami da hamdala</p><p><br /></p><p>"Allah gagara musali, Allah mai girma da Rahma, Allah nagode ma, Alhamdulillahi, Alhmdulillahi Alhmdulillahi"kalman da Daddy yaita nanatawa kenan, Alwala suka dauro sukayi raka'a biyu bakara yima Allah godia, nan suka dan kara shawara kana Sulaiman yabar wajen Daddy cikin farin ciki. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p> Sai da suka dawo kada masjid suna zaune dukkansu a babban parlorn suna cikin abinci, bayan sun kanmala ne Daddy yayi masu bayanin komai, Suma kabbara kawai sukai tayi gami da yima Allah godia, Nasiha sosai Daddy yayi masu a k'arshe yayi masu Addu'a gami da samasu Albarka, Inna ma Nasihar tayi yakuma kara da sa Albarka wanan rana kowa cikin farin ciki yake mara musaltuwa. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Nan danan Afifah ta dau waya takira AFRAH da fatty ta sanar da su duk bayanin da Daddy yayi, sanan ta Kira yaya Musty da yaa Abdulnaser ma ta sanar masu, suma a side dinsu murna sukayi sosai dayima Allah godia, kan kace mai har sunzo yima Daddy murna, Daddy sai samasu albarka yakeyi, ranan Sulaiman yakoma Abuja, Musty da Fatty ma haka d'an Mommy shii duk tadamu wai yadawo da ita, haka aka rabu cikin farin ciki. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Suna barin gidansu AFRAH, gidansu Abdulnaser sukayi, Ummie ce ita da sister Anty murja sai Anty Baraka suna hira" kingani banace maku ba yanzo sai ku iya ganinsu" ummie tace tana murmushii, </p><p><br /></p><p>"Ai ka kawota da kanka ka hutashemu" cewar Anty Murja</p><p><br /></p><p>Ita AFRAH smiling taayi tana gaidasu, cikin sakin fuska suka amsa gami da tan bayanta karfin jiki ta masa da alhmdulillahi </p><p><br /></p><p>"Ni ban gane ba, nakawota da kaina kamar ya? " Abdulnaser yace yana kallan Anty Baraka </p><p><br /></p><p>"Dama ko bakuzo ba Xamuzo mutafi da ita, Inace wata na 7 take zata shiga na 8 kow? " anty Baraka baraka tace</p><p><br /></p><p>"Toh wai akaita Ina? "</p><p><br /></p><p>"Gidanan zata zauna, yanzo kagane kow" Ummie tace tana kallan shii</p><p><br /></p><p>"Ehhh nagane" yace a hankali </p><p><br /></p><p>"Da kyau sai ka koma ka hado mata duk kayyaki da shopping dinda kayi"</p><p><br /></p><p>"Toh amma gobe zatagoma school fa"</p><p><br /></p><p>"Toh sai akace kuma anan ma bazataje ba ko? Kai mai yasa nakada kawaici ne wai? " aunty Murja tace</p><p><br /></p><p>"Barshi karyayi kawaicin, nan dai zata zauna har tayi 40days mayb ma tafi" ummie tace </p><p><br /></p><p>"Ahhh Ashe nima nan din zandawo kenan"Abdulnaser yace yana ficewa daka Parlorn </p><p><br /></p><p>Dariya kawai sukayi, AFRAH kam wajen Huraira ta shige, dan sai gobe zasuko school amma ita sai Wednesday ma zata koma. </p><p><br /></p><p>Babu yanda ya iya haka ya kwaso duk a binda Afrah zata bukata yakawo gidan, shima kuma ya dauko nashii dan shima zaman zayyi, </p><p> Abbah kam shi zamansu ma Dadi yamai kulin yana ganinsu, Abdulnaser ke kaita sch Driver ya daukota bayan la'asar kuma ita da Huraira suje strolling, haka suke fita kulin har takoma sch itama sai kuma weekend intazo</p><p><br /></p><p>da su Inna sukaji Afrah na gidan sirikarta sosai sukayi murna, duk sati suke zuwa dubata, inzataje awo hospital kuwa hadda Ummie akezuwa, sosai Ummie ke kula da ita kamar mai haka Abba, anty Baraka, da sauran yan Uwa, Aunty Rabiela ma kulin cikin video call suke, Abdulnaser kam babu kunya shima ko gaban waye, AFRAH najin dadin gidan sosai, Hafiz kam kulin sai yazo dan wani irin mugun shiri sukeyi wanda ko da yaya Sulaiman da ABDULL basuyi irinsa ba, dan Hafiz ya natsu sosai yanzo haka restaurant da AFRAH xata bude komai hannunsa yake. </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Cikin wata daya komai ya chanza cigaba bud'e da daukaka duk Daddy yasameshi dan sana'arsa nada yakoma na shinkafa kuma wanan karan sosai Allah yasa mai hannu, ganin Hafiz suna dan business da Abdul yasa Daddy kara masu jali sosai sukayi murna gami da addu'a. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yawan zuwa gidan Da Humaira keyi amso sak'o intadawo weekend ko zuwa hira wajen Inna yasa yaya Sulaiman ya ganta yakuma yaba dan Humairah akwai natsuwa da tarbiyya sanan ga iya gayu da wayewa. </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> Su Daddy suntare a sabon gidansu dake nan marafan da sati daya AFRAH ta haihu baby boy, bawani wahala tasha ba, murnar da sukayi Allah ne kawai ya san iyakansa dan fada ma bata lokaci ne, kafin kace mai yan katsina sun iso amma wajen Mommy suka sauka sai dai suxo barka, haka family Mima, ga yan adamawa dangin Ummie da Abba, ga yan uwa da abokan arziki, Daddy yazo yaga yaro yakuma samai albarka, Inna kuwa ba'a cewa komai ba'abar yan *Biebie Dee Novel group da Da Biebah place da kuma D'an HAKKIN da ka RAINA fan group* a baya ba kaf dinsu sai da sukazo barka zuga guda kamar... 🤣😂🏃🏻♀ I love you all ❣💯</p><p><br /></p><p> Fatty ma cikin ta ya girma dan wata 5 cikin na6 tayi kyau sosai abinta, Xarah kam ta haihu baby girl Fanan babynta mai kyau </p><p><br /></p><p> Abbah da kanshi yasama jariri Suna Ahmad, ranan suna kam Mommy da Mami taronsu da ban,sukayi kudi yayi kuka dan komai an tsarashi irin namasu hali, haka gidanan Ummie ma da yanwanta, Naira yayi kuka anci ansha ankuma sha pictures, maijego tayi kyau sosai tasa kaya, haka dai taro yatashi lafiya kowa nasan barka tare da abubuwan da aka raba masu k'ayatarwa, haka AFRAH da Ahmad sunsamu kaya sosai wanda ni bazan iya fada ba. *kawai Allah raya Ahmad*👏🏻🤸🏻♀</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Anyi suna da kwana 5 Abdul yawuce Camp, yabar Bussine wajen Hafiz, kaya aketuro masu daka Dubai da China na maza da mata sanan materials na maza da shadda. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Afrah tanasamun kula fiye da tunanin mai karatu dan Ummie sosai take kula da Afrah, haka Aunty baraka, aunty murja Mommy kam ba'acewa komai, kafin suyi 40days AFRAH da babyta sunyi mugun kyau ga Ahmad da kyau komai na Abdulnaser hadda dimples hasken fatane kawai na AFRAH, koda sukayi 40days satin farko Adamawa sukaje gaba daya su hadda Ummie da Abbah jirgi suka bi, sati na biyu katsina sukaje shima a jirgin a sati na ukune sukaje zaria hadda Mommy da Fatty datazo amma ranan suka dawo, a ranan nekuma da dare akamayar da AFRAh gidanta...</p><p>[12/18, 09:04] BIEBIE DEEE: *D'AN HAKKIN DA KA RAI NA...* </p><p><br /></p><p><br /></p><p> _REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITES'S(We don't just entertain and educate,we also touch ♥ of the readers_)</p><p><br /></p><p> _story/written by_</p><p> ~Biebie Dee~🌸</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _Dedicated 2 amazing sister Afrah Bhai_</p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> *#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*</p><p># *IG PML WRITERS*</p><p># *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*</p><p># *http://maryamsbello.blogspot.com*</p><p><br /></p><p>*wanan LAST page din nakune Pure moment, Allah karemin ku, Ameen*</p><p><br /></p><p>*SADNAF*</p><p>*AXLAND ( SWEETHEART)*</p><p>*MSB*</p><p>*UMMIE GARKUWA*</p><p> gaisuwa mai yawa da fatan alkhari.... </p><p><br /></p><p><br /></p><p>*PAGE 85*</p><p><br /></p><p> </p><p>""""""Wannan dare Abdulnaser da Afrah ansha soyayyah ba kada'n ba, sai addu'an ALLAH barsu tare kawai, kwana ta biyu da dawowa Ummie ta kawo mata Mai aikinta da kuma rainon Ahmad Sa'adatu, Lafiya lau suke zaune dan daka sa'adatu har AFRAH baduda problem duk da sa'adatu bawata babba bace amma batada sa magana sam gashi tana kula da Ahmad sosai. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Afrah ta haihu da 2 months aka sa bikin Yaa Sulaiman da Humairah 2 weeks kawai, babu sauki wajen Afrah, yayar amarya kanuwar ango, haka Abdulnaser ma babu zama haka Hafiz da ABDULL, Daddy dan lalle zayyi aure, mommy da Inna ma ba sauki🤣</p><p><br /></p><p>Su Mommy suyi lefe nagani nafad'a anzuba kaya kaman me, komai mai kyau da tsada ne a cikin kayan, haka aka Kai kaya kowa nata san barka da sa albarka</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Biki nata matsowa yan uwa na nesa irin su Anty Rabiela, Anty Shuwa da anty Umma tun biki nasaura 1weeks suka iso Nigeria, yeeeeeeeee fada bata lokaci, Yan katsina, zaria da yan abuja duk sunzo Kai Sulaiman yayi goshii bikinsa yayi jama'a bana wasa ba, haka Faty da Family mijinta duk sunzo, Abdul, Hafiz duk an yi gayyata babu zama babban waaa na aure, Inna kam ai walima na musanman ta shirya, wanda su Mom fauxy, mom musa, mum ishaq ne a gaba gaba, Mami ma tap gayya tayi banda yan katsina hadda jama'arta nan kaduna dan Sulaiman na hannun dabanta ne, ran kamu Amarya tayi kyau haka ango kamar kasacesu hmmmmm Afrah kam tayi wani mugun kyau ita da Ahmad ga girma da yaron yayi kowa daukanshii yaketayi dan yaron chubby ya had'u walhy *wayyo biebie niji Kaman nasace Ahmad na gudu*🤣</p><p><br /></p><p> Ran Friday aka daura aure, wanda duban jama'a suka halarta, yinin biki ma yayi kyau so Afrah, Zarah da Husnah ansha kyau an haska, Fatty kam sai fama da gown takeyi dan ciknta ya girma, chan gidan ango amarya ta wanku tasha kyau, haka ummie da jama'arta haka aunty Baraka mai masaukin baki tasha kwalliya kawai gskia biki tayi kyau babu karya. </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kafin a Kai amarya gidanta, gidan surikanta aka fara kaita, nasiha sosai mommy da Daddy sukayi ma amarya haka akayi da ita gidan ta dake bayan government house, Ana kaita shiryawa akayi akawuce Dinner shima dai ansha kyau ankashe naira, washe gari bud'ar Kai kuma akayi walima ranan kowa yatse.. *Allah bada zaman lfya*</p><p> Amarya xaria zata fara zama sabida school, weekend wai xatayi a kaduna. </p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Fatty ma ta Haihu baby girl, time din Ahmad yayi girma sosai kusan 5 months, har Abuja aje kasa suna wanda ya had'u sosai anma baby sunan Mommy Musty Rakayyah za'ana kiranta da ifrahhhh</p><p><br /></p><p>🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸</p><p>Haka rayuwa taita tafiya cikin dan watani kowa na cikin farin ciki da kuma walwala, Bud'i da haske da D'aukaka Daddy ya samesa, haka Sulaiman, Abdul sai Hafiz da Bussine ya amshe shi sosai, Abdulnaser da Afrah Musty da Fafy kowa na cikin kwanciyar hankali shida iyalinsah. </p><p><br /></p><p> Husnah ta haihu itama bby boy Muhammad suna cemai Hanmmad. </p><p><br /></p><p> </p><p>Mommy da kanta taba Abdul Afifah dukda yanzo ta shiga jss3,da hannu biyu Abdul ya amsa Afifah, Daddy da Inna sunyi murna sosai da wanan had'i haka Sulaiman, Hafz, Faty da Afrah, kundai san Afifah da watanta tar so bawani problem aka samu da ita ba shima Abdul din dake ba galfrd gareshi ba duk babu wani matsala da'aka samu da tashiga ss1 za'ayi auran, Hafiz kam yarinyan uncle Isma'l kanuwar Zaynab yakeso a chan katsina Rabi'atu amma Ummie akecemata.</p><p><br /></p><p> Yanzo Mommy babu ruwanta Lafiya lau take zaune da kowa daka yan katsina har yan zarian, da bar shiga k'awaye yan karya yan uwanta sisters dinta da yaranta sune friends dinta. </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Anty Zulaiha tayi aure wani abokin Daddy ta aura itace ta biyu, gidanta nan a shooting range. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*SEVEN YEARS LETTER*</p><p><br /></p><p>AFRAH ce zaune a wani parlor da yaji kayan more rayuwa iri iri, sanye take da super wax dinkin fited gown, tayi kyau har ta Gaji, Afrah tayi Kib'a kadan ba sosai ba, da kunga ta, Kunga yar gayu kumaa mai kudi d'an yanzo restaurants 2 gareta ga brkry 2 shima sanan *Afreey house of cakes & ice cream* da ba a dade dayin launching din bud'e wajen bah, ga laboratory da take da shii na kanta (kuu Afrah tayi kud'i wallahi) </p><p> wani littafi take dubuwa, yaraney su uku na hango biyu mata wanda da ganinsu twins ne bazasifi 4yers ba sai na mijin a bayansu wanda baiwuce 6yers ba yana binsu, a guje twins din suka haye kujeranda Afrah ke zaune Kai suna cewa"Mami kinga Ya Ahmad ko? Tsayuwana na gyara da kyau ina kallan yaran dan dazo banga face dinsu ba.. Lol koman su daya da Afrah komai irin na maminsu sakin baki nayi ina kallan yaran dan sun birgeni sosai </p><p><br /></p><p>"Mami kinga fa uztaz hadi ne yazo wai bazasuje ba, Anty Sa'a ta masu magana wai o'o" ya karasa maganan yana kanne idanu</p><p><br /></p><p>Kallansuu Afrah tayi sanan tace "Oyaa Najma, Najwa tashi ku wuce ko a fasa zuwajen su Inna har wajen Ummie da Abbama bazakuba, tinda bakusan karatu"</p><p><br /></p><p>Cikin sauri suka tashi duka wuce Afrah tabisu da Ido tana murmushii, ta ci gaba da duba takardan, tana Zaune Abdulnaseer yashigo parlon, xama yayi kuasa da ita gami da jan hancinta, aje takardan tayi nata kallanshii cikin so da k'auna" ina angels dina suke? " shima naganshi cikin 3 quarter da white T-shirt yayi kina na jindadi da kwanciyan hankali, gawani fresh dayayi, Dama Abuka da handsome ga kuma mud'i </p><p><br /></p><p>"Suna chan suna karatu ustaz yazo"</p><p><br /></p><p>"Ohh hakane"</p><p><br /></p><p>"Suna gama sai muwuce kow" tayi magan tana daga mai gira</p><p><br /></p><p>"Ina xamu?"</p><p><br /></p><p>"Gida mana yau ai karshen wata, tin jia mommyn Ifrah(Faty) tace sun shigo kaduna "</p><p><br /></p><p>"Hakane fa meeting kow?"</p><p><br /></p><p>"A'a yawo"AFRAH tace tana mik'ewa tsaye</p><p><br /></p><p>"Zan kamaki yarinya"</p><p><br /></p><p>"Toh gani kamar a kama Amma babu dama" tace ta rugawa a guje, tashi yayi yabi bayan ta yana daria</p><p><br /></p><p>Bayan su Ahmad da twins sun gama karatun k'ara shirya masu akayi cikin wasu designer gown na Najma Pink color na Najwa pitch color sai wani while hula na gayu sai low fas kowa kalan gown dinshi hadda wani side bag na gayu naga an masu crossing sai kamshi sukeyi 💋😍 twins sun bani sha'awa wallahi, Ahmad kam shida Daddysu shadda suka fara tas dikin 3 quarter suyi kyau, Afrah kam cikin lace na ganta mai uban tsada back da touch din red.. Hmmm sunyi kyau over, mota suga shiga sai gidansu Daddy. </p><p><br /></p><p> ABDUL kam Afifah na ss1 aka daura masu aure, time din she was 15yrs, da farko NNPC yake aikin, Afifah na ss2 tayi waec, result na fitowa, shida ita sukawuce Istanbul chan Afifah tayi degree, inda shikuma yake aiki dawani company kuma yana sch din shima, 4 Afifah tagama sch dinta shima 2years kawai yayi ya kanmala, bayan Afifah tagama karatunta ne suka dawo Nigeria, suna dawowa ABDUL yafara aiki a wani babban company nayi motoci, Afifah kuma tazama lawyer sai da suka dawo Nigeria Afifah ta Haifa seeyama mai kama da Abdul sak. </p><p><br /></p><p>Sulaiman ma yayi kudi sosai, Humairah kam tana aiki a ministry of Education. </p><p> Hafiz yazama babba dan kasuwa k'asa kasa yake fita siyo kaya matar shii Ummie kuma Norse ce Babba a nursing home da kenan kaduna</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p>Malali sukayi direct, Gwanga road suka shiga daka frkon layin gidan yake, wani katafaren gida ne upstairs, horn yayi gate man ya budemai ya shiga, a k'arshe yayi parking dan duk an rigasu zuwa" lallai yau muyi latti" Afrah tace</p><p><br /></p><p>Muryan yaran sukaji suna cewa " Mami pleasemu sauka"</p><p><br /></p><p>"Babu mai fita sai nagama parking" tare suka fitoh yaran sukai ciki a guje suna kiran sunan yan uwansu. </p><p><br /></p><p> Babban parlor ne mai girman gaske, Daddy, Musty, Hafiz da Abdul na hango cikin Parlorn, karasa wajen Afrah da yara suyi dan gaidasu, gaidasu sukayi suka amsa cikin fara'a, Abdulnaser kam sai da ya fara zuwa wajen da Inna mommy, Farty, Afifah da sauran yaran suke sanan yayi wajen su Daddy. </p><p><br /></p><p> Hira akai tayi sai da akayi sallan azahar sanan suka zauna a makeken dining table dn cin abinci, kowa cikin shigar alfarma, Sulaiman da Humairah yaransu biyu Abdullahi(Khalifa) da Maryam, sai hafiz ya zama dan kasuwa sosai shida matar shi ummie suma yara biyu garesu salis( hanif) da Aliyu, Adul da Afifah kam 1 seeyama, sai Fatty da Musty yaransu uku Ifrah, khadija( Afrah) masake dn Afrah sai Khalid, haka sukeyi duk karshen wata su hadu da karfafa zuminci, bayan sun gama nasiha Daddy yayi kamar yanda yasa ba sanan suka cire mutanan da zasu Kai hajji wanan year din, bayan sun gama aka rufe taro da addu'a, kowa ya dau iyalinsa, Sulaiman da nashi iyalinsa gidan Ummie sukayi haka Abdulnaser sa nashi iyalin, Adul da hafiz kam nan gida suka barsu tinda su yan gida ne. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka rayuwa yaci gaba da tafiya bad'i daukaka da kwanciyan hankali kowa yasameshii, duk bayan wata biyu suke zuwa katsina tare da shatara na arziki Arfah sister Afrah ma 2 months ya rage ayi aurenta a Sadiya zasu zauna da mijinta sai Fahad ya kusa kammala Masters dinsa yana U.S, Mommy da mami sosai suke zuminci a tsakaninsu, Yanzo Mommy babu ruwan ta yada duk yaro na kowa ne, gidanta fal da yan mata datake rik'ewa na yan uwa kowa kirki takemai kuma lfya take zaune da kowa cikinsu. </p><p><br /></p><p> </p><p> Bayan bikin Arfah ne gaba daya su suka wuce Umara, hadda su Mama, uncle Junaid, uncle, Kannan Daddy, anty Zulaiha wanan karan hadda Xainab da mijinta Muhammad da yaronsu Masjid, gasu Nana Azeezah,Inna Safeya da dai yan uwa da yawa, 2weeks sukayi duk suka dawo Nigeria amma banda Afrah day Abdulnaser Su zasuje New York, suka jona Ummie da yara sukuma suka harba gaba. </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p>Abdul na san Afifah kuma yana kula da ita haka itama kasancewar goyan Afrah yasa baya samun problem sam daka wajenta, Daddy, mommy Inna da sauran yan uwa kowa nasan barka da rayuwar auransu. </p><p><br /></p><p>Fatty ma Alhmdulillahi sai godian Allah bata problem, haka Hafiz ma Alhmdulillahi </p><p><br /></p><p>Afrah kam ita ta dabance kulin mijinta kara santa da k'aunar ta yake, haka dangin mijinta, itama kyauta masu take sosai ba kadan ba gami da girmamasu, Afrah kam tayi kudi takuma yi suna sosai Abdul ma haka Mami kulin cikin Alfari take dasu haka Daddy da Mommy ma. Komai dai masha Allah. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Alhmdulillahi</p><p> Alhmdulillahi </p><p> Alhmdulillahi </p><p> Alhmdulillahi </p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>_anan nakawo k'arshen book dina watou D'AN HAKKIN DA KA RAINA... Allah sadamu da Alkhari sa Amen, Laifin da nayi cikinsa Allah kayafeni, kuma readers kuyaceni, ALLAH sa mudace AMEEN_</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*gaisuwa mai yawa da dukkan Writers na online Allah kara baseerah, fasaha, da hazaka, ya karemu daka dukkan sharri na fili Dana boye AMEEN*</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *MASOYANA banda bakin gode maku sai dai Addu'a wallahi, nagode nagode sosai Allah bar zuminci yakuma karemin ku kulin da koda yaushe nagode sosai*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*GROUPS kuna da yawa gskia, duk na gaisheku kawai*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Bazan taba mantakuba*</p><p><br /></p><p>Ummu-Adulnasee </p><p>Aunty Maijiddah musa </p><p>Aunty Rabiela (Maman arfat) </p><p>Mommana Rabi'atu SK maashi</p><p>A'ISHA A Moh'd (aunty) </p><p> AntyBillyn Abdul </p><p>Ummie auta</p><p>Aunty Baraka </p><p>Mom amir</p><p>Mman Heeshmer </p><p>Aseeya Bakori </p><p> Wallahi kuna da yawa sosai much love for u all</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Biebie Dee*🌸🌹</p><p>07039732859</p><div><br /></div>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-19272740045595570142021-01-24T06:20:00.001-08:002021-01-24T06:20:08.480-08:00Mafarki na complete hausa novels<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-z8bkFn95iYM/YA2B7PLdH0I/AAAAAAAAJgU/aBso4Tld7eAWBNwCCF7WPVBX7KjkOw9qACLcBGAsYHQ/s2048/Mafarki-na.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="Mafarki na complete hausa novels" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-z8bkFn95iYM/YA2B7PLdH0I/AAAAAAAAJgU/aBso4Tld7eAWBNwCCF7WPVBX7KjkOw9qACLcBGAsYHQ/w320-h248/Mafarki-na.jpg" title="Mafarki na complete hausa novels" width="320" /></a></div><br /> 👰🏼 *MAFARKI NA* 👰🏼<p></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Written by*💅🏻💅🏻</p><p>*Salmah Ali Wada*</p><p> *(Aunty)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS (P•M•L•W)*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Both on true life story*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Page 1🔚</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dai dai matan fada road danja ta tsayar da mu,garin leke leke irin nawa Idona yakai kan wata fara mota wani had'ad'd'en guy ne a ciki wayyo Allah na! Looking him handsome guy,</p><p><br /></p><p>Da Sauri na kuma gyara glass din dake idona, nan naga ya kira wani mai saida counter ya siya dai dai nan danja ya bamu hannu cikin nutsuwa yaja motar sa inda me adai-daita mun shima yaja, wayyo amma guy din nan ya tafi da tunanin Salmah wayyo!</p><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p>Har muka fara tafiya idona be bar kallon sa ba,sai da muka hau play over sannan ya bacewa gani na,</p><p><br /></p><p>Wata nannauyar ajiyar zuciya na saki,murya mai adai-daita ne ya katse mun tunanin da nake "wai bamu zo inda zaki sauka bane",</p><p>" yi haquri gaban kad'an zan sauka"</p><p><br /></p><p>Haka na shiga gida jiki na ba k'wari,Umma na iske a falo tna waya sai da ta gama sannan nace mata "Umma na dawo" "to kin gama komai" </p><p><br /></p><p>"Gobe zan koma" " to Allah ya bada sa'a" nace "Ameen"</p><p><br /></p><p>Na tashi zan tafi naji Umma tace "ke" tsayawa nai "lafiya kuwa na ganki wata iri kuma sai wani murmushi kike kamar wadda tai gamo"?</p><p><br /></p><p>Hmm Umma ke nan gamo nai amma na alkhaeri na fad'a a raina amma a fili murmushi kawai nai mata nace " lah Umma bakomai" kawai weather d'in garin ne tai min dad'i "to maza kije ki d'ora girki ni meeting zan fita before 2:00pm" naga ma komai amma gaba d'aya yinin ranar da tunanin unknown guy na huni.............. </p><p><br /></p><p> </p><p> ❤❤</p><p> ❤</p><p><br /></p><p>" waya na ne yai ringin da sauri na d'auka ganin me kira na,king of my hrt sunan da nasa masa,</p><p><br /></p><p>" haba Salmah Queen kin san kuwa ynda na matsu lokacin yazo amma ki zance a d'aga kuwa, tab Ae ko ma mene k'ya karasa a gida na kwana nawa ya rage"</p><p><br /></p><p>Cikin muryan shagwab'a nake magana "kasan had'a aure da karatu kuwa da wuya" " bawani nan anjima,zan kawo miki invitation card d'in sannan zan ma driver magana sai ki fad'an tym d'in da zai dinga zuwa" </p><p><br /></p><p>"Tom shikke nan baby sai anjima"</p><p><br /></p><p>Kashe wayar nai tare da rungume ta ina wani murmushi ni kad'ai nasan irin son da nake ma Prince d'ina</p><p><br /></p><p>Haka aka fara shirin biki gyara ba Wanda ban sha ba har wani kyau na k'ara sai dai kash! Gaba d'aya Umma tace na cema prince ya daina zuwa .</p><p><br /></p><p>Tun ranar laraba aka fara kamu wayyo kar kuso kuga irin kyaun da Salmah tayi masha Allah,</p><p><br /></p><p>Daman ga Salmah slim beauty,with chocolate skin,hmm pinky lips, and sexy eyes, duk Wanda ya ganta sai ya kuma kallon ta gaba d'aya prince jiyake kmar ya d'auke sabida kyaunta</p><p><br /></p><p>Haka akai ta party iri iri like fruity day,Fulani day,mother's night, sisters day da dai sauran su ranar lahadi da misalin karfe 11:00 dubban mutane suka shaida auren masoyan,</p><p><br /></p><p>Tunda naji maroka suna fad'a na fara kuka,</p><p>Baby kwata ce take tsokana ta "amarya d'auko Riga kin zama d'aukko hula" Ae kuwa tuni kuka na ya kara girmama take suka daina suka dawo bani haquri a haka har yamma tayi,</p><p><br /></p><p>Aunty zainab k'anwar ma ce ta shigo "wai ina Salmah ne har yanxu baki shirya ba" </p><p><br /></p><p>"Aunty kinga Tun d'azu take kuka tak'i tashi ko abinci tak'i ta ci mama" ta fad'a</p><p><br /></p><p>Cikin sigar lallashi aunty Zainab tasa nai wanka ta shirya ni cki wata exclusive supper wax sky blue ta nad'e ni da blue din lafaya sannan ta feshe ni da Arabian perform, tuni nai kyau</p><p><br /></p><p> waya k'awaye na suka Ciro suka fara yimin photo duk da fuska ta a rufe take amma naji suna fad'an kyaun da nayi</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nan akai min fad'a sannan aka wuce dani gidana</p><p><br /></p><p>Haka jama'a sukai ta santin gidan wata mata naji tana magana " kai amma gidan ya dace da ita gata mai kyau gidan ma haka" "Ae kuwa wata ta cafe da mijin ma mai kyau fatan dai Allah ya bada zaman lafiya" suka amsa da Ameen.</p><p><br /></p><p>Haka aka watse aka barni ni ka dai tsoro duk ya cika ni ga ynwa da tun safe ban ci komai ba,</p><p><br /></p><p>Motsin tafiya naji da sauri na kuma rufe fuska ta cikin muryar sa me dad'i yai sallamah a hankali na amsa</p><p><br /></p><p>Gefe na ya zauna ya salam k'amshi turaren sa naji Wanda nake mutukar so</p><p><br /></p><p>Zame min lafayar Dana rufe fuska ta yayi "tsarki ya tabbata ga Wanda ya halicci wannan surar, amma baby love meyasa kikai wannan kuka haka kamar wadda za'a kai ki gidan mak'iyin ki"?</p><p><br /></p><p>Cikin ragowar kuka na nace" ni Umma " too "lallai an fad'a miki cewar bazaki dinga zuwa bane"?</p><p><br /></p><p>Nan yai ta lallashi na, da kansa yaje kitchen ya d'aukko plate da cups kajin da ya siyo ya zuba sannan ya zuba fresh milk yago kazar yayi " to Salmah queen bud'e bakin" kau da kai nayi " "kai me kike nufi ne?"</p><p><br /></p><p>"Ni na koshi" "ban yarda ba, bari naji Ae zan gane in baki ci abincin ba" ciki na ya shafa yar naji jiki na yayi,</p><p><br /></p><p>"Kin ji cikin kamar bakomai a ciki koma kice kin koshi mazabud'e bakin ki kan nai miki dura" </p><p><br /></p><p>A hankali na bud'e ya kai hannu zai sakan ke nan......</p><p><br /></p><p>Umma ta girgiza ni da karfi "ke wannan wane irin bacci kike haka tuntuni anyi sallahr asuba </p><p><br /></p><p> firgigit na zabura na tashi daga nannauyyan bacci </p><p><br /></p><p>"Kalli karfe nawa ynx Tun d"azu nake kiran ki amma naji ki shiru" a hankali na kalli agogon dake dakin 6:45 </p><p><br /></p><p>"Kiyi haquri umma" "ke tafi ni tun jiya na rasa meke damun ki, maza kitashi kiyi sallah ki gyara gidan ni, zan huce su husna skul" </p><p><br /></p><p>K'arfe 7:30 Umma suka fito</p><p>" Umma Allah ya kiyaye Hanya" "ameen"</p><p><br /></p><p>Nan na gyara gidan na shiga wanka cikin wata doguwar Riga ta material orange da green na shirya na yfa green din mayafi da takalmi sai na dauko orange din jaka na zuba credentials dina na fita skul</p><p><br /></p><p>Haka ma shiga skul department din mu na tafi ba mutane a ciki office d'in sectere na shiga </p><p><br /></p><p>Yana miko min wani file naji wani k'amshi ya doki hanci na ban dago ba na cigaba da abin da nake,</p><p><br /></p><p>"Sannu malam" naji anfada cikin wata murya mai dad'i "yawwa Ahmad kashigo ne" "eh wllh" juyowar da zanyi wazan gani ya salam guy d'in jiya da nagani ne,</p><p>Ina kallon sa naga yana kallo na "sannun ki" ya fad'a yana min murmushi " a hankali nace "yawwa"</p><p><br /></p><p>Parlon office d'in na fito na zauna a d'aya daga cikin kujerun office d'in ina k'ok'arin had'a takardun nawa zama yai kusa dani da yake a 3seater na zauna "can I help u"? Murmushi kawai nayi " muga credentials d'in" k'arba yai yna had'a min ta gefen Ido nake satar kallon sa,</p><p><br /></p><p>Yana yi yana min baya ni ina d'agowa karaf muka had'a ido dashi a kunyace na sunkuyar da kai na, "OK zaki iya submitting d'in sa koda yake bari naga" ya tashi yashiga ina beyi dashi nan yai submitting ni kuma nai signing sannan muka fita </p><p><br /></p><p>"Nagode da kulawan ka" "ah bakomai" ynx sai ina"? Ya tambay "gida zan tafi" Tun yanxu bazaki zauna muyi hira ba" uhmmmm nayi wani murmushi Wanda ni kaina nasan in nayi yana tafiya da hankalin Wanda naima, </p><p><br /></p><p>"Ai zan yi girki ne kar Umma tadawo ban gama ba" " OK "</p><p><br /></p><p>Nan muka tawo " to zo nakai ki mana" da sauri na kalle shi wani killer smiling yayi min "irin wannan kallo haka sai kace wadda nace zan sace" a'a kayi haquri nagode" nan muka fara tafiya zuwa bakin gate "sunana Ahmad" muka had'a ido hmmm "nace name" </p><p><br /></p><p>"What of you"? " Salmah "</p><p>*Salmah queen*" ba zato ba naji ya fad'a wallhi gabana har faduwa yayi,tsinkar muryar sa nayi yace " amma kamar ke nagani jiya" anyya kuwa kawai nace" Dan har ynx ban gasgata abinda kunne na yaji ba wai *Salmah Queen*</p><p><br /></p><p>Banga wannan tunanin ba naji "tom Salmah queen can I have your number"? </p><p><br /></p><p>Kallon sa nai " ko rowar za'ae min?" "A'a" lalubar aljihu yayi "af kinga wayar yana mota ban taki naga" ba musu na mika masa number d'in sa yasa sannan yai dialling tana shiga ya miko min " to Salmah queen sai minyi waya" "to nagode fa" na shiga adai-adaita shi kuma ya koma cikin skul.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ina komawa gida nai Sauri na fad'a kitchen Dan 1:00yayi waya na na dauka na tura masa da message Dan nagane number d'in</p><p><br /></p><p>_Aslm thank for your concerns Allah ya kara zumunci_ </p><p><br /></p><p>Ko wayar ban ajiye ba kiran sa ya shigo "Salmah queen kinje gida lafiya" muryar sa ta doki kunne na "lafiya lau"</p><p>"Pls I will call u lttr zan yi sallah" " to Ae mana addu'a"</p><p><br /></p><p>"Kar ki damu za'ayi" ya kashe wayar </p><p><br /></p><p>Tundaga wannan lokacin muke wani lafiyayyen mutunci</p><p><br /></p><p>As usual ya kira ni da Salmah queen "am not deserve it fa" nace</p><p> "Why you say dat wllh kin cancanci fiye da haka,ni ba wannan ba zan zo gidan Ku sabida akwai maganar da nake so muhi mai muhimmanci" </p><p>" tom shikke nan Allah ya kawo ka lfy"</p><p><br /></p><p>Ran da yace zai zo ban sami cikkaken bacci ba sabida d'auki da farin ciki,</p><p><br /></p><p>Ranar da zai zo rnar Friday haka nai k'walliya kamar ba gobe cikin wata atamfa pink da purple masha Allah ni kai na san nayi kyau ina zaune ina jiran zuwan sa amma gabana har faduwa yake misalin 5:00pm ya kira ni yace ya iso....dammmm kirjina ya buga..........</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*I wish my dream are converting to reality* </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>ya Allah ka taimaken haka na fita kirjina na bugawa kamar fado koda me yazo min ohooo cikin sallama na isa inda yake yayi kyau yana sanye da k'ananan kaya..........</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nan na kawo k'arshen wannan takai taccen littafin nawa *Mafarki na* both on true life story </p><p><br /></p><p>Abinda nai dai dai Allah yabani lada Wanda nai ba daidai ba Allah ya yafe min,fatan sako na zai fadakar da ku,</p><p><br /></p><p>Ki kasance mai aji a matsayin ki na 'ya mace ba daga kinga namiji in kinji kina son sa ki fada masa ba,bance hakan yna da illa ba amma kusan halin namu na yanxu,bakowa ne zaki ce kina son sa yai miki kyakkyawar fahimta,kiyi addu'a kinemi zabin Allah indai har alkhairi ne sai kiva yazo miki da kansa in km ba alkhairi bane Allah ya musanya miki da Wanda ya fishi</p><p> Allha ya bamu abinda yafi alkhairi Ameen•</p><p><br /></p><p>*Taku har kullum*</p><p>*Salmah Ali Wada*</p><p> *(Aunty)*💅🏻💅🏻</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Love you all my heart!!!😍😍😍😍😍</p><div><br /></div>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-72005788176698634922021-01-20T09:35:00.003-08:002021-01-20T09:35:41.677-08:00RAYUWAR-WASU HAUSA NOVELS<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-DGAk9-G4wtE/YAhpe8hVDNI/AAAAAAAAJgA/sblDV1lmBG46DuEKo3nNb_BCNwCOcF89gCLcBGAsYHQ/s2048/RAYUWAR-WASU.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="RAYUWAR-WASU HAUSA NOVELS" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="310" src="https://1.bp.blogspot.com/-DGAk9-G4wtE/YAhpe8hVDNI/AAAAAAAAJgA/sblDV1lmBG46DuEKo3nNb_BCNwCOcF89gCLcBGAsYHQ/w400-h310/RAYUWAR-WASU.jpg" title="RAYUWAR-WASU HAUSA NOVELS" width="400" /></a></div><br /> [3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣<p></p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>```NA........ ✍🏼```</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Assalamu Alaikum wa rahmatullahi wa barakatuh.... I'm back again💃🏻, Banyi wannan novel din dancin zarafin wani ko wata ba.. Idan yazo daidai da halinki to ki gyara...*</p><span></span><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••._</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p> ```I'M PROUD OF YOU MY DEAR... I LOVE YOU SO MUCH sweety, KODA DUKA LITTAFIN SUNANKI ZAN AMBATO BAN BIYAKI BA```</p><p><br /></p><p> *❣Bilkisu bk* wannan page din nakine ke kadai, I'm truely blessed to have you in my life, Ina matukar farin cikin dawowarki...Allah ya Kara maki lafiya Sweet heart 😍</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*PAGE 1➖5*</p><p><br /></p><p>Wata yarinyace da bazata wuce shekaru shabakwai da haihuwa ba zaune a daki tayi tagumi se kuka takeyi, hankada labular dakin da taji anyine yasa tai saurin dag'o kanta, ido hudu sukai da wata mata wacce ake Kira da Inna. </p><p> Inna harararta tayi tace" ke Dan ubanki bazaki fito kimun wanke wanken bane ko ni kike jira nai miki? Yarinyar nan mai suna husna ta mik'e tace" inna kiyi hakuri yanzun nan zan fito, karma ki fito nidai na fita kuma Kafin na dawo ki tabbatar kin gyaramun ko ina a cewar" inna..</p><p><br /></p><p>Inna na ficewa husna ta sake wani irin kuka me ratsa zuciya tace" kaico na, na shiga uku, yanzu haka rayuwata Zata kasance kullun cikin bakin ciki! Ta zurfafa a tinani taba ba shine mafita ba hakanan ta tashi tai abun da inna ta umurceta tayi, tana cikin yine sai ga wata yarinya ta shugo da sallama cikin natsuwa tace" yaya husna ai da kin bari idan na dawo sai nayi, husna ta kalleta tace" uhm Kedai khadija Kije ki cire uniform dinki Dan inna ta shugo taganki anan kinsan bazataji dadi ba, khadija ta tabe baki tace" to shikkenan husnah, khadija tayi daki itakam husna taci gaba da aikin da takeyi, </p><p><br /></p><p> Khadija na daki after ta cire kayan makaranta ta zauna itama tace" wai me yasa inna take hakane? Kenan yanzu wasu idan basu suka haifeka ba sesui ta ba mutun wahala abun da babu kyau..khadija taga bazata iya zama ita kam ba tuni ta fito tasama husna hannu suka cigaba da aikin tare, suna cikin yin sharar tsakar gidan ne inna ta dawo taga khadija wani ashar ta zuba sannan tace" ke husna bance ke kadai zaki aikin ba Dan me naga khadija nayi kuma? Tayo kanta da gudu ta fara duka, khadija na cewa" Dan Allah inna ki mata hakuri wallahi ni nace zan tayata ba ita tace" nazo ba... Inna bata saurareta taci gaba da dukan asma'u (husna) seda ta gaba mata ligis sannan ta waigo kan khadija tace" in k'ara ganinki kina wani abu a gidan nan nasan me zan miki, </p><p> Khdijat tace" inna kiyi hakuri ni macene dole nayi aikin cikin gida, inna tai mata wani irin mugun kallo tace" _bazakiyiba tunda ubanki ai Kasa hakura yayi Kafin na haifoki yaje ya samo mana mugun iri, Mayyar yarinya_ *karku manta da wannan kalmar na samo husna* agaba zasuji ya akai aka samo husna har tazo gidan...</p><p><br /></p><p>Husna na dok'e duk abun duniya ya isheta ga kuma maganar da inna tayi wai itace mugun iri, wani ajiyar zuciya tayi tace" a zuciyarta wallahi baba na dawowa ita dole ma tabar gidan nan., inna da khadija kam daki suka shige inna ta ciro Dan tsiran data siyo taci ta mik'a ma khadija tace" ungo kice, khadia ita Sam abun da mahaifiyarta takeyi bata kyautawa, shuru kawai tayi tace to inna na gode amma ina na HUSNA? wani harara da inna tai mata yasa da sauri ta sa tsiran a baki tanaci ne amma bawai don ranta yaso ba.. </p><p><br /></p><p> Husna kuwa ta gama aikinta tsab ta sama waje ta zauna a tsakar gida cikinta se Kiran churuma yakeyi, iyayanta ta tuno ko suna raye ko suna mace Allah kadai yasani..addua tai musu taji gaba dayama yunwar ya tafi.. Tana zaune ne Sega baban khadija ya shugo da sauri yace" asma'ul husna yana ganki a waje ko basanan ne? Inna najin muryar mijinta ta fito tace" kasan husna bameson hayaniya bane nayi nayi da ita ta shugo wai iska take ji, Husna duk mamaki ya kmata yanzu yanzu makirar matarnan har ta shirya Zance, Baba yace" ok to shikkenan aka wuce wajen....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Haka rayuwar husna ya kasance kullun cikin bakin cikin Gashi batasan kowa nataba, kotayi yunkirin guduwa sai tace" inta tafi yanzu inama Zata dosa tunda ba kowa ta sanine, nan ne dai yazammata wajibi ta zauna da dadi ko ba dadi.. </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Kuci gaba da biyoni*</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>```NA........ ✍🏼```</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••._</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>Dedicated this page to you my love, my twieny, my happiness, my jinin jiki my everything *EMNOOR AHMERD DON* bby ki huta domin kina tashe a hrt din ummiey Xeey😍</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*PAGE 5➖10*</p><p><br /></p><p>*TOSHEN LABARIN*</p><p>Asma'u (Husna) dalilin zuwanta gidan baba (kabir) </p><p> mahaifin asma'u (husna) Alhaji aminu Dan garin kano a wata unguwa kurna, Yanada mata guda daya maryam sunyi auran soyayya har Allah ya azurtasu da yarinya guda daya asma'u ana ce mata husna, sun bata cikakkiyar kulawa da tarbiya daidai gwargwado har takai 10years lokacin ta fara girma, Ananan Ananan se wata rana Alhaji aminu da matarsa maryam suka yanke shawarar kawo ziyara garin kaduna, suna cikin tafiyane Alhaji aminu yaga gittawar wani shanu kan kace meye nan take sukai hatsari, subhanallah, </p><p> Ashe shanun nan ba shanu bane na yan cultism ne (yan shan jini) ne, suna hatsarin mutane suka taro kan kace meye Wanda suka haifar da hatsarin har sun dauke asma'u sunyi gaba.. Mutane kam duk ba Wanda ya lura, kowa ta ceto ran Alhaji Aminu da maryam akeyi, direct asibiti aka nufa dasu dan cikinsu ba Wanda yake hayyacinsa, seda kusan sati daya sukace" ai akwai wata yarinya batafi 10 years ba, yar suce, Asibitin ya dauka ba'aga yarinya ba, wanda suka kawosu sukace basuga ko wace yarinya ba, nan Ciwo ta dawo musu sabuwa na rashin yarsu Husna da sukai, da yake masu tawakkaline hakanan suka hakura amma kullun suna zullumin ko zasu ganta, kuma kullun cikin rokan Allah suke kuma aka tayasu da addua Allah yasa a ganta</p><p><br /></p><p>Wanda kuma suka sace husna, antafi da ita gidan yankai kai amma Allah be basu ikon aiwatar da abun da sukai niyya ba, ogan ne yace" karsui mata komai yarinyar tana da kyau yace" a kawota dakinshi, nan aka kawota da yake mahaifiyar ta tana Dan koya mata addu'o'i tana shiga dakin sukai Ido hudu da ogan, addua tayi yace" ga waje ta zauna, ta zauna batabar fadin _innalillahi wa inna ilaihi rajiun ba da hasbunallahu wa ni'eemal wakeel_ shi kanshi yasan yarinyar ta fi karfinshi Dan ajikinshi shima yaji.. Dan tabbas addu'a ba karya bane, Kasa komai shi ma yayi yace" akawo mata abinci, aka kawo husna ta kafe ita fa batajin yunwa, nan aka kawo mata abun sha nan ma tace" bazata sha ba... ogan yaji yarinyar tamai Dan ko ba komai she's damn beauty *tanada kyau* ya kalle asma'u da hausarshi da bata fitowa sosai yace" mene sunanki? Ta kyallale da dariya tace" ba haka ake fada ba menene sunanki akecewa" ogan yai mamaki matuka yanda yarinyar take magana, yace" yes tell me tace" sunanan Asmau ana cemun husna" yace huzna? Tace" a a husna, yace" ok na rik'e, ita sam tama manta da halin da take seta tino da mahaifiyarta ta fara kuka tana cewa mamana, mamana, tunda ta fara Kiran sunan mamanta ogan yaji gaba daya hankalinshi ba'akwanceba, nan take ya Kira wasu mutane wai a kaita wani dakin! Nan sukazo suka dauketa suka kaita dakin da ogan yace"</p><p><br /></p><p>Bayan sun kaitane suka dawo wajen ogan sukace" Oga munyi abun da kace muyi yanzu me kkeso ai ma yarinyar? Ogan yace" no please don't do any bad thing to her, ko ajiyemun ita ina son yarinyar nan, sunyi mamaki sosai yanda yarinyar ta shiga ran Oga GATA ba budurwaba balle sui tinanin wani abu, daya daga cikinsu yace" Oga Kodai zakai keeping dinta ne har ta girma se ka dinga amfani da ita? Shiiii Oga yace" kar ka sakemun irin wannanar maganar, intact ni kaina bansan mezayi da ita ba just yarinyar tamun ne, </p><p> Sukace okay nan ya ciro kudi ya basu yace" duk wani kaya na wasa Dana sawa da su sweet duk kuje ku siyo mata please... Sukace" angama Oga, suka tafi kasuwa yi mata siyayya</p><p> Itakam husna ganin dakin duk ta bi ta rude tace" na shiga uku, taga wani blanket Me kyau a kan gado taje ta taba taji mutun, wani ihu ta saka wacce ke baccin itama ta farka suka fara ihu duka..jin ihun da Oga yayine ya fito ya shiga dakin ya gansu, tsaki yayi" yace" ok daki daya aka hadaku? Ok ku zauna kunji ba abun da zai faru daku, yai ficewarsa, </p><p> Dayar da yake tafi husna wayau da shekaru tace" kema satoki akai ko? Husna ta daga kai tace" eh kema haka? Dukansu dai eh ne amsarsu, nan suka fara kuka dayar me suna khairat tace" ki dena kuka ni na kusan 1 year anan abun da nakeso dake shine kita addua Allah yabamu ikon fita daga nan gidan, ai kin iya addua ko? Husna ta daga kai tace" eh tace to shikkenan dukansu suka shiga innalillahi wa inna ilaihi rajiun.. Suna zaune Sega Wanda oga ya aika dinnan sun kawo mata kayan da ogan ya aikesu</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>```NA........ ✍🏼```</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••._</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>Dedicated to all my fans # I love you wujiga wujiga❣</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*PAGE 10➖15*</p><p>Suna zaune ne Sega Wanda Oga ya aika dinnan suka kawo mata kayan da ogan ya aikesu, suna ajiyewa suka fita, khairat ce" ta bude kayan tai tsaki tace" ta Allah ba nakaba itadai husna bin khairat da ido kawai takeyi</p><p><br /></p><p> Bayan sati daya Alhaji aminu da matarsa har har sunji sauki sun koma gida, amma tamkar marasa lafiya saboda an rabasu da farin cikinsu, inama ana saida da a kasuwa da sunje sun siya, asma'u ita kadai ce farin cikinsu Gashi yanzu bata a gidan! Kowanninsu kana gani kasan ba cikin kwanciyar hankali suke ba, amma to ya zasui? Hakanan suka hakura! </p><p><br /></p><p> Bangaren su Husna kuma satin ta daya a gidan, kullun da dare sai Oga yazo ya zaunar dasu ita da khairat sui ta hira, Yau ma kamar kullun suna cikin daki sai ga ogan nan ya shugo ya samesu zaune sunyi shuru ya kalla khairat yace" akwai abun da kuke bukatane? Khairat tai banza da shi, Husna ce me karfin hali tace" eh munaso muje gidan iyayan mune, Ogan a fusata ya kalleta a zuciyarshi yace" badan ina son yarinyar nan ba da sai ta sani cikin daren nan, yana tinanin zuci ne ta kara da cewa Kaji please ka kaimu wajen iyayanmu, kallonta yayi yace" bazaki zauna da niba a nan gidan? Kada kai tayi alamar a'a sannan ta fasa kuka nidai ka kaimu wajen su mamanmu, Bacin rai yaji a fusace ya Kira ma'ai katanshi yace" wa ennan yaran sunaso su Tona mana asiri kui maza ku fitar dasu a nan gidan, nan take suka buga ma khairat da husna kai dukannsu tsintar kansu sukai a waje</p><p><br /></p><p>Khairat ta ganta a wani daji da gudu take ta tafiya ga dare yayi har Allah yasa ta fito cikin gari ta sama wasu mutane tace su temaketa, nan ta basu labarin halin data shiga sukace Insha Allah zasu temaka mata har taje gidan iyayanta.... </p><p><br /></p><p> Ita kuma Husna koda ta tsinta kanta a waje ga dare yayi, tama rasa ina zataje, kuka taketayi me Susa zuciya, wani Babban tifa ta samu a bakin titi ta shiga karkashin tifan (motor kwasan yashi) ta cire zaninta ta kwanta ta lulluba abun tausayi, bacci takeyi me dadin gaske dan Allah ya temaketa tabar gidan mugun mutumin nan... </p><p><br /></p><p> Gari ya fara wayewa masu Motor tifa sunzo zasu dauka motarsu su wuce wajen aiki, sai daya daga cikinsu yace" kamar nunfashi nakeji ko? Dayar yace" wani irin nunfashi kuwa, dayan yace" wlhi kuwa mudai duba, aiko suna cikin haske haske suka hasko husna a karkashin motar, Allah sarki dayan yace" haskata da sukai Husna ta tashi firgigit, tana dan Allah kar ku yankani kuyi hakuri, daya daga cikinsu ya daka mata tsawa yace" ance miki mu yan yan kan kaine? </p><p> HUSNA a rude tace" kuyi hakuri, ta fito sumi sumi duk ta zama abun tausayi, dayan yace" Meya kawoki nan wajen?</p><p><br /></p><p>Kuka sosai takeyi nan ta basu labarin komai, sun tausaya mata matuka sannan sukace Allah ya raba na gari da mugu tace" Ameen, dayan yace" yanzu ya za'ai kenan? Daya yace ai mu kaita wajen me unguwa kawai dan mu bamusan ya zamui da ita ba, kuma kaga bedace ba sam mu riketa a hannunmu... </p><p> Haka ko akai suka Kama hannun husna sai gidan me unguwa</p><p><br /></p><p>Sallama sukai sanan suka shiga wajenshi, nan suka sanar dashi ga abun da yake faruwa, Me unguwa beyi Kasa a gwiwaba ya tambayeta tace" tabbas hakane ya k'ara umurtan ta data bada labarin da kanta, tsab ta fada. </p><p><br /></p><p> "mamaki ya kamashi, nan aka baza a radio duk Wanda yarshi ta bace" yazo ko itace, kowa yazo yace ba yarshi bace, Anyi cigiya har an gaji, har Allah yasa Baba Kabir mijin inna yazo ya roka alfarma a bashi ita duk da beda hali sosai amma Insha Allah zai kula da ita kuma duk randa aka ga iyayanta zai bada ita dan be taba haihuwa ba a rayuwarshi</p><p> Me unguwa da sauran mutane sukace to shikkenan Allah ya tayashi riko yace" ameen</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*_To kinji dalilin zuwan husna gidan baba Kabir kenan_*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Xeexeeee✍🏼</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>*FA'IZA ANFA* ina tayaki murnar KAMMALA littafinki me suna *D'AN FASHI* Allah ya Kara basira dear faxeey sai munjiki a book dinki na gaba</p><p><br /></p><p>*PAGE 15➖20*</p><p><br /></p><p>_CIGABAN LABARIN_</p><p>baba yai shigewarsa daki, Inna ne ta leko ta ga Husna still tana tsakar gida, wani harara tai mata tace" yar matsiyata kawai, maganar nan ba karamin sosa ma husna zuciya yayiba amma seta share dan she can do nothing to her</p><p><br /></p><p>Baba ne ya kwalla ma husna Kira, tazo cikin natsuwa yace" tun rannar banji Kin karamun maganar makarantar ba ko bazaki koma bane? Susa kai tayi tanaso tace wani abu amma tsoron inna take ji dan tace ba makarantar da Zata koma, sedai yarta ce khadija zatai makaranta,</p><p> Baba ya kara magana yace" inajinki, zatai magana kenan Sega inna ta shugo tace to me kuma take ce maka? Baba Kabir dariya yayi yace" ba abun da muke cewa maganar makaranta mukeyi! </p><p> </p><p> Inna taba baki tayi" tace to yan Boko, yanzu wannan katuwar yarinyarce zakace Zata koma boko ai tunda tayi js3 ta gama makaranta kuwa, salon taje ta dakko mana abun magana! </p><p> Maganar ta batawa malan kabir rai yace" Kinga a kullun kidinga wa mutun kyakkyawan zato wannan wace irin magana kikeyi haka? Nan Inna ta fara sababi wai ba Dama ta fada gaskiya akan wannan yar yarinyar har malan zaizo yana fada mata magana, nan ta shiga kuka kuma tace" nasan a rina wai an sace zanin mahaukaciya ni nasan kafison ta akan Khadijat, tunda Gashi tun Kafin mu sama khadijan ai kaje ka Kasa hakuri ka samu wannan shegiyar yarinyar, sannan ta fita, Da yake Malan yasan halin nata, Allah ya kyauta yace" ita ko Husna na tsugunne tace" dan Allah baba ina neman alfarma</p><p> Yace" to inajinki, kabarni na bar gidan nan bazan iya zama ba a cewar Husna, baba kallonta yayi yace" Husna kiyi hakuri Inanan tare dake kidena damuwa da halin wannar matar kinajina ko? Husna to kawai tace dan tasan bazata iya ma baba musu ba.. Mikewa tayi ta koma tsakar gida abun tausayi</p><p><br /></p><p>Yamma nayi ta shiga daki tasa uniform dinta na islamiya tai tafiyarta, tana zuwa ta hadu da kawarta me suna Zainab, Zainab tace" naganki wani iri menene? Husna tace" wlhi ki bari kawai duniyar nan ta isheni, banjin dadin komai! Zainab tace" husna kiyi hakuri duk tsanani yana tare Da sauki, kici gaba da addua kawai kinji! husna tai murmushi tace" sai yasa nakeson kasancewa dake kullun sai kin farantamun rai Zainab tace" Lol ba komai mu biya karatu Kafin malan ya shugo</p><p><br /></p><p> °°°°°°°°°°°°°°°</p><p>Bangaren Iyayan husnah kuwa duk tinaninsu yanzu kusan 4years husna ta mutu, har Allah ya k'ara basu wata yarinya suka maida sunan sunan husna,</p><p><br /></p><p>ana ce mata husna karama..cikin ikon Allah yarinyar tsab husna babbancinsu kadan ne husna babba farace while husna karama kuma baka, har sun cire ri gaba daya kullun sedai suita mata Addua.... Wannan kenan</p><p><br /></p><p> ➖➖➖➖➖➖➖</p><p>Bayan Husna ta dawo daga islamiyane, tana shiga ko zama batai ba Gashi ta gaji, inna tace to malama ga kayan miyanan sai kije ki jajjaga ki daura wa mutane girki kuma kafin magrib kin gama, wani takaici Husna taji tace" hmm Wannan matar bazata barni na huta bane hakan, kullun aiki, bakomai Allah ka sakmun, nan na cire kaya tai maza tazo tai abun da inna tace...</p><p><br /></p><p>Bayan ta gama ne tayi sallah tai azkar dinta tana zaune akan sallaya, sallamar wani yaro sukaji wai ance" Husna tazo, karaf a kunnan inna, fitowa tayi tace" kaje kace mai tace bazata zoba, yaro ya fita yaje ya sanar da abun da aka cemai, </p><p><br /></p><p> Inna kuwa binta da kallo tayi tace" to yar iska, ba sai kince yazoba aurar dake zamui mu huta, tun yanzu kin fara Kiran maza suzo miki ko?</p><p> </p><p> Gaban husnah ne ya fadi tace"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*PAGE 20➖25*</p><p><br /></p><p>Gaban Husnah ne ya fadi tace" wallahi inna ni bansan waye yazo ba, inna takai mata duka tace" rufemun baki yar banzan yarinya, tun kina karamar ki zaki lalace, itadai khadija tana daki tanajin abun da mahaifiyarta takeyi amma ba yanda ta iya shuru tayi dan bata da ikon da zatai mata magana.. </p><p> Husnah ta kara bude baki tace" kiyi hakuri inna, ana cikin hakane sai ga baba kabiru ya shugo ya sama Inna a gaban Husna yasan masifar ta takeyi, </p><p><br /></p><p> Baba matsowa kusa da su yayi yace" lafiya kuwa? Inna ta waigo cikin huce tace" ina lafiya anan wannan yar banzan yarinyar nan zataja mana abun magana yanzu wani ya kamota a waje wai ya ganta da wani suna iskanci... Gaban baba ne ya fadi yace" Anya kuwa? Husna tace" wallahi baba ba gaskiya bane tun dazu inanan wajen, nan danan inna ta fara salati wai yarinya ta kulla mata sharri wai tayi karya kenan! </p><p> Baba shima yasan ba gaskiya bane Yace" kedai wallahi kiji tsoron Allah, tun randa yarinyar nan tazo gidan nan kke nuna mata kiyayya karara, haba</p><p><br /></p><p>Maganar da baba yayi kamar ya kunna ta, Nan inna ta fara sababi wai ai dama ita tasan haka Zata faru, akan wannar yarinyar ze karyata ta, masifa take sosai ita kam husna in banda tsoro da gabanta nata fadi ba abun da yakeyi, tun da take bata taba ganin mace mai masifa da mugunta kamar inna ba, se masifar ta take, baba yace" Husna ta tashi ta shiga cikin daki shima yai wucewarsa daki, har ya shiga dakin kuma seya kwalla Husna Kira, yace" kome inna zatai mata kar ta ji haushi, haka *rayuwar wasu* yake, akwai su da mugunta Dan Allah karta dama kanta, To tace" sannan ta mike ta tafi dakin baccinsu ita da khadija....</p><p><br /></p><p>Tana shiga gado ta fada ta fara kuka sosai, tace oh ni Husna haka rayuwata Zata kasance? *Rayuwar wasu* gwanin sha'awa amma banda ni kukai tayi sosai khadija nata bata hakuri, Husna tace" ni bake kikai mun komai ba wallahi badan baba ba guduwa zanyi inje in karace rayuwata a wani wajen...Khadija ta rungumeta tace" dan Allah aunty kar ki tafi ki barmu, kiyi hakuri komai yai farko zaiyi karshe itama inna Allah ya dawo da ita kan hanya.. Husnah kawai jinta takeyi azuciyarta tace kayya, Anya kuwa?</p><p> Da tinani barkatai tai bacci, batai bacci me tsayi ba ta tashi ta fara nafilan dare, Sai da tai addu'o'i sosai sannan ta koma bacci shima bata dade ba aka Kira asuba..</p><p><br /></p><p>Bayan tayi sallahr asuba ne tana zaune wasu zafafan hawaye suka zubo mata, iyayanta ta tuna Gashi abun takaici kwata kwata ta manta inda suka, addu'a tai musu gari na waye wa ta tashi ta fara aikin data saba tun safe. Wanke wanke tayi sannan ta dauka Dan kamun Da sukesha ta ta dama bayan ta gamane ta dakko littafi tana karatun abun Da aka koya musu a islamiya </p><p> Koda inna ta hangeta zaune hararar ta tayi dai dai da lokacin da baba yazo zai fita</p><p><br /></p><p>Kallon husna yayi yace"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Kuci gaba da biyoni*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p> Ummiey Xeey</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p> *Dedicated to Umar M SHARIFF fans*❣</p><p><br /></p><p>*PAGE 25➖30*</p><p><br /></p><p>"Baba kallon Husnah yayi yace" yar baba karatu akeyi ne? "Eh tace sannan ta kara da cewa" dazu nazo gaisheka bakanan ina kwana baba" "amsawa yayi da lafiya lau ma'u, Allah dai yayi albarka kinji? Tace" Ameen sai ka dawo yai ficewarsa</p><p><br /></p><p> Innace na zaune a daki duk haushin as'mau ya isheta sallamar makwabciyarta taji, Inna ce ta fito dauke da farin ciki a tare da ita tace" marhaban lale, makwabciyarta tace" kaman zan wuce Ashe Kinanan! Inna tace" eh wallahi shugo daga ciki mana, tace" toh</p><p> Bayan sun gaisane makwabciyarta tace" Naga su asma'au har an girma har yanzu dai ba labarin iyayanta? </p><p> Inna ta taba baki tace" gatanan dai ni wallahi aminiya bason yarinyar nan nake ba fa, da akwai inda zan kaita wallahi da nakai, makwabciyarta tace" to me zai hana ki amfani da ita wajen neman kudi? Tunda dai Kinga ba juya komai kikeyiba ki dinga daura mata talla ko ko ki turata gidan aiki tane nemo maki kudi</p><p><br /></p><p>Inna ta washe baki taji labari me dadi tace" Allah ko aminiya? Kinga shikkenan Allah yasa a k'ara saceta kota hadu da ajalinta Kinga shikkenan na rabu da ala kakai, dadan haushinma malan duk yabi ya damu da ita kome takeso nan danan yake mata mu kuma oho.. Makwabciyar ta tace tabdijam adaidai ma kenan dan nikam banga amfanin zamanta agidan nan ba, in banda halin wasu yaushe dan waje zai fi dan gida? Gaskiya ki gagauta turata aikin ko tallan shawarace fa! Inna tace ai wannan shawarar yayi sosai aminiya na gode amma kai naji dadin zuwanki, makwabciyar tace" bakomai ai Muna tare ni zan tafi duk abun da kika yanke shine dai dai.... Inna tace to nagode har bakin kota ta rakata </p><p><br /></p><p> °°°°°°°°°°°°°°°°</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu, malan kabir da inna suna zaune suna hira, inna tace" Malan ina neman wani abu a wajenka, malan yana cin goro yace" ina jinki, inna tace" Dan Allah husnah ne naga tun da ba boko Zata koma ba me zai hana ta dinga zuwa wanke wanke haka? Malan zaro Ido yayi yace" gaskiya ban yardaba bada yawuna ba, duk kokarin da nakeyi bakya gani? Har sai kin tura ta aiki? In abun dadine ki tura yarki mana.. Inna tace" ai kaga khadija yarinyace, Malan yace haka ma husna yarinyace! </p><p> _Itadai husna tana daki tana jinsu, taso baba ya yarda dan a ganinta haka ne samun saukin ta_</p><p><br /></p><p> K'in yarda Da malan yayi, inna tashi tayi fuuuu sai cikin daki tace" to Wallahi se taje aikinnan, shidai malan bece mata komai ba, mamakin halayar matarshi yakeyi</p><p><br /></p><p> *Washe Gari*</p><p>Inna ce ta Kira khadija tace taje ta Kira mata saude (makwabciyarta) to khadija tace sannan ta fita, tana zuwa ta sanar da sakon da mamanta ta aiko ta, Saude tace" ok ki jirani mu tafi, basui minti ukuba se ga sunan sun dawo..</p><p><br /></p><p>Suna shuguwa, inna ta aika Khadija Dan bataso tasan maganar da zasu tattauna, lokacin itama husna an aiketa </p><p> Inna ce ta fara magana tace" malan yaqi amincewa fa! Saude tace" sai kikace mai mene? Inna tace" cewa nayi sai taje, saude tace" kash ai da bakimai musu ba amma hakan ma bata baci ba, yanzu abun Da zamui shine, dama akwai wani gida da ake neman me aiki ance in kawo yarinya kuma sukeso, gobe se mu kai husna, amma ko da wasa kar ki bari malan ya sani, inyaso koda wata rana ya tambaya ina take sai kice tana zuwa islamiyar safe ne tunda dama aikin 9 zuwa daya 1pm sukeso</p><p><br /></p><p> "Inna shewa tayi tace" kai amma naji dadi sosai sosai, saude tace" bakomai bari na tafi goben ma hadu!</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Ummiey Xeey*</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p> Where is my *Aishan Umma*... Your page is here. Tnx for your love & support Allah ya barmunke 💋</p><p><br /></p><p>*PAGE 30➖35*</p><p><br /></p><p>Saude tace" bakomai bari na tafi goben ma hadu, tana fita Inna ta Kira HUSNA take sanar da ita in Allah ya kaimu gobe za'a kaita wajen aiki, wani dadi husna taji kamar tai tsalle dan hutu yanzu yazo mata, zaman kadaic yanzu ya Kare dan ko yushe tasan Zata kasance cikin busy, shurun da tayine Inna tace" bakya sone? Ai se kinje shi, Husnah tace" to Inna Allah yakaimu, A wulakance inna tace Ameen, Ta Kara da cewa" dan haka ki Shirya fes, ga 30 nan kije ki siyo omo ki dan wanke kayanki masu datti, AMSA husna tayi tace to"</p><p><br /></p><p>Allah Sarki husna, Fitowa tayi taje siyo omo, se dadi takeji dan at least ko ba komai Zata huta kuma zataji me dadi dan haka tai maza ta siyo omon tazo ta fara wanki, tana gamawa aka Kira salla tai shirya ta tafi islamiya. </p><p> koda taje islamiya ta hadu Da zainab kawarta take bata labarin ansamo mata aiki, zainab ma Murna sosai ta tayata, sannan tace" amma sa sai kinyi hakuri, kinsan *RAYUWAR WASU* akwai wulakanci a ciki, balle ma suga kana musu aiki, nufina kana kasansu, Husnah murmushi tayi, tace" Zainab ai wannan da sauki a wajena akan wahalar da nakesha Wajen inna... </p><p> Zainab tace" Hakane gaskiya, amma ki kula da kanki kinji, Allah ya temakemu, Husna tace" Ameen,</p><p><br /></p><p>Suna cikin hirar *RAYUWAR WASU* yanda rayuwar kowa daban, wasu tausayi, wasu mugaye, Malan ya shugo musu karatu dan haka suka ajiye hirar, suka maida hankalinsu kan karatu ahaka har aka tashi... Zainab tayi gida itama husna tayi gida</p><p> Koda taje gida taga inna faram faram tayi mamaki sosai dan wannan ne karo na farko datai mata dariya, sannu da gida tai ma inna sannan ta wuce ta cire uniform, ta fito ta amsa jajjagen da inna takeyi, tana gamawa ta daura abinci</p><p> Da daddare Khadija suna kwance da Husna, husna tace" gobefa zan tafi gidan aiki, zare Ido khadija tayi tace" gidan aiki kuma? Ba baba ya hanaba? Husna tai dariya tace" duk da haka Nikam gwanda na tafi ko na huta,, </p><p> Khadija bataji dadin maganar ba data duba kuma taga Gaskiyane, tace" to aunty husna Allah ya temaka husna tace" *Ameen* kowo yai baccinsa</p><p> </p><p>_Washe gari_</p><p>Husna ta tashi kamar lokacin data saba tashi, tai aikace aikacen Da zatai, tai wanka ta shirya, malan kabir na fita, Inna da kanta taje ta Kira saude akan sun shirya, saude tace" to muje gidan Muja mata kunne! </p><p><br /></p><p> Tafiyar minti 3 Sega saude da inna sun shugo, daki suka nufa sannan husna ta bisu, ba kwalliya tai ba amma tayi kyau sosai, nan ta zauna suka fara mata kashedi kamar haka, kome aka bara kar taci ta bari ta kawo gidan tace to, kuma kudin aikinta na wata ba ita za'a dinga ba ba inna da kanta zataje ta amso, tace" shima to, sannan kuma banda kwalliya da yawa dan kar dan gidan yace" yana sonta, tace" to shima taji, sannan suka tashi suka tafi gidan hajiyar</p><p><br /></p><p>Suna fitowa keke napep suka tare, sukace a kaisu ung GRA yace" okay</p><p> Tafiya minti kadan sukai, suka isa, Fitowar da Husna zatai taga gidan mekyau, Alhamdulillah tace" a zuciyarta, su inna da saude suna tafe itadai tana binsu a baya har suka isa wani kofa, saude ce ta bubbuga akace yes suwaye? Saude tace" mune, wata yar karamar yarinya tazo ta bude musu, hajiya Farida tana ganinsu ta sake musu murmushi tace" sannunku da zuwa, Sukace" yauwa hajiya sannan suka sama waje suka zauna</p><p><br /></p><p>Bayan sun gaisa, Husna karema dakin kallo tayi tsaf, Saude ce tace" hajiya ga yarinyar nan sunanta Asma'u amma ana ce mata husna, hajiya Farida tace" Masha Allah, kun mata bayanin komai ko? Aikin Karfe tara zuwa 1 na ranane, Saude tace" eh mun mata, hajiya Farida tace" yauwa wanke wanke ne da wankin toilet da share share se wankin yara, Husna ta dago kanta cikin natsuwa tace" angama hajiya Insha Allah, hajiya Farida taji dadi sosai yanda yarinyar ta ansa dan ansha kawo mata yara amma sam basuda kunya</p><p> </p><p>Hajiya Farida tace"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Kash I'm tired mu hadu gobe*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Ummiey Xeey*</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>*Dedicated to zauren uⓂmiey xeey.. Loves you plenty 😍*</p><p><br /></p><p>*PAGE 41➖42*</p><p><br /></p><p>Hakadai rayuwar Husna ya kasance kullun sedaje gidan aikinta, yanzu kusan one month amma har yau baba beson tana zuwa aikiba</p><p> Yau ne ta shirya tsab Zata tafi, Tayi kyau sosai skin dinta ta fara murjewa da kyau dan ba karamin dadin take kwasha a gidan nan</p><p><br /></p><p> Tafiya take har ta sama napep tace akaita GRA ung rimi, suka daidai ta da me napep, suna isa ta ciro kudi ta bashi tai shigewarta gidan, koda taje yau hajiya batanan tana office, wani iri taji a tsorace dai tai aikinta, tana kitchen ne tana goge goge, Usman ya shugo, yace ta dan samai ruwan wanka a kettle idan yayi zafi takai mai dakinshi a cikin bukiti, kamar zata ce" bazata kai ba kuma dai ta kyaleshi, yana yin zafi ta dauka ruwan takai side dinshi, setaji kamar muryan wata a cikin dakin, seta fara tinanin Anya ma ba mace bane a dakin? Wata zuciya kuma tace" ko wa ka gani kamai kyayyawar zato, seta share itakam taje tai abun a zatai, tana gamawa tunda hajiya batanan ranar tun 12 ta koma ma gida</p><p><br /></p><p>*Washe gari*</p><p> Haka ranar ta ta sake komawa gidan still hajiya batanan, ta tafi wajen aiki, tana shiga ta dakko kayan ameerah ta fara wankewa, jin muryar Usman tayi yace" ga boxer's dina nan ki wankemun kinji, dagowa tayi a fusace tace" nifa abunda kkemun ya fara isanka, badon kai aka kawo ni nan gidan ba, binta da Ido yayi yace" yar kauye kin sama waje, idan baki wankemun ba sena bata maki rai, wawiya kawai, abun ya kuluta tace" ni ba wawiya bace, wani mari ya sakar mata seda taje kasa, rike kumatunta tayi se kuka takeyi tace" on ni Husna, Ina ganin rayuwa kala kala, </p><p> Usman dariyar mugunta yai mata yace" yar banza kawai nasan maganinki,</p><p><br /></p><p>Yajuya ya tafi, kuka tayi sosai taga ba sarki se Allah, jika boxer's din tayi tana gama wankin ameerah ta wankemai tas, a zuciyarta tace" wlhi mugunta ba kyau ne da duk sai na barbada barkono a ciki, tagama ta shanya taje tai sauran ayyukan, kafin ta gama kayan sun bushe, ta kwaso takai ma ameera daki tasa a wardrobe Kafin me guga yazo</p><p><br /></p><p>Sannan ta kwashe nashi takai mai daki,Tana shiga ta same Umsan a kan gado, binta da wani irin kallo yayi da ni kaina bansan wani irin kallo bane wannan, yace" banza ba'a koya miki sallama bane? Yi hakuri tace" sannan yace duk randa ya sata abu tai mai musu wallahi seya bala'in bata mata rai, to tace" ta mik'a mai boxer's din, tana mik'a mai ya bude su yace" kin ma raina ma kanki wawau, boxers dina sababbi amma ji yanda kika dafar mun dasu ya watsu mata, yace" maza ki tashi ki kara wankemun su</p><p> Shidai mus'ab yana daki yaji hayaniya yace boss wai meye ne? Nan usman yace" kaya na bata ta wankemu ta k'ara samun datti a ciki, mus'ab bushewa da dariya yace" tab lalle ma bakisan waye ya Usman bane maza tashi kije ki sake wankemai, Usman yace" help me tell her my bros, ji tai kamar ta kwalla ihu, badab tanajin dadi a gidan ba yau kam da tace" tabar aikin gidan nan, hakanan ta tashi jikinta ba kwari taje ta sake wankemai ta shanya, Gashi time din tafiyarta yayi amma tana tsoron tafiya saboda Usman, hakanan ta hakura ta jira har suka bushe sannan ta kwashe ta kai mai ya duba yace" kinci sa'a yarinya Da yau kinsan babbancin ruwa Da kalanzir, batace komai ba ta mike tai tafiyarta gida CIKE da bakin ciki, ko Ina kaje ba dadi, tirr da *Rayuwar wasu*</p><p><br /></p><p>Tana isa gidansu, baba ta gani, a kofar gida, Allah yasa bega sanda ta sauka a napep dinba, sallama tayi mai, yace" ha'a daga Ina husnah, tace" innace ta aikine baba, yace ok, Allah dai yai miki albarka yar nan tace" Ameen tai shigewarta gida..... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>Dedicated this page to my dear *ASY KHALEEL* You mean so much to me❤</p><p><br /></p><p>*PAGE 35➖40*</p><p><br /></p><p>Hajiya Farida tace" Masha Allah, gaskiya yarinyar ta shiga raina, husna smiling tayi a mind dinta tace wlhi nima hajiyar nan tamun da akama bazatai muguntaba. inna najin haka wani bakin ciki taji tace" inama y'ata na kawo ko Allah yasa tayi dace dan Dan gidan ya aureta..! </p><p> Nan dai Suketa hira, su saude sukace zasu tafi hajiya Farida ta dakko kudi masu yawa ta basu, Sunyi mamakin kudin sosai dan kusan 10k ne basuzata zasu samu ba, Sukaima hajiyar godiya sosai, sannan ta rakosu har bakin gate suka wuce, </p><p> Hajiya Farida na dawowa, ta iske husna inda suka barta, Ce mata tayi" kije ki cire hijab muje na nunnana maki wajen Da zaki dinga aiki, ki sake jikinki dani kome kkeso ki sanar dani kinji, to tace" sannan ta mike ta bi bayan hajiyar</p><p><br /></p><p> Side din maza ta fara nuna mata tace" wannan dakin Usman ne shine babban Dana, yagama karatunshi a Egypt, shekarunshi 27, wannan kuma na mus'ab ne second born dina yanzu he's just 25years, Zaki dinga zuwa kina wanke musu toilet da sharan daki, Okay tace" sanan ta kaita chan bayan wajen wanke wankensu, Ta nuna mata tace" nan muke wanke wanke, Husna tace" to hajiya Insha Allah, haka ta nuna mata ko Ina na gidan, sannan suka dawo pallow.. Sune zaune Sega Ameera, ta fito itace wacce ta bude musu kofa dasuka shugo, tace" wannan ne autata yanzu ta gama secondary school, Masha Allah tace" sannan ta mike tace" hajiya ba aikine? Hajiya Farida dariya tayi tace" yanzu dai babu, husna tace" ok, Tana zaune a kasa, suna kallon TV... Sallamar Usman da mus'ab sukaji, </p><p> _Usman da mus'ab ya da kanine amma kuma duk inda zasuje tare suke zuwa ko wanninsu beda aboki inda ban uwanshi ba idan ka gansu kamar twin's_</p><p><br /></p><p>Yanayin usman shi irin black beauty ne, beda tsayi sosai yanada eyes Masha Allah, jikinshi dan dai dai</p><p><br /></p><p>Hajiya Farida ce" ta Amsa sallamar suka shugo suka sama waje suka zauna! Mus'ab ne ya kai idonshi kan Husna yace" mum who is this? Hajiya farida tace" me aikine muka samu, sanan usman ya kalleta tsab yace *hmmmm* ko me ya ayyana a mind dinshi Ohon mai a gaba zamuji</p><p> Gaishesu tayi suka amsa suka bita da wani irin kallon yar kauye..</p><p><br /></p><p>Mus'ab ne yace" bari naje side dinmu nagaji mum, Usman yace" wait for me mu jera tare, haka suka fito daga dakin mum itadai Husna binsu da kallo tayi, </p><p> </p><p>Sun isa part dinsu Usman ya wani tintsire da dariya yace" bros mun sama yar aiki da gani zatai aiki sosai, Mus'ab shima dariya YAYI yace" ato aikuwa zatasha aiki, ni yarinyar se aslow bawai tamun sosai bane, Usman yace" tab Ina ruwana ai indai zatai aiki banda matsala da ita yana magana ya shige dakinshi ya fada kan gado</p><p>Koda ya fada kan gado, phone dinshi ya dauko naga yai dialing Wani suna ansa _HONEY_ Ringing biyu ta dauka tace" heeelloooo Honey! Wani nunfashi yaja yace" kai na a wuya Ina baki hakuri, dayan bangaren tace" uhm how's you kai fa dama kirkinka kadan ne! Yace" hmm nasani </p><p>Tace" to how far </p><p>Yace" lfy lau kawai dai nakira kine mu gaisa, tace" aiko nagode tnx tai katse waya, Suna gama waya tsaki yaja yace" *this girl kamar bata gane me nake nufi ba* ajiye wayar yayi baccinshi yasha, shi kuma mus'ab yan shiga daki wanka ya shiga yasa karamar riga da gajeron wando ya fara chatting 😀</p><p><br /></p><p>Husna na zaune hajiya ta kawo mata wani hadadden ferfesun Kaji lolz. Naga wasu har sun fara hadiye miyau, hade da shinkafa da miya ae zobo yaji kayan kamshi, tagode tace" a zuciyarta kam taji dadi sosai dan yaushe rabon da taci irin wannan abinci, tun randa aka kaita gidan *Oga* hamdala tayi a mind dinta, sannan tai bismillah ta fara ci</p><p><br /></p><p> Cin abincinta take a tsanake, har ta gama ta kwashe kayan zuwa wajen wanke wanke, ta gama aikin da zatai musu sannan gajiya ta bata 100 tahau napep ta koma gidan da lokacin tashinta yayi, ta AMSA tai mata sallama sai gobe... </p><p><br /></p><p> Koda ta koma gida ta tarar da yan wanke wanke, batace komai ba ta Kama tayi kokcin islamiya nayi ta tafi</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Where is Aisha A Muhd💋 your page is here... Kiyi yanda kikeso wannan page din nakine *ke kadai*</p><p><br /></p><p>*PAGE 43➖44*</p><p><br /></p><p>"Baba yace Allah dai yai miki albarka wannan yar" Ameen tace" sannan tai shigewarta gidan, tana shiga Allah yasa inna</p><p> batanan dan haka tai sauri ta sa uniform din islamiya dan tayi latti, fitowa tai baba yai mata saita dawo. </p><p> Yau ma kamar kullun husna na zaune da aminiyarta Zainab take bata labarin wahalan da Usman yake bata kullun seyace tamai kaza tayi kaza, tana gama fada ta fashe da kuka" Zainab ce" haba Husna ai inda sabo kin saba kedai kiyi hakuri, Allah zai saka miki, kuma kici gaba Da addua Allah dai ya kawo mana chanjin rayuwa me kyau, Husna taji dadin maganarta tace" Ameen, dan haka Zainab tace" to ki dena kuka dan Allah, Allah na sane da komai Husna tace" hakane, ranar dai Zainab ta kwantar ma husna da hankali sosai</p><p><br /></p><p>*Bayan kwana biyu*</p><p> husna ce" a gidan aikinta yau tagama aikin da sauri, tana zaune suna hira da hajiya farida, Usman ne ya shugo, yace ma husna ta kawo mai abinci, tace to, zata tashi ta nufa kitchen yace" ba yanzuba dan anjuma irin 12:30 tace to, </p><p> Hajiya farida na jinsu tace" Usman kenan sarkin son girma, husna tace" uhm, kuma cikin ikon Allah kokadan Husna bata taba nunawa hajiya farida muguntar da usman ke mata ba. </p><p><br /></p><p> 12:30 nayi kwata kwata shi Usman yama manta sunyi da husna zata kawo mai abinci, yana daki shi da honey hajiya farida sam batasan abunda danta ke aikatawa ba kuma ko alama daya bata ganiba, Husna ce ta mik'e ta shiga kitchen taji dai gabanta na fadi amma se ta share, abincin Usman ta dauka ta nufa part dinshi, murda abun kofar Da zatai kenan taga Usman da wata a a kwance suna iskanci, ai sake foodflask din abincin tayi hade da kwalla wanni irin ihu, nan danan suka dawo hayyacinsu, Usman najin muryar hajiya tana Husna Meya farune? Kafin ta Iso yai maza yace Budurwan nan ta shige toilet ya kwashe kayanta yasa a wardrobe, ya zira jallabiya, ya iso kusa da Husna wacce ta ke duk'e a kasa ta rike kai, saiga hajiya farida! </p><p> Tace" mai ya farune? Cikin muryar shi na rashin gaskiya yace tuntube tayi, hajiya farida tace" ka fadamun gaskiya nasanka da masifa halan tsawa kai mata ko? A'a yace" itadai husna na duke tanajin karya kiri_kiri</p><p><br /></p><p>Hajiya farida ne ta Kama hannun husna ta mikar da ita sukai pallow, jikin husna ba inda be rawa, tunda take bata taba ganin abun da ya firgita taba kamar usman data gani, Usman kuma su hajiya da husna na tafiya wani zufa yaji ya zubomai ta ko Ina, da sauri ya jefa ma budurwan nan kayanta yace" maza ta saka, itama jikinta na rawa ta saka yai maza ya bude mata kofar baya ta samu ta fice, koda ta fita hankakinshi be kwanta ba dan tsoro yakeji Husna zata iya fadawa hajiyarsu ko dan muguntar da yake mata</p><p><br /></p><p>Gaban shi ne keta fadi Dan tsoron abun Da zai biyo baya yakeyi.. </p><p><br /></p><p> Itakam hajiya Farida se tambayar husna takeyi Meya faru, Husna tace":Tsawa yai mun na firgita, hajiya farida tace" ni nasani kiyi hakuri kinji, nasan halinshi sarai, karki damu, husna tace" to hajiya itama dai karyan tayi dan bazata iya Fadan abun da tagani... </p><p><br /></p><p> Seda ta sarara bugun zuciyarta yadan ragu, sannan tace zata tafi! Hajiya tace to shikkenan sai goben kinji ki gaida su mamanki, Sun fito kenan Sega Usman, wani harara hajiyarshi ta sake mai shi duk tinaninshi husna ta sanar da ita abunda ya faru! </p><p> </p><p>Daki ta Shugo ya biyota ta banka mai harara tace wuce ka bani waje katon banza..... Jin gabanshi yayi dassss ya fadi</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ku ci gaba Da biyoni hope Kuna enjoying </p><p><br /></p><p><br /></p><p>*For comment Only*</p><p>08164640126</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Ummiey Xeey*</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>Dedicated to *Meelat, & real khady* loves you irin Sosai dinnan </p><p><br /></p><p>*PAGE 45➖46*</p><p><br /></p><p>Usman Jin gabanshi yayi ya fadi gham, Cije labe yayi yace Yarinyar nan zata sani yai wucewarsa daki ya goge kayan da husnan ta zubur, zama yayi a daki maganar hajiyarsu se maimaita ta yakeyi _wuce ka bani wajen katon banza_ ji yayi ya kara tsanar husna, </p><p> Ita kam husna tun data koma gidan se kallon abun takeyi, kenan ba shakka ranar data kawo mai ruwan zafi tabbas muryar macen taji a dakin, abun se yawo a zuciyarta yakeyi, taba idan ma ta damu ita zata sha wahala seta share</p><p><br /></p><p> Shikam Usman kwata kwata da daddaren ranar kasa zuwa bangaren hajiyarsu yayi, Duk ya kusa safiya tayi yaga Husna ya tambayeta ko ta fadama hajiyar ne</p><p> Aiko Washe gari tana zuwa tun kafin ta Shugo gate ya tareta yace" ke zonan ya wani murtuke fuska, zuwa tayi yace" husna Kin fadama hajiya abunda ya farune? Eh tace nafada sai mai? Gabanshi yace gham, shikkenan na shiga uku, ji yayi kamar ya kai mata duka dan haushi, kallon zaki sani yai mata, sannan yace" wuce zamu hadu ai.. Gidan ta Shige abunta</p><p><br /></p><p>Tana shiga taga hajiya ta gaisheta, sannan ta fara aikin gabanta har ta gama, </p><p><br /></p><p>Usman na kofar gida hajiya ta kirashi a waya lokacin husna na zaune tace" kana inane? Yace" gashinan a kofar gida tace" ka shugo Ina son ganinka, gaban shine ya fara dukan uku uku yace" shikkenan yau karyata ta kare, wallahi yarinyar nan zata sani, tazo ta sama gindin zama har da munafunshi ko, shi duk a tinanin shi Husna da gaske take ta fada mata, kuma maganar da yai mata yanasha ta kara zuwa ta sanar da hajiya ne.. </p><p> Shuguwa yayi da sallama yayi ya sama waje ya zauna a kasa, hajiya tace" usman kai abun da kai ya dace kenan? Kana babba! Ji yai kamar yai fitsari a wando dan tsoro da kunya, kasa motsi ma yayi zufa ya fara zubumai, Hajiya ta jarau da cewa badakai nake magana ba? Me yasa bakajine? </p><p> Dago kanshi yayi idonshi yai ja, yace" Dan Allah hajiya ki gafarceni, tace"rufemun baki kawai, duk me aikin da ka kawo gidan nan sabida masifarka da da Shouting dinka sukesa subar gidan nan yanzu me Husna tai maka? Wani sanyi a ranshi yaji kamar yai tsalle ya gane Ashe HUSNA bata fada gaskiya abun da yafaru ba</p><p> Dago kai yayi yace" hajiya kiyi hakuri na miki alkawarin bazan sake ba, yana kai maganar suka hada Ido da Husna, </p><p><br /></p><p> Hajiya tace" to shikkenan kadai chanza for good Kaji? Yace" ok hajiya ya mike ya shiga daki CIKE da farin ciki yace" gaskiya yarinyar nan tayi</p><p><br /></p><p>Tun daga lokacin yaji yana sonta amma kuma bazai iya auranta ba saboda ya wuce da class dinta sosai</p><p><br /></p><p> Zata tafine, shima daidai time din da ya dakko matarshi, yace shugo in kaiki gida, tace" a a, Hajiya tace" Kaji dai husna ki shiga mana meye a ciki, zata shiga sit din baya ya juyo yace ni ba driver dinki bane ki shugo gaba... Mtsww tayi, ta shugo gidan gaba suna tafiya ya kalleta yace" yanzu nasan zakiji a zuciyarki cewa InaSonki ko? Allah ya kyauta tace" yace" good yarinya kinsan gaskiya, barama kiji dai dalilin da yasa nace zan fita har na ce ki shugo na rage maki hanya, Binshi da Ido tayi ita sam kwata kwata be burgeta</p><p><br /></p><p>Yace.....</p><p> Ya soma magana tana kallon bakinshi ta mirrow (madubi) yace" wallahi da kin kuskura kin fada ma hajiya wani magana, da sai kin bar gidan nan kota tsiya kota arziki, tsaki tayi" yace kibi a hankal yarinya kinsan dai da Wanda kike tare, nan danan se tsoro yazo mata bata kara cewa komai ba</p><p><br /></p><p>Se Surutanshi yakeyi itakam ko qala bata ceba, har akazo dai dai layinsu, tace" inka sama waje ya kalleta yace" meye wani inka sama waje sai kace wani driver dinki ai se kice akwai nan.. Ita dai duk ta kosa ta sauka tace nan ne, yai parking amma yaki bude kofar</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>```Dedicated to my Bilkisu Bk & khady fresh.. Inaso ku sani Kuna da babban matsayi a hrt dina💋```</p><p><br /></p><p>*PAGE 47➖48*</p><p><br /></p><p>Ya kalleta yace" meye wani in ka sama waje sai kace wani driver dinki? Ai se kice akwai nan! Ita kam husna duk ta kosa ta sauka tace" to akwai nan</p><p><br /></p><p> Wani irin parking yayi, ta murda kofar zata fita taga Ashe ya kulle, ce mai tayi dan Allah ka bude, yanda tai maganar ya shigeshi sosai har tsakiyar kanshi, binta DA Ido yayi shi kwata kwata ma ya manta me tace, Kara magana tayi "tace Dan Allah ka bude mun kofar na fita, A zuciyarshi Wow yace" kai wannan yarinyar ta hadu ta ko Ina sedai kash bazan iya soyayya da itaba</p><p><br /></p><p>Bude mata kofar yayi, tai sauri ta sauka ta fada wani lungu, dan tsoro takeji kar wani ya ganta yai mata mummunar fassara ko kuma akai gulma wajen inna ace wani mai mota ya kawota!</p><p><br /></p><p>Tana tafiya se sake sake takeyi a zuciyarta tace" Allah dai ya raba na gari DA mugu ameen</p><p><br /></p><p>*USMAN* bayan ya koma gidane ya hadu da abokinshi kuma kaninshi, Mus'ab yake tambayarshi daga Ina yake haka da tsakar ranar ne! Usman yace" aww yarinyar nan nakai gida, Mus'ab yace badai husna ba, eh usman yace" mus'ab ne ya zare Ido yace don't tell me you fall in love with her Kodai yaudararta zakai? </p><p> Wani nunfashi Usman yaja yace" ganinan dai I like the girl but tamun local da yawa, abokaina ai se sun mun dariya, sanin kankane yan mata ke biyoni amma aga na bige da soyayya da wannan? Mus'ab dariya yayi sosai, harda rike ciki yace" kai Allah dai yasa mu dace Usman yace Ameen</p><p><br /></p><p>°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°</p><p>_Bayan Shekara daya, Usman gaba daya yasama Husna Ido, kome takeyi idonshi kirr na kanta, zuciyarshi kam ta kamu da sonta..._</p><p><br /></p><p>Inna ne zaune da Husna suna yar hiransu, balle taga wata yakusan zuwa karshe, itadai burin inna kudi, kudi, kallon Husna tayi dakyau, taga kyanta kara yawa yakeyi, tayi bul bul tayi fresh, da alama hutu ya zauna mata, Wani bakin ciki taji tace" aranta lalle ma har husna ta fini kyan jiki, mikewa tayi, ta dakko gyale fuuu ta fita se gidan Saude, Saude na ganinta tace" mutumiyar ya akai ne? Nan inna ta zayyane mata komai, Saude tace" kwantar da hankalinki, meyai zafi? Ae se a chanza ko? Inna kwashewa da dariya tayi tace" sai yasa nake sonki, saude tace uhmmmm</p><p><br /></p><p>Sati, shekaru natayi, kullun Son Husna na karuwa a zuciyar Usman, yau husna tazo aikinta ta gama da sauri, Usman ya shugo dakin Hajiyarsu yaga husna zaune, kallo daya yai mata ya ga yarinyar fa k'ara kyau takeyi, ga dukiyar fulaninta sunyi girma, nan danan shaidan ya fara mai huduba, Karfin hali yayi ya fita dan sab za'a iya samun matsala</p><p><br /></p><p> Daki ya shiga gabanshi ya fara dukan uku uku... To fa, Wata zuciya tace" ka fada mata mana wqta zuciya kuma tace" Kaji tsoran Allah, Toilet ya shiga ya watsa ruwa, sannan ya kwanta, yana kwance kamar ance ya Leka window, husna ya hango tana kwashe shanya, kayan da tasa sun dan matseta, boobs dintane ya fito sosai duk da ba wasu manyan nan bane amma ya mata kyau sosai, kura idonshi yai akanta, yaga idan ya ci gaba da kallonta bazai iya controlling kanshi ba dan haka ya fada gado ya rungume pillow... Yana ganin siffar Husna</p><p>Kara matse pillow yayi a chest dinshi, nace to fa Aiki yaga maza.. </p><p> Ita kam husna basan ma me akeyiba wai kunu awani gida, tana gamawa ta sako hijab dinta tayo gida, Sallamar da zatai kenan inna taci karo da ita a tsakar gida, wani harara tai mata Husna tace" to ni kuma me nayi? Sannu da gida tai ma inna wani harara ta kara balla mata, Shuru husna tayi ta sama waje ta zauna, ta fara tinanin abubuwa da dama, shurun da inna taga tayi a tinaninta saurayi take tinani, wani mari inna ta sake mata hade da cewa dan ubanki wato SOYAYYA kike YI KO? </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>```NA........ ✍🏼```</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p>*EMNOOR AHMAD DON* Missing you badly 😭</p><p><br /></p><p>*PAGE 49➖50*</p><p><br /></p><p>Shurun da inna taga tayi a tinaninta saurayi take tinani, wani mari inna ta sake mata hade da cewa" dan ubanki wato SOYAYYA kike YI KO"? </p><p> Husna ta fara KUKA tace" wallahi inna ba wani soyayya da nakeyi, dawa zanyi? Inna ta dakko bulala tai mata dukan tsiya tace" dan ubanki ni kike tambaya ko, Husna se kuka takeyi, seda inna tai mata ligis sannan ta koma daki, Ita kawai inna haushin husna takeyi, Dan harsashen da takeyi ba gaskiya bane! </p><p><br /></p><p>Husna daki aa shiga taci kuka sosai, tace" Ya Allah ka sakamun, Allah ka kawomun mafita, ni na gaji da wannan wahalar, tagama kukanta ta kwanta a dan karamar katifanta, abun tausayi.. A yan kwanakin nan dai husna bawai zaman dadi takeyi a gidan nan ba, kuma ko taje gidan Aiki, shima Usman yai ta kallonta duk tabi ta tsargu,</p><p><br /></p><p>Haka dai RAYUWAR husna ya kasance yau dadi gobe bakin ciki, ita kwata kwata batajin dadin rayuwarta, Sedai tai ta addua, Allah ya kawo mata mafita.. </p><p><br /></p><p>Kamar wasa husna na zaune yau ma kamar kullun hajiya batanan, ta gama aikinta ta dakko wata rigan shan iska dan lokacin zafine, taga ba kowa a gidan, tasa dan batai tinanin ma Usman nanan ba! </p><p> Tana zaune se Usman ya shugo dakin, wani irin kunya taji, kuma idan tace zata tashi ta dakko hijab kunyar zatai yawa dan tsab usman zeta kalleta, ba yanda ta iya hakanan ta zauna, usman ya gama abinda zaiyi ya fita yana lura da ita, </p><p> Seda ya shiga daki wata zuciyar tace" kai wallahi banzane, ga yarinya available kai abun Da zakai da ita amma kaqi, nan Take ya kwalla mata Kira yace ta kawo mai Apple juice din dake cikin fridge, "To tace" ta TASHI ta dakko hijab dinta tayi dakin tana shiga ta shugunna tace" Gashi, mikewa yayi ya kulle kufa, ya kalleshi tace" Usman me kke nufi? </p><p> "Abunda zuciyarki ta fada miki shi nake nufi a cewar usman" gabantane ya fadi Sosai tace" na shiga uku na lalace, Wuka ya dakko mata yace" wallahi idan kikaimun ihu, sai na yankaki ba Wanda ya sani! </p><p> Husna tsugunnawa tayi a gabanshi ta fara kuka ya toshe mata baki, tana Dan Allah kar kai wannan mugun aiki dani, Kaji tausayina, Rungumeta yayi tana tureshi, yace" Ina sonki ne Husna, wallahi sonki ne ya jefani zan aikata wannan abun dake, </p><p><br /></p><p>Kara rok'anshi sosai takeyi amma Ina banza da ita tayi, turata gado yayi, tun tana ihu har na dena jin ihunta, seda Usman yaci ma burinsa sannan ya kyaketa, Husna kuka sosai tayi, ta samu dakyar ta fito a dakin lokacin still ba kowa a gidan, ruwan zafi taje ta saka ta gaggasa jikinta Dan kar a gane zuciyarta cike Da bakin ciki,</p><p><br /></p><p>Ta gama shiryawa kenan zata tafi Sega hajiya farida ya shugo, kallo daya tai mata tasan something is wrong, Hajiya farida ne tace" Husna Meya faru, kikai kuka ji yanda idonki duk ya kumbura, Nan Husna tai maza tace" hajiya yau dakyar nai aikin nan kaina ne keta ciwo, Hajiya tace" ayyah sannu Allah ya kara sauki, Husna tace" Ameen hajiya ta dakko magani ta bata tasha, husna zata tafi kenan Hajiya tace" bari ba Kira Usman ko mus'ab duk wanda yake gida ya kaiki, Husna tasan Usman ne ke gida gabanta ne ya fadi dan kar suje hanya yai mata na biyu, tana zaune Hajiya ta Kira Uaman yace" gashinan zuwa, manyan kaya yasa kamar bashiba, yana zuwa Hajiya tace" ka kaita gida bata da lfiyane, To Usman yace" amma shi kanshi yasan abun da yai be daceba</p><p><br /></p><p>Fita yayi husna na binshi a baya, taji kamar tace" bazata jeba Dan dai kar hajiya ta gane wani abune, hakanan ta shiga Motar, Usman ya fara driving, suna tafe ba wanda yacema kowa komai, Husna idonta se zubar da kwalla take, tana ganin inda zai bi ya sadasu da gidan su taga be beba, ya bi wata hanyar a zuciyarta tace" Shikkenan yau sai Allah, Ina kuma zaije da ni duk wanda yai mun be isheka bane? Tana maganar ne amma sam batasan ya fito fili ba.. </p><p> Shuru yayi da alama ta batashi tausayi, yace" Dan Allah Husna kiyi hakuri, wallahi sharrin shaidan ne kuma Dan Allah Ina rokanki karki sanar da kowa ki rikemun alkawari, bawai nayi wannan abun da in bata miki rai bane, wallahi Sonki ne ne ya hanani sukuni har shaidn yaci galaba akaina kiyi hkuri Dan Allah, banza dashi tayi idonta se zubda hawaye yakeyi... </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>*PAGE 55➖56*</p><p><br /></p><p>"Nan take Take Malan ya rubuta mata saki daya abun da bai tabi yi mata kenan ba" sanan ya mik'a mata</p><p> Inna bawai ta iya karatu bane, yar ta khadija ta Kira tace dubamun me babanki ya rubuta, Zare Ido khadija tayi tace" ya sakeki saki daya, Khadija runguma m amanta tayi se kuka tare sukeyi, inna tace" yau na shiga uku, Ina zani tsofai tsofai dani, wallahi ba inda zanje, baba najinsu yai banza dasu tuni yaje wajen me ung ya sanar dashi yar da suka bashi ga abun da ya faru nan! </p><p><br /></p><p> "Ita kam Husna koda ta fito tafiya take dai dai wani bakin titi tana tafiya Sega Wasu Samari su Biyu Manya a kalla zasukai 32years cikin Wani babban mota kana gani kasan motor manyan yarane (big boys) ta yanko titin kenan tana tafiya hankalinta gaba daya be jikinta, su kuma Gasu sun danno Motar da karfi wani wawan birki suka ja, ji kake _kiiiiyy_ mufeed ne da yake driving yai sauri ya tsaya suka fito tare da farouk da yake zaune dayan bangaren</p><p> Farouk ne ya kalleta cikin tausayawa yace" Baiwar Allah Ina zaki haka baki ganine? Bin su tai da kallo seta tuna ranar da aka saceta, ta gansu guys din masu kyau tace a ranta ya Allah kasa ba dasu na sake haduwa ba, jin shurun da sukai batai magana bane Mufeed yace" aboki kamar bata magana fa, kasa tai da kanta tama rasa me zatace masu, Farouk ne yace" nima naga alama, yanda bata maganar nan idan zamu temaka mata ya zamui kenan? Wuya zamusha Kawai, Mufeed yai tsaki yace gaskiyane, mu shiga mu wuce kawai Allah dai ya tsareta daga sharrin mugaye Suka juya suka nufa motarsu, kararaf Sukaji Tace" Ameen wai gowa sukai Abun ya basu mamaki!</p><p><br /></p><p>Farouk yace" ikon Allah dama kina iya magana tun dazu Muna magana kikai banza damu? Kuka ta saki tace" inayi Dan Allah ku temaka mun Dan Allah, Farko Sunji tsoro dan a zamanin nan ba kowa zaka gani ka temaka mai ba..., Farouk yace" zamu temaka maki, mufeed shidai Binsu da Ido yayi, Farouk yace" mufeed bakace komai ba! Agogon Hannunshi ya kalla yaga 10:00 ya kusa yace kasan munada aiki a office ko, just ta fada mata tsakaninta da Allah ita mutun ce kar muje ku dakkowa kanmu, HUSNA tace" Wallahi Ni mutun ce, Okay yace sannan yace mata ta biyosu in badamuwa Insha Allah zasu temaketa, tace to nagode, bude sit din baya tayi ta sama waje ta zauna, mufeed ya fara driving be tsaya ko inaba Se babban court din dake katsina, suna shiga suka sama parking space sukai, Farouk da mufeed har sun fito </p><p><br /></p><p> tace" musu Dan Allah yunwa nakeji, Mufeed ya kalleta yace" ok zaka KAWO maki abinci yanzun nan kuma kar ki sake ki fita daga Motar nan kinajina ko? "Eh tace" ba' ai minti 5 ba Sega wata mata dagani ma'ai kaciyar wajen ne irin masu saida abinci nan ta KAWO mata abinci lafiyayye ta amsa, ta fara ci, a zuciyarta tana cewa oh ni husna rabona dacin wannan abincin tun Ina gidan Su Hajiya farida nan ta fara cin abinci har ta gama Sannan tadan takura kadan tayi bacci a sit din bayan Motor</p><p>°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°</p><p><br /></p><p>Shi kuma Usman kwanciyar da yayi ba sai zazzafan zazzabi ya kamashi ba, kan kace meye jikinshi ya fara rawa sai yunkirin Amai yakeyi,</p><p><br /></p><p>Gabanshi se dukan uku uku yakeyi, Su hajiya farida da mus'ab da autarta suna zaune a pallow se jamamin rashin husna sukeyi, hajiya farida ne tace" jeki dubamun yayanki a daki, ya kan nashi, tana shiga taga halin da yake ciki da gudu ta fado kan Mamanta tace" mummy Uncle Usman zai mutu, da sauri dukansu suka nufa dakin, yanda suka Ganshi sunyi mamaki sosai, nan take hajiya ta Kira abbansu da yake be gari yace ga doctor Abubakar nan zaizo dubashi ya jikin nashi? Hajiya tace da sauki, Yace" Allah ya Kara sauki tace" Ameen </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>*PAGE 51➖52*</p><p><br /></p><p>Shuru yayi da alama ya batashi tausayi, yace" Dan Allah Husna kiyi hakuri, wallahi sharrin shaidan ne kuma Dan Allah Ina rokanki karki sanar da kowa ki rikemun alkawari, bawai nayi wannan abun da in bata miki rai bane, wallahi Sonki ne ne ya hanani sukuni har shaidn yaci galaba akaina kiyi hkuri Dan Allah, banza dashi tayi idonta se zubda hawaye yakeyi,</p><p><br /></p><p>Shurun da tayi, yasa yaci gaba da driving har ya kawota kofar gidansu, Allah yasa ba kowa ta sakko tai maza ta shige gidan, tana shiga Nan ba ba kowa a tsakar gidan inna batanan, Daki ta shige tasa kanta a kasar pillow tai kuka ma'ishinta, idonta suka kara kumbura, duk lokacin data tino da abun setai ta hawaye,</p><p><br /></p><p>Washe gari inna taga duk tabi ta chanza tai wani iri, tace" wai meke damunkine? Husna tace" Inna kaina ne keta ciwo tun jiya, Sannu tace" mata amma a zuciyarta Allah ya k'ara inna tace"</p><p><br /></p><p> Kwanan HUSNA Uku ahaka bataje aikiba, Duk Usman yabi ya damu dan ko yasan tabbas ta dalilinshine yasa Bata zoba, Musamman zai kintsa yaje layinsu ko Zai ganta amma Ina ko me Kama da ita be taba ganiba, Washe gari har Kwana 4 hajiya bataga Husna na ba, kintsawa tayi taje gidan, ta sama Husna a wani daki a kwance duk ta dan rame, tai mata sannu da jiki har ta dan bata kudi Husna tace" tagode sannan hajiyar ta tafi! </p><p> Bangaren Usman kuma hankakinshi ba karamin tASHI shima yai ba dan be ganin husna, shima ya dan rame yayi duhu abunka da mara gaskiya</p><p> </p><p>Tun daga ranar Husna bata Kara zuwa gidan ba, hajiya tasha zuwa ta tambayeta ko dai an mata wani abun ne sai tace" a a ita ta gajine kawai, ahaka Har Hajiya ta hakura!</p><p><br /></p><p>Usman kuma yayi kuka Sosai, Gashi bazai iya zuwa gidan yace" ta fito ba dan yasan ba zuwa zatai ba.. Amma kullun addua yake Allah yasa wata rana su hadu</p><p><br /></p><p> *Bayan wata daya* </p><p>Inna na lura da Husna sab, kallonta takeyi dan gaba daya ta chanza, se laulayi husna takeyi, ta rasa yanda zatai, itada ba zama da hijab takeyiba ba amma yanzu kullun cikin hajib da zubar da miyau,</p><p> ""Yau Inna na zaune a tsakar gida Sega Husna ta fito da gudu tana kakakin amai, salati inna tayi tace" yau me zangani ba makawa wannan yar ciki gareta, Sa6a hijab dinta tayi se gidan Saude, Tana zuwa aikuwq tai sa'a Saude nanan tace" zo ki tayani gani! Saude da gulma, ta biyota suna shiga gidan suka ganta se kakarin Amai take irin na masu laulayin nan, Salati itama Saude tayi tace" tab a wannan gidan.? Ke Dan ubanki wayai miki ciki, gabantane ya fadi russs, ta mik'e daidai da shuguwar Baba kabir</p><p><br /></p><p>Baba kabir najin hayaniya, yaje wajen yace waye ba lafiya? Inna tai wani dariyar mugunta tace" husna ce ta dakko mana abun magana! Ciki gareta, baba kasa tsayawa yayi yace" CI me? inna tace" Ciki mana, ai ga irintanan, ita yar so ko? Yar da tafi yqr cikinka ai GATA gaka nidai bazata zauna a gidan nan ba wallahi, dama abun da inna take nema kenan, nan ta fara sababi, Kan kace meye unguwa ya dauka Husna tayi ciki</p><p><br /></p><p> Baba daki ya shiga ya Kira Husna wayai miki? Sedai tai ta kuka ba AMSA, ranar kwarai baba yai mata fada sosai, abun ya bashi mamaki matuka, a ranar Husna ba wani bacci tai ba, cikin darene ta tashi ta fara tinanin guduwa a gidan Dan ko ta zauna bawai zaman dai zatai ba, Harhada kayanta tayi, duk ta kosa asuba tayi........ </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>```Dedicated this page to```</p><p>Biebie Dee🌸</p><p>Mar°Ahmad</p><p>Ruqeey Ce</p><p> I love you guys😍</p><p><br /></p><p>*PAGE 53➖54*</p><p><br /></p><p>Cikin darene Husna ta tashi ta fara tinanin guduwa, dan tasan muddin ta zauna a gidan nan to tabbas ba zaman dadi zatai ba, habaici ma kadai zai ta ta kusan mutuwa dan inna bawai sonta takeyiba, </p><p><br /></p><p> Harhada kayanta tayi duk ta kosa asuba tayi,se kallon agogo takeyi amma Ina gani take kamar ba tafiya yakeyiba, Kiran sallar farko taji wani irin dadi, fitowa tayi tai alwala tai raka'atanil fijr ba ita ta mike akan Sallayar ba har se da ta idar da asuba, Khadija ta tayar tace kije ki alwala ki sallah, lokacin baba shima ya fita, tana ganin khadija ta Shiga bandaki ta tattara inata inata tasamu ta fito waje, koda Khadija ta dawo dakin bataga Husna ba, bata damuba dan tasan Husna intaga dama tun asuba take tashi ta fara aikace aikace sai yasama bata damuba. khadija na idar da Sallah ta koma bacci abunta</p><p><br /></p><p>Ita kam Husnah tana fitowa, rasa inda Zataje tayi, ga se zubar da miyau takeyi, ga yunwa tanaji daka ganta seta baka tausayi, tafiya takeyi amma sam batasan Ina zata tafi ba tace Oh yanzu *RAYUWAR WASU* Haka take, zuciyarta tace kema ba gashinan ba yanda rayuwarki ta kasance, wani zafafan hawaye suka zubo mata tace " ya Allah ka dubani kasa Alheri ne wannan tafiyar. </p><p><br /></p><p> Gari ya waye rasss baba yaji shuru husna batazo ta gaisheba, a tinaninshi Fadan da yai matane yasa batazoba, aiken khadija yayi yace taje ta kiramai Husna, Khadija tace" baba wlhi nima ita nake nema tun da asuba ban gantaba, nan take baba yaji gabanshi ya fadi Gham! Yace" me kikace? Tace tun da asuba baba nima nake ta nemanta, Inasha ma tana aikin cikin gidane na tashi banji motsinta ko kadan ba, baba Inna ya kwalla na Kira yace" gashinan ae Kinsa asma'u ta gudu ko ke abu me kyau ne haka? Ko akwai wanda ya wuce kaddarane? Nan Inna ta fara masira tace" to ni Ina ruwana, ni na aiketa tai cikin? Ko da tai ai bani na koretaba, Baba Yace" kece mana jiya fa inaji kikace badai ta zauna a nan gidan ba, Wallahi idan bakije kin nemo taba ranki zai mugun baci, mtssw tace"sannan ta dauka hijab, ta fito, koda ta fito, koda ta fito bata wuce ko Ina ba se gidan hajiya farida, a tinaninta ko nan zata</p><p> "Inna na shiga ta samesu duka a pillow tai sallama dagani sunsan hankakinta ba kwance ba, tace" Husna tazo nan gidan tun asuba bamu ganta, hajiya farida tace" kai Wallahi Husna batazo ba wani abun ne ya faru? inna bata tsaya ce musu komai ba ta juya, *Usman* kuma ana cewa ba aga Husna ba wani mummunar faduwa gabanshi yayi, a zuciyarshi yace *NINE SILA* innalillahi, nan take ya nema natsuwarshi ya rasa, har hajiya farida ta lura dashi tace" Usman Meya farune? Yace" wallahi wani irin ciwon kai naji yanzun nan, tace" ayyah Sorry je kasha magani ka huta, Nan sun shiga jimamin to Ina Husna zataje? </p><p> </p><p>Mikewa yayi tana tafiya wani duhu duhu yake gani, daki ya shiga ya kulle ya fara wani irin kuka, se Alokacin ya Kara nadaba yasan tabbas abunda daya aikata ba abu me kyau bane, dadin dadawa ma yasa tabar gida, cusa kanshi a cikin pillow yayi yaci gaba da kuka Sosai seda yai ma'ishi sannan yadanyi shuru bawai dena kukar yayi ba....</p><p> Koda ya dan tsagaita da kukan, innalillahi yaketa fada, waata zuciyar tace ka tashi ka fita ko Zaka ganta kabata hakuri akan abun dakai mata, har ya mike ya dauka mukulli, wata Zuciya kuma tace" yo inka fita kanada tabbacin Inda zaka gantane? Dawowa yayi ya fada kan gado luuuuu... </p><p> *************</p><p><br /></p><p>Inna kuwa tafiya take tama rasa Ina zata sa kanta Dan tana komawa baba yace Ina Husna tace" bata gantaba to ba karamin bacin rai zata taddaba, taci nemanta har ta gaji ba yanda ta iya dawowa gida tayi, </p><p> Tana shuguwa baba wani irin kallo yai mata alamar Ina Husnah? ita kanta Tasan itace silar barin Husna gidan. Kuka ta fara tace" Mlan duk inda zanje ko Zan ganta Wallahi ban ganta ba.. </p><p> Nan take malan ranshi ya baci ya rubuta mata saki daya.. Abun da bai taba yi mata kenan ba</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>*PAGE 57➖58*</p><p><br /></p><p>Usman ne kwance su hajiya na kanshi, Karar knocking din kofa sukaji, Mus'ab ne yaje ya bude kofar, yana budewa doctor ya gani ya mai iso har cikin dakin, Nan doctor ya fara aikinshi ya mai gwaje gwaje, har ya gano BP dinshi ya dan hau, nan yasamai ruwa yamai duk abun da zai mai yace" zai tafi idan akwai wata matsalar akirashi "Su Hajiya sukace to shikkenan mungode"</p><p> Da fitar dashi, hajiya taga jikinshi da dan sauki take tambayarshi me ya faru har BP dinahu yayi high, "usman ce wa yayi ba bakomai hajiya, Tace" hmm naji dai amma ban yardaba bari dai naje na daura mana girki mus'ab ka kula dashi Ina zuwa, tai ficewarta, </p><p><br /></p><p>Da fitar tane" mus'ab ya kalle bro dinshi yace" yaya kasan dai baka da aboki kama ni ko? Kuma damuwarka tawace ko? Usman "eh yace amma kwata kwata be so mus'ab ya fara wannan maganar ba yasan inda ya dosa, Gashi Usman din ba yanda zayi dole ya fadamai gaskiya, </p><p> Musa'ab yace to Dan Allah meke damunka? </p><p>Usman ya fara magana idonshi cike da kwalla yace" nayi babban laifi, na aikata HARAM, wallahi nine sanadiyar barin Husna gidansu, Mus'ab ya sake baki yace" ammm banganeba, </p><p><br /></p><p>Usman mikewa yayi daga kwaciyar da yake yace" nayi taping din Husna, dalilin da yasa ta dena zuwa nan kenan kuma nasan ma ba zata a gidan su zatai ba kagani duk na naja yana kaiwa karshe ya fasa kuka</p><p> "Innalillahi wainna ilaihi rajiun mus'ab yace hade da fadin why Yaya Usman me yaja ka aikata haka?</p><p><br /></p><p>Usman yace" hmm kabari kawai tsautsayi da sharrin shaidan, nan Usman ya sanar dashi tun farkon abun da ya fara hadasu na ganin shi da tai da wata tun daga lokacin shima yaji yana sonta, Wani nunfashi mus'ab yaja yace to shikkenan yanzu dai aikin gama ya gama, Sekai ta Istighfari kuma dan Allah kar ka sake, ita kuma Insha Allah zamu bazama nemanta se inda karfinmu ya kare! Usman yaji dadi har cikin ransa yace" to nagode nan dai Suketa hirarsu har hajiya ta dawo taga jikin bashi ma da sauki, a ka samakai abinci yaci har drip din ya kare amma ka ganinshi kasan akwai damuwa cikin Ranshi,</p><p><br /></p><p>Hakadai ranar wunin usman ya kasance duk a takure yai wani iri</p><p><br /></p><p>••••••••••••••••••••••••••••••••••••••</p><p>Bangaren Su Mufeed kuwa bayan sun shiga court (kotu) ha sun gama judging wani case suka fito dashi da Farouk suga shiga cikin Motar zasu wuce kaduna, su sun ma manta kwata kwata akwai wata Husna a cikin Motar </p><p> Farouk ne ya kalleta yace" kalle, se sharar baccin ta takeyi, muffed yace" oh yanzu ya zamui da itane? Farouk yace" why not ka wuce da ita part dinka tunda ba kowa? Ni kaga akwai matsala? Mufeed yace" Allah ko? /Farouk yace yes gaskiyar kenan kaga se idan muka gama bincike akanta se musan abun da zamui, Mufeed yace" hakane, Allah yai man jagora sukace Ameen, Mufeed yaja mota suka wuce</p><p><br /></p><p>Suna tafiyane Husna ta farka daga bacci, abunka da mai ciki ta fara tara miyar a baki, Farouk ne ya waigo yace lafiya? Se yunkirin amai take kan kace meye tayi amai a Motar, Mufeed kam be dena driving ba yana kallonta ta mirror a zuciyarshi yace" hala ma irin yaran nan ne da basajin magana, taje tayi ciki dan *RAYUWAR WASU* haka take, Farouk na ya kalle abokinshi ya juya harshe da turanci yace" _like she's pregnance_ Mufeed ya daga gira yace" _hmmm that's what am thinking,_ but koda yake duk wani bayani yana wajenta, muje kawai.... Suna tafe suna hirarsu har suka isa Ung dosa inda Mufeed yake kenan!</p><p>[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂</p><p>WANNAN PAGE DIN nakane Alone.. *HAYATU BABA ZUBAIRU✍🏼* Wishing an amazing day and many great things to come to youuuu.. </p><p> *HAPPY BIRTHDAY TO YOU*</p><p>*/ღ˚ •。* ❤ ˚ ˚✰˚ ˛★* 。 ღ˛° 。* °*❤</p><p>🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂</p><p><br /></p><p>*PAGE 59➖60*</p><p><br /></p><p>Yana shiga ya sama parking space yayi, Farouk yace" kalle har yanzu ba bacci takeyi ya zamui kenan, "Mufeed ne ya dan bubbugata yace tashi" afirgece ta tashi ta fara waige waige shap tama manta a inda take, Farouk ne yace" ki fito mana jin kafarta tai nauyi dakyar dai ta samu ta sakko suna tafe tana binsu a baya, </p><p> Wani dan madaidaicin falow taga sunshiga, Mufeed ne ya zauna se Farouk shima dan haka itama ta zauna, se tinati takeyi a zuciyar ta Allah dai yasa ba yan iska bane, kardai ace sun yaudareta ta biyusu sui abun da zasui da ita Dan tasan wasu mazan haka suke, shuru tayi, Farouk yace" to Alhamdulillah, yanzu dai abunda mukeso dake shine ki sanar damu, dan kinsan zamanki anan bazaiyuba ko? Eh tace" tana shirin yin kuka dan gaba daya ji tai ta tsana rayuwarta, farkon wanda sukafara salwantar mata da rayuwa shine yan yankan kan nan da suka dauketa da yanzu tana tare da iyayenta</p><p> "Mufeed ne yace munajinki ba kuka zaki mana ba kuma tsakaninki da Allah mukeso Insha Allah zamu temaka miki, nan ta fara kuka tana sanar dasu duk abun da ya faro ds ita, tun daga ran da iyayenta sukai accident aka saceta, ta samo ta kubuta tazo gidan Malan kabir, Inna bata sonta, har Dai Allah yasa aka neman mata aiki Daganan ne Wannan iftila'in ya sameta, nan Inna ta fara bala'i wai badai gidanta ba to a tinani na idan ba gidan na bari ba ba samun kwanciyar hankali zanyiba, shine na gudu har Allah yasa na hadu daku, Bata boye masu komai ba ta fada.... Wani irin tausayi Farouk yaji tana bashi, Mufeed kam kasa komai yayi ya kalleta yace" ke inkinsan karya kike mana ki fada mana gaskiya Dan mudinnan da kike gani lawyers ne, kar mu yanke hukunci yazo ba haka bane, kuma idan. Mukai finding out mukaga karyane wallahi zaki fuskanci hukunci... Husna kuka takeyi sosai tace wallahi maganar nan da nafada muku ba karya bane, Wani munfashi Mufeed yaja... Yace" zaki iya kaimu gidan da kika fito? Akwai abun da zamui ne, tace" eh Zan kaiku yace" ok... Zamui magana akai anjuma, yanzu ga wannan dakin, ya nuna mata wani room yace" kome kike bukata akwai a ciki, idan kuma wani abu kike so ki dinga sanar dani... To tace</p><p><br /></p><p>Ta tashi ta shiga dakin fadawa akan gado tayi ta fara kuka mecin rai, tace" oh ni rayuwata haka zata kare? Farouk ne ya leko, yace" ki dena kuka Insha Allah zamu tsaya miki... </p><p><br /></p><p> ********************</p><p>Bangaren su Usman kuwa har yanzu be dawo normal ba duk lokacin da ya tina shine sikar barin husna gidan bejin dadi*</p><p><br /></p><p> Washe gari kamar yanda yai alkawarin zaije nemanta, tun wuri ya tashi shi da mus'ab brother shi sukai wa mamansu karya akan zasukai ziyarane, tace" to adai kula da hanya kuma Karku dade, to kawai sukace suka mik'a Hanya, tafiya suke duk lungu da sako da sunga dandazon mutane sai sun Leka, ko wata mace sukaga tana tafiya sai sun bita har gabanta dan gizo suke musu sesuga tamkar HUSNA... sunyi yawo ba iyaka, basu gantaba, hakan ba karamin daga mai hankali yayi ba</p><p><br /></p><p>Sungaji da nema basuganta, they have no option hakanan suka dawo gida, koda shigarsu gida hajiya taga Usma wani iri take tambayarshi me ya faru! Cemata yayi kawai kanshi ke ciwo! Tace yasha magani ya kwanta,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>*Thank you all masoyana.. Nagode sosai da Addu'a.. Nasama sauki Alhamdulillah.. Allah dai yabar so da kauna... I love you plenty*❤❤</p><p><br /></p><p> *•••AISHAN UMMA TA•••*</p><p> _Ina Tayaki murnar kammala littafinki me suna *MEELA_ADEEL* kinyi kokari sosai... Allah ya Kara basira sweet mamma na_</p><p>❤❤❤❤❤❤❤❤❤❤❤</p><p><br /></p><p> </p><p>*PAGE 61➖62*</p><p><br /></p><p>_Washe Gari_ hakanan usman ya tashi da matsanancin ciwon kai shi komai ma bemai dadi.. Gashi yanzu shikkenan bazai sake ganin husna ba! Hakanan ya tashi ya dauro alwala yazo tai Sallah, ya roka Allah, Allah ya Kara shiryashi, Kuma Allah yasa duk inda Husna take tana hannu na gari</p><p><br /></p><p>Yana idar da adduan.. Kwanciya yayi akan sallayar, Sega Mus'ab ya shugo, ganin yanayin da yake mus'ab ya tausaya mai matuka... Ya dafashi Yace" bro Sekace ba jiya doctor yazo ya dubakaba? Kana tinani da yawa idan Hajiya ta gano kaine silar barin Husna gidan kasan ranka zai baci... Just be strong plz kamanta da komai</p><p><br /></p><p>Wani kirkikar murmushi Usman yayi Wanda beyi niyya ba yace ok dear bro..nan Mus'ab yace hmm you see since morning bakaci komai ba kalle breakfast dinkafa! Zanci usman yace" mus'ab yace better ooo!! </p><p> </p><p> Bangeren su Mufeed kuwa Tun jiya bayan fitarsu da farouk kasuwa sukaje suka dan siyowa Husna kaya, da duk Wani Abu dai da 'ya mace take bukata suka kawo mata, tayi farin ciki sosai. A mind dinta taji dadi tace' oh watakilama da ko gidan iyayena nake bazan sama haka ba</p><p><br /></p><p> Bayan kwana biyune Mufeed na fallow yana zaune ita kuma husna tana Bed room Wani Irin ihu me firgitar da mutun yaji Husna tayi, da gudu ya leko dakin me zai gani? Jini yagani yana kwarara a kafarta... Subhanallah yace" da Sauri ya isa gunta yana Sannu, Sannu baiwar Allah.. Saboda Wani Irin juyo da cikinta ke yi kasa amsamai tayi, daukarta yayi yayo waje da ita yana shirin Sata a cikin mota kenan Sega Hajiya mahaifiyarshi ta window ta hangoshi, ta Kara kallonshi rik'e da husna a hannu ga jini na biyo kafanta, Ihu ta sake hade da fadin INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN tace" jin Muryan mamanshi yayi kafin yasa husna a mota har mahaifiyarshi ta fito tace" mufeed mezangani yau? ta fasa kuka... Nan itama ta fadi kasa sumammiya... </p><p><br /></p><p> °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°</p><p>Bangeren Su ainihin iyayan Husna kowa su sun sadakar ma GABA daya husna bata a duniya.. Dan kullun Addu'an Allah yajikanta da rahama suke.. Allah sarki..</p><p> Bangaren Malan kabir kuwa Rayuwa yamai kunci, kullun ya tino da halin matarshi sai yayi tir dashi, Irin matan nan ne na yayansu sune yaya, 'yayan Wasu kuma oho, Wani kwalla ke shirin zobomai, ya dake, dan kullun harsashenshi zai ga husna.. Addu'a yayi yace ya Allah kasa tana hannu nagari.. Ameen </p><p> </p><p>°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°</p><p>Mufeed na tsaye yaga mahaifiyarshi ta fadi, nan hankalinshi yai matukar tashi, dakyar ya samu yasata a Mota itama, Be wuce da su ko inaba sai asibiti, Ana zuwa Kowanne aka bashi dakin Da zai kwanta.. </p><p> Ana shiga da husna aka dubata aka sanar da Mufeed cikin dake jikintane ya bare.. Alhamdulillah a zuciyarshi yace" Sannan ya Kira Babban aminshi yake sanar dashi ga abun dake faruwa ba... Nan take ya sanar da matarshi yace please ta daure ta hada mai ruwan zafi da abinci yanzu zasukai asibiti</p><p> </p><p> Ummi ce matar farouk ta tambaya waye ba lafiya? Yace my dear please idan munje kya gani, ta lura yana cikin damuwa that's why amsar daya bata taja bakinta tai shuru taje tai abun da ya umurceta, ba'ai 40mins ba ta gama duk abun Da zata, tace" mai nagama mutafi ko? </p><p> Ok yace" ya dakko key suka nufa asibitin</p><p> </p><p>Suna shiga suka ga mufeed a reception yana zaune alamar shima be kwanciyar hankali, tasowa yayi ya karaso inda Suka suka gaisa yace' muje ko! Dakin mummy suka fara zuwa sukaga bata farkaba dan haka suka wuce inda Husna take, tana kwance suka shuga, Inda take suka gaisheta da jiki, tace" Alhamdulillah, Ummi matar farouk Tun shuguwarta taga yarinya kyakkyawa ta fara tambayar kanta shin waneni wannan kuma? Meya hadasu da wannan? Gata dai badai Irin wayayyun nan ba amma gaskiya she's damn beauty, nunfashi taja tace baiwar Allah sannu? Husna ta daga kai a mind dinga tace" tabbas ko ba a fadamun ba wannan matar farouk ce dan na Tina randa suka dakkoni, farouk yace" ba yanda za'ai na kaita gidana saboda inada mata!! </p><p><br /></p><p> Sunyi kusan 30mins A dakin Farouk yace" ummi matarsa ta koma gida zaizo.. Bataso haka ba dan ba yanda zatai ne yasa tace" ok.. Taso ta zauna yaji kwakwaf wannan kuma waye? Dan haka tai tafiyarta amma zuciyarta dam yake da tambayoyi</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Ummiey Xeey*</p><p>[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>*Dedicated to Muhammd lawal❤... Nagode sosai da son book dinnan da kake*</p><p><br /></p><p>*PAGE 63➖64*</p><p><br /></p><p>Ummi tafiyarta tayi amma zuciyarta cike yake dam da tambayoyi.. </p><p> Bayan ta tatafine, farouk ya sake kallon Husna yace" sannu tace" yauwa. Sannan ya maido kallonshi kan Mufeed yace" kaima sannu da kokari! Zai amsa kenan Sega wata nurse ta shugo tacewa Mufeed mahaifiyarka na Kira, Husna najin haka gabantane ya fadi gham tace" yau kashina ya bushe</p><p> </p><p> "Kallon Husna yayi yace mata Muna zuwa" daga kai kawai tayi</p><p><br /></p><p>Su Mufeed suna shiga yaga ran mahaifiyarshi a bace yace" sannu hajiya, kin amsawa tayi, farouk ne ya gaisheta Sannan yace mata ya jiki? Ta amsa da dasauki, Sannan hajiya mum din Mufeed tace" Mufeed yanzu abun maganan, daka dakkomun kenan KO? Wato mace ka kawo Daki kana abun dakaga dama KO? Sai yasa yasa yan kwanakin nan na rasa gane kanka, to Yau ALLAH ya Tona maka asiri</p><p> Ba Mufeed ba hatta Farouk seda ya girgiza akan maganar hajiya, hawaye Mufeed ya fara, Farouk ne yai karfin hali yace" Wallahi hajiya ba hakabane, Rufemun baki tace" Sannan ta Kara da cewa kai me yasa baka kaita dakinkaba, AI kaga kanada mata, dukkansu shuru sukai kamar Wanda ruwa ya cinyesu, hajiya tace" *only Son* wuce kubani waje ka matukar bani mamaki... </p><p><br /></p><p>A fusace Su farouk suka fito dakin, Mufeed ne ya dake hannunshi a bango yace" ya salam yanzu wazai fuskanceni? Na shiga ban daukaba bata fidda barawo, farouk yace" hakane kayi hakuri, Allah na tare damu kuma zai bayyanar da gaskiya insha Allah... Wani Nunfashi Mufeed yaja irin ran maza ya baci sosai... </p><p><br /></p><p> Ita kuma hajiya bayan fitar Su Mufeed, waya ta daga tai calling din Alhaji mahaifin mufeed, yana Abuja.. yaji muryanta somehow yake tambaya lafiya kuwa? Cikin shesshekin kuka take cewa" Ina asibitine Alhaji, baban mufeed yace" meke faruwa? </p><p> Hajiya tace" Wannan Dan ne ya dakko mana magana! </p><p> Alhaji yace" too badai akan aikinshi bane KO? Hajiya tace" wata yai ma ciki!! Ci what? Alhaji ya fada, Sannan yace ganinan zuwa komun dare</p><p>Ok tace" ta katse waya! </p><p><br /></p><p> Bangaren Husna kuwa tun fitowar Su mufeed se addu'a takeyi Allah yasa ba maganarta akeyiba, Wata zuciya tace" kinama yaudarar kankine kinsan tabbas za'ai maganarki tana cikin tinani ne Sega Farouk ya shugo dakin, yaganta cikin wani yanayi yace meyafarune? Tace" Dan Allah nagode da taimakon da kukai nun amma Dan Allah wannar maganar Sirrine tsakanina dakai, karka bari abokinka yaji, yace" ok inajinki</p><p>Husna tace" Dan Allah Zan gudu!! Zare ido yayi yace" mene? </p><p>"Ta Kara cewa Zan gudu"</p><p>Ganin Mufeed kawai sukai a ward (dakin)</p><p><br /></p><p>Basusan duk hirar da sukeyiba Mufeed naji, Daka mata tsawa yayi yace" You're very Stupid!! A wannan yanayin da kike cikene zakice zaki gudu? Well you're free to go, kenan duk labarin da kika bamu karyane? Kuka ta fara tace" Dan Allah kayi hakuri naga ta dalilinane mahaifiyarka ta kwanta a sibitin nan! Kuma wlhi labarin da na fada muku ba karya bane, mufeed ne ya kalleta, yace" yace" ahhh you don't have to worry, mu mukace zamu temaka miki, Kuma insha Allah, Allah zai temakemu gaba daya.. Duk da dai batasan meye ya fada duka ba, amma hankakinta yadan kwanta tace" nagode. Farouk ne yace bakomai, mufeed kam Ko A be Kara cewa ba! Hakanan dai sukai spending kusan 30mins a dakin Sannan Suka fita, koda Suka fita, magrib tayi, sallah farouk yayi Sannan tai musu sallama ya tafi wajen amaryanshi Ummi</p><p><br /></p><p>Yana shiga ummi ta tare mijinta da hug, tamai sannu Da zuwa ya gajiya? Yace" Alhamdulillah, Sannan ta hadamai ruwan wanka, yaje yayi, after ya gama wankan ne yayo alwala time din ankira sallah isha'i, ya gaji be samu yaje masjid ba Dan haka yayi a gida, yana idarwa ya matarshi ta kawo mai lafiyayyan jallof shinkafa da wake yaji manja ga kifi se kamshi abincin yakeyi, </p><p> "Ya kalleta cikin shaukin So yace" sweethrt kullun fa bana gajiya da wannan abincin naki, </p><p>"Ummi tace Allah KO"</p><p>Farouk yace" yes dear </p><p>Ummi tai smiling tace okay lemme feed you.. Shima smiling din yayi yace da KO naji dadi yanda na gajin nan</p><p><br /></p><p>Tana feeding dinshi suna hira seda tacika main ciki fam Sannan yace" sweet hrt Alhamdulillah I'm ok, </p><p>Ummi tace" Masha Allah</p><p>Sannan ta tattara kwanukan wajen takai kitchen tadawo Suka fara hirar masoya</p><p> Anan ne take tambayarshi wai wannan wacece dazu dasukaje gaisheta a hospital wannan tar budurwan! Dan hade rai yayi yace" *YAR AMANA CE* tace" yar amana like how? Yace yanda kikaji ankawo mana itane aka wani case ne Ok tace" Dan tasan irin aikinsu na lawyers</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>_Dedicated to my sweet heart, my sweet cocumber, my chocolatey my Everything_ *REAL KHADY* you mean so much to meeee💪🏼💯</p><p><br /></p><p>*PAGE 65➖66*</p><p><br /></p><p>Farouk ne ya kalle matarsa ciki da tsantsar so, amma wani bangaren na heart dinshi kuma yana tino halin da Mufeed yake ciki, </p><p> Ummi ganin Farouk be cikin hayyacinsane tace" Sweet heart muje ka kwanta ko? OK Yace mata muje suka Shiga daki....</p><p><br /></p><p>Bangaren Husna kuwa tana kan gado ga azaban cikinta na ciwo ga tinanin yanda rayuwarta ya kasance, kuka takeyi sosai a yayin da shi kuma mufeed se yawo yakeyi a cikin asibiti.</p><p><br /></p><p>Around 10pm ne Alhaji Baban mufeed ya shugo asibitin..yana zuwa yaci karo da mufeed a reception wani harara ya balla mai sannan Yace" INA aka kai mahaifiyarka? Jikin mufeed na rawa ya shiga gaba babanshi na binshi a baya har suka Isa dakin da'aka kwantar da mahaifiyarshi</p><p><br /></p><p>Da azama Alhaji ya Isa kusa da ita yana hajiya ya jikin naki? Da sauki tace" </p><p> Mufeed ne ya kalla babanshi dama be gaisheshiba Yace" daddy, you're highly welcome,INA wuni, kallon da dad dinshi kadai ma da yai mai yasan me zai fito bakinshi.. _I don't need your greetings!_ dad said" wani iri mufeed yaji a mind dinshi, Mahaifiyarshi ce tace" hmmmmm!</p><p><br /></p><p> Sannan ya kalle matarshi Yace" hajiya meya faru? Nan ta bashi labarin komai, tana tsayene ta window kawai taga ya dakko wannan budurwar yarinya duk jini na binta, Innalillahi wa inna ilaihi rajiun dad Yace" sannan ya kalle mufeed Yace" Ashe kai mutumin banzane? Kenan karatun Dana turaka kasar waje Allah Kadai yasan ta'asan da kayi, dama hausawa sunce "kwana 99 na barawo, rana daya name kaya, Yau Allah ya tona asirinka</p><p><br /></p><p>Zaiyi magana kenan! Babanshi ya daka mai tsawa Yace" don't say anything wuce ka bani waje, mufeed cikin bacin rai ya fito daga dakin zai wuce kenan Husna ta hangeshi fuskarnan ba annuri da alama iyayanshi suka bata mai rai kuma tasan duk saboda ita ne..cikintane ya d'ura ruwa a mind dinta tace" yau na Shiga uku,nasan wannan mutumin sai yadau hukunci yanda aka batamai rai!</p><p> </p><p> Shi kuma mufeed yana fita rasama Inda zaije yayi mota ya shiga ta saka karatun qur'ani sannan yadan sama natsuwa</p><p><br /></p><p>Bangaren Iyayan mufeed kuma bayan mufeed din y fita, Alhaji ya kalle matar Yace" Hajiya saboda Allah kina mene har haka ta faru? Saida nace ban yarda ya koma part dinnan ba har se randa yai aure saboda irin haka yanzu ga shinan!</p><p> Hajiya hankalinta gaba daya be jikinta tace" to Alhaji ya xanyi, Ko da a part din nawa yake lokacin da zai kawota ba Sani zanyiba, Alhaji Yace" kai Allah dai ya kyauta...Kodai dama ya taba miki maganar zaiyi aurene baki fadamunba? Hajiya tace" wallahi a'a kasan dai ko an mai ma maganar sai Yace" shi ba yanzu ba..</p><p><br /></p><p>Oo oo ohh Alhaji Yace" Allah dai ya kara tsare mana zuri'an mu saboda Yayan Yanzu wasu da yawa ka haifesune baka Haifa halinsuba...Dan *RAYUWAR WASU* sedai muce Allah ya shirya..hajiya tace" Ameen</p><p><br /></p><p> *Washe gariii*</p><p>Tun wuri matar Farouk ta tashi ta sa ruwa a flask, Farouk ya shirya yayo asibiti, A waje ya sama mufeed duk yai wani iri yake tambayarshi meya faru?</p><p> Mufeed Yace" kasan matsalar ai duk kan Husnan nan ne daga temako? Farouk dafa kafadar mufeed yayi Yace" kayi hakuri everything will be ok..</p><p>"Insha Allah mufeed Yace" sannan suka wuce dakin Su mum</p><p> Suna shiga Farouk da mufeed suka gaishesu, amma suka amsa na Farouk sukaqi amsa na mufeed, kamar yai kuka amma ya daure</p><p> Dakin yayi shuru na yan mintina sannan Baban mufeed Yace" Look Farouk inaso na tambayeka wani abu </p><p>Ok Yace" Sannan dad yace,.........!</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kuci gaba fa kasancewa dani....</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>```Find a heart that will love you at your worst and arms that will hold you at your weakest.```</p><p><br /></p><p>*PAGE 67➖68*</p><p><br /></p><p>Baban mufeed ne Yace" look Farouk, I want to ask you something</p><p> Natsuwa Farouk yayi Yace" ok Daddy, shidai mufeed na zaune a gafe</p><p><br /></p><p>Dad zai fara magana kenan hajiya tace" Alhaji ka dakata kawai wannan case din bananan bane Kar inji abun dazai kara dagamun hankali!</p><p><br /></p><p> Toooo Alhaji Yace" amma dai naso nayi magana, Gaban mufeed ne Yace" gham Amma wani bangaren na heart dinshi Yace" to tunda bakai kai ba meya dameka...</p><p> Su mufeed ne suka fito, Farouk Yace" aboki karfa ka damu, kasan bakai kai ba wlhi ko a kunbanka, kabi ka damu ka hana kanka sukunu, Hmm mufeed Yace" kasan iyayanmu irin wannan bawai dauka da sauki sukeyiba..duk da bani nai ba walhi aka matsamun zance nine.</p><p> Smile Farouk yayi Yace" karka fara laifin da bakai ma kace kai kayi, </p><p>Mufeed Yace" to ya sukeso inyi? </p><p>Farouk Yace" ka tsaya kan gaskiyarka ni zan wuce may sai zuwa anjuma..Ok Mufeed Yace ya rakashi har bakin mota sannan ya dawo..</p><p><br /></p><p>Abubuwa dai birjik a mind din mufeed, ko aiki be cika zuwa ba kullun yana cikin damuwa abun tausayi..</p><p><br /></p><p> *Bayan Kwana biyu*</p><p>HUSNA taji sauki Alhamdulillah, itama haka mahaifiyar Mufeed taji sauki, Har an sallamesu amma basu tafi gida ba, mufeed na jiran Farouk, ba'ai minti 15 ba se ga Farouk yazo, nan ya gaishe dasu hajiya da Alhaji, </p><p><br /></p><p>Ita Kam husna tunda taji an sallamesu, ta ayyana a ranta insha Allah yau seta gudu, tunda tasan yau karyanta ya kare, Dan tasan ko Me zatai hajiya ba barin ta ta koma gidan zatai ba...to wai ma idan ta koma dakin wa zata zauna? Da wannan tininin na barta</p><p><br /></p><p>Shi kuma mufeed da Farouk dama sun yanke shawarar idan suka kai Su mummy gida zasu dawo dole Su saman ma Husna waje Su kwato mata yancinta</p><p><br /></p><p>HUSNA CE se leken Su mufeed take a dakin da aka kwantar da Mahaifiyarshi, Suna shirin fitowane Husta ta shugo dakin ta tsugunna</p><p>Hajiya, Alhaji, farouk fa mufeed kowa yayi mamakin ganinta, Alhajine Yace" wannan fa daga ina? Hajiya ta juyar dakai tace" itace yarinyar da nake maka magana ai, Wanda mufeed ya.....! </p><p>Ohh Alhaji Yace" suna shirin fita kenan Husna cikin muryar tausayi tace" _Dan Allah Alhaji kuyi hakuri, d'an ku mufeed kwata kwata beda laifi, wallahi temakona sukayi, dashi da Farouk, nazone na baku hakuri akan Zargin da kukewa mufeed ba haka bane na rantse harga Allah_ </p><p>su Alhaji da hajiya sororo sukai a dakin, Hajiya tama rasa me zatace" too too too tace, </p><p>Zuciyan mufeed kam fari kal atleast zargin da sukemai Susan ba haka bane, Alhaji kuwa Bin Husna da ido yayi, Bayan Husna ta gama maganar ta kenan tace" to Mufeed da Farouk nagode, Ni na tafi sai wata rana, Yanda kuka temakeni Allah ya temakeku, tai mikewarta ta fice...</p><p><br /></p><p>Mufeed kamar ya kamo gefen hijab dinta Yace" karta tafi amma ina ba dama! Hakanan yana gani ta fita.</p><p> Dad ne Yace" to Mu tafi ko? Hajiya tace" eh me zamu jira, Nan Mufeed yaje ya tada mota, Farouk na dayan bangaren, Mum da dad kuma suna sit din baya Suka zauna...nan take ba bata lokaci mufeed ya fara driving.. </p><p> Tun fitar Husna hankalin kowa ya tashi balle mufeed, Ita kanta Mummy da Taga husna hankalinta yadan tashi, suna tafiyane amma Hajiya a ranta tana cewa Ya Allah kasa naga wannan yarinyar, </p><p>Aiko mufeed na driving yasha kwana kenan! Sega Husna ta koma da baya da gudu saura kiris ya kabeta, Innalilahi Yace" yaja burki kiiiiii..</p><p> </p><p> Hajiya da hankakinta yafi kowa tashi tace" mufeed yayane? Shuru yayi fitowar da hajiya da Alhaji zasui kenan sukaga Husna a doke a wajen tana cewa Dan Allah Ku kasheni, Ku kasheni na huta..nan take hajiya da Alhajin sukaji tausayinta. Se a lokacin suma sukaji yanda yaronsu yaji </p><p>Daya ganta, dole duk wani mai tausayi yaga Husna ya tausaya mata,</p><p><br /></p><p>Hajiyane ta kama hannunta tace" kizo muje kinji, kamar Husna bazata bita ba hakana ta shiga motar Suka wuce gida...zuciyar Mufeed yai fari,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>_Wannan page din sadaukarwa ce gareku manyan mata_</p><p>*Ruqeey ce*</p><p>*Mamin nasreen*</p><p>*Amina Ibrahim &*</p><p>*Mummy's frnd*</p><p>Ina yinku irin sosai dinnan💋💋</p><p><br /></p><p>*PAGE 69➖70*</p><p><br /></p><p>"Mufeed driving yakeyi amma gaba daya hankalinshi be tare dashi,</p><p> "Husna kam tunda ta shiga motor in banda kuka ba abun da takeyi, hajiyane da Alhaji duke ta bata hakuri, akan tayi shuru, Husna kam a mind dinta tana cewa" kaico na naga rayuwa Kala Kala taci gaba da kukanta </p><p><br /></p><p> Mufeed kam tinanin Husna yake tayi, yanda take shan wahala a rayuwa, Har ya wuce gidansu bema sani ba, Alhaji ne yace" d'an nan lafiyar ka qalau kuwa? Se a lokacin mufeed ya dawo daga dogon tinanin da yakeyi, yace" afuwan ya seta kan motar zuwa cikin gidan! </p><p><br /></p><p> Suna isa kowa yaje yayi alwala yai sallah Sannan aka tare a fallow, itadai Husna tana gefe tana jiran taga abun dazai faru, Hajiyane tace" baiwar Allah, Meye babban dalilin barinki gida Har wannan abubuwan Meya faruwa dake? </p><p> </p><p>"Husna ce cikin kuka sosai ta soma basu labarin abun da ya faru da Ita tun daga kan accident din da iyayanta sukai, aka saceta, Har Allah yasa Malan kabiru ya Dakkota zuwa gidanshi, daganan matarshi bata sonta, anan ne aka neman mun aiki, duk kudina na karshen wata seta amshe, Har Tsautsayi ya fadamun yaron gidan yamun ciki, to tun daganan tsangwama da habaici matar malan kabiru kullun takemun, wai badai a gidanta, ni kuma ina ganin guduwana shine sauki, to Anna ne na fito da sassafe ina jin jiri ga amai ga yunwa inaji Har Allah yasa na hadu da wa ennan bayin Allah Suka temakamun ta nuna *mufeed da farouk* shine ya kawoni dakinshi, amma koda Nazo ko sau daya be tabama kwana dakinba, sedai ya shiga mota ya kwana.. Har nai miscarriage (bari) to anan ne kika ganmu, ta gama fada kenan ta fashe da kuka ta tashi tace" nagode sosai da karamcin da kukai mun ni zan tafi Sai wata rana..,. Gaba daya dakin sun matukar tausaya mata Valle Alhaji da hajiya dan wannan ne karo na farko da Suka fara jin tarihin rayuwarta, Hajiyane ta rungumeta tace" ba inda zakike, munyi miki alkawarin zamu temaka miki</p><p><br /></p><p>Ita Husna kuwa fisge jikinta tayi a jikin hajiya ta ruga da guda zata bude kofa, da Sauri Su mufeed Suka mik'e ya daka mata tsawa "yace Idan kika kuskura kika fita ko? Hmm</p><p> </p><p>"Tsawar da mufeed yai matane yasa ta dakata dan Ita gaba daya tsoron Shi takeji, kowa a tsaye ya kalleta yace" wuce Ki zauna, jikinta a sanyaye ta dawo ta zauna Su kam kallon ikon Allah kawai sukeyi, Nan take hajiya taji kaunar yarinyar a ranta, dan haka Suka yanke shawarar zata zauna a gidan, amma kuma Mufeed yace" Sai ya dau babban mataki akan *inna matar malan kabiru* dan tana daya daga Wanda Suka jefa Husna cikin tashin hankali </p><p><br /></p><p> Dan haka aka bata Daki, Mufeed yaje ya dakko mata yan kayayyakin da yai saimata, Farouk kuma suna zaune matarshi ummi ta kirashi yace" gashinan zuwa! </p><p><br /></p><p>Dan haka Alhaji da hajiya Suka shiga Daki, Husna ma haka ta shiga dakin da aka bata, Mufeed kuma ya raka farouk yana dawowa ya wuce part dinshi yai wanka ya kwanta a gado, tinanin Husna kawai ya fadomai, Ji yake yana mugun Sonta, kuma yana tausayinta, yanzu kenan da hannun bata gari ta fada shikkenan haka rayuwarta zata kasance a wulakance, Mufeed kam na kwance besan sanda yace" *I love you my Husna ba* </p><p><br /></p><p>Farouk kuma yana shiga gida matarshi Ummi taci kwalliya kana ganinta kasan Beloved husband dinta take jira.. Yana shiga sukai 4eyes dashi wani sanyi taji a mind dinta da salon tafiyarta ta karaso inda yake tace" welcome sweet heart, ya rungumeta sukai Daki! </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bangaren Su hajiya kuma, Koda Suka shiga Daki da Alhaji, kowa shuru yayi na dan mintuna, Alhaji yace" ikon Allah *rayuwar Wasu* fa haka yake! </p><p><br /></p><p>Hajiya ma tace" uhm gaskiya na tabbatar da rayuwar Wasu haka yake, yanzu fa da mun barta ta tafi Allah kadai yasan Wanda zai temaketa yanda zamanin nan ba kowa keda tsoron Allah ba</p><p><br /></p><p>"Alhaji yace Ki bari kawai zamusan yanda za'ai a sata makaranta kawai dan zamanta bazai yuwa hakanan ba, Hajiya tace" Allah ya temakemu yace"ameen</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>```Keep smiling😊, b’coz life is a beautiful thing and there’s so much to smile about.```</p><p><br /></p><p>*PAGE 71➖72*</p><p><br /></p><p>Husna kuwa</p><p> Tun da ta shiga dakin samun waje tayi ta zauna, se tinanin guduwa ya fado mata a ranta tace" yanzu da na gudu ina Zan nufa? Alhamdulillah tace" Sannan ta tashi ta shiga toilet tai wanka tai alwala, ta ziro duguwar rigan da Mufeed ya siyo mata, da tasa yai mata das a jiki kamar dama dan Ita akayi</p><p><br /></p><p> Around 8:30 ne Su Hajiya da Alhaji da Mufeed suna zaune kan dinning suna cin abinci, hajiya taga ba Husna, kwalla mata Kira tayi akan yazo Su zauna suci abinci, Husna ta fito tama manta ba dankwali akanta ga gashi yazubo mata ta leko tace"</p><p> Hajiya a a dakin ma ya isheni, bari dai Nazo na eba, ta fito ta eba hankalin mufeed gaba daya yana kanta yaga ta yi kyau ne, kasa ckn abincin yayi seda Alhaji yai gyaran murya sannan Mufeed ya gane abun da yayi, Alhajine yace" murya a kasa baka da kunya ko? Sosa kai mufeed yayi yace" uhm no dad, Hajiya tace" meyake faruwane? Alhaji yace" ba ruwanki nida yaronane, tace uhm AI kunfi kusa... </p><p><br /></p><p>Husna kuwa, tana daki, fara cin abinci tayi taji dadi sosai, ta cinye sab, Ita robonta dataci abinci me dadin gaske haka tun tana gidan aiki, gashi ta na so ta Karo hakanan ta hakura tace" uhm ba gidan ubana bane.. Allah sarki</p><p><br /></p><p>Su Alhaji sun gama cin abinci kenan daidai lokacin da Husna ta fito, taga hajiya na kokarin kwashe kwanuka tace" hajiya Ki barshi, kafin hajiya ta fara magana Har Husna ta kwashe takai kitchen, da taga kitchen din irin yayi Baja Baja ta tsaya gyarawa daganan ta fara wanke wanke, hajiya taji shuru ta leko taga Husna na wanke wanke Sa mata albarka tayi, kuma taji dadi sosai, Husna tace" bakomai, a zuciyarta tana cewa tab AI wannan aikin me saukine a wajena</p><p><br /></p><p>Seda ta gama komai Sannan ta fito ta samesu a pallow tace" saida safenku, Ji Mufeed yake kamar yace Ki tsaya dan dama saboda Ita ne ya tsaya a pallow din, gashi tace" saida safe.. </p><p><br /></p><p>Misalin 9:30 ne mufeed ya shiga dakinshi dan bacci ina, bacci ya gagara se juyi yake yana tuno kamamnin Husna yanda yaganta dazu, kamar wani mahaukaci ya tashi ta fara yin yanda tayi dazu, Shi kanshi abun ya bashi dariya, dan haka ya dawo ya kwanta dakyar bacci yai awon gaba dashi, koda yai baccin ma nan ma ba tsira yayi ba mafarkin Husna yakeyi barkatai wai gashinan suna park, suna shan iska, ko kuma suna hira </p><p><br /></p><p>Su hajiya kuma bayan fitar Mufeed suma Daki shuka shiga, hajiya seyabawa da hankalin Husna takeyi, Alhaji yace" gaskiyane abunda baka saniba baka saniba da Har munfara zargin ko danmu tarbiyarshi ya lalace Ashe ba haka bane, Allah dai ya kara tsare kullihi musulmi, Ameen, </p><p><br /></p><p>Sannan Alhaji yace" ya batun maganar makarantar ta? Hajiya tace" banko mai magana ba se gobe, Alhaji yace ok barshima Zan mai da kaina hajiya tace ok</p><p><br /></p><p>*Washe gari*</p><p>saboda Monday ne da hajiya ta tashi da wuri dan hadawa maigidanta da Mufeed breakfast dan Kar sui latti, tana kitchen taji tafiyar mutun waigawar da zatai taga Husna tace" kafin tai magana Har Husna ta tshugunna ta gaisheta ta amsa, Sannan tace" hajiya me za'ai? Ki kawo kawai nayi kije ki huta, Hajiya tace" kai yar nan AI da kin barshi ma nayi just arish Zan soya se yar miya se kayan tea, Husna tace" karki damu hajiya nayi aikin da yafi wannan ki kawo wlhi, </p><p> Hajiya tace" kai amma nagode bari na koma Daki nai ida azkhar dama bangama ba, kan kace meye Husna har ta harhada komai ya kasance ready akan dinning,</p><p><br /></p><p>Sannan taje ta sanar da hajiya, kara dai shimata albarka tayi, Husna na shiga Daki Mufeed yaga abinci akan dinning, ya zauna kenan Sega hajiya da Alhaji suma sun fito Suka zauna gaba daya sukai having breakfast dinsu, Mufeed kam cewa yayi" kai Hajiya gaskiya irin wannan zaki dinga mana dasafe, yayi dadi sosai, yana magana yana lashe hannu</p><p><br /></p><p> Hajiya tace" to sannunka bani nayiba, Husna ce" zare ido yayi yace kai!!! Yanaso yayi comment amma ba dama saboda mahaifinshi nanan dan haka yai shuru, amma dai be dena santin abincin ba... </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan sun gamane Mufeed Har ya dauka jaka zai fita dad dinshi yace" yanason magana dashi, Ok yace"</p><p> Wannan dad ya fara magana kamar haka! Mufeed in kasama lokaci inaso ke nemo ma Husna makarantar Boko da islamiya, </p><p><br /></p><p> gaban Mufeed yaji yace" gham</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kuci gaba da kasancewa dani</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*FB PAGE..* </p><p>https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*PAGE 73➖74*</p><p><br /></p><p>Gaban mufeed ne yaji yace" gham, shuru yayi nadan lukuta, dad dinshi na lura dashi yace" anything wrong? </p><p> Girgiza kai Mufeed yayi yace" a a amma dai dad da da da.... </p><p><br /></p><p>Be karasa maganar ba dad dinshi yace" my wish is your command, so kake ta zauna ba arabi ba boko? A a mufeed yace" sannan yace" zanyi kokari a duba insha Allah, smile dad dinshi yayi yace" Allah ya tsare Sai ka dawo, Mufeed yace" Ameen Dad</p><p><br /></p><p>Koda Mufeed ya fito da tinanin maganar babanshi ya tafi wajen aiki, maganar se yawo yake mai, Har abokinshi Farouk yake tambayar"</p><p>Wai ina Husna ne? Nan Mufeed yace" I'm in love with her, kuma wallahi I want to marry her!! </p><p> </p><p>Zare ido farouk yayi yace" you most be joking, </p><p>"I'm serious Mufeed yace" farouk yace babban magana, yau Mufeed kaine da maganar aure??</p><p><br /></p><p>Mufeed yace" kwarai kuwa, nine, Suprise farouk yace"</p><p>Mufeed yace" meye abun mamaki, ni ba mutun bane ko dama ance bazanyi aure bane? Farouk ya fara magana yana murmushi yace" woo wane ni, abun da mamakine kai da ban tabaji ma kana maganar aureba duk yan matan da suke kawo kansu gareka baka sauraran kowa, se yau rana tsaka kace ma Husna zaka aura, AI akwai mamaki, </p><p><br /></p><p> Shuru Mufeed yayi yace" uhm nima haka kawai fa naji jarinyar tamun, kuma naji ina san ta kasance matata, very good farouk yace" sannan yace Su hajiya sun sani ne kuwa? A a Mufeed yace" Dad ne fa wai na nemo mata school ni kuma yanda take da kyan nan da hankali yaushe Zan bari taje chan wani ya ganta yace yana so, dariya hahaha farouk yayi sannan yace maza an shugo gari, ka manta lokaci da nace yarinyar nan tanada kyau, kace ba wani kyau da take dashi se yanzu ka gani kenan ko? Mufeed cikin burin kunya yace" eh naji dai, yanzu kaban shawara, </p><p><br /></p><p>Farouk yace" shawara guda dayace kawai ka nemo mata islamiya inyaso boko din ko tana gidan ka se kai, good idea Mufeed yace sannan kowa ya ci gaba da harkokinshi Har Suka tashi daga office din</p><p><br /></p><p>****************************</p><p>Koda Mufeed ya dawo nan ma Ganin Husna yayi tare da mahaifiyarshi suna kitchen suna abinci, kayan da tasa yai wani mugun mata kyau, idon Mufeed kyar akanta duk husna taji wani iri a daddafe dai ta samu Suka kammala, shikam mufeed fallow ya dawo</p><p>husna ta fito daga kitchen kenan, taci karo Mufeed a pallow again, wani kallon I love you ya jefo mata tajita duk wani iri</p><p><br /></p><p> Daki ta shiga tace" ya salam meke shirin faruwane haka? Me wannan guy din yake nufi,</p><p><br /></p><p>Shikam Mufeed be ki kullun ya dinga ganinta ba, a zuciyarshi Har cewa yake inama ace time din Dana dawo daga malesia ne da Idan na kura mata ido se Allah, hakanan ya karace zaman Shi a pallow din husna kam taqi fitowa</p><p><br /></p><p>A yan kwanankin nan husna Sam bata yarda da da irin kallon da yake mata ba, a zuciyarta tana tsoron Kar abun daya faru fa Ita ya sake faruwa da Ita dan haka kwata kwata da taji motsinshi seta boye</p><p><br /></p><p>Da dadarene husna na juye ruwa a bucket tana kitchen zatai wanka, Shi Mufeed yana sha mum dinshine a kitchen ne dan haka ya shiga kai tsaye, yana shiga sukai ido hudu da husna, ajiye kettle din tayi jikinta na rawa tace" dan Allah kayi hakuri, Shi abun dariya ya bashi yace" meya faru? Tace inajin tsoro ne, Smile yayi yace karki wani ji Tsoro *HUSNA ina sonki kuma Zan aureki* sake baki tayi tace" wane ni kafi karfina, jin tafiyar mummy yayi, ya daga mata gira yai ficewarshi, itakam Husna tsayawa tayi abun na bata mamaki</p><p><br /></p><p>Chan taji hajiya nama Mufeed magana tace" Ya maganar kamarantar? Mufeed karya yayi, yace" na mata magana! Nace zuwa jibi laraba kenan ta kintsa nakaita, Masha Allah hajiya tace"</p><p><br /></p><p>Husna da take tsaye a kitchen abun mamaki ya bata ko yaushe Mufeed yai mata magana oho, dan haka ta dauka ruwan zafinta takai Daki, tayi wankarta</p><p><br /></p><p>Bayan tayi wankanta ta dauro alwala tazo tai sallahn magrib tanajin hayaniyar Su Mufeed da Hajiya a pallow taqi fitowa, shikam Mufeed duk haushi yabi ya isheshi, ganin husna bata fito ba, yai wa mum sallama, itama tanajin ya fita ta fito tai joining Hajiya Suka fara kallon Arewa 24 ana wani film </p><p><br /></p><p>Bayan Mufeed ya shiga dakinshi, ya lalubo wayarshi yaji babu Ashe ya manta dashi dakin Hajiya, dan haka ya dawo, zai dauka yaci karo da kyayyawan yarinyar da yakeson gani a ko yaushe, dan haka daga daukar waya ya bige da kallo shima...se satar kallon husna yake </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Team Mufeed*😍</p><p>[4/15, 2:29 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM* </p><p> _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_</p><p><br /></p><p>*FB Page* </p><p>https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>*Where is Maryam Aliyu A* mar'ahmad your page is here, I love you so much💋💋💋</p><p><br /></p><p>*PAGE 75➖76*</p><p><br /></p><p>Kallo Sukeyi amma idon mufeed na kan husna, Ji tai ta kasa zama a pallow din dan haka tace hajiya saida safe, maganar datai mufeed kam ya bashi haushi, Hajiya tace" har zaki kwanta?</p><p>Eh tace ta tashi tai wucewart daki, tana shiga gado ta fada, tafara tinanin wai shin me yaya mufeed yake nufi ne haka? Da wannan tinanin tai bacci</p><p><br /></p><p>Bangaren mufeed shi kuma tun time din d husna ta shiga daki ji yai kamar ya bita too faa, Dan be gama ganin kyakkyawan fuskarnan ta ta ba...yana zaune wata zuciyar tace" what are you waiting for? Wanda kazo Dan ita ta tafi daki kai me kke jira? Phone dinshi ya dauka yai wa mamanshi seda safe, Itama hajiya da taga kowa ya tafi bacci kashe kayan wutar dakin tai itama taje ta kwanta</p><p><br /></p><p>Mufeed tun da ya shiga daki kasa samun natsuwa yayi, Kwanciya yayi Amma ina kasa bacci yayi, Dan haka ya mik'e yama rasa me zaiyi, rarumu waya yayi zaiyi dialing numbern farouk ya tuna fa yana chan tare da matarshi, kuma beso ya takuramai dan haka ya kyaleshi, hakanan ya kwanta besan ma sanda bacci yai awon gaba dashi ba, a cikin baccinshine yai mafarkin wai gashinan shi da husna akan dining tana feeding dinshi, smiling yayi, be wani Dade a baccin ba ya farka, a ganshi a gado wani tsaki yaja, dole ya sake addua yai bacci</p><p><br /></p><p>*Washe gari*</p><p>Kamar kullun husna ta saba tashi da wuri kasan cewar weekend ne, kitchen ta fito tana so ta hada musu break fast, motsi hajiya taji ta fito, husna CE ta gaisheta, hajiya tace" bakya gajiyane? Da kinje kin kwanta se 10 tunda yau ba aiki, mufeed ba fita Zaiyi ba, Ok tace" ta koma daki tai kwanciyarta</p><p><br /></p><p>Misalin 10am din hajiya da taji shuru bata fito ba dan haka ita da kanta ta Shiga kitchen ta hada komai na breakfast, sannan tazo ta jera kan dining, tana cikin jerawane, Sega Husna ta fito tace" laa hajiya badai kin gama ba?</p><p><br /></p><p>Hajiya murmushi tayi, tace" aiko na gama kinga kema kin huta ko? Husna tace uhm Amma ba haka nasoba, hajiya tace" bakomai, je kiyi wanka kizo muci abinci, toh tace" ta juya tai daki</p><p><br /></p><p>Tana Shiga dakin kamar an jefo mufeed, yana ganin abinci a Jere a dining ya nufa ya zauna, Hajiya ta fito kenan tace" har ka tashi kenan? Sosa kai yayi yace" eh wlhi ina kwana hajya?</p><p>Lafiya lau ta amsa sun fara hira kenan Sega Husna ta fito cikin wani atamfa Riga fa siket yayi mata kyau sosai, Dosowa wajen tayi cike da faduwar Gaba, Tasa waje ta zauna itama, hajiya ta kyalleta tace" kinyi kyau, duk'ar da kanta kasa tayi ta fara wasa da yan yatsunta, </p><p><br /></p><p>Mufeed kam dam tun da yaga ta fito dama idonshi na kanta, mind dinshi yace" kai masha Allah, ahaka suna dan Fira har suka gama, zai fita kenan ya juyo yace" Husna, anjuma ki shirya zan kaiki makarantar islamiya ai miki registration, Toh tace"</p><p><br /></p><p>Mufeed na fita, gidan abokinshi farouk, ya wuce, nan ya sameshi da matarshi se hiran masoya sukeyi abun ya burgeshi...</p><p><br /></p><p>Farouk yace" abokina ya akai ne? Yace" walhi Alhamdulillah, akan dai maganar rannan ne</p><p><br /></p><p>Farouk yace wato kananan kan bakarka ko? Mufeed yace kai ma ka sani ae, itadai ummi na jinsu bata ce musu komai ba,</p><p><br /></p><p>Sun taba hira sosai wajen yanda zasu bulluwa wannan al'amarin, farouk ya bashi kafin gwiwa sosai, sannan yamai fatan alheri sukai sallama ya dawo gida</p><p><br /></p><p>Misalin 4:pm, Husna ta shirya, tana zaune Sega mufeed yace" mu tafi ko malama? Daga kai tayi sannan sukai waa mama sallama tace Allah ya tsare</p><p><br /></p><p>Sun fito harabar gidan, mufeed ya tada mota yace" Bismillah ki shugo mana, Bude back site tayi, yace" no Husna ki shugo gaba mana?</p><p><br /></p><p>Uhm tace" sannan ta bude front sit zauna</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Ummie Xeey*</p><p>[4/15, 2:29 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM* </p><p> _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_</p><p><br /></p><p>*FB Page* </p><p>https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>_Woooo where are you ♻exclusive ladies... The whole page is for you guyz, inajin dadin zama daku Allah ya kara hada kawunanmu_ *#ONE LOVE*💘💘</p><p><br /></p><p>*PAGE 77➖78*</p><p><br /></p><p>Husna ce tace" uhm sannan ta bude front sit ta zauna</p><p>Mufeed kam kallonta yayi yai smiling sannan ya tada motar ya fita a harabar gidan!</p><p><br /></p><p>Suna cikin tafiyane kafin su karasa school ne yace" Husna nace ina sonki baki cemun komai ba? Itadai shuru tamai har suka isa makarantar</p><p><br /></p><p>Nan ya fito akai mata komai sannan aka bata class akace no need ta koma gida, ta zauna kawai tayi karatu, Ok mufeed yace" da zai tafine ya kirata yai mata nasiha akan ta maida hankali, kuma ta san d frnds din da zatai Hulda, infact shi beso ma ta kula kowa, Yace" ya tafi sai ya dawo daukarta, Tace Ok Allah ya kaimu,</p><p><br /></p><p>Husna na shiga Aji, taga duk yan yarane ma ba wasu manya sosai, dan haka taje kusa da wata yar babba kamarta a zauna, nan dai suka gaisa tace" sunanta Husna, kawar kuma tace" Sunanta Khadeeja...</p><p><br /></p><p>Khadeja irin wayayyun yaran nan ne, itama boarding school aka kaita har ss2 ta gudu sai yasa batai islamiya da wuriba, </p><p><br /></p><p>Nan dai suka fara karatu har aka tashi, Yau dinnan da haduwa amma Jinin Khadija da husna ya hadu sosai..</p><p><br /></p><p>Misalin 6pm aka tashi, Khadija da husna suna tafe har bakin gate, khadija tai gida husna kuma ta tsaya jiran mufeed, magana taji from no where akace" Zo mu tafi ko? Firgita tayi, sannan daga baya ta gane muryan waye, sannu da zuwa tace" shikam bece komai ba illa binta da ido da yai, gaba daya shi mufeed yarinyar na burgeshine,</p><p><br /></p><p>Husna ce taga kallon ya isa haka tace" yaya mufeed mu tafi gida kaga Kar hajiya tayi fada"</p><p><br /></p><p>Ok yace" sannan yace wlhi kullun ina son kasancewa dake, itadai uhm tace ta bude mota sannan shima ya shiga, koda ya shiga ba Wanda yacewa kowa komai har suka isa gida, suna shiga hajiya tace" oyoyo y'ata sannu da dawowa </p><p><br /></p><p>"Husna yauwa tace" sannan ta shiga daki Dan ajiye takardu, mufeed ne yace" ni ba'acemun ba, hajiya dan hararanshi tayi, sannan yace" uhm bari na je dai nai alwala time din magrib ya kusa, hajiya tace" atoh, bayan mufeed ya fita a dakin, Husna ta fito ta Dan kakkama ma hajiya aikacen aikacen gidan suka kammala kafin magrib, kowa yai sallah sannan sukaci abinci 10pm nayi kowa yai bacci Dan sun gaji</p><p><br /></p><p>Mufeed kam daya Shiga daki, kiran abokinshi yayi, yake sanar mai da cewa ya furta mata yana sonta!! Farouk yace" me tace? Mufeed yace" shuru tayi, Farouk yace very good yanzu kawai ka sanar dasu hajiya, Ok mufeed yace sannan sukai sallama</p><p><br /></p><p>Washe gari kamar kullun husna ta tashi tai duk abun da zatai kafin lokacin islamiya,</p><p>Time nayi Sega mufeed, ya shugo yace" ki sameni wajen mota, ok tace" yai ficewarshi, yana zaune Sega husna ta fito, nan take ya dauko wayarshi ya kashe mata hoto, ita duk bata saniba</p><p><br /></p><p>Takowa tayi har wajen motar sannan ta shiga, taga kamar yadin uniform din ta akan screen din wayarshi, Amma bata gani dakyau ba Dan batasan waye ba kuma bazata Iya tambayarshi waye ba sai yasa ta basar</p><p><br /></p><p>Haka suke ta tafiya, har suka isa, tana zuwa bakin gate taci karo da kawarta, khadija, kiranta tayi, ta tsaya suka jera tare, </p><p><br /></p><p>Khadijane tace" wannan yayankine? Gaskiya yanada kyau, husna ji tai wani kulolo ya tsaya mata a zuciya yana da kyau? To me wannan yarinyar take nufine?</p><p><br /></p><p>Haka dai suka shiga Aji, Amma yanayin husna daka ganta kasan abu na damunta, khadijace tace" menene yar uwa? Karyan dole husna tayi tace" iyayena nake tinawa! Wani kallo khadija tai mata irin bata gane me take cewa ba, khadija tace" wanchan ba yayanki bane? Girgiza kai tayi tana hawaye tace" a a! Khadija abun ya bata mamaki tace" Amma naga kuna kama, meye dangartakarki dashi???</p><p> </p><p>Husna ta fara kuka tace" nasan zaki rikemun amana bari na baki tarihin rayuwata, khadija ta gyara zama tace" inajinki....</p><p><br /></p><p>"Nan Husna ta fara cewa"</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>.</p><p>Ummiey Xeey</p><p>[4/15, 2:29 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM* </p><p> _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_</p><p><br /></p><p>*FB Page* </p><p>https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>*Emnoor Ahmad don* I miss you like crazy......😭😭</p><p><br /></p><p>*PAGE 79➖80*</p><p><br /></p><p>"Husna ce ta fara kuka tace" nasan zaki rikemun amanata, Khadija tace" insha Allah, </p><p>Husna tace to bara na baki tarihin rayuwata, khadija ta gyara zama tace" inajinki</p><p><br /></p><p>Nan husna cikin shesshekin kuka ta fara magana tace" kinga wannan dinnan d kike gani shi ya cece rayuwata da yanzu bansan Inda nake ba a rayuwata, Farkon labarina ya farane tun ranar da zamu kawowa yan uwanmu ziyara daga kano zuwa Kaduna, anan mukai accident, kinsan mutane ba tsoron Allah, ganin iyayena da sukai, ba cikin hayyacinsuba, wasu yan yankan kai suka saceni, Nan khadija ta zare ido, tace Allah sarki, daganan Allah yasa ogansu jinina ya hadu dashi, kullun seya kawoun kayan dadi naki ci, da yake ina addua Allah bai basu sa'a akaina ba hakanan aka fito da ni daga wannan gidan, daganan aka kaini gidan me unguwa na hadu da wani malan kabiru yace zai daukeni, indai takaice miki labarin banji dadin zamn gidan nan ba, Anan ne takaini gun aiki, na hadu da yaron matan, yai mun fyade, A'uzubillah Khadija tace" lalle kam ta fada a zuciyarta kaidai kaga mutun bakasan wahalan da yake sha ba</p><p><br /></p><p>Husna taci gaba d cewa to tun daga ranar da inna matar mlm kabiru, ta lura ina da ciki, zagi, tsangwam ba wanda banshaba, karshe kawai na yanke hukuncin guduwa dan ta hakane zan sama sauki</p><p><br /></p><p>"Ina cikin tafiya ni kaina bansan ina zanjeba ga jiri, ga yunwa ga amai, kinsan ciki se ahankali, kawai Allah ya jefo su yaya mufeed da Farouk Nan Suka temakeni, har mufeed ya kaini gidansu, anan ne cikin ya bare, yazo zai kaini asibiti kenan mamanshi ta ganshi, Toofaa khadija tace" lalle kin ga *RAYUWA* </p><p><br /></p><p>hmmm haka dai ta bata labarin yanda akai komai, har shuguwarta islamiyar nan, Amma bata sanar da ita cewa mufeed na sonta ba kinjii dai labarina tan gamawa ta fashe da kuka</p><p><br /></p><p>"Khadija tace Wallahi kinban tausayi, Amma ki godewa Allah ma da kika fado hannu na gari, yanzu dai ki dena kuka komai zaizo karshe, dakyar dai husna tai shuru, ita kuma khadija ta fara bata labarin rayuwarta</p><p><br /></p><p>"Tace nidai sunana Khadija ina zaune d iyayena lfy lau, gaskiya ba abun daya faru dani, intact dai Alhamdulillah komai daidai, kema karki damu, Allah na tare dake, ki manta da komai ki rike Allah, Zakiga komai naki naci gaba..Su kuma Su mufeed Allah ya Saka musu da alheri....tace" Ameen</p><p><br /></p><p>Ranar dai ba wani karatun kirki sukai ba, har aka tashi, ko wanninsu ya tafi gida da daukin amininshi, Husna kam ta sama kawa har ta kosa gobe tayi</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hakadai rayuwarsu ta kasance kullun cikin zumudin juna suke, daka kalla husna kasan Alhamdulillah yanzu damuwa ta Dan ragun mata duk saboda friend, at least ta sama abokiyar hira duk da a school kadai suke haduwa</p><p><br /></p><p>Shikam mufeed kullun kara sonta yake, idan yananan Saturday & Sunday kullun yaje dakkota yaganta da babban aminiyartau se yaji kishi, a mind dinshi yana inama dashi ake wannan hiran!</p><p><br /></p><p>Yaune sun tashi, yazo daukanta yaganta dai da babban kawarta, kamar yace" ke Kar ki sake mata magana Dan shi mufeed bameson yaga Wanda yakeso tana Hulda d mutune bane, hakanan dai ya hakura har yana hararar khadija saboda kishi,</p><p><br /></p><p>Yace" husna shiga muje....Khadija tace" Bestie sai gobe, husna tace" ok bestie byeee</p><p><br /></p><p>Mufeed na jinsu yace a zuciyarshi" zakuci kaniyarku da bestie dinnan...lol</p><p><br /></p><p>Murtuke fuska yayi yace" waye wannan daga zuwa ko 1month bakiyiba zaki fara jajiban kawaye anan ne ake chanzawa mutun ra'ayi, itadai batace komai se surutanshi yake irin ran maza ya baci dinnan</p><p><br /></p><p>Suna Isa gida, Mufeed yaga Car (Mota) din babanshi, yaji dadi sosai, Dan dama be gari kwana biyu, yanzu mufeed Nada damar dazai sanar d mahifishi abun dake ranshi, Dan haka yai parking suka shiga tare</p><p><br /></p><p>Suna shiga suka tarar da alhaji da hajjya a falo, nan suka gaishesu, husna tai daki mufeed kuma ya tsaya gun dad dinshi</p><p><br /></p><p>Suna hira, Magrib yayi babanshi yace" zuwa anjuma yanason magana d mufeed yazo ya sameshi, Ok mufeed yace"</p><p><br /></p><p>Misalin 9:pm mufeed ya shiga dakin babanshi da sallama, ya sameshi d hajiya suna hira</p><p><br /></p><p>Alhaji ya kalle mufeed yace" wato duk abun Dana tsara seka chanzako? Ba harda boko nace kasa Husna ba, dan me bakai abun Dana saka kaba yanzu kusan 2moths</p><p><br /></p><p>Budan bakin Mufeed yace" dad I'm sorry dalilin da yasa bansata boko ba ina son aurantane!!!</p><p><br /></p><p>Hajiya da Alhaji suka zare ido sukace mene???</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dan jin cigaban labarin sai kuci gaba da biyoni</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[4/19, 3:22 PM] Ummi Abubakar😃: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM* </p><p> _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_</p><p><br /></p><p>*FB Page* </p><p>https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wooo where are you *Safiyya A Yunus😍* _your page is here...Naga Book masha Allah, Allah ya kara Basira dear_</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*PAGE 81➖82*</p><p><br /></p><p>Budan bakin mufeed yace" dad I'm sorry dalilin da yasa ban kaita boko ba inason aurantane!!!</p><p><br /></p><p>Hajiya da Alhaji suka zare ido sukace mene???</p><p><br /></p><p>"Mufeed ne yakara kaskantar da murya yace" ina son aurantane, hajiya dai tai shuru, Alhaji kuma yace" Mara kunya har zaka duba idonmu kace zaka aureta To Sam ban yardaba, dad ya mike yabar dakin!!</p><p><br /></p><p>Hajiya tai sororo a zaune shima mufeed kasa motsi yayi, Hajiyane tai karfin Hali ta mike tabi Alhaji, </p><p><br /></p><p>Bed room dinshi ta bishi, taga ya zauna yayi tagumi, hajiya ne tace" haba Alhaji, meye dalilin da yasa bazaka amincewa d'an mu ba?</p><p><br /></p><p>Alhaji cikin fushi yace" haba Matata taya za'ai na amince mai? Bayan bebi umurnina ba, ni bama haka ba, nafiso ya sama yarinya me asali, duk da nasan ta fada mana iya gaskiyanta be zama lalle gaskiya bane, Hajiya tace" hakane Amma Dan Allah kayi hakuri, </p><p><br /></p><p>Suna cikin magana kenan Sega mufeed ya shugo idonshi yayi jajur gab yake da zubar da kwalla, yazo ya tsugunna gabansu yana basu hakuri akan su amincemai ya aura Husna</p><p><br /></p><p>Alhaji Sam yai kamar bemasan mufeed na magana ba, "mufeed ne ya kara da cewa dan Allah abba kayi hakuri, se a lokacin dad ya kalle mufeed yace" na Riga na fada maka kuma bazan chanza ra'ayina ba...ka tashi ka fita ka bai waje</p><p><br /></p><p>Allah sarki uwa, Abun da alhaji yai wa mufeed Sam bataji dadi ba, Dandai ba yanda zatai ne, "mufeed ne ya mik'e yaji kafafunshi sun mai nauyi, dakyar ya fito yazo wucewa ta pallow kenan yaga Husna.... I'm a loser ya fada a mind dinshi, yana fita wasu zafafan hawaye suka zobomai, dakyar dai ya karasa daki, koda ya shiga daki nan danan yaji duniyar gaba daya batamai dadi, yanzu abun da yake burin samu shikkenan bazai samu ba, ji yai kanshi ya fara ciwo, kwanciya yayi a gado, abun tausayi be dade ba bacci yai awon gaba dashi...</p><p><br /></p><p>Hajiya kuma se ba alhaji hakuri takeyi tunda shi da kanshi ya nuna yanaso yayi hakuri kawai, inyaso sa bishi da addua"</p><p><br /></p><p>Alhaji yace shima fa sam karma ta sake mai maganar auransu dan bayuwuwa zaiyiba dan haka taja bakinta tai shuru.</p><p><br /></p><p>Mufeeed kam Dama tun da ya shiga daki yai bacci bashi ya farkaba se 3 na dare, yana tashi ya duba yaga 3 toilet ya shiga ya dauro alwala yazo yana fadawa Allah bukatunshi, bashi ya koma bacci ba har seda akai sallar asba'i</p><p><br /></p><p>Bangaren su hajiya kuwa an kammala kayan break fast, har 11 shuru mufeed baizoba, Alhaji shima yadan damu yasan dalilin qin zuwanshi Amma ya basar, Hajiyane tace" naji wannan yaron shuru bari dai na je nadubashi ko lafiya, Alhaji binta da kallo yayi kamar yace kar taje amma shima yanason sanin wani hali danshi ke ciki</p><p><br /></p><p>Hajiya ne ta tashi ta tafi part dinshi ta murda kofan taji a kulle, buga kofar sosai tayi, shi kuma mufeed cikin bacci yaji kamar ana knocking kofa, dakyar dai ya tashi, yaje ya bude yaga ashe hajiyarshi, </p><p><br /></p><p>Kallo daya tai mai ta gane mufeed beda lfy, dan idonshi yayi ja, kuma irin beda kuzari haka, Son meke damunka tace"</p><p><br /></p><p>Girgizakai yayi, alamun ba komai, hajiya tace" I can't believe this, taba jikinshi tayi taji zafi *ramm* subhanallah tace" hade da cewa sannu Son, yauwa yace, "tace bari naje na fadawa babanka baka da lfiya,"</p><p>Har ta juya zata tafi ya kamo hannunta yace" mum please don't tell him na gwammace na mutu tunda dad yace bazan aura Husna ba</p><p><br /></p><p>Hajiya ne tace" you're mad kar in karajin wannan maganar a bakinka, mahaifinkane, ka dade kana mai biyayya kar Dan yace bazaka aura husna ba ka qi mai biyayya, Mufeed shuru yayi, sannan hajiya ta fita!!</p><p><br /></p><p>Koda ta fita da rawar jiki ta isa gun alhaji tana cewa" Alhaji kazo son beda lafiy, Alhaji smiling yayi a mind dinshi Dan yasan musabbabin rashin lafiyarsa, be bar wajenba seda ya kira doctor dinsu yace" maza yazo akwai Patient a gida, doctor yace ok!</p><p><br /></p><p>Bayan Alhaji ya gama waya da doctor ne ya kalle hajiya yace" muji in ganshi, itadai Husna na gidan Amma batasan wainar da ake toyawaba, tagadai mufeed be fito ba tana sha ma aikine ya rikeshi</p><p><br /></p><p>Hajiya na tafe Alhaji na biye da ita har suka isa dakin mufeed, a kwance suka taddashi ya rike kai, abun yaba Alhaji dariya, a mind dinshi yace" yaro yaso Aure, Dan Alhaji irin iyayen nan ne Wanda suke friendly da yayansu, kusa dashi Alhaji yazo ya dafashi, yace ya jikin?</p><p><br /></p><p>Mufeed cikin wani irin murya Wanda kanaji kasan Abu na damunshi yace" dasauki dad, </p><p><br /></p><p>Babanshi dariya yayi, Sannan yace"Allah ya kara sauki, mufeed yace Ameen, suna zaune daga doctor ya kira Alhaji yana sanar dashi ya iso...</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey xeey</p><p>[4/19, 3:23 PM] Ummi Abubakar😃: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM* </p><p> _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_</p><p><br /></p><p>*FB Page* </p><p>https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>_Respect people’s feelings. Even if it does not mean anything to you, it could mean everything to them._</p><p><br /></p><p>*PAGE 83➖84*</p><p><br /></p><p>Babanshi dariya yayi, Sannan yace" Allah ya kara sauki, mufeed yace Ameen, suna zaune sega doctor ya kira Alhaji yana sanar dashi ya iso...</p><p><br /></p><p>Alhaji yace" okay sannan ya mik'e ya fita yamai iso har cikin dakin mufeed, Nan doctor ya fara gwaje gwajenshi, har ya gwada BP dinshi yaga yayi high sosai,</p><p><br /></p><p>Doctor din was shocked daya gani, yace" Amma Alhaji meke damun yaron nan haka cikin lokacin kadan jininshi yahau sosai, gaban Alhaji ne yace gham!! Hajiya a mind dinta kuma tace Subhanallah,</p><p><br /></p><p>"Alhaji yace doctor please kayi duk abun da zakai, Dr yace ok insha Allah, Amma fa gaskiya in akwai wani abun da yakeso a bashi Dan BP din nashi ya sauka in ba haka ba kuma akwai matsala, Insha Allah Alhaji yace" nan dai doctor yamai duk abun daya kamata, yace zuwa anjuma in drip din ya kare a kirashi ok sukace sannan yar tafiyarshi,</p><p><br /></p><p>Hajiya tace" mu tafi ko Alhaji ya huta, Jikin Alhaji a sanyaye yace" ok</p><p><br /></p><p>"Suna fita mufeed ya raromu wayarshi ya kira abokinshi, yake sanar dashi ga yanda sukai da dad, Farouk beji ddi ba shima Sam Amma yace" yayi hakuri gashinan zuwa inyaso se Su tatauna, Ok yace"</p><p><br /></p><p>Hajiya kuma suna komawa part dinsu taga Husna har ta daura sanwar rana, tace" kekam baki hutawa, husna tace" ae gwanda na rage miki aikin kafin na tafi islamiya, hajiya dai tace" aiko nagode, tanajin son yarinyar har cikin ranta...sannan hajiya tace" yayankifa beda lafiya!!</p><p><br /></p><p>Gaban husna na yai mugun fadi, hajiya na shigewa daki tai maza ta dakko hijab dinta tai dakin mufeed da gudu, tana zuwa bakin kokar kuma taji kunya ta kasa shiga</p><p><br /></p><p>Minti daya, biyu uku, taga dai ba sarki sai Allah ta murda kofar, tana shiga da sallama sukai 4eyes Dashi, wani murmushi ya sakar mata aranshi har yaji wani sanyi, itakam duk kunya yabi ya isheta, karasowa tayi a kunyace ta sama waje ta zauna ta gaisheshi, sannan tacemai ya jiki? Yace" Alhamdulillah, sannan tace" kamaci abinci kuwa?</p><p>A'a yace" </p><p>"tace bari naje dakkoma sannu, </p><p>Shidai binta da ido kawai yakeyi, Dan komai tayi kara birgeshi da sonta shiga jinin jikinshi yakeyi,</p><p><br /></p><p>Aiko mik'ewa tayi taje ta dakkomai break fast dinshi, dawowar da zatai kenan, taga farouk a cikin dakin, nan kunyarta ya karu, a sanyaye ta gaisheshi, sannan tace" yaya mufeed gashi, ita Sam bata daukeshi saurayiba, Dan tun temakon da sukai mata wani girmama na musamman take basu, bayan ta ajiye abinci, tace" yaya gashi kaci, Abun ya burge farouk yanda yaga tana kula dashi sosai, </p><p><br /></p><p>Farouk ya tafa hannu yace" masha Allah, amaryan mu ashe dai kinason abokin nawa!!</p><p> </p><p>Ji tai maganar ya mata banbarakwai, nan take taji wani iri tana so ta fice, mufeed yace" ya zaki tafi bayan bazan Iya ci in baki kusaba? Kunya taji sosai ta rufe ido da Sauri ta fice, abun dariya ya basu sosai, sukace Husna akwai kunya!!</p><p><br /></p><p>Bayan fitar tane, Nan mufeed ya kwashe labarin komai yanda sukai da Alhaji ya sanar da farouk, </p><p>Farouk" yace karka damu, zamui magana da Alhaji, nan dai suka gama hira </p><p><br /></p><p> Ummi matar Farouk kam ta kira, se kira take, wai tana missing dinshi, abun burge mufeed ykeyi, hardai ya gaji ya amsa wayar yace" gashinan dawowa ba cinyeshi zanyiba, Nan dai taji kunya tacemai ya jiki!! Misalin 6pm farouk ya koma gida</p><p><br /></p><p>Ita kuma husna tana dawowa gida daga islamiya bata wuce ko inaba se dakin mufeed, tana shiga taga drip din da aka samai yama kare,</p><p><br /></p><p>Tana kokarin cirewa kenan, mufeed yace wait baki iyaba, tace Allah na Iya, ai lokacin dana kwanta a asibiti naga yanda akeyi, yace ok shikkenan ciremun nagani, tana kicikicin ciremai drip din kenan Sega Alhaji da hajiya sun shugo, husna ta tsorata, Su hajiya da Alhaji abun mamaki ya basu, wato dama wa ennan yaran soyayya sukeyi ko? </p><p><br /></p><p>Tana cirewa, Hajiya tace" sannan, dasauri husna ta fice, Alhaji kuwa kasa cewa komai yayi</p><p><br /></p><p>Kuci gaba da biyoni</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[4/19, 4:13 PM] Ummi Abubakar😃: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM* </p><p> _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_</p><p><br /></p><p>*FB Page* </p><p>https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>*Aisha a muhd😍 & Aishan umma😍* woooo uwayen dakina...Halinku na gari ya biku a duk Inda kuke..Gaskiya ina sonku har cikin raina...Allah ya kara daukaka.... *I love you*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*PAGE 85__86*</p><p><br /></p><p>"Husna na gama ciremai drip din, "hajiya ta kalleta tace sannu"</p><p><br /></p><p>Da sauri husna ta fice, Alhaji kuma kasa cewa komai yayi,....Mufeed ne yace sannunku hajiya!!</p><p><br /></p><p>Alhaji kallonshi yayi yace" banace bazaka aureta? Danme zaka dinga inviting dinta har cikin dakinka? Kai soyayya dadi ko?</p><p><br /></p><p>Mufeed kwata kwata beji dadin magar abbanshiba, ba yanda ya iya, "Sorry daddy yace" sannan suka sama waje suka zauna</p><p><br /></p><p>Hajiyane ta kalle d'anta cike da tausayi "tace son how are you feeling now? "Alhamdulillah mufeed yace" </p><p>Tace" Allah ya kara sauki yace Ameen...suna zaune doctor ya kira, yake tambayar ya jikin nashi, yasan dai by now drip din ya kare ko?</p><p><br /></p><p>Alhaji yace" Alhamdulillah, eh ya kare, mumma ciremai basai kazoba, Doctor yace" To Alhamdulillah adai kula da jikinshi kuma ya dinga shan magungunanshi, Alhaji yace Okay!!</p><p><br /></p><p>Suna dakin aka kira magrib, Dan haka Alhaji ya fita yaje yai sallah, hajiya kuma tace" ok inanan koda ka dawo, Dan haka yana fita itama alwal tayi tazo ta sallahn ta, bayan ta idar ne tazo kusa da mufeed ta shafa kumatunshi, tace" nasan kana tare da damuwa Amma insha Allah zan maka kokari kaji?</p><p><br /></p><p>Mufeed ne ya kalle mamanshi wasu zafafan hawaye suka zubomai, yace" Dan Allah mummy ki temakemi wlhi idan na rasa husna akwai matsala, Hajiyarshi ta matukar tausayamai Dan tasan radadin so, tace" karya damu, suna cikin hirane Alhaji ya dawo, nan suka zauna har 10pm ganin jikinshi da saukine yasa suka koma part dinsu...</p><p> **********</p><p>Haka dai rayuwar mufeed ya kasance daga kanshi kasan something is wrong with him...be da wani kwanciyar hankali </p><p><br /></p><p>Duk ya rame yau kusan 2weeks kenan,</p><p><br /></p><p>Yana zaune yaji wani mugun son husna se shigrshi yake, mik'ewa yayi ya nufa dakin babanshi, yai sa'a hajiya itama tana wajen, zube musu a kasa yayi ya fara kuka Dan Allah abbanshi yai hakuri, kamar bemasan yana yiba, Dan haka ya rike kafan babanshi yana kuka, har abun yaba hajiya haushi ta daka mai tsawa tace" kai kayi hakuri tunda ya riga ya yanke hukunci, nima kaina banga aibun husna ba...Alhaji inma kana tinanin husna shiiyace" to ba haka bane!!</p><p><br /></p><p>Alhaji yana jinsu, bece musu komai ba, mufeed ne ya mik'e yace" nasan ku kuka haifeni, kunada ikon ku juyani yanda ya kamata, Amma abba tunda na nuna ina son husna Ku amince mun mana</p><p><br /></p><p>Babanshi cikin zafin rai yace" ban amince maka... Mufeed gaba daya jin kalaman babanshi ya rude, ya mik'e ya fita, Ashe koda ya fitan ba daki ya wuce be waje yake shirin fita, Chan *buba* _ya kwalla wa su hajiya da alhaji kira, yace" Hajiya lafiya kuwa? Ga mufeed nan zai fita kuma da alama ba cikin hayyacinsa yakeba_ kan kace meye, Hajiya da Alhaji da gudu suka fito, Hajiya taje ta kamoshi, she fisge fisge yake, Dakyar dai suka kamoshi, suka shugo dashi daki</p><p><br /></p><p>Hankalin Alhaji yai matukar tashi yanda yaga mufeed cikin kankanin lokacin ya chanza, har kwakwalwarshi tana shirin birkicewa... </p><p><br /></p><p>Mufeed kam se kubarni na fita, Ku barni na fita yake ta maimaitawa, nan aka samai karatun al'qurani, sannan Alhaji ya kira abokinshi farouk yai maza yazo,</p><p><br /></p><p>Da'aka samai karatun Alhamdulillah yadan fara dawowa hankalinshi, nan ake ta tofamai addu'o sannan ya dan dawo normal, Amma, Husna na shugowa dakin kuwa komai ya rikice, mik'ewa yayi yazo daf da ita kuma sai ya koma ya zauna....</p><p><br /></p><p>Itadai husna da gudu ta fita, cos batasan wainar da ake toyawaba...</p><p><br /></p><p>Hajiya hankalinta ya tashi, farouk saboda yasan komai yace" Dan Allah, Alhaji kuyi hakuri Ku auramai husnan mana, kaga da yanda hankakinshi yake nema ya gushe........</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Lol.....bara muga ko Alhaji zai yarda ko a'a....kuci gaba da kasancewa dani</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[4/20, 12:43 AM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM* </p><p> _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_</p><p><br /></p><p>FB Page </p><p>https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/</p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>Shout out to *Zauren UⓂmiey Xeey...* _Gaskiya inajin dadin yanda kuke son wannan littafin nawa...Allah yabar kauna yan uwa...zan rayu daku, zan mutu da Ku Abadan da ni daku zamu zauna_</p><p><br /></p><p>*PAGE 87➖88*</p><p><br /></p><p>"Farouk yace m sorry daddy, duk d bansan dalilin da yasa kace mufeed bazai aura husna ba, Amma ya kamata ka duba, kaga fa yanda yake shan wahala!</p><p><br /></p><p>Wani nunfashi Alhaji yaja...yace" to shikkenan, na amince ya aureta, Zumbur mufeed ya tashi yana kallon babanshi, gani yake kamar a mafarki, mufeed besan time din, Daya mik'e ba yaje gaban dad dinshi yana nagode Abba.. Hajiya gaba daya abun tausayi ya bata yanda mufeed yake Abu..</p><p><br /></p><p>Alhaji shima kanshi mamaki abun ya bashi...tabbas kalma daya ka furtawa mutun zai Iya sanadin wargazar da farin cikin mutun, haka zalika kalma daya zata Iya sa mutun farin ciki na har abada.... *Take note readers* </p><p><br /></p><p>Bayan dakin yadau shuru na wasu mintinane, Farouk ya kalla mufeed ya sakar mai murmushi, hajiya tace" bara Mu baka waje qila zaku zanta,</p><p><br /></p><p>Alhaji yace" NO ki zamanki ai komai dake za'ai, kan kace meye hankalin mufeed Alhamdulillah ya dawo, chest dinshi ya dena bugawan nan</p><p><br /></p><p>Alhaji nan sukai magana an yanke auran nan da sati biyu, Komai Alhaji zai ma mufeed, bangaren wasu kaya kuma hajiya zatai wa mufeed... Atakaice dai auran gata za'ai musu</p><p><br /></p><p>Sun gama tattaunawa...Mufeed da farouk suka wuce part din shi, nan fa suka fara shirye shiryen yanda abun zai kankama</p><p><br /></p><p>Mufeed yaji dadi sosai...da ya tuno Husna se yace" a zuciyarshi she's mine, se yai smiling</p><p><br /></p><p>Bangaren Su Alhaji kuma tun fitar Su mufeed, hajiya taje ta kira husna, tazo cikin ladabi da biyayya ta zube a kasa, Hajiyane ta fara magana kamar haka</p><p>"Husna kiyi hakuri mun zarce wani hukunci ba tare da kinsani ba..duk da muna zargin ko hakan ne, bamu sani ba, Zamu aura miki Mufeed, please kiyi hakuri!! </p><p><br /></p><p>Da sauri husna ta dago kai ta kallesu, tana son cewa wani Abu Amma ta kasa, "Alhaji yace in akwai magana kiyi, </p><p>Husna cikin murya me sanyi tace" ah ah ba komai, nagode da komai da kukaimun, Kun sharemun hawaye Sosai, Allah ya saka muku d gidan Aljannah, "sukace Ameen"</p><p><br /></p><p>Alhaji matuka yaji dadin yanda Husna keda tarbiya, shima kanshi yaji yana sonta. </p><p><br /></p><p>"Sukace Shikkenan, Ta tashi ta tafi daki, tana shiga Alhamdulillah tace" a zuciyarta Dan ita gani take inba mufeed dinba waye zai aureta? Ranar dai wuni tai Dan murna gashi ba islamiya bare taje taba kawarta labari</p><p><br /></p><p>***********************</p><p>Farouk yana shiga gida, matarshi Ummie, taga se fa'a yakeyi, itama smiling tayi, "tace yau kuma me gida dame akazo mana?</p><p> Farouk kara yalwata murmushin shi yayi yace" dear wife mu shiga daki dai ko, nan ta kama hannunshi sukai daki suka baje a pallow, Nan ya soma bata labarin ina wannan yarinyar? Wanda mukaje hospital dubata?</p><p><br /></p><p>Ummiey tace" eh na ganeta, Nan farouk ya gaya mata komai mufeed zai aureta, ansa bikin nan da sati biyu, Har zuciyarta taji dadi, Tace" to Alhamdulillah insha Allah kuwa gobe zanje, tun yanzu mu fara sabawa, </p><p><br /></p><p>Farouk yace" dadai yafi kam....nan suka ci gaba da hirarsu.. </p><p><br /></p><p>Ummie ce zaune, se tinanin Husna take, a zuciyar ta tace Allah sarki, Yanzuma irin yan gyran amaren nan da ake ba samu zatai ba, Wani tausayin husna taji, Kome ta tuno naji tace" Allah ya kaimu gobe</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Washe gari*</p><p>Tun Wuri Ummi ta tashi tai duk abun da zatai, misalin 10.am ta gama komai Dan haka farouk ya kaita gidan Su mufeed, ya kira husna yace" ga matar shinan, ya kawota ta gaishesu Su saba...lol husna ta gane Ummi, ita ta kawo mata ruwan zafi time din suna asabiti, Dan haka t rufe ido wai ita kunya...</p><p><br /></p><p>Ummi ce ta kama mata hannu sukai daki, nan suka kara gaisawa...Ummi ce t fara magana kamar haka" amarya bakya laifi, yanzu wani shirye shirye kikeyi?</p><p><br /></p><p>Husna tace" ba komai, Ummi tai murmushi tace" nayi tinanin haka, nan ta bude yar jakarta ta dakko mata wasu kayan mata, dan gyarab jiki, duk ta nuna mata yanda zatai amfani dasu, kuma insha Allah zatai kokari kusan kullun ta dinga zuwa, dan komai ya kammala cikin tsari...Husna tace" kai ammafa nagode, nagode, bansan me zancemiki, </p><p><br /></p><p>Ummi tace" bakomai ai muna tare, nan husna ta fito da wani number tace" ta kira mata ita kawartace a islamiya, aiki ba musu ummi ta amsa ta kirat, nan husna suka fara hira, tace" ansa mun rana fa nan da sati biyu, Khadija tace" haba? Dawaye?</p><p>Husna tce" yayana mana</p><p>Khadija tace" to Masha Allah, yimun kwatancen gidanku Nazo, aiko tayi,</p><p><br /></p><p>Bayan sun gama wayar ba'ai 30 mins ba Sega khadija ta shugo, nan fa suka hadu su 2 seba husna yan shawarwari suke yanda zata gyara jikinta, da yake sun dan fita wayewa...aikuwa taji dadi sosai nan take ta fara amfani da wasu.......kai mata</p><p><br /></p><p>Gaskiya husna taji dadin haduwa dasu, misalin 12 Ne, Khadija tace" zata tafi, sukai mata godiya sosai...</p><p><br /></p><p>Husna lol..tun randa aka ce mata zata aura mufeed wani kunyarshi takeji, around 5pm ne Suna zaune da Ummi sega mufeed da farouk sun shugo, kirari farouk ya fara mata wani kunya duk yabi ya ishe husna, Mufeed kam kunyarnan da takeji wani kara sonta yakeyi, </p><p><br /></p><p>Amaryata yace" Dan kunya husna batasan lokacin da Ta bude baki cikin muryanta me sanyi tace _Dan Allah yaya ka dena_ abun dariya ya basu dukansu, farouk yace bara mu barki haka, My wifey taso mu tafi ko?</p><p><br /></p><p>Ummi ok tace" sannan ta fara shiri, suka wuce gida....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da daddarene..kowa ya hallara a pallow</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Danci gaban labarin sai Ku biyoni</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ummiey Xeey</p><p>[4/22, 12:08 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣</p><p> *RAYUWAR WASU*</p><p>❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄</p><p><br /></p><p>NA........ ✍🏼</p><p>*UⓂmiey Xeey Abakson*</p><p><br /></p><p>*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM* </p><p> _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_</p><p><br /></p><p>*FB Page* </p><p>https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/</p><p><br /></p><p><br /></p><p> _•••°°°Devoted to......°°°•••_</p><p>*Miss Zarah Mansur😍*</p><p><br /></p><p>```Dedicated to duk me suna asma'u yau takwarar ku tana birthday....```</p><p>*24___04___2018*</p><p><br /></p><p>*Hip hip hip hurray🎈🎈🎈*</p><p><br /></p><p>*EMNOOR AHMAD DON*</p><p><br /></p><p>_May this day be the beginning of another beautiful year for you. May there be pleasant surprises, loads of joy and infinite happiness. Wish you a very happy birthday._</p><p><br /></p><p>🎈🎈🎈🎈🎈🎈🎈🎈🎈🎈</p><p>_Zan rayu dake, zan mutu dake, Abadan dani dake zamu zauna....har Aljannah insha Allah_</p><p>🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂</p><p>_It's your day baby.....have fun... Stay bless....Allah ya albarkaci rayuwarki sweet heart_</p><p>*HAPPY BIRTHDAY ONCE AGAIN*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*PAGE 89__90*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Da daddarane kowa ya hallara a pallow, suna kallon T.V mufeed ne ya mik'e yace" dad bari naje na kwanta akwai aiki gobe okay yace" Amma yana lura dashi like sun ta kuramai ne yaso dagashi sai husna, da Alhaji ya lura haka har mufeed ya fita ya kirashi, yace ya zauna, Alhaji ya kalla Hajiya yace" muje ciki ina son magana dake...Ran mufeed ba karamin fari yayi ba,...dan dad dinshi mutun ne me lura sosai</p><p><br /></p><p>Dasu hajiya suka shiga daki, Alhaji yace" bafa wata magana bane, kawai naga kar mushiga hakkin yaron nan ne kuma naga alama yanaso yai magana da husna sai yasa nai dubaran haka, "Hajiya tace aikuwa ka kyauta nan suka ci gaba da hirarsu yanda bikin zai kasance</p><p><br /></p><p>Bangaren mufeed kuwa, tun dayaga Anbasu waje matsowa kusa da husna yayi, itakam se matsawa takeyi, A ranshi yace" kita matsawa akwai ranar da zan kamaki ae, ganin taki zama kusa dashi yasa ya kyaleta, nan ya fara mata irin hira, haka Amma bawai ta sake jikinta bane...ita duk tsoro takeji wai Kar Alhaji Su fito Su samesu haka, that's why bata sake jikiba, Sun dan yi hira dai har yake tambayanta me take bukata itadai tace" bakomai, hakanan yaga kamar tana tsoronsa ya kyaleta yace" saida safe...ta tashi ta kulle part dinsu, ta tsaya ta window se hangenshi takeyi, har ya juya ya dawo ya manta key dinshi, still tana wajen, ta tsunduma kogin soyayya, knocking din kofa taji da sauri ta bude.</p><p><br /></p><p>Abun ne ya bashi mamaki wai ya akai yana knocking ta bude, Husna kallonshi take tayi ita duk duniya ba Wanda takeso yake burgeta kamar shi, har ya dauka key dinshi idonta na kanshi, abun yama mufeed dadi at least yanzu ya gane tana sonshi, Zai tafine ya matso kusa da ita daf, ya hura mata iska a fuskar ta, nan ta dawo daga dogon tinanin da take, ya kalleta yace" jeki kwanta, ta bude baki ta fara magana cikin yanayin Irin soyayyan nan ya kamata tace" ina jirane ka fita na kulle.</p><p><br /></p><p>Yai murmushi yace" a a muje na rakaki daki ki kwanta kawai, kamo hannunta yayi, har kofar room dinta ya kaita yace oya shiga dakin, good nyt my baby, ita kasa cewa komai tayi, daki ta shiga ta fada tinanin mufeed kawai takeyi, </p><p><br /></p><p>Yana ganin ta shiga, ya kira Hajiya yace" good night,</p><p><br /></p><p>Tace" ok har ka wuce dakine? Yace" a a ina Pallow, tace okay se gata ta sakko daga upstairs, tace" akwai maganar dama da nakeso muyi, a inane kakeso Ku zauna? Anan gidan ko kuma zaka gaggauta karashe ginin Kane?</p><p><br /></p><p>Mufeed yace" a a mamma anan ne inyaso daga baya semi koma chan tace okay, Tunda dare beyiba ka kira masu gyara, tun yanzu Suzo gobe, inyaso insunzo se asiyo duk abun da za'a bukata agyara maka part din, ok yace yai mata sallama</p><p><br /></p><p>Yana shiga ya kira masu aiki, akan suzo gobe akwai yan gyare gyaren da za'ai sukace ok Allah ya kaimu,</p><p><br /></p><p>Washe gari Monday tun 6 ya tashi, yai wanka beyi break fast ba, cos ya Dade beje wajen aiki ba, yai wa iyayanshi sallama zai tafi se Friday zaidawo, se leke yakeyi ko zaiga husna amma ina, itama tanajin muryanshi kamar ta fito, ta kasa dan jiya daya rike mata hannu kunyarshi takeji, da yaga bai ganta ba yai wucewarsa gidansu farouk, cos tare zasu tafi, yana shiga yaga farouk na break fast nan shima ya zauna, har farouk namai tsiya wai gauro...ummiey nata dariya tace" ai dai ya kusa samun mata dai ko? </p><p><br /></p><p>Mufeed yace" yauwa fadamai dai, suna ci suna barkwanci har suka gama suka nufa wajen aiki...</p><p><br /></p><p>***********************</p><p>Masu aiki kam sunzo, da yake dad Nanan shi ya basu komai, ba wani gyara ma bane me yawa, penti ne kawai akayi, a duka dakunan, Masha Allah yayi kyau</p><p><br /></p><p>*Bayan kwana biyu*</p><p>Dad gaba daya sunje sunma mufeed siyayyan komai, daga kan atamfa, less komai dai da ake sawa a akwati, bayan sunyi siyayyan basu wuce ko ina ba se gidan kanin babanshi Alhaji zubair da yake rafin zuwa a Kaduna a chan aka ajiye komai </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bangaren Su mufeed kuwa kwanan Su biyu, baiji muryan Husna ba, Ya kalle farouk yace" kai gaskiya farouk kana kokari sosai, wlhi kwana biyu da banga husna ba duk na gigice, Farouk yai dariya sosai, yace" tun baka aureta ba? Idan ka aureta kumafa?, " mufeed yace ai ba zuwa ko INA... Farouk yai daria sosai yace" lalle damafa Ku irinku da bakwa labarin budurwa idan kukayi se Ku nuna kunfi kowa Iya love, mufeed ya dariya yace" eh din nidai bari na kira.....</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hope kuna enjoying.... Love you alL</p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-478906265417226682020-12-05T23:26:00.000-08:002020-12-05T23:26:55.265-08:00TAKARI COMPLETE HAUSA NOVEL<div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-oUOrtCgJgqE/X8xwYmblUCI/AAAAAAAAJdE/qhRNl10OAVoJ28CAx1cyJS4-yEoke0Y8gCLcBGAsYHQ/s2048/TAKARI.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em; text-align: center;"><img alt="TAKARI COMPLETE HAUSA NOVEL" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-oUOrtCgJgqE/X8xwYmblUCI/AAAAAAAAJdE/qhRNl10OAVoJ28CAx1cyJS4-yEoke0Y8gCLcBGAsYHQ/w320-h248/TAKARI.jpg" title="TAKARI COMPLETE HAUSA NOVEL" width="320" /></a></div><p> [10/3, 14:27] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈ </p><p> 👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣</p><p> 1⃣</p><p>👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣👣</p><p> BY</p><p> </p><p> 🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p> 🐎 HUGUMA WRITERS🐎</p><p>Kir, kir kir kir kir, </p><p> fanfom bohle kakeji, Yara ne da matan aure keta diban ruwa a bakin bohol kamar yadda akasaba akowani kauye. </p><p> Yarinyace yar shekara goma sha daya ke saman karfen tana buga ruwan yan uwanta biyu sunata faman tarawa suna kwashewa gefe. Dahaka har suka gama ciki duk wani kaya da suka zo dashi gurin.</p><p> Wani dan gidan laka suke shiga da ruwan duk rigan jikin su yajike kunsan duk ruwan yana komawa cikin roban da suke daukan ruwan.</p><p> Randa ne irinta laka suke zuba ruwan aciki duk bakin randan ya fashe , harda faci akaimay da siminti . akwai shukan Iccen shuwaka a,tsaye gefen randan ruwan .</p><p> Inna yar kulu tafito daga cikin dakin lakan da saboda tsufa har ya dan duka kamar zai zube, amma haka yar kulu ke rayuwa acikin dakin tare da yan marayun diyan ta su hudu hafsat fatima mariya sai Abdul wanda suke ce ma datti saboda sunan mahaifin babansu ne akasa ma yaron.</p><p> Kai amma yau hafsi kunyi saurin samun ruwa akan lokaci, hmmm inna aikin san wanan aikin yar gidan kice , fadima . Wlh layin su kuburah taci, tace atabau mun riga su bada ashirin din mu dole aka kyale mu, muka diba aida layi ko kusa damu baizoba. Fadima ce ta fado cikin gidan dawani katon bahon ruwa akanta tana haki ataimaka asauke ta. </p><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p> Inna yar kulu na fada tasauketa, ; haba fadima wanan bahon yafi karfin ki wlh , ai wanan sai ya buda maki gaba ,</p><p>bahon waki,ka dauko ne ? Wlh na Asiya ce na dauko ka kafin diba yazo garesu, Don Allah yar nan kibar daukan roba mai girma kada ciwo yakamaki banda kudin kaiki ko wurin mai agangama balle asibitin gari </p><p> Dagudu ta koma donta maida roban da ta dauko na ruwa.</p><p> Inna tagama kwasan tuwo taba kowa nashi uku kwanon su guda datti nashi daban sai inna ita kadai tsugunne abakin murhu bisa wani dan guntun kujeran katako , tanayi tana kara masu miya a tasu kwanon.</p><p> Duk talauci da maraicin su yar kulu da yaranta baisa tai masu sakaci da karatun addini ba dana zamani haka suke zuwa karatusu ,babu mai taimaka masu sai Allah sai yar sanar, saida kamun koko da inna takeyi haikan garin ansanta da wanan sanar basai yaranta sunje yawon talla,ba.</p><p> Yau ba akaratun boko sungama aikinsu tunda safe suna sauri sutafi makarantar islamiyar su don malam bugunsu yakeyi idan an makara.</p><p> Gefen hayar su ta islamiya su kaga wasu mata su uku a tsaye suna gaisawa , cikin ladabi su hafsat suka gaida matan , suka tafi.</p><p> Kai wanan matar akwai karfin hali ,wlh inji Ramatu daya daga cikin matan da ke tsaye agefen haya wakenan? inji ; Gajiye , yar kulu mana matan marigayi sani mai shago ai yaran tane nan suka wuce mu taki bari kowa yadaukar mata ko guda ne,Wai a cewar ta itace zata tarbiyar da diyanta don haka ko aure taki yi waisai yaran sun girma , sunyi aure da farko har andauki yar babban amma saboda nacin yar kulu kan wai sai yarinya tayi ilimi dole akadawo mata da yar ta , yanzu duk dangin ta sun kyaleta da abinta dama mijin ba,asan asalinshi ba, Itace uwa itace uba.</p><p> </p><p> Yar kulu tana da tauhidi azuciyar ta yarda da Allah da kuma duk wani kaddaran da yasamay ta , hakan yasa batasa wa,ranta wani kwadayin duniya ba ita dai akullun taga Allah yabasu abinda zasu ci su sha basai ta tara wani abin duniya ba.</p><p> Kwadayinta su samu dan ilimin zaman duniya data lahira, koda sunyi aurene su iya karanta ko yar wasika ce </p><p> Saidai mutanen kauyen suna dauka wani girman kaine irin nata , ita wacece da zata hana yaranta talla. </p><p> GAJIYE takasa zama ta kasa tsaye yanzu yar kulun da tasani itace da wa"yan nan yaran haka jari gida ba,asan yadda za,a sarrafa suba tawani nacewa wai ita yara na karatu ba,talle wata sana,a kwarara. </p><p> Aiko gobe dole in koma kano wurin hajiya in ji yara yan shekara nawa take bukata idan naga da irin su acikin yaran yar kulu tau nikan abin yazo min da sauki wlh basai na shiga yawon bida ba ga abu a gida,,,,,, ,,,,,, ,,,, </p><p><br /></p><p> 🐎 ZEE MAKAWA 🐎</p><p> 🐎HUGUMA🐎 🐎WRITERS🐎</p><p>[10/3, 14:35] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 2⃣ </p><p> 👣👣👣👣👣 </p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> BY </p><p> 🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWa🐎</p><p> 🐎. HUGUMA WRITERS 🐎</p><p><br /></p><p> KANO KANO,,,, KANO koda maikazo an fika,,, hmmm inji kanawa .</p><p> Gajiye ce zaune saman tabarma an aje mata kwalban coca cola mai sanyi ga shinkafa da miyar naman shanu tanaci, ,,,,,,,</p><p> Hajiya mai sharwali nazaune agefenta suna hira ,Gajiye kinsan wancan karon ba abin kware, kika kawo min ba shiyasa banison kara harka dake ,,,,,,,,,</p><p> Hmmm hajiya kenan aikinsan wanan karon akasi akasamu insha Allah wanan karon </p><p> ,a samu matsalaba.</p><p> Hajiya mai Sharwali wata matace mai zaman kanta a garin kano , tana harko ki kalakala na bidan kudi, </p><p> Cikin irin hakane suka hadu da gajiye a,motar haya, tasamo yan mata guda biyu daga jahar katsina. Gajiye ce ke cewa hajiya wa"yanan yaranki ne kuwa sai take fada mata ai , aikatau tadauko su daga kano . Nan ta dinga ba Gajiye labarin yadda harka tasu take da irin kason da ake ba duk wata dillaliya, hajiya tace saidai wanan karon ita ba dillancin zatayi ba daukan kanta ne zatayi don ita ma zata fara nata harka ce.</p><p> Sun, kulla harka da gajiye har ta ke kawowa hajiya maisharwali yan mata daga sashe sokoto.</p><p> Tunda gajiye tadawo gida take tunanen hanyar da zata fara bullo ma al,amarin.</p><p> Saboda tasan idan har taci nasaran daukan wa,"yanan yaran na yar kulu lalai zata caba so sai </p><p> Don ita a,nata haukan duk yaran biyu masu wayo zata kwashe ma yar kulu, taje taci riban duniya dasu. Sam bata damu da halin da yar kulu zata iya shiga ba.</p><p><br /></p><p> Yar kulu na,ta,tsan kamun kokon ta taji sallama ta ansa ,,,,, Saidai bata gane , kowace bakurwar ba , don yar birnice , "tashigo ba irin matar kauyen , su na majidadi</p><p>bane ; wanan "tawaye dayawa </p><p> Bayan sun gaisa Gajiye tace nasan diyar kulu bata gane ni ba ko? </p><p> Gaskiya ban gane kiba inji Inna ,,,,,, nice Gajiye diyar dada makwabtar ku na kusa da massalancin sarki, a,a,a,aikuwa nagane yanzu kice min abokiyar fada ta itace kuwa.</p><p> Nan aka shiga hiran yaushe rabo tsakani,,, inda Gajiye ta labta karyan ai aure takeyi a kano harda yaranta, biyar, tazo ganin gida, Ida takawo tsaraba taba inna , su sabulun waka dana wanki sai manshafawa da su turare da turmin zani guda,,,,,,, da kyat inna ta karbi kayan bayan Gajiye ta nuna bacin ranta . jiki a sanyaye Inna ta karbi kayan tare da godiya .</p><p><br /></p><p> Sanu sanu shakuwa mai karfi yashiga tsakanin inna da Gajiye don tace ma inna yar kulu sati biyu zatayi ta koma .</p><p> Ko yaushe inna tai abinci zata ba hafsat ta kaiwa Gajiye nata , har sati biyu ,yacika ta koma ,Inda ta fito. </p><p> Tare da tunanen yadda zata shawo kan yar kulu nan gaba.</p><p> Inna yar kulu , nata kokarin kula da iyalenta tarbiyan su da duk wani kulawa da yadace uwa taiwa danta. </p><p> Su ko mutanen gari gani sukeyi girman kaine kawai yasa yar kulu sa "ya" yanta yin karatun boko ba talla, sai bakar wahala take yi a,kansu.</p><p> Hafsat ta dan girma don duk wani kiran diya mace ya bai,yana mata, </p><p> Hafsat bata da hayaniya sosai, ita farace irin farin yaran fulanin kauye na a,sali batada jiki sai gashin kai ja . Idan tana tafiya kamar ta kalle .</p><p> Fadima bata kai hafsat fari,ba amma tadan fi hafsat jiki kadan tanada round face , fadima bata magana amma akwai ta da zafin nama tafi hafsat kuzari sosai , ita,ko mariya da datti zubinsu guda.</p><p> Mahaifin su yarasu tun da aka haifi datti da wata biyu , yayi hatsarin mota a hanyar shita zuwa cikin garin sokoto sarin kayan tiredan shi. </p><p> Tun alokacin rayuwa ta canza ma iyalin marigayi malam Adamu mai tireda danshi, mutumin kirki wanda yasan darajan iyalin shi.</p><p> Yazo kauyen dogon daji daga yola ya biyo wani dan uwanshi da suke sanar fata tare daga karshe sai Allah yai zaman shi nan kauyen dogon daji ta cikin jahar sokoto .</p><p> Allah ya hadashi da inna sukayi aure shine dalilin zaman shi nan kauyen har Allah ya karbi ranshi.</p><p> </p><p> 🐎ZEE MAKAWA🐎</p><p> 🐎 HUGUMA 🐎🐎WRITERS🐎</p><p>[10/3, 14:39] +234 703 602 1388: ✈✈✈KANO TO JIDDA✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 3⃣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p><br /></p><p> </p><p> Bayan sati uku Gajiye tadawo kauyen dogon daji da sunan tazo bukin wata diyar yar uwanta, </p><p> Gidan bukin yacika gwargwadon yadda ake buki a kauye ,</p><p> Tuwo ne na shinkafa sai miyar alaihu da kulili , shimata da yara keta kwasa suna ci. Su Gajiye sune kirjin buki manyan yan birni zaune take ta hakince a saman tabarman roba</p><p> Akawo mata wanan akawo mata wancan ,,,, Saidai ita duk hankalinta baya guri kofa take kallo taga shigowar yar kulu.</p><p> Sai bayan sallah la,asar inna yar kulu ta iso gidan bukin abisa gaiyatar da Gajiye tai mata jiya da dare bayan ta iso harda ankon taimasu , su uku nafitar buki.</p><p> Jamma,a da dama wurin bukin suna mamakin zuwan yar kulu wurin wanan buki saboda ita ko haihuwa kayi da dare take zuwa taimaka barka,. Idan kuma aurene za,tazo taima Allah sa albarka ta,tafi. </p><p> Yau, sai gashi tazo harda anko kayan da Gajiye taimasu. koda yake mutane sun san akwai zumunci da zaman makwabtaka atsakanin su tun asali.</p><p> Anci ansha a,wuri tuwo da zobo mai zafi ko sanyi babu amma haka a,ke ta wasoso</p><p> Inna na gefe guda saman tabarma duk a takure take saboda bata saba shiga jamma,a ba haka.</p><p> Uhmmmm wai inna "yan mata ne inji Gajiye, tana tambayar yar kulu ?</p><p> Aiko suna gida lafiya lau kina dai min rowan yaran nan, yar kulu </p><p> A,a,a habadai Gajiye in,banda abin,ki aike uwarsu ce ta yaya zan maki rowar su ,,,,,,</p><p> Haba ai,sai Gajiye ta, gyara zama saboda tarkon ta yafara kama wa,</p><p> Ainaga ko wurin bukin baki bari sunzo ba yar kulu, ai,kamata yayi a, ce suna nan tunda gani a gari. Cikin kunya da kamala inna ke magana aikinsan basu da lokaci irin haka tunda suka dawo diban ruwa suka wuce islamiya sai gab da magriba suke dawowa,,,,,</p><p> Kinga ko basu da lokacin zuwa nan gurin amma insha Allah kafin kitafi zanturo maki su, su gaisheki,,,,,,,,,</p><p> Hira sosai mata ke,tayi wurin kamar yadda Gajiye da inna da wasu mata ke gefe guda suna tasu hiran.</p><p> Acikin hiran ne Gajiye kece ma inna akwai diyar mijinta zata haihu insha Allah inta haihu zuwa sabon wata zata zo ta,tafi da su hafsat suje mata buki,,,,,,,,,</p><p> Dam,,,,,,, gaban yar kulu ya fadi aje birni da yaranta ina sam baizai sabu ba,,,, ko a mafarki ma balle ai in yaranta sunje birni to kafansu kafanta ,,,,,, saboda birni ai a can yara ke lalacewa ,,,,,,, </p><p> Gajiye nata magana amma sam inna bataji ba tana can tana tunane a zuciyan ta.</p><p> Hmmm komai wayyon ki sainaci kudin diyar ki inji Gajiye acikin zuciyar ta don ta kulla inna tai nisa da tunane kuma fuskan ta ya nuna bata amince ba,,,,,,</p><p> Bayan taro yawatse Gajiye taba inna kayan buki wadatacce wai takaima yaranta</p><p> Ramatu, Gajiye ta bida don ta taimaka mata da batun yaran agurin innna.</p><p> Bayan buki da kwana daya Ramatu ta shigo gidan inna ,</p><p> kai kai kai maraba da Ramatu ke ce , yau agidan namu, </p><p> Nice yar kulu hanya ce tabiyo dani nace bari nashigo in maki yaya gajiyar buki .,,,,,, </p><p> Aiko nagode wlh </p><p> Bayan sun zauna andan yi hira ,Can Ramatu ta kawo zancen zuwa birnin yaran inna.</p><p> Aiko yar kulu kiji </p><p>dadi wlh, Gajiye yar birni zata dauki diyanki zuwa birni da ma ace nice aida yanzu nafara kuri agari ,,,, </p><p> Take innna ta canza fuska aiko Ramatu tashiga aiki zuga ,,,,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p> 🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p><br /></p><p>[10/3, 16:22] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 4⃣</p><p> BY </p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p> </p><p><br /></p><p> Zaune yar kulu take suna cin abinci da yaranta.,,,,, Yau ma kamar kullun nasiha take masu akan zaman duniya.</p><p> A duk yanayin da suka tsinci kansu su dinga hakkuri da duniya don duk abinda kai hakkuri zakaci riban agaba,,,, Fadima ta dago kai ta kalli mahaifiyar tasu tace inna koda an zallunce mu kina nupin kada mu rama sai muyi hakkuri,,, </p><p> Kware kuwa inji inna ko baki son Allah ya rama, maki, ne da zaki rama da kan ki ????.</p><p> A,hankali tadago ta,kalli inna tace,Inaso tafadi a sanyaye.</p><p> Murmushi inna tayi ta kauda kai so da kauna da tausayi yaran nata yakara shiga zuciyar ta, Tundai fadima wace tafaye zafin acikin su,,,,,</p><p> Daidai wanan lokacin itama Gajiye tana cikin mawuyacin halin da matsinancin tunane a kano,,,, tana tunane hanyar da zata bullo ma inna ,,,, Don tasha Alwashin wanan karon intazo dongon daji da yaran inna zata dawo kano. </p><p> Saboda lokacinda sukayi alkawari da hajiya mai sharwali ya kusa cika. </p><p> Muskudawa tayi tare da gyara zama dan taji dadin tunanen. Ahaka har barci ya kwasheta bata gama tunanen taba.</p><p> Kwana biyu tana shirye_shirye </p><p>Komawa, dogon daji, har barci take rasawa don tsantsar tunanen yadda zata riski yar kulu.</p><p><br /></p><p> Dogon Daji</p><p><br /></p><p> Karfe uku na rana tasauka garin, don ,haka gidan, Ramatu tanufa kafin taje gidan su, don jin yadda abubuwa ke tafiya ta fannin, Ramatu.</p><p> Saida safe Gajiye tai sallama gidan inna,,,,, inna nadaga cikin daki tana sallah walha tadanyi gyaran murya, alamun sallah a ke yi. </p><p> Cak taja ta tsaya kamar mara gaskiya a,tsakar gida,,,, tana dan waige ,waige har idonta yakai ga dan guntun kujerar innna dake gefen daki jingine... Tsab tabi gidan da ido tana kallo tana wani yatsune fuska azuciyar ta tana fadin ,,,, kai dadina da kauye kenan wlh,.</p><p> Komai nasu na tsafta ne ji randan ruwanta duk da sun tsufa amma an wani lulube shi da wani marfi mai fadi gidan gashi na lakane amma jiko ina tsab,, </p><p> In a gida nake aiko tashi banyi ba yanzu balle har inyi gyaran wuri.</p><p> Motsin dataji shi yasata dagowa da sauri takai diban ta akofar dakin .</p><p> Hakan yai daidai da fitowar inna a,daki a,a,a lalai marhabin mutanen birni ne yau a garin namu . </p><p> Cikin sakin fuska da murmushi suka gaisa cikin natsuwa.</p><p> Inna ta koma daki tashinfida tabarma mai haske tace bisimillahgag shigo daga ciki,,, batare da bata lokaci,ba Gajiye ta shiga suka kara gaisawa abisa al,ada irinta bahaushe idan kai bako gaisuwa kusan biyu akeyi,,,,, </p><p> Hira sosai sukeyi na yanayin lokaci,,,,,,, A cikin hiran tasa Gajiye ta sako zancan daukan yara. </p><p> Saida inna tanisa sanan tace, a gaskiya Gajiye bawai bani son yaran nan su, gusa, kusa dani bane,aa,Kinsan amana suke gare ni Allah yai ma mahaifin su rasuwa, batare da nasan asalin gidan su ba,. saidai zuciyata tana fada min cewa insha Allahu zasuga danginsu koda kuwa bani raye ne. </p><p> Saboda hakane yasa nake kokarin ganin nabasu ingattancen rayuwa,.</p><p> Saida gajiye ta gyara zama tace inbada abinki yar kulu ai zuwa kawai zamuyi sudanga inda nake kwana biyu indawo dasu. </p><p> Kinga aiko watan wata rana su zasu kai kansu inda nake don zumunci ko? </p><p> Shiru inna, ta karayi tana nazari maganar gajiye acikin ranta. </p><p> Gajiye kibari sainayi shawara da yaya na malam sale duk abinda yace zakiji kafin ki wuce. Nakuma gode da kulawar ki,,,,,,</p><p> Malam sale yayane ga inna, "Saboda haka kamar yadda inna tace haka tayi tasamu malam sale ta fada mai duk yadda sukayi da Gajiye shiru malam sale yayi yana nazarin maganar da yar kulu tazo masa dashi .</p><p> Can ya nisa yace tau yar kulu mutum yazu ba abin yarda bane , Saidai kuma ita Gajiye din ai ina ganin ta gida ce koma dai maiye aibazata wuce nan ba.</p><p> Cikin murya mai rauni Inna tace tau yaya duk abinda kace insha Allah haka za,ayi.</p><p> Malam sani ya lura inna batason tafiyan kokadan,,, Sai yace kiyi hakuri diyar kulu addu,a zamu Allah yakai su lfy yadawo muna dasu lfy tace ameen </p><p> Inna tace zata koma sukayi sallama ,Sai dai shi malam sani yasan cewa inna bata amince da wanan tafiyar ba,,,,, tausayi Gajiye da bata taba haihuwaba yakeyi kuma gashi har ta taya diyan " yar uwan shi idan har bai bada baki ba Gajiye bazataji dadi ba,,,</p><p> Dasanyi gwiwa inna ta dawo gida .</p><p> </p><p><br /></p><p> 🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p>[10/3, 16:28] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 5⃣</p><p> BY</p><p> 🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Inna yar kulu zaune a dakinta cikin dare bayan ta idar da sallah dare kamar yadda tasaba, Tana kai kukanta ga Allah akan Allah yasa wanan tafiyan da za,ayi yazama mata alheri, </p><p> Allah kuma tsare mata yaranta aduk inda suka shiga.</p><p> Duk wanan addu,an da takeyi a cinkin zuciyar ta takeyin shi, ,,</p><p> Shin wai ma wazata tura wanan tafiyan cikin hafsat da fadima .</p><p> Duk iya tunanen ta takasa tantance wacce zata bari a,tafi da ita,,,,,,,,</p><p> Washegari karfe takwas na safe sai ga Gajiye acinkin shirinta na,tafiya,,, A,zuciyanta tana fadin ai,tunda malam sale ya yarda bazan kara kwana ko guda ba kada in,zo in samu matsalar tafiya,,, Don ita ga haukanta duk yaran biyu zata tafi dasu saboda samun banza.</p><p> Da sallama tashigo yar kulu ta, tare ta da mutunci, Saidai acan cikin zuciyar ta addu,atakeyi ,,,,,, </p><p> Bayan sun gaisa cikin gimama juna,,,,, Sai yar Gajiye tace tau ina fatan yaran sun shirya ko ?</p><p> Innna dake shirin mikewa ta dauko mata koko tadakata tace yaran kuma ,"eh mana inji Gajiye bada hafsat da fadima zamu ba ,,,,,,,, habadai Gajiye idan na,bakisu dukka nidawa zan zauna au baga Maryam da DATTIJO ba,,,,, a,a gaskiya hakan bazai yiba , ai,ko mutun gudan dazan baki kawai dai don kece an riga anzama daya</p><p> Duk da ran Gajiye ya baci amma sai tadake tanuna ai ba komai ko hakan ma ai, ta gode tunda an,yaba da ita har anbata,,,,,,,, Saidai acikin zuciyar ta fada takeyi,,,, yo ga matsiyaciya nizaki kulla ma tsiya inga samu inga rashi haba wanan wata irin shu,umar mace, ce</p><p> Muskudawa tayi tare da gyara zama dan taji dawa zata tafi,,,</p><p> Juyowa inna tayi daidai lokacin tai ajiyan zuciya gami da cewa,,,,,,, Ban riga na gama shawaran ko dawa zaki tafi ba tukun ,,,, au mutafi da hafsat ma tunda itace babba.</p><p> A,aa gaskiya hakan zaiyi wuya donkin ga itace maidan wayo daga cikin su. Kinga ko zaiyi wuya inbari tayi nisa dani . Duk da yake fadima itace kusan ke taimakawa hasfsat din, kinsan abu ga tallakka ai sai a hankali.</p><p> Acikin zuciyar gajiye tace duk kigama tsiyar ki sai naci riba dake,,, </p><p> Inna abu yasha mata kai tara wace zata tura birni,,,,,,,,Caraf fadima da ke da saurin wayo da fahinta tace inna nizani abar hafsat dasu maryam </p><p> Aiko inna taji dadin hakan don dama tana shakar zuwan hafsat, Saboda shiru shirunta yai yawa za,a iya cuta mata batare da ta dauki wani mataki ba.</p><p> Fadima duk da yarinyace amma ta gane cewa inna batason zuwar hafsat din don ko cikin dare , da ta, farka taji inna na,maganar ,,,,,,,</p><p> Duk zancen da inna tayi cikin dare fadima naji ,,, A ,hakanan ta kwanta zuciyar ta fam da tunane tana fadin,,,,, Kiyi hakkuri inna tunda kin riga kinyi alkawari ,, nayi alkawarin ni fadima nizanje koda kuwa zuwan nada illar kamar yadda zuciyar ki ke fada maki ,,,, kuma gashi kinyi alkawari baki son fasawa,,,, kada Gajiye taga rashin cika alkawarin ki.</p><p> Kuka inna tasaka tana fadin Allah yaimaki,albarka fadima ,,,saboda ta fahinci fadima tagane manufar ta.</p><p>Kiyi hakkuri zan maki addua ,,, Sanan kuma ina son jan hankalinki duk da nasan tarbiyan da nayi maku, amma dai inason kisan yanzu birni zaki ba kauye ba ,,,,Don Allah ki kula ki kauda kai ga abin duniya ba ruwanki da abin mutane kiyi abinda yakaiki watau zumunci ki kulada rayuwar kamar kina a gabana,,,Don Allah ki kiyaye ki kare mutuncin ki,,, Sannan nasan ki da rawan kai to ki rage don Allah,,,, Allah yayi maki albarka yakare minke daga duk wani abinki ya azurta min ku da ilimi mai amfani ,,, Zancigaba da yi maki adduan alheri har randa akadawo min dake ,, Allah ya kaiku lfy</p><p> Da kyar ta kai maganar ta da kuka a fuskanta.</p><p> Gajiye ta mike tsaye tana fadin haba yar kulu sai kace wani guri zata haka.,,,,, aiki kwatar da hankalinki fadima gida zata.</p><p> Hmmm Gajiye aikin san danyau saida fada ,,, tau hakane kuma </p><p> Gajiye tace ina kayanta akadauko wasu yan tsumakara da duk basufi huduba acikin wata tsohuwar leda bage baka aka bata </p><p> Kuka fadima keyi ta kankamay yan uwanta tana kuka kamar bazasu kara haduwa ba,,,Gajiye tace haba fadima ki yi hakkuri daina kuka ba wai dadewa zakiyi ba ai idan zan dawo tare zamu dawo, ba wai an rabu ne gaba daya ba . Wanan kuka haka ai sai yasaki ciwon kai.</p><p> Gurin inna takoma ta kara riketa tana fadin inna ki yafe min dan Allah ,,,, ita ma inna fadi takeyi cikin kuka baki man komai ba fadima Allah ya kai ku lfy.</p><p> A waje suka tarar da,su Ramatu da wasu yan uwan gajiye suna jiran fitowar su,</p><p> Haba shiru haka inji Ramatu ai mundauka kun fasa zuwa yaune,,,, </p><p> A,a ,a haba dai mun dai tsaya adan kintsa ne kinsan rabuwar da da mahaifi da wuya tun dai irin wanan da ba,a taba zuwa ko ina ba.</p><p> A haka suka samu motar da zata kaisu sokoto nan bakin hanya ,,, Ana daga masu hannnu fadima ma tana daga masu hannu tana kuka har saida ta daina ganin su,,,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p> 🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p>[10/3, 16:34] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 6⃣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p><br /></p><p> Girmamawa Gareku masoyana👏👏,👏</p><p> ANTY Mariya SB</p><p> Hafsat yusuf </p><p> Safiya mai Huguna</p><p>Fatima Garba Teema luv</p><p> Maman Rufaida </p><p> Maman Ihsan</p><p> Anty Amal. </p><p> Nagode maku sosai,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> ( FARKO )</p><p><br /></p><p> Allah sarki ,,,, Yau litani itace rana ta farko da ni fadima nafara fita nabar kauyen mu dogon daji dake cikin jahar sokoto ,,,itace kuma rana tafarko da na fara shiga mota.</p><p> Tun ina kuka har nadaina gabana ko yanata faduwa ina ta rintse idona ,,,,,, anawa haukan wai,na ga itace na ta gudu .</p><p> Ba ai wani dadewaba muka shigo garin sokoto .</p><p> Muna isa tasha muka samu motar kano saura mutum uku, Gajiye ta biya kudin mutun uku din wai batason a matseta a mota.</p><p> Tun a sokoto nafara ganin canjin fuska a wurin Gajiye. Cikin hali irin na yaro nadan sa guiwar hannuna bisa ciyar ta haba aikawai naji ta fisgar min da hannu ta hankadeni gefe guda . tace kada ki kawo min sakarcin nan irin wanda uwar ku ta koya maku,,,, </p><p> A, hankali nadaga idona na kalleta idona tab da hawaye,,</p><p> Wani irin a jiyar zuciya nayi na maida fuskata hanyan titi,,,,,,, Ga fitsari ya cika min mara amma tsoron Gajiye ya hanani magana saida naga fitsari na batun balla min mara nasa , ihu cikin kuka nace wayyo Allah fitsari nake ji </p><p> Driver yataka burki da sauri yana fadin subahanallah shine baki magana,,,,,, Gajiye takai min rankwashi akai tace ja,ira fita da sauri kada ki min ajikina. kafin in tsuguna har yafara fita ko.</p><p> Karfe uku da rabi muka shiga KANO, zokaga kallo wurin yar kauye in waiga nan in waiga nan . muka sauka a saman hanya Gajiye takara tsaida wata a daidaita sahu sukayi jinga akaita Tarauni. </p><p> Mun isa tarauni cikin dan kan kanin lokaci, Gajiye ta biya mai adaidaita sahu kudin shi yatafi </p><p> Wani gida muka dosa gidan akusan tsakiyar layin gidan yake, saidai yanayin wurin yaimin kama da kasuwa a gurin saboda yawaan mutane da kuma abin hawa. </p><p> Gidan yana darumfa ga katuwar baranda an shimfida tabarmar roba babba ga benci kuma an jera su kala kala </p><p> Muka zagaya ta baya naga wasu yaran mata suna ta gaida Gajiye,,,,,, HAJIYA tana ciki ne inji gajiye tana tambayar "yan mata wata gutuwa tace mata eh tana ciki,,,, Dakata nan kijirani inji Gajiye . </p><p> Daya daga cikin yan matan tace Allah sarki Yumma dibi wanan yar yarinyar don daukar alhaki wai itama ankawota aikatau ko bauta,,,,,,, Yarinya da uwar ki tasani da bata barki kinzo ba . </p><p> Duk da yarinya nake saida cikina yabada kara naji wata iri don, Kande mai aya tagarin mu tana muna hiran yadda turawa suka dinga bautar da mutane da yadda shehu yazo ya dinga yaki da kafirai,,,,,, wanan zancen na kande na tuna.</p><p> Wata murya ta katse min tunane na tace Sukaina ance kiba wanan bakuwar yarinyar abinci taci inji hajiya</p><p> Saida nagama cin shinkafa da miya sai wani ganye da aka zuba sama,,,, bantaba cin ganyen ba sai na yayeshi gefe naci shinkafar kawai mai shegen dadi da nama guda uku aciki, aka kawo min ruwa masu sanyi nasha nayi hamdala.</p><p> Ina gamawa na mike naje gurin wacce akace tabani abinci nakai mata kwano takarba tana fadin kin koshi ko nace mata eh,,,,, saidai don Allah inason inyi sallah ne .</p><p> Tadafa min kai tace Allah sarki zoto in gwada maki wuri, wani dan daki takaini ansa wata tsohuwar kwali agefe tace min yi nan, muma anan , muke dan labewa muyi,,,,, dam sallah kuma ake labewa ayi nafadi haka a zuciya ta.</p><p> Ina cikin sallah naji ana fadin hajiya tace wai a,shigo da bakuwar yarinyar da tazo yanzu </p><p> Akace mata ina sallah takoma tafada masu,,,</p><p> Bayan na idar wanan Sukainar tace min inzo muje gurin hajiya,,,,Da sallamata na shiga su,biyu ke cinkin dakin maikama da shago, GAjiye tana zaune samar tabarma, itako, hajiya mai sharwali na saman wata kujerar roba fara.</p><p> Cikin gimamawa naje har gabanta na rusuna nace ina wuni hajiya takarba min ba yabo ba fallasawa, najuya na gaida gajiye itama,,,,Ido matar ta kuramin ina nan a tsugune har nadan wani lokaci,,, ina ganin matar nazari takeyi akaina.Dakin yai shiri nawani dan lokaci, kaina yana kasa duke, naji muryan matar tana fadin a,gaskiya Gajiye don dai kin fada min matsalar ki data uwar yarinyar gane da bazan dauki karaman yarinya irin wanan ba .</p><p> Ai wanan wahalar rainonta kawai mutun zaiyi Ita, ko Gajiye tana fadin ayi hakkuri hajiya , ataimaka muna.</p><p> A,zuciyata nace taimako kuma ashe dama inna sayar dani ta hada baki da Gajiye suyi shine ban sani ba ,,,,,, Allah sarki inna har talaucin da ake kira muna yakai hakan,,,,,, wasu kwalla masu zafi suka sulalo min ga fuskata na share hawayena na dan, gyara tsugunawa na,sake cewa, Allah nagode ma da ba hafsat tazo ba don ita bata kaini lfy ba ance tana da shawara ajikinta kuma inda tazo ya saurayinta I,Lu zaiyi yadda suke son juna,,, kusan mu kauye da yarinya takai shekara goma zancen aure yafara ke nan duk wani abu na mata zata fara iyawa....</p><p> Ina cikin tunane naji hajiya nacewa to amma gaskiya bazan baki kudin taba duka sai naga yadda yanayinta yake . Ai ba matsala inji Gajiye nasan insha Allahu zakiyi alfahari da ita.</p><p> HAJIYA taba Gajiye kudina ina kallo tanata washe baki har kune ita kakanta ya yanke saka.</p><p> Hajiya ta waigo tana fadin maye sunanta ne Gajiye ta ansa da fadin FATIMA saidai mu can kauye muna ce mata FADIMA ai, to shike nan sunar yayi kinsan mu nan muna canza ma mutun suna saboda bat,da, kama,,,, </p><p> Da Gajiye zata tafi tajawoni gefe taja min kune tana fadin to fadima ki kula da duk wani aiki da a,kasaki kuma banda kwadai don nasan kinga abinda baki saba gani ba don Allah ki kula sosai </p><p> Wanan kudin kuma zan je dogon daji in kaiwa mahaifiyarki su tasan abinda zatayi dasu,,,, (kaji makirci) irin ta tsofin kilaki,,,</p><p> Har ta fara tafiya cikin muryan kuka nace Inna nan zaki barni tace, "eh fadima amma zan rika zowa ina dibaki ke kuma dan abinda kika tara saiki bani inkaiwa maman ki.</p><p> Wasu hawaye masu zafi da kunar rai suka kara sulalowa a idona nace to kigaida su hafsat,,,,,,,</p><p><br /></p><p> 🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA WRITES🐎</p><p>[10/3, 16:40] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣</p><p> BY </p><p> 🐎ZAINAB MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p> </p><p> Akullun ina gode maku yan Huguma groups gaba daya da kuma TEEMA Luv Hausa Novels</p><p> Anty mariya sb </p><p> Anty hafsat yusuf Ali</p><p> Godiya dubu dubu gare ku.</p><p> </p><p><br /></p><p> Tun wucewar Gajiye sai nasamu wuri gindin wata bishiya na zauna nayi ta gumi,,,,,</p><p> Ina kallon yan matan dake ta ai yu kan su babu mai kula wata daga cikin su, Wacce naga tana karban kudi kuma nake ganin itace babban su, naga ta biyo ni tace zo kira cin abinci, don idan muntafi gida sai da safe zamu sake cin wani</p><p> Ido na fitar waje, nida inna ta saba aje muna fura da koko duk wanda yadawo ko yashigo yadiba yadda yake so yasha har dare watabi kuma da dare taimuna tuwon mu mai dadi muci.</p><p> Yau nice wai sai gobe zan karya Allah sarki rayuwa.</p><p> Sai misalin takwas nadare muka rufe shago , ina rugumay da dan kulin kayana cikin leda ta baka,,,, naga wani mai adaidaita sahu yazo muka lodu ciki mu biyar , </p><p> Tafiya maidan nisa yayi damu sai gamu wani dan gida karmi baida get amma ginane kamar ginan mutun daya,,,,,, Falo sai dakuna guda biyu agefe da makewayi a bayasa andanyi makewayin kwano dan karami ashe inda muke kewaya wane , shi wancan naciki na hajiyace ita kadai.</p><p> Muna shiga dakin naga sun,jawo wata tsohuwar tabarman roba sun shinfida </p><p> Kowa nata wasoson wurin kwanci saboda sunga bakuwa suna ganin ai wurin bai isar mu . Daya daga cikin su ko ince wacee dazu tace nakara cin abinci tace, min ,zo nan ki kwanta wurina ni sai in kwanta kasa,,,,,,,,, Naga taciro wani tsohon zanin ta, tashinfida akasa ta jawo ghana most go din ta, ta aje allamar filo ke nan, koda na kalli sauran naga suma duk sunyi irin yadda tayi.</p><p> Nima hakan nayi nadan aza ledar kayana na kwanta</p><p> Sai,naga wasun su, sun tashi suna wankin yan kayan su watau ke nan basu da time din wankin kayan su sai cikin dare suke wanki in,sun dawo sai su shanya kafin gari ya waye ya bushe,,,,,,,,,,</p><p> Rugaiyya ta dan juya tace min maiyye sunar ki kaunata, ? nace mata fadima .</p><p> Allah sarki tace daga ina aka dau koki nace dogon daji ,tace ina ne kuma hakana nace mata can can ,,,,,,,</p><p> Tace to ki kula da aikin da,duk a,kasaki kinji ,,,,,,, Nace to </p><p> Saita nuna min sauran tace wacan itace Yumma wacan Mari wacan Sukaina nikuma Rugaiyya kinji kuma kowa kice mata anty nace to,,,,,,, </p><p> Karfe hudu na asuba ina cikin barci na mai dadi naji ankai min duka a baya ana fadin tashi dan Allah kinji mu kwashe shinfida,,,,,, Tunda an fada maki barci kikazo yi, aida ki zauna gida kita barci, amma tunda uwar ki nason kudi ai barci baiga idonki ba yarinya.</p><p> Anty Sukaina ce ke fadin hakana , Rugaiyya tace haba dai Sukaina yakamata ki tausaya wa wanan yarinyar dan Allah bai kamata mu matsa mata , ba,ai,,,,,,</p><p> Mari, dake gefe tana gyara kunshin kayanta tace ai bidan kudi tazo yi kamar mu,,,,</p><p> Yumma tace ai maganar Rugaiyya gaskiya ne idan munyi tunane kamata yayi muso junan kamar yan uwa ba wai mudinga cuta wa junan mu ba,,,,, mutaru mu rufawa juna asiri .</p><p> Saboda wanan yarinyar tayi karama da yawa gaskiya ,rashin taudasayine kawai irin na mutane da kwadanyi iyayye kuma ,,,,,</p><p> Nidai ina jinsu ina kallon kowa da irin halinta.</p><p><br /></p><p> Cikin duhun nan sukayi sharan gida suka goge , wasun su ,suka debo ruwa a famfo suka cika wani katon roban ruwa,,,,,</p><p> Kafin karfe shidda yayi har an wanke wake ankai nika,,, </p><p> Mai adaidaita sahun jiya, yazo yadauki Yumma da mari da markaden wake da su, mai ,yatafi ,dasu </p><p> Sukuma sauran naga sun hura wuta a wajen gidan mu suka fara suya,,,,, </p><p> Duk wanan abin nadauka hajiya bata a gida sai misalin karfe takwas ,,,Rugaiya tashiga gida ta bata ruwan wanka tafito tsab da ita </p><p>, aka zo a kadauketa zuwa shago.</p><p> Koda tara na safiya yayi duk mun hada komai cikin gida, muka rufe gida, muma mukatafi shago rayuwar ke nan </p><p><br /></p><p> 🐎ZEEE MAKAWA 🐎</p><p> 🐎 HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 16:43] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈ </p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 8⃣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p><br /></p><p> Godiya ga masoyana yan uwa na </p><p> Mariya SB</p><p> Hafsat Yusuf da maman Rufaida</p><p> Ummi Rabiu da maimuna Adam duk a huguma group</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tundaga wanan rana rayuwar ta fara canza min, nasan mayye duniya, Ruyuwa ce ta bauta ko , ko tarashin galihu,,, gamunan dai haka gari zaiwaye muna dare ya riske mu a wahalce,,,,,,,,,,, </p><p> </p><p> Gari yawaye rana ya hudu daga gabas alokacin muna suyan kosai a acikin uguwar mu kafin mutafi shago,,,, </p><p> Ni aiki na shine a zuba min kosai da yawa a far roba indaga bin gidajen masu kudi in sun fito da safe suna saya suna sadaka,,,,,, </p><p> Abayana almajirai ke bina wa yanda ke karban sadaka ,,, idan nai sa,a za,a iya saye robar kosan gaba daya alokaci guda ,,aba ma almajirai sadaka .</p><p> Bakaramin cigaba hajiya tasamu ba ganin irin ribar da take samu damu yasa ta kara yawan kosai da muke sayarwa har da gudun mawar koko a wurin mu,,, kawai mutun yazo ya,saya koko da kanci inda kana son sikari mu zubama,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Da rana zuwa goma mun isa shago don fara abincin rana. Wanan yazama ka,ida dole goma taimuna a,shago, duk da aikin mu yafi yawa kuma munfi kawo kudi masu yawa,,,</p><p> A gaskiya ina jin dadin zama da sababin yayyen da nasamu suna kula dani sosai saboda ko aiki sukaga zaimin yawa zasu taimaka min dashi</p><p> Duk da dai aikina bawani mai yawa bane sosai,,,,,,, Idan an,ci, abinci nice zandauko kwanoni in hada su gurin wanke wake muna da almajirai masu wanke muna,, Sukuma abasu abincin da akaci aka raga suci</p><p> Wata rana natafi dauko kwanon da akaci abinci a tsallaken shagon mu ,,,,,,, abinka da yar kauye ban kulaba ashe akwai mota tafe kawai jinayi wata wuta ta,gitta min tun lokacin bansan inda nake ba,,,,,, </p><p> Muryam mutane nadiga ji sama sama akaina wasu na fadin ai,tana motsi ku,taimaka akaita asibiti,,</p><p><br /></p><p> Bankara sanin indanake ba,,,, ita hajiya mai shar wali ana fada mata ta mike da sauri tai waje ,,Tana fadin kada ku bari yagudu ku kama min kowaye,</p><p> Tana wani fiszege fiszege irin abin nan na yan duniyan mata</p><p><br /></p><p> A she driven wani alhaji ne ya dauko yara zuwa gida daga makaranta ,,, </p><p> Asibiti aka, kai fadima ,Likita ya,dibata ga babu kariya saidai inda tadan ji ciwo.</p><p> Likita ce za,a bani gado aga yadda jikin zaidan kasance tukun,,, </p><p> Hajiya kan kakanta ta yanke saka,, saboda mai motar da aka bugeni shi yadauki dawainiyar zamana asibiti </p><p> Abubuwan marmari da su kayan tea haka aka jibga muna su ga kudi wurin dubu hamsi yace a,yi duk lalurar da za,ai min inbasu isaba a tambaye shi,,,,</p><p><br /></p><p> </p><p> Tun daga wanan ranan da na kwanta ciwo bana iya cin komai daga kwanciya sai kwanciya , itako hajiya duk abinda aka kawo daga gidan Alhajin cinyewa takeyi.</p><p> Har kusan kwana goma ina cikin wanan halin, </p><p> Tunanen gida da kewan yan uwa na yadawo min sabo acikin zuciyata ,,,, Saidai kaga hawaye na zuba min a ido idan antambayeni ko maye sai ince ba komai ,,,</p><p> Naramay na yankwamay duk nasake sai yar wuyan da na danyi saboda rama.</p><p> Duk kudin da hajiya tasamu gurin Alhaji ssboda ni baisa tabar min fada ba wai lalaci ne kawai don ina mata bakin cikin dan cikin kosan da take samu ,,,,,,</p><p> </p><p> Rugaiyya sukan ce min inyi hakkuri hakana hajiya take ko kana ciwo bata tausayi ka, ita dai kaji sauki ka,bido mata kudi kawai,,,</p><p> Sannu a hankali na fara samun sauki ina danjin kwarin jikina,, </p><p> Nikan zauna a daki ni,kadai inyi ta kuka saboda a, tunane na da sanin inna ta nake cikin wanan halin.</p><p> Abayana naji ana ce min kiyi hakkuri fadima addu,a kadai zamuyi har Allah ya kawo muna saukin wanan rayuwar,,, Don Allah bai manta da mu ba yana sane da halin da, muke ciki watara sai lbr in munyi hakkuri </p><p> Tashi ki share hawayenki ki saki jiki ki koma kamar kowa kada ki sake saka kanki cikin wata sabuwar ukuba kinji</p><p> Rugaiyya ce ke min wanan maganar </p><p> Nace mata to, nabita da kallo har ta shiga cikin gida fito da kayan suyan kosai, </p><p> Murmushi nayi azuciyata naji tausanyin kan mu sosai naji kuma ina kaunar Rugaiyya har cikin zuciyata. </p><p> Saboda tun farkon zuwana tana nuna min kauna, tankar ni yar uwartace tajini.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wanan ciwon danayi yasa hajiya sanin dadina sosai tagane inada rana sosai a,gurinta .</p><p> Saboda yawan kudin da take samu aduk safe, yanzu ya rage yawa sosai,,,, </p><p> </p><p> A haka na daure nakarasa jin sauki a bakin shagon mu don tun ban iyawa ina bin bango har na daure na zama normal . Naci gaba da harkoki na kamar kowa,,,,,,, </p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🐎 ZEEE MAKAWA🐎 HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 16:52] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 9⃣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p> </p><p> HUGUMA GROUP </p><p> ALLAH YA DAUKAKA </p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Hankalin inna ya tashi kware ganin, yanzu kusan wata uku ke nan Gajiye batazo garin su ba kuma babu lbr ta</p><p> Inna tai sallama gidan, Ramatu suka gaisa cikin mutunci , sai shiru yabiyo baya har wani dan lokaci</p><p><br /></p><p>Inna,ce ta kauda shirun tace, shin wai Ramatu ya lbr Gajiye ne naji shiru tunda suka tafi , har yau bajin ko sakon gaisuwar su ba.</p><p><br /></p><p> Ramatu sai da hanjin cikinta yakada itama don da farko batayi tunanen hakaba ,,,, saidaga baya da ta fada ma mijinta yadda akayi har Gajiye tawuce da fadima sai ya hauta da fada,,,,,,,,</p><p> Yace ashe dama da hadin bakinta aka cuci inna yar kulu, </p><p> Gashi gari yadauka saboda kwadai tabari Gajiye tawuce mata da diya birni, Ashe cutar ta akayi,</p><p> Yace ma Ramatu tazauna da shirin duk randa asirinsu yatonu yar kulu taso diyar ta wlh shi ba,dashi cikin wanan rikicin ba.</p><p> Tun lokacin hakalin Ramatu yake a tashe tana tunane ranan da yar kulu zata tambayi diyar ta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ramatu tai shiru kamhar ruwa ya cinye ta, nadan wani lokaci </p><p> Sai can ta nisa tace ,,, A,gaskiya yar kulu banda lbr Gajiye ,</p><p> Asalima dai wlh ban san garin da take zaune ba,,, saida naji kamar an ce kano take zuwa sarin kaya daga sokoto.</p><p><br /></p><p> Inna da ke zaune saitaji wani jiri yana kwasan ta , Allah ya taimaka a zaune take da a tsaye ne da tafadi.</p><p> Cikin karfi hali inna tace ban fahice kiba fa Ramatu?. </p><p> Gaskiya maganar,ke nan yar kulu, </p><p> Gajiye ban iyace maki ga,garin,da take.</p><p> Nima yadda take zuwa ganin gida hakane yasa muka dan shaku,,, amma da tunda tai aure birni bawai nasan ina take da zama bane balle insan lbr ta.</p><p> </p><p> Habadai Ramatu zancan kikeyi kawai,, kizo har gidana kusan sau biyu akan inbari Gajiye ta, tafi min da diya taga inda take amma sai kice min wai yau aike bakisan Gajiye ba haba dai,,,,</p><p> </p><p><br /></p><p> Tun inna da Ramatu suna rikici su biyu har takai makwabta sun fara shigowa saboda gane ma idon su.</p><p> Daga gidan Ramatu, gidan yayanta malam sale tanupa </p><p> Batare da bata lokaciba ta zayyana masa yadda sukayi da Ramatu.</p><p> Shiru yayi cikin tashi hankali yanisa yace </p><p> Hakika yar kulu harda laifina ,,,,,,,,Don kamata yayi dakika kawo min shawara in tsaya in bincika kafin in yanke hukunci</p><p> </p><p> Cikin kuka inna tace ita,kan kaiconta da har takasa rikon yar mareniyar Allah da tabari har Gajiye ta cuce ta.</p><p> Tacigaba da fadin gajiye kin cuce ni da har kika yaudare ni nabaki yar diyata da sunan sati uku yau gashi har wata hudu ke nan,,,,</p><p> </p><p>Malam sale yatafi gidan maigari yakai karan maganan,,,, kowa yayi mamakin wanan maganar</p><p> Maigari yace to ai shi anfada mashi cewa yar kulu ta tura diyar ta birni wurin neman kudi.</p><p> Bawai yadda malam sale ya fada mashi ba,,,,</p><p> </p><p> Ramatu da inna duk suna zaune a zauren mai gari kaida ganin inna kasan tana cikin tashin hankali so sai </p><p> Bayan mai gari yayi gyaran murya wurin yayi tsit,,, sai yafara da addu,a tare da neman tsarin shedan. </p><p> Yar kulu muna son jin bayanin tafiyar diyar ki daga bakin ki, duk da yayan ki malam sale yazo yai muna bayani. Sai dai muna son ji daga gare ki.</p><p> </p><p> Inna takawo bayanin tun farkon haduwar su da Gajiye da kuma Ramatu ,har yadda akayi ta wuce mata da diya da irin zargin da gari ake mata </p><p> Takare bayanin ta cikin kuka tana fadin ko yan uwana ban yarda na basu rikon diyana ba saboda gudun zuciya ,,,, </p><p> An bukaci Ramatu tayi bayanin abinda tasani , Ita ma Ramatu bata boye komai ba duk yadda sukayi da Gajiye saida tafada a zauren maigari.</p><p> </p><p>Zauren yai shiru kowa da abinda yake sakawa azuciyar shi. Maigari yai gyaran murya yace,,, Dake yar kulu da Ramatu duk Gajiye tai maku wayyo ta gwada maku wayewa,, amma ai gajiye mutumiyar banza ce.</p><p><br /></p><p> Yanzu addu,a zamuyi ma yarinya Allah ya tsare muna ita duk inda take Allah kuma yadawo muna da ita gida lfy.</p><p> Zan tura abinciko min duk inda Gajiye take cikin kasar nan anemo muna ita tazo tai muna bayani da kanta.</p><p> Maigari yakara ba inna yar kulu hakuri yace ta kwantar da hankalinta Allah zai dawo mata da diyar ta lfy. </p><p> Yace kuma wanan yazama maku darasi arayuwan ku,,,,,,, Don yanzu ba,a yarda da mutun koda ko kasan shi ba,aba mutum amma kai tsaye haka,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 16:55] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈. </p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 🔟</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p> </p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p> Hafsta Yusuf Ali </p><p> Mariya SB</p><p> Fatima Garba Teema luv </p><p> Fadila Lamido novels</p><p> Musha karatu group novel </p><p> Maman Fati group novel </p><p> Duk ina ma wanda ke cikin wa "yan nan,groups din fatan, Alheri Allah sada mu da alherin da ke cikin wanan wata mai albarka👏👏👏👏👏👏</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Zaune muke a bakin shagon mu, anyi, ruwan sama,an,dauke , Kasan cewar lokacin ruwan sama, ne babu wani kasuwa da muke samu yanzu sosai. Saidai manejin kasuwa .</p><p><br /></p><p> To amma fa hajiya ce maiganin hakan ,,,,,, mudai mun,san ana samu. Ciniki daidai gwargwado </p><p> Wata yar doguwar rigace ajikina dinkin yai min yawa rigar Mari ce da tagaji da ja tayar shine Rugaiyya ta ce indauka in wanke indinga sawa .</p><p> Tun lokacin da nazo hajiya bata taba yimin dinki ba,,,, yan kayana duk sun kode sunzama ragga,, </p><p> Amma wai haka take ce muna wai mu kaza mai ne, </p><p> Ko sabulun wanki a sace muke saye mudan wake kayan mu </p><p> </p><p> Wani lokaci kuma masu sayen abincin mu sukan dan yi muna alheri jefi jefi,</p><p> Sai dai Rugaiyya ta ja min kunne cewa kada indinga wasa da maza,,,,, kuma ka in,yarda in naje gurin tallan kosai kada in shiga cikin gida in tsaya daga waje</p><p> Aiko alheri akai muna hajiya muke ba wai acewar ta tana tara muna ne idan zamu gida saita hada muna da kudin aikin mu.</p><p> Zaman danayi jira nakeyi agama gyara kayan miya inkai wurin markade. </p><p> Bayan angama gyarawa nace ma Sukaina tabani kudin nika , saitace ai atabau tabani kudi tundazu </p><p> Wasa wasa muka fara wanan rikicin har gurin hajiya muka tafi,,, </p><p> Sukaina tace ai tun kafin ta wanke tabani kudi</p><p> Hajiya tasa aka cajeni kaf ba,aga komai ba aguri na</p><p> Amma sai hajiya tashiga zagina tana fada inda take shiga banan take fita ba,,,, wai ai dama halina baida kyau shiyasa uwata ta kawo ni yawon duniya tun ina,,,,, yar karama dani , wai, min shegiya mai shegen ido kakafe,da fari kamar gonar madara gakinan kaman akalla ki kulun kina cimin abinci a,banza baki auki </p><p><br /></p><p>Yau duk inda kika kaimin kudina wlh sai kin tono minsu angaya maki barikin banza nafito yi ,</p><p> Ta, daka min tsawa saida na firgita Munafuka ina magana kin kafeni da shegun idanun nan naki, fita kiban wuri,,,,,</p><p> Sim sim na fita ina sharban kuka,,,,, hakana na dauki nikar nadoshi manika ina hawaye.</p><p><br /></p><p> Matar dake muna nika ba ba,haushiya bace bayerabiya .ce,,,,, Cikin hausan yarbawa take min magana</p><p> Yaron hajiya maynene ya , samay,ka,ka nayi kuka yau, na fada mata duk yadda akayi ,,, tace wlh don dai nice kawai zatayi kuma na bata tausayi amma, in,don hajiyace bazatayi ba, don hajiya bakyau,,,,,</p><p> Bayan nadawo daga nikan sai hajiya tace wai wa,ya,bani kudi nabiya kudin nikan,,, nace mata kyauta a,kaimun nikan .</p><p> Aiko hajiya tace karya nakeyi kudinta ne dama naso in mata sata ne,,, Ta samayni taimin dukan tsiya har saida bakina ya kun bura </p><p> Saida yamma muna tatara kaya,muna kaiwa a cikin shago sai ga kudin da Sukaina tace tabani angani kasan wani roba ta aje ashe ,,,,,,,, </p><p> Rugaiyya ranta ya baci ta,fisge kudin taje ta nuna ma hajiya ,,,</p><p> Borin kunya hajiya ta kamayi tana fadin shegu da ban yi mata haka ba da shikenan ashani abanza,,,,,,,,,,</p><p> Kafin safe bakina ya kumbura sindib saikace an aza min dutse akai nake jinsa, hakan yasa nake jin zazabi yana son kamani</p><p> Rugaiyya ce, takama kula dani, taña dan gasa min wurin da ruwa mai dan dumi, tasayo min kwayoyi ta ba ni tace in,hadiye .</p><p> Hakana wuni ranan ina dan jin zazabi ajiki na.</p><p> Saida hakan bai hani zuwa tallan safe da nasaba yi ba na kosai,,,,,,</p><p> Aikin shago ne kawai yan uwana suka taimaka min yi </p><p><br /></p><p> A haka rayuwar tamu tadinga tafiya yau dadi gobe zafi. </p><p> Girma kuma na zo mun a hankali , duk bautan da mukeyi bai sa Hajiya ta dan tausaya muna ba sai dai kulun cikin kara sabon sana,a mukeyi</p><p> Ita dai tayi kudi by all means ,,,,,,</p><p> Idan naga yara za su makaranta sai intajin wani iri a,zuciya,ta. Sai dai duk da haka dan karatun da ke a kaina bai fita ba dan ina iya karanta wasikar hausa tsaf kuma zan iya ta turanci ita,ma saidai aimin dan gyara kadan</p><p><br /></p><p>Na riga na hakkura da duk wani halin da zan tsinci kaina banda wata matsala yanzu a,rayuwana sai dai kawai na bidan ma hajiya kudi,</p><p> Gwargwado yanzu hajiya ta wadata damu har takan dan yaba mu,</p><p> Wani lokaci har da kyauta takan dan bamu kamar dari biyu biyu ko kuma ta siyo muna dan abin marmari mu ci</p><p> Wanan kuma yasamu asaline tun ranar da wata kawarta tazo shagon mu taba mu kyauta da zata tafi,,,, </p><p> Tun agabanta muka fara ba hajiya kudin, sai bakuwar tace aa ,habadai mai sharwali kibar masu abinsu mana wanan ai kyauta nabasu..</p><p> Mudai muka fita waje muka bar su a cikin suna magana,,, </p><p> To tun tafiyar bakuwar komai ya canza.</p><p> Abakin Sukaina mukeji wai ashe bakuwar taima hajiya wa,azi tace mata amana fa muke a,gurinta</p><p><br /></p><p>Shine dalilin ganin canji da muka gani ga hajiya,,,,,,,</p><p> </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎. HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 17:05] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 1⃣1⃣</p><p> BY </p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p><br /></p><p> Godiya ga masoyiya kuma anty na HAFSAT YUSUF ALI </p><p> </p><p>Almost true life story</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hajiya mai sharwali ta bunkasa sosai yanzu kusan duk maison cin abincin kware shagonta zai zo ,,,,,,,</p><p> Abincin mu gaskiya yana da dadi sosai , saboda duk wani kayan hadi muna zubawa acikin aikin mu.</p><p> Mukuma muna tsayawa tsakani da Allah muyi mata aiki babu kissa ko cutar wa,</p><p> Yumma da Rugaiyya sun sha fada min cewa hajiya itace , gatan mu a garin kano .</p><p> Saboda zamanta mukeyi nan, ba zaman wani ko wata ba.</p><p> Wanan maganan nasu yakara min kwarin gwiwa wajen yadda da hajiyan mu kamar yadda muke kiranta,,,</p><p> Karfe shadayan rana, idan kazo shagon mu zaka samu mun gama dafa abinci kala kala,</p><p> Mundan gyara jikin mu don kada masu sayen abincin mu suga kazantar mu,,,,,,,</p><p> </p><p><br /></p><p> Yau ma kamar kullun mun gama aiki muna zaune muna jiran masaya, abincin,mu su,zo </p><p> Wata ma,aikata dake kusa damu nan cikin tarauni suke ,,,,,,, Suke zuwa sayen abincin indan sun tashi break, fast.</p><p> Daidai lokacin da suke zuwa cin abincin bamu da lokaci kan mu,saboda aiki kayi yawa kowa da abinda zai, ce a,kawo mai, yaci,,,,,,,,</p><p> </p><p> Daidai wanan lokacin da ko hajiya bata da lokacin kanta,,,,, Wata hadadiyar mota mai ruwan kalar kakin soja tazo ta faka bakin shagon mu.</p><p> Hankalin kowa dake wurin ya kai ga wanan motar kusan , minti goma ba,a bude motar ba.</p><p> Koda,kofar,motar ta bude, Karfar wata mace ce tafara fitowa da shi tawaje amma bata fito da jikinta ba,,, </p><p> Gashi kusan duk wanda ke wurin hankalin shi naga wacce zatafito cikin motar,,,,,</p><p> </p><p> Wata matace baka yar doguwa kyakyawa girma yadan fara kamata kadan, ita ta,fito daga cikin motar mayafin ta a kafada sai dan jakar fos data rika a,hannunta,,,,,</p><p> Hajiya na gani matar ta mike tsaye tana fadin a,a,a ,,,,,,</p><p> Wanake gani kamar zinaro ,matar tai,wani far da ido taware hannaye tana fadin nice mai sharwali,,,,,, </p><p> Suka rugumay junnan su cikin farin ciki da an,nashuwa,,, </p><p> Nan hajiya ta umurce mu da mukawo wa bakuwa abinci, tana fa mubarshi,, amma hajiya na fadin mu kawo duk abinda ke gare ,,,,, </p><p> Mari tace tirkashi ,yau kan munyi bakuwa mai muhinmanci kenan ,tunda har hajiya tace mukawo duk abincin da muka girka kalala wa bakuwar.</p><p> </p><p> Koda nashigo da turen ferfesun kayan ciki dana kifi danye nasamu hajiya da bakuwar ta sun baje ana yaushe rabo,,,,,,</p><p> Bakuwar ta cire gyalenta tanawani juyawa agaban hajiya ,, hajiya nafadin wai Zinaro kece haka don Allah</p><p> Zinaro tace yo mai yai min tsinanen zafi mai sharwali ,,,,, mayye duniya ,</p><p> Wai yaushe kika zo kasan madai,,,,, </p><p> Bakuwar tace aini ma abinda yabani mamaki kenan mai sharwali naga,kusan kowa da akai zamar harka a saudiya amma ke bangan kiba . sai na tambaya akace min aikina nan gidin murhu kina halaka kanki,,,, </p><p> Shin may ku,kazo yi ne a,kasar ?</p><p> A,a buki mukazo mana kinsan Alhajiji yai aure wancan satin,,, </p><p> Waye kuma Alhajiji Zinaro, ta kalli hajiya galala tace kina ko kasan ga mai sharwali</p><p> Au tana gyara kafadan riganta, </p><p> Tace shugaban yan daudu mana nakasa kinsan yayi aure daga saudiya shine mukazo kawo amarya,,,,,</p><p> Hajiya ta girgiza kai cikin daurewan kwakwalwa tace gaskiya ban san shiba.</p><p> Tace anya kuwa a garin nan ma kike kuwa ,,,, sarkin yan daudun nakasa zakice baki sani ba ,,,,</p><p> Hajiya tace yo nazama kifin rijiya yanzu ai</p><p> Bani zuwa ko ina daga wanan runfar sai gida aikin kenan.</p><p><br /></p><p> Yo kin zo kano kin boye ana can a,nata harka a saudiya </p><p> Kai habadai yo aike ma dai kinga a,lama aiko </p><p> Eh aiko nagani.</p><p> Haba dai don Allah kizo kawai acigaba da harka dake, har wa"yanda basu kai ki ba sun take balle ke.</p><p> </p><p> Haka muka dinga shigowa muna, mata sannu da zuwa ,muna fita .</p><p> Ke sharwali duk ke keda wanan harkan haka?</p><p> Harka kuma ina? Gasu nan mana,wa yan nan zukazukan yan matan haka ,, yo aike kice min kin take </p><p> Kika tafi dasu saudiya ai nabaki watan ni kadan kin take kenan har abada,,,,</p><p> </p><p> A haka bakuwa Zinaro ta dinga zuga hajiya tana cusa mata ra,ayin fita da mu zuwa saudiya bidan kudi</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p>[10/3, 18:54] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 1⃣2⃣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Hajiyan mu takasa yin barcin kirki yau,,,, hiransu da hajiya Zinaro ke dawo mata a, rai.</p><p> Sai juyi take tayi tana jin muryan zinaro na fadin in kika tafi dasu saudiya aikin take,,,,,, </p><p> Nan da nan shedan ya rinjaye ta ,taji kawai zuwa saudiyan take da bukatar yi.</p><p> Ta,manta duk wanan baiwar na samu da Allah ubangiji yai mata nasa nan kano.</p><p> Kafin asamu mai,sa,ar kasuwa inda ake samun, ciniki irin nata sai an tona.</p><p> Allah Allah gari ya waye takeyi , don taje gidan Zinaro .</p><p> </p><p>Kwatancen da Zinaro taimata na masaukin su shi tabi, batasha wani wuya ba wurin gane gidan</p><p> Cikin kankani lokaci ta isa dawanau inda gidan da zinaro take a,karshe wani layi. </p><p> Gidan ginan jan bulo ne sai kato,kofar baki karfe da ke manne da ginar,,, </p><p> Koda hajiya tai sallama wani dan saurayi fari dogo , yazo ya bude mata kofar ta shiga .</p><p><br /></p><p> Ginan gidan gaskiya ba laifi komai ya hadu daidai da zamani ,,,,,, kujeru ne manya manya sai, kayan kallo dana kida saiti masu kyau.</p><p> Ga dinning table agefe guda,,,, sai wata kofa da zata sada ka da kitchen , shima kitchen din ya hadu sosai komai na bukatar zamani akwai a cikin kitchen din.</p><p> Wasu samari guda uku tagani acikin falon gidan suna game kowanin su dagashi sai wandon tree quater, da yar singilati.</p><p> Sukayi ma hajiya sannu da zuwa ,,,,, guda daga cikin su ya , shiga ciki fada ma zinaro bayan kamar minti biyar yafito.</p><p> Yace ance tashigo daga cikin uwar dakin.</p><p> </p><p> Hajiya Zinaro zaune a gaban mirrow tana shafa mai dagani daga wanka tafito.</p><p> A ,a mai sharwali kece tafe da safen nan </p><p> Hajiya na washe baki tace wlh nice zinaro.</p><p> Tun shekaran jiya da kika tafi kin barni da tunane kala kala azuciyata. </p><p> Shine nace bari inzo don bansan lokacin da zaki koma ba.</p><p> Zinaro ta lakato mai da yatsanta tana shafa ma kafarta tace,,,, "eh gaskiya zan wani dadewa ba zan koma kinsan yanzu ba wani harka sosai a cikin makka kamu sukeyi don haka a jidda ko Riyadh, </p><p> Sunta dan jefa hiran wa yanda sukayi zama dasu alokacin da suka fara zuwa aikin TAKARI na farko,,,, </p><p> Zinaro na bata lbr ai wasu sun dawo gida wasu kuma suna can wasu kuma sun rasu dadewa.</p><p> Cikin samarin dake zaune falo guda ya shigo yana fadin hajiya yau sai mun sayo kayan miya agidan nan don wanda yarage baida yawa kuma sun fara lalacewa.</p><p> Tace kadauki ga kudi can kaje ka sayo abinda duk yadace asaya.</p><p> Bayan fitar saurayin hajiya tace wa " yanan yaran "yan uwanki ne ko </p><p> Dariya sosai hajiya tayi tace yan uwana na,bariki ba ,Da su nazo daga can </p><p> Saurayi nane da abokan shi,,, saurayi fa kikace to may ye aciki don nace saurayi nane. </p><p> Hajiya takura mata ido har dan wani lokaci tace kai haba Zinaro,,,wa " yanan yan yaran zakice wai samarin ki yo ai wanan, ma mun kusa haihuwar su, Idan ma bariki kike so ai sai ki samu daidai dake amma ba wa yan nan yara ba</p><p> Wani irin dariya zinaro ta kyalkyale dashi na shakiyan ci gami da aje roban man da take shafi gefe guda tana rufewa,,</p><p> Ta ce lalai mai sharwali baki akasan don ina ganin ma ko a kanon kauye kike. Ai wa yan nan yaran sufi manya dadin sha,ani don su idan kika basu kudi kadan sai su biya maki bukatar ki fiye da yadda kike tsamani,,, kallonta kawai mai sharwali ke yi,,,,,,,,</p><p> Ta shashantar da maganar ita dai hajiya duk al,ajabi ya kamata, mamaki takeyi da wanan irin hali na su zinaro,,, </p><p> Saida tagama shirin ta tsab suka fito falon inda zinaro ke ma hajiya tayin samarin ko akwai wanda yai mata taja guda</p><p> Ai barikin nawa baikai can ba Zinaro inji hajiya </p><p> Taufa ashe har yanzu da sauranki maisharwali. Don ko kinga su nan ba karamin riba naci dasu ba zuwan mu wanan bukin,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Zama akayi sosai da hajiya da zinaro taba hajiya shawarwarin abin da yakamata a,yi saboda tafiyar su saudiya.</p><p> Komai an,kan,mala game da tafiya duk wani hanya da za,a bi an yi,,,</p><p> Hajiya taba da kudade masu yawa saboda komai yatafi daidai</p><p> Aiko kafin hajiya zinaro tabar kasan komai ya zama daidai,,,,,,,,,</p><p> </p><p> Lokacin tafiya kawai za,ajira yayi abar kasan zuwa sabuwar duniya</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p>[10/3, 19:02] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣 </p><p> 1⃣3⃣</p><p> BY </p><p> 🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA WRITERS🐎</p><p><br /></p><p>Ina duk masoya novel dina fatan alheri , nagode kware da kulawan ku yan uwa </p><p><br /></p><p> Anty Mariya SB Allah ya baki lfy </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tunda hajiya ta dawo daga gidan zinaro mukaga canji sosai a wurin ta, Sai fa,ra,a takeyi da kowa</p><p> Mudai namu idanu kawai tunda babu daman mu tambaye ta,,,,,,,</p><p> Ai yukan mu kawai mukeyi kamar yadda ya kamata ,,,,, saidai mun ga hajiya kamar tana cinikin gidanta da shagon ta dawasu...</p><p> </p><p>Mukan ba matsalar mu bace iyaka naji Sukaina yar sa ido na fadin kila hajiya zata maidamu gidajen mu don tana gani zata koma makkah da zama ne.</p><p> Jin haka yasa na fara murnan zan koma gida very soon, </p><p>Zanje inga hafsat dina da dattijo dan kani na ,,,,, har nace sai in saya masu bread da lemo in kai masu ,,,, haka nadinga sake sake a zuciyata,,, </p><p> </p><p> Wasu mutane sukazo su biyu wurin hajiyan mu sun dade da ita cikin shago,,,,, </p><p> Hajiya takira Yumma tace taje tafada muna kowa ya gyara jikin shi da,kyau za ,a dauki photo ne. Aiko muka shiga murna za muyi photo.</p><p> Ta,ba mu, wasu kaya masu kyau doga yen riguna tace kowa yasa,a photo dashi,</p><p> muna ta murna zamuyi photo ban kwana da juna tunda ance hajiya zata bar kasa ne.</p><p> Sam bamu kawo cewa damu za,a tafi ba,,,,,</p><p><br /></p><p> Bayan mai photo yadauke mu ya wuce da kwana biyu hajiya ta turo wata mace tazo tai muna kitso da kunshi masu kyau</p><p> Munata murna muka fito shar da mu kamar wasu yan birni,,,,</p><p> Tundaga ranan da akai muna kitso bamu kara zuwa shago ba kuma ,,,,, </p><p> Kayan dadi muke ci a gida babu wani tsangwama da ake muna yanzu,,,,</p><p> </p><p>Bayan kaman kwana hudu tsakani cikin dare muna hira a falon gidan mu</p><p> Sai hajiya ta fito ta zauna a gefen mu duk mukayi shiru,,,, </p><p> Waya take yi alokacin amma saboda ladabi sai duk mukayi tsit wurin.</p><p> Tana gama wayan takai dibanta gare mu ,,,,,,, lokacin tai wani dan gyaran murya sai duk muka kara maida hankalin mu gareta.</p><p> </p><p> Tace duk ina son ku bani hankalin nan ku saurare ni da kyau ,</p><p> Mukayi shiru cikin ladabi, tafara magana, </p><p> Tace dukan ku, ku ,biyar, zamu bar kasan nan zuwa kasar makka gobe da asuba insha Allah </p><p> Nasaida gida na da wasu yan abubuwa nawa, saboda tafiyar mu,,, nasan cewa baza mu dade ba shiyasa ban fada ma kowa cikin yan uwan kuba saboda dazaran angama aikin hajji zamu dawo nan kano muci gaba da sana,ar mu,,,,,,</p><p> Naga ,su Sukaina duk suna ta,murna sai Antyna Rugaiya ce naga bata wani murna sosai kamar sauran. </p><p> Naga kowa ya shiga hada kayan shi,,, sai hajiya ta shigo dakin na mu da kanta,,,,,, Tace muna ba wasu kaya masu yawa zaku dauka ba kada ya wuce kala biyu kubar sauran idan mun dawo sai kuyi amfani dashi,,,,,</p><p> A , haka muka dan tsinci dan abinda muke so mukabar saura da niyar in mun,dawo mu kwashi abin mu zuwa gida,,,,,,,</p><p><br /></p><p> Tunda asuba masu adaidaita suka zo suka kwashe mu zuwa filin jirgi </p><p> Hajiyar mu ce da wasu suke ta zirga zirga a wurin mudai muna gefe guda, muna jiran ,,, Yadda za,ayi damu </p><p> Barci nake ji inna hamma Rugaiyya ta ce in kwanta ajikinta kafin , hajiya mu,tazo daukan mu,,,</p><p> Ina cikin barci naji ana tashins natashi firgigit dani naga an bamu wasu kumshi kaya ance kowa ga nashi ,,,</p><p> Wai goro ne a ciki dasu kayan miya irin namu na nan kasar ,,, wasu kuma wai turamay zani ne a cikin kunshin da sukayan amfanin mata,,,</p><p><br /></p><p>Barcin da bankara yi ba ke nan duk inda zamu don a auna mun je an muna komai da ya kamata ,,,,, Kuma cikin ikon Allah kowan mu ta samu tafiya saboda an hada mu da wasu mutane can da ban waidasu zamu.</p><p> </p><p> Allah mai ikon shi yau ni FATIMA Mohammed Sani ,ce acikin jirgin sama zuwa makka ,,, wai a sanadin yar ga aiki yau kuma suna zai koma TAKARI,,,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p> HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 19:06] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 1⃣4⃣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎 </p><p> </p><p><br /></p><p> </p><p>Yan uwa musulumai na, duniya ina muna murna da sallah Allah ya kara ma musulunci daraja da dauka </p><p> Allah ya rupa ma kowa asiri Ubangiji kataimaki dukkan al,umman musulmai ameen👏👏</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> (Dogon Daji)</p><p><br /></p><p> </p><p> A gaskiya kamar yadda mai gari yayi alkawarin cewa zai taima ,haka din ne kuwa don ya taimaka sosai wlh wurin neman Gajiye,,, </p><p> Yakuma fadi a masallacin jumma,a ataimaka ayiwa fadima addu,an Allah yadawo muna da ita lfy,</p><p><br /></p><p> Aiko mutanen kauyen mu su kasa Gajiye gaba da tsina da Allah waddai da ita.</p><p> Wasu sukace ai tayima inna maganine kafin tadaukeni wasukuma suna fadin ai kwadai ne yakai inna badani ,,,, wani gefen kuma sunce ai anfada masu an,sayar dani ne wurin yan yankan kai don Gajiye har tayi arziki a birni ko.</p><p><br /></p><p> Wanan maganganu sune suke kara tayar ma inna da hankali sosai ,,,, duk tabi ta ramay bata cikin hayacinta so sai yanzu,,</p><p> Yayana hafsat ma da ta,fita sai ta dawo gida da kukan ta,saboda gorin da ake mata acikin gari.</p><p> Inna kullun tana kai kukanta ga Allah ,, Allah ya tsare mata fadima,tar</p><p>duk inda take,,, tana kuma tuba da cin amanan mareniya da tayi</p><p> </p><p> Ana cikin haka kawai saiga Gajiye wani mutumin kauyen mu ya gani a Abuja a kasuwan wuse,,,,,,,,</p><p> Bata ganshiba yayi ta binta har yaga gidan da take ya tambaya ko nan take akace mashi eh lalai a nan take zaune tana haya,,,</p><p> Ya aika gida cewa yaga Gajiye har ma gidan da take zaune ya bincika anfada mashi,,,</p><p> Cikin kwana biyu mutanen dogon daji suka zo wurin wanan mutumin</p><p><br /></p><p> Da taimakon jami,an tsaro aka kamata ,,, tana ta fada tana fadin ita mai tayi daza,a zo har nan inda take zaune ai mata cin zarafi irin haka suka ce ai kawai tazo gida mai gari ne ke bidan ta.</p><p> Koda aka isa dogon daji da ita tana wani,wuri wuri da ido har aka kira inna yar kulu tazo kofar maigari,,,,,, </p><p><br /></p><p>Maigari yayi gyaran murya ya bude taro da addua , da kuma yima mutanen shi ,nasiha na su ji tsoron Allah aduk lamarin su na duniya,,,,, su sa Allah agaba saboda zafin ne ma baya kawo samu,,,,,,</p><p><br /></p><p>Bayan dogon jawabin mai gari yayi ,,,,, Sai duk jikin Gajiye yai sanyi. </p><p> Gaba daya an daureta da jijiyoyin jikin ta,,,,, Ko magana ta kasa yi sai gyara zama take yi.</p><p> Duk da sanyi da a,keyi ita zufa take yi kawai. Kafin mai gari yayi bayanin shi sai tace,,, A gaskiya mai gari nasan na cuci yar kulu, </p><p> Nai mata wayo na dauki yar diyar ta da sunan zuwa ganin gida wurina.</p><p> Gaskiyan al,amarin dai shine nakai yariyar kano wurin aiki ne ba wai sayar da ita nayi ba.</p><p> Wurin wata amiyata na,kaita ai,katau, a kano.</p><p> Kuma gaskiya anbani kudin aikinta na shekara na,cinye saboda hakane ma yasa ban dawo gida ba don gudun kada mu hadu da yar kulu .</p><p> Ta nakai nan duk sai wurin yadauki salati,,,,,,</p><p> Wasu ,suna tama Gajiye tir da Allah waddai da halin kwadai irin nata.</p><p> Saida mai gari yayi da gaske yasamu wurin yai shiru,,,,,,,,,</p><p> Aka natsu maigari yace ko Gajiye zata kai su malam sale da wasu mutum biyu inda Fadima take su dauko ta tace "eh zatakai su insha Allah</p><p> Saida gaskiya bata da kudin da zata biya hajiya mai,sharwali,</p><p> Maigari yace kada ta da,mu, shi,zai biya hajiya kudinta,,,, </p><p> Aka shirya yadda tafiyan zai kasance idan an,tashi.</p><p> Daga karshe Gajiye ta roki gafara inna yar kulu tana hawaye, tana rokon gafara,,,,,</p><p><br /></p><p> Maigari ya hada masu tafiya zuwa kano wajen dauko fadima,,,</p><p> Tun karfe shidda na safe suka bar garin dogon daji zuwa kano,,,,,,,</p><p> Sun isa kano da karfe biyun rana ,,,,, saida sukaje sukaci abinci tukun kafin su wuce shagon hajiya,,,,,,</p><p> Koda sukaje shagon hajiya sai Gajiye taga wurin duk ya canza mata ,,,</p><p> Ta,isa wurin wata mace fara kakaura da tagani tana gyara wuta tai mata sallama </p><p> Matar ta ansa mata cikin hausanta da ala,mar harshen yare,,,, </p><p> Bayan sun , gaisa da matar, take tambayar hajiya mai,sharwali, mai wanan shagon </p><p> Sai matar tace gaskiya bata santa ba ma don ita sayen shagon tayi wurin dillalai,.</p><p> Aiko Gajiye ta daura hannu akai tafara kurma ihu tana fadin ta shiga uku ita Gajiye haihuwar mutum biyu ,,,,, </p><p> Ina mai sharwali ta, tafi da diyar mutane,,, ita dai wanan matar tace wlh bata sani ba don ita daga lagos tazo kano ta sai shago ita yar ghanace,,,,,</p><p> Gajiye sai ihu take kurmawa mutane nata kallonta ,,,,,,, a, haka mutane suka taru aka zagaye su don jin ba,asi.</p><p> </p><p><br /></p><p> Wakilin sarki yace aidama munsan karya kikeyi mutumiyar banza kawai kinzo ki sayar da yarinya kin gudu ki ce wai anan kika kawo ta,,,, Gajiye sai sharban kuka takeyi tana bidan agaji</p><p><br /></p><p> Ana cikin haka saiga wani dan tsoho yazo yatambayi ba,asin abin da yafaru akagayamai komai yai shiru nawani dan lokaci.</p><p><br /></p><p> Can yace gaskiya indai matar da yasani ne tana saida abinci a wanan shagon tasai da shago ta wuce saudiya dayaranta duka.</p><p> Yau kusan kwana uku ke,nan da tafiyanta. Kuma shago da gidan ta dashi akayi ciki su duk ta sayar tabar kasan,,,,,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 19:11] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 1⃣5⃣</p><p> BY </p><p> 🐎ZAINAB IDIRS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Hafsat Yusuf</p><p> MSS ILLYAS</p><p> Nerbilar</p><p> Mariya SB</p><p> Fatima Garba</p><p> Ina maku godiyan kulawa da ni da kuke na gode fatan alheri gare ku ko yaushe,,,,,,,,,</p><p> </p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p> (Labarin Fadima Takari)</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mun isa filin jirgin jidda lfy , muka bi layin bincike akai muna screening na shiga kasar da niyar zamu yi sati biyu muna ibada,,,,,,</p><p> Muna fitowa wajen sai, ga hajiya zinaro tare da wani bakin mutum sun zo daukar .</p><p> Tun a mota aka fara hiran harka zai yi kyau tunda babu wanda yasamu matsala daga cikin mu,,,,,,</p><p><br /></p><p> Wani gida aka kai mu mukan sai kallo mukeyi munga larabawa da kuma yanayjn kasar tasu</p><p> Mundan zauna baifi minti goma ba aka dan bamu abinci bawai don mun koshi ba,,,,,, Rugaiyya ce tace min in,tashi muyi ramuwar sallah da bamuyi ba,,,,,</p><p> </p><p> Muna cikin sallah sai ga hajiya Zinaro da wani sun shigo suna fadi, oya oya kowa takawo bizan ta za,a aje mata kafin mu koma don kada ya bace a hannu mu,</p><p> Jiki na rawa muka mika ma hajiya zinaro,,, sai kawai ta dawo ta gaban mu tace,,,,,</p><p> Ina son kowa ya saurare ni da kyau, tanu muna biza din tace kunga wanan , mukace eh tace to idan ba dashi ba bu batun komawa gida Nigeria sam,,,,</p><p> Saboda haka mun karbe na kowa cen ku ne sai kowan ku ya kawo muna kudin da muka biya masa aka hada wanan biza din kuma ya ba da ribi a sama,,,,,</p><p> Sanan zamu ba mutum abinshi ya koma gida ,,,,,, </p><p><br /></p><p> Wani irin ihu naji Yumma tayi cikin kuka tana fadin don Allah hajiya kuyi hakuri ku maida mu gida don Allah kada ku bar mu anan </p><p> Ke rupe muna baki kinji inji katon mutumin da suke tare da Zinaro yace ma Yumma,,,,,,</p><p> Sauran ma kuka naga suna yi nidai ina tsaye ina kallon su ido wuri, wuri dani</p><p> </p><p> Daga nan aka kwashe mu lokacin dare ya fara zuwa wani wuri madan nisa saman wani dutse gidan yake dan karami daganin ginan kasan na da ne,,,, kuma na tallakawa ne ,,,, muna fita motan hajiya Zinaro ta karbi kayan su goron da muka zo da shi tace ma hajiya sai ta dawo zataji yadda za,ayi,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p> Tunda hajiya Zinaro ta aje mu bata leko mu ba , ga yunwa ga matsi ya ishe mu,,,,,,</p><p> Hajiyan mu ta dan shiga damuwa rashin ganin dawo wan Zinaro,</p><p> Wacce ta tafi da dan kudin da hajiya ta kulla zamu je mu ja jari da shi,,,, </p><p> Wata makwabciyar gidan da muke Laila yar katsina itace ta dan tai maka muna da abin da zamu ci,,,,,,</p><p> Data,ga la,lai zinaro ba zata dawo ba kuma da alama ta yaudari hajiyan mu ne,,,,,, Sai hajiya Lai,la bata nuna ma hajiya ai yaudaran ta akayi ba sai ta ba hajiya shawaran mai zai hana mu fara bidan kudi tunda muna da yawa ,,,,,,,</p><p> Shawaran matar hajiyan mu ta dauka,,, mata ita taima hajiya hanyoyi kakala don mu fara sana,a a jidda,,,,,</p><p> </p><p> Aiki aka samo muna a gida jen larabawa don mu samu abin kula da kan mu,,,,</p><p> Gidan wasu turawa nasamu aka kaini inda zan dinga kula ma matar da yaron ta na goye gaskiya na ji dadin aiki a gidan saboda da turanci muke magana </p><p> Ita kuma antyna Rugaiyya goge goge a ka samo mata a wani ma,aikata,,,,, saidai Hajiya Laila tace aikin ba mai dadewa bane zamu bari mu koma Riyahd ne,,, saboda can anfi samun kudi,,,,,</p><p><br /></p><p> Uwar dakina Rita ba laifi gaskiya iyakata daukan yaro in,dan mashi wasa sai ku ma da dare indan nane dinshi ta tafi gida ne nake aikin</p><p> Amma ina samun kulawa sosai daga wurin Ritan,,,,,</p><p> Ina yarinta sosai alokacin don haka ban damu da komai na duniya ba,,,,, </p><p> A lokacin da zamu fara aiki an muna huduba cewa ba ga albashi kawai zamu dogara ba,,,, zamu dan rika hadawa da , dabara samun kudi bawai muce sai abinda aka bamu ba,,,,, </p><p> </p><p> Yan uwana kowa na na,shi aikin daidai sun fara sabawa da aikin bidan kudi,,,, </p><p> Ranan lahadi da mutanen gidan mu zasu je wurin ibadan su sai suka sauke ni gida wurin hajiya kafin su dawo,,,,</p><p> Nasamu hajiyan mu bata jin dadin jikinta dan abinda aka bani in kawo mata ,,,,,,,, Da kyat ta iya dagawa donta gani ko may ye acikin katon ledar da nashigo dashi,,,, </p><p> Duk hajiya sai naga tabani tausayi sosai ,,, amai tafara yi can kuma sai gudawa,,,,,</p><p> Nakama ta na kaita ban daki na gyara mata jiki,,, tea mai kauri na hada mata daga cikin kayan tea da aka bani inzo dashi daga gidan aikina,,,</p><p> Hajiya bata dade da kwantawa ba sai barci yadauke ta,,,</p><p> Natashi nadan gyara mata dan tsukaken dakin namu,,,, daidai naga ma gyara Rugaiyya tadawo daga wurin aikinta,,,</p><p> Munyi murnan ganin junan mu sosai da Rugaiyya ta rungumay ni tana hawaye,,,</p><p> Sai nasa hannu na nashare mata nace kai anty kibar kuka mana ,,, tace Fadima aidole inyi kuka tunda bansan ranan da zamu bar wanan kasar zuwa gida ba,,, nace mata ai babu komai</p><p> Mundan jima muna hira tana tanbayana lbr inda nake aiki daku ma yadda nake zama dasu,,,,,</p><p> Tace fadima don Allah duk ritsi kada ki yarda ki zubar da mutum cinki na diya mace,,,,,, ki kama darajan kanki don Allah </p><p> har zuwa lokacin da Allah zai kawo muna mafita nace to,,,,,</p><p> Iyayen gida na suka dawo suka,zo suka daukeni muka koma gida,,,</p><p> </p><p> Kamar yadda akace aikin wata biyu zuwa uku zamuyi haka din ne kuwa </p><p> Saidai ni abin yayi min daidai don dai uwayen dakina ma sungama contract din su zasu koma garin su,,,, </p><p>Kayan afani masu yawa nasamu wurin su</p><p> Nakawo ma hajiya ta sayar muka hada yan kudin mu muka kulla sai birnin Riyadh,,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 19:15] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 1⃣6⃣ </p><p> BY </p><p> </p><p><br /></p><p> 🐎ZAINAB IDIRIS MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p>Muna godiya ga ubangijib mu sarki Allah da ya nuna muna wanan lokaci mai albarka , Allah ya bamu damana mai albarka ,,,,,,,, </p><p> Jinjina gareku yan huguma group , musan man Anty hasfsat yusuf da anty mariya sb sai mai group din safiya Abdullahi huguma ,,, </p><p><br /></p><p>Almost true life story,,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> GARIN RIYADH </p><p><br /></p><p> </p><p>Garine mai cike da jama,a kala kala ,,, saboda kasan cewar garin itace babban birnin kasar saudiya,,,,,,</p><p> Bamu sha wani wahala ba sam wajen samun aiki gaskiya,,,, da taimakon hjy laila muka samu wuraren ai yukan mu still wani gidan raino aka kara kai,ni.</p><p> Wanan karon wani katon gida aka kaini mai kyau ga shuke shuke iri iri a gidan . Muna shiga gidan naga tunda nake bantaba ganin gida irin wanan ba. Cikin gidan wani swimming pool ne,ga ruwa yana ga ruwa yana bulbulowa ta cikin wasu duwatsu,suna ba wa grass carpet ruwa da fulawowi , Abin takar a film nake kallo ba ido biyu ba ,don dai ni bantaba ganin irin haka ba arayuwa ta,,,,,,,</p><p> Ina ta murna a rayuwata zan ji dadi ashe ba gidan da muke nupin zuwa bane muka shiga,,,,,</p><p> Bayan hjy tayi sallama wani dan matashi mutum yafito ,,,,,</p><p> Cikin harshen larabci yake tambayam mu wa,muke bida ne tace gidan Al, shahideen bin Utuman mukazo </p><p> Sai yace mata ai ba nan bane sai ta kara gida na gaba,,,,, </p><p> Kusan gidan iri daya ne amma dai akwai bambanci a,gina gidan iri daya,ne dan bambancin kadan ne,,,,,</p><p><br /></p><p> Muna shiga cikin gidan muka iske wata, balarabiyan mata, a,kata faren falonta na alfarma tana kallon talabijin tashar tashar makka ce daidai lokacin da suke sallar azahar .</p><p> Matar ba wata babba ce ita ma tana saye da dogon riga sai wani dan karamin hijab akanta,,,carbi rike a hannun ta guda tana ja a,hankali cikin natsuwa,,,,,,</p><p> Ta ansa muna sallamarmu cikin fara,a daidai lokacin kuma ta mike tazo da fara,ar ta tare mu,,,,, </p><p> Suka rungumay juna ita da hjy Laila ta sunbanci gefen kumatun hjy Laila,,,,,,, ni, dai ina gefe ina kallon ikon Allah , wai ashe gaisuwa ce hakanan ,,, sai kuma naji sun buge da yaren larabci,,,,,</p><p> Ina dan gefe tsaye naga hjy Laila tana magana tana nuna ni, da alamar magana ta akeyi,,,, dariya naga sun sa har fararen hakorar matar ya dan baiya na waje,,,,</p><p> Hannu matar ta mika min alamar inzo gurida a</p><p> Nazo tai min yadda suka gaisa da hjy ,,, sai ta dan lakaci kumatuna tai wani magana cikin larabci. </p><p> Tajawo hannu na ta zaunar dani kusa da ita,,, maganar cikin larabci take fadin wai gaskiya tana so ,na , saidai nayi karama da aiki,,,,, amma idan zan iya yimata rainon yarinyarta zata daukeni,,,,,,</p><p> Tana shafar kaina tana magana cikin mutunci da girmawa,,,</p><p> Sukayi cinikin aikina da hjy Laila,,,,, </p><p> Mama Nailabin ta shiga daki ta dauko kudi masu yawa, wanda ni alokacin bansan adadin su ba taba hjy Laila wai kudin aikina ne</p><p><br /></p><p> Hjy Laila takira ni gefe tace min to ita zata wuce don Allah in kula da aikina kada in, bari a samu matsala ko kadan daga fanni na don maman, Nailabin tana da kirki so sai,,,</p><p> Tunda,ga wanan ranan aikina yafara a gidan Al,shahideen bin Utuman ,,,, </p><p> Ni duk wanan abin da akeyi hankalina ya,na can a wancan gidan da muka fara shiga na farko ina son in koma wurin ruwan nan da naga yana fita acikin duwatsun nan dake malala a green carpets ,,,,, </p><p> </p><p> Daki guda aka bani ni kadai dakin babu dai ne babu acikin shi don dai wasu abin ma dai ni ban taba gani ba koda nai zama wurin madam Rita a,jidda muna kallon film din su, na, turawa ,amma banga irin haduwa haka ba,,,,</p><p> Maman Nailabin mace ce mai yawan ibada ga natsuwa da kuma sanin darajan mutum,,,,</p><p> Ita,ma a,nata bangaren tana jin dadin yadda nake kula mata da yar ta so, sai ,musan man, goyata, da nakeyi anytime,,,</p><p> Abinda ban sani ba ashe akwai camera a,dakin na suna kallon duk wani abu da zan ma yar su,,, kusan kwana bakwai ana daukar irin kulan da nake wa Nailabin,,,,,,, abin ya basu mamaki don idan tana kuka nai lalashinta batayi shiru ba nima kukan nakeyi,,,,, acikin kukan kuma zan jawo yarinyar inta lalashin ta,,,,,,, sai mun gaji muyi shiru,,,,don kan mu,.</p><p> Barci kuma kusan a jikina takeyin shi ko a goye ko abisa cikina.</p><p> Jindadin hakan yasa baban Nailabin ya sayo min kayan sawa iri,iri ,,,,,, idan ka gani baza ka ce fadimar kauye bace</p><p> Saboda son da nakewa Nailabin da kula da ita tsakani da Allah yasa </p><p> Iyayen ta sukayi shawar taimaka min ,,,,,makarantar da ke unguwar su suka sani makarantace ta "ya" yan masu kudin kasar sai wani da wani ke makarantar,,,,komai dakwalarcin ka dole kasan abu kafin wata biyu,,, Ranan alhamis da jumma,a ba mu zuwa .</p><p> Amma lahadi da asabar har da yamma muke zuwa ,,,, </p><p> Hakan yasa suka dauki wata yar aikin don kula da Nailabin ,,,, ita wanan matar balarabiya ce yar uwan,,su.</p><p> </p><p> Tunda natafi gidan aiki na ban, karajin labarin yan uwan tafiya na ba.</p><p> Karatu da rainon Nailabin kawai nasa a gabana .</p><p> Duk lokacin da zan wuce makaranta sai na laika wanan gidan na kusa da mu indinga kallon yadda ruwa ke fito wa cikin dutse yana zuba a kasa.,,,,,,,, </p><p> Cikin haka wata rana, na leka naga ba kowa a wajen gidan ,,,,,,, Cikin sanda na lalaba har naje inda ruwan yake fitowa nadinga tara hannu na ruwan yana zubu min,,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 19:37] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈ </p><p> 👣👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 1⃣7⃣</p><p> BY</p><p> </p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Jinjina gare ku yan uwa na na huguma group novel da fatima luv group novel, da fadila group novel, musha karatu group, maman fati group novel,,,,,, nagode maku kware wlh Allah bar zumunci,,,👏👏👏👏👏</p><p><br /></p><p>Almost true life story,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Sam ban jikaran bude kofan da akayi ba daga cikin gidan</p><p> Wani balarabe ne abayana cikin jallabiya fara sai kan shi saye da jan kafiya,,,, Da alama fada yake min</p><p> Bayanshi wani farin mutum ne saye cikin kananen kaya ,,,,, wandon jens sai wata bakar riga tie shet mai guntun hannu,,, hannu shi na rike da waya yanayi,,,,, </p><p> Cikin fushi, na farkon yai niyar jawoni baya ,,,, amma sai wanan wanda nake gani da alma shine oga,,, Ya daga mai hannu cikin wata murya da banji ba yace ya kyale ni kawai,,,,,,,</p><p> Baiko kara waigowa ba ya nupi wata bakar mota da ban ko kula da tana cikin gidan ba ma sai yanzu ,,,,,, cigaba nakara yi da wasa da ruwana duk na jika jiki na dashi</p><p> Saida nagaji nafito don kai na badon wani ya hanani ba ,,,, , Koda nafito ido yai wani ja alamar nasha wasa da ruwa.</p><p><br /></p><p> Wanan balaraben na farko na,gani tsaye yana jiran in fito ya rufe kofan da na sata nashigo ta ciki,,,,,</p><p> Harda bye, bye na mai da zan wuce duk na jika kayana sai digan ruwa sukeyi.</p><p> Sadaf sadaf nake shiga gidan mu don kada agani cikin kaya jikake,,,,,</p><p> Jinayi anja min kune ta baya kawai saina sake jakata ta makaranta ta fadi kasa,,</p><p> Jikina yadauki bari ,,,,,,,,</p><p> Muryan shi kawai naji nagane baban Nailabin ce ke magana yakama yi min fada ina naje tundazu antashi daga makaranta amma ni ban dawo ba,,, gashi hankalin su ya tashi sosai </p><p> Ina dan magana cikin rashin gaskiya nace motar ruwace taimin bari akai ,,,,,, </p><p> Baice min komai ba kunsan su larabawa basuyi ma diyan su fada irin namu nan Nigeria</p><p> Maman Nailabin tazo da sauri ta jani zuwa bandaki ta sake min ruwan dumi tace in sauri in watsa in fito,</p><p>Kada sanyi ya kamani, don su tsoron mura sukeyi sosai don bai raga masu. </p><p><br /></p><p> Tun wanan ranan in,zandawo sai nadan tura kofar gidan inji ko zanyi sa,a injita ,a,bude,,,,,</p><p> Yau ma ina turawa naji a,na min hon din mota abaya na koda na waiga saina tabas gidan za,a shiga nadan, Rakube jikin bango gidan har aka bude get motan tashiga,,,,</p><p> Nima nadan sudada nashiga ciki kafin arufe get din bayan motar na labe har, na cikin motar yafito,,, nadauka mai shi ya shige ciki ne sai nafito daga inda nake labe na nufi gurin ruwan dutse nafara tara hannu na ke nan naji ance ke baki gudun cuta yakamaki ne wai,,,,</p><p> Firgita nayi dajin maganar shi ina shirin gudu na hadu da gudan mutumin ta bayana.</p><p> Yace min in fita cikin tsawa suku, suku nafita ina dan waigen bayana kamar wace za,abiyo baya,,, da guda na karasa waje</p><p> Ina jin sun rufe get din su garam da karfi nikuma na aza da sauri nashige gidan mu</p><p> </p><p> Ina shiga gida nadinga jin hayaniya da kuka abinda bantaba jiba muryan mace na kuka tunda nazo kasar,, shi,naji yau a,gidan mu,,,</p><p> Matar da ke kula da Nailabin ce ,nagani tsugune tana kuka sai wasu maza guda biyu da alamar jami,an tsaro ne su,,,,,</p><p> Maman Nailabin nata sharbar kuka ita kuma ,Nailabin din tana hannun wasu masu fararen kaya</p><p> karar mota naji ta asibiti anzo kofar mu,,, saida naga anfita da Nailabin kamar matatta a hannu ,ai bansan lokacin da na fara kurma ihu ba ina fadin nashiga uku da larabci ina tambayan may yasamu yar kaunata,,,,</p><p> Muna kallo aka wuce da ita zuwa asibiti cikin motar mu, muma muka bisu a baya,,,,,</p><p> Muna shiga asibitin ko fita ba muyi ba akace mu juya zuwa gida ai Nailabin tarasu,,,,,,,</p><p> Munyi kuka sosai hankalina ya,tashi da mutuwar wanan yarinyar sosai don wlh duk da nasan ina son yara ,,, to itakan Nailabin nata daban ne don cikin yan watanin da nayi dasu mun shaku sosai da ita,,,,,,</p><p> Bayan sati biyu da mutuwar Nailabin tunda safe maman Nailabin tace in shirya muje</p><p> Wani wuri mukazo ba mutane da yawa agurin amma akwai jami,an tsaro sosai,,,,</p><p> Sai naga anfito da wata mata ansa mata wani bakin buhu an rufe mata fuska dashi,,,,,</p><p> Aka tsugunar da ita ana bude mata fuska sai naga ashe matar nan ce mai raino ,,,,, tana ta fadi da larabci wai ba itace ta kashe ta ba,,,,</p><p> Kukanasa nima wi,wi nari,rike maman Nailabin duk na shishige mata ajiki ina,noke kaina ajikin ta,,,,,,,</p><p> Muna ji muna gani akasare mata kai,,,,,,</p><p> </p><p> Tun lokacin a tsorace nake a gidan nan,,,,,, sai daga baya nake ji ashe mai, rainon Nailabin itace ta wurgo ta daga saman gado sai akayi sa,an wuyan ta ya kare ,,,</p><p> Ita kuma bata san akwai camera ba,a dakin. Nima sai a lokacin nasan cewa akwai camera a duk gidan,,,,</p><p> Ansa muna cassette din mun kalla naga baban Nailabin yana kuka da hawayen shi,,,,</p><p> Sai sun baka tausayi wlh,,,,</p><p> </p><p> Ni abinda ban sani ba ashe su maman Nailabin ba mutanen kasar saudiya bane,,,</p><p> Mutanen kasar Egypt ne su aiki ya,kawo su saudiya kawai ,,,</p><p> Uguwar , da nake uguwace ,ta ,engineers din matatar mai ta kasan saudiya . duk wanda kagani aunguwar mu kusan a matar mai yake ,,,,, sai babban kusan kasar ke wurin...</p><p> Bayan yan kwanaki, sai baban Nailabin ya shigo gida ina dakina ya kirani nazo nadan zauna .</p><p> Yace min Fatima zamu koma kasar mu don ban iya kara zama wanan kasar ,idan na zauna zandinga tuna Nailabin dina ne ko yaushe.</p><p> Kuka nasa sosai ina fadin zanbisu.</p><p> Dakyat ya bani hakkuri ya lalashe ni nai shiru, yadauko takardu yabani yace min wanan shedar gama makarantar da nayi ne yakarbo min ,,,yace in ina da sha,awar karawa gaba ina iya zuwa.</p><p> Yakawo kudi masu yawa yabani yace inkai ma hajiyan mu </p><p>Ina kuka sunayi suka maidani har gidan hjy Laila,,,,,,,</p><p> Rabuwana da su maman Nailabin ke nan, mutanen kirki da bazan taba mantawa dasu ba arayuwata saboda sun tai maka min da abubuwa da dama ,a rayuwata ga ilimi nasamu ga kuma waye ,,,, </p><p> </p><p><br /></p><p>Hakana nadawo gidan da hajiyan mu ta kama da zama ,,,,</p><p> hajiyan mu tayi murna sosai da abin arzikin da nadawo dashi har da albarka ta dinga samin</p><p> Tana cewa da a,ce duk kan mu zamu samu irin abinda nake samu ne ai da mun koma gida ba da dadewa ba,,,,,,,</p><p>.</p><p><br /></p><p> 🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 19:44] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 1⃣8⃣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p>Fatan Alheri gare ku yan uwana kuma abokai da kuma masoya wanan novel din nawa</p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p> GARIN MAKKA</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ba mufi wata biyu ba muka bar garin Riyadh muka zo garin makka saboda lokacin zuwa umarah ya kusa kuma baza,a wani dadewa ba za,afara aikin hajji,,,,,</p><p> Hjy Laila ta taimaka ma hajiyan mu muka samu wurin zama a garin makka can saman wani dutse ne ta bayan gari,,,,</p><p> Akwai kau,yuka da dama a bayan dutsen akasarin mu yan zuwa cirani nan muke zama a gefen gari.</p><p> Munyi sa,an samun wurin zama maidan kyau sai,dai matsalar hawan saman dutsen da ba mu sababa</p><p> Hjy Laila taba da shawaran mu dan fara saida abinci kafin baki su kara cika gari don Umurah sau kadan afara, ,,,,,</p><p> Masa ,muke sayarwa da shinkafa kaza,da miya sai shinkafa da wake da maidayaji da salad,,,,</p><p> Wani lokaci harda fura muke sayarwa</p><p> Wasu samari majiya karfi hajiyan mu ta dauka aiki suke sauko muna da kayan abincin mun kasa don gaskiya bamu iya saukowa dashi mu,,,,,</p><p><br /></p><p> Allah naba,mu,sa,an sayar da abincin mu don gaskiya ba laifi mutane, suna yabawa, da aikin mu.</p><p> Idan mun saida abincin mu da wuri sai kuma mu canza kama, zuwa wurin bara kafin agama abincin marance,,,,,</p><p> Mune kanani muke zuwa yin bara sukuma antyna Rugaiyya suna zuwa su saro gumama su dinga sayar wa a saman gefen titi ,,,,Saidai da anji jiniyar jami,an tsaro dagudu za a sheka abar kayan don da sunkama mutun to babu sauki wulakanci zasuyi ma mutun su kuma kaika duk kasan da suka ga,dama suyar da kai</p><p> Wanan maganar da aka fada muna tun zuwan mu aka koya muna gudu,,,,,</p><p> Mukuma masu bara za,a samu nama danye fresh mai kyau, shiza a,daura ma,mutun agefen kafa ko hannu, da ka kalla saudaya baka kara waigawa ka diba,saidai ka bada sadaka ka wuce</p><p> Za,a daure ma mutum kafa ko hannu idan kani sai ya baka tausayi kamar kayi kuka,,,,,zaka, ga kamar dungu ne kawai mutun haka aka haife shi,,,,</p><p><br /></p><p> Wani kuma za,aba mutum keken guragu ka, nade cikin ke kamar mai shan inna kana dan wani nokewa kamar gaske,,,,</p><p> Duk wanan salon baran na, iya su kamar nadade cikin harkan.</p><p> </p><p> Musalin karfe shadaya na rana ,,,Daidai in da motoci ke cunkoso dayawa ,,, wutan titi yanuna masu alamar su tsaya tukun,</p><p> Nazo da muryana kamar ta rarara ina fadi cikin harshe larabci </p><p> Ina fadi a,taimaka min da abinda zan kai ummeena asibiti</p><p> Wata mota na,nufa mai glass karara ana ganin wanda ke bayan motar zaune yayi irin kwanciyar bayan motar nan,,,,,, Fari dogo kan shi, sai shining yakeyi da ka diba kasan akwai jindadi wurin wanan mutum din,,,,, </p><p><br /></p><p> Hankalinshi, Yana ga laptop din shi yana ta dikilanta dagani, hankalishi yadauku sosai,,,,, ,, Jin murya na,da yayi ta i,she da kuwa, yadan, dago kashi don yaga mai wanan muryan rarara ,,, </p><p> Ya dago a hankali yakai diban shi inda nake tsaye ,,, yakau da kai,, sai,kuma naga ya waigo ni da sauri</p><p> Daidai lokacin wutan ba da hannu na titi yanuna kore ,, alamar a,wuce anbada hanya ,,,,</p><p> Daidai lokaci ya dauko kudi masu yawa cikin wata jaka agefen shi,,,yamiko min na karba ina ta godiyan jin dadi.</p><p> Motar ta wuce nakai dibana ga kudin saida na fidda ido na don ganin yawan kudin da ke hannu na.</p><p> Cikin Aljihun, rigata mai zip, da hajiya tai muna, na kulle, ina murna wanan rana mai albarka </p><p> Motar ta,dan wuce green light din kadan saina bayan yace ma driver ya,ga kamar ya gane wanan yarinyar kuwa saidai ya manta inda yasanta,,,,,,,,,</p><p> Sai driver yace bai kalleta ba don haushi taba shi saboda nasan baka son hayaniya baka kaunar masu wanan dabi,ar baran musan man ma bakar fata</p><p>,,,,,</p><p> Bayan mundawo wurin sa,na,ar mun ta marance, Mungama saida komai namu zamu tafi gida</p><p> Saina jawo antyna Rugaiyya, gefe na nuna mata kudin da na samu yau, Ido ta zaro waje</p><p> Ina kika samu wanan kudin fadima na fada mata ,yadda akayi tai shiru nawani dan lokaci.</p><p> Sai,tace min mutafi gida to.</p><p> </p><p> Koda muka isa gurin hajiya itama saida tayi mamakin wanan kudin masu yawa ,,, ta,dinga samin albarka tana ta washe baki,,,,</p><p> </p><p>Antyna Rugaiyya nasamu waje, zaune gefenta nima nazo na zauna ashe, kuka,takeyi a wajen bansani ba saida na yi mata magana sai naji tai min shiru nakai dibana ga fuskanta sai naga hawaye,,, </p><p> Rugumay ta nayi ina kuka nace mata may yasa may ki yar uwata ,,, kuka yakara kubce mata,,,, </p><p> Tace fadima baki ganewa ne ke,,,,yanzu don Allah haka zamuyi ta bautawa hajiya bazata maida mu gida ba,,, idan har tace sai mun biyata kudin jirginta ai ina gani dai yanzu ta samu ko</p><p> Amma wanan ai bauta mukeyi mata cin amanar yai yawa,, </p><p> Nadafata nace aikin san tun agida aka bata mu ,, muyi mata bauta ko ,,, saboda haka sai muyi hakuri har ranan da Allah zai kawo muna mafita,,,, Dan Allah ki daina wanan kukan hakana pls,,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA 🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 19:49] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 1⃣9⃣ </p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKWA🐎</p><p><br /></p><p> Gaskiya muna saki a wanan zamanin da wasu abu biyu da manzon Allah Annabin Rahama yai kwadai ta muna yinsu zai kaimu Aljanna barin su zai iya kai mu wuta. Hakin,makwabtaka da Zumunci ,,,,, Allah ubangiji yabamu ikon kula da makwabtan mu da kuma yin zumuci da yan uwan mu Ameeen👏👏👏👏</p><p><br /></p><p>Yan uwana yan Huguma group ina maku godiya kulun tare da sauran yan wani group da ban fadi sunan su ba,,,,,,</p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ni fadima na iya bidan kudi kala,kala kamar yadda kusan kudi baya isan TAKARI , Duk wani sallon bara da sana,a an koya min na iya gani yar shekara sha uku zuwa sha hudu,,,,,</p><p> Amma hajiyan mu tana alfahari da ni sosai wlh saidai bata fadi a,gabana acewanta idan ta yabani a,gabana zan yi sanyi indaina samo mata kudi,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Watan Azumi ya kama ibada akeyi yanzu sosai yan kasar mu ta Nigeria dama wasu sauran kasa she ,sun cika garin makka da kewayen ta sosai,,,,, </p><p> Munji dadin wanan cikar don kasuwar mu ta budu so sai</p><p> Muma muna kokari wurin zuwa ibada,,, Rugaiyya tabamu shawaran kulun kafin, mu fara sana,a mu ,ko,karta mu ,shiga cikin Masijid muyi , Dawafi </p><p><br /></p><p> Yauma kamar kulun misalin karfe sha dayan rana nakusa cikin dandazo jama,a ina Dawafi,,, kafin in fita in fara bara don bamu abinci saida Yamma muke yi,,,,,</p><p> Dandazon yan Serbia sokayo kaina duk sun matse ni banko iya nunfashi saboda kowa nason ya kai bakin kofar shan madara,,,,,</p><p> Ji kawai nayi an,dagoni Cak daga cikin rutsun da aka matseni, An ajeni gefe guda,</p><p> Saida na maida nunfashi na daidai naga wani mutum dogo, fari, kyakyawa gabana yana min fada ,cikin harshen larabci muryan shi kamar yana lalashina amma daga yanayin fuskan shi fada yakeyi min,,,,</p><p>Ke wata irin yarinyace wai kina ganin taron yan Serbia kowa na kaucewa ke bakijin tsoron su ,zo su, tatakaki, su wuce ,,,,</p><p> Nidai tunda nasamu na tsira ban ko tsaya nai mai godiya ba na wuce abina ,,,,,,,,,</p><p> </p><p> Bayan kwana biyu da yin wanan rutsun cikin haram da nayi fitar kutsu ,,,, </p><p> Dadai da angama sallah azahar lokacin baran mu yayi ke,nan .</p><p> Saidai ni nakan canza hanya ne bani zama guri daya,,, idan nai kwana daya ko biyu sai in can wata kofar in kuma canza sallon barana</p><p> </p><p>Yau ma kamar kullun sabuwar kofa na sake ina zaune kamar wata mara hannu ina bara sai naga anzo daidai kwanon bara na , an ,aje, min kudi sabbi fill acikin kwano ,,,,</p><p> Koda na daga kai inyi godiya sai naga mai,shi har ya wuce ko,,,,, bayan maishi, kawai nagani amma cikin daga murya nake mai godiya,,,,,</p><p> Kudine masu yawa nagani ,Aiko baran da na bari ke nan ranan ban kara zama ba.</p><p><br /></p><p> Kwana uku tsakani kuma na canza wata kofa don zan canza kama ,,,,, </p><p> Kofar da ake shiga da gawa don ayi mata sallah itace na zauna na kawo wani nama na aza akafa na sai kuda ke bi,,,,</p><p> Duk da nasan ba kowa ke bi ta wanan hanyar ba sai lima,mai da wasu manyan malamai da mutanen masu son yawan ibada su ke yawan bi wanan hanyan sai ko idan andauko gawa ,,,,,</p><p> Idan mun zauna muna yawan samun sadaka daga yan uwan mamata,,,, bakowani mai bara ke yawan zaman nan ba don wasu tsoro suke ji,,,,,,,</p><p> </p><p>Muna zaune tare da yan tsirarun almajiran da ke waje jama,a nata bautar Allah aiko sai a,kace ga gawa nan za,a shigo dasu na wasu mutanen da sukayi hatsari ,,,,,</p><p> Cikin Almajiran mu Atika da take zaune kamar gurguwa aiko sai ta manta yadda ta nade kamar musaka,,,, dadai taji ana fadin tarik tarik tarik aiko saita mike tsaye tana shirin gudu,,,</p><p> Wata mata, dake gefenta zaune tare da mijin ta tanuna ma mijinta Atika,,, tai, mai bayani cewa itace fa, zaune kamar gurguwa, dazu,,, saiko ya mike, yadanko wuyan Atika ta baya, nan suka fara rikici, tana fadin yasake ta tun suna yi su biyu har takai sunfara ji</p><p>Jama,an da ke,wurin ko sukayo kanta wasu na duka wasu na fadin akaita wurin jami,an tsaro,,,,, muna zauna saiga wata da gudu take fada muna ai ankama Atika,,, nan tashiga yi muna bayani ,,,, kafin kace kwabo yan bara sun shiga watsewa saida wanda ke da nakasar gaskiya,,,,,,</p><p><br /></p><p> Maimakon in gudu sai kawai na nufi gurin da aka kewaye atika ana duka tanata tsala ihu,</p><p> Wani balarabe ya rike mata wuyan riga ta baya,,,, </p><p> Duk tausayinta ya kamani,,,,</p><p> Sai kawai nai kukan kura nafada cikin taron nadauko naman da nasa akafa kamar gyambo na jefa ma taron aiko sai aka watse da gudu ,,, daidai lokacin jami,an tsaro suka iso suma saiko naja hannu Atika muka ar,ta da gudu nace mata mu raba hanya,,, </p><p> Ina cikin gudu na ji an,fisgoni anzaunar dani bisa wani abin sallah har jamian tsaro sukazo suka wuce mu kaina na duke,,,,,,,</p><p> Saida naga lalai sunyi nisa sai nayi niyar mikewa in gudu</p><p> Muryan wanda ya jawoni ranan daga cikin taron Serbia wa naji,,,, yana fadin ki tsaya nan har sugama bincke ,,,, duk wanan maganan baiko waigo inda nake ba,,,,,</p><p> Ana tada sallah la,asar namike nabi jam,i akayi sallah tare dani ,,, koda naga an,kusa sallamewa sai na sulale a hankali batare da sanin wanda ya taimakeni ba,,,,</p><p> Kafin ace haka har lbr yakarade yan bara cewa ankama Atika Ankama Atika,,,,</p><p> Koda nadawo gida ban fada ma kowa ga abinda ya faruba yau,,,,,</p><p> Cikin dare na fara barci kawai naji ana tashina ,,,, nikuma lokacin ina jindadin barci na don dan lokacin da muke samu muyi barci kadan ne ba muda time,,,,,</p><p> Jin murya hajiyan mu danayi shiyasani mikewa dasauri ,,,barci na ya watsake kamar bani ba.</p><p> Waje ta fito dani sai naga wasu mutane su uku tsaye maza biyu da mace guda,,,</p><p> Hajy tace masu itace wanan ko sukace eh itace</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA 🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 19:57] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 2⃣0⃣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎 </p><p>🐎HUGUMA GROUP & KAINUWA WRITERS GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yan uwa musulumai muso wa "yan uwan mu abinda muke so wa kan mu,,,,,, </p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ido na kara ra budewa inga ko suwaye ke bidana cikin wanan daren</p><p> Gaskiya ban san su ba kuma ban taba ganin su ba ma,</p><p> Babu abinda ya fado min a raina sai abinda ya faru dazu a wurin bara</p><p> Aiko sai naji gabana yai wani dam,,,,,,</p><p> Muryan daya daga cikin mutanen ya katse min tuna ne na, ,,,,</p><p> Yace fadima munzo ne muyi maki godiya ,bisa ga irin taimakon da kikayi wa yar uwa guda dazu,,,,, </p><p> Agaskiya ba kowane zaiyi irin wanan taimakon ba ,,, kuma inba don ke ba agaskiya yau Atika da dubun ta ya cika gaskiya,,,,</p><p> Ni,ko sai wiki wiki nake yi a gefen su ,Don gaskiya banso hajiya tasan wanan zancen ba don zata iya duka na,,,,,</p><p> Sukayi wa hajiya godiya suks wuce abinsu</p><p> </p><p><br /></p><p> Tab suna wucewa aiko hajiya ta ja min kune tana fadin ashe baki da hankali ki,kaje ceton wata maimakon ki gudu shine ke wai gaki uwar tausayi ,,,,, </p><p> Aida ankamaki da kin raina ma kanki wayo , idan halinki ne gobe ki koma </p><p> Duk fadan da takeyi kaina yana kasa ban daga kai na ko kalli inda take ba,,, fada iya fada dai nasha shi wurin hajiyan mu ranan,,,,,</p><p> Lokaci ya ja yan umarah sukazo suka rage yawa bakamar lokacin azumi ba.</p><p><br /></p><p> Yanzu mun fi bada karfi da ,"yan buga buga,sayar da kaya da abinci , dakuma yan aikin da,ba,arawa,,,,,, kafin lokacin aikin hajji yayi.</p><p> </p><p>Ni,kan dan kewaya gida je muna dan yin aikatau saidai ni gaskiya ban faye son wanan ,irin aikin ba nafison bara da talla yafi mun,,,,,</p><p><br /></p><p> Ko da muka dawo gida daga wurin bidan kudi ,, yau nasamu hajiyan mu da wasu mata a gidan mu,,, </p><p> Saboda haka ban tsaya inji ko suwaye ba,,, sai nadan fita waje,,,,</p><p> Wai ashe wasu matane yan kun,giya sunzo gurin hajiya ne suji idan zata shiga a,dashe ,,,, saboda tana da yara aiki gwargawado ,,,,,</p><p> Ma,ana akwai kudi sosai a wurinta </p><p> Inaji dasu Yumma da anty Rugaiyya suka dawo hajiya na basu shawaran cewa zata fara zuba adashe indan ankwashe mata sai mu dawo gida Nigeria dazama kwatakwata don ita ,ta fara gajiya da zaman TAKARI</p><p> Rugaiyya bata yarda da wanan shawaran na hajiya ba saboda tasan halin matan TAKARI basu da tabbas,,,</p><p> Kowa na iya cutan dan uwan shi,,,,</p><p> </p><p><br /></p><p> Bayan kowa yayi barci sai Rugaiyya ta tadani ,taimin alamar mufita waje,,,,,</p><p> Bayan munje waje shine take fada min shawaran da hajiya ta fada masu ,, duk da yarinya nake sai kawai naji ban yarda ba,,,</p><p><br /></p><p> To amma may ye abin yi kafin dai mu tashi muka tsaida shawar guda,,,</p><p> Abinda hjy zinaro taima hajiyan mu ban manta da shi ba don har gobe yana cikin zuciyar hajiya , Kuma Zinaro itace sillan zowan mu wanan kasar,,,,</p><p> Amma daga karshe yaudaran hajiya tayi ba ko lbr ta.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yanzu duk wani abinda muka samu zamu raba biyu muba hajiya rabi, saura kuma mu boye abin mu ba wanda yasani</p><p> Saboda muma munyi wayo mukuma dan san mutane kadan</p><p> Duk da hajiya bata barin mu muna shiga mutane sosai kulun fada take muna.</p><p><br /></p><p> A, cikin irin wanan yanayin narashin nayi muka samu gyaran wani shago,, kamar yadda kuka sani cewa, indan lokacin aikin hajji ya gabato jama,a daga kowani ,yanki , na, kasan suna shigowa gari don saida kayan ,</p><p> Saboda baki mahajjata masu zuwa aikin hajji</p><p> Irin hakan yana kawo muna samun kudi sosai ,,, akan, dauke, mu aikin gyaran shago sauran wuraren masana antu,,, akasari su sai wanan lokacin suke bude shago.</p><p> Idan mahajjata suka wuce baza,akara budewa ba sai kuma wata shekara tadawo,, Za,a bude ta,,,,,,</p><p><br /></p><p> Mun samu wanan aikin a,wani babban shagon saida kayan sawa na zamani , na maza da mata da yara moderate masu kyau ,,, </p><p> Sai kuma gefe guda kayan gyaran daki ne kala,kala irin na matan zamani gudan gefen shagon kuma kayan kitchen ne na zamani masu kyau iri, iri ,,, shagon karshe na kayan turare ne kala kala masu kamshi sosai.</p><p> Wata hajiya tasamo muna wanan aikin gyaran wurin, </p><p> Munyi aiki sosai mun gaji yauce rana ta karshe da zamu gama aikin mu ,, </p><p> Kuma za,a sallamay mu mutafi,,,</p><p> Ina cikin shagon kayan sawa ina dan gyaran wani wuri,,, </p><p> Dai dai,ta inda nake tsaye naga wallet din wani mutun yafadi ,kasa amma banga fuskan mai shi ba,,, ina dai iya hango kafar shi,,,,,,,</p><p> Da sauri na sauko daga inda nake nazo nadauki wallet din bandai bude ba inga ko may, ye a ciki ba,</p><p> Cikin sauri sauri nake ta diban kafar mutane ko zanga takalman mai wallet din ban gani ba,,,,</p><p> Gabda zai zauna cikin mota ni kuma na sheko da dan gudu ina bidan mai wanan wallet din sai nayi arba dashi zai shiga mota,,,</p><p> Cikin sauri na nufe shi ina daga mai hannu ,alamar su tsaya,,,</p><p> Koda ya waigo sai yaga aidashi nake magana,,, sai yadan tsaya yajirani,,, Yana mamakin ganin wanan yarinyar kuma a shagunar shi,,,, </p><p> Mika mai wallet din nayi kawai na juya batare da na tsaya ko yin wani bayani ba,,,,</p><p> Mamaki yakama shi, yasan dai ko babu kudi acikin akwai kusan riyar dubu dari ga kuma American dollars gefe guda aje ,,,,,,, gashi kuma na kawo mai abinshi babu wata alamar da ta nuna antaba komai acikin wallet din,,,,</p><p> Cikin mamaki yake binta da kallo yana fadin anya kuwa wanan yarinyar ba aljanna bace kowa ,,, </p><p> Ko ina sai na ganta kuma bidan kudi zanga tana bida yau kuma gashi Allah ya bata kudin amma sai ta dawo min da su,,,,,</p><p> Kuma batare da ta tsaya ko in bata wani abuba daga ciki,,,</p><p> Yakoma don ya ganta ,,, saidai ansamu akasin hakan maimakon takoma cikin shagon ashe bata shiga ciki ba,,</p><p> Wucewa tayi zuwa wani shago dake gefen su sayen kayan sanyi don su sha,,,,,</p><p> Ko ina andiba ba,a,ganta ba babu ko almarta acikin shagon,,,,,</p><p> Azuciyan mutane wurin sai suka kama mamaki anya kuwa mutunce ma yagani kuwa kodai ya dan shiga tunane har yaga kamar hakan,,,</p><p> Kusan zai wuce yaji Rugaiyya na fadin ina fadima ,, ina fadima tazo su tafi gida,,,,</p><p> Ahakan yabar wurin saidai yana kiyastawa azuciyan shi wata,rana zaiganta ai,,,</p><p><br /></p><p>Yana barin gurin tadawo da kayan sha niki,niki acikin leda,,</p><p> Suka dan samu wuri gefen da babu kowa suka sha</p><p> Dazasu wuce mai kula da shagon yai masu godiya yabasu kudin da oganshi yabayar araba masu,,,,,</p><p> Kudine masu yawan gaske saboda jindadin yadda sukayi decoreting din wajen yayi kyau sosai .</p><p> Shiyasa aka basu kudi masu yawa don yabawa da aikin nasu.</p><p> Cikin murna da farin ciki suka wuce gida,,,,</p><p> A hanyane fadima ke fada masu aita sinci wallet din wani mutum amma dai tayi sa,a taga mai shi har tabashi abinshi.</p><p> Sukaina ta dafe kai don takaici tace fadima ki mayar mai fa?</p><p> Ashe har yanzu baki da wayo ke, kudin da muke bida kamar mutashi sama Allah ya ba ki shine zaki mayar ma mai shi,,,,,</p><p> Rugaiyya dake gefe zaune tace au dake ce ashe bazaki mayar mai da kudin shiba kenan,,,,</p><p> Gaskiya fadima bata,kyauta ba inji mari aida bataso inta da ta kawo muna mu muraba,</p><p> Hmmm inji Yumma aiko an baku baku zaku kashe su ba hajiyace zata kwashe su duk inda kuka aje su,,,,, shin wai kunsan duk lokacin da muka fita sai hajiya ta caje kayan mu.</p><p> Ni ma,ranan da nabar zabirata agida nakoma indauko shine nasamay ta tana ta cajin kayan mu</p><p> Naikamar bangane,ta,ba nadauko abina nafito,,, </p><p> Hmmmm ai intasan wata batasan wata ba,,, kawai sai anwayi gari ta bide mu bata gan mu ba,,, don daini nakusa gudu daga wurinta ,,,bintu tace zatai min hanya mutafi kasar yamal mu zauna can,,,,,</p><p>"Ke,Mari kada kifara hakan wlh kibari kawai mu koma gida yadda muka zo,,,</p><p> Insha Allahu bamu dawama cikin wanan ukubar dole watarana gida zamu.</p><p> Haka sukai ta shawara a tsakanin su har suka isa gida,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 20:41] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 2⃣1⃣</p><p> BY</p><p><br /></p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p> </p><p> Yan uwa mu kyautatawa yan uwa musulumi ako yashe ladan ka yana ga Allah</p><p><br /></p><p>Kainuwa group novel da Baiwa group novel ina kara mika godiya na gare ku tare da masayana kuma yan uwana na huguma group,,,,,,,</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Almost true life story,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p> ( Lokacin Aikin Hajji )</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Wanan lokacin gaskiya muna jin dadi sosai don lokaci ne na harko ki kala,kala </p><p> Muna kuma ji tankar agida muke,,, duk lokacin danaga yan Nigeria musaman mata jinakeyi kamar kada na bar su su tafi.</p><p> Zandinga kyautata masu ta hanyoyi daban daban </p><p> Ko abincine zamu sayar masu shi da araha, ne saboda son su da mukeyi tankar a,gida muke.</p><p><br /></p><p> Yau ma kamar kulun muna suyar dankalin turawa da kwai da safe tun karfe biyar muke fara aikin mu saboda yawan masaya da muke da su masu son abasu dankalin da kwai,,,</p><p> Saidai duk da yawan da akaiyi, muna ,,,,munayi muna, kallon hanya kada yan bagaladi su zo su riske mu agurin,,,,</p><p> Don basu da tausayi ko kadan da sunzo kumune kawai bayan sun facalar da kayan suyar tamu sai kuma su yi cikin mu da duka da taki kamar jakkai,,,,,</p><p> Shiyasa da mungansu zamu sheka mushige cikin Alhazai mu boye,,, saidai wani lokaci zamu hadu da wasu marasa imani su nuna mu akwashe mu zuwa kasar mu,,,</p><p> Azubar da mutum wulakance babu ko kudin mota balle sutura ,,, duk abinda kasamu acan zakabar shi,,</p><p> Wasu su wawashe ganimar su.</p><p> </p><p> Rana yai zafi mutane yawanci sun shige cikin masallaci sun labe, </p><p> Nafito da kayan sayar wan da su hajiyan mu suka sai dila na gumama ,suka raba kayane masu kyau ne sai nadan fito dashi nakai bakin titi indan sayar </p><p> Gaskiya ba laifi na sayar da kayan duk an rufe ni a,na saye muna da yawa a,gurin masu kaya jama,a sun taru,,,,</p><p><br /></p><p> Sai kawai naji ance Lah Fadima da sauri na waiga don inga kowaye kekirana hakanan,,,</p><p> Juyawan da zanyi sai naga malam jibo makwabcin gidan kawu sale, gida biyu ne a tsakanin mu da shi a dogon daji.</p><p> Aiko da murna ta ina dan ihun jin dadin ganin shi danayi abin kamar amafarki,</p><p> Muka dan gaisa dashi natan baye shi lbrn kowa nagida,,,,, Na, tambaye shi masaukinsu yai min kwatance nace mai zan zo Insha Allah,,,,</p><p> Yau kowa yagan,ni cikin farinciki nake,,, saboda jinakeyi kamar a gida nake,,, </p><p> Ko antyna Rugaiyya ban fada mawa ba naita boyon maganar azuciyata, </p><p> Tundaga ranan da na gane masaukin malam jibo nadinga da wainiya da shi so sai,,,, nakawo kaya masu yawa da kudin da muke boyewa nida Rugaiyya na,bashi nace ya kaiwa inna da yan uwana,,,,</p><p><br /></p><p> Munyi da malam jibo zaizo yaga gidan mu,,,,,, har na shirya don in,zo in kai,shi sai nayi wani tunane kawai sai nafasa.</p><p> Tundaga ranan na canza wurin zama ban yarda mu hadu dashi kokadan,,,, </p><p> Saidai ni ina ganin ko,yaushe da alamar ni yake bida da ido.</p><p><br /></p><p> Mun samu kudin saida abinci sosai dana gumama </p><p> Malam jibo ya shiga damuwar rashin gani na don shi yaso gaskiya yaga gidan mu da kuma hajiya don yaji ta bakinta yadda akayi tazo dani nan batare da sanin iyayye na ba</p><p> Saidai kassh hakan bai samu ba dole yasamu wuri ya dunkule sakon dana bashi zuwa gida.</p><p><br /></p><p> Har yanzu ina yawan zuwa wurin dawafi in nafito bara sai nagama dawafi sai in samu wuri inda ba hayaniya inyi shirin barana ,,,,, batare da wani yagan ni ba.</p><p> </p><p> Mukan bi har cikin gidajen Alhazai mata da dare koda safiya mukai masu tallan haja masu kyau da amfani </p><p> Saboda hajiya Laila tasan duk wani abinda mahajjata ke bukata ,,, itace ke taimakon hajiyar mu da shawaran abinda zamu dinga sayar wa</p><p> Saboda samun kasuwa .</p><p> Matsalar mu guda hajiyan mu bata da godiyan Allah duk abinda ka iya samowa bata yabawa saidai ta kushe.</p><p> Yau mana,kamarr, kulun nayi ciniki ga kuma kayan gumama na sayar nakumayi bara ajihuna fam da kudi nakawo mata </p><p> Gashi kuma ina jin ciwon kai tun daren jiya ,saboda rashin barcin da ban samu nadan yi ba, don, ina tunane gida ,,,,</p><p> Tun da naga malam jibo gida yadawo min sabo azuciyata</p><p> Ina ba hajiya kudi nafada mata kaina yana,min ciwo sai kawai tace min wai ,,,, in koma kafin sallah magriba inyi baran maran ce,,,, </p><p> Bance mata komai ba nafito inajin , wasu hawaye masu zafi na bin fuska suna sauka kasa.</p><p> Ga kuma ciwon kan nawa kamar ana karamin shine,,,,</p><p> Nazo gefen Haram na samu guri nadan zauna sai she,shekar kuka nayi ,,,, Don gaskiya ban iya kara yin wani bara yan ciwon kan yana damuna sosai,,,,,,,,,</p><p> Ina cikin wanan halin kaina a,duke sai kawai naga an miko min handcarchef,,,,,,Fari mai shegen kanshin irin turaren nan ta kasan larabawan tsakiya,,,,,,</p><p><br /></p><p> 🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 20:45] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARU✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 2⃣2⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAW🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP 🐎</p><p><br /></p><p> Rikon Amana wani abu ne mai nauyi a,rayuwa, indan bazaka iya ba kada ka dauka domin saba ma rikon amana yana iya jefa bawa acikin bala,i</p><p> Allah ubangiji yabamu ikon rikon amanan dake kawunan mu👏👏👏👏</p><p><br /></p><p><br /></p><p>A kulun ina maku fatan alheri a rayuwa yan Huguma group ,Kainuwa group, Maman Fati , Baiwa group, Fatima luv group, tare da sauran yan uwa masoya wanan novel din nagode nagode nagode👏👏👏👏</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Batare da na,kalli wanda yabani ba sai kawai na rike handcarchef din na goge fuskata da ke hawaye,,, amma hannu na guda yana rike da kaina da ke min wani irin ciwo,,,,,,,</p><p> Na share dan gutun majinan da yaleko min ta hanci mai, kama da ruwa,,,, sai na mayar ma mai shi da abinshi,,,</p><p> Cikin larabci yake tamabayata mai yasamay ni ,sai na nuna mai kaina </p><p> Baikara yimin magana sai kawai naga ya mike yace min intaso muje, yaimin alama da hannu in,biyo shi, </p><p>Sai na tashi nabi bishi,, batare da nayi wani tunane ba,,,</p><p> Wayan shi yaciro naga yana magana ,,,,, kafin mintina kadan saiga wata mota mai kama da kifi a tsaya,agaban mu, tana tsayawa, aka bude bayanta yai min alamar inshiga na fada ciki.</p><p> Ina shiga wani irin sanyin A, C da kamshi yadake ni sai kawai naji yanayin yai min dadi na fara lunshe idanu na a, hankali, </p><p> Wai, ashe daga haka na suma ban sani ba,,,,</p><p> Hankalin wanan mutum yatashi kware da yaga na rankwafo mai da zamana acikin mota ba,a,fi ko minti biyu da fara tafiya ba,,,, </p><p> Cikin daka tsawa yake ma driver magana yayi sauri su, isa, asibiti dani,,,,</p><p> Cikin yan mintina suka iso asibinti </p><p> Yakira wani abonkishi likita yai mai bayanin gashi damara lfy bakin asibi aka turo wasu masu daukan mutum suka daukeni sai ciki.</p><p> Nadauki dan lokaci ban farfado ba ,,,, da taimakon Allah nadanyi atishawa mai karfi kowa yayo kaina,,,,</p><p> Bayan "yan aune ,aune da akaimin sai aka gane cewa ina fama steeretret</p><p>ne ban da hutu ko kadan aiki yaimin yawa ina bukatar hutawa kadan</p><p> Aluran barci akai min daga nan bansan inda nake ba kuma,,, saida komai ya kam,mala likitan yaja hannu shi suka fito waje,, </p><p> Ahamed ina kasamo wanan yariyan ,,,, likitan ya kashe shi da ido,,,,</p><p> Shiru yai mai ya busar da iska ,,, kawai ta baki sai hannu da ya dunkule ,kamar mai shirin nashin wani</p><p> Dr Umar banda lokacin baka ansa yanzu kaiwai dai served her life pls.</p><p> Ido yabi Ahamed din dashi yana ta tunane azuciyar shi ,,,,,,</p><p> Don dai a iya sanin da yai mai baida kowa anan shikadai ke zaune wanan kasar, kuma ba wai wani mai shiga harkan jama,a bane balle ace, </p><p> Dokan mu bamu wuce karfe goma na dare a waje yau gashi har kusan sha biyu babu alamar fadima ,,,,,</p><p> Tun abin baidamu hjy ba har ta tashi , tana fada ta tada sauran tace masu ,,, su tashi gaskiya yau ba lafiya ,,, fadima tabace don ,sometimes nakan riga kowa dawowa gida kuma ina fin su samun kudi don zafin namana, </p><p> Rugaiyya dama idon ta biyu ne batayi barci ba tana ta tunanen ida natafi,,,,</p><p>Tuncikin dare ake bidana ba,aganin niba har gari yawaye babu lbr na .</p><p> Hakalin hajiya ya kara tashi sosai ,,,, </p><p> Duk inda akasan muna zuwa anje babu fadima</p><p> Kuma ba wanda yace ai yagan,ni</p><p> Hajiya tana kuka tace aiko tashiga uku in wani abu yasamu diyar mutane,,,, may zatace a,gida .</p><p> Ko banza bada sanin kowa nawa ta zo dani saudiya ba, gashi kuma laifin nata ya karu na bace.</p><p> </p><p> Tunda nafara barci wanan mutumin bai tafi ba yana gurina yaje yadawo hankali tashe,,,,</p><p> Azuciyan shi yana fadin ai dole hakan ya samay ta ,,,, don wanan yariyan batada hutu son kudinta yai mata yawa.</p><p> Shin wai ma ita wacece ma dai da take wanan irin bat da kama kala,kala gani yar karama dani ,,,,,,</p><p> Washe gari musalin shadayan rana likita yace asamo min abinci in,ci</p><p> Mutum yafita sai gashi da abin lafiyaye cikin take away da abinsha yakawo min.</p><p> Baifi rabin a,wa ba da shigowa na farka zubur dani.</p><p> Yunkurin mikewa nayi sai naji nurse na fadin kin tashi na kada mata kai alamar "eh .</p><p> Natambayi nurse din ko a ina nake sai,tace min asibiti, zubur nayi na mike zaune, </p><p> Waya kawo ni saita nuna min wanda ke tsaye bakin kofa hannu acikin aljihu, gudan hannu shi waya yakeyi, baka ma sanin akwai mutum yana waya a dakin.</p><p> Nai kokarin dagowa zaune sai naji na kasa nakara yun kurawa intashi ,,, ya nufo gadon danake yana fadin ina zaki haka,,,.</p><p> Nikuma inace ma nurse karfe nawa tace min shabiyu saura na rana </p><p> Subahanallah nace na, mike da karfi zaune ,,, duk sukayo kaina har shi mutumin da ke tsayen suna kokarin kamani </p><p> Ina zaki yace min ina fadi da karfi banyi sallah ba , har rana tayi hakan </p><p> Nurse din tace ai inbari tukun indaji karfin jikina sai intashi inyi saboda nakai a,wa bakwai ina barcin hutu ko fiye,,,,</p><p> Ko saurarenta banyi ba na sauka saman gadon zata tare ni sai mutumin ya daga mata hannu alamar ta rabu dani kawai,, intashi da taimakon nurse din nasamu natashi ta kai makewayi ,,, takunna min ruwa masu dumi nayi wanka nayi alwala na nafito,,,,,,</p><p> Yana tsaye gefe yana kallon yadda nake sallah atsanake kamar ba yar karamar yarinya ba,,,, cikin fidda ka,idodin sallah nakeyi har nasamu na gama.</p><p> Azuciyan shi sai mamaki yakeyi wai ita wace wanan yariyan haka ,,, wani fuska gani saliha wani fuska kuma macuciya,,,,,,,yana cikin tunanen yaji motsin Nurse tadawo,,,, </p><p> Nadan jima ina addu,a wurin ina idar wa yajawo ledan abincin ya aje min gabana yace min inci in nagama zai zo in mai kwatancen gidan mu sai ya je yafadi ina nan asibiti.</p><p> Saida naci abincina nakoshi sosai nai kat,,,,,Nurse tabani magani na da likita yarubuta akasawo nasha natashi a hankali nakoma bisa gado na kwanta nai kamar ina barci sai nurse din tadan fita.</p><p> Inajin tafita na bude ido na namike zubur a hankali na leka naga babu kowa sai na gyara rolling din gyalena da kyau nakama hanya,,, har nadanyi nisa sai nadawo nadauki ledar magani na da sauran abincina nafita cikin sanda </p><p> Allah yataimakeni nasamu nabar asibitin batare da kowa yaga fitana ba. </p><p> Duk da ina jin dan jiki cikin sauri nasamu har nakai bakin titi natare taxi na shiga saida mukadan yi nisa na tuna aibanda ko sisi a hannu na ce ma mai taxi yadakata nai matuwa zan sauka yanata fada nasauka nasan dai ko banza nayi nisa da asibitin </p><p> 🐎 ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/3, 20:46] +234 703 602 1388: ✈✈✈ TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 2⃣3⃣</p><p> BY </p><p>🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Yan uwa musulumai muyi hattara da zamani komai na iya faru daga wayewar zamani musan,man (Zina) mu, nisan ci zina akwai ta zuciya ,akwai ta ido akwai ta tafiya, da sauran su ,,,,,,</p><p> Allah kaba ikon nisantar ta Ameeen 👏👏👏👏👏👏👏👏</p><p><br /></p><p> Group din kainuwa da group din maman fati ina muku fatan alheri ko yaushe,,,,,, Huguma group Allah yasa,alheri</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ina zuwa layin mu na ga yan uguwar mu na ta kallo na .</p><p> Wasu kuma mamaki ne karara a, fuskan su , </p><p> Nai sallama na shiga cikin gidan mu.</p><p> Hajiya ta mike ta rungumay ni tana hawaye ,,,, tana, fadin ina kika shiga fadima,,, tun jiya ake bidan ki.</p><p> Ban bata ansa nasamu wuri na zauna gefe, saboda rashin karfin jikin da ban banji sosai ajikina.</p><p><br /></p><p> Ledan magani na natura mata agabanta don ta gani,,,, ta,kara zaro ido waje tana tambayana mai yasamay ni.</p><p> Nakwashe lbrn abinda nasani nafada mata,,,dakuma gudun danayi daga asibitin .</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Saida nayi kwana biyu banjin karfin jikina sosai ,Ita,ko hajiya sai korafi take min wai naki murmurewa in koma wurin bara.</p><p><br /></p><p> Yanzu kan nadan ji sauki nida kaina na shirya fita yau,</p><p> A,hankali nake tafiya har na iso kofar masallaci dai dai kofar shiga Bin dawood nasamu gefe na zauna na hada kaina da gwaiwa na .</p><p> Yakamata ace nasaba da wanan kamshin turaren Al, madinal nuriya, .</p><p> Cikin sauri nadago kaina ,saboda nasan kamshin turaren wanan mutumin da ya taimakeni ne har kusan sau biyu.</p><p> Mukayi ido biyu dashi abinki da mara gaskiya, saina dukar da kaina kasa, Nadan gyara zama na kadan gefe na ya shimfida salayar shi,</p><p> Batare da ya fuskance ni ba yace min ya jikin na ansa da </p><p>Alhamdullah baikara ce min komai ba sai yaci gaba da lazimin shi baiko kara kallon inda nake ba,,,</p><p> An idar da sallah azahar ina son in je gurin barana .</p><p> Kamar yasan abinda nake sakawa a,zuciyata sai naga,ya mike tsaye ,, ya,miko min kudi masu yawa yace inkai gida basai nayi bara ba yau .</p><p> Hawaye kawai ke zuba min a idona ko godiya na kasa yi mai ,,,</p><p> Hakana na dan lalaba nakai ma hajiya kudin tana ta washe baki tana fadin koke fa, da kina nan kwance da wazai bamu wanan kudin masu yawa haka,</p><p> Nidai bansan komai gamay da wanan mutumin ba amma haka yadinga taimaka min da kudin bara har naji saukin jikina.</p><p> Itako hajiya bata taba tambayana ina nake samo eanan kudin sabbi fil dasu ba ka kamshin turaren shi dake man,ne makudin</p><p> Rugaiyya ce ta lura da hakan saboda idan na raba biyu zan bata wanda muke boyewa kulun ranan ina bata sai tace min Fadima ,,,, </p><p> Nace na, am wake baki wanan kudin masu yawa haka kulun,,,</p><p> Shiru nayi nadan wani lokaci,,,,ina wasa da yan yatsun hannu na,</p><p> Takara maimaita tambayar ta </p><p> Cikin tsanaki na warware mata tun lokacin da na fara ganin shi amasallaci har zuwa yau,,,,</p><p> Tanisa a, hankali tace kuma bai fada maki koshi waye ba, nace mata a,a </p><p> Shiru takarayi tana nazarin maganata,,,,,</p><p> Kidai bi a hankali kiji don mutum abin tsoro ,,,</p><p> Inda nadanji sanyin maganar taki dakikace yakaiki , asibiti kuma ya ce ki gwada mai gidan ku</p><p> Kada kiyarda wani yasan gidan ku fadima, saboda hajiya kin ji.</p><p><br /></p><p> Tunda naga naji sauki sai ban kara barin mun hadu da wanan bawan Allah ba,,, </p><p> Na canza gurin yin harkokina,</p><p> Sai inje in saro kaya irin su jakkuna takalma da dai sauran kayan da nasan mata na bukata indinga bi masaukin Alhazai ina sayar wa ina samun riba masu yawa.</p><p> Hajiyan mu sai tana rena kudin da nake kawo mata wai sunyi kadan ita tafi gane ma indinga fita bara,,,</p><p> Yafi kawo mata kudi da yawa,</p><p> Da,taga naki zuwa baran ranan da nakawo mata kudin cikina sai ta watsa min su afuska ta dinga surfa min zagi wai ina mata bakin ciki yanzu,</p><p> Don karta sa,mu karuwa dani tun tana zagi har ta hau,fada da duka na </p><p> Saida na,jibgu sosai wurin hajiya san nan nasamu maceta aka, kwace,ni kacal a, hannuta.</p><p> Duk wanan dukan baisa na koma wurin da zanga bawan Allah nan mai taimako na ba.</p><p> </p><p> Sannu sannu mahajjata suka watse kowa ya koma kasar shi akabar mu mu yan labe muna ta labe laben mu don kada akama mu.</p><p> Don da ankama kasai yadda hali tayi da mutum</p><p> Irin wanan lokacin ba komai muke samu ba so sai </p><p> Don haka mazan mu da matan mu yan takaru, sai mu dinga bin gidaje mu aikin , ana biyan mu kudi,</p><p> </p><p> Muma dai irin hakan ne ta kasan ce damu,,,</p><p> Wani Alhaji aminin hajiyan mu ne ,ina, ganin,shi,yana yawan zuwa wurinta anytime,,,</p><p> Shi yataimaka mata yasamo muna guraren da zamu dan dinga neman kudi don kada a zauna hakana.</p><p> Duk da aikin da muke dan yi muna zuwa bara dan lokaci lokaci, saboda kasan cewar kasar makka kullun cikin yawan baki take baka gane dare da rana anytime akwai jama,a agarin.</p><p><br /></p><p> Abinda bamu sani ba nid antyna Rugaiyya shine Sukaina ta gane inda muke boye kudin mu ,,,,, sai kawai muga kudi yana rage yawa .</p><p> Nidai tunda naga kudi na rage yawa nadauka antyna ce ke dauka tana wanu lalurar ta da shi </p><p> Ita kuma da taga haka sai ta dauka ai nice ke dibar kudin, saidai, da ta,ga da gaske ana zarar kudin so sai ,,,,,,</p><p> Tace min Fadima may kike saye da kudaine haka, </p><p> Cikin mamaki nace kudi wasu kudi kuma tace wanda muke tarawa mana,,</p><p> Ni tunda nake ban taba daukar ko kwandala ba acikin su,,,, </p><p> Yo nima may zan saye da kudi ,,,,, kaya dai tun wanda baban Nailabin sukayi min sunake ta sawa ajiki na har yanzu.</p><p> </p><p> Nanda nan naga ta shiga cikin wani hali takai zaune tana fadin mun shiga uku ,,,,,,,,,</p><p> Akwai wace ce tagane inda muke aje kudin mu har take diba.</p><p> Nadauka ko kece ai saida naga abin yai yawa shiyasa natanbaye ki yau.</p><p> Nima nadauka kece ke anfani dasu ai,,,, yo wani amfani kudin da saura kadan mu hada kudin komawa gida mu huta da wanan bakar wahalan,,,,,</p><p> </p><p>Cikin bacin rai tace aikuwa zangane ko wace take muna wanan sherin.</p><p> Tundaga ranan muka canza gurin boye kudin mu,,, amma muna dan aje saura a,gurin.</p><p> Antyna ta kula kulun zamu fita Sukaina ce ke zama ta bayan fitar mu,</p><p> Yau bayan duk mun fita sai akabarta abaya tana fadin wai sai ta dan gama abinda zatayi zata fito,</p><p> Har Yumma da mari suna mata ba,an wai tadai saba da zaman na baya yanzu,,,</p><p> Bayan fitar mu da yan mintoci sai kawai tanufi wurin da antyna take boye kudin can bayan fridge din mu kasan wani tsohon basket da muke tara tsofafin kayan mu ciki,,,,</p><p> Ta bude raggan da muke kule kudin ke nan Rugaiyya tashigo dakin sukayi arba da juna,,,</p><p> Ragan da sauran dan kunshin kudin ta karba a hannu ta ta juya tana fadin mun barki da Allah muguwa,,,,,,</p><p> Cikin daga murya tana borin kunya take fadin ,,, eh andauka din aike ma sata kike wa hajiya shiyasa nima nake dauka,,,,,</p><p> Ashe wai saurayi tayi dan bagaladi shi take bawa kudin so sai,,,,</p><p> Shikuma sai yaudar ta yake yi yana karban mata kudi yana lalata da ita,,,,,</p><p> Wai ba zai bari akamata ba,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎 ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP 🐎</p><p>[10/3, 20:51] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 2⃣4⃣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Allah ubangiji bai yo mu daidai ba, indan harka ga wanda yafika to kaima kafi wani, </p><p> Don haka yan, uwa, kai ma wanda yafika fatan alheri , karkayi masa hassada, kai kuma Allah zai maka sakaiyan na Alheri,,,,,,,</p><p><br /></p><p>HUGUMA GROUP ina jin, jina maku tare da KAINUWA GROUP,,,, MAMAN FATI GROUP Allah yakara dauka nagode nagode,,,,,,,</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> (NIGERIA)</p><p> DOGON DAJI</p><p><br /></p><p> Ranan da malam jibo yadawo ranan ya kai sakona gidan mu da</p><p> kanshi,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p> Inna tana zaune bakin murhu tana hada miyar marance sai taji a,na kwada sallama kofar gida,,,,,, </p><p> Yaranta duk suntafi makarantan islamiya ,.</p><p> Takoma daki tajawo hijab din ta tayafa,,, zuwa ganin wanda ke mata sallama kofar gida,,,</p><p> Takusa kawai kofar yai daidai da yaran sun dawo daga makaranta,,,, </p><p> Su sukafara gaisawa da shi, suna fadin Alhaji ho Alhaji ho ,Yaushe ankadawo yace yau munka sauka,,,,</p><p> Sai ga inna ,,,,,, Alhaji jibo kaina tafe lalai da dawon ku,,,,</p><p> Banyan sundan gaisa inna tana gefe guda,tsugune tana sauraren abinda yakawo shi gidan ta ya,u,,,, </p><p> Ya tura mata sakon gabanta yace yar kulu tace na,am, Ya,sake cewa, Fadima ta tacce inkawo maki wanga sako ,,,,,,,,</p><p> Zubur inna ta mike don kaduwa jin sunan fadima da taji anyi,,,, yaciga ba da fadin awo, ita,taban wanan sakon tacce inkawo maki inda kike</p><p> Kuma tana gaishe ku,,,,</p><p>Aiko motsi bata iya yiba daga inda take,,,, </p><p> Hasfsat ta tace kaga fadima shin kaka,fadi ,,, yaca, A,woo da ijjiyan ga na,u, naganeta,</p><p> Aiko inna,sai kuka ita dayara tana fadin wayyo ita Allah fadimarta wayyo fadimata,,,, </p><p><br /></p><p> Fadima don Allah kiyafan ni nakai ga haka,,,, malam jibo dake gefe rakube shima hawayen yake gogewa,,,,</p><p> Yai gyaran murya tun jama,a basu taru yace ke hafsi shiga da kayanga ciki tukub na,,,,</p><p> Shiganta keda wuya sai ga jama,a sun fara taru gidan jin kukan yar kulu da yaranta</p><p> Shin wai mi ka faruwa, na, nanga? </p><p> Fadimata yaggani makka ,, makkafa ? A,woo ita,ta kuwa naggani da ijjiyaga nau,</p><p> Nan yashiga basu lbr yadda suka hadu da fadima dakuma irin tai makon da tayi mai har da sayayan tsaraban da ta tayashi yasaye.</p><p> Abuguda ya boye bai fadi ba gudun datayi na kaishi masauki, ta,,,</p><p> Kowa yana ta al ajabin wanan maganar ta malam jibo watau fadima na nan da ranta a,makka zaune daram,,,</p><p> Kuma hannu mutanen kirki masu mutunci,,,</p><p> Yayi hakan ne don cire zargin yarinya kamila mai kirki fadima a,zukatan mutane ,,,</p><p> Saida komai ya lafa an watse kowa ya koma gidan shi yana fadin albarkacin bakin,shi </p><p> </p><p> Cikin dare inna ta tada hafsat ta bude masu sakon da fadima ta aiko dashi,,, sugani.</p><p> Dogayen riguna ne da zanin gado cottoning masu kyau kala biyu sai kudi wanda ya kai kimani kudin Nigeria dubu dari,,,,</p><p> Aiko hankali inna yakara tsshi sam bata yarda da maganar malam jibo ba.</p><p> Tunda safe tadauki kayan taje gidan yayanta malam sale ta kai mai ,, shima yana gani yaji tsoro ,,,, Anya kuwa yarinya karama kamar fadima zata bada wanan sakon akawo mata gida,,,</p><p> Sana,ar may takeyi can da har ta samun wanan kaya haka masu kyau da tsada,,</p><p> Ya tashi yaje gurin </p><p> malam jibo dakan, shi ,nan malam jibo yakara yi mai bayani daladala har ya fahinta,,</p><p> Malam jibo yakara yiwa kawu godiyan irin dawainiyar da nayi masa acan,,, </p><p><br /></p><p> Duk da malam sale yakwantar wa inna da hankali yaba kowa sakon shi,yan uwana sunata murna da sakon da na aiko masu dashi,,,, </p><p> Amma ita inna ji takeyi kamar tayi ihu taganta makka,,,,</p><p> Magana ya kama yawo agari malam jibo yaga Fadima a,makka tare da matar da Gajiye ta sayar mawa ita,,,</p><p> Har zuwa akeyi ganin sakon da fadima ta aiko da shi anata mamaki,,,,</p><p> Bayan kwana biyu inna tadauki kudin takai wa malam sale tace yayi abinda yadace da kudin</p><p> Shiko, sai yace tacire masu yawa asai kiwo da su saura ta sai abinci suci ita da yarant,,,</p><p> Har inna taso taki wanan shawaran malam ya dan lalabata ,har yashawo kanta tayarda ,,, yace kowa da hanyar da Allah yai mai na arzikin shi killa arzikn fadima da, su yana can ne shiyasa yakai fadima har can inda kowa nata bai taba zuwa ba gashi kuma malam jibo yace tana zaune da mutanen kirki.</p><p> </p><p> Da haka inna tadan sake jikinta taba kowani yaro kayanshi tace yasa</p><p> Zanin gado kuma za,a ,aje ma Hafsat na aure ,,dama aurenta ya kusa,</p><p><br /></p><p> Tun lokacin inna yar kulu ta kara maida hankali ga addu,a tana neman Allah yakara kare mata tar diyar ta Fadima,,,,,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA NOVEL🐎</p><p>[10/3, 21:02] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 2⃣5⃣</p><p> B Y</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Daure ka/ki biyayya ga iyayenka domin watarana ,kaima mahaifine/mahaifiya</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Godiya nake,wa,antyna Hafsata yusuf da anty mariya sb, Anty safiya mai huguma, da babban marubuciyar littafin Dan maliki ,,,,,,,,</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> AHAMED</p><p><br /></p><p>Wanene Ahamed wai,,,,,</p><p><br /></p><p> "hmmm ,,,,,,</p><p> </p><p>Ahamed wani bawan Allah ne dan shekara talatin da haihuwu, fari ne irin farin da bazaka iya gane cewa ba,aciki , jinsin larabawa bakake yake ba, Saboda sajewan da jikin shi yayi danasu.</p><p> Dan Nigeria ne,da ke zaune a babban birnin Riyadh ta kasar makka,,,</p><p> </p><p> Karatu mahaifin shi yakaishi yi can ,,Daga nan wani kamfani tatar mai ta kasar saudiya ta dauke shi aki saboda kwazon shi da zama gwani, afanin, gyara gyaran. Kayan nauran mai wanan fannin. </p><p> Engineering ne a maikatar da yake aiki,kwanzon ,shi, da zama gwani, yasa suka ki barin ya bar kasan,,, anturashi sauran kasashen duniya, yaje yakaro ilimi sosai,,,,,</p><p> Sauran referners na kasan saudiya masu zaman kansu suna hayanyan shi ,, Don gyara masu na,urar su, idan sun samu matsala aiki,,,</p><p> Don ,haka kudi,na shigo mai ta kowace hanya time to time, kamar ruwa,</p><p> Ahamad mutum ne shiru ,shiru wanda bai son magana kuma shi baison hayaniy akusa dashi </p><p>Mutum ne,wanda bai wasa da ibadan shi ko kadan, duk abinda yakeyi lokacin sallah bai wuce shi,,, ,,, hakan yasa ko da yaushe zaka samay shi a masallaci yana ibada,,,,,</p><p> Saikuma, ranakun aiki ba kullun ne zaka ganshi ba . </p><p> Yanada sha,awan business sosai don hakane ma yabude wasu sha guna masu kyau da kaya masu ma,ana acikin garin Riyadh da kuma garin makka,,, shagunonin suna tashe sosai saboda kayane irin nazamani zaka gani acikin su,,,,,,,</p><p> Idan lokacin aikin hajji yayi hutu yake dauka ta musam man danyin ibada .</p><p> Baya kaunar irin da bi,ar da yaga matan Nigeria suna yi acan don haka shi ko sadaka baya ba irin su,,, don yasan kwadai ne kawai yakaisu bawai rashi ba.</p><p> </p><p> Ahamed haifafen garin maduguri ne,,,, mahaifi sh,i shine, Zannah garin maduguri,,,</p><p> </p><p> Tun yana jariri maihafan shi suka rabu,,, hakan yasamo, a,saline, tunda daga komawa gida shan ruwan zafi da mahafiyar shi tayi,,</p><p> Yan uwanta suka rike ta, a gida suka ce bazata dawo ba ,</p><p> Dama ba wani dadi auren yayi,ba, aure ne,na,gidan ,aure na danki yan uwa suka hada ,, tare da sa hannu mahafiyar mahafin shi watau Zannah lawal,,,,,,,,, </p><p> Mahaifin shi a Landon yazauna inda ya auro hajiya mama, a,can suka hadu da ita kaunar wani abokin shine da sukai karatu Can, </p><p>Ganin kirkin dakega zannah lawal yasa yasa yayan Amina ya hadusu aure dayake shi mutum ne mai hakuri saiko ya amince da tayin abokin nashi,, </p><p> A,kano aka daura aure aka kai mashi ita can inda yake aiki london,,,</p><p> Saida hjy mama ta haifi diya uku duk maza sanan ,,,, suka dawo Nigeria da zama,,,,,, irin dabi,un ta yasa mahafiyar ,Alhaji lawal Zannah tace dole ne ya bidi yar gida ya aura.</p><p> Saboda gashi da abin hannushi amma badama yan uwan shi suzo gidan shi,,, sai ace aibasu fadi cewa zasu zo aranan ba, </p><p> Dole mutum ya hakkura ya koma inda yafito, ko kuma yuwa takar mutum.</p><p> Ire iren wanan halin yasa maifiyar shi ta je can kauye cikin dangi tasamo mai mata yar asali da mutunci.</p><p> Tunda aka kawo,ya ghana gidan zanna ta koma kamar boyi boyinsu itace mai masu aikin komai agidan.</p><p> Wani fitina ma wai,sai dare yayi karfe tara zatayi masu pepper soup na kifi, ko kaji ,ko kayan ciki,,,</p><p> Ahaka ,yaghana tai ta bauta agidan bawani jindadin aure da tasani.</p><p> </p><p><br /></p><p> Da rabon cikin Ahamed yazo, lokacin hjy mama ta tafi garin kano ganin gida ,shi ne, rabon Ahamed,, yaratsa tsakanin su,,,</p><p><br /></p><p> Aiko tunda mama tadawo taga alamar ciki ga yaghana ,,,,,,, aiko ina wuta tasakata,,, </p><p> Fitinar ma sai ya,kara karuwa fiyeda na da,,, ga lalurar ciki ga wahalar aikin gida</p><p> Taramay taiwani fayau, da ita, </p><p> Da haihuwar yazo mata tsohuwar dakemasu aike da,sharar gida itace ta kama mata ta haihu ta haifi danta mai kama da uban shi sak,,,</p><p> Saidai shi yaron yafi uban haske da kuma hanci,,, na uwar yadebo,,,</p><p> Har kwana biyu ba,a fada ma maigidan,Yaghana ta haifu ba , bakula kuma ba abinci mai dadi irin da yakamata aba mai haihuwa, da ita da dan jaririn ta duk suna cikin wahala,,,,, </p><p> Saida tsohuwar nan mai shara, taga diyar mutane na shirin mutuwa , sai ta saci jiki tafita taje tafada ma wasu dangin su, a,cikin gari,,,,,,</p><p> Sukuma suka aika ma mahafiyar zannah lawal dontazo ta ceci diyar mutane </p><p>Tsohuwar batayi sanyi da gwaiba ba,,, tai masu dirar safiya agidan,,,,,</p><p> Yayi mamakin ganin su da safe haka,, har mama ta fara fadin,,,</p><p> Tau mu bamu san zaku zo ba gashi bamuyi abinci karin kumalo da kuba, </p><p> Tsohuwar tadaga mata hannu tace aje abincin ki ,, ina yariyar mu,da ta haihu,</p><p> A,lokacin zannah yafito da ido waje yace yaghana ta haihu ne ,,, takama wani inda inda tana cewa dama naso in surprise dinkane ,,,, </p><p> Ranan yadan yi ta maza yadaka mata tsawa yace Amina ashe baki da imani ne haka ban sani ba</p><p> Yi min shiru inji mahaifiyar shi ai,duk abinda takeyi da saninka don kai ka daure mata ,,,</p><p> Fito min da yarinya na gida ne gashinan mubar maki ki jika kisha babu dan uwan lawal da zai kara zuwa nan muddin ina raye,,,,</p><p> Wani daki da akayi acan bayan dakunan ,su aciki yaghana ke jego, acewar mama wai kada tabata cikin gida da karni.</p><p> </p><p><br /></p><p> Tunda tsohuwa tazo ta,tafi da yaghana garin su bai samu zuwa gida diban su ba,,,, da ranan suna ya zagayo yan uwan lawal,su,kasa ma yaron sunan mahafin lawal,,,,, watau Ahamad</p><p><br /></p><p> Saida suka kai kusan sati uku agida, lawal mahaifin Ahamad,yazo masu da kaya niki niki dana uwa dana yaro,,,</p><p> Tsohuwa taita masifa tace yatafi da kayan shi ita kudin shi baida may su ba ,,,, </p><p> Dama ta yi wanan hadin ne don kada zumuncin shi dana,"yan,uwan shi ya lalace,, nan gaba yasa ta aura mai diyar kaunar ta,,,,</p><p> Saboda idan akawai yar uwanshi agidan, aidole dangi suzo gidan ganin ta koda mama bata so,,,,,,</p><p> Sai gashi ashe shi mijin hajiyace sosai bata sani ba,</p><p> Sani Allah sani Annabi ya tara ma tsohuwa jama,a aka bata hakkuri tayarda zata karbi kayan da yazo masu dashi,,,, amma batun komawa sai yaghana ta huta tukun ita da yaronta,,,,</p><p><br /></p><p> Yau zaizo gobe zai zo shiru, kake ji,, koda yazo kuma har ya koma baiyi maganar komawan su ba,,,, ganin haka wani yayan yaghana yabishi har can birni yakarbo mata takardan saki</p><p> Ya fada mai cewa da ma don zumunci su da tsohuwa suka bashi yagana don tsohuwa da uwar su aba,guda suke,,, </p><p> Kuma koda uwar su tarasu tsohuwa ce ta koma tankar uwar su itace ke masu komai da yakamata uwa tayi wadanta</p><p> Yace to kagani babu yadda za ayi taso abu wurin mu mu hana mata .</p><p> Mungode ma Allah tunda munyi mata biyyaya munbaka kaunar mu ,</p><p>Amma kai, ka kasa mata biyayya ka rike muna kauna amana,,,,,,,, </p><p> Tunda dan uwanshi ke magana yasada kan,shi akasa baidago ba har yakai karshen maganan shi.Tabbas yasan gaskiya ne yakasa yi ma mahafiyar shi biyayya akan wanan auren ,, wai kuma badon baison yaghana bane ,aa yana son ta amma yarasa dalilin rashin kulatan da baiyi.</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p>[10/4, 07:53] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 2⃣6⃣</p><p> BY</p><p><br /></p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Dan uw/ "Yar uwa , Daure ka/ki rike sallah akan lokaci domin zata sama, hasken a,fuska sanan , Watara zata taya ka kwanciyar kabari ,,,,,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p> Anty safiya mai huguma Anty hafsat yusuf da anty mariya sb kulun fatan alheri na gare ku bai karewa , Allah yasa mu dace da rahamar sa,,,,,,,👏👏👏👏👏👏</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Almost true life story,,,,,,.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tun lokacin da aka yaye Ahamed sai rikon shi ya koma hannu tsohuwa watau kakan shi,,, </p><p> Ita kuma mahaifiyar shi yaghana tai wani aure nan kauyen su ta auri wani malamin arabiya mai karantar da yaran garin,,, hankalinta kwance,,,</p><p> Tunda hajiya mama ta lura da cewa Alhaji lawal yana yawan zuwa kauye kai ziyara,wurin " yan uwan shi,,,,, hakan yasa,ta yin tunane,yan zu saboda Dan shi, yake yawan zuwa kauyen,,,, kuma yana kai mai abin arziki har yan uwa suna samu suna amfana da Alhaji lawal din,, jifa,,,,,, Ta mance cewa uwar shi ma tana kauyen zaune</p><p> Aiko sai ta tadda fitina wai ai ita,ce ya,dace, tarike Ahamed a hannunta ba wai akashi kauye ba,,,, kulun cikin cewa takeyi yanzu , shi wanan yaron a kauye zai tashi ga yan uwan,shi a birni kada yazo sufishi wayewa,,, tana wani tausa murya,,,,,,</p><p> Da, irin wanan dadin bakin har taciyo kan Alhaji lawal,,,</p><p> Watarana bayan yaje kauyen sai ya fito da zancen tafiya da Ahamad birni,,,,</p><p> Nanda nan tsohuwa ta haushi da fada tace babu mairabata da Ahamad ,,,tunda gurin macuciyar matar sa,ce zai kai shi,</p><p> Ko uwar yaron yaya takare balle dan karamin yaro irin haka,,,</p><p> Hakana yakoma batare da yadauko shi ba,,,,</p><p> Ta naganin ya, dawo batare da yaron ba ai,sai takara haukacewa, </p><p> Dataga dagaske baza taci nasarar dauko yaron wurin tsohuwa ba sai ta caza sallon takon ta,,,,</p><p> Tafara aika masu da abin arziki akai ma yaron,</p><p> kusan anshi baibar kowa ba , sai mutane suka dauka aita canza halinta ne,,,</p><p> Bayan kwana biyu sai tadauki yaran ta, taturasu hutu kauye ,,, aiko abinka da yaro nan da nan suka saba da yan uwan,shi, sabo sosai sukayi</p><p> Da za su dawo hutu mahaifin su Alhaji lawal yazo daukan su ,.</p><p> Sai Ahamad yasa kukan cewa zai bisu birni,,, tsohuwa ta hana ,,,,,</p><p> Saida yan uwan lawal suka sa masu baki akan cewa zai je yasa shi makarantar boko ce irin na yan birni don kada yan uwa suzo su fi shi nan gaba.</p><p> Da wanan dabaran Ahamad ya dawo birni da zama amma da sharadin cewa zai dinga zuwa hutu kauye.</p><p> </p><p><br /></p><p> Tun da suka iso mama taga da Ahamed ne sai taji kamar ancire mata kaya,,,,</p><p> Da daki guda ta ajeshi da yaranta ,karamin dan ta Suraj yana fitsarin kwance sai tace ai ,Ahamad ne yayi shi ,,, sai taita dukan shi,,, </p><p> Karshe ma dakin uwar shi inda suke aje shirgin kayan su can tasa aka maida yaron shi daya yake kwana,,,,</p><p> Duk wanan abin Alhaji lawal bai sani ba,,, </p><p> Saidai yakan lura dacewar yaron baya walwala sosai cikin yan uwa,</p><p> Sai yadauka ai rashin sabone,</p><p><br /></p><p> Makarantar da su salis da suraj suke zuwa ta diyan masu hannu da shunine na garin ,,,, can aka fara sa Ahamad .</p><p> Amma da ga karshe saida mama tayi makar kashiyan da aka maida Ahamad wani dan karamin makaranta na kudi nan kusa dasu,,,,</p><p> </p><p> Inda yan uwanshi sukaje karatu shima can yaje karatun shi na secondary FGC minna anan sukayi karatun su har suka kare, </p><p> Yaran mama suna gaba da Ahamad su tasa Alhaji lawal yakaisu karatu kasar turawa , A,cewan mama can anfi karatu da sanin aiki,,,</p><p> Batasan ta bata tarbiyan yaranta bane ,,, don tunda sukaje sai babban yafara bin kungiyar mawaka suna waka da rawa a clubs maidan dama daman shine umar nabiyun dan mama shi yana karatu amma yana da shan giya sosai, Suraj kuma wasan kwallon dawaki yakeyi can babu zancen karatu</p><p> Lokacin da Ahamad yagama karatu za,a turashi waje sai mama tai,ta shige da fice wai sai abarshi nan gida don kada su watse babu kowa agida,</p><p> Da har Alhajin,ya yarda da hakan sai kuma abokin shi kuma aminin shi yayan mama yabashi shawar yaturashi saudiya ya yi karatu can</p><p> Ai ko mama ina wuta tasaka wanta aciki tana fadin da ma bai son ta shiyasa zaice afita da Ahamad waje,,,</p><p> Tun lokacin suka fara samun matsala da yayan nata ,,,, </p><p> Saboda matar yayan nata tafada mai yadda Amina tamaida Alhaji lawal da yan uwanshi,,,, yai mata nasiha taki bari </p><p> </p><p>Kafin Ahamad yawuce saida yazo,Auno kauyen mahaifinshi don ya sallami tsohuwa da mahaifiyar shi,</p><p> Babu wani sabo tsakanin Ahamad da mahaifiyar shi ,,, ko yaje garin Auno baya yawan zuwa gurinta ,</p><p> Saboda saidai suyi ta zama a daki ba mai madan uwa magana sai yagaji yayi mata sallama ya wuce.</p><p> Dama yanzu da ta haifi yara mata uku bayan shi agidan malam ,,, dasu yake dan hira har yagane halin da suke ciki</p><p> Da zai wuce abin da da mahaifi sai yaghana taji ba dadi aranta</p><p> Dole tafidda kunya taima mijin ta malam magana akan atai maka wa Ahamad da addu,a,,,,,</p><p> Wani ruwan rubutu yabashi sai kuma nafil filin da ya rubuta mai yace ya fakeyin su koyaushe,,,,,</p><p><br /></p><p> </p><p> Ahamad na,a shekara farko ,a karatun shi,akaba Alhaji lawal Zannah borno </p><p> Lokacin kuma ya aje aikin gwaunati yakama harka sana,oi,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 08:00] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣 </p><p> 👣👣👣👣👣 </p><p> 2⃣7⃣ </p><p> BY </p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Nasan cewa mutuwa na jirana, kowani lokaci,,,, Don haka sainake ta tanadin guzuri,,,,, Na,kware don shirin gamuwa da Ubangijina Allah subbahanahu, wata,ala,,,,,</p><p> Ya Allah kasa muyi kyakyawan karshe,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gaisuwa da jinjina ga masoyan TAKARI nagode da nuna min kulawan ku ,,, ina kara gode ma yan huguma group novel and conversation da suka kara min kwari gwiwa inci gaba da rubutuna nagode nagode</p><p> </p><p><br /></p><p>Almost true life story,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ina zaune bakin masaukin mu saiga hjy Laila tazo da murna na ,natashi natare ta,, saboda takoma muna kamar yar uwan uwa,,,</p><p> Muna ganinsu kamar sune yan uwan da muke dasu acan,,,,</p><p> Cikin harshen larabci take min magana tana tambaya na ina hjy take ,,,,</p><p> Cikin rashin damur ansan da zan bata nace ai sun fita da Alhaji Ali dan takari,,,, </p><p> Sai naga tafidda ido waje,, tace watau ,Maisharwali bata rabu da wanan macucin ba ko,,,,</p><p> Duk nasihan da naimata nata ja baya dasu macutane , amma taki,,</p><p> Ba magana ta bace don haka sai natashi naje na bude fringed nadauko mata lemon kwanko mai sanyi nakawo mata dan abin taunawa na aje mat,,,,,</p><p> Takama samin albarka tanata yabawa da irin halin mu na hakkuri da hajiyan mu.</p><p> </p><p> Ba,ai wani dadewa ba sai ga hajiyan mu ta dawo ita da Ali dan takari ya sauke ta a mota suna wani irin dariya kamar wasu matasan zamani.</p><p> Ta labulen window falon mu muke hangen su,,,, wani irin tsaki hjy Laila taja ,,,,, har saida na waigo ta,,,</p><p> Tace kaiyya Allah waddain naka ya lalace.</p><p> Fita nayi waje naje naje, nakarbo ma hajiya hand bag dinta,,</p><p><br /></p><p> A,a,a Lailas ke ce yau a gidan lale marhabi da ke,, tana kwabe bakaken kayan jikinta ,,</p><p> Saida tacire nasaman tazauna da atamfa yar Nigeria ajikinta,,</p><p> Itama ruwan sha da lemo nakawo mata ,,,</p><p> Tace a,a barshi kawai fadima akoshe nake sosai,</p><p> Saida hjy Laila ta kare shan lemon ta tukun sanan suka fara gaisawa na yaushe rabo kusan wata uku ke nan.</p><p> Nidai nafita waje don nakarasa aikin dake gabana,,, amma ina iya jiyo maganar su ta waje.</p><p><br /></p><p> Yanzu mai sharwali duk nasihar da nai maki na ki rabuda Ali takari ,, baki dauka ba ashe,,</p><p> Wlh ina jimaki abinda zaije yadawo nan gaba,,</p><p> Ali takari ba mutumin kirki bane ,, hakana ya yaudari wata aminiyar kawata,,,</p><p> Haba haba hakadai kike gani,, amma ai bazan yarda har hakan ya faru ba kawai dai wani dan business ne ya hadamu,,,,</p><p> Tunda hjy laila ta fuskanci hajiyan mu bata son maganar sai tace Allah ya sauwaka.</p><p> </p><p> Daman nazone infada maki ansamu wurin aiki da yaranan zasu fara, aiki,ba wani dogo bane kafin lokaci yayi.</p><p> </p><p> Akwai aikin girki akawi na gogegoge, akwai naba filawa ruwa, </p><p> Kinga saiki san yadda zaki rabasu don kece ke zama da su,,,,, kinsan inda yadace kowa taje,,,</p><p> Godiya hajiyan mu tayi mata sosai ,,, kuma ta nuna jindadinta da taimakon da hjy laila tai mata,, </p><p> Tace zata dawo bayan kwana biyu ta kai kowa gidan aikinta,,,,</p><p> </p><p> Ranar litani tun tara na safe hjy laila tazo,,,</p><p> Rugaiyya zata dinga girki a gidan wasu larabawa ne, </p><p> Yumma zata dinga gogegogen wani gidan masu kudi sai sukaina da zata, dinga kula da yara wata mata, mari zata aiki awani restaurant ne,,, nice ban samu wuri ba tukun ,,,,,,</p><p> Ankai kuwa gidan aikin shi yafara aiki sosai don ba wasa acikin harkan bautane kawai tsantsarta ake yi,,,,</p><p> Wai bidan kudi a wahalce za ,a wuni wahal ce za, a kwana,,, ba hutu ko kadan,,,</p><p><br /></p><p> Sai bayan kusan sati uku aka,samo,min gidan aiki wani gida ne ,, zan dinga zuwa ina ba flowers ruwa sau biyu a yini sai kuma in watsa ma tsuntsayen da ake kiwo abinci time to time,,,,</p><p> Gaskiya naji dadin wanan aikin so sai duk da ba wani aikine mai yawa ba amman akwai albashi mai yawa sosai,,,,</p><p><br /></p><p> Tunda safe zanzo Sai in ba Flowers ruwa zuwa takwas in an gyara ma tsuntsaye wuri in yini ina watsa masu abinci suna ci,,, da yamma kuma in kara ba Flowers ruwa </p><p> Sai in tafi gida sai kuma gobe,,,,,</p><p> </p><p> Ba,ni,kadai ce mai aiki agidan ba akwai maza biyu sai wata yar dattijiwar mata,,, </p><p> Ana, bamu abincin ci sosai kuma yinshi akeyi kamar irin namu na gida, Nigeria,</p><p> Don haka nake dan tsayawa in ci abinci na sosai ,,,, Don duk dadewan da nayi a saudiya ban saba da abincin su ba,,,</p><p> Warin tafarnuwa da sauran kayan hadin su yakan damay ni sometimes, saboda hakan nafi son inci shin kafa kaza kawai.</p><p><br /></p><p> Tunda na fara aiki a wanan gidan ban taba zagayawa ko ina ba daidai inda aka ajeni aiki dai gurin nake zama inyi aiyukana ,,, har da marance sai in tafi,,,,</p><p> Tsuntsaye ne masu tsada ake kiwo agidan, wani gefe har da dawakai da rukuma suma ana kiwon su agidan,,,</p><p> Aikin mu kawai mukeyi babu ruwan wani da wani balle ko wani magana ya hada mu.</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Abinda na dan lura da shi, shine masu gidan basu nan don dai mutoci ne kawai a parke , wurin haraban aje su,,,</p><p> Amma fa , kulun gidan kwal yake yana kyali kamar akwai mutum,a cikin shi ,. </p><p> </p><p> Duk sakon da nake bugawa zuwa wurin aiki na, yau akwai babbanci sosai,</p><p> Abinda na,lura dashi yau da nazo aiki na naga flowers anbasu ruwa suna ta diga dis, dis,,,,, Sai na,wuce wurin tsuntsaye don in basu abincin su, wanda gayanan birjit buhu, buhu,,, </p><p> Can sai natarar da tsuntsaye suna hira alamar a koshe suke,, kunsan tsuntsu da tsaba, nawatsa masu naga kamar, zasuci ,</p><p> Sai suka taba kadan sukabar gurin,,,,,</p><p><br /></p><p> Jikina sai yai,sanyi nan,danan nadauka ai an,kore ni aiki kawai saboda , gazawana,,,</p><p> Sai,naganin agaban hajiyan mu tana ta duka na, </p><p> </p><p> Hani,niyar dawakai da aka fito da su yadawo dani cikin hankalina, </p><p> Duk dawakan afito dasu waje sunata harbin iska,,,,,,, Daga inda nake tsaye ina iya hango,gun,gun wasu larabawa sun kewaye dawakan anata yaba su,,,,</p><p> </p><p> Mai kula da, su yana hidimar su yaje yadawo,,,,, gashi ba ruwan kowa da wani cikin mu,, kowa aikin gaban shi yakeyi,,,,</p><p><br /></p><p> Sai dibara ya fado min inje gurin dattijiwan nan mai abinci in tambaye ta ko may ke faruwa ,agidan,,,,</p><p> Kitchen na nufa wurinta, tana tsaye ta motsa abinci nai mata sallama ,,,,,</p><p> Cikin tsoro tawaigo ni tace cikin sauri may kike so may yakawo ki nan ,,, tajero min tambayar lokaci guda,,,,,</p><p> Ta, hada hannayenta biyu wuri guda tace dan Allah inkoma bakin aikina kada inja muna matsala nida ita,,, banzo wurinta ba da masu gidan basu nan sai yau danaga suna nan, har da dan turani takeyi don inbar mata guri,,,,</p><p><br /></p><p> Gwiwa ba karfi na,bar gurin nakoma sashen da nake aiki, na,,,, </p><p> Bayan mun gama cin abinci, sai kawai akabamu odar mutafi gida aikin yau yakare,,,</p><p> A , hanya inda zan jira mota naga anata wucewa da dawakai da rakuma,,, acikin motoci,,,</p><p> Wasu kuma akasa ake tafiya dasu,,,</p><p><br /></p><p> A motar da natare nake jin wai yau za,ayi wasan dawakai da rakuma har da giwaye,,,,</p><p> Ko wani fani da nasu sashe daman al,adan larabawa ne aduk shekara ana wanan wasan tseren dabbobin sosai,,,,</p><p> </p><p> Maimakon in,tafi gida na wuce wurin bara </p><p> Inna gefe ina bara sai naga wata balarabiya tanama wani mutumi tsamay,,,, </p><p> Allah yakai idona , nagani, A hankali naje kusa da ita nai mata maganar inbata bari ba wlh yanzu za,a sare mata hannu agurin nan,,,,,</p><p> Taso ta dan turza saina nuna mata wanda taiwa tsamay a,aljihu yanzu ,,,</p><p> kuya ya,kamata agurin tai min godiyar rashin tona ta da banyi ba,,,,</p><p> Hakalina yanaga kallon yan wasu kauye da sukayo ado dawakai inata masu guda,,,</p><p> Saina kamar cikin kunena anafadin mubar bara ne kuma mun koma sata,,,</p><p> Ban waiga ba amma kamshin turaren shi yasa nagane kowaye,,,, cikin rashin wai,gawa in dibe shi nace la,la,la bani fatan inkai ga hakan,,,</p><p> Itama warning nake mata ai.</p><p> Koda na waiga yabar gurin kamar walkiya,,,,</p><p><br /></p><p> </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 08:07] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 2⃣8⃣</p><p> BY</p><p>🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p>Nasan cewa rabona ba wanda zai same shi, saboda Allahu subbahanahu wata,ala nikadai ya,ba rabona dai dai abin da zai bani, shiyasa hakalina ko yaushe a kwance yake, saidai ina tunanen nima may zanyi in nuna godiya na ga Allah,,,,,,,,</p><p><br /></p><p>Anty mariya SB da sister hafsat yusuf, sister Aishert da miss illayas tare da duk wata wacce take kaunar novel dina duk ina maku fatan alheri arayuwan ku,,,,,</p><p><br /></p><p>Almost true life story,,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Nadawo gida ina murnan nadawo da yan canji kudin da nasamo wurin baran da nayi,,,</p><p> Hajiyan mu ce na iske tare da wasu mutane ana rike ta tana wani hauka kamar sabuwar mahaukaciya,,,,</p><p> Hakalina sai ya tashi sosai, duk da ban fahinci halin da take ciki ba,, amma naji tana fadin Ali takari ni zaka cuta har cikin gidana,,,,,</p><p> Azuciyana nace taufa yau may kuma ya hada hajiya da Ali takari,,,</p><p> Hankalina yai mugun tashi sosai wlh saboda yadda hajiya ke kuka kamar karamar yarinya.</p><p> Dabara ya fado min azuciya ta ,,,,, saboda nikadai ce a gida sauran yan uwana duk suna gurin aikin su,,,nima sa,a akaci nadawo yau da wuri,,,,</p><p> Wayan hajiya Laila nakira, nakuma ci sa,a tana cikin garin makka ranan sun shigo yin wani hidimar gaban su,, don abin ba hutu,,,</p><p> Agurguje nai,mata bayanin hajiyan mu ba lafiya kuma bansan ko may yafaru da ita ba,,,</p><p> Na boye mata abinda naji ,saboda maganar ranan nan danaji sunayi kan Ali takari ,,don kada taki zuwa,,,</p><p> Kusan awa daya da rabi sai gata lokacin ma yan uwana sun fara dawo wa daga gurin aikin su,,,</p><p> Hmmm wai kusan wahalal da mukeyi kulun ,aboye muke gudun kada akama mu,,,</p><p>Wahalce mutun zaitafi haka kuma zaidawo,,,</p><p><br /></p><p> Hjy Laila na iso wana naji hajiya ta kara rusa sabon kuka wiwiwi ,,, tana fadin Ali yace ni shida Zinaru ,,, sunci amanata wlh,,, </p><p> Duk abinda natara ya,wa,washe wai zamuyi business daga nan zuwa Dubai da Nigeria,,, ashe cuta,ta zaiyi ,,, gashi yanzu ya gudu min da komai </p><p> Hatta albashin yaran nan dakika karbo yana gurin shi dasu ya wuce, don rashin tausayi komai bai barmu da shi ba,,,,</p><p> Ihu muka shiga kurmawa muma saboda yaudaran yai yawa sosai.</p><p> Zinaro taci nata yanzu kuma Ali dan takari yaci nashi,,,,</p><p><br /></p><p> TAKARI TAKARI inji hajiya Laila ai inbaka iya duniya ba baka zuwa nan yin takari, saboda duk wanda kikaga yabar kasan shi na haihuwa yazo nan bidan kudi ,,, to takowace hanya zai iya bidan su dan kar ya koma gida ba komai,,,,</p><p><br /></p><p> Daga karshe dai tasamu taciwo kan hajiya tadan lafa kukanta tace kuma zatayi karashi ga shugaban nin su,,, idan yana ganin ya ci bulus ne to karya yakeyi wanan karon saidai in yabar kasan saudiya,,,,,</p><p><br /></p><p> Tundaga wanan lokacin muka samu kan mu cikin wani mawuyacin hali,,,</p><p> Bamu da komai na anfani Ali ya wawashe mu kaf ,yayi tafiyar shi abin shi,,, </p><p> Idan mutum yaje gurin aiki dan abincin da yaci sai mu rago ma hajiya mukawo mata,itama taci</p><p> Gashi yanzu ba lokacin azumi bane ko aikin hajji balle mu samu aikin yi,,,</p><p><br /></p><p> Da, taimakon hjy Laila mutumiyar kirki muka dan samu dan abincin ci muka aje agida muna maneji dashi.</p><p> </p><p> Tun wanan lokacin hajiyan mu ta dan fara ciwo kadan kadan gashi bata da kudin zuwa asibiti a auna ta,,,,,</p><p> San,nu sannu ciwo nata mata karfi ajikinta,,</p><p> Sai gashi harta kai wasu daga cikin mu yanzu basajin tsoron hajiya sam,,, sai abinda sukaga dama sukeyi kawai,,,</p><p> Tunda naga ciwon yana batun kada hajiya takaik kwance sosai ,,,,, batare da sanin antyna Rugaiyya ba na debi kudin mu da muke tarawa nakai hajiya asibiti,,, Aka auna ta akace tana dauke da cutar hawan jini,,,,</p><p><br /></p><p> Nasayo mata magani da dan abincin da yadace muka dawo gida yinin ranar banje gurin aikina ba, inata hidima da hajiyan mu,,,,,, </p><p> Duk wanan abin da nake mata sai ido take bina dashi saboda bata da bakin magana amma ina ganin hawaye masu zafi na yawan fitowa a idonta,</p><p><br /></p><p> Washe gari koda naje gurin aikina sai na iske ashe masu gidan suna gari tun jiya wai,,, </p><p> Ance idan nazo inzo in,karbi sauran kudin ranakun danayi aiki in wuce,,,,,, </p><p> Wani falo ne akace min in shiga ina jefa kafana wani sanyi da kamshi kamar kamfanin gidan turaren Al,Rahaf nashiga ,,,</p><p> Sanyin A,C da kuma TV bango suna ta aikin su,,,, acikin falon ,,, duk yadda zanyi lbrn falon ban iya fadin ,,abinda ke cikin shi duka,,,</p><p> Zaune may shi yake ya ba kofar baya ,amma kan shi na duke yana latsar laptop din dake gaban shi,,,, dagani hankalinshi na kan abinda yake browsing,,, </p><p> Duk karan da tv keyi ana ta wasan tseren rakumma sai ihu ke tashi,,,,</p><p> Nima da na shigo hankalina yana ga TV ina kallon wani dan yalalon balarabe yana kokarin wuce sauran samar rakumin shi,,,</p><p> Aiko bansan lokacin da nakama tafen hannu naba ina fadin yisauri yisauri,,, </p><p> Cikin sauri ya waigo tareda mike wa tsaye lokaci guda ido waje yana nuna ni,,, </p><p> Niko a lokacin ina kokarin kara tafa hannu na saboda murnan star dina zai ci,,,</p><p> Hannu da ban tafa ba kenan ,, Saboda gani Ahamad tsaye agabana wanda ayanzu duk inda naganshi zan iya she,dashi,,,,</p><p> Nakama ja baya a,hankali a,hankali har kusa kai karshen kofan cikin tsawa yace min may yakawo gidan shi,,,</p><p> Gidan shi na nuna gidan da yatsa nace la,la,la ainan gidan aikina ne ni,,,</p><p> Al,mustapha Al,mustapha ,,,, cikin sauri may shi yashigo falon mai kama da fadar wata masarauta,,,, </p><p> Ni Ahamad yanuna ma mai sunan Al,mustapha,,</p><p> Yanatanbayar shi may kawo ni gidan shi har aka bani pass na shigo mai falo,,,</p><p> Yace mai ai nice wacce ke kula da tsuntsayen gida da banzo aikiba jiya </p><p> Yakara nuna ni yace ita wanan din </p><p> Hannu ya nuna min alamar inbar falon,,,</p><p> gudu gudu na fita cikin falon sim,sim dani.</p><p><br /></p><p> Ina zaune in jiran aban kudi na in wuce sai naga Ahamad yafito cikin shiga ta matasan larabawan zamani ,,,, Sai, kam,shi ke tashi,,,ya zo ya wuce tagaba,na batare da ko ya kalli da nake ba</p><p> Wurin harabar aje motocin gidan ya nufi wata mai kama da kifi kusan ko yaushe nazo gidan nakan ta kallon motocin ,,,,saboda suna burgeni,</p><p> Kamar walkiya ya harba motar shi yabar haraban gidan ,, nabi shi da ido kawai ,,,,,ina fadi a,cikin zuciyata dama nice awanan motar</p><p> Naji ace min intashi incigaba da aikina anfasa sallamata,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 08:20] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 2⃣9⃣</p><p> BY</p><p> </p><p> </p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> </p><p> Duk wanda baiji tsoron Allah ba to tabbas zai ji tsoron abinda Allah ya halitta,,,,,</p><p> Allah bamu ikon bauta mashi da tsarkaken zuciya,,,,,, </p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ina godiya gadukkan masoyana na Allah barmu tare cikin mutunci da kaunar junan mu,,,</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Nishi takeyi guda guda daga kwance ,,, yayin da kowar mu ke sauri fita zuwa wurin aikin shi,,,</p><p> Har na shirya zan fita sai na tuna cewa hajiya bata karya ba tun jiya ina ganin bataci komai ba,,,</p><p> Dole na kwabe rolling dina nacire bakaken kayan da na sa,a,saman na zauna dagani sai wani dan wando jeans sky colour da riga fara,mai dan hannu iya gwiwar hannu.</p><p> Wanka na fara yi mata sai kuma na gyara gurin kwanciyar ta dafa mata abinci mara nauyi ,,,</p><p><br /></p><p> Nidake fita da shidda na safe sai gani yau har kusan goma na safe ,,, koda na iso na samu an min duk aikina ,,,</p><p> Al,mustapha yace may yasa yanzu nake makara ne,,, nafada mai ummi na ce bata da lfy ,,, ina dan kula da ita ne kafin inzo amma zan gyara,,,,</p><p> Tunda naga cewa zan samu matsala a wurin aikina sai nake tashi tun karfe hudu na asuba in yi duk wani abinda ya dace ,,, saboda gudun makara,</p><p> Tun lokacin ban kara ganin Ahamad ba ,,, koda yake ma ko tazo ba sani zamuyi ba tunda ina can gurin abokan hirana tsuntsaye yini nakeyi ina masu watsin abinci,,,</p><p> </p><p><br /></p><p> Yau ko da nadawo gida na samu Rugaiyya ta dawo take fada min cewa gidan da take aiki sundawo daga tafiyar da sukayi,,,,</p><p> Nan muka hadu tare da ita muka gyara hajiyan mu ,, nadan fito da ita kofar gidan mu don ta dan kara warware wa,,,</p><p> Da alamar taji dadin hakan don yau harda yar hira munyi da ita,, awajen </p><p> Matsala guda ce take min complain kafarta takeji yana mata nauyi sosai,,,</p><p> Tundaga rana nake dan yawatawa da ita acikin uguwar mu duk da yake saman dutse muke,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kofar kitchen din su yake kallo daga bakin kofar shiga falon su,,, duk wani motsi da takeyi idon shi na a,kanta wanan abin ya fara isan ta gaskiya ibadon wanan aikin yazama kamar na dole ba da tabar masu gidan su,,,</p><p> Duk lokacin da maigidan yake a gida matsalar da take fuskanta kenan ,,</p><p> Idan sun hada ido wani lokaci har lasan lebon shi yakeyi kamar maye,,,</p><p> Azuciyar ta tace ka boye matar ka ko kuda baya ganin ta amma ni ka hanani shakat da wanan mugun kallon </p><p> </p><p><br /></p><p> Cikin dare suna kwance da matar shi tace mashi maigida nasan duk halin da kake ciki da yar aikin mu ,,, babu matsala zan kawo maka ita har nan gidan tadawo da ,kai na,,,, ni nasan kufi sha,awan wa,"yan nan matan fiye da mu matan ku,,,</p><p> </p><p> Tundaga wanan ranan matar ta fara rarashin anty na Rugaiyya tana wani haba haba da ita,</p><p> Abinci lafiyaye ake bata tana ci sai kuma sutura masu dan kyau da aka sayo mata,</p><p><br /></p><p> Tundaga ranan da aka sai mata wa,yan nakayan sawar masu kyau antyna tafara shiga damuwa saboda tana yawan tsorata da mugun kallon da maigidan ke mata yana shafar gemay shi yana lunshe ido,,,,,</p><p> Tundaga ranan tadawo gida cikin damuwa,,, tana shigowa ta jefo min ledar kayan da aka sai mata ajiki tana kokarin cire yar bakar rigar da muke sawa sama,,, Don wanan kowa yasan al,adan larabawa ne, bayan sungama kwaliyan ciki dole akwai bakar riga da hijjab ko gyale da zaka rufe fuskan ka dashi takalmi kuma mun fi sa flat cover,,,, </p><p> To muma TAKARI ,, haka mu tamu shigar saidai lokacin umurah da aikin hajji wasu sukan dan yi dressing din kasar su,,,,</p><p> Ledar nabida kallo ina fadin may ke cikin wanan ledar yar uwa, nakai dibana zuwa gareta don jin ansa,, yo kibude mana ki gani,, kayane masu kyau dogayen riguna da yan kayan unders aciki rigunan kala hudune,,,</p><p> Daga ina daga uwar daki na matar hamza Abdallah,, </p><p> Nakalla nakara juya kayan nace gaskiya suna da kyau, halan sun samu wani alheri ne haka,, ta waigo tadan debeni dadai lokacin tana cire kayan kan,ta,,, azuciyar ta, tace ansa may zan baki maryam da sauranki nasan bazaki fahince ni ba,,,</p><p> Kawai sai ta wuce dakin hajiya don ta gaida ita,,,,</p><p> Tanunawa hajiya kayan ,takuma bata dan abin sa ma bakin da tazo mata dashi,,,</p><p>Dakin nashigo na zauna gefen gadon hajiya nace mata,,,,,</p><p> Gaskiya hajiya yakamata ki fara fita hakana koda Haram ne ki dan dinga zuwa kina dawafi , zaifi maki wanan zaman , agida kulun .</p><p> Zama wuri guda zai ta kara maki bakin cikine arayuwar don babu ranar da wanan damur zata barki in bakibar tuna wa ba,,,,</p><p> Rugaiyya tace ai na fada mata ba yau ba saboda naga tadan ji saukin jikin nata ai</p><p> Saida hajiya ta gyara zaman ta kadan tace insha Allah zan gwada zuwa ,,, kuma nagode maku sosai da kulawar da kuke bani ,,,, ayadda na dinga cuta maku amma sam baku gujeni,,, sai ma kara shigata jiki da ku,keyi,,,,</p><p> Amma sai gashi Sukaina da mari sun fi karfina don suna ganin banda komai yanzu,,,,</p><p> Takare maganar ta ta tana share kwalla,</p><p> Dama tunda bata da lafiya nadawo dakinta da kwana saboda dare,,,</p><p> </p><p> Ankara min yawan aikin gidan yanzu saboda mai kula da goge,goge baida lafiya kwana biyu baya zuwa,, ,,,,,, Bance komai ba </p><p> Tunda safe nake zuwa inyi aikina kafin wani lokaci sai wanan tangamay,may falon yakoma sai kyali yake yi kawai,,,</p><p> Gyaran mace da na miji ba daya ba,,,,don komai na falon sai nai mai tas ,,,,</p><p> Koda Ahamad yazo daga Riyadh inda yafi zama saida yayi mamaki yadda yaga canji a,falon mustapha yai mai bayanin cewa wanan yariyar mai ba flowers ruwa ke gyarawa saboda mai kula da gurin baida lafiya ,,,,,</p><p> Shiru yayi acikin zuciyar shi yana nazarin rayuwa irin na fadima,,, da kwazo , yarinya karama amma ace duk abinda za,a samu kudi akansa zata iya,,,</p><p> Gaskiya yana son jin labarin wanan yarinyar dakuma sunar ta da inda tafito,,,,,,</p><p> Sabod tsoro lamarin ta yake bashi,, ace duk inda yaje sai yagan ta,,,,,</p><p> Almustapha yadawo dashi daga wanan tunanen yana fadin amma kayi hakkuri nima nasan bazata iya ba don dai kada abar gurin hakane yasa nace ta dinga taimakawa,,, amma daga yau,,,,, Hannu yadaga mai alamar yadakata,,, hakana, yace wurin yayi kyau fiye da da kuma ko da mutun uku akace sunyi wanan aikin zanji mamaki balle wanan yar ficikan yarinyar,,,</p><p> Ina gurin Flowers ina basu ruwa yafito cikin wani bakin jallabiya, mai laushi, yana shaning, Sai kamshin turare shi Al, madinal ,noor </p><p> Jin kamshim kawai nayi nasan cewa shine yafito,,, ,,,,Waya yake yi azahiri amma ni yake kallo cikin zuciyar shi yana fadin wanan yarinyar bata gajiya ne da aiki,,,,,,,, Saida yagama wayan shi atsaye,,,</p><p> Al,mustapha yakira yanuna mashini ,yace aiki nawa nakeyi gidan </p><p> nan, yafada mai duka,,,</p><p> Saida yadan nisa yace ,, haba Al,mustapha, aikin ai yai ma mutum yawa ,, katausaya mata mana,,,</p><p> Yadan sosa kanshi, yace za,a gyara insha Allah,,,,</p><p>Duk abinda suke fadi inajin su,,, </p><p> Amma ban waiga na kalli inda suke ba don ma kada in gaishe shi,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 08:21] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 3⃣0⃣</p><p> B Y</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Duk Abinda bawa yatarar akabarin sa na alkhairi ko na sherri to, Tabbas shi ya aikata abinshi, domin Allah subahanahu wata,ala ba,azzalumi bane baya zalunci acikin mulkinsa,</p><p> Ubangiji mu sarki Allah mu na rokon ka kabamu ikon aikata alheri arayuwar mu👏👏👏👏</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ina jinjina maku yan TEEMA Luv group novel, Yan HUGUMA group, gaskiya banda bakin gode maku saidai in maku fatan alheri arayuwar ku ako yaushe, Duk masu kaunar TAKARI novel ina maku fatan alheri Allah yai muna Rahama acikin rahamar sa,,,,👏👏👏</p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yana tafiya a saman titin 57 up zuwa kwanar , massfala junction, Yafito,ne da,niyar zuwa, wasu,shagunar su na, saida kayan sawa,, na maza, saboda,lokacin da ake odar sabin kaya kafin mahajjata su zo ya kusa, za,diba kayan da suka dan dade sai ayi gwanjon su akawo wasu sabi lates,,,,,</p><p> Wayar dake mane cikin aljihun shi tayi yar tsuwa ,</p><p> Duk da sautin ki,ra,ar ,wasu yan yaran rabawa dake tashi cikin sauti mai dadi a,motar tashi bai hana shi jin wanan tsuwar ta wayan shi ba,,,</p><p> Rage gudun da yakeyi da motar shi yayi don diba mai kiran nashi ,, idan ba mai muhinmanci bane ya aje har ya sauka,,,</p><p> Ganin sunan da ke a screen din wayan yayi barobaro ABBANA. Jikina rawa yadan samu gefen titi ya perker motar shi gefe guda, fuskanshi manne da yar guntuwar murmushi wanda sai kila bayan wata yake irinta,,</p><p> Saida yabari kiran ya tsinke tukun don haka al,adasa take indai kirace daga Nigeria bai,dauka saidai shi yakira ka saboda yawan cajin kudin da akeyi ma mai shi,</p><p> Cinkin sallama yafara magana sai mahaifin nashi ya ansa mai asanyaye shi don duk kusan halin mahaifin nashi ya dauka,,,</p><p> Haba babana wai fushine kakeyi damu ko kuwa dai rashin kulawa da mune yasa yanzu ko yar wayan ma da kake bugowa don muji lafiyar ka, ka daina sam,,,</p><p> Murmushi yayi mai tsada har uban na jinshi tacikin wayar,,,,Cikin muryan tashi mai kama da baya son magana sai dole,,, la,la,la, Abbana, haram,,haram ,,,,,</p><p> A,kawai dan business din danakeyi a Dubai ne yanzu wanda yadan dauke min hankali da komai,, kwanan bana cikin lokacina ko kadan wlh,,, amma ina mai roko da ayafe min dan Allah ,,, naso in,zo but time ne banda sosai yanzu insha Allah nan badadewa ba zan shigo Nigeria ,,,,</p><p> Uban yace a,a kayi zaman ka mu ai zamu zo don mu gan ka, dama na bugone infada ma cewa zamu zo umurah nida maman ku don adiba muna lafiyanta,</p><p> Yadan yi murmushi yana susan kanshi kamar agaban uban yake yace, amma kilama zan riga ku zuwa, </p><p> Shima uban dariya yakarayi,, yakauda zancen yana fada mai cewa harda tsohuwa yake son su zo don taga dan lelenta, saboda tana damun su da zancen shi,,,</p><p> Yace ashe inada babban bakuwa kenan dole in samu lokacin in ma wanan zuwan shiri na musan man,,,</p><p> Sundan yi hirar lokaci da kuma yan uwa,,,,, sosai </p><p> Sukayi sallama uban yana ta farin ciki da jin dadin dan nashi ,,,Saboda hankalinshi, uwa,uba ga ilimin addini ,kusan duk abinda zakuyi dashi cikin ladabi da kuma tarbiya irin na larabawan asali zai ma,,,,</p><p> Lunshe ido uban yayi yana tuna su salis da ya kai turai karatu ,koshida yazauna turai har ya haifesu can baijin turancin tsiyar da suke mai inyana waya dasu,,,</p><p> Garashi ladabi ko waye suna kokarin bashi hannu su gaisaa ba kunya sam ga al,amarinsu,,, </p><p> Sabanin Ahamada da duk zaman ku bakajin yai turanci saidai laranci, cikin tsanaki,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Shiko Ahamad karasawa yayi shagon nasu, yadan didiba abinda yakamata ayi wa shagon nashi,,,</p><p> Yadawo gida cike da tunanen zuwan mahaifan nashi,, </p><p> Bazuwan kowa yafi mai dadiba kamar na yar tsohowar nan babarbara mai yawan fitina,,,</p><p> Annurin fuskan shi ta dan sauya lokacin da yatuna cewa bada mahaifiyar shi ba cikin masu zuwa gurin shi,,,</p><p> Rashin mahafiyar shi tare dasu yana yawan kona mai zuciyar shi in,yatuna.. Duk wanan daular da suke samu agidan su bada ita ake ci ba,,,,,, Duk da yana kokarin tura mata da abin anfanin rayuwa yadda yakamata saboda tun yana yaro ,yana jin tsohuwa na yawan yi mai addu,an Allah yasa yasamu ya kula da mahaifiyar shi da yan uwan su,,,,,,,</p><p> Saidai abinda ke dan yi mai sanyi ya lura dacewa inda take aure yanzu tana cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya,, kuma mijin nata yana nuna mai karanci sosai kamar shi ya haifeshi ,,,</p><p> malam na yawan lurar dashi addini tun yana karami inyaje hutu kauyen,,,</p><p> Shiyasa har gobe yana ganin mutuncin shi don yarike mai uwa amana.</p><p> Da wanan tunanen shiga falon shi ,,, ya wurga da key din motar shi a bisa kujer da ke gefen shi,,,,</p><p> Kujera mafi kusa dashi ya zauna gami da dafe kanshi, da hannun shi guda,,,</p><p> Hjy mama hjya mama , hmm,,,, </p><p> Ya lunshe idanun shi yabi lafiyan kure da yake zaune ya jiginu da yan shi yana murmushi mai nuna bakin ciki a fuskan mutun.</p><p> Shi duk labarin da aka fada mai nazaman maman shi da ita bai kona mashi zuciya kamar yadda tadinga gwada mai rashin kauna kirikiri ba boyo ko kadan, </p><p> Idan har wasu na iya boye mugun halisu ita sam bata iya boye nata,, akan shi,,,,</p><p> Duk abin da baban shi zai mai na alheri saida in bata sani ba za,ayi shi inko tasani yaza ma tarihi,,,</p><p> Koda kuwa za,ayiwa yan uwanshi ne idan anzo gare shi sai salo ya canza ,,,,,</p><p> Falon yabida kallo nadan wani lokaci yanisa saboda yasan cewa tunda yatare wanan gidan nashi mama bata shigo saudiya ba,,</p><p> Tun yana zama a Riyadh ne kawai ta sangidan shi amma sai da ta nuna hassadanta cewa, ina yasamu wanan kudin haka.</p><p> Waiko dai uban shine ke turo mashi da kudi aboye,,,</p><p> Inba haka ba ya zaifi yan uwanshi samu wuri haka,</p><p> Cikin fushi tabar kasan , </p><p> Ashe lokacin da taje turai ziyaran yaranta ta dauka sunfi Ahamad jin dadi ne da samu wuri,.</p><p> Donshi baya magana kuma baya nuna cewa shidin wani abu ne can</p><p> Har aikin da yakeyi baban baifada mata ba saida tazo tagani da idon ta,,,</p><p> Amma duk da hakan bata gamsu da cewa komai na Ahamad din ne ba </p><p> Gani takeyi ai na company da yake aiki ne aka bashi ya zauna,,,,,</p><p> </p><p> </p><p> 🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 13:32] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 3⃣1⃣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> GiBA wata,kalmace mai saukin fada saida kuma mai nauyi ce wurin fasarar ta Allah ya haramta, zina, sata, shangiya, da kakausar harshe ,,,,saikuma gashi duk GIBA tafisu karfin haramtawa, ,</p><p> Allah zai iya yafe ma bawa tsakanin shida bawan amma banda tsakani bawa da bawa,</p><p> Yan uwa munisan ci Giba atsakanin mu </p><p> Yi,da junan mu shiyafi komai faruwa yanzu,,,,GIBA watau Gulma,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Gaisuwa da fatan alheri dukkan masoya TAKARI NOVEL ,,,,,,, Antys din huguma ga jinjinan ku nan na girma akoda yaushe,,, </p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Girki ta hada masu lifiyaye irin ta kasar su ,, ta shirya masu akan dining table ,,,,</p><p> Akawai dakin da aka tanadar masu don hutu agidan ,can takoma don ta dan huta bayanta kintsa jikinta tsab da sungama takwashe kayan tawanke sai kuma gobe indan Allah yakaimu basu kara cin wani abinci mai nauyi kuma,,,,,</p><p> Yau ma hakan ne ,, kiranta akayi a intercoms din gidan don kowani daki mai aiki akwai shi, agidan.</p><p> Cikin sauri tagyara rolling din kanta ta isa falon ,,Zau,ne suke saman kujerun dake kewaye da dining table din,,,</p><p> Cikin gimamawa ta gaisu tana dan dukawa na ban girma ga shugaban ka,,,</p><p> Idon shi kur akanta ko kifta su baiyi ,,shi akulun wanan yarinyar kara sha,awa ta yakeji a ran sa, ,,,,,,</p><p> Sai wani lunshe ido yakeyi kamar may maye,,</p><p><br /></p><p> Matar tace ma anty na ta kwashe kayan abincin sungama zasu fita amma don Allah tadan jira su har su dawo kafinta wuce ,</p><p> Rugaiyya ta ansa cikin gimamawa, </p><p> </p><p> Har wani lokaci basu dawo gida ba sai zuwa dare lokacin badamar tabi hanya zuwa gida yan bagaladi na hanya,,,</p><p> Cikin damuwa da fargaban iri iri zuciyar ta yake,, don tasan cewa hankalin yan uwanta zai tashi sosai don duk inda mutum ya dole yadawo kafin dare yayi,,,</p><p> Matar ce tai mata bayanin cewa tayi hakkuri ta kwana da safe zata kira Albani din ta taimata bayanin cewa tana tare da su,,, </p><p> Saboda dole ne duk wanda ya kawo ma ka mai, aiki ka dauki lanbar wayan ,Albani din shi ,,,,</p><p> </p><p> Cikin rashin jindadi ta isa dakin da take hutu aciki idan tazo gurin aikin.</p><p> Uwar dakin nata ce tashigo dakin cikin fara,r ta da sakin fuska, Ma,isha bata da jiki sosai gajera ce maidan tsawon fuska,,, takai kimanin shekara talatin da wani abu da haihuwa,,</p><p> </p><p> Cup take rike dashi a, hannu ta wanda ke cike da madarar shanu mai kyau mai kauri ta asali ,ko kallon cup din kayi kasan madarar yadauki sanyi,, so sai,,</p><p> Gefen gadon da Rugaiyya ke sama ta zauna wanda ita kuma Rugaiyyan ke kokarin tashi ta zauna saboda girnamawan, shigowar uwar dakin nata dakinta,,,,,</p><p> Ta mika mata cup din tana fadin tasha madarar don zaimata amfani sosai,,,,, kallon madar Rugaiyya keyi kamar batasan ko maye madara ba da mamaki,</p><p> Mika mata cup din tayi gami darike mata hannu guda tana murmushi, tace madarace mukasha ,shine nakawo maki naki don nasan kina gidan yau kinzama bakuwata,,, takarbi cup din tana godiya.</p><p> Saida ta tabbatar tasha sai tamike tana ce mata tasake jikinta mana ainan ma gidane ko bata saba da su bane har yanzu,,,</p><p> Dan murmushi tayi cikin girmamawa tana fadin ai ba ko mai tunda za,a fadama Albani din ta, cewa tana nan saboda dare yayi mata yau,,,,,,,</p><p> </p><p> Shiko maigidan yana can saman bene, daidai wani dan dake saman harabar gidan nashi yakasa tsaye yakasa zaune, yaje yadawo yana mazurai, da ido yana lunshe su yana shafar gemun shi,,,,</p><p> Ahaka matar tacin masa tsaye yana yawo tsakiyan haraban su yana dunkular hannun shi,,,</p><p> Tabayan shi ,Ma,isha ta rugumo , shi,.</p><p> Yai wani ajiyan zuciya a hankali, </p><p> Yajuyo da Ma,isha ahankali ta gaban shi suna fuskantan junan su,,,</p><p> Itace ta fara magana ,, tace nasan ganin da kaima wanan yariyar a yau ,shiyakara saka cikin wanan yanayin maigida,,,</p><p> Yace wani abu nake tunane kawai ba wanan ba,,</p><p> Jan hannu shi tayi suka koma ta cikin bedroom dinsu,,</p><p> Tace mai magida na riga na gama shirya komai ko ,,,yadan yi murmushi ya rungumota,</p><p>Tace nan,da dan anjima kadan kana iya zuwa gareta ,,, kalassss,,,</p><p> Ta juya tana shirin kwanciya ,,, </p><p> </p><p> Amma cikin zuciyar ta tana fadin ita tasan cewa baza ta iya gamsar da maigidan nataba in badon haka ba bazata yarda da wanan akidar tashi ba,,,.</p><p> Saidai kasssh duk yadda tayi yafi gane ma bakaken mata don acewar shi sunfi dadi da juriya dasu,</p><p> Yakuma sheda mata kuma itama din tasani kusan gidajen da kaga yariya bakar fata tana aiki to aiki biyu ne da ta lalurar maigida sai kuma ta zahir,,,, amma bakowa keda wanan akidar ba sai wanda zuciyar shi takekeshe,,, </p><p><br /></p><p> Saida yadauki dan lokaci yana gyara jikin shi,,,,yagama duk wani shiryeshirye shi na kwanciya,,, azuciyar shi yana kiyasta yadda zai kasance da Rugaiyya yau,,, yana fatar tafi waccan da tatafi dadin harka saboda ko banza Rugaiyya tafi, wacan kurciya,, </p><p> Saida kuma yakan tuna irin dadi damore rayuwa dayayi da,zakkiya yar, kasar, niger,,,, yaji dadin zamanta dasu sosai, ita,din ma,tasamu alheri awajen shi dakuma matar shi,,, idan ko Rugaiyya haka take zai kasan ce mai farin ciki </p><p>Don haka dole yasan irin yada zai kyautata mata da kuma irin kyautar da zai mata,,, dan yajar ra,ayinta,,,</p><p> </p><p> Rugaiyya tagama shirinta tsab ta kwanta,,</p><p> tare da addu,oin neman tsari daga Allah kamar yadda ta saba,,</p><p> Saidai duk, jikinta bata jin karfin shi ,sam tunda tasha madaran da ma,isha ta bata jitakeyi kamar duk gabobin jikinta basu aiki,,,,,,</p><p> Tana kwanci Barci mai karfi,ya dauketa, daga kwancinta,,,</p><p> </p><p> Tafe yake a hankali yake tafiya, cikin dogon baradan dake gidan inda dakunonin yan aikin gidan yake a jere ,,, kusan duk basu yan aikin basu ciki, kasancewar dare ne mafi yawan su sun tafi gida basu kwana agidan ,,,</p><p> Kofar dakin yatura a hankali yai ,sa,a kofar a bude take,batare da yasha wani wahala ba,,,,, </p><p> Tsayawa yayi yana kare,mata, kallon irin halittan da Allah yai mata gaskiya ba laifi yasan zai more rayuwar sa anan,</p><p> Cikin barcin da takeyi mai nauyi take jin ana shafarta,, a,hankali ta gyara kwanciyar ta don ta dauka ko duk dadin barcine a gidan masu kudi,, </p><p> Shiko gogan yaji dadin hakan don yadauka ko shi ta gyara mawa yan kayar fulanin ta sunyi ciciko sunyi tsaye,,</p><p> Nandanan yashiga su ya,,,,,,,,,</p><p> Shafarta yakeyi gami da tsotson wasu sasan jikinta,,,</p><p> Ahankali ta bude idon ta dake tap da barci mai nauyi,,,</p><p> Duk da barcin da ke idon ta bai hanata zabura ba da kokarin mike wa, zaune, cikin tsoro,,,,,,</p><p> Shiko gogan sai ce mata yakeyi cool dawn cool dawn , ,,,,,,</p><p> Data ga zaicigaba saita kama ture shi tana fadi ,,,.la,la la, zina haramu,,,</p><p> Kiss yakara kokarin kai mata,,,,</p><p> Aiko tasa hannun ta da karfi da ja gemen shi iya karfin ta saida yayi wata yar kara, na wahala ido waje, ,,,,,</p><p> Allah yabata sa,a ta jawo Cup din da aka bata tasha madara shi,,,,ta buga mai a fuska jin zafin da yayi yakai mata mari yakai mata wawan mari, cikin fushi</p><p>,,,,,,yasa hannun shi guda ya rike mata wuya, gudan hannun, yana shafar fuskan shi inda yaji kamar sanyi ashe jini ne,</p><p> Ta kara kai mai cizo a wuyar hannun shi guda,baisan sanda zafi ya sa yasake ,ta ba,</p><p> Dakarfi ta ture shi gefe tasamu ta sauko sama gadon ,tasa hannu taja rigarta da ta cire gefe </p><p>,, Sa,arta guda yamanta da yashigo hankalinshi yadauke da ganinta da yayi kwance bai rufe kofa ba,,,</p><p><br /></p><p> Da guda tafita hanyar zuwa get din gidan duk suna a rufe ,, </p><p> Dabara yafado mata tashige parking area na gidan tashige karkashin wata mota landrover,,, talafe tana maida nunfashi ahankali kamar za,aganta takeji ita,,,</p><p> </p><p> Yadafe fuskanshi da hannu guda don jinin dake zuba mashi dakin matar shi yanufa don yasan ba inda zatabi tafita gidan da daren nan ,,,,,</p><p> Matarshi naganin shi tataso da saurinta tana tamabayar shi ko may yafaru haka,,, jayeta yayi gefe yana fadin kinsan cewa wanan yarinyar ba irin wacan da kika samo min bace kika,kaini ta jimin ciwo</p><p> Sai nasa andaure min ita sai an fitar da ita kasan nan,,,</p><p> Hakana yaita fadar shi ita kuma tana gyara mai gurin da jinin ke zuba ga zafin cizon da akai mai,,,</p><p>gurin yai ja jarir,,,</p><p><br /></p><p> Shike ta fada yana ce ma masu gadi su diba ko ina , nagidan akamo mai ita,</p><p> Duk sun diba har gurin motocin da data,ke kwance tana jin su sai addu,a takeyi abakin ta,,,,</p><p> </p><p>Kiran sallah akeyi ko ina taji lokacin da yake fadin kada a bude kofar gidan har sai sun dawo sallah asuba,,</p><p> Ita kuma lokacin tana daidai bayan dakin maigadi,,,</p><p> Allah yabata sa,a maigadin yashiga daki dauko abu,,, aiko ta lalaba tafice dagudun tabar gidan ,,,,</p><p> Gudu taitayi tana waigen bayanta ko ana binta abaya, ,har Allah yasa tasamu mota masu zuwa dawo sallah asuba tabiyo,,</p><p> </p><p> Yadda naga dare haka naga rana don ina cikin mugun damuwar rashin dawowar yar uwata kuma masoyiyata maikaunata da alheri,,,,</p><p> Don dai ni nasan cewa ba gudu tayi ba akwaidai wani dalili mai karfi sosai,,,</p><p> Gari yafara yin dan haske mutane sun fara zirgazirga nafito wajen gidan mu natsaya batare da kowa yasani ba,,,</p><p> Sai ko ga Rugaiyya nagani cikin tashin hankali da firgita janta nayi gefe nace ta nuna babu komai har kowa yafita don ba wanda yasan batadawo gida ba,,,</p><p> </p><p>Hankalina atashe nabata ruwa tai wanka muka shirya kamar kullun, mukafita gidan ,,, </p><p> Saida mukai nisa da uguwar mu sanan muka rike, junan mu mukaita kuka, </p><p> Saida mukayi mai isar mu ba mai bamu hakkuri sai Allah,</p><p> Nice nadanyi karfin hali na fara magana cikin sheshekar kuka, ahankali nake tambayar ta may yafaru da ita,,,,,,,,</p><p> Kara rugumay ni tayi takara rusa sabon kuka dakyat na samu tadan tsagaita kukanta,,</p><p> Sannu ahankali ta warware min komai tun farkon yadda al,amarin yafaru da ita , dakuma yadda tasamu ta tsira</p><p> Mun aje cewa koda hajiya tace ta koma gidan aiki bazata koma ba wanga karon,,,,</p><p> Haka muka dunguma dani da ita muka tafi gidan aikina a,ranan</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 13:37] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 3⃣2⃣</p><p> BY</p><p>🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎 </p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Almost true life story,,,,,</p><p><br /></p><p> Imani acikin zuciya take ba,a zahiri ba , Allah yana amfani da aiyukan mune, na zuciya,bana zahiri ba Allah yakara muna imani 👏👏👏👏👏 , Ameen,,,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tunda safe muke barin gida zuwa gurin aiki na ,ba mu dawowa sai da dare ,,, </p><p> Don muna gudun kada azo a,kama Rugaiyya ,,, kamar yadda mugun yai ikirari, cewa zai sa afitar da ita acikin kasar da karfin tsiya,,,</p><p> Koda mukadawo Yumma ke tambayar mu ina Rugaiyya ta,tafi yan gidan aikinta sunzo har sau biyu bidan ta,,,,</p><p> Cemata,nayi ta kyale su don ta,canza wani guri aiki ko,,,</p><p> </p><p> Tun lokacin bamu kara jin komai ba tun muna dari dari ha muka gaji muka sake jikin mu,,,</p><p> Saidai hajiya bata san cewa bata zuwa aiki ba,, abin da muke gudu shine kada lokacin kawo kudi yayi bamu kawo mata ba,,,</p><p> Duk zuwan da mukeyi da Rugaiyya masu gidan basu sani ba dayake gefen mu daban ne,,</p><p> Shiyasa har muka dan dauki lokaci, agidan ba wanda yasani,,</p><p><br /></p><p> Shirin zuwar yan Nigeria umurah akeyi, su hjy mama,</p><p> Sai gyaran gidan ake tayi sosai tundaga fentin gidan har furnitures ancanza sabo sai kuma kayan electronic sabbi nayayi lates,</p><p> Gidan yakara wani haske fayau kamar ancan wani fasalin gina ne,,,</p><p> </p><p>Al,Mustapha yake fada ma wanan yar dattijiwan mai aiki suna son karin yan aiki mutum biyu ,,,,,, mata biyu mata maza kuma uku,</p><p> Daidai lokacin na shigo kitchen din don dawo da kayan abincin na,,,</p><p> Saida nabari yafita nadawo gurin matar nai mata ,,,</p><p> hannu na bibiyu nake rokon ta don Allah ta taimaka ta daukar min Rugaiyya daga cikin ma,aikatar,,,</p><p> Shiru tayi tana nazarin maganata, </p><p> Can tace inzo mata da ita gobe tagani ko zata iya,,,</p><p> Nace mata aitana nan gidan tare muke zuwa,,,,nan nabata labarin abinda yafaru da Rugaiyyan agidan aikinta</p><p> Gaskiya matar ta tausaya muna sosai tai muna alkawarin zata gwada aikin ta tagani ko ta iya,,,</p><p><br /></p><p> Washegari kuwa ta,fara gwada aikin Rugaiyya ,tagani ko zata ,iya,,,</p><p> Abinci muka hada mata maidadi kusan kala uku tare da abin sha,,, mafi saukin hadawa,,,</p><p> </p><p> Kofar, Get din gidan aka wagalle, motoci ne guda uku suka shigo gidan maigidan ne wanda yai tafiya zuwa kasar Dubai tare da baki ,,,,</p><p> Yaje wani aikine na gagawa a kamfanin wani mai kudi a,Dubai .</p><p> Inda yai masu gyaran wata na,urar,</p><p> Tatan mai da kusan mutun uku ana,daukowa don su gyara hakan baiyi ba,,,</p><p> Shima shiganshi tabiyu ke nan ,ana biyun Allah yabashi sa,ar gyarasu,,</p><p> Wanan gyaran ta sa yasamu alheri sosai ,,, </p><p> Don har gurin Abu Abdullah , aka kaishi don su gana,,</p><p> Abu Abdullah wani matashin dan kasuwa ne akasar Dubai, mai tsananin arziki da dukiya akasar ta Dubai,,Arzkinshi bana haye bane na gadane,,,,, ,</p><p> Duk,wanda yagan shi,, dole maishi yasamu alheri sosai arayuwa,,,, Don mutun ne wanda shi kanshi bai san yawar arzikin shi ba,</p><p> Shiyasa duk mutumin da ya yimai abin farin ciki arayuwa shi,har yaji dadi,</p><p> shikuma zai jika maishi da daula daida gwargwado,,,,</p><p> Saiga Ahamad yaci sa,ar wanan daular shima,,,, </p><p> Don dama Abu, Abdallah,yayi bakin cikin rashin aikin na,urar da Ahamad ya gyara mai, kasancewar kafin a,yarda mashi ya mallakesu saida yasha wuya sosai don an nuna mai hassada so sai, tun mahaifin shi nada rai suke wanan project din,,,,,,</p><p> Yana murnan sunshigo hannu sai kuma gashi,sun,ki aiki yadda yakamata,,,, ,,,,,,,</p><p> Angwada engineers har biyu kafin,Ahmad,abin sunki aiki ,,,,,</p><p> Wani abokin karatun Ahmad da a,ka,kira dan paris tare sukayi karatu da yaje karo ilimi, a,kasar paris,,,</p><p>Abokin shiya, ce akira Ahamad dake saudiya agani,,, yasan dawuya in bai iya gyara su,, ,,,,,</p><p> Cikin ikon Allah sai gashi ko ya tayar dasu duka,,, ukun yanzu ba su da wata matsala,,,</p><p> Jindadin hakan yasa,</p><p> Aka shirya yar karamar walima don farin cikin wanan nasarar da akasamu,,,,</p><p> Wurin walimar ya hadu da abokai kala kala, harda baban manajan companonin, Abu Abdullah, agurin.</p><p> Bayan waliman shima yagaiyace shi zuwa gidan shi shan green tea,,,,,,</p><p> Nan ne suka kulla,business dashi,,,</p><p> Yakumayi ma Ahmad alkawrin za su shi cikin harkan kasuwancin su sosai,,,</p><p> To shine yadawo gida yau tare da abokan shi yan Nigeria da suke can saudiya tare,,, </p><p> Su sukaje airport su ka taroshi saboda murnan alherin da yasamo,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kusan su biyar ne suka shiga tangamaymay falon nashi cikin raha da farin ciki kowa na fadin albarkacin bakin shi,,,,</p><p> Al Mustapha ne keta dawainiya dasu,,, </p><p> Daya daga cikin su yace aishi yunwa yake don tun safe baiyi break fast ba ma,,</p><p> Abinci yace akawo masu suci,,, </p><p> Cikin sauri Almustapha ya shiga gurin yar dadtijiwar matar mai abinci yana fada mata baki na bukatar abinci,,,</p><p> Gabanta ne ya fadi don dai yau ba itace ta girka abincin ba mune akaiwa gwaji aiki yau,</p><p> Bataboye mai ba tafada mai aiko yabita, da fada, har yana ikirarin cewa har ita sai ya kora aikin nan,,idan har ansamu matsala,,,,,</p><p> </p><p> Abinci suke ci suna hirar su, na duniya,,, daya daga cikin sune ya tsiyaya hadin sobo da mukayi na ainihi,,, yasha,,,</p><p> Dago kai yayi yana tambayar Ahmad inna yasamo mai ,mai aiki kamar agida Nigeria ,, aishi rabon da yaci abinci irin tamu ta Nigeria har ya manta wlh,,,,</p><p> Shima gudan dake gefe yace kai wlh ka rigani magana ne umar,,,</p><p> Wanan abincin yasa na tuna da gida sosai yau,,</p><p> Almustapha dake gefe yana jiran ayi mai complain yai wani irin ajiyar zuciya gami da hamdala, saboda sam baison abinda zai bata wa maigidan nashi rai,,,</p><p> Don Ahmad mutum ne mai yawan hakkuri duk abinda kaji yai magana to abin akwai matsala akai,, don haka yake taka tsantsan dashi,,,</p><p><br /></p><p> Muko muna can matan nan tasamu gaba tana tamuna fada wai naja mata hasarar gurin aiki mafi daraja da ta,taba samu arayuwar ta,,, fada take yi kamar zata doke mu,,, mun dukar da kai kasa Rugaiyya tana ta bata hakkuri,,</p><p><br /></p><p> Cikin girmamawa da kula ya bakowaninsu kyautar da saida suka girgiza da shi ganin ,,,,, kudin daya basu mai yawa haka ko bakin godiya basu samu ba,,,</p><p> Yace umar mayye amfanin mutum yasamu bai kyautatawa natare dashi ba,,, </p><p> Nasamu amfani sosai a, wanan tafiyar kaga kuma da muke tare aidole in taimake ku,,,</p><p> Baysn sun wuce Ahmad yakira Almustapha ,,,</p><p> Duke yake yana serching wani sabon engine a,cikin computer shi,,, kanshi na duke ,,,,,</p><p> Yace Almustapha wayai muna abinci yau agidan nan ,,,,, shiru mustapha yayi kashi na duke akasa,, dama yasan dole atuhu mayshi da wanan laifin maigirma, dan ba kowani abinci oga ke ci ba ,.ko ita wanan matar saida yagwada ta kafin adauketa,,</p><p> Idon shi yadago yakai diban shi ga almustapha,,, bakaji bane yakara tambayar shi,,,</p><p> Cikin in,iniya yace mai dama dama ,,yau wanan matar bata da lafiya ne shine ,,, shine nasa wanan yariyar mai ba Flowers ruwa, ta yimuna,,,,</p><p> What ya,mike tsaye,, gami da ture computer shi gefe guda,, </p><p> Yace kana nufin wanan yar yarinyar tai wanan abincin yace mai na,am,itace maigida,,,,,,,,</p><p> Kai yakama girgizawa yaje yadawo,atsakiyar falon,</p><p> Azuciyar shi yana tunanen anya fadima mutunce, kuwa,,, yarinya kamar wata Aljanna gaskiya lamarinta akwai bincike don dai she is to young da wa, yanan abin da takeyi gaskiya,,,</p><p>Don dai ko agida Nigeria,kamar wanan yarinyar bata isa tayi wanan girkin haka,ba,,,</p><p> Yajuyo inda mustapha yake tsaye yace tana ina,,,,,</p><p> Sim sim na shigo falon hade da sallamata sai faduwar da gabana ya,keyi, don dama jira kawai nakeyi akirani ,asallameni,,daga aikin gidan,,,,, ko dayake nasan cewa mun yi aiki yadda yakamata don ni banga abin laifi aciki ba,,,</p><p> Amma sai naga almustapha da wanan matar duk sun tsorata, nima shiyasa hankalina ya daga </p><p>Don ina gudun inyi sanadin barin aikinta,,,,</p><p> Gyafe guda,nadan rakube a falon,kamar zan shige a,kasa, don ladabi,,,</p><p> Saudaya yadan daga ido ya kalleni yakauda kai,, azuciyan shi ya jita kamar wata ta kirki wani lokaci kuma ta iya shedan ci,,,,</p><p> Cikin kakausar murya yace min,, Keda wa kuka hada abincin gidan nan ,,, nikan nace masa Rugaiyya ce,</p><p> Da sauri ya kalli inda almustpha yake tsaye kamar mai rokon gafara,,,,,,, </p><p> Dukan su shida almustapha,,sukace Rugaiyya nace eh,,,,,</p><p> Nai masu bayanita kamar yadda naiwa matar nan,,,</p><p> Ita ma,Rugaiyyar,kiranta akayi har matan nan mai abinci,,,,,,, saida yadan yi nazarin mu sanan yafara magana cikin muryan shi mai taush,,,,,</p><p> Yai muna godiyan aikin da mukayi masa na,yau tunda, har bakin shi sun yaba, da aikin mu,,,,,,</p><p> Sai kuma yabar zancen yafara wani</p><p> Ida yace muna mahaifan shi zasuzo daga Nigeria yana son don Allah mu basu kulawa ta musan man dakuma girmamawa, duk wani bukatar su da dawainiyar su mu taimaka masa dashi don shi ba mai zama bane,,,,,,,</p><p> Yakawo kyauta da yawa ba duk, wanda ke gidan, </p><p> Kyautar ta girgiza duk wani saboda kusan albashin mutum kashi biyu ,,,,,</p><p> yaba kowa agidan yace alherin da yasamo gurin tafiyar dayine, shi ne muma yabamu,mulasa musa mai albarka arayuwar,,shi,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 13:43] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈. </p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 3⃣3⃣ </p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Duniya saida kudi Lahira kuma saida hali na alheri,, Allah yasa mu dace,,,</p><p> </p><p> Gaisuwa da Jinjina ga Yan Huguma group tare da sauran masoyana na takari novel,,,</p><p> </p><p> Almost true life story,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Jirgin air max ta sauke bakin Nigeria tun karfe hudun asubahi,,</p><p> Sannu a hankali mutocin da suka ,, kwaso su daga airport suke tafiya dawo,wa gida,</p><p> Daga gurin taron bakin Nigeria, motoci ukune jere na farko driver ke janye da wasu maza su biyu,,, Saita biyun Ahmad ke jan motar,babanshi ne da hjy mama sai tsohuwa,aciki,,,,motar ta uku kuma Wasu yan matane su biyu sai driver, da,ke jan su,,,,,</p><p> Mu,na, gidan dama tunda safe duk wanin abinda yakamata muyi don taron bakin, munyi,,, saboda tunda muka zo bamu zauna ba , Don saboda aiki da yai muna yawa, </p><p> ,,,Aikin yau, ba kadan bane don yawa gare shi sosai,</p><p> abincine da abinsha kala kala muka hada,irin ta taron baki na musan man,,,,,</p><p> </p><p> Cike da doki nake son sai naga wa,"yan nan bakin da kowa ke ta rawar kafa saboda da zuwan su har mai gidan, namu,da muke ma aiki, </p><p> Wanda ko kallo mutum bai ishe shi ba da wuya kaji yana magana dawani agidan inyazo dan dama dama Almustapha ko kuma bawani dogon magana bane,,,,,,,</p><p> Duk girman gidan nan saida, hayaniyar isowar bakin,mu duk ya ruda gidan da murna da kuma dararakun su, irin na yaushe rabo,,,,,</p><p> Suna shigowa muka dinga kaimasu gaisuwa ,,, suna ansa muna da larabci don ina ganin basu ga almar mun iya hausa ba saboda yanayin shigar,mu,,,,</p><p> Wata yar tsohuwa daga cikin su tafi dauke min hankali saboda yadda naga kowa na haba,haba da ita ,,,,</p><p> Almustapha yasa aka kwashe masu kayan su zuwa cikin dakunar gidan</p><p><br /></p><p> Abinci muka gabatar masu dashi suna gamawa,sai wurin kwana,muka kai kowan su yaga inda zai sauka,, agidan mu mata mu muka taimaka wa su matan zuwa masaukin su,,,,,,,</p><p> Duk wanan dawainiyar da mukeyi, da baki maigidan yana zaune a gaban wani desktop din shi dake falon kamar bashi keda bakin ba,,, yana kallon movement din kowa har mu yan aiki ,, amma azahiri zakadauka aiki yakeyi daga zaunen,,,,</p><p> Ba abinda da yafi bani sha,awa kamar yar tsohuwar da aka so da ita ,, wace zata iya kai shekara kusan,,, tamanin da hayi ,aduniyar kila, </p><p> Duk abinda takeyi hankalina yana gurin ta duk wani motsin da zatayi sha,awa yake bani wlh,,, gata da fada irin na tsofi,,,, </p><p> Zuwa nayi nakira Rugaiyya don tazo, ita,ma taga yar tsohuwar mai ko,kari, kamila mai yawan ibada,, ,,,,,</p><p> Muka dan labe gefen labule muna lekenta </p><p> Zaune take a dakin da akai mata masauki agidan da ,alama tasbihi takeyi a zaunen don bakinta nata motsi ga tasbaha a hannu ta,,,,</p><p> muna nan labe bayan dan labulen da muke leken ta,,,Dan hira mukeyi,,,. muna dariya a hankali komai nata yana burgeni </p><p> Nace dama ace wanan tsohuwar kakatace,,,wlh Rugaiyya da naji dadi so sai naso ace nima ina da yan uwa haka har da kaka,,,, da kullun ina tare da abina ina bata kulawa,,,</p><p><br /></p><p> </p><p> Koda ban waiga ba,naji kamshin turaren shi ya bure muna hancin mun hakan ya nuna muna cewa maigidan ya gurin,da muke labe,,,,,,</p><p> Da sauri na sake labulen da na dan hankade muna leke.</p><p> Nayo baya daniyar gudu sai kawai na,ji na yi karo da kafa, shi,,,</p><p> Ahankali, nadago kaina nakai dibana gare shi,,, fuskan shi a daure murtun,,, </p><p> Muka dan zagaya ta bayan shu muka wuce sim sim da mu,,,</p><p> A,she duk abin da muke fadi yana tsaye bayan mu hannayen shi cikin aljuhun wandon shi,,, ido ya zubu muna, har muka bace mai,,,,,,</p><p><br /></p><p> Bayan su yabi da kallon mamaki ,, azuciyar shi yace may wa,"yan nan yaran ke nufi ,,,,</p><p> Suna nufin basu da kowa ko may ,, lalai sai na samu time inji labarin su,,, yadan leka don yaga may muke kallo wurin tsohuwa,, yaga ai zaune take tana ibada,,,</p><p> Murmushi yayi yace mai ran karfe ke nan hajiya tsohuwa ,,,,</p><p> Ba ita ba ba mai iyawa da hjy mama,,</p><p> Don yasan ko wanan zuwan da akayi da ita don shine tazo,,</p><p> Tunda Abba bai fada mai da ita za,azo bada fari,,,,</p><p><br /></p><p> Saboda aiki yau mun makara sosai bamuje gida da wuri ba,,,</p><p> Almustapha yasa driver ya kai mu gida , don dare yayi. Ana iya kama mu,,,</p><p> </p><p> A , hankali muka shiga gidan namu gami da sallama, </p><p> Mun iske kowa na harkan gaban shi , takalmana tomy na cire na wurgat gefen da muke aje takalmi, </p><p> Sai niliyata danake warware a hankali, don indan ji iska ajikina , dagani sai yar wando da riga da suka dan matse min jiki kamar wata diyar larabawa kaina dana kule da ribon shima na dan walwale shi don in samu saida agida,,,,</p><p> Nakai kallona ga sukaina ina tambayar ta hajiya fa,,</p><p> Tace min ita ma bata ganta ba tunda tadawo, ido waje nake kallon Sukaina Don ai wanan rashin imani ne,,,,, aiko banza hajiyace silar zuwan mu nan,,,</p><p> Inga mutunci aidole mu mutun ta,ta,,,,,</p><p><br /></p><p> Daki na fada da sauri na,,,</p><p> Kwance na samu,hajiya jiki ba kwari </p><p> Cikin tashin hankali nake tambayar ta ko tasha maganin ta,,, ban tsaya jin ansar taba nafita waje da sauri na,,,</p><p> Tea na hada mata mai kauri sai ruwan dumi da na jona mata tai,wanka nabata maganin ta, sha,,,,,</p><p><br /></p><p> Tunda safe kuma na tashi na kara hada mata abin kari , nabata maganin ta,sha,,</p><p> Nacewa Rugaiyya ta tafi,ni bazanje ba ,yau,,,,,</p><p> Hajiya ce tace min in tafi ai taji sauki yau sosai,,,</p><p> Hakana natafi badon raina yaso ba, don gaskiya naso in kula da hajiyan mu sosai,,,saboda tausayi take bani don ni har a raina kamar inna nake daukar ta,,,</p><p> </p><p> Muna isa tun da safen nan muka hada masu abin karyawa ,,,kamar irin na mutanen Nigeria mu,,,</p><p> Bayan komai ya kam,mala mun jera masu a, dining table ,,,</p><p> Daya daga cikin yan matan nan tafito tace muna, wai baza ta iya cin abincin mu ba, wai akwai warin tafarnuwa aciki da yawa,,,</p><p> Duk da nasan cewa bamu sa tafarnuwa ba acikin girkin mu,,,</p><p> Saboda wanan dattijuwar matar da muke aiki tafada muna yan Nigeria basu son tafarnuwa don haka kada muyi masu girki da shi,,,</p><p> Jiki ba kwari muka kwashi kayan da niyar mukara zuwa mu dafa wani,,,</p><p><br /></p><p> Muryan maigidan mukaji abayan mu ya na fada, muna cikin larabci mu ,maida komai inda yake mu wuce kuma kada mu dafa abinci rana dasu,,, </p><p> Zasu tafi haram masijid yin dawafi daga can zai su wuce asibiti da hjy mama,,,</p><p> Yana ma matar da muke aiki tare bayani,,,</p><p><br /></p><p> Ya juya wurin yarinyar da yakira da mairo, idan abincin baiyi maki ba kina iya shiga kitchen ki dafa abinda kike so,,,</p><p> Aikin dafa abinci sau biyu kawai nai alkawari dasu , ba,kowani lokaci suka ga dama suke aikin ,ba</p><p> Amma in,kinga zaki iya biyan su hakin aikin da zasuyi maki sai su je suyi maki, wani irin wanda kike ra,ayi ko yafada cikin nuna serious,,,,,alamar ba wasa ga zancen shi,,, </p><p> Tsohuwan nan ce abaya shi,ta karbe zancen da cewa ai basu san darajan mutum ba su ,</p><p> Sun dauka kowa za,su iya takawa don su na da kudin hakan ,,,</p><p> Saboda irin rashin tarbiyan da ba,a , nuna masuba, agidan su,,,</p><p> Kasan cewa agida yan aikin su kamar bayin su suke,,,</p><p> Sabanin nan da komai a,ka,ida akeyin shi,,,,</p><p><br /></p><p> Daidai lokacin na iso bakin taburin cin abincin ina kokarin taimaka ma tsohuwar don ta zauna,,,</p><p> Plate nadauko mata ,sai kuma tambayar ta da nakeyi cikin hausa may za,a zuba mata,,,</p><p> Kallon gefen da Ahmad yake tayi, tace mai,, kai nifa banjin larabcin da wanan yariyar ke min,,,</p><p> Tsohuwa ai hausa take maki ita madin, inji Ahmad,,,</p><p> Cewa tayi may zakici azuba maki,,,,</p><p> Murmushi nadan yi kadan har fararen hakorana suka dan baiyana waje,,,bayan na zuba mata sai na bar dinning area din don in,cigaba da aikina dama don in,danji dumin tsohuwar naje kusa da ita,,, kalon mamaki yabini da shi ,,,,</p><p> Ina wucewa naji tana fadin ita wanan min ma yar aiki ce hakan ,,,</p><p> Bai bata ansa ba sai mairo ce tace ai tunda kika ganta tana aiki nan kema kin san yar aiki ce</p><p> Wata kila anan aka haifeta , ma,,</p><p><br /></p><p> Dakin yar tsohuwar nan nashiga na gyara mata komai tsab kamar ba,a bata ba,,,</p><p> Na kun na kayan kamshi ko ina gidan yadauki kamshi na musan man,,,</p><p> Sai sanyin AC da ya karade ko ina na gidan,,,</p><p><br /></p><p> Ahmad ne yafito daki cikin shirin shi nafita, jallabiya yasa fara tas ma laushi da sulbi kan shi da yar karamar hula fara sol itama, sajen shi ya kwanta lub a fuskan shi kamar shiyayi kansa,,,</p><p><br /></p><p> Hannu shi rike da dan makulli motar shi,,,,</p><p> A tsakiyar falon ya tsaya yana ba Almustapha umurnin kula da komai yadda ya kamata,,,</p><p> Mahaifin shine suka fito tare da hajiya mama,, suma a cikin shirin su ,,,</p><p> Tana wani yatsine yatsinen fuskanta kamar wacce gidan bai mata ba,,,</p><p> Azuciyar ta kuwa sai mamaki takeyi da irin canjin da tagani ga Ahmad ,,, budi da arziki yataso ma yaro kamar shi yafi kowa iya karatu,,,</p><p> Tasan duk yadda Alhaji yai mata rantsuwar cewa baida masaniyar komai gamay da,sana,ar da Ahmad din keyi,,,</p><p> Ba wai ta yarda bane jira take yi kawai da su koma gida dole asan yadda za,ayi gaskiya,</p><p><br /></p><p> Tsohuwa ake jira tafito su tafi tace ita atabau baza taje ko ina ba ,, </p><p> Su tafi kawai don ita tagaji sai gobe zata fita,</p><p> Haka suka tafi batare da ita ba,,,,</p><p> Hakalin maigidan bai kwanta ba da barinta da akayi gida ,,, yasan dai da wata a zuciyar tsohuwa,,,,</p><p> </p><p> Suna wucewa nice tafarko dana fara zuwa wurinta ,,,</p><p> Ina dan tambayar ta a hankali take bani ansa nace mata Nigeria akwai nisa ko tace min eh ,,,</p><p> Kina son zuwa ne da sauri na bata ansa da eh</p><p> Dariya tayi kawai don ita tana dauka ni haihuwar can ne,, bansan Nigeria ba,,,</p><p> Kafarta da naga tana dan shafawa almar ciwo nace mata ina zuwa ,,,, </p><p> Fita nayi zuwa zuwa wurin mama,mai aiki don naga tana yawan,shafa magani ciwon kafa akafar ta dana tanbaye ta sai tace min man zaki ne da na jimina take shafawa akafar,,</p><p> Shina karbo nazo na shafa ma wanan tsohuwar nadinga yi mata masaj din kafar a,hankali ,,,,</p><p> Kafin wani lokaci har barci mai nauyi yadauke ta ,narage mata karfin A,C ,,,naja kofa ,ahankali nafita,</p><p> Saida tai barcin ta sosai ta tashi na hada mata ruwa maizafi tayi wanka tana fitowa nakawo mata abincin ta har daki ,,,,,,, </p><p> Miyar kaza da dankalin turawa sai su kabej da saurasu yanuna sosai dai yadda zata iya ci fresh milk a cup amma ba mai sanyi ba kware,,,</p><p> Taji dadin wanan kulan da nai mata aranan so sai,,,</p><p> Ahmad basu dawo gida ba saida takwas na dare,,,,</p><p> Alokacin kuma hankalina yakoma ga hajiya ina son in koma in diba jikin ta inji inda sauki,,,</p><p> Gashi masu gidan basu dawo ba, kuma ban iya wu,cewa inbar tsohuwa ita kadai </p><p> Don jinta nakeyi kamar mun saba dadewa,,,</p><p> Ita ko sai kallo na takeyi ina bata mamaki ,, azuciyar ta tace wanan yarinyar karama tasan yin komai ,,,</p><p> Ga wa,"yan nan manyan yan matan da mama ta dauko ko ruwan shayi basu iya dafawa ba, injita,,, gashi kuma don samun wuri irin na mama ta nace sai anzo da su umurah ,,</p><p>Duk da tagane wayon zuwan da kayi dasu don Ahmad din,tane sabod,,,,,, , </p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 14:06] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈ </p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 3⃣5⃣</p><p> BY</p><p> </p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p>Recite Hassbunallahu wani,imal wakeel 450 every morning if possible pls,,,,,</p><p><br /></p><p> Soyayyata gare ku bai karewa yan uwa,,, Hannah Rabiu ,Maman xarah ,Ayheert, Precious Hindu, Miss Ayush, Maman Mu,Allim, Maijiddah Harazami, Anty Aynah ,Salamatu sale maina, sai su big antys Anty mariya sb Anty Hafsat Yusuf,Anty Safiyà Abdullahi, da Maman Fareeda,,, all in Huguma groups novels fatan alheri gare ku kullun,,,,</p><p> </p><p>Almost true life story,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Saida nagama da lalurar hajiyan mu tukun sanan na shirya zuwa gidan aiki,na cikin sauri da fargaba,,,,,, </p><p> Cikin sauri nake tafiya don nasan cewa yau kan na,makara </p><p> Almustapha mugu, yana iya korata ko yai min wani sabon wulakanci don naga almar baida imani sam,,,,, kawai dai nasan nikan yau, saidai, gyaran Allah kawai,,,,,</p><p> Ahankali na tura get din don kada aji karar shigowo na,</p><p> Ina bude get din gidan saina ga masu gidan a atsaye ana masu loading kayan su,</p><p> Daidai wurin da ake parking motocin gidan,,,</p><p><br /></p><p> Karan bude get din danayi ,shiya yasa duk wanda ke wurin hankalishi, juyuwo, </p><p>Lokaci guda kusan kowa ya kallo kofan shigowar, don aga ko waye mai shigowar,,,,</p><p> Daga inda nake tsaye A,laman gaisuwa nai masu daga nesa kadan,,,,,</p><p> Sai naga Alhaji lawal zanna,ya kirani da hannu alamar inzo inda suke,,, ,,,</p><p> A,hankali natako Na,isa gurin , cikin ladabi,,,na kara gaishe su,</p><p> Nuna min hjy tsohuwa yayi da hannu , yana min alamar intafi gurin ta,,,,,</p><p> gurinata naje batare da nasan inda zamu ba,,</p><p> Naga, kawai aka bude min kofar mota da alamar inshiga babu wani mussu ko tsoro azuciya na,,,,,,,</p><p> Nashiga,, saida na zauna da kyau na lura ashe, bani kadai ce za,a da ni ba har da </p><p> Rugaiyya na acikin motar da mama mai abinci, kai kusan duk kan gidan sai mutane kadan aka bari ,, ,,,</p><p> </p><p> Tafiya mukayi mai nisa sosai don ni azatona wani unguwa zamu,, sai kawai naga anata tafiya kawai mai nisa,,,,</p><p><br /></p><p>Motar mu bai tsaya ko inna ba, sai birnin madina, akofar, wani gida hadade wanda in nace in tsaya fadin kyaun gidan da fasalin shi zanci lokaci,,,</p><p> Kayan aka,dinga shiga da shi cikin gidan da muka zo,,</p><p> Sai a,wanan lokacin natuna cewa tafiya mukayi fa ke nan kuma gashi ban fada ma hajiyan mu ba, wacce na bari cikin wani hali,,,,,</p><p> Shiru nayi nadan lokaci nashiga damuwa har ban inya boye damuwar dana shiga,,,,,</p><p> Jinayi an,dafani ta bayan kafada na,</p><p> Ta jiyo dani a,hankali muna fuskantar juna,,,</p><p> Rugaiyya ce,, tace nasan cewa kin shiga damuwa ne saboda rashin fada ma hajiyan mu da bamuyi zamu zo tafiya ba ko, </p><p> Na kada mata kai alamar eh,</p><p> Kuma gata bata da lafiya,,, nasake ce mata eh</p><p> Hannuna yana rike da nata take min wanan maganar, </p><p> Zan yi magana tadaga min hannuwan ta ,alamar inyi shiru,,</p><p> Shirun nayi don bin umarnin ta, amma na bita da ido,,,</p><p> Taci gaba da maganar ta, fadima ni maigidan mu ,</p><p> sharif Ahmad yaiwa maganar tafiyan mu jiya,, zuwa nan garin madina inda na nuna mai cewa ai hajiya ta amince sosai da maganar har tana mai godiya,,,, </p><p> Ido waje nake kallon ta don mamaki, </p><p> Wanan karon nai magana nace ,,,</p><p> Amma kinsan hajiya na bukatar mu don bata da lafiya, ko,,</p><p> Tace mukuma zuwan munan yafi muna komai dadi fadima,,,,</p><p> Ki kula fadima da yau,</p><p> Tunda mukazo wanan kasar duk yawon da akeyi damu kin taba ganin ko jin ance muzo birnin madina inda Manzon Rahama yake, muyi ziyara,,</p><p> Na girgiza kai a,hankali alamar aa, </p><p> tace to wanan damace Allah yabamu don muzo mu ziyarci ma,aiki Allah,mai rahama maijinkai,</p><p> Jin hakan danayi munzo garin da Annabi yake sai naji zuciyana tayi min dadi sosai ,na manta da komai dakowa,</p><p> sai ma naga may muke jira bamuje munyi ziyara ba,, tun yanzu,,,,,,,</p><p> A,gidan, inda aka sauke mu</p><p> Dakin mu guda ,da hajiya tsohuwa da mama mai aiki kamar yadda hajiya tsohuwar ta bukata ai mata , ,ta fison a,hadata damu don zata samu abokan hira,</p><p><br /></p><p> Saida mukayi wanka muka ci abinci, da aka shirya, muna kafin mu iso, garin,</p><p> Don mun iske wani mai aiki agidan amma na miji ne,</p><p> mushirya tsab saidai kayan da nazo dasu sune nakara sawa ajikina kasan cewa ban zo da kaya ba,,</p><p> Rugaiyya ta jefo min wani dogon riga baki mai wasu ratsin duwatsu blue a hannun, shi sai dan gyalen da zan yane fuska na,,,</p><p> Dayake mun san yadda ake shirin kafin kace haka mun fito tsab, da,mu,</p><p> zakace ko mune ma diyan masu kudin,</p><p> Ai muna fita falo mairo na ganin mu tace itama sai munyi mata dressing kamar irin ta mu ,,</p><p> Hakan mukayi mata ita da yar uwar ta jamila,</p><p> Tare muka fita zuwa masallacin Annabin Rahama, gaba dayan mu,, gidan,,</p><p> Sai hjy mama dake gefe tana sham kamshin ta</p><p> kamar,yadda takeyi kulun, </p><p>Idan, ka kalli fuskanta babu dadin gani ,, bata dariya ko kadan ,</p><p> Gata bakace wulk da ita dogowa karfafa, ga izza da tsiwa, da isa kamar wata yar masarautar kano,,</p><p> Ashe haushin hjy tsohuwa hjy, mama,keyi,</p><p> Don tace sai anzo da "yan akin gidan makka , madina </p><p>, Don may hjy zata dinga jawo yan aiki a jikin ta suna shiga mutane haka,,kamar yan gida,,,,,</p><p> Ita sam bata yarda da wanan akidar ba ,,,</p><p><br /></p><p> Massalaci muka nufa gaba dayan mu gidan,</p><p> sai dai duk wanan abin banga shariffudeen Ahmad cikin mu ba, Almustapha, ne kawai cikin mu watau ,,,Ahmad, baizo ba,,,</p><p> Acikin masallaci, annabin rahama mukayi sallah la,asar tare da dandazon jama,an, dake cikin masallacin </p><p> Mutum zai dauka cewa ko lokacin aikin hajjine yayi,ne wanan irin cikan da akayi </p><p> Kai ubangiji Allah mun gode ma da kayi mu musulumai har muka samu wanan falalan nazuwa ziyarar manzon rahama,,,,,</p><p> A haka Muma mu,kabi sahun jama,a akayi sallah jam,i, da mu,,,</p><p> Muna idar da sallah a,cikin jam,i muka tashi in group zuwa wurin ziyaran ma,aikin Allah S,A,W,</p><p> Munga jama,a ranan nan kamar duk birnin madina akatara acikin wurin,,,</p><p> Duk wanan cikan da ritsin wurin ina makale da hannun hajiya tsohuwa gam a hannu na,,</p><p> Abinda ya fado min a rai shine hiran hajiya laila da hajiyan mu a makkah,,</p><p> Lokacin da ta dawo wani ziyara datazo madina suna hira ni kuma ina dakin ina jin su,,,</p><p> Wanan hiran nasu yazo min acikin zuciyana kamar yanzu akayi shi,,</p><p> Musalin da tayi nadinga bi saiko gashi cikin sauki mun iso gab da kofar shiga Rauda,,,,</p><p> Da sallama muka shiga ciki ,,,, Wani irin sanyi kamshi da ni,imar da bamu taba jiba arayuwa shi muka ji agurin,,,</p><p> Mukayi sallah nafila raka,a biyu dai saitin green carpet din da ke seti da kabarin annabin mu,, muka kara gode ma Allah da Annabin shi,,,</p><p> Mundan jima muna addu,a ,mun gaida masoya kuma sahabban annabi da suke wurin tare,,,</p><p> A hankali naja hannu hajiya tsohuwa don mubar wurin kafin yan bagaladi suce muna exist,,,, exist exist muka fita ta wani kofa mafi kusa,,,,,,</p><p><br /></p><p> Wanan tafiyan yasa nasamu sausauci sosai gurin hajiya mama,,,</p><p> Don dai tasan cewa mu yan gari ne sosai,,</p><p> A,haka muka dinga ziyarar duk wanu guri da yadace mutafi na tarihi ,,,</p><p> Duk inda zamu ina tare da hjy tsohuwa nazama kamar nice idonta,,</p><p> Mun saba dasu mairo sosai don muna kaisu sayayya kayan English wear masu kyau,,</p><p> Mukan fita tare muyi ta daukan photo tare dasu,,</p><p> Alhaji lawal zannah yabamu kudi tare da su mairo da jamila ,kowa yaje yasai abinda yake so kafin mu koma makkah,,</p><p> Cikin dare Sheriff din mu ya sauka birnin madina daga Riyadh,, ashe yaje wani aikine can company nisu na Riyadh,,</p><p> Yau kuma yabiyo jirgi don akwai likitan da zasu gana dashi da Alhajin su gobe da safe,,,</p><p> Zuwa jibi mu koma makkah,,,,</p><p> </p><p> Wani shago muka shiga mukayi sayayya sosai don su kusan komai a madina suka siya wai ance masu yafi kaya Qualities </p><p> Hjy tsohuwa ma na sai mata kaya sosai a wanan shagon </p><p> Dazamu fita muka sai kayan motsa baki da na shaye shayen gwangwani.</p><p> Adakin mu mukayi bajabaja da kaya zaki kala kala saura nasawa hajiya mu cikin kayan ta nace takai tsaraba gida.</p><p> </p><p> Saida muka gama komai su har sunyi wanka sun kwanta natashi ina gyaran wurin da muka bata da ciye,ciyen da mukayi,, marana naji yadaure min </p><p> Da kyat na iya,daga kafa ta daga inda nake tsaye,,,</p><p> Sainaji yadan lafa min,,</p><p> Nacigaba da aikin da nakeyi,,,</p><p> Ciwon sai gaba gaba nakejin yana min,,,</p><p> Barci yadan daukeni aiko nafarka gigice ina wani irin kugi da nishi mai karfi,,,,</p><p> Cikin barci hjy da Rugaiyya suka farka a razane,,,</p><p> Amai nakama shegawa ga mara na ya daure tam,,,,</p><p> Kawai ban san lokacin da nafara mulmula akasa ba kamar macijiya,</p><p> Ga amai ina yi,,,,</p><p> Rugaiyya tasa ihu saboda rudewa, da firgita don duk iya zaman mu tare ban taba irin wanan ciwon ba,,,</p><p> Abinda zan iya tuna wa shine hjy ke tambayana may yasa mayni,,</p><p> I,hun da sukeyi yasa kowa fitowa acikin firgice,,</p><p> Suna tambayar su make faruwa,</p><p> Mairo ce ke fadin wanan yar karamar yar aikin nan ce zata mutu,,,</p><p> Daidai lokacin sheriff din mu Ahmad yafito dakin shi cikin jallabiya mai ruwan milk mai budaden hannnu kamar banga,,,</p><p> Cikin sauri yafada dakin shida mustapha da kowa yafito dakin shi kusan lokaci guda</p><p> Hjy mama tana zuwa taga halinda nake ciki sai ta fara fada wai ai ga irinta nan anjawo wa mutane magana,</p><p> Inyanzu na mutu a hannusu dole hukuma ta kamasu ta tuhumay su,,</p><p> Zataci gaba Alhaji lawal zannah yadaga mata hannu yace mata is ok pls,</p><p> Kibar mu muji da abinda yafaru, inke bakisan kaddaraba mu munsani ,,</p><p> Idan Allah yace a hannun mu zata mutu ba makawa sai ta mutu agurin mu,,,</p><p> Kingaki yadda da kaddara shine cikar imani,</p><p> Fatan mu Allah yabata lafiya, dole tai shiru badon taso ba,,,</p><p> Sheriff din mu, Yana diban yanayin da nake ciki yazaro wayan shi yakira wani likitan ma,aikatan,su, yai mai bayani,, likitan yace azo dani asibitin kawai, don zaifi,,,,,,,,,</p><p> Almustapha dayaji karshen wayan ya yunkura zai daukeni </p><p> Wani tsawa Sheriff Ahmad yabugamai cikin kaukausar murya,,</p><p> Saida kowa dake falon yakallo shi cikin firgici,,,</p><p> Hannu laulausar rigan dake jikinshi ya gyara wuri guda,,,</p><p> Dauka daya yai min sai gani kamar 4month baby a hannu shi,</p><p> Cikin sauri yake tafiya abayan mota yasani,</p><p> Shike jan motar yanayi yana waigen bayan shi ,don yaga yanayin da nake ciki,,,,</p><p> Sultan Abdullarahaman, specialist hospital ya nufa dani,,,,</p><p>Muna zuwa Wani kati yaciro cikin aljihun shi yamika ma wani balarabe da ke gaban wata computer,,,</p><p> Saida yasa katin yadago ido yakalli Ahmad da,kyau sai kira cikin asibitin akazo da keken daukar mara lafiya aka daukeni zuwa ciki sai wani irin kugi nake yi,,,, </p><p> Likitoci uku ke kaina duk abinda yakamata suyi min suyi,</p><p> Sundauki dan lokaci sanan suka fito,,,,,,,</p><p> Babban likitan yakira Sheriff Ahmad zuwa office din shi don jin bayanin matsalata,</p><p> Rugaiyya tana bayan shi hankali tashe,,</p><p> Bayan yan rubutun da yayi sai yakalli Ahmad yace,</p><p> Bawani matsala bane mai yawa,mungane cewa period ne zata,fara shi yazo mata ahaka,</p><p> Kuma gaskiya irin hakan zai iya, jawo mata matsala nan gaba,,,,,</p><p> Amma yanzu mun bata magani zamu barta nan</p><p> har nan da kwana uku muga yadda maganin zaiyi mata aiki idan munga bai karbeta ba sai mu canza mata wani,maganin</p><p> Tana yawan shan zaki wanda haka shima yabada gudun mawa wurin blocking din hanyar da jini zai fito mata,,,</p><p> 🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 14:12] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 3⃣6⃣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Wadatar zuciya ya tabbata ga mutumin da akulun yake gode ma Allah akan kowacce baiwar da Allah yayi masa komai kankantarta ,kuma baya kai karan ubangiji Allah a, wurin wani halittansa.</p><p> </p><p><br /></p><p>Happy new year 1st muharram 1439AH</p><p>O ALLAH!</p><p> Make it easy for us to utilise the year better than the last for achieving everlasting blessing in JANNAH Allahuma Ameen👏👏👏</p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p>Saida likitocin suka gama yi min komai yadda ya kamata,, suka kaini dakin da za,a kwatar dani kamar yada sukayi bayani,,</p><p> Kwance nake ina barci acikin kwancir hankali, </p><p>Ba kamar dazun da nake ta kugi ba,</p><p> Sheriff din mu, Ahmad ne dakin sai Rugaiyya dake gefe guda tsaye cikin takura da tashin hankali, ,,</p><p> Tana tunanen zuwan da mukayi batare da sanin hajiyan mu ba,,,,,</p><p>Jin muryan sheriff Ahmad, datayi yadawo da ita cikin hankalinta,,</p><p> Batare da ya kalleta ba yace,</p><p> Ina iyayen wanan yarinyar suke,,,</p><p> Jin wanan tanbayan yasa Rugaiyya yin hawaye,</p><p> Gefen navain dinta tasa tana goge hawayen da ke bin, fuskanta ,a hankali,</p><p> Jin shurun da yayi yasa shi dan waigota a hankali don yaga ko tana jin tambayar da yai mata,,,,,</p><p> Ga mamakin shi sai yaga hawaye take gogewa, ma,ana tambayar yai mata ciwo ke nan,,,</p><p> Dakin yai niyar bari, don yana ganin bata da niyar bashi ansa</p><p> Yana batun barin dakin don jin shirun yai yawa,</p><p> Sai yaji muryanta tana cewa iyayen mu suna Nigeria,,</p><p> Nigeria ya kara nanata sunan,,</p><p> Wayazo daku nan,kasan sanan may yakawo ku,,, to,,</p><p> Rugaiyya bata boye,mai komai ba tabashi labarin tunzowan mu gurin hajiya</p><p> Har zowan damu, saudiya ,duk ta, bashi labarin mu, tun farkon har zuwa lokacin da muka fara aiki a gidan shi,,,,,</p><p> Shirun dataji yayi shiyasa ta dan daga kanta kadan ta dube shi,</p><p> Sai taga tunane yakeyi shima din,,,</p><p> Abinda yafado mai arai tunda ta fara bashi labari shine irin son kudin da mutanen yazu keda shi wanda har zaisa asake yarinya kamar wanan har wata kasar </p><p> Wai zuwa neman kudi diya mace ai ba abin yin sakaci bane,atarbiyanta,</p><p> Yatuna lokacin da yazo karatu farko akasar saudiya akayi case da wasu mutanen kasar Cameron,,,</p><p> Inda wani yazo da yara maza matasa yasa aka sare ma wasun su hannu,saboda su dinga bara suna samo mashi kudi,,,</p><p> Wanda yin hakan ba bisa ka,ida ba guda daga cikin yaran yasamu matsala har takai ga ankai shi asibiti.</p><p> Nan akaita bincike har aka gano gaskiyar maganar,,,</p><p> Tun wanan lokacin yatsani duk wani mai irin wanan halin na bauta,,da yara kanani,,,</p><p> Wanda akasari mutanen mu bakaken fata ke wanan dabi ar,</p><p> Sam bai son yaga irin wa,yan nan masu wulakanta kasu da sunan neman kudi,,,</p><p> koda a,hanyane don abin kunyane ace mu mukafi kowa wulakantar da kai akasa mai tsarki,,,</p><p> Zuciyan shi namai kuna yabar asibitin don zuwa gida saboda gari ya soma wayewa sosai,,</p><p> Gashi kuma zai kai Alhajin shi ganin likitan shi dake nan zaune cikin birnin madinan, wanda saboda ganin likitan yazo garin dama dashi da hjy mama,,,,,</p><p><br /></p><p> Saboda samun saukin dana danyi ban farka ba daga barcin,, barcinake yi hankali kwance, sai Rugaiyya dake gefe guda zaune,</p><p> Tunda na kwanta barci ban farka ba har kusan awa bakwai , ina ta barcin saboda irin alluran da akaimin don in huta,</p><p> Sheriff din mu zuwan shi biyu ban farka ba,,,,</p><p> </p><p> Sanu a,hankali, nadan motsa kadan ,,</p><p> a,hankali nakara,motsawa,duk jikina ban jin karfin sa,saboda yai min wani, nauyi,,nakara gyara kwanci na,,,,,</p><p> Saidai idona arufe yake har lokacin,,,,,</p><p> Muryan Rugaiyya naji tana min sannu da jiki tana dan gyara min kwanciyar danayi,,,,,</p><p> </p><p> A, hankali na bude idona , naga Rugaiyya zaune a,saman wani kujeran roba blue, kalar na asibiti,, saina gane cewa a asibiti nake</p><p> Kaina,na,dan gyara a,hankali, don inji dadin kwanci,,</p><p> Hakan yabani damar yiwa dakin danake ciki kwance, kallon tsab,,,,,</p><p> Turo kofan da akayi ne a hankali muka,kai kallon mu ga kofar dakin gaba dayan mu don muga mai shigowa,dakin,,</p><p> Subiyo ne suka shigo dakin sheriff din mu Ahmad, da almustapha,,,</p><p><br /></p><p> Hannu mustapha yana rike da kayan abinci, yazo gab da gadon da nake kwance ya aje kayan abincin saman wani dan drower dake gefen gadon majinyata,,, </p><p> Ina ganin almustapha sai na kauda kaina gefe guda batare da na kalli gefen, inda yake tsaye ba,, </p><p> Saboda ban manta da zafin marin da yai min ba a makkah, daga taimako sai mari,,,,</p><p> shikuma sheriffudeen din mu,ya riko ledoji farare masu tambarin asibiti, guda uku a hannun shi,,,,,</p><p> Magani ne acikin guda,</p><p> Guda kuma kadan pad ne har laida hudu,,cikin ledar gudan,,,</p><p> Sai su underwears quality masu kyau, </p><p> Ajewa yayi gefen inda Rugayyai take,yana mata bayanin batare da ya kalli gefen da nake ba,,,,,</p><p> Almustapha yabar dakin don ya lura ina fushi, dashi har yanzu gudun kada Sheriff din, mu yaji cewa ya mare ni shine yafita,,,,,</p><p> Batare da ya kalle inda nake ba yacewa wa Rugaiyya ta ,tadani zaune takaini bayi ta,gyara min jikina takuma koya min yadda a,keyi idan ana period,,,, </p><p> Saboda ya fahinci ban san komai ba gamay da al,adan dana fara yi,,,,,,</p><p> Saita bani abinci inci indan nagama nurse zata zo tabani magani,na insha,,,,</p><p> Bai tsaya ba shima yafita dakin ,,,,, yana fita sai Rugaiyya ta kira suna na muna fuskantan July na,,,</p><p> Nan dai, Rugaiyya ta koya min yadda zan gyara jikina dakuma abinda duk yakamata inyi in mace,na period,,,,</p><p> Sai a lokacin na fahinci halin da nake ciki </p><p> Wani irin kunya da nauyi yakamani sosai saboda zuciya ta ta raya min kowa agidan yasan abinda nake ciki kenan,,</p><p> Nazauna bakin gadon da nake naci gaba da tunane watau ashe irin abinda su sukaina da mari kai har ma da antyna Rugaiyya sukeyi kenan nake cewa suna sakaci da ibadan su,,,</p><p> Yau nima gashi yazo gareni </p><p> Kunya ne yakamani so sai don duk gidan kowa yana min kallon nasan wani abu ke nan,,,</p><p> Ban san lokacin da wani hawaye masu zafi suka sulalo a fuska na ba,,</p><p> Natuna da inna na da yan uwa na,,, a wanan lokacin ,</p><p> Azuciyana nace idan Allah yayi komawa wata gida inna taga ina wanan abin nasan tabas zata zargeni dayin wani mugun abinda ba daidai ba,,,,</p><p> Wanda ninasan cewa ina iya kokarina wajen kula da mutuncina da inna tace min inkula dashi lokacin da zanbar gida,,,,, </p><p> Acikin tunanen naje bayi nayi duk yadda tace min inyi nagama nadawo,,,</p><p> Muryan Rugaiyya naji tana cewa kici abinci fadima za,abaki maganin ki kisha,,</p><p> Dataga kuka nakeyi shine tashiga rarashina tana fada min cewa ai bakomai bane duk macen da takai lokacin yi batayi ba to tabbas wanan mace bata da lafiya ne,,,</p><p> Hakadai taita kwantar min da hankali har nadan sake jikina na dan ci abinci,,,,</p><p> Tundaga wanan lokacin banyarda mu hada ido da sheriff din mu Ahmad sam don wani irin nauyin shi da kunya nake ji,,saboda yasan lalurar da nake ciki,,,,</p><p> Abinda ban sani ba ashe ba wanda yasan ko may yasamay ni,agidan </p><p> Don yasan cewa wanan wani sirine mai nauyi ba,abinda kowa zai sani bane,,,,</p><p> Daya koma gida kuma ce masu yayi ai zaki nasha da yawa shiya ja min ciwon ciki,,</p><p> Hjy tsohuwa ta nuna mairo da ido tace wanan ja,irar yarinyar tasa su shan shi jiya saida nai masu magana akan kada su sha tarin alawal danaga sun sayo</p><p> Amma basu ji ba, saida suka sha abin su,,</p><p> Yanzu gashi kin jawa yarinya wahala,, saboda ke kin saba da sha tun a,gida</p><p> Mairo tashi , tashige daki tana magana ciki,ciki hjy tace ja,ira fito waje mana ki fada inkin isa,,,,</p><p> Hjy mama da takaici duk ya ci ta azuciyan ta,,,ko magana bata samu yi, ba don dama bataso azo da hjy tsohuwa ba wanan tafiyan </p><p> Ta,sone su zo su, kadai da ita da Alhaji da yan matan da take riko, kawai </p><p> Saiga hjy tsohuwa ta tubure masu akan sai tazo ta ga dan lelenta Ahmad,,,</p><p> Kuma duk ta gane nufin hjyn waidon kada suzo su cinye ma Ahmad kudin shi,,,</p><p> Tunda anki bari mamanshi tazo da yan uwan shi, shine kulun korafin hjy tsohuwa,,</p><p>,,,,,</p><p> Nasamu sauki sosai don inka ganni bazakace nice mai rashin kafiyan ba,,</p><p> Saboda duk yadda ake kula da mutum nasamu kula daga wayan nan mutanen kirkin masu arziki da sanin ya kamata,,,</p><p> Sun maidani tankar yar uwan su ta jini,,,,,,</p><p> Ashe bell din company da sherrifudeen din mu ke aiki su ne zasu biya duk kudin da aka caje ni a asibitin,,,,,,</p><p> Lokacin da za sallamana yayi ,</p><p> Aka sallamay ni nadawo gida,,, </p><p> Hatta Alhaji lawal zannah yayi farin ciki da dawowana, saboda ya nuna muna farin cikin shi fili da dawo na,,,,,</p><p> Hajiya tsohuwa taimin fadan cewa in kula da lafiyan jikina in,daina shan zaki tunda gashi saboda zakin da mukasha har saida nayi ciwon ciki kamar zan rasa raina,,</p><p> Acikin zuciyar mu nida Rugaiyya muka gane cewa sheriff din mu bai fada masu ko may yasamay ni ba har nai ciwo, watau ya boye min sirina,,,,,,</p><p> Gefen dayake na,kalla nakoyi sa,a muka hada ido dashi cikin kunya da alamar ko in kula anashi bangaren kowan mu ya,kauda idon shi ga,dan uwa,,,,</p><p> Washe gari da safe jinin ya tsaya min banga komai,tun da,daren har zuwa, da safe yau,,,,,</p><p> Nasamu Rugaiyya a kitchen tana aikin abin karyawan mu na,fada mata, </p><p> Tadan yi murmushi ta dafani tace kwana uku ke nan zaki dinga yi fadima, </p><p> Aiko kinyi sa,a,,,,</p><p> Taimin bayanin yadda zan tsarkake kaina bayan nagama jini,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mun shirya komai duk kayan mu anyi parking,</p><p> zamu koma makka zuwa marance yau insha Allah</p><p> Dama rashin lafiya na yasa suka kai har wanan lokacin,basu koma ba,,,,,</p><p> Hjy tsohuwa tace min sai na kaita tayi ziyarar ban kwana a Rauda,,</p><p> Cikin shirin mu nida ita muka fito don mu samu motar da zata kai mu massalacin,,,,,</p><p> Akofar gidan namu muka hadu da sheriff din mu Ahmad ,</p><p> Da baban shi Alhaji lawal da hjy mama,</p><p> Ido suka bimu dashi almar tanbaya ina zamu a fuskan su,,tunda sun san cewa yau za,a wuce,,</p><p> Hjy tafada masu zan kaita ziyara ne kafin mutafi tana son tayi ziyarar bankwana a Rauda,</p><p> Wani irin mugun kallo sheriff din mu yai min saida na tsargu da wanan kallon</p><p> Kayan dake hannushi yamiko min alamar in kai mai ciki,gida,,</p><p> Lokacin da nazo ansan kayan sai ya sausauta, muryan shi,,</p><p> Yake ce min cikin larabci nida banda tsarki shiga massalaci shine zan bi hjy zuwa massalaci, </p><p> Saida naji kamar in,dauke wuta saboda kunya,,,</p><p> Akunyace idona akasa nace mai nayi tsarki yau insha Allah don har nayi sallah asubah,,,</p><p> Cikin rashin yadda yasa yashiga ciki don ya tambayi Rugaiyya,,,,,</p><p>🐎 ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 14:14] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 3⃣7⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS</p><p> MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Cikakkiyar nutsuwa da wadatar Ruhi ya tabbata ga mutumin da tunanen laifukansa ya hana shi hangen laifin wani,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Masoya na asali ko yaushe Maman Nasiba, Mamam Ayman, Sahura Ismaeel ,Anty Batu,ul, sister ,Zainab Ibrahim ,Maman yahy musa ,Anty Hadiza, Ibrahim, maman Rufaida,Anty mariya sb da Anty hafsat yusuf</p><p> Fatan Alheri gare ku da karewa lfy da duniya,,, tare da duk sauran yan huguma group👏👏👏👏</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Almost true life stor</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Allah yadawo da mu makkah lafiya, sai dai tafiyan marance, mukaiyi sai,cikin dare muka iso garin lokacin duhu yayi sosai,</p><p> Saboda tafiyan na marance ne kuma ba gudu mu,kekayi,ba, tafiya ce ta hankali kwance,,,,</p><p> Saboda haka agidan sheriff din mu muka sauka da muka iso, dole, a nan zamu kwana da su,,,, </p><p> Sam ban so hakan ba na so a,ce muntafi gidan kodan inga hajiyan mu,, wace na bari ba lafiya,,,</p><p> Dakin hjy tsohuwa muka kwana kamar yadda ta bukata,</p><p> ,tsohuwa mai albarka ga sanin darajan dan adam,,,</p><p><br /></p><p> Mun samu gidan na sheriff din mu, ba laifi an gyara ko ina, tsab,</p><p> duk da munyi tafiyan kwana biyu,,,</p><p> amma wa yanda akabari gadin gidan sunyi kokarin ,sosai komai neat muka samay shi kamar akwai mutane,,,</p><p> Don haka bamu sha wani wahala ba gurin gyarawa gidan da muka iso,,,,,</p><p> Yau, Saura kwana uku bakin mu, su koma gida, Nigeria, shiri kawai suke tayi, kowa ana mai parking din kayan shi,,,</p><p> Tun da muka,iso na so mutafi gida a wanan lokaci, don ina ganin mun shigo garin makka sai naji ina son mutafi ,,</p><p> saboda hankalina yana wurin hajiyan mu,</p><p> Amma Hakan bai samu ba don shirin tafiyan da ake tayi,,na bakin mu , </p><p> Wanda agaskiya banso rabuwa da su ba musan man hjy tsohuwa,,,,</p><p> Ga jamila da mairo sun sani gaba sai na kaisu shagon,, Top ten sun sawo kaya let's one,,</p><p> Dole a haka nadaure na raka su,shagon Top ten din ,,dake kan hanya sharmansoor,, naso ace natafi gida tunda safe wlh,,</p><p> Muna shiga shagon naga duk sun rude sun ma rasa wanda zasu zaba ,aciki,</p><p> Magana nayi da walk services na shagon nace yanuna muna inda zamu zabi kaya na kware , </p><p> Sunyi sayayya so sai agurin </p><p> Kudin da tso huwa tabani in kara mata kaya itama na sawo mata abubuwa masu kyau da ma,ana,,,,</p><p> Saida kusan duk sayayyan ta na yan mata ne ita ma,,, sai kuma jallabiyan maza masu kyau da sayo mata,,,</p><p> Muka koso kayan mu niki niki muka dawo gida dashi,,,</p><p> Ko ,da muka dawo,gida, duk yadda naso nabar gidan kafin dare yayi hakan bai samu ba gareni</p><p> Don,hjy tsohuwa tace sai nakaita tayi dawafin ban kwana, a Ka,aba,,,,,</p><p> Sai dare muka dawo kuma cikin daren nan nabiyo hanya ni,kadai saboda Rugaiyya tace baza tabi hanya ba cikin dare don kada,,,yan, bagaladi su,kamata,</p><p> Mutane jefi, jina ne a unguwar tamu,, </p><p> Duk da mutane sun fara shigewa gida saboda dare daya dan soma yi,, </p><p> Hakan bai hana wasu makwabtan mu su gane ni ba,,,</p><p> Wata makwabciyar mu ne anace da ita,lamilami ta fara ganina, tace min fadima ce nace eh,,,</p><p> Yo ance muna kun gudu kunbar hajjiya mana,, </p><p> Ban,bata ansa ba nawuce cikin gidan mu kai,tsaye,,,,</p><p> Su ,Sukaina ne zaune suna dan ciye ciyen su sai Yumma da ke wanki a gefen famfo,</p><p> Ido suka bini dashi suna mamaki ina nafito cikin wanan daren , haka, </p><p> Don kusan sati kenan ana cigiyar mu agari,</p><p> Don, inda duk san,sanin takari yake, anbada cigiyar mu,,,,, saboda suna zaton mun gudune munbar hjy wanda yin haka yana jawo takari irin mu,kanana matsala,</p><p> Don da mutun ya gudu yabar uban gidan shi gara yan bagaladi su kama ka,,,</p><p> Ana cikin kururuwan mun gudu nida Rugaiyya </p><p> Sai gani nadawo gida hankali kwance abina, batare da alamar wani tashin hankali ba,,,</p><p> Ban tsaya ta kansu ba don nagane nufin su,</p><p> dakin hajiyan mu na fada kai tsaye,,</p><p> Kwance take cikin wani irin mugun yanayi wanda ko kai waye dole ta baka tausayi,,,,</p><p> bata iya dagawa daga kwance, da take,,</p><p> A,firgice nanufi inda take kwance, na rugumay ta, ina kuka</p><p> Ina,cewa hajiya may yasa may ki haka kika zama haka cikin lokaci guda,,,</p><p> Ina mai,daga muryana, Cikin kukan nake cewa duk a rasa wanda zai kaiki asibiti sai abarki haka,,,,</p><p> Yumma ce ta fado dakin tana cewa fadima ai na sayo mata yan kwayo yi na sha kuma ina bata abinci,</p><p> Ko yumma bata fadi ba,</p><p> Dama nasan cewa ita kadai ce zata iya dan kula da hajiya, cikin su,,,,</p><p> Dan sauran hajiya bata da wani daraja a idon su yanzu ,</p><p> Saboda sun girma kuma idon su ya bude,</p><p> Su anasu wautan suna ganin cewa hakan da sukeyi ma hajiyan shine daidai saboda ai itace tafara cutar mu tun a gida,, Nigeria,,,,,,,</p><p> Sun kasa yarda da kaddara cewa Allah yariga yanufi sai mun zo,, munyi wanan bautar koda da kafane sai munzo kasar saudiya munyi takari,tunda hakan na cikin destiny din mu,,,,,</p><p> Na juya wurin yumma nace taci abinci kuwa tace min tunda rana ba kuma ba sosai ba,,,,</p><p> Dama kudin da Alhaji lawal zannah yabamu a madina don muyi sayayya muma,,</p><p> yana ajikina don haka fita nayi zuwa,</p><p> wani shago can kasan mu inda ake saida kayan gasawa iri iri na ci da sha,,,</p><p> Naje nadan siyo mata dan abinda nasan zata iya ci,,</p><p> A cikin daren na gyarata tsab tare da taimakon yumma, ,don su sauran ko kallo ban ishe su ba,</p><p> nabata abinci taci tasha maganin da yumma ta sayo mata,,,,,</p><p> Tana kwance Gefen kafar ta nazo nadan zauna ,ina kokarin bude inda nasa kudi don in kidaya su.</p><p> kudin wanda,ke cikin jikina ko zasu i,she mu zuwa asibiti gobe,,,</p><p> Yumma kuma tana gefe tana, cin sauran abincin da hajiya ta rage,,</p><p> Muryan hajiya naji kasa kasa tana cewa ina muka je kwana biyu bamu gida ina Rugaiyya,</p><p> Ban boye mata ba nace mata madina mukaje ziyara tare da iyalin Sheriff din mu, da suka zo daga Nigeria,,,,,,</p><p> Shiru tayi tunda Maganar dama na dole ne</p><p> daga hakan bata kara cewa komai ba,</p><p>Saidai ajiyar zuciyan danaji tayi ,ahankali, ta gyara kwancinta</p><p> Dama tun da nake kirga kudin da ke ajikina dan zamu tafi asibiti da su da safe ,naga mari da sukaina suna min wani kallo, kasa kasa suna magana,,</p><p> Nasan cewa suna iya sace kudin in, nai barci,,</p><p> Aiko haka din ne, ina cikin barci, gefen hajiya kwance dama na faki idon su na canza ma kudin wuri,,</p><p> Cikin barci naji ana lalabata caraf na rike mata hannu nace lafiya,mari ce</p><p> Saicewa tayi wai tana bidan wani abune data aje daidai inda nake kwance,</p><p> Duk da nagane nufinta sai,kawai, na,gyara mata don ta diba abin,</p><p> nikuma daga haka barcin da ban koma ba ke nan,,,</p><p> Tashinayi na fara gyara muna gida da duk wani abu da yakamata muyi, amma suka yi don son kai,,,</p><p><br /></p><p> Tunda safe muka ziyarci asibiti da ni da hajiyan ,mu </p><p> Allah ya taimake ni muka ga likita da wuri saboda mun fito da wuri daga gida,,,,</p><p> Bayan yan aune aunen da a,kayi wa hajiya aka gane cewa jininta ya hau sosai , kuma tana sakaci da shan maganin da likita ya dorata akai</p><p> Don haka tana bukatar aimata wasu allurori har da karin ruwa, aciki,,, </p><p> Tafiya nake yi, a,hankali,</p><p> Yan kudin da nazo dasu asibiti nake ta kirgawa saboda ina ganin cewa baza su ishe mu abinda ake bukatar yi ma hajiya, ba,,,</p><p> Jinayi nayi karo da mutun agabana har yan kudi nawa suka zube kasa,</p><p> Banko kalli wanda yasa nazubar da kudin kasa ba ,hankalina ya ga kudin magani,, kada iska yajamin su su rage yawa,,</p><p> Duka wa mai shi yayi yana tayani kwashe kudin ,,,,,,</p><p> Saida ya miko min kudin na karshe ne da,yataya ni kwasa,,</p><p> ,Sainaji kamshin turaren Sheriff din mu Ahmad,</p><p> Da sauri kuma cikin mamaki hankalina, yadawo,nakai dibana gare shi, </p><p> Shidine kuwa ,shikuma daidai ,</p><p> Lokacin yana mikewa tsaye daga tsugun nin da yayi don kwashe min kudin,,,,,</p><p> Hjy tsohuwa tana a bayan shi tsaye da a,lamar bata jin dadin jikin ta,, ita ma,,</p><p> Batare da yakalleni ba ya ja hannu hjy don suwuce zuwa wurin likita,,</p><p> Sai alokacin hajiya ta ganni don dama batasan cewa nice ba,</p><p> Tanbayana takeyi cikin mamaki ko ya akayi na biyo su asibitin tunda safe, wa ya fada min suna asibiti,, </p><p> Shiko sheriff din mu azuciyar shi cewa yakeyi,</p><p> wanan yar wahalan kuma ko may yakawo ta nan tunda safe yarinya kamar aljanna duk inda kabi zaka ganta,</p><p> Can kuma yatuna kodai jinin nawa bai tsaya bane, shine nazo ganin likita,,,</p><p> Muryana dayaji cikin hausana da ba daidai ba Ina fadawa hjy tsohuwa cewa nakawo hjy ta asibiti ne,,, saboda nadawo na samayta bata da lafiya sosai,,, </p><p> Saboda girmamawa da nuna kulawa sai naji bazan iya wucewa inbar su shida hjy tsohuwa ba</p><p> Kodan irin so da kaunar da yar tsohuwar ke gwada min,,,</p><p> kawai sai na tsinci kaina da,bin,su abaya har zuwa office din likitan da zasu,,gani,</p><p> Bayan anyi ma hajiya booking din likitan da zata gani, ,,, </p><p> An,yi komai har a lokacin muna tare dasu sam na ma mance cewa da hajiyan mu muke, a,asibitin,,,</p><p> Takardan maganin dake hannu ya buka ta ,,,</p><p> Na bashi yakarba yadan diba kadan </p><p>Sai naga yawuce inda ake saida magani kai tsaye, batare da yai min magana ba,,,</p><p> Maganin yasiyo min harda ledar ruwan da za,akara ma hajiyan mu,,</p><p> Inda take ya buka nakai shi,</p><p> hajiya na zaune gefe ta wani, makure gefe, duk ta mokade kamar ba itace hajiya mai sharwali ba,,</p><p> Koda mukaje, Kallon banza naga yai mata,</p><p> Wanda saida na tsargu, sosai da irin kallon</p><p> duk da tana cikin ciwo baisa ya tausaya mata ba, saboda irin mugun halinta na cutar da kananin yara,da tayi batare da sanin iyayen su ba,,,</p><p> Sai kawai naji banji dadin yadda naga yana kallon hajiya ba, </p><p> Saboda aiko da nake tallaka kuma ,yar aiki shi ai, yakamata a mutunta min yan uwana nima,,, ,,,</p><p> Sam ni bansan cewa Rugaiyya ta fada mai abinda ke tsakanin mu da hajiya ba.</p><p> Tun,a madina</p><p> Ko yanzu yasan cewa nice zan walaha shiyasa ya taimaka mata,,,</p><p> Allah yataimake ni hajiyan mu tadan warwale sosai don duk ledojin ruwan da akasiya ta zuke su ajikinta</p><p> Sai bayan kwana biyu aka sallah may mu daga asibitin </p><p> Taji sauki sosai wlh,,,</p><p> Kusan kwana biyar nayi banje aiki ba, ina fama da hajiyan mu,,,</p><p> Yau danaga taji sauki sosai nace mata ta kula da jiknta zanje wurin aiki don kada in yi laifi da yawa,,</p><p> Gashi nadauki lokaci ban je ba ban kuma dauki permission ba,,,</p><p> </p><p> Saida na tunkari gidan sanan natuna cewa hajiya tsohuws sun wuce kila, </p><p> Gashi bamu samu yin bankwana cikin dadi ba ,</p><p> Ina can asibiti da hajiyan mu</p><p> </p><p>Ashe basu samu wucewa ba a lokacin don jikin hajiyan da likitan ta ya dan tsay da su,</p><p> Ina shiga nanufi inda Rugaiyya na take aiki ,saboda mun kwana biyu bamu haduwa , ko ,agida sau guda tasamu lokaci taje asibiti diba hajiya,,,</p><p> Abincin da tagama nataya ta dauka zuwa babban falo don mu jera,</p><p>a saman table,</p><p> Amma azuciya na ina mamakin yawan abincin da ta dafa, </p><p> Sam ban kawo cewa bakin mu suna nan ba,,</p><p> Ina shiga falo naga su, mairo da jamila suna game tunda safe haka,</p><p> Dakin hajiya tsofuwa na nufa don ina kewanta dama sosai </p><p> Dan shakuwar da mukayi kwana biyun nan yai yawa,,,</p><p> Sheriff din mu ne zaune dakin tare da ita sai,dai fuskan shi da alamar ba, sauki amaganar da sukeyi,, da hajiyan fuskokin su a daure yake,,,</p><p> Cikin sauri na juya zan koma waje,,,,,,, </p><p><br /></p><p>🐎 ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 14:14] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 3⃣8⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p> </p><p><br /></p><p> Murna farin ciki da annashuwa, sun tabbata ga duk wani mutumin kirkin da tunanen, Hisabi ya hana shi tara dukiya ta hanyar haramu,,,,</p><p><br /></p><p> Gaisuwa da jinjina gaduk wanda ya fahinci ma,anar wanan littafin</p><p><br /></p><p> Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gefen hajiya tsohuwa nadan rusuna nagaishe ta cikin ladabi da biyayya,</p><p> Zandaga in wuce take tambayana jikin hajiyar mu, inda take ce min taso zuwa ta dibata ,</p><p> Saidai itama din likita yace tadan samu hutu wuri guda shiyasa bata zo ba,,,</p><p> Sheriff din mu dake zaune gefe ya mike a lokacin zai bar dakin</p><p> Barin zancen namu tayi taci gaba da magana dashi ,</p><p> Tace kadaiji abinda na fada maka, </p><p> Ka maida hankali kaje Nigeria ka diba ma haifiyar ka da yan uwan ka ,zama anan kashare kowa ba zai maka ba,</p><p> Kasan cewa itama uwar ka tana da hakki akanka don tana bukatar ganin ka ,</p><p>Saidai don bata magana ne amma nasan cewa azuciyar ta bata jin dadi</p><p> Sanan batun wa yan nan yan matan sam ban yarda da inkara hada zuri,a da yan uwan Amina ba </p><p> Yadda mahaifinka yake tauye haka akeso kaima a,tauye min ka ,</p><p> Shiyasa ina jin cewa za,a kawo su nan don kazabi guda daga cikin su nace dani za,ayi wanan tafiyan sai naga yadda za,ai wanan hadin auren in ina da rai,,,,, </p><p> Kanshi yadan sosa kadan ya jingina jikin shi da bangon dakin hannayen shi na zube a aljihu kamar yadda yake yi,</p><p> Yace haba hjy na fada maki ki kwantar da hankalin ki wanan abin ba zai yiyu ba sam nariga na fada ma ,Abba da kuma ita maman </p><p> Idan ma hadin zumunci suke so aiga su Suraj can da salis sun gimay ni kuma yan uwan su ne akai masu su su aura mana</p><p> Hajiya tsohuwa da alama zancen yadan yi mata dadin ji,</p><p> Don murmushi nagani a fuskanta,</p><p> Daidai zai fita yace ma hjy Dama ina son in zo Nigeria saboda ummina, da yan uwa ,</p><p>Sai kuma malam mijin ummi ina son ganinshi sosai,,,</p><p> To dadai yafi maka walhi </p><p> Inji hajiya tsohuwa ke fadin hakana</p><p> Har yasa kafa guda zai bude labulen kofar takara ce mai , akula da kyautawa duk wanda ke da bukata in har da halin kyautatawan,, Saboda kyautata zumunci wani abu muhinmin a wurin Allah,,,</p><p> Nasan kana yi ya kokarinka da yin aike, to ka kara ka dinga kai kafar ka don yafi lada,,</p><p> Kadinga ziyar da kula da lafiyan maihafiyar ka da yan uwan ta,, </p><p> Sai kuma maihaifin ka wanda a,halin yanzu na bukatar ku, kaga yan uwan ka ba wanda yasan alkiblan su kuma uwar su bata son sam ayi zancen su ko kadan,,,</p><p> Tana kara ce mai mahaifinka Amadu maihafinka</p><p> Saboda yana bukatar kulawa da komai nashi yanzu,</p><p> Wanan matar tashi sam ban yarda da ita ba,ko a,da, balle yanzu,,,,,</p><p> </p><p> Bayan fitar shi dakin sai dan shiru yabiyo dakin nadan wani lokaci,</p><p> Fadima nace na,am hajiya tace nagode maki kware Allah yai maki albarka,</p><p> Kikara kula da kanki kinji saboda rayuwar wanan zamanin dace ne,,</p><p> Kuskure kadan zai iya jefa rayuwanka cikin wani hali,,</p><p> Hawaye nabin fuskana nace mata nagode,</p><p> Takara cewa zan yiwa Amadu magana akan ku ku duk kanku,</p><p> Saboda naji dadin zama da kowan ku,,,</p><p><br /></p><p> Washegari munaji muna gani su hajiya tsohuwa sukai muna na, baki,</p><p> Sallama akeyi cikin bacin rai don anso rabuwa ba,</p><p> Sunji dadin mu muma munji dadin su,</p><p> Motocin su da yan rakiyan su yatashi zuwa birnin jidda don ta nan zasu tashi,,,,</p><p> </p><p> Tunda suka wuce sai nakoma wata iri banda kuzarin yin koma zuciyana baimin dadi ko kadan,</p><p> Yadda nake aiki da yanzu na rage yi sosai,,</p><p> Nafi yawan zama wurin tsuntayen gidan ,</p><p> Sheriff din mu yanzu bai zama garin sam saboda yana yawan busy </p><p> Tsakanin Saudiya da Dubai zuwa Nigeria,</p><p> Akwai wani business da suka hada da Abu Abbdullah company da ke Dubai ,w</p><p> Wanda shi sherrif din mu shine zai kula da wanan business din ta kasa shen biyu, idan har hakan yasa mu,,,</p><p> Mukan ana mu bangaren rashin zaman shi bai damay nu ba sabodo muna samun kulawa sosai ,a,gidan,</p><p> wanda takai yanzu har Yumma itama anan take aiki </p><p> Ana bamu abuwan bukata sosai bamu cikin wahala ko kadan bakamar da ba,, da muke yawon bara da kuma aiki gidaje da kamfanoni,mutane</p><p> Kudin aiki mu kuma zar albarka,</p><p> </p><p> Hajiyan mu tana samun kulawa sosai daga gare mu yanzu,</p><p> Ina yawan kaita ganin likitan ta cikin lokaci,</p><p> Hjy laila kuma tana iya nata kokarin ita ma</p><p> Yanzu mun kai kusan shekara biyar ko shidda a makka,</p><p> Mun san ko ina agarin</p><p> Indan ma gida zamu koma inajin da akwai kudin komawar mu,</p><p> Saidai yin fasport din ne matsala gare mu,,</p><p> Don shuganbani mu na takari suna da wani kungiya ta musan man wanda duk kusan wani movement din dan takari yana idon su,,,,</p><p> Indai ba kama mutum akayi ba to basu yarda mutum ya bar kasan haka na kai tsaye,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sauri nakeyi in isa gidan aikin namu saboda yau nadan tsaya gyara muna gida,</p><p> Koda na isa nassmu kusan duk ma,aikatan gidan a kofar babban falon gidan ana masu jawabi,</p><p> Sheriff din mu yazo ke nan yana gari,</p><p> Ahankali na samu guri na tsaya don sauraren jawabin nashi,</p><p> Daidai inda yake cewa lokacin zuwan mahajjata ya kusa yana son kafin lokacin mun bar wanan gidan zuwa sabon gidan shi,</p><p> Ida yake so akaro mai ma,aikata wa yanda zasu rika dafa abincin karama ana kaiwa kowani san sani na mahajjata,</p><p> Yace wanan aikin kuma sabon Company su ne zata dauki nauyin yin hakan,,,,,</p><p> Daka karshe yace muna zuwa karshen wanan watan kuma zamuyi sabuwar uwar daki ,wata,u ma,ana zaiyi aure zuwa nanda wasu yan kwanaki,</p><p> Saidai duk a wurin nafi kowa farin ciki da wanan zancen danaji,</p><p> Nan danan na natuna da maganar su da hajiya tsohuwa, na ranan,, </p><p> Bayan mun watse ana ta kus kus din batun auren sherriff din na mu</p><p> Nidai nasan cewa koma wace,ce matar zatayi halin kware tunda sherriffudeen din mu shima yana da hali maikyau har yan uwan shi,,,</p><p> </p><p> Shirye shiryen aiyukan da za,ayi na Karama aketayi kusan duk abinda za,a bukata an tanada ko</p><p> Kayan aiki ne irin na,zamani kala,kala aka kawo,</p><p> Ranan da wa,"yan da zasu diban aikin sukazo daga Dubai sai, yakasance sheriff din mu baya gari amma dai yana hanyar shi ta shigowa makkah daga Riyadh</p><p> Baturen na masu turanci duk sai akayi shiru don basu fahince shi, gashi Almustapha bai gida yadan fita,</p><p> Nazo wucewa sai naga ana wanan draman natsaya ina kallon su</p><p> Allah yasa nadan fahinci abinda baturen ke nufi,</p><p> Da dan saurina na,isa,gurin na fara ba shi ansa a,hankali tambaya yake yi cewa nan ne gidan sheriff din mu, ko sai kuma yace sunyi waya yace mai yazo, nan ya,jirashi yana kan hanyar shi ta zuwa makkah,</p><p> Na,kaishi karamin falon danaga ana sauke baki, aciki musan man maza na bashi abinsha da dai duk taron da za,ayi wa bako,</p><p> Har na juya zan wuce baturen yace min ni sister din mr LAWAL ne nace mai a,a ni maide ce mai aikin gida,</p><p> Baiyar da ba don dariya yayi min kawai</p><p> A,bangaren sheriff din mu kuwa yana can yanata kiran layin Almustapha amma bai dauka ba, saboda yabar wayan shi agida yadan je yadawo bazai dade ba,</p><p> Ranshi duk a bace sanin cewa ba, wanda zai tari wanan bakon don bakon baijin larabci,,,,,,</p><p> Sai dukan sitayarin motar shi yakeyi yana fadin Subbahanallah, saboda gani yakeyi indan tun zuwan mr Williams baisamu taro mai kyau ba ai zai iyacewa akwai matsala ga aikin,,,</p><p> Bansan cewa mr Williams yana bayana ba lokacin da nafita zuwa wurin tsuntsaye na don in basu abinci karo na biyu,,,,,</p><p> Jinshi kawai nayi yana wasa da Akun da ke cikin wani kejin golden ,</p><p> Dariya yabani nan muka dinga shiriritan turanci da shi saboda ni nadauka bai gane may nake nufi ba,</p><p> Amma na,ta,karkare sai watsa wanakeyi duk yadda na samu ashe kusan duk daidai nakeyi,</p><p> Mu cikin dariya da mr Williams da ke kyokoyon Aku, kuturu, </p><p> Saiga Sheriff din mu gabana hannan shi sada kamat kulun a, aljihu </p><p> Musa,bi,a sukayi da mr Williams din suna dan dariya, </p><p> Inda yake bashi hakkurin dan matsalar delay din da akasa mu,</p><p> Yace mai no no ai yasa mu taro mai kyau daga little sister yana nuna ni,</p><p> Nikuma a lokacin ina dan gyara wurin da abincin tsuntaye yadan zube a kasa,</p><p> Wani kallo yaimin da bansan kowace iri bace,</p><p> Amma dai nasan cewa kallon nada wani ma,ana</p><p> </p><p> Tun lokacin in mr William yazo to sai ya zagaya inda nake gurin tsuntaye na,,,</p><p> Mundayi hira sosai don yana son yadda nake turanci na yana sashi dariya,,</p><p> </p><p> Duk wani aune aune dazasu yi don gane inda zasu aje ma,adanan su, sunyi kuma anci nasara sosai,</p><p> Dadina da ubangidan mu watau sheriff din da ya samu alheri duk wanda ke tare dashi zai samu </p><p> Don haka mun samu kyauta so sai daga gareshi,.</p><p> Saboda nasaran da suka samu wajen kafa company Abu Abdallah a saudiya,, da Nigeria,,</p><p> Lokacin da mr Williams zai tafi saida yasa akakirani nadan yi mai turancina nakuma kaishi wajen 'Aku suka dan yi hira dashi,, </p><p> Sheriff din mu da su Almustapha suna tsaye suna kallon shirmay mu,</p><p> Da zai tafi yarike hannun sherrif din mu, yana masa magana gamaydani,</p><p><br /></p><p> Tun lokacin da mr Williams ya wuce da yan kwanaki shima, Sheriff din mu yayi tafiya zuwa Nigeria,</p><p> Almustaphane ke fada wa mama mai abinci cewa sherrif yatafi wurin iyayen shi,</p><p> Amma ba zai dade ba zai dawo don ankusa fara azumi,</p><p> Yanzu da wuri nake wucewa gida saboda aiki yadan yi sauki yanzu,,</p><p> Hajiyan mu tana kula da shan maganin ta yanzu sosai ina yawan kaita ganin likita time to time,</p><p> </p><p><br /></p><p> Jirgin mangal air line yasauke bakin saudiya a Nigeria cikin su harda sheriff din mu ,</p><p> A kano suka sauka saida ya kwana a wani hotel dake kusa da airport din,</p><p> Tunda safe ya dauki drop sai Maiduguri , saida ya kusa kaiwa state din yai ma wani,cousin brother din shi waya wanda ake kira da bashir, </p><p> Shida bashir suna, shiri sosai, duk da bashir din yadan girmay shi kadan amma nasu yazo daya sosai</p><p> Kauyen hajiya tsohuwa ya wuce direct inda mahaifiyar shi take zaune tana aure, da yaranta,,,</p><p> Bashir ne yazo yatare shi saboda zuwan bazata da yayi masu,</p><p> Hjy taji dadin zuwan Ahmad duk ta rude ta rasa inda zata sa,shi </p><p> Saboda farin ciki ganishi da tayi,</p><p> Lokacin da ya isa dare ya somayi don haka hutawa yayi kadan yadan ci dan abincin da hjy ta gabatar mai</p><p> Wurin malam yatafi mijin mahafiyar shi, a cikin daren nan</p><p> Don dama bashir ya sanar da malam din zuwan Ahmad din,,,,</p><p> Bayan gaisuwa da yaushe rabo sai dan shiru ya biyo baya,,,</p><p> Malam ne yadan yi gyaran murya yafara magana,</p><p> Yace kamar yadda suke kiran shi Alhaji karami kwana da yawo </p><p> Murmushi yayi yace kuyi hakkuri malam abubuwan ne suka dan yi min yawa acan,</p><p> haba Alhj karami ai ko,bakazo don kowa ba kazo don nan yar tsohuwar da kullun zancan ta bai wuce naka,</p><p> Ayi hakkuri malam za,a dinga kulawa insha Allah,,</p><p><br /></p><p> Sheriff din mu ya fiddo da kudi masu yawa daga Aljihun shi ya dan kidaya yace ma malam wanan kudin malam don Allah ina so abaiwa bayin Allah suyiman saukar Al,kur,ani maigirma da kuma sadaka ga mabukata dafatan Allah ya biya muna bukatun mu na Alheri,</p><p> Muna son zamu yi wani company na global da zamu kawo daga kasar Arabs country ,wanda in hakan yai muna dadi zamu kawo wasu company na abincin kasa shen waje,,,,</p><p> Sai kuma wanan abama duk wani dan uwan su, Yabi yasa min albarka,</p><p> Yabi kaunar shi dake bi mai wacce malam ya haifa tare da Yaghana, mahaifiyar Ahmad,,</p><p> Malam yai shiru nadan wani lokaci ,, yana kallon kudin </p><p> Can yace Alhaji Amadu,</p><p> Ahmad yace na,am malam aikin may kakeyi a can har kasamu wanan kudin haka</p><p> Duk da nasan cewa kaidin yaro mai hali nagari tun kana karami amma saboda canji lokaci da yanayi nasan dan Adam na iya canza wa,,</p><p> Ina fatan rade radin da matar mahaifinka keyi na cewa kana sa,na,ar saida miyagun koyoyi a kasa mai tsarki har ka tara dukiya mai yawa,</p><p> Wanda jin hakan da mahaifiyar ka tayi har yasa tadan shiga cikin wani yanayi ita da hajiya tsohuwa</p><p> Gabanshi ne yabada wani irin dam,</p><p> Har yadinga jin wani irin jiri na shirin kwasan shi, Allah ya taimaka, zaune yake </p><p> Tunda Ahmad ya dukar da kai bai iya dagawa ba saboda bakin cikin irin kazafin da hjy mama tai mai,</p><p> Bashir ne yaiwa malam bayani duk irin cigaban da yake samu acan da kuma wanan na yanzu da suke shirin yi a wanan kasar,,</p><p> Dayake malam mutune mai wayeyen kai nanda nan yafahita yagane cewa sherin da hassadan kishirya uwace kawai,</p><p> Duk da,dama riga yasani don tun lokacin da matarshi yaghana watau maihaiyar Ahmad taji wanan labarin daga bakin, matar, yayan nata,</p><p> Wanda ke fada mata abinda hjy mama ke fadawa yan uwan mijinta da sukaje taron su da ,dawo wa umurah,</p><p> Malam najin wanan zancen ya tashi cikin dare yai nafila </p><p> Har kusan sati guda yana nafila Alheri kawai yake gani gamay da Ahmad din </p><p> Tun lokacin zuciyar shi ta tabbatar mai da kuma amincewa da Ahmad din</p><p> Ko wanan maganar yayi shine kawai don Ahmad din yakara gyara halinshi sama da na da,,,</p><p> Bayan malam yakara mai nasiha da kuma jan kunen shi gamay da duniya dakuma mutanen duniya,,,</p><p> Cikin gida akai mai iso gurin mahaifiyar shi,</p><p> Bayan sun gaisa shiru yadan biyo baya kamar yadda suka saba tun yana karami bata iya sake jiki tayi wani dogon zance da shi,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 14:22] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 3⃣9⃣</p><p> BY </p><p> 🐎ZAINAB MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ya, zo sunnah ta ma,aikin Allah SAW cewa ka,nemi Gafaran dan Uwanka a Karshen ko Wacce Shekara, ina neman Gafaran Ki idan na Bata Miki ina Sane ko bana Sane ni na Yafe Maki in har kin Saba min,,,,</p><p><br /></p><p>Anty Amal Anty safiya Anty mariya Anty billy galadanci, maman rufaida maman fareeda maman ikram sadiya maijjidda harazami Rahma Anty Batu,ulu Duk ina maku fatan alheri tare da fatan gamawa lafiya da diniya,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Daga kai yayi a,hankali ya dan kalli mahaifyar tashi ,</p><p> Sai kuma ya juya a,hankali ya dan kalli dakin da suke ciki, </p><p> Inda ya dan yi tunanen cewa a,nan take rayuwar ta, a cikin wanan dakn haka,</p><p> ita da "ya," yan ta, yatuna irin gidajen da shi yake dasu yanzun haka a,saudiya,</p><p> Tausayinta ne,yakama shi, Don yasan cewa daidai da rana daya bata taba ronko shi komai ba na rayuwa,</p><p> Sanan gan shi ita da, shi i yasan cewa basu wani, morewa rayuwar su, nazaman da da,mahaifiya ba sam,,,,,</p><p> Saboda irin rayuwar da yatashi a ciki batare da mahaifiya shi,ba </p><p> Dan dama dama yadan samu kulawar , kaka, kadan.</p><p> Yasan cewa Allah ne ke tare dashi kawai,ga al,amarin shi,,, ,, </p><p><br /></p><p> Shirun ne yadanyi yawa ,adakin , sai yadan kau da shiru ,yake tambayar ta sister's din shi,</p><p> Yaganah tadan gyara daurin lafayan ta ,</p><p> A inda take zaune gefen gadon ta, a,takure cikin shigar, lafayan da ta nade duk jikinta da shi,</p><p> Dakin sai kamshin turare ke tashi irin na yan maidugurin asali,,</p><p> Indan ka ganta,A cikin kamala take maganar ta, tana bashi ansar cewa suna makaranta kwana amma, shekarar karshe suke, yanzu</p><p> Nan da sati guda zasu kam,mala karatun su gaba daya, insha Allah,</p><p>Azuciyar shi Yayi mamakin ace har yaran sun kam,mala karatun su bai sani ba,,,</p><p> Lalai maganar hjy tsuhuwa ne yana sakaci da al,amarin mahaifiyar shi, sosai,,,,</p><p> Wacce kamata yayi ace tana cikin hutu, yanzu saboda yakai lokacin da za,ace ta huta, da komai</p><p> Saidai ina, duk lokacin da yaso yayi mata wani abu na musan man sai yaji kamar andaure shi,, ba zai iya yi mata komai ba in yai niya,,</p><p> Kuma yasan cewa yana turo ,ma mahaifin shi da kudi masu yawa koda yaushe ,</p><p> Wanda ya ci ace mahaifin nashi, yanzun haka angyara mata muhallinta, da su,</p><p> Sai gashi yazo yasamay ta a cikin irin wanan yanayin na jiya wayau,</p><p> Babu wani almar tanajin dadi a,rayuwanta sam,,,</p><p> Shiru yadan kara ratsa dakin ,,,,</p><p> Wanan karon yaghana ce ta danyi kokarin yin magana da dan nata,</p><p> Nasiha tadanyi mai gamay da zaman duniya</p><p> Sai kuma maganar aje iyali ,da take tambayar shi, cewa ance mahaifin shi zai hada shi aure da yar abokin shi ko,</p><p> Inda taimai nasihan a kan rikon amana, da gaskiya da, kuma kula da hakin aure,</p><p> Namu har kulun shine mudinga maka addu,an fatan Allah tare da gamawa da duniya lafiya,,,,,</p><p><br /></p><p> Tabbas yaji dadin wa, "yan nan magan ganun sosai, musan man kamar yadda take tasai mai albarka, abinda bai taba jiba,,,,,,</p><p> Don tunda yake da, ita basu taba dadewa irin na yau ba suna magana, ko hira,</p><p> Lalai yana da sa,a sosai a wanan tafiyan nashi,, insha Allah tunda yau harda albarka yasamu gurin ta,,,,,,</p><p> Daga karshe ya ciro kudi masu yawa ya aje mata agaban ta,</p><p> gabanta ne ya fadi don tunda take bata taba ganin kudi masu yawa ba haka, </p><p> Yadago kai da niyar yai mata bayani akan kudin,</p><p> Kaifin yai wani magana yaghana tace a,a, yaro bani bukatar kudi daga gare malam da hjy tsohuwa ba su rage ni da komai ba a,rayuwa na,</p><p> gashi kaima din kana aiko muna da sako lokaci lokaci ta wurin hajiya tsohuwa</p><p> Kabar kudin ka wai don akwai hidi momi agabanka da zakayi,,,</p><p> Ya, Cewa wanan kudin ina so ki samu wani sana,a kifara yi dashi,,, </p><p> wanda kudin zasu dinga shigo maki kafin in aiko maku dashi,,,,</p><p> Sai kuma wurin su yabi kaunar shi da aka fara yiwa aure, ita ma,ina so adan taimaka mata da wani abinyi,, </p><p> Sanan bashir zaizo da masu aikin gina ina so ai maku gyaran wanan gidan ya koma irin na zamani,,</p><p> Duk da bata son su hada ido da dan nata, don yawan kunyan shi da take ji yasa ko daga kai batayi idan yana gabanta,,,</p><p> Amma yau,saida ta daga idon ta da sauri takaleshi</p><p> Tace a,a gyaran wanan gidan ba karamin aiki bane ,</p><p>malam kuma yana yawan gyara muna shi lokaci lokaci kawai ka barshi mungode,,, </p><p> Baice mata komai ba yai mata sallama zuciyan cike da tunane iri iri</p><p> Watau tsohuwa tana taimaka wa manshi da sunan shi,,,</p><p> Bai san ya zai gode ma wanan boyar Allah ba mai kaunar shi a,kullun,,,,,</p><p> Da zai tafi yakona gurin malam,sukayi sallama </p><p> Inda malam ya kara dan tatanawa dashi,akan aikin da zai turo aimasu da kuma zancen yan kanan shi da zasu kare karatun secondary bana,,,,,,</p><p> Suma yana son ya taimaka masu,,,,,</p><p> Don suci gaba da karatu,,,,</p><p><br /></p><p> Gidan tsohuwa ya koma ya kwana cikin dakin shi na yarinta dake gidan,,, wanda bata yarda ta sa kowa acikin shi ba,</p><p> Dakin fes dashi kamar akwai wanda ke kwana aciki, don yawan gyaran da take sa ana ma dakin,,,,</p><p> Washe gari Saida ya karya kumallo da safe ya kuma, dan gana da wasu daga cikin yan uwan shi ,</p><p> Inda yai masu dan alheri so sai, yakuma, yi masu, bayani irin aikin da yake a,can kasar saudiya dakuma irin aiki dake gaban shi yanzu,</p><p> wanda zasuyi yanzu anan kasar ta Nigeria</p><p> Ya,yi masu wanan dan bayanin ne</p><p> Don kawai yadan wanke zargi da shankun sa da suke yi </p><p> tunda hjy mama tasa zargin shi, azukatan yan uwan nashi,. ,,,,,,,,</p><p> Sun ko gansu kuma sunyi aman na,dashi</p><p> Inda har,wani kanin mahafin shi kecewa</p><p> munyarda da zancenka Alhaji karami , tunda dayawan mun je mungani kuma mutanen mu in suntafi sunaganin ka ,har yau bamuji komai na assha daga gareka ba ,</p><p> Shiyasa koda tazo tai, taimuna wanan mugun tabon azuciyan mu, bamu dauka don ba mu yarda da ita ba sam </p><p> Don mu kowani ne yazo ya fadi wanan zancen baza mu yarda ba balle ita din</p><p> Ai, In,ma sherine kusan kanta taimawa don diyanta tunda suka tafi turai ba wanda yazo kasan nan ko sau daya suna can suna holewar su, </p><p> Itace mai binsu idan tana bukatar ganin su,, sai ta fake da cewa taje ziyaran sune,,don karatu yai masu yawa,,,,,,</p><p> Kuma labari ya samay mu cewa shashanci suke koyo a turai din,,</p><p> Da haka ya rabu da su sunata zowa suna mai sannu da zuwa da kuma godiya akan kulawar da yanuna masu cewa shidin nasu ne don bai ki su ba,,,,,</p><p> Da murna da farin ciki ya nufi garin Maiduguri,, </p><p> Don yagana da mahaifin shi kafin ya wuce zuwa Abuja inda zasu ga wasu kusoshin gwaunati kasar ta nigeria don su fara kaddamar da shirin su,,,</p><p> Na kafa company global da sauran masana,antu,,, acikin kasa,,,</p><p> Mr Williams zaizo, Nigeria inda za su hadu shi Abujan su gudanar da,komai,,,,,</p><p> Yasamu Alhaji lawal zannah a katafaren gidan shi da ya gina a G R A uguwar da mafi yawan mazauna wurin tsofafin masu mulki kasane da manyan attajirai sune mazauna wanan uguwar,</p><p> Mahaifin nashi yayi murnan zuwan shi so sai ,</p><p> Don dai dan nashi ya cika mai alkawain ya nuna mai cewa shi dan halas ne</p><p> Don yazo akan kiran shi dayayi kuma yaimai alkawarin zuwa gashi kuma yazo din,,,</p><p> Ga uwar gaiyar wanu,irin kallon da taron da yasamu gurin ta,, hmmm,hjy mama saidai kawai ayi shiru dama yasaba dà irin hakan daga gareta,,,,</p><p> Bawani sabon abu bane hakan da tayi mai don inda sabo yasiya da halinta,,,,,</p><p> Amma ita in,taje gurinshi ji irin taron da yake mata kamar itace mahaifiyar shi, Ankawo mai abinci inda ya nuna ma mahaifinshi cewa akoshe ya ke,</p><p> Murmushi dattijon yayi kadan ,daidai lokacin da yake zama a daya daga cikin kujerun dake wurin da aka tana da don cin abincin,, </p><p> Yace ma dan nashi, babana baka iya cin abincin mu ne yanzun nan ko kuwa, a koshe ka,ke,</p><p> duk da yagane cewa dan nashu, baison cin abincin hjy mamane kawai saboda hajiya tsohuwa ta hane shi tun yana yaro,,,,,</p><p> Ada bai dauki maganar dagaske ba amma da yafara girma yana wayau, sai yake fahintar cewa</p><p> lalai mama zata iya cutar dashi ,</p><p> don tana iya masa komai don ta salwantar da shi aduniyar nan </p><p> don haka yake taka tsantsan da al,amarin ta,,</p><p><br /></p><p> Don yakauda zargi ga zuciyar mahaifin nashi sai yadan isa bisa tebur din cin abincin ya dan zuba fruit, salad kadan yana sha ahankali,</p><p> Alhaji yadan yi murmushi irinta manya ya kalli dan nashi </p><p> yace mai babana kayi imani da Allah azuciyar ka</p><p> cewa ba Amina ba duk wani mahaluki na duniya bazai iya cutar da kai ba insha Allah,,,,,</p><p> Duk da asiri taci annabawa Allah balle mu,</p><p> Kaidin mutum ne mai kula da yawan ibada da tsare dokokin Allah,</p><p> Yadda yakamata ,,,,, kuma nasan cewa duk wani kariya tsuhuwa ta tanadar maka dasu tun kana karamin yaro har izuwa yanzu,,,</p><p> San nan ina sane da duk wani gudun mawar da mijin mahaifyar ka ke yima,</p><p> Nikaina ina da wata yar alaka da shi wanda bakowane yasani ba kasancewar shi malam din mutum nei mai gaskiya da rikon amana,</p><p> Kuma inajin dadin yadda ka dauki malam din tamkar mahafin ka,,,,</p><p> Kakula ka kuma kara kula sosai da al,amura, su</p><p> Kaga yan uwanka da ke turai sam ban gane ma komai ba gamay da karatun da sukaje yi a can turai din</p><p> banda dan banzan kudin da nake ta tura masu,</p><p> Inbadon Allah yayini nai karfin arziki ba da yanzu na durkushe kasa warwaras,</p><p> Kuma mahaifiyar su bata son sam ayi mata zancen su,, ido nasa masu ita da su</p><p> Yakare maganar nashi yana hade wani irin malolon bakin ciki,, da ya tokaro mai a makogwaron shi,,,</p><p> Duk sai dan yaji badadi azuciyar shi,</p><p> Ada yadauka cewa uban bai damu da rayuwar shi ba sam,</p><p> Amma yanzu sai yake fahintan cewa ashe duk wani motsin shi mahaifin nashi yasa ni halarci ne kawai yake nuna rashin ko in kula gaban hjy,mama,,,</p><p> Muryan Abba ta dan dawo dashi seti,</p><p> Yace gamay da yarinyar da nai ma magana badiyar kowa bace illa diyar Alhaji abokina kuma amina,</p><p> Wanda ya nuna min cewa yana son hada zuri,a da daya daga cikin yara na da nashi,</p><p> Hakan yasa naga ba wanda yadace da wanan hadin sai kai,</p><p> Don duk cikin ku ba wanda zan iya tunkara kai tsaye da wanan zancen sai kai </p><p> Duk da kaima din bawai zan tursasa ka akan dole sai kayi bane ,aa kawi in kaga zaka iya sai kaje kuga juna da yarinyar intayi maka shi ke nan</p><p> Ahmad yadan dukar da kanshi kasa yace a,a Abba basai naje ba idan yariyanyar tayimaka is ok banda matsalar koma ni</p><p> Da mamaki mahaifin ke kallin shi wanda bai,taba zaton abin zaizo mai, cikin sauki haka ba</p><p> Hakika babana kadai halas ne tabbas nasan ka gado halarci gurin iyayen mu sosai</p><p> Don bakowani yaron wanan zamanin bane za,ayi juyashi cikin saukin kai haka ba</p><p> Tundai yadda kake jin kanka acikin lokacin ka, hakan ga, ga,kudi ga ilimin kowani iri katara,,</p><p> Nandai yabar komai wurin Alhajin nashi, akan yayi duk yadda yakamata don shi baida lokaci wada tace na kanshi yanzu,,,</p><p> </p><p> Abuja yawuce ranan inda yabi jirgin da yatashi marance zuwa birnin taraiyan,</p><p> Saboda mr William's jirginsu zai yi saukan asuba ne,,</p><p> </p><p> Komai ya kan kama a can birnin taraiyan inda shugaban ni sukayi farin ciki da wanan masana,antar da za,a kafa acikin kasa don cigaban kasa da al,ummanta,,</p><p> Kwanasu uku suka juya zuwa Dubai don kai takardun rije,jeniyar da akayi da Nigeria,</p><p> Al,amarin auren shi kuwa Alhaji da bashir tare da sauran yan uwa suka gudanar da komai kamar yadda addini da al,ada suka tanada,,,</p><p> Anje kano wurin iyayen amarya anyi komai cikin tsari,</p><p> Ansa lokacin daurin aure nan da sati uku masu zuwa </p><p> Don mahaifin nata yace yafi son taje can tayi azumi agidan mijinta,,,,</p><p> Duk wanan zancen hjy mama bata da labari saida aka tsaida komai na buki sanan yayan nata ta bugo mata,</p><p> Ga hauka irin nata aiko saita hau fada tana cewa an munafunce ta,</p><p> Ai diyar yayanta mace wace ta ke tayar wa taso hada auren ta dashi amma shine yayan nasu zai masu wanan cin layin</p><p> Hauka iri iri da zagi anjishi gurin hajiya mama,</p><p> inda take cewa ita ba ruwanta da wanan auren cin amana da yayan nasu yayi,,</p><p> Komai cikin mutunci aka,yishi tare da yan uwa da abokan arziki </p><p> Inda ango nacan Dubai yana yin sha,anin gaban shi,</p><p> Bashir ne yake gudanar da komai da yakamata ango yayi</p><p> Hjy tsohuwa tayi bakin ciki sosai da akace yar uwan hjy mamace Ahmad ya aura kuma tayi fada har tagaji inda akaita bata hakkuri,</p><p> Daga karshe tayi waya da Ahmad din yakwantar mata da hankali har ta dan huce, </p><p> Amma badon ta so ba yaghana dai batace komai ba ga al,amarin .</p><p> </p><p><br /></p><p> A saudiya kuma muna can abin mu munata harkokin gaban mu don ba wani aiki mai yawa da muke yi kamar da</p><p> Don tunda muka samu wanan aiki da hajiya laila tai muna hanya aikin gidan sheriff din mu</p><p> Agaskiya mun rage wahala so sai bakamar daba don yanzu ko abinci bai muna wuya</p><p> yanzu duk yan gidan mu sun,dawo da aikin su nan gidan </p><p> saboda aikin da za,ayi na abincin azumi dana lokacin aikin hajji , watau abincin Karama,,</p><p> A, yau muke sa ran dawowar sherrif din mu daga dogon tafiyan dayi nakusan wata guda, zuwa gida Nigeria da kuma kasashen larabawa ta tsakiya,,</p><p> Munyi aiki sosai saboda dawo wan nashi,,,,,,</p><p> , aikin kamar su ,,gyaran gida zuwa yin abinci mai kyau da kula da dabbobin gidan, saboda kada sheriff yace mun barsu da yunwa </p><p> Wanda agaskiya da yana nan da bai nan duk gudane muna kula da komai tamkar yana gari,,,</p><p> Don shi kuma ,akidar shi da ya iso daga tafiya in yayi, gurin dabbobin shi zai fara zuwa yadan diba lafiyan su sai dan yi wasa da su kadan san nan ya shige gida,,bai kara fitowa indan ya shige,,</p><p> Yau ma hakance ta kasance ina wurin da nake kiwon tsuntayen</p><p> Jiminan da ake kiwo a,gidan tana miko min wuya ta ina tsokanar ta ina ta dariya dagani sai tsutsayen a wurin,,,</p><p> Dariya na nake tayi hankali kwance don ganin tana son ta tsakwace min hannu niko ina cirewa cikin sauri,,,,</p><p> Kamshi yan company al,rahab naji duk ya cika min hanci na </p><p> Ko ban waigaba nasan Sheriff ne tsaye a wurin,</p><p> Don ni Har yanzu nauyin shi nake ji sosai tun lokacin da yasan cewa na fara period, ban son in,ganshi,,,</p><p> A,hankali yataka har zuwa inda kejin Akun shi yake,,</p><p> Sannu da zuwa nadan yi mashi sama sama lokacin yana magana da Akun na,shi,,,</p><p> Saina dan saci kallonshi naga yadan ramay har da baki yadanyi, kadan </p><p> Ganin bankalin shi naga tsuntsun yasa nadan juya ahankali don in,tafi,</p><p> Zan wuce shi naji muryan shi yana ce min ya jikin hajiyan mu,</p><p> saida nai mamakin jin wanan tanbayar daga bakin sheriff din na mu daidai wanan lokacin, dayake tare da gajiyan tafiya,,,</p><p> Nace mai taji sauki </p><p> Yace min, ,I hope tana ganin likitanta har yanzu nace mai </p><p> eh, kawai</p><p> Cikin gudu gudu nabar wanjen,</p><p> Don kada yakarayi min wani tambaya kuma,,,</p><p> Yagane ni sarai kunya shi nake ji </p><p> amma dai shi ina ruwan shi tunda yasan cewa mace nake</p><p> kuma ai dole inyi wanan abin,,,</p><p> </p><p>Bayan yadawo da kwana biyu mukayi baki daga Nigerian </p><p> Sai murna nakeyi da rawar kafa ganin ga mutanen Nigeria sun zo</p><p> Don ji nakeyi kamar zasu bani labarin inna na,,,,,</p><p> Sunkai su goma maza da matan su </p><p> duk da mu bamu fahinci komai ba saidai munga ana ta gyara wuri </p><p> kamar irin dakunan dake rufe ba kowa acikin sh, kuma ba ko,,yaushe ake bude su ba,,</p><p> Sai gashi Yau ,duk an bude su ana ta gyara ana sa wasu kaya kamar na kwalliyan mata aciki, su,,,</p><p> Nidai ban fahinci komai ba </p><p> Sai kusan yamma zamu tafi gidane mama may abinci take ce muna wai muzo da wuri gobe saboda munga anyi baki yan kawo amaryan sherrif din mu daga Nigeria,,,,</p><p> Amarya na kara maimata maganar na ta,,,,,,,,</p><p> </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 14:25] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 4⃣0⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎 </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Murna da annashuwa sun tabbata ga mutunin da tunanen hisabin Allah ya hanashi tara dukiyan ta hanyar haramu,,,,</p><p><br /></p><p> Yan Huguma groups da Teema luv group maman fati group, mama nawal group Allah ya kara dauka yasa mugama da duniya lfy,,,</p><p><br /></p><p>Almost true life story,,,,</p><p><br /></p><p> Ta ce min eh</p><p> ai sheriff din mu yayi aure ,itace aka kawo shiyasa muka ga jama,a sun zo daga Nigeria,,,</p><p> A gaskiya munyi murna sosai dajin cewa sheriff din mu yayi aure</p><p> Farin ciki fal azuciyan mu saboda munyi sabuwar uwan daki,</p><p> Duk da ba musan halin taba mun dai yi murna da hakan,,</p><p> Ranan cikin farin ciki muka bar gidan muna jin dadi</p><p> Muna zuwa gida labarin da mukaje ma hajiya dashi kenan yau </p><p> Duk da bamu san ko wace ce, amaryan ba daga cikin bakin da,su kazo,,,,, </p><p> Saida muka gama komai muna zaune sai Rugaiyya ke min ita gaskiya bata ga alaman amarya daga cikin bakin da suka zo ba ,,,</p><p> Saboda may kikace haka inji yumma </p><p> Naga duk kamar ba yara bane kuma babu wace tadan nuna alamar lulubi ko wani dan jin kunya kunya, hakan ga kamar yadda amare ke yi,,</p><p> Ina gefe ina gyarawa hajiyan mu kayan wanki da nayi mata tun daren jiya </p><p> Yau da safe ban samu gogewa ba,</p><p> Hiran su yasa nadan shiga tunane cewa aiko koni din banga alamar wata yar gaye ko amarya wani sign na amarya ba cikin bakin,,,,</p><p> Sukaina ce tace ita,ko gani takeyi kamar wanan bakar mai dan rawan kan nan itace amaryan </p><p> Don taji lokacin da take cewa don may za,a ajeta dakin kasa </p><p> Ita tafi son sama tare da na sheriff,</p><p> Sai wata mata daga cikinsu tace ai tunda nan yabaki sai kiyi hakkuri dashi hakana</p><p> Taji ana cewa Nafisa don Allah kibi wanan mutumin asan nu kin daifi kowa sanin yadda akai wanan auren ,,,,,</p><p> Ki diba fa shekara nawa kina zama agida kuma kiji yadda kaunar mahaifinki tanuna hassadan ta da auren naki</p><p> Yanzu duk wani jidakai ko wani girmankai da iya boko irin naku yakare</p><p> Indan har kina son wanan daulan yafita hannuki kina ji kina gani to bissimillah ki ga ki ga ,,,, </p><p> Bata karasa maganar ba taga ina falon ina hada masu abinci sai tai shiru</p><p> Banji karashen maganar tasu ba inji Sukaina,,,,</p><p> Cabdijam inji Anty Rugaiyya </p><p> inko har wanan din itace matar gaskiya wata killa ba shi yabide ta kamshi ba,,,</p><p> Duk hiran da suke yi ina jinsu sai nazarin maganar nakeyi</p><p> Karshe na nisa nace koma dai may,ye aishi ya, auro abinshi mukan namu aiki mu bar masu guri,,,</p><p> Can cikin dare mun fara barci sai kawai muka dinga jin ihu har na tashin hankali,</p><p> Nai zubur zan tashi infita sai hajiyan mu tace min walahi duk nafita dani za,a hada </p><p> Tace min Askarawa ne da yanbagaladi suka kawo samamay yau shiyan mu,,</p><p> Wata kila watace suka gani suka biyo ta har nan don suka ma</p><p> Jin haka duk mukasha jinin jikin mu don tsoro, daidai kofar mu suka tsaya suna ta buga ma wa, yanda suka kama tsawa,</p><p> Muna labe munyi shiru kamar ruwa yaci mu ba wanda yayi ko dan guntun motsi cikin mu</p><p> Hakan da suka ji tsit yabasu damar wuce don suna zaton ba takari acikin gidan ,,,,,</p><p> Don da datakari da masu shi sunji tsoro sun fito dagudu, suna batun tserewa,</p><p> Amma jin shirun dasukayi unguwar tamu yayi,</p><p> yasa suke zaton sauran gidajen duk na,larabawa ne kawai,ba wani sauran takari wajen,,,,</p><p> Munajin tashin motocin su muka firfito, daga inda muka boye,saida wasun mu suka kewaya don tsoro,,</p><p> Nice, ta,farkon fitowa wajen gidan mu</p><p> don muga kowace ce aka kama daga cikin ,</p><p> Duk da gari bai karkare waye ba,</p><p> Amma mun,gane cewa lawisa ce aka kama</p><p> kuma ita lawisa din nan tanada diya biyu,mace da namiji,,,,,da ta samu dawani balarabe</p><p> yaran kuma sun biyo balaraben sosai,,,,,</p><p> Ashe koda aka kamata bada yaranta ba saboda ganin da sukayi yaran farare ne,,,</p><p> Haka muka karasa wanan daren cikin fargaba da tashin hankali,,</p><p> Dasafe kafin in,wuce naje gidan su lawisa na diba yaran nata,,</p><p> Aiko nasamay su zaune yaran suyi kuka sun gaji </p><p> sun hada kansu wuri guda sunyi tagumi zaban tausayi</p><p> Jawo su nayi zuwa wurin hajiyan mu</p><p> Aiko hajiya naganin mu tamike tsaye </p><p> tana,cewa, fadima kina da hankali kuwa </p><p> Kowa baije yadauko ma kanshi wahala ba ke zaki je ki dauko muna</p><p> muna fama da kan mu ,muma tamu ta,ishe mu ,,,,</p><p> Shiru nayi saida nabari tagama magana nace haba hajiya wa yan nan yaran fa suna bukatar taimako a yanzu,</p><p> Sanan kituna wasila fa tana iya kokarinta da mu,</p><p> Idan baki da lafiya muna gurin aiki takan zo tana diba muna ke,,,</p><p> Sauran yan uwana da basu fita ba sukayo kaina ca,,,, </p><p> Kamar zasu cinyeni dan ya,,</p><p> Yaran na takure gefe guda sundan rgumay hannun su ,sun wani man,ne majunan su ,zaban tausayi</p><p> Jawo su nayi nai masu wanka cikin sauri nadauko abinda zan karya kumallona da shi nabasu, </p><p> Har dan abinda zasuci darana saida na hada masu,shi ,sanan nafita zuwa wurin </p><p><br /></p><p> Nikaina nasan cewa yau,na makara sosai, </p><p> Ina fita taxi, Kai tsaye na fito na mika ma mai taxi kudin shi ,</p><p> Duk da naga Almustapha a,kofar shiga gidan namu, kauda kaina nayi gefe kamar ban ganshi ba,</p><p> Don shima yasan cewa bazan gaishe shi ba,</p><p> Fada yafara yi min baiko kai aya biyu bu nadaga mai hannu alamar ya isheni hakana,</p><p> Cikin mamaki yake kallo na yana kuma yaba karfin hali irin nawa ,</p><p> Har shine zan daga wa hannu,</p><p> To yau kowaye min tsaye sai nabar gidan nan ,haka yake fadi azuciyar shi,,,</p><p> Na ci gaba da magana ina cewa shike nan don muna aiki bamu da incin kanmu ko wani lokaci na kan mu,</p><p> Ai yakamata a,dinga muna uzuri aduk lokacin da aka ga mundanyi wani abu bawai adauki matakin da babu dalili ba</p><p> Da in tsaya kana mari na ko zagina duk lokacin da kaga,,,,</p><p> Ban samu karasawa ba naga Sheriff's atsaye gaban mu yana muna wani irin kalon mamaki,</p><p> Mari mari fa,, Almustapha ,Subahanalla subahanallah ka doki mace macen ma,,,,,</p><p> Sai ya kasa karasa wa, naga kawai ya dunkule, hannunshi ya dan daki gudan da shi yana fadin subahanallah,,,</p><p> Nikan nasa kai na wuce cikin gidan ina jin yana cewa yaushe kai wanan aikin bansani </p><p> Ko kana dukan mace ita wanan din may zaka daka acikin ta,,,</p><p> Wuce wa yayi ciki gidan ran,shi bace dagani kasan yayi mugun, hasale ,yabar almustapha a wurin bakin get din, cikin damuwa,,,,,</p><p> Don ko yaga fushi yau karara a,idon sheriff din,,nashi wanda rabon shi da yaga wanan fushin yadade,,,,</p><p> </p><p> Ban tsaya yin komai ba gurin tsuntaye nafara zuwa sudake da rai na basu abincin su,,</p><p> Don kusan kowani tsuntsu da kalar abincin shi,</p><p> Ruwa kuma akwai wanda nake sama ,magani acikin nasu, ruwan shan da samun kuzari da lafiya,,,,,</p><p> Danaga komai ya kam,mala sai na bar gurin aikin zuwa cikin gida don inyi aikina,,,</p><p> Daidai gurin da dawakai da dabbobin gidan suke yake tsaye ya rike ciyawa a hannun shi yana ba wani dan farin doki karami,,</p><p> Ke yace min cikin tsawa saida naji tsoro wanan kiran,</p><p> Ya,akayi mustapha ya mare ki yaushe ya,mare kuma a ina,,</p><p> Wani tambaya zan ansa daga cikin ukun,,,</p><p> Duk da ina jin kunyan shi yau sam banji ba</p><p> Saboda dama tun da daren jiyan abinda akayi wa lawisa a,kasan ya tayar min da hankali sosai ,</p><p> saboda naga bamu da wani gata ko daraja a, wanan kasan.</p><p> Batare da na bashi ansa ba sai na fashe da kuka mai kuna zuciya</p><p> Yana ganin na fara kuka sai ya rintse idanun shi don bacin rai jiyakeyi kamar a watsa ma garwashin wuta ajikin shi,,,,</p><p> In akwai abinda ya tsana yaga mace cikin yanayin kuka ko ban tausayi,</p><p> Ganin idona rintse yasa shi ya sulale yagudu yabar wurin don bai iya daurewa yana jin wanan sautin wanan kukan a rashi ,,,,,,, </p><p> Ni ko,kukan da , samun yin ,shi ,shiya dan sa naji wani dan sanyi azuciya na</p><p> Koda nagama kukan na dan kai dibana inda nagan shi tsaye sai naga wayyau, ba kowa wurin,</p><p> Haka na wuce nabar wurin jiki ba wani kwari don jinakeyi kaman ban iya tafiya,, </p><p> Ashe da sheriffudeen din mu yabar inda nake tsaye komawa yayi sama yana tunane azuciyan shi,,</p><p> May yasa almustapha zai dauki hukunci mai tsanani akaina,haka har da mari mari fa,,,,,,,,</p><p> Wurin nabari zuwa ciki don inyi aikina,</p><p> Ina shiga cikin gidan sam na manta cewa akwai bakin, agidan mutanen Nigeria dasu kazo jiya,,, saboda tashin hankalin da nake ciki,</p><p>Wa,daga cikin bakin,suna falon gidan zaune su,nata har kokin su,</p><p> Sai narasa ta ina zan soma aiki na ma , tsayi nayi wuri guda,,,</p><p> Don ku san ko, ina akwai mutane a falon,,,,,</p><p><br /></p><p> Ina nan a tsaye tsakiyan falon sai naga wata yar dattijiwan takari bakuwace daga cikin mu, ta zo inda nake tana min murmushi ,,,,,</p><p> Cikin girmamawa take magana da harshen</p><p> larabci takecewa tundazu take jiran shigowa na ,,</p><p> tai min sannu da zuwa,</p><p> Tace min itace mai kula da aikin goge goge yanzun agidan</p><p> Da duk wani aikin da ya kushi cikin gida,</p><p> </p><p>Mamaki ne ya kamani don naga aiko jiya nice nayi wanan aikin,kafin muje gida,,,</p><p> Sai,gashi jiya zuwa yau da safe wai an canza wata mai yi,,,</p><p> Kenan an,dakatar dani daga aikn ake nufi ko,,,</p><p><br /></p><p> Daidai zan fita inbar falon naji mama mai abinci nace min inzo indiba ko abincin da suka dafa yayi ,,, kalonta nayi itama cikin mamakin</p><p> Don suna son su ba mutane abin kari,,,</p><p> Nuna kaina nayi ina waigen gefe da gefe na ina, nufin ni takewa magana kuwa,,</p><p> , tace min eh,,, dani take</p><p> Ba mussu nabi bayanta zuwa inda naga tabi, kitchen ta nufa,</p><p> Abinci ne na alfarma aka hada masu kyau da dadin gani,sai kamshin dadi ke tashi,,</p><p> Tana kokarin bude min kulolin abinci nace mata la,la,la ta bari don Allah komai ya yi,</p><p> Mama mai abinci tace min in bari ,in,diba in gani, in, akwai wanda bai yi ba sai su sake,dafa,wani,,,,,, </p><p> Nace mata yayi haba mama, yau kika fara wanan aikin,</p><p> Ta danyi murshi kawai na nuna kula da girmamawa</p><p> Niko duk mamaki ya cika zuciyana ga dinbin tanbaya min fal a,rai,,,,</p><p> Bayan anjera komai wurin very neat, ,</p><p> Rugaiyya tace min inje in fada ma mutanen gidan cewa table is ready,,,</p><p> Bayan mun fita Rugaiyya ke min bayanin cewa yanzu aikina shine kula da duk wani al,amarina aikin cikin gidan, nan nice da alhakin kuwa, dashi,,,,</p><p> Don Almustapha ancanza mai wuri zuwa can company</p><p> </p><p> Nace ma Rugaiyya yanzu duk yawan mu sai nida nake yar karamar ku za aba wanan aikin</p><p> Wanan aikin aida mama mai abinci yadace bani ba</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎🐎</p><p>[10/4, 14:26] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 4⃣1⃣</p><p> BY </p><p>🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> A, kulun muna gode ma Allah Subbahanahu Wata,ala daya Halice mu a matsayin musulumai,</p><p> Ya Allah muna kara gode maka da ka bakayi mu kafirai ba,</p><p> Allah yakara ma musulunci daraja da daukaka 👏👏👏</p><p><br /></p><p> Allah ya kara rufa ma duk al,uman musulumi na duniya asiri</p><p><br /></p><p> Almost true life story</p><p><br /></p><p> Maimakon in yi farin ciki da cigaban da nasamu ,</p><p> Nikan hankalina yana gurin irin wulakancin da akeyi wa yan takari,,</p><p> Ga lawisa ta wuce tabar yaran ta acikin duniya, batare da sanin makomar su ba,,</p><p> Shin wai may yasa ake zuwa wanan aikin mai wahalar tsiya ,</p><p> Wahalar da ba riba ko kadan sai in Allah yataimaki mutum,, yatar fa wa garin mutum nono to shine zai tsira da dan wani abu,,,</p><p> Duk abinda aka girka a,gidan ranan , saida na sdibar wa,su hajiyan mu da yaran nan, na lawisa,</p><p> Tun lokacin tashi baiyi ba nabar gidan aikin na mu,</p><p> Sauri nakeyi zuwa gida don inkai ma hajiya abinci suci,</p><p> Natafi da niyar gobe insha Allah zan daure in ma sheriff din mu magana ina son ataimaka mu,na indinga zuwa gida da wuri don indan kula da hajiyan mu da yaran lawisa,,, ,,,,,</p><p> Cikin sauri sauri na isa gidan tun ban shigaba nake jin dan she,shekar kukan yar macen yarinyar,</p><p> Wacce ban ko san sunan ta ba ma </p><p> Da, sauri na karasa shiga ciki don jin ko maya sami yaran</p><p> Hajiya na zaune gefe tai tagumi, sukuma yaran sun dan tsuguna daga bakin kofa shigowa cikin gida,,,</p><p> Banko kalli hajiya mu ba wacce ta nuna mamakin ganina nadawo yanzu </p><p> Tun lokacin dawowar mu baiyi ba,</p><p> Yaran nake tambaya hankali tashe komay yasamay su suke kuka</p><p> Ganin danayi basu da niyar yin magana,,,</p><p> yasa na wuce ciki kawai tubewa nayi ,nacire dogon rigar da nasa sama,</p><p> Nakoma dagani sai wata yar doguwar riga English wear kalar sky colour ,wace duk ta man ne min jikina rigar irin na yan Brazil's din nan ce </p><p> Sai kaina da na daure dawani ribon mai kama da gashin mussa, kalar fari kwal</p><p> wani dogon yan kune fari ne a,kune na, takalman kafana dama munfi sa cover shoes, don , muji dadin gudu idan an biyo mu,,</p><p> Plates najawo guda uku na fara zuba ma hajiyan mu abincin ta kala kala ,nakai mata </p><p> Nadibar ma wanan yaron nashi saida na cika mai plate , nabashi tare da abin sha,</p><p> Na hada muna nida wanan yar yarinyar a plate guda,</p><p> Cikin lalashi da hikima nasamu yaran suka ci abinci , </p><p> Har suka dan sake jikin su dani, inda nake tambayar su sunan su,</p><p> Namijin yace min sunan shi umar macen kuma Aisha,,,,,</p><p> Saida naga hankalinsu ya kwanta sanan natashi na gyara wurin da mukaci abincin mu tsab ,,</p><p> Umar da Aisha,naja zuwa gidan su, don indan diba cikin kayan su koza a,samu wani abinda zai masu amfani ,</p><p> Muna fita naga yan kabilar larabawan dake gurin suna ta kallon mu,</p><p> Duk da sun tausaya ma yaran amma basu iya yin komai, gamay da uwar tasu,</p><p> Wani halarci da suke muna shine, indai kana zama a unguwar su baza su taba tona bakar fata ba in har yan bagaladi sunkawo samamay shiyan,,,,</p><p> Acikin gidan na lawisa naga wasu hotuna da takardun ta sai yan tsun makaran kayan ta dana yara,,,</p><p> Nadan tsinto masu masu dan kyau daga cikin kayan,,</p><p> Muka fito gidan,,,,,</p><p> Nasamu su Rugaiyya sun,dawo gida ko, takara zo muna da wani abinci wanda zamuci da dare,</p><p> Au ke fadima har yanzu yaran nan natare da ke,</p><p> Ashe shiyasa yau kika bar wurin aiki da wuri ,</p><p> don ki dawo wurin yaran na,ko, fadima baki da tsoro ko,,</p><p> Aiko kin dauko muna wani sabon magana wlh, bamu iya da kan muba shine kuma zaki jajibo muna wani sabon taulali,,,</p><p> Saida na bari ta gama maganar ta , </p><p> Sanan nace yanzu idan mu bamu taimaki yaran nan ba wazai taimaka masu bayan mu, awanan uguwar</p><p> Kutuna cewa muda lawisa duk guda ne tun da itama takari ce,kamar mu </p><p> dakuma irin taimakon da tai muna lokacin da mukazo nan gurin,, bamusan kowa ba,,</p><p> Hajiya ce ta katse min zance na da cewa ai sai kisan yadda zakiyi dasu,</p><p> Don nidai ba ruwa na gaskiya, </p><p> mukan mu , ba musan yadda zamu kasan ce ba,, da tamu rayuwar ba balle</p><p> Allah zai dibe mu nidasu insha Allah na katse zancen kowa,,, </p><p> daga haka ban kara ce ma,kowa, komai ba</p><p> na,tashi nafara tanadar wa yaran da inda zasu rika kwaci,</p><p> Ina gamawa na wanke masu yan kayansu da zasu sa, gobe, don duk kayan nasu na da dauda,,,,</p><p> </p><p> Washegari saida naga na tanadar masu da komai sanan na bar gidan zuwa aiki,,,, zuciya na nata min sake,saken yadda zan ma Sheriffudeen din,mu bayanin akan taimakom da nake so ai min, don in samu kula da yaran nan,,,,,,</p><p> Ina shiga gidan Kai tsaye gun tsuntsaye na,na nufa ,,,</p><p> Don ina ba,su abincin, su, </p><p>Saboda sune ban son makara zuwa wurin aikin, saboda sam ban son barinsu da yunwa,,</p><p> Gashi kuma mun saba da juna,,,</p><p> Amma ina zuwa wurin naga wani dan saurayin bakar fata bakon fuska, ne, agidan, yana watsa masu abincin su,,, </p><p> Tsaye nayi nisa da shi,kadan da inda yake ina kalonshi cikin mamaki,</p><p> Daidai lokacin naji karan bude kofar baya nadan waiga inga kowaye ke fitowa,,,</p><p> Sheriff din mune tare da wata bakar mata matar bata da wani tsayi gajera ce mara jiki,</p><p> Duk da ta lailaye jikinta da lafaya mai ruwan yellow sai dan adon duwatsu churculate colour dake jikin lafayan</p><p>Ina iya hango gabanta kamar ba komai, hannunta zanen kumshi ne irin namu na yan Nigeria,, yayi baki wulk</p><p> Takalmin ta ma charculet ne amma mai dan tsinin duduge, wanda nake ganin takalmin ya taimaka mata wurin karin tsayin ta </p><p> Sai wani kamshin turare kamar na turara garwashi da takeyi mai dan dadi wanda ban iya fassara kamshin shi,,, abindai siri ne kawai,,,</p><p> Gefe guda nadan ja na tsaya, don in basu hanya su wuce </p><p> tare da masu barka da safiya,</p><p> Batare da ya kalleni ba ya ansa min a dakile</p><p> Wani irin kallo yaimin mai alamar, may nake yi anan ,,, kaina aduke nayi cikin gidan takofar da suka fito,,,,,,, </p><p> Idon shi naga dan takarin nan mai ba tsuntsaye abinci,</p><p> Wanda baiko kula da inda nake ba, ma tunda na zo</p><p> Saida yaga shigewana yadawo da idon shi kan hanya,,,</p><p> Ita wanan din wace,ce ita habibi,</p><p> Matar ke tambaya ,batare da yabata ansa ba ya wuce yabar ta, tabishi da dan saurin ta,,,</p><p><br /></p><p> Yau kida na shiga cikin gidan banga bakin mu ba </p><p>Sai gidan ya koma shiru ba kamar kwana biyu da akai yawa ba,</p><p> sai mu kadai ne ke ta zirga zirgan mu a cikin gidan,,,</p><p> Daidai lokacin da aka gama, hada komai na abin karin safen su bisa, dinning table din, ,,,</p><p> Lokacin su ma suka shigo cikin falon kai tsaye inda table din yake ke suka nufa,,,</p><p>Maigidan ne a gaba, matar na binshi</p><p> Yaja kujera guda ya zauna,,, don suci abinci</p><p> Inda yake zaune naje kusa kadan dashi,,,</p><p> Ina gyara wasu cups da suka danyi nisa kadan da shi,,,</p><p> gyara cups din na keyi ashe kamshin turaren zam,zam lau,, da,na dan murza a jikina yana tashi ban sani ba,,</p><p> Jin kamshin yayi har cikin zuciyar shi,,,, idon shi lunshe kadan,,, yabude su a,hankali</p><p> Jin yake Duk kamshin ya wani sukur,kuta shi wanda hakan ba halin shi bane,,,,,,, cikin dibara ya kauda kanshi gefe guda,</p><p> Yace min cikin larabci in barshi kawai zasu iya hada abincin, ai </p><p> Saidai indan ba ka saurara da kyau,ba bazaka ce anyi magana a,wurin ba,,, saboda tausa muryan dayayi</p><p><br /></p><p> Ina kallo yadda matar ta cika plate fam da abinci,,, wai ita zataci,,,,</p><p> Cikin gidan nashiga don in di ba ko an,gyara masu, dakunan su duk na gidan ,,,,</p><p> Aiko kafin in,sauko kasa matar har ta cinye kusan rabin abincin plate din da ta zuba,,</p><p> Idona na fitar waje don mamakin ta</p><p> kallon abinda nake kallo sheriff din mu ke yi,, shima</p><p> Bin inda idona yai saiti yayi,,, aiko sai yaga plate din matar nake kallon ido waje don mamaki,</p><p> Kara diban abinda nake mamakin yayi,</p><p> Ai, shima da ya lura ta cinye wanan tulin abincin saida mamaki ya kamashi,,,,,,</p><p> Tana gani na tace min inzo in zuba mata juice a cup,</p><p> Hannu yadaga mata alamar a,a,</p><p> Yace mata she is not a Made,,</p><p> Cikin larabci yace min in bar wurin,</p><p> Tana son tambayan shi to amma ba fuskan hakan,,,</p><p> </p><p>Duk Jina yau nakeyi , kawai ba wani kuzari ,ajikina,don, yau ban yi, wani motsa jiki ba ,</p><p> Saboda aikin komai banyi ba agidan , don akwai masuyin komai da nakeyi a,da,,,,</p><p><br /></p><p> Almustapha ne mukayi kicibis da shi daidai fita wurin kofar shigowa falon , gefen shi nabi,</p><p> Zan wuce shi ba tare da na gaishe shiba ,</p><p> Yace min tun jiya yake bida na don yai min wani dan bayani gamay da aikina, da zan rika yi yanzu,,,,</p><p> Amma saidai ya tambaya ance mai natafi gida da wuri jiya,,</p><p> Kuma yaga, ai, lokacin tafiyan mu baiyi, alokacin, da ya tambaya</p><p> Ko kallon shi banyi ba nace mai</p><p> Sai acire kudin da na wuce kafin lokacin tashi nayai a,cikin albashi na ko,</p><p> Don abinda naje yi gida yana da muhinmanci gareni sosai,,,,,,</p><p> Duk abinda mukeyi da ansan da nake ba shi idon sheriff din mu na kan mu saidai baijin maganar mu sosai saboda yar tazaran dake tsakanin mu da su,</p><p> Amma dai ya fahinci ba jittuwa a,tsakanin mu,,</p><p> Shiku Almustapha galala, ya saki baki yana kallon inda nabi da ido,</p><p> don kuwa nagama bashi mamaki,</p><p> Yana kuma tunanin waidama haka nake banda kunya ashe,</p><p> Kokuwa, yanzune nakoya a sanadin marin da yai min,</p><p> Don a,iya sanin shi da ni, ina da tarbiya da kuma girmama naga ba, dani,</p><p> </p><p> Karar wayan sheriff din mu da yadau ruri yadawo dashi cikin hankalin,shi,, </p><p> A,hankali ya mike daga kujerar darnnig din batare da ya ko kalli inda matar take ba ya,</p><p> Yajowo cout din shi ya,aza saman farar rigan dake jikin shi ,yanufi hanyar fita falon ,</p><p> Cikin yanayin yin waya, yana wayan yana tafiya zuwa wurin da aka Parker motar da zai shiga yau,</p><p> Almustapha na bayan shi rike da yar briefcase din shi baka wace ke dauke da takardunshi da laptop din shi,</p><p> Kaman ance min in,fito daga cikin wani kofar da zai sadaka da garden din gidan , </p><p> don indiba aikin da akayi yau wurin,</p><p> aiko na,hango,shi zai fitan ,,,,,</p><p> Da sauri na karaso inda suke dai, lokacin ya bude motar zaishiga,,,,,</p><p> Ina dan maida nunfashin </p><p> saurin da nayi nakara so wurin motar,</p><p> Yana gani na ,naji yana sallama da wanda yake wayar dashi,</p><p> Juyo wa yayi cikin mamaki yana kallona, da mamaki,</p><p> Cikin ladabi nake cemai taimakona na nake son yayi don Allah</p><p> Sai ya gyara tsayuwar shi da kyau don ya saurare ni</p><p> Nace mai don Allah alfarma nake nema don indinga tashi aiki da wuri saboda ina,da yaran da nake kulawa dasu da kuma hajiyan mu,</p><p> Cikin mamakina da ganin iya karfin halina, na tun karar shi, danayi kai tsaye babu shakka komai yake mamaki na,,,</p><p> Nace koda za,a rage min yawan albashi nane zan yarda indai za,abarni in tafi da wuri,,,,</p><p> Kallon mustapha yayi da ,alamar su tafi kawai,</p><p>Ya shige mota batare da ya bani ansaba ,,</p><p> Sukabarni tsaye kimkam,,,motar nabida kallo,</p><p> Koda na waigo don in koma cikin gida sai kawai naga matar danake zato itace amaryan sheriff din mu duk da basu dace ace miji da mata bace,,</p><p> Tsaye tana min wanu irin kallo,</p><p> Batare da na damu da kallon taba nazo shigewa cikin gida,</p><p> Tsawa ta daka min cikin turanci take min magana, </p><p> Sai nikuma nakama yi da larabci ina fadin ni,banda lokacin sauraren ki je ga mijin ki can kamar yadda akewa wanda baijin yare,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>[10/4, 14:27] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 4⃣2⃣</p><p> BY</p><p> 🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p><br /></p><p> Idan bawa yana sallah ba wani hijabi tsakanin shi da Allah indan har ya kyau,tata sallah shi, don haka yan uwa mudinga tsananta addu,oin alokacin da muke sallah domin biyan bukatan mu,,,,</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,,,</p><p><br /></p><p> </p><p> Shike jan motar Almustapha yana gefen shi zaune sun fito ne da niyar zuwa diba shagunan saida kayan su don ana son ayi gwanjon su , </p><p> Za,a,shigo da wasu, sabin yayi ,</p><p> duk shekara kusan haka shagunonin keyi a kasan saudiyan,</p><p> Ayi canjin kayan shago zuwa sabbi, da ake yayi,</p><p> Dai inda go slow ya danyi yawa suka dan rage saurin da sukeyi,</p><p> Sheriff Ahmad ya,kauda shirun da ke cikin motar, </p><p> Batare da ya kalli mustaphan ba yace mai </p><p> Ya akayi har ka mari wanan yarinyar ,</p><p> Riban may zaka samu da ka doke,</p><p> Shinka san cewa darajanka da kiman ka sun rage agareta da ma wasun ta,,</p><p> Cikin rudu almustapha wanda ranshi ke jagule dama ,</p><p> Yace kuskure ne wlh akasamu , bada niya namare ta ba,a sali, ma dai kawai hakan na tsinci kaina da ai,katawa </p><p> Wanda danasani ne ke min gizo ko yaushe zamu hadu da yarinyan nan</p><p> Ganin motocin da suka rage yawa yasa shima kutsawa ta cikin su yadauki hanyar zuwa maicizo, don tanan zasu fara,,</p><p> Mace wani halittace, maidaraja da tausayi, da kuma,,, daukakawa ,saboda muna da uwaye mata muna da kane mata watakila ma watarana zamu haifi diya macen,</p><p> Kaga komai ilimin mace ko mai waye wanta sai ta bidi taimakon namiji,,,,,</p><p> Nitun ina karami ina jin tausayin tsohuwa saboda ban iya manta wahalar da ta sha dani,</p><p> Kayi kokari ka gyara tsakanin ka da wanan yarinyar ina ga zaifi,ma sauki,,,</p><p> </p><p> Kulun ina kokarin kare aikina kuma ina komawa diba yara da hajiya cikin lokaci,</p><p> Abinci kuma ba ,a hana min diban yadda nakeso inkai masu, abinda banyi shine dibar abincin da ba,adafa ba,,,</p><p> </p><p> Kowa yasan yadda garin makka ake kwantsama rana kamar kace wayyo Allah </p><p> Yau rana a,keyi sosai don haka mutane sun samu wuri sundan lalabe </p><p> Duk da zafin ranan da akeyi bai hana masu niyar fita wurin ibada yi ibadarsu ba,,,</p><p> Saboda kowa yasan cewa kulun cikin baki garin yake masu zuwa ziyara,</p><p> Da wuya ai ruwan saman da yakai sau biyar a shekara cikin makka,,,</p><p> Zafin ranan yai yawa da alamar yau akwai rabon ruwar sama ke nan agarin,,,,,</p><p> Iska ce a,kafara masu kaya nata har,harada kayan su ,don kada ruwan ya samay su,,,</p><p> Daidai wànan lokacin muma muna saman titin,57up ,,</p><p> Almustapha ne ke jan mu yau sai nida ke gefen, driver </p><p> Amaryan sheriffudeen din, mu tana baya zaune tana ta latsan wayan da,ke hannun ta,</p><p> Yau,ce ranan farko da muka fara fita da ita,</p><p> Itamadin inga fitar ta kenan na farko,</p><p> Taso fita ita daya amma sheriff yace baiyar da ba dole duk inda zata saidani,</p><p> Wanan dokan yai mata zafi sosai,</p><p> Don agabana akai case din ,</p><p> Tafito cikin shirinta tasa wasu kananan kaya tana tako daidai , </p><p> Shikuma yana zaune falo gaban laptop din shi wanda zance shine abokin hiran shi koyau she, </p><p> Daga waya sai laptop zaka ganshi da su yana latsawa,</p><p> Karan takalmanta dayaji yasa shi dan dago kan shi a,hankali ya kalli inda take saukowa a,step din,</p><p> Kan shi ya kawar daga, kallonta ,, sai kuma ya cigaba da abin da yakeyi, batare da ya,waigo ta, ba,,</p><p> Ita ko azatonta ta burgeshi ne hakan da take yi,,,</p><p> Saida ya bari ta karaso kusa da shi cikin rausaya da rangwada irin na yan bariki,,</p><p> Habibi na shirya fa, zantafi,</p><p> Batare da ya kalli gefen da take tsaye ba yace mata,</p><p> Ina fa tace mai wurin gyaran kan da nace ma da kuma , yin wasu yan sayaya,</p><p> Still kanshi na ,a duke yace a,hakan ko kuwa da sauran shirinki ,</p><p> Tadan dibi shigan da tayi yace ,ahakali taga ai,baida wani illa, yar dogon riga ce sai dan gyalen da ta yane kanta dashi,</p><p> Batare da yakaleta ba yace,,kitunafa nan saudiya ne ba turai ba,</p><p> Ko ba komai kina gaban tushen musuluncin ki,</p><p> Duk da nasan ba,arasa masu irin al,adan ki amma nidai ba,agida na ba gaskiya,,</p><p> Kamar yada , dama na fada maki sharudan zamanki a gidan nan,,</p><p> Gaskiya bazan iya lamuntar wanan irin shigar ba,</p><p> Sanan ki sani fita daga yau ,bake da driver zaku din ga fita ba dolene, kifita, ke da wanan yarinyar mai kula da duk har kokin gidan nan,</p><p> Zamanto duk inda zaki tasani kuma kuje tare da ita, </p><p> Saboda haka na,dauketa wanan aikin</p><p> Ita wanan yarinyar wace wai da za,adinga hadani da ita,,,</p><p> Alamar oho yanuna mata da hannun shi saidai hankalinshi naga laptop dinshi kamar bada ita yake zancen ba</p><p> Yadan dago kai yace mata, idan kuma kin ga hakan nada matsala, zaki iya fita ,din fine,,,</p><p> Fuskanta ya nuna alamar bacin rai karara, ,azuciyan ta ji takeyi kamar tace ta fasa,,,</p><p> saidai kuma har in ta fasa din kanta da yadamayta da kaikayin rashin wankewa ya,zatayi,,,</p><p> Dole jiki ba kwari ta zauna ga dayan kujeran dake falon tana cewa, </p><p> Ina yarinyar da zamu tafi,</p><p> Waya yadauka daniyar akirani sai ya hangoni kusa da su ,nida mai goge gogen falon ina nuna mata, wani aikin da baiyi kyau ba,</p><p> Dayake akwai dan nisa a tsakanin mu dasu, sai yai min alamar inzo da hannu ,nai kamar ban ganshi ba sai matar da muke tare ce ke fada min ana magana dani,,,</p><p> Cikin ladabi na isa gurin da suke,,, batare da yakalleni ba yake min bayani zamu fita tare da matar shine ,zan kaita wurin gyaran kai .</p><p> Cikin ladabu na ansa tare da dan kallon gefen da take ,</p><p> Ko kallon arziki ban samu ba,</p><p> Muje kawai nace mata,</p><p>Kanshi yadan dago dan</p><p>bini da kallon mamaki</p><p> don baiga ko na dan shiga ciki ba, don indan gyara yadda yaga wasu mata na yawan yi,idan zasu fita,,,,,,,</p><p> Tun fitar mu ko kallo na batayi ba, balle muko danyi wani maganar arziki, da ita,</p><p> Almustapha ke tanbaya ina zai kaimu,</p><p> Atakaice na bashi ansa nace mai nabililabilah,</p><p> Batare da na kali inda yake ba</p><p> Nikaina ansar bata bani ma,ana ba,akune na ba,sam daurewa kawai nayi nafada mai,</p><p> Don ban son yiwa nagabana rashin mutunci sam,, </p><p> Amma hakan dai naga damar fada don in fanshe haushi na,,,</p><p> Kanshi kawai ya girgiza cikin wayancewa,gamida basar da disgashin da nayi,</p><p> Shiya dan daure yace min wani road zamu nakara fada mai a tsiwan ce, </p><p> Gaskiya wurin ba laifi don wani kilantacen wurine wanda matane kawai ke zuwa wurin manya da yara,</p><p> mun samu mata da dan dama suna jiran layi,</p><p> Kasan cewan mun dan san juna da wasu daga cikin yaran aiki yasa na danyi muna hanya wata dabata fito aikin ba ta gyara mata kan,</p><p> Aka wanke mata,kafan ta, da gyaran kunbar hannayen ta,</p><p> Muja futo zuwa wani dan babban shago tasai wasu yan kayayaki bukatar ta,</p><p> Kadan,Pad kawai nadauka a shagon kasan cewa lokacin period dina ya kusa zowa,</p><p> </p><p> To a,hanyar mu ta dawowa gidane wanan hadarin yatare mu,</p><p> Sararin samaniya nakare wa kallo yadda lokaci guda yanayi ya canza gari yayi duhu,</p><p> Almustapha jan motar shi yakeyi hankali kwance abinshi,,,</p><p> A,hankali na mayarda diba na kan matar sheriff ta gefen idona, dai lokacin tai magana tun fitar mu, dani tace Allah ya taimake mu wanan yariyar tasan, wasu, tana magana da almustapha</p><p> Tana dan kara leka window motar tace haka ake iska agarin nan,</p><p> Kafin ta rufe baki wata irin iska kamar guguwa ce ta taso tuni wuri ya turnike da kura, </p><p> Cikin sauri duk muka daga glass din motar don kurar ya mamaye ko ina,,</p><p> A, hankali Almustapne,,, yake tuka motar don ko ganin hanya ba,ayi sosai,</p><p><br /></p><p> Matar sherriff duk ta tsorata tace don Allah mudan tsaya har kuran ya lafa, mukara sa gida don gaskiya tana ganin tafiyar mu a haka hatsari ne</p><p> Ganin da nayi zai tsaya yasa nai mai magana cikin larabci, </p><p> Nace mai yasan sheriff yace kada mudade ko ,kuma gashu mun kusa kawo wa gida,</p><p> Umurnina yabi ya ja motar ahankali,, har muka isa gida lafiya,,,</p><p> Daidai isar mu gidan wata iska mai karfi ta kara gwaucewa da ruwa mai karfi yabiyo iskan,</p><p> Hakana balle murfin motar nafuto cikin sauri zuwa cikin gida,</p><p> Iska na kwasar kayan mu duk tsirangalin kafar mu yana baiyana asarari saboda kada kayan mu da iska keyi,</p><p> Atare muka fada falon gidan nida matar sheriff wace ban san ma tana bayana ba,,,</p><p> Don nadauka zata zauna amotane har ruwan ya lafa,</p><p> Wata ajiyar zuciya na saukar yayin da naji rufewar kofar falon,</p><p> Sheriff ne tsaye a tsakiyan falon yana muna wani irin mugun kallo,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>[10/4, 14:28] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 4⃣3⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p> </p><p><br /></p><p>Al most true life story,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Fuska a a daure yake kallon mu, cikin tsawa tsawa yake magana ,</p><p> Ku wasu irin mara hankaline kuna ganin yadda gari ya canza kala ,</p><p> Yanayin da kowa ke gudun shiga cikin sa saboda kariyan lafiyan mutum,</p><p> Shine ku ka biyo cikin shi haka don rashin sanin ciwon kai,</p><p> Cikin hausa yake fadan duk da hausan ba wai nuna tayi masa ba,</p><p> Sau,biyo muna hada ido dashi lokacin da yake ta faman fadan,,.</p><p> Ina noke kaina a,kasa kamar badani yakeyi ba,</p><p> Duk da Cikin fada yake magana sai naga kamar lalashin mu yakeyi ba fada bane yakeyi,</p><p> Sulalewa nayi zuwa cikin gida don rigar da ke jikina ya fara jikewa ,don haka sanyi ya fara bimin jiki ko,,</p><p> Ido yabini da shi yana mamakin irin girman da ya hango nadan kara yanzu, kafin mu shigo,</p><p> Ashe tunda yaga hadari yakasa zaune ya kasa tsaye, hankali a tashe, don baisan halin da muke ciki ba, </p><p> Saidai yayi amanan cewa baza mu biyo wanan iskan ba,</p><p> Saman dakin shi ya tsaya, dai inda zai iya hango ta,waje yana yi yana dan leken hanya,</p><p> Aiko sai gamu cikin wanan uban iskan mun doso gida,,</p><p> Mamaki ne ya kamashi haikan ta yadda muka iya kasadan biyo hanyan hakana ba wani fargaba ko tashin hankali</p><p> Har fitowan mu yana kallon mu da yadda iska ke kwasan mu kafin mu shigo gidan</p><p> Cikin sauri yarigamu isowa falon bayan yariga ya kare muna kallon mamaki ko rashin hankali,</p><p> Itama wucewa tayi batare da tabashi hakkuri ba, don gani take gaskiya ya fara takura mata,,</p><p><br /></p><p> Dakin da aka tanadar min na gidan nashiga , don indan gyara jikina,</p><p> Ina shiga batare da bata, lokaci ba, don dama duk nayi futub da kura gashi kuma na jika kaya na sama,</p><p> Cire bakan rigan da nasa sama na yi </p><p>Nakoma dagani sai dan wandon jens dark blue, na mata wata yar karaman riga pink mai guntun hannu ke jikina,, </p><p> Sai ribon mai kalar baki dana dan daure kaina dashi,</p><p> Nasamu wuri gefen gadon dake dakin na dan baza bakar rigan nawa don yadan bushe kafin in wuce,,</p><p> zaune nake ina kokarin cire takalman da ke kafa na, ahankali ya turo kofan hannu shi rike da tawul fari,</p><p> Ban san lokacin da na mike tsaye ba ina wage wage ko zan dan samu abinda na rufa ma jikina, alokacin ba komai adakin don ban barin kayana agidan kamar yadda sauran ma,aikata keyi,</p><p> Towel din ya jefo min tunda ya gane nufi na ,,</p><p> Shiko aganin shi baiga wani abin da har zan boye ajikina ba ,</p><p> Yar ficir dani kamar mage,</p><p> Juyawa yayi yabar dakin cikin sauri,</p><p> Shi dai tausayi wanan yariyar ke bashi a,rayuwan shi don koda baiji tarihina ba yakan tausaya min duk lokacin da muka hadu,</p><p> A dakin ta yasame ta tana kara gyara kwaliyar da akai mata a wurin akafar</p><p> Cikin dan dakikan lokaci ya kalle gyaran kan nata ya kauda idonshi tamkar baigani ba,,</p><p> Tasowa tayi tana wani rangwada ita adole tayi kwaliya ma miji,,</p><p> Tana batun rungumay shi yace cikin dakiyar fuska maynene haka pls,</p><p> Bana son irin wanan shashancin pls,</p><p> Sha shanci fa kace ,kana ,a matsayin mijina zakace min sha,shanci,</p><p> Nifa Ahmad bangane may kake nufi ba dani yau kusan satina uku kenan agidan nan </p><p> Amma ba wani nuna cewa ni matar kace, balle ,,,</p><p> Bata karasa maganar ta ba daidai lokacin nai sallama dakin dauke da cup din ruwan shayi mai tururi ,</p><p> Dai lokacin kuma wani sabon ruwa yakara gwaucewa kamar da bakin kwarya,,,</p><p> Shayin na gabatar mata ,wanda nasamu gundun mawar harara, </p><p> Bisa tebur din dake dakin na aje mata nafito abina,,,,</p><p> Dakina nakoma don naga yau abin ba dama,</p><p> Wajen window dakin na zuge glass din nadan tsaya, ina kallon ruwan </p><p> Wata zuciya kuma tana tuna min hajiyan mu dasu Aisha da umar ko yaya suke yau cikin wanan yanayin,sanyin</p><p> Danagaji da kallon ruwan baidauke ba sai kawai na kara cire rigana na fada bisa gadon mai wani katon bargo da laushi, nace barina dan huta kafin ruwan yadauke in,tafi gida,,,,</p><p> Har gari yai duhu ruwa ake ta tsulawa bakama hannun yaro,</p><p> Niko kwance nayi barci mai nauyi ne yai awon gaba dani,</p><p> inata barci abina don jin dadin wanan yanayin danayi,</p><p> Nadunkule wuri daya na,hada hannaye da kafana wuri daya na nadae, kamar wata yar mage,,,,</p><p> Kusan sau biyu ya shigowa dakin don ya ta dani daga barci,</p><p> Amma yana samuna dunkule ina ta sharar barci na, daganin yanayin da nake barcin yai min dadi,</p><p> Yasan cewa ko kadan bani da lokacin hutu balle har na barci don hakane ma koda yaga magrib ya kusa daidai lokacin da aka hana barcin marance yayi ,,</p><p> Sai yai niyar zuwa yata dani, saboda bai yarda wani ya shigo mai cikin gida har inda nake </p><p> Don ni dakina ya ta ciki ne inda kusan inda nasu yake,</p><p> Sabanin nasu rugaiyya dake can ta baya kadan inda hanyar kitchen yake,</p><p> Sanin da yayi cewa ina gidan yasa shi, zuwa kirana don in, tashi ,,,</p><p> Ganin ina ta barcin ne har yanzu yasa shi juyawa ya koma, yata tausaya min cikin zuciyar shi,</p><p> Shidai baisan dalili ba kawai yarinyar tana bashi tausayi so sai wlh,,,,,</p><p><br /></p><p> Arazane na mike akan gadon gami da salati , nazaune atsakiyan gadon kafana lankwashe cikin na juna,,</p><p> Nadan lunshe idona kadan don barcin bai sakeni ba,,,,</p><p> Azatona magaruba bai mayi ba tukun, yanayin dai garin ne haka, nadan kara lumshe idona daga zaune,</p><p> Idona yana rufen naji kamshin turaren shariff din wanda yakara dawo wa daniyar yatasheni daga barcin,,,</p><p> Jinkamshi yasani saurin bude idona saidai banyi sa,a ba yariga ya wuce ko tunda ya leko tagan ni a zaune,,,,.</p><p> Kallo nakaiwa agogon bangon dakin zubar na sauko kasa don ina gizo,,, idona ke min ba wai takwas saura nadare,,,, agogon ya nuna,</p><p> Bayi, nafada nadauro alwala na gabatar da sallah a gagauce,,,,</p><p> Ina idar wa natashi na nufi hanyar cikin gida don indiba abinda gidan keciki ,,,,,,</p><p> Don koni dan karen yunwa nake ji don harda kugi cikina keyi,</p><p> Ina tafe duk su hajiya nake tunane ko yaya suke can ko may zasu ci tunda ba girki takeyi ba,,,</p><p> A dining nasamay sherriff din zaune yana cin abincin shi daya,,,</p><p> Haka kawai ganin shi yasa kirjina bugawa don na tuna da fadan da yai muna dazu,</p><p> Yanzu gashi don jin dadi da samun,wuri na zo nayi kwance inata sharar baci kamar wace Abadan bata da aikin yi,,</p><p> Cikin girmamawa na gaishe shi,,,, </p><p> Amma maimakon ya ansa min sai dago wanan yadaurarren idanun nashi ya watso min, wanda kulun yakale ni dasu ban iya gane komai acikin su,</p><p> Shima tambayana yayi kinci abinci kine,</p><p> Batare dana bashi ansa ba</p><p> nace madan bata fito bane, sai kawai na nufi hanyar zuwa dakin ta, nashiga da sallamata,</p><p> Zaune take cikin wata yar rigar barci wanda yake dan iya nuna surar ta waje,</p><p> Dan damtsen hannuta yadan wani murde kamar na matashi kato,,,</p><p> Kanta duk da an gyara shi wai yau yawani yi tsirma tsirma dashi dayake guntun gashi gareta,</p><p> Waya takeyi, har na juya kamar in wuce sai na hago cup din dana kawo mata shayi dazu saina nufi inda yake indauko,</p><p> Jin maganar da tajeyi awayan yasani faduwan gaba duk na,riki ,</p><p> Saida nayu kokarin saita kaina, don kada tasan cewa ina jin hausa,, don ita duk dauka takeyi, banjin hausa ko dan turanci sai larabci kawai </p><p> Abinda naji tana fadi shiya tayar min da hankali sosai hankali,sosai </p><p> Cikin rashin damuwa da inajinta tacigaba da fadin, </p><p> Wlh duk da auren dukiya nai mai salwa yanzu ina son Ahmad,</p><p> Kafin in fara yaudarshi sai na dan more rayuwata dashi,</p><p> Hmmm zancan kawai hjy ke yi, kina tsan manin cewa zai ta bani kudine a haukace,</p><p> Ganin da tayi nadauki cup din kamar zan fita taimin alama da hannu cewa wai in dakata har ta gama wayan,,,</p><p> Cigaba tayi da maganar ta, Salwa don dai baki ganshi bane shiyasa kike cewa hakan</p><p> Yo nima dana fara ganin shi ai,saida na manta da plans din mu,</p><p> Takare karshen zance da cewa ai dole inbi a,hankali don in Daddy yagane plan din hjy duk mun mutu Salwa,,,</p><p> To sai kin kirani din,,, takashe wayan tana kallon inda nake tsaye </p><p> Niko alokacin duk nagama rudewa kokarin saita kana kawai nayi,,,</p><p> Yadda naga ta dan zuba min ido yasa nadan tsargu,</p><p> Saidai kuma naji tayi dan tsaki tace, waima ko taya zan ma wanan mara hausan magana fahince ni,,,,,,</p><p> A,lamatai min kawo mata abin sha jiki ba kwari nabar daki nata,,,</p><p> Hankalina a,tashe anya kuwa ba munafuntar Sheriff wanan matar keyi ba, au har ma shakukeyi inji wata zuciya tace min hakana keda yanzu kikaji komai ,</p><p> agaban ki fa akai maganar komai kina ji ba labari aka baki ba ji kijayi,,,</p><p> To inko hakane gaskiya akwai aiki ja agabana </p><p> Wurin wasu kujeru dake tsakiyan coredon gidan na isa na zauna gami da buga tagumi, don dai inji dadin tunane, don gaskiya dole in taimaka ma Sheriff nima saboda shima yataimaka min a rayuwat, lokaci da dama,</p><p> Minti goma tsakani na tashi na shiga dakin </p><p> Wanan karon bisa gado take kwance tayi daidai da ita saman gado da alama akai abinda take tunane,</p><p> Dakatawa na danyi na kare mata kallon tsab sai naji wani tsanar ta ya shiga zuciyana,</p><p> A sanyaye na karasa gareta na aje mata dan tiren da na hado mata abin shan sama wani dan stol .</p><p> Juya nafito dakin nabar mata cike da tsanar ta,a raina,</p><p> Tausayin Sheriff din naji ya kaman,,,</p><p> a gaskiya dole ne indan taimaka mashi batare da sanin saba,</p><p> Ajiyan zuciya nasaukar daidai lokacin da nagama tunane mafita,,,</p><p><br /></p><p> Dole wanan ranan agidan muka kwana, saboda dare yayi ba damar mu fita waje,,,</p><p> Tunda safe dana tashi bayan mun kanmala komai, </p><p> Naje gun mama mai abinci na fada mata cewa, zanje gida indiba yaran nan biyu,</p><p> Batare da nafada makowa ba na gidan n sulale naitafiya na,</p><p> </p><p> Motar shi yadauka don zai je yadan zagayo wurin aikin su dake cikin gari ,,,,</p><p> Har yadan fara tafiya sai ya lura da wani leda a,gefen kujera, daukowa yayi yadiba sai ya mayar inda yaga ledar, aje,</p><p> Har Saida yaje yadawo inda zashi ne yadauko ledan ya shiga dashi cikin gida,</p><p> Dakin shi yashiga da ledar ya aje, batare da yayi cigiyar mai ledar ba,</p><p> Falo yadawo don yadan huta, saidai yana zama sai yaga ai kamar yadda yabar falon dazu da safe haka yakara samun shi,,,</p><p> Wayan intercom yadauka yana son kirana </p><p> Yayi kira kusan sau uku amma ban,dauka</p><p> A fusace ya fito falon yana kokarin yaga ankira ni, saidai an fada mai fita zuwa gida amma nace bazan da de ba zan dawo, yan zun nan,,</p><p> Ranshi bace yakira almustapha yai mai kaca kaca kan sakaci da aikin da nakeyi,..</p><p> </p><p> Agidan mu kuwa gaskiya nasamu hajiya ta kula da yaran don ta basu abinci kuma tai masu wanka,</p><p> Suna gani na suka yo kaina da murna suna nuna farin cikin su na gani na da,sukayi,,,,,,,,, </p><p> Jawo su nayi a jikina ina farin ciki da ganin su,</p><p> Saida muka gama yar hiran mu naje gurin hajiya muja gaisa na fada mata cewa ruwan samane ya hanamu dawo jiya,</p><p> Tace min ai,gara da muka tsaya can don da munce zamu biyo hanya za,a iya kama mu a,lokacin,</p><p> Nadan kai wani lokaci a gidan tare da hajiya da yaran inda na dan kara gyara wuri,</p><p> San nan mukayi sallama na koma cikin sauri don sai yanzu nafarga d lokacin da muke ciki,</p><p> Tabas nasan cewa na bata lokaci sosai a gida tare dasu hajiya,</p><p> </p><p> Ina shiga gida tun abakin get aka fara fada min cewa Sheriff yana bida na,</p><p> Babu fargaban komai atare dani nasa kai cikin gidan don ansa kiran Sheriff</p><p> Da salamana na shiga falon, zaune yake cikin shigar cort da wando irin ta maza, saidai ya cire cort din ya sagale ta gefen kujera,, daga shi sai wata farar riga yar ciki mai dogon hannu,</p><p> Tare yake da wani bakon mutun sun zuba tulin takardu suna diba,</p><p> Ganin yana aiki kuma ba shi kadai bane agurin yasa nai shirin juyawa don in,bar wurin,,,,</p><p> Ke yace min cikin daga murya saidana dan ja baya kadan </p><p> Ina kikaje lokacin aiki , kin ko san ka,idar aikin da kikeyi kuwa,</p><p> Kaina yana kasa bandaga ba balle in kalle shi,</p><p> Wakike son yabar aikin shi yakama maki naki aikin dibà nan ki gani yadan sa yatsan shi yagoga dan teburin glass din,</p><p> Tare da nuno min ya tsan wai indiba ingani ido nadan daga nakali abinda yake gwada min </p><p> Saidai ni,banga ko mai ba,</p><p> Amma shi cewa yayi wai aiga datti nan ko ina a falon ,</p><p> Falon nakara bida ido don indiba kozanga dattin da yake nuna min banga komai ba,</p><p> Shiru kawai nayi ina sauraron shi,har yakare, kuma daga yau in har zaki iya aiki da mu to dole komai naki yadawo nan gidan, har kwanan ki,,,</p><p> Saidai kalman shi ta karshe ce ta razana ni har na fidda idona waje,</p><p> Waje don kidima,</p><p>Idan har bazaki iya ba ga hanya nan ki tafi, sai in,dauki wata,</p><p> Kawai ya juya yaci gaba da abinda yakeyi batare da yakara kulani ba,</p><p> Nadan dan yi,jim nadan wani lokaci don mamaki kalaman shi da yai min cikin kakausar murya </p><p> Cikin yar muryana mara sauti nace mai,amma kasan cewa inada tsohuwar da bata da lafiya dakuma yara,,,,,</p><p> Zancigaba yadaga min hannu batare da ya juyo yakaleni ba idonshi naga aikin da yakeyi </p><p> Yace hakan naga dama kuma ban shirya jin ko wani irin korafi ba a yanzu</p><p> Idan zaki iya kije kiyi inko bazakiyi ba,</p><p> Yahada hannayen shi wuri guda alamar ma,assalam </p><p> Falin nabari cikin sanyin gwiwa don na ma rasa ta, ina zan fara,</p><p> Kitchen na nufa nakira antyna Rugaiyya na fada mata duk yadda mukayi yau da sheriff din,</p><p> Flower da zata kwaba tayi ambuss da shi don abincin dinner ta dauka a wani dan silver ,</p><p> Tana fadin fadima inbanda abinki aikema kinsan aikin ki aikine mai daraja ,ba aikine na wasa ba,</p><p> Don kinsan duk wani kulawa na mutanen gidan nan yana akanki ne</p><p> Wanda ko da acikin dare ne bukatar hakan yataso dole ne ki yi aikin ki,,,</p><p> To idan baki nan waye zai masu fadima,</p><p> Kinsan cewa wanan aikin da muke yi a gidan nan yafi duk aikin da mukayi a wanan gari sauki,ga kuma kudi masu albarka da ake bamu </p><p> Koda kin fadawa hajiya bazata yarda ki bar wanan aikin ba sam,</p><p> Don haka tun wuri ki wa kanki fada ki zauna gurin aikin ki</p><p> Zanyi magana ta daga min hannun da take kwaba flower dashi tace min ya isa, </p><p> Ina dai yaran da kika jajibo wa kanki wahala kike tuna ne ko,</p><p> Kaina kada mata alaman eh, tace min to ai mu ,muna gida zan dan dinga kula maki dasu gwargwado,</p><p> </p><p> Hakan ne dalilin dawo wana ,da zama gidan aikinawa,</p><p> Don ko hajiya da naje gida na fada mata ansar guda ce in koma can kawai din,</p><p><br /></p><p> Yau kusan satina guda agidan ban zuwa ko ina kulun ina cikin gida , bawani kwareren aiki amma wai aiki nakeyi a,hakan,</p><p> Yau da marance kamar kulun mun gama komai mun hada aikin mu na yau</p><p> Na shirya cikin wasu doga yen riga mai dan kalar rainbow,</p><p> Ina dakina ina kallo wani tashn da ake yin wani gasan talent na larabawa,</p><p> Sai naji kamar marana yadan murda min aikuwa sai gaba na ya fadi don in har ban manta ba yau nake expecting din period dina,</p><p> Gashi kuma banda magani anan yana gida na bari,</p><p> Kadanda nasawo ranan da muka fita da a,maryan sheriff ya fado min arai,</p><p> Ban gama tunanen da nakeyi ba naji wayan dakina nakirana,,,</p><p> Alamar ana bukatana acikin gida,</p><p> Zaune suke a haraban gidan shida wasu baki suna tataunawa, </p><p> Kayan jika makoshi suka bukata, </p><p> Lafiya lau nakawo masu, na juya nabar wurin nabasu baya kadan aiko sai na kasa cira kafana,</p><p> Dukawa nayi wurin nadafe cikina,</p><p> Marana kamar zai fashe nake ji na,</p><p> Bango na dan fara bi don insamu inkai dakina,</p><p> Aiko na kasa, idona ya kade yayi ja,</p><p> Cup da magani naga an miko min,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>[10/4, 14:30] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 4⃣4⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p> </p><p>Matan huguma group Allah ya kara daukaka, </p><p> Allah ya shirya muna zurian mu ,yasa mugama da duniya lfy,,,,,,</p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ban san lokacin da na karbi maganin natura baki ba duk da ban gane kalar magani ba kowane,irine nidai muradina insha magani,,,</p><p> Cikin rawar hannu na karbi cup din na,sha ruwan kadan,</p><p>Ina hade, Ruwan da magani Nakara dunkulewa wurin, saboda wani irin azaban ciwo da naji,,,,,</p><p> Duk da ina jin kamshin perfume din shi ya,na tashi yana shiga min cikin kai,,</p><p> yau ciwo ya hana ni yin re,acting din komai,</p><p> Kamar kar maganin da ruwa su shiga cikina aiko sai na kara dunkulewa saboda wani irin azaban ciwo dake damuna,</p><p> Cup din na sha ruwan yana rike hannun shi , ya wurgat da cup din gefe guda,</p><p> Dafa min kafada yayi yace min in dan tashi in shiga ta cikin gida,,,</p><p> Ai,kafin ince zan tashi wani irin amai ne ya zo min nai kokarin indan kauce da kaina,gefe, kadan don kada aman ya taba shi,,,,</p><p> Amma, ina kafin in haka aman yazubo ko,,,,,</p><p> Duk na,wanke mai jiki da shi,,,,</p><p> Sannu kawai yake ce min, cikin nuna rashin da muwa,</p><p> Ina samun yin aman sai nakama wani irin zufa, kamar nasha ruwan masu mugun zafi,</p><p> Idona yadan kama rufewa a hankali, ahankali har ya rufe lub,</p><p> Nai lu, zan fadi kasa yai kokarin yasa hannu shi guda ya tallaboni dashi, </p><p> Almustapha yakira da sauri ta cikin wayar shi,,, ya fada mai ya zo da sauri ga in da yake,</p><p> Almustaph yana zuwa yaga irin yanayin da nake ciki, shima sai hankalin shi ya tashi,,,</p><p> yace ma Almustapha ya dan rike ni su kaini daki, na,,,,,</p><p> Har mustapha yakai hannu zai rike ni ,</p><p>Komai Sheriff yatuna sai kuma</p><p> Yace mai dakata ,kada ya tabani,</p><p> Cak yadaga ni sama kamar wata baby yai cikin gida dani mustapha na ce mai ba asibiti zasu dani ba,</p><p> Bai saurare shi ba cikin gidan yayi dani,,,</p><p> Anty nafisa na zaune tana waya saman wasu fararen kujeru, ta hango shi dauke dani ga mustapha yana binshi a,baya cikin tashin hankali,,,,,,,</p><p> dakina suka kaini,direct</p><p> Ya shimfidar dani saman gado,</p><p> Ganin ina zufa yasa suka kuna min AC, a,dakin,</p><p> Barci ne mai karfi yadaukeni cikin dan kakanin lokaci ,kamar yadda dama maganin ke min aiki da nasha,</p><p> Indai har nasamu nai amai to zan yi dan barci indan na farka sai inji ciwon yadan lafa min,,,</p><p> Kofan dakin yajawo ahankali, yarufe min,,,</p><p> Sai a lokacin hankalin shi yakai ga rigar shi dana sharara mai,amai akai,</p><p> Cikn sauri batare da yace ma Almustapha komai ba,ya nufi hanyar shiga shiyan da dakunan su yake,,,</p><p> Almustapha da aka bari tsaye da mamaki yakalli kofan dakin da nake kwance yakuma kalli hanyar da sheriff yabi,,,</p><p> Zuciyan shi cike da wasiwasin akan rashin lafiyar nawa,cikin dan kan kanin lokaci haka,</p><p> Anty Nafisa ce tsaye a falo cikin mamaki da kuma son sanin may ke faruwa, ne haka, har mijin nata tadau koni, ajikin shi,</p><p> Jikin da take muradin tabawa koda yantsan shine bata samu ba yau ga common yar aiki, cikin shi dumu dumu,</p><p> Wuce ta, ya,yi fu,u yahaura sama abinshi, Inda dakin shi yake, batare da yako kali inda take ba,,,,,,</p><p> Bin,shi tayi da kallo har ya bace mata, daidai lokacin da mustapha ya fito shima daga inda nake,,,,</p><p> Mustaphane,, yagaishe ta cikin girma,mawa zaidan wuce ,,take tambayar shi may ke faruwa ne,</p><p> Yace mata banda lafiya ne shine suka taimaka min ,,zuwa daki,</p><p> Baki ta tabe nuna ko in kula,,,</p><p> Yana shiga dakin shi ya wurgat da rigan tun a kofa, </p><p> In akwai abinda yaki jini arayuwan shi ne yaga ,amai ,,, </p><p> Idan yaga amai bai iyan komai ko abinci bazai iya ci ba a ranan ,,,,,,</p><p> yau gashi , an mai amai a jiki, amma yadaure dashi a hakanan</p><p> Subbahanallah, rin,tse idon shi ,yayi tare da sake shower akanshi, ruwa nata zuba mai,,,</p><p> Yafi kusan minti goma a haka yadauki sabulu da soso duk ya goge jikin shi dashi, don ji yakeyi kamar aman ya mane mai a fatan jikin shi,,,</p><p> Yadauki lokaci da dama acikin bayin san nan yafito, </p><p> Ya dan gyara jikin shi jallabiya kawai yasa don lokacin sallah magrib ya kusa,,, saboda har in yana gari duk sallah da zaiyi cikin jan,i ne,,,,,</p><p> Koda yafito zuwa masallaci Nafisa tana zaune, falo ta kure karar tv tashan yan rawan kasar turawa, keta ,tashi,, kamar gidan yan rawan disco,,,,,,</p><p> Mamaki yakamashi fal a zuciyar shi,,,,,, don shi tunda yake gidan baitaba sanin ma akwai wanan tashan ba a,talabijin din,</p><p> Batare da yai mata magana ba yadauki remote din dake saman dan karamin tebur din yarage karan tv,</p><p> Yasa kai yafita zuwa masallacin unguwar inda Shek Abdullaraham bin, Inus,, keba da salla, wanda duk ke wanan uguwar yana jin dadin limancin wanan bawan Allah,,,</p><p> </p><p> Barcin da baifi awa biyu ba da,dan wani kai,,,, nayi, nafarka,</p><p> Zubur na mike,daga barcin, inda naji marana yai min karfi kamar na hade dutse,, </p><p> Ko kari nayi natashi,Wanka nashiga nayi,</p><p> nafito bakin mirror naje nadan dubi kaina naga nawani ramay kamar wace tayi wani dogon jinya </p><p> Sallah na fara gabatar wa ina zaune ina addu,a abinda yafaru dani dazu yafado min a rai,</p><p> Cikin mamaki nadan motsa kadan lalai ba shakka sheriff udeen din, mune yabani magani na,</p><p> To a ina yasamay shi sai kuma natuna ai shine ma yakaini asibiti a birnin madina kuma yai min komai,a lokacin har naji saukin jikina</p><p> Oho,,, ,, hmmm watau wanan mutumin ,Don tsananin kulawar shi bai manta da lokacin yin period dina ba,ke nan yake nufi ko may</p><p> Wa,iyazu billah,, ashe duk wani motsi nawa yana kula dashi kenan,,</p><p> Da wanan tuna nen natashi zuwa cikin gida don in gabatar masu da dinner dinsu,</p><p> Saboda har yanzu ina dan jin jikina marana ban iya tafiya sosai,</p><p> Amma ya zan iya hada ido da sheriff din namu,,</p><p> Ko da naje falon kowa na falon zaune cikin dabara nake komai, na hada ma anty nafisa nata, nazo gefen da yake don in hada mai sai yace min yau bazai ci abinci ba in bashi juice kawai sai tea da zai sha anjima, kawai,,,</p><p> Tsayin da nadan yi don in saurari bayanin shi, yasa marana ya kara kullewa wuri guda sai wani irin azaba ciwo ke kokarin taso min,</p><p> Cikin hikima nadan yi dabaran barin wurin,</p><p> Muryan shi naji tun ban wuce ba yana cewa idan nasan cewa banda lafiyane inje inkwanta mana</p><p> kada in jawa kaina matsala tunda ba kullun ne mutun zaiyi lafiya ba,</p><p> Inkuma har ciwon ya matsa min ne inje inga likita ko za,a san may ke damuna,,,</p><p> Wayancewa nayi na,ce mai kainane kemin ciwo kawai, zai fada min zuwa anjima</p><p> Dadabara naja kafana zuwa cikin dakina,, yabini da kallon tausayi</p><p>Ina shiga dakin na haye gado na ,</p><p> Na dunkule wuri guda kamar yar mage duk kafana nashige dashi cikin jikin na nade wuri daya,</p><p> Saida nadan samu barci kadan a,hakan bandade ba na farka don ina son in dan fita, in karsa aikina </p><p> Ina zuwa Falon shiru yayi bakajin motsin komai sai karar naurorin dake aiki a falon,</p><p> Kayan tea da yace zai sha na hado mai acikin wani dan karamin ture,</p><p> Nakai bisa tebur din cin abincin su na aje,</p><p> Saida na kusa gama abinda nakeyi a bisa tebur din,</p><p> Na,hango shi zaune can wani dan corner da aka kebe afalon , bakowa ke zuwa wurin ba ,sai shi,</p><p> Don koda nazo gidan nafara aiki saida almustapha, yai warning dina kan zuwa wanan gurin,</p><p> Glass ne aka kewaye wurin dashi sai wasu kujerun masu taushi da tulin takardu, akwai alkur,ani mai girma da sauran litatafan addini ciki, sai computers iri iri,</p><p> Nikan shiga sau daya a sati don gyara wurin,</p><p> Ashe shi tun dazu ya gurin yana tura sako a computer wa mr William,</p><p> Koda zai fito saida suka kwashi artabu da nafisa kancewa, gaskiya ita bata yarda duk dare a ce mutun sai ya fita,,,,</p><p> Ba wani kulawa tsakann miji da mata hankade ta yayi gefe yafito abin shi yabarta tana mita,,,,,</p><p> Ita abinda bata sani ba shine bata cikin rayuwar shi sam don jinta yake yi kamar ba mace ba,</p><p> Shi duk da bai taba taraiyya da wata mace ba a,duniya sai ita,</p><p> Yansan labarin mata yakaranta komai a cikin wani, littafin </p><p> Mai suna, Surar ya mace na wani shahararen balarabe marubucin addini, musulunci, wanda ya, wallafa duk yanayin kowace irin mace,</p><p> Ita ko nafisa tadauka bai fahinci komai gamay da ita,ba </p><p> Tunda tanaganin tasha gyara wurin mamanta kafin tazo duk wani sadda baru da kayan mata an hada ta dashi,</p><p> Shiko anashi ban garen </p><p> Biyayya kawai yake wa tsohon shi kanta saboda ya fuskanci cewa baban nashi nason wanan hadin auren,,,,</p><p> </p><p> Daga inda nake tsaye na hage shi, zaune yamaida hankali ga abinda yakeyi,kuma hankalin shi a kwance yake aikin </p><p> , bai,man san cewa, ina cikin falon ba alokacin,,,</p><p> Hankalin shi duk ya,naga computer shi,</p><p> sai yaji a,jikin kin shi cewa bashi kadai ke a falon ba</p><p> Da akwai alaman mutun a falon, baigama tune ba,</p><p> yaji motsi a bayan shi lokacin yasan cewa na shigo falon,</p><p> Daidai lokacin da nake aje cup din da zai sha tean cikin dan karamin tiren da na hada mai kayan tea din ciki,</p><p> Naje in juyo haka sainaga mutun gaba na tsaye, </p><p> saida nadan firgita, saboda tsoro, nadan waiga inda yake zaune naga tabas shi din ne a gaban nawa,</p><p> Kalo guda nai mai na,kauda ido na gare shi, saboda rigar barcin dayasa cotton ce tana nuna mai surar jikin shi waje,</p><p> Muryan shi naji yana fadin keda baki da lafiya may yasa kika fito yin aiki idan natashi shan tea din ai zan kira nafisa ta hada min,</p><p> Ki koma kawai ki,bar shi koni da kaina zan hada,,, , ba musu na juya don dama daurewa nake duk banjin dadi sam,</p><p> Nafara tafiya naji muryan shi yana cewa kin ko ci abinci</p><p> kai na kada mai alamar a,a </p><p> Batare da yakara magana ba naga yafara hada kayan tea din da na aje mai asaman tebur, din ,,,,,, tea mai kauri ya hada min ya miko min yace inje insha</p><p> Ya miko mi magani, yace Kuma in,tabbatar da nasha shi yanzu kafin in kwanta,nasamuace tare da godiya,,,</p><p> Nabar falon a duduke zuwa dakina,</p><p> Tausayina yakara kamashi, don harga Allah yana tausaya wa wanan yar yarinyar da aka sako ma,duniya ta yi rainon ta,, </p><p> Tunda nasha tea din da maganin da aka bani sai naji marana, da ya kulle min tam yadan sake sosai har nadan ji saukin ciwon </p><p> wani barci mai karfi ya kwashe ni, a hakan ,,</p><p> Bani na farka daga barcin, ba sai daidai lokacin da ake ta kokarin kiran sallah asuba, </p><p> Dama daidai wanan lokacin nake tashi, koda agida nake don fara ayukan mu, yau da kullun,,,,</p><p> Jina nayi cikin yanayin bako tare dani watau period yazo min, hakan yasani ni kara yin lankwas bisa gadon,</p><p> Da kyat nasamu natashi zaune na rarafa zuwa bayi don in,tsab tace jikina,</p><p> Bayan nafito sai na tuna cewa aiko nasiyo kadan pad ranan nan da mukafita da anty nafisa</p><p> Shinake ta nema cikin dakin tunda nasan cewa ban je dashi gidan hajiya ba,</p><p> Turo kofan akayi duk da ina cikin wata duguwar rigan da zura bayan fito wana wanakan,</p><p> Saida naji kunyan ganina hakan da yayi ba wani saya jiki,.</p><p> Yajikin yace min nace mai da sauki ledar dake hannun shi ya,miko min, yace min ina wanan ne kike bida,</p><p> Ledar pad dina dana sayo da muka fita nida NAFISA </p><p> Juyawa yayi yana ce min indinga kula da rayuwata tunda ni kadai nasan irin wahalar da nake sha,</p><p> Wayyo Allah kamar in shige cikin kasa don kunya kila yafi minti goma da fita ban iya daga ko kai ba balle in cire kafana, </p><p> Saida naji alamar bakona zai iya zubowa anytime nai saurin kai ma ledar kalo,</p><p> Tabas ledan kadan pad din da na siyo ne, ranan,</p><p> Haka nadaure na dan shiya jikina tsab cikin nasa wando da rigar jeans don gudun wahala,</p><p> Abokiyar aikina ce ta shigo dakina da ture a hannun ta ,</p><p> Kayan tea ne acikin shi sai sauran abin karin kumalo </p><p> Nai,mata godiya tace min sheriff ne yace akawo min nan kuma insha magani na,</p><p> Daga haka bata kara cewa komai ba ta wuce abinta,</p><p> Tundaga wanan ranan ban kara yarda mu hadu da sheriff ba ko a cikin gida </p><p> Saima muka fara wasan yar boya da shi yana sane da nufi sarai amma yakamar bai gane ba,,,</p><p> Yai tafiya zuwa Riyadh don dama yafi zama can din saboda aikin shi akusan can yafi yawa </p><p> Yanzu daine ma da su,ke kokarin bude wanan mai,ai,katar ta Abu Abdallah, </p><p> Shiyasa yake dan yawan zama cikin garin makka so sai,</p><p> Duk kwanakin da yayi bai gari cikin dadi da walwala nayi su, ban shakar komai,</p><p> Daga anty Nafisa kawai nake dan samun takura wani lokaci, don tana da yawan sa aiki,</p><p> Amma dai ba laifi ina ina jurewa da takurar ta, </p><p> </p><p> Yau aiki yai muna yawa don saida muka gama abincin dinner sai anty nafisa tace muna wai bata son wanan saidai muyi mata wani mara nau,yi taci,</p><p> Don haka dole muka koma girka wani </p><p> duk da marance yayi muna, amma bai hana mu yin sauri ba,</p><p> Mun,gama komai muna jerawa a table ,ina dan wake ,wake na na larabci ,</p><p> Sai kawai hancina ya sanar min da akwai mutum abayana don fitinanen kamshin turaren sa, da ya gauraye falon,</p><p> Waigawa nayi kadan don in,tabbatar ko da shi din ne,</p><p> Don koda bai nan gidan namu baidaina kamshin sa ba tankar yana gari,</p><p> Ina waigowa naganshi tsaye yana kokarin karba waya hannu shi rike da briefcases din shi,</p><p> Wayan yake karbawa amma hannkalishi naga reni ,,,, ganin hakan danayi yasa nataka a hankali har zuwa inda yake nakarbi dan briefcase din nashi cikin ladabi ina mai sannu da zuwa,</p><p> Koda nabada baya ido yabini da shi yana mamakin yadda yaga nakara girma cikin dan lokaci guda,</p><p> Dai lokacin yakare wayan shi yana kokarin sa wayar a aljihu yadaga kai gefe anty Nafisa ce tsaye tana kallon shi,, cikin mamaki,,,,</p><p><br /></p><p>[10/4, 14:31] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 4⃣5⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Koda suka hada ido da Nafisa sai ya wayan ce zance saboda gudun zargi,</p><p> Yace mata kidiba fa karamar yarinya tafiki hankalin , </p><p> Ke ko gaisuwa baki iyawa mitun ,</p><p> Tace au to anan zan gaishe ka a gaban yan aiki,</p><p> Bai ce mata komai ba ya haura sama, abinshi,,</p><p> Yau kusan kwana biyu da dawowan Sheriff Ahmad daga Riyadh,</p><p> Babu zaman gida yanzu sam gare,sh,</p><p> Don tunda yadawo aiki sukeyi tukuru, don kusan komai na kamfanin su ya gama haduwa ko,</p><p> Yana zaune a office din shi,sai ga abokin shi Yusuf da suke zama tare a kasar saudiya tun zuwan shi kasar suka hade da yusuf din </p><p> Shima karatu yazo yi daga kasar ghana,</p><p> Halinsu yazo daya shine suka kulla abota, </p><p> Allah kadai yasan sirin su,</p><p> Shi ya aika ma Yusuf din yazo yaga sabon ma,aikatar da suka hada, wanda tallafin ABU Abdallah ya taimaka masu komai ya hadu,</p><p> Inda shi Ahmad din ne zai kula da duk wani aiyuka na kasa shen, biyu saudiya da Nigeria,,, </p><p> Yusuf yanu farin cikin shi sosai yayi mai addua da fatan alheri a rayuwan , </p><p> Office din suka koma bayan sundan gama zagayawa cikin company.</p><p> Zaune yake saman kujera irin da ake samu a kowani kayataccen office,</p><p> Hannu yasa ya zuge nicktie din wuyar shi gadan,</p><p> Yadauki daya daga cikin lemon gwangwanin da aka aje, masu, agaban su,,</p><p> Saida ya dan zuki lemon yakai diban shi ga Yusuf wanda ke kokarin diban dabino a cikin wani dan plate,</p><p> Yusuf din ne ke fadin bamuzo dai munga madam ba har yanzu,</p><p> Ina fatan bakayi fushi ba damu,</p><p> Don dama mun yi magana da sauran Friend's cewa zamu hadu karshen wata mu kawo maku ziyara,</p><p> Saida yadan juya kujera tukun sanan yace ai ba wani matsala,,,</p><p> Kafin Yusuf yaci gaba da maganar shi, sai shi Ahmad din ya tare shi da wani zance,</p><p> Wai ya batun form din danayi ma gana ne, </p><p> Duk da Yusuf yagane abokin nashi bai son zan cen da sukeyi ne shiyasa ya basar da ita,,</p><p> Yace mai Af, kaga ko na manta dasu cikin mota, na fa</p><p> An samo form din har ma guda uku, don dama biyun da kai requesting suna bukata sai nayi sa a aka bani uku,</p><p> Idan mun fita sai inbaka su,</p><p> Sunda jima suna hira gamay da wuraren aikin su, dakuma kasa shen su,</p><p> Yusuf din yai haraman komawa don a madina yake zama shi, </p><p> Tun bayan gama karatun su nan yasamu nashi aikin a wani makaranta,, yana koyar wa,zaman shi sai yafi karfi a madinan,</p><p> Sun mike lokaci guda sun musabi,a Yusuf din ke ma Ahmad magana akan yayi kokari ya rike amana </p><p> Don sanin halin shi dayayi kan ko bai son abu zai iya hakuri yayi abin,</p><p> Don haka ma yasan cewa ko wanan auren na abokin nashi ba,ra,yin shi bane ,</p><p> Don tunda suke baitaba jin yai mai zancen wata mace ba saida zancen </p><p> Tsohuwa dana mahaifiyar shi,</p><p> Sai ko kwanaki da yai mai zancen yana son form din makarantar su don ya siyawa sister dinshi,,,</p><p> Kafin su rabu saida suka dan tatauna so sai kan zancen,,,,</p><p> </p><p> Yau a gajiye yadawo gida, dom haka yana dan bukatar hutu kadan,</p><p> Wanka yayi kafin lokacin sallah yayi ya wuce masallaci bai dawo wa sai an idar da sallah isha,i,</p><p> Acikin shigar jalla biya fara kal, mai yar guntun hannu yake,</p><p> Zaune yake saman kujerar yadan kishin gida kadan kafanshi mike a saman wani dan stol dake gaban kujerar, ,,</p><p> Hannu shi guda ya sa ya dafe kan shi, kamar wanda kan shi ke mai ciwo,,,,</p><p> Nasan cewa idan yana cikin wanan irin yanayin bai son damuwa sam</p><p> Saboda nataba, yi mai katsaladan watara naganshi zaune irin,hakana nadinga buruntu da kayan da nake jerawa a dinning har cup ya fado ya fashe,</p><p> Aiko ya mike tsaye ba shiri, naji ya ce Ya, Subahanallah,,</p><p> Kofa yanu min da in fita falon , </p><p> Nikuma ina kokarin nuna mai cewa zan kwashe glass din da yafashe, ne</p><p> Wani uban tsawa yadaka min ban san lokacin da bar falon ba, don tsoro,</p><p> Ina zan yarda wanan katon yamake ni,</p><p> Saida nabari yafita nadawo na kwashe glass din ina yi ina waigen hanyar shigowa,</p><p> Shiyasa yau dana ganshi a hakan nake taka tsantsan da aikina,</p><p> Hankalina na ga abinda nakeyi sai kawai , ban san cewa anty NAFISA ta shigo falon ba,</p><p> Jin muryan shi kawai nayi cikin wata irin tsawa yake magana Idon shi ya yi ja alokacin ,,,</p><p> Yace Nafisat nafada maki tun jiya Umurni na baki ba wai uzuri na ce ki kawo mini ba ina fatan kin gane,</p><p> Yadda yai maganar shi ya ba kowa dake falon a,lokacin, tabbacin ba alamar wasa acikin zancen nashi,</p><p> Da sauri ta juya rai bace ta shige dakin ta yabita da harara,</p><p> Muda ke tsaye a gefe wani irin mugun kallo ya watso muna,</p><p> Yamike yabar falon cikin bacin rai shima,</p><p> Nikan ko a jikina don nasan wanan fadan manya ne, kuma mata da miji,</p><p> Dakinta na shiga don in gabatar mata da abincin su na dare,</p><p> Waya nasamay ta tana yi cikin fada, take magana</p><p> Yanzu ummi kamana zaice wai tunda zai yi baki dole sai naje kitchen da kaina na shirya masu wani abincin alfarma, irin ta mu ta gargajiya, wai yan aikin shi basu iyaba</p><p> Yo ni ina zan iya girki ko na mutun biyu bale na mutun fiye da ashirin,,,</p><p> Gaskiya saidai yaji kunya amma na fada mai cewa bazan yi komai bani,</p><p> A bangare wace take cewa ummi hakuri naji tana bata , tana cewa abinda zaki samu lada kuma zai jidadi kila ya baki kudi masu yawa a sanadin hakan,,,</p><p> Duk hakkurin da ake bata bata yarda ba sam dom tace ita bata da matsala akan kudi dashi don ko ma may tace tana so zai siya mata, ne,,,</p><p> </p><p> Niko tunda naji wanan hirar ta nafisa sai na dan shiga halin damuwa don nasan cewa koma su waye zasu zo suna da matukar mahin,manci a gareshi,</p><p> Don haka na kudiri aniyar zan fidda shi wanan kun yan isha Allah,</p><p> To saidai matsalar ban san wani rana bane bakin zasu zo muna,</p><p> Almustapha ne yafado min a rai,</p><p> Nasamay shi yana shirin fita,</p><p> Da dan saurin nakarasa inda yake, shiko yana gani na sai yadan dakata min,</p><p> Bayan nagaishe shi ne nake tambayar shi don Allah ko yasan ranan da bakin Sheriff zasu zo,</p><p> Yace min aibanda gobe ne zasu zo abokan sheriff ne da da matan su, da suke zaune nan kasar saudiya sune zasu zo ziyar shi don suga amaryan shi,,,,,,,</p><p> Naidai nasamu almustapha yai min bayanin komai a cikin hikima,</p><p> Najidadin jin wanan bayani sosai duk da bayanin yazo min a kuraren lokaci,</p><p> Banshiga cikin gida ba direct wurin su Rugaiyya na nufa,</p><p> Naimata bayanin komai acikin tsanaki ba mu bata lokaci ba maka kama shirye,shiyen kayan da za mu bukata wurin aiyukan,</p><p> Tun wanan, lokacin ban samun zama gida ina nan ,ina can, sai zirga zirgan nakeyi kawai,,,</p><p> </p><p> Duk da ya lura da cewa ba wani shiri da nafisan kewa bakin nashi , hakan baisa yadauki wani mataki ba,</p><p> Ido kawai yasa mata don yaga gudun ta,</p><p> Azuciyan shi kuma,yasan abinda ya kulla zai matan nadaukan fansa,</p><p> A,na mu bangaren bayanin da mustapha yai min na taron abokin shi guda da sukaje wani dan kasar mali </p><p> Shi mukayi amfani da shi muka dan can za namu salon,,,,,</p><p> Washegari, tunda safe muka tashi masu gyaran gida nayi masu yin girki suna yi,</p><p> Nai decoration din wani fili dake cikin gidan da duk wani abu da ba hause ke gyara gida dashi,</p><p> Hjy laila ce ta taimaka muna da duk wani abinda zamu bukata,</p><p> A fanin abinci munyi masa, da miya tuwon shinkafa da miyar ganye, tuwon alkama da miyar kubewa,danye, danbun shinkafa yaji carvege, sai pepper soup nakifi da na kayan cikin rago,</p><p> Sai fura da nono mai kauri wanda yasha sanyin fridge,</p><p> Ga kunun tsamiya da sugari, har da shimkafa da wake da salad,</p><p> Komai an shirya gwanin sha,wa, Idan kagani sai ka dauka ko agida Nigeria ake wani buki ,,,,,,</p><p><br /></p><p> Tunda ya iso haraban gidan yaga canji sosai har takai idon shi ya hango mai haraban da muka gyara inda za a ci abincin</p><p> Batare da ya nufi gurin da aikai decorating din, ba ya wuce cikin gida direct </p><p> Ya mai jin dadin hakan da yagani </p><p>Itako tana zaune falo tasa wani material, ja,dinkin shi yadan matse mata jiki,</p><p> Ta bayan ta yazo yadan rugumay ta kadan saboda farin cikin abinda yaga tayi don sai yau yadan fara cire shakkun ta da yake,</p><p> Godiya da taji yana mata yasa tatsaya sororo tana, kallon shi cikin mamaki,</p><p> Kafin yai wani magana itace tafara magana,</p><p> Tace ban fahince ka ba fa habibi, </p><p> Murshi yadan yi yajawo zuwa cikin jikin shi yana fadin wanan surprise din haka,</p><p> Tace na may ke nan fa, na taron bakin da kikai muna,</p><p> Tadan daga hannu ta alamar aa bata da masaniya ita,</p><p> Cikin mamaki ya ke kallon ta takara cewa wlh ban san may kake magana ba aikai </p><p> Ture ta yayi daga jikin shi rai bace,</p><p> Idan bake bace towa yayi wanan aikin ,cikin ikon Allah dai dai lokacin na shigo falon cikin shigar irin ta hausawa </p><p> Atamfa ce zani da riga koriya da dan ratsin flawer yello cikin jikin atamfar dinkinta yadan matse min jikina dan dagwas,,, sai gyale dana dan yafa yellow akai na</p><p> Da kagan ni, Duk alamar girma ya dan bayana min, dan kuguna yadan ciko cif cif ,kirjina yadan kunburo alamar dai nadan kosa komai na girma ya baiyana sosai ,ajikina,</p><p> Ban ko kula da su ba ina kokarin nuna wani dan center carpet da za,a dauka zuwa waje</p><p> Kallo duk suka bini dashi na mamaki,</p><p> Sai a lokacin nagan su tsatsaye,,,</p><p> Batare da wani damuwa ba nadan gaishe su cikin girmawa,</p><p> Nacigaba da abin da nake yi abina,</p><p> Da mamaki yabar wurin zuwa sama inda dakin shi yake,</p><p> Yau gezena,shadda yasa mai ruwan chuculate,, dinkin tazarce ne ,,,sai hula yar zanna bukar yar asali da yakafa akan shi ,,,,agogon company rolex yasa a hannu shi takalma bakake, suna wani irin kashe ido,</p><p> Yusuf ne yabugo mai waya cewa gasu nan sun iso ,</p><p> Cikin fara,a nake taron bakin zuwa cikin katafaren falon mu, daguda guda sukai ta iso wa gidan har suka gama zuwa, </p><p> Saura mutum guda ya rage baizo ba, wanda naji suna cewa Ali baba ,, wai ai baida iyali anytime zai iya iso, daga yamal,,,</p><p> Agaskiya duk wanda yazo wanan yar walimar taron amaryam Sheriff din mu ya yaba da irin tarbon da akai mai sosai,</p><p> Zirga zirga nake tayi cikin jama, don gabatar masu da abin tabawa ,,</p><p> Gefen mata daban na maza daban amma duk da haka ana iya ganin juna don duk guri gudane,</p><p> Wata yar matashir mata fara yar kabilar yarbawa ce, da baby ta, ina ganin haihuwar fari ce mata,</p><p> Yaron yanata kuka tunda sukazo, tayi lalashi yaron yaki yin shiru,</p><p> Kusan kowa a wurin ya tausaya ma yaron yadda yake ta faman tsala ihu,</p><p> Zuwa nayi na karbe yaron a hannu ta nawuce cikin gida dashi, da ita,</p><p> Ruwa nasa masu zafi nai ma yaron wanka wurin cire pampers naga a she kashi yaron yayi,,,</p><p> Naimai wanka na gyarashi tsab tabani wani kaya na saka mai,</p><p> Lokacin da muka fito wajen taron, mu tararda har an fara cin abinci kowa sai yabawa yake yi da irin girkin da akayi, </p><p> Nafisa tana gefe fuskata babu ko alamar fara,a </p><p> Tun matan abokai na janta da yar hira har suka gaji su ka kyaleta,,</p><p> Tana ta wani matse fuska kamar mai jin warin mutane,</p><p> Muna ji suna hiranta kasa kasa suna cewa wanan ai ta tsofe ma Ahmad </p><p> Wata kuna tace yo ai auren zumunci ne inbashi ina zaikai wanan ai gwago ce,,,</p><p> Gyalen da nasa yana da sulbi sosai, gashi kuma ban iya yafa gyale ba dama sai dai inyi rolling din kaina kawai, gyalen yanata sabule min,</p><p> Ga kuma yaro a hannu na, duk na tsawala ina kokarin mika yaron wurin uwar shi sai gyalen ya karkare faduwa kasa,</p><p> Subbahanallah aiko idon maza caaaaa akaina cikin sauri na jawo gyalen na mayar akaina, daidai lokacin naga sheriff din mu yai min wani irin kallon banza </p><p> Wanda banji dadin hakan ba, </p><p> Duk sai naji na tsargu wlh,</p><p> Don ni ban san may nayi ba,</p><p> Daga inda yake yaga nadan shiga damuwa sai yadan yafito ni da hannu, Sukaina ce ke fada min yana kirana,</p><p> Cikin ladabi na isa inda suke zaune shi da su Yusuf,</p><p> Fura yace min in debo masu a cups, </p><p> Nakai masu furan sai santi sukeyi,,</p><p> Ga al,adan su duk wanda zai tafi sai ya aje wani kyauta mai muhinmanci arayuwar ma,auratan wasu na bada kudi masu yawa, suce aba ma amarya wahalar girkin ta,</p><p> To muma dai haka din ne don wani katon tire aka dinga zuba duk wani gift da aka samu a wurin</p><p> A gaskiya ba laifi don dai an samu alheri so sai,,,</p><p> Muna kallo bakin mu suka dinga barin mu da guda daguda har suka watse suka bar mu mukadai agidan,</p><p> Saida na ga duk mun gyara ko ina agidan sanan nasamu natsuwa, </p><p> Kayan gift din na hada wuri guda na nufi cikin gida da su wurin anty nafisa,</p><p> A Falo na samay shi zaune yana waya daganin shi yana cikin nishadi yau</p><p> yana ganin zan wuce da kayan gift din,inkai ma,anty nafisa,, dakinta sai yadakatar dani da hannu </p><p> naja nayi tsaye cak wuri guda,,,</p><p> Ina sauraron shi inji mai zai ce min,</p><p> Yana gama wayan ya dakai diban shi gare ni</p><p> yace min in,bude komai yagani a gaban shi na ,aje kayan </p><p> nan na duka nadinga cire kayan guda gudu ina kuma karanta mashi,sunan wanda yaba da gift din</p><p> Abin mamaki ina kai ga na karshe sai naji yace min, duk gift din kayan sawan in dauka,</p><p> Kudi kuma in dauka in raba ma duk wanda mukayi hidimar dashi,,,</p><p> Saura in,dauka,cikin mamaki nadago kaina don jin zancen shi,,,</p><p> Zan yi magana ya dago min hannu yace min ya isa</p><p> Jiki ba kwari na tashi don in wuce,</p><p> Sainaji yace min yagode da fitar dashi kunyan da nayi,,</p><p> Ina dan murmushin jin dadi ban san cewa anty nafisa tana bayana tsaye ba tun lokacin da na fara nuna mai kayan,</p><p> Gani ta dayi tayi murtuk da fuska yasani dan ja tsaye ,</p><p> Kauce mata nayi nadan bi ta gefen ta nawuce abina da kayan</p><p> Muryan ta naji tana magana cikin tsawa take cewa wanan ai wulakanci ne,</p><p> tayaya zai dauki kayan yaba yar aiki</p><p> Acikin azama naji yace mata wace,ce yar aiki,</p><p> Nida take gani zaman kaunar shi da suke ciki daya yake dauka, ba matsayin yar aiki nake ba.</p><p> Yace ko kin taba ganin yar aiki tafidda shugabanta kunya kar yadda taga nayi a yau din</p><p> Yace ko kintaba yakara tambayar ta cikin tsawa,,</p><p> Nidai na wuce abina nabarsu nan yana ta gagasa mata maganganu masu zafi,</p><p> Bayan na aje kayan dakina gurin Rugaiyya na tafi,</p><p> Na bata labarin yadda duk mukayi da Sheriff din kan gift din su,,</p><p> Ta dafa min kafada tace fadima halinki ne na alheri ya ja maki,</p><p> Duniya ance indan baka da kudin da zaka taimaka wa mai kudi to kataimaka mai da karfinka,</p><p> Kinga kinfitar shi kunya , </p><p> yin hakan yasa shi jin dadin alherin da kika mai a yau ko mai yai maki kin can can ci hakan ne fadima,</p><p> Tana fadi tana har hada kayan ta don zuwa gida na mika mata kudin duka nace mata ta aje cikin wanda muke tarawa,,</p><p> Ashe duk kudin na a cikin jikin ta nan take boyewa gudun kada a sace muna,</p><p> Saida ta hada komai tadauki jakar ta da dan abincin da zata kaiwa su hajiya da su Umar,</p><p> Kawai sai naji banji dadin da zata wuce ba jinayi dama muntafi tare don ina kewan su hajiya, ina son ganin su ina son in kwanta tare da su muyi ta waka da labari har barci yadauke mu kamar yadda mukeyi kullun,</p><p> Ina kallo ta wuce ni raina yai min baki,kirin </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Rugaiyya har ta kai kusa da gida ashe bata sani ba yan bagaladi suna biye da ita, </p><p> Tundaga unguwar su sheriff din mu suke biye da ita tunda sun san cewa duk bakin da akayi sun koma garu wan da suka fito, su,,,</p><p> Bata ankara ba kawai taji sun kewaye ta sun mata circle, ba ta da daman gudu,,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎 ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>[10/4, 14:31] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 4⃣6⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA 🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p>Allah ka tai Maki Musulumi Duk Inda yake,,,, ,Ya Allah Karufa ma Kullumin musulumi na Duniya Asiri Ameen</p><p><br /></p><p> Anty Halima Garko </p><p><br /></p><p>Almust true life story,,</p><p><br /></p><p> </p><p> Wa,iyazu billah abinda kawai take fadi kenan idon ta a rintse ,</p><p> Inbanda Allah ba wani abinda take iya fadi,</p><p> Basu yi wani dogon bincke ba suka gane cewa takaru ce ita bata da takardan zama yar kasa,</p><p> Rugaiyya bata basu wani wahala ba don haka bata wani sha wuya ba, wurin su,</p><p> A, haka suka tafi da ita zuwa inda ake tara kamamun irin su,,,</p><p> Duk wanan abinda yafaru a idon wani makwabcin mu ne, yana ganin an wuce da ita ,</p><p> Da saurin shi ya isa gidan hajiyan mu yana sheda mata duk abinda yafaru,</p><p> Sun yi kuka sunyi bakin ciki sosai wlh,</p><p> </p><p> Ina can dakina jiki ba kwari tunda anty na ta,tafi har na kwanta sai naji bana jin barci , duk da gajiyan dake jikina,</p><p> Don haka sau,kowa nayi daga kan gadon na zauna kasa,</p><p> Kanya gift din da aka bani na jawo ina fitar wa guda guda ina kalon su,</p><p> Duk kusan dogayen riguna ne har guda hudu nace a raina sai muraba nida Rugaiyya na</p><p> Sai kuma dikin shadda redmaid masu kya kusan guda uku suma nazabi guda nace biyu in bata tasa don tana son irin wanan kayan tun muna kano,,,</p><p> wani kwali da najawo waya ce mobile cellular mai shegen kyau, cikin kwalinta tare da tarkacen ta,,, </p><p> Aiko ina ganin wayan ban san lokacin da na ture komai na hau murna ba,</p><p> Koda banda wanda zan kira na dade ina sha,awar waya kodai photo na kalla kuma inyi game,</p><p> Jona ta nayi a wuta don ta samu caji,</p><p> Ganin wanan wayan yasa nakasa karasa kallon kayan da nakeyi,,</p><p> Nakoma saman gado na kwanta ina jiran wayan tayi caji,</p><p> Maganar da naji sheriff nayi da matar shi yafado min a rai na,</p><p> Allah sarki sheriff ai nice ka taimaka don ban manta irin taimakon da yaitamin can baya kafin ma inzo gidan shi,,,</p><p> Juyawa nakarayi ina Allah Allah gari yawaye in nuna ma Rugaiyya wayata,</p><p> Da haka barci barawo ya dauke ni,</p><p> Firgice natashi duk jikina yajike da zufa,</p><p> A c na kalla naga yana aiki, har nadan gyara kwanci sai mafarkin da nayi ya fado min a rai,</p><p> Gabana ne ya fadi dammmm,,,</p><p> Tiryan tiyar na fara tuna abinda nagani a mafalkin nawa,</p><p> Rugaiyya ce ke shiga cikin wani abu mai matakala kamar gidan sama tana murmushi tana min bye,bye,</p><p> Zubur na mike don wani zafi naji tundaga kafana har cikin kaina,</p><p> Bayi na fada nai wanka cikin daren nan nadauro al,wala nazu nayi nafila raka,a hudu,</p><p> Nan wurin na zauna har akai asuba </p><p> sam jikina bana jin dadin shi wlh,</p><p> Barci ya kara kwashe nan gurin da nai sallah asuba,,,</p><p> Wanan karon Aisha yar karama nagani ta kankamay ni ajikin ta,,, tana kuka,</p><p> Zubur natashi sai naga ashe har hasken rana yafito yau ban fita ba,</p><p> Cikin sauri nadan gyara jikina kodan make-up din danakan yi yau ban tsays yi ba,,,</p><p> Kitchen nanufa direct ina shiga sai naga yau mama mai abinci ce ita kadai tana aikin breakfasts taya ta nayi muna sauri don kada sheriff din mu yafito bamu gama aikin mu ba,,</p><p> Tun ina hakkuri har nakai ga magana nace ma mama yau babu wace tazo daga gidan hajiya wai ko lafiya</p><p> Ba,afi minti uku ba sai ga su sun shigo , daganin su suna cikin tashin hankali,</p><p> Ban kula sai cewa nayi aikin da muka sha jiya duk ya sa mu gajiya,</p><p> Nadauki kayan break din nafara kaiwa falo aiko na iske sheriff na saukowa daidai lokacin muka gaisa da shi sama,sama nakoma don in dauko sauran kayan</p><p> Abinda kune na yaji Sukaina na fadawa mama mai abinci yasani yanka wani irin ihu, daga inda nake,</p><p> Duk suka razana don basu san cewa har nadawo ba,</p><p> Yake jiki nayi nafadi ina ihu mai kunar zuciya,</p><p> Duk wanda ke gidan sauri take yi ya iso inda ihun nawa yafito,</p><p> Kusan ta,tare suka iso gurin,</p><p> Duk kan mu kuka muke yi har mama mai abinci,</p><p> Cikin tsawa Sheriff din ke tambayar mu abinda ya faru,</p><p> Sukaina ce tai karfin halin fada mai abinda yafaru da Rugaiyya jiya bayan tabar nan gida a hanyar ta na zuwa gida,,,</p><p> Shima ya shiga tashin hankali sosai wlh don baiji dadin ace ta sanadiyar shi hakan yafaru ba,</p><p> Inda na rakube jikin wani standing fridge ina kuka ya kalla,</p><p> Ya kau da kai don jin tausayi saboda ya tuna da labarin da Anty nawa taimai a madina lokacin da banda lafiya,</p><p> Nafisa duk da bata jin larabci tasan cewa wani abu munmuna ne yasamu Rugaiyyan,</p><p> Barin kitchen din yayi zuwa falo inda Nafisa itama ta rufa mai baya,</p><p> Da ya juyo ya ganta ya dakata, har ta iso yace mata, ke baki da tausayi ne abin kuka yasamay su , amatsayinki na mace yar uwan su baki tsayawa ki basu hakkuri,</p><p> Sai cewa tayi yo ni maizan masu tunda basa jin hausa basa jin turanci,</p><p> Ta kaici yakama shi yama rasa may zai ce mata, yaji sanyi,</p><p> Ga sautin kukana yana ji har inda yake tsaye, yana tayar mai da hankali,,,</p><p> </p><p> Muryan mama mai abinci ne naji tana cewa inda za,aga cikin shugaban nin mu na takari ai masu magana wata kila akwai yadda za,ayi sufitar da ita,</p><p> Jin hakan yasa hajiya laila ta fado min a rai,</p><p> Batare da bata lokaci ba na koma daki na na shirya cikin bakaken kaya irin namu nadauko takalmana Tommy nasa nadan gyara fuskana kadan jakata nadauka,</p><p> Nafita cikin sauri taxi natare nace akaini Masfala, by pass,,,</p><p> Tafiyan minti kusan hamsi yakai mu maspalan naba mai taxi kudi </p><p> Gidan hjy laila na nufa kai tsaye nasa may ta tana shirin fita, wai zata SHARMANSOOR gidan wata aminiyar ta batada lafiya,</p><p> Kallo daya taimin tasan ba lafiya,</p><p> Cikin tashin hankali take tambayana may yafaru,</p><p> Ina kuka nafada mata abinda duk yafaru da Rugaiyyan</p><p> Itama hankalinta yatashi sosai wlh,</p><p> Tashi mukayi zuwa gidan wani Alhj Aliyu bandi shugaban matasa na wanan erea din</p><p> Bayan bayani da mukai mai ne ya nisa yafara fadin akwai kudi ko da zasu bi sugani ko za,aiya fitar dasu,</p><p> Nace ma hjy laila duk kudin namu na wurin Rugaiyya dashi ta wuce,</p><p> Kassh yace yawani dafe kan shi, yace ashe ba zancen bi kenan</p><p> Kusan wuri uku mukaje amma zancen shine akwai kudi,</p><p> Daga karshe dayake hjy laila bata iya cin amana ba sai tace min in kyale su mudawo gida,</p><p> Gidan ta muka koma tai ta min nasiha ta kwantar minda hankali,</p><p> Muna nan zaune kafin in tafi mukaji ana sallama da hjy laila mun dauka ma ko maganar Rugaiyya ce aka samu wani labari</p><p> Da saurin mu muka fito shugaban matasan takari na uguwar da mukafara zuwa wurin shine yazo,</p><p> Yan dan wani sosa kai yana gyara yar falmaran da ya aza saman nalabiyan,</p><p> Hajiya tace mai Alhj bandy lafiya dai ko sai yace a,a dama nazo inji cewa ita wanan din a ina take da zama,</p><p> Kai haji bandy walahi kafita idona,</p><p> Kaida keda mata uku a ina zaka sa wanan din </p><p> Haba hjy kada muyi haka dake fa tace mai har hiya da haka ma sai muyi,</p><p> Inajin haka na banka mai wata irin hara na wuce cikin gidan hajiya,</p><p> Ban wani dade ba nai sallama da hajiya laila mata mai mutunci da karan ci </p><p> Taimin alkawarin zata zo gidan hajiyan mu don jin bayanin may ake ciki.</p><p> </p><p> Koda na isa gidan hajiyan mu a tsorace na samay su ita da umar da Aisha,</p><p> Suna gani na duk sukayo kaina suna kuka, </p><p> Tausayin su ne ya kamani har cikin raina tundai hajiya kuka takeyi kamar wace akaiwa mutuwa mai karfi,</p><p> Saida naga maran ce yayi nace zan koma gida saboda yanayin hanya,nai ma hjy alkawrin zandawo badadewa ba,,,,,,,,,</p><p> Ashe can gida kuma hankalisu duk ya tashi saboda rashin gani na da basuyi ba, din fita nayi batare da na fada ma kowa ba,</p><p> Ina shigowa gida nagan su hankali a tashe duk sunyi tsaye cirko cirko a wajen gidan </p><p> Fadawa nayi a jikin Yumma ina kuka mai kona zuciya cikin sauti mai ban tausayu</p><p> Dafani naji anyi a hankali nadan waiga sai naga sheriff din mu tsaye bayana handkerchief ya miko cikin dakiyar murya yace min kukan ya isa </p><p> A hankali nadan tsagaita kukan nawa, Almustapha yace ma abude masu yumma dakin ma,aikatn dake ta baya su zauna ciki kafin ansan abin yi,</p><p> Ina ji haka cikin kuka nace hjy da su Umar fa,</p><p> Wurin wa za abarsu,</p><p> Da Yumma suka tafi dashi hargidan namu sun samu har sun rufe gida ta kwan kwasa musu dakyat suga bude masu bayan muryan ta da sukaji </p><p> komi da muke bukata yumma ta ta dauko muna </p><p> bawani abinda zai iya nuna shedar cewa mun yi zama, agida koda anzo bincike,,</p><p> Sam bansan cewa anje dauko hajiya ba dasu umar,</p><p> Gani Aisha kawai nayi ta rugumay ni tabaya,</p><p> Wani irin dadi naji dana gansu tare da mu,</p><p> Ashe ko mungode Allah mun gode ma sheriff din mu, </p><p> Don cikin dare yan samay suka kawo muna farmaki don suna zaton cewa ba rugaiyya bace kawai a shiyan,</p><p> Koda suka shiga gidan namu ba kowa sai yan tarkacen mu na aiki,</p><p> Basu gane komai sukatafi don sun san cewa ko sun tanbayi mutanen uguwar ba su gane komai,</p><p><br /></p><p> Tunda akasa su,a ajirgi kasar, Niger jirginya je ya sauke, </p><p> Dayake ita tana da kudi tab ga jikin ta sai bata samu matsala ba sosai,</p><p> Motar zuwa Nigeria ta shi ga sai kano,</p><p> Da wayon ta tabar gida don haka bata sha wani wahala ba wurin gane gidan su,,</p><p> Mahaifiyar ta na daka a soron gidan su taji sallama </p><p> Tana waigawa sai taga wata yar gayu kamar Rukaiya amma dai wanan din tana da haske </p><p> Zuwa tayi da gudu ta rugumay mahaifiyar nata tana fadin </p><p> Ashe da rabon zan kara ganin ku ,</p><p> Nan ,da nan gida yacika da jama,a yan zuwa gani bakuwar makka,.</p><p> Kamar yadda takari kan dawo aimasu rade radin sun je yawon duniya ne hakane yafaru ga Rukaiya </p><p> Zancen ya bazu dan kauyen nasu Rukaiya tadawo daga yawon takari da tabi wata hajiya mai kudi saudiya,</p><p> Tadawo bata da komai, sai hakorin makka da tasa a bakinta,</p><p> Ita dai komai batace ba don yanzu ba lokacin bayani bane,</p><p> Saida komai ya lafa bayan kwana biyu cikin dare ta zauna da yan uwanta tai masu bayanin irin rayuwan da tayi a makka, </p><p> Tabasu labarin abinda hajiya tai muna da kuma yadda ta baro mu can,,,</p><p> </p><p> Sai bayan komai ya lafa matane tasamu wani malami tace ya raba muna kudin tsakani da Allah yadda baza ta cuta min ba.</p><p> Bayan an raba kudin sai tafara business da nata,</p><p> Saboda a lokacin duk matasan garin su maza, ba wanda ya nuna yason ta don gani sukeyi karuwan ci ne taje yi can,,,</p><p> Sai wani dan uwantane mai mata guda ace wa dashi hamza shine ma yadan nuna yana ra,ayinta,</p><p> Bata kulashi ba don tasan cewa baza tai zaman lafiya da matar shi ba don haka share kowa tayi,</p><p> Takama sana,ar ta haikam, taje kano tasaro kaya kala,kala zo kauyen su ta,saida,,,,,</p><p> Cikin hakane ta hadu wani dan kasuwa a kano wanda ya yaba da hankalin ta yanuna yana son ta da aure,</p><p> Ko shi Harunan da yazo neman aurenta saida aka ja shi gefe aka fada mai yakosan ta taba zuwa yawon duniya har kasar saudiya,</p><p> Duk da hankali shi yatashi sosai da jin wanan maganar sai yadan dake yana son ya kara gwada hankalin ta yagani,</p><p> Kamar ta sani bayan ya koma gida suna waya shine ta dan bashi labarin rayuwanta kadan,</p><p> Saida ya nisa tukun sanan yace mata ai an fada mashi akauyen su da sukazo,</p><p> Saidai shi yabari ne dama yaji daga bakin ta kozata fada mai,</p><p> Idan har bata fada mai ba to tabbas gaskiyan mutanen kauyen ne yawon baza ta,tafi,</p><p> Saigashi kin fada min da kanki,</p><p> Rukaiya nayarda dake dari bisa dari don bakowace mace ce ba zata iya fadin gaskiya haka,</p><p><br /></p><p> Kafin ayi bukine ta shirya tafiya zuwa sokoto,</p><p> Kamar yada akai mata kwatancen garin mu,</p><p> Da yake tafiyan safiya tayi sai ta isa sokoto da dan wuri wuri marance bai riga yayi ba sosai</p><p> Motar da zai kai ta dogon daji tayi shata ,</p><p> Ana batun kiran sallah magriba ta isa garin dogon dajin</p><p> Tambayan gidan inna yar kulu tayi batare da bata lokaci ba aka nuna ma driver gida ,</p><p> Har kofan gidan namu ya kaita</p><p> Yafido mata da kayan ta, taciro kudi tabashi tana godiya</p><p> Wasu yaran makwabtar mune da ke wasa saman yashin da aka tare gefen gida makwabcin mu,</p><p> Sutakira sukazo suka kwashe mata kayan ta zuwa cikin gida,</p><p> Ina dake alwala taga yara nata shigowa da kaya niki niki akai,</p><p> Sai kawai ta dakatar da alwalan tana kallon ikon Allah </p><p> Saboda dai yar matashirya matan da ke bin yaran inna bata taba ganin ta ba,</p><p> Asalima dai ba yar gari bace, ita daganin ta</p><p> Sundan gaisa sama sama sai anty tace abata buta taje tayi alwala</p><p> Ba musu inna ta bata butan itama,,,</p><p> Tabar man kaba kato inna ta shimfida masu a waje don suyi sallah</p><p> Bayan sun gama ne sun gaisai sai shiru ya biyo baya,</p><p> Anty ce ke tanbayar Hafsat da datti kanin mu </p><p> Mamaki inna tayi da jin bakuwar birni har tasan sunan yaranta</p><p> Can dai inna ta daure tace ban fa waye kiba yar nan,</p><p> Rugaiyya tai murmushu tace daga wurin fadiman ki nake,</p><p> Wacce ke saudiya zaune</p><p> Cikin kidima inna ta kara matsowa kusa da Rugaiyya tana rike ta tana fadin ina fadima,</p><p> Allah kada ka kasheni sai ga fadima na roketa gafara,</p><p> Rugaiyya ta kwashe duk labari na da ta sani ba inna har zuwa ranan da aka kamata,</p><p> Saida inna ta nisa san nan tai ajiyar zuciya mai karfi </p><p>Sai kuka shaaaaaaaaa</p><p> </p><p> Nandai suka kusan kwana suna labari kamar sun san juna dadewa,</p><p> Tunda safe tadauko kudina taba inna mu ,.</p><p> Sam inna tace bata karba takoma dashi can biirni taita juyawa,</p><p> Saida kyat akasamu ina tadan dauki dubu dari uku kawai daga ciki,</p><p> Anyi ta zuwa gani bakuwar inna,,</p><p> Dakuma son jin wai fadima na makka,,,,,,, </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p><br /></p><p>✈✈✈TAKARI✈✈✈ </p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 4⃣7⃣</p><p> BY</p><p> </p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p><br /></p><p> Son duniya bala,i ce don babu komai acikin duniya fa,ce rudin shedan, </p><p> Kusani cewa duniya saida kudi, lahira ko sai da hali mai kyau,,, </p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,</p><p><br /></p><p>Zaune nake saman gado na cikin wasu rigar barci light pink, wando da riga,</p><p> Nadan sa ma kaina wani hula mai hooking din kan mutum,,,, baka jin komai sai karan A, c dake ta faman aiki,</p><p> Kusan irin zafin da ake yi a wanan kasan,</p><p> Shiyasa idan kana tafiya zaka ga tankin ruwan sanyi masu kudi sun aje gefen gidajen as a sadakatujar, sai dai mutun ya tsiyaya yasha ya wuce,,,</p><p> Shiyasa koda yaushe,AC kune yake muna,,,</p><p> Aisha ce a tsakiyar kafafuna tai barci sai dan buga mata kai da nake yi don ta samu tayi barci da kyau kamar yadda uwaye kewa diyan su,,,</p><p> Wasu hawaye masu zafi ke tsiyayo wa daga ido na, babu kakauci,</p><p> Kallon yariyar nake yi wace tausayin mu ya ke kara sa hawayena zubu min, </p><p> Yanzu a haka zamuyi ta zama ba wani galihu atare da mu </p><p> Kulun gamunan kamar wasu marasa gaskiya, ashe mu,</p><p> Kamshin da naji yasa nasan kowaye a dakin nawa,</p><p> Kallon agogon da ke dakin nawa nayi goma da rabi na dare yanzu,</p><p> Sheriff nace cikin siririyar murya, gyara kan Aisha nakeyi don in tashi ,</p><p> Hannu yadaga min alamar in zauna inda nake,</p><p> Ina zaune shima yasamu gefen guda abakin gadon yazauna,</p><p> Batare da ya kalleni ba yake magana,</p><p> Bazaki daina wanan kukan haka ba ko,,,,, ko so kikeyi ki shiga cikin wata matsala, wanda zai saki cikin wani hali,</p><p> Yakamata yanzu ki bidi mafitar da zai fishe ki,ne baki zauna kina wanan kukan ba,</p><p> Dan sheshekan kukan nake yi kadan kadan </p><p> Muryan shi nakara ji yana cewa kin taba yin karatu ne kai na kada mai alamar eh</p><p> Nafada mai ko aji nawa nake agida kafin gajiye ta zo dani kano,</p><p> Sai kuma karatun da na a Riyadh wanda baban Nailabin yasa ni,,,</p><p> Ina takardun naki, suke, nace mai suna nan </p><p> Ya mike yana fadin da safe ki kawo min indiba, ingani,</p><p> Ki kwanta hakana ki daina wanan kukan zan san yadda za,ayi ku koma gida duk kan ku Insha Allah,</p><p> Banko yi mai godiya ba yafita gami da jamin kofar daki na,</p><p> Koba komai naji dan sanyin wanan maganar tashi sosai </p><p> Don ko waye ke cikin wani hali yana son maidan bashi magana,</p><p> Don haka gyara ma Aisha kwanci nayi najawo bargo muka shige ciki,</p><p> Ba da wani dadewa ba barci yadau ke ni tare da dokin gobe yayi,,</p><p> </p><p> Washe gari ban fito ba saida nayiwa Aisha wanka muka gyara jikin mu,</p><p> Nida ita gurin da hjy mu take muka nufa don mu gaishe ta kafin in fara aikina,</p><p> Umar na dakin tare da hajiyan mu, nan nakaishi ya kwanta don kar mu barta ita daya,</p><p> Saboda yaron nada kwazo yana kuka da hajiya,</p><p> Wanka nasa shi yayi bayan na gyara masu daki yadda yakamata,</p><p> </p><p> Saida nadiba komai na abincin gidan da aka dafa,kamar yadda ya kamata sannan nakai saman tebur din su,</p><p> Nashirya komai neat ,bandade ba naji fitowar su,</p><p> Nafisat na bin shi a baya tana cewa gaskiya ita ba tagane ba duk inda zata sai ace dole saita fita da wanan yariyar</p><p> May ake nufi da ita ne ko yana nufin wanan yarinyar ta fita wayewa ne,</p><p> Sai alokacin ya juya yadan dube ta cikin takaici,</p><p> Ya kuma juya ,yacigaba da tafiya zuwa dinning table , yaja kujera yazauna,</p><p> Saida nagama hada mai abinda yake son ci ina kokarin wucewa,,,</p><p> Yace min in shirya zamu fita da nafisat unguwa cikin ladabi na ansa mai da toh,,,,</p><p> Har na juya zan wuce sai yace min,,, ina takarda da yace in bashi, cikin sauri naje nadauko mai nakawo mashi</p><p> Batare da ya duba ba yasa cikin briefcase din shi yarufe,</p><p> Wani wawan harara nafisat ta watso min daga inda take tsaye,,,</p><p> Niko, ko in,kula nai mata,,,,</p><p> Dakina na nufa na dan kara gyara jikina sama,sama,</p><p> Natura Aisha wurin su hajiyar mu har in dawo</p><p> Duk cikin sauri sauri nake,komai don kada in sa nafisa jirana har inyi laifi,</p><p> Aiko ina zuwa a mota nasamu, su ita da driver zaune suna jira na </p><p> Ina ganin su sai nadan ji shock kadan amma sai na dake ban nuna ba,</p><p> Zaune take tana dakilan wayan ta ko kallo ban ishe taba tayi wani kicin kicin da fuskanta,</p><p> Nadan masu sallama nagaishe ta,</p><p> A wulakance,ta ansa min gaisuwar nawa, gami da watsa min harara,</p><p> Tace min sai ki shigo mutafi tun dazu muna jiran ki,</p><p> Sai lokacin da kika ga dama zaki fito,</p><p> Ke wanan yariyan na lura da ke tunda kin samu shiga gurin maigidan shine,</p><p> Kike kokarin hada kanki da ni wlh ni maganin ku zan yi,, yar kauye kawai matsiyaciyar banza</p><p> Sai na gwada maki cewa tsintacciyar mage bata zama mage,, </p><p> Naikamar banjita ba,ban masan dani ta ke</p><p> zancen ba ,,,,</p><p> Ina ganin haka na bude gaban mota nashiga abina nai ko in kula da ita,</p><p> Saina kama magana da larabci da driver ina ce mai ina zamu ne,</p><p> Yace bata fada mai ba shima, kawai sai muka sa kai muna ta tafiya,</p><p> Haka muka hau titi babu wanda ke maganar cikin mota,</p><p> Har mukayi dan nisa da gida </p><p> Danaji shirun yai yawa a motar, sai kawai na jawo wayana dake cikin jakata na fara, game,,</p><p> Aiko tana kyala ido taga wayana da nake game da ita,</p><p> Ji kawai nayi ta wauto wayar daga hannu na tajuya tajuya sai naji tayi tsuki kawai ta wurga min saman cinya na,</p><p> Mashal plaza muka je cen kusa da top ten plaza,</p><p> Kayan make-up tadan saye da sauran kayan bukatun mata,</p><p> Muna futowa muka shiga cikin top ten ,</p><p> Anan naga kayan yara masu saukin kudi sai na dan sai ma Umar da Aisha </p><p> Saboda duk kayan su mubar su can gidan mu,</p><p>Kuma badamar wani yaje ya kwaso masu,,,,</p><p> Ina kallon anty Nafisa na saurin zuwa biyan kudi don kada ta hada danawa,</p><p> Dariya tabani kawai don inda sabo nasaba da halinta, don komai nata ba mai ci agidan nan,,,,, nidai na biya kudina cikin chiefest price, saida nayi mamaki, jin kudin cikin sauki haka,na,,,</p><p> </p><p> Bayan mundawo, gidane tawuceni fuuuu zuwa cikin gida, kayan nakwaso zuwa dakin ta,</p><p> Koda nashiga nata nasamayta har ta dan kwanta saman gado, tana waya,</p><p> Daidai lokacin tana fadin wlh duk tsiyar da zamuyi salwa saidai muyi </p><p> Mutun ace bai san darajan mace ba shi nashi kawai zuwa aikini kodyau,she ,,ni gaskiya ban iyawa,</p><p> Saida kawai ace wai yar aiki ce zata raka mutun don kitifi,</p><p> Kayan da ta sawo nake gyarawa asaman dressing mirror dinta </p><p> Amma azahiri ita nake sauraro ba wai aikin nake yiba,</p><p> Yaushe ne zaki ba da sakon a kawo don in fara barbada wa dan banza,.</p><p> Wani iri naji lalai wanan matar batada dama aiko zamu kwasa da ita ke nan,</p><p> Muryanta naji ta cigaba da fadin ai ina nan ina kokarin binciken inda takardun suke fara daukowa</p><p> Kalonta nayi cikin sauri wanda ita din ma,kallo na tayi batare da zargin ko naji may take cewa ba,</p><p> Tai min nuni da hannu cewa in wuce,</p><p> Daki na nakoma cikin yanayin damuwa, don nasan cewa akwai aiki ja agabana,</p><p> </p><p> Tundaga wanan ranan nafar sa ido ga al,amuran nafisa sosai,</p><p> Tundai ma danaga wata bakuwa tazo wurita daga Nigeria </p><p> Wai umurah matar tazo shine aka bata sako takawo wa nafisan,</p><p> Aiko zargina yazama gaskiya don wasu magunguna ne kuli kuli a,kabata</p><p> Bayan kwana kamar uku, da kawo sakon Allah yabani sa,a ta tafi ganin masaukin bakuwar </p><p> Anso zuwa dani sai na kwanta nace banda lafiya,</p><p> Suna wucewa na kwashi sakon maganin sai masfala gidan hajiya laila,</p><p> Duk wanda muka bude an rubuta bayan nin shi da yadda zatayi amfani da shi,,,</p><p> Hjyan ce tai min dabara tasamo kayan mata masu kyau muka sa mata cikin kowani leda, ,,,ba wanda bamu canza ba </p><p> Nadawo gida na mayar mata da abinta inda taje,</p><p> Naci gabada harko kina,</p><p> Ina kallon ta lokacinda take barbada mai wanda akace ta sa mai ga abincin shi,</p><p> Dariya yakamani nagudu zuwa dakina naci dariya na can kamar in nutse,</p><p> Washe gari koda nashiga in gyara mata daki na isketa tayi daidai sanan gado tana wani lagabewa,</p><p> Aikinta takeyi waya, tana fada ma salwa cewa kwanan nan batasan may yasamu Sheriff ba don bai ko tausaya mata, </p><p> Dariyan keta yakamani </p><p> Nace lalai hjy laila takai tsuhuwar bariki,</p><p> </p><p> Yanzu hankalin mu kwance gaskiya don mun rage wani fargaba kasan cewar muna da mafaka mai muhinmanci,</p><p> Baza,a taba zargin muna da halaka da takari ba in mun fita don duk inda zamu da motane ba wani labe labe ko bin lungu lungu, gudun kada akama mu,</p><p> Yauma nafito ne don in sayi kayan abincin mu da yadan kare,</p><p> Ina cikin wani shago sainaji hayaniyar mutane a kofar shagon,</p><p> Da sauri na biya kudina nafito bakin shagon da ,</p><p> Wasu takarine askarawa suka biyo su uku gudan wai tana suyan dankalin turawa sukuma saura su tsaye abakin titi suna saida gumama da rana,</p><p> Suna ihu suna bidan agaji amma ba wanda ko yakalli inda suke,</p><p> Inaji yar matashirya wace muna iya yin wari da ita tana fadin cewa uwar da ubanta duk suna gari ita ba takari bace,</p><p> Cikin dakiyar zuciya ganin kowa yaki ceton ta naje gurin nace masu ai,yakamata suyi mata uzuri tunda sunji abinda tace</p><p> Jinda sukayi larabcina tsab bakamar na yan koyo ba yasa sukadan saurareni,</p><p> Suka kalli yanayina sai sukaga banda alamar shigan banza </p><p> Nan shugaban nasu yace min intanbayeta ina iyayenta, </p><p> Karya nai masu nace iyayen ta suna nan harda kakaninta ma nabasu wrong address ,</p><p> Wanan yariyar tasamu tasha da kyat wurinsu nima dim gabana sai faduwa yakeyi,,,,,</p><p> </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p><br /></p><p>✈✈✈TAKARI✈✈✈ </p><p> 👣👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 4⃣8⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p> </p><p> Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Saida naga cewa mun daina ganin yan bagaladin mun masu nisa sosai</p><p> Daidai,Lokocin na danyi ajiyar zuciya, nakalli yariyar da muka kwato daga, hannu yan bagaladin,,,,,</p><p> Wace sai dan she shekar kuka takeyi tana, ajiyar zuciya kai da kai tanayi, tana dan share hawaye, a fuskanta,,,</p><p> Dafata nayi ina Tabayarta ko daga wani unguwa take</p><p> sai da ta dan share hawayen da ya dan silalo mata,</p><p> lokacin take ce mun ai daga wani dan kauye dake kusa da gari, take shigowo ,</p><p> Kauyen baida nisa da cikin gari can tsakan wasu duwatsu yake, larabawan daji ke zama agarin</p><p> Inda Mafi yawan yantakaru sun fi labewa a kauyu, ka mafi kusa da garin makka, don gudun kora,,,</p><p> Gida nazo da ita, nadan bata abinci ta ci ta, huta, amma duk a firgice take saboda tayi fitar kutsun yau,</p><p> saida naga hankalinta ya dan kwanta,san nasa a,kaita har inda zata samu motar da zai kaita kauyen na,su,</p><p> Tawuce tana ta zabga , muna godiya tana sharan fuska,,,,</p><p> Muna tsatsaye a waje duk jikin mu yai sanyi </p><p> Don muma mun san cewa bamu wuce hakan ba,,,</p><p> Duk sai ta bamu tausayi wlh,,,, wasun mu harda kuka,</p><p><br /></p><p> Washegari dayake ranan weekend ne saboda su kasar saudiya,Alhamis da jumma,a, ce weekend nasu,,,,</p><p>Don haka nasan cewa mai gidan yana gari don duk sallar jumma,a a garin makka yake yin ta,</p><p> Hakane ma yasa yafizama a garin fiye da ko ina, don yana yawan yin dawafi duk ranan jumma,</p><p> Shiyasa mukatashi dawuri don muyi aiyukan mu saboda tun karfe goma yake wucewa masajid </p><p> Saboda koea yassn cewa idan kakai shadayan rana da wuya kasamu cikin masallacin saidai kasamu gefen masallacin ta waje koshi a mamatse,,</p><p> Don haka, Tunda safe natashi don mu yi aikin mu cikin lokaci kafin ya fita,</p><p> Nasan cewa yana dakin motsa jiki don halinshi hakan da yadawo daga sallah asuba indan sungama karatun Al,kur,ani maigirma,</p><p> sai ya sauya kayan shi zuwa na games wear,,,</p><p> Idan nasan yana dakin yin exercise ka,ida ne dole inkai mai cup da goran ruwa mara sanyi guda sai kuma milk mai sanyi ,sanyi guda,</p><p> A gefen wani dan standing table dake gefe tsaye nake aje mai,</p><p> Duk da nasan cewa bai shan koda rabin kofin milk din saidai hakan bai hana kulun in aje mai ,milk din ba, amma,na ruwa sha, kan shanyewa yakeyi kafin yafito,,,,</p><p> </p><p> Yauma haka dine ya kasance,,, ,yana tsaye yanata tafiyan daba iyaka bisa exercise machine,din shi,,</p><p> A hankali na shigo dakin hannu nadauke da tire din drinks,</p><p> tunda nashigo nagan shi saye da dogon wando irinta maza masu exercise, da bakar singilati, sai yar karamar tawul da ya, rataya saman wuyan shi,,,</p><p> A hankali na isa saman dan tebur din na aje mai dan ture din da na hado mai drinks din ciki,</p><p> Na juya don in fita dakin,</p><p> Karar waya shi da yaji,,,yasa shi dan tsagaita tafiyan da ba tsayi din, dayakeyi,,,</p><p> Da hannu ya nuna min gefen da wayar ke yar tsuwa,,,</p><p> Nagane nufin shi indauko mai ita yake nufi,</p><p> Wayoyi ne kusan guda uku a wajen, ashe,,,</p><p> Ita mai tsuwar ita ce nadauko mai, ashe wanyan mutanen Nigeria ce, sunan yan uwan shi ne kawai aciki sai abokai shi, yan kasar Nigeria,</p><p> Malam baba naga an rubuta baro,baro, a fuskan wayan</p><p> Ina mika mai wayan yadiba yaga kowa ne ke kiran shi yanzu cikin wanan lokacin daga nigeria </p><p> don yasan cewa ana batun sallah asubu ne yanzu haka a Nigeria </p><p> Tunda munan a,lokacin karfe bakwai darabi nasafe, ne</p><p> Wanda yayi, daidai da karfe hudu darabi na asuba, a Nigeria,</p><p> Yana ganin sunan malam saida yaji gaban shi yafadi, don yasan cewa ba kiran lafiya bace</p><p> Don iyakar malam din yakira shi da misalin karfe biyun rana na nageria lokacin muku ma ana batun yin sallah la,asar</p><p> Daidai lokacin danaga yadaga wayar</p><p> Nikuma ina shirin barin dakin sai naji yana fadin Innallahi, </p><p> Da karfi na waigo don nasan cewa wanan kalman ba karamar kalama bace ,sai idan tashi hankali yasamu bawan Allah,</p><p> Ganin ina kallon shi cikin tashin hankali yasa shi dan controlling din kan,shi,,,</p><p> Jinayi yana fadin tun,yaushe ne ciwon yafara mata haka malam,</p><p> Sainaji ya ce dan Allah malam akaita asibitin Maiduguri zai ma Abba waya kafin ku zo, asan abinyi,</p><p> Karshe dai yace ma malam din insha Allah gashi nan zuwa, shima,</p><p> Batare da yadauki ruwan da na aje mai,ba yasauko daga machine din,yanufi hanyar fita, dakin yana fadin ,</p><p> Kiramin Almustapha, da sauri,,, pls</p><p> Bayan shi nabi cikin sauri don zuwa kiran almustaphan, din</p><p><br /></p><p> Kafin wani dan lokaci komai na tafiyan shi,an kan mala mai, anshirya komai zuwa Nigeria</p><p> Su Almustaphane suka kaishi jidda don booking din jirgin su kayi tun kafin su iso ,jidda wasu ne sukayi mai hanyar komai, don sun saba dashi,tun baro Nigeria dayayi zuwa nan</p><p> Suna isa sunyi sa,a dama an mai booking din jirgi</p><p> kusan daidai time din da jirgin zai tashi su, suka iso wurin</p><p> </p><p> Mudai mun san cewa ba tafiyar lafiya sheriff, yayi wanan tafiyan ba</p><p> don ni agabana akai mai waya din, akan mara lafiyan da yatafi,</p><p> Amma sai gashi ga mamakin mu,</p><p> munga matar gidan sai busha shanta takeyi,ba abinda yadamayta,ita</p><p> Don har wata kawa tasamu wai ita yar lici,,,, wata fara duk man bilicin ya bata mata fuska kamar kuturuwa, </p><p> Tana magana tana kashe ido tan turo baki, wai ita yar takari,,</p><p> Saboda yanzu kusan sau biyu kenan ina ganin Yar lici agidan namu,</p><p>Wace hararane kawai ke rabani da ita, idan tagan ni,</p><p> Don ina ganin ta sai naji kawai batai min ba don wata irin gogagiyace da ganin ta,,,</p><p> Tunda sherrif din mu ya wuce zuwa nigeria </p><p> suke zama a falo suna ta sa kade kade da raye raye dasu, wake,waken su ,na bin rawar,</p><p> Mu ko, Sai, Abinci da muke ta aikin dafawa, kala kala,</p><p> Don basu koshi sam sanan</p><p> Ga wani irin shewa da sukeyi kamar an gafarta masu, zunuban su</p><p> Yau duk nagaji da aikin da mu kasha saidai kuma idan na tuna cewa sheriff din mu yayi tafiya cikin tashin hankali sai inji duk zuciya na ta min,suya,,,</p><p> Duk da bansan koma may ye matsalar ba, ,hakan baisa nadaina jin bacin rai ba,don nasan ba ta kyauta wa mijin nata ba</p><p>,Don inga mutunci ai duk abinda yasamay shi ai yasamayta, itama,,,,</p><p> Amma sai ga amatsayin matar shi tana, ta holewar ta, ba abinda yadamay ta ita,,,,,</p><p> Duk gidan kowa sai mamakin ta yakeyi, don dama da ganinta kaga tantiriya,</p><p> </p><p> Tafiyan shi da kwana biyu ina zaune dakina ina gyara ma Aisha kai sai naji wayan intercoms na dakina ya na ruri da alamar ana bida na afalon, gidan,</p><p> Batare da bata lokaciba na isa falon, cikin sauri,</p><p> Almustapha ne nagani tsaye yana jirana da waya a hannun shi </p><p> ,ina isowa yamiko min wayar, dake a hannun nashi,wace dama a kune take nikawai ake jira inzo in ansa,,,</p><p> Nakara wayan a kune na ina mai sallama,</p><p> Muryan sheriffudeen din muna ji cikin muyar mara sauti daji zuciyan shi badai</p><p> yana mai kara yi min sallama shima,</p><p> Nakarba da wa,alaikumu salam,</p><p> Yace min don Allah yana son in taimaka mai in gyara mai wasu dakuna daga cikin gidan</p><p> wasu dakuna ne ke cikin gidan da baki ke sauka wanda ke kusa da shiyan nafisa,</p><p> Sai kuma yacigaba da fadin,</p><p> Kuma in yi kokari don Allah, in,bidi abincin da masu ciwon sugar ke ci in,tanadar mai su agidan kafin ya iso,,,</p><p> Cikin siririyar muryan da take dauke da kama da kasala,</p><p> Yace ina ji na ce eh ina madaga mai kai kamar yana gani na,,,, yace min</p><p> Idan har ina bukatar kudi in tamabayi Almustapha zai bani,</p><p> Sai dan shiru ya biyo baya,saina ji yana magana,,</p><p> Yace yaji ance nafisat bata gida kuma ko jiya yakira an fada mai cewa tafita,</p><p> Saina ce mai nayi ai badadewa zatayi ba yanzu zata dawo,,,,</p><p> Cikin tsawa yake fadin kira na ukune fa yai mata yanzu </p><p>Yakare da fadin ina fatan kin fahinci duk abinda nace ai,min ,,, </p><p> Cikin sanyin murya nace mai to insha Allah za,a yi,</p><p> Daga karshe kuma nai masu fatan iso wa lafiya, tare da</p><p> fatan Allah yaba mara lafiya, lafiya ya ansa da fadin ameen ya gode,, yakashe wayan,,,</p><p> Almustapha na mika ma wayan sai yake ce min sheriff yace ya bani wasu kudade dazanyi amfani da su,,,,</p><p> Kudin da yabani sai naga suyi mugun yawa don haka,saina, nadauki dai wanda zai i,she ni </p><p> na mayar mai da saura,,, </p><p> Mamaki yakamashi saidai baice min komai ba ya juya kawai ya wuce, abin shi,</p><p> Nikuma nakoma cikin gida ina tunanen maganar da muka yi da sheriff din, </p><p> Ashe mahaifiyar Sheriff ce bata da lafiya ciwon sugar ya kamata,</p><p> Shine ta rikice masu, acikin dare har hankalin malam mijin ta yatashi,</p><p> Don yadda ciwon yabugeta sun dauka ko bazatayi ba</p><p> Shine malam din yakira sheriff din a rikice yana fada mai abinda yasamay ta,</p><p> Asibitin FMC Maiduguri aka fara ajeta kafin sheriff ya iso, daga saudiya,,</p><p> Mahaifin shi Alhj lawal zannah shi yadauki dawai niyar duk wani abinda akai mata a asibitin </p><p> Ya basu kulawa sosai yadda duk yakamata, yanu cewa ita din kaunar shi ce ta ji,</p><p> Isowar sheriff din mu keda wuya yaga halin da mahafiyar nashi keci yasa duk hankalin shi yatashi sosai</p><p> yasa akai mata biza ita da malam mijinta </p><p> Da,kuma yan kan,nen shi mutum, biyu zuwa saudiya </p><p> don mahaifiyar nashi,tazo saudiya adiba lafiyar jikinta da kyau aji komay ye matsalar da ke damunta,</p><p> Shine ya dinga bugo ma nafisa waya don ya fada mata abinda yake so ai masu kafin ya su iso, da bakin nashi,</p><p> Ita kuma bata gida yanata bugowa anace mai tafita,</p><p> Ranshi ya baci sosai yana mamakin ina taje haka cikin garin da bata san kowa ba,</p><p> Duk taka tsantsan dayakeyi a,kanta baihana ta yin abin da ranta ke so ba,</p><p> Don a bincikin da yasa bashir ya yi a kanta ya,fada maicewa tana shan drugs, tun a makarantar da tayi a kasar waje,,,</p><p> Baida yadda zaiyi ne saboda umurnin mahaifin shi yake bi, shiyasa ya aureta har ya zauna da ita dole,</p><p> Ashe shine dalilin da yasa bai yarda ta fita ita kadai sai tare da ni,</p><p> Wanan maganar Sirun sune shiyasa baifito fili yace ga abinda yake so indinga kula mashi da ita ba,</p><p> Sai dai yasan cewa ga wayo da irin hankalina zan iya kula da duk wani movement nata,</p><p> Ita wanan kawar nata da samu salwa ce ta sa a,hadasu asaudiyan don matar ta iya harka so sai,</p><p> Zata dinga samo mata kowani irin abu take bukata ,,, </p><p> </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 4⃣9⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost true life story</p><p><br /></p><p> Duk wani shiri da yakamata muyi mun kammala shi ko zuwan bakin namu kawai muke jira isowar su</p><p> Sai misalin magrib suka iso garin kasan cewar ba su sauka da wuri ba,</p><p> Mun, masu taro na mutunci yadda yakama ta, mu nu,na namu kulawan gare su so sai,,,</p><p> Don duk kusan wanda ke gidan a lokacin mun fito waje don taron su,</p><p> Jinda kowa yayi cewa mahaifiyar cikon sheriff ce bata da lafiya za,azo da ita,</p><p> Suna fitowa a mota nariga nasan cewa motar da almustapha ke ja itace za,a sata aciki don haka gurin motar na nufa,</p><p> Dan jin kadan ba,a bude motar ba, hakan yasa muma mukayi tsatsaye cirko cirko a wajen,</p><p> Gaban motar nanufa don inga ko may yasa mustaphan bai bude kofar ba,</p><p> Ina zuwa gurin na rike hannu motar kenan sai naga an bude gefen driver,</p><p> Maimakon inga mustapha ke jan motar sai naga Sheriff din mune yajawo motar dakanshi,</p><p> Jayewa nayi kadan don in bashi wuri ya fito, ina mai sannu da zuwa,</p><p> Yana mai ansa kuma hankalin shi naga ya bude gambon kofar motar tabaya da ke ta daidai saitin wurin zaman driver,</p><p> Wata yar matace wace bazan iya cewa taikai dadtijiwa ba take kokarin ta,fito daga cikin motar,</p><p> Gurin na isa da sauri na don in taimaka mata wanda hakan yai daidai da shima sheriff ya miko hannu shi don ya taimaka mata,</p><p> Batare da na damu da inbarshi ya taimaka mata ba nai azamar riko mata kafadar ta ta baya kandan </p><p> Sainaji tadan yi wani irin ajiyar zuciya, kadan tare da fadin Alhamdullahi ala kulli halin,</p><p> Ina rike da gefen kafadar , ta har zuwa dakin da sheriff yace mu gyara masu,</p><p> Wanda yafi dan girma da kayan alatu acikin shi, na nufa da ita </p><p> Sai sannu kowa ke mata,</p><p> Shiko sheriff tunda yaga nazo kamata sai yabar min ita don yasan cewa zan iya,, </p><p> Kuma ganin dayayi a hankali nake takawa da ita yasa hankalin shi ya kwanta,</p><p> Amma yana bin mu abaya a hankali shima,</p><p> Kujeran dake dakin na zaunar da ita sama a hankali,,</p><p> Sai a lokacin da naga ta zauna sanan ido yakai ga sauran abokan tafiyar na su,</p><p> Wani dan dattijo ne baki dogo aje dan gemu mai rabi fari da baki yarata wani dan jan kyale a wuyan shi</p><p> Dagani koba fada maka ba kasan cewa shiga ce irin ta shehunan mu na Nigeria,</p><p> Bayanshi kuma wani matashi shine, baki cikin shigar wandon jeans dawata riga baka anyi rubutu da wani abu kamar gold cikin manya haruffa,</p><p> An rubuta we are d leaders of tomorrow,,,,</p><p> sai wata yarinya wace zan iya cewa chuculate colour ce ita,</p><p> Tasa wani buje da rigar na less, ta sa hijab baki saman kanta, tana rike da jaka, baka again,</p><p> Ganin mara lafiyan ta zauna duk suna kanta suna mata sannu yasa ni fita dakin don in gabatar masu da dan abin sha kafin su zo cin abincin su,,</p><p> Daidai zan fita yar bakuwar budurwan tace min dan Allah ina son in dan kewaya pls</p><p> Saida nadan saurara da kyau nagane hausan nata,</p><p> Bayin da ke manne cikin dakin na nuna mata,</p><p> Koda nafito daga bayin don in fita zuwa, dauko masu drinks sai na samu,</p><p> Sheriff din mu ne, rusune gwaiwa bibiyu, akasa, gefen kan mahaifiyar tashi saitin kanta yana mata magana cikin tausayawa,</p><p> Shikuma dattijon ya saman kujera kusa da kafafun ta,</p><p> Drinks nakawo musu cikin tire, na aje masu a saman stol </p><p> Duk da cikin dare suka iso hakan bai hanani gabatar masu da abincin lafiyyae da muka hada masu </p><p> Tun misalin karfe biyar na marance, mukayi masu komai </p><p> Har ita mara lafiyan nida kaina na hada mata abincin ta,</p><p> Agabanta na hada mata abincin nata, wakene sai ganyen lansir da kore da nadan hada mata dashi naimata shi ruwa ruwa sai kaza danai mata gyara nadaban yadda nasan cewa zata dan iya ci,,</p><p> Alhamdullahi do gaskiya ta dan ci abincin sosai </p><p> Sunyi mamaki don sunce rabon da taci abinci maidan waya haka yadade,</p><p> Natsiyaya mata ruwan Apple da carrot, wanda na markada wuri daya sanan nadan tace mata shi,</p><p> Duk iyalin nata nagefe suna kallpn yadda nake fanam dawai niya da ita,</p><p> Cikin larabci sheriff yace min in kai wayan sauran dakunan su shi malam zaizauna da mama a wanan dakin ne nasan da toh,</p><p> Lokacin shima yafito daga dakin suma bakin ni suka biyo bayan yai masu bayanin cewa zan kaisu dakin cikin harshen Kanuri,,,,,</p><p> A falo sukayi kicibis da Nafisat wace dawo wanta ke nan daga wurin da taje,</p><p> Idonta yayi jawur kamar garwashi, sai wani dan rausayawa takeyi indan ba ka gane ba zakace she is normal,</p><p> Kallon mamaki yake mata don da jiyakeyi bawai ya gaskanta bane,</p><p> Don shi mutun ne mai afani da badili ba zahiri ba,</p><p> Zuwa tayi ta batun rugumay shi tana fadin habibi ,,</p><p> Yaushe ka iso,</p><p> Ai baka fada min cewa kana hanya ba,</p><p> Yanzunan nadan fita,</p><p> Jakar ta na hannuta da ke batun faduwa na karban mata zuwa daki,</p><p> Nadan yi saurin ce ma, sheriff din mu,wani daki zan kai wanan bakon saurayin,</p><p> Sai nuna min yayi da hannu batare da yayi magana ba,</p><p> Yandan bita gefenta yawuce zuwa sama, ranshi a bace,</p><p> Dakin da ke kusa da nawa nakai yar budurwan sai saurayin dake can hanayar fita daga falon,gidan,,</p><p> Na nu makowan su inda zai dinga yin komai agidan,</p><p><br /></p><p> Daki ya shiga jikin shi a san yaye saboda tsanan bacin ran da yashiga donganin yadda nafisa ta koma,</p><p> Gashi inba idon shi ke mai gizo, ba yaga har rama tayi gashi ta danyi duhu ,ta yi baki ,,</p><p> Itace ta shigo dakin nashi cikin irin dauriya nan</p><p>na yan kwaya,</p><p> Tana fadin ya hanya ya mutanen, takama nuna sama da yatsan ta maganar nata yaki fito wa, </p><p> Toilet ya fada yabarta nan tana shirmay ta,</p><p> Alwala yadauro daniyar zuwa masallaci </p><p> Kwance yasamay ta saman gadon shi tana ta nasarin barcin ta hankalinta kwance,</p><p> Tsaki yaja cikin takaici, yafita yabar mata dakin,bata masan inda take ba,</p><p> </p><p> Kafin in kwanta barci danaga shehi a falo tare da sheriff din mu,</p><p> Sai na koma wurin, </p><p>Ummi, na is,kete kwance tadan dun kule waje guda,</p><p> A C dake aiki naje direct nadan rage ma karfi,aiki,</p><p> Dago kai tayi tana min godiya, </p><p> Tambayar ta nayi ko akwai abinda take so kafin mu kwanta</p><p> Duk da tace a,a saida na koma naje na hada mata kayan tea na aje masu adakin sa masu kayan kamshi a dakin sai ruwan wanka da na hada mata,,</p><p> sanan nai masu saida safe nafito,</p><p> Ina fitowa muka hadu da sheriff a kofan dakin zai shiga shima yai masu saida safe,</p><p> Nadan rusunna na gaishe shi, hannu kawai yadan daga min kamar kulun, batare da ya ansa da baki ba,</p><p> Yana shiga yaga yadda na kara gyara masu ko ina ga kuma kayan tea da na hada masu saman wani dan stol</p><p> Dadi yaji so sai cikin zuciyar shi don baiyi tsan manin hakan ba sam,</p><p> Sai gashi yar karama dani nayi abinda yadace ace matar gidan ce tayi shi,</p><p> Washe gari sheriff yana dawo daga gurin sallah dakin da su yaghana suke ya nufa ya diba lafiyar ta, Alhamdullahi jikin yadan yi mata sauki sosai,</p><p> hakan ya da yagani yasa shi dan kwantar da hankalin shi,</p><p> Inda yace masu zai je ya shirya dom su je asibiti da wuri,</p><p> Muma,dai Washegari tunda safe muka tashi tunda munsan cewa munada baki agidan hakan yasamu hi samakon yin aiyukan mu,</p><p> Koda sheriff ya fito ya iske ko ina nagidan fes har abin karin kumallo mun hada ko,</p><p> Batare da bata lokaci ba shima ya ci nashi sama sama don hankali shi wurin kai Ummi asibiti,</p><p> Sam ban kawo cew dani za,a asibitin ba ,</p><p> Allah yatai make ni muna gama aiki na fada wanka nafito tsaf dani cikin shirgar dogurwar riga yau ja ce ajikina ba baka ba,</p><p> Tsaye nake inadan gyara wurin da na gama hada tea a kitchen ina son in kaiwa hajiyar mu,</p><p> Muryan mustapha naji yana cewa sheriff yana magana dani a falo,</p><p> Koda nafito na iske kusan kowa a tsaye har da yaghana da bata da lafiya,</p><p> Tsoro nadan ji don nadauka ko nayi laifi ne, kallo na yayi yana fadin mutafi ko,</p><p> Batare da nasan inda zamu ba nagyara dan daurin rolling dim kaina, narufe ko ina inda nasan cewa gashin kaina zai iya fitowa,</p><p> Nadan kali mahaifiyar nashi naganta cikin shiga na kamala,</p><p> Lafaya tasa duk ta rufe jikinta tsab baka ganin ko ina nata sai tafin kafarta dana hannu,kawai,,</p><p> Shima mijin nata yana saye da jallabiya fara kal da alamar yau yafara sata,</p><p> Sheriff din mu yadan kali dan saurayin yace mai Salim ka tsaya gida har mu dawo, tukun,,,</p><p> Ke kuma Amal da wanan ya nunani da hannu ku kama ummi kuzo muje,,,</p><p> Mota muka shiga sheriff da shehi ke gaban motar saini da yaghana da Amal ke bayan motar inda mukasa yaghanar tsakiyar mu,</p><p> A hankali yake tukin motar yana yi yana dan waigo mahaifiyar tashi don yaga yanayin ta,</p><p> Saida gaskiya ni kallon yana yawan damuna don duk ya waigo kafin ya kai indon shi ga ummi kamar yadda naji yakira yaghana din,</p><p> Sai idon mu ya hadu, sainake dan shiga tsarguwa saboda nice a gefen da ge facing din shi,</p><p> Dana hakan na yawa sai na maida idona gefen titi ina kallon jama,a daketa wulgawa da shaguno nin da suka cika kowani titi, nagarin makkah,</p><p> Sultan Abdulraham specialist hospital muka tsaya bakin get inda muka karbi pass din mu yasa kai ya shige cikin katon haraban asibitin,</p><p> Wuri yasa mu ya perker motar Amal ce tadan rikawa ummin hannu aiko tace don Allah ki sake min wanan duk tafiku iya lalabani,</p><p> Kallona sheriff yayi yana min magana kadan kadan indan rike ummin a hankali pls, na ansa mai da toh,,,</p><p> Har office din da zamu zauna ganin likita nakaita na zaunar da ita, </p><p> Ruwa tace muna tana so, don haka da sauri na nafita can wani shago bakin get na siyo muna ruwa roba biyu guda na zam,zam baida sanyi guda kuma mai sanyi na riko muna, shi,</p><p> Na iske sheriff tare da ita ina zuwa na balle bakin roban ruwan nayi bissimillah nabata tasha,</p><p> Bamuyi wani dadewa ba aka,kiramu kunsan su bakamar kasar Nigeria bace </p><p> likitoci ne na kowani fanni birjit sun fi ashirin ako wani fanni aiki ne kawai ba </p><p> Shehi da sheriff suka shiga da ummi sai aka bar mu nida Amala, zaune,</p><p> A, lokacin Amal tadan kaleni tace mim ita sunan ta Amla,</p><p> Saida nadan yi takaitacen murmushi san nan nace mata fadima,</p><p> Nakauda fuska na daa gare ta, batare da na kara mata magan ba,</p><p> Sundan jima kadan sai gasuvsun fito da ita saman wani dan keken asibiti mai kama dana guragu,</p><p> Wani dan matashin balarabe mai karfi yana tura kekenn</p><p> Mikewa mukayi tsaye lokaci guda cikin fargaba,</p><p> Da larabci sheriff ke min bayanin cewa zaije yadawo don za,akwantar da ummi ne sai an gano ko maye matsalar ta tukun,</p><p> Cikin rashin jin dadi maganar muka bi bayan su har zuwa dakin da za,a ajeta,</p><p> Dakine lafiyaye mai kyau komai akwai adakin kamar mutun yana gida,</p><p> A gaskiya ummi ta sha awo sosai don tun da aka kaita dakin muke ganin likita kala kala </p><p> Wanan group din suzo sutafi wasu su zo,,,</p><p> Nida sheriff ne masu zirga zirga don wani lokaci kafin yadawo anbada wani test din dole nice zanje in yi kafin yadawo,</p><p> Don haka duk mungaji,amma sam ban yarda na nuna cewa nagaji ba,</p><p> Abin mamaki har muna batun tafiya gbaigana u labarin matar sheriff a asibitin,</p><p> Har Amal ta kai ga tambayar shi ko lafiya bata gan, ta ba,,,</p><p> Ce ma Amal yayi bata jin dadi ne,</p><p> Sai a wanan lokacin natuna cewa banci komai ba fa yau, cikina ya soma ruri ,.</p><p> Ban ko gama wana tunanen ba wana na yai dan tsuwa alamar kira ya shigo min,,</p><p> Cikin dan sauri nadauki wayar da na aje gefena ina dan diba lambar,</p><p> Nakara wayan akune na ina mai ansa sallama,</p><p> Idanuna su kai kan sheriff, yakafe ni da ido da alamar yana son yasan wanene yakira ni awaya,</p><p> Jin da yayi ina kwatancen inda dakin da muke yasa shi barin kallo na,</p><p><br /></p><p> ZEEE MAKAWA24/10/2017, 1:50:11 PM: Maman Safwan: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 5⃣0⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p> </p><p>Almost true life story,,,</p><p><br /></p><p> Allah ya karama Annabi darajja da sahabban sa,,, </p><p> Jumma,atu mubarak yan uwa musulumai,,,</p><p> </p><p> Almustaphane tare da bakon saurayin nan mai suna Salim suna dauke da kwandon abinci, da abinsha, a hannayen su,</p><p> Nina karbi basket din hannu almustapha, nakai inda zan aje na aje,,,</p><p> Ahankali nadawo inda nake tsaye, nadan tsaya muna kallon ledar ruwan da ake kara, wa Ummi,</p><p> Almustapha gefen da nake yazo ya tsaya gab dani, ,,,</p><p> Shima kallon ruwan da ake kara wa Ummin yake yi cikin tausayawa,</p><p> Dan juyowa yayi daidai saitina ya ce min Aisha na can yau tana fitina wai sai ankawo ta gurina,</p><p> Murmushi nayi nace mai tunda tazo aibantaba dadewa waje hakaba, batare dani ba</p><p> Yace yau kan Yumma tasha rigima sosai</p><p> Ina dan murmushi don tuna Aisha da irin rigimar ta,</p><p> Ina,dan juyo sai ko muka yi ido hudu da Sheriff din mu,</p><p> Dake tsaye daidai saitin inda muke, </p><p> Hannu shi cikin aljihu yadan jingina da gina kadan,</p><p> Ashe idon shi na inda muke muna magana da mustaphan</p><p> Wani irin harara Ya watsa min,</p><p> Tare da wani irin mugun kallo na zaki gane kuren ki,</p><p> ,bansan lokacin da na sada kaina kasa ba,</p><p> Don kallon ya firgita ni sosai,</p><p> Tunda ni bansan abinda nayi mai ba, yai min wanan kallon na kishi ga hankalin ki, da ni,</p><p> Shiko Almustapha sai kara fada min yadda Aisha ke fitinar yakeyi,,,</p><p> Duk nadan daga kaina sai mun hada ido dashi daga inda yake tsaye suna magana da shehi,</p><p> Ganin da tayi mustaphan ba daina yimin kus,kus din da mukeyi zai yiba saboda bai lura da sheriff din ba da kallon da yake muna,</p><p>Don baya yaba ma sheriff din,,,,</p><p> Daurewa kawai nakeyi ina yar dariya kasa kasa,</p><p> Muryan , sherrif naji gab da mu yana ce min naje muci abinci da Amal a waje</p><p> Kafin in yi wani yunkurin tashi wurin saina ji muryan shehi yana cewa kamar ruwan baya tafiya ko,</p><p> Da sauri ya juya zuwa inda ummi take kwance don ganin robar kara ruwan</p><p> Sai kawai naji duk banjin dadi saina dan shiga halin damuwa, </p><p> Saboda ban iya fassara laifin da nayi ake min wanan kalon warning din,,</p><p> Abinda ya kawar minda damur dana dan shiga shine,</p><p> Farkawan da Ummi tayi daga barcin da takeyi sanadiyar dan taba mata hannu da akayi,</p><p> yasa nadan saki jikina da sauri na naje gurin ta ka,fin kowa ya isa ciki</p><p> Sauri ina mata sannu da jikinta, Ruwa tace zata sha saina dan daga kaina nakali inda yake ina fada ma sheriff din bukatar ta wanda dama idon shi naga mahaifiyar nashi,</p><p> Shima gurin gadon ya iso, yadan duka daidai saitin kan ta yace mata tayi hakkuri, Ruwa ake kara mata tabari indan ruwan ya kare sai abata, tasha ruwan shan,,,</p><p> Cikin sanyin gwiwa ya Mike ya na tafiya yana ce min cikin larabci koda ruwan yakare kada in bata ruwan tasha don akwai tests din da za,azo aimata dan anjima kadan,</p><p> Barcin ne yakara daukanta mai nauyi duk ina tsaye, akanta sai likitocine keta zuwa da dawo kanta, suna aune aune don su gane ko may ye matsalar ta </p><p> Amal tana gefe zaune ita da salim cikin damuwa ganin irin wahalar da mahaifiyar nasu keyi,,, </p><p> Muna nan zaune mukaji takon takalma tun daga nisa kwas kwas sai duk hankalin mu yakai ga kofar shigowar don gani ko waye,</p><p> A,she Nafisa ce tashigo asibitin da marance lip,,,, cikin shigar wando da riga irin na yan Pakistan, take,</p><p> Ta yafa mayafin kayan ta rufe kanta da shi,,,</p><p> Tana shigowa ko wani gaisuwar kirki bata yi wa koda shehi datagai dattijo ba cikin mu balle su Amal dake tsaye gefe</p><p> Direct wurin gadon da ummi take kwance ta nufa, </p><p> Tadan dibata tana tabe baki kamar mai jin wani, bashi ,bashi</p><p> Ta dan jin tsaye,muma ba wanda yako kulata,</p><p> Ko minti goma batayi ba da zuwa tace zata wuce,,,</p><p> Har takai kofa tajuyo tana min tabayar ina habibi cikin turan ci,,,</p><p> Da larabci nace mata yana can gurin ansan result din test din da akayi, wa ummi,</p><p> Yafuto ni tayi da hannu alamar in kai ta inda yake,</p><p> Ba musu na dan gyara na nufi hanyar zuwa lab, da ita,</p><p> Dan tafiya mukayi maidan nisa sanan muka isa gurin, da yake,</p><p> Zaune yake saman kujerun da aka tanadawa mutane,</p><p> Saidai kan shi yana duke, ba wai kalon jama,a yakeyi ba,</p><p> Dagani jira yakeyi yaji an kira shi, kawai,</p><p> Muryana da yaji cikin lokacin da bai yi tsamani ji, ba yasa shi dagawa da sauri, </p><p> Yana dagowa saida idon shi yabani tsoro</p><p> Saboda Idon shi yayi jajir kamar wanda yai kuka,</p><p> Nikan nasan cewa ma kukan yayi ,don ko dazu dana kai mai wani takarda da aka bamu na iske shi zaune cikin mota shidaya yana kuka,</p><p> Ganina dayayi yasa shi yadan wayance, don kada in san cewa kuka yakeyi,,</p><p> Tausayi yabani saboda mahaifiya ai ba wasa bace,</p><p> Don gani nima kusan kulun da tunane inna nake wace nake ganin kamar ban kara ganin ta a duniyar nan,</p><p> Gashi tunda naga makwabcin mu ban kara ganin wani dan garin mu ba, </p><p> Balle ma yanzu da ban bara ban talan gumama atiti kida alhazai sun zo balle inga idon sani,,,,</p><p><br /></p><p> Yana dagowa kan shi yagan mu tare da nafisa aiko sai naga yakara tamke fuskan shi tam </p><p> Kamar wanda aka aiko mai da mugun labari,,,</p><p> Ita sam bata damu ba sai wani dan kokarin shige mai da take batun yi,,,</p><p> Nikan wucewa nayi don nakoma dakin da ummi ke kwance,</p><p> Don kada su bidi wani abu ban kusa,</p><p><br /></p><p> Gida zamu koma don saboda asibiti majinyata basu kwana aciki,saidai mai jiya kawai da nurse's,</p><p> Saidai gaskiya shi shehi yace sam bazai koma ba zai tsaya asibitin, tare da ummi ne,,</p><p> Saida Sheriff yadan yi shige da fita aka bar shehin ya kwana, agurin nata,</p><p> </p><p> Mu hudu ne a cikin motar a hanyar mu ta komawa gida </p><p> Sheriff ke jan motar duk da dare yayi sosai,amma baka gane wa saboda hasken da garin keda shi ko ina,</p><p> Zakaga duk hasken fitilo ne ya haske ko ina a garin jama,a kuma basu daukewa har galin Allah yawaye,</p><p> A hankali yake jan motar bakajin komai sai sanyin A C kawai dake ta aiki amotar , kirar Jeep baka, wulk,</p><p> Murya a raunane yadan juya gefen da salim yake ya na magana, dashi,,,</p><p> Yace, yanzu salim kun san cewa ummi batada lafiya kuka barta har ciwo yacita haka ba wanda ya kirani a waya, ya fada min,</p><p> Yanzu saboda Allah kunyi min adalci ke nan,</p><p> May ye amfanin samun da nayi a,duniya,</p><p> Har, da za,ace wai mahafiyata tana dauke da ciwon yunwa ulcer da hawan jini har yai mata mugun kamu, haka ban sani ba,</p><p> Amal ce ta katse mai maganar shi tace wlh yayan mu Kada kaga laifin mu</p><p> koda mun ce zamu fada ma sai ummi tace batayafe mu fada ma ba,</p><p> Wai kada mutayar ma da hankali, tunda kana iya kokarinka akan mu bai kamata mu dinga sama wasu wahala ba hakana,,</p><p> Wai zai zama kamar rokon ka muka yi ,</p><p> Salim ya karbe zancen da cewa ai ni koda yaushe nikan ce ma ummi sai na fada ma, tunda mutane zasu ga kamar cewa ka kasa kula da lalurar mu ne bawai daga ummin bane,,,</p><p> Ya ci gaba da fadin,,</p><p> Aiko wanan kiran da Shehi yai ma bada son ranta bane saida yaga ta rikice shine yadaga waya yakiraka,</p><p> Tsuki yayi yana mai kada kan shi cikin bacin rai,</p><p> ,azuciyar shi kuma, yana tunane kawaici irin na mahaifiyar na,shi har yai yawa, watan ita dai haka Allah yai mata rayuwar ta cikin sanyin hali,</p><p> Hmmm Allah guda gari bambam ,,,,,Wai hausa ne sukeyi haka wanda sai da kyat nagane may suke cewa,</p><p> Get muka shiga ,muna paker motar mu mukafito,</p><p> batare da Amal ta tsaya ba tai niyar wucewa cikin gida abinta don duk a,gajiye take,</p><p> Niko lokacin na dauko basket din da aka kai muna abinci da rana ga flasks din ruwan tea da nake kokarin dauka wa cikin motar da hannu na guda,,,</p><p> Wani wawan tsawa ya,daka mata ta,tsaya wuri guda cak,</p><p> Tare da yi mata masifa, wanda ita dai duk iya saninta dashi baitaba yi mata hakan ba,, </p><p> Kayan dake hannu na yace mata ta tayani kwasa zuwa ciki,</p><p> Flasks din ta karba a hannu na ba shiri, jiki a sanyaye,</p><p> Shi kuma salim ya kwaso sauran kayan da muka kwaso daga asibitin,yashiga dasu,</p><p> Bin mu yayi da ido yana tausaya min irin wahalar da nasha yau,</p><p> Shin wai ita wanan yarinyar haka zuciyan ta yake ne,</p><p> Don dai gaskiya inbadon yasan ni tun ban karasa kai haka ba da sai yace kila don asani nakeyi wani abu,</p><p> Amma shi duk abinda zanyi sai yaga na tsakani da Allah ne babu kissa aciki,</p><p> Tsaki yaja lokacin da yake kokarin rufe motar,</p><p> Da ya tuna da Nafisa,</p><p> Wace ta nuna mai halin ko in kula, ga mahaifiyar shi,</p><p> Shi yarasa ita kowace irin mutunce mara tunane da lissafi,</p><p> Ace ankawo mahaifiyar shi asibiti daga Nigeria</p><p> Amma wai har ta biyo shi asibiti tana request din kudi a wurin shi,,,</p><p> Ita bata da aiki sai dai yawan tambayar shi kudi da bukata</p><p> Kuma sai yau yakara sanin halinta sosai don,ganin halin ko in kula da ta nuna mai akan ciwon mahaifiyar shi,,,</p><p> Da wanan tunanen ya shiga cikin gidan,,,, </p><p><br /></p><p> Satin mu biyu muna cikin wanan sintirin zuwa asibiti da gida,</p><p> Inda ummi ke jiyan jikinta,</p><p> Saidai gaskiya ba laifi jikin nata yayi sauki sosai </p><p> Don yanzu har ummi na iya tashi mudan yawata cikin asibitin da ita,</p><p> Shakuwa sosai ya shiga tsakani na da Amal da Salim, </p><p> Saboda yawan zaman da mukeyi wuri guda, da su,</p><p> Sai ya kasan ce kamar mun san junan mu da ma ,har ina jin dadin su fiye da zaman da muka danyi da su jamila da mairo da suka zo kwanaki</p><p> Duk da nasan cewa Amal ta girmay ni sosai amma hakan bai hanamu zama guri guda ba da ita,</p><p> Muna mu,amula kamar kawaye,</p><p> Har tafiya Sheriff din mu yayi zuwa Riyadh yin wani aiki na musan man da yataso mai shi da mustapha suka tafi,</p><p> Nice yabarwa kula da duk wani lalura na asibitin </p><p> Har zuwa lokacin da suka dawo daga tafiyan </p><p> Tafiyan da kusan itace tafiyan da ta zama makowa nagidan alheri nan gaba,</p><p> Don ko Sheriff din mu yasamu cigaba sosai don yanzu ya samu sa hannu a kusan mafi yawan company tatar man fetur ta kasa,saudiya,</p><p> Saboda kasan cewar shi kwararen engineering da suka sani </p><p> Saboda suna ganin cewa zai iya barin kasan any time daga yanzu saboda hada hannu da suka ga yayi da company Abu Abdallah dake Dubai,</p><p> Cikin dare ya iso garin don haka direct asibiti suka nufa,</p><p>Suna iso wa lokacin su Amal na waje suna shan iska, </p><p> Nikuma ina tsaye kanta ina kokarin hada mata ruwan shayi,</p><p> Jin anyi yasa na waiga inga ko waye don nadauka ko Amal ce</p><p> Sheriff ne sai su almustapha dake binshi abaya,</p><p> Gurin mahaifiyar nashi ya nufa direct tana zaune saman gadon asibitin jikin ta yanuna alamar tasa mu lafiya sosai,</p><p> Mun mai sannu da zuwa inda yake ansa muna cikin muryan shi maikama da yanajin kasala ko yaushe,,,</p><p> Da kyat yake magana mai karfi don in kaji muryan sheriff to ta baci,rai ya gani tare da mutun ,,,</p><p> Waje nafita batare da sanin kowa ba don in dan basu wuri su dan zanta, shi da yan uwan shi don kusan nice kwai bare,,a cikin su,,,</p><p> A samane dakin da aka kwantar da ummi yake, don haka waje nafito, nadan tsaya,,,</p><p> Daga sama inda nake tsaye ina kallon ina iya hangen katon agogon nan dake mane a kofar shiga masallacin ka,aba,</p><p> Wanda duk inda kake cikin garin makkah za ka iya ganin shi </p><p> mutanen dake shige da fice cikin kofar asibitin, nake dan kallo jefi jefi,</p><p> A zuciya na kuma ina, Tausayin yadda naga sheriff ya,damu da mahaifiyar shi ne yakamani,</p><p> Don nasan cewa idan yai wanan irin tafiyan yadawo bai fita ko ina har wajen kwana biyu,</p><p> Yana gida yana hutawa saboda gajiya </p><p> Saidai in rana,kun ya dace da jumma,a a ne acikin ,, shi,,,, Amma yau sai gashi direct asibitin yanufa don gani mahaifiyar shi,,,,</p><p> Ya shiga yaga ni ,Yana,Ganin jikin ummin yayi sauki sosai yasa shi fitowa daniyar komawa gida, don yadan huta ma ranshi kadan,, </p><p> Turus yayi daga bakin kofar dakin lokacin da fito, </p><p> Don, yaga fadima tsaye wace hankalinta na ga kallon waje saidai kuma hawaye take gogewa a fuskanta</p><p> Wace ita kadai ce tsaye a wajen,,</p><p> A,hankali yatako zuwa kusa da inda take yadafa karfen dake gaban su, yace mata lafiya,</p><p> Kaduwa tayi duk jikinta sai yakama rawa saboda jin muryan da tayi na bazata, alokacin,</p><p> Kara tambayar ta yayi ko may take ma kuka hakana,</p><p> Cikin daburcewa tace mai ba,kuka takeyi ba abune ya fada mata a idon ta,</p><p> Bawai ya yarda da ansar data bashi bane kawai ya barta ne don yasan bazai samu ansa ba, a lokacin,</p><p><br /></p><p> Nafisa ce zaune a falo tana waya ga Tufan da Anabi, aje agabanta sai madarar kwali wanda kwalin yasha rabar sanyin, friged ,da ke aje gefe guda tare da cup,</p><p> Waya take yi a,binta hankali kwance tana yi tana tsunkar Anabi din tana kadawa baki,</p><p> Sautin kidan yan kasar sudan ya tashi a cikin tv, dake man ne a falon, a hankali,</p><p> Kafarta guda saman dan stol din tangaran da ke falon</p><p> Har ya shigo falon yakare mata kallon Allah waddai,ya hau sama bata ankara da shi ba,</p><p> Sai gab da zai shiga dakin shi taga wulgawan shi,</p><p> </p><p>Cikin sauri ta tashi ta rufa mai baya ,</p><p> Tana shiga ta iske yana na balle butur din rigarshi yana son shiga wanka,</p><p> Ta bayan shi tazo ta rugumay shi tana sun,sunar shi,</p><p> Batare da yace mata komai ba yadan juya ta kadan ya wuce zuwa bayi,</p><p> Ido tabishi dashi tare da mamakin wai shi wani irin mutum ne haka,</p><p> Sam mace bata agaban shi, </p><p>Kwanan shi kusan uku baya gari yanzu kuma da yadawo gashi ya nuna mata bata a gaban shi,</p><p> Zaunawa tayi tana jiran shi ya fito daga bayin,</p><p> Daure da rigar wanka yafito ajikin shi ga mamakin shi sai yaga Nafisa kwance rub da ciki, saman gadon shi tana dan daga kafar ta da ta mayar baya, a hankali sai hannuta da take, lalatsa wayanta, dagani abinda takeyi a wayan yadauke mata hankali sosai,</p><p> Wardrop ya nufa ya ciro wata jallabiya mai ruwan A,she,colour yasa </p><p> daidai yana zura rigar ta taso daniyar rugumar shi ,,</p><p> Dakatar da ita yayi cikin tsawa, yakama hanyar fita dakin,</p><p> Binshi tayi abaya tana fadin walahi ita tagaji da wanan halin ,</p><p> May wai yake nufi da ita ne ma, da zai dinga mata wanan wulakancin ita yau tana bukatar shi,,,,,</p><p>Daidai lokacin mukayi, Ido hudu dashi kuma a,daidai lokacin da take wanan furucin nata,</p><p> Ji yayi kamar ya nutse a kasa don kunya, </p><p> Saidai kuma ya basar da zancen nats kamar ma bada shi takeyi ba,,,</p><p> Ita ko bata daina ba sai kara ci gaba da fadin kalmar da bata dace ba da takeyi,,,</p><p> Takardan da muka dawo dashi wanda zai je yayi filling, gobe akan gwajin da za,ai wa ummi na karshe,,,,</p><p> Na mika mai gami da juyawa da sauri, don ganin irin halin da na riske su ,.</p><p> Dakatar dani yayi don jin bayanin abinda takardan ya kunsa,,,</p><p> Batare da bata lokaci ba nai mai bayanin takardan a gurguje don jin irin hucin da Nafisat ke yi a bayana kamar wata zakanya,</p><p> Da sauri sauri na,sauko saman step din don ji nake kamar zata biyo ni a bayana,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>24/10/2017, 1:50:13 PM: Maman Safwan: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 5⃣1⃣</p><p> BY</p><p><br /></p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p> 🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p> </p><p> Almost true life story,</p><p><br /></p><p> Tun karfebakwai na,safe muke asibiti don yaune gwajin karshe da za,ayi wa ummi,</p><p> Kuma ance ya kasance muna wurin kafin a shiga da ita</p><p> Saboda zasu fitar da result din abin da yake damun ta </p><p> sosai, hankalin mu yatashi jin cewa ya kasance suna gurin ,</p><p> Anshiga da ita wani dan daki da zasu sa mutun cikin einjin don awo,</p><p> Muna waje tsa tsaye dukan mu cikin da muwa saboda bamusan ko wani irin saka mako zamu samu ba,</p><p> Shehi da sherif din mu sai addu,a suke yi daga inda suke tsatsaye,</p><p> Ina gefe tsaye bakin kofa, sai Amal da ke daidai inda nake tsaye ta dan zauna Salim kuma ya na daga waje zaune,,cikin zulumi,,</p><p> Jin karan bude kofar da akayi ne yasa hankalin mu duk koma gurin, da aka bude kofan</p><p> Wani, Dan likitan balaraben yafito yana mai cire kayan da yayi aikin da shi </p><p> Ummi ce aka garo ta kamar matatta, babu ko alamar ta na motsi ko kadan,,,,,,,</p><p> Aiko muna ganin haka muka bi bayan su da sauri, , cikin tashin hankali</p><p> Kwance take saman gado asibtin inda nunfashin ta ke tafiya a hankali </p><p> Wanda zaka gane hakane a jikin dan abin nuna nufashin dake mane kusa bango, gefen kanta,</p><p> Dakin yayi tsit ,ba wani mai kwakwaran motsi cikin, sai karan fanka dake tashi da sauran na,urorin</p><p> Waje na sulale ba wanda yasani nakoma narike karfen da ke saiti da dakin mu,</p><p> Bansan lokacin da na fara hawaye ba,daga haka har nadinga kuka wiwi ni kadai a waje,,,</p><p> Bakomai yasani kuka ba sai ganin halin da ummi ke ciki duk da gatan da aka mata,,</p><p> Sai kawai tunanen Inna da ke yawan damuna kwanan nan, yadawo min sabo</p><p> Ganin da nayi zuri,an ummi,duk sun kewaye ta cikin damuwa da tashi hankali,</p><p> To inda Inna na ce yaya zatayi,</p><p> Sai tuna ne ko cikin wani hali take ciki yanzu haka,</p><p> Idan ma tana cikin damuwa ne ba wanda, ko wani rashi lafiya saidai hafsat tayi ta kokari,</p><p> Ita daya batare da ni ba,</p><p> Kenan ni bazan samu ladan da "ya" ya ke samu wurin iyayen su ba</p><p> Hakan ke sa duk naga babba ina kokarin tausaya mai,</p><p> Don nasan cewa nima inna na tana can tana bukatar taimako </p><p> don hafsat ba,zata iya ba ita kadai,</p><p><br /></p><p> Kuka ne ya zo min wi,wi babu kakautawa,</p><p> Jin kukan da sukayi yasa su duk fitowa inda nake gaba dayan su,</p><p> Duk sun kidime, don basu san,komay yasamay ni ba haka,na ba yanzu yanzu</p><p> gashi nice mai kokari wanjen kula da ummi </p><p> Amma yau na gaza sai kuka nake yi masu duk hankalin su sai ya tashi,</p><p> Shehi ne yazo kusa dani ya na tambayana cikin larabci ko may yasamay ni ko banda lafiyane inyi magana mana ko zasu fahince ni,,,,</p><p> Sheriff yana daga baya tsaye ido kawai ya kafa min yana sauraren sautin kukana kamar wanda ake watsa ma ruwan zafi a zuciyar shi,</p><p> Ganin da yayi dattijon da su salim su dan riko min hannu,</p><p> Yasa shi yin magana daga inda yake </p><p> Muryan shi sukaji yana fadin baba kyale ta,</p><p> Gida take tunane babu abinda yasamay ta </p><p> Da sauri nadaga ido na dasuka yi jajir,saboda kuka, ina kallon shi cikin mamaki yadda san abinda yasani kuka,</p><p> Takowa yayi a hankali har zuwa inda nake, duke </p><p>Ya dan dagoni tsaye da hannu bibiyu, sai ya rugumay ni ajikin shi yana dan buga min baya yana cewa ,</p><p> Hayya hayya, alamar ya isa niko sai na kara nokewa sosai a cikin jikin nashi,</p><p> Nakara aza kuka sosai, duk hankalin su sai yakara tashi,,,</p><p> Abinda yasani dan tsagaita kukan jin karan yar da jakar hannu Nafisa da tayi abayan mu,, wanda </p><p> Kusan kowa ya juya don gani ko may ye yafadi hakana a lokaci guda,</p><p> Banda ni da kaina ke ajikin sheriff din mu wanda nake ji tankar yayana na ji daya</p><p> Wanda tun zowa na garin makkah yake taimako na da alheru</p><p> Wanda a,halin yanzu shine yazamo min jigon rayuwata tamkar uwana da ubana nake jin shi</p><p> Tunda har a sanadina ya iya daukan dawai niyar mu gaba dayan mu nida yan uwan tafiya na batare da gazawan hakan ba,</p><p> Wanda ko sau daya bai taba nuna muna kyama kamar yadda sauran masu kudi kewa yan aiki,ba</p><p> Muryan ta ya dawo da hankalin kowa daga kallon jakar da tayar akasa,</p><p> Ahmad gaskiya ban fahinci may kake nufi da wanan yar ficiciyar yarinyar ba wace na tabbatar da ko da haila bata fara ba</p><p> Balle, nasa cewa koda hannu ta karike ba wani abinda zai kara ka dashi na jin dadi,</p><p> Jayeni yayi a jikin shi a hankali ya dan jingina ni ajikin Amal,</p><p> Tako daya yakai gare ta yace,</p><p> Ke Nafisa Allah waddan hali irin naki hali irin na rashin imani da rashin tausayi,.</p><p> Shin ma dai kina cikin hankalin ki kuwa kodai yau din ma kiyi shaye shayen naki ne, daki ka saba,</p><p> Kalman shaye sheye da ya furta shiyasa ta kaduwa so sai,,,</p><p> Don bata taba tsan mani yasan tana shan drugs ba,</p><p> Saita wayance zancen da cewa ni ban san ko ta ina </p><p> Ka,hada alaka da wanan yar munafukan yarinya ba mai shegen iya yi,</p><p> Yarinya kamar manyya ta wani kafe ka da idon ta kamar gonar madara,</p><p> Walahi nayi hating din wanan yariyar a rayuwa na,,,,</p><p><br /></p><p> Shehi ne dake shiru tunda tafar surfa min zagi imani duk ya kashe shi yana tsaye sai mamaki ta yake yi</p><p> Kowata irin mata Allah ya Ahmad haka da ita, wace bata ko san maye aure ba balle dalilin yin auren, ,</p><p> Dama shi yana ganin ta yasan cewa bata da tarbiya,</p><p> Ba,irin matar da yaso Ahmad da ita ba ke nan,,,</p><p> Sai ga shi yau tanu ita din kowace,ce wurin yi ma yaron kirki kamar Ahmad</p><p> zancen na haushin wai har kazafi take kokarin yiwa Ahmad din </p><p> da cewa wanan yar karamar yarinya kirki mailadabi, </p><p> Don haka shehi din yace mata</p><p>Yo, wanan din ai tana bukatar kulawa ne bawai ita din, ta kula da mutun ba, kamar </p><p>Yadda yaga ita ce wai mai kula da su</p><p> Wa na min din aiba wace za ai wa sheri bace irin wanan domin kwazon ta yayi yawa ga kowa,</p><p> Batare da shehi yakai karshen maganar shi ba ta juya tana kuka batare da ta shiga gurin ummin da sai taga dama take zuwa gaishe ta ba,</p><p> Koshi sai idan hjyn ta tai mata fada a waya take dan zo,wa</p><p> Duk zanan mu asibiti zuwan ta na uku ke nan,yau din da tazo,</p><p> Shiko sheriff, baiko damu da tafiyar ta ba idon shi na akaina ganin da yayi Amal na min dan magana kasa kasa ina daga kaina,</p><p> Cikin dakin da ummi take kwance muka shiga nida Amal </p><p> Ido yabimu da shi har muka shige,</p><p> Duk ranshi bai mai dadi,ba, ga matsalar kukan da nake ta faman yi ga kuma, sherin da nafisa taimai gaban yan uwan shi,,,,,,</p><p> .Koba,a fada ba yasan kukana bai wuce dayan biyu ,ba,</p><p> Ko kukan zaman mun a haka kamar bayi ko kuma na tuna yan uwa na gida</p><p> Tunda bazaice don ganim yanayin jikin ummi danagani yau nake wanan kukan ba,</p><p> Ai inda sabo na saba daganin ummi din a haka </p><p> Saida ya lura yaga nadaina kukan, nadan sake jikina kadan</p><p> Salim ya karbo muna shayi,</p><p> muna zaune muna sha. Coffee din nida Salim da Amal,</p><p> Sukan sha abinsu ,sukeyi sosai saidai ni gaskiya shan bugi nake yi wanawa ,</p><p> don cup din da dan storot din da ake tsotson coffee din kawai na rike inayi kamar mai sha,</p><p>Sai kuma can nai shiru, ina tuna ne,</p><p> Mu ukune zaune saman kujerun dake fuskantar dakin da ummi ke ciki, Tsakiyan su nake zaune nai shiru, da cup din coffee din ahannu na,</p><p> Ido ya zura min daga inda yake zaune,sai a lokacin ya lura da cewa na ramay nayi baki,</p><p> Gaban shi ne yafadi dam,</p><p> Yace kar dai a ce aikin da nakeyi ne yai min yawa haka ,har na dan ramay batare da yasani ba,</p><p> Aiko dai kada ya shiga hakkin yar mutane, da yawafa,</p><p> Yasan cewa dama nayi yar karama da wanan irin dawainiyar da nake yi,</p><p> Kwazo kawai irin nawa kesa ana sani wani abinda ya kamata babba yayi,</p><p> Tashi nayi don injefa cups din kwalin da muka sha coffee din a dustbin </p><p> Lokacin yakara ganin yar raman da nayi ba kadan bace,</p><p> Saidai kawai nadan kara girma ne ta kasa na,kadan saboda nadan buda alamar girma, ya fara baiyana min,</p><p> amma zuwa sama na duk na dan ramay sai dai na dan kara tsayi sosai,,</p><p> Shehi ne yakatse mashi tunanen shi da cewa, Wanan matar takakuwa diyar cikin aminin mahaifin naka ne,</p><p> Murmushi yadan yi natakai ci dai dai lokacin da yake kauda idon shi akaina lokacin ina kokarin zama inda natashi,</p><p> Yace ma Shehi a gaskiya baba ni bansan komai gamay da gidan Alhajin kano ba don ni dai nasan cewa tun ina yaro saudaya ma nataba zuwa gidan lokacin da zamu koma hutu, suraj yace ma driver ya bida mu ta kano din,</p><p> Kuma muna komawa gida hjy mama ta haushi da fada don may sukaje dani har aka ba mu kyauta iri daya dana,su,</p><p> Tun wanan lokacin naji duk wani dangi na hjy ma ma yafita min arai, na,,,</p><p> Abba na ne yai wanan hadi nikuma na wakilta bashir na mu na wurin kawu sale da ya gabatar da komai kamar yadda Abba ke so ayi,,</p><p> Nadauka cewa Abba zai yi min zaben alheri ni ba wai irin wanan zaben na danasani ba,</p><p> Kuma duk abinda take min bazan iya fada ma Abbana ba don nasan cewa zai iya shiga wani hali idan yaji,,,,</p><p> Haka na wuni arana cikin rashin walwal, duk tunanen yan uwana ya addabe ni ya hanani shakat,,</p><p> Bayan mundawo gida duk wanda yagani aranan yasan ban cikin hayacina da akwai abin dake damuna,,,</p><p> Ina saye da rigar barci ajikina doguwar riga ce pink sai hula fara da rufe kaina na kawo zani nadaura saman rigar,</p><p> Har nadan kwanta sai na tashi saboda da muka dawo,,</p><p> Kowa yaci abinci amma ni na kasa cin komai don haka kitchen na nufa don in dauko madara in dan sha,</p><p> Har na dauko sai naji wani sabon kuka yazo min har yafi nadazu,</p><p> Ashe Amal na biye dani zuwa kitchen din, ganin da tayi ina kukan </p><p> Hakalinta ya tsahi ta je da sauri takira, sheriff wanda ke zaune yana latsan laptop din shi a falo,</p><p> Cikin sauri ya taso ya biyo ta har kitchen din inda nake durkushe da kwalin madara a hannu,</p><p> Jinayi yana ce min, Ta,al ya ukhti, Ana asfan,,</p><p> A hankali nadan daga kaina sai nagan su a tsaye bisa kaina,</p><p> Namike da sauri, nafada masu ajiki shida Amal ina mai kara sautin kukan nawa,</p><p> Har daki na yakaini saman gado inda Amal ta dan tsiyaya, min milk din a cup ta miko min,</p><p> Ba musu nakarba saboda irin kallon da yake min,,,saida nasha kusa rabin cup din namika mata ta karba ta juya don ta mayar da cup din da sauran milk din</p><p> A gefen gadon yake zaune shi ma ya hada hunnu shi biyu wuri guda ya dun kule, su,</p><p> Nan yake ce min natuna da inna ne ko, </p><p> Don ganin da nayi ma ummin su ko ba musu na kada mai kai alamar eh,</p><p> Yace min in yi hakkuri bada dadewa ba zan tafi gida insha Allah</p><p> Dago kai nayi da sauri na kalle shi don in gaskanta maganar nashi,</p><p> Muna hada ido dashi yadaga min kai alamar eh, </p><p> Gaskiya da na,hango a idon shi yasa na gaskanta zancen nashi,,</p><p> Amal dake tsaye kofa tadan kara sa shigowa daga ciki, dakin </p><p> Ai Amal bata ko zauna ba aka turo kofan cikin fushi </p><p> Idon mu duk kofan yake kallo don mamakin ko waye ya turo kofa haka,</p><p> Nafisa ce a fusace daganin ta kasan tana cikin fushi saida ta kare muna kallon rainin wayo gaba dayan, mu, duk ka ukun sanan ta juya tana </p><p> Kallon banza Sheriff din yabita da shi batare da yai wani magana ba yatashi gami da ce muna saida safe,</p><p> </p><p> Yanafita Amal da rakashi da kallo tace wanan shegiyar sai nayi maganin ta don naga bata da mutunci sam wlh,</p><p> Ranan nan mu uku, muka kwana mun sa Aisha tsakiyar mu,</p><p> Washe gari da ciwon kai na tashi sosai saboda kukan da nasha yin nin jiya din,</p><p> Nice kullun mai kokarin tashi don inga an yi duk wani aiki da yakamata ayi da safen,</p><p> Jinda kowa yayi shiru yau gidan ba motsi na ba a,lamana sam </p><p> Yasa wasu daga cikin yan gidan namu fito,</p><p> Ciki harda Amal da Salim ,</p><p> Don Amal tun asuba ta koma dakinta ta kara gyara kwanciyar ta,</p><p> A falo Salim ya tsaya ganin cewa rana yadan yi saboda zuwan mu asibiti wurin ummi, gashi almost to time,</p><p> Amal ce takware da nake ciki yadda ta gani cikin bargon yadan bata tsoro,</p><p> Kwance nake ina rawan sanyi, ga wahaye tab ga ido na </p><p> Aisha na gefe na zaune tana kallo na ina jin lokacin da ta tashi tana ta dan jijigani cikin bargon</p><p> Tana cikin hakane sai ga Amal Allah ya kawo muna don ban iya dagawa sam wlh,,</p><p> Da sauri taje ta kira Sheriff wanda suka hadu yana shirin saukowa kasa ,, Dakin da nake suka nufa duk kan su hankali ta she,</p><p> Yana kallo na a yasan cewa har da fever ya kamani,</p><p> Ina nan dunkule sai kuma naji amai na shirin kamani,,</p><p> Da sauri suka taimaka min zuwa wurin mota, sai makyarkytan sanyi nakeyi,</p><p> Ina dunkulewa,wuri guda</p><p> Muna isa asibiti aka wurin doctor kamal abokin shi ya kai mu,</p><p> Ina ji lokacin da sheriff ke ma doctor bayanin komai tamkar nice ke bayani,</p><p> Bayan an rubuta magani ya kasan ce har da allura za ai min guda,</p><p> Aiko nan muka kwashe ta da nurse din don naki bari taimin Allura sam </p><p> Sheriff yasa Amal ta rike ni gam ina ta tsala ihu ina fadin Anna tazza habb</p><p> Suna waje suna ji na dagashi har Salim din murmushi suke yi suna min dariya,</p><p> Ina fitowa ina dan share hawaye na,muka hada ido da Salim da shi ,sai duk suka kwashe da dariya,</p><p> Hararan Salim din nadan yi tare da turo baki alamar jin haushin su,,,</p><p>Gida aka dawo dani saboda yau badamar zuwa asibitin da ummi ta ke nima ina fama da kaina,,,,</p><p> Barci mai nauyi ya dau ke ni bani na farka ba sai daidai lokacin sallah azahar </p><p> Duk da nauyin da jikina yai min bai hana ni tashi zuwa don inyi sallah ba</p><p> Abinda nagani yasani mamaki so sai don koda ake ma doctor bayanin abin da yasamay ni ban. dago cewa sing of period sheriff ke bayani ba don yanzu nadan rage yawan ciwon mara kadan bakamar da ba,</p><p> Don duk wani abu mai zaki na rage shan shi yanzu saboda irin wahalan da nakeyi,</p><p> Jiki ba kwari nadawo nakara nadewa saman gado, ,,,,, </p><p> </p><p> Allah ya sa na dan ji saukin jiki na so sai har ina dan yin aiyukana na cikin gida</p><p> Yau ne muke sa ranan za,a sallamo ummi daga asibiti</p><p> Saboda samun saukin da tayi sosai jikin ta ya komal normal tasa mu lafiya,</p><p> Duk wanda ke gidan yazo taron ummi da dawo, anayi mata barka da arziki ,,,,,</p><p> Zaune kowa yake a falon anata nuna farin ciki muko sai zirga zirgan hada masu abincin lunching mukeyi don bayan azahar ne suka dawo gidan</p><p> Nafisa ce zance kusan karshen zuwa tariyan ummin wace tafito cikin kasaita da isa,</p><p> Batare da ko wani dar ba tasamu daya daga cikin kujerun ta zauna,</p><p> Sanan takewa ummin gaisuwa,</p><p> Daga haka mikewa kaiwai t ta koma dakin ta tana tafiya tana wani juya kwan kwaso, ta da karfin dole,</p><p> Ido kowa dake falon yabita da shi da mamaki irin hali ta na ko in kula da takewa ummi</p><p> Mudai ba musan cewa ita din yar uwar hjy mama bace balle mu fasara zance da wani manufa</p><p> Iya kadai muna ganin rashin tarbiyanta da kuma nuna wulakanci ga kowa,</p><p> Muryan Amal ce ke fadin dama hjy tsohuwa ta fadi gashi ko ya bayyana</p><p> Jinin su hjy mams ba jinin alheri bane tasan cewa wahala kawai aka hada yayan su dashi,,</p><p> A cewar ta wanan aida ta samu wuri da tafi hjy mama iya sheri,</p><p> Dadin abin yayan su ne bai bata wuri ba,,,</p><p> Ummi ce ta kwabe Amal din da fadin ta dai sa ido ga abinda bai shafe ta ba,</p><p> Sheriff na jin duk abinda Amal ke fadi dakuma kwabeta da ummi tayi baice komai,</p><p> </p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>24/10/2017, 1:50:14 PM: Maman Safwan: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 5⃣2⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🎁 *NASIBI* *WRITERS ASOCIATION*🎁</p><p> </p><p> N 🎁 W 🎁 A</p><p><br /></p><p> Dawowan Ummi gida da kwana biyu muka lunch zuwa sabongidan gaba daya gidan har hjy mu,</p><p> Saidai gaskiya wanan gidan yafi karfin wan,can tsoho gidan sosai gida wanda bazan tsaya maku bayanin shi ba, don girman shi,</p><p> Haka kuma naji yana waya akan wani gida daya saye a Abuja Nigeria inda naji yana cewa zaizo yagani kwanan nan,</p><p> Allah ya nufa da ummi za ai wanan shagalin komawar,</p><p> A ciki muka fara azumin watan Ramadan company su yafara aiki sosai a kasar wanda Allah ya basu nasaran samun kwastamas ta ko ina afadin kasar</p><p> Abinci sosai ake yi na bada karama wata katuwar mota ce ake wa loading abincin buda baki mai dadi, akai bakin haram aje anabadawa hade da abin sha ruwa da lemon kwanko da dabino,</p><p> </p><p> Wani irin shakuwa da aminci mukeyi tsakanin nida Amal da salim,</p><p> Kusan ko yaushe idan ba aiki nakeyi ba zaka samay mu tare,</p><p> Muna hira ina koya mata larabci ko kuma muna karatun novel na hausa da tazo da shi,</p><p> Ummi na jin dadin zama dani kamar yadda nake nin dadin zama dasu.</p><p> Shehi yaso ya koma gida amma Sheriff ya hana acewan sheriff din ya tsaya yayi umurah tukun sanan ya tafi,</p><p> Inda ya aika wa sauran iyalan she da abin azumi batare da sanin shehi din ba,</p><p> Bashir yaba yakai masu duk yan uwa nagari Auno din sun samu wanan kyautar daga dansu jikan su Ahmad,wanda suke kira da baba karami,</p><p> Sai bayan kwana biyu iyalan malam Shehi,suka kira Shehi din a waya suna mai godyan kudin da yaturo masu,</p><p> Cikin mamaki shehin yace masu gaskiya bashi bane,</p><p> Saida uwargidan shehi tace bashir ne yakawo masu shine Shehi yagane cewa Ahmad ne ya masu aike,</p><p> Da safe Sheriff zaiyi tafiya zuwa yamal ,</p><p> Da sallama yashiga bangare da su ummi suke inda ya samay su zaune suna lazimi , </p><p> Ya gaishe su cikin girmamawa da ladabi, ya juya gurin ummi yana tambayar ta lafiyan jikin ta,</p><p> Muryan shehi ce ta katse mai maganar da yakeyi da ummi din</p><p> Dai lokacin nagama hadawa ummi abincin da zatayi break tasha maganin ta,</p><p> Kasancewa rashin lafiyan ta baibari tayi azumi,</p><p> Likitoci sun hanna ta yin azumi saboda ulcer fa yai mata yawa, da ita da hjy mu ce basu azumi tare nake shiga kitchen in hada masu abinci. </p><p> Shehin yace hakika Ahmad kakai yadda ake duk wani mumini yakai ,</p><p>Musan man wurin kyautata wa yan uwa,</p><p> Kayi koyi da yadda hadisin mazon rahama yazo muna,</p><p> Akan idan zamu yi alheri muyi shi batare da hannu hagun mu yasan hannun daman mu yabayar da alheri ba,</p><p> Banda abinda zance sai dai in kara gode ma bisa ga alherin da kaiwa iyali har mada yan uwana,</p><p> Hakika da kai da mahaifiyar ka ku alheri ne gare ni,</p><p> Fatana gare ka shine Allah yabaka zuri,a masu albarka wa yanda zasu gado halin ka, </p><p> Saidai gaskiya wani hanzari ba gudu ba shine,</p><p> Sai shehi din yadan yi shiru kadan kamar kalman da taye son furtawa tana da nauyi,</p><p> Lokacin kuma nagama hada ma ummi abinci a gabanta,</p><p> Namike da niyar barin dakin sai naji muryan ummi nace min dan tsaya in bude mata drink din dana aje mata,</p><p> Kallona sheriff din yayi shima ahankali yakali kwankon lemon da ke gaban ummi,</p><p> Shehi yacigaba da fadin gaskiya kana bukatar kara iyali Ahmad,</p><p> Ahmad din da kanshi ke duke saida yadan daga yakali shehi din,</p><p> Shehi yakada mai kai alamar kware kuwa, saboda nan gaba akwai matsala inhar bakayi hakan ba,</p><p> Kai baba shehi kenan wanan din ma yayana iya da ita balle inkara jajibo wa kaina wani ma tsala,</p><p> Murmushi shehi din yakara yi yace zakayi ne Ahamad ko ba shiri idan har lokacin karawan yayi,</p><p> Da haka sukayi sallama yatafi yamal diba wani company tatar mai mallakin gwaunatin kasar saudiya da ya samu matsala ya tsaya </p><p> Zaije yada da sauran abokan aikin shi su tafi,</p><p> </p><p> Muna ganin Sheriff yai tafiya ,muka yi shawaran zuwa zaga gari,</p><p> Nida su Amal naima driver da nake fita dashi sayayya magana akan zai kai mu unguwa, washe gari,</p><p> Sai da zamu fita nake fada wa ummi cewa zamu dan fita don suga gari,</p><p> Tace muna kada mu dade saboda ba sanin garin mukayi ba, </p><p> Dariya kawai nayi don nasan guri guda gudane ban sani ba,indai har idon garine,</p><p> Don ba inda bamuje yawon bara ba, a garin,</p><p> Cikin shirin mu ta alfar ma muka fito inda koni shigar tawa tabani sha,awa sosai,</p><p> Wata doguwar rigace ta larabawan Jordan nasa,ban taba sa waba,,, Rigar nafisa ce dayaje Dubai kwanaki yasayo mata ,</p><p> Tun nan inda yaba ta tajefo min tace batasa irin shi ita,</p><p> Itama Amal shigarta yai mata kyau sosai </p><p> Mun hade da Salim a gurin mota, har mun zauna driver zai tada mota sai ga nafisa da saurinta,</p><p> Wai mu fito zata fitane itama,</p><p> Nidai ina baya ina jin su har ina shirin balle murfin mota in fita Amal ta hana ni</p><p> Salim dake ta gaban mota ne yace mata sai kiyi hakkuri idan mun dawo kyatafi,</p><p> Yace ma driver ya mota mu wuce muna jinta tana ta haushi kamar wata tababiya </p><p> Har mukabar gidan suna mata dariya kamar mahaukaciya,</p><p> </p><p> Munje gurare da dama agarin na nuna masu gurare tarihi sosai,</p><p> Sai kuma wasu shagunan kaya da muka ziyar ta, da gurare saida kayan abin motsa baki,.</p><p> Amal duk ta rude sosai dagani wani katon shago na saida kayan sawa na mata da yara,</p><p> Saida naga tagama rudewa ina mata dariya, daga karshe nake fada masu cewa ai shagon Sheriff ne ,.</p><p> Na nuna masu wani na saida kayan maza dasu carpet din sallah iri iri </p><p> Baki suka sake suna mamaki har cikin mota suna kara tambayana nace masu wlh nashi ne,</p><p> Wasu manyan motoci da sukayo loading mutane wanda da,alama baki isowar su kenan motar naga tana ta kallo har tana waige,</p><p> Nace mata ai indai wanan garin ne kada kiyi mamaki darin su sushigo kamar haka,</p><p> Nace mata gari ne da zaki ga taron bil,adam kamar duk duniya aka tara tundai ranan jumma, ranan da duk yan kauye da kewaye sun shigo ga baki sai kiga garin yazama kamar ba ko isakan shaka,,</p><p> Duk da dare yayi saida nakai su wasu shaguna dake cikin kasa inda shagunane sunfi guda dari akarkashi kasa akajera su birjit,</p><p> Shagon saida zinare dayafi kowani girma wurin nakaita,</p><p> Saida Amal tace min don Allaj fadima mu fita haka sanyin wurin nan ma yai min yawa ga girman wanan shago kada yasani mafarki pls,</p><p> </p><p> Har muka isa gida tana santin shagunar da duk mukaje,</p><p> A bakin get mukayi tozali da sheriff wanda yafito da niyar zuwa masallaci sallah cikin jallabiya baka , mai dogon hannu kan shi da "yar fula karama fara, sai Almustapha dake gefen shi shima cikin farar jallabiya,</p><p> Tunda na hangoshi sai naji gabana yafadi don musan cewa bayau ne zai dawo ba, sai zuwa jibi,</p><p> Kamar munafukai muka fito motar muna dan nonokewa , </p><p> Duk da yagane nufin mu bai ce muna kowulakan ,</p><p> Salim ya kalla yace mai ya harama zuwa sallah kafin ata da jam,i,</p><p> Muna shiga gida har mun manta da zancen nafisa ashe ita tana nan tana ta hauka tun wucewar mu,</p><p> Akan dole sai an dauki mataki akan mu tunda munyi mata wulakan</p><p> Masifa take tayi yasa ginan gida jen su ba irin namu na Nigeria bane,</p><p> Balle wani yaji yadda take masifa ,saboda su ba halin su bane,</p><p> Ina dakina bayan mun idar da duk sallolin mu sai natashi ,ina cire kayan da sa ajikina ji kawai nayi ambankado min kofa da karfi </p><p> Najuyo don ganin kowaye yai min wanan irin shigar daki,</p><p> Allah yasa ban cire riga ba nadai cire dan kwali da su yan kunneya na,</p><p> Nafisace tsaye tana wani irin haki gyalenta a hannu ta rike shi don masifa,</p><p> Tana batun finciko ni taji anjata baya da karfi ko da ta waiga saitaga sheriff ne ,wanda dawo wanshi kenan daga masallaci , zai shigo yaga wulgawanta ,zuwa sashen mu,</p><p> Sanin halinta dayayi yasa shi biyo ta yaga ina zata,</p><p> Ganin da yayi dakina ta dosa yasa shi biyo ta har ciki, ganin yaje yeta yasa tafara </p><p> Ai ko sai tahaudura min ashar ,bakar Ashar,</p><p> Takara yo wa kaina gadan gadan, hakan yasa na boye bayan sheriff din wanda bakin ciki ya hashi yin ko yin magana</p><p> Ganin da yayi cewa bazata fita dakin ba shikuma mutum ne wanda baison fitina </p><p> Hannu na yaja zuwa waje, muka barta can dakin,</p><p> Aiko saita sa kuka wi wi, wai ya wulakanta ta saboda yar aiki,</p><p> </p><p><br /></p><p> Tundaga ranan sheriff ya hanani duk wani aiki da yashafe fan,nin nafisa tunda tace sai ta halakani,</p><p> Hakuri Shehi yaba shi so sai tare kara mai karfin gwaiwa, akan ya jure,</p><p> Wanan fitinar da NAFISA tayi yasa muka sake jiki ga fadan da muke tsan mani gurin she,</p><p> </p><p> Koda yaushe Amal tana bani labarin Nigeria dakuma labarin yan makaran tar su da sukayi karatu tare,</p><p> Ina jin dadi wanan labari sosai ,</p><p> Idan tana bani sai in yi kwance in yi shiru ina saurare ta gama yanzu da banda wani aiki sosai a gida sai aikin ummi,</p><p> Can mukan zauna muyi ta hirar mu,</p><p> Har kusan lokacin shan ruwa sanan indan fito inyi aikina,</p><p> Aikin yanzu baida wani yawa kamar da iyakata kula da masu ayukan gidan,</p><p> Saikuma in dan zagaya inga abinda yadace ayi ma ma,aikata,</p><p><br /></p><p> Azumi na Ashirin baba Shehi yai haramar komawa gida don sallah wurin sauran iyalin shi,</p><p> Shirye shiye sosai a,kayi mai ,</p><p> Ummi tatura mu munje munyi wa yan uwarta sayyaya sosai </p><p> Jin da nayi ance hjy tsohuwa guri guda take da su, baba shehi yasa naje nasiyo mata maganin ciwon kafa da kuma magani ciwon ido,</p><p> Naba baba shehi yakai mata cikon kayan da na hada naga Amal ta jefa wasika tace akaiwa hjy tsohuwa,</p><p> Ana gobe malam zai wuce nashiga dakin su inkai wa ummi fruit sald kafin ta kwanta </p><p> Sai na iske malam she da yaran shi Amal da Salim, yana basu wani dan abu suna lasawa,</p><p> Har na juya zan fita yace min yaki "yata sai na dawo nasamu gefe nadan tsuguna daidai saitin da Amal take yace min indawo</p><p> Ni abinda tabasu yadibo ya bani in lasa,</p><p> Na lasa yace min in miko mai hannuwa na na mika mai yakama hannu na dama ya murza min wani abu fari kamar takarda sai naga abin yashige min a jiki,</p><p> Inata juya hannu ko zan gashi banga abinba yabi lafiyan jiki,</p><p> Karshe yace min intashi in tafi Allah ya tsare masu mu mukace Ameen gabadayan mu,</p><p> Washegari malam shehi yawuce yabar mu da kewan shi sosai,</p><p> Dattijo mai dadin sha anni, dakuma fadin gaskiya,</p><p> </p><p> Saura kwana biyar sallah da dare har na kwanta sheriff yace akirani a falo nasa may shi yace min gobe in shirya in raka Amal madina kuma ga goben zamu dawo,</p><p> Sanin da nayi tsakanin Makkah da madina akwai nisa sosai yasa nadaga kai na kalle shi sai yace inda bamu gama bada wuri zamu iya kwana har jibi in sun gama mudawo,</p><p> San mako mukayi tunda safe muka kana hanyar madina,</p><p> Amal ta dauka ai ba wani tafiya bane mai nisa sai taga har ana batun marance bamu isa ba, nan ta waigo inda nake ta kallon dogon dajin da ma,aiki manzon Allah SAW sukayi tafiya hijira saman rakumai daga makkah zuwa madina,</p><p> Gaskiya mu munzo cikin musulunci mai dadi dibafa a mota muke ta tafiya haka amma bamu kai ba,,,,,</p><p> Amal ce ke ce min fadima har yanzu nace mata saura kadan insha Allah,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>24/10/2017, 1:50:16 PM: Maman Safwan: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 5⃣3⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP ND NASIBI GROUP🐎</p><p> 🎁 *NASIBI WRITERS ASSOCIATION* 🎁</p><p> 🎁N🎁W🎁A</p><p><br /></p><p>Ku _yi Afuwa arayuwan ku</p><p>Kuyi sasauci ,arayuwa,ku</p><p>Ku yawaita murmushi da godiya ga dan uwan,</p><p> Sadaka na kariya sosai ga bawa ranan tsayuwa jiran hisabi,</p><p> Allah yasa mudace,</p><p><br /></p><p> Yan huguma group ban taba mantawa da ku ban manta alherin ku gare ni,</p><p>Nagode Nagode Nagode</p><p><br /></p><p>Almost true life story,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Gab da sallah la,asar muka shiga garin na madina garin da duk duniya babu inda takaita gaskiya da son jama,a garin mutanen kirki ga mutunci, garin da ba ruwan ko da sa ido ko hassada ga dan uwa,</p><p> </p><p> Cikim larabci nai ma driver mu yusuf magana nace ya wuce damu direct mai kai gaisuwa mu kuma kwaso lada tunda</p><p> Mun makara nasan cewa baza su samu yin abinda yakawo su ba yau sai gobe, </p><p> Don haka goben ba,la,lai bane musa mu zuwa da wuri kafin mu wuce,</p><p> Saboda nasan cewa madina bakamar garin makkah bace gari da komai acikin natsuwa akeyin shi,</p><p> Al,umman garin madina daban suke da sauran mutanen garuruwan su maci kusa,</p><p> Karfe goma anrufe massalaci Annabin rahama ba,a bari kowa ya kwana acikin shi,</p><p> Bakamar masallacin makkah bane da wasu ma anan masaukin su yake,</p><p> Nan suke kwana suke komai,</p><p> Iyaka sai in anzo shara su dan kwashe kayan su su a,gyara wuri sai su dawi</p><p> A gaskiya koda banda wayo nasan cewa kasar saudiya kasa ce mai albarka da hakkuri da jama,a,</p><p> Duk yadda mutum yake suna hakkuri da shi indai har ibada kaje yi,</p><p> Ba irim mu takari masu zuwa da wani manufa ba na dan ban don tara dukiyar duniya,</p><p> </p><p> Saida muka kusa isa kusa da massalacin na juya nai ma su Amal da Salim bayanin abin da nagaya wa driver ,</p><p> Suma suka ce gaskiyane, nai ma Yusuf driver magana don Allah yayi kokari yakai Salim wurin ziyara manzon rahama idan an, sallamay sallah nafada mai duk yadda zai yi,</p><p> Cikin dauki Salim ya bar mu ya matsu su shige,</p><p> Saboda gajiyar da muke da shi,</p><p> Bayi muka fara shiga muka dan gyara jikin sanan muka dauro Alwala muka fito,</p><p> Duk da wurin ya cika tab da jama,a tun awajen baisa mun tsaya wajen ba ciki na rikewa Amal hannu muka kutsa Allah ya taimake mu muka samu wuri kusa da wasu yan tsufi mutum biyu mata, mutanen Indonesia</p><p> Muna zama yar tsuhuwar guda ta gyara muna wuri muka zauna gab da su jiran afara sallah gudan ce ta miko muna hannuta guda da baida tasbaha muyi mu,sabi,a da ita, </p><p> Bayan an salamay tsuhuwar guda tace muna mudan taimaka masu suna son suyi ziyara kada a matse su a gurin,</p><p> Tare muka jera da su har cikin Rauda, kusatawa naitayi cikin jama,a har bisa green carpet din nan da akace shine saitin kabarin Annabi yake,</p><p> Dole nice na tsaya masu suka samu sukayi sallah raka,a biyu sukayi gaisuwa ga maikin Allah tare da sahabban shi guda biyu da aka rufe su kusa da kusa,</p><p> Sanan na samu nima nabi ayarin wasu yan Syrian nayi nawa raka,a biyun na addu,a </p><p> Batare da bata lokaci ba na jawo yan tsuffin nan da Amal mukayi Exist kafin akore mu,</p><p> Anan muka sha ruwa mukayi buda baki dayake watan azumi ne bamuyi wahalan sayen abinci ba ga karama nan kalakala ana bi layi layi ana ajewa sadaka saboda Allah da Annabi batare da kasan kowa yakawo ba,,,</p><p> Sai bayan sallah isha,i muka, bar masallaci zuwa masaukin mu,</p><p> Dayake nasan gidan sai nai gaba wurin nuna masu, kowani sashi,</p><p> Kafin mu kwanta muna dan hira mu a falon gidan wayata na gefe wacce bata da wani amfani inba game ba dom nasan cewa banda labar kowa da zakira,</p><p> Shine samu yafi iyawa, gadai waya dankareriya amma ba lambar kira saidai gamen da sauran abubuwa,</p><p> Cikin ikon Allah wai yau wayan itace tayi kara alamar ana kirana,</p><p> Salim ne yace kirana akeyi nace mai, a,a bakira bane,</p><p> Yace to may nace mai oho, </p><p> Wayanta kara yin ruri alamar kira nabiyu ya kara shigowa kuma,</p><p> Shi yai min received ya kara min a kune na,</p><p> Abin mamaki wai muryan Sheriff din mu naji radam awayan nawa yana sallama,</p><p> Saida nadan daga wayar nakalla cikin mamaki sanan nakara sawa a,kune na,</p><p> Jinayi yana ce min ya muka isa nace mai lafiya,</p><p> Kafin yai wani magana namika ma Amal,</p><p> Saina koma gefe ina mamaki, don ance kira saida sim to aini ko sim din bansa ba balle insa kudi,</p><p> Abinda yafado min arai shine kafin mu bar makkah a daren jiya su sheriff da Salim suna zaune nazo wucewa Salim ke cewa sai faman rike waya nakeyi kamar wace za,akira </p><p> Yace min inbashi wayan ya gani na mika mai naga yafara game sai nawuce na barshi da ita, kawai </p><p> Sai zuwa zan kwanta nazo nasamu wayan an aje min samar wani dan tabur dake gefen kujerar zaman Sheriff inda yake yawan zama ya bude system din shi,</p><p> Anan nasamay ta aje nadauka ina gode ma Allah nafisa bata gani ba, aida yau narasa wayan ke nan,,,,,</p><p> Ban kai karshen tunanen ba naji muryam Salim nace gashi zan bata, </p><p> Dama da larabci yake min magana ni dashi dinma yacigaba dayi min ko yanzu,</p><p> Yafada min cewa kada mu makara gobe zuwa wurin da zasu don Allah inyi sakko in kai su na ansa da fadin na,am insha Allah,, da haka yakashe wayar yana mai min godiya</p><p> Wayar nabida kallo kamar yau na fara rikata mamaki fal a,zuciyana,</p><p> Amal tace min aiko tunda yawa na da sim zata kira wasu kawayen ta da sukayi karatu a FGC bauchi tare , saboda ta fada masu cewa itakan tana saudiya,</p><p> Ganin mamaki a fuskana Salim yace min halan bansan cewa ansa min sim bane , yace min jiya Yayansu yasa min sim sabo yakuma yi loading din kudi saidai baisan ko nawa bane a ciki,</p><p> Bamu dade ba muka kwanta saboda musamu zuwa inda zamu da wuri da safe,</p><p> </p><p> Karfe takwas na safe yai muna a office din mutumin inda ya kaimu wani guri da za,ai muna interview,</p><p> Nikan yar rakiyace don haka binsu kawai nakeyi hankalina kwance sabanin su danaga duk sun shiga damuwa, sosai</p><p> Kwantar wa Amal da hankali kawai nakeyi,,har nasamu naga tadan shiga natsuwa,</p><p> Lokacin da aka kira su sai na zauna ban tashi na bisu ba,</p><p> Mutum ya waigo yace min in yasauri mana intaso kada muyi delay </p><p> Na dan waiga gefena inga kodawa yake magana sai naga tabas dani yake saina ce Ana, yace min Na,am</p><p> Da mamaki natashi na gyara nabisu baya tare muka shi mu uku,</p><p> Abu na farko da na lura dashi shine sun fara diba shigar mune, sai kuma natsu,</p><p> Bawani dongon tambaya sukai muna ba sundai tatace takardun dake gaban su cewa mudin ne bawasu bane,</p><p> Don haka suka ce muna mufito waje,</p><p> Mamaki min fal a zuciyata don ban san ko may ke faruwa ba,</p><p> Mutumin da yai muna jagora ne yake ce muna gaskiya munyi sa,a sosai saboda shigar da mukayi ya nuna masu cewa muna da kamala kuma sun auna tarbiyan mu sunga ba mu da matsala shiya sa muka samu saukin interview din,</p><p> Amal ce ta kallo ni don ina ganin ta tuna da yadda mukayi jafin mubar gida dazu </p><p> Don wani dogon riga tadauko English wear zata sa na ce ma, la,la,la,</p><p> Kada tasahi nazaba mata wani dogon jallabiya baki maidan adon duwatsu bakake naba ,sai ta kama ce min ita gaskiya bata iya wanan shigar tamu kulun mutun ko yayi kwaliya mai kyau sai yadauko wani bakin riga cen ya aza sama,</p><p> Ban kulataba na gyara mata rolling dinta baka ganin komai nata sai dan fuskanta kadan duk da bataso bataki tanawa ba,</p><p> Munfito falo naga Salim da wandon jeans da riga yar karama duk ta matse mai damtse hannunbshi surar jikin shi yafito,</p><p> Shima magana nai mai yai kamar zai make ni da dan filon dake kan kujerar falon sai nadan kauce ina dariya </p><p> Amal tace mai nima kaga yadda tasani shiga kamar wata yar shi,a can</p><p> Zuwa yayi yasako jallabiyar shi fara, tare da yar fullashi fara,</p><p> Yafito nace mai to ko kai fa, ya zakazo wa mutane haka kamar mai zuwa wasan wrestling,</p><p> Dariya mukasa muka sa gaba dayan mu, sai muka, fita zuwa wurin mota,</p><p> Hannu na Amal tarike gam batare da taimin magana ba,</p><p> Har muka gama komai tana rike da hannu na cikin nata,</p><p> Saida muka shiga mota don dama mun fitogaba dayane da niyar komawa gida,</p><p> Amal take ce min kai Fadima anya kuwa, ke ba,, sai kuma tai shiru, </p><p>bataci gaba da magana ba,</p><p> Wata ce tai yar tsuwa alamar kira yashigu, nadauka tare da yin sallama cikin tatausar murya ya ansa yana ce min </p><p> Yacigaba da cewa shukuran shukuran ya ukhtin Ana asfan,</p><p> Murmushi nayi kadan har fararen hakora na suka dan baiyana afili,</p><p> Ashe sautin murmushi har inda yake yaji shi, alamar naji dadin yabon da yai min,</p><p> Kafin yafadi wata magana sai na mika ma Amal wayan ,jinayi tana cewa yayan mu nice </p><p> Dariyan danaji tana yi yasa nadan waiga gefenta sai naji tace walahi yayan mu Fadima Allah bata wayo itace fa tasa mu wanan shigar har ina fada da ita,</p><p> Salim harda maketa yatashi yi don tace baza mu fita dashi hakana,</p><p> Salim din ya karbe wayan hannun ta shima yashiga hira da dan uwan nashi,</p><p> Akarshe yadan ihu da murna najin dadi yana fadin an aikawa wa yayan mi cewa duk andauke mu a makarantar </p><p> Murna mukasa a cikin motar Allah yasa Yusuf gwanine da saidai yadda hali yayi, kawai,</p><p> Bayan mundan tsagaita murnan Amal ke ce min wai yaya nasan cewa suna considering da shigar mutun ,</p><p> Saina bata labarin lokacin da baban Nailabin zai sani karatu yadda mukayi a makarantar, dasu wurin ganin shigar da wasu sukayi,,</p><p><br /></p><p> Mun isa gida lafiya cikin murna dafarin ciki dakin ummi muka wuce direct, </p><p> Yadda nags sun rugumay ta nima kusan hakan naje na rugumay ta tajowo ni sosai cikin jikinta, </p><p> Bansan lokacin da na fara hawaye ba, ummi tace a,a,a tajeye Amal takara jawoni sosai cikin jikinta tana share min hawaye tace asha fadima godiyan da zakiyi wa Allah ke na ta dagoni tana mai girgiza kanta tace min inyi sadaka in nafila ingode ma Allah shine abin yi ba wai kuka ba,</p><p> A gasikiya ni dai bansan may zance wa wayan nan mutane ba don godiyar da baki bai yi sai dai shukuran,</p><p> Saboda irin halarcin da suke gwada min yai yawa walahi banda wani matsala yanxu sam</p><p> Matsalata gudane itace Nafisat wace kusan kowa agidan taza mai ciwon ido,</p><p> Har maigidan takai mai ko ina, arayuwa bin umurni mahaifi ne kawai yasa shi yin hakuri,</p><p> Dana tashi gurin hajiyar mu na nufa naje naimata bayanin komai da akeci,</p><p> Taimurna so tayi farin ciki dajin bayani da nai mata inda tayi min addu tare da kara roko na gafaran abinda taimin can baya,</p><p> Har kullun ce mata nakeyi ni batai min komai ba don komay yafaru da mutun tab batacen al,amari ne,</p><p> Tun ran gina tun ran zane duk abinda zai samayka saifa yafaru,</p><p> Don haka zuwa na gurinta da kuma zuwa na makkah koba ta dalilin taba saina zo</p><p> </p><p> Sheriff din mu bai gida yatafi Riyadh gurin aiki don haka koda muka dawo mun samu baya gari,</p><p> Don haka hankalin mu kwance, muke komai kasan cewa gidan mu na yanzu babba shiyasa badole bane wani yaga wani inba da wani dalili ba,</p><p> Nafisat zan iya cewa rabon da naganta tun ranan da ta,tashi shaka na aka ceceni gurin ta,</p><p> Yanzu wanan kawar data samu itace tadauko mata yar aiki wace itace ke mata komai,</p><p> Mudakeyi da duk andakatar da mu, ko sai dai muyi aikin mu na tsakar gida zuwa fannin sheriff </p><p> Komai na sheriff nice mai kula da su duk da kasan cewar shi ba mai zama gida bane ,,,</p><p> Anytime yana gurin aiki,n shi, shida Mustapha,</p><p> Yau na zo zan wuce ta ban garen dakin nafisat aiko sai naji muryan su kasakasa ita da yar lici </p><p> Waya na dan na record </p><p>Daidai lokacin tana cewa, gaskiya yar lici, malam garin nan aikisu baici don daini gaskiya banga wani canji ga Ahmad ba yace sai na kori wanan yarinyar ajiki na aiko zaiyi amma gashi bata tare dani har yanzu nakasa samun kan Ahmad din</p><p> Kada kidanu uwar daki komai zaizo daidai insha Allah kinsan cewa,</p><p> Yanzu watan azumi ne basu faye yin irin miyagun asiran nan badon iskokai andaure,su</p><p> Ko shekaran jiya dazai wuce na yi,nayi dashi yaban wasu yan kudade amma sam yaki,</p><p> Sai ce min yayi kyautar shi sai yaga dama kuma ko yayi niya idan mutum yatambaye shi shi bai badawa kuma,</p><p> Dama yau nazo in fada maki cewa akwai wani malami dan kasar ghana da yazo gurin shi zamu kafin ya koma,</p><p> Don insha Allah wanan karon sai mun gwada mai mun fishi sani duk wani takon shi,</p><p> Har zan wuche saina da tsaya nakara saurarawa, jinayi nafisa tayi dan tsaki tace wlh indan yafi karfi na sai kawai insa akashe min shi har shegeyar uwar tashi kawai ingaba da komai nawa,</p><p> Sainaji sun tafa,</p><p> Kafana naji baiko iya dauka na don tsoro, dabayabaya nabar gurin nakoma dakina</p><p> Aiko atake zazzabi ya sauka min</p><p> Gazafin ciwo ga tunane ya isheni, azuciyana</p><p> A kan gado na zube sanan na lumshe idona bugawar zuciyata kawai nake sauraro yadda yake kara karuwa,</p><p> Meye abin yi? Tambayar da nayiwa kaina ke nan</p><p> Cikin wani hanzari na mike nafada bayi don inyi alwala sai kawai naga bani da tsarki, ,,,</p><p> Adadafe ranan naje kitchen haka na daure nadafa masu hjy da ummi abinci har dani,</p><p> Adakin na koma don in nazauna dakina tunane zai min yawa nikadai,</p><p> Acan naita fama da ciwon mara na ana min sannu,</p><p> Dana danji sauki saina debi abinci don in,dan ci </p><p> Nafara ci nakai cibiyu nabiyu kena sai mukayi arba da </p><p> Sheriff wanda ke tsaye bakin kofa yana kokarin dauko wayan shi, dake tsuwa aljihun shi,</p><p> Cibin na mayar don kunyar danaji yakamani,,yai min wani irin kallo na C U, Salim dake bayan shi ne ke fadi kai amma fadima,</p><p><br /></p><p>_ 🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>24/10/2017, 1:50:21 PM: Maman Safwan: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 5⃣5⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p><br /></p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>🎁NASIBI WRITERS ASSOCIATION🎁</p><p>🎁N🎁W🎁A</p><p><br /></p><p> Almost true life story</p><p><br /></p><p>A kofar gidan da maman umar tai kwatancen take muka tsaya gidane mai hawa goma sha biyu gidane wanda yan umarah ko aikin hajji ke zama aciki shi,,,</p><p> kimanin dakuna ,dari da hamsim ke cikin gidan ,</p><p> Nice nafita zuwa wajen yan matan takarin da naga suna saida abincin a kofar gidan,</p><p> Na,tambaye su ko bakin da suka sauka da ga Nigeria suna ciki,</p><p> Ko sun tafi, tunda anyi sallah ba za su tsaya ba wuce zasufara yi,</p><p> Tunda nasan cewa tashigo kasan ne amatsayin wacce tazo yin umurah,</p><p> Kuma nasan muddin bata samay muba zata iya zaman boyo bazata koma ba sai taga yaranta,</p><p> Nuna min wata mata da ke xaune ta ba mu baya, tana saida wasu kayan tarkace akofan masaukin da mukazo sukayi,,,</p><p> Matar tana da dan tazar damu kadan don haka ba lalaine taji maganar muba daga nisa,</p><p> Na,isa gurin da take zaune ta kasa kayan su takalma da rigunar barci sai su hijab,</p><p> Duk wanan abin su Almustapha da Salim na cikin mota suna kallon na </p><p> Sallama nai wa matar ta waigo a hankali daidai lokacin tana ciniki da wani mutum mai son sayen hijjab agurin ta</p><p> Fadimar mama Sharwali,</p><p> Tamike tsaye,cikin sauri ta dafe kirjin ta tana dan kokarin waigen bayana kazata ga garan,</p><p> Cikin kidima da rudewa take ce min Umar da Aisha fadima suna ina don Allah,</p><p> Dama nasan cewa zasu samu taimako daga gurin ku insha Allah ,,,,</p><p> Sai kuma ta fashe da kuka, mai tsuma rai, ,,, ganin da nayi tana shirin tara muna mutane,</p><p> Yasa ni jawo hannu ta muka nufi, motar da mukazo da ita,</p><p> Muna bayan motar nida ita take ce min tunda aka kamata da kwana biyar aka wuce da ita kasar ghana can jirgi ya zube su,</p><p> Allah yasa tana da dan kudi ajikin ta shine tasamu tazo gida dashi, katsina,</p><p> Tana fadin wanan maganan sai zuciyana tatuno min da Rugaiyya na,</p><p> Nace ko tayi sa,a tasamu jirgin yan Nigeria ankaita gida,</p><p> Sai natuna cewa koma ina aka kaita insha Allah tana da wada,tacen kudi wanda zasu kaita, gida,,,,</p><p> Motar muna tsayawa umar ne yafara taron mu, ya inda flower's suke yana wasa </p><p> Tsaye yayi cikin mamamki yana kallon uwar don gani yakeyi kamar idon shi na gizo ne, </p><p> Zuwa yayi ya rungumay ta, tam yana cewa ummi ke ce ko kuwa ummi may yasa kika gudu kikabar mu ,</p><p> Tun yana surutu yana sambatu, har yagaji yai shiru yana sha shekar kuka,</p><p> Aisha kan fafir kin zuwa tayi wurin mahaifiyar nasu ba yadda ban yi da ita ba amma sam taki, </p><p> tace ita,sam bata zuwa, gurin uwar,,,,</p><p> Saida Sheriff yadawo nagabatar mai da ita tare da yaran nata </p><p> Inda nake zaune itama yarinyar anan take zaune duk falon yayi tsit kamar ba, kowa ciki,</p><p><br /></p><p> Saida yandayi gyaran murya san nan ya fara magana, bayan sallama yai ma Allah godiya da ya nufe mu da ganin wanan ranan, mai albarka da anfani </p><p> Saida yai ma kowa dake wurin nasiha so sai mai kashe ma bawa jiki da kara imani a zuciyar mutum,,</p><p> Sanan yajuya inda duk muke zaune har ummi da su Yumma da hajiyan mu, </p><p> Yafara da tambayar ta yace itace ta haifi yaran kokuwa tace mai itace,</p><p> Yace to yanzu zata bar kasa saudiya da su ne ko kuwa zata kara zama acikin kasar ne kaman da,</p><p> Amatsayin yar takari, Saida tashere wani gumi da ya keto mata, tunkun sanan ta dan daga kai ta kalleshi, </p><p> Hannu bi,biyu ta daga tacewa don Allah yatai make ta ya ce,ci rayuwan su,</p><p> Idan tace zata koma bata da kudin jirkin daukar yaran,</p><p> Kuma idan taje dasu Nigeria za,ace yaran basu da uba ,</p><p> Nasan cewa ganin da naimata ta,tana kuka zai iya sani kukan nima, </p><p> Don haka dagawa na tsab rike da hannun Aisha muka shige ciki,</p><p> Ina tashi yabi inda nabi da kallo yasan abinda zanje yi ,, watau kuka ke nan,</p><p> Yace mata tadaina kuka zai taimaka yaba su sana,ar yi wanda zasu dan samu,</p><p> Amma fa su sanda cewa nada wani dan lokaci insha Allah zai taimaka masu kowa ya koma gida,</p><p> Kafin yabar kasan, kowan su yayi murna akayi godiya ,</p><p> Bayan an watse ummi tadinga samai albarka tana mai godiya,</p><p> Ina ciki ina kallon Aisha cikin tausayi don nasan cewa tabbas za,a raba mune da ita ne yau</p><p> Shiru shiru ina ciki ina jiran azo ace min in kawo Aisha zasu tafi sai naji shiru, </p><p> Jin shirun yai min yawa saina dan gyara mata kwaciyan ta a hankali na fito waje,</p><p> A hankali nake saukowa daga step din dagani na kasan banda wani kuzari ajikina,</p><p> Shiru naji wurin yayi ba motsin kowa, a wurin cikin mamaki nakarasa saukowa ,</p><p> Ganin ba kowa yasa wuce wa dakin ummi,</p><p> Don in gani ko may ke faruwa nida nabar falo tab da mutane , dazu sai gashi cikin yan mintina nafito banga kowa ba,,,</p><p> Ummi ce kawai adaki daganin ta ta idar da sallah nafila ne don dai lokacin sallah da sauran tsamu</p><p> Gefen kujerar dake dakin ta na,dan samu gefen hannun kujerar na zauna,</p><p> Inajiran ta shafa addu,an da na samay ta, tanayi,</p><p> Ina dan wasa da yatsun hannu na ina lankwasa su,suna ba dan kara wani dawani dan sauti,</p><p> Muryam Sheriff ne naji yai sallama dakin, zubur nayi na gyara zamana ,tukun a tsorace nadan waiwaya kofar shigowa dakin na ummi,</p><p> Barka da rana, nace mai cikin sanyayan murya,,, </p><p> Saida ya dan kalli gefen da nake zaune sai ya kauda kanshi</p><p> Wani, irin dan guntun murmushi ya makale, agefen fuskanshi , yace yawa,</p><p>Sai Yace min nazo ne in ma ummi ruwan hawayen da nafi kowa iya zubar wa, itama tagani ko,</p><p> Sigar da yai maganar sai yasa nadan sake jiki ga tsoratar danakeyi mai</p><p> Tun jiya ban son mu hadu dashi,</p><p> A hankali yatako yazo ya shiga dakin,,</p><p> Ta inda nake zaune dole zai wuce tagabana, yana sanye da farar T shirt an rubuta agaban rigan iam proud to b a Muslim, da jan kala, sai dogon wandon chunus da yasa mai kyau kalar ruwan toka,, Wani farin agogo ya makala na kamfanin D&G wato, Dolece & Gabbana, sai wasu fararen takalma masu daukan ido ruffafu, dasu, amma a kofa yacire takalman,</p><p> Yazo tagabana yawuce hancina kamar cikin kwalban turare na nutsa shi,</p><p> Don kamshi shikam sheriff Allah yabashi son kamshi sosai don har abin ya bi mai jiki,</p><p> Don ko wuri ya zauna yatashi kamshin bai barin wurin, </p><p> Danaga ya shigo saina dan mike da niyar in fita waje,</p><p> Cikin saurin yace min in zauna abina ba zama zaiyi ba sako ne yazo fada mata,</p><p> Kaita dago a hankali tana kalllon shi, saiyake ce mata Abban shi yai mai waya zasu iso nan da gobe insha Allah,</p><p> Adduan tadan katse cikin lokaci guda , tace sai in koma wancan gidan naka ke nan ko har subar gari,</p><p> Dan murmushi yayi wanda yakara mai kyaun fuska,</p><p> Yace koda sunkai su dari ne insha Allah inada inda zan aje su ummi, basai kin bar gidan ki ba,, </p><p> Idan baki so su ganki ne ,har su koma babu wanda zai ganki,daga cikin su,, </p><p> Tace aishi zannah dan uwa hauwa nane ka ga bazan ce ban kin ganin shi mu gaisa amma sheri irin na hjy mama nake ma gudu,</p><p> Saboda gwanace ta kware wurin kulla sheri</p><p> Nidai Inajin su nai tsit kamar ruwa ya cine,</p><p>Don nauyin da nake ji, </p><p> a dakin sai nakoma takure cikin su gashi ina son fita tun farko ya hanani,</p><p> Ya ce ummi ki kwantar da hankalin ki don mama a halin yanzu kinfi karfin duk wani sheri da zata iya yi maki yazama tarihi insha Allah</p><p> Ummi tace ai inaga halin nasu a jini yake don kusan itama wanan yarinyar ta wurinka ba inda tarage halin Aminar</p><p> Saidai kawai muce Allah ya gyara tunda kun riga kun gaurayu da su ko,</p><p> Yace amin a sanyaye ya dan satan kallon na inda nake zaune,, </p><p> Duk hiran da suke yi shida ummi kaina yana kasa ban daga ba don duk a tsawale nake, cikin su</p><p> Saboda ba maganar da za,ayi agabana bane,,,,, </p><p> Sai alokacin ma natuna da nafisa don tun wurin cin abincin sallah jiya ban kara ganin ta ba</p><p> Dakina na koma batare da na tambayi ummi maganar mahaifiyar su umar ba,</p><p> Amal ce ta fado min a raina don nasan cewa zanji komai da yafaru a wurinta, gamay da maman su umar din,,</p><p> Tana zaune saman gadon ta duk tai dadaya da kayan ta wai ta fara shirin tafiya makaranta ne, inji ta dariya nai mata nace ai akwai sauran time,</p><p> Da sallama na karasa shiga dakin nata, tana duke tana ta faman gyaran takardun ta,</p><p> Wani littafi mai hoton wasu ma,aurata nagani a gefen ta sai na jawo nadan fara diban hoton dake jikin bangon </p><p> Nace mata gaskiya sunyi kyau sosai wallahi, </p><p> ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 5⃣5⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p><br /></p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p>🎁NASIBI WRITERS ASSOCIATION🎁</p><p>🎁N🎁W🎁A</p><p><br /></p><p> Almost true life story</p><p><br /></p><p>A kofar gidan da maman umar tai kwatancen take muka tsaya gidane mai hawa goma sha biyu gidane wanda yan umarah ko aikin hajji ke zama aciki shi,,,</p><p> kimanin dakuna ,dari da hamsim ke cikin gidan ,</p><p> Nice nafita zuwa wajen yan matan takarin da naga suna saida abincin a kofar gidan,</p><p> Na,tambaye su ko bakin da suka sauka da ga Nigeria suna ciki,</p><p> Ko sun tafi, tunda anyi sallah ba za su tsaya ba wuce zasufara yi,</p><p> Tunda nasan cewa tashigo kasan ne amatsayin wacce tazo yin umurah,</p><p> Kuma nasan muddin bata samay muba zata iya zaman boyo bazata koma ba sai taga yaranta,</p><p> Nuna min wata mata da ke xaune ta ba mu baya, tana saida wasu kayan tarkace akofan masaukin da mukazo sukayi,,,</p><p> Matar tana da dan tazar damu kadan don haka ba lalaine taji maganar muba daga nisa,</p><p> Na,isa gurin da take zaune ta kasa kayan su takalma da rigunar barci sai su hijab,</p><p> Duk wanan abin su Almustapha da Salim na cikin mota suna kallon na </p><p> Sallama nai wa matar ta waigo a hankali daidai lokacin tana ciniki da wani mutum mai son sayen hijjab agurin ta</p><p> Fadimar mama Sharwali,</p><p> Tamike tsaye,cikin sauri ta dafe kirjin ta tana dan kokarin waigen bayana kazata ga garan,</p><p> Cikin kidima da rudewa take ce min Umar da Aisha fadima suna ina don Allah,</p><p> Dama nasan cewa zasu samu taimako daga gurin ku insha Allah ,,,,</p><p> Sai kuma ta fashe da kuka, mai tsuma rai, ,,, ganin da nayi tana shirin tara muna mutane,</p><p> Yasa ni jawo hannu ta muka nufi, motar da mukazo da ita,</p><p> Muna bayan motar nida ita take ce min tunda aka kamata da kwana biyar aka wuce da ita kasar ghana can jirgi ya zube su,</p><p> Allah yasa tana da dan kudi ajikin ta shine tasamu tazo gida dashi, katsina,</p><p> Tana fadin wanan maganan sai zuciyana tatuno min da Rugaiyya na,</p><p> Nace ko tayi sa,a tasamu jirgin yan Nigeria ankaita gida,</p><p> Sai natuna cewa koma ina aka kaita insha Allah tana da wada,tacen kudi wanda zasu kaita, gida,,,,</p><p> Motar muna tsayawa umar ne yafara taron mu, ya inda flower's suke yana wasa </p><p> Tsaye yayi cikin mamamki yana kallon uwar don gani yakeyi kamar idon shi na gizo ne, </p><p> Zuwa yayi ya rungumay ta, tam yana cewa ummi ke ce ko kuwa ummi may yasa kika gudu kikabar mu ,</p><p> Tun yana surutu yana sambatu, har yagaji yai shiru yana sha shekar kuka,</p><p> Aisha kan fafir kin zuwa tayi wurin mahaifiyar nasu ba yadda ban yi da ita ba amma sam taki, </p><p> tace ita,sam bata zuwa, gurin uwar,,,,</p><p> Saida Sheriff yadawo nagabatar mai da ita tare da yaran nata </p><p> Inda nake zaune itama yarinyar anan take zaune duk falon yayi tsit kamar ba, kowa ciki,</p><p><br /></p><p> Saida yandayi gyaran murya san nan ya fara magana, bayan sallama yai ma Allah godiya da ya nufe mu da ganin wanan ranan, mai albarka da anfani </p><p> Saida yai ma kowa dake wurin nasiha so sai mai kashe ma bawa jiki da kara imani a zuciyar mutum,,</p><p> Sanan yajuya inda duk muke zaune har ummi da su Yumma da hajiyan mu, </p><p> Yafara da tambayar ta yace itace ta haifi yaran kokuwa tace mai itace,</p><p> Yace to yanzu zata bar kasa saudiya da su ne ko kuwa zata kara zama acikin kasar ne kaman da,</p><p> Amatsayin yar takari, Saida tashere wani gumi da ya keto mata, tunkun sanan ta dan daga kai ta kalleshi, </p><p> Hannu bi,biyu ta daga tacewa don Allah yatai make ta ya ce,ci rayuwan su,</p><p> Idan tace zata koma bata da kudin jirkin daukar yaran,</p><p> Kuma idan taje dasu Nigeria za,ace yaran basu da uba ,</p><p> Nasan cewa ganin da naimata ta,tana kuka zai iya sani kukan nima, </p><p> Don haka dagawa na tsab rike da hannun Aisha muka shige ciki,</p><p> Ina tashi yabi inda nabi da kallo yasan abinda zanje yi ,, watau kuka ke nan,</p><p> Yace mata tadaina kuka zai taimaka yaba su sana,ar yi wanda zasu dan samu,</p><p> Amma fa su sanda cewa nada wani dan lokaci insha Allah zai taimaka masu kowa ya koma gida,</p><p> Kafin yabar kasan, kowan su yayi murna akayi godiya ,</p><p> Bayan an watse ummi tadinga samai albarka tana mai godiya,</p><p> Ina ciki ina kallon Aisha cikin tausayi don nasan cewa tabbas za,a raba mune da ita ne yau</p><p> Shiru shiru ina ciki ina jiran azo ace min in kawo Aisha zasu tafi sai naji shiru, </p><p> Jin shirun yai min yawa saina dan gyara mata kwaciyan ta a hankali na fito waje,</p><p> A hankali nake saukowa daga step din dagani na kasan banda wani kuzari ajikina,</p><p> Shiru naji wurin yayi ba motsin kowa, a wurin cikin mamaki nakarasa saukowa ,</p><p> Ganin ba kowa yasa wuce wa dakin ummi,</p><p> Don in gani ko may ke faruwa nida nabar falo tab da mutane , dazu sai gashi cikin yan mintina nafito banga kowa ba,,,</p><p> Ummi ce kawai adaki daganin ta ta idar da sallah nafila ne don dai lokacin sallah da sauran tsamu</p><p> Gefen kujerar dake dakin ta na,dan samu gefen hannun kujerar na zauna,</p><p> Inajiran ta shafa addu,an da na samay ta, tanayi,</p><p> Ina dan wasa da yatsun hannu na ina lankwasa su,suna ba dan kara wani dawani dan sauti,</p><p> Muryam Sheriff ne naji yai sallama dakin, zubur nayi na gyara zamana ,tukun a tsorace nadan waiwaya kofar shigowa dakin na ummi,</p><p> Barka da rana, nace mai cikin sanyayan murya,,, </p><p> Saida ya dan kalli gefen da nake zaune sai ya kauda kanshi</p><p> Wani, irin dan guntun murmushi ya makale, agefen fuskanshi , yace yawa,</p><p>Sai Yace min nazo ne in ma ummi ruwan hawayen da nafi kowa iya zubar wa, itama tagani ko,</p><p> Sigar da yai maganar sai yasa nadan sake jiki ga tsoratar danakeyi mai</p><p> Tun jiya ban son mu hadu dashi,</p><p> A hankali yatako yazo ya shiga dakin,,</p><p> Ta inda nake zaune dole zai wuce tagabana, yana sanye da farar T shirt an rubuta agaban rigan iam proud to b a Muslim, da jan kala, sai dogon wandon chunus da yasa mai kyau kalar ruwan toka,, Wani farin agogo ya makala na kamfanin D&G wato, Dolece & Gabbana, sai wasu fararen takalma masu daukan ido ruffafu, dasu, amma a kofa yacire takalman,</p><p> Yazo tagabana yawuce hancina kamar cikin kwalban turare na nutsa shi,</p><p> Don kamshi shikam sheriff Allah yabashi son kamshi sosai don har abin ya bi mai jiki,</p><p> Don ko wuri ya zauna yatashi kamshin bai barin wurin, </p><p> Danaga ya shigo saina dan mike da niyar in fita waje,</p><p> Cikin saurin yace min in zauna abina ba zama zaiyi ba sako ne yazo fada mata,</p><p> Kaita dago a hankali tana kalllon shi, saiyake ce mata Abban shi yai mai waya zasu iso nan da gobe insha Allah,</p><p> Adduan tadan katse cikin lokaci guda , tace sai in koma wancan gidan naka ke nan ko har subar gari,</p><p> Dan murmushi yayi wanda yakara mai kyaun fuska,</p><p> Yace koda sunkai su dari ne insha Allah inada inda zan aje su ummi, basai kin bar gidan ki ba,, </p><p> Idan baki so su ganki ne ,har su koma babu wanda zai ganki,daga cikin su,, </p><p> Tace aishi zannah dan uwa hauwa nane ka ga bazan ce ban kin ganin shi mu gaisa amma sheri irin na hjy mama nake ma gudu,</p><p> Saboda gwanace ta kware wurin kulla sheri</p><p> Nidai Inajin su nai tsit kamar ruwa ya cine,</p><p>Don nauyin da nake ji, </p><p> a dakin sai nakoma takure cikin su gashi ina son fita tun farko ya hanani,</p><p> Ya ce ummi ki kwantar da hankalin ki don mama a halin yanzu kinfi karfin duk wani sheri da zata iya yi maki yazama tarihi insha Allah</p><p> Ummi tace ai inaga halin nasu a jini yake don kusan itama wanan yarinyar ta wurinka ba inda tarage halin Aminar</p><p> Saidai kawai muce Allah ya gyara tunda kun riga kun gaurayu da su ko,</p><p> Yace amin a sanyaye ya dan satan kallon na inda nake zaune,, </p><p> Duk hiran da suke yi shida ummi kaina yana kasa ban daga ba don duk a tsawale nake, cikin su</p><p> Saboda ba maganar da za,ayi agabana bane,,,,, </p><p> Sai alokacin ma natuna da nafisa don tun wurin cin abincin sallah jiya ban kara ganin ta ba</p><p> Dakina na koma batare da na tambayi ummi maganar mahaifiyar su umar ba,</p><p> Amal ce ta fado min a raina don nasan cewa zanji komai da yafaru a wurinta, gamay da maman su umar din,,</p><p> Tana zaune saman gadon ta duk tai dadaya da kayan ta wai ta fara shirin tafiya makaranta ne, inji ta dariya nai mata nace ai akwai sauran time,</p><p> Da sallama na karasa shiga dakin nata, tana duke tana ta faman gyaran takardun ta,</p><p> Wani littafi mai hoton wasu ma,aurata nagani a gefen ta sai na jawo nadan fara diban hoton dake jikin bangon </p><p> Nace mata gaskiya sunyi kyau sosai wallahi, </p><p> Sai tadan,diba tace ai yan uwan mu ne wanan bashir kenan dan yayan ummin mune, ita kuma matar yar uwan su ummi ce ta haifeta,</p><p> Cikin littafin na bude na fara karatu, sai naga sunaye ne mutane da lambobin su birjit,</p><p> Batare da ta waigo ba Amal ta,ke ce min sunayen abokaina ne da mukayi karatu da su a bauchi,</p><p> Ina ta karantawa tana dan yi min bayanin wasu masu mahin manci, daga cikisu,</p><p> Har nakai ga wata Khadijat Abdullahi dogon daji,</p><p> Zubur na mike don jin sunan dogon dajin dayi,</p><p> Nace mata ita tasan dogon dajin ne bata waigo ba tace min a,a ita kawai a school suka hadu da ita Khadijat din amma yar kano ce,</p><p> Nace Anty,Amal tace ummm dataji kiran ba na wasa bane sai ta dan waigo ni,</p><p> Nace dongon daji fa sunan garin mu ke nan,wata wata kila, ita Khadijat din yar garin muce,</p><p> Don Allah ki taimaka min ki buga mata waya muji ko Allah yasa yar garin namu ne, ita din ne,</p><p> Nakara cewa don Allah Anty Amal ki taimaka min kikiramin ita,</p><p> Batare da ta waigo tace min to naji, amma sai kin kwashe min wa,yan,nan takardun kin mayar,</p><p> Babata lokaci natashi na kwashe duk kayan da ra baza saman gadon </p><p> Har abinda batace ba saida nayi mata adakin</p><p> Ya,mutsa fuska tayi tana fadin, ke nifa Khadijat ba wai muna wani shiri da ita bace,</p><p> Ko wanan lanbar ma ina karba ne tana gurin kada taji daban shiyasa nace abata,</p><p> Nakara cewa haba Amal tace o Amal ko nace anty Amal,</p><p> Tace min in kawo wayana takira ta,</p><p> Aikafin takira layin Khadijat din saida takira kusan mutum uku kafin takira tana fada masu cewa tana kasar saudiya,</p><p> Saida taga dama don kanta tai dialing din noban khadijat din</p><p> Yako shiga amma har wayan ya katse ba a dauka ba,</p><p> Kusan kira biyu mukayi ba,a daukan wayan,</p><p> Dole muka kyale amma raina a bace,</p><p> Washe gari tunda safeg</p><p> Ina saye da yar doguwar rigar danayi sallah da ita ajikina ban riga na shiga wanka ba tukun,,,,</p><p> kirana aka yi ta intercoms din daki na</p><p> Cikin sauri sauri na sauko batare da na canza kaya ba,</p><p> Ina zuwa nadinga jin wani iri kugi da huci a saman ,dakuna kamar wani irin halitta ne yashigo muna,</p><p> Kusan duk kowa yana tsaye ina zuwa sai nake tambaya ko may ke faruwa haka na ne,</p><p> Almustapha ne yace min in shiga dakin matar sheriff ne sautin ke fitowa gashi kuma Sheriff bai gida yatafi wurin judging tunda safe,</p><p> Ba bata lokaci na fada dakin, Nafisat ce kwance cikin wani irin hali ga. kwalaben sirup nan kusan kala biyar tayar a kasa gefen gadon ta,</p><p> Ina shiga na tallabo ta aiko sai kokarin sakewa takeyi kamar mara rai,</p><p> Saketa nayi da sauri na fito dakin nata cikin tashin hannankali,</p><p> Nace ma almustafa yasa adauko min zuma da madara da sauri,</p><p> Ana kawowa nayi dibara nabude bakinta na tura mata kusan cokali biyu na zuma,</p><p> Aiko yana shiga cikin ta tai wani irin yunkurin amai, saida kowa ya watse don sun dauka ko ta shake ni ne,</p><p> Sheriff ne tsaye da kayan games ajikin shi yana mamakin ihun da yake ji tun shigowar shi get,</p><p> Sai gashi kuma yaga kowa na batun gudu,</p><p> Cikin tashin hankali mustapha ke mai bayanin abinda ke faruwa,</p><p> Dasauri ya haura sama dakin nata koda ya shigo tana kwance sharbat da ita saman jikina,</p><p> Ga wani irin amai da take kwarawa,</p><p> Maman su Umar na tsaye daga kofa rike da goran zuma da na madara,</p><p> Cikin tashin hankali yake kallon ta yana tambayar may yasa may ta haka,</p><p> Ban kai ga bashi ansaba idon shi ya kai ga kwalaben kayan mayen da ke zube kasa gefen gadon ta,</p><p> Cikim tashin hankali ya fidda idon shi waje don mamakin </p><p> Wani aman ta kara zubowa mai wari,</p><p> Sainace wa maman Umar ta miko min goran madaran da ke hannu ta shima cikin hikima na dura mata shi Allah ya ban sa a,a ta sha sosai,</p><p> Sai wani irin amai ya zubu mata, sai kawai jikin ta ya sake ta </p><p> Duk sheriff ya rude yama rasa may zaiyi,</p><p> Ganin da yayi mata haka yasa yace mu kamota muje asibiti,</p><p> Nace mai idan mun kaita asibiti haka za,a tuhumay ka sosai kai ma,</p><p> Yagane may nake nufi shi yasa shi yin shiru don hukumar kasan saudiya indan sun fara binciken lamari sai sun gano harda abin da ba suyi niya bincike ba sai sun gano shi, ga mutum</p><p> Nafada mai cewa zata samu sauki sosai,insha Allah idan ta farfado saboda naga irin haka a makwabciyar gidan su hajiya laila ,</p><p> Dakin na gyara mata tasa sai abin kamshin daki da nasa don dakin ya rage warin da yakeyi, </p><p> Abinci naje kitchen nadafa mata maidan nauyi saboda nassn cewa tana fafadowa zata bidi abinci ne taci,</p><p> Sheriff duk mamakin wanan yarinyar ya kama shi ,, yace,kai yarinya karama da shegen wayo da dabara haka, </p><p> Ummi tashiga cikin wani irim yanayi na,damuwa,</p><p> Tayaya har Alhji zanna ya bari danshi ta auri wanan yarinyar da bata da tarbiya ko kadan,</p><p> Ita dai tasan cewa duk da Alhj zanna mutun ne shiru shiru,</p><p> To amma bai yadda da aikin assha a gidan shi </p><p> To ta yaya zai ma Ahamad wanan hadin haka,,</p><p> Sai misalin karfe ukun rana nafisat ta farka daga barci tana mai dan bude idon ta da yai mata nauyi sosai,</p><p> A hankali ta bude su gabadaya idon ta ya sauka kaina ina tsaye gefe guda,</p><p> Ina kallon ta,ta kara lunshi idon nata tayi kamar zata tasahi amma ta kasa, yun komai,,,, </p><p> Matsowa nayi kusa da ita ina mata sannu,</p><p> Ta yunkura ta tshi saikawai taji ai bata iyawa sam </p><p> Nagane nufin ta sai naje kusa da ita nadan tallafa ta ta bayan ta sai tayi kokarin hanani amma ganin da tayi bafa zata iya ba</p><p> Saita hakkuri da intaimaka mata din,</p><p> Saina kara riko saita dan dago daga kwance, nataimaka mata muka sa,uko daga saman gadon </p><p> Munkai tsakar dakJain's ga sheriff fuskan shi murtuk kamar bai taba yin dariya ba</p><p> Wani wa,wan kallo yai muna, nikan sai na noke kaina</p><p> Da taimako na nasamu taci abinci sosai tako shi,</p><p> Ganin da nayi sheriff yadawo dakin yasa ni fita waje </p><p> Sai a lokacin nasamu nadan gyara jikina tsab nafito shar dani,</p><p> Noban wayan yar dogon daji ya fado min a rai na tashi nadauki waya zuwa dakin Amal</p><p> Ina shiga tace min gaskiya fadima bansan cewa baki da zuciya ba sai yau wlh,</p><p> Nagane nufin, ta don haka, Kafin taci gaba sai nace mata kowa yataimaki wani Allah na taimakon shi, saboda Allah nayi saboda kuma Sheriff wanda hakan ba karamin rufin asirin shi bane</p><p> Cikin jin haushina takara kiran labar wayan amma sai bai shiga ba,</p><p> Haka na hakkura nakoma dakin nafisa nasamu ta kara yin barci </p><p> Dakina nadawo daniyar indan kwanta kafin anjima kadan</p><p> Barci mai nauyi yadauke ni sai gab da sallah magrib na farka</p><p> Nayi barcin kusan awa hudu,</p><p> Sallah nagabatar cikin sauri, sai nayo waje domin yuwa nake ji banci komai tunda safe dana danci kwai kadan ,,,</p><p> Saboda ina fara ci natuna da aman da nafisat tayi sai na kasa ci,</p><p> Ina fitowa falo saiko mukayi arba da hjy tsohuwa da Abba, sai </p><p> Da ihu naje nafada mata ajikin ta ina murna na manta da duk wa yanda ke falon zaune</p><p> Saida na natsu san nan naga wayanda suke tare, cikin ladabi nagaida kowan su nai masu sannu da zuwa</p><p> Abinci naga batar masu sai kuma masaukin da aka kai kowan su,</p><p> Fafir hajiya tsohuwa tace ita sai dakin ummi zata sauka ko kuma na Amal,,,, </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 5⃣6⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎🎁NASIBI WRITERS associations</p><p>🎁</p><p> 🎁N🎁W🎁W</p><p> </p><p> Almost true life story,,,</p><p><br /></p><p> Washegari natashi tunda safe na hada masu break fast, yadda yaka mata tare da taimakon su yumma,</p><p> Saida kowa ya kamala,break din ya sanan aka dawo falo aka zau zauna,</p><p> Ina tsaye ina hada kayan da suka gama cin abinci da su sai naji Allah Alhaji lawa zanna yana cewa a kamalo mai kowa da yakamata a kira mai agidan,</p><p> Falon yai tsit kowa na jiran ana sauraren abinda za a ce masu,</p><p> Wani takarada Abban yafitar daga cikin aljihun jallabiyar shi,</p><p> Sai da,ya fara bude taro da addu,a tukun sannan ya, kallo kowa dake falon,</p><p> Hjy tsohuwa tana zaune kusa da ummi,</p><p> Salim da Amal su gefe guda suma zaune, </p><p> Sai Sheriff da nafisat dake zaune kusan wuri guda </p><p> Duk da ba karfin jikinta take ji ba daurewa kawai tayi tadan fito tana yatsinar fuska,</p><p> </p><p> Alhaji zanna yace ubana mun zo ne wannan kasar don mu tatance wani takarda sako da aka tura wa hajiya acinkin kayan da aka kai mata sako daga nan,</p><p> Sai lokacin Sheriff ya dan daga kanshi yadan kali Abban da ke magana ,mamaki yakeyi don bai san kowa yaba da sako zuwa wurin hjy ba,</p><p> Jin falon yai shiru yasa Abban yace ma hajiya tsohuwa ,</p><p> Hajiya wane ya aika maki da sako,</p><p> Sai tace wanan yariyar mai kula da ku, tana dan waige ,waige ko zata gan ni,</p><p> Cikin mamaki sherrif yace fadima </p><p> Ta kware itace,</p><p> Ta aiko min da sakon wani magani dana taba saye na ciwon kafa da kuma na idanu,</p><p> Acikin sakon ta jefa wanan takardan</p><p> Ta nuna takardan da bakin ta daidai inda Abba ya aje takardan</p><p> Sheriff yace mai takarda ya kumsa Abba,</p><p> Sai Abban yace yanzu kuwa zaka ji,</p><p> Don inba zuwa nayi da hjy taga lafiyan ka kuma taji zancen daga bakin ka,ba ,ba,zata taba yarda cewa lafiya kake ba,</p><p> Saboda Abba yasan cewa kazafi akai wa nafisa a takarda don ba halinta ba ne</p><p> Asani shi diyan Aminin shi suna da tarbiya sosai,</p><p> Salim akasa yaje yakirani,</p><p> Lokacin ina nagama wanka ina gyara jikina kafin hjy tsohuwa tafito inda sukeyin mitin,</p><p> A cikin sauri da kuma shakku na isa falon gidan </p><p> Inda suke zazaune ana jiran in, iso,</p><p> Gefen kujera nasamu nadan labe cikin ladabi nakara gaida su,</p><p> Alh zanna ya kalle ni azuciyar shi yace kai mutun abin tsoro ne,</p><p> Ji wannan yariyar da ko yaushe nake ganin kirkin ta wai itace yau take wanan kullin sherin don kawai ta raba ma yara hannkula, su,</p><p> Ina gama gaishe su sai Abba yace min fadima "nace na,am Abba</p><p> Yace, ke ,ce kika aikawa hjy da sako nace eh yace harda takarda aciki </p><p> sai nayi dan shiru ina tunane. takardan may ke nan kuma,</p><p> Yace ke ce sai nace eh cikin rudewa, </p><p> Abba yace Alhamdullahi,</p><p> Yace Ahmad wani irin zama kakeyi da matar ka har yakai wanan yariyar taima hjy sako akan azo a ceci rayuwan ka kafin , nafisa ta halaka ka,</p><p> Zubur na mike ina nuna kai na nace la,la,la haram, haram bani bace, </p><p> Bantaba rubuta wasika ga kowaba zuwa Nigeria,</p><p> Tsawa Abban yadan daka min, yace bayan mun tambaye ki kin ce muna kece ki, aika,</p><p> Ina kuka wi,wi, ina sharban majina,</p><p> A hankali sheriff yadan daga yakalle ni cikin tausayi,</p><p> Saboda yasan cewa koda nice ma din ai ba karya nayi ba saidai kassh,</p><p> May yasa fadiman tai mai haka, saboda yasan cewa ko shi yakai karan nafisa gurin Abba abinda zai faru ke nan</p><p> Abba baison ace ga laifin ta sam,</p><p> Shiyasa yake hakkuri da komai taimai ,</p><p> Saidai fa gefe guda na zuciyar shi tana ce mai bani ce nayi wasikan ba , akwai dai, gaskiya,</p><p> Nafisa ce cikin karfin hali tana magana tace Abba bansan ko mai nayi wa wanan yariyar ba,</p><p> Ta hana ni shakat agidan mijina,</p><p> Idan nai magana yace min ita din amana take gareshi,</p><p> Hjy tsohuwa tace ke rufe muna baki zuriar yan sheri aiba don Allah kuka mamaye min jini na ba,</p><p> Ta Allah ba taku ba,</p><p> Abba na jin hajiyan shi sai yadan yi murmushi don yasan cewa bakin jinin Amina ce yashafi duk danginta,</p><p> Jin kukan danakeyi yai yawa yasa sherrif dinmu yin maga a wurin,</p><p> Yace, Abba ina takardan Abba yadauko takardan ya nuna mai yace gashi nan, daga nesa inda yake zaune,</p><p> Yace bani son kaga abinda aka rubuta don sheri ba kyau,</p><p> Saboda ni nasan cewa ko yaushe ne ma waya kana fada min lafiya lau kuke da matar ka,</p><p> Tashi yayi har inda Abba yake yace rubutun zan gani kawai bawai zan karanta bane,</p><p> Dan dagowa da takardan yai mai kadan,</p><p> Da sauri ya waiga gefen da Salim da Amal ke zaune yace cikin ku wake da wanan handwriting din,</p><p> Salim yadan waiga gefen da Amal take zaune yana dan kallonta cikin mamaki,</p><p> Yace mata ko ke ce tadan girgiza kanta cikin alamar, rashin gaskiya, tace ,a,a</p><p> Kawai dai sheri ne ni nasan ba gaskiya bane,</p><p> Tausayi naba Salim ganin irin kukan da nakeyi ga kuma Abba nata min fada ina kuka cikin gumza,,</p><p> Amal ce ta rubuta ni nace ta rubuta mu aika wa hjy tsohuwa da shi ko zata zo ta ceci yayan mu daga bala,in da nafisa ke son jefashi cikin wanan kasar,</p><p> Kowa waigawa yayi inda salim din ke magana,</p><p> Har zaici gaba sai kawai yaji saukar mari a kumatun shi, sheriff ne yai mai wanan marin masu kyau,</p><p> Sheriff yace shine tundazu ana magana kai shiru ka share mutane ,kasa anata cin zarafi yar mutane,</p><p> Abba ya daga hannu shi ma sheriff yace kyale shi,</p><p> Ai nasan cewa zasu iya tunda uban su ne yakawo wanan takardan,</p><p> Inda yayi halin dattako aida bai bari takardan yakai hannu hajiya ba,</p><p> Ita kuma hjy tsohuwa ta cabe zan cen da fadin Shehi baida laifi don ko bayan nasa an karanta min takardan </p><p> Saida na kirashi don inji daga bakin shi sai naga ai baima san komai gamay da sakon ba,</p><p> </p><p> Duk bayanin da sukeyi baisa nadan tsagaita kukan da nakeyi ba,</p><p> Sheriff yai min magana da larabci wai inyi hakkuri inyi shiru,</p><p> Mai hakkuri bai iya fushi ba dama, ummi ce tafito falon cikin kamala,</p><p> Don ko ina na jin ta arufe yake lif baka iya ganin komai nata saboda wani zunbudede hijjab da tasa,</p><p> Fuskan ta na saye da wani farin medical glass da man mai</p><p> Idan zatayi karatu nake ganin tana sa shi,</p><p> Guda guda take take takawa a tsakiyan falon,</p><p> Guri ta samu gefe guda ta zauna a hankali,</p><p> Shiru tadan yi yayin da duk falon kowa yai shiru, saboda mamakin fitowar ta,</p><p> A hankali ta dago kanta tace, yaya lawal nadauka ko da kowa zai ce Shehi bai kyauta ba don naji kana cewa ubansu ne yakai sakon tundaga nan har nigeria </p><p><br /></p><p>Ke nan da sanin shi yakai sakon takardan da yara suka aika ma Umma dashi ki,</p><p> Ta dan girgiza kai tace Allahu akbar, tace</p><p> Ina zaton kai mai kareshi ne don kusan kafi kowa sanin kowaye shehi din,</p><p> Kamar yadada shi wanan din ta nuna sheriff da kai ,</p><p> Ke kokarin rufe zancen don gudun bacin ranka ina haka shima shehin ke yi, don gudun barna goma, tsakanin kaida aminin ka,</p><p> Inda yai niyar fadin abin da zaman nasu ke ciki da ya fada ma tun yana nan kasan,</p><p> Saboda kasan halin da ka jefa dan ka aciki, </p><p> In badon Allah ya taimake shi ya hada shi da zama da mutanen kirki ba da yanzu labari yacin maka,</p><p> Ido ware bashi kowama don ba mai tsanmanin ummi zata iya wanan maganar mai tsawo haka kuma akan Ahmad,</p><p> Matar da tana iya yini batai maganar dayafi goma ba,</p><p> Nunani tayi da baki tace inta wanan yar marainiyar Allah bata can, canci haka ba daga gare ku gaskiya,</p><p> Kudiba fa duk guda nawa take da har za,ace komai itace mai gudanar wa nagidan nan</p><p> Aida ganin haka kunsan cewa baiwace kawai daga Allah,</p><p> Tamike tsaye tana cewa naso ace ajiya ka iso wanan garin kila da ka koma yau din</p><p> Inda nake tsugune nasha kuka tazo, tadan dagani,</p><p> Tanafadin Kada Alhakin wanan yarinyar ya kama ku wlh,</p><p> Ka binciki taka diyar mugun halinta kafin ka tuhumi diyar mutane,</p><p> Tajani zuwa dakinta ina kuka, wi, wi </p><p> Yaune rana na biyu danayi danasanin zama gidan sheriff din mu</p><p> Ido yabi mu dashi yana mai tausaya wa yarinyar sosai,</p><p> Salim ne ya walwale masu komai gamayda irin zaman da akeyi da nafisat tunzo wansu,</p><p> Irin abinda suka gani dakuma recoding din da wani yayi awaya sukaji har zuwa irin abinda yafaru jiya agidan,</p><p> Shiru falon yayi don saurare Salim da kuma jimamen halin nafisat da basuyi tsanmani ba, daga duk wani da ,da yafito gidan mahaifin nata,</p><p> Alhj zanna yace azuciyar shi lalai yanzu ba wani fa,ida ga mutum ya kai yaro shi karatu nisa da gida, </p><p> Musam man kasar turai inda yara ke koyo mugum tar biya</p><p> Mai makon yaro ya koyo karatu sai kum yaro ya koma kiyon bakar dabi,a,,,</p><p> Niko muna shiga daki da ummi tadauko min lemon gwangwani mai sanyi tabani kai na girgiza alamar ban sha,</p><p> Maimakon insha din sai kukan dana kara sautin shi sosai,</p><p> Ido ummi tasa min kawai don tasan abinda akai min akwai cin zuciya sosai,</p><p> Afalo kuma hjy tsohuwa ce ta sa masu fitinar lalai sai nafisat tabar gidan nan</p><p> Inba haka ba ita zata wuce da shi don kada nafisa ta jawo masu kashe mutm akashe mata shi abanza,</p><p> Salim yace aida za ta iya da baki zo kin samay shi. </p><p> Don ko abinda akayi jiya ya i,she shi shiga wani hali,</p><p> Tana jin haka ta mike takama jan hannun Ahmad wai subar falon </p><p> Dariya kowa yasa afalon don sun san cewa a rude take,</p><p> Alhj zanna ne yaiwa Ahmad alamar yabita kawai don shi zafi sauki,,</p><p> Dama yana bidan hanyar fita ne daga falon tun lokacin da ummi ta wuce da fadima hankalinshi ya ke tashi kamar ya,bisu duk kansu biyun </p><p> Saboda bai taba ganin ummi cikin bacin rai ba irin haka</p><p> Ga kuma yar mutane akan gaskiyan ,ta an musguna mata rayuwar ta ga banxa yau </p><p> Yana zuwa dakin ya iske ni jikin ummi nasa kaina saman ciyan ta ina ta rusa kuka mai tsuma zuciya,</p><p> Tsayawa yayi daga kofan dakin yana jin sautin kukan kamar digon garwashi ake watsa mai ajikin shi,,</p><p> Idon shi a lunshe suke ya nadan kada kafan shi gudu, a,hankali a hankali</p><p> Hajiya tsohuwa ce tafado dakin tana cewa nidama nasan cewa haka zai kasan ce don duk zurian su Amina babu na albarka ciki</p><p> Ganin da tayi ina kuka yasa ta tsaida fadan nata, ta samu guri tazauna tace min inyi hakkuri ai gaskiya tayi halinta, ko</p><p> </p><p> Hakana na wuni a,ranan ba wani walwala tare da ni dakin su ummi nakoma can kuryan gado na dunkule wuri guda tunane kala kala nayi shi aranan,</p><p> A gaskiya inda nasan yadda zanyi in koma gida wurin inna na danayi nakoma wurinta don in huta da gorin duniya kala,kala da nake sha </p><p> Saboda dai nisan cewa ina iya kokari naga cewa komai nawan nan gidan yana tafiya daidai</p><p> Amma sai gashi yau wai ni ake zargi da kokarin wargaza zaman lafiya atsakanin ,masu gidan, </p><p> Hawaye ne yakama dan silaluwa daga idona yana gangarowa a,fuska,</p><p> Tissue aka miko min ki bandaga kaiba nasan cewa sheriff ne, batare da ya ko kalin ind nake ba yake magana,.</p><p> Kiyi hakkuri ni nafi kowa sanin an maki abinda bai dace ba ayau, </p><p> Saboda anzarge ki akan abinda baki aikata, ba,</p><p> Saida kisani cewa shi mai gaskiya yana tare da Allah koyaushe,</p><p> Saboda haka ina son kitashi kije kiyi aikin ki kamar yadda kika saba kamar kullun,</p><p> Idonshi dana kalla naga ai ba wasa kokadan aciki yasani shirin mikewa zuwa waje,</p><p> Ummi ce ta fito daga bayi da alwalar ta ganin da taimai gani nikuma ina shirin tashi,</p><p> Yasa take kallonshi cikin mamaki, da tuhuma,</p><p> Kafin tayi magana shi yarigata,Ce mata yayi aiki yake son nai mai </p><p> Tace mai ya ina sauran ma,aikatan gidan suke da ba,zaa iya sa wani aikin ba sai ni,</p><p> Zaiyi magana tadan daga mai hannu alamar ba wasa acikin maganar ta,</p><p> Fita yayi yabarni dole, adakin ummi din ,</p><p><br /></p><p> Nafisace tare da wan mahafinta da Alhj zanna da sukazo daga Nigeria,</p><p> Yace agaskiya nafisa kin ba mu mamaki wai ace acikin zuriar Alh har akasamu mace mai wanan dabi,ar</p><p> Inbadon Allah ya taimaka ya hada ki da yaro mai kirki dan arziki wanda yasan ya kamata,</p><p> Aida agida nigeria ki kai wanan abin dayanzu mutunci da martaban gidan ku ya zube ko, ga idon jama,</p><p> Yanzu kinga babu yadda za,ayi dole mu koma dake gurin iyayen ki kamar yada hjy tsohuwa ta bukata,</p><p> Kinga idan kwai sauran zama a tsakanin ku sai ki dawo,</p><p> Wani irin kuka nafisat tasa tana cewa ai mata hakkuri bazata kara yin </p><p> Ko wani irin abuba maka mancin irin wanda tayi tace rudin shedan ne,</p><p> Saidai kiyi hakuri ki rungumi kaddara don kinji ma kun nuwar ki abinda tsohuwa tafadi</p><p><br /></p><p> Mu muna shirin wuce wa madina wurin karatu duk wani shiri munyi, tare da taimakon sherff din mu</p><p> Inda yai muna sayaya tafiya madina,, karatu sosai </p><p> Tundaga kayan sawa har abin da ake so muzo dashi daga makarantar duk yai muna tanadi,</p><p> Ba abin da ya rage,</p><p> Kuma yai muna albishir din cewa da maman su umar zamu tafi itace xata dinga yi muna aikin a binci da gyaran gida </p><p> Su kuma mutanen Nigeria suya ta kokarin shirya nasu kayan don komawa gida, da mugun labari,</p><p> Babu yadda nafisat batayi ba don Sheriff yabari ta fita amma fafir yaki yarda,</p><p> Ganin da tayi bazai bari ba yasata cewa nice zan raketa </p><p> Bada son raina ba dole nashirya muka fita tare da ita,</p><p> Wani lungu mai yawan takari, kuma gasunan birjit kamar a kasar Nigeria ko wani kasa</p><p> Gidan su yar lici ne ashe mukazo </p><p> A,mota tabar ni tace min in,zauna injira tawai,</p><p> Wanigida nan kusa dasu yar lici suka do nan suka nufa, </p><p> Wani dan yakwamamen saurayi yafito </p><p> Daga nesa ina iya hangen duk abinda sukeyi </p><p> Ko ban rantse ba ina iya ganin wani abu ya basu cikin laida fara haka irin laidar company </p><p> Cikin dibara takada abin a jakar ta, tadan gyara kamar ba abinda faru. </p><p> Saida nabari mun dawo gida tadan fita sai naje nakwashe duk maganin </p><p> Aiko tunda ta diba taga bakomai inda ta boye sai,duk ta rude </p><p> Bakunya tana fadin wai an mata sata </p><p> Amma takasa fadin abinda aka sace matan,</p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 5⃣7⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUM GROUP🐎</p><p>🎁NASIBI WRITERS ASSOCIATION🎁</p><p>🎁N🎁W🎁A</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,</p><p><br /></p><p> Labarin da naji natafiyan nafisat yatayar min da hankali sosai agigice natafi side dinta,</p><p> Da sallama na ,nashiga dakin nata,</p><p> Kwance take saman gado ta dunkule waje guda da ka ganta kasan cewa tana cikin damuwa sosai,</p><p> Kallo daya nai mata sai naji wani irin tausayin ta yakamani,</p><p> Jin datayi alamar anshigo dakin nata shiyasa ta dan gyara kwanciyar ta kadan, tadawo da kallon ta sai tin kofar shigowa dakin,</p><p> A hankali nadan karasa har bakin gadon nata,</p><p> Kusan wani dan lokaci ba wanda yace kala tsakanin nida ita,</p><p> Gefen gadon inda kafarta yake, nai saurin isa gurin,</p><p> Maimakon inyi magana sai kawai nadan fara kuka mai tsima rai,</p><p> Shiru tayi nadan wani lokaci tana jina,</p><p> Saida ta daure sanan ta iya ce mim kin ji cewa zanbar gari ko,</p><p> Nadan gyada kaina alamar eh,</p><p> Tace min hakika fadima ke yarinya ce karama wacce tasan ya kamata a rayuwa,</p><p> Ta dan dago daga kwacen idon ta sun gada sun yi ja jajir, dagani tayi kuka sosai,</p><p> Sai jiya nagane cewa kina kauna na fadima, nakuma gane cewa duk abinda kikeyi ba don kowa kikeyi ba sai don Allah,</p><p> Nayi nadama da danasanin kuntata makin da naitayi, abaya wanda dana sani in rugumay ki,takar yar uwata saboda irin yadda kika rikeni,</p><p> Tsayin wani dan lokaci babj wanda ya,iya cewa kala acikin mu,</p><p> Ahankali na dan iya bude bakina nace don Allah idan har na saba maki kiyafe min don Allah</p><p> Tashi tayi ta zauna da kyau tace da sauri haba fadima duk iya zaman da nayi daku nice mai yawan saba maki,</p><p> Saboda rudin shedan da mugan kawaye, </p><p> Duk kokarin da zakiyi kifitar dani kunya kin yishi fadima don gudun kar zamana da mijina ya baci kinyi iya kokarin ki wajen gyara min zama,</p><p> Don ko jiya ina sane da cewa kece kika dauke abin da yar lici ta bani </p><p> Wanda in badon kin dauke a,yadda nake ji ajiyan wlh da nasha mai isata saidai su Abba su ganewa idon su irin abinda nake yi,</p><p> Kinga duk da Ahmad yasan abinda nakeyi da kuma irin plan din da muke shiryawa akanshi baisa ya canza min ba ko ya nuna min cewa, yagane komai,</p><p> Duk sai jiya wurin bayanin da salim yayi yass nagane cewa kece kika taimaka ma rayuwa na sosai,</p><p> Wanda in badon ke ba da ban san ya zata kasan ce dani ba awanan kasar,</p><p> Masu daukan doka a hannu ba sai ta baci ba </p><p> Tausayin tane yakara kamani so sai bansan lokacin da na rike taba ina kuka, ajikinta,</p><p> Ina fadin kada kitafi don Allah kiyi hakkuri ki zauna tare da mu,</p><p> Itama din kuka takeyi na nadama sosai da danasani</p><p> Mundan kai wani lokaci a hakan ba mai ba wani hakuri a dakin sai itace ma tai karfin halin cewa don Allah intaya ta rokon Allah akan irin rayuwar da take ciki,</p><p> Sai a lokacin nakula da cewa nafisa bata jin dadin jikinta har yanzu karfin haline kawai takeyi,</p><p> Abinda tayi yanzu yayi matukar bani mamaki saboda sai nake gani kamar a mafarki nake ba wai nafisan da nasani bace har take cewa in yafe mata ,,</p><p> Kai duniya abin tsoro ne gaskiya,</p><p> Idan bakabi duniya a sannu ba saidai tagama dakai karaf daya badai kai ka gama da ita, ba,,,,</p><p> Muna a haka ban mu fargaba sai jin muryan sheriff mukayi ya bakin kofa, a,storace muka waiga duk kan mu,,</p><p> Inda yake tsaye, fuska a daure, Gabana saida yafadi don tsoro,</p><p> Takowa yayi zuwa cikin dakin yanawa nafisa wani irin kallon kyama, Nima dai kallon nashi nakeyi da kumburarun idan nu na da su ka sha kuka acikin kwana kin nan,, </p><p> Tabayana yayi yana fadin may kukeyi anan dakin , wurin wanan mara,imani,</p><p> Kafin in bashi ansar tambayar da yai min sai nima na wurga mai tawa tambayan</p><p> Nace mai Sheriff din mu don,Allah kazama mai yafiya da uzuri ga duk wanda Allah ya hada ka zama dashi,</p><p> Kayi hakkuri kayafe mata kada ka bari ta wuce a,haka cikin wanan yanayin da take ciki</p><p> Dan dariyar yake yayi tukun ya juwa zuwa kofan dakin da ya shigo yana cewa </p><p> Da kin fara bani ansar dana tambaye ki kafin ki ce zaki min halin yan adam,</p><p> Bayan shi nabi da sauri don naga cewa yana shirin barin dakin,</p><p> Amma sai bancin masa ba don ya bi hanyar fita wajen gidan ne,</p><p> Daki na koma don in yi nazarin abin yi don gaskiya ban son tafiyar nafisat sam wlh,</p><p> Ina shiga dakin Amal ce kwance a saman gado na , tadauki wayana tana dakila,</p><p> Tana ganin na shigo dakin tajamin wani irin uban tsaki,</p><p> Tadan kalleni ta tabe bakinta idonta na saman wayan dake hannu ta, ta min ,</p><p> Wai ke fadima wata irin yarinya ce wai da bata da zuciya haka,</p><p> Wanan matar da har kike wani shishigin zata tafi, kinsan komai akanta,</p><p> Sanan saboda tsabar kiyayyan da take maki har iki,rari tayi da cewa sai ta halakaki, agaban kowa,</p><p> Kuma taso taiwa yayan mu sheri da kazafi duk akanki,,</p><p> Wai shine rashin zuciya kalar taki har kina kokarin tayar ma kanki da hankali,</p><p> Akan hukuncin da magabata suka yanke, ke ina ruwan ki da maganar manya da har zaki sa kanki aciki,</p><p> Jin da nayi tace maganar manya sai jikina yai sanyi lankwas saboda nassn cewa gaskiya Amal ta fada min bawai ba,</p><p> Kan gadon nakaraso na zauna jiki ba kwari ajikin gadon nadan jingina, gami da yin tagumi da hannu na guda,</p><p> Ido tazuba min da alamar mamaki take kallo na</p><p> Cikin tausayawa nake magana, nace haba dai Amal da ba,a yafe ma mutum aida Allah ya shudemu ko kamar mutanen farko,</p><p> Saboda irin aiyukan zunubi da sabon Allah da dan Adam ke aikatawa akulun,</p><p> Zancen Amal takawar tana fadin ke fadima waiko ma kin shirya kayan tafiyar ki kuwa,</p><p> Sai a lokacin nadan yi murmushin karfin hali nace har may zan shirya Amal</p><p> Hararana tayi tace min ina kayan da yayanmu yasaya muna badasu zaki ba </p><p> Sanan kinsan cewa dasu Aisha da Umar zamu tunda da maman su za,a tafi,</p><p> Sai alokacin nadanji wani dan shakat azuciya na jin ance aida su Umar zamu tafi </p><p> </p><p> Washegari muna kofan gida duk kanmu gaba dayan mu su nafisa da Abba da wani dan uwar su nafisa wanda ya wakilci,, mahaifinta sai hajiya tsohuwa ,</p><p> Nafisa tafito cikin shigar kayan indiya wando da riga sai gyalen da ta dan rufe kanta da shi ,</p><p> Kallo daya zakai mata tabaka tausayi saboda koba komai taga samu taga rashi,</p><p> Saboda samun miji gare ta irin sheriff din mu ba wasane ba gareta, saidai dayake, ,, ba,adai fidda tsanmani kawai,</p><p> Ni, a haukana ganin nakeyi, Duk wanda ke wurin ya,na tausayin nafisat,ne,,</p><p> Ashe ni ban sani ba kowa dake wurin, murna yakeyi da tafiyan ta don duk ta ishe su agidan basu da yadda za,suyi ne kawai</p><p> Kuma shi sheriff ba mai daukar magana bane da yakori kusan kowa na gidan,</p><p> Ina hada ido da ita sai naji wasu yan kwalla nabakin ciki na batun sulalo min,</p><p> Amal ta kula da hakan sai ta dafa min kafada tace min hjy tsohuwa na magana dani,</p><p> Muna kallo suka wuce agaban mu ba mu da yadda zamu yi da ita,</p><p><br /></p><p> Mumadai gadan gadan shirin tafiya mukeyi zuwa madina inda zamu fara wani sabon rayuwa,</p><p> Gaskiya sheriffudeen Ahmad yai muna na mijin kokari sosai </p><p> Don ni azatona wanan gidan nashi da nasani,na ma,aikatar su dake madina zamu zauna</p><p> Ashe abin ba hakana ba hakana yake ba,, </p><p> Don gata ne na sosai akai muna wani dankareren gida mai kyau aka sai muna a tsakiyar gari anan zamu zauna ,</p><p> Gidan baida nisa sosai da makarantar mu, da kuma masallacin haram,</p><p> Zamu iya yin karatun mu ,zamu ,kuma samu yin ibadar mu a sau,kake ,</p><p> A gaban ummi muke ana gobe zamu bar garin tana muna fada kamar yadda duk wata uwa ta kware zata iya yiwa danta fada,</p><p> Tai muna nasiha sosai da ja muna hankalin kanmu guji don abin duniya wanda hakan shi yafi yawa ga alumma yanzu , </p><p> daga karshe tai muna nasiha akan kuka da ibadar mu fiye da komai na duniya,</p><p> Sai fatan alheri da taimu dakuma muriki junan mu cikin amana da fahintar juna,,,</p><p> Shiru mukayi dakin saboda nasihar nata duk ya kashe muna jikin mu, sosai wlh,</p><p> </p><p> A hankali yake saukowa daga matakal jirgin idon shi mane da wani dan farin tabarau wanda yadan kara ma fuskan shi kyau </p><p> Fari dogo kyakywa dashi matashi ne maiji da lokaci da ganin shi,</p><p> Shigar shi kawai ta isa taba mutun ansan hakan. </p><p> Kallon garin yake yi a tsanake yana anyana cewa lalai tsarin garin tayi mai daidai,</p><p> Hotel din filin jirgin yadan kama don yadan huta gaji kafin ya kira dan uwan nashi dayai ma tafiyar bazata,</p><p> Saida yadan huta sanan ya kira da uwan nashi don ya sanar mai cewa yana kasar tasu pa</p><p><br /></p><p> Saidai fa ni gaskiya jama,a tun lokacin da nasamu admition dina har zuwa yau ban yi wa sherrif din mu godiya ba </p><p> Don haka yau na kudiri aniyar sai nayi mai godiya kafin mu wuce gobe, insha Allah,</p><p> Falo shi yake zaune bayan yagama cin abinci , duk da ba wani abincin, mai yawa yake ci ba so, sai,</p><p> Hankalishi yana ga kalon wasan polo, da akeyi a,tv falon, shi din</p><p> Da sallama na na,isa gurin da yake zaune na gaishe shi cikin ladabi da biyayya,,,</p><p> Dan juyowa yayi cike da mamakin gani na a wanan lokacin ,</p><p> sai kuma ya kauda kai shi zuwa ga kallon tv da yake yi,, </p><p> Sai dai ina ganin shi,,gaskiya naga ya ramay min sosai ya kuma yi dan baki,</p><p> Kai,na na kasa nace nadan gaishe shi,,ahankali batare da naji ko ya ansa min ba</p><p> Nace mai nazo ne in mai godiya bisa ga irin kokarin da yai muna nida yan uwana,</p><p> Har zanci gaba da magana dana fara </p><p> sai wayanshi tai yar tsuwa,</p><p> Hannu ya mika tare, da Dauka wayar yana dan yi yana waigen tv ,</p><p> sallama yai ma wanda yakirashi cikin murmushi,</p><p> Bayan sun gaisa da maishi naji yace what a surprise, kake shirin yimin Suraj,</p><p> Waida gaske kakeyi kana cikin saudiya, shine koka fada min cewa zaka shigo insan irin taron da zan ma,ka,</p><p> Ai yana fadin haka sai ya mike bai kara bin ta kaina na ba naji yana kiran mustapha tawaya suzo suje, wurin dauko suraj da yashigo gari,</p><p> Bayan sheriff din na,mu nabi da kallo daga inda nake tsugune, ina mai mamakin kowaye wanan da yabugo wanan wayan,, </p><p> Komadai waye yanada muhinmanci sosai ga sheriff din mu,</p><p> Tunda daga bugo wayan bakon ya mike tsaye cikin murna da farin cikin zuwa taron shi, </p><p> A tsaye suka samay shi daidai inda yai masu kwatancen cewa yake,</p><p> Tundaga motar da yaga anzo taron shi da ita ya ce a ranshi kalai maganar mama yana da kamshin gaskiya,</p><p> Cikin farin ciki da so da kauna suka runguma junar </p><p> Wani irin dadi Ahmad din ke ji azuviyar shi ganin yau dsn uwsn shi yakawo mai ziyar a inda yake</p><p> Ai Suraj bai rude ba sai da yaga irin gidan da suka tunkara wanda ake nufin cewa , wai Ahmad ne, ya mallaka, shi,</p><p> Wani irin dan huci yayi mai fidda iskan zafi abaki saida kusan kowa na motar yaji shi,</p><p> Sai yadan basar da cewa duk gajiya ce saboda yafito nisa,</p><p> Sai cikin dare suka karaso gidan don haka ni koda suka isa har na kwanta barci, abina,</p><p> Saboda ina tashi da wuri yin aiki safe, shiyasa na saba da kwanci da wuri,</p><p> Wani bangare guda na gidan aka ware mai inda akaimai masauki ke nan,</p><p> Maman su umar ce ta gabatar masu da abinci</p><p> Kasancewar tana da kula da aikinta ga tsabta ga iya girki kamar na wani gidan saida abinci,</p><p> </p><p> Na shirya komai nawa har na Aisha sai dan abin da ba, arasa ba kawai nabari adakin namu,</p><p> Da safe ma saida na hada ma sheriff komai yadda nasaba sanan na wuce don inyi wanka in shirya,</p><p> Dogom riga na sa yau pink kalar ta amshe ni sosai, ajikina,</p><p> Ina kokarim daura dan kwalina naji intercoms din dakina yai kara alamar kira daga falo,</p><p> Cikin sauri nafito dan in ansa kiran oga na sheriffudeen Ahmad,</p><p> Zaune suke su biyo a dining table din suna kokarin fara bude abincin</p><p> Saida nagan su su biyu sanan natuna cewa ai yana da bako </p><p> Gashi kuma abincin shi, shi kadai na aje agurin table din,</p><p> Cikin ladabi na iso tare da sallama na,</p><p> Sheriff din wanda kanshi ke din ban kasa yadago daniyar yimin bayanin in karo masu plates da spoon,</p><p> Sai idon shi ya caraf ga irin kwaliyar da nayi yau din,</p><p> Cikin mamaki da kuma shauki yake min maganar cikin harshen larabci,</p><p> Yace min bansan yai bako bane nakawo mai abinci kamar shi kadai,</p><p> Nace ma la, agaskiya ban sani ba saidai ina mai neman afuwan gare,. </p><p> Saida ya dan lunshe idon shi kadan yace min ba matsala ina iya zuwa in karo masu ,</p><p> Shi ko bakon jin muryan dayayi kamar s,na busa sarewa yasa shi dan waigowa,</p><p> Sai yaga wata yar sabuwa mata shiyar budurwa ce ke tsaye a bayan shi tana wanan zazakar muryan,</p><p> Ganin da yayi suraj yadan bini da kallo yasa shi ce min inbar shi kawai zasu yi manage da wanan na gaban su,</p><p> Ban karasa fita ba itama Amal tashi dining erea, din cikin shiga ta kamala,</p><p> Azuciyar suraj yace kai Ahmad din ya hada kyawawan yan mata haka may su keyi agidan ne wai,</p><p> Jindayayi Amal na magana cikin harshen kanuri yasa shi budar baki da mamaki yana kallonta, sai ya hango dan kama da tayi da mahaifiyar Ahmad yagana,</p><p> To ita kuma waccan ta farkon fa ,hakan yai daidai da kara waigawa dayayi yana kallon hayar kofan da nab </p><p> Sheriff ya kula da shi sarai shiyasa ya canza shawara koda zu,</p><p> Saima ya tuna cewa ai yau zasu wuce madina abinsu,</p><p> Don haka sai yai bar wanan zancan zucin da yake, </p><p> Suka hauhirar yaushe rabo </p><p> Suna gamawa sukaje gurin ummi don ya gashe ta </p><p> Ummi tayi farin cikin zuwa ziyarar dan uwan shi dayayu, tundaga kasar turai har nan </p><p> Bai ai,wani dadewa ba salim ,yasa kowan mu fitowa da kayan shi don Aloda a motar da zamuyi tafiyar da ita,</p><p> Wata yar far mota ce ake ta loader kayan mu a cikin, wace da alama da ita zamuyi tafiyar,</p><p> Kowan mu yafito cikin, shiri shi, gun ,hajiyar mu na nufa don mu bankwana da ita,</p><p> Allah yagani banso wucewa inbarta ba saiga shi itace ma ta kara min kwarin gwiwa akan in tafi in yo karatuna watara zai amfane ni ne,</p><p> </p><p> Ganin da suraj yayi munfito ana muna rakiya yasa shi tambayar ko ina zamu haka na</p><p> Atakaice yabashi ansa da fadin madina,</p><p> Yakara tambayar shi may yasa bazami bi jirgi ba </p><p> Yace mai ai jirgi bai shigowa garin makka, sai dai sauran garuruwan dake gefen makka,</p><p> Wata tambayar yakara watso mai saboda may jirgi bai zuwa,</p><p> Dan murmushi sheriff yai mai yabashi ansa atakaice da cewa Ka,abah,,,</p><p> Ganin da sheriff yayi muna kokarin shiga motar yasa shi saurin karaso wa wurin mu duk da Almustapha ya yi a ranging din mu yadda yakamta, amma saida yasa aka maida umar wurin salim dake gabar motar tare da yusuf driver,,,,</p><p> Daidai motar zata tashi kowa na daga muna hannu mukayi ido biyu da ni da sheriff wanda naga bakin shi na motsi yana fadar wata kalma da ban gane ba,,,</p><p> Da sauri na kauda idona cikin nashi wanda hakan yadan sashi wata makalalan dariya,,,,,,</p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 5⃣8⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p>🎁NASIBI WRITERS ASSOCIATION🎁</p><p>🎁N🎁W🎁A</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,,,</p><p><br /></p><p> Haka motar mu ta harba saman titin hanyar garin madina,</p><p> Tafiyane mai tsawo a gaban mu, saboda ba wani gari maidan girma da mutum zai gani ko ya ce zai dan yada zango,</p><p> Gidan larabawan kauye ne jefi jefi a cikin dajin,</p><p> Danjin wanda babu yalwan manyan itatuwa sai dai tsaunika madai daita da zakai ta gani,</p><p> Mun dan yi nisa sosai dagarin makkah duk zukatan mu badadi sam</p><p> Ina tunanen hajiyar mu ne koda yake nasan cewa Yumma zata kula da ita sosai </p><p> Muryam salim naji yana cewa wai shi wanan ta ina yafito yazo muna nan ne,</p><p> Amal da tadan kai kwance daga bayan motar, ta dan jingina jikin ta a sit din motar</p><p> Tace yazo gurin dan uwan shi ne mana, tunda kasan dole suyi zumunci tsakanin su,</p><p> Salim yace nikan duk ban yarda da yaran mama wlh don suna iya yin komai ga yayan mu,</p><p> Ina jinsu sai alokacin nadan yi magana nace ma su au</p><p> Wanadin dan uwan Sheriff ne, aiko naga kamar suna da dan kama da junan su,</p><p> Saidai sheriff yadan fishi tsayi da fari ko,</p><p> Salim ya ce kai basu da wani kama a ko kadan, ai shi Yayan mu duk kawu ya kwaso,</p><p> Suko sun biyo mahaifiyar su ce inaga tundai yanayin jikin su yanada kama,</p><p> Haka sukayi ta zancen su muba jin su har suka gaji sukayi shiru, don kan su,,,</p><p> Bayan isan mu ne mukasan cewa an canza muna gida,</p><p> Ida muke zaton zamu zauna ashe ba a nan bane,</p><p> Munyi farin ciki sosai na ganin irin gidan da aka kama muna,</p><p> Afalo muka zube gaba dayan mu, </p><p> Salim ne yace bari ya, tashi yadan zagaya gidan, don yaga dakin da zai dauka,</p><p> Kafin yatashi ne Yusuf driver ke mai bayanin akan dakunan,</p><p> Yace sheriff yai mai bayanin inda dakin kowan nen mu yake,</p><p> Dani da Amal dakin mu kusa da na juna ne, sai maman su umar dake can ta bayan mu kadan kusa da kitchen,</p><p> Salim da Yusuf driver mu nasu bangaren daban mai kama da namu side din </p><p> Suna ta farkon shigowa cikin gidan ne su,</p><p> Komaimirrow agidan ba wanin abinda zamu ce mun bukata na zamani,</p><p> Maman Umar bata da sanyin jiki muna zuwa bata bi ta gajiyan da muke dashi ba </p><p> Kitchen ta fada ta dafa muna abinci mai saukin sarafawa,</p><p> Daga nan kowan mu ya fada dakin shi don gyara inda zamu zauna, </p><p> Dakin bai bukatar wani gyara komai neat ne, akwai gado da mirrow sai wardrobe , sai tv da dan karamin fridge, dake dauke da kayan sanyi,</p><p> </p><p> Washe gari tunda safe muka shirya saboda yaune, zamu fara shiga lectures,</p><p> Makarantar babba ce ita jami a mafi girma agarin madina,</p><p> Bamu samu wani matsalaba wurin gudanar da komai,</p><p> </p><p> Ahakana mika dinga karatun ba kama hannun yaro,</p><p> Muna samun kula sosai ga sauran yan uwan mu dalibai don ganin da suke muna cikin shigar mutunci koyaushe,</p><p> Sannu sannu na fara fice a department din mu kowa yasan da ni,, koya malami yakoyar dani insha Allah zan hadace shi akaina,</p><p> Wanan kokarin yasa nadan fara fice sosai ga kawaye na,</p><p> Mun hadu da yan Nigeria can da dama , suma sunzo karatune kawai,</p><p> Akwai wata Salimat yar kano damukr yawan hadewa wurin karatun mu da ita,</p><p> Saidai ayadda na fahinta ita matar aure ce, don ba yarinya bace,</p><p> Dafarko salimat bata kulani amma ganin da tayi inada kwazo sosai yasa ta dan sake jiki dani,</p><p> Hakan yasamo asaline watarana da akai muna test bata zo ba sai na kokarta nai mata,</p><p> Kafin in mata saida nasha wuya aranan don da kyat nasamu information nata,</p><p> Bata shigo school ba sai bayan kwana biyu ,Ashe bata da lafiya newai kuma tarasa wanda zata aiko,</p><p> Abin mamaki saida akazo rabon test din sai taga ai har da ita kuma abu guda muka samu,</p><p> Ina can gefe ban ko kali gefen da take ba na,</p><p> Ina karatuna sai ganin ta nayi gaba ta dafa fan table din dake gabana tana mai yi min sallama, </p><p> Ahankali nadago kai na kalle ta ina mai ansa mata sallamata </p><p> Sai take ce min tazo ne taimin godiya don tasan cewa duk wanda ke wanan ajin na computer science ba wanda zai iya taimaka mata bayan ni,</p><p> Naso in boye mata cewa bani bace nai mata amma ina sai tace min,</p><p> Ba yauba ina lura dake kina da hakkuri da sanin yakamata,</p><p> Nimatar aure ce mijina ya hanani hulda dakowa don gudun gurbatar tarbiya,</p><p> Shiyasa kikaga ban kula kowa acinkin wanan department din na mu </p><p> Don gudun saba ma Kama train da tadauka kafin tazo, amma inyi hakkuri zatayi wa mijin ta bayani komai gamay dani</p><p> Tundaga wanan lokacin muka yi sabo da salimat sosai,</p><p> Inda nagane cewa ita kadai ke zaune a gidan ta, karatu yakawo ta madina ,</p><p> Mijin ta yana Nigeria da zama,,salimat tana da kishiya a Nigeria wace nake gani kamar yar kasuwa ce tana kano to Dubai,</p><p> Nafahinci hakane indan suna waya da mijin in ta tambaye shi yara da maman su sai yace ai ta tafi dubai. Koyace ai tadawo rana kaza,</p><p> </p><p> Karatun da mukeyi bai hana mu yin ibadar mu ba, don kusan kulun muna zuwa sallah a haram , saidai ba kowani lokaci ba,</p><p> Amma sallar ranan jumma,a bata wuce mu sam,</p><p> Saboda itace ranan weekend muna zama tun safe har dare acan </p><p> Ranan alhamis mukan taya maman umar gyaran gida da sauran aiki gida da ya kamata</p><p> Idan mundawo wani lokaci mukan dan zauna da maman Umar mudanyi hira kokuma in koya ma su Umar da Aisha karatu,,,</p><p> Kusan watan mu guda a madina, Sheriff din mu yazo ziyar mu, tare da ummi da hajiyan mu, </p><p> Munji dadin wanan ziyar so sai don ji mukayi kamar mun kai shekara bamu gansuba,</p><p> Koda suka iso bani gida mun fita dani da Aisha, munje wurin gyaran kai ,</p><p> Wurin baida wani nisa da gidan mu sosai don haka da kafa muka tako dazamu dawo,</p><p> Waje nasamu sheriff shida,Almustapha, yana waya a,lokacin,</p><p> Tunda na bude gida zan shigo idon shi ke akaina, nima ganin da nai masu na bazata yasani mamaki,</p><p> Cikin fara,a na isa gurin su ina masu sannu da zuwa,</p><p> Kamar yadda yake ansa min a dakile yau din ma hakane,</p><p> Cikin zuciyar shi kuma sai mamaki yakeyi, may yarinyar ga ke ci haka tawai wanan girman cikin lokaci guda,</p><p> Anyako madai tana karatun kuwa kodai jin dadinta kawai takeyi abinta sai kuma wata zuciya tace mata a,a ina bayazatayi hakana ba don yasan ni da kokari sosai,</p><p> Balle ma yasancewa ina son karatu sosai arayuwa na,</p><p> Muryan mustapha ce takatse mai tunanen shi inda mustaphan ke ce min ina mukafito haka,</p><p> Nikuma ina washe bakin murnan ganin shi,nace mai ai,nafito can wurin gyaran kaine, nida Aishan</p><p> Azuciyar shi yace badai tsafta ba kan wanan yarinyar akawai kulada kai,</p><p> Ciko na shiga inda yabi bayana da kallo da sauri ya kauda kanshi don gudun yin sabo,</p><p> Saboda wani irin mugun girma yaga nayi mai lokaci guda, saida gaban shi yafadi,</p><p>Inashiga cikin gida, kuma nai arba da ummi da hajiyar mu zaune a falon mu,</p><p> Da dan ihu na, naRugumay su ina murna,na daidai lokacin shima sheriff ya shigo cikin gidan </p><p> Saida nagama murna na san nan natuna cewa, aiba abasu komai ba na dan motsa baki,</p><p> Da sauri na shiga na hado masu kayan sanyi a ture tare da dan fruit ,</p><p> Ummi tace aidama nace diyata bata gidan ne tunda naga ko ruwan sha ba,abamu ba balle,</p><p> Ina dariya ina tsiyaya mata a cup nace mata murnan ganin ku ne ya hanna ta baku ai,</p><p> Sheriff na zaune yayi kicin,kicin da fuskan shi,na iso da cup da lemon zan zuba mai,</p><p> Agaban shi na dan tsugun na gab dashi sai kamshin, turaren na da ke hawa mai kai,</p><p> Yana min wani irin kallon mamaki a fakaice,</p><p> Bayan nadan tsiyaya mai ne nadan dago kaina a hankali nace mai ga lemu na yasha</p><p> Hannu yadaga min kawai alarmar godiya,</p><p> Natashi a hannakali cikin tafiyar da ni ban masan cewa ina yin irinta ba, nabar gurinshi </p><p> wurin mustapha nanupa don shima in tsiyaya mai,</p><p> Ban karasa kawai wurin mustaphan ba naji karan cup din da na zuba ma sheriff lemo ya fadi,</p><p> Cikin sauri na aje cup da gwangwanin lemo agaban mustapha na juyo wurin sheriff da sauri,</p><p> Lemon ya zube a kasa har yadan taba mai rigan shi kadan,</p><p> Ruwan da ke gefe na bude nadan zuba mai daidai inda lemon yataba mai riga,</p><p> Cikin rudewa na cire gyalen da na yane fusaka na dashi na fara goge mai wurin,</p><p> Kaina da akai ma gyara sai kamshi ke tashi ya dan tsira ma ido</p><p> Yana kallon yadda gashina ya kwanta lub bakikirin da shi,</p><p> Ga kamshin mangashin dana turare na ya rude wurin ,,,</p><p> Idonshi yadan rintse kadan gabanshi nata faduwa,</p><p> Don shifa gani yake wanan kamar ba fadimar yar takarin da ya sani bace,</p><p> Saboda canzawan nawa yayi yawa cikin dan lokaci guda haka,</p><p> Idonshi yadan kara lumshewa yana mai dan maida nufashi, a hankaki ta yadda ba mai iya ganewa,</p><p> Cikin kidima naje da sauri nadauko moper na goge kasan , Sai faman yi mai sannu nakeyi,.</p><p> Saida na gama gogewa san nan hankalina yadawao daidai</p><p> Ko da na daga kai in kara yi mai sannu sai naga idon shi a lunshi sainadauka ko ranshi ne ya baci ,</p><p> Cikin sanyin murya nace mai dan Allah yayi hakkuri ba san zai zube mai ajiki ba ,,</p><p> Idon shi yabude wanda naga kwayar idon shi yai ma jajir ,saida naji tsoro,.</p><p> Hannu yadaga min alamari is ok,</p><p> </p><p> Bayan fitar su sheriff ne muka zauna muna ba ummi da hjy labarin makarantar mu </p><p> Nafada mata yadda ake karatu a wurin da kuma salimat da na hadu da ita,</p><p> Wacce yanzu nake jinta tankar wata yar uwan na najikina,</p><p> Nan sukayi muna weekend saida sheriff da mustapha ba anan suka sauka ba su,</p><p> Washe gari sheriff yace min zaiyi baki,</p><p> Mudanyi mashi abincin da zasuci don wani meeting zasuyi </p><p> Shago mafi kusa natafi ta sayo duk wani abin bukarar da zamuyi amfani da shi,</p><p> Don mu a shago ake saida kayan abinci a can ba wai a kasuwa ba, </p><p> Abinci kala kusan biyar muka hada masu nida maman su Umar,</p><p> Saida muja gyara falon yayi neat sai kamshi ke tashi ko ina, da sanyin A C</p><p> A,babban dinning table muka hada masu wurin yayi kamar za ai wani dan kwara,kwaran walima,</p><p> Su hudune suka shigo dai almustapha da ke tare da sheriff ko yaushe, suka zama su biyar,</p><p> Sun gaida ummi da hjy cikin ladabi da girmamawa,</p><p> Bayan dan hiran lafiyar jikin ta da sukai mata wanda duk kusan bayanin hajiyar mu ne ma mai basu ansa, don ita ummi bata magana,</p><p> Nice shigo falon cikin wata doguwar riga ja, wacce a hannu ta kawai da kasar rigan keda ado,</p><p> Saida na gashe su tunkun sanan na juya wurin da sheriff yake nai mai bayanin abinci is ready</p><p> Wani irin kallo yai min wanda ban iya fadan dalilin hakan,</p><p> Ina cikin damuwan naji muryan wanidaga cikin bakin yana fadin masha Allah,</p><p> Ahmad kai keda kauna haka akasan nan kuma ban sani ba</p><p> Sai naji sheriff dake kokarin jawo plate agaban shi yace to aikaga yanzu ka sani ko,</p><p> Batare da jin kunyar kowa ba a wurin shi mutumin ke ce min </p><p> Sunan shi Ali Baba don Allah yana son in soshi, dama yadade ya son mata mai irin duk siffan dake gare ni bai samu ba,</p><p> Ashe ma wanan mugun yana da ita a gida yabarni kulun ina cigiyar yar matashiya, mai,,,,,,,,</p><p> Sheriff dakatar dashi da fadin Aliyu is enough don Allah kazo gaban yar yarinya kana faman zuba shirmay kamar wani karamin yaro,</p><p> Wanda aka kirada Aliyu yace to be Frank ba wasa a zance Ahmad naga sister ka kuma ina so </p><p> Idan har ba zaka taimaka min ba nida kaina zan bidi so a wurinta gakuma ummi a gari,</p><p> Bai kakarasa yasake ce mai ban fa son shirmay wanda ke karatu zaka zo ka damay ta, ka koya mata shirmay,</p><p> Aliyun yana dariya yace o shirmay ko zaka gani in shir may zan koya mata</p><p> Sai ya sauko daga kujerar da yake zaune yadan tsuguna kasa yai kasakasa da muryan shi yace ma sheriff ina wuni yaya,</p><p> Gabadaya falon suka sa mai dariya banda sheriff da ya dan tsuke fuskan shi,</p><p> Yace ma Aliyu dan iska wanan ta wuce yaudar ka ka koma can wurin yan duniya irin ka kuyi tayin duniyar cinku,</p><p> Yace Iam telling you wanan karon wlh ba wasa acikin magana na Ahmad,</p><p> Nidai ina gama zuba masu abinci na wuce ciki abina batare da nasan ya suka karasa ba,</p><p> Ina shiga dakin kiran wayan salimat ya na shigowa mani,</p><p> Nadauka tare da yi mata sheri ina cewa anty amaryan ke nan,</p><p> Tanbayana tayi bata gan mu ba masallaci wanan weekend din,</p><p> Sai ina fada mata cewa wlh su ummi ne da hjy sukazo muna weekend harda yayan mu</p><p> Fada takama min tace lalai fadima baki da kirki yanzu har su ummi su zo arasa wanda zaikirani yafada min cikin ku</p><p> Hakuri na bata nafada mata cewa suna nan ai tukun don sheriff na wani dan aiki ne,</p><p> Taimin alkawalin zata zo zuwa marance insha Allah,</p><p> Ina jin hayaniyar su sheriff har suka gama suka fita,</p><p> Inda Aliyu ke ce mai yakirani muyi sallama dan Allah ko kallon shi baiyi ba don takaici,,</p><p> Sai kuma gani nafito zanje gurin maman Umar dake aiki a baya,</p><p> Duk da sheriff yasan cikin rashin sani nafito amma saida yaji haushina sosai,</p><p> Aliyu na mai dariya yace brother in-law kaga ikon Allah ko ga ta tafito da kanta,.</p><p> Banko waige su balle insan sunayi wurin da zani nasa kai, har zan shige sai naji shi yana cewa yar uwa dan tsaya min inzo pls </p><p> Waigawa nayi kowani angul banga kowa da yake ma magana ba sai ni don haka sai na dan dakata mai, </p><p> Ya tako cikin tafiya gayu har inda nake tsayee,</p><p> Yace shi sunan shi Aliyu baba dan kasar Nigeria ne shi mutumin katsina ne aiki yazo yi a wanan kasar daga Nigeria,</p><p> Kuma baida mata amma ya gane ni yana so na kuma yai ms sheriff bayani komai,</p><p> Mamaki yakamani kamar ni yar aiki wanan dan gayun zaice yanaso </p><p> Sai nadan leka don inga ko da mai ganin mu </p><p> Aiko sheriff ne tsaye cikin wani irin mugun kallon da yake min ina nai abinda ba daidai ba.</p><p> Dayagane cewa na ga sheriff ins jin tsoro sai yace min ba matsala zaidawo ya gan ni amma may ye suna na</p><p> Cikin sauri zan wuce nace mai fadima,,,,,,</p><p>🐎ZEEE MAKAWA</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 5⃣9⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p> Cikin hikima da dabara Aliyu baba yafara koya min So,</p><p> Saboda bayan tafiyan su sherrif yakawo muna ziyara alokacin ni bani gida ina school </p><p> Noban wayata yace salim ya bashi zai kirani yaji ko banda bukatar komai,</p><p> Salim bai fada min ba lokacin da na dawo har kusan kwana biyu,</p><p> Misalin tara na dare naga komai da nakeyi nasamu guri nadan zauna indayi nazarin wani takardan da muke da test akanshi cikin sati mai zuwa,</p><p> Wayana naji yana kara, cikin mamaki nadauka don nasan cewa ba, a kirana a wsnan lokacin,</p><p> Bakon noba ne nagani mai kiran don dai dama daga Salimat ne sai Sheriff din mu ko shi ba koyaushe yake kirana ba,</p><p> Sai kusan karshen wata zai kiramu yaji ko muna da bukatar wani abu,,,,</p><p> Cikin girmamawa nayi sallaman, , adayan bangare naji an,ansa min tare da yar sautin murmushi,</p><p> Bayan haka sai dan shiru ya biyo baya,</p><p> Can naji maishi na fadin fadima baki gaidani ko,</p><p> Ya salam nace don jin sunana da mai shi yakira, balle ko ince ai wrong noba ne,</p><p> Yakara ce min hakana sai nace mai ina wuni to yace min lfy, yatambayeni ya karatu nace mai Alhamdullah,</p><p> Ya ce min kin san kodawa kike waya kuwa, nace mai a,a sai yace min</p><p> Ina waya ne da Ali baba abokin Sheriff Ahmad,</p><p> Dam gabana ya fadi don natuna cewa sheriff yai muna fada sosai akan duk wace take kula maza zai dakatar da karatun ta yai mata aure,</p><p> Tuna hakan da nayi yasa nafara bashi hakkuri kamar wace tayi wani laifi</p><p> Nace mai don Allah yayi hakuri kada ya kara kirana don in yabari akaji za,afadama sheriff,</p><p> Dariya nabashi yace min to wazaiji aishiyasa ma yakirani yanzu don yasan cewa ina daki na ni kadai,</p><p> Hakana yaita min dadin baki irin na maza, ina jin shi duk na matsu takashe wayan saboda sai ina ganin kamar za,azo akamani ina wayan,</p><p> To tundaga ranan yake kirana duk dare da sunan wai mu gaisa,</p><p> Da haka da haka yaita cusa kanshi gareni, tun ina iya boyewa har na fara rashin boyewa ko gaban waye ma zai iya kirana kima musha hiran mu,</p><p> Yanzu hankalina ya kasu gida biyu ga karatu ga soyayya, Ali baba akaina kuma duk biyun ina kokarin kulawa da su,</p><p> </p><p> Yanzu karatu mu ya fara nisa sosai don gaskiya bamu da lokaci irin da,</p><p> Gashi kuma tunda mukazo bamu taba zuwa hutu makkah ba </p><p> Ko anyi hutu a madina muke tsaya abin mu muyi hutun mu Bamu zuwa ko ina,</p><p> Salim ne yatafi makka bayan mun samu wani dan gutun hutu,</p><p> Bayan yadawo ne yake sheda muna cewa ai sheriff yai aure a dubai wata yar Nigeria ce amma acan take zama wai yar kasuwa ce,</p><p> Nayi murna so sai da jin cewa sheriff yayi wani aure, </p><p> Nace ma salim ya labarin nafisat sai yake ce min ai tana Nigeria amma ance wai basu rabuba don Abba ya hana sheriff ya bata takarda,</p><p> Kawai sainaji dadi wlh har cikin raina don ban son rabuwar su da nafisat sam,</p><p> Amal kuwa saida ta gama jin labarin da salim ke min sai, tayi dan guntun tsaki tace wanan ai auren shirmay ne</p><p> Kaji ance mata yar kasuwa aikai kasan babu wani abin kwarai aciki sai barikan ci kawai,</p><p> Duk da sheriff yake dan uwanta ne amma, Sai naji haushi kalman nata</p><p> Naga cewa ai yin auren yafi mai daraja da zama hakana ba mata,</p><p> </p><p> Yau dagani har Amal da mama su Umar agidan maman salimat mukayi ni don tayata aikin taron mijinta da zai kawo mata ziyara daga nageria</p><p> Saida mukaga komai yayi tsab mukayi mata sallama muka bar </p><p> Lokacin da muka iso namu gidan sai muka tarar da baki </p><p> Sheriff ne tare da wata mata fara sol da ita, saida bata da tsayi don ina iya cewa gajera ce,</p><p> Da murnan mu muka tare shi, wanda yaji dadin hakan har cikin ranshi,</p><p> Nice ma na kula da matar wace ke zaune gefe tana wani shan kamshi,</p><p> Nagaisheta nai mata sannu da zuwa, a yatsine ta ansa min, </p><p> Azuciya na nace taupa abin jiya yadawo ke nan,</p><p> Amal ma a gadarance tace mata sannu, </p><p> Wanda hakan ya nuna sheriff baiji dadin hakan ba shima,</p><p> Maman Umar takawo masu dan abin sha tana tambayar su komay za,a dafa masu,</p><p> Da hannu ta nuna adauke abin shan kamar wace aka aje ma kashi agabanta tace ita bazataci komai, ba sai sunje hotel,</p><p> A hankali na duka zaukwashe kayan sai sheriff yai min ahannu alamar indakata da shi,</p><p> A hankali yazuba lemon stwberry, a cup din wanda yai sanyi sosai sanan ya jawo wani dan gutun snack ya na ci,</p><p> Bansan lokacin da nai ajiyan zuciya ba wacce har takai mai akunen shi</p><p> Da sauri yadan kalloni yana mamakin ajiyar zuciyar nawa,</p><p> Wanda dama mamakin yadda yaga nakoma yakeyi , don a kulun yagani sai yaga na kara wani irin girma,</p><p> Hira sukeyi da salim inda na dan tashi a hankali na koma kan kujerar dake falon gefe guda na zauna</p><p> Saidai daga inda suke muna jin hirar komai, niko irin kallon da matar ke min ne yasani komawa gefe na zauna,</p><p> Don ina zaton ta san cewa ni yar aiki ce kuma gani ina watayawa kamar kowa,</p><p> Wayana ne yadauki tsuwa alamar kira ya shigo ,</p><p> Duk wanda ke falon saida yadan kalleni alkarayi ,,,,</p><p> Dan basarwa nayi har kiran ya katse, ido sheriff yadan zubo min ganin kiran ya katse ne yasa shi dan kauda kai</p><p> Kiran nawa aka karayi cikin rashin damuwa nadauki kiran tare da dan yin murmushi a fuska na</p><p> Bandamu da barin wurin ba don nasan babu mai jina a inda nake kuma nai tsabar keantar da muryana bamai jin abinda zan fada,</p><p> Bayan mun gaisai sanan na tambaye shi ya aiki, yace ba wani nadai gane inbani nakiraki ba watau ke baki iya kirana fadima,</p><p> A hankali nace natuba zan fara kiran,</p><p> Abin mamaki dariya naji ya kwashe dashi, sai nadan yi murmushi nima daga inda nake,</p><p> Sai yafara magana da dan saurisauri yake ce min jirgi zai shiga shine ya bugo min don muyi sallama zaije wani akine a paris,</p><p> Sau biyu muna hada ido da sherrif yayin da nake wayan, sai nadauke kaina daga gefen su nacigaba da wayana ,,</p><p> A hankali naimai fatan alheri tare da Allah tasa</p><p> adawo lafiya ina mai yin murmushi cikin kashe murya na,,,</p><p> Daidai lokacin da nakashe wayan nawa ne muka ido hudu da sheriff din mu wanda yazubo min idon shi da suka dan sauya daga fara,a zuwa fushi, </p><p> Sai naga ashe kusan kowa dake falon ni yake kallo ban sani ba</p><p> Mikewa nayi abina nawuce wurin maman Umar a kitchen,</p><p> Tundaga wanan lokacin sai hiran nasu yadan rage karfi sosai,</p><p> Nasamu ta hada masu abincin labawa mai saikin dahuwa ga dadi,</p><p> Najera a tire nadauko nakai masu har gaban su na aje,</p><p> Ina cewa ga abinci nan nasan zaku iya cin shi don ba mai nauyi ne ba,</p><p> Sai alokacin yadan sake fuska kadan yai ma matar da ko sunan ta bai gabatar muna ba balle yace muna ai matar shi ce,</p><p> Abincin suke ci hankali kwance har da ita matar sai salim da ke taya su cin abincin,</p><p> Amal tace wai yaya bakuwa ce kayi don bamu santa ba, kuma na ganku atare, </p><p> Yanajin dadin zama da kan nen shi sosai don yana son su saboda sune mafi kusanci da shi fiye da kowa,</p><p> Murmushi yayi kadan ya kalli salim tace baka fada mata tayi sabon anty bace,</p><p> Saida Amal ta dan kalli matar tace to, nida ke gefe ina kokarin jona tv na juyo da sauri ina fadin masha Allah,</p><p> Gaskiya munyi farin ciki kuma muna mata sannu da zuwa da fatan zaki kula muna da dan uwa fiye da komai a rayuwan ki,</p><p> Koba komai tadanji dadin hakan don tasan nafi Amal dama tunda har nai mata fatan alheri,</p><p> Sundan kai wani lokaci a tare da mu anata hira tsakanin shi da yan uwan shi,</p><p> Inda aziza ta fahinci cewa yana son yan uwan shi sosai saboda bataga abinda yake ba muhin manci ba kamar su,</p><p> Don ta kula ko awaya yake magana dasu zaidade suna hira yana nuna jindadin shi,</p><p> Saidai tasan cewa bata sami karbuwa ga Amal ba sam</p><p> Shakata guda ne ni saboda tace niba yar uwsn shi bace ta jini amma yada yake kula dani yana daure mata kai so sai,</p><p> Wayana yakara tsuwar kira again, </p><p> Wanan karon salimat ce ke kirana tana fada min mijin ta ya iso ko </p><p> Bansan lokacin da nadayi dan ihu murna ba nace mata tai mashi sannu da zuwa ,</p><p> Nan nake fada mata nace mata ai yayan mu yazo da amaryan shi mai kyau da ita,</p><p> Wanan magana yaiwa Aziza da sherrif dadi don na fahinci cewa yana son aziza sosai,</p><p> Nikuma duk abinda yake so ina son shi don yawan kaunar da ya nuna min tun farko,</p><p> Da murna nake fada ma Amal sakon salimat Amal din tayi dan dariya tace ashe yau anty amarya ce,</p><p> Basu wani dadewa ba sukai muna sallama zuwa masaukin su,</p><p> </p><p> Acikin barci naji tsuwar waya na kamar kada in tashi sai dai nadaure na ansa kiran ,</p><p> Amma abin mamaki mai kiran ya boye nobar shi,</p><p> A cikin harshen turanci mai shi ke min magana,</p><p> Dafarko yace min sorry da damuna da yayi ina barci na,,</p><p> Sai na ce ba komai amma dan Allah dawa nake magana ne,</p><p> Shiru ne yadan biyo baya, jin danayi ba ansa yasa nace ma maikiran kada ya kara kirana ni matar aure ce ,</p><p> Idan yakara zan fada ma mijina,</p><p> Dan murmushi yayi yace good ina iya infada ma mijin nawa, </p><p> Ganin da nayi zai jani da dogon zance yasani kashe wayar gami da tsaki, nagyara kwancina,</p><p> </p><p> Anashi bangaren jinda yayi nace zan fada ma mijina yasa shi dagaba yace kai wanan yarinyar,</p><p> Tashi yayi tsab yakoma cikin bedroom inda Aziza ke kwance tana jiran shigowar shi,</p><p> Ce mata yayi baki yi barci bane, saitace mai a,a,</p><p> Yana shirin kwancine ta jeho mai tambaya ,, dayasa shi yin tsit,</p><p> Tace mai wai Ahmad ya kuke da wanan yariyar fadima ne,</p><p> Batare da shakkunta ba ko jin wani dar yace mata yar uwatace itama,</p><p> Tace mai maman ku guda ne da ita din ma,</p><p> Atakaice yace mata aa, yar uwata ce kawai,</p><p> Saida tanisa sai ta dan juyo setin shi tace mai ke nan akwai aure a tsakanin ko ko,</p><p> Cikin firgita da jin kalminta yasa shi saurin waigo ta da karfi yace baki da hankali, aziza,</p><p> Sister dinace fa sai tace and so what,</p><p> Kallonta yakama yi a kufule,</p><p> Ita ko kodar bataji ba, irin halin nan na kasaitatun mata,</p><p> Daga haka baikara cemata komai ba ya kwanta zuciyar fam da wasiwasin,</p><p> Tunda safe muka hada masu break fast din su tsab ,</p><p> Amal takira shi tace mai ko salim ya kawo masu abincin su inda suke ne sai yace mai aa kawai sujirashi gayan zuwa suci tare,</p><p> Kowa ya zauna a table din don cin abincin sai ni kadaice ban zo ba,</p><p> Salim yace yafada min suna jirana,,,, </p><p> Salim na fada min duk saina rude don gaskiya ban taba cin abinci agaban shi ba,</p><p> Table din nazo na zauna kowa na cin abinci niko sai wasa da cibi dake hannu kawai nakeyi,</p><p> Aziza ta kalli sheriff takali fadima tace man kici abinci mana yar uwa</p><p> Dan murmushi nayi nadan dibi ruwan chayi dake gaba nadan kurba kadan sai naji gaskiya ban iya sake jikina a gaban shi hakan,inci abinci,,,</p><p> Tana kallon shi taga ya ture kayan abinci ya mike ya ce mata zai je yadawo ta zauna nan ta jirashi zai je yadawo,</p><p> Ido tabishi da shi don mamaki tabas akwai wani dan feeling da sheriff ke boye wanan yariyar amma koma dai maye zata bincika,, </p><p> Ga mamakin ta sai kuma taga yanafita nafara cin abincina nomal kaman bani bace nakasa ci dazun,,,, </p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA</p><p>✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 6⃣0⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p> </p><p>Ya Allah ka azurta muna dukkan Aluman Mususllumi da lafiya, arziki ilimi mai amfani a rayuwar duniya da lahira,</p><p> Jinjina da fatan alheri gare ku masoya na asali yan huguma groups gabadayan ku ina kara maku fatan alheri, </p><p> Banta mantawa da ku yan uwa na asali ,Anty,Hafsat yusuf, Anty,Mariya SB, Mama farida ,Anty Safiya mai huguma, Maman Rufaida, daduk wani wanda ya cancanci in rubuta sunan shi ban rubuta ba, nagode, nagode, nagode maku kwarai da karfin gwiwar da kuka bani, tun farko har yau gani ga shafi na sitin daidai cikin hikimar ubangiji,,,,,👏👏👏👏👏</p><p><br /></p><p>Almost true life story ,,,,</p><p><br /></p><p> Aziza ce a masaukin su dake cikin masurin hotel din nan mai suna, Al,ni,imati</p><p> Waya takeyi cikin kasaita da nuna isa ita wata kawar da taje Turkey sarin kayan furniture's</p><p> Ai kawai kibari hindu, duk maganin su zanyi har shi din,</p><p> Ai tunda nasamu har ya shigo hannu to shi sunan shi sorry don nan da wani dan lokaci sai yadda na juya shi,</p><p> Ke dai kibi sannu aziza don kinsan cewa in badon taimakon Abu sultan ba da babu yadda zai amince ya aure ki haka,</p><p> Kidibi tun lokacin da kike binshi amma ko kallo baki ishe shiba,</p><p> Saukin ki guda da Abu sultan ya shirya muna wanan plans din cewa ke, marainiyace kuma ga mijinki ya mutu kina son miji mai mutunci wanda keda tsoron Allah da kuma kauda kai ga abin duniya ,,,</p><p> Shewa suka danyi ta cikin wayar tace mugu wai shi nan ustaza kada</p><p> Komai wayon shi sai naci kudin nan,</p><p> Gabadaya sai na mallake komai nashi sannan in barshi a tutar ba bu,</p><p> Wani dan guntun shewa suka kara yi, tace nasan ki mutumiyar baki da wasa ga duk wani abinda kike so,,</p><p> To su yan uwan fa ya zaki dasu, </p><p> Tace kai haba Hindu saikace kin mata da kowa cece aziza kuwa,</p><p> Motsin da taji kamar ana murda kofan dakin su za,a shigo shine ya hana takara sa zancen tace ma kawar nata Hindu sai wani lokaci ma karasa,</p><p> Mao kula da sashen sune yadau kowa sherrif kayan da yasayo a reception room, </p><p> Tana kwance tui da ita samar gado daga ita sai wani dan towel da ba ko rufe mata habar kataran ta guda ba,</p><p> Yana gani yadan kauda kai gefe, kadan </p><p> Duk da take matar shi ce ta sunna bai son irin halayyanta saman don ita nata matsalar bata da kamun kai ko kadan,</p><p> Abinda yafara notice ke nan irin tantiran matan nan ne ita </p><p> Sai bayan Abu sultan yasa shi ya fada tarkon su ne yake dan gane wasu daga cikin halaiyanta, da basuyi mai ba,</p><p> Abu guda ne tana kula da duk wani bukata nashi sai kuma yana ganin tana kula da duk dokan da yasa mata,.</p><p> Saida ya gama kintsa jikin shi sai ya koma saman kujeran dake fuskantar gadon ya zauna ya jawo system din shi suna fuskantar juna,</p><p> Yana cikin aiki take, ce mai amma gaskiya na yaba da halin wa yan nan kanen naka wlh,</p><p> Dan murmushi yayi na jin dadi har cikin zuciyar shi,</p><p> Tace saidai ita Amal akwaita da dan jan aji ba kamar Fadima take ba don duk kusan hiran mu da fadima mukayi shi ,</p><p> Ai halinsu ba guda bane su nada banbanci so sai,</p><p> Da irin wanan kissan tai ta jan shi hira akan mu shi ko duk sai yaji dadi a ranshi cewa matat shi na son yan uwan shi,</p><p> Kenan baza,a samu matsalar komai ba daga gurin ta akan su,,,,</p><p><br /></p><p> Tafe nake acikin sauri amma tunane ya,addabeni sosai ,agogon hannu na na duba da sauri sai kuma ,nakai kallo na ga katon agogon dake makale bakin shiga department din mu,</p><p> Tabbas ya nayi latti har ankusa rufe shiga class din don ka,idace hakan,,,</p><p> Sauri na kara na isa class din dai lokacin da malamin shima zai shiga,</p><p> Guri na samu nazauna gami da yin tagumi, don dai gaskiya komai ban fahita ba daga lecture din na yau,</p><p> Gashi kuma salimat bata shigo ba yau kasancewa mijin ta yazo ganinta</p><p> Ana tashi ban tsaya jiran komai ba kamar yadda mukan dan saba yi indan muntashi sai mundan tsaya mun fahintar da junan mu tukun </p><p> Yau taxi na tare zuwa gida don ban son in wahal da yusuf yazo ya kaini kuma ace yadawo daukan su salim,</p><p> Ina sauka nadauko kudi zan mika wa mai taxi mukayi arba da sheriff wanda motar su ke shigowa kwanar gidan mu a hankali,</p><p> Yana baya zaune shida aziza, tun cikin motar yai min wani mugun kallo,</p><p> Zan shige gida cikin tsawa ya kira suna na cak na ja natsaya wuri guda,</p><p> Ina kikafito cikin rawar murya nace mai school yace ina yusuf yake da baije yadauko ni ba har na shigo taxi</p><p> A,hankali nadago idona da sukayi dan ja kadan nace mai ban son ya wahala ne ni banda lafiya ne shiyasa yau nadawo nabar su Amal, sai anjima Yusuf zaije yadauko su,, </p><p> Bina yayi da kallo kawai yace matar nashi tafito motar tashiga ciki yana zuwa, </p><p> Duk da ranta ya baci amma sai ta dake ta nuna aiba komai, ta bini muka shiga cikin, gidan tare,</p><p> Daki nafada nadan rage nauyin kayan jikina,</p><p> Nafito dagani sai wani dogon wandon da riga mai yar guntun hannu, dai dai iya damtsen hannu na, kaina nasa mai hula baka,</p><p> Inda take zaune tana waya duk kamshin ta ya karade falon namu kamar ba mace ba,</p><p> Abin sha na hado mata cikin tire na aje mata agabanta, najuya nabada baya</p><p> Ido ta bi bayana dashi har nakai saman kujera na zauna kafa na guda nadan taushe guda yana kasa,</p><p> Acikin ziciyar ta tace kai wanan yarinyar Allah yayi halittan shi wallahi jita kamar ita tayi kanta yar karama da ita amma komai nata acan acan gwanin ban shawa, wlh,</p><p> Wanan dai nasan cewa na isa haihuwar ta da ace ban bar kauye ba,aure akai min da wuri da gaskiya zan iya haihuwar ta,</p><p> TV na kuna mata tasha ralabawa suna wani film na ban dariya aciki,</p><p> Ganin da nayi ta gama wayan yasa nace mata ga abin sha nan tasha kafin agama abinci,</p><p> Dan murmushi tai min kadan tace ai a koshe nake kedai saidai ko zuwa anjima,</p><p> Ban kwashe kayan ba sai na barshi agabanta, namaida hankalina gun TV,</p><p> Da na kula wasan bai mata dadi ba sai nafara bata labarin wasan a hankali, ina dan mata bayani,</p><p> Amma kaina yana saman kujerar da nake zaune,</p><p> Hausana dariya yake bata don ji takeyi kamar larbci nake yi ba hausa ba,</p><p> Tace min nako taba zuwa Nigeria, kafin in bata ansa sai aka turo kofar falon tare da sallama, shi,</p><p> Naji kunyar yada yazo yasamay ni ba wani kayan kirki ajikina wlh,</p><p> Don inda nasan cewa zai dawo ne da ban fito hakana ba, falon ganin da nayi dagani sai itane yasa ni fitowa a hakan</p><p> Almustapha zai shigo dauke da ledar sai yai sauri yatare shi ya karbi ledan da ke hannun shi yace ya koma wancan bangaren su salim ya jira shi,, </p><p> Saida yai kamar zai dan da ki aziza da ledar dake hannun shi, cikin tsigar wasa sai ta dan noke cikin kujera,</p><p> Ganin suna dan wasa da junan su yasa nai niyar barin falon,</p><p> Da hannu ya nuna min inzauna, sai na koma na zauna saman kujeran din </p><p>Magani ya bare a hannu shi sai yadan kalli inda aziza take yace mata tazuba min drinks a cup,</p><p> Daman wanda nakawo mata yana nan ban dauke ba,</p><p> Tadan tsiyaya min ta miko mashi tana wani dan murmushin kissa,</p><p> Maganin da nake sha ne na hana ni ciwon mara yasawo min ashe,</p><p> Cikin mamaki na karba dole na wasta abakina yamiko min ruwan juice din yace in hade da shi,</p><p> Sai ya miko min leda mai dauki da pada har kusan sunki uku,</p><p> Duk kunya ya kamani narasa inda zan sa kaina don nauyi,</p><p> Duk abinda ke faruwa aziza na kallonmu cikin mamaki don dai bataji nace mai ga abinda ke damu na, ba cewa kawai nayi banda lafiya shine ya juya yaje yasayo min wanan kayan</p><p> Saida yaga nadan sha maganin san nan yatashi yakoma inda aziza take zaune yadan zauna gab da ita yana mata magana kasakasa murmushi kawai naga tayi mai ,</p><p> Yamike tsaye yana fadin sai sun dawo kenan acikin hausar shi da ba ta kware ba,irin hausan kanuri, </p><p> Idona a,TV yake amma zuciyana na wurin balaguro </p><p> Sai mamaki nakeyi ashe sheriff ya iya soye wa,</p><p> Ita wanan da alamar tafi nafisa farin jini gurin sheriff don nafisa ko kwatan kwacin haka bata samu ba,</p><p> Muna hada ido da ita sai muka sakarwa juna da murmushi,</p><p> Tace min amma dai yayanki na son ki da yawa gashi har yasan time din period dinki,</p><p> Ban bata ansa ba saidai dariyan da nayi kawai,</p><p> Anan inda nake mai nauyi yadauke ni saboda haka maganim ke min,</p><p> Sheriff yadawo ya samay ni kwance a kan kujera nadunkule wuri guda ina barci na hankali kwance ita ko aziza tana charting da Hindu tana nuna mata irin kayan da tayi oda akasar Turkey,</p><p> Kallon tausayi yai min ji yayi kamar ya dauke ni yakaini saman gado daki na, don yasan cewa idan na tashi jikina zai min ciwo a haka,,,,</p><p> Maman Umar yakira yace tazo ta tadani zuwa daki in kwanta,</p><p> Wayana yadan yi tsuwa kafin in farka daga barcin a,hankali yadauki wayan yayi hanyar waje da ita hankalin aziza bai kai gareshi ba tana can tana hira da hindu,</p><p> Kallo sunan mai kiran wayan yayi sai yaga narubu, Al noor, baro,baro</p><p> Ya maimaita sunan a hankali alnoor,,,,,,,,</p><p> Ya danna pick kafin wayan takara katsewa yasa, a kunen shi ba tare da yace hlo ba,</p><p> Muryan Ali baba yaji yana cewa sweet sahiba, mun gama meeting din ga shinan zan taso yanzu jirgin mu zai tashi,</p><p> Jiyayi kamar ya wurgata da wayan kasa ta raratse a kasa don ta kaici, </p><p> Watau ashe koda ya hanani kula da Ali baba, saida na kulashi,</p><p> Kai amma Ali baba yakai katon shege ji yayi kamar afili yake ya shake shi don takaici,</p><p> Nan da nan barebarin suka hau,</p><p> Jin shirun da Alin yayi yasa yake cewa hlo hlo,</p><p> Muryan sheriff da tai kama da ta zaki yace kai dan iska na fada ma cewa kafita hanyar wanan yarinyar tun farko to tana da aure a kanta </p><p> Inba hakaba zan iya halaka ka wlh ,,,,yana mai kashedi cikin kakausar murya,</p><p> Alin baba ya kalli wayar tamkar sheriff yake kallo a filin yace lalai ashe za,a ji mu da kai ke na Ahmad lawan zanna ai ban taba son abu inyi saurin jayewa ba da sauri,,,,</p><p> Abincin da bai ciba ke nan ranan saboda bacin rai,</p><p> Yasa noban na Alin a block,,</p><p> Kamar kada yaba ni wayana yakeji saidai kuma yace bari kawai ya mayar min dashi, tunda yayi blocking line din,,</p><p> Ai zai kama ni nan gaba indai ban daina ba ,</p><p> Abinda bai sani ba duk layin na Alin gudu uku ina dasu, a wayana,,</p><p> Amal tadawo cikin fushi don na bar school batare da najirata ba kuma Yusuf yace bashi ya dauko ni zuwa gida ba yau,,,,,</p><p> Maman Umar ne ke fada mata cewa banda lafiya ne shiyasa nadawo da wuri yau,</p><p> Sheriff na can saman kujerar dinning yana magana da Mr William, a video call,</p><p> Wurinshi tawuce direct kamar bata ga aziza ba,,,</p><p> Yayanmu sannu da aiki a hankali yadago yace, mata baiji ta gaida aziza ba,,</p><p> Cikin dan turo baki tace nafa gaisheta bata dai karba min bane,</p><p> Murmushi kawai aziza tayi mai nuna da magana gaba,</p><p> Saida suka ci abinci su ka huta tukun duk lokacin sheriff' yana gidan mu yana ta aikin wasu takardun masu yawa,</p><p> A hankali yake tambayar Amal da salim dake gefen shi,cikin yaren kanuri,</p><p> Batare da yadago kan shi ba yace mata tun yaushe nafara waya da Alin baba,</p><p> Gaban Amal yafadi dajin wanan tambayan don batai zaton jin haka gare shi ba</p><p> Cikin dan rashin gaskiya take gaya mai cewa gsakiya bata sani,</p><p> Abinda yakeyi ya wane ya dan kura ma Amal din ido, nawa nidan lokaci can yace mata, wayan da yabugo mata yau har yana cewa agaida ke ba gaskiya bane ko,</p><p> A,hankali tacd gaskiya koni tai min fada nadai ki saurarenta ne kawai,</p><p> Amma ayi hakkuri bazan kara ba,</p><p> Kafin yai wani magana su Umar ne da Aisha suka dawo daga school cikin uniform din su, </p><p> Jallabiya ce fara sol na maza sai na mata bakar jallabiya don duk kusan haka uniform din yaran kasar yake,</p><p> Direct gurin sheriff suka nufa sukayi mubayi,a dashi cikin murna da dokin ganin shi,</p><p> Sheriff yana son yaran sosa, haka kawai yaji yana son su,</p><p> Duk yagan su sai yaji kamar ace shine mahaifin, shi,</p><p> Wasa yadan yi dasu kafin su shige ciki cikin nuna kulawa,</p><p> Tunda muka zo yasa Yusuf yasa wata makarantar dake acikin unguwar mu,</p><p> Hakan da yakeyi da yaran yasa ni da uwar su muke kara mutunta Sheriff din namu,</p><p> Don yana da kokarin kula da duk wani wanda ke kar kashin shi,</p><p> Salimata ne tazo da mijinta don ya ganmu yayi muna godiyar dawai niyar da mukeyi da ita don duk wani kula juna da mukeyi tafada mai,</p><p> Kuma ya yaba da hankalin mu so sai tun bai ganmu</p><p> Nan suka zauna falo da sheriff suka danyi hiran gida Nigeria </p><p> Sai marance lis na farka daga barcin ganin da naima salimat ne yasa ni dan mamaki har kasa irin gaisuwar mu na yan Nigeria nai mai saida kamar yadda kowa ke fadi wai ban iya hausaba,</p><p> Muna ta hira sai naga kamar Aziza a matse take da zama agurin tana ta ya mutse fuska kamar mai jin warin mutane </p><p> Nace mata koza ta dan shiga daga ciki ta huta ne </p><p> A,a tace min kawai don duk ta matsu su wuce ashe tundazu take mai test a waya akan su tashi su tafi tana son taje tayi wanka,</p><p> Sai yafita batunta kamar baiji ta ba,</p><p> Sunyi musayar noba da mijin salimat sheriff yai mai alkawarin in ya shigo Nigeria zai ne may shi insha Allah,,,,</p><p> Da haka sukayi sallama damu suka nufi masaukin su, don duk aziza tagwada mai tagaji sosai </p><p> Ashe duk hiran da akeyi sheriff yana nan yana ta harara na ne kawai ya ma rasa ta inda zai bullo min akan zancen,</p><p> Sai bayan wucewan su ne ce Umar yadauko min wayana in diba, </p><p> Kusan 4miss call nagani da layin etisalt din Ali baba </p><p> Nai mamaki da bai kirani da layin da ya saba kirana dashi ba,</p><p> Kiranshi nayi sai yace min in bari yakirani </p><p> Yace tundazu yake kirana don sundan sauka wata kaaane adan huta amma insha Allah yakusa tasowa,</p><p> Har zan kashe waya sai naji muryan shi yana ce min fadima Ahmad yana gidan ku har yanzu ko ya wuce ,</p><p> Damamakin yadda yasan cewa Ahmad na garin yasa nace yafita sun tafi inda su ka sauka,</p><p> Cikin sanyin murya yace min ya akayi yadauki wayan ki,</p><p> Da mamaki nace yadauki wayana fa,aini ga wayana a hannu na,,</p><p> Dan murmushi yayi har inaji tawayan yace min suyi waya dashi dazu tawayana </p><p> Indai bari inyazo zaimin bayanin komai,</p><p> Mukayi sallama yakashe wayan,.</p><p> Aiba shiri na ce ma Amal taji wai sherrif ya dauki wayana yau har sunyi magana ,,</p><p> Cikinbko in kula tace min may yasa na aje wan inda zaigani</p><p> Nafada mata yadda mukayi tun dawo wana gida har yadda,</p><p> Nayi barci nabar wayan, nawa a falo, inda yagani yadauka</p><p> </p><p> Amasaukin su duk abin duniya ya ishe shi taya har Alin baba ya samu karbuwa a wurina </p><p> Saboda iya sanin da yai min ni mace ce msi kamun kai da sanin mutuncina na "ya mace</p><p> Saikuma gashi Alin na so ya cutar da ni ,</p><p> Baikai karshen tunanen shi ba wayan shi taikara, Abba ne yakira shi,</p><p> A sanyaye cike da girmama wa ya gaishe da Abban daga can dayan sashen Abban yace mai ya aiki ta jama,a</p><p> Ya ce to babana ina nan dai ina ma tuni akan matar ka kayi hakkuri kazo kadauki abin ka </p><p> Tunda tagyara halinta yanzu duk wanan mugun rayuwan ta daina su,</p><p> Shiru Ahmad din yayi yana sauraren shi,,, shi</p><p> Cikin hikima da iya kwanrar murya yaje fada ma Abban shi cewa yayi aure a dubai,</p><p> Abban yai dan shiru nawani dan lokaci,</p><p> Can yace ma sherrif din babana kai aure batare da sanin mu ba,</p><p> Yace Abba kayi hakuri auren ne yazo min abazata wlh,</p><p> Shiru Abban yayi tare da cewa to Allah yasanya alheri ya ansa ahankali da cewa Ameen,</p><p> Can Abba yace to ya makomar ita nafisat din yake yanzu,</p><p> Dan shiru yayi tukun sai yace yana nan Abba,</p><p> Zanzo insa agyara mata gida a Abuja ta zauna can, don yanzu kusan aikina zai dan koma can Nigeria ne,</p><p> Sukayi sallama da Abban da shi,</p><p> Abban yai dan shiru yana kallon wayan yana mai tausaya ma dan nashi saboda irin sanyin zuciyar shi,,,, </p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 6⃣1⃣</p><p> BY </p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p> AMINCI WRITERS ASSOCIATION</p><p>🎁NASIBI WRITERS ASSOCIATION🎁</p><p>🎁N🎁W🎁A</p><p><br /></p><p> Almost true life story</p><p> </p><p>Aiki sosai so sheriff sukayi a garin don company su da Abu Abdallah ya yi girma sosai kusan duk manyan biranen kasan na saudiya sun kafa ma,aikatar su,</p><p> Sai bayan kwana biyu Alin yazu gurina lokacin sheriff ya wuce washegari ke nan,</p><p> Nai mai komai nataron bako nida Amal yai muna tsara masu kyau kayan sawa ne irin na matan kasar Paris,</p><p> Sai wasu set din sarka da dan kune masu tsada gaske,</p><p> A falon mu na sauke shi, inda ya samu tarbo na mutunci daga gurin maman Umar,</p><p> Duk kunya ya lunlube ni don tunda nake bantaba tsaya da saurayi ba da sunan soyayya,</p><p> Yausai gashi wai nice akazo wa hira ,</p><p> Cikin dakiya da daurewan zuciya nake duk na wani daburce,,,</p><p> Daguda guda kowa ya watse falon aka barni da gani sai, Alin kawai,</p><p> Shiru yadan biyu baya kadan. Kaina yana akan wayana ina dan daddanawa,</p><p> Jin shirun da nayi yasa nadan dago kai inga komai yakeyi,,,</p><p> Ido muka hada dashi, ashe zaune yake yakura min ido kawai yana kare min kallo,</p><p> Acikin zuciyar shi yana yaba min komai nawa yayi mai yadda yake burin ya mallaki mace,</p><p> Dadin dadawa gashi ni yar karama ce sosai , don yanzu haka ban fi sha bakwai ba , yake gani,</p><p> Kunya ne ya kamani ganin irin kallon da yake min</p><p> Tambayana yayi yace min ya yaga na yi shiru, irin taron da zan mai kenan </p><p> Duk zumudin zuwa yaganenin da yake yi,</p><p> Da sauri nadan dago kaina nadan kalleshi sai kuma na kawar zuciya na fal da mamakin shi amma sai na dake na ce mai</p><p> Cikin murya mai jan ra,ayi da daukan hankali wanda ni kai naban san ina yi ba,</p><p> Nace wani kuma irin taro kake bukata wanda yafi wanan din da nai maka,</p><p> Matsawa yayi zuwa dayan kujeran da ke fuskanta na yace,</p><p> Yace min look fadima ina son kisan cewa aure nake son yi da ke </p><p> Very soon ba dadewa ba so ina son ki fadamin gaskiyan zuciyan ki </p><p> Don kisan yanzu ni bazance na tsaya wani wasan soyayya ba,</p><p> Indan kin amince min zan ga Ahmad yakaink gurin iyayyennki don in gabatar da kaina garesu</p><p> Yakarashe zancen yana mai komawa saman kushin din, yadan jingina bayan shi da makarin kujerar</p><p> Yakura min ido alamar yana jiran asa ta,</p><p> Jin shirun da nayi yasa shi kara ce min,</p><p> Ke nake sauraro don banson zuwa wurin Ahmada batare da naji wani kwakwaran magana daga gare ki ba</p><p> Ke nake sauraro fa na tsinkayi muryan shi cikin kun,nuwa na, </p><p> Bansan lokacin da nadan dan,dago kaina ba muka hada ido sai na sakar mai dan guntun murmushi,</p><p> Ok kina nufin kice min kin amince min ke nan ko</p><p> A hankali nadan daga mashi kai alamar eh,</p><p> Cike da mamakin wanan saurin amince mashu danayi yake yi</p><p> Don bai dauka abin zai zo mai da suki irin haka ba</p><p> Ajiyan zuciya yayi yadan tsinki Anebi da maman Umar ta aje mai acikin plate din dake gabashi tab da kayan fruits,. </p><p> Yana taunan Anebin din yake ce min ya akayi ranan na aje wayana har Ahmad ya dauka </p><p> Murmushi kawai nayi batare da na bashi ansa ba na ce,</p><p> A hankali nace mai lokacin banda lafiya ne, acikin mamaki yake ce min har ciwo nayi shine ban fada mai ba,</p><p> Haka mukai ta dan hira jefi jefi dashi cikin rashin walwala,</p><p> Sai marance lis yai muna sallama zai tafi kuma yace muna ba kwana zaiyi,</p><p> Har bakin motar da yazo da ita na rakashi, </p><p> Cikin kulawa da kuma kewar juna muke sallama hannu na yana irike da Aisha,</p><p> Wace keta dan kokarin in saketa taje tadan yi wasa,</p><p> Muryan Alin ce ke ce min Can I trust You fadima,,,sai na kada mai kai ahankali. </p><p> Yace duk ritsi da zamu shiga da Ahmada kada kice mai kin jaye zancan auren mu nida ke a nan gaba ,</p><p> Pls sai ya hada hannu shi guri guda duk ka biyu yai min alamar rokon Abu,, </p><p> Yashiga motar shi yana daga min hannu ciki shaukin so da kauna mukayi sallama da junan mu,,,,</p><p> Saida motar shi ta ba ce min da gani san nan nadanyi ajiyar zuciya na koma cikin gida,</p><p> </p><p> Ina shiga gida na iske Amal tsaye da wayana a hannunta </p><p> Fuskanta kawai na kalla nasan cewa akwai magana ,</p><p> Inda take tsaye na nufa cikin damuwa nake tambayar ta ko lafiya naganta haka,</p><p> Batai min magana ba saida ta zauna saman kujera ta miko min wayana a hanmukeq,</p><p> Nakarba ina ma wayan kallon mamaki, sai kace zan fahinci wani abu acikin wayan,</p><p> Wuri na samu nima na zauna gefen ta kadan don nasan cewa da magana a irin yanayin da naga Amal ciki ,</p><p> Fuska a daure batare da ta kallo ni ba tace yayan mu ne ya bugo waya kisan idan ya bugo sai ya tambayi kowa abashi su gaisa nace mata eh hakanane </p><p> Yatambaye ni ina kike nace mai kina barci sai yace min ba gaskiya bane,</p><p> Don bai taba ganin kinyi barci by this hours ba,,,</p><p> Sai ce min yayi kina waje tare da Alin ko , shirunayi kafin in bashi ansa har ya katse wayar ko,,,</p><p> Wani dan dum naji sai kuma akarshe nace to ma maye na boyo aciki tunda ai dole yasani</p><p> Sai kuma na tuna irin warning din da yai muna kafin muzo karatu,</p><p> Nace to in har yafitar dani ai Alin zai iya karasa biya min kudin karatun har in karasa abina</p><p> Amal ido ta kura min tana kallo na ina cikin nazarin abinyi,</p><p> Sai tace min gaskiya fadima yadda kika bari har son Alin ya shige ki baki kyauta ba,</p><p> Tunda kinsan cewa yayan mu yai muna nasihan akan kada mu yarda mu kula kowa har sai mun gama karatun mu,,</p><p> Tunda ta fara magana bakinta na tsura ma ido har ta kare zancen nata,</p><p> Gani irin kallon da nake mata yasa tagane cewa nayi nisa ko cikin wanan tarkon da na fada,</p><p> Tace nidai shawarar da zan baki shine a matsayina na yar uwanki kuma mafi kusa dake shine </p><p> Kibi a,hankali tunda har kikaga yayan mu ya nuna bai ra,ayin hakan, to ki daina </p><p> Saboda shi namiji ne kuna shi ke tare dasu shiyasan halin su,</p><p> Don dai kinga bazai cutar da mu ba,</p><p> Tagumi nayi da hannaye na ina kallonta,</p><p> Itakuma sai taci gaba da fadin namiji abin tsoro ne, </p><p> Kibi a hankali don yanzu muke idan lokaci yayi sai muyi abin mu, </p><p> Magana kawai takeyi nikuma jinta kawai nakeyi don nayi nisa ko,</p><p> Ta lura da ni sai ba wai na yarda da shawaranta bane,</p><p> Don haka tashi kawai tayi tai shigewar ta tabar min falon,</p><p> Hakan da tai min sai naji banji dadi ba,</p><p> Hutu mukeyi dama ba wani karatu mai dan yawa agaban nima shigewa nayi abina,</p><p> Tunjiya nake cikin rashin walwala saboda maganganun da mukayi da Amal,,,,</p><p> Maganar tasani cikin damuwa don dai gaskiya ina son Alin </p><p> Amma kuma maganar sheriff tayi min tasiri azuciya na</p><p> Saboda irin taimakon da yadinga min ba cutar wa a rayuwa saidai shukuran tsakani na dasu,</p><p> Shin idan har naki bin maganar wanda yake kamar uba gare ni ai nayi butulci mai karfi ,</p><p> Tsuwar da wayana keyi yasani dan farfadowa daga cikin tunanen da nakeyi </p><p> Sai gabana ya dan fadi don nasan cewa sherrif ne ke kirana tunda tunjiya bamu gaisa ba </p><p> Wanda akullun dole yagaisa da kowan mu,</p><p> Saboda yaji lafiyan mu Sunan Salimat ce nagani ta ke kirana, </p><p> Saida nadanyi sanyayan ajiyar zuciya danaga itace,</p><p> Ina dauka tacs min mufito mutafi masallaci don mu samu jam,in jumma yau,</p><p> Cikin sauri natashi na shirya don sam na manta cewa zamu iya makara idan mun wuce shadayan rana bamu fita ba,</p><p> Bandau wani lokaci ba ina shiri nafito abina tsab dakin Amal na nufa itama acikin shirin ta nasamay ta duk da tun jiya sama sama muke da ita,</p><p> Saboda maganganun da mukayi da ita din,</p><p> Ganin datai min yasa tamike don tasan inda zamu,</p><p> Da kafa muke rafiya zuwa sallah jumma,a kudi nadauka da zamu fita,</p><p> Duk da saurin da mukayi mun iske har ta wajen haraban duk jama,ane zazaune suna jiran lokaci,</p><p> Har Ciki muka kusa muka samu wurin zama,</p><p> Saida naga mundan zauna nafito waje saboda na tabbatar da mun samu gurin zama ko,</p><p> Wurin saida alkama natafi na saye mai yawa, da hannu na naita watsa ma tanatabaru cikin masallaci wanan alkaman sadaka, akan ina bidan sauki ga al,amarina,,,</p><p> Saida nagama watsa masu san nan na nufi hanyar toilet naje nadauro wani sabon alwala nadawo inda mukasamu guri na zauna,</p><p> Har Umar da Aisha muke tafiya masallacin don haka da dan kulan abincin su muke zuwa don sai dare muke barin masallacin,</p><p> Har aka idar da sallah akayi na la,asar muna nan zaune,</p><p> Kafin ai sallah magrib muka tafi ziyaran rauda, muna dawowa muka fito wajen harabar masallacin don idan an idar da sallah mu samu hanyar fita dmukeyi </p><p> Muna nan zaune aka fara bude lemar haraban masallacin suka fara ma haraban feshin ruwan almuski da sanyi na,un,,,</p><p> Muna na har aka tashi saida mukaga Salimat ta shiga gidan ta sannan muka kama hanyar namu gidan,</p><p> Gab da zamu shiga kwanar layin gidajen mu ne kiran wayan sheriff yashigo min ,</p><p> Namika ma Amal wayar ta karba tare da yin sallama nan ya sheda mata cewa zai dawo saudiya gobe insha Allah muma yanason mu hadu a garin makka agoben tunda hutu mukeyi</p><p> Duk da ina son zuwa makka yau sai naji,</p><p> Sam sai banji dadin hakan ba araina saboda ina gudun haduwar mu da Sheriff din mu,</p><p> </p><p> Tunda safe mukabar garin madina zuwa makka, </p><p> Kallon dajin kawai nakeyi wanda har kullun ina naga nisan tafiyan da mukeyi a mota, sai in kara jinjina ma Annabin rahama tare da masoyin shi Abubakar,</p><p> Da su arakumi sukayi hijara daga makka zuwa madina,</p><p> Amal ke ce min idan mun isa muje muyi umurah, kafin mu isa gida </p><p> Tunda sheriff yace daga Malishiya zai zo goben,</p><p> Kinga kafin ya iso mun sauke nauyin ko,</p><p> Kai kawai na daga mata don nasan cewa wanan tafiyan kusan don nice za,ayi shi,,,</p><p> Muna shiga gari muka wuce mukayi umurah duk kan mu,</p><p> </p><p> Yau shekara daya dawata tara ke nan rabonmu da garin makka,</p><p> Kallon ko ina na garin nakeyi cikin jin dadi da tuna wasu abubuwan da suka faru da ni lokacin ina yar karama da nazo garin,,,,</p><p> Lunshe idona nayi ina tuna Rugaiyya ta yar uwata masoyiyata mai kaunana tsakani da Allah</p><p> Hawaye naji masu zafi sundan sulalo min a fuska na daga cikin idona,</p><p> A hankali na goge su sai kawai naji raina yawani yi min bakikirin wlh, </p><p> Nanda nan kewar Rugaiyya yadawo min sabo fill a zuciya,</p><p> Ko saudaya banta tunanen cewa wai Kudina yana gurin Rugaiyya ba,</p><p> Iyakadai ina mata fatan Allah yasa tasamu ta tsira da kudin ba,a karbe mata ba,,,</p><p> Gidan na Sheriff yana nan tsab kamar yadda muka wuce muka barshi </p><p> Saidai tun shigar mu naga wasu yan bakin fuska agidan ba wa yanda nasa ba ne ada,</p><p> Ina murna yau zanga yumma da su Sukaina da Mari,</p><p> Hjy ma fushi zandanyi da ita tunda sau guda taje tadiba ni ,</p><p> Amma duk dadewan nan ko waya babu </p><p> Troller's din mu aka kai muna cikin gida har da su maman Umar da mukazo wace muke jin dadin zama da ita sosai ,</p><p> Matace mai sanin yakamata kuma batayarda ta saba ma ko gudan mu,</p><p> Idan kuma taga zamuyi abinda ba daidai ba batayarda muyi shi,</p><p> </p><p> Dakina na fada tunda mukazo nashige abina nafada bayi nai wanka nadauro alwala,</p><p> Bayan na sallamay sallah na nadan zaina gurin ina dan tunane,</p><p> Daga nan natashi don inje ingaida hajiyan mu da su yumma, tunda nazo basu zo suntare ni ba,</p><p> A hankali na ke tafiya cikin wani dogon riga mai kama da silk ina tafiya yana shaking,</p><p> Ina zuwa sashen dakunar su sai nai turus, wuri guda ganin dakunan nasu duk arurufe suke, ba alamar akwai mutane aciki,</p><p> Da saurina karasa har kofan dakunan nasu sai ga ,alamar andade ba,a cikin daku nan don duk wurin yayi dan datti da yanan gizo </p><p> Hakan bai isheni shedaba saida nadan tura kofan inji ko abude suke,</p><p> Gabana yaba da dam dam dam,</p><p> Cikin wani irin sauri nake tafiya kamar zan tashi sama, don sauri,</p><p> Tunane nakeyi azuciya ina hajiyan mu da su yumma, ina yan uwana, ina gatana ,</p><p> A falo mukayi kicibis da sheriff shida Salim ganin da yai min cikin tashin hankali kuma yasan daga inda nafito,</p><p> Cikin daga muryan da bantaba yi ba agabanshi yau nai magana da larabci mutanen akbass nake magana cikin sauri sauri nace ina hajiyana da yan uwana suke,</p><p> Ido ya kura min kamar wanda ba zaiyi min magana ba, </p><p> Sa can yai magana cikin murya mai taushi fa natsuwa yake ce min </p><p> Shine gaisuwar da zan mai kokuwa shine karatun da nakoyo,</p><p> Sai alokacin nadan sami nadan yi kokarin natsa kaina guri guda,</p><p> Nagane cewa ban ma gaisai dashi ba, sam na ma kasa ganin cewa yanzu ya iso gidan daga tafiyan da yace yayi,,</p><p> Dakin shi ya haura sama batare da yakara yin wani magana ba,</p><p> Wurin Amal natafi tana zaune tana gyara kayanta, cikin jakar hannunta,</p><p> Ina shiga na fada jikin ta ina wani irin kuka mai gumza,</p><p> Duk hankalin Amal din sai yatashi, saboda ganin irin kukan da nakeyi </p><p> Da kyat tasamu tadan lalashe ni nadan tsagaita kukan nawa,</p><p> A natse take tambayana komay ke faruwa nakwashe abinda nagani gurin dakunan nasu nafada mata,</p><p> Karazancen da cewa kodai yan bagaladi sunzo sun kama su ne ba,afadamin ba,</p><p> Sai kuma nakara shige mata cikin jikinta ina wani irin kuka mai tsuma rai da zuciyan bawa,</p><p> Har maman su Umar saida ta iso dakin don jin ko mai ke faru ne haka,</p><p> Amal tadan dago min kai tace indan saurareta inji dan Allah,</p><p> Jin danayi tace dan Allah yasa nadan tsagaitata kukan nawa,</p><p> Ina saurarenta, tace min fadima kinsan dai duk inda suke yayan mu yasani ko , kai nadan kada alamar eh,</p><p> Tace kuma dai kinsan bazai bari ai masu wulakanci ba ko,</p><p> Kallonta nakeyi ina naxarin zancenta a hankali,</p><p> Ganin da tayi nadan tsagaita kukan yasa ta fara share min hawayena da hannun ta a hankali,</p><p> Bata barni ba saida taga nasamu dan natsuwa, tukun sanan tayarda naje daki na </p><p> Ranan ko abinci banci ba hakana nasamu guri nadan kwanta don indan samu natsuwa,</p><p> Tunda na kwanta ban tashi ba sai cikin dare, nafarka, natashi, nadauro alwala, nazo nayi nafila raka,a hudu kamar kulun </p><p> Saida gari ya waye san nan na tashi a hankali naje na gyara jikina tsab nafito cikin shigar wasu jajayen, da dan ratsinyau</p><p>ki,baki kayan yan na mutanen Japanese ne mata, rigan yanada dan budewa a kasan shi sai dan guntun hannu daidai, gwiwar hannu,</p><p> Bakin gyale nasamu nadan daure kaina dashi,</p><p> A hankali na ke tafiya kamar banson taka kasa, fito wa nayi zuwa falon gidan </p><p> Don indan samu abinda zan danci saboda tun jiya ban ci komai ba, yunwa nake ji yau</p><p> Zaune suke shida Salim a dinning table din suna cin abinci su hankalo kwance,</p><p> Ganin da nayi masu shi yasa nai niyar komawa daki sai kuma wata zuciya tace min ban gaida sheriff ba,</p><p><br /></p><p> Takawa nayi har inda yake nadan karasa cikin ladabi na gaishe shi nai mai yaya hanya,</p><p> Salim yai min tayin abinci, yace min ya dauka ko nima barcin nakeyi don baiji motsina ba,</p><p> Batare da nace mai komai ba nawuce kawai zuwa cikin kitchen inda na saba diban abincin mu,</p><p> Saboda gaskiya ban iya zama inci abinci agaban sheriff din mu, yana kallo nha</p><p> Har nakai kofar shiga side din da zai sada ni da kitchen din sai naji muryam sheriff, cikin harshen larabci yana ce min inzo, a hankali nadawo har inda suke kujera dake gefen Salim ya gwada min in zauna sama,</p><p> Sai naji wani dummm narasa yadda zanyi sai naga ya mike yabar gurin yana waya, </p><p> Nawaiga a hankali sai naga yabar falon gaba daya, hakan yasa naji dadin zama nazauna naci abinci na hankali kwance,</p><p> Saidai zuciya cikie take fam da tunanen inda yan uwana sukaje,</p><p> Batare da sani wani </p><p> Ina tashi wurin maman Umar na nufa don inji komay mafitar zancen,,,</p><p> Itama dai hakkuri tabani tace min in bari zata bincika min a hankali, </p><p> Amma dai duk ida suke shariff yasani ai </p><p> Kusan kwdayataso baice min komai ba nikuma cikin damuwa nake sosai</p><p> Ranan da muka cika kwana biyu ne ina zaune a daki na ina nazarin a kan wani sabon computer da yafito sai naji anturo kofar dakin na a hankali,</p><p> Nadauko ko Aisha ce sai dai kamshin turaren da ya ruda min hanci yafada min kowaye</p><p> Cikin shigar kananin kaya yake yau kayan sunyi mugun karban jikin shi,,</p><p> In ganin shi sai nayi niyar saukowa daga saman gadon , </p><p> Hannu yadaga min a hankali yai min nuni da inzauna inda nake,</p><p> Gefen mirrow dakin yaje yadan tsaya yajingina jikin shi da mirrow</p><p> Hannu shi cikin aljihun Kafan shi na harde cikin guda,</p><p> Ido yadan zuba min kusan na minti biyu sai yakira suna na ahankali, nakarba,</p><p> Ina mai dan dago kaina shima ahankali nadan kalle gefen da yake sai na sauke idon nawa</p><p> Yace min wani irin tambaya kikai min shekaran jiya, </p><p> Shiru nayi ba ansa yakara ce min haka yakamata kiyi tambaya,</p><p> Ko kinga cewa hjy zata bace a gida nane,</p><p> Karshe yace hjy da sauran yaranta sun koma gida Nigeria, dammm dammm gaba na ya harba </p><p> Wanan karon kallon shi nakeyi cikin ido sosai saidai na kasa dole na sauke kwayar idona da yacika fam da hawaye,</p><p> Na maimata maganar nace sun koma Nigeria,</p><p> Yaushe, kuma ta yaya san nan nifa , </p><p> Ni may yasa suka wuce suka barni, sai kawai nasa kuka mai bala,in tsuma zuciya, </p><p> Ganin da yayi nafara kukan yasa shi fita dakin cikin sauri, duk da yaso son yai min bayani komai amma ina bai iya tsaya yanajin kukan mace a gaban shi hakana,, </p><p> Nai kukana har saida nagaji banda wani bayani dole na hakkura na maida lamari na ga Allah,</p><p> Sati biyu zamu yi a makka don haka muna garin sheriff ya wuce zuwa Nigeria wurin wani aiki dayataso mai akan sabon kamfanin su,</p><p> Don haka mu kadai yabari a gidan,,</p><p> Ganin da nayi bai gari yasa na shirya zuwa masfala wurin hajiya laila, don inji bayanin abinda ke faruwa tunda na fuskanci sheriff baida niyar fada min komai,,,</p><p> Ina zuwa sai nai rashin sa,a ance hjy laila ta koma birnin Riyadh da zama </p><p> Haka nadawo gida hankalina tashe, banda wani sukuni ko kuzari tare da ni ko kadan</p><p> Maman su umar ne nasamu take dan kwantar min da hankali yanzu, </p><p> Saiko Amal wace take iya kokarinta wurin kula da al,amarina ,</p><p> </p><p> Saidaga baya na fahinci cewa aziza ba ,a garin take da zama ba ashe wai a Dubai take zama don a can take sana,a har tagamu da sherrif din mu awajen wani taron yan kasuwan kasashen afirika da akayi,</p><p> Tun lokacin ta lake mai so sai, da taga gurinta ya cika, </p><p> Tana son sheriff don yayi mata kuma tana ra,ayin kudin shi ,,,</p><p> Wanan zuwan da yayi Nigeria har da batun dawowa da nafisat gidan shi yakai shi,</p><p> Nafisat zata zauna a Abujane tunda yanzu zaidinga zuwa aiki can sosai,</p><p> Ita kuma aziza zata dinga zuwa nan saudiya ko kuma shi yaje can inda take,</p><p> Ya iske kaunar shi yayan su Amal ta hai ko suna ba,ayi ba </p><p> Yai mata sha,uku na arziki ita da mijinta har su shehi da sauran yan uwa sunji dadin wanan zuwan nashi so sai,</p><p> Kamar yadda maman su Umar tai min alkawarin bincken labarin su hjy mu haka din ne ko </p><p> Saida ta binciko mai tazo min da labarin yadda maganar yake cewa hjy da su yumma sunkoma gida ne da taimakon Sheriff saboda gwaunatin saudiya tasa anata binciko mata duk inda takari suke zaune akasan </p><p> Hakan da yagani ne yasa yai masu bizan komawa gida suka koma tare da su yumma,</p><p> Saidai akwai sauran bayanin da batai min ba tadan boye min su,</p><p> Jin hakan da nayi yasa nadan ji sanyi azuciya na sosai ,,,,, </p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 6⃣2⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,,</p><p><br /></p><p> Har muka kare hutun mu a makka Sheriff bai dawo ba daga tafiyan da yayi, don yace daga Nigeria zai biya kasar Italy </p><p> Mundawo madina lfy, munci gabada gudanar da karatun mu lafiya,</p><p> Bamu da wani matsalar rayuwa yanzu don koda yaushe sheriff yana turo muna da kudi</p><p> Duk da babu abinda muka rasa na rayuwa amma sai ya aiko muna da kudin nan,</p><p> Salimat tasamu ciki mai wahal da ita sosai, don kusan duk abinda taci sai ta amayar da shi,</p><p> Don haka yanzu kusan karatun mutum biyu nake yi , inyi nata inyi nawa,</p><p> Saboda gaskiya ba yabon kai ba wlh ina da gwargwadon kokarina sosai,</p><p> Shiyasa koda nake hada aiki na da na Salimat ba wai wani mugun wuya nake sha sosai ba,</p><p> Dagani har Amal muna iya kokarin mu wurin kula da ita saboda inkaga yadda ta koma sai ta baka tausayi sosai,</p><p> Ganin irin wahalar da take sha ne kuma gata gidan ita kadai ne aciki yasa mijin ta yabugo min waya cewa don Allah yana son mu taimaka mai salimat tadan dawo wurin mu ta zauna har taji dan sauki,</p><p> </p><p> Saboda nasan cewa nima laba ni akayi sai ban boye mai gaskiya ba nace zan bugawa sheriff yawa in fada mai idan ya amince zan fada mai saita dawo gidan namu,,,</p><p> Sai da nafara yiwa Amal bayanin komai inda ita ma tace gaskiya Salimat tana bukatar taimako don ita kadaice a gidan batare da kowa take zama ba,</p><p> Tace min inwa sheriff magana ko zai yarda, </p><p> Saida dare bayan na gama komai kuma na tabbatar cewa shima yanzu duk inda yake ya dan natsu ,</p><p> Watakila yana sama computer shima, </p><p> Sainai dialing din noban shi,</p><p> Zaune yake shida aziza a falon su na garin Riyadh, tayi dan filo da cinyan shi ,</p><p> Shiko yana aikin latsan system din shi, wayar shi tadan yi kara kadan </p><p> Bai dauka ba saida kiran ya kusa tsinkewa dakanshi,</p><p> Sanan yadiba yaga kowaye,</p><p> Sunan fadima dayagani shi yabashi mamaki ,</p><p> Saida yakara maimaita sunan san nan ya ansa sallama da nai mai cike da mamaki yake don dai gaskiya bantaba kiran shi a waya ba saidai shi din yakiramu yaji lafyan mu,</p><p> Saida na gama gashe shi sai kuma nadan shiru, jin shirun da nayi ne yasa shi yadan daga wayar nashi yadiba kona kashe ne sai yaga ina online,</p><p> Hlo yace na ansa mai da naam yace min lafiya dai ko,</p><p> Cikin inda inda nafara mai bayanin salimat da kuma abinda yasa nakirashi, </p><p> Saida yagama jin bayani na san nan yace min fadima na ansa da naam </p><p> Yace kina ganin dauko da zakuyi ku aje agida bai zama maku matsala nan gaba kadan </p><p> A hankali na ansa mai da cewa a,a dan murmushi kawai naji yayi,</p><p> Yace min idan har kunga cewa hakan bazai shafi lafiyan karatun kuba ai is ok, </p><p> Nakasa boye farin cikina saida ya gane daga inda yake don na manta cewa ban kashe waya ba yaji sanda nake ihun murna ina fada wa Amal cewa ya yarda </p><p> Murmushi yadan yi wanda har saida aziza ta dan dago kanta takaleshi,</p><p> Bayan ta maida kanta kan ciyan yashine take tambayan shi ko may yafaru, </p><p> A,takaice yabata ansa yace mata shida su fadima ne ke waya kawai daga nan bai kara ce mata komai ba,</p><p> Yacigaba da aikin shi na tura sakon ni dayakeyi, amma zuciyan shi fam da tunanen son baby a ranshi, gashi da mata amma ba wace keda alamar haihuwa acikin su,</p><p> Ganin da yaiwa babyn sister shi daya je Nigeria ne tun lokacin yaji yafara son haihuwa don duk wanda ya ganshi sai ace aida shi baby ke kama wai kamar su guda lokacin yana karami </p><p> Don haka sai yaji yana son yaron aranshi sosai,</p><p> Kafin yadawo duk wani abin jin dadi na jarirai saida yasawa yaron,</p><p> Sai kuma yanzu maganar cikin Salinat da nai mai yasa shi cikin wani tunane mai dan zurfi,</p><p> </p><p> Aziza yace cikin dan kasalalen murya ta ansa da umm sweet sahibi,</p><p> Yace mata when are u ready for our babies,</p><p> Wani dan shock taji wanda saida kyat ta iya saita kanta kafin tadan dariya </p><p> Tawani shake murya tace tun yanzu sweet sahibi,</p><p> Saiyadan dagota yace da sai yaushe kike shiri ke,</p><p> Tadan kashe mai idlafiya nan da two years coming ko,</p><p> Yace mata u are out of ur sense,</p><p> Niko yau ki shirya kikarbi dan Riyadh basai ma gobe ba,</p><p> Dariya suka sa gaba dayan su, saida suka dan tsakaita dariyan ne yasa ke ce mata gaskiya ina bukatar haihuwa, very soon </p><p> Aranan wanan maganan aziza ta kwanada shi azuciyar ta washe gari maganar na cinta sai taji sheriff dake kokarin daura tie din shi awuya yana ce mata ihope kin karbi ajiyan baby ko,</p><p> Murmushin dole ta sake don maganar baby nan yana tayar mata da hankali sosai walahi </p><p> Ya manna mata kiss a goshi yafita yana mai mata sallama,</p><p> Bayanshi tabida kallo bayan wucewar shi,</p><p> Wayan ta ta jawo dake gefen filo aje,takira layin Hindu ,</p><p> kira guda Hindu ta dauki yawan tana dariya,</p><p> Jin muryan Aziza cikin tashin hankali ne yasa tagane cewa ba lafiya</p><p> Tambayan Azizan tayi komay ke faruwa ne haka,taji ta badadi tunda safe haka,</p><p> Aziza tace bari Hindu Ahmad nason ya dauko min wani sabon bala,ai ne wai shi haihuwa yake so,</p><p> Dariya Hindu tasa mata mai cin zuciya , saida tayi mai isar ta tace</p><p> Aziza yar lashi, yo ke da mai kike nufi, </p><p> Ko kin manta cewa matashi kika aura, </p><p> Ai hakan nacikin ilar auren shi da na hango maki,</p><p> Shiyasa naso kiyi hakkuri da yan tsofin Alhazan da muke bi don su ba batun haihuwa gare su saidai life </p><p> Don sun riga sunyowa bariki shiri kafin su shigo sun aje dukiya sun kuma tara iyali,</p><p> Amma ke kudi da kyawon shi da kurciya suka debe ki,</p><p> Yo aiko shi in baice yana son haihuwa ba yan uwan shi na son suga zuriar shi </p><p> Nidan Allah kin isheni da zance Hindu kiranki nayi inji may abin yi yanzu,</p><p> To ki saurara da kyau don wanan maganar ba tawaya bace kibari har mu hadu sai musan abin yi,</p><p> Ahaka suka rabu hindu na ta kwantar mata da hankali cewa ta kwantar da hankalinta komai zai zo mata da sauki insha Allah,</p><p><br /></p><p> Mu uku muka tafi gidan su salimat da salim da maman umar mun samayta tana jin jikin ta sosai yau, </p><p> Kayan sawan ta kawai muka dan diba sai wasu tan abin bukatu na mata da na tataro matasu cikin jakka hannunta,</p><p> Salim ya jawo mu zuwa gida da ita, ahankali yake tafiya da ita duk kyawon da hanyoyin keda baisa salim yin gudu ba saboda tausayin irin halin da yaga Salimat </p><p> A dakina mukayi mata masauki ,tundaga wanan lokacin maman umar ke kokarin kulada salimat</p><p> Don itace tasan yadda harkan ciki yake duk abinda salimat tace zataci shi za muyi mata, </p><p> </p><p> Hjy mama tare da yayan ta akasar Spain taje ganin likintan ta da ke diba mata kafa ,</p><p> Zaune suke duk kan su saman kujerun da ke falon tana ta faman surfa masu masifa,</p><p> Akan may har suka bari Ahmad yafi tara abin duniya akansu ita bataga amfanin karatunsu a turai ba gashi duk wani dan dukiyan ta turo masu shi, </p><p> Suraj ne ya katse ta dacewa, haba mama arziki fa na Allah ne duk yadda mukaso yin shi idan Allah bai nufa ba baza muyi shiba sai lokaci yayi,</p><p> Imun shiru tace mai acikin daka tsawa kai ai kafi kowa bani mamaki har nan fa muka shirya dakai zakaje ka dibo muna wani irin sana,a yakeyi haka, har yai wanan mahaukacin kudin dan karamin yaro dashi,</p><p> Duk kun girmay shi fa amma jiku dan Allah bawani wanda zaitada wani, da cikin ku,</p><p> Suraj yace duk iya binciken da zanyu wlh nayi anaje amma banga wani abin tir da yakeyi ba,</p><p> In mabaki sani ba kisani mama don yanzune kudin shi zasu kara habbaka saboda ya hada hannun jari da Abu Abdallah na Dubai wanda ake gani kamar yafi kowa yawan dukiya a kasar ta Dubai da kewayenta </p><p> Salis wani irin dogon tdaki yaja yace niki duniya zai tara ba abinda zai damay ni</p><p> Koma dai may ye ai nasan cewa dan uwa na ne shi,</p><p> So ni banga abinda zaisa hankalinki yana tashi haka ba wlh,</p><p> Yasa hannun shi a aljihun shi yadauko karan sigarin shi ya kuna yakashe guntun asha nar,</p><p> Saida yadan busar da hayakin yace mata shi yatafi kuma daga yau kada akara kiranshi akan maganar Ahmad,</p><p> Yabuga kofa yafita abinshi, yawuce zuwa club,</p><p> Rai bace tabishi da kallon mamaki tajuyo wurin sauran saitaga su,ma suna kokarin wucewa ne,</p><p> Aikawai saitasa masu kuka wiwi,</p><p> Suraj ne yje yadan tsunguna gabanta yakama hannayenta biyu wuri guda yace mama kibi sannu </p><p> Zamu san abin yi nazuwa dan wani lokaci</p><p> Kidaina tayar da hankalin ki haka kinsan kinada hawan jini fa,</p><p><br /></p><p> Balaifi yanzu na sake jikina sosai nadaina dar,dar din da nakeyi akan maganar Alin kulun kamar kara girma nakeyi,</p><p> Don yanzu na zama babban mace nayi wani irin hip, irin na mata masu cikakkiyar kira,</p><p> Fatan na yayi man wani dan lub lub tamkar irin na larabawan Pakistan </p><p> Kyau na da kamala na sun baiyyana sosai, dakaganin ni saikayi sha,awar kakara kallo na,</p><p> Ko tafiyana yasake yanzu ga suturu na alfarma ana sayo mun duk kasar da sheriff yaje aiki zai kwaso muna kayan da matan kasan kesawa na alfarma,</p><p> Amal takan min sheri tace wai fadima may sirin wanan canjin naki ne, sainake ce mata ai itace za,a tambaya </p><p> Saboda ni gani nakeyi tafini haduwa sosai,,,,itama din tasan cewa nafita haduwa shiyasa bata yarda, idan nace nafita haduwa,</p><p> Salimat tadan ji sauki yanzu mukan fita jefi,jefi zuwa makaranta tare da ita, saidai ba kulun ba</p><p> Yau ma hakane munyi jiran salim ya zo da mota yadauke, mu a school jin shi shiru da mukayi yasa muka dan fara ta,takowa da kafa, </p><p> Dan dogon tsaki Amal taja tace ban san may yasa Salim yake muna haka ba yanzu,</p><p> Ni gaskiya da ace mata suna jan mota a kasan nan walahi da sai ince yayan mu yasaya muna wata motar </p><p> Mufita harkan jiran salim ko yau saiya gama bata muna lokaci, tadan kara jan guntu tsuki,</p><p> Dariya maganar ta tabani nace aiko Salim yana iya kokarin shi damu yaudai ne akadan samu akasi,</p><p> Sanan kuma kinsan cewa babu yadda za,ayi yan saudiya su yarda da tukin motar mata akasar su,</p><p> Saboda tunkin motar mace yana cikin gurbatar tarbiyan diya mace,</p><p> Kinga ashe su ko bazasu taba yarda abada wanan dokar akasar su,</p><p> Duk wani abinda zai kawo masu lalacewan matasa da gurbatar addini bazasu taba yarda dashi ba,</p><p> Ba muyi wani dan nisa da makarantar ba sosai sai mukaga an park muna wata mota fara sol da ita har farin ta yana cin ido, </p><p> Duk inda mota takai da kyau wanan motar takai can,</p><p> Amal ce gefen da motar tadan tsaya sai salimat na tsakiyan mu nice agefen karashe,</p><p> Nacikin motar yadan zuke glass din motar baki balarabe ne daganin shi matashine saidai ba yaro bane kwarai,, salama yafara muna,</p><p> Da larabci yake magana yace muna may yasa muke tafiya cikin rana haka,</p><p> Muzo mu shiga ya sauke mu gida, mufada mai inda zamu</p><p> Sukan duk sai naga alamar tsoro a fuskan su saboda gani sukeyi zai cuta muna na</p><p> Kallo guda nai mai daga yanayin shigar shi har maganan shi sai nagane cewa saboda Allah ne zai taimaka muna,</p><p> Amal na bude ma gaban motan nida salimat muka shiga baya,</p><p> Basuyi min wani mussu ba duk muka shige ina mai kwatance kawai sai ya gane layin mu ,</p><p> Tundaga nan bai kara ko kallon gefen mu ba,</p><p> Muna shiru mukayi cikin natsuwa har muka isa gidan mu,</p><p> Naimai godiya nafito har zan shige sai yake ce min dan Allah mukama mutuncin mu badadi agan mu asaman hanya haka muna tafiya da kafa,</p><p> Godiya nakarayi mai muka shige abin mu cikin gida,</p><p> A falo sukai min ca waidaga ganin mutun sai kawai insa su fada motar shi, ni bani ganin komotar shi abin kallo ne, </p><p> Daga yau idan zan shigane inshiga ni daya,</p><p> Dariya duk suka bani don sai yanzu nagane nufin su,</p><p> Saida na samu wuri nadan zauna sanan nadan kalli Amal nace mata</p><p> Kinsan abinda yasa ya taimake mu tace a,a nace mata saboda tafiyan da mukeyi dakafa maza na ganin mu wanda hakan baidace ba ,</p><p> Wani wanda baida tsoron Allah zai iya shiga wani hali mara kyau idan yagan mu da kafa,</p><p> Mace abu ce maidaraja da kima ba abin wasa bace,</p><p> Saida na kalle shi tsab nagane cewa ba bu yaudara kishin addini ne kawai yasa yataimaka muna,</p><p> Sai alokacin naji sundayi ajiyar zuciya nace mata ai tana ganin shi tasan cewa badan karamin gida ba ne</p><p> Tsatsan addin ne kawai azuciyar shi,</p><p> Tundaga wanan rana bamu kara yarda mun tako da kafa ba,</p><p> Tafiyan mu da kafa shine zuwa masallaci kawai,</p><p> Salimat cikin ta yanata kara girma saidai tadan rage yawan alolayin ciki yanzu </p><p> Kwadai kawai take so na abu mai sanyi, koda yaushe,</p><p> Zaune take ta ta faman shan ice cream roba roba ta aje agabanta,</p><p> Dakatar da karatun da nakeyi nayi na tsaya kallon ta,</p><p> Ina mamaki yadda take shan ice cream haka a yini batare da yafita ranta ba,</p><p> Dan cikin nata yadan taso sama Allah ya taimake ta rigunan,ta kusan duk dogaye ne in bashi ba daduk basu daukanta,</p><p> Maman Umar ta kawo mata wani dan ruwan shayi mai suna azahab lai, green tea ne kusan matan larabawa idan suna da ciki shi suke yawan sha, don yana rage ma mace yawan zaki da sanyi </p><p> Yanasa baby kuzari tun a cikin ciki, sai ciki yakai kaman wata biyar ko shidda ake shan wanan ganyen shayin,</p><p> Kusan duk wani green tea yana ma mace mai ciki wanan taimakon,</p><p> Zama tayi da cup din tea din a hannun ta don ta tabbatar da cewa tasha tea din </p><p> Saboda ralura cewa bata son shan shayin saidai ice cream kawai komai dare zata fito falo ta zauna tasha sanan ta kwanta,</p><p> Robobin ice cream din na,kwashe gefe guda na ce mata sai tagama shan ruwan shayin sanan inbata abinta, </p><p> Tadan jingina da bango tace min baki ganewa ne Fadima, </p><p> Bawai bani son shayin bane walahi wani irin suya nake jin zuciyana yake min shiyasa kikaga ina son insha ice cream din koda yaushe,</p><p> Amal tafado dakin ta iske muna wanan rikicin da Salimat,</p><p> Tace ma salimat gaskiya tasan cewa mu nan duk bamu san komai gamay da ciki ba,</p><p> Amma tunda maman Umar ta ce mata tadinga sha zai taimaka mata dan Allah tafake da shan shi kada azo asamu wani matsala, nan gaba,</p><p> Salimat tasa hannu ta karbi cup din shayin ta kurbe shi gaba daya,</p><p> Daga inda nake zaune naga tana ya mutsa fuska sai tabani dariya </p><p> Duka takai min tace min ai ita ma watarana zata ramane,</p><p> Kafin inbata ansa sai wayana yashiga ruri alamar kira ya shigo min </p><p> Alin babba ne, tashi nayi niyar yi inda fita daga waje don kada su damay ni da hayaniya</p><p> Amal ce tadan harare ni cimin wasa tace min wazan gudu mawa cikin su, </p><p> Dadariya nabar dakin falo na koma muna waya inata dan dariya na,</p><p> Sam banji alamar mutun ba saidai kaiwa kamshin da ya mamaye min hanci na tako ina </p><p> Ahankali na bude idona sai ko nai arba da sheriff tare da salim tsaye a tsakitan falon namu,,,,,, </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 6⃣3⃣</p><p> BY </p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p> &</p><p> AMINCI WRITERS ASSOCIATION GROUP</p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p> </p><p> Hannu shi ya miko min alamar in,bashi waya na, </p><p> Wani iri naji a,raina don da kamar kada in bashi sai wata zuciya tace min kada shedan ya rude ki,</p><p> Mika mai wayan kurun duk abinda zaiyi ki gani kiji yafi ki,mai taurin kai don sheriff yafi karfin haka gare ki,</p><p> Cikin sanyin jiki na mika mai wayan jiki ba kwari nayi niyar tashi inbar wurin </p><p> Alamar inzauna inda nake yai min shima gefe guda yasamu ya zauna ran shi bace,</p><p> Kashe wayan yayi yadibi noban wanda nake magana dashi , </p><p> Idon shi ya nuna mai cewa Alin ne, zuciyar shi ji yayi kamar Alin na kusa yau yagane kuren shi,,,</p><p> Cikin wata irin murya yace fatima, may yasa wai bazaki min kyakkyawan fahinta ba,</p><p> Wallahi da za ace min kece ke wanan halin batare da nagani da ido na ba bazan taba yarda ba, </p><p> Kifahince ni fatima bada wani manufa nakafa maku wanan dokar ba sai don kwakwarar hujan dake gare ni akan ku,</p><p> Duk kan ku kuna da tabaibayi akan ku wanda yin hakan agare ku babban ilace agareku ,kuna da bambanci mai yawa da da, da yanzu, try to understand me,</p><p> Mace mai shekaru irin naku suna bukatar kulawa da sa,ido akan duk wani motsi nasu, don gudun fada ma halaka,,,</p><p> Wanan da bi,ar bataku bace, na san koke ba lafin ki bane nasan kowaye Alin nakuma san sherin shi, fiye da kowa,</p><p> So don haka ina rokonki fatima daga yau kada kikara barin sherin Alin yayi tasiri azuciyar ki , wanda yin tasirin zai iya ilatar maki da rayuwan ki , agaba,</p><p> Kaina dukar ina kallon kasan falon sai kawai na ji kunyar kaina da kaina, da har na bari shedan da Alin yayi nasara akaina kan kin umurni da kuma dokan da sheriff yasa muna, tun farko,</p><p> Saidai kuma naji sam yananu baya zargina, don haka zargin da naje tunanen yake min yawanke araina tas</p><p> Tabbas sheriff da zuciya daya yadaukeni har cikin ran,shi </p><p> Don gashi ya fada min gaskiya kamar yadda zan iya fada ma Amal ,</p><p> Yakuma rikeni kamar yadda yake rikon ita Amal din,</p><p> Ina fatan zaki fahinci kalamai na da kyakkyawan manufa fatima,,</p><p> Cikin sauri na gyada mai kai na alamar eh nafahinta din,</p><p> Idona da yacika taf da hawaye dama jira kawai sukeyi su zubo suka samu hanyar silalowa, daga idon zuwa saman fuska na,</p><p> Da kyat nadan iya bude bakina nace ma,sheriff dan Allah yayi hakkuri insha Allah ban kara tsallake dokan shi,</p><p> Murmushi yayi mainu alamar dacin rai, yadan gyara zaman shi yace nasan ki fatima nasan halikin wanan aikin bayinki bane aikin Alin ne kuma zanyi maganin shi don yasan halina fiye da kowa </p><p><br /></p><p> Nuna min hanya yayi alamar ina iya tafiya, </p><p> Dan dar dar nayi nayi narashin sanin abinyi tukun </p><p> Kara dagowa ina mai bashi hakkuri,</p><p> Kan sa ya dan rausaya gefe yace pls u can go, ki kula da kanki daga yau, </p><p> A sanyaye ganin idon shi na akai na yau ko kauda su bai yi kamar da, nadan juya a hankali nabar falon,</p><p> Ido yabini dashi zuciyar shi cike da mamakin yadda halittana ya koma cikin dan kankanin lokaci,</p><p> Juyowa yayi inda salim ke zaune yana kallo da sauraren mu,</p><p> Yai wani irin sanyayan ajiyat zuciya, gami da kutawa </p><p> Yace Alin Alin hmm hmm, zamu hadu, dakai,</p><p> Ina shiga daki nafada saman gado ina wani irin kuka mai tsuma zuciya,</p><p> Salimat bata hanani ba saida taga nayi kuka mai i,sata tukun don kaina nadan tsaigaita,</p><p> Ruwa ta miko min tace insha, ba musu nakarba nadan kurba na mayar mata da cup din,,,</p><p> Nakara matse waje guda zuciya tab da takaici da danasanin yarda da naiwa Alin har yai galaba da soyayyar shi akaina,</p><p> Gashi cikin ruwan sanyi sheriff ya walwale min manufar wanda ni nakas fahintar shi tun farko,</p><p> Nadan kara hadiyar zuciya na takaici na ce araina sheriff zai min daukar maiyawan son maza ce ni, kila,</p><p> Sainaji wani irin mugun kunya da nauyi yakamani,</p><p> Salimat ce ta dafani shiru tadan yi nawani lokaci tana mai kura min ido,,</p><p> Suna,na takira a hankali </p><p> Na ce mata na,am a hanakali </p><p> Ido ta kura min tana nazarina ,</p><p> Ta ce min fadima kiyi hakkuri ki daina wanan kukan haka pls </p><p> Sai tai shiru bata kara cewa komai ba kamar mai tunanen wanin wani abu,</p><p> Can sai tace min naganki da sheriff a falo dazu, kuma nasan wanan kukan yana da nasaba da ganin da nai maku din dake dashi da salim,</p><p> Kifada min ko may ke faruwa da ke haka,</p><p> Wani irin nauyi naji azuciya na da kunya, sai na janye hannunta daga dafa nin da tayi,,,</p><p> Karo na biyu ta koma kirana tace min kina jina </p><p>Kar ki boye min komi ki daukeni tankar yar uwar ki fadima,,,</p><p> Wani sanyi naji a raina, naga ai maganar ta gaskiya ce, komai na son abokin shawara,</p><p> Dakyat nai shiru na labarta mata komai tundaga farko har karshe dakuma irin taimakon da sheriff yai min a rayuwata,</p><p> Bakina ta kurawa ido tunda nafara mata bayani</p><p> Cike da mamaki take jin cewa ni ba yar uwa su Amal bace </p><p> Asali ma dai ni yar takari ce ba wata ba,</p><p> Cikin mamaki take kallo na tana nu,nani,tace min fadima ke takari ce takari fa,</p><p> Tai wani dan ajiyan zuciya tace min gaskiya ki gode ma Allah don kin shigo takari da kafar dama,</p><p> Don kisan cewa babu wani abu cikin takari banda kaddarar rayuwa kala kala, </p><p> Don takari da kyata yake sha in har yasamu komawa gida da lafiyan shi yagode ma Allah,</p><p> Ke gashi Allah ya hada ki da dan albarka kin samu har zaki hada digree din ki asanadiyar takari,</p><p> Tace zan baki shawara kamar yada duk wani dan uwa zaiba nashi shawara,</p><p> Agaskiya baki kyauta ba fadima yadda kikayin nan da ace shi ba mai sanyin halin bane zai iya daukan mataki akan ki, tunda ga kaunar shi ma tayi kokarin kiyaye dokan daya sa maku</p><p> Kiyi kokari duk wani doka dakuma abinda zai cutar da shi ko ke ,ki kare shi daga gareshi,</p><p> Takara dan dafa min kafadana tace min kikula fadima duk dokar dayasa maku ki kiyaye shi pls, babu cutarwa acikin shi insha Allah,,,</p><p> Tagumi nayi da hannayena ina kallon ta</p><p> Ina kuka nace mata insha Allah zan kiyaye daga yau,</p><p> Tace min to ki daina wanan kukan hakana kisake jikin ki,</p><p> Asake nace mata to yanzu yazanyi in ba sheriff hakuri </p><p> Tai dan murmushi tace ai yana da saukin kai sosai don da wani ne da abin bai kyau,</p><p> Tace min ki kwatar da hankalinki text zakiyi mai kiba shi hakuri,</p><p> Sai kuma kiyi kokari kisan yadda zaki nuna mai agaban shi cewa ke din diyace kin rabu da Alin din har abada,</p><p> Tadanyi murmushi tace kinga hakan zaisa yasan cewa shi din ya isa dake, kuma ke mai bin umur ni ne,</p><p> A sanyaye nace mata nagode kwarai da kulawar ta,</p><p> Tace min ai itace da min godiya ba ni ba,</p><p> Tunda nashiga ban fito ba dama, </p><p> Nadan gyara cikin wata yar riga da ta matse min jiki tam, nadauko wayana da niyar zuwa falo indan samu wani abu, in ci,</p><p> Sam basan cewa yau sheriff a gidan mu ya sauka ba ganin cewa wancan karon ba,a nan ya sauka ba,</p><p> Ina shiga falon wayana yana tsuwar kira ya shigo ko bandiba ba nassn cewa bakowa bane sai Alin ne</p><p> Shine din kuwa, da sallama ta karba wayan Sheriff dake zaune agaban computer shi yai shiru yana sauraren ta da kuma mamakin abinda yakawo ta falo cikin daren nan,</p><p> Gurin fridge yaga ta nufa tabude tadauko lemun gwaba da corns acikin leda kujera da ke kusa da ita ta zauna,</p><p> Tana shan lemun tana waya sai yagane cewa yunwa yafito da ita yanzu,</p><p> Muryan ta yaji tana cewa adake nan yanzu nafada maka cewa banda lokacin wanan agaba na, </p><p> Sai yaji tadanyi shiru tana sauraren maganar da ake fada mata, tana kurban lemun da ke hannunta tana jefa corn din guda guda a bakinta,</p><p> Tace aiko mada sheriff din ne yace min in rabu da kai yayi gaskiya tunda ya isa akai na, </p><p> Zai iya sani zai kuma iya hana ni, duk lokacin da yaga dama,</p><p> Balle kawai zato kakeyi, sheriff baiko da labarin ina tare da kai, yanzu,</p><p> Kawai ra,ayi nane in maida hankalina a karatuna indaina bata lokacina </p><p> Don ni ba yanzu zanyi aure ba ,,,</p><p> Haka mukayi ta musayar magana daga karshe nai warning din shi cikin kakkausar murya akan daga yau kada ya kara kirana pls,,</p><p> Idan kuma yakara zan fada ma sherrif don yadaukan min mataki akanshi,</p><p> Murmushin takaici naji tayi yace ai baku isa ba daga ke har Ahmad din, </p><p> Nace mai Allah yafika Alin duk yadda kaso ka cutar da ni Allah bai yarda na,kashe wayan ina ta fada kamar yana a fili inda nake,,,,</p><p> Sheriff yasan cewa ban gashi ba har nagama natashi zuwa cikin daki abina,</p><p> Cikin tausayin hali irin nawa yabini da ido har na shige part din mu,</p><p> </p><p> Cikin dare nai mai text nabashi hakuri nakumayi mai alkawarin cewa bazan kara yin abinda baiso ba insha Allah,</p><p><br /></p><p> Hindu na zaune tana fuskantar aziza wacce du ta dan ta da hankalinta,</p><p> Cikin tausa murya tace ma aziza gaskiya kamata yayi kisan yadda kikayi dabaran janshi kuje wurin likinta da yasan kan ciki sosai </p><p> Tunda naga ke kina ra,ayin hakan,</p><p> Hindu gaskiya ban son inyi loosing din Ahmad a rayuwa na don naga alamar in banyi da gaske ba wanan maganar na iya kawo muna matsala arayuwar mu, nan gaba,</p><p> Aziza na fada maki cewa ki kwantar da hankalinki tunda har kina son mijinki zan yi iya kokari na inga cewa kin mallaki baby, tare da shi,</p><p> Sundan dade suna ta tattaunawa akan yadda zasu shawo kan sheriff zuwa wurin wani likita a kasar indiya, wanda zai diba su da ita dashi,</p><p> </p><p> Bayan kamar sati yai mata waya cewa zai je Nigeria gurin Nafisat, </p><p> In akwai abinda taki jini shine taji cewa wai ita aziza tana da kishiya, </p><p> Don ita arayuwa bata kaunar kishiya sam koshi don son da take mai ne yasa har ta amince </p><p> Kuma ganin da tayi cewa shi ba mazauni guri daya bane,</p><p> Yadda sukayi da aziza haka sukayi da Nafisat akan haihuwa, itama din tadan shiga cikin rudu, </p><p> Don ta tabbatar da cewa sai Allah in mahaifar ta na iya daukan ciki saboda yawan kwayoyin da tasha tun tana yar secondary tafara harkan shan kwaya,</p><p> Wanda ansha warning din ta cewa zai iya mata illa amatsayin ta na mace,</p><p> Don haka maganar ya tayar mata da hankali, </p><p> Tunda safe ta ziyar ci wani likitansu inda yaba ta appointment cewa taje tadawo aimata gwajin agani ko zata iya daukan ciki,</p><p><br /></p><p> Saura kusan shekara guda yarage min inkare karatuna, don haka ba bu kama hannu yaro, babban burina shine nagama da sakamako mai kyau </p><p> Danagama in wuce Nigeria wurin yan uwana da iyayye na ,</p><p> Don babu ranan da ban tunawa da inna a cikin rayuwata,</p><p> Karatun sai yazamamin biyu saboda salimat cikin ta ya tsufa sosai yai mata wani irin girma kamar cikin ta gwaye,</p><p> Duk zaman da takeyi agidan mu bata taba haduwa da sheriff ba sai yau , koda ya iso itace zaune dirsha afalon mu duk da sanyin A C dake ta aiki a falon ita sai zufa takeyi,</p><p> Duk kan mu munfito muna mai sannu da zuwa yazauna yana kokarin cire sock din dake kafar shi, </p><p> Drinks nahado mai a ture na zo na aje mai gap da shi,</p><p> Wani irin kamshi da sanyin A C suka hade suka canja launin shakar mutum </p><p> Yadda naji nashi kamshin shima haka yaji nawa kamshin cikin kasala ya dan kara dukowa yadauki cup da niyar zai zuba ma kanshi sai hannu mu suka hade wuri guda da sauri naga yaje hannu shi yana fadin </p><p> Subbahanallah, cikin lunshe idon shi duk wanda ke falon saida yadan waigo mu,</p><p> Na tsiyaya mai ahankali yakarba tare da fadin Shukuran,,,</p><p> Sock din kafan shi da yacire don ya dan sha iska na duka gefe ina tsincewa, mangashin da nai gyaran kaina na dashi ya kara shaka,</p><p> Tun lokacin yadan ritse idon shi cup din drink rike a hannun shi,</p><p> Salimat ce tayi kokarin tashi daga inda take zaune sai ta kasa dariyan da yaji na Amal yasashi dan bude idon shi daga zurfin tunanen da yashiga,</p><p> Abu kamar wasa sai salimat takasa cire kafar ta ga sheriff a falon duk mun rasa dabaran da zamuyi don ta samu ta tashi don tashi da kyat takeyi,</p><p> Dan tabur din da ke gaban sheriff nainiyar indan tura dakafa idan yaga haka zai maida hankalinshi ga tebur din har salimat tasamu ta daga don naga kunya take ji, </p><p> Sainai rashin sa,a nafada dani da tebur din duk saman jikin sheriff wanda ke zaune yana waya,</p><p> Ji kawai yayi nafado mai a jikin shi babu shiri gaba daya na,</p><p> Wani irin yarrrrrr gaba dayan mu muka, naso in mike sai dan kune na ya lake mai a aljihun rigar cort din shi tagaba,</p><p> Duk kamshi kaina yana shaka a hanncin shi,</p><p> Wanan karon bai samu kiran subbahanallah din ba </p><p> Rikeni ya dan yi gam ajikin shi yadda har muna iya jin hucin junan mu, yasa hannu shi guda yazagaye ni dashi, a hankali ya cire dan kunin a jikin rigan shi,,,</p><p>Duk wanan abin rabin Idon shi a lunshe yake,</p><p> Salimat har tasamu tadaga ,</p><p> ni ba,a sake ni ba,</p><p> Sai can yadan sakeni a hankali yace min are u, ok, </p><p> Kai kawai na iya kada mai tare da mikewa tsaye cikin sauri,</p><p> hannun shi na rike da ni har saida yaga na mike da kyau , ya sake ni a hankali,</p><p> Sai yace min b/careful</p><p> Daga haka sai, yamike zubur yadauki wayan shi dake saman hannun kujera yayi hanyar waje,</p><p> Alokacin ita kuma, Amal tasa min wani irin mugun dariya tace min daga zuwa taimakon salimat gashi nan natashi jin ciwo,</p><p> Inbadon a jikin yayan su nafada ba da tabur din yajin man ciwo abanza,,,</p><p> Duk maganan da takeyi ban fahintan ta saboda wani abu da na,ke jin yana , min yawo ahankali cikin jikina har kwakwalwana ,</p><p> Abinda bantaba sanin ana,jin shi a rayuwa ba yau shi ne naji ga jikin sheriff din,</p><p> Har takaraci dariyan ta tagama ban ce mata uffan ba </p><p>Saboda weak din da jikina yai min,</p><p> </p><p> Yanafita waje cikin mota yashiga da niyar ya bar gidan ko yasamu dan relief a zuciyan shi,</p><p> Don tunda yake bai taba jin irin wanan yanayi ba,</p><p> Don dai da shi yadauka cewa duk mata iri daya ne ba banbanci,</p><p> Ama yau yafara shedawa cewa akwai banbanci sosai a tsakanin mata,</p><p> Shi bai tada motar ba kuma shi bai fito ba,</p><p> Ahaka salim yazo yasa may shi zuwan salim din ne har yadan yi kokarin saita kanshi,</p><p> Suka fita cikin gari da salim din, dole badon yaso ba yau salim din ne mai jansu a mota,</p><p> Don shi jin shi yakeyi kamar duk an zare mai lakkan jikin shi gabadaya</p><p> Barci daine barawo har ya iya dauka na don da na rintse idon abinda yafaru nida sheriff nake gani, </p><p> Duk na rasa sukuni sai juyi nakeyi kamar wacce, ake muntsula, ajiki</p><p> Da haka har barci ya sace ni cikin wanan yanayin, </p><p> Washegari tunda safe natashi nafada kitchen don in hadawa sheriff abin karin kumallo don idan yana garin ko in munje hutu makkah nice mai yi mai duk wani hidimar da ta shafe shi,</p><p> Don kowani yayi mai yakama korafi ke nan kamar zai tashi sama, </p><p> Amal bata so sam tasa hannu ga duk wani abinda yashafi aikin sheriff din,</p><p> Don gudun korafin shi,</p><p>Nasan cewa yanayin aikin su na madina tunda safe suke fita su dawo zuwa karfe dayan rana,</p><p> Shiyasa nake tashi da wuri in mai break fast,</p><p> Ina gamawa na fada dakin mu don indan watsa ruwa a jikina,</p><p> Salimat ce na iske cikin wani irin yanayi, naban tausayi,</p><p> Gurin da take na nufa cikin sarsarfa, tana kasa kusa da hanyar shiga bayin mu</p><p> Ta dan zauna tayi dai,dai da ita tana maida nunfashi guda guda,</p><p> Dasuri nakarasa gurin ta ina mata sannu,</p><p> Kai kawai tadan daga min alamar ansawa ta na cizon bakin ta da kyat sai gumi dake ta zubu mata kamar an,tsa mata ruwa,</p><p> Duk sai na firgice na duka saitin ta ina mata sannu,</p><p> Tace min cikin karfin hali fadima kila haihuwa zan yi,</p><p> Ido waje nace mata what cikin karfin hali ta daga min kai,</p><p> Nace to barin kira maman umar tazo muje asibiti ko,</p><p> Har nakai kofa sai naji tayi wani irin nishi gami da salati mai karfi,</p><p> Aida sauri nayo kanta ina fadin sannu salimat</p><p> Wanan karon bata karba min ba ido kawai ta zuba min duk sun firfito waje,</p><p> Sai naga tafar wani irin nishi makarfi</p><p> Da sauri na rungumay ta ina kokarin daga ta sai naji duk taimin wani irin nauyi, kamar ba salimat ba,</p><p> Kafin in kifta ido har ta sullubo yar baby ta tana fama calara ihu irin na jarirai,</p><p> Wani irin mugun tsoro naji yakamani, don bans an abinda zan iya taimaka mata dashi ba,</p><p> Idonta a lunshe tana hamdala tace min fadima kira maman umar da sauri tazo</p><p> Aiko aguje na kwasa da gudu na manta sam banda wani rigan kirki ajiki, </p><p> Sai falo ina ihun kiran maman umar,</p><p> Suna falo suna break sukaji ihu na kowa sai ya watso min ido don jin komai yafaru hankalinsu tashe,</p><p> Da sauri maman umar tafito kitchen din cikin rikecewa,</p><p> Mu kaci karo a kofar kitchen din da ita, </p><p> Ina haki nace salimat ta haihu,</p><p> Duk a rude suka tashi tsaye cikin mamaki suna kallo na,</p><p> Maman umar da sauri ta shiga dakinta ashe ita dama da shirinta take,</p><p> Muka bita diiiii abaya sai dai wanan karon akofa na tsaya munajin baby nata tsala ihu duk ta karade gidan ,</p><p> Sai da tagama gyara su sanan ta miko muna yar baby fara sol da ita kamar uwarta, an nade ta cikin farin shawul,</p><p> Amal akafara ba sai ta wuce direct inda Sheriff yake tsaye nisa da mu cikin damuwa,</p><p> Saida yakare mata kallo ban sha,awa sanan ya kalli gefen da nake tsaye yace min indauko mai dabino da ruwan zam,zam cikin sauri natafi na debo mai su nakawo mai</p><p> Na iske yanawa baby kiran sallah da yagama yakarbi dabino yadan tauna yasa mata abaki,</p><p> Yakama dan lasa mata ruwan zam zam din,</p><p> Saida yagama yadago kai mukayi arba dom dama duk mun kewaye shi,</p><p>Da sauri na dukar da kaina kasa</p><p> 🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>,✈✈✈TAKARI✈✈✈ </p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 6⃣4⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p> 🐎 HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost true life story,</p><p><br /></p><p> Saida komai ya lafa, ne kowa ya dan natsu guri guda, </p><p> Maman Umar tagama gyara komai sai ,Sheriff din ya shigo dakin don yaiwa salima sannu da kuma barka da arziki,</p><p> Ina kitchen naje hada mata abincin da zata dan ci , abinci mara nauyi nai mata,</p><p> Sam basan cewa ya shigo dakin ba don da banshiga ba alokacin,</p><p> Salimat nagani na ta ce min sannu fadima da kokari,</p><p> Nagode kware da hidimo min ki,,</p><p> Gare ni Ubangiji Allah ya baki miji na gari,</p><p> A kunyace na ansa mata da amin aiba komai,</p><p> Sai alokacin nagan shi tare da su Amal da Salim suna ma baby wasa,</p><p> Amal tace aidole ki godewa Fadima salimat, tunda itace yau nurse mai karban haihuwa </p><p> Cikin mamaki Sheriff yace, what fatima, yana mai dan nuna ni da yatsa yace </p><p> Yace interesting nd welldon,</p><p> Ke yar karama da ke har kin iya karban haihu kuma agida,</p><p> Dan murmushi nayi gami da sadda kaina kasa,,,</p><p> Amal tace ai fadima tayi kokari don daini gaskiya bazan iya ba,</p><p> </p><p> Sheriff yace gaskiya dole a,tafi asibiti da baby da uwar don adiba lafiyan su</p><p> Yadan kalli gefen da salimat ke zaune tana wani irin zufa yace mata kin san kunyi kasada kware don haihuwa ya tatare da matsala acikin shi</p><p> A sanyaye tace wallahi sheriff a bazata abin yazo min don ban dauka cewa haihuwa bane,</p><p> Allah yasa fadima tazo itace ta taimake ni,</p><p><br /></p><p> Acikon mota sheriff zaikai mu asibiti tare da Salimat da baby ta,</p><p> Amal ta mika min baby tace in zauna da ita agaban mota itada Salimat su shiga baya,</p><p> Ahankali yake tuki motar sai kira,an dake tashi nawani dan saurayin matashin balarabe,</p><p> Baby tai dan wani hirgita kadan tare da ajiyan zuciya madan sauti,</p><p> Cikin sauri sheriff yadan duko inda nake zaune da ita ,yadan kware showul din yana diban fuskan babyn </p><p> Wace ke ta sharan barci abinta,</p><p> Amal na kallon mu daga bayan mota da suke zaune, daidai lokacin ta dauke mu hoto a hanka, batare da sani na ba</p><p> Saida muka je aka diba lafiyan jariri da na uwa aka tab, batar da duk suna lafiya,</p><p> Sheriff ne da kan shi yabuga ma mijin salimat waya yasheda mai cewa salimat ta haihu,</p><p> Sunyi mamaki sosai don duk dauka akeyi ba month din haihuwanta ba ke nan,</p><p> Ba karamin kokari sheriff yayi ba saikace shi akaiwa wanan haihuwan </p><p> Satin ta biyu a saudiya mijinta yazo yadauketa zuwa Nigeria ,</p><p> Yai muna godiya sosai kafin su wuce , duk bamuso su tafi da baby Asma,u, ba wai sunan mahaifiyar mijin ta ke nan,,,</p><p> </p><p> Karatun mu mukaci gaba dayi duk da bawai dogon lokaci yarage muna ba,</p><p> Saidai karatun namu sam bai hanamu yin ibadan mu ba,</p><p> Ko yaushe muna zuwa muyi sallah idan an idar da sallah mushiga muyi ziyara </p><p> Mufito wani lokaci kuma salim ne zai kwashe mu ga mota yakai mu baki,ya muyi ziyaran kaburbukan bayin Allah da sukayi sha hada,</p><p> Ina son zuwa ziyara a bakiya don ko ba komai zakaji wani karin imani nashigan ka,</p><p> Don zaka dinga gani kamar ace sahaban manzon Allah SAW dake kwace cikin wanan makabartan zasu tashi ka gansu, </p><p> Sai mutun yaji indan ana bada tarihin su kamar ace shima a wanan lokacin aka halicce shi yazaman to a cikin su,</p><p> Gurine da akayiwa security ankewaye shi da waya saidai ka tsaya ko kuma idan zaka iya hawa dutse ka,hau kaje kai masu addu,</p><p> Salim yana yawan sha,awar zuwa ziyara a bakiya, don kusan duk ranan alhamis sai yakaimu ziyara munyi masu addu,a tare yiwa kan mu ,muma fatan cikawa da kyau da imanin ubangijin mu,</p><p> </p><p> Za,zaune muke duk kan mu cikin falon muna hira, kamar yadda muka saba yi indan weekend ne zama mukeyi inda mun dawo daga masallaci ayita hiran rayuwa</p><p> Yau,ma hakan ce ta kasan, da mu,</p><p> Amal ce zane a tsakiya ta magana wayanta yana a hannun ta tana dube dube,</p><p> Photo na dake cikin wayan ,sai idon ta yakai ga wanda tai muna ni da sheriff da baby Asma,u, wace muke ce ma husna,</p><p> Saida tadan tsaya taima hoton kallon tsab sanan take gwada muna,photo,</p><p> Mamaki yakamani kware daganin picture don basan lokacin da ta dauka, ba,</p><p> Idan ka gan mu a cikin photo zaka zaci cewa ko wasu ma,aurata ne nida shi,,,, </p><p> Salim yace kai dama ace wanan baby na yayan mu aida basan irin farin cikin da zaiyi, ba,</p><p> Kusan koyaushe sai yai min korafi akan yana son haihuwa , yana son yasamu baby shima,</p><p> Ace ai wanan baby shi don yace hjy tsohuwa tana yawan yimai korafi indan sun hadu,</p><p> Amal tace banga wace ke shirin haihuwa ba cikin wa yan nan yan gayun mata nashi,</p><p> Tace du matan nashi ni gaskiya basuyi min ba babu wace ta dace dashi acikin su,</p><p> Sai lokacin nasa masu baki a,zancen su, da sukeyi </p><p> Nace ,a a Amal ai aure mukaddari ne matan mutun kabarinsa,</p><p> Aiko duk matan nashi suna son shi kuma idan lokacin haihuwan su yayi ai zasu haihu komai fa dan lokaci ne,</p><p> Daga haka ban kacewa ufan ba, daga zancen nasu,</p><p> Wanan zancen yasa naji duk tausayin sheriff yakamani nai alkawri araina insha Allah zan sa shi a,addu,a ta, koyaushe,</p><p> </p><p> Aziza ce zaune duk ta rikita mai lissafin shi adole sai sunje sunga likita a kasar Germany, yadibata</p><p> Saida yagama jin korafinta yadan yi murmushi yace aziza mubar ma Allah zabin sa idan lokaci yayi sai yaba mu bawai sai munje muna ta nuna rashin tawakkalin mu akai ba,</p><p> Allah da yayi mu bai manta da muba,</p><p> Ganin da yayi shima dai din yana son yaga baby shi a duniya yasa har ya amince mata</p><p> Bayan aune aunen da sukayi likita yatabbatar masu cewa lafiya lau, maigidan yake kuma ita ma din zata iya samun ciki saida akwai wani abokin shi dan kasar indiya yafishi kwarewa ta wanan fan,ni sosai,</p><p> Don haka yace suna iya zuwa su ziyarce shi,</p><p> Bayadda aziza batayi da sheriff ba amma yace shi tunda lafiya lau yake bai zuwa ko ina,</p><p> Itada hindu sukaje gani doctor Khan a indiya din bayan duk wani awo da zai mata yayi ya,kam,malla ne yake sheda mata cewa, agaskiya mahaifarta bazata iya daukar ciki ba da kanta saidai inda zata yarda ai mata artificial insemination, to ko shi din sai kila ne cikin zai iya tsaya mata,</p><p> Haka suka dawo gida cikin tashin hankali ,don tasan cewa idan ko har baza ta haihu ba , ba makawa sai sheriff ya kara wani aure tunda nafisat itama har yanzu gata can shiru ba wani labarin ciki,</p><p> In akwai abinda bata kauna shine taga Ahmad dinta, da wata mace koda ko abokiyar aikinsa ce,</p><p> A ranan tashi yi mai mita ke nan , shi mamaki ma take bashi, saboda irin mugun kishin ta,</p><p> Tun ajirgi take ta rusawa hindu kuka, hindu tai rarashin kawar nata har tagaji,</p><p> Jiki ba kwari tadawo mai a Dubai suka hadu yana ganin ta tagane cewa batai nasaran tafiyan ta ba ,</p><p> Shima dai din cikin zuciyar shi baiji dadi ba, </p><p> Saida dare bayan sun gama komai sun kwatane take mai bayanin da likita yai mata, saida ta boye mai cewa ance ko artficial insemination din bazai zama dole ya tsaya mata ba,</p><p> Tana kai karshen zance yamike har zaune daga kwancen</p><p> Yana fadin tir Subbahanallah wa,iyazu billahi </p><p> Ai wanan rashin imani ne da kuma aikin jahilci, taya za ace mutum bai imani da Allah ,</p><p> Idon shi yai ja sosai don irin masifan da yake ta balballa mata,</p><p> Yakawo mata aya da ku hadisai masu kashe jiki,, yai mata,</p><p> Rai bace sukayi barci a wanan ranan batare da kowa ya kara cewa tak ba,</p><p> Tunda safe ya shirya tafiya a ranan saboda bacin rai yabaro Dubai din zuwa saudiya,</p><p> Satin shi guda ta wuce Nigeria saboda wayan da akai mai cewa hjy tsohuwa ba lafiya sosai,</p><p><br /></p><p> Yana zuwa yaga irin yanayin da take ciki yasa adauko ta zuwa asibitin Abuja,</p><p> Cikin ikon Allah hjya tadan samu sauki,don tasamu kulawa sosai, </p><p> Acan Abujan ma bai tsira daga fitinar nafisat ba don ita ma din so takeyi suje suyi gwajin haihuwa ita dashi don aji ko may ye matsalar,</p><p> Shi mutun ne mai kokarin fitar wa natare dashi da hakkin zaman tare,</p><p> Don haka baki zuwa ba bayan da likta yai ma su shiya tayar wa nafisat da hankali,</p><p> Inada yace masu mahaifar ta ya samu matsala drug's din da take sha yasa ba zai taba iya daukan ciki ba,</p><p> Cikin takaici suka iso gida ga kukan da nafisat ta i she, shi da shi </p><p> Suna shiga gida tazauna tai tagumi hannu bibiyu ta ta zub da hawayen bakin ciki,</p><p> Tunda ya ajeta ya fita bai dawo gidan ba sai cikin dare yadawo,</p><p> Zuciyan shi duk ta jagule mai,</p><p> Duk kan su, su,biyu kusan case din su guda ne, ba zasu iya daukar ciki dan dama azizan da yake tana kan tracings na doctor ne tukun,</p><p> Yana sa ran cewa zata iya samun ciki indan har Allah yakawo,</p><p> Hakuri nafisat ta kama bashi akan don Allah yayi hakkuri kada ya bari iyayyen ta suji wanan zan ce, </p><p> Bai samu ce mata komai ba saboda bacin rai,</p><p> Tunda safe yaje gidan Bashir don yagaida hjy tsohuwa don tace sam bata zuwa gidan nafisat ta zauna</p><p> Saboda hakane aka kaita gidan bashir din don ta zauna can</p><p> Bayan sun gaisa ne da hjy sai ga ya shigo dakin dauke da,yar diyar shi tana wasa da fuskan baban nata,</p><p> Sheriff Ahmad ya mika hannu don yadauke sai taki, zuwa, ta kara rungumay mahaifin nata,</p><p> Bashir yadan hada kai da fuskan yar yarinyar yace, baki zuwa daddy ya,dauke ki ko,</p><p> Dariya yar diyar tayi na kuyya,</p><p> Hjy dake kwance gefe tace, yanzu Alhaji karami ba zan ga zuriar ka ba , sai bayan na mutu,</p><p> Sai tadan kama kuka kamar wace akai ma wani abu,</p><p> Dakyat suka samu suka lalabata shi da bashir, har tai shiru yai mata alkawarin cewa,</p><p> Insha Allahu zata gani bama zata mutu ba sai ta yi ta goya mai zuri,an shi,</p><p> Dahaka tadanji sanyi ,sanyi tai shiru tana fadin Allah yasa Allah yasa,</p><p><br /></p><p> Amal ce ke son muje makkah mudan yi hutu can ni na rasa may yasa yanzu Amal ke son muje makka hutu,</p><p> Badon naso ba nashirya muka tafi, muka rufe gida sai makkah </p><p> Cikin dare muka isa garin don haka kowa dakin shi ya nufa saboda gajiya ga dogon tafiyan da mukasha,</p><p> Dasafe natashi da dan ciwon kai don haka ban fito ba barci nakoma yi,</p><p> Sai da rana yayi so sai na samu kan nawa yadan dai,na min ciwo,</p><p> Nafito cikin wani buje da riga yar rigar ta matse min jiki duk suran jikina yafito da kyau,</p><p> Sai bujen rigar da yani bude kamar dawisu daga kasa, shi gyalen jayan ne nadan yi rolling akaina, sai takalmana plat shoes da nasa akafa na,</p><p> Abinci na yana a cikin cooler saman tebur saboda dama nasan cewa any time natashi zan iske abin karin nawa da zafin shi,</p><p> Sam na manta cewa yau weekend ne Sheriff nagida yau baya fita ko ina sai massalaci kawai zai,sa,shi fita gidan,</p><p> Na zauna kenan zan fara cin abinci Salim yafito yace min yajikin nawa </p><p> Saida naja kujera na zauna tukun nace mai naji sauki dama gajiyan jiya ne kawai yan sa min ciwon kai,</p><p> Har zai fita nace mai dan Allah ina son in nagama yaikaini kundifal zan je in dan siyo wasu yan kaya ne da na manta bandauko ba,</p><p> Salim yace min zasu fitane da mustapha yanzu,</p><p> Cikin rashin damu nace mai ba matsala zan tafi da taxi idan na kare ai,</p><p> Ina ganawa na gyara jiki na tsab ba inda zaka iyagani surar jikina a waje don na rufe shi lif,</p><p> Taxi natare da niyar in shiga zuwa kundifal sayen kayan kwaliya irin na mata ,</p><p> Har zan bude motar naji maganar Sheriff a bayana yana cewa</p><p> Cikin dakarkiyar fuska yake ce min ina zan je batare da izini ba duk sai na dan dabur ce,</p><p> Don nasan cewa ina fita ko ina ai batare da fada ma kowa cewa ga inda zani ba,</p><p> Balle ma ni yar takari ba lasi,. </p><p> Aiko ina zan iya kutsawa dan nema kudi cikin gari batare da wani shamaki ba,</p><p> Wata zuciya tace min kidibi kan ki a,yada kika koma yanzu, ba da bane </p><p> Kina da ban banci sosai da da din,,,</p><p> Naba mai taxi hakkuri yatafi najuya da niyar komawa cikin gida </p><p> Sai dai ina ina kaiwa tsakiyan compound din gidan naga yafito da wata, </p><p> Landrover jeep let's one ban ma ko taba sanin yana da ita sai yau nagan shi da ita,</p><p> Bude min gidan gaba yayi ta gefen shi na zauna,.</p><p> Nasan cewa mawuyacin abune sheriff ya ja mota da kanshi saidai aja shi,</p><p> Ina zama ya sa lock yakule ko ina , wani irin sanyi da kamshi motar keyi,</p><p> Batare da ya kalle ni ba yace min ina zan tafi ne ma wai,</p><p> Cikin murya kasa, kasa nace mai ka Kundifal plaza zani,</p><p> A hankali yake tukin motar cikin gwanewa kira,ar sudes na tashi a hankali don kusan ko yaushe kira,ar shi yake sawa a motar shi,</p><p> Natakure wuri guda cikin rashin wal,wala, saboda bawai nasba dashi bane har yanzu,</p><p> Dan dama dama idan su Amal da salim na kusa nikan dan sake jikina kadan in suna hira insa baki,</p><p> Tambayar bazata naji yai min saura wata nawa mu kare school, cikin dan in,da,inda nace ina ganin kamar takwas yarage muna nace mai,,,</p><p> Yace o iam not even sure gani kawai nakeyi ko,</p><p> Abinda yasa ni dan yi murmushi ke nan yau a gaban shi ,</p><p> Nace takwas din daine kawai,</p><p> Zaiyi wani magana wayan shi tayi tsuwa alamar kira yashigo mai,</p><p> Nikan sai na maida hankalina saman titi ina ta kallon manyan gine ginen da ake tayi acikin gari ina mamaki irin cigaban da kullun aje samu agarin,</p><p> Agaskiya gwaunatin saudiya na kokarin wurin kula da jin dadin al,uman kasan don komai na,zamani su na kokarin su yi shi akasan daidai yadda bai saba ma shari,a ba,</p><p> Mun kusa kawai wane hankalina yakai ga wata yarinyar takari yar baka da ita tana tallan kaya a saman hanya duk tayi zufa saboda rana gata kuma a tsorace take don tana yi tana waige waigen yan bagaladi,</p><p> Tausayi yarinyar tabani don da gani yar sabon shigane,</p><p> Wani irin ajiyan zuciya nayi wanda har ya dan baiyyana afili,</p><p> Shima yana lura da hankalina yana gurin yarinyar da nagani yasan cewa dole in tuna wani abu dama,</p><p> A hankali na furta Alhamdullah, wanda ban tsan mani zai kai a kunen shi ba saboda dan rage karan kiran da ya yi lokacin da zai fara waya,</p><p> Kallona naga yayi cikin sauri yana mai dan lunshe ido yana sallama da mai wayan</p><p> Wanda nake kyautata zaton aziza ce don naji yana cewa saita zo din, </p><p><br /></p><p> A cikin shago sashen saida kayan mata naje nadan zabo abinda nake bukata,</p><p> Sheriff ne na hango can layin saida kayan mata expensive one yanata dibawa yana zabe, </p><p> Tsayawa nayi ina kallon shi da mamaki a raina nace ashe dama shima zaizo sayayyane, a gurin,,,</p><p> Kallin shi kawai nakeyi da naga yayi layin saida gold ina binshi a baya ahankali ,</p><p> Wasu yan kune da sarka masu kyau Dubai naga yadauka, yamika mamai binshi abaya asa a gram,</p><p> Saida yagama ya,hada kudin dana wanda nadan zaba, ya biya, aka kai muna kayan har cikin mota,</p><p> Bayan mun shiga mota ne nafara yi mai godiyan kayan da ya biya min</p><p> Hannanu shi yadaga tare da rike min yan yatsuna da nake kokarin yi mai godiya yana ce min la,la,la,</p><p> Basai nai mai godiyaba yace duk abinda yai min kamar yaiwa kanshi ne don na can can ci hakan agare shi,</p><p> So daga yau duk abinda yai min baya son in kara yi mai godiya ko kadan,</p><p> Yana mai kallon gefena yace nagane ko nadan gyada kai a hankali alamar eh,</p><p> Inba mafarki nayi ba to tabbas yadan murza min karshen yatsa na abinda yasani cikin dan rudani kadan ,</p><p> Koda muka isa gida na dan tsaya na kwashe mai kayan da nasawo na hada da nawa,, </p><p> ban kawo ko mai a raina ba </p><p> Zan shiga ke nan naga motar Almustapha da salim a,she har da Amal suka fita ban sani ba,</p><p> Gani da kaya niki,niki a hannu na </p><p> Mun rigasu shiga ciki sai nawuce daniyar in kaimai kayan part din shi tsayawa yayi yana kallo na da mamaki yace min ina zan kai kayan </p><p> Tsaye nayi sororo nadan kali kayan shima na kale shi sai yace in tafi dasu duk nawa ne,</p><p> Cikin mamaki ido bude nake kallin shi,</p><p> Jin tafiyan su Amal dayayi shigowa yasa shi shigewa part din shi nan nadan tsaya sororo da mamaki </p><p> Wai yau ni fadima yar takari keda wanan kayan alfarman dana ga ansiya a,kundifal,</p><p> Jiki ba kwari na wuce dasu dakina kafin su Amal, su shigo ciki,</p><p> </p><p> Sai cikin dare na bude kayan nadiba gaskiya saida gabana ya fadi sosai gani irin kayan da sheriffudeen din mu Ahmad ya saya min,</p><p> Dan kit din gold din na bude inata shafan set din a hankali,</p><p> Tex nagani ya shigo min a wayana, </p><p> Kaman kada in karanta sai na bude short note ne kamar haka </p><p> Wear d blue dress tomorrow morning ,,,</p><p> Da sauri nakai kallona ga blue dresses din dake gabana, nadan daga shi wani dogon rigane mai shegen kyau na yan lebon, ka taushi ga santsi, </p><p> Dogo ne har kasa da wani irin aiki a gaban rigar da fararen duwatsu, sai dan gyalen shi da ribon dake makale a jikin shi,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 6⃣5⃣</p><p> BY</p><p>🐎 ZAINAB IDRIS MAKAW🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost true life story,</p><p><br /></p><p> Bakaramin mamaki text din yabani ba saidai ban gama mamaki ba naji anturo min kofar dakina,</p><p> Firgigit nayi natura kayan gefen gadona na zauna kamar ba komai nakeyi ba,</p><p> Amal ce tashigo dakin da murmushin ta zo har inda nake tadan zauna bakin gado tace min,</p><p> Ashe baki barci ba nace mata eh, saita ke ce min yanzu yayan mu ke fada min cewa wai gobe akwai inda zamu da karfe, hudun marance,</p><p> Sainake cewa ko kin sani shine yace min yafada maki ai kin san da zancen </p><p> Mamaki yakamani tunda nasan cewa bai fada min komai ba,</p><p> Iyaka ce min yayi insa blue din kaya gobe kuma bai fada min komai, ba ai,,,</p><p> Washegari sai ban fito ba har wani lokaci ina daki ina karatu abina kusan ba wani abin da zan bukata wanda babu shi,</p><p> Aisha ce tazo min dakin da kukan ta wai umar ya dake ta,</p><p> Dole natashi nafita daga buyar da nakeyi yau, agidan don kusan ince </p><p> Yau ba wanda zaice yagani acikin gidan sai maman umar da taji shiru tabiyo ni dakina da abinci na tace min inci</p><p> Ta hanyar baya nabi don kada su gan ni cikin rashin sa,a sai gashi na hade da salim </p><p> Murmushi yaimin kadan yace wai fadima maye sirin ne kulun fa sai kara girma kikeyi da kyau,</p><p> Salim baka gajiya da zolaya kai ni yau ko mirrow ban diba ba bale in gyara fuska na,</p><p> Kafin inkai wurin Umar din saigashi yasamay mu inda muke tsaye da salim,</p><p> Nadan mai fada akan ya daina saurin dukan mutun ,</p><p> Idan yasaba ba zai ji dadi ba nan gaba in ya girma,</p><p> Nan na fara ba salim labarin marin da Almustapha yai min lokacin da na raki hajiya tsohuwa dawafi,</p><p> Salim yadinga yi min dariya kamar a lokacin abin yafaru, </p><p> Nima dai dariyan na kama nacigaba da fada mai yadda nadinga ji kamar in rama marina in gudu alokacin</p><p> Salim yana nunani yana dariya yace fadima an fada min cewa bakyaji kina karama sosai,</p><p> Dariya muka karasawa gabadayan mu nayo baya da niyar in dan waiga gefen tsuntaye na ingani sai naci karo da </p><p> Sheriff tsaye cikin wasu yan kananin kaya sunyi matukar daukan shi kamar shi yayi kan shi,</p><p> Fuskan shi atamke babu alamar dariya cikin dan dukawa nayi cikin ladabi na gaishe shi,</p><p> Batare da ya ansa ba yake ce ma salim yabi yo shi sutafi,</p><p> Saida naga sun bace min azuciya na ce bahagon mutun ba,a gane gabas dinka sai kaso,</p><p> A falo nukayi kicibis da Amal tace min kin gama kwanciyar dakin kin fito ne,</p><p> Murmushi kawai nai mata don nasan komay zance mata bazata yarda ba sam </p><p> Ita madai din shi tabi ni dashi tana tafiya tace min fadima karfe uku da rabi zan shigo wurin ki mu gyara jikin mu don tafiya zuwa wajen walimar da za,ayi na yan African Youth Found mazauna saudiya saboda tallafawa yan uwa musulumi kasa shen,baka ken fata ,</p><p> Nace mata to a zahiri </p><p> Amma cikin zuciya sai cewa nayi wanan ba wurin zuwan yar takari ba ce saidai ku masu hali,</p><p> Bama zan koyi rigimar cewa zan tafi ba tunda ko mai gidan bai sheda min ba,</p><p> Kuma na hadu dashi dazu bai ce min komai ba kenan wanan fitar bai shafe ni ba,</p><p> Saidai in ita Amal din keson ta kasa dani,</p><p> </p><p> Hakalina naga littafin da nake karatu na course dina danakeyi,</p><p> Hankalina yatafi sosai ga abinda nake nazari akai,</p><p> Amal tashigi dakin da yar fara,ar ta ganin da tai min zaune ko niyar tashi don in shirya banda,</p><p> Zama tayi gefen gadon da mamakinta ta fisge littafin a hannu na,</p><p> Wani irin ajiyar zuciya na sake nadago kaina nazuba mata idona cikin nata,</p><p> Lokaci guda na karanto bacin rai a kwayar idon nata,</p><p> Muryan ta naji tana cewa lalai ma fadima baki da dama,</p><p> Yanzu duk tuna makin danayi cewa zamu fita yau kuma fitan mai muhin manci ne sosai bai sai kin maida hankali ba don mushirya da wuri shine zaki zo ki kama karatun ki,. </p><p> To san nu alhudahuda sarkin karatu,</p><p> Na, uhum Amal ba hakana bane gaskiya naga cewa sheriff baice dani za,a wanan gurin ba kamar kece kawai ke kokarin zuwa dani,</p><p> Dariya tadanyi min mai dan shewa tace o watau ni daban ce da ke yau ko,</p><p> Saboda yayanmu bai fada maki cewa, dake za,a ba da bakin shi shine rashin daukar maganar tawa da gaskiya ko,</p><p> Murmushi nayi nace a,a wlh ba hakana bane,,</p><p> Ta,tare nida cewa hakanane mana,</p><p> Jiya da yafada maki cewa zaku fita da bakin shi aikin shirya kun fita mu biyu, ko,</p><p>Jin na kaina nayi nace haba Amal ko jiyan ai a hanya ne tafiyan ya hadamu,</p><p> Tana mikewa tsaye tana cewa ki dai tashi da iya salon takon ki ki shir kin ji don ba,zaki samu bata lokaciba</p><p> Dama tun safe nagane nufin ki kina wani noke ma wanan tafiyan don baki son zuwa,</p><p> Gaskiya ba hakana bane kawai dai bani ,,,,</p><p> Hannu tadaga min tace min kin makaro yarinya zuwa ba fashi don sai kin je shi,</p><p> Fita tayi tabarni da tunane fam azuciya saboda irin canjin yanayi dana nake gani iri ga sheriff din mu</p><p> Nifa yar takari ce wana wuri kuma wurine na bada donations ga kungiya to ni mai zai kai wurin,</p><p> Wurin da yan kasan Africa daban daban musulumai ke haduwa don tallafawa al,umomin su,</p><p> Har na kwanta da niyar ban zuwa sai kuma hudubar salimat yafado min arai nakuma tuna da irin hararcin da sheriff ke min tun haduwa na dashi koma bai ce inje tunda yar uwan shi ce tabukaci inje aidole in tafi,</p><p> Wanka nafada yi bayan nafito nadade gaban dressing mirrow, gashi na nafara gyarawa bayan na gama sai na fara gyaran fuska na</p><p> Ina gama gyaran fuska sai text din nan na jiya yafado min a raina,</p><p> Kayan nadauko nasa nadaura dan ribon din kayan na kama kaina dashi,</p><p> Nida kaina nakarewa kaina kallo a,mirrow saina ga ashe rigar tsakiyar ta a matse take ta ciki tasama andan buda ta</p><p> Ajiyar zuciya na saukar a hanakali ina kallon kaina wainice fadima inna yar kulu na koma haka yau,</p><p> Najawo kit din sarka da aka siya min jiya jiya na daura ma wuyana nasa dan kunen </p><p> Wohoho sai kin gani da kanki zaki karasa bayanin yarda na koma,</p><p> Daidai lokacin naji anturo kofan dakin nawa, ko ban diba ba nasan cewa Amal ce </p><p> Sainace mata Amal kidiba kigani yarda nakoma yau ni fadima yar takari diyar inna yar kulu yar mutan dogon daji, nice,,,,</p><p> Bankarasa zancen bada naji shirun yai yawa sai na waiga inga may yasa tai shiru bata ansa min ba,</p><p> Sheriff ne tsaye ya zuba min ido cikin shigar wasu kayan Indians Pakistani, farare sol kayan wando da riga kayan sun karbi jikin shi sosai </p><p> Takowa yayi a hankali cikin tafiyan shi na kasaita, irin na matasa masu tashen nairai,</p><p> Yatako har inda nake tsaye gaban mirrow,</p><p> Gyalen kayan yadauko ya mika min yai min alamar in yafa ma kaina batare da yai min magana ba ya juya yafita yana mai kallon agogon hannun shi da yadaura,</p><p> Ina gama shiri a bakin kofa nasamay duk cikin shigata alfarma, irin ta musulumai,</p><p> Motocin ne guda uku a jere waje kowani yakai akirashu mota,</p><p> Dan jin nayi tsaye don basan ko wace zamu shigaba nida Amal,</p><p> Salim ne yai min magana kasa kasa yace min waccan farar itace zan shiga, </p><p> Ga mamakina sai naga Amal ta nufi gudan motar wadda naga mustapha ya shiga bayan ta itama dai din bayan motar tashiga,</p><p> Nadan waiga na kusan nikadai ce a,tsaye wurin don salim har yafara tafiya zuwa motar da zai shiga tare da wani mutun bakon fuska da nagani,</p><p> Banda zabi motar da salim yagwada min inshiga itace din na nufa,</p><p> Ina isa kusa da motar da driver motar ke rike da gambun motar yana jiran karaso wana,</p><p> Ga mamakin da zan gani ciki sheriffudeen din mu ne Ahmad zaune a bayan motar yana waya,</p><p> Kamar in,koma baya don fargaba,</p><p> Sai kuma, nadaure nai dan kokarin shiga na zauna ahankali,</p><p> Batare da na waiga gefen da yake zaune ba na takure gefe guda kamar ankai buzuwa yaye,</p><p> Yana gama wayan dan kallo ni a hankali yace ko sanyin A C yaimin yawa ne na takure wuri guda, </p><p> Nadan kada kaina alamar a,a </p><p> Bai ce min komai ba kuma yadan tatara hankalin shi ga titi ya na kallon hakali kwace,</p><p> Mun iso gurin wani babban dakin taro ne da ake kira da King Fahad central, holl, </p><p>A cikin larabci akai rubutun,</p><p> Nan muka dosa don ni nasan gurin mu kanzo bara ko goge goge, indan anawani occasion, a lokacin da nake takari</p><p> Motoci ne birjit agurin ga security nan kala kala, sai mutun yaji tsoro indan bai saba ba saboda irin tsaron da akasa agurin,</p><p> Ko ina hasken fitilo ne keta wal,wal,wal suna haska mutane, dake guri kala kala,</p><p> Koda mu muka fito daga motar zuwa cikin dakin taron,</p><p>Akwai dan tafiya maidan nisa kafin mu shiga cikin dakin taron,,</p><p> Tafiya muke yi a jere da juna batare da dayan mu ya yi magana ba, muna gab, da shiga dakin taron naji sheriff din mu ya riko min hannu na, yarike cikin nashi sai sanan yadan rada min akune ne ya ce min</p><p> Kinyi kyau sosai, fatima,</p><p> Sai naji, nakasa controlling kaina </p><p> Kamar a mafarki naji zancen nashi ji nayi kamar in nutse acikin kasa saboda kunya,</p><p> Ban tanka ba daidai lokacin kuma ,muka kutsa kai cikin dakin taron wanda ke cike da yan uwa musulumai bakaken fata, na kasa kasa</p><p> Shigar mu keda wuya a ka fara taken kasar saudiya, tare da daga tutar su mai photon dabino da takkuba,</p><p> Bayan angama malamai kala kala suka dinga jero addu,oin su tare da yin nasiha, akan cigaban addini, musulunci,</p><p> Abinda na lura dashi agurin shine duk wanda keda mata ko miji gefen su daban tare da tawagansu, </p><p> Wanda kuma basu zo da matan su ba suna gefe guda na maza gefe guda namata,</p><p> Saida aka nuna muna inda gurin zaman mu yake ne nagane cewa ashe su mustpha na bayan mu cikin tawagar company Abu Abdallah wanda sheriff ne ke jagoranta su,</p><p> A gaskiya tsaya infadi irin kyaun da mukayi aguri bata lokacine,</p><p> Yan jarida ne kawai keta faman daukan photo kala kala a,gurin</p><p> Zaune nake kusa gab da sheriff din mu idan ka gamu zaka dauka ko wata mata da miji ne sabon aure saboda yarinta na ya baiyana sosai , daka diba kasan cewa Allah yayi hadin shi agurin ,,,,,</p><p> Koma mai nawa baka iya gani sai dan round din fuska na kawai ya dan baiyyana afili,,,,</p><p> Kowa nata harkan gaban shi sai donations ake ta bayar wa kala kala, </p><p> Yawancin duk wanda ke gurin zaka ga yana magana da abokin tafiyar shi,</p><p> Banda ni dake zaune gefen sheriff ina ta faman, dan wasa da wayana dake a hannu na,</p><p> Banyi aune naji ana kiran sunan sheriff da tawagan shi sufito suba tasu gudunmawar,</p><p> Hannu yamika min nagane nufin shi nima sai na miko mai yadan makale hannun nawa cikin kafadar shi muka mike atare, lokaci guda,</p><p> Kyauta sheriff ya gabatar irin ta alfarma da bajinta da kuma kulawa da addini, </p><p> Inda jama,a keta sa masu albarka dashi da kamfanin su,,,</p><p> Andayi hira dashi har ake tambayan shi sunan amaryan nashi nadauka zai ce aziza ko nafisat,,,</p><p> Sai kawai naji ya fadi suna na full da mamaki nadan kalleshi cikin dabara, sai yadan kashe min ido guda </p><p> Duk wani irin kunya da nauyi ya kamani agurin, duk wani motsinawa yana akan idon sheriff tunda naje gurin banyi magana da kowa ba,</p><p> Yana rike da hannu na duk gaisawar da yakeyi da jama,a</p><p> Jinayi ana dan tafawa a hankali abayan mu, batare da na diba ba kowaye ba tun da ba wai sanin su nayi ba,</p><p> Na ance kai amma ko gaskiya kun dace da hakan aida kace min in bar maka ita din takace bana kowa ba,</p><p> Gabana yaba dam don ko ban waigaba nasan cewa wanan muryan Ali baba, ne </p><p> Alin ya zagayo da kyau ta gaban mu yasa hannu cikin aljihun shi yana muna wani irin mugun kallo,</p><p> Doctor kamal abokin sherrif na gurin bai gane may Alin ya ke nufi ba sai ya ce </p><p> Walahi nayi farin ciki da wanan auren na Ahmad fiye da kowani auren da yayi abayan </p><p> Don wanan itace daidai da aure ka</p><p> Alin da ke gefe yace o ko asai akace yayi kwace ga wani don kawai tazama mallakin shi,</p><p> Sai lokacin sheriff yace ma Alin kai dama dan akuya ne acikin mu karasa wacce zaka bida sai wacce keda aure akanta,</p><p> Murmushi Alin yayi yace wacce da aka kwace ake shirin aure ko,</p><p> Zaici ga ba da magana security din company su sheriff sukazo suka dan jaye Alin din gefe </p><p> Inda muka ratsa tagaban shi tare da sauran tawagar mu muka wuce shi cikin mamaki,</p><p> Almustapha,ne yai, mai dan bayani a takaice sai yabimu da wani irin kallon mamaki har muka bace mai da gani,</p><p> Danaga mun fito daga dakin taron nadauka zai sake min hannu nane sai naji yadan kara rike min su tsam,</p><p> Ahaka har muka shiga mota, ranshi a bace akan abinda Alin yai mai ne,</p><p> Tafiya motar keyi sit ba wanda ke magana daga cikin mu,</p><p> Can naji sheriff yakara kamo yan yatsun hannu na ya dan matsa su a hankali,</p><p> Sai nai kokari jaye su,saboda nasan cewa ba abu mai kyau ba ne hakan haramun ne,,,</p><p> Amma ga mamakina sai naji ya rike su gam yadan daga kai ya kalle a hankali, </p><p> Cikin wata irin murya mai kasala yace min, haram haram kada ki haramta min abinda Allah ya hallata min pls,</p><p> Haka na kyale shi yai ta yadda yake so da yan yatsun nawa,</p><p> Mun kusa shiga kwanar unguwar mu naji rikon da yai min har yafi na dazu,</p><p> Duk jiki sai naji ba karfi, daga rikon hannu sai naji, ya kwantar dani a saman kirjin shi ya rike ni gam kamar zai maida ni acikin zuciyar nashi,</p><p> Inajin yadda zuciyar nashi ke bugawa sai wani irin tsoro da fargaba ya kamani,</p><p> Ga driver nata tuki mota amma sai,nake ganin cewa kamar a tsaye yake wuri guda ba tafiya yakeyi ba,</p><p> Duk na storace na shiga wani yanayi nadaban wanda ban taba shiga ba,</p><p> Saida motar ta tsaya naji yai wani irin ajiyan zuciya madan sauti,</p><p> Sai a lokacin nasamu ya sake ni a hankali,</p><p> Inajin yasake ni, ban ko tsaya jiran wani abuba na balle gabun motar</p><p> Dai dai lokacin naji muryan shi cikin kasala yana ce min Shukuran shukuran nafita da sauri,</p><p> Bina yayi da kallo har na bace mai da gani sai yakoma yadan jingina bayan shi da sit din motar ya lunshe idon shi</p><p> Sai yaji yadan tabo wani abu daidai inda nayashi ashe wayanane nabari saboda sauri,</p><p> Daidai lokacin da zai dauki wayan nawa ne yaji massage ya shigo mai atashi wayan</p><p> Batare da ya diba ba ya shiga cikin gida </p><p> Dakin shi yawuce harda wayan nawa, </p><p> Saida ya kan,mala komai yafito falo dauke da wayoyin mu a hannu shi,</p><p> Alokacin ne yabude wayan shi don ganin sakon nidake gare shi,</p><p> A sako na hudu ne yaga wani sako da Amal ce ta turo mai shi,</p><p> Yabude don yaga kowani irin sako ne taturo mai,</p><p> Photo mu da ta daukeni ni,dashi da baby asama,u, lokacin da aka haifeta zamukaita asibiti,</p><p> Saida ya gyara zaman shi da kyau don photo ba karami burgeshi yayi ba,</p><p> Waya na ya dauka daniyar yakaimi abina, </p><p> Da sallama ya,shigo dakin kwance nake rub da ciki tunda muka dawo inata gaman fidda hawayen takaici da bakin ciki may yasa sheriff yai min hakana vc. </p><p> Sai kuma naji muryan shi adakin dai dai wanan lokacin zubur nai niyar mikewa daga kwan ciyar da nayi,</p><p> Zama yayi gefena tayadda babu dama in tashi zaune </p><p> A hankali yace min may yasa nake kuka don ya taba ni ko kuwa don ban so,</p><p> Ya cigaba da fadin in yi hakkuri komai naga yayi da sannu zan gane manufar shi, </p><p> Sai dan mike tsaye tare da aje min wayana gefen bedside,</p><p> Yace inkula da kai pls saida safe,</p><p> Duk kan mu wanan daren ba wanda yai barci a cikin dadi don kowa da abinda yake tunawa,</p><p> Ba komai sheriff ke tuna ne ba sai wanan photo da Amal ta turo mai photo da yasa duk hankali shi yau yakara tashi,</p><p> Ba abinda yake bukata da muradi arayuwan shi yanzu kamar a ce matar shi tasamu ciki,</p><p> Niko ina can ina cewa wai ko sheriff na cikin hankalin shi saboda duk iya sani nada shi ban taba ganin shi ko jin yayi wani harkan banza agabana ba </p><p> Sai yau ko yau din ma yana kirarin cewa wai kada in damu ,</p><p> Hmm aiko dole ne indamu da haka naita sakawa ina warwalewa, nikaida sai Aisha dake gefena kwance tana barcin ta hankali kwance sai naji dama ace nice ke barci haka hankali kwance,,,</p><p> </p><p> Washegari muka wayi gari da babban bakuwa, Aziza ce tazo daga Dubai don ita yanzu can tafi zama, da tana zuwa Nigeria kaida kai amma yanzu ta daina,</p><p> Zuwan ta yasa nadan saki jikina kadan wai ni ina gudun tagane abin da yafaru ni da mijinta,.</p><p> Sai har yanzu ban iya hada idona sam da sheriff saboda wani irin mugun kunyar shi da nauyin shi nake ji sosai walahi </p><p> Da ina da dama dana koma madina in karasa hutuna acan don zaifi min</p><p> Shiko ina lura da shi da munda hada ido ko nai wani dan motsi sai yadan wani lunshi idon shi,</p><p> Don hakane ma na koma daki abina ban kara fitowa ba,</p><p> Photo da Amal ta turo mai ne ya dauka yake nunawa Aziza yana mata bayani akan photo,</p><p> Saida ta kalli photo tsab sai wani tunane da tadade tanayi ba mafita yafado mata a rai </p><p> Cikin wani irin yanayi ta dan gyara zaman ta don taji dadin yin nazari akai</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 6⃣6⃣</p><p> *BY* </p><p>🐎 *ZAINAB *IDRIS**MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP 🐎</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,</p><p><br /></p><p> Tabbas wanan yarinya yakamata ta taimaka mata, badon komai sai don hakan zaifi mata sauki da rufin asiri,</p><p> Ganin da tayi cewa sheriff din mu yayi barci mai nauyi yasa fito daga dakin </p><p> A cikin duhu take tafiya saboda kashe duk wani haske dake falon da akayi </p><p> Saboda koyi da,sunnan maikin manzo sallalahu alaihim wasallam,</p><p> Sai yanzu nake jin yuwa na dan damu , dama bani abu bane abinci drink's ne nake yawan sha, da corns,</p><p> Don haka na tashi nafito falon gidan don inda samu abinda zan agaza wakaina, dashi,</p><p> Dayake ahankali nake tafiya na sai naji kamar ana magana kasa kasa acikin falon don haka sai nadan rage tafiya na don jin kowaye, cikin wanan uban dare,</p><p> Ga mamaki na sai naji muryan mace kuma da harshen hausa take magana,</p><p> Kara matsawa nayi daidai gurin da sautin ke futowa,</p><p> Aziza gabana yaba da dam,</p><p> May takeyi haka acikin dare koma dai may ye sirine bata son kowa yaji ta,</p><p> Har zan juya sai wata zicuya tace min indan dakata inji ko da kadan ne,</p><p> Murya kasa,kasa take cewa Hindu na fada maki cewa bazan samu matsalaba ga wanan yarinyar insha Allah zata yi yadda nake so,</p><p> Hindu tace Aziza wanan maganar ba karamar magana bace fa, maganace da ke bukatar siri acikin ta,</p><p> Kinga ko gara mufita waje can mu samo wacce zata yi muna aikin mu cikin rufin asiri batare da kowa yasanaikin</p><p> Sai, Muba ta kudi mu sallame ta tayi gaba in bukata ya biya,</p><p> Azizs tace hindu wanan yarinyar itace zata iya zama dai,dai da nufin mu, baki ganewa ne shiyasa,</p><p> Hindu, tace kidai bari mu, mukara dibawa ko zamu samu wacce ta dace da aikin</p><p> Haka sukai ta sakawa suna walwalewa a tsakanin su,,</p><p> Ina labe ina jin su duk jikina yai sanyi kamar in zunduma ihu,</p><p> Ban gushe daga inda nake labe ba naji motsin Aziza alamar tagama waya zata dawo, dakin su,</p><p> Shan jinin jikina nayi na lafe a bango, saida tazo dai kusa da inda nake labe sai kawai taja ta tsaya dai gurin,</p><p> Gabana yafadi dam don a,zatona tagan ni ne har na rufe ido na ,nasadakat kawai ta gani,</p><p> Shirun da naji yasa nadan diba sai naga a she, wayan take kashe,</p><p> Saida naji takon, kafarta ta wuce har ta haura sama dakin su ta rufe,</p><p> Nai ajiyan zuciya, da sanda na la,laba nadauki lemu na koma daki na hankalina a tashe,</p><p> Juyi nake tayi barci ya ki dauka na, sai, Tunane kawai nake saboda bansan kowa ni irin shiri ba ne zasu ai,watar, hakana,</p><p> Hakana na kwana da wanan tunane cikin zuciya na sai sake sake nake tayi har gari yawaye,</p><p> Tsakani na da sheriff tunda wanan abin yafaru tsakanin mu bamu kara haduwa ba,</p><p> Sai na bari rana yayi nasan cewa yafita zan dan fito waje,</p><p> Yau nasan cewa yatafi ma,ia,katar su ta Riyadh aiki, </p><p> Don yaune ranan zuwan shi can Riyadh din sai ya kwana biyu ko uku zai dawo garin makkah,</p><p> Wando da riga nasa wandon jeans baki ,mai kafar pencil sai yar wata riga da nasa wanda tsawon, rigan yatsaya min iya gwiuwa na, hannu shi ma hakana ya tsaya min,</p><p> Bakin gyale na daura a kaina, sai fuskana da ban mai wani makeup ba,,,</p><p> A hankali na,tako zuwa falon gidan Salim na samu zaune, yana kallon wani shirin na Arabs got talents, </p><p> Sai Amal dake gefe tana waya cikin kashe murya kamar wacce batason aji may take fada,</p><p> Gefen salim na zauna don muyi kallon tare, ban wani dade da zama ba, wayana yadinga tsuwar alamar kira in agaza mai,</p><p> Salimat ce takirani dan ihun murna nayi don jin dadin jin ta, danayi</p><p> Dauki wayan ina fadin maman As,mau nayi fushi gaskiya,</p><p> Tace ,a,a haba dai fadima idan kinyi fushi dani ai ko na shige su,</p><p> Nace kawai kin wuce, abinki ko ki tuna da mutane </p><p> Tace fadima kin san matsalar Nigeria har kauye saida naje gashe su, wani guri babu ko services da zan kira ki,</p><p> Yanzu ma mun dawo kano ne shine,nace barin kira ki mu gaisa kiji motsin diyar ki,</p><p> Munyi hira sosai har ina ce mata gaskiya na matsu ta dawo walahi ina kewan ta so sai,</p><p> Amal da tagama waya ta zagayo ta baya na ta fisge wayan ta shiga yiwa salimat ,sheri </p><p> Karshe dai taba mu hakkuri tace muna zata dawo bada dadewa ba Insha Allah,</p><p> Saida muka natsu daga dariyan salimat da muke yi ne,</p><p> Sai Amal ta jefo min tambaya wai fadima lafiya bakya fitowa waje duk kwana nan,</p><p> Salim dayaji tambayar Amal sai na ji yana dan gyaran murya kamar wani mai shirin yin magana,</p><p> Gaba dayan mu mukai diban mu gare shi, don ji ko ganin may zai ce,</p><p> Dariya yakama yi yana ce muna ya mukr kallon shi haka, </p><p> Amal tace fadi dai muji may zaka ce, kada kabari a ciki ya kashe ka, kai daya,</p><p> Sam ban gane mai yake nufi ba sai naji Amal nace kai dai kace ba ni nace,</p><p> Aji shi a bakin ka ba ruwana,</p><p> Kafin wani da cikin su yakara fadin watakalma Aziza ce tafi to daga sashen su cikin shirin fita, </p><p> Daya daga cikin wasu saitin kujerun da ke can gefen mu ta zauna a saman guda, </p><p> Waya takeyi tana wani murmushi tana gyara rigar da tasa da kyau,</p><p> Duk hankalin mu ya gurin kallon TV da salim keyi,</p><p> Amma dai gaskiya muna kallon ta ta wutsiyar idon mu, </p><p> Tundai ni da na ke fargaban shirin da naga tana kokarin aiwatar wa, a boye,</p><p> Muryan ta na tsinkaya cikin murmushi take magana daidai lokacin ta taso daga inda take zaune zuwa gurin da muke,</p><p> Cikin murmushi take cewa fadima unguwa za mu tafi yanzu , Ahmad yace kece zaki rakani ko tana fadi tana wani kashe ido irin na yan duniya,</p><p> Gaba na yadan fadi don jin abinda tace </p><p> Sai kawai na tuna da abinda naji tana fadi a waya,</p><p> Ganin da tayi kamar ina dan tuna ne yasa tace min ko baki son fitar ne yau, ai sai in fasa har zuwa gobe</p><p> Sai mu fita ko, takalleni tana wani kashe murya </p><p> Saida nadan yi ajiyan zuciya saina ce da sauri, haba, haba,</p><p> Ai kawai muje barin dan sa asshifal dina a sama kawai,</p><p> Nakoma daki nadauko wata sabuwar Asshifal, baka mai kyau na za saman jikina nada nan nagyara daurin dake kaina ya koma rolling sai na aza dan gyalen wanan Asshifal din saman rolling din kana gani na kasan nayo shigar mutanen musuluman kasar, Sydney </p><p> Ina fitowa falon inda take jira na muka hada ido da Amal saita sakar min wani irin uban harara,</p><p> Cikin larabci tace min indai bi a hankali da wanan</p><p> Murmushi kawai nadan yi mata don kada aziza ta gane cewa da ita mukeyi,</p><p> Yusuf driver ne zai ja mu, muna shiga mota sai tace min ince mai kada yai tuki sosai yabi da ita a hankali pls,.</p><p> Haka ko yakama tuka motar a hankali yake tukin ,</p><p> Naima yusuf magana nace yasa muna ki,ra,an Shuriem don ina son kira,ar shi sosai,. </p><p> Idanuna nadan lunshe ina sauraren kira,ar ina kuma bin shi a hankali, sai ina tuna ne a gaskiya ba abinda yakai alkur,ani dadin sauraro,</p><p> Muryan Aziza naji tana cemin acikin hausa shagon, saida kayan masu kyau zamu fara zuwa idan mun gama sai mu tafi wurin gyaran jiki ,,</p><p> Sabon shagon da aka bude a cikin Bin,Daewood na kai ta sainaga duk ta rude saboda kyau wurin </p><p> Komai akwai acikin shi shagone tundaga sama har kasa sai inda idon ka ya tsaya, da gani,</p><p> Ganin cewa danayi gamu cikin massalacin Ka,aba ai yakamata mudan yi koda nafilla raka,a biyu ne kafin mu wuce,</p><p> Nace mata idan mun gama sai mu tafi muyi sallah da dawafi, ko</p><p> Saida ta dafani tana murmushi tace min idan munce mu tsaya yin dawafi ai zamu makara da zuwa gurin gyaran jikin mu ko,</p><p> Sororo nayi saboda mamakin ta, ga wasu can nason suzo kota halin ka,ka </p><p> Allah bai basu ikon zuwa ba, ita gata tasamu har tana barin damar ta a banza,</p><p> Haka nabi bayan ta da mamaki fam a cikin zuciya naita</p><p> Saidai ina ta jiran inji ko zanga wani abin da yashafi maganar da naji tanayi a waya ranan</p><p> Sai banji komai ba shiru,,</p><p> Hakan yasani nadan sake jikina da ita</p><p> Munashiga shagon kayan kyalkaylin mata, sai, tafara jidan kaya masu kyau </p><p> Masu kuma tsada hatta su undies sai da muja jido su kamar hauka,</p><p> Har zan shiga wani shagon saida kayan kamshi sai ta kirani,</p><p> Da sauri nadawo wata riga ce mai masifar kyau irin tamu matasa yan mata,</p><p> Kala kala different design masu kyau, kowani da gyale ko wani abayan hada shi mai kama da alkyabba,</p><p> Cikin sha,awa tadinga gyada kai, tana, yaba kyawon kayan tana cewa wanan kan sai ku yan mata, fadima,</p><p> Ina kallonta takwashi kusan guda biyar kala kala,</p><p> Ina tsaye gefe ta biya kudin kayan ,mamaki kawai nakeyi irin yawan kudin da naji an ambata akan kudin da mukayi sayayya haka,</p><p> Saina tuna cewa ai ita,</p><p> matar sheriff ce fa ita dole in ganta da kudi hakana,</p><p> Muryan ta naji tana cewa Sannu fadima na gajiyar da ke yai ko,</p><p> Na gode kware ki ji bayau ba ina son fitowa inda zaga gari rashin samun abokin tafiya ne yasa ban fito,</p><p> Saida Ahmad yace min in je dake ai kin san ko ina a garin ke,</p><p> Tace sai kuma ban samu fuska agurin kuba kin san dangin miji tundai Amal na fuskanci bata ra,ayina takare maganan cikin muryan tausayi</p><p> Nace a,a haba dai aiko muna son ki sosai kedin ai matar,yayan mu ne kin ga ko dole mu soki, </p><p> Tunda muna son shi, aidole muso duk abinda yake so ko,</p><p> Cikin nishadi tace min kai amma kuwa yau naji dadin zancen ki walahi </p><p> Ban san cewa haka zan samayki ba ai da tun tuni mun dade da shakuwa a tsakanin mu,</p><p> Rashin ganin fuskan da banyi ba ne agurin ku yasa ko zama ban son yi wurin Ahmad,</p><p> Bansan lokacinda da wata yar dariya ta subce min ba nace kai haba hjy saboda mu zaki ki zuwa gurin mijin ki. </p><p> Muda ba ma,a garin muke ba, saida irin haka in munzo kawai, sha mudan wuce, abin mu,,,</p><p> Tsayawa tayi tana min wani kallo cikin mamaki tace hai fadima,</p><p> Fadima kema kinsan cewa gurin ki kawai nake dan samun sauki acikin ku muryan ta yai wani rau, rau kamar zatayi kuka,</p><p> Ban iya cewa komai ba don tabani tausayi harga Allah,</p><p> Haka muka karasa har inda muka aje motar mu a bakin tin da ke gefen haramm,</p><p> Daga nan muka wuce wurin gyaran jiki,</p><p> Ga mamaki na nadauka ko itace kawai za ai mawa sagashi dani da ita duk an muna</p><p> Nakoma kamar wata yar bakaken indiya komai na sur mace da nake da shi yakara fitowa tsab ajikina,</p><p> Tun a mota Aziza ke yaba irin kyaun da nayi sai murmushi nakeyi kawai don nasan cewa ba karya tayi ba ,,</p><p> Saida muka kusa shiga unguwar mu ne take ce min duk fa ke na siyo ma wayan nan rigunan ,</p><p> Cikin mamaki na,kalleta nace ,a,a aikin san cewa bani kadai bace sai dai ni da Amal ,</p><p> Sai ga tadan bata rai kadan can kuma tadan sake ranta tace kece kika rakoni kuma kedai na siyawa ,</p><p> Ba matsala zan raba da ni da ita kin ga tasamu albarkaci na aiko,</p><p> Har muka kara gida tana min hiran jin dadin da tayi na ganin nasake jiki da, ita,</p><p> Ko ba a fada ba nasan cewa Sheriff din mu yadawa daga tafiyan da yayi taniyar yin kwana biyu a babban headquarter kasar saudiya watau Riyadh,</p><p> Da mamaki nakai kallona ga motar shi da naga yana yawan shigarta,</p><p> Kamar Aziza ta gane mamakin da nakeyi azuciya sai tace ashe har sun iso don dama yau ba zai kwana a can ba don suna da wani meeting da ma,aikatar su gobe, Insha Allah,,</p><p> A falo muka samay su duk kan su har almustapha sun baza wasu takardu a gaban su suna dibawa,</p><p> Sallaman da mukayi ne yasa kowa dagowa kai don yaga ko suwa ye,</p><p> Dammm gaban shi yafadi saboda ganin da yayi ko yaushe kara canzawa kawai nake yi,</p><p> Cikin kwarewa da shagwaba take mai magana, har ka iso Sweet habibi,</p><p> Kai kawai ya kada mata alamar eh , ga kaya ahannu mu niki niki ta,isa inda yake tadan man na mai kiss a tsakiyan goshin shi,</p><p> Sai ta,Zube saman kujerar dake gefen ta tana cewa wassh Allah na duk nagaji wallahi,</p><p> Aikin da sukeyi yadan aje gefe guda yadan kalle ta yace,</p><p> U are to lazy, wanan dan fitan da kikayi kike cewa wai, kin gaji,</p><p> Suna juna wani irin kallo cikin shaukin so,,</p><p> Kayan nazo gaban ta na zube gefen kujera datake zaune,</p><p> Kai yadago A,hankali ya bini da kallo sai kuma yawani lunshe idon shi a hankali kamar maijin barci , </p><p> Kamshin turarain da yaji ina yi duk yakara rikida shi,</p><p> Kamar mai rada yace mata wai har ina kukaje ne haka yau kuka kwaso wanan kayan mai yawa,</p><p> Ke kaya basa isan ki dai ko nuna ni tayi da hannu ta guda tana cewa yau ai duk kusan sayayyan ga mai su can,</p><p> Muna hada ido da Amal takara sakar min wata uwar harara da yafi nadazu,,,</p><p> Ida nake tsaye ina,sha wata uwar harara daga Amal yadan kalla lokacin kuma hararan da Amal take min yabani dariya,</p><p> Sai yayi sa,a ina dariya a lokacin, Abinda yadade baigani ba ke nan tun ina yar karama a Riyadh lokacin da nake shiga cikin ruwa ina wasa agidan shi,</p><p> Murmushi ne ya subce mai ba shiri saboda tunawa da yayi da wanan lokacin </p><p> Saboda yaga yadda nake wasa daruwa har dawo yakeyi ya tsaya ta glass din falon shi yana kallo na ,,</p><p> Saboda haka kawai yaji in burge shi dan banda tsoro ko fargaba kai tsaye nake abina,,,</p><p> Aziza ce tace min inzo in kwashi kayans intafi dasu,</p><p> Tazabe duk wanin abinda take bukata daga ciki tabar min sauran tarkacen da rigunonin,</p><p> Da alama sheriff yaji dadin hakan da tayi har cikin rashi yace mata</p><p> Kai amma dai wanan fitar dama na tane ko ,</p><p> Tadan rausaya kanta tace aikasan dole in saya mata tunda har ta bata lokacinta ta rakani batare da nuna gazawanta ,,,</p><p> Ina kwasan kayan gurin Amal na nufa direct dasu nara dai dai nace mata ta zabi duk wanda take so tabar min kashi guda,. </p><p> Dariyan yake tayi ko shi don yayanta ya gurin ne don kada yace wani abu da bata karbi kayan ba,</p><p> Amal tace a,a ki bari kawai in dauki wanan,</p><p> Wani dan rigar barci kawai ta dauka,</p><p> Tundaga wanan ranan wani irin shakuwa da amin taka ya shiga tsakani na da Aziza ,,</p><p> Amal tai min fada taimin nasiha tace inyi hankali da ita don yar duniya ce,</p><p> Badan Allah take so na ba ita tana ga da wani manufa take jana ,a jikin ta,</p><p> Sai naga cewa kawai, kamar dai don basu ra,ayinta ne kawai,</p><p><br /></p><p> Yau shiru tunda safe banga Aziza ba a waje ganin da nayi cewa anytime tafito sai ta nemay inda nake ,</p><p> Yasa da banganta a waje ba na hausama zuwa dakin su,</p><p> Kwance take rub da ciki nai sallama a hankali ta ansa min ,</p><p> Tajuyo daga rub da cikin da tayi kwancen, sai naga fuskan ta ya kunbura idon ta da almar tayi kuka ma,i,shin ta,</p><p> Subbahanallah nace da sauri na isa gurinta ina mai kokarin dafa ta,</p><p> Nace cikin rawar murya hjy mai yasa may ki ,ko baki da lafiya ne,</p><p> Duk lokaci guda na sako mata wanan tambayar a jere da juna</p><p> Girgiza min kai tayi kamar karamar yarinya,</p><p> Ta, bude baki da kyat tace min babu ko daya </p><p>Fadima</p><p> Matsalata tafi karfin fahintar ki kona fada maki bazaki gane ba saboda,</p><p> Ke yarinyace, shiru nayi kamar ina na,zari, can nace to amma anty aiko banza gane ba ai zan yi kila taimaka maki ta wani hanya ko,</p><p> Saida tadan shere wani hawaye dake shirin fito mata daga cikin idonta, ta hade miyau da karfi sanan ta mike da ga zauna </p><p> Hannaye na takama duka biyu ta hada wuri guda tace Fadima inda zaki fahince ni da kin san cewa muna cikin tashin hankali dagani har Ahmad saboda matsalar da ta samay mu,</p><p> Sai duk naji na matsu da insan kowata irin matsala ce haka wadda har yasa wanan jarumar matar kuka haka ,</p><p> Dan Allah hjy ki daure ki fada min koma maye ko zan san abin yi pls,</p><p> Fadima muna cikin matsala rashin haihuwa nida Ahmad munje asibiti likita yace bazan iya daukan ciki ba,</p><p> Sai kuma tasa kuka wi,wi,</p><p> Sai naji duk hankalina yatashi,, saboda wanan maganar ba karama bace ga duk wani mahulukin da yasan ciwon kanshi,</p><p> Tana shere hawaye taci gaba da fadin ,sai wanan test din da mukayi na karshe likita yace muna inda zan samo wata wacce zata taimaka min asa mata cikin ma,ana ai mata dashen cikin</p><p> Idan ya fara girma sai amayar min da abina yace yana ganin haka zai sa in samu baby,</p><p> Kinga kuma shi Ahmad baya ganin laifin kanshi sai nawa kinji halinda naje ciki fadima, tanayi tana kallon fuskana don taga irin re,action din da zan nuna,</p><p> Fuskana fal da tausayin su ban san lokacin da nafara kuka ba ,wi,wi, nima don ba karamar magana bace wanan,</p><p> Mutun kamar sheriff ace ba zai haihu ba, treble,,</p><p> Muryanta naji tana cewa amma fa kada ki fada ma kowa wanan sirinane da mijina na fada maki,</p><p> Saboda yarda da nai miki yasa har na fada maki sirina,</p><p> Hmmm hmmm</p><p> Wani sabon kuka nasa mai tsuma rai an muka rugumay juna mukai ta kuka har saida muka gaji,</p><p> Nakoma dakina fam da tunane da tausayin su,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 6⃣7⃣</p><p> BY</p><p>🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,,</p><p><br /></p><p> Cikin dare na kasa yin barci mai nauyi saboda yawan tunanen da ke ta addabata,</p><p> Juyi kawai nake yi ina faman ajiyan zuciya da dan guntun tsaki,</p><p> A, gaskiya na tausaya ma sheriff din mu so sai yanzu ace duk tausayin shi da mutuncin shi bazai haihu ba,</p><p> Ashe haka wasu Allah ke halittan su, batare da haihuwa both miji da mata,,</p><p> Saboda ni nadauka cewa mutun guda akan ce baya haihuwa mijin ko matar,</p><p> Amma su sai,gashi wai duk kan su case din su gudane,</p><p> Babu mai karfin haihu daga cikin su,</p><p> Dan sanyin da naji shine cewar da tayi idan an yi dashen cikin za su iya haihuwa insha Allah,</p><p> Kwancin bai min hakan yaban damar mike na shiga bathroom na dauro alwala na fara nafila ina fadin bukata na, a wurin Allah,</p><p> Nafilan nan da nadan samu na gabatar yasani jin sanyi a zuciyana ,</p><p> Har na dan samu barci maidan nauyi yadauke ni zuwa asuba ,</p><p> Hakan ne ma yasani makara da sallah asuba,</p><p>Saida gari yadan yi haske nafar ka zubur da salatina a baki,</p><p> Saidai duk jikina ba karfi hakana naje nadauro alwala,</p><p> Ina zaune inda na sallamay sallah asuba ina ta kwarara ma sheriff da iyalin shi addu,a,</p><p> Shawar da na yanke tun cikin dare shi na yi niyar aiwatar wa,</p><p> Amal na dakinta kwance nafito nace mata zan je masjidul nana Aisha ,,</p><p> Da mamaki ta kalleni daga kwancen da take tace min tunda safe haka,</p><p> Murmushi nadan yi mata, nasamu gefen gadon ta, na zauna ina gyara belt din takalma na,.</p><p> Ido takura min har na kare daura belt din sai tace min may ke damun ki fadima,</p><p> Cikin dan basarwa nace mata kamar ya fa,</p><p> Hmmm kawai tace min,</p><p> Sai kuma tace bana son ki sa kanki acikin fitinar da ba zai amfane kiba, wlh</p><p> Saida na mike tsaye da kyau nace mata ba wani fitinar da nasa kaina, aciki Amal kece dai ke hasashen hakan,</p><p> Amma for me ba komai ina fadin haka na sa kai nabar dakin </p><p> Zuwa masjidul bai dauki wani lokaci saboda sanin hanyoyin da na yi acikin sauki,</p><p> Ina isa nai addu,a na dauro niyar umrah nadinga addu,a da larabci, da hausa kai har mada turanci duk na hada ,</p><p> Saida na gama dawa,fi, nadawo daidai saitin indararon nan naita zuba addu,a </p><p> Saikuma na koma daidai kofar dakin naba mukamin ibrahim baya, nadinga kwararo addu,a agurin,</p><p> Dalilin dayasa nai haka gurin hjy Laila nataba ji suna hira da hajiyar mu cewa indan mutum yana neman haihuwa koda dan uwan shi ne keson haihuwa,</p><p> Sai yaje yayi dawafi, ga bakwan karshe saika dada addu,a agurin indararo saboda anasa rai cewa guri ne da duk abinda ka roki ubangiji agurin zai ansa ma insha Allah,</p><p> Indan ka gama sai ka dawo daidai saitin kofar shiga shi ai,nihin dakin ka,aban ka tsaya tsakiya, inda hali ka dauki ruwan zam,zam kayi wanan dawafin da shi,</p><p> Karoki Ubangiji Allah bukatar ka insha Allah Allah zai karba ma mutun,</p><p> Wanan ruwan zam,zam din sai kaba wa wace ko wanda ke da lalurar haihuwa ko wani ciwo yasha ya shafa tare da bissimillaj,</p><p> Sanin danayi cewa Aziza bazata sha ruwan ba kila ko nakai mata yasa ban dauki ruwan nayi mata dawafin da shi ba,</p><p> Saidai addu,an da na tsaya tsakanin mukamin Ibrahima da kofar dakin ka,aba nayi na Allah yataimaka ya bawa sheriff din mu haihuwa mai albarka a rayuwan shi,</p><p> Tare da kwararo wa sauran al,umman musulumi a ddu,a,</p><p> Daga karshe na tsaya daga can gefen yamma kadan nadibi ruwan zam,zam nasha sai nayi nafila raka,a biyu </p><p> Nagode ma ubangijina subbahanahu wata ,ala,</p><p> Dana gama nadade gurin zaune na zubawa dakin ido sai naji wasu hawaye masu dumi suna zubowa daga ido na,</p><p> Nadade a hakan sannan natashi nasamu guri na zauna a gefe guda,</p><p> Ranan anan nai sallolina har i,sha,i ina gurin,</p><p> Sai da dare na zo hanya don in tare taxi zuwa gida sai na dinga jin hayaniya,</p><p> Ko ban waiga ba nasan cewa yan bagaladine ke kokarin kama wasu daga cikin yan yawon takari,</p><p> Hakane ne kuwa don dai daga inda nake inajin muryan su sunacewa Nigeria,</p><p> Duk da hayaniyar da akeyi agurin bai hanai jin kuru,ruwar matar da aka kama ba</p><p> Azuciya na ,na,ce ya Allah yasa mutanen mu su daina wanan kazamin da bi,ar , tazuwa yawon takaru ba lasisi shiga kasar,</p><p> Idan ma mutum na so za,s iya bashi, lasisi idan har yabi ta hanyar daya dace,</p><p> Saida na ji cewa ni a halin yanzu zan iya zuwa ko ina saboda ina da kardan zama akasar ,,</p><p> Wanda bakowa ne yai min wanan hanyar ba sai sheriff Ahmad Lawal Zanna,</p><p> Zuciyata jinta nakeyi tai min shakat kamar an cire min wani nauyi acikin ta, </p><p> Haka na dunfari gida cikin wal,wala da sakin fuska ba wani damuwa atataredani,</p><p> </p><p> Har kusan karfe shida sheriff baigan ni ba kuma baiga, na fito waje ba koda ko falon gidan ne,</p><p> Duk iya kannewar da zaiyi yayi har dai yakai ga tambayar Amal cewa yau bai gana fito ba koda sau dayane waje, ko lafiya nake,</p><p> Sai wannan lokacin Amal ke mai bayanin cewa tunda safe natafi masjidul</p><p> Kuma dama nace zan dan dade yau ban dawo ba,</p><p> Don haka lokacin da na iso gida suna zaune shida Aziza saman dinning table suna cin abin dinner,</p><p> A hankali nayi sallama cikin katafaren falon gidan namu wanda ba lalai bane wanda ke ciki yaji muryan mutun da ga kofar shiga,</p><p> Ganin da nayi masu zaune su biyu suna cin abinci yasa nayi niyar wucewa batare da na gaishe suba,</p><p> Aziza ce tafara gani ,wanda a zahiri ba haka abin yake ba, sheriff yarigata gani na sai yai wani irin sanyayan ajiyar zuciya,,,</p><p> yadai daure ne yai kamar bai gan ni ba , don alokacin inda ban dawo ba da saura kiris yaja almustapha suje bida na,</p><p> Aziza ce ke min fadima yau ina kika shigane haka tunda safe naje dakinki yafi sau biyu ban ganki ba,</p><p> Naso mudan fita zuwa cikin gari kadan,</p><p> Saina dan yi mata murmushi yake kawai badon komai ba sai wanda ke gefenta dake min wani kallo </p><p> Da ban iya cewa ga irin shi ko ma,anar shi,</p><p> Bangaren da nake tsaye yadan kalla yace min ina tafi ,</p><p> A marairaice kamar mai shirin kuka nace mai masjid natafi,</p><p> Yar karaman harara yasakar min yana kada spoon a plate yace, </p><p> Oho ashe yanzu duk inda kiga dama saiki sa kai kawai ki tafi batare da sanin kowa ba,</p><p> Nankan shiru nayi masa don banda ansan da zance duk da dai na fada ma Amal cewa zan fita,</p><p> Yace je ki duk abin da kiga yafi maki je ki yi tunda ba ki under control din kowa,</p><p> Jiki ba kwari batare da kuma na iya cewa yayi hakkuri ba na shige ciki, abina,</p><p> Tunda dai nasan cewa ba wani mugu wuri naje ba,</p><p> Ina shiga daki,na Ko Nanfal dina ban cire ba,Amal tashigo dakin tana cewa</p><p> Gaskiya yau fadima baki kyauta tun safe fa kika fita duk da nasan cewa ga inda kika tafi ai bai kamata ki kai har dare haka ba,</p><p> Don nagajarce zancen ko zan samu saukin bacin ran da naji nace,</p><p> Amma dai Amal na fada maki ai kafin in fita ko,</p><p> Kafin Amal tace wani abu sai naji murywn sheriff yana cewa </p><p> Don kin fada ma Amal ni kin fada min ne ko,ko zaman Amal ki keyi a nan,</p><p> Kaina yana kasa don ganin da nai wa sheriff tsaye a tsakiyar dakina</p><p> Yacigaba da fadin idan wani abin yaje yasa may ki can fa ya kike son muyi</p><p> Ace tun safe mutum yabar gida sai yanzu yana mai diban agogon hannun shi,</p><p> Acikin sanyin murya nace mai dan Allah kayi hakkuri bazan sake irin haka ba insha Allah,</p><p> Ido yadan kura min nadan wani lokaci kamar mai nazari na tukun sai kuma ya juya yabar dakin batare da yakara magana ba,</p><p> Dagani har Amal wani irin ajiyan zuciya mukayi na fargaba,</p><p> Amal takai zaune saman gadona tace min gaskiya Fadima yau kin batawa yayan mu rai sosai wlh,</p><p> Yayi fadan fitar ki ke kadai batare da kowa ba yace wai laifina ne da nabari kika fita kedaya ban hanaki ba,</p><p> Murmushi nayi nakai zaune ina cewa haba dai sakace wata bakuwar gari ,</p><p> Bace wa zan yi halan,</p><p> Kada dai ki kara irin wanan halin pls,</p><p> Kofar dakin aka turo maman Umar ne dauke da abinci kala kala cikin wani dan keken tura abinci zuwa dakuna,</p><p> Cikin mamaki naje cewa may yasa takawo min abinci har daki aida tabari infita waje in diba ko,</p><p> Dukawa tayi tafara zuba abincin tace min sheriff yace mata ta tabbatar da naci abinci kafin in kwanta,</p><p> Amal dake zaune gefe na tadan tabe baki tace kaji yar gatan yaya ko har da abincin ma sai yasa a,yi gadinki har ki ci ko,</p><p> Maman Umar tace ai hakan yana da kyau don kinsan cewa fadima ai zaman amana take gare shi kin ga ai dole ya kulata,</p><p> Taciki abinci kala kala aplate tamiko min daga inda nake zaune a bakin gado na,</p><p> Kawai don tace min ance mata sai naci shiyasa nadan tsakuri abincin kadan,</p><p> Nace mata na koshi saidai fruit salad din duk munsha har Amal din,</p><p> </p><p> Nasan cewa yanzu sheriff yana falon shi yana tura sakonne a system din shi,</p><p> Duk dare sai yayi wanan aiki in da duk yake </p><p> Hakan yabani damar fitowa don in kara bashi hakkuri kamar yadda Amal da maman Umar suka ce min</p><p> Dogon rigace ajiki tunda nafito wanka na sauya ta,</p><p> Sai plat shoe's ne akafa na shi ma baki mai photo yar kwakwa karama kamar buzubuzu haka,</p><p> Ganawa wautar na manta cewa da ba yanzu bane don haka ko mayafi ban dauka ba , tunda naga cewa ai a cikin gida ne kuma sheriff ne fa wanda yasan ni tun ina yar karamana,</p><p> A hankali na tako har inda yake zaune saidai ba sakon yake turawa ba shiru yayi yarike gefen habar shi da hannu guda da alamar tunane yake yi,</p><p> Jin motsin da yayi a bayan shi yasa yadago a hankali yadubi gurin da yaji motsin,</p><p> Sai mukayi idi biyu dashi, amma sai naga kwayar idon shi ya kada yayi ja sosa,</p><p> Da sauri batare da tunanen komai ba nace subbahanallah ,</p><p> Barci kakeji ne, nasa mu kaina da tambaryan shi,</p><p> Shiru nadan wani lokaci bai ansa min ba, </p><p> Saidai yadan girgiza min kai kawai,</p><p> Ikon Allah saikuma nakara cewa kana ciwon kai naga idon ka ja,</p><p> Murmushi yau sherie din yai min da alamar tambayar nawa ya bashi dariya </p><p> Yana mai kura min ido shi ja da suka rine yace, min,</p><p> Bawa ni ciwon kai illa keda keson ki tarwatsa min kwakawalwata, fadima har ke zaki fita kibar gida tun safe har dare baki dawo ba,</p><p> Cikin sauri nakai durkushe a kasa nace mai kayafe min dan Allah insha Allah bazan sake ba,</p><p> Da wata dakusarshiyar murya ya ansa min yace gaskiya baki kyauta min ba fadima,</p><p> Kaman zan yi kuka nakara cewa ya yi hakuri pls,</p><p> Kafin yai wani mafana sai mukaji muryan Aziza abayan mu tana cewa haba dai habibi,</p><p> Ai tunda har ta bada hakkuri takamata ka yafe mata hakana pls,</p><p> Tazo inda nake tsugune tadan dagoni tace mai haba dai ai koda laifin da tayi yafi haka yakamata kayi hakuri ,,</p><p> Kujeran dake gefen shi ta zainar da ni tana mai dan jan shi da hira irin ta masoya duk da na lura bai son ansa mata sai dai yace eh, ki uhum atakaice,</p><p> Saidai takan dan jefani cikin hiran nasu jefi jefi,</p><p> Hira sukeyi abin su, cikin kwanciyar hankali, a,takure nake a cikin su kamar wace a ka tsure,</p><p> Amal ce tafi daukan cup a kitchen tagan ni zaune acimin su,</p><p> Daman hanyar gudu nake bida,</p><p> Aiko ina ganin ta na mike ina mai yi masu saida safe ,</p><p> Aziza ce ke ce min kin gudu ke nan fadima baza ki zauna muyi fira ba ke nan,</p><p> Kada ki manta cewa gobe tunda safe nake son mi fita,</p><p> Kafin ta kai karshen zancen yatare da fadi ba inda zan fita kuma, tunda nafita yau,</p><p> Da mamaki take kallon shi tace mai ai guri. Gyaran kai kawai zamu tafi </p><p> Nidai ban san ya suka karasa ba na wuce nabar su, abina,</p><p> Washe gari ina son indan motsa jikina sai na fada kitchen wurin masu aiki tare mukai aikin da su </p><p> Najera komai a dinning table din falon ,kamar yadda nassba yi da kafin intafi school,</p><p> Lokacin da sheriff yadawo gida shida almustapha, direct sashen shi yanufa </p><p> Saida yan gyara jikin shi yarage yawan jayan dake jikin nadhi bayan ya watsa ruwa, </p><p> Sai yafito ,wurin abinci ya nufa don shi baya cin abin a waje ko ya ya kyau abu yake sai dai wanda aka girka agidan shi,</p><p> Don haka da yadawo yai wanka yadan kintsa kafin yai komai sai ya fara cin abinci tukun</p><p> Zaune suke da Aziza sai salim da ke tare dasu Amal tunda aziza tazo takaurace ma yawan zama falon sam,</p><p> Acewar ta wai aziza batai mata ma,</p><p> Wai ruwan yan duniya ke ga aziza, </p><p> Don hakane ma bata son irin yadda taga inayi da aziza din,</p><p> Cibin farko da yakai bakin shi sai ya tsaya cak ,</p><p> Duk wanda ke table din sai ya bishi da kallon mamaki komai yasa ya dakatar da cin abincin ,</p><p> Fadima ya furta a hankali Aziza ta ce fadima ya ce na,am sai tadan fara waigawa kozatagan ni afalon, </p><p> Ga mamakinta batagan ni saitace mai yafaru da ira,</p><p> Cikin murmushi yace mata ya akagi tashi kitchen ai muna girki,</p><p> Aziza tace kamar ya don ban fahinta ba sai yace mata, wana girkin nata ne,</p><p> Har suka kare cin abincin tana mamakin shi,</p><p> Wani irin shakuwane a tsakanin mu haka ace har da girki in nayi zai gane,</p><p> Dan murmushi tayi maikama da na mugunta,</p><p> Batayarda ba sai da taje kitchen din ta tambaya suka ce mata tabbas nice nayi girkin</p><p> Dakina ke ina kokarin jona waya a cikin chaji naci kam shin turan sheriff a dakina ko ban diba din ba shi,</p><p> Ya saye da jallabiya mai ruwa assh colour, </p><p> A bakin kofar dakin ya tsaya yana karewa dakin kallo kamar yau ya fara shigo,</p><p> Tambaya ya jefo min da ga inda nake tsaye,</p><p> Ya akayi nai,cooking yau agidan nan,</p><p> Cikin mamaki na dan kallo shi nace mai cinkin han kali </p><p> Kawai dai nayi ra,ayin yin hakane, </p><p> Saida yadan dade tsaye yana min wani irin kallo mai kama da kallon sha,awa, sai nai sauri nadan waiga in ko may yake kallo a jimina hakana,</p><p> Hakan da yagani sai yai saiuri ya juya yabar dakin,</p><p> Mamaki wanan sauyin na sheriff nake ji saidai gaskiya ban wo komai araina ba,</p><p> Sai kawai na shere zan ce,,,naci gaba da aikina</p><p> Waje muke kusan duk kn mu gidan muna shan iska ne saboda mudan shakata,</p><p><br /></p><p> Salim na badminton shida sheriff a gefen can nisa da mu, kadan,</p><p> Wayan aziza yai kara dai dai lokacin da Amal ke shirin tashi zuwa cikin gida tadauko drink da ma nice zan tafi sai Amal tace min wai in bari ta,tafi don zata danyi wani abu acimi dama,</p><p> Hinduce mai kiran saina dan tashi cikin dabara nabar gurin don kada in takura masu,</p><p> Bayan sungaisa take tambayar ta ko tagama plans din datakeyi sai tace mata tana dai gab da gamawa,</p><p> Sundanyi hira kadan takashe eayan lokacin da taga Amal tafito daga cikin gida da tuen kayan drinks ,</p><p> Amal naganin ta kashe waya tace azuciyar wanan akwai kakar mata ganin da taimin zuwa yasa tajadhe eayan sherin da takeyi,</p><p> Fuska a sake take min zancen wai kawar tace bata da lafiya a dubai tana son kafin mu koma indan tafi in rakata indawo </p><p> Don yanzu idan tace ita kadai zata sheriff ba zai yarda ba,</p><p> Amal ta kalleni don ta ji mai zan ce sai taga na shiru bance komai ba, har muka tashi, dagurin shan iskan,</p><p> Adaki kamar Amal zataciyeni danya, saboda bacin ran da tanuna min,</p><p> Saida nabari ta gaba,</p><p>Cikin ruwan sanyi nace mata,</p><p> Amal nidake ba daya muke a gidan nan ba kituna cewa fa niyar aiki ce bai wata shakikiyar maigidan nake ba, kamar ki taimakone kawai Allah yaza mai yai min harkikaga ina zama ahaka daku,,</p><p> Shiru tayi tana nazarin magana na nace kin san cewa aziza mata sheriff ce kina ganin cewa zata sani abu ko tasao in mata abu in ce a,a,</p><p> Saboda haka kin ga dole in mata biyayya ke kina da damar dazakiyi mata komai don ke yar uwan mijintane,,Sabanin ni </p><p> Duk da haka kibi a hankali don wana yar duniya ce sosai,</p><p> Koda Aziza ta fada ma sheriff cewa tare zamu tafi, saida yai dan mamakin hakan </p><p> Irin shakuwar da yaga mun yi abin na dan bashi mamaki arayuwan shi,</p><p> </p><p> An muna shirin komai na zuwa dubai nida Aziza Amal jitakwyi kamar ta kamani tai min dan karen duka,</p><p> Rabona da shiga jirgi tun lokacin da muka shigo kasar saidiya da yan uwa na sai gashi yau kwasan tafiya yakamani,</p><p> Hjy hindu wata iri garmakekiyar mace ce ga tsawo ga kiba, muryan ta irin dan shakakken nan ne,</p><p> Ana ta kain i gurare ina ta dauka photo kusan duk inda naje,</p><p> Saidai guri wani likta da ta, ce min in rakata,,</p><p> Likitan indiya ne yanata turanci kusan maganar shi sai naji kamar ai yashe fe ni sosai</p><p> Ama da muka fito sai take ce min doctor yace dazata samu yar matashi kama zai san dabar da yayi yataimaka masu </p><p> Saikawai tasa min kuka acikin motar wai ita yan inda zata samu wace zata taimaka mata ai mata dashen shi take naima,</p><p> Ita bakomai ba sheirriff take tausayi,</p><p> Har muka kawo gida ina tunane mai zurfi araina </p><p> Nace idan ban yarda bafa watace can za,a dauko ta taimaka watakila ba mai halin kware bace tazo ta haifa ai bala,i,</p><p> Tana falon zaune na samay ta zaune a hankali nakira sunan ta nace mata hjy insha Allah ni zan yarda intaimaka maki ai min wanan dashen</p><p> Jawoni tayi ajikinta tana murna da magana na da na fada mata harda kukan taba fayce majina</p><p> Sai godiya take zaga min wai ta gode da rufin asirin da zan mata,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 6⃣8⃣ </p><p> BY </p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎 </p><p>🐎 HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,</p><p><br /></p><p> Saida ta tabbatar da cewa komai ya kanmala ga duk wani shiri da suke aiwatar wa,</p><p> Acikin shewa suke ta hiran su tafawa kamar ea yanda akaiwa bushar da gafara,</p><p> Saida Hindu tadan kurbi drink din dake gaba tukun sanan ta aje cup din saman table ,</p><p> Takalli Aziza wace take kokarin zuba nata drink din a cup ,</p><p> Tace mata wlh Aziza ban ta dauka wanan maganar, zai zo muna a cikin sauki haka, ba,,,,</p><p> Itama din kurban drink tayi tana lunshe idon ta a hankali,</p><p> Saida ta kara kurbawa sanan ta,aje cup din gefe,</p><p> Tace hindu Allah kawai yatai make akan wanan yariyan don kinga bawai kwadai bane ko ko ne man guri ,a,a </p><p> Hakatake, kwai wai ita sarkin tausayi, da wauta, idan ba tsabar wawanci ba da rashin wayo </p><p> Ko a ina ta bajin cewa, an ana dashen ciki idan ya kosa acire amayar inda akeso,</p><p> Aikawai dana samu anyi mata wanan dashe gaskiya, ninafi kowa sa,a da murna arayuwana, </p><p> Sai kuma idan lokacin da take tsamani, za,a cire mata, cikin zuwa nawa yayi sai kuma in samu sabon dabara in bullo mata da shi ,,</p><p> Sukayi wani irin shewa suka taba a tsakanin su, don murna da farin ciki</p><p> Taci gaba da cewa kima da zaran ta haihu karbe dana zan yi batare bat lokaci </p><p> Nasan cewa kuma dole dai yaro yai bearing din sunan uban shi da nawa,,,</p><p> Hindu ta dan gyara zaman ta kadan tace, aina san cewa zaki iya yin koda fiye da hakane, mutumiyar </p><p> Tamika mata hannu suka tafa cikin shewa,</p><p><br /></p><p> Doctor kamal ne zaune a office din shi da cikin asibitin sarki fahad,,,</p><p> Asibitin da ke a kan shifidaden titin, khalifas road's</p><p> Kujerar dayake sama tana dan juya shi a hankali, </p><p> Cikin dariya yake maganar shi a gaskiya Ahmad kana bani mamaki ace mutum ya zauna ya hali irin wanan kamar ba namiji ba</p><p> Shiko dai kana tsoron matan kane baka son ransu ya baci kake wanan rufa rufan da baida anfani,</p><p> Kadiba fa yau shekara kusan uku kenan da yin wanan auren naka, </p><p> In a lokacin kana ganin cewa yarinyar nan she is young yanzu fa da takai mallakin hannakilin ka,.</p><p> Sheriff dake kokarin mike wa da ga kujerar da yake zaune </p><p> Yake ce ma doctor kamal ni bansan ko may yasa kake yawan damuwa da wanan zancen ba,</p><p> Ina son kasan cewa ni ba saboda komai har na yarda a wanan lokacin aka daura wanan auren ba sai kawai don in tsirar da mutunci su daga wulakancin da ake shirin masu,</p><p> Saboda hakan kawai zan yi in masu gata su koma gida acikin mutunci,</p><p> Hmmm nifa tun wancan lokacin bawai nayarda da manufar ka bane,</p><p> Ai ba kai kadaine namiji da zai iya taimakawa ba ko,</p><p> Ina ga takaru nan yan uwasu da suke aure saboda kawai su zauna akasar sudan yi yadda suke so indan sun tashi tafiya sukashe auren kowa ya kama gaban sa,</p><p> Wasu kuma shikenan har abada su zauna atare,</p><p> To ni na fadama cewa don in tallafa wa wanan yarinyar yasa har na amince,</p><p> Doctor kamal din shima mike wa yayi daga kan kujera suna fuskantar juna su,</p><p> Cikin kashe ido yace ma sheriff Ahmad yan zufa ,</p><p> Duk a cikin taimakon ne hakan kamar yadda nagan ku a,wurin taron African youth development found,,</p><p> Baiyi mai magana ba har yakai bakin kofar fita office din sanan yadan waigo yana kallon doctor yana gyara kwalar riganshi,</p><p> Yace ban san abinda yasa kake sa kan ka ga abin da bai shafeka ba yan zu kamal,</p><p> Yabuga kofar daidai lokacin da doctor ke cewa zan zo har gida mu karasa zancen,yafadi yana dariya,,,,</p><p> Yana fitowa Yusuf ya bude mai mota ya shiga, suka fara hanya,</p><p> Yace ma Yusuf suwuce zuwa gida kawai, saida motar tazaunu a saman titin ne yakai kallon shi ga dogon agogon da yake tsaye a tsakiyar gari,</p><p> Wanda duk inda kake cikin garin makka zaka iya hango shi a tsaye,</p><p> Sai kuma ya dan lunshe idon shi a hankali gami da yin sanya,yaar ajiyar zuciya,</p><p> Tinyar tinyar abin yafara dawo mashi a rai kamar yanzu aka yi zan cen</p><p> A lokacin da matsi ya kai matsi ga duk wata takari dake zama a cikin kasar saudiya batare da lasisi ba,</p><p> Hjy Lailai ce tare da wani takaru na miji sukayi mai sallama a kofar gidan shi,</p><p> Cikin mamaki yake kallon su don yasan cewa baida wani halaka da su to may yakawo su gidan shi,</p><p> Bayan sun gaisa ne shiru yadan biyo baya sai shine yake ce masu ko daga ina suke,</p><p> Hjy ce ta tayi karfin halin fara magana don daga cikin su,</p><p> Ta ce mai sun zo gurin shi naiman taimako akan yaran takarin da ke aiki, agidan shi,</p><p> Shiru yayi kadan yana dan sauranta</p><p> Tace mai ansa mu wanda yaje yafada yan bagaladi cewa suna nan gidan shi,</p><p> Shine sukazo neman taimako akan cewa suna son ya taimaka ya rufa masu asiri don idan aka gane cewa su takari ne da gaskiya za,a iya yi masu mugun wulakanci don hakane ma tazo tare da wanan Alhj tanuna wanda suke tare,</p><p> Inda shikuma yadan gyara tsayin shi ya shiga yiwa sheriff bayani yadda abin yake cewa komai zai iya faru dasu, </p><p> A ,kakauce yace to may ye mafita aciki sai Alhj yace zaiyi kokari ya samo wanda za,a daura wa aure da mutun gudan su idan yaso koda za,azo sai a nuna wanan takardan kan cewa yan uwar su ne sukazo daga kasar su yin umrah bawai zama sukeyi ba,</p><p> Magana dai takai har Alhj na batun dukawa kasa akan sheriff yarufa masu asiri ya yarda akawo wani na miji adaura aure,</p><p> Sunbar wurin shi da niyar cewa zasu dawo tare da mijin bizan da zasu dauko ne,</p><p> Shine Almustapha yakara yi mai bayanin yadda abin yake sai yaga rashin dacewar hakan ,,,</p><p> Sai tunanen shi da na hjy laila yazo daya don hakane ya yarda akan cewa za,a daura mai aure da Fadima saboda yasan cewa yar karamace ni daga cikin mu </p><p> In yaso idan yagama shirin yarda zai taimaka ya maida mu gida Nigeria gaba dayan mu sai ya maishe mu,</p><p> Saikuma ya hasale min auren shi tunda dama, ba wai da sani na bane,</p><p> A massalaci aka daura auren bayan sallah jumma,</p><p> cikin din bin al umman musulumi da suka halarci sallah jumma,a na ranan,</p><p> Alhj umar mai takari sarkin takarin tsakiya da Shehi mijin mahaifiyar sheriff, sune suka zama uban amarya,</p><p> Inda Su doctor kamal su ka tsaya a bangaren ango,</p><p> Murmushi yakarayi saboda tuna abinda yafaru bayan dawowar su, daga wurin daurin auren,</p><p> Inda abokan shi suka sa shi agaba akan su na son su san kowacece wanan Amaryan,</p><p> Sai ce masu yayi su bari idan lokaci yayi na su sani zasu sani,,,</p><p> Auren yaba duk wani abokin Ahmad mamaki saboda basu da masaniyar hakan don sun san cewa bai ko zancen aure da su, </p><p> Sai mamaki sukeyi ko wace,ce amaryan da basu san labarinta ba,</p><p> Kudin sadakin da a kabayar a masallaci Alhj umar sarkin takari ya kawo ma sheriff yace yarike a hannu shi asamu abinda akayi ma amarya na samun karuwa, cigaban ta,</p><p> Sai yaba Shehi mijin mahaifiyar shi bayan yai mai bayani duk yadda maganar yake,. </p><p> Don adinga juyawa kudin kafin in girma ko in wuce Nigeria,</p><p> Saidai shi a lokacin har ga Allah taimakon mu yayi don gudun wulakanci,</p><p> Saidaga bayan auren ne aka gane ko waye kewa yan takari wanan sherin wurin hukumomin kasar na saudiya </p><p> Inda shima akasamu wasu suka tona mai asiri, akan harkan saida kwayoyi, dayakeyi,,,</p><p> Duk da auren na sheriff da fadima yana nan daran. </p><p> Sarkin takari yace abar shi saboda gaba zai mata amfani tunda tana cikin kasar har yanzu,,,</p><p> Saidai yanzu ne kuma gaskiya, yake dan ji wani abu agamay da fadimar wace ada banda tausayi ba abinda yarinyar ke bashi,,,</p><p> A hankali yai ajiyar zuciya don yasan cewa duk wanan abin fadimar bata da labari</p><p> Saboda kafin ta dawo yasamu damar daukan nauyin hajiya mai sharwali tare da sauran yaranta zuwa gida Nigeria tare da guzuri mai tsoka wanda zasu iya tallafawa kan su idan sun koma gida Nigeria</p><p> Wanan abin yai ma su dadi so sai inda hajiya ta roke shi alfarman rike mata amanan fadima yarinya mai kirki da mutunci,</p><p> Saboda tayi dana sanin zuwa yawon takarin da tayi don abin bai amfana ta da komai,</p><p> Yanzun haka yazo ganin doctor kamal kam yawan damuwar dake damun shi,</p><p> Inda doctor yagano abin dake damun sheriff har ya sako mai zancen auren shi,,,</p><p><br /></p><p> Jirgin safiya muka biyo zuwa saudiya a,Riyadh muka sauka sai muka karasa garin makka kafin ayi sallah azuhur duk muna cikin garin makkah,</p><p> Dakina na wuce don indan huta saidai kuma zuciya na fam yake da zunlumi da tunanen abinda ke gabana,</p><p> Gashi kuma maganar siri ne ba bu damar in fada ma wani,</p><p> Duk da basan ko ya maganar dashen ciki yake ba nasan cewa abune mai girma,</p><p> Saidai inda nake jin saukin al,amarin shine kawai in ance indan yafara girma za,a cire ne amayar mata da abinta a cikin cikin ta</p><p> Wanan abin zan yi shine kawai don sheriff din mu mutun mai mutunci da sanin yakamata,</p><p> Koma maye ai dolene in sadakar da rayuwa na agare shi don in,taimaka mai kamar yadda shima din yataimaki rayuwa na ta fan,ni daban daban,</p><p> Tunda muka dawo daga wanan tafiyan Amal tagane cewa ina cikin damuwa, sosai tunda ba haka tasan nake ba,</p><p> Tunda ta tambaye ni nace mata ba komai tun lokacin tasan cewa bazata gane komai ba kawai ido tasa min,,,</p><p> Ita ko Aziza ba abinda ya damay sai farinciki kawai takeyi da an,nashuwar ta,</p><p> Aziza taima sheriff bayani cewa likitan ta yace nanda dn wani lokaci yanason ta koma tare dashi don zai dan gwada wani fasaha akasu tayadda ciki zai zauna mata,</p><p> Cikkn rashin yarda da maganar ta yace Aziza na fada maki cewa bani bukatar wanan plan din naki pls,</p><p> Nabarwa Allah al,amari na idan Allah yatashi bani haihuwa basai natafi wata uwar duniya ne ma har inda nake zaibani</p><p> Kisani cewa rabon mutun bai wuce shi, idan kikayi imani da tawakkali sai ubangiji maji rokon bawan shine sai ya karba muna addu,an mu,,,</p><p> Kuka tasa mai , maitsuma rai yadda yakasa daurewa har yabar mata dakin </p><p> Yafito waje,</p><p> Ga mamakin shi sai ga alamar innuwar mutun a cikin duhun daren,</p><p> A hankali yanufi gurin da ganin kowaye wajen zaune,,, fadima ce zaune cikin wanan duhun ta hada kafa da gwaiwa da alamar akwai abinda ke damun ta, </p><p> A hankali ya furta sunan ta cikin mamaki, </p><p> Sai na dago kaina nimadai din cikin mamakin may yafito da shi cikin wanan lokacin haka,</p><p> Tambaya yawatso min a gagauce, lafiya, may kikeyi haka anan cikin wanan lokacin,</p><p> Bakomai na iya furtawa, cikin dan karamin,sautin,</p><p> Gefen guda yasamu yadan zauna gab da inda nake, </p><p> Yadan kura min ido na dan wani lokaci,,</p><p> Can yace fadima har yanzu kina akan tunanen yan uwanki ne da suka tafi, kokuwa da akwai wani abinda ke damun ki ne azuciyan ki,,</p><p> Maimakon inyi magana sai kawai nadan girgiza mai kai alamar a,a,.</p><p> Kamar mai rada ya ce fadima baki da wanda yafini duk cikin fadin kasar nan,</p><p> Amma ace kina cikin wani hali nadamuwa wanda har zai hanaki sukuni da samun barcin </p><p> Duk ki fada min to waye kike da shi bayan ni da zaki fadamawa,</p><p> Ban kara cewa komai ba kawai dai sai nai shiru saboda nasan cewa duk tsananin tambaya bazan taba fada mai komay ke damuna ba,</p><p> Saboda alkawarin da na dauka na boye wanan babban sirin ga kowa,</p><p> Sai bayan raina, ba mai jin cewa ai nice nataimakawa sheriff, </p><p> Shima dai din shirun yayi har takai kamar babu kowa agurin saboda shirun da ya ratsa gurin,</p><p> Duk sai yaji ba dadi acikkn zuciyar shi, saboda yasan cewa lalai akwai abinda ke damun wanan yarinyar sai zurfin ciki irin nata bai bari ta fadi, komadai may ye zai kokari yasa mata ido sosai ,a,al,amuranta </p><p> Wata ajiyar zuciya ya sauke da karfi gamida fesar da wata iska irin ta dan relief din nan,</p><p> Yakara daga ido ya kalle ta sai wani irin tausayinta ya kamashi yasan cewa tana kokari dole ta shiga cikin irin wanan yanayin,</p><p> Narashin kowa nata kusa da ita hatta wace takawo ta kasar ta wuce tabarta,</p><p> A,hankali ya dan matso gab da inda nake zaune dan kalleni cikin tausayi,</p><p> Ya sa hannun shi yakamo hannu na yadan matse cikin nashi,</p><p> A raunane yace min kiyi hakkuri fadima da zanran kin gama karatun ki nida kaina zai kai har gaban iyayenki insha Allah,</p><p> Yakara matse hannu na acikin nashi yace min tashi kije ki kwanta ki dan huta zan san abinda zan yi ,</p><p> Kala ban ce ba na mike da niyar in wuce saidai kuma hannu na na rike a cikin nashi,</p><p> Shima dai din tasowa yayi a hankali ya zo gab dani yadan matse ni a kirji shi tayadda har ina iya jin yadda zuciyar shi ke bugawa,</p><p> Cikin sauri nayi kokarin kwace kaina daga jikin nashi, amma ina yarike ni gam,</p><p> Saida yai ra,ayim kanshi nasamu yasake ni</p><p> Tunda yasaakeni ban ko kara waigawa ba nai ciki da sauri, ina maida nunfashina ahankali,</p><p> Nadade barci bai dauke ni ba tu nen sabon salon da sheriff ya bullo min da shi nason ko yaushe ya hada jikina da nashi nakeyi,</p><p> </p><p> Hakana nakwana cikin wanan damuwar gari nawaye nasamu maman Umar wace yanzu take min kamar yar uwata jini,</p><p> Data saura min cikin fadin saudiya saiko salimat da ke tare dani,</p><p> Ban inya boye mata komai ba tana wankin kayan su umar a laundry saida ta matse kayan takuma gama jin bayani na </p><p> Saita zauna a dayan kujeran da nake zaune gefe ta dan kamo hannu na ta kalli kwayar idona tace min</p><p> Fadima kin dai fi kowa sanin cewa sheriff ba mutumin banza bane balle mu tuhumay shi </p><p> Don idan sani ne na dokokin Allah ke ma kinsan cewa yasan komai fiye da sanin mu,</p><p> Don haka wani zargi bai ko taso ba a tsakanin ku,</p><p> Tace kawai ni abinda na fahinta yana maki hakane don daukar ki dayayi kanar yar kaunar shi,</p><p> Kinko ga dole ne ki dinga gani irin haka ,saboda haka kada ko kisa wani zargi a tsakanin ku dashi,,,.</p><p> Wanan maganar na maman Umar yasa nadan ji sanyi araina nafitar da duk wani zargin sabon canjin da nagani ga sheriff din,</p><p> Hutun mu ya kusa karewa ga kuma shirin tafiyan da Aziza keyi dani zuwa gurin dashen cikin da za ai min na aje mata baby ta da zanyi,</p><p> Nasan cewa dole Ina kallo Amal da salim za su wuce madina don cigaba da karatun mu wanda daga wanan hutun insha Allah mun gama karatun mu ke nan,</p><p> Saura kamar sati biyu mu koma wurin doctor aziza a kasar indiya su Amal suka koma madina </p><p> Wanda sam sheriff baiso ace sun tafi sun barni ba saboda da yasan cewa yanzune zamu karatun mu na karshe,</p><p> Amal sun wuce da kwana biyu Hindu ta bugowa Aziza waya cewa su hadu Nigeria saboda wasu kaya da sukayo oda akasar chaina ance jirgi ya nutse dawa su don haka dole ne suje su ganewa idon su abinda ke faruwa,</p><p> Bada son ranta tabar kasar saudiya zuwa Nigeria da niyar bazata dade ba saboda tafiyan da zamuyi,,,</p><p> Tun da marancen ranan nake jin jikina bana jin dadin shi sam ga kuma gidan duk kusan kowa ya watse gidan yai min girma,</p><p> Don hakane saina dan koma dakina na kwanta daniyar kila indan nasamu barci na tashi zandan ji damar jikin nawa,</p><p> Mun muna mafarkin danayi yssa na farka inata zufa a goshina, duk da na farka daga barcin ina iya tuna mafarkin</p><p> Maciji nagani a cikin daki na yavkokarin shige min ajikina, </p><p> Naje in gudu sai kuma na kara gani gida ya nufoni gadan gadan ya shige min a jiki,</p><p> Innalillahi kawai nake iya furtawa a bakina ban iya koda daga hannu na don jiki na duk naji ba karfi,</p><p> Daidai lokacin naji takon kafar sheriff zuwa dakina,</p><p> Don nasan cewa in bashi ba wanda ya isa yatako har inda nake,</p><p> Da sallama ya shigo dakin saidai a kwance yagan ni da alamar ba lafiya tare dani ,</p><p> Da sauri yakaraso inda nake kwance ya na tambayar ko may yasamay ni ,</p><p> Baki na bude da niyar in mai magana sai naji ban iyawa,</p><p> Sai hawaye da suka dan biyo kumci na </p><p> Tabayana yakeyi arude baki da lafiya ne na kada mai kai almar ,a,a </p><p> Sai ya lura cewa na dafe kaina</p><p> Yakoma da sauri yadoko man magani yabani,na samu nasha </p><p> A hankali ya hawo gadon yadan rugumoni ajikin shi yana min addu,a sai nayi wani irin ajiyar zuciya ,</p><p> Na lunshe idona ina ji ina shakar kamshin turaen shi tun ina danjin karan A C har barci yadaukeni </p><p> Tundaga lokacin ban kara sanin inda nake ba,</p><p> Dasafe koda natashi sai kawai nakamajin jikina ba karfi ko ina nawa ciwo yake mun,</p><p> Na koma ko tashi da kyat nake iyawa don nauyin da nakeji ajikina,</p><p> Acikin wanan halin har azizata dawo tasa may ni a hakan ,</p><p> Saboda son ranta duk da taga banda lafiya saida ta tafi da ni wanan tafiyar hakana,</p><p> Sau kin abin tare da sheriff muka tafi yana ta faman nan nan da ni,</p><p> Ranan da mukaje washe gari duk muna office din likita da su inda lita naga yakaini su wani daki su biyu,</p><p> Bayan sunfitone aziza tace ma liktia ya dibani banda lafiya,</p><p> Saita ja sheriffs da hira akan harkan maikatar su,</p><p> Ina shiga likita yace in kwanta awin farko naji yace in tashi da sauri gabana ya fadi,</p><p> Sainaji yace min infita kawai basai yadibani ba zai dai bani magani,</p><p> Shiko sheriff tunda na shiga hankalinshi na gurin mu yanayi yana kallon hanyar office din doctor saigani nafito,</p><p> Tana gani na fito ta mike tsaye,,,,,,,,,,</p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 6⃣9⃣</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost true life story</p><p><br /></p><p>A hankali nafito da ga dakin likitan jiki ba kwari, Aziza tana ganina ta taso cikin sauri ta tare ni ta na fadin sannu fadima ya jikin naki,</p><p> Sheriff na tsaye gefe guda ya tsura min ido babu ko kiftawa, hannayen shi zube a cikin aljihun ,shiru yayi kawai yana kallon mu,</p><p> Wani dan takarda da doctor yace zai bani na magani , shine doctor yasa akawo muna don aje asiya maganin</p><p> Sheriff ne yakamata yatafi amma sai aziza ta caraf ta karbe takarda tace in zauna taje tadawo tana mai kashe min ido alamar kada in fada ma sheriff komai </p><p> Mamaki tabashi na rawan kan da yaga tana yi da ni,</p><p> Kofar dakin likitan ya duba inda sunan shi da phone number doctor ke rubuce,</p><p> Ya kwashe a wayan shi,</p><p> Saida yagama ruburun shi kaina na duke kasa alamar dai bana jin dadi ajikina, sam yasa na bashi tausayi,</p><p> Ya dan matso kadan kusa dani yace min mai ke da mun ke ne fatima,</p><p> Nai narai narai da idona wanda ya nuna alamar hawaye aciki nace mai nima ban sani ba fa</p><p> Aziza ta dawo dauke da ledar magani a hannu ta, tun anan cikin asibitin ta balla min tace min Insha,</p><p> Kwanan mu biyu a indiya muka dawo straight zuwa saudiya,</p><p> Hankalina gurin karatuna don haka ban ko huta ba na kama ha yar madina tare da Yusuf driver,</p><p> Saidai kafin in wuce Aziza taja min kunne sosai akan in bi a hankali dan Allah kada in yi garaje,</p><p> Kamar ince mata nifa likita bai min komai ba dan injin kawai yadora min a mara yace min sauka in fita,</p><p> Saidai kuma ina tunanen cewa kodai haka din ne dashen cikin da tace za,ai min,</p><p> Tunda nadawo Amal take ganin kamar na canza mata, sosai don ta lura da cewa ban son yawan magana kamar da</p><p> Sai kuma nida ke yawan cewa muji masallaci yanzu sam ban zuwa saidai in kwanta in ta barci, kawai,</p><p> Salimat tadawo da yar diyar tayi wayo sosai yanzu tazama big girl,,</p><p> Karatu nakeyi mai wahala yanzu sosai don dai duk inda na zauna sai kawai inta zuba gyangyadi,</p><p> Banda wani aiki sai barci,</p><p> Zaune muke falo muna hira da Salimat da ta kawo muna yini yau agidan mu kasan cewa yau ba karatu,</p><p> Duk irin abinda muka aje na ciye ciye a falon fruit kawai nadan dauka na sha,</p><p> Hira muke yi duk kan mu amma ni sai jefi jefi nake basu ansa daga inda nake zaune nadan dunkule wuri guda,</p><p> Salim yafito da shigar yan RACE don yana yawan zuwa wurin wasan race,</p><p> Gab da inda nake dun kule yazo ya dan zauna,</p><p> Wani irin kamshin turen dayasa yadaki hannci na,</p><p> Sai naji wani irin a,mai, yazo min a gigice natashi da sauri na</p><p> Wani irin kallo duk kan su suka bini dashi, sai kuma suka kalli junan su cikin mamaki ,,,</p><p>Ina shiga, dakin na nufi toilet nafara sharara amai saida nayi kamar zan amaye hanji na duk ka,</p><p> Amal ce tsaye bayana ta kura min idon mai nuna kallon mamaki,</p><p> Gado na fada nadan kwanta don inda huta saboda jikina duk yasake min,</p><p> Tunda muka dawo saudiya sheriff ke kula da yadda aziza ke wani farin ciki tana nadewa wuri guda,</p><p> Hakan yasa ya maida hankalin shi sosai gurin ta don yana son ya fahinci ko may ke faruwa da i ta hakana,</p><p> Saidai bai fahinci komai daga gareta ba,,amma hakan baisa ya daina sa mata ido ba,</p><p> Tare suke shi, da Aziza a cikin motar shi ke tukawa yau ba driver ba zai kaita wani shagon saida kayan shafa,</p><p> Saboda yasan cewa shagon na matane, yasa yacewa Aziza ta shiga ta fito </p><p> Aziza ta dauki yar poss din ta data sa kudi a ciki tabar babban jakar nata acikin mota saboda nauyi, ciki harda wayan ta,</p><p> Tana shiga sai ya dan gyara zaman shi a kujerar ta, a hankali,</p><p> Wani dan farin takarda yaga zai fito daga cikin jakar nata,</p><p> Sai yai zaton cewa kila wurin sauri ne ta jawo takardan gashi har zai fadi kasa,</p><p> Abinda yagani shiyasa shi gyara zama cikin firgita, takarda ne risit, na Artificial Insemination pregnant, mai dauke da sunan hajiya dakuma wata,</p><p> Yarinya yar kimanin shekara sha takwas da haihuwa,</p><p> Date ya diba sai gaban shi ya fadi, ras, saboda daidai ne da kwanan watan da Aziza tace tace mai likita yace ya na bukatar suje tare da shi a gwada sperm din su agani ko zai iya produced din baby acikin sauki,</p><p> Tabbas kuma sunje din har an debi sperm din nasu shida ita, an je gwadawa,</p><p> Fatima what ya mike zaune da inda yake zaune ya bude ganbun motar shi cikin tashin hankali,</p><p> A haukace yake kamar ya cin ma Aziza ciki ya shaketa, don ya matsu ta fito yaji may yasa akai artificial insemination don ya hana ya fada mata yace bai so don shi ba jahili bane,</p><p> Kuma wace ce akai ma dashen don risit yanuna cewa ba, Azizar bace,,</p><p> FATIMA zuciyan shi takara nanatawa sai yace ina yasan fadima da kaifin hankali da sanin ya kamata,</p><p> Kafin yai wani abu sai yaji karar wayan Aziza da tabari acikin jakarta yana ruri,</p><p> Kamar ya share sai kawai yasa hannu ya dauko wayar yadan na daukar kira batare da yai magana ba</p><p> Yaji murya Hindu ta,na fadin Aziza kina ko kula da time din komawar ku asibiti da yariyar nan don a binciki ko cikin na cikin koshin lafiya,</p><p> Bai karasa jin zancen ba ya kashe wayan cikin tashin hankali,</p><p> Idon shi ya kade ya komar kamar garwa shi, wuta, don bacin rai,</p><p> Aziza ce ya hango tafe tana tafiyan ta na kasaita ta nufo motar su,</p><p> Kafin ta iso yayi kokarin gyara motion din shi saboda dan nazarin da yayi akan maganar,</p><p> Bayan an gama sa mata kayanta a,buth din motar su tashigo motar tana fadin wassh Allah na duk na gaji tana mai kokarin dauko jakarta tana sa poss din ta ciki,</p><p> Fuskan shi ta dan kalla sai taga duk yanayin shi yacan za,</p><p> A hankali takara diban shi tace mai may yafaru taga duk ya can za lokaci guda,</p><p> Saida yasa hannu ya ahafa sumar kan shi yadan lashi busashen laben shi da yake ji kamar ba miyau,a bakin shi,</p><p> Yadan ce mata may kika gani halan tace haba dai sweet habibi, ai ba haka na barka ba</p><p> Dan murmushin yake yayi yace mata, kawai waya nayi da masu sauke muna injin din da mukayo oda yau wai kuma sun fasa sai nan da sati biyu killa,</p><p> Taidan dariya maikama da fito tace to ai ka huta, kai kenan kullun cikin aiki baka da hutu,</p><p> Har suka isa gida ita kadai ce keta zuban ta, bai ce mata komai </p><p> Sai tunane yakeyi yadda zai bullo mata idan ya kare binciken shi,</p><p> Tsaye yake da waya a hannu shi,yan saye da farar jallabi mai dan yagwai a gabn rigar anyi kamar anyi saka ajikin shi,</p><p> Noban Salim yake kira don ya fara tambayar shi,</p><p> Bayan salim din yadauki waya sun gaisa ne,</p><p> Ya danyi shiru jin kadan can yace ma Salim duk lafiya kuke ko Salim ya ansa da eh,</p><p> Yace, kowa na zuwa makaranta kamar yadda yadace ko suka ce mai eh,</p><p> Can yace to ita Fatima fa lafiya take, yakara ansa mai da eh Salim din yadan daga wayan yakamar yayan nashi yana ganin shi,</p><p> Sai kuma yakara maida wayan a kunnen shi ,,yacigaba da sauraren dan uwan nashi,,,,,,</p><p> Kashe wayan yayi cikin damuwa yasa hannayen shi biyu ya tokare su ga karfen da ke kofar su,</p><p> Yai shiru, tare da yin tunane kala kala azuciyar shi,</p><p> </p><p> Duk irin abin cin da salimat tasan cewa ina yawan ci su tagabatar min a gabana</p><p> Kassh amma yau kamar ta aje min guba nake ganin abincin,</p><p> Zargin salimat yafito daidai lokacin da na toshe baki har hanci na saboda wani amai da nake ji, yana taso min,</p><p> Sai bayan nagama aman nadawo falon ta, na zauna hankali,</p><p> Salimat ce naji ta dafamin kafada, ahankali nadago idona na kalle ta,,</p><p> Saida, ta zana kusa dani har takai muna iya jin hucin juna tace min fadima may yasa may ki,</p><p> Da sauri nadago nace mata may kika gani halan Salimat,</p><p> Nadan gyara daurin dake kaina kadan nace mata kawai ina ganin cikina yai min dadti ne kawai,</p><p> Ido ta kura min tace look fadima kisani cewa ba wai daukar wasa nai maki ba jinki nakeyi tamkar yar uwata taji kaunata wacce muka fito ciki daya da ita,</p><p> A hankali nadan dago kaina kalli Salimat sai kuma na dukar da kaina kasa,</p><p> Tabbas nasan cewa ban jin dadi jikina duk kwanakin nan, ba abinda ke min dadi gashi sam bana son jin koda kamshin ture na hatta sabulu wanka idan naji kamshin shi zuciyana duk sai ya tashi,</p><p> Indinga jin amai na taso min </p><p> Wanan karon hannu na biyu duk ta hada wuri guda tadan kara matsowa gab dani ta kalleni da kya sai naga wasu hawaye suna fitowa daga cikin idon ta zuwa kumcin ta,,,</p><p> Kai muka hada wuri guda nida ita mukayi kuka mai isar mu saida muka gaji,</p><p> Can tai karfin hali tace fadima wayai maki wanan abin</p><p> Waya cuci rayuwan ki haka</p><p> Ya akayi ki ka aikata zina,</p><p> Kalman da tasa na zina ciki shiyasani kallonta da sauri ina ce mata la,la,la tunda nake ban taba sha,awar zina ba balle har in aikata ta,ta,,,,,</p><p> Ta kalleni da kyau tace min waiyai min ciki toh</p><p> Dukar dakai na nayi don bansan ta inda zan fara mata bayani ba,</p><p> Kawai sai na dake mata akan lafiyata kalau, kawai dai banajin dadi ne,</p><p> Ido kawai tasa min bawai ta yarda da maganar da nai mata ba,</p><p> </p><p> Zaune nake saman gadona ba abinda ke fitamin sai hawaye,</p><p> Ina tsoro da fargaban maganar Salimat, tunda ta fara ganewa kada Amal ma da muke tare ta gane,</p><p> Allah Allah nakeyi har Aziza ta cire cikin ta kada wanda yagane cewa ina da ciki,</p><p> Don gudun zargi irin wanda Anty Salimat tafara min,</p><p> Nasan cewa ana iya jefe ni idan har hukuma taji,</p><p> Sheriff mutun ne mai yawan ibada nasan cewa sam bazai lamince min ba,</p><p> Ihun da naji Amal tayi ne daga dakin ta yadan katse min tunanen da na zurfafa ciki,,,</p><p> Da murnan ta iso har inda nake kwance ina kokarin tashi,</p><p> Fada min tayi saman jiki na da karfi saida naji wani irin abu cikin karfin hali da daurewa na dan mike ina mata dariyan yake</p><p> Tana murna ta na fadin Ummi nan acikin saudiya , tadan kara fadowa saman jiki na sai naga ta mike da sauri ta hadiye murnan data,keyi,</p><p> Ta dan kalle ne cikin firgici tace min fadima jikin ki da mugun zafi </p><p> Baki da lafiyane haka sai nadan wayan ce zancen kawai,</p><p> Lafiyata kalau may kikaji halan</p><p> Wani kallo ta watso min gami da dan taba gefen wuya na,</p><p> Kafin tai magana sai nace mata yaushe ummi ta iso tace wai yau takai kusan sati uku ai</p><p> sundai ki fada muna ne don kada muce zamuzo,</p><p> Nima na nuna farin ciki na sosai da zuwan ummin,</p><p> Don haka washegari muka shiga shirye shiryen taron Ummi da zata zo ganin mu daga makkah,</p><p> Duk abincin da a ka dafa komai na kasa ci daga ciki sai</p><p> "Ya,yan itace kawai nake sha kamar hauka, abinda takeyi tabari da sauri ta nufi hanyar kitchen hankali ta tashe ga abinda take hasa she</p><p> Kirana tayi daga kitchen din tace min inzo in kama mata aiki,</p><p> Ina shiga warin man da take suyar rotinar ya nashi hanci ai sai naci kamar in kurma ihu,</p><p> Kofar baya na nufa ina shirin kakarin amai,</p><p> Cikin sa,a aman bai zoba na, taso da kyat da niyar in koma ciki </p><p> Maman Umar din ce dai na ci karo da ita tsaye da cibin tsamar rotinar a hannun ta tana min wani irin kallon tuhuma, </p><p> Nai kamar ban gane nufinta ba nai niyar shigewa na ciki in barta,</p><p> Tareni tayi tana ce min, may take shirin gani a tare da ni haka,</p><p> Duk yadda naso in noke mata saida ta tsaidani amma fir nace mata Iam, ok</p><p> Sai kusan Yamma lis bakin mu suka iso saboda nisan da ke a garin wanan karo harda sister din su Amal wacce ke aure da yaronta aka zo,</p><p> Zokaga irin murna da farin cikin da muke yi a ranan,</p><p> </p><p> Sheriffudeen Ahmad shine yashigo karshe daga cikin su ,</p><p> Daidai lokacin nafito daki da murna na nafada bisa jikin Ummi,</p><p> Nalafe nadan wani lokaci batare da nai magana ba,</p><p> Itace ta dagoni a hankali tana min kallon mamaki tace fadima ke ce haka, </p><p> Sai na kara noke kaina ajikin ta ina dan dariya,</p><p> Sheriff na tsaye ya kura min ido gaban shi na faduwa saboda irin masifafen canjin dayaga nayi na lokaci guda,</p><p> Nai wani irin fari ko ina nawa ya ciko cif,cif kamar wata katuwar budurwa,</p><p> Gashin jikina yayi kwance lub, lub fatana yakara wani shiki da haske,</p><p> Jinda nayi su Amal na mai sannu da zuwa yasa nadan daga daga jikin UMMI na nufi gurin shi don in gashe shi,</p><p> Yana tsaye cikin shigar turawa yasa suit a jikin shi,</p><p> Har na isa gab da inda yake idon shi na akaina, yana min wani kallo cikin sha,awa,</p><p> A,hankali nai mai sannu da zuwa kamar yarda muka saba idan yazo,</p><p> Yadago yakalleni idon shi yayi wani jajir kasala ta sauko masa da kuma wata irin sha,awa,</p><p> Tana fisgan shi,,</p><p> Gabada ya lokaci guda duk ya birkice, wuri guda,</p><p> A sanyaye ya ansa min da cewa ya nake,</p><p> Nace mai lafiya lau,</p><p> Amal tace wai lafiya lau ko jiya da dare jikinta kamar garwashin wuta, yake don zafi,</p><p> Muryan bakuwar da suke tare ne da su tace wanan ce fadimar,</p><p> Amal tadan jawo ni tace itace fa kedai anty falmata,</p><p> Mai suna falnatan tace masha Allah sam barka,</p><p> Nadan murmushi yake na ce mata barka da han ya anty cikin ladabi da girmamawa</p><p> Hannu ta miko min alamar inzo gurin ta natako a hankali na zauna gefen ta inda ta nuna min,</p><p> Mukayi gaisuwa na musabi,a</p><p> Saida sukayi sallah har mu sannan muka zo falo gabadayan mu gidan don cin abinci dinner da aka shirya ma zuwan su</p><p> Su salim da Amal sai washe baki sukeyi,</p><p> Dan yaron Anty falmata na karba ina mai wasa UMMI tace min in aje shi kawai inzo muci abinci, </p><p> Kamar in ce bazan ciba sai dai nadaure natafi don kada UMMI taga banyi mata biyaya ba,</p><p> Sheriff dake zaune gefe da tasbaha a hannu shi guda, </p><p> Yanajiran azuba mai nashi sai dai duk idon shi na ga duk wani motsi nawa a fakaice,,,,</p><p> Wani irin shauki so da kaunar fadima kawai ke fisgan shi, </p><p> Ji yayi kawai yana son ya kasan ce tare da ita,</p><p> Bude abinci da maman Umar tayi don ta fara zubawa mutane yai daidai da shakar kamshin abincin da nayi,</p><p> Har ina ture Amal gurin tashi da sauri na toshe bakina da hannu guda na shige daki,</p><p> Duk suka bini da kallo gabadayan su,</p><p> Amal ce tace bansan wanan sabon salo da fadima ta dauko ba walahi duk aka bude abinci ko ta shaki warin turare sai ta ce wai ita mai, ta fadi karshe da alamar nuna ko oho,ho,</p><p> Ba sheriff ba hatta UMMI saida taji wani irin shock din zancen na Amal wacce ita bata kosan tanayi ba,</p><p> Ture kujerar dake gabanshi yayi ya nufi dakin nawa,</p><p> Ina ciki duke a bakin toilet inata kakarin amai </p><p> Ina,gamawa, sai nadago daniyar in ja kafa na zuwa kan gado na</p><p> sai na ji na kasa kuma ga sheriff a,tsaye gaba na ya kura min ido kur cikin tuhuma,</p><p> Ganin shi danayi tsayen cikin kallon tuhuman da yake min shine,</p><p> Yasa na, dan ja kafana nadafa bango don kiris ya rage min in fadi a yadda nake ji,</p><p> Hannu ya mika min alamar in miko nawa dole na mika mai hannu yakamani a hankali har ya kaini saman gado </p><p> Yazaunar dani ko yanzu ido yakara kura min, a hankali na sada kaina kasa </p><p> Don ban iya jure wanan kallon,</p><p> Muryan shi naji yana fadin may ke damun ki fatima,</p><p> Bakomai na ce mai haiyya ,,,</p><p> Kai kawai yakada yakoma falo zuciyar shi na ta mai wani irin tuhuma, akai na,</p><p> Lokacin da yashiga falon duk ido suka sa mai don jin ko ya mukayi,</p><p> Banda UMMI daketa cin abincin ta, mama umar ce ta yan ko min fruit a plate ta nufo daki na dashi </p><p> Sai Amal tace shine kawai abincinta yanzu nayi fada amma bataji sai ,,, bata karasa ba ya daka mata wani irin tsawa saida ta firgita don tsoro,</p><p> Ita batasan cewa maganar shi jinta yakeyi kamar zubar ruwan zafi a zuciyar shi,</p><p> Ummi tace Amal kin faye surutu da yawa kiyi mata fatan Allah bata lafiya kawai ba wanan surutun naki ba,</p><p> Sheriff baici abincin ba tashi yayi ya fita kawai duk suka bishi da kallo </p><p> </p><p> Ina kwance ba barci nakeyi ba idona biyu hannu na rike da handout ina kokarin dubawa amma tunane ya hana ni shakat,</p><p> Sheriff na dakin nawa cikin wata jallabiya baka yasa yar fulla fara daidai tsakiyar kai,</p><p> A hankali nadago idona na bishi da kallo har ya zauna, kusa dani </p><p> Minti kusan biyu da zaman shi duk munyi tsit dakin yace Fatima na ansa a tausashe da na,am,</p><p> Yace min tun yau she ne rabona da inyi period, dina, </p><p> Sai a lokacin na tuna da zancen period din da nakai wani lokaci ban gane shi ba, fa,</p><p> Kuma batare da na damu ba na share zancen kawai, abina</p><p> Ganin da yayi cewa bazan asa mai ba yasa shi mikewa yabar dakin cikin tashin hankali,</p><p> Washegari kowa kokarin cin break fast niko yayan itace ne a gabana inata masu shan hauka,</p><p> Ummi ce ta min Fadima koba kyson cin abinci ki daure kici hakana kinji ko zaki amayar ba duka zaki fitar ba dole a samu wanda yadan tsaya maki a ciki </p><p> Don kinga bake kadai bace yanzu, </p><p> Maganar bai wani bamu mamaki ba tun da bawai mungane ko may take nufi bane,</p><p> Sheriff ne cikin kamar hasala yace min in shirya ya kaini asibiti kawai,</p><p> Batare da wani bata lokaci ba na mike zuwa shiryawa,</p><p> Ina fitowa naji muryan anty falmata na cewa UMMI sun dace a gaskiya da yaya wannan itace daidai da shi walahi, </p><p> Yariyar ta burgeni sosai walahi,,</p><p> </p><p> Cikin shakku da fargaba nai wanan tafiyan zuwa asibiti ina ta rokon Allah yasa kada aga komai a tare dani,,,</p><p><br /></p><p> Likita ya auna ni yadda ya kamata inda yace, ma sheriffudeen Ahmad matarka nada ciki na wata uku kwance a maranta, kuma munyi bincike abinda ke ciki lafiya lau yake,,,,</p><p> Wani irin dam dam naji azuciya na sai naji kamar in kurma ihu don fargaba da rasahin sani mako mata ga sheriff a halin da muke ciki,,,</p><p> Sai yanzu nake nadama da danasai ciwo ne na rashin shawar da banyi da kowa ba har haka yasa may ni </p><p> Nasan cewa konayi rantsuwa yafi dubu ba mai yarda da cewa ba zina nayi ba,</p><p> Aziza Aziza may yasa zaki min haka na pls, keda kika ce da zan ran ciki yadan tsaya zakizo a cire maki abinki amayar maki shine zaki min haka Y pls, Y,</p><p> Wani irin kuka mai tsuma zuciya nakeyi a can ciki ciki don tsananin nadamar da ya lulubeni,</p><p> Motar naji anyi parking da karfi har saida na dan razana,</p><p> Nadogo kaina a hankali na kalli inda muke don ni azatona mun kawo gida ne,</p><p> Gefen maikatar su ne ya parker motar hakana,</p><p> Yafidda wayan shi da sauri naga ya bidan wata nonba hankalina duk ya tashi don na dauka hukuma zaikira</p><p> Can kuma naga ya tsaya yajowa ni takarda a cikin yar briefcase din shi, yadiba wani rubutu,</p><p> Sainaji yadan yi ajiyar zuciya kadan</p><p> Kaina yana kife inata aikin kukan da yasa may ni,</p><p> Kiran mai shi yayi naji yana cewa, doctor, Khan,</p><p> Sai yadan zagaya bayan mota don suyi magana,</p><p> Bayan sun gaisa ne da doctor yake mai bayanin ko shiwaye,</p><p> Nandai yadinga jefo ma doctor tambaya akan artificial insemination din da matar shi tazo da yariya don ai mata ko yayi a lokacin,,,</p><p> Doctor kan yace mai no, no,no d girl is already have two, week's pregnant b4,</p><p> </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣0⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,</p><p><br /></p><p> Motar yashigo tare da mai da kofar motar da karfi,,,</p><p> Saida nadan firgita, don tsoro, hakan bai hana ni cigaba da she,shekar kukan da nakeyi ba,</p><p> Shiru ya yi kawai ya dan kura min ido don takaicin wanan kukan da nakeyi yake ji ji yakeyi kamar ,,</p><p> Make ni saidai kuma da yai dan tunane sai kawai ya dan murmusa kamar bashi bane ke cikin bacin rai yan mintitika da suka wuce,</p><p> Jin hannun shi nayi ya dafani a hankali, tare da anbatar suna ,</p><p> Batare da na dago kai ba kuma ban iya ansa wa ba saidai na dan tsagaita kukan nawa kadan,,,</p><p> Wani irin ajiyar zuciya mai nauyi ya yi tun kun kafin ya fara zance shi,</p><p> Yadan dago min kai a hankali da niyar mu yi ido biyu dashi, </p><p> Amma sa na saurin kwantar da fuska saboda ban iya jure jimirin kallon shi ido da ido hakana,</p><p> Sai yadan yi murmushi kadan ,</p><p> A, hankali naji shi kamar may rada yace min nawa Aziza ta saye ki har kika amince da zuwa ai maki, dashen ciki ajinki ki,</p><p> Jin nayi shiru kamar ruwa ya ci ne saboda ba kara min mamaki nayi ba jin cewa yasan da zancen dashen ciki a jikina,</p><p> Wanan karon cikin daga murya, yake maganar shi,,,</p><p> Ina hankalinki yatafi, ina wayonda nasan ki dashi, ina amfani ilimin da kike yi yake, </p><p> Ashe ke zaman da kikayi da su hjy as a takari bai sa kin san halin dan adan ba, har yanzu,</p><p> Yadan tsagaita fadan yai shiru yana maida nun fashi guda guda kamar wanda zai make ni,,</p><p> Yace ki godewa Ubagiji Allah da wanan abin bai zama tabbatace da kin san kowa ye dan adam,</p><p> Nadago fuskana, cikin sauri jin danayi yana cewa wai dashen bai faru ba ,</p><p> Bayan yanzu likita ya yagama fada muna cewan ina da cikin wata uku a jikina,</p><p> Kamar yagane mamakin da nakeyi sai yace na,am kina da ciki a halin yanzu amma bana dashe ba, ciiii</p><p> Saina kasa daurewa inji abinda zai ce gaba nace,</p><p> Amma duk halin da nashiga ciki sheriff saboda kaine </p><p> Don ka na sadakat da rayuwa har akai min wanan dashen don farincikin ka,</p><p> Kataimakeni da yawa arayuwa wanda narasa may zanyi in saka ma dashi </p><p> Saiga Aziza ta samayni da bukatar intaimaka mata ai maku dashen ciki ajikina idan ya isa cirewa sai acire amayar ta da abinta a jikin ta,</p><p> Yan security da suka ga motar mu tadan dade tsaye gefe ne suka dan iso gare mu suna tanbayar mu ko lafiya ,</p><p> Sheriff yace lafiya shida matar shice,</p><p> Batare da yakara magana ba yaja motar zuwa gidan su na ainihi da nasa wanda mukafara zuwa garin madina muka sauka aciki dasu hjy tsohuwa,</p><p> Cikin gidan ya umurce ni da shiga ba tare da yin musu ba na bishi a baya,</p><p> Falon gidan muka zauna, </p><p> Yace in fada mai gaskiyar yadda mukayi da Aziza tun farko,</p><p> Batare da naso ba kuma banda yadda zanyi dole yasa na kwashe duk irin magan ganun da muka yi da Aziza har da likitan su nafada mai,,,.,</p><p> Dan teburin katakon dake gefen shi yabuga da karfi yace,</p><p> Aziza y pls y may yasa kikai kokarin rushe min farin ciki na,</p><p> Yamike tsaye yana cewa, Ya Allah, Subbahanal, Wallhamdullah Allahu, Akbar,</p><p> Kuka naci gaba dashi cikin sauti mai kashe zuciyar mutun dake sauraren kukan,,</p><p> Ji nayi ya zogab dani ta yarda har zan iya jin nun fashin shi yace min,</p><p> In dakatar da wanan kukan da baida wani amfani gareni,</p><p> Cikin kukan nace ya barni inyi kuka don abin kuka yasamay ni ni fadima may zan je gida in cewa mahaifiyata da yan uwana,</p><p> Yau nice dauke da ciki cikin da ba uban shi, atare da ni,</p><p> Shiiii naji yace min kamar yadda ake tsaida yaro idan yana kuka,</p><p><br /></p><p> Cikin san yayyan murya yace min fadima cikin jikin ki ni ne uban shi,</p><p> Ni nai maki ciki da kaina kika samu wanan ciki, najikin ki batare da an maki wani dashe ijin ba,</p><p> Asali ma banda labarin plan din ku da Azaiza koda hakan ya faru,.</p><p> Zubur na mike tsaye da ga zaunen da nake cikin mamaki nace </p><p> Nace sheriff kada ka zolaye ni pls</p><p> Bantaba jin kayi wani abinda ba daidai ba a rayuwar zaman da nayi tare da kai,</p><p> Balle har ta kai ga kayi wa kanka sherin yin Zina da ni fadima har takai ina dauke da dan shegen ka,,</p><p> Banko karasa zancen ba yayo cikina cikin zafi,zafi yana fadin kada ki sheganta min baby na fatima,</p><p> Dan cikin ki dan Sunna ne kamar yadda kowa wani dan sunna ya ke tin kaho da ubanshi ni ma haka cikin dake,jikin ki ya, ke tin kaho dani Ahmad lawal a matsayin uban shi,, na sunna,</p><p> Da mamaki nadago saboda gani nakeyi son haihuwa yasa shi wanan haukar, da ikirari,</p><p> Anya kuwa sheriff ne ke wanan zance, ina yawan alherin shi da addinin shi ya tafi,</p><p> Kamar ya gane may nake nufi, ko tunane araina,</p><p> Sai naji shi ya rungumay ni cikin jikin shi,</p><p> Magana yake min kamar rada, rada kamar kuma akwai, wani kusa da mu wanda,zaiji may zaice min,</p><p> Yace min Fatima ki kwantar da hankalinki, ki saurare ni da kyau , kiji bayanin da zan maki,</p><p> Ina rugumay a cikin jikin shi naji shi yana fadin </p><p> Ina son ki yafe min akan maganar da zan fada maki, </p><p> Yau shekara uku da wasu yan watan ni ke nan da aure na da ke fadima, </p><p> Dasauri na dan jaye jikina daga jikin shi ina mai kallon mara hankali ko kuma wani zautace,</p><p> Ya ce min yes abinda kikaji haka yake,</p><p> Tun zuwan ku nan madina bada wani dadewa ba wanan abin yafaru,</p><p> Shehi shine hjyn ki tasa ya wakilci auren ki, dani tare da wani dan takari na tare da su,</p><p> Ni na hanna afada maki a wanan lokacin saboda a lokacin nadauka auren rufin asiri ne kawai mukayi,</p><p> Nikuma, ina son ko ba komai ki samu ilimi daidai gwargwado, yadda zaki amfanana nan gaba,</p><p> Sai dai ba a dauki wani lokaci mai tsawo ba naji kawai ina bukatar wanan auren namu yaza mai daurewa har abada,,,</p><p> Na,kara daga kai na kalle shi, cikin mamaki,</p><p> Yadaga min kai tare da kafadan shi yace yes, I mean it,</p><p> Aure na da ke mutu ka raba ba wai na jeka na yi ka ba ne,,,Auren nadan wani lokaci kadan, a, a kireke a ranki cewa nida ke sai mutuwa,</p><p> Idona tab da hawaye, nace Sheriff yace min shiiiiii yasa dan yatsan shi ga baki alamar in yi shiru,</p><p> Tun da farko Fatima ban yarda cewa ina son ki ba nadai san cewa duk wani lamari naki tausayi yake bani,,,</p><p> Amma sai ga shi cikin ikon Allah naji na fara son ki, </p><p> Ban gama tabbatar da cewa ina sonko da gaske ba sai, </p><p> Sai lokacin da na sanki diya mace na dan dani zumar ki, nakuma gane baiwa da ni,imar da Allah yai maki, duk baki a cikin hankalinki,</p><p> A lokacin na tabbatar wa kaina ko zan rasa raina ba zan taba rabuwa da ke ba,</p><p> Ya nuna min cikina da hannun shi yace min ni nayi abina da kaina batare da taimakon wani likitaba,</p><p> Kara dagowa nayi nakalle shi again,,</p><p> Lokacin da baki da lafiya a makkah da Aziza tasamu urgent call daga Nigeria nadago da sauri na ina mamaki </p><p> Baki da lafiya aranan kina, ciwon ki na mara da kikeyi lokacin da kika gama period dinki,</p><p><br /></p><p> Sai na dukar da idon kasa, wani irin kunya naji, alokacin,, sai,</p><p> Abinda ya faru ya fara dawo min dan tunawa tiryan tiryan a lokacin,</p><p> Dana farka bayan nasha maganin da sheriff ya bani barci mai nauyi yadauke ga kuma tsoron mafarkin macijin da nayi sai kuma gidan da ba kowa a,lokacin mun rage yaw,</p><p> Ina farkawa Sheriff nagani akaina cikin damuwa a fuskan shi ina tashi yai ajiyar zuciya , </p><p> Shi ya taimaka min zuwa bayi har nakai kofan shiga bayin yace min idan nashiga tunda nayi mafarkin maciji in,yi wankan tsarki kafin in fito,</p><p> Sai na waigo da mamaki ina dan tunanen saboda mafarki da na yi,zanyi wanka,</p><p> Kawai dai sai na shege abina batare da wani kwankwanto,ba,</p><p> A bayi kuma ruwa zafi nafara anfani dashi, sai,daga baya nasa masu dumin da yace min indan shiga shiyasa har na dan ji saukin zafin da nake ji ,</p><p> Nadade acikin ruwa zafi na,gasa jiki dasu, hakan yasa har nadan iya, inya tafiya kadan da na fito , dana fito duk zafin da nake ji dazu ya rage min,,,,</p><p> Bayan nayi sallah ne, nakoma na kwanta tare da shan maganin da sheriff yakarabani a lokacin,,,,</p><p> Tunanen da yaga ina yi yasa shi yin shiru yana kare min kallo cikin tausayi,</p><p> Ina kai karshen tunanen nadago kaina da sauri muka hada ido sai ya kada min kai alamar eh haka zancen yake ai,</p><p> Durkusawa nayi kasa nakara rushewa da wani sabon kuka wi,wi,</p><p> Shiko, sheriff, Ido kawai yasa min nayi kuka mai isa na batare da yalalashe ni ba,,,</p><p> </p><p> Fadima wanan kukan da kike yi yafi maki dadi ga wanda Aziza taso jefa ki aciki,</p><p> Nadago kai nakalle shi may ye babbacin hakan da wanda taso sani ciki,</p><p> Aini gare ni duk dayane, basu da bambanci agurina ,</p><p> </p><p> A cikin zuciyar shi , wani iri yake ji gamay da fatiman , saboda duk ta birkice mai a lokaci guda,</p><p> Sai lumshe ido yakeyi, tuna ne kala kala, na shiga zuciyarsa, </p><p> Idon shin kan a kyakkyawar matar tashi,</p><p> wace yake ji tankar ya hadeye ta don so, a yan zu</p><p> Sai fadi yake cikin zuciyar shi yana cewa, Allah nagodema da kabani wanan yarinyar a matsayin mata ta,</p><p> kuma uwar "yaya na, anan gaba tabbas wanan yarinyar kyautace daga ubangijin shi,,</p><p> Duk da girman shi da kuma kudin shi da ikon shi, sai ga sheriff tsugune a gaban yar karamar yarinya fadima</p><p> Yadan riko hannu ta ya hade cikin nashi yace mata, </p><p> Fatima kiyi hakkuri ki rugumi kaddaran da Allah ya kawo muna ,ba don mun yi mai laifin komai ba,a,a hakan dai yaga daman bamu namu rabon,,,,</p><p> Cikin rashin fahinta, na kara kallon shi, inda yaci gaba da maganar shi,</p><p> Saidai ina son ki san cewa ni agare ni cikin yai min daidai, kuma yazo min a lokacin da nake bukatar shi,</p><p> Don Allah kadai yasan dalilin dayasa wanan cikin yasamu a wurin ki ba,a wurin ta ba can daban ,,,,</p><p> Don haka ni bawa ne mai rungumar kaddara, a,duk ta yanda kaddara ,yazo min,,,,</p><p> </p><p> Ya mike tsaye yana cewa idan kin gama kukan ki sai ki share hawayen ki, </p><p> Mutafi in kuma anan kike son mu kwana har ki huce U are welcome,</p><p> Da sauri na mike tsaye don gani nakeyi kamar zai kara tursasa ni ne kuma,</p><p> Yadan yi murmushin ganin irin mikewar da nayi cikin sauri don yasan cewa aikin gama ya,gama ko,</p><p> Ina batun fita daga falon yace min dakata a inda kike tukun, cak na ja, na, tsaya guri guda don bin umurnin shi,</p><p> Yai dan taki kamar biyu ya iso inda nake yace min,</p><p> Wanan zancen ban son kowa yaji ina son ki barni da Aziza tukun ,,,</p><p> Kai kawai na gyada mai alamar naji,,</p><p> Ji nayi yadan rungumu ni zuwa, jikin shi, a,hankali naji yakai hannun shi saman marana yana dan shafawa a hankali,</p><p> Jin danayi bazan iya jure hakan ba don yau saina ga yakoma min kamar ba sheriffudeen Ahmad din da nasani ba,</p><p> Zukewa nayi na silalo kasa na zamay jikina daga nashi a hankali,</p><p> Yadan kalli inda nake tsaye ina maida numfashi na guda guda,</p><p> Saida ya lashi laben shi yadan shafa kan shi kadan yai murmushi, kawai,,, </p><p> A, Lokacin karfe kusan daya na rana, don haka muka wuce gida </p><p> A mota kowa da abinda yake kullawa azuciyar shi, </p><p> Nidai kamar a mafarki nake jin zancen cikin nan nawa,</p><p> Wai yau ni fadima diyar inna yar kulu ce, ke dauke da cikin wani na miji batare da sanin mahaifiyata ba,</p><p> Ni dawani irin ido zan kalli inna na,</p><p> May yasa hjy ta wuce tabar ni a saudiya </p><p> Data tafi dani da hakan bai faru ba ,</p><p> Ya Allah ni kuma irin tawa kaddaran rayuwan ke nan,</p><p> Abinda muke ji ko gani yana faruwa, yan takaru sun koma gida da goyo ko ciki shi yafaru akaina,,,</p><p> Gab da zamu shiga kwanar unguwar mu ke nan, nake wanan zamcen zuccin </p><p> Ganin da yayi nafara shirin sulalo da wasu hawayen yace min </p><p> Idan har ina son Amal su gane irin halin da nake ciki ne to sai in matsa inta kuka,</p><p> Dole nadan goge hawayen dake shirin fito min cikin kunar zuci</p><p> A hankali nafito daga cikin motar yana tsaye gefe guda yana min wani irin kallon tausayi,</p><p> Shikam shi gaskiya duk da ya son haihuwa baiso hakan ta kasance dani ba a lokaci guda sai kuma yai istigifar cikin sauri don yasan cewa ba ai ma Allah shishigi,</p><p> Har na shige ciki yana tsaye yana kare min kallo cikin tausayi,</p><p> Ummi ce nasamu a falo zaune tana kallon yadda ake ta kiran sallah a garin madina da kewaye cikin tv,</p><p> Da murna ta tare tai min alamar inzo inda take, in zauna,</p><p> Ina zamake nan take ce min ina mijin nawa yake ne yatafi dani ya barsu da tunanen ko lafiya tun dazu,</p><p> Da mamaki nake kallon UMMI watau duk sun san da cewa ni matar sheriff ne dama </p><p> Amma ba wanda yataba fada min</p><p> Anty falmata ce takawo min fruit cikin plate ta zauna kusa dani tace ce min in sha kozan dan ji karfi jikina tunda bana son komai,</p><p> Sheriff yashigo UMMI ce ke rambayar shi cewa ko mun ga liktata sai yake cewa daga can muke ai,</p><p> Ya zauna da niyar cin abinci sai wayar shi tai kara,</p><p> Aziza ya furta a sanyaye yadan daga kai yaga irin re,action din da zan nuna,</p><p> Niko da sauri nadago kaina muka hada ido nai saurin kawar wa gefe,</p><p> Aziza ke sheda mai cewa zata iso saudiya tana son zuwa ta ziyar ci, su fadima ta dan dade bata gan su ba,</p><p> Sai yake ce mata hakan nada kyau ai shima suna gurin mu sun zu da su UMMI ziyar mu,</p><p> Cikin yawan take ce ma yaka ganar min fadimar pls,</p><p> A, fadima tai wani girma tayi kyau da ita ai,</p><p> Tai murmushin mugunta har yana jinta,</p><p> Yadan daga wayan yakalla kamar itace yake kallo a fili,,,,</p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣1⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p> Almost true life story,,,,,</p><p><br /></p><p> Su biyu ne, zaune a bayan motar ita Hindu wacce ta dade rabon da tashigo kasar saudiya </p><p> Tafi zama can Dubai suyi harkokin su ,saboda can ne world businesses center,</p><p> A hankali hindu tai ajiyan zuciya tace kina kokari Aziza nasan cewa in ba don wanan habibin naki ba da babu abinda zaisa ki irin wanan tafiyar haka mai nisa,</p><p> Saida tadan yatsine baki kadan sannan tare bari kedai a,gaskiya koni wani lokaci ina yawan mamakin kaina,</p><p> Duk nabi na su,su ce akan wanan bawan Allah,</p><p> Idan wani yace min zan iya tsaya in bata lokacina ga wani da namiji irin haka, ada wlh zance karyane,</p><p> Hira ce sosai sukai tayi tsakanin su gamay da auren Ahmad da Aziza tayi,</p><p> Sai gab da sallah magrib suka iso madina daga birnin Riyadh,</p><p> Cikin farin ciki kowa ke taron su, ana masu sannu da zuwa, </p><p> A hankali na, sauko daga saman gadona da Amal ta ce min ai sun iso,</p><p> Na, dan gyara rolling din kai, rigar da nasa rashin sani yasa ni sashi don ban zaci cewa yana nuna cikin nawa ba,.</p><p> Saboda yadan matse ni kadan kasancewar yanzu duk wani sura nawa yafito ,</p><p> Irin yadda mai sabon shigar ciki kanyi kyau, tana,haske haka na koma,</p><p> Falon nashigo cikin natsuwa, nake tafiya, sallaman da nayi a falon shi ya maida hankalisu gare ni,</p><p> Duk kan su sunga baiyanar cikina adai,dai wanan lokacin,</p><p> Aziza tamike tsaye don mamaki ta tako har inda nake ta riko min hannu,</p><p> Sam takasa boye farincikin da take ciki, ta ma manta cewa abin siri ne,</p><p> Sai tafara dan ta,taba min jiki cikin mamaki, tana ce wa iye fadima wanan kyawo haka</p><p> Gaskiya abin yayi kyau sosai,</p><p> Shigowar Sheriff kenan cikin falon don shima yadade baya gida tunda safe yafita sai yanzu yadawo,</p><p> Amal da ke gefe tai wani dan guntun tsaki wanda yasa kowa ya kallota,</p><p> Sheriff shigowa dakin idon shi akaina ya sauka, </p><p> Sai kuma ya kula da irin rikon da Aziza tai min,</p><p> Cikin hikima naga ya dauke mata hankali don ta sake,</p><p> Juyawa tayi wurin shi babu ko kunyar UMMI da ke falon tawani kama sunbantarshi,</p><p> Ina ganin haka najuya don in koma dakina sai UMMI tace min </p><p> Fadima zo nan ki zauna mana karki koma daki ki kwanta ,</p><p> Badon naso zaman falon ba na koma kusa da ummi na zauna,</p><p> Saida komai yadan lafa ne, kowa na sa harkan gaban shi </p><p> Aziza tazo har dakina ita da Hindu, suna shigowa </p><p> Aziza da sauri ta karaso har inda nake, ta janyo ni zuwa jikinta ta rungume tace fadima,</p><p> Kingama min komai aruyuwana tunda kin sama min abin faricikina da kuma alfahari,</p><p> Kin gusar min da duk wani bakin ciki da tashin hankalin da dagin miji zasu iya kumsa min nan gaba ,,</p><p> Saikuma ta juya inda Hindu take tsaye tana fuskantar ta, tace,</p><p> Hindu Duk wani barazan nan da zai taso nan gaba ina mai tabbatar maki cewa zan iya jurewa intun kareshi ga ko waye,</p><p> Saboda abinda nake nema nasa mu ko,</p><p> Suka dan tafa gami dayin dan shewa,,</p><p> Ashe duk wanan zancen da Aziza keyi a idon sheriff din mune bata sani ba,,</p><p> Maganar ta doke har cikin ranshi,</p><p> Jiyayi kamar yai magana a wanan lokacin, </p><p> Saidai kawai yadake yace bari yaga iya gudun su tukun,</p><p> Ina tsaye daga inda nake idona ya ci,ciko da kwalla, mamaki su da kuma tausayin kaina ya kama,ni,</p><p> Lalai mutum ba kyau wallahi ji yadda Aziza taita lalashi na akan in taimaka mata amma tun yanzu har ta fara ikirarin cewa zata iya fuskantar kowa akan wanan case din, </p><p> Hmmm mutum,</p><p> Saida suka gama shewan su ta waigo taganshi tsaye, a kofar daki ya zubo mata ido,kawai, sai basar da ita ya nuna mata cewa baiji komai da take fadi ba,</p><p> Cikin halin ko in kula yake ce masu may kuka samu haka kukasa fadima a gaba kuna murna,</p><p> Sai taji kamar ta fada mai komai a wanan lokacin don duk abinda zaiyi ayita </p><p> Sai kuma ta tuna cewa ai a kasar saidiya suke, </p><p> Yanzu ana iya sa ajefe su ko a rataye su bari kawai idan ta koma ta sanar dashi ko da tawaye ne,</p><p> Yafi,mata alheri lokacin cikin ya kara girma sosai ta yadda baza,a iya zubar, wa ba,, idan har an gane plan din ta,</p><p> </p><p> Suna fita dakin na durkushe inda nake tsaye na fara wani irin kuka mai tsuma zuciya ni kadai a daki babu mai lalashina,</p><p> Ji nayi andafa nadago kaina a hankali don inga ko waye,</p><p> Maman Umar ce ta shigo dakin </p><p> Ta tasheni a hankali ta jamin hannu zuwa bakin gado ta, zaunar da ni,</p><p> Ita ma din dai samun wuri tayi gefen gado ta zauna a hankali, </p><p> Tace min fadima duk da kina boye min matsalar da ki,ke ciki,</p><p> A, gaskiya ni bazan iya sa ido ingan ki a cikin wanan hali ba,</p><p> Kifada min may ke faruwa ne don in san ta inda zamu bullowa lamarin,</p><p> Saidai kafin kice min komai yanzu haka salimat tana hanyan zuwa </p><p> Idan tazo dole ne muji abinda ke faruwa dake,</p><p> Salimat ce tashigo don yiwa UMMI sannu da zuwa acewar ta,</p><p> Wanda ko azahiri ba haka zancen yake ba, maman umar ce ta bukaci da tazo,</p><p> Ganin da nai mata acikin shirinta yasa nagane cewa anan zata kwana ke nan,</p><p> Batai min magana ba a lokacin munyi hira sosai da su Amal har wani lokaci,</p><p> Mu kayi, shirin barci, sai a lokacin maman umar tashigo dakin itama,</p><p> Saboda mun san cewa a lokacin kowa na gidan yai barci,</p><p> Salimat ce ta fara matsamin akan lalai sai na fada masu halin da nake ciki </p><p> Saboda banda wanda ya wuce su a halin yanzu,</p><p> Dafarko na rasa taya,ya zan fada masu cewa wai, ni fadima ina dauke da cikin da ban tantace kowaye uban shi ba har yanzu,</p><p> Shin cikin dashe ne ko kuwa cikin sheriff ne, da yake ikirarin shi uban ciki,</p><p> Kaina na sada kasa saboda na rasa ta hanyar da zan fara zancen nawa,</p><p> Sai da takara kwantar min da hankalina ne </p><p> Na labarta masu komai tunda ga farkon zancen da aziza ta yaudare ni har zuwa dashen cikin ta kaini aimin,,</p><p> Da kuma abinda sheriff yafada min da mukaje asibiti,</p><p> Lokacin ne na fashe da wani irin kuka na ban tausayi,</p><p> Suma dai din kukan sukeyi, </p><p> Cikin kukan ne nake cewa may zance wa mahaifiya idan Allah yayi komawa na gida,</p><p> Nakara sa wani kukan kuma, </p><p> Maman Umar ce ta dan dakatar da mu daga sharban hawayen da mukeyi,</p><p> Tace min fadima ba karya sheriff yafada ba,nikaina nasan cewa kina da auren shi, akanki da dadewa </p><p> Da sauri nadago kaina ina kallon ta cikin mamaki,</p><p> Saboda haka maganar shi abin dubawa ne ,</p><p> Sanin halin sheriff da mukayi shi zai sa mu kara gaskanta da maganar shi,,</p><p> Saida salimat tadan dade tana nazari sai take cewa,</p><p> Inko hakane gaskiya Fadima kin yi sa,a arayuwar ki </p><p> Saboda kowace mace na kokarin ace ta mallaki miji irin Sheriff Ahmad,</p><p> Mutum mai tausayi da sanin addinishi ga taimakon na kasa da shi,</p><p> Kawai yanzu sai mu jira kamar yadda kikace yace zai dauki mataki akan aziza macuciya,</p><p> Wacce taso ta yaudari yar marainiyar Allah, saboda son kai da iya ha,incin tallakawa, ko na kasa gare su,</p><p> Haka Salimat da maman Umar sukaita lalashi na har saida suka ga nadan samu na tsuwa,</p><p> Salimat ta roke ni akan in kwantar wa kaina da hankali in ba sheriff hadin kai ta yadda zai samu yaci nasara akan azizan,</p><p> Naji dadi kasan cewa tare da su yau don ko ba komai na samu, dan natsu ga irin nauyin da zuciya na yai min duk cikin kwana kin nan</p><p> Ranan haka muka kwana muna hiran mu suna kara bani shawara akan in daure da kaddaran da yasamay ni,</p><p> Sai kusan asuba muka dan samu muka dan ritsa idon mu, bada wani dade wa ba muka ji kiran sallah ya karade ko ina,</p><p> Da safe saida salimat ta daidaici kowa na falo wurin yin break fast tasa na yin kwaliya cikin wani super wax mai ruwan green da dan adon flower yellow,</p><p> Cikin kayan sallah da ummi ke aiko muna dasune daga Nigeria ,</p><p> Dinkin ya matse ni cib,cib duk da ban iya daura dan kwalin atamfaba yau nadan kokarta, na dana wa kaina,</p><p> Kurciya na fito da kyau duk wanda ya kalle ni yasan cewa sweet seventeen ce ni,</p><p> Duk da ban son kamshi saida salimat tasa na daure nadan murza,</p><p> Tare muka fito falon da ita ina dauke da baby As,ma,u, a hannu na,</p><p> Fitowar namu yasa kowa kallon kofar dakin namu,</p><p> Tunda na tunkaro kofar idon sheriff ke akaina, itako Aziza tana min wani kallon jin dadi da farnciki hakarta ya fara cin ma ruwa,</p><p> Mai makon mu zauna asaman dinning table din sai muka zarce inda ummi take zaune saman wani carpet,</p><p> Aziza tace wa maman Umar ta dibar muna abinci ta kai muna,</p><p> Ina kallon miji da matar cikin su na rasa wanda yafi jin dadi gani na ahakan, yau,</p><p> Amal ce ta ce kai fadima waiko kece kuwa kodai gizo idona ke yi min</p><p> Salim yace gaskiya fadima nima dai ban fahinci ko may sirin ba fa,</p><p> Wani iri naji azuciya na saidai kawai nadan basar da zancen da yin murmushi kawai,</p><p> A, gaskiya babu yadda za,ayi in iya cin abincin nan da maman Umar ta aje min,</p><p> Spoon din nadauka, narike kawai na, kama wasa dashi, ,,</p><p> Ummuce tace min inci koda kadan ne,. </p><p> Duk yadda naso in daure inci nakasa,</p><p> Ikon Allah to may kike so kici yanzu ko haka kike son ki zauna da yunwa aciki,</p><p> Saida nadan marairaice murya nace UMMI ice cream zan sha,</p><p> Nan kowa yasa ko min ido, da caaaa akaina, </p><p> Saida naji wani dan nauyi, </p><p> Kafin ummi tai magana sheriff ya riga kowa yace baki da tausayi ne fatima,</p><p> Ki tausaya wakanki mana, tunda safen nan abu mai sanyi haka,</p><p> Hindu tai shiru cikin zuciyar ta tana tunane kodai sheriff yasani ne,</p><p> Amma ai da yasani da yai magana indai wanan mai kawo wa mutun Allah kusa ne,</p><p> Aziza ta ce ,a,a ha kawai idan ra,ayinta kenan dan Allah kubarta ta sha abinta ai ra,ayi ko,,.</p><p> Fruits maman umar takawo min cike da plate, ta aje min aiki na fara sha kamar hauka dama wani irin yunwa nakeji, sosai,</p><p> Plate din da nasha fruit na dauka da niyar zuwa kitchen in kaiwa maman Umar,</p><p> Daidai dan dogon corridor da zai kaika kitchen din naji an jawo ni da karfi,</p><p> Nadauka faduwa zanyi a lokacin sai naji na fada ajikin mutun,</p><p> Kamshin turaren shi yasa nagane sheriff ne,</p><p> Tsintar kaina nayi da kara noke kaina sama kirjin shi </p><p> Saboda dadin kamshin turaren shi dana shaka,</p><p> Da mamaki yakara matse ni cikin jikin shi, maimakon in zuke saina dan kara shigewa,</p><p> Hindu ce tagan mu acikin wanan yanayin, ta window dakin da take ciki,</p><p> Kara ware idon ta tayi don ta kara gaskanta idon ta ,</p><p> Tabbas nice da Ahmad zuwa tayi don takira Aziza tazo ta ganewa idonta, </p><p> Abinda tagani, don bazata iya fada mata da baki ba ,</p><p> Saboda irin son da Aziza takeyiwa Ahmad, idan batagani da idon taba bazata gaskanta taba,,</p><p> Daukana yayi cak daga wurin zuwa ta cikin garaje din motar ta inda ba mai iya ganin mu,</p><p> Saida na shaki mai isata na dan jaye jikina da sauri,</p><p> Sai a lokacin naji wani irin mugun kunya har ban iya daga idona don kunya,</p><p> Cikin dan kashe murya yace min fadima don Allah ki daina shan kayan sanyi pls kada ku samu matsala, keda baby na,</p><p> Sai alokacin na tuna rashin kunyar danayi yanzu,</p><p> Cikin kunya nadaga mai kai alamar naji,</p><p> Hindu na tajan hannun aziza zuwa wurin window suna laikawa tana fadin kidiba kiga ikon Allah da kanki,,,</p><p> Bakowa wurin wayau sai dogon corridor kawai suke hange,</p><p> Wai Hindu may kika gani ne haka ke jana, kamar wata rakuma,</p><p> Hmmm ba zaki gane ba idan nafada maki, tunda baki gani ba balle ki gaskanta, da idon ki,,</p><p> Fadamin may kika gani ne wai tadan gyara tace Ahmad dinki da wanan yarinya mai kayan cikin ki ya rungumay ta</p><p> Dariya tasa mata tace af ai saikiyi indai Ahmad ne haka yake ji da yan uwan shi , </p><p> Aishiyasa kikaga na daure ina son in kamo shi da kyau, </p><p> Kallon mamaki Hindu kemata na rashin gane gaskiyan da tagani,</p><p> </p><p> Har na kama hanya da niyar wucewa zuwa cikin gida, </p><p> Yace fatima na tsaya cak gobe zamu ganin likita </p><p> Don haka kada ki manta pls,</p><p> Nakada mai kai nawuce ciki </p><p> Dariya nake bashi yanzu sosai rashin yin maganar da ban so na kara komawa yar karamar yarinya sosai,</p><p> Doctor yakira suka shirya abinda in munzo goben za afada,</p><p> Doctor ya dinga mai dariya cikin zolaya yana fadin zai fada man gaskiya ne kawai, idan munzo</p><p> Washegari cikin dakewa yace Fadim ki shiya in maida ke asibiti likita yakarasa diba ki,</p><p> Likita ya kara dibani ya dan yi rubutu a wani dan pepper </p><p> Sanan ya fuskance mu yace a gaskiya Ahmad baby baida isasar kuzari saboda rashi kulashi da bakuyi,</p><p> Ban fahinta ba inji sheriff yace ma doctor </p><p> Doctor yace ma sheriff baka yawan yin sex da madan don haka baby baida wani kuzari aciki,</p><p> Hakan ma na iya sa abincikin cikin ya zo da matsala,</p><p> Harda dan zaburan mamaki sheriff yayi,</p><p> Sai yadan kalloni don yaga ya zanyi </p><p> Likita ya ce katabbatar da daga yau kafara aiwata da komai yadda yafara,</p><p> Wani irin kunya ne ya lulubeni a wurin kamar in nutse,</p><p> Wai nice ake cewa inyi taraiya da Sheriffudeen Ahmad a matsayin mata da miji,</p><p> Haba haba tayaya hakan zai faru kuwa,</p><p> Har muka fito ba wanda ya iya magana daga cikin mu,</p><p> Maimakon mutafi gida sai naga sheriff ya dauke har zuwa wani lafiyayyen gida yashiga har ciki da motar shi,</p><p> Ganin danayi haka nadan kalleshi da mamaki </p><p> Batare da yakalleni ba yabani ansa yace taimakona zakiyi fatima kada baby na yashiga cikin wani hali pls,</p><p> Ina ji inagani sheriff ya rabani da kayan dake jikina a hankali, , yana mai bani hakkuri da kuma kara yi min dadin baki,</p><p> Haka sheriff ya shiga aiwatar da aikin sa lokacin da idona yake a rintse saboda ba zan iya hada ido da sheriff ba ayau,</p><p> Sai lokacin da komai ya lafa, yaga damar hakkura da kanshi, badon ya gajiba,</p><p> Yadan kamo habar na yana kokarin mu hada ido dashi duk da kukan da nakd kunzawa,</p><p> Yadan rugumay ni saman kirjin shi,yana shafa min kaina a hankali yana bani hakkuri,,,</p><p> Shirun da yaga nadan yi yasa yadan kura min ido yana lunshewa, sai tunane kala kala yake idon shi kyan akaina, yana gode ma Allah da yabashi wanan yarinyar mai tarin baiwa da ni,ima</p><p> Hakan yasa yatuna da ranan da ya fara kusantar ta duk da ba ta cikin hayacin ta amma ya rude balle yau da take kusan idon ta biyu,,,</p><p> Hawaye masu zafi suka dinga zobu min duk wani farinciki da fatan da nakewa rayuwa na ya rushe a yanzu a dalilin wanan cikin najikina,</p><p>🐎ZEEE. MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣2⃣</p><p> BY </p><p>🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,</p><p><br /></p><p> Ina kwance na kasa koda dan motsawa daga inda nake </p><p> Nasan cewa tawa takare kenan tunda har haka yafaru da ni </p><p> Tare da kuma mutumin da nake ganin mutuncin shi fiye da kowa aduniya,</p><p> May zance ma duniya, may zan fadawa inna na, tare da sauran yan uwa na,</p><p> Jin da nayi yadan rugumoni ta baya shi yakara sani wasu irin hawaye masu dumi,</p><p> Suna silalo wa daga idona </p><p> Zuciyana tana min wani irin radadi da soya,</p><p> Lunshe idon shi yayi yana tunane kala kala na shiga zuciyar shi idon shi kan yar kyakyawan matar shi,,,</p><p> Murmushi jindadi yayi ya kara mirginowa dai inda nake kwance,</p><p><br /></p><p> Ban ankaraba naji shi yana shafar min mara ahankali dai inda "da ke kwanci, acikin ciki,</p><p> A lokacin naji yayi wani irin ajiyar zuciya mai sanyi,</p><p> Kada ki fushi ko kuma zargin Ahmda da baburuwan shi da yin ikon Allah,</p><p> Fadima na ji yana fadin ada can babu wata kalman So ko Kauna a tsakani na, da ke,,</p><p> Saidai tarin tausayi da dakuma taimakawa irin ta tsakani musulumi da dan uwan shi musulumi,</p><p> Sai kuma kyautatawa irin ta anfito jinsi daya,</p><p> Koda na aure ki kisan cewa ba na aureki bane </p><p> Koda na aureki bawai na aureki bane da niyar mu zauna irin haka na mata da miji ko abokin rayuwa, aa nadan wani lokacine kawai har in dan yi maku shiri kukoma gida,</p><p> Sannu a hankali idanuna suka fara hasko min wasu abubuwa daga gareki,</p><p> Tun ban yarda cewa ina sonki ba fatima sai gashi lokaci, guda idanuna na bukatar suyi ta kallon ki, </p><p> Kunnuwa na suna son suyitajin muryan ki, , haka har komai nawa yakoma kaunarki da taisayin ki kawai, ke min yawa azuciya,</p><p> Ban kara tabbatar da hakan ba sai lokacin da kuka zo hutun da ya wuce a makkah,</p><p> Tun wanan lokacin naji sha,awarki na yawan damu,</p><p> Hakan yasa na kasa samun sukuni har Allah ya nufeni da saniki a matsayin diya mace wacce ni ne mutum na farko da na fara kusantarki a rayuwan ki,</p><p> Sai lokacin da na dadani zumar ki nagane yadda kike ,</p><p> Na tabbatarwa kaina kozan rasa banzan iya rabuwa dake ba farima,</p><p> Akanki na gane cewa mata suna suka tara, saboda ada duk bugu guda nakewa mata,</p><p> Ashe abin ba hakana yake ba, da, akwai banbanci sosai a tsakani,</p><p> Duk cikin matana kece mace ta farko da na fara huda mata budurcin ta,</p><p> Alhalin duk auren yan mata kuke a wuri na ,,,,,</p><p> Yadan kara matseni a jikin shi kadan yace </p><p> Yai kamar yana shakan kamshin gashi,kaina,</p><p> Yace, Fatima kin taimaki rayuwana da abubuwa da dama kusan ince kin sadaukar da duk wani lokacin ki a kaina,</p><p> Duk wani abinda zai tai maki rayuwa na kin yi min su tun kina yar karamar ki,</p><p> Yakara jan suna na a hankali yayi wani dogon ajiyar zuciya </p><p> yace Fatima don Allah ki kasance a tare da ni ki taimaka min kibar wanan baby dake jikin ki yasa mu walwala ,</p><p> Saboda ki haifo min shi cikin koshin lafiya,</p><p> Yace har in zaki min haka to kisan da cewa kin gama min komai da nake fata arayuwa,</p><p> Mamaki maganganun dayake suka bani har saida nadan yi ajiyar zuciya,</p><p> Sheriff da nasani mai mata irin Nafisat da Aziza yan gayu shine ke wani zuzutani agaba haka,</p><p> Yakara fadin fadima ki fahince ni pls da sannu zaki gane ko waye Ahmad, </p><p> Haka dai yai ta lalabani har saida yaga nadan samu natsu </p><p> Sannan yakyale ni saida naga fitowar shi daga bayin,</p><p> Ko yagane cewa ina jin kunyar shine, yasa yadan fita ta falo kaman mai yin waya,</p><p> Na dan lalaba na mike, nafada bayin ,</p><p> Ruwa masu zafi nasamu ya ciki min a bath, nashige ciki a hankali, ina wanka wasu hawaye masu zafi su ka dinga zubo ,</p><p> Wani irin bakin ciki da tausayin kaina nake ji,,,</p><p> Ina fitowa na kimtsa jikina tsab kafin ya shigo,</p><p> Yadawo dakin cikin shirin shi tsab kamar ba shi ba,</p><p> Kallo guda yai mata sai ta bashi tausayi yadda yaga tadan takure gefe,</p><p> Yarinyar da ada yake dauka yar karamar yarinya yana raina mata wayo,,</p><p> Yau itace wace ta kawar mai da duk wani, kwadayin daya dade, yanayi ga diya mace,,,</p><p> Dan gefe na yazo yadan zauna,kusa dani, yace min kin shirya muje ko ,</p><p> Yanayin muryana na dole yaba mutum tausayi, nace mai eh,</p><p> Yakara tambayana ko akawo min abinci inci na kada mai kai kawai nayi,</p><p> Ya ja wani dogon numfashi yace to tashi muje ko,</p><p> A, hakali na mike saidai yanayin tafiya na yadan canza sosai </p><p> Ya dan tsaya daga baya yana kallon yadda nake takawa cikin dabara, yadan girgiza kan shi kawai,</p><p> Azuciyar shi yace yarinyar na bukatar kulawa gakiya dole ne yadauki mataki da wuri,</p><p> </p><p> A falon gida muka samu kowa zaune wasu na hira wasu na kallon tv ,</p><p> Sai ummi ce zaune da casbaha a hannun ta, tana ja,</p><p> Shigowar mu yasa Aziza shiga cikin wani guntun tunane </p><p> Shin tare muka fita da sheriff ko kuwa ya akayi muka hadu,</p><p> Abin mamaki sai naga yarikide min kamar da kamar bashi bane yaga min wa yan, nan kalaman dan lokaci kadan da suka wuce,</p><p> Anty falmata ce ke min sannu da jiki, dakuma tambayana ko zan ci wani abu,</p><p> Kifin inyi magana muryan Amal ne take cewa ai don taga kowa na damuwa da ciwon ta ne shiyasa taje kara narkewa mutane,</p><p> Abarni kawai idan naji yunwa nida kaina ai zan bidi hanyar abinci,</p><p> Ummi tace mata amma Amal baki da tausayi yarinya tana fama da lalura irin haka har zakina ce a kyale ta,</p><p> Dan murmushin yake nai ma Amal kawai azuciya na kuma ina cewa ummi ta kyaleta tana da gaskiyar ta sanin da tai min bana yan zuba,,,</p><p> Maman umar takawo min fruit's masu dan sanyi da kuma lemon kwanko,</p><p> Nadanci kadan sai kuma yau naji kawai ban ra,ayin ko fruit din </p><p> Wani irin amai ne yataso min narike bakina da hannu guda da sauri nature kayan plate din gefe na fada daki, na,</p><p> Aziza ce ta tashi da sauri tabi bayana don ita azaton ta ina shirin zubar da cikin ne,</p><p> Nafito daga bandaki ke nan tafado min cikkn daki a hasale,</p><p> Cikin tashin hankali take maganar ta, fadima may kikaje kikayiwa dana,</p><p> May aka baki ki kasha kike wanan aman haka,.</p><p> Don lafiya kalau kibar gidan nan koda natashi akace min kin tafi asibiti, wai,</p><p> Tana batun kara matsowa kusa dani , ni,ko ina tsaye ina kallon ta cikin mamaki,</p><p> Muryan Sheriff ne mukaji ta bayan mu yana cewa,</p><p> Aziza cikin ki ko nawa da mamaki ta waiga inda yake tsaye tana mai kallon mamaki,</p><p> Cikin rashi, facinta, ta ke mai, kallon shi wani iri,</p><p> Ya buga mata tsawa yace may kike zaton zatayiwa cikin da ke da uban shi,</p><p> Cikon da baida uba wanda ba,a yarda dashi shine ake ma yunkurin halakawa akoda yaushe,</p><p> Yanuna ni amma ba irin wanan mai uban ba, kuma uban mutum mai tsoron Allah irina ba,</p><p> Macuci wanda zai cutawa rayuwar yariyar da bataci ba batasha ba,</p><p> Ya karaso inda nake tsaye ya kama min hannu a hankali yace min in zauna,</p><p> Za taimagana yakara daga mata hannu yace may zaki fada min </p><p> Aziza shin mugun kudurin da ki kayi niyar yi, da yar mutane ko kuwa nida kike,so ki kulin ,sheri kikeso yi min bayani,,,</p><p> Dan murmushi tayi irin na yan duniyar mata, </p><p> Ta tako har inda yake tsaye,</p><p> Itama wani irin harara ta dankara mai tace kana nufin ka gane nufina akan wanan cikin da nasa ai mata dashe ko may,</p><p> Ya buga mata tsawa yace ke dan Allah yimin shiru, </p><p> In ba haka ba yanzu in kira maki hukuma atafi da ke,</p><p> Aiko kamar ya tunzura ta, ,, matstawa tayi har gaban shi ta rike kugun ta da kyau,</p><p> Tace har yanzu ban fahinci irin butulcin da kake shirin yi min ba,</p><p> O saboda rashi tausayi Ahmad shine zaka ce wai yanzu kai ne uban wanan cikin </p><p> Saida ya dan murmusa kadan yace mata, </p><p> Aziza kin so ki cuce Allah bai yarda ba kamar kuma yadda kikaso ki cuta wa mata, ta fatima da mugun nufin ki na kudirin sai kon haihu ko ta halin kaka,</p><p> Ai idar har kina son haihuwa da kin haihu da kanki </p><p> Kiga alokacin zan san cewa ki na kaina na</p><p><br /></p><p> Cikin nuna alamar bata fahince shi ba take maganan ta still,</p><p> Tace au kana nufin kun hada baki ne da fadima ku cuce ni,</p><p> Tobari kuji,</p><p> Sperm dinka da nawa likiti yai amfani dashi yasa ma fadima </p><p> Kaga kenan abinda ke cikkn cikin fadima nawane nida kai ,,</p><p> Ita nata wahalar kawai shine tai min rainon ciki idan ta haife in karbi baby na nagama da ita,</p><p> Idan kuma har kana da ja ga wana maganaa shirye nake da muje wurin duk wani hukuma ta duniya don ai muna sheri,</p><p> Saida sheriff yadan kallo inda nake zaune lokacin da tai kalamin ta na karshe,</p><p> Kafin wanin su yai wani zance muryan UMMI ce ke tambayar may ke faruwa ne haka,</p><p> Shiru duk kan mu ukun mukayi a lokacin,</p><p> Mamata dan kalli gefen da yake tace mai matar ka bata da lafiya kazo kuma kuna daga mata hankali haja a gabanta,</p><p> </p><p> Cikin mamaki take kallon ummi ta nuna inda nake da yar yatsarta tace</p><p> Fadima ce matar Ahmad kuma,. </p><p> Saita bushe da wani irin dariya tana tafa hannayen ta,</p><p> Tace mamaki yau kuma kulin sheri ne haka wai don aimin dabaran rabani da abinda na kwallafawa rai,</p><p> To karyan ku don baku isa ba wlh,</p><p> Ganin da yayi idonta ya rufe zataima harda ummi rashin mutunci yasa shi cewa cikin tsawa get, out my friend,</p><p> Ai baka isa ba Ahmad sai naji matsayin da kuke son ku sa cikina aciki tukun,</p><p> Ummi da bata fahinci zancen ba sai take cewa Alhamdullah mata biyu da ciki lokaci guda,</p><p> Aziza takara kawai ummi kallo tace wai nida wace matar tasa,</p><p> Wanan karon falmata ce a kofa jin da sukayi fitinar yana kara yawa suka taso gaba dayan su zuwa dakin ,</p><p> Tace kina nufin kice baki san cewa fadima matar shi bace tobarima kiji don inaga ita din ta rigaki auren shi, tana mai nuna inda nake zaune,,,</p><p> Tawani kyalkyale da dariya kamar wata tababa, </p><p> Tace yau naji na gani,</p><p> Hindu ce tayi kokari ta kusa kai cikin dakin taja hannun Aziza tana fadin ki kwantar da hankalinki Aziza muji bayanin su,,,</p><p> Hindu wa yan nan mutanen suna son su raina min wayo,</p><p> Kiji fa wai cikin da nasha wuya kafin samun shi ,shine yau suke son su cuta min akan shi,</p><p> Yai dan murmushi yace mata Hindu ki barta har in bata yarda ba sai mu koma gurin likita taji da kunnen ta ko,</p><p> Cikin fushi ta fita dakin Hindu ta mara mata baya,</p><p> Adakin su take ta zirga zirga taje tadawo,</p><p> Hindu tace saida na fada maki cewa karki yarda kiyi wanan plan din da wanan yarinyar kika ce min ai baza a samu matsala komai ba ke kinyarda da ita to yanzu gashi irin abinda ta jawo maki,</p><p> Kidiba irin wahalar da mukasha, da irin kudin da muka kashe akai,</p><p> Hanna tadaga wa hindun tana hade wasu miyau masu daci tace,</p><p> Bar wanan zancen Hindu aiba zaiko sabu ba wai bindiga a ruwa,</p><p> Ni za,ai wa wanan drama din,</p><p> </p><p> Da sauri ta jawo jakarta ta lalibo wayarta, </p><p> Number doctor Khan takira bayan sun gaisa take sheda mai cewa tana son su zo wurin check up da da wanan yarinyar , </p><p> Doctor Khan yai dan shiru nawani lokaci, can yace mata, </p><p> Ai bai ma wanan yariyar komai ba saboda yarinyar nada ciki already a lokacin,</p><p> Hakan yasa baisa mata komai ba don babu zancen yin artificial insemination, ga wanda ke da ciki,</p><p> Yakare zancen da cewa ta diba prescription din da yabata tagani zata ga komai ai a rubuce,</p><p> Da sauri ta jawo jakar da tasa takardun a ciki diban farko ya nuna mata cewa ba ai min wanan dashen ba,</p><p> Ta wurgar da wayan don ta daina jin zan cen doctor Khan wanda kamar ruwan zafi yake kwararo mata a kune,</p><p> Sai a lokacin take tuna nen cewa kudin da ta tura mai na aikin tabbas bai cire ba har tanawa Hindu complain din haka,</p><p> Aiko nan da nan idonta yakoma kamar garwashin wuta,</p><p> Sun wani kade sunyi jajir</p><p> Yau ita Aziza za aiwa rainin wayo haka,</p><p> Ita Ahmad zai wa cin amana haka,</p><p> Tare da yar yarinyar da take ma daukar yar ficiciya,</p><p> Wasu irin hawayen bakin ciki suka ahiga zubo mata, daga idon ta,</p><p> Tarike kan ta da hannu biyu,tana fadi sharaf saman gadon ta,</p><p> Tashiga rusa kuka kamar wata yar karamar yarinya,</p><p> Ita Aziza za aiwa rainin hankali irin wanan babu abinda zata sa agabanta wanda bata samay shi ba,</p><p> Babu wani wanda zai mata wanan rainin hankalin ta kyale shi,</p><p> Kowaye dole ne saita dauki fansa akan wanan cin fuskan da ake shirin yi mata,</p><p> Hindu ce takara kwantar mata da hankali akan cewa ta bari,a bisu a hankalin har ta dau fansa a,kan duk wani cin amanar da Sheriff yai mata,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Dan Allah kuyi hakkuri saida na gama typing tun a,round six saboda yau weekend ne ashe banyi storing ba sai ya goge kuma wlh nagaji da typing,</p><p> Pls kuyi min afuwan 👏👏👏👏👏</p><p> </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣3⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,</p><p><br /></p><p> Ina daki takure wuri guda, sai tunanen abinda Aziza tace min yanzu keta min yawo a hankali,</p><p> Watau Allah ne ya rufa min asiri da ya kawo min sanadin wanan cikin, najiki,</p><p> Da Allah kawai yasan irin bakin ciki da tashin hankalinnda zan shiga, akan wanan cikin ukubar da ta , tashi sani,,</p><p> Salimat da Amal suka shigo dakin a tare, yadda salimat tagan ni zaune, cikin damuwa,,</p><p> Amal ce tazo,Gefena ta zauna muna dan fuskantar junan mu nida ita,</p><p> Naji muryan ta na fadin Fadima a gaskiya kin bani mamaki kwarai,</p><p> Yanzu ace har kin yi wanan plan din keda Aziza muna tare wai ban sani ba fadima,</p><p> Tana kada kafa tana magana cikin fushi, ,</p><p> Takara waigowa takale ni tace min fadima na fada maki cewa Aziza ba mutumiyar arziki ba ce,</p><p> Ki ka ki yarda da duk wani shawaran da nake baki akanta,</p><p> Ki ga mace haka ai kema kinsan cewa ba tsarar yin ki bace,</p><p> Salimat tace Amal ke nan, ai ke ayadda ki,ka gane kowaye Aziza Fadima bazata gane hakan ba ,</p><p> Don tazo mata da fuskan musulunci ne saboda fadima ce tie get din ta dama,</p><p> Kawai kirabu da mutun macuci,</p><p> Yanzun dai ai Allah yafita yakuma fi sherinta,</p><p> Ina jin su amma har suka kare maganan da zasu yi ban iya daga kai na kalli inda Amal take ba,</p><p> Saboda kunya dakuma wani irin nauyinta da nake ji,</p><p> Don nasan cewa tanzu tasan cewa sheriff yai min ciki</p><p> To a yaushe ,kuma a ina, ?</p><p> Sai kawai na ji wani irin hawayen bakin ciki na silalowa da ga idona,</p><p> Subbahanallahi fadima na hanaki wanan kukan baida amfani wlh kisan cewa bake kadai ba ce yanzu,</p><p> Amal ta dafani tace min haba matar yayan mu </p><p> May kuma zai saki kuka matas sai nakara jin wani zafi,</p><p> Da bacin rai kamar in ta dukan ta, nake ji,</p><p> Salimat ta kawar da zancen da Amal ke ta tsokanata, </p><p> Ta ce min waiko fadima kina karatu kin san fa mun kusa fara exam ,</p><p> Sai a lokacin na tuna da zancen wani karatu can don, har na man da zancen karatun naga abinda yafi karatu fitina,,,</p><p> Saida Amal ta dan fita dakin Salimat tasamu tadan matso kusa dani kadan tace min,</p><p> Bana son wanan kukan dakike yi fadima watau baki rugumi kaddara ba ko ,</p><p> Mutum zai iya yiwa kasan abinda Allah bai tashi yi mai ba,,,</p><p> Nadan girgiza mata kai, kadan tace, kinga dai yawan bacin randa kikeyi zai iya jawo maki wata lalura,</p><p> Ki daina haka na ,ki godewa irin baiwar da Allah yai maki,</p><p> Haka taita min kalamai masu dadi har hankali yadan kwanta nai mata Alkawarin insha Allah zan daina,,,</p><p> Naji tai shiru nadan wani lokaci, can tace min </p><p> Fadima ina son ki yarda da mijiki don gudun shiga hakkin aure ,</p><p> Ada rashin sani ne yanzu ko kin san komai sai ki dauki damaran kyautatawa a tsakanin ku,</p><p> Saboda gujewa wa fushin ubagiji ki, </p><p>Da ma duk wanda yakama, hanyar Aljanna zaita haduwa da abubuwa, masu wuya wanda zuciyar mutun bataso</p><p> Haka na wanda yakama hanyar wuta shima zaita haduwa da abubuwa da zuciyar shi ke so,</p><p> Shiyasa aka ce daga cikin hakkuri, da ake son mutum yayi cikin rayuwan sa </p><p> Harda hakkurin biyayya ga Allah da manzonsa, da kuma,hakurin yarda da kaddara kowace iri ce dan gujewa sabon Allah,,,</p><p> Ki daure ki ja mijin ki a,jiki shike karasa shakuwa da yarda ta kara dauruwa a tsakanin ma,aurata,</p><p> Kisa ni cewa duk kan ku uku matan shine, kowa ce da ga cikin ku da halinta zai zauna da ita,</p><p> Don haka kada ki bari abarki abaya,</p><p> Idan baki zama ta farko ba kada ki bari ki zama takarshe a gurin shi,,,</p><p> Shiru nayi ina ta ina jin wani kuna a zuciya na,,</p><p> Ina kuma,sauraren ta har ta kare ta mike tana fadin cewa gobe in shirya zamu tafi ziyara don in kai wanan cikin gurin ziyara,</p><p> Hakan yasa nadan murmusa don ni kaina nasan cewa na dade rabona da zuwa ziyara,</p><p> </p><p> Duk ilahirin gida jen shi yasa ansa mai CCTV a boye batare da sanin kowa, ba,</p><p> Saboda tsaro da gudun wani abinda za a iya kara kullawa,</p><p> Maganar Salimt ne keta min yawo a kwakwal wa na,cewa in bi mijina to ta yaya, hakan zai faru,,,</p><p><br /></p><p> Washe gari da safe na fito falo ko zan dan wal,wale kafin mutafi ziyara rauda, anjima,</p><p> Aziza da Hindu sun sa sheriff tsakiya kamar ba bu abinda ya faru ,jiya tsakanin su,</p><p> Azuciya na ,nace tabbas salima kin yi gaskiya zama saida gwanan cewa,</p><p> Ummi ce ta fara hangoni ta ce min a fatima kin tashi ko zo ki zauna nan ki karya kinji,,</p><p> Sai nadan waiga inda suke zaune don gaishe su ,,,</p><p> Muna hada ido da Azizat tai min wani irin wawan, harara </p><p> Sai na dan dukar da kaina don a gaskiya ban iya mata rashin mutunci ko kadan,</p><p> Sheriff yace min inzo in zauna gefen su sai nadan marairaice murya na nace mai gurin UMMI zan zauna nagode,</p><p> Sautin murmushin shi na ji itama azizan shi tawaiga don ganun abinda yakewa murmushin,</p><p> Nice yabi da ido har na zauna, kusa da inda ummi ta mayar kamar dakinta gefe guda daga cikin falon,</p><p> Wai don ta jaye mai hankali shi daga gare ni sai ta dauko jam tana shafa mai a bread din shi tana wani , kokarin matse jikin ta da nshi,</p><p> Tamiko mai yace a,a barshi kawai na koshi zan je in sha fruit, da mai cikin can,,,</p><p> Itama yunkuri tayi ta mike tsaye tana fadin barin riga ka kagin ka isa, nima in taya ku,,</p><p> A hankali ya lunshe idon shi yai dan takaittacen murmushi,</p><p> saboda yasan cewa Aziza nada wani manufa azuciyar ta gamay da ni,</p><p> wanda ba zai taba yarda hakan ya faru da, ita insha Allah,</p><p> Dar dar nake da ita ta zauna tana wani nan ,nan da ni,</p><p> Sai kawai naji fruit din sun fita min a rai sam,</p><p> Ganin da yayi ta takura min har ban iya shan fruit din yasa ,</p><p> Shi mikewa yana cewa zai je ya dawo, yanzun nan,</p><p> Yana fita tabini da wani mugun kallo wanda bani ba har ummi saida ta tsargu da ita, </p><p> Suka tashi suka bar falin zuwa cikin dakin su da suka sauka,</p><p> Suna shiga Hindu tayi shewa tace mutumiyar kin yi wlh kinga gun ma da kika daure kika nuna afili cewa ba komai,</p><p> Kinga yanzu sai mu fara shirin yadda za mu bullo wa lamarin,</p><p> Tun bayan faruwan wan rikicin sai yau na kira sheriff a wayana wayanda bansan inda ma na jefata ba, da,,,,</p><p> Kiran farko yadauka yana mai cewa Assalamu aikum,</p><p> Cikin siri,riyar murya na ansa mai sai kuma na kasa mai magana</p><p> Nai shiru kawai ina kalon kasan daki,</p><p> Muryan shi naji yana cewa fatima kiyi magana mana,</p><p> A hankali na ke ce mai zamu tafi Rauda ni da salimat , anjima kadan,</p><p> Shiru yayi can yace aida ni yakamata mu tafi bada salimat ba don muje mu gaida fiyayyen halitta tare da Sahabban shi, ko,</p><p> Amma tunda da salimat zaku tafi sai kun dawo saboda ni har na riga kuzuwa don yan zun haka daga can nake dawo,</p><p> Dàn Allah ku kula da kan ku saboda irin yawan da akeyi wurin ,</p><p> A hankali na ce mai to,</p><p> </p><p> Tare muke da Salimat harda Ummi da falmata duk sun biyo mu,</p><p> Bayan munyi sallah muka isa cikin rauda don ziyara,</p><p> Nidake kokarin wajen tare wa, mutane fili don suyi nafila, raka,a biyu,,</p><p> Sai gashi yau na kasa dole nice aka tarewa gaba da baya har na samu na,idar da sallah na dade zaune gurin ina rokon Allah mafita akan lalura, ta tare da naiman kariya, daga duk wani sheri,</p><p> Ummi da falmata suna kallon yadda nake komai nawa acikin tsanaki da kwanciyar hankali,</p><p> Hakan yasa su kara godewa Allah da ya Ahmad irin matar da suka dade suna mai sha,awan yi,,,</p><p> Muryan falmata ne yakatse ni lokacin da nake tsaye ina ma manzo na salati,</p><p> Tana fadin kiyi adduan Allah bayas da masu albarka, dayawa,</p><p> Maganarta yasa ni dan yin murmushi kadan, kunya yakamani na dan dukar da kaina kawai,,,</p><p> Motar salim ce muka shiga, ina baya tare da anty Falmat da Salimat ummi ce gaba tare da Salim</p><p> Munje har bakiya aranan, </p><p> Muna kan hanyar mutadawo wane Sheriff yakira layi na,</p><p> Yace min ina fatan kun kama hanyar dawo wa yanzu saboda baby na kada ya wahala,</p><p> Kin san Allah ya sauwakawa mace mai ciki kaifin ibada,</p><p> Cikin jin kunya don banson zance yai nisa don gani nakeyi su falmata da salimat na jin mu ,</p><p> Na ansa mai a hankali da fadin eh,,</p><p> Mundawo gida lafiya bawa ni damu atare dani ko kasala kamar yadda nasaba ji ajikina duk kwanan kin nan,</p><p> Duk wanda yagan,ni yasan cewa ina cikin walwala yau din,</p><p><br /></p><p> Abin mamaki yau harda dan abinci da ummi tasani gaba saina ci nadan tsankwara kadan,</p><p> Batare da nayi amai ba,,ni kaina nayi murnan hakan </p><p> Don har nake cewa salimat yau banyi amai ba,</p><p> Haka mukai ta zama gidan mu tab da baki kala kala,</p><p> Kowa ta shi irin lalurar da ya kawo shi</p><p>Irin Aziza da zaman hada plan kawai sukeyi a madina,</p><p> Saidai tayi rashin sa,a saboda ta manta cewa a babban birnin da isalama take ne duk cikin duniya,</p><p> Annabi yace idan duniya ta kusa kare har addini zai kasu kashi kashi, kuma duk islam ne </p><p> To idan har ana son a gane alkibila ta gaskiya aje garin Madina,</p><p> Har duniya ta tashi garin Madina suna akan sunna ce ta gaskiya,</p><p> Baza su taba canza alkibil da manzo ya dora su akai ba,,,,</p><p> Don haka addini ce sahihiya a madinan kusan duk bukata ta alheri ta wanzuwa ga bawa, amma banda na sheri,,,</p><p> Duk yadda taso ta fara aiwatar da niyar ta takasa dole suka shirya tafiya komawa Dubai har suje su kara hada sabon plan in yaso sai su dawo da shirin su,,,</p><p> Washe gari tunda safe suka shirya da niyar bin nirgi daga madina,zuwa Dubai,</p><p> Ina tsaye a dakina ina shirin fita zuwa school yau,</p><p> Aziza ta turomin kofar daki ,</p><p> Jin yadda aka turo kofan yasa na kalli hanyar shigowa da sauri, don inga kowani mara hankali zai min haka,</p><p> Ganin yanayin da takene ba cikin kwanciyar hankalin ta take ba yasa ni nadaure na gaishe ta, acikin sakin fuska,</p><p> Hannu ta daga min alamar inyi shiru,</p><p> Tadanzo gabana tazagaya harta bayana ta na kare min kallo </p><p> Ina tsaye cikin doguwar riga mai yar guntunwar hannu, baka tadan matse ta tsakiya, sakuma kasar rigar tadan bude kamar rigar indaya </p><p> Flower farin zare ne akai yi mata a tsatsaye nikaina nasan cewa rigar tai min kyau so sai,</p><p> Saida takare min kalli da kyau tadawo ta gabana ta tsaya gab da ni har muna iya jin nunfashin junar mu,</p><p> Ta nunani da dan yatsan ta tace fadima ina mai tausaya ki da kika yaudari Aziza a rayuwan ki,</p><p> Aziza ba a cutar ta a kwashe lafiya, kisani cewa </p><p> Ahmad nawa ne kaida bada kowace mace ba haka kuma wanan dan dake a cikin cikin ki nawane har abada ,,</p><p> Wani karfin hali naji yazo min da tace hakana,</p><p> Nadan kali inda take tsaye tana wani dan buga kafa nai dan murmushi irin mai ba mutun haushi</p><p> Nace mata, tunda har Ahmad din da kike gadaran cewa naki ne ke kadai bada kowace mace,ba</p><p> Gashi yau yadawo ga yar karamar yarinya har yakai ga mata abin dake kikadade kina bida da kudin ki da ilimin ki,</p><p> Taiwani kukan kura kamar zata shake ni, ashe Hindu nata wajen kofa tana kallon masu shigowa da fice agidan,</p><p> Ta rike mata hannu ta baya tana fadin ki,kan mantacewa agarin da shariar musulunci tafi karfi muke aziza,</p><p> Takai kusan minti biyu tsaye tana min wani irin mugun kallo na tsana </p><p> Ina tsaye kyam ina kallonta babu kowani tsoro,</p><p> Ganin kallon bai da alamar karewa yasa nadan geza da gefenta nayi tafiyana zuwa wurin mirroww na din in daura dan kwalina,</p><p> Saboda time na kure min na zuwa school,</p><p> Tai wani irin kutawa Hindu najan ta suka fita dakin suna fadin cewa zamu hade dake yarinya very soon,</p><p> Saida suka fita nabi suda kallo kuma ina mamakin kaina wai yau nice na iya tsayawa gaba da gaba ina bawa aziza ansa </p><p> Duk da nasan cewa bata da gaskiya amma nasan cewa hakan bsidace ba tunda ita ba warin yina bace,.</p><p> Kafin indaura Naifal dina Yashigo dakin rike da yar briefcase din shi, da alamar cikin sairi yake,,</p><p> Saida yai min wani kallo na sha,awa tukun sanan yace min ya muka kwana,</p><p> Ina tsaye nadan jingina da mirirrow kaina yana kasa,</p><p> Nace mai Alhamdullah,</p><p> Masha Allah yace, yakaraso ya man namin kiss a tsakitar goshina,</p><p> Kunyan haka da yake min nake ji sosai</p><p> Muryan shi naji yana cewa ina son in je in sauke su Aziza airport yanzu, </p><p> Yana fadi yana kallon agogon hannunshi,</p><p> Yadan kallo ni yace min kada ki damu kanki da duk wani barazanan da aziza zataimaki </p><p> Ashirye nake da daukar mataki a kanta,</p><p> Har zai fita sai na tsinci kaina ina may mai fatan alheri da adawo lafiya,</p><p> Saida yadan waigoni don mamaki,,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣4⃣</p><p> BY </p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost true life Story,,,</p><p><br /></p><p> Tun tafiyar su Aziza sai gidan namu yakoma normal kamar yadda muke ada can babu wani haya niya,</p><p> Daga can sheriff ya bugo muna waya cewa yatafi Riyadh ba zai samu dawo wa ba.</p><p> Hakan yakara dan sani na sake jikina kadan don in samu time din yin karatuna,</p><p> saidai kusan ko yaushe ina daki na kwance ko ina karatu,</p><p> A yau mun tashi da wuri saboda zamu dan yi test,</p><p> Saboda haka a tsatsaye muka shirya don saurin da mukeyi,,</p><p> Muna shirin fitane Ummi ta tsaida ni akan cewa bazan fita gida batare da na yi break fast ba,,,</p><p> Gudun kar wani abu yaje yasa may ni acan daga salim har Amal dariya suka kamayi,</p><p> Ummi ta ce ai bani kadai ba waidon ina da ciki tace, a,a duk musulumi ba,a so yabar gidan shi batare da yasamu dan wani abu yasa a baki ba koda one spoon na koko kona tea, ne</p><p> Saboda yin hakan ya a tare wa bawa, kaddara, so sai,</p><p> Tace amma ku yanzu saboda ilimin zamani duk kun can za akidar alherin da aka dora mu akai</p><p> A hankali na koma na dan hada ruwan coffee kawai batare da nazuba wani abu ba na </p><p> Nasamu guri nadan zauna nasha,</p><p> Ina tunanen irin alherin da Ummi da yaranta ke min akoda yaushe, abin baiko lissafuwa, </p><p> Muryan Salim ce ta katse, min yar tuna nen da nashiga,</p><p> Yana cemin idan nagama inyi sauri mutafi in ko zan zauna ne inkara narkewa </p><p> Shikan zai tafi ne,</p><p> Murmushi na saki gami da mikewa tsaye ina ma su Ummi sallama,</p><p> Allah sarki rayuwa haka abubuwa sukai ta dan faru acikin yan kwanakin nan ,</p><p> Wuni mukeyi yanzu zungur a makaranta saboda muna gab da fara exam </p><p> Hakalina a kwance yake don har naka dan manta da lalurar dake tare da ni,</p><p> Abinda ke a gabana kawai shine exam da nasawa rai kamar may </p><p> Burina kawai inga na gama wanan karatun,da nakeyi ko zan san ida na dosa da tushi,</p><p> </p><p> Yau ni kadai ce na na dawo, gida , saboda na rigasu fitowa </p><p> Sai kawai naji bazan iya tsayawa in jira su ba, natari taxi yakawo ni har kofar gida,,</p><p> A kusa da kofar gidan mu kadan naga wasu matasa biyu suna gyaran motar su, </p><p> Da alamar lalace masu tayi kila,</p><p> A hankali na wuce su zuwa ciji batare da na kula su ba,</p><p> Ina shiga ciki naji cikin,</p><p> Gidan namu shiru kamar ba kowa aciki, nadiba inda ummi ke yawan zama a falo, bata gurin itama,</p><p> Ina mamakin ko ina suka tafine sai na ji muryan su ta bayan gida don haka sai ban tsaya bin ta nasu ba,</p><p> Daki na nufa nasamu guri na kwanta, don indan, hutu ,Agajiye nake so sosai,,</p><p> Barci mai nauyi yai a,won gaba da ni, so sai,</p><p>A, cikin barcin nake jin kamar ina shakewa numfashina yana dan sizing a hankali,</p><p> Allah yatai makeni nadan bude idona, a hankali,</p><p> Wani dan kya mushashen bakin balarabe nagani rike da wata farar takarda a hanni shi,,,</p><p> Ganin da yaimin na farka yasa shi kokarin jada baya a hankali,</p><p> Ina son in yi ihu amma nakasa ko da dan motsawa, daga kwancen da nake,</p><p> Allah yaban iko nadan yi ihu da karfi har mama Umar dake kitchen saida tajini tare da su ummi mama umar na kawowa suna cin karo da wanan mutumin </p><p> Ya,bita tagar dake facing din baya yadira waje,,</p><p> I,hun danayi yasa kowa saurin zowa inda nake, a lokacin ne kuma idona yake rufewa a hankali,</p><p> Cikin rudani da tashin hakali kowa dake gidan yake </p><p> Shigowar Salim yasa su dan natsuwa nan maman umar tai mai bayani ihu na kawai sukaji,</p><p> Saidai lokacin da zata shigo ta hadu wani dan saurayin bakin balarabe yana kokarin fita ta window tagar dake kusa da dakina,</p><p> Salim bai jira komai ba yakira yayansu ya fada mai abinda ke faruwa a hankali, </p><p> Alokacin yana can U S A suna kokakarin kara hafbaka company nonin su ,</p><p> Asibiti aka kaini direct har lokacin ban ko da iya dan motsawa ,</p><p> Likitoci sunyi iya kokarin su don gane may ke faruwa da ni,</p><p> Tun karfe ukun rana da abin yafaru ba agane komai basai kusan shabiyu dare aka gane cewa a shaka min wani powder wanda zai gusar min da hankali har na kwana kusan uku ko biyu,</p><p> Daga U,S,A ,sheriff yataso ranan duk da uban aikin dake gaban shi,</p><p> Sai asuba ya iso garin madina, ,a masallacin dake kusa da asibiti yai sallah asuba sanan yakaraso cikin asibitin,</p><p> Kwance na ke sharkaf dani sai ta nunfashin da nakeyi ta na,urar taimakawa mutun ne za,a gane cewa ina da sauran rayuwa ajikina,</p><p> Duk wanda ke gurin a cikin tashin hankali yake, saboda irin yanayin da nake a ciki,</p><p> Sheriff kawai akayarda ma yashiga inda nake saboda tsaron guri ba,a yarda kowa ya shiga sai wanda ya ke,zama dolen ka, miji ko mata sai kuma mahifan mutun,</p><p> Yana shiga yadan ja ya tsa daga kofa yana min wani irin kallon tausayi,</p><p> A, hankali yatako jiki ba kwari har zuwa bakin gadon da nake kwance,</p><p>Durkusawa yayi gab dani yana kare min kallo, sai kace bani bace fadimar da yasa ni cikin dan lokaci guda duk na zabge</p><p><br /></p><p> Hannu na yarike a hankali ya dan duka agefen gado yana min kallo acikin tausayi,</p><p> Zuciyar shi duk ta cunkushe da bakin ciki da bacin rai ga wani radadi da zogi da yake masa yawo a zuciyar shi,</p><p> Yadan daga kai ya kalli gefen da nake kwance tausayi na yakara kamashi sosai,</p><p> Da sauri ya mike daga bakin gadon kamar wanda aka mintsira, yasoma zagayen dakin yakasa zaune ya kasa tsaye,</p><p> Duk da sanyin A, C dake dakin bai hana shi karyo da wani irin zufa ba, alokacin,</p><p> Wanene wanan mutumin da ake tunanen cewa ya shiga mai gida,</p><p> May yake bida a gurina, ko kuma waya turo shi, yazo yai min hakan</p><p> Juyawa yayi a hankali yana kallon yadda nake fitar da numfashi a hankali,</p><p> Sai kara jin tausayi na yana shigar shi,</p><p> Yadan lunshe ido yana tuna yanayin da yasan ni da shi tunfarko, ganin da yai min,</p><p> Son wasa da ruwa, murmushi dayawan yin kwazon aiki, sai yar tsiwa ,ga hangen nesa, surutu idan tasan mutum, saikuma iya yin fushi, uwa uba kykkyawan zuciyar da Allah yabata saboda bata rikon mutum duk laifin da ka iya yi mata,</p><p> Ya furta a hankali fatima ke ba kowa ce amma kuma kina da komai da kowa ke so,a tare da ke,</p><p> Halaiyarki kadai ya ishi ni abin alfahari,</p><p> Zama dake yasa ina iya zama da yan uwa na akoda yaushe,</p><p> Fatima bazan iya jure rashin mace irinki ba, aduk lokacin da na kalleki, yana wanke min duk wani damuwa da maraicin rashin saboda iyayyena da ban yi ba abaya,</p><p> Saboda ita gata mace kuma yar karama amma ta dangana ta jure da rashin ganin yan uwanta da batayi ba,,,</p><p> </p><p> Cikin ikon Allah da tai makon Likitoci suka samu da kyat Allah ya basu sa,a nadan farfado,</p><p> Daga dogon sumar dole da ,aka sani,</p><p> Sheriff ne tsaye yana fuskantar inda nake kwance sai likitocin da suka dan zagaye ni ,,,</p><p> Abuna farko da akafara yi shi ne diba, lafiyan baby da ke a jikina,</p><p> Sun tabbatar da lafiya kalau baby yake saidai weak din da abin cikin, cikin nawa yayi, kawai,</p><p> Wani irin yunwa na farfado dashi, wanda har jikina rawa yake yi,</p><p> Duk wanda ke kusa saida yai mamakin irin abincin da naci, yau,</p><p> Nida kowa yasan cewa bani cin abinci sai gashi nakusa share plate guda ina gamawa na kara kwantawa, sai barci,</p><p> Haka sheriff yakwana kusan a zaune ranan don da na motsa abinci zanci,</p><p> Sai yakasan ce duk wani motsi nawa idonunshi na akaina musanman rana yana tare da ni,,</p><p> Sai bayan kwana biyu na san cewa a,asibiti nake kwance,</p><p> Nayi mamakin hakan kware da gaske don ban san ko mai yakawo ni ba,</p><p> Sai lokacin da askarawan saudiya suka shigo gurina don suyi min dan bincike,</p><p> Abinda nasani kawai na iya fada masu,</p><p> Suka rubuta tare da shaida wa sheriff cewa an kusa cin nasarar gane ko waye wanan mutumin,</p><p> Saida jikina yai min karfi sosai aka sallamo ni daga asibiti,</p><p> Bayan sun tabatar da cewa lfy ta kalau, har baby nawa,</p><p> Saibayan kamar sati guda aka gaiyaci Sheriff a office din bincike sun gane cewa yaron da yai yunkurin shaka min wanan powder daga Yamal yake,</p><p> Kuma bincike ya nuna cewa sun dade suna bibiya na ,</p><p> Sai a wanan ranan Allah yaso basu sa,a,</p><p> Sheriff najin cewa daga Yamal suke sai, ya mike tsaye yana fadin Alin Alin </p><p> Bayan an gane cewa Ali baba ne yaturo su kuma daga shi har su , sun bar kasan tun wani dan lokaci </p><p> zuwa kasar turawa inda Alin din ke aiki yanzu,</p><p> Wanan abin yaiwa Sheriff ciwo so sai saida kuma yasan cewa komai dadin dadewa zasu kara hadewa da Alin din insha Allah,</p><p> Kowa yaji mamakin cewa wai Alin ne yaturo atafi dani a cewar shi wai dole ne sheriff yai min na aure shi,,,</p><p> </p><p> Kulawa ta musan man nake samu so saidaga sheriff tare da sauran yan uwan shi,</p><p> A haka na fara rubuta jerabawa na karatune sosai babu kama hannun yaro,babban burina shine in sama sakw na results mai kyau dan in amfana da abina nsn gaba,</p><p> Kusan ko yaushe, ina samun sakon cards da kuma gaisuwa da fatan alheri daga Sheriff,</p><p> Saida mukayi first exam din mu sheriff ya ce ma ummi yana son ya kaini kasashen waje s diba lafiyar jikina dakyau da na baby shi,</p><p> Jin haka yasa sam bakawo komai ba a,raina jin danayi cewa zamu tafi ganin likitane,</p><p> Amma sai nake cewa Salimat yanzu duk irin kokarin da likitocin saudiya sukayi akaina za,ace kuma sai ankaini wani guri,</p><p> Nace mata nidai gaskiya nafi gamsuwa da aikin su tunda su, yan uwa nane musulumai </p><p> Wa yan can ko kafirai ne wa yanda ba sa kaunar cigaban musulumai sam,</p><p> Salimat tace ai saikiyi shin dake da baby da baby duk mallakan shi ne kuma kudin shine zai kashe bana ki ba iyakar ki, zama ajirgi yar uwa,</p><p> Dole haka na Salimat ta shirya min kayana a yar karamar kit muka tashi zuwa Riyadh da marance saboda tafiyan dare zamuyi zuwa kasar paris ,,</p><p> Tun a madina da mukayi sallama da su salim da sukayo muna rakiya,</p><p> Nafara ganin canji ga sheriff,</p><p> Sai a wanan tafiyar nasan cewa ashe dama ban san kowaye sheriff Ahmad lawal ba,</p><p> Saboda ya canza min ga sheriff din da nasani ya koma ma min wani can da ban,</p><p> Wata irin mahaukaciyar soyayya yake nuna min wanda bantaba sanin cewa akwai shi ba har za,a iya yiwa mace shi ba,</p><p> Tunda muka kasance a guri guda koyaushe kusan sheriff ya man,ne a jikina</p><p> A marci kawai yake ta faman kwasa abinshi, al,amarin yaki barinsa balle, yaji na gundure shi,</p><p> Sai kuma wani sabon shagwaba yazo min wanda ni sam ban ma san cewa ina yi ba sai fama langabewa nakeyi</p><p> Wanda iyakar gaskiyana ke nan saboda ban saba irin haka tare da namiji ba,</p><p> Sheriff yakoma min kanar wani wawa saboda yawan like min dayake har takai yadan daina fita wurin harkokin sa sosai, koda yaushe yana like da ni </p><p> Saida fadima taga abin banawasa bane ya sa taimai maganar abinda yakawo ta </p><p> Murmushi ya yi yajanyo ta zuwa jikin shi yace mata haba Fatima aikwai wani likitan da yafi iya,awone a yanzu,</p><p> Kiya addu,a kawai Allah ya sauke ki lafiya ki haiho mi baby mai kama da ke ,</p><p> Kunya ta kamata, ta kwantas da kanta sosai a kirjin shi,</p><p> Cike da shagwaba tace to amma aini ce min kayi zan zo a kara diba lafiyata ne so sai,</p><p> Ya ce in bada ke Fatima kina ganin cewa akwai wanda zai auna ki da kyau bayan ni,</p><p> Ya dan kara janyo ta kadan yace kidan kara daurewa nan da wani sati zamu koma gida insha Allah,</p><p> Danbuga kafar ta takamayi alamar ita bata yarda ba wayo kawai yake mata,</p><p> Yadan lunshe ido yace fadima bakya jin dadin kasan cewa atare da ni ne koko ya, ya ne a,</p><p> Tace ni kawai dai gida nake son komawa gurin su Amal,</p><p> Yasan cewa ba laifinta bane, don bawai ta saba dashi bane irin haka yasan cewa dama sai a hankali,</p><p> Saboda duk yadda yaso ta cire kunyan shi fadimar ta kasa hakan,</p><p> Satin su biyu cif a paris suka wuce kasar italy daga italy suka wuce dubai,</p><p> A ranan fadima ta godewa Allah da yai mata wanan baiwar da daukaka a,rayuwan ta,</p><p> Ina rungumay a jikin shi ,don haka yake min duk inda zamu indan har tare zamu fita,</p><p> Ajikin shi zan man,ne har inda zamu ba zai sake ni ba,</p><p> Wasu makullaiya ya miko min yace min makullaiyan moticin kune wanan keda su,</p><p> Nafisata saboda nasan cewa saudiya basa barin mata su tuka mota yasa za a wuce maki da shi Nigeria </p><p> Idan kintafi can zaki dinga amfani da ita,</p><p> Murna zanyi ko farin ciki, sai kawai naji baki na yana zuba godiya,</p><p> Yace mu a,a ni ban son godiya kinfi kowa sani, </p><p> So nake kawai ki so fiye da komai da kike so aduniya sai kuma sai zuria masu albarka da zaki dinga bullo min,</p><p> Daga karshe in kasance namijin dayafi kowa dace da gyaran wurin gado,</p><p> Murmushi na danyi nace mai insha Allah zan kwatanta,.</p><p> Murshi yayi kawai a ran shi yace badai wayau ba Fatima,</p><p> Sosai wanan karon ya matse ya ce min Fatima banda wani guri yanzu a rayuwana da ya wuce in samu zuri,a masu albarka indan kikai min haka nagode Fatima,,,</p><p> Wanan maganar da yayi ta karshe yasa yabani tausayi sosai ban san lokacin da na shige cikin jikin shi ba sosai,</p><p> Ji nayi ya nemo bakina ya man,ne da nashi, wuri daya, can wata duniyar na tsinci kaina irin duniyar mai nuna kalar kore shar,</p><p> Wanda kesa ka manta da kowa da komai naka,</p><p> Fatima sai godiya take ga Allah ubangiji subahanahu wata,ala da wanan baiwar da yai mata lokaci guda,</p><p> Matsalarta guda yanzu shine mahaifiyar ta da yan uwanta su ne matsalar dake da mun ta,</p><p> Idan ta tuna kowani irin hali suke ciki yanzu sai hankalinta yatashi so sai,</p><p> Don haka ko yau da ta tuno da su sai ta tsinci kanta da rashin walwala.</p><p> Da jin komai na duniyar yafita mata a rai gaba daya,</p><p> Lokacin Sheriff da yafita zuwa maikatar su na Abu Abdallah ya shigo masaukin nasu,</p><p> Hannun shi rike da yar briefcase din shi dake dauke da laptop dinshi da sauran takardun su,.</p><p> Ganin da yai mata cikin irin wanan yanayin yasa ya nufe ta da sauri yana mai aje yar case din shi saman kujera,</p><p> A gabanta ya durkusa ya dan kamo hannun ta ya ce may yafaru ne fatima,</p><p> May ye matalar ki fada min pls,</p><p> Duk sai tambayar yakara ruda ta, nan da nan idon ta ya dan ciciko da hawaye,</p><p> Sai hankalin Sheriff yakara tashi,</p><p> Yace haba fatima kada kimin haka pls ki fada min damuwar har in akwai </p><p> Farin cikin ki shine nawa fatima, don ke ce kusan duk wani kwanciyar hankalina,</p><p> A hankali nadan zamay daga rikin da yai min na ce,</p><p> Ina tuna maifiyatace da yan uwa na, saboda ban san irin halin da suke ciki ba acan,</p><p> Ba karamin dukar zuciyar shi wanan zancen yayi ba saboda yasan cewa gaskiya fatima ke yi,</p><p> Shi yakamata ya fara tuna wa da hakan tun kafin ta fara magana</p><p> Amma sai abubuwa suka sha mai kai har ya shafa da zan cen,</p><p> Ki kwantar da hankalinki Fatima idan har Allah ya sauke ki lafiya dole muje su gan ki da akwai shirin da nakeyi gamay da hakan,</p><p> Hakadai yai ta mata dadin baki har ta hakkura tadan kara sake jikinta shiko yai ta kwasar garan shi,</p><p> </p><p> Ba karamin sayayya Sheriff yai min ba din kayane irin na matan manya na alfarma ya saya min</p><p> Suturu ne masu tsadan gaske ya saya min, irin kayan matan larabawa tsakiya ma su tsadan gaske,</p><p> Wasun su suna hade da alkyaba mai hade da hula,</p><p> Sai dogayen riguna different design masu kyau da daukar ido kowani da abin lailayan jikin shi,.su takalma da jakkuna kala kala,</p><p> Ita da kanta tace mai kayan sun isa haka,</p><p> Saboda cika mata ido da sukayi, ga kayan baby unicef da ya saya suma masu tsadan gaske,</p><p> Murmushi yayi da tace mai kayan sun isa hakana yace fatima shigar ki ta alfarma cikin suturu ne mutunci na banda wani buri arayuwa na banda in kyautatawa iyalina da yan uwana,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣5⃣</p><p> BY</p><p>🐎 *ZAINAB* *IDRIS* *MAKAWA* 🐎</p><p>🐎 *HUGUMA* *GROUP* 🐎</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,,</p><p><br /></p><p> Jirgin da zai sauka birnin madina, ran daren Laraba muka shigo,</p><p> Salim ne yazo taron mu shida wasu mutum biyu, cikin farin ciki da kwanciyar hankali muka sauko </p><p> Kallo guda zakaiwa sheriff kasan cewa ya samu lafiya fiya da ,da ya wani murje yadan kara kaurin jiki kadan gawa wani haske da yakara,</p><p> Muna hada ido da salim naga yai min wani kallon mamaki, yana murmushi,</p><p> Mungama clearing na komi ,muka fito cikin air port din ,motoci ukune muka jera zuwa gida,</p><p> Katuwar pickup din dake bayan mu an lodo mata kaya saida ta shake fam,</p><p> Muna tafe salim nata zolaya na yanata mamakin irin kyaun da nakara cikin dan lokaci guda,</p><p> Ina jin duk abinda yake fadin saidai ban iya ansa mai alokacin saboda duk a gajiye nake </p><p> Ga wani irin barci da nake duk ya kara saukar min da kasala ajikina,</p><p> Maimakon mu tafi gidan mu inda muke sai naga mun yi parking a wani kyakyawan gida mai kyau da kuma girma sosai,</p><p> Sai alokacin Sheriff dake gefe na zaune yadan waigo yana kallona </p><p> Ya dan duko kadan daidai saitin kunne na yace min welcome to your new house, fatima,</p><p> Da sauri na mayar da dibana akan gida cike da tunane iri,iri,</p><p> Dan kallon shi nayi da mamaki sai kawai yadan daga min kai kadan alamar eh,</p><p> Cak naji nunfashi na kamar ya tsaya min saboda mamakin, jin wai wanan gidan gidan da zan zauna ne,,</p><p> A,zuciyana nace ni fadima diyar inna yar kulu ce zata shiga cikin wanan katafaren gidan mai kyau,</p><p> Ginan gidan yakai gina a gaskiya kowa yasan yadda gidajen saudiya suke da kyau da tsari kamar ba hannu yai aikin ba,,</p><p> A hankali na fito motar sheriff yafito inda nake a ya dan rika min hannu cikin kulawa da so da kauna,</p><p> Mukashiga cikin gidan gami da sallaman mu,</p><p> Kallon mamaki kawai nake bin gidan da shi, saboda irin tsaruwar da gidan yayi,</p><p> Motsi da naji alamar akwai mutum a gidan ya sani daga kai da sauri nakai kallona ta gefen da naji motsin,</p><p> Don in ga ko waye, hakan yai dai da lokacin da mama Umar ke kokarin bude falon gidan don mu shiga,</p><p> Mukayi ido biyu da sauri na ja hannu daga jikin sheriff na nufe ta da murna na,</p><p> Muka rungumay juna cikin murna da son junan mu,</p><p> Kafin in mata wani magana saiga salimat rugumay da As,mau tana muna lalai mar ha bbin,</p><p> Bansan lokacin da na sake maman Umar ba na nufe ta, na rugumay su,</p><p> Gyaran muryan da sheriff yayi ne yasa muka dan waiga ya tsaye inda na barshi hannu shi a cikin aljihun shi </p><p> Yana muna kallon cikin nuna alamar in bi a hankali pls,</p><p> Sukuma su Salimat cak suka tsaya gaba dayan su suna min wani kallon cikin mamaki,. </p><p> Murmushi na sake masu, gami da karasa ga kujerun da ke falon nadan zauna,</p><p> Ganin kallon yai yawa yasa na dan kalli kaina ina mamakin ko may sukaga na canza ajikina suke min wanan kallon,</p><p> Cikin natsuwa na dan kalle su nace anty Salimat, wai may nayi ne kuke min wanan kallon haka,</p><p> Kafin su bani ansa Amal ta fado falin da kusan gudu,gudu,sauri,sauri,</p><p> Tana zuwa ta fada min ta rungumoni ajikin ta, muka dan kankame junan mu cikin murna da an nashuwa da jin dadi,</p><p> Sai a lokacin naga UMMI tsaye, a bayan Amal, tana muna murmushi,</p><p> Tana fadin, a a tafiyan cikin, dare haka, aiko saidai jirgi kam,</p><p> Tsam,tsam na isa gareta saboda kunyar ta da nake ji na dan rugumay ta, </p><p> Haka aka hau murna da farin cikin dawo war mu lafiya,</p><p> Ganin da Ummi tai min na a gajiye nake yasa ta cewa ya kamata mudan huta kafin a kira sallah,</p><p> Kowa yace gaskiya kam,</p><p> Wata sabuwa wani kato bedroom mai dauke kayan alatu iri, iri Amal ta kai ni,</p><p> Mamaki duk ya cika ni jin cewa wai shine daki na,</p><p> Cikin mamaki da kuma nuna hankali nake karewa dakin kallo,</p><p> Fitar Amal ya bani damar cire kayan da ke a jikina a, hankali don duk a gajiye nake a lokacin,</p><p> Sheriff ya shigo dakin a lokacin shima a gajiyen yake saboda dan bata lokacin da jirgin mu yayi a Dubai kafin ya taso,</p><p> Ta bayana yadan zo yana kokarin tayani cire rigar,</p><p> Saida yaga ya cire saura yar breezeir kawai da dan bujen ciki yasa ya dan kyale ni, rigar barcin da nagani a saman gado nadauka, na sa ajikina,</p><p> Sai a lokacin na fahinci cewa ashe wai daki guda zamu zauna da ni da sheriff ,</p><p> Tirka shi, ga ummi ga su salim da Amal zan zauna da shi daki guda </p><p> Gaskiya da sake bazan iya ba sam </p><p> Yagane mai nake nufi sarai, saidai bai nuna min yagane ba, wanka yaje yayi yana fitowa ina zaune bakin gado har yanzu sai ce mun yayi bangaji ba ke nan tun da ban kwanta ba ko,</p><p> Nadai san cewa bazan yi wanka ba a cikin daren nan ba, ko,</p><p> Saida na dan bata rai nace, ni gaskiya dakin Amal zan koma,</p><p> Kafin in wani maga sai kawai naji ya kwantar dani ta baya a hankali,</p><p> Bada son raina ba dole na hakkura hakana na kwanta tare da shi daki daya,</p><p> Duk da gajiyan da muka kwaso hakan bai hana mu farkawa da wiri ba don yin sallah a suba ,</p><p> Sai dai ina idar,wa na kara kwantawa kuma ,sai wani barci mai nauyi yakara daukana,</p><p> Yuwa kawai ya sani farkawa, da ga barcin,</p><p> Wanka nayi nafito cikin shigar wata doguwar riga irin ta matan Brazil,</p><p> Rigar light blue ne, har kasa take saidai hannuwan ta shara shara ne haka bubude, cotton ne sosai sai wani sulbi da yauki takeyi, nasa yar gyalenta na daure kaina,</p><p> Saida naci abinci so sai na koshi a lokacin ne, nake tambayar anty falmata,,</p><p> Amal ke sheda min cewa ta koma gida tun bayan wucewar mu da kwana uku,</p><p> Gaskiya banji dadi da ta wuce bani a gari ba don, </p><p> Salimat da ke gefe take ce min fadima waiko kinga yadda kikawani kara girma ga fari dakikayi,</p><p> Kinyi wani kyau sai kace irin matan nan da muke gani a TV ko muji rabarin su,</p><p> Murshi kawai nai mata nace aike dama kullun haka kike cewa idan kin kwana biyu baki gan ni ba,</p><p> Tace gaskiya wanan daban yake, ba kamar na kullunba Allah sai kace an maki wani famfon girma,</p><p> Duk muka dara gaba dayan mu dake a cikin falon </p><p><br /></p><p> Mun dawo bamu wani dade ba sheriff yakoma harko kin sa,</p><p> Sosai yanzu arzikin sa ke ta bunkasa kamar daga sama,</p><p> Ikon Allah ke nan, don har yan uwan haihuwan shi su suraj yana kokarin taimaka masu </p><p> Duk da hassada da bakin cikin da hjy mama ke nuna mai hakan bai hana shi sasu cikin harko kin shi ba,</p><p> Don suma din sungane gaskiya tunda wayayyu ne ba su bari hjy mama ta ruda su ba,,</p><p> Mahaifin su yaji dadin wanan abin da Ahmad yayi wa yan uwan shi ya sha albarka so sai da fatan alheri ga tsohon,</p><p> Hankali na a kwace na ci gaba da harkokina sosai saura yan kwanaki mu gama karatun mu,</p><p> Gashi da mun gama zasu tafi Nigeria don daurin auren Amal da Almustapha da za,ayi a can mahaifar su, Amal din,</p><p> Ranan da na samu wanan labarin gaskiya nayi farin ciki sosai saboda nasan cewa Almustapha mutumin kirki ne ,</p><p> Kuma gaskiya sheriff yayi dibaiya so sai wuri bashi yar uwan haihuwar da ya aura,</p><p> Almustapha mutumin kasar Sudan ce , gurin aikin su guda da sheriff yana zama a matsayin yaron sheriff ne,</p><p> Hakan sai wani shakuwa da yarda yashiga a tsakanin su, </p><p> Har abin yazama masu kamar zumunta,, mai karfi a tsakanin su,,,</p><p> She nice ban sani Amal sun dade suna soyayya da almustapha ,</p><p> Wani irin rana ake fatsamawa agarin kowa kagani yadan samu wuri yadan boye ma wanan zafin ranan,</p><p> Don haka nima ina fitowa daga exam nakira driver mu na ce yazo yakai ni gida,</p><p> Don haka, a cikin wanan ranan nadawo daga makaranta a gajiye nake saboda nauyin da cikina yafara yi min ga kuma zafin ranan da akeyi, yau din</p><p> Ina shiga gida dakina na fada da niyar in tube kayanan jikina inda watsa ruwa ,</p><p> Aziza ce kwance a she me,me tayi da daya a saman gadona tana waya abinta hankalin ta kwan ce</p><p> Da yar mamaki makale a fuskana, na tsaya sororo tsaye ina kallon ta,</p><p> Allah yabani ikon karanto mata addu,oin kariya daga duk wani sherin dake tare da ita,</p><p> Cikin daurewa nai mata sannu da zuwa </p><p> Hannu kawai ta daga min batare da ta ansa min ba,,</p><p> Ganin danayi wulakanci take son tai min kawai yasana juya daniyar in fita waje, sai ce min tayi daga yau kada inyi gigin cewa zan tako mata daki,</p><p> Da kyar na iya lalubo na tsuwata wuri guda nace mata dan Allah tayi hakkuri bansan cewa tana ciki ba,</p><p> A hankali nadawo baya ina mai rufo mata kofar dakin,</p><p> Duk gajiyar da na debo da zafin da nake ji sai na bide su na rasa, alokaci guda,</p><p> Wani irin duhu da na tashin hankali nake gani don gani aziza ba alheri bane gareni,</p><p> A hankali nake tafiya cikin yar doguwar corridor da ke sada mutun da daku nonin gidan</p><p> Zuciya tab da tausayin kaina saboda dama nasan ko mijin suwa na aura,</p><p> Daga Aziza har nafisat na san su nasan halin su, </p><p> Jikina gabada daya yayi san yi na rasa ma wani guri zan dosa a lokacin,</p><p> Maman Umar ce ta fado min a rai gurinta na nufa kitchen,</p><p> Itama din tana gani na ta taso cikin sauri ta tare ni, tace min cikin larabci kada in nuna ma Aziza nadamu da zaman ta a dakina ko kadan tace min ta gyara min daki guda dake gudan bangaren mu,</p><p> Murmshin karfin hali nayi mata nace mata aiba komai rayuwace duk hakan,</p><p> Maman umar ce ta jagorance ni zuwa dayan dakin kusan komai na dakin iri dayane da wanda nake a ciki,</p><p> Saidai dan banbanci kadan dakuma irin kayan bukatu da yasa min ciki,</p><p> Ko wanka da nake ma sauri banyi ba na fada saman gado na kwanta a hankali,</p><p> Ashe tun fita har dawowan mu da maman Umar Aziza ta labe tana kallon mu,</p><p> Tai wani dariyar mugunta ta koma cikin dakin tana karewa dakin kallo saboda irin tsaruwan da dakin yayi,</p><p> Tai mamakin yadda sheriff ya haukace akan yar karamar yarinya alokaci guda,</p><p> Mai wanan yar kwailar yarinyar keda shi wanda ita bata dashi har yake rawan kai akanta,</p><p> Zanyi maganin ta in har don wanan cikin yake wanan rawan kai haka zata barar da cikkn kowa ya huta,</p><p> Don ta riga tasha alwashin cewa bata barin garin nan sai taga cewa ta halaka cikin dake jikin na ni, fadima,</p><p> Idan yaso tasan kuma yadda zata raba wanan aure da yake ikirarin cewa ya dade da,aure bada sanin ta ba,</p><p> </p><p> Niko tunda naga aziza tazo sai nake tsoron cin komai na gidan duk da maman Umar na iya kokarinta wurin ganin cewa</p><p> Tana kula da duk wani tako da kuma kulli da Aziza keyi, akaina,</p><p> </p><p> Gurin Salimat nake yawan zuwa inci abinci kafin in dawo gida, ko kuma kafin in tafi school sai in biya incika cikina fam, in wuce,</p><p> Sannu a hankali maman Umar ta san kwaso min wasu kayan bukata na tadawo min da su cikin dakin da nake zaune, a yanzu,</p><p> Ganinda Aziza tayi cewa duk wani kullin da takeyi bai ci yasa ta sake min fuska faran faran,</p><p> Duk da yarinya nake hakan baisa na yarda da shimfidar fuskan sherin da take, kulla min ba,</p><p> Satin Aziza guda a gidan ,duk su Ummi har Amal ba su san cewa ba,a dakina nake zama ba,</p><p> Kuma gashi kusan ko,yaushe muna tare da Amal amma ban taba fada masu cewa ai Aziza adakina take ba,</p><p> Sai a yau da Amal tazo gurina ansan hand dryer dina saboda nata yadan samu matsala,</p><p> Da yar sallamata tafada dakin kamar yadda mukeyi a kullun,</p><p> Ganin mutum tayi saman kadon tim kamar antara kayan wanki, wuri guda,</p><p> Duk da tasan cewa ciki ke gareni amma dai ban kai ko kwatan haka tari ba,</p><p> Da mamaki ta isa har bakin gadon tana kare ma aziza kallo cikin tsana da kiyayya, take mata kallon raini,</p><p> Takara juyawa takalli dakin tsab taga cewa ba wani alamar da ya nuna cewa na kwana acikin dakin,</p><p> Cikin sauri tafito waje zuwa wurin Ummi don ta fada mata cewa bata ganni ba a daki na sai dai aziza dake kwance,</p><p> Maman Umar da ta dauko min abin breakfast wanda ta kasa ta tsare a kitchen din ko gusawa bata yarda tayi ba saida ta gama min komai tadauko zuwa dakin da nake ciki,</p><p> Ina zaune dagani sai yar doguwar rigar barci har kasa mai yar kuntun hannan shimi,gefen rigar ta kasa andan tsa, tsaga ta, kaina babu dan kwali,</p><p> Kusan atare suka shigo dakin ina zaune a gaban mirrow da waya a hannu na,</p><p> Cikin mamaki da masifa Amal take min wani irin kallo ,</p><p> A hankali maman umar ta aje min abincin a saman wani dan stol ta na kokarin gyara dakin ,</p><p> Amal tace min cikin fada fadima ban gane ba shin da yardan ki Aziza ta zauna maki a daki ko kuwa ,</p><p> Saboda may zaki dawo wanan dakin ki zauna kibar mata dakin ki, </p><p> Murmushi nai mata na jawo dan teburin abincin a gabana wanda, nadade banci abincin gidan ba,,</p><p> Kafin in bata ansa maman Umar ta kwashe yadda akayi tun ranan da Aziza ta iso muna school ummi tace a kaita dakin da sheriff yace a dinga aje baki nagida,</p><p> Amma sai tace ita ina ne dakin Sheriff maman umar tace mata ai daki guda muke </p><p> Sai tace to ita a nan zata sauka,inda sheriff yake, da tace mata to ni fa sai cewa tayi wai in koma dakin baki</p><p> Dakin sheriff nata ne ita dashi fadima bata kai matsayin da zata zauna inda taje zama ba,</p><p> </p><p> Da sauri Amal ta juya cikin fushi tabar dakin nawa, A dakin Ummi ta samay ta rai a bace take mayar ma ummi da komai dake faruwa agidan </p><p> Hakalin UMMI yatashi matuka don sam bata zaci hakan ba daga Azizan,</p><p> Ina kwance a daki kasan cewa yau ban shiga school, yasa da nagama abin da nakeyi sai na koma na kwanta , saboda in samu indan huta,</p><p> Jin sallaman Ummi na daga sama a cikin dakina nayi mamaki kware har na nuna mata hakan a fuskana,</p><p> Mikewa nayi zaune daga kwanciyar da nayi, ina mai gaida Ummi, dake kokarin zama saman yar kujerar da aka a je a cikin dakin</p><p> Shiru yadan biyo bayan zaman nata,</p><p> Can takira sunana a hankali tace may yasa kibar ma Aziza dakin ki </p><p> Alhalin kisan cewa wana dakin shine dakin ki na halal malal,</p><p> Saboda ko wanan gidan saboda ke ce yasa aka gyara shi,</p><p> Idan har ba zata zauna inda yace na baki ba da ai sai ta koma inda tafito </p><p> Don ni ba ga abinda yakawo ta wanan garin ba tun da Alhajin karami baya kasar, ban san zaman may take anan ba,</p><p> Saida na barin ummi ta kare zancen ta duk kai na yana a kasa,</p><p> Can nadago kaina ido na sunyi raw ,raw alamar kuka ,</p><p> Nace , La, ummi ai ba komai anan din ma inda nake babu wani matsala gaskiya,</p><p> Ummi kinsan cewa ita ce, matar sheriff, itace ta can can ci zama a wanan dakin bani ba,</p><p> Ummi kinsan cewa aurena da Sheriff kawai nufi na ubangiji amma ai ni ban kai matsayin auren shi ba,</p><p> Ummi tace min assha, fadima aure ai baida wani can,can ta ko sa,ayi,</p><p> Abune mukaddari daga Allah, </p><p> Idan har kikace haka to gaskiya baki godewa Allah da ni,imomin da yai maki ba,</p><p> Nace a hankali na gode mana Ummi, baga shi ko ina godiya akai ba,</p><p> Dan murmushi na manya mai nuna cewa yaro dai yaro ne tai min,</p><p> Tace fadima wa,yan nan kishi yoyin naki da kike gani basu san Allah, don basa aiki da maganar Allah,</p><p> In bashi ba gaskiya da batayi wanan abin kunyar da tayi ba </p><p> Donko kowa yasan cewa ai ba dakinta bane dakin ko,</p><p> Son zuciyane kawai irin na marasa tsoron Allah, wa yanda basa tsoron gamuwar su da Allah</p><p> Aida tana da imani da ta tausaya maki acikin wanan halin da ki ke ciki haka,</p><p> Amal ko tana waje sai faman kiran layin dan uwan su takeyi bata samu ba,</p><p> Sai a na karshe ne tasamu layin nashi ya shiga,</p><p> Bayan sun gaisa ne take tambayar shi ko yasan cewa aziza tana saudiya kusan sati guda,</p><p> Yadda yai ihu mamaki saida Amal taji shi,</p><p> Yace nafada mata cewa ina na turkey muna kokarin muga cewa duk kayan mu ansa a conterner neno anturo muna dasu gaba daya,</p><p> Maimakon Amal taji yai magana sai taji kawai ya ma kashe layin nashi gabadaya,</p><p> Dif kake ji,</p><p> Wani haushe yakamata tadan kali wayar tai tsaki, </p><p> Tace in fa yayan mu yasan cewa bazai iya daukar wanan amanar ba gwara kawai saki diyar mutane </p><p> Don kada su taru shida matan shi su cuta min, tunda duk sun fini wayo da sani ta duniya,</p><p> Azizs na daki abinta hankali ta akwance sai waya takeyi ta yarda zata samu ta samu, sa,ata taci </p><p> Nasarar lalata min cikina ko ta halin kaka, sai taga bayan cikin nan,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣7⃣</p><p> B Y </p><p>🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,</p><p><br /></p><p> Assalamu Alaikum yan uwa musulumai,</p><p> Dan Allah a tsakanin marubuta da makaranta yakamata asamu kyakyawan facin ta,</p><p> Bawai challenge's ya shigo ciki ba, idan har marubuci tayi wani abin da yadan kauce wa addini ko tarbiyan mu yakamata akirata in prevent aimata gyara ,</p><p> Babu wanda yawuce gyara aduniya, tundai na fannin addin mu,</p><p> Yima marubuci cin fuska a bainin jama,a baida amfani wlh,</p><p> Wanan rubutun da kuja ga munayi abune mukaddari daga Allah, akwai masu so soyi amma Allah bai basu ikon yi ba,</p><p> Bakaramin wahala ke cikin rubutun novel ba yan uwa,</p><p> Yakamata duk yadda marubuciya tai novel din ta a gode mata, indan har da gyara akira mutun a gefe not in public aimai gyara,</p><p> Pls mukuma marubutan Allah yakara bamu hakkuri a tsakanin mu mukara daurewa da makarantar , duk abinda kayi ba aima korafi akai ba, wanan abin baida ma,ana ne ,,,,,</p><p> Idan nafadi ba daidai ba ina mai rokon gafaran ku yan uwana,👏👏👏👏</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> Kitchen din shiru yake babu kowa acikin shi sakamakon kashe na,urar da zata sada ma kitchen din da ruwa,</p><p> Hakan yasa ma,aikatan fita waje don ganin ko may ye matsallar ,</p><p> Maman Umar abin ya bata mamaki kasancewa ko a daren jiya itace tayi aikin karshe a kitchen din kuma ruwan yana zuwa normal,</p><p> A hankali ta fito daga dakinta tana tafiya cikin sanda har ta shiga kitchen din,</p><p> Saida ta leka ta tabbatar da ba kowa a waje lokacin ta ciro wani dan koya daga cikin gefen breast din ta ta jefa a cikin flower sinasir da maman Umar ta kwaba ,</p><p> Tafito da sauri tana dan waige waige, bayanta,</p><p> Tana shiga dakin ta tashige bayi ta wanke hannuwan ta tsab, takoma saman godon ta kamar wacce bata tashi daga barci ba,</p><p> Bayan angyara matsalar ruwan maman Umar ta dawo taci gaba da aikin ta,</p><p> Tanagamawa ta jera komai a carpet saura kuma masu ci a table aka kai masu nasu, saman tebur,,</p><p> Saida kowa kusan ya hallara a falon wurin karin kumallon safe,</p><p> Kusan nice ta karshen zama a falon saidai ba a saman kujera na nufa ba,</p><p> Wurin Ummi na nufa don a saman carpet, take zama ,</p><p> A hankali na dan durkusa gami da kara gaida Ummi karo na biyu,</p><p> Saida na sawa plate dina komai da nake sha,awa, nadan tsiyaya ruwan sha, a cup na aje a gefe na,</p><p> Nai bissimillah nadauka zankai wa bakina,</p><p> Aziza dake zaune daga gefen mu ta kura min ido, Allah Allah take yi in kai a bakina,</p><p> Daidai lokacin da zan kai a bakina sai wayana dake gefe yadauki ruri </p><p> Mayar da sanasir din nayi cikin plate na, nai saurin daukar wayan , diba massage din,</p><p> Ganin nobar Amal, da nayi yasa ni saurin ta shi kusa da Ummi , </p><p> Kada kici abincin nan fadima ,</p><p> Kuma in kin karanta kada ki dago kai ki debe ni pls,</p><p> Gashi dai nagama karantawa amma sai na kasa daga kaina sama, </p><p> Wani irin mugun tsoro ne yakamani saboda nasan cewa Amal bata maganan banza </p><p> Maimaikon in juya sai na mike kawai daga, gurin da niyar tashi ,</p><p> Muryan Ummi ce na ji tace min fadima da wo mana kici abincin cikin sanyin murya nake ce mata,</p><p> Ummi zan dauko ma salimat takarda ne a daki, yanzu zan dawo, sai kuma wani dabara yafado min nace ma ummi bari ma dai intafi da abincin daki na kawai sai inci a can,</p><p> Wani wawan ajiyar zuciya Aziza tayi,jinda tayi cewa zantafi dakina in ci,</p><p> Mutun biyu ne Allah yanufa suci sanasir din, dayake suna da rabon wahala,,</p><p> Da Salim sai Ummi duk yadda Amal taso ta hana Ummu ci acikin hikima hakan baiyi, ba,</p><p> Ciwon ciki ne mai karfi ya turnike su sai ,</p><p> Tun ana abu wasa wasa har takai ga anyi rushing din su asibiti,</p><p> Nan likita yai masu dan bayani akan cewa akwai abinda sukaci Allah nai yatai make su sun kawo su asibiti da wuri,</p><p> Yace amma inda mace mai cikine taci gaskiya da abin yafi nan worse,</p><p> Jin hakan yasa hankali kowa tashi kowa da abinda yake tunane acikin zuciyar shi gamay da abinda likita yace,</p><p> Kwanan su biyu , a asibitin aka sallamo su zuwa gida,</p><p> Har a lokacin Amal batace min komai gamay da text din da tayo min ba,</p><p> Hakan dai danaga irin wahalar da su ummi suka sha yasani shan jinin jiki na sosai,</p><p> Sai yakasan ce duk gidan hankali na a tashe yake so sai,</p><p> Gurin Salimat na tafi da kukana nafada mata duk yadda mu kayi da Amal,</p><p> Itama dai shawara tabani sosai akan yadda zan zauna da kowa agidan </p><p> Tace min akwai abinda Amal take zargi a gamay da ni,</p><p> Hakan yasa tunda ga wanan ranan Salimat ce ke kawo min abinci a boye ko kuma intafi gidan ta ince a can,</p><p> Yau bazan tafi school ba don haka na koma nadan kwanta don in huta,</p><p> A can cikin barci na rika jin kamar ana tabani sama sama,</p><p> Sai kuma na dinga jin kamar ana kiran suna na a hankali,</p><p> Cikin karfin hali na bude idanu na a hankali, tayadda ba kowa zai iya gane cewa na bude ido na ba,</p><p> Aziza ce tsaye da wani abu kamar jan kyale a hannun ta,</p><p> Can kasan gadona naga ta duka ta aje kyalen a hankali kuma ta taso ,</p><p> Ta kama hanyar kofar dakin fita zuwa waje,</p><p> Ido kawai nabita dashi a hankali har ta kure min </p><p> Bakina duk adduan da na sani na tsari saida nayi shi a lokacin wani ba ni ko karasa shi nake daukar wani,</p><p> Sai da na tabatar ta wuce tundazu sai na sauko da bissimillah tare da naiman tsari ga Allah ,</p><p> Ta gefe gudan nabi ban yarda na bi ta inda nagantaba tsaye,</p><p> Bayi na fada da wayana nakira Salimat na sheda mata abinda nagani,</p><p> Ba,adauki wani lokaci ba ta shigo gidan da shirinta,</p><p> Ita da Amal ne suka dauke wanan jan kyalen suka samo wani jan kyale na rigar Amal irinshi suka aje mata agurin,</p><p> Mamaki duk ya kashe mu, Salimat ce tafara magana daga cikin mu,</p><p> Tace wai may yasa wanan matar batada imanine haka,</p><p> Mundade muna shawara a tsakanin mu so sai,</p><p>A ranan ga dare ya raba amma sam babu alamar barci a ido na,</p><p> Duk da nasan cewa sun fitar da mugun abin a dakina </p><p> Tunane nayi ko may yasa sheriff yin tafiya tun ranan da yadawo batare da yadauki ma aziza wani mataki ba ,</p><p> Ajiyar zuciya na saukar cikin tausayawa kaina ina tuna nen wanan sabon rayuwa da na tsinci kaina a cikin sa,</p><p> Gaba sai bugawa yakeyi saboda alamar gitawa da naga anayi ta dan hasken da ke hasko min ta jikin window daki na,</p><p> Na rintse idona ina ci gaba da addua acikin raina,</p><p> Saboda na sadakar da raina cewa nawaya kare kawai a wanan ranan,</p><p> Can kuma sai naji shiru nadaina jin motsin komai kuma naga a daina wanan gittawan da ake ta min,</p><p> Duk da nasan cewa na rufe dakina yau da makulli, amma hakan bai hanani jin tsoro ba,</p><p> A haka barci barawo yazo yadan yi awon gaba dani,</p><p> Sai da asuba nafarka cikin dan firgita don ji nayi kamar za a shigo min ,</p><p> Saida na kwanatar da hankalina sannan na gane cewa ai ba komai har yanzu,</p><p> Saida na tabbatar da cewa gari ya waye kuma tabbasa kowa yadan fara fitowa waje </p><p> Natashi naje nai wanka nafito kenan ina shiri naji alamar ana buga min kofan daki da karfi kamar za,a tsaga shi biyu,</p><p> Na nufi kofan pa gigice nabude a hankali, hannu na guda yana rike da dan towel din da nake tsane jiki na da shi,,</p><p> Ga mamakina Aziza ce tsaye tana ganin na bude daki naga tai wani irin shock na nuna alamar mamaki,</p><p> Kallonta nakeyi sosai babu kaukautawa,na zuba mata ido, nima,</p><p> Ganin da nayi cewa , kallon nata bana girma da arziki bane,</p><p> Kallon tababiya naimata na kallo ta wani irin shekeke, </p><p> Na juyawa nayi da zumar in koma cikin dakina,</p><p> Sai naji ta turo kofar ita ma da karfi kamar zata bangaje ni,</p><p> Turus na tsaya gami da rasa na yi hannuna, yana rawa, ina kallon ta don inga abida zatayi,</p><p> Cikin tsayin wani lokaci shiru ya biyo baya sai dai na kula da ita kamar tana kokarin kallona tana na,zarin wani abu,</p><p> Nadai daure da nagaji da kallon kallon da mukeyi na ce mata lafiya dai ko hjy,</p><p> Cikin dakewa ta ce min da akayi may fa,</p><p> Cikin rawar murya nace mata, naga kamar kina bukatar wani abune a nan,</p><p> Ta buga min wata uwar harara ta kuta saida gabana yai mugun faduwa da ga ni irin yadda tai min,,</p><p> Tawani irin juya da karfi kamar mai fada da iska tawuce, </p><p> Nanta bar ni tsaye da mamakinta,</p><p> Gakuma wani irin tsoro da firgicinta da ya kamani </p><p> Don nasan cewa a yadda taimin yanzunan zata iya aiwatar da komai akaina,</p><p> Inda tawuce tabarni nan nake tsugune amma tsabar fargaba abinda take shirin yi min yasa ni zarya a corridor</p><p> Ina ta tunanen mai yasa Aziza take farautana haka saboda kawai na auri mijin ta ne ko ko may,</p><p> Da sauri namike na isa inda wayana yake jone a caji na ciro cikin sauri na kira layin ,</p><p> Sheriff tsayin wani lokaci naji shiru, sai can daga bisani naji computer tana gaya min wayar a kashe take,,</p><p> A rude na nemi layin Amal, itama hakan ne ta kashe wayar ta,</p><p> Sai dabaran kiran Salimat yazo min,</p><p> Ina samun ta ta dauka,nan na shiga, fada ma Salimat cewa tazo ba lafiya,</p><p> Hankalina a tashe nake maganar , hakan yasa tace min gata tafe,</p><p> Kafintazo saita bugowa maman Umar waya tasheda mata cewa tazo dakina da sauri ta diba mata halin da nake ciki,</p><p> Maman Umar tasamay ni na dan rakube a bakin gado ina kuka,</p><p> Ban boyewa maman Umar komai ba tun abinda Aziza tai min safiyan jiya,</p><p> Har zuwa cikin dare dakuma yadda mukayi yanzu da ita,</p><p> Salimat tafado dakin a rude nafada mata duk yadda na kwana a dakin da kuma abinda mukayi da ita yanzu</p><p> Saida ta nisa sosai can tace min shawar guda zan baki fadima,</p><p> Tace min ina passport dina nafada mata cewa yana nan,</p><p> Ita ta shirya min duk yadda komai zai kasance gare ni,</p><p> Tasa maman Umar ta kwaso min duk wani abin bukatana adakin dakuma wasu kudi masu yawa da naita boyon su da dadewa,</p><p> Salimat ta kwashe kayan zuwa gidan ta batare da sanin kowa ba,</p><p> Ta yadda ko CCTV ba za a gane cewa kaya ta dauka ba,</p><p> Duk wani motsin da za a yi a wanan yini a tsorace muke nida su salimat da maman umar don ko ruwan gidan nadaina sha yanzu,</p><p> Azizako sai fita takeyi tana dawo tare da wata yar doguwar takari fara wace tayi bleaching duk ta kode,</p><p> Ranan dole tare muka kwana da maman Umar adaki daya,</p><p> Washegari tun da safe nai shirin zuwa makaranta, saboda kasancewar itace ranan da zan rubuta jerabawar karshe,</p><p> Ina kallon Ummi cikin tausayawa saboda har yanzu jikinta baida wani karfi sosai,</p><p> Amal tana ta jana da hira saidai sama sama naje dan ansa mata,</p><p> Can dai tace min wai may yasamay ni ne yau taga duk bani cikin hayacina sosai,</p><p> Nadan kakaro murmushin dole nace haba Amal yaune fa zan gama exam dina aiko kinga dole in dan damu,</p><p> Dazamu tafi naba maman umar takarda nace taba sheriff idan yadawo kasan ,</p><p> Ina gama exam ko min ti biyu bamu karaba muka dauki shatan taxi nida salimat sai jedda,</p><p> Ina rugumay da Aisha wace mamata ta ce min in wuce da ita duk inda zani tabar min ita,</p><p> Batare da bata lokaci ba akai muna screening duk na ka gu inga mun shiga jirgi </p><p> Ina jin anfara kiran yan jirgin mu sai kuma kuma al,amarin ya juye min duk naji ba dadi, a raina, </p><p> Saboda nasan cewa Ummi bazata ji dadin abinda nayi ba, </p><p> To amma yaya zanyi dole ne in tserar da rayuwana ,</p><p> Karfe tara na dare jirgin mu yatashi daga jidda zuwa Nigeria,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎[11/5, 5:57 PM] +234 816 741 8349: ✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣6⃣</p><p> BY</p><p>🐎 *ZAINAB*IDRIS *MAKAWA*</p><p>🐎 *HUGUMA* *GROUP*🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Jirgi dare ya biyo zuwa saudiya, A, Riyadh ya sauka ,</p><p> Daga Riyadh, shiga mota sai madina,</p><p> A madina safiya tai ma shi,,a cikin gidan mu,,</p><p> Mudai mun tashi munga bako don mun san cewa saura kusan sati guda ko kwana goma yadawo,</p><p> Tsaye nake bakin dressing mirrow dina ina dan gyaran jikina saboda ina son inyi samako zuwa wurin salimat inci abinci,. Don yau natashi ina jin yunwa sosai,</p><p> A, hankali yaturo kofar dakin cort din shi na sagale a kafadan shi, hanaye shi zube a cikin aljihuwaye shi,. </p><p> Waigowa nayi don inga kowaye yashigo min daki a lokacin,</p><p> Kafin ma in karasa juyawa hanncina ya isar min da sakon sheriff ne,</p><p>Mamakin gani shi na yi a wanan lokacin da safe haka, </p><p> Don nasan cewa badai ta madina yai landing ba don da Salim ya tafi dauko shi,komai dare</p><p> A hankali yatako har inda nake tsaye yazo ya rugumay ni ta baya, </p><p> Yana kokarin juyo dani don in yi facing din shi da kyau,</p><p> Cikin yar siririyar murya nace mai sannu da zuwa ya hanya a lokaci guda,</p><p> Dan murshi yayi dai, dai lokacin da ya man na bakin shi cikin nawa yana fadi a hankali wani zan ansa maki cikin gaisuwar,</p><p> ,Alokacin kuma maman Umar ta turo dakin don ta kawo min abin breat fast,</p><p> Takoma da baya cikin sauri tana fadin muyi hakkuri batasan cewa yana a ciki ba, </p><p> Asalima dai batasan yadawo ba, daga tafiyan , ganin ta baisa ya sake ni ba niko duk nauyi da kunya ya rufe ni,</p><p> Ta koma da baya baya, tana mai bada hakkuri tajawo kofar dakin,</p><p> A lokacin yakara dan matse ni cikin jikin shi sosai, ya dan sun sunan kamshina yana wani lunshe ido,</p><p> Amma sai na dan jaye jikina dagana nashi a hannkali, cikin hikima</p><p> Sai yadan tsaya tsaye sororo yana kallo na,</p><p> Najuya da niyar indan gusa daga gare shi kadan,</p><p> Sainaji ya riko min hannu na ta yadda bazan iya juya wa ba da kyau,</p><p> Kokari yayi mu hada ido amma sai na kasa saboda gaskiya bazan iya ba don har yanzu mugun nauyi da kun yar sheriff nake ji,</p><p> Murmushi yayi yadan kalleni cikin tausayi yace min,</p><p> Fatima bakiyi murnan dawo wana bane,</p><p> Nadan dago da sauri na kalle shi nace saboda may,</p><p> Sai yaji kawai na bashi tausayi, don ko ba komai yasan cewa ina bukatar kulawa so sai a yanzu, da cikina yafara girma sosai</p><p> Kuma gashi wana yar ballija,un ta zo ta takuramin,</p><p> Sai a lokacin yakare wa dakin da nake ciki kallon a hankali,</p><p> Sai yaji wani mugun tausayina yakara shigarshi,</p><p> A lokaci guda yaji sam bai kyauta min ba ,</p><p> Saiya dan tsaya jin yana dan tunane da nazari,</p><p> Yarasa abinda zaice min sai ya sakar min hannu, a hankali,</p><p> Wanan lokacin ne rana na farko da yaji yaji kunya na da nauyi na sosai, aran shi</p><p> Ada kam baidauki wai don ya aureni zai sa yaji wani abuba akaina, ba</p><p> Sai gashi yar karamar yarinyar da yake ji yake kuma gani kamar bata da wayyo , tana batun wuce wa da lissafin shi,</p><p> Yau yana jin kunyarta da nauyin ta, sosai </p><p> Don yasan cewa an raina mata hankali da yawa kuma baisa tace zata dauki mataki ba, akai,</p><p> Ko ta kirashi ta fada mai abinda ke faruwa, ko da a waya ne,</p><p> Kenan ta bar mai hukunci a hannun shi, sai yaji wani iri a ranshi yace kada Allah ya kamani da laifin hakkin wanan yariyar fa,,</p><p> Bakin mirrow yasa mu yadan zauna kadan, yana facing di na,</p><p> Cikin son mu hada ido yake har yanzu , duk na gane nufin shi sai naki daga kaina</p><p> Niko sai kokarin gyara Nafal dina kawai, nakeyi batare da na kalle shi ba,</p><p> Sai lokacin Yace min fatima lafiya kika dawo wanan dakin da zama,</p><p> Cikin mamaki na dago kaina a hannkali na dan kalle shi don tambayar ta zama ta rainin wayo ko hankali,, nake gani,</p><p> Yakara nanata tambayar sai na dan dago kadan cikin sanyin murya nace mai ba komai,</p><p> Yanayin muryan danayi dole taba mutum tausayi so sai ,,,</p><p> Sai yace to may yasa ki ka dawo nan din kuma,</p><p> Can fa yafi maki nan, don kinga nan ba wani abin da akasa sosai don jin dadin ki,</p><p> Shiru nayi, saikuma na ga kamar ai baisan cewa Aziza tana gidan ba shiyasa,</p><p> Yake min mugun tambayar nan, da nake jinta har cikin raina,,, </p><p> Ji nayi ya kara riko min hannu karo na biyu,</p><p> Yace min ko dakin bai maki bane,,,</p><p> Sai nai rau,rau da ido na kamar mai shirin kuka nace </p><p> Matar ka fa ke ciki wancan dakin , tayaya zan zauna a ciki tare da ita bayan tace wanan dakin baidace dani ba </p><p> Saboda dakin kune kaida ita, </p><p> Asalima ita sam bata yarda da cewa ka aure ni ba don bata da wanan tabbacin,</p><p> Cikin hasala gami da mikewa ya ce may yasa baki kirani kin fada min cewa Aziza tana gari ba don in dawo ,, cikin lokaci,</p><p> Kinsan fa cewa Aziza zata iya maki komai don ba tausayi ke gare ta ba,</p><p> Nace banyi zaton cewa zata iya kai har war haka agarin nan ba don baka nan,</p><p> Shiyasa ban kiraka ba saboda nadauka cewa zata tafine bayan kwana biyu,</p><p> Yaja dogon nun fashi yana kokari cire nicktie din dake a wuyan shi,</p><p> Sai a lokacin nadan daga kai na kalleshi nace mai, ai ba komai tunda ita bakuwa ce idan ta gama abinda takeyi, tafiya zatayi,</p><p> Wanan kalami da nayi yafi komai nauyi a tare da shi,har wani dan gumi ya ke keto masa ya rasa abinda zai ce min,</p><p> Yai dan tagumi ya kura min ido yana nazarin wasu abubuwa, da ga zuciya na</p><p> A hankali na ce mai don Allah kayi hakkuri, ina son in karasa shiryawa don zan fita school ne,,</p><p> Sheriff yace haba Fatima wanan hakkurin da kike bani yana kara min kunya da nauyin ki, </p><p> Ki daina bani hakkuri dan Allah,ke ce yadace in baiwa hakkuri da zalluntar da Aziza tai maki,</p><p> Ke da dakin ki da komai na sirin ki a ciki tasa kikafita kikabar mata daki </p><p> Kikadawo nan ki zauna saikace wata bakuwa ko wace batada iko da gidan ta,</p><p> Wanan gidan naki ne don ki na saya don farin cikin ki da na yan uwana,</p><p> Ita na ta gidan na Dubai da Abuja don tace bata iya zama a saudiya saboda zafi da kuma yanayin garin da bai mataba,</p><p> Niko kinga zamana anan yake saboda anan Allah ya tsagamin arzikina,</p><p> Kinga ko dole in gyarawa iyalina inda zamu zauna cikin don rayuwa tare da yan uwana,</p><p> Dan murmushi nayi mai,irin mai, nuna alamar bakin ciki azuciyar mutum,</p><p> Nace bam cancanci kabani hakkuri ba sheriff saboda ko da can nasan wanan rayuwar zai biyo baya daga matan ka,</p><p> Babu wacce ban san abinda zata iya ba da wanda baza suyi ba,</p><p> Don haka don nadawo nan ai ba wani abu bane saboda duk cikin gida gudane kuma dan bambancin dakin kadan ne kawai,</p><p> Saboda haka duk wani cin fuska da aziza ko nafisat za suyi min zan hakkura dashi matsayin ba rayuwata ko lafiyata zasu yi kokarin tabawa ba,</p><p> Da sauri ya rufe min baki yana fadin ki daina fadin haka Fatima ,</p><p> Ya dade rugumay da ni a jikin shi yana dan shafa min baya kamar wacce tai kuka ake lalashi,ta,,</p><p> Sai kuma ya sake ni da sauri naga ya wurga da tie din shi saman gado, yafita waje da sauri,</p><p> Ina ganin fitar shi nai sauri na suri yar jakata na fita cikin sauri nabar gidan,</p><p><br /></p><p> A kwance take abinta saman gado tayi wani shamay shamay da ita tana ta kwasan barcin ta a hankalin,ta kwance,</p><p> Daskarewa yayi wuri guda yana mata kallon takaici da tsana,</p><p> Mace kamarta ace,bata ina kwanciyan cikin kimtsi ba, ko na tsuwa, </p><p> Wanan ai sha shan ci ne,</p><p> Kwace take tana saye da yar doguwar, riga, kusan duk rabin cinyarta a waje yake, tim,,</p><p> Saida ya gyara tsayi yadan lalubo natsuwar shi saboda takaici da haushin ta da yake ji,a lokacin,</p><p> Gurin gado ya nufa rai a bace, don yasan cewa ko sallah batayi ba a lokacin,</p><p> Labule dakin yadan daga sai hasken rana yadan baiyana,</p><p> Dan bubuga mata kafa yayi tai wani irin mika, tadan bude ido da niyar yiwa mai shi masifa,</p><p> Sai sukayi ido biyu da sheriff, dake tsaye fuska tamau, a gaban ta,</p><p> Harara ya dankara mata yace mata kinyi sallama dai kuwa,</p><p> Takara yin mika tace yanzu nake batun tashi in yi fa,</p><p> Yakara tsayawa saitin kanta yace may kike yi a dakin Fatima kuma,, cikin wani irin dakiya yai mata magana,,</p><p> Ban fahince kaba Ahmad ,</p><p> A ina kake son in sauka dama </p><p> Cikin mamaki yace mata duk gidan nan ba wani daki ne sai wanan da Fatima take aciki,</p><p> Daga kwance tai wani gyara kwanciyar ta tace ina, wanan shine dakin ka,</p><p> Kuma aciki na sauka,</p><p> Shout up my friend, baki da ko kunya da zaki fadi wanan maganar,</p><p> Itama dai wani mikewa tayi zaune, tace,</p><p> Ta dankara mai wata muguwar harara, tace ban fahici hausar ka ba ada amma yanzu nagane nufin ka sosai </p><p> To bari kaji, niba wulakantancciya ba ce, balle ka wulakantani ka kaini masaukin baki kace in sauka a ciki,</p><p> Ya buga mata tsawa da bai taba mata irin shi ba sai yau yace, </p><p> Ke dan Allah ki yi min shiru, in ba haka ba, yanzu ki san ko waye Ahmad,</p><p> Tayi murmushi ta mike tsaye daga zaunen da take, </p><p> Tazo gaban shi, gab da shi ta tsaye da kyau a gaban shi tace , au tau, </p><p> Ashe da ban san kowaye Ahmad ba zaune nake da kai kawai,</p><p> Tayi wani irin murmushi mai nuna takaici,</p><p> Ai,Saika gwada min ko kai waye yau in gani tunda na shiga dakin yar kwailar matarka saboda ita saika dake ni ko,,,</p><p> Tana wani jijiga jiki da kafa,</p><p> Kafini sanin ko wacece Aziza,kuma kasan kadan daga cikin aiki iskancina ya damay naku ya shanye,</p><p> Ahmad ni bani kwadayin dukiyar ka kai kawai nake so,</p><p> Wani malalacin kallo yai mata a lokacin da tace ita bata da mu da dukiyan shi,</p><p> Batasan cewa CCTV ya tona mata asiri ba ko,</p><p> Taci gaba da fadin akan wanan yar kwailar baka isa ka wulakantani ba,don kaga ina sonka har za kai min wulakanci a kan wata,mace,</p><p> Yau ran yan maza ya baci so sai, gashi ba halin shi bane bugun mace ko zagi,</p><p> Kafin yadauki wani mataki maman Umar tashigo daki don dafa mata ruwan zafi </p><p> Ganin da tayi Aziza natawa sheriff masifa kamar zata dake shi, ta juyo zuwa gurin su da sauri </p><p> Kafin tai magana sai ya juya yabar dakin rai a bace,</p><p> Dakin da nake yakoma yana shiga ya iske har na wuce ko,</p><p> Ya samuri ya dade a tsaye yadan dafa bango, ya na ta tunane,</p><p> Idanu shi sun juye sun yi ja jarir tunda yake baitaba tozarta irin yau ba,</p><p> Wai matar da yake aure ce hakana kamar zata dake shi,</p><p> Inda ace shi mai dukar mace ce bugu daya zaimata sai an zuba mata ruwa,,,</p><p> Itako Aziza yana fita dakin idon ta yakade, yai jawur, ta dinga tuna ko ita wace da har za,ai mata wulakanci akan fadima,</p><p> May fadima ke nufi da itane a rayuwa yadda take son Ahmàd ace yau, shida kan shi har zai mata wulakanci akan yar aikin matar shi,</p><p> Wasu hawaye suka zubu mata na bakin ciki ta fada saman kado ta shiga rusa wani irin kuka,</p><p> Saida ta gaji ta mike don kanta, tace fadima sai na ga bayan ki kafin in bar kasan nan,</p><p> Gobe bazaki kara tsaya min agaba ba,,,</p><p> </p><p> Gidane ginan laka irin na kauye duk da gidan tsohon gidane bazaka gane ba saboda sabon yaben da akaiwa gina ga sabon jinka asa asaman rufin dakin ya koma kamar sabo,</p><p> Ta kofar dakin ayin mai sabon shafe irin na kauye laka laka,siminti ,siminti,</p><p> Darni gidan na subur karan dawa ne akayi amfani da shi,</p><p> Ga icen zogala da na durumi an zagaye darnin gidan da su gefe tulun na ruwa ne da babban randar ruwa suma sabbi fil da su,</p><p> Daga can gefe han yar zuwa yauce (makewayi) turke ne na raguna manya manya sai wani fasashe rada inda ake zuba ma dabbobin abinci,,</p><p> Ga kaji nan sunkai goma irin na gargajiya suna ta kiwo atsakar gidan,</p><p> Tafito dakin da tana gyara daurin zanin ta da ke kokarin banyewa irin daurin zanin yan kauye da ake tankwahewa gefe guda,</p><p> Hannu guda na dauke wani dan karamin kwarya,</p><p> Cikin kwaryan gumba ne wanda zata dama kunu dashi don karin kumallin su na safe,</p><p> Inna yar Kulu ke nan mahaifiyar Fadima,da ke zaune a garin dogon daji mai rijiyar biri,zam,zam dake acikin jahar sokoto,</p><p> Duk da mutanen kauyen nawa inna yar kulu kallo wata wacce ta ke cikin wani irin daula ,</p><p> Ga kiwon tumakai da akuyoyi da takeyi, ga kuma shanu har biyu da ta turke gefe guda,</p><p> Duk cikin kudin da Ruggaiya ta kawo masu ne, duk da inna taki karban kudin duka a hannunta,</p><p> Bakin murhu ta zauna tana dan gyara iccen da ke kama da kara sai tarin hayaki da ya bude gidan dashi wanda har makwabta a na iya hagen shi,</p><p> Alamar cewa ke nan ta hura wuta a gidan ta kasan cewa bakowani gida ake dama kunu ko yin wani abin kari ba,da safe,</p><p> Saidai fura da za,a aje a cikin wata r langa ko kwarya ko fanteka, </p><p> Wanda aka dama tun jiya ko kuma an kirba shi tunjiya, yayi tsami har yagaji, </p><p> Shiza asama ruwa a motsa kowa yazo yadinga diba, a yar korya ko roba ana sha,kamar yadda kowa yasan kowani kauyen hausa sukeyi,</p><p> Abinci sai ranan jumma,a ake dan yin tuwon shikafa ko na dawa, yara su dinga murna suna fadawa junan su cewa yau jumma,a </p><p> Kowani gida za,ai girki tuwo da miyar yakuwa da alaihu, da kabewa,</p><p> Wasu kuma tuwon kullun dawa da miyar danyar kubewa ,,ko kuka, fara fat da ita,</p><p> Hakan yasa suke ganin cewa inna ita tanajin dadin ta sosai don tun filazan ita gidanta tana dafawa yaranta abinci ko ba dadi sai sunyi shi sau ukun nan,,,</p><p> Gidan inna ko yaushe tsab yake da shara, duk da kiwon da takeyi bai hanna ka gane cewa tayi shara, a rana,</p><p> Saida ta gama dama kunun ta sa ma mariya kira wacce ke daki tana shirin zuwa makaranta boko ita da dan autar inna Abdul wanda suke cewa datti,</p><p> Mariya tafi cikin kayan makarantan ta tazo inda inna ke dan motsa mata koko a cikin wata yar roba mai fadi,</p><p> Inna tace mata ta koma daki ta dauko sukari a cikin leda wanda suka siyo jiya ya rage,</p><p> Alokacin Datti ya shigo gida da yar leda baka a hanun shi wanda ya sayo kosai da shi,</p><p> Ya mika wa inna laidar tadan jawo wani dan plate din silver ta kasa masu kosan kashi uku ,kowa guda guda,</p><p> Saida Datti ya fara shan kokon ne yace inna ai na manta ban hwda maki ba,</p><p> Kai wai wani irin yarona haka duk sanda kattaho cin abinci sai kayi dumi, (magana)</p><p> Waga dabiar banzata koda yaushe ina hwda maka, </p><p> Ko ni,an inna ki kasani ko wani sabon batu na yyajiya shina shika son shi,hwda muna,</p><p> Ke,ke ke banison shegantaka kejiya,</p><p> Mariya dake gefe takalli Abdul tace tadan tausa murya don kada inna taji su tace, </p><p> Shin minana kaka son cewa Adullahi,</p><p> Ke ko ni an bashi tun da wanda abin yya shahwa tace in bari to ni mi nika hwdi kuma,</p><p> Inna dake jin su ta waigo takawai mariya rankwashe akai tace </p><p> Kai waga diya anyi yariyar kawai, </p><p> Shin kuna sauri kutaizuwa makarantaga ko ko sai kun yi abinda mallam yattabi jikin ku,</p><p> Abdull daya tashi yana sa takalmin shi na roba na makaranta saida yakai kusan fita bakin gida ya waigo inda inna ke tsaye ta sance kullin kudin da tayi a gefen zanin ta,wanda zata mariya kudin kashi, haka yara ke kiran irin wanan kudin safen da uwaye ke basu dan sayen dan wani abu,</p><p> Ya waigo cikin dan daga murya don inna taji maganan,</p><p> Yace mariya ke,</p><p> Macen nata wadda akacewa ta sace fadima ita ta naggani jiya ana taratara da inta anka hiddo ta cikin mota wai bata da lahiya ,</p><p> Tasamu mutuwar jiki,na shina za,ashiga da ita cikin gidan su dan isah yyacce wallahi tallahi shikam sam bagidane ba tunda yawon dandi ttahito ,</p><p> Wassani ko mugunyar ciwona, takkwaso ta taho ta watsa musu duk su mace har ita,</p><p> Inna da mariya da ke tsaye suna sauraron shi duk sun maida hankali gare shi,</p><p> Cikin karaji inna yar kullu tace , shin wata macce na kaka nuhi,</p><p> Badai Gajiye ba ta gidan su Dan isah </p><p> Ya awo ita ta mana naka nuhi,</p><p> Ko yanzu da natai z duduwa mai kosai maganan na nijjiya suna yi ita da tunba,</p><p> Salati inna yar kulu tasa sai da duk yaran suka kallo inda take tana ta rafka salati,</p><p> Shinka wa hwda maka wagga mugunyar magana,</p><p> Nihw da ijjiyana naggani inda muka warigi dadare nan na motat tatsaya aka tambaye mu gidan su dan isah,</p><p> To, to to kutai zuwa inda zakuna dawagga bakar labari dakkatare mu da shi tunda wagga farar sahiyan,</p><p> Bayan hita yaran sai duk maganar da Abdull yafadi ya dami inna acikin zuciyar ta duk sai taji bata da sukuni, </p><p> Tana gama duk wani dan aiki dake gabanta tashiga daki tadauko hijabin ta tasa tasa ma kofar dakinta kwado padlock,,, kamar yadda takeyi idan zata fita ,,</p><p> Gidan su yar Ammo mai masa tafara shiga don jin ko maganar gaskiya na ttajiya,</p><p> Aiko tana shiga, cikin gidan su yar Ammo ko gaisauwa bata barin sunyi tace </p><p> Tace aho yar kulu, agaishiki,</p><p> Inata ingwaiya,</p><p> Kun kwan lahiya,</p><p> Kedai wagga an ko gaisuwa ban bari munkayi ba,</p><p> Shin nicce ko ke jiya </p><p>Minana, inji ina,</p><p> Batunga da anka hwdi mana Ganiye ta tazaka naniyagga da cutar kabari kusa, </p><p> Ke ga dadi yayi kai ke nan,</p><p> Ta ballo goro da tadauko daga cikin radan ruwan ta ta balla ta miko wa inna dan guntun balli,</p><p> Inna ta ce a,a ha, aini yanzu sam banicin gora, wadda nicci shi hakana zaita wahalsam,</p><p> Shina, sa, dai nibari kedai,</p><p>To yanzu a,a ankaciki da ita shi,</p><p> Kedai bari yar kulu am,</p><p>Ance saida maigari yakkiranwo dan isa da kainai yamai hwada </p><p> Yanzudai can dakin da suka aje tumakainai da can na yaggyara mata,</p><p> Jin haka sai tausayin Gajiye ya kama inna tun bata ganta ba,</p><p> Ita da su Yar Ammo suka tahi gaida Gajiye inda suka hadu da wasu mata, yan gulma sunyo turuwa sun gano gajiye zasu fito daga cikin gidan,</p><p> Suna gani inna sai suka kama magana cimin tausayi </p><p> Allah sarki ke gani ba dakanta ttataho gaisheta,</p><p> In, nita wallai banzuwa gaida wagga bakan mace </p><p> Wadda taimin sanadin batan "yata ta salwanta cikin duniya,</p><p> Sherin tana kacin ta,</p><p>Inna dai tabi ta gefen su ta raba ta wuce batare da ta tsaya sunyi wani dogon gaisuwa ba,</p><p> Cikin gidan kuma suka iske wasu tsatsaye gefe ana ta maida fadi,</p><p> A ho yar kulu inji wata bakar mata yar likutitiya da ita,</p><p> Kema ketaho nan niya inda Gajiye kiga wadda Allah yai maisheta,</p><p> Jin yar kulun da Gajiye tayi an ambata daga cikin dakin da take kwance cikin ban tausayi, yasa ta dan yin yunkurin dagowa da sauri,</p><p> Nan take mata suka sa ihu suna shirin watsewa da gudu, don tsoro ,,</p><p> Inna ce tai karfin halin shiga don ta leka taga Gajiye saita ganta kwance cikin, kazanta duk ta bata jikin ta, salati ina tayi tadibi wanan matar tace mata,</p><p> Habadai inno a,a kuka barin maralahiya cikin wanga kazanta haka,</p><p> Ke yar kulu waka zuwa kusa da ita yakwaso wakainai cutar zamani,,</p><p> Cikin karfin hali innata ce abata baho ,</p><p> Inno ta ce a,a walla wakabada baho nai a halaka mai,</p><p> Dan haka inna ta koma gida dasauri ta dauko bahon ta sabo da hafsi ta aiko mata, dashi lokacin da ta haihu ba goyo,</p><p> Wanka inna tai mata ta gyara dakin tas tasa turaren wuta na tsuke sai dakin yadan canza kamshi,</p><p> Saida ta gama mata komai saita bata dan sauran kunun da suka sha dazu ita da yara,</p><p> Hakan da inna taiwa Gajiye sai kawai ta kama zubda hawaye tana cewa inna ta yafe mata dan Allah, </p><p> Dan tasan cewa ta cuce su ita da diyarta,</p><p> Dan isah ne ya shigo gida cikin sauri lokacin da yan gulma suka fada mai cewa inna taiwa Gajiye wanka,</p><p> Can yadan tsaya ta kofa ya ce ,</p><p> Shim ina yar kulu inata ce gani nan ,</p><p> Yace mikkai ki wanga kasada, innatace tamay fa dan isah,</p><p> Wankafa ankace kin mawagga muguyar bakuwa da tazzaka da cutan zamani,</p><p> Ganiye na kuka tana fadin ita ba cutan zamani ke jikinta ba,</p><p> Hawan jini ne yakamata,</p><p> Yace kaji yan nema bakar mugguya, aniyar ki ta biki,</p><p> Lokacin da kike, Gajiyen ki wakika kulawa cikin mu,</p><p> Yanzu da ciwi yakam maki shinakin kasan kina da yan uwa nananga ko,</p><p> Innata ko ni am dan isa karaga mata ko taji dan dama dama,</p><p> Shin dawane zataji,wagga tsiyaye dakaka mata ai shizaisa takara kawai kwance,</p><p> </p><p> Hakana inna tadauki dauniyar Gajiye har abincin ta,</p><p> Anna cikin haka watarana Allah yakawo Ruggaiya taxo ganin inna ita da mijinta suka zo ma inna da kayan masarufi kamar yadda takeyi bayan duk wata uku uku saitazo ganinsu takawo masu kayan amfani ,</p><p> Inna ta ba Ruggaiya labarin gajiye sai Ruggaiya tace kai inna kusan dai duk halinki ashe fadima ta kwasa ke nan,</p><p> Inna tace to maye duniya ai mutum bai wuce gaddaranshi,</p><p> Allah ya nufi Gajiye ce sanadiyar rabani da yar diyata</p><p> Amma ko kusa ban rike taba don nasan cewa komai mukaddarine,</p><p> Rugaiyya ta taimaka ita da mijin ta don akai Gajiye asibitin sokoto dan agane ko may matsalar ta,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>[11/5, 5:58 PM] +234 816 741 8349: ✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣7⃣</p><p> B Y </p><p>🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,</p><p><br /></p><p> Assalamu Alaikum yan uwa musulumai,</p><p> Dan Allah a tsakanin marubuta da makaranta yakamata asamu kyakyawan facin ta,</p><p> Bawai challenge's ya shigo ciki ba, idan har marubuci tayi wani abin da yadan kauce wa addini ko tarbiyan mu yakamata akirata in prevent aimata gyara ,</p><p> Babu wanda yawuce gyara aduniya, tundai na fannin addin mu,</p><p> Yima marubuci cin fuska a bainin jama,a baida amfani wlh,</p><p> Wanan rubutun da kuja ga munayi abune mukaddari daga Allah, akwai masu so soyi amma Allah bai basu ikon yi ba,</p><p> Bakaramin wahala ke cikin rubutun novel ba yan uwa,</p><p> Yakamata duk yadda marubuciya tai novel din ta a gode mata, indan har da gyara akira mutun a gefe not in public aimai gyara,</p><p> Pls mukuma marubutan Allah yakara bamu hakkuri a tsakanin mu mukara daurewa da makarantar , duk abinda kayi ba aima korafi akai ba, wanan abin baida ma,ana ne ,,,,,</p><p> Idan nafadi ba daidai ba ina mai rokon gafaran ku yan uwana,👏👏👏👏</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> Kitchen din shiru yake babu kowa acikin shi sakamakon kashe na,urar da zata sada ma kitchen din da ruwa,</p><p> Hakan yasa ma,aikatan fita waje don ganin ko may ye matsallar ,</p><p> Maman Umar abin ya bata mamaki kasancewa ko a daren jiya itace tayi aikin karshe a kitchen din kuma ruwan yana zuwa normal,</p><p> A hankali ta fito daga dakinta tana tafiya cikin sanda har ta shiga kitchen din,</p><p> Saida ta leka ta tabbatar da ba kowa a waje lokacin ta ciro wani dan koya daga cikin gefen breast din ta ta jefa a cikin flower sinasir da maman Umar ta kwaba ,</p><p> Tafito da sauri tana dan waige waige, bayanta,</p><p> Tana shiga dakin ta tashige bayi ta wanke hannuwan ta tsab, takoma saman godon ta kamar wacce bata tashi daga barci ba,</p><p> Bayan angyara matsalar ruwan maman Umar ta dawo taci gaba da aikin ta,</p><p> Tanagamawa ta jera komai a carpet saura kuma masu ci a table aka kai masu nasu, saman tebur,,</p><p> Saida kowa kusan ya hallara a falon wurin karin kumallon safe,</p><p> Kusan nice ta karshen zama a falon saidai ba a saman kujera na nufa ba,</p><p> Wurin Ummi na nufa don a saman carpet, take zama ,</p><p> A hankali na dan durkusa gami da kara gaida Ummi karo na biyu,</p><p> Saida na sawa plate dina komai da nake sha,awa, nadan tsiyaya ruwan sha, a cup na aje a gefe na,</p><p> Nai bissimillah nadauka zankai wa bakina,</p><p> Aziza dake zaune daga gefen mu ta kura min ido, Allah Allah take yi in kai a bakina,</p><p> Daidai lokacin da zan kai a bakina sai wayana dake gefe yadauki ruri </p><p> Mayar da sanasir din nayi cikin plate na, nai saurin daukar wayan , diba massage din,</p><p> Ganin nobar Amal, da nayi yasa ni saurin ta shi kusa da Ummi , </p><p> Kada kici abincin nan fadima ,</p><p> Kuma in kin karanta kada ki dago kai ki debe ni pls,</p><p> Gashi dai nagama karantawa amma sai na kasa daga kaina sama, </p><p> Wani irin mugun tsoro ne yakamani saboda nasan cewa Amal bata maganan banza </p><p> Maimaikon in juya sai na mike kawai daga, gurin da niyar tashi ,</p><p> Muryan Ummi ce na ji tace min fadima da wo mana kici abincin cikin sanyin murya nake ce mata,</p><p> Ummi zan dauko ma salimat takarda ne a daki, yanzu zan dawo, sai kuma wani dabara yafado min nace ma ummi bari ma dai intafi da abincin daki na kawai sai inci a can,</p><p> Wani wawan ajiyar zuciya Aziza tayi,jinda tayi cewa zantafi dakina in ci,</p><p> Mutun biyu ne Allah yanufa suci sanasir din, dayake suna da rabon wahala,,</p><p> Da Salim sai Ummi duk yadda Amal taso ta hana Ummu ci acikin hikima hakan baiyi, ba,</p><p> Ciwon ciki ne mai karfi ya turnike su sai ,</p><p> Tun ana abu wasa wasa har takai ga anyi rushing din su asibiti,</p><p> Nan likita yai masu dan bayani akan cewa akwai abinda sukaci Allah nai yatai make su sun kawo su asibiti da wuri,</p><p> Yace amma inda mace mai cikine taci gaskiya da abin yafi nan worse,</p><p> Jin hakan yasa hankali kowa tashi kowa da abinda yake tunane acikin zuciyar shi gamay da abinda likita yace,</p><p> Kwanan su biyu , a asibitin aka sallamo su zuwa gida,</p><p> Har a lokacin Amal batace min komai gamay da text din da tayo min ba,</p><p> Hakan dai danaga irin wahalar da su ummi suka sha yasani shan jinin jiki na sosai,</p><p> Sai yakasan ce duk gidan hankali na a tashe yake so sai,</p><p> Gurin Salimat na tafi da kukana nafada mata duk yadda mu kayi da Amal,</p><p> Itama dai shawara tabani sosai akan yadda zan zauna da kowa agidan </p><p> Tace min akwai abinda Amal take zargi a gamay da ni,</p><p> Hakan yasa tunda ga wanan ranan Salimat ce ke kawo min abinci a boye ko kuma intafi gidan ta ince a can,</p><p> Yau bazan tafi school ba don haka na koma nadan kwanta don in huta,</p><p> A can cikin barci na rika jin kamar ana tabani sama sama,</p><p> Sai kuma na dinga jin kamar ana kiran suna na a hankali,</p><p> Cikin karfin hali na bude idanu na a hankali, tayadda ba kowa zai iya gane cewa na bude ido na ba,</p><p> Aziza ce tsaye da wani abu kamar jan kyale a hannun ta,</p><p> Can kasan gadona naga ta duka ta aje kyalen a hankali kuma ta taso ,</p><p> Ta kama hanyar kofar dakin fita zuwa waje,</p><p> Ido kawai nabita dashi a hankali har ta kure min </p><p> Bakina duk adduan da na sani na tsari saida nayi shi a lokacin wani ba ni ko karasa shi nake daukar wani,</p><p> Sai da na tabatar ta wuce tundazu sai na sauko da bissimillah tare da naiman tsari ga Allah ,</p><p> Ta gefe gudan nabi ban yarda na bi ta inda nagantaba tsaye,</p><p> Bayi na fada da wayana nakira Salimat na sheda mata abinda nagani,</p><p> Ba,adauki wani lokaci ba ta shigo gidan da shirinta,</p><p> Ita da Amal ne suka dauke wanan jan kyalen suka samo wani jan kyale na rigar Amal irinshi suka aje mata agurin,</p><p> Mamaki duk ya kashe mu, Salimat ce tafara magana daga cikin mu,</p><p> Tace wai may yasa wanan matar batada imanine haka,</p><p> Mundade muna shawara a tsakanin mu so sai,</p><p>A ranan ga dare ya raba amma sam babu alamar barci a ido na,</p><p> Duk da nasan cewa sun fitar da mugun abin a dakina </p><p> Tunane nayi ko may yasa sheriff yin tafiya tun ranan da yadawo batare da yadauki ma aziza wani mataki ba ,</p><p> Ajiyar zuciya na saukar cikin tausayawa kaina ina tuna nen wanan sabon rayuwa da na tsinci kaina a cikin sa,</p><p> Gaba sai bugawa yakeyi saboda alamar gitawa da naga anayi ta dan hasken da ke hasko min ta jikin window daki na,</p><p> Na rintse idona ina ci gaba da addua acikin raina,</p><p> Saboda na sadakar da raina cewa nawaya kare kawai a wanan ranan,</p><p> Can kuma sai naji shiru nadaina jin motsin komai kuma naga a daina wanan gittawan da ake ta min,</p><p> Duk da nasan cewa na rufe dakina yau da makulli, amma hakan bai hanani jin tsoro ba,</p><p> A haka barci barawo yazo yadan yi awon gaba dani,</p><p> Sai da asuba nafarka cikin dan firgita don ji nayi kamar za a shigo min ,</p><p> Saida na kwanatar da hankalina sannan na gane cewa ai ba komai har yanzu,</p><p> Saida na tabbatar da cewa gari ya waye kuma tabbasa kowa yadan fara fitowa waje </p><p> Natashi naje nai wanka nafito kenan ina shiri naji alamar ana buga min kofan daki da karfi kamar za,a tsaga shi biyu,</p><p> Na nufi kofan pa gigice nabude a hankali, hannu na guda yana rike da dan towel din da nake tsane jiki na da shi,,</p><p> Ga mamakina Aziza ce tsaye tana ganin na bude daki naga tai wani irin shock na nuna alamar mamaki,</p><p> Kallonta nakeyi sosai babu kaukautawa,na zuba mata ido, nima,</p><p> Ganin da nayi cewa , kallon nata bana girma da arziki bane,</p><p> Kallon tababiya naimata na kallo ta wani irin shekeke, </p><p> Na juyawa nayi da zumar in koma cikin dakina,</p><p> Sai naji ta turo kofar ita ma da karfi kamar zata bangaje ni,</p><p> Turus na tsaya gami da rasa na yi hannuna, yana rawa, ina kallon ta don inga abida zatayi,</p><p> Cikin tsayin wani lokaci shiru ya biyo baya sai dai na kula da ita kamar tana kokarin kallona tana na,zarin wani abu,</p><p> Nadai daure da nagaji da kallon kallon da mukeyi na ce mata lafiya dai ko hjy,</p><p> Cikin dakewa ta ce min da akayi may fa,</p><p> Cikin rawar murya nace mata, naga kamar kina bukatar wani abune a nan,</p><p> Ta buga min wata uwar harara ta kuta saida gabana yai mugun faduwa da ga ni irin yadda tai min,,</p><p> Tawani irin juya da karfi kamar mai fada da iska tawuce, </p><p> Nanta bar ni tsaye da mamakinta,</p><p> Gakuma wani irin tsoro da firgicinta da ya kamani </p><p> Don nasan cewa a yadda taimin yanzunan zata iya aiwatar da komai akaina,</p><p> Inda tawuce tabarni nan nake tsugune amma tsabar fargaba abinda take shirin yi min yasa ni zarya a corridor</p><p> Ina ta tunanen mai yasa Aziza take farautana haka saboda kawai na auri mijin ta ne ko ko may,</p><p> Da sauri namike na isa inda wayana yake jone a caji na ciro cikin sauri na kira layin ,</p><p> Sheriff tsayin wani lokaci naji shiru, sai can daga bisani naji computer tana gaya min wayar a kashe take,,</p><p> A rude na nemi layin Amal, itama hakan ne ta kashe wayar ta,</p><p> Sai dabaran kiran Salimat yazo min,</p><p> Ina samun ta ta dauka,nan na shiga, fada ma Salimat cewa tazo ba lafiya,</p><p> Hankalina a tashe nake maganar , hakan yasa tace min gata tafe,</p><p> Kafintazo saita bugowa maman Umar waya tasheda mata cewa tazo dakina da sauri ta diba mata halin da nake ciki,</p><p> Maman Umar tasamay ni na dan rakube a bakin gado ina kuka,</p><p> Ban boyewa maman Umar komai ba tun abinda Aziza tai min safiyan jiya,</p><p> Har zuwa cikin dare dakuma yadda mukayi yanzu da ita,</p><p> Salimat tafado dakin a rude nafada mata duk yadda na kwana a dakin da kuma abinda mukayi da ita yanzu</p><p> Saida ta nisa sosai can tace min shawar guda zan baki fadima,</p><p> Tace min ina passport dina nafada mata cewa yana nan,</p><p> Ita ta shirya min duk yadda komai zai kasance gare ni,</p><p> Tasa maman Umar ta kwaso min duk wani abin bukatana adakin dakuma wasu kudi masu yawa da naita boyon su da dadewa,</p><p> Salimat ta kwashe kayan zuwa gidan ta batare da sanin kowa ba,</p><p> Ta yadda ko CCTV ba za a gane cewa kaya ta dauka ba,</p><p> Duk wani motsin da za a yi a wanan yini a tsorace muke nida su salimat da maman umar don ko ruwan gidan nadaina sha yanzu,</p><p> Azizako sai fita takeyi tana dawo tare da wata yar doguwar takari fara wace tayi bleaching duk ta kode,</p><p> Ranan dole tare muka kwana da maman Umar adaki daya,</p><p> Washegari tun da safe nai shirin zuwa makaranta, saboda kasancewar itace ranan da zan rubuta jerabawar karshe,</p><p> Ina kallon Ummi cikin tausayawa saboda har yanzu jikinta baida wani karfi sosai,</p><p> Amal tana ta jana da hira saidai sama sama naje dan ansa mata,</p><p> Can dai tace min wai may yasamay ni ne yau taga duk bani cikin hayacina sosai,</p><p> Nadan kakaro murmushin dole nace haba Amal yaune fa zan gama exam dina aiko kinga dole in dan damu,</p><p> Dazamu tafi naba maman umar takarda nace taba sheriff idan yadawo kasan ,</p><p> Ina gama exam ko min ti biyu bamu karaba muka dauki shatan taxi nida salimat sai jedda,</p><p> Ina rugumay da Aisha wace mamata ta ce min in wuce da ita duk inda zani tabar min ita,</p><p> Batare da bata lokaci ba akai muna screening duk na ka gu inga mun shiga jirgi </p><p> Ina jin anfara kiran yan jirgin mu sai kuma kuma al,amarin ya juye min duk naji ba dadi, a raina, </p><p> Saboda nasan cewa Ummi bazata ji dadin abinda nayi ba, </p><p> To amma yaya zanyi dole ne in tserar da rayuwana ,</p><p> Karfe tara na dare jirgin mu yatashi daga jidda zuwa Nigeria,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣8⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p>Almost true life story</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Addu,an Ku a,gare ni tankar wani ruwa, ne mai karawa fulawa karfin tofowa daga kasa </p><p> Banda abinda zance maku sai dai in muna fatan alheri kasancewa a aljannan fiddausi a tare ranan gobe kiyama,</p><p> Allah ubangiji ya kara rufawa duk kan musulumi asiri duniya da lahira,</p><p> Allah yasa muna cikin wa,"yanda Annabin rahama zaiyi alfahari da su gobe kiyama, Ameen Ameen 👏👏</p><p> Nagode kware da irin kaunar da kuka nuna min tare da kulawa da fatan alherin ku a gareni</p><p> </p><p><br /></p><p> </p><p> Muna tsatasye saboda jin da mukayi cewa matafiyan wanan lokacin su matso kusa,</p><p> A hankali na daga kaina na kalli Salimat wacce ke tsaye rugumay da baby Asma,u a kafadar ta,</p><p> Wani irin hawaye masu zafi da kuma kunar zuciya, suka dan silalo min daga ido na,</p><p> A hankali cikin dishashiyar murya ta kuka nake wa Salimat godiya bissaga arin taimakon da taimin,</p><p> Itama muryan ta a dishe take min magana, fadima naso ace wanan tafiyar da Sheriff zakiyi shi, </p><p> Saboda irin dadewar da kikayi baki gida kuma gashi yanzu kina a cikin lalura,</p><p> Kinga zargi da tuhuma zai biyo bayan isarki, gida a haka,</p><p> Saida na hade wasu miyau masu daci tukun nakuma goge hawayen da yakara zubo min na ce ai Allah shine shedata ,</p><p> Mundan kai wani dan lokaci a tsaye gurin salimat ta , tabani shawarwarin yadda zanyi idan na sauka a Nigeria, saboda tace saukar safiya zamuyi,,</p><p> Muna a haka har aka kira mu zuwa cikin jirgi, hanun ta na kama, saboda umurnin karshe da mukaji,</p><p> Na sake ta a hankali na nufi cikin jirgi, tafiya daya biyu sai kuma na juyo da sauri na nufota na rungumay ta,</p><p> A gabanta na tsaya, Itama kuka tasake mai karfi a lokacin, ta rungumoni zuwa jikinta, tace min kiyi hakkuri kinji hakuri zakiyi fadima </p><p> Kowa da irin rayuwar da Allah ya zana mai, ke taki kaddaran ke nan fadima,,</p><p> Ina kuka tanayi nasake ta dole badon mun,so ba,</p><p> Karfe tara na dare daidai jirgin mu ya ta shi daga birnin Riyadh zuwa Nigeria, </p><p> Tunda jirgi ya rufe nake kuka saida nagaji don kaina, nayi shiru tare da lomo tankar mai barci Al,amuran da dama suka dawo min tamkar yau suka kasan ce,,</p><p> A cikin jirgi ma ina ta dan sheshekar kuna, Ina tuna kalamin Salimat a gareni na karshe inda take ce min fadima ki gashe min da iyayen ki da yan uwanki insha Allah da na dawo Nigeria zan bide ki,</p><p> Kuka na sake a lokacin dan, tunawa da wanan kalamin,,,</p><p> Na kan kame Aisha dake gefe na tana barci abinta hankalin ta a kwance,</p><p> Ina kallo kowani set mutane na ta barcin abinsu niko idona, kem nakasa koda rintsawa a lokacin,</p><p> Saboda tunanen da ya addabi zuciyana, a lokacin, nasan cewa nayi nisa ke nan da su Sheriff da su Amal,</p><p> Can kuma wani sabon tunane yazo min ,</p><p> Ko yaya zan riski inna na da yan uwana,</p><p> Sai kuma kewan hafsi da mariya ya zo min fam a hankalina,</p><p> Ta gefe na naji wata yar siririyar murya na ce min hjy ko akwai abinda kike bukata ne,</p><p> A,hankali nadago na kalli gefen yar matashirya ma,aikaciyar jirgin ce ke min wanan tambayar,</p><p> Kai kawai na girgiza mata alamar a, a kawai sai naji tai min godiya ta wuce a hankali,</p><p> Sai kusan asuba jirgin ya sauka a filin jirgin malam Aminu kano, </p><p> Sain da jirgin ya sauka saida yakara wasu yan mintina masu tsayi sannan aka, bude kofar a ka manna matakalan jirgin,,, </p><p> Ban ko motsa daga mazauni na ba ina zaune har kowa ya gama fita,</p><p> A hankali na kama hannu Aisha muka sauko ,</p><p> Koda na sako kaina wajen jirgin sai naji na nashaki wata iska, mai yar tiririn dumi,</p><p> Saidai a cikin raina wani sanyi naji yau yau ni fadima ni ce a cikin kasar Nigeria,</p><p> Abinda nadade ina mafarki da tunanen hakan,</p><p> Sai gashi yazo min da sauki,</p><p> Bayqn shekara takwasa da nayi rabona da kasar ,</p><p> Sannu a hankali nake saukowa daga jirgin na rika aje kafa na ina maida yar uwar ta,</p><p> Sai na lura da cewa duk wanda ya ganni sai ya kara kallo na karo na biyu,</p><p> Ashe ni ban sani ba tafiya ta da irin shigar da nayi yana nuna cewa ni din wata hamshakiya ce ko matar wani babban mutun </p><p> Saboda yanayi na ya nuna a ,sarauce ko koma mulke nake komai nawa,</p><p> Wanda ni sam ban san cewa haka nakeyi ba,,,</p><p> Shigar da nayi irin dogon rigar nan ce mai mannewa a jiki nasa a ciki, </p><p> Sai sama nakawo daya daga cikin ire, iren dogayan rigunan da Sheriff ya saya min lokacin da mukaje kasar Arab ta tsakiya da kuma Dubai,</p><p> Don haka daya daga cikin su na sa a sama, rigar alkyaba ce mai tsananin tsada rigar da ganin ta kasan cewa ta matan mayan ce,</p><p> Ko a cikin larabawan sai wace ta isa take sanyata,</p><p> Yau ni fadima diyar inna yar kulu itace min a jikina,</p><p> Hular alkyabar ma tana da ban sha,awa, sosai, don zan iya rufe kaina da ita lif ,</p><p> Indan kuma naga dama zan iya sake wani dan mayafi dake manne a jikin rigar, ko in dan zarga shi yana rito a kasa,</p><p> Kamar na yafa shi, idan kuma mutum bai so sai ya sake shi ya biyo alkyabar ta baya kawai,</p><p> Toni sai na dan yafo yai min tamkar dai irin matan masarauta larabawa,</p><p> Alkyabar har wani dan jan kasa takeyi ina ta faman dan kamata a cikin style, Aisha na rike da hannu na guda, cikin shiga ta ban sha,awa itama,</p><p> Sai wani kamshi mukeyi saboda irin turaren dake a jikin mu,</p><p> Muryan wata yar matashiyar budurwa naji a gefena tace min dan Allah yar uwa ki dan tsaya muyi photo pls,</p><p> Sainai mata murmushi nace mata ai ba damuwa,</p><p> Mungama clearing na komai mun fito wajen airport din kadan ,</p><p> Ga kayana agabana kusan akwati uku ne da trolley dina,</p><p> Sai kuma nasake ganin wa yan nan yan matan da mukayi photo da su dazu acikin wata mota sun dan tsaya a gabana,,</p><p> Wacce nake tsanmani ita ce babba daga cikin su ce take magana yanzu,</p><p> Tace min har yanzu masu daukarki ba su iso bane,</p><p> Sai maganar da Salimat tafada min yafado min a rai inda tace min kada in nuna alamar cewa ni bakuwa ce a kano,</p><p> Don in banyi hankali ba zan iya fadawa mugun hannu,</p><p> Sai nadan yi murmshi nace ai zan tare taxi zuwa cikin gari yanzu,</p><p> Karamar ta riga babban magana tace anty safiya mu rage masu hannya mana, pls,</p><p> Sai naga mai suna safiyan tadan waige ni tace min idan badamu hajiya sai mu sauke ki inda zaki sauka don dama muma sako mukazo karbawa maman mu,</p><p> Driver su ta umurta da ya kwashe kaya na zuwa cikin Burt din motar su,</p><p> Saida mu fara tafiyane safiya ta dan waigo inda nake tace min wani unguwa zamu sauke ki hjy </p><p> Cikin murmushi nace mata inda zan samu motar zuwa dogon daji,</p><p> Takara maimaita sunan garin tace dogon daji,</p><p> Inane hakana kuma pls ta kalli yar uwar ta ita kuma sai tace wi malam Abu ka san dogon daji,</p><p> Tana tambayar drive su,</p><p>Shima dai cewa yayi gaskiya bai sani ba,</p><p> Safiya tace gaskiya hajiya ina ganin kawai muje dake gida indan yaso in kin dan futa sai a tambaya maki ko,</p><p> Sai nayi masu godiya da wanan taimakon da sukayi min,</p><p> A hankali gari na kara yin haske har muka isa uguwar su ta G R A </p><p> Ina kallon ko ina a unguwar gini ne na zamani kalakala kamar ba kudi aka kashe ba gurin yin su,</p><p> Wani katon get maigadin gidan ya wagale muka shiga,</p><p> Sai a lokacin nasha jinin jikina ganin wanan irin katon gidan da muka shiga, nakara matse hannu Aisha acikin nawa,</p><p> Ina karanto addu,an da yazo min a baki a daidai wanan lokacin,</p><p> Wata yar matashir dadtijiwar mace na tafi daga wani daki zuwa falon sanye da hijab har kasa hannu ta rike da tasbaha,</p><p> Cikin fara,ar ta take masu sannu da zuwa tana sa masu albarka,</p><p> Ganin da taimin tare da su yasa tai saurin kallon su da mamaki,</p><p> Karaman ce ta zagaya gurin hjy tace umma bakuwa ce muka zo da ita daga saudiya take sai muka ga ba,azo daukanta gashi kuma gari bai gama wayewa ba alokacin shine muka bata lift zuwa cikin gari,</p><p> Sai a hanya ne muke tambayar ta ko wani unguwa zata shine take fada muna cewa ai wani gari zata ba anan kano zata tsaya ba,</p><p> Hjy ta dan kalleni jin da tayi cewa aiba a kano zan tsaya ba,</p><p> Kujera ta nuna min tace in zauna mana gamu a tsatsaye,</p><p> Gashi nadauko gajiya atare da ni,</p><p> Bayan na zauna ne take kara tambayana inda zan tafi,</p><p> Nikuma a lokacin nake kara gasheta ,,,</p><p> Bayan mun gaisa ne take kara tambaya ko wani gari zantafi,</p><p> Nace mata dogo daji,</p><p> Saida ta kara nanata sunan garin saita dan kalle ni tace min a wata jaha garin yake sai nai shiru,</p><p> Ido hajiya ta tsura min nadan wani lokaci can ta juya inda safiya take zaune tace ki kaita dakin ku tadan huta kafin a hada abin kari,,,,</p><p> Da alamar dakintane takaini ita safiya din don gani katon photo ta danayi a gefen gadon tare da na mahaifiyar ta </p><p> Wankanayi nadauro alwala nagabatar da salla da ban samuyi ba, tunda asubah,</p><p> Barci yadaukeni inda nake ,zaune ina lazimi, nadan wani lokaci,</p><p> Daidai lokacin da na farka ne hjy umma ta shigo dakin na safiya,</p><p> Ganin da nai mata yasa ni kokarin tashi zaune, takaraso inda nake zaune tazauna gab da ni bisa bakin gado, nadan gyara zama na, na gaisheta, shiru yadan biyo a cikin dakin nadan wani lokaci,</p><p> Can tace min may sunan ki diyata, a hankali nacr mata fadima, tace min masha Allah suna mai kyau,</p><p> Fadima kina da aure , tambayar da taimin yasani saurin daga kaina na kalleta sai kuma na dukar da idona a kasan dakin ina mai wasa da yan yatsun hannu na,</p><p> Can dai na ce mata eh,</p><p> Sai naji tayi murmushi irin na manya tace min naga alama ai don kina da natsuwa so sai,</p><p> Dogon dajin garin kune ko garin mai gidan ki,</p><p> A hankali nace mata garin mu,</p><p> Sai mukayi shiru gaba dayan mu,</p><p> Can tace min ki sake jikin ki da mu fadima Allah ne ya hada mu dake </p><p> Ai ba yau ba nake tura yarana dauko min sako ko kuma ni inje da kaina amma bamu taba dauko kowa a motar mu ba don gudun shiga matsalar rayuwa,</p><p> Takara dan matsowa gab dani tace kada kiji komai ki fada min ko may ke faruwa da ke haka</p><p> Don tun shigowar ki gidan nan nake zargin kamar akwai abinda ke damuwar ki,</p><p> Nai shiru ina tunanen maganar ta da ga karshe dai na daure na fada mata dan kadan daga labarina,</p><p> Yadda Aziza ta sani gaba don ganin ta halakani ko ta halin ka,ka,</p><p> Taiwani irin ajiyar zuciya tace gaskiya fadima kina da sauran kurciya atare da ke </p><p> Aida ba ki wuto Nigeria ba da a gidan Salimat kika zauna har minin ki ya dawo sanan kuma ai saudiya ba Nigeria bace akwai security ta ko kada kiyi mamaki duk wani plan nata hukuma saudiya suna sane da ita,</p><p> Sai nadan dago kaina da sauri na kalleta ta daga min kai alamar eh kware da gaske kuwa,</p><p> Kada kiyi mamakin jin hakan daga gare,</p><p> Sai tace to yanzu dai yadda za,ayi kitashi ki je ki yi breakfast tukun kafin a tambayo min ko wani state garin ku yake,</p><p> Lokacin kusan bakwai da rabi na safe, don haka ban tsaya jiran komai ba na tashi na dan kimtsa zuwa falon gidan,</p><p> Saida muka gama yin breakfast din ne su safiya take dan ja na da hira kadan kadan, ina bata ansa jefi jefi,</p><p> A lokacin hjy umma ta shigo falon cikin shirin ta na zuwa office, </p><p> Daidai lokacin malam Abu ya kirata a waya yake sheda mata cewa a cikin jahar sokoto dogon daji yake,</p><p> Ta iso gurina cikin fara,ar ta tace min fatima kin ji a she a cikin jahar sokoto kuke,</p><p> Don haka zaki bari har gobe idan kin huta malam Abu driver yakai ko ya ,ya,</p><p> Sai da na dukar da kaina kasa nace, a,a umma yau dai zantafi insha Allah,</p><p> Tunda akwai lokaci shiru hjy umma ta yi har nawani dan lokaci, sai kuma naji ta dafani a hankali ta ce fatima ba,damuwa zan sa a kaiko gida yau insha Allah,</p><p> Daga haka bata kara cewa komai ba sai ta mike tsaye tadaga wayan ta tana kiran layin malam Abu driver,</p><p> Karfe takwas da wani abu mukabar garin kano muka dauki hanyar sokoto,</p><p> Ina bayan mota nida Aisha ina ta kallon hanya da irin cigaban da garin kano yasamu yanzu,</p><p> Saida mukabar gari da nisa muka kama hanya dakyau </p><p> Nadinga kallon irin yadda titin Nigeria suka lalace, </p><p> Sai natuna da yadda titin kasar saudiya suke da kya da lafiya</p><p> Amma dai ba garuruwa da yawa kamar munan kasar, Nigeria,</p><p> Yayinda muke ta kara shiga gargada da kuma rashin kyauwon hanya,</p><p> Duk hakan bai sa nadamu ba nidai gurina kawai inga mun isa gurin su inna na kawai,</p><p> Bayan irin mugun gudun da malam Abu yayi da mu saboda yana da gurin komawa yau, kano,</p><p> Sai kusan la a,asar muka shiga garin sokoto, duk a gajiye muke </p><p> Sabosa lalacewar hanya da baida kyau, ko kadan,</p><p> Saida muka dan yi nisa a cikin garin malam Abu yadan samu wani guri gefen gari yake wani dan fari saurayi mai suffan fulani dake gaban wani shago,</p><p> Ko ina ne hanyar zuwa dogon daji,</p><p> Dan saurin yace mikewa zakayi inda kaga godabe ga ta lakwasa zakabi, har sai ka kai inda flyover, sai ka kara dau hanya kamike street,</p><p> Malam Abu yai godiya yakama hanya, damu ina baya sai waige waive nakeyi ina kallon garin sokoto da mamaki,</p><p> Kwatacen saurayi muka bi har Allah ya kai mu inda muka mike hanya zuwa garin dogon daji,</p><p> </p><p> Mun isa lafiya mukaga katon signboard da aka rubuta alamar iso wa garin dogon daji,</p><p> A hankali malam Abu ya gangara zuwa cikin gari ina baya ina raba ido ko zan gane gidan mu sai dai gaskiya na kasa ga ne wa,,</p><p> Kamar yadda kowa yasan cewa kauye a na yin daba daba na matasa dakuma manyar dadtijai ko a garin dogon daji ma haka muka gani</p><p> Kasan cewa marance yayi sosai a lokacin kusan kowa na waje, gurin hira,</p><p> Wani daban yan matasa malam Abu ya tsaya da motar shi,</p><p> Yadan yafito wani dan matashi dake tsaye gaban saura yana ta zuba surutu,</p><p> Da sallamar shi ya matso gurin mu saidai idon shi na bayan mota don yaga ko suwaye a cikin motar,</p><p> Dan Allah tambaya muke yi malam Allah yasa na sani </p><p> Gida inna muke tambaya ,</p><p> Inna wacce ina inna ai yawa aggaresu garin ga,</p><p> Daidai lokacin suma abokan hiran matashi suka iso gaban motar mu,</p><p> Yawaiga yana cewa yan uwan shi da ke tambayar shi kai wai minana,</p><p> Tambayana sukai wai gidan inna suka tambaya</p><p> shina nice masu wassan iyakan innan da aggarin ga,</p><p> Daga bayan mota nace masu inna yar kulu maman mariya da Abdull,</p><p> Sai mutum guda daga cikin su yace kai gidan yar kulu na sarakuwa illu teacher,</p><p> Sainag duk sun juya inda wasu yan matasa keta wasan guje guje,</p><p> Sai yace Dule kai, dule taho nan ga wata mace na tambayar gidan yar kulu </p><p> Da sauri yaron da akakira da Dule ya iso gurin da motan mu yake,</p><p> Yana wani dan lake cikin motar ,</p><p> Wacce ta katambayar gidan mu sai na farko ya nuna mu,</p><p> Shin wata ta nicce, sai ya kara lekawa can yace shin ko fadima ta,</p><p> Baiko tsaya na bashi ansa ba ,sai ko ya juya sheka da gudu yana fadin ita ta wallah </p><p> Sauran ma suka bi shi da gudu suna ihu, suna fadin fadima ho fadima ho,</p><p> Wani mutum yataso yatare yaro guda daga cikin su </p><p> Yana fadin kai minana kuka wagga dabi,a kuwa haka,</p><p> Sai yaron yace wai fadiman da ankace Gajiye ta saisuwa a saudiya </p><p> Ita ta tta, zakka, inda muke yau,</p><p> Kai dan neman ga wa hwda maka ita tah </p><p> Yaron yace Dule kanin ta munkajiya yana ihun fadima ta zakka </p><p> Shina muma munka bishi baya muna hwadi ta zaka,</p><p> Malam Abu yabi bayan yaran a hankali inda yaga sun dosa,</p><p> Daidai kofar gidan ya samu guri ya Parker motar shi,</p><p> A hankali nadaga kaina na kalli gidan inda aka haife ni kuma mahaifiyana take rayuwa da yan uwa na aciki,</p><p> Sai naji wasu hawaye masu zafi sun dan gangaro min a fuska na a hankali,</p><p> Abdull ya na shiga cikin gida tare da abokan shi ya iske inna zaune a bakin murhu tana kada miya,</p><p> Ganin da tayi masu kamar wa yan da aka koro daga waje yasa ta mikewa tana tambayar </p><p> Minana shin kuka shigowa idan mutun haka cikin tashi hankali,</p><p> Abdull yace walleh inna fadima ta tazzaka </p><p> Zubur inna ta karasa mikewa da abin kadi a hannunta tace </p><p> Mikkace shin? ya ce a wo </p><p> Fadima dai da kinka sani </p><p> Mariya daga daki tace </p><p> Kaikan Dule wallah kaga buni da wagga muguwar dabi,a</p><p> Wacce fadima shin ? fadiman da ko saninta bakayi ba zakace wai ita ta, ta taho,</p><p> Yace walleh in karya na ni kai shegeni ke inna, </p><p> Da ijiyana niggane ta, cikin wata mota,</p><p> Da sauri nakara mayar da dibana kan gidan cike da tunane, iri iri a zuciyana,</p><p> Na balle murfin motar nafito rike da hannu Aisha,</p><p> Ina karewa gidan mu na kasa kallo cikin tausayi nake tuna cewa wai mutane ke kwana acikin shi haka,</p><p> Kai tsaye na nufi hanyar shiga cikin gidan inada aka tare kofar dawani katon katako mai kama da icce,</p><p> Da sallama na kutsa kaina cikin gidan,</p><p> Inna na tsaye tana sauraren mariya dakewa su dule fadan haukar da sukazo masu dashi,</p><p> Ganin da tayi min na shigo yasa ta tsayawa da maganar da takeyi,</p><p> Da inna taga ta tsaya ta kurawa kofar shigowa gidan ido yasa ta waigawa itama da sauri, ta kalli kofar gidan,</p><p> Cak na ja na tsaya guri guda don jin danayi numfashi na yana kokarin daukewa </p><p> Sakin abin kadin dake hannu ta tayi ya fadi kasa don kaduwar da tayi,</p><p> Tace shin fadima ke ta ko kuwa gizo idona kayi,</p><p> Gudu gudu da sasarfa na isa gurin inna na na rugumaya ta,</p><p> Abin mamaki Itama inna rugumay ni tayi sai kuma mukasa kuka gaba dayan mu, nida inna a lokaci guda,</p><p> Muryan danake bege nake tunawa in yi kuka ko kuma ya hanani barci naji yau kamar a mafarki a bayana,</p><p> Tana cewa shin fadimata wagga ko kuwa wata ta,</p><p> Wani irin juyi nayi na sake inna na fadama hafsi muka runguma junan mu,</p><p> Muka dan dago muka kara kallon junan mu sai kuma muka kara rungumar juna cikin karfi sai mukasa dariya cikin murya mai cike da farin ciki ,</p><p> Takara dagoni tace walleh fadima har yanzu ban gaskanta cewa keta ba,</p><p> Nakar rungumo su lokaci guda ita da inna ina fadin kasa, kasa ,I miss u sai kuma nasa kuka mai tsima rai,</p><p> Ta bayana naji muryan Aisha tana fadi cikin larabci cewa zata tiyi fitsari,</p><p> Nadan dago fuska na da yayi caba caba da hawaye nadubeta nace tazo in cire mata wando in kai ta,</p><p> Sai a lokacin su inna sukaga Aisha,</p><p> Da muke tare, sai kuma kallo ya koma gurinta, kowa da mamaki fam a zuciyar shi,</p><p> Mariya da tagane ko may Aisha zatayi yasa tai saurin riko hannunta daga wurina zuwa bayi,</p><p> Hafsi takara matsowa kusa dani tace shin fadima ta a haka shin, cikin mamaki tana ta faman taba min jiki cikin mamaki,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 7⃣9⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Cikin dan kankanin lokaci duk labari ya karade gari dogon daji cewa,ai fadima ta dawo da ga inda Gajiye ta saida ita,,,,</p><p> Mutane sai tururuwan zuwa gidan mu sukeyi don tabbatar da zancen</p><p> Wasu kuma suna zuwa don gulma ne saboda irin yadda ake fada masu na koma kuma na,zo da diyar larabawa tare da ni,</p><p> Malam Abu ya sa aka shigo min da kayana cikin gida, mu,</p><p> Da taimakon mariya duk aka shiga da kayan dakin innan mu,</p><p> Duk da lokaci ya kure amma malam Abu driver ya ce a lokacin zai koma kano wai,</p><p> Wasu jallabiya masu kyau na mata na bashi yakawai safiya da Amman,</p><p>Shikuma na bashi irin ta maza, sai hjy umma da na baiwa turare da tasbah mai tsada,</p><p> sai fura ta shinkafa dakar hannu da nono mai kyau, inna tabayar akaiwa hjy umma,</p><p> Nasan cewa idan nabasu tun acan kano, baza su karba ba saboda kawaici,</p><p> Shiyasa nai wanan dabaran na bari sai malam Abu zai koma in ba shi sako ya kai masu,</p><p> Yawanci zaga cewa idan tafiya ta riske ka, har marance yai ma, zaka wuce wasu yan garuruwa da wutan lantarki, </p><p> Amma da ka shiga garin da zaka ko bangaren da kake sai kaga dundum babu wutan ,sai bakin duhu ko yan haske a yan tsirarun shagunan kauyen,</p><p> Don haka na lura cewa tun zuwa na har yanzu nepa ko kil basu muna ba da wuta,</p><p> Har kusan karfe goma dare jama,a ke ta shigo min barka da zuwa,</p><p> Ban kara samun lokacin zama da yan uwa na ba tun bayan isowana da muka dan kebe da su,,</p><p> Mariya ce ta raka, wasu gungun mata da suka fita a karshe,,,</p><p> Sai tabi bayan su tasa wa kofar gidan mu sakata, ta yadda ba wanda zai kara shigowa muna, gida kuma daga wanan lokacin,</p><p> Hakan yasa muka dan samu daman zama da yan uwa na a wanan lokacin,,</p><p> A hankali natashi daga inda muke zaune da su hafsi na koma inda inna take zaune </p><p> Tana kallon mu cikin so da kaunar irin ta uwa da diyanta indan sun hadu,,,</p><p> A hankali na riko hanun inna na tare da wasu irin hawaye masu zafin fita, daga ido ,,,</p><p> Masu dacin sauraro a kunnuwar mai jin ta</p><p> Nadago fuskana da yai cab cab da hawaye, nadube ta,</p><p> Nace mata inna dan Allah ki yafe min duk abinda na aikata a bayan tafiya na,</p><p> Wanda duk iya kokarin da nayi inga cewa nadawo gida gurin ki lafiya Allah bai nufa ba,</p><p> Da sauri gaba dayan su da tunda na fara magana sukayi tsit suna sauraro na suka kai kallon su ga Aisha,</p><p> Wacce ke kwance saman gadon karfen inna tana barci da alamar duk zafi ya damay ta da sauro,</p><p> Na dan yi shiru na kasa ci gaba da maganar da nake yi </p><p> Saboda kunar da zuciya na take min don ban san koda wani ido zan kalli inna in fada mata cewa nayi aure ba,can,,,,</p><p> Batare da sanin su ba har ma da cikin wata biyar a cikin jikina,</p><p> Inna kuka kawai tasa ita ma don ko ban karasa zance, na ba tasan cewa ba magana mai dadi zan fada ba a wanan lokacin</p><p> Saboda yadda taga ina kuka, wi, wi,</p><p> Hafsi ce ta taso tazo inda nake gurfane a gaban inna,</p><p> ta dan rugumay ni tace min,</p><p> Fadima am, ko ni bari kuka haka kejiya ko,</p><p> Ganin ki ma dai, da mun kayi ya wadatar damu da komi, wallah,,,</p><p> Ke san duk mutum bai wuce kaddaranai,</p><p> Tunda Allah yyah nufa kinka dawo gida lahiya lumui , aimu,</p><p> Godiya dai mukai gare shi ,</p><p> Duk abinda ya hwru da keyya ba lahinki na ba fadima,</p><p> Ko kusa baki da laihi sam,cikin wagga harkan,</p><p> tunda bake tah kin ka tai da kanki ba, </p><p> kai ki na ankayi,</p><p> Ke, ga ko, laihi naga wadda, ta tai, da ke,,,</p><p> Wani sabon kuka nasa sosai alokacin da tafadi haka</p><p> Ke, ko ni am share hawayen ki kejiya ko,,</p><p> Mariya da ke gefe guda tana sauraron mu ta ce,</p><p> Shin wai mi, na na abin kuka ,</p><p> Ai kowa ma na da kin ka gani, shina da, abin hwdi har da tus,suwa,</p><p> Bagare, ki na ah hwrau ba,</p><p> Sai yanzu na gane nufin su da sauri na kalli inna nace mata ,,,</p><p> Wallah wallahi inna tunda nabar ki ban taba aikata zina ba a rayuwa ta kuma ban taba daukan abin wani ba,,</p><p> Da sauri suka kara kallo na cikin mamaki da ya baiyyana a fuskokin su, lokaci guda,</p><p> Wa,a,dda waga diya shin, </p><p> Inji hafsi,tana kallo na cikin tambaya da son karin bayani,</p><p> Da sauri na kalli inda Aisha take kwance abin ta,</p><p> Duk da kuka nakeyi, alokacin, saida, tambayar ta yasa nai murmushin karfin hali, </p><p> Don jin inda suka dosa da zancen</p><p> Nace wanan in na isa haihuwar ta ai zaku ce kila ina haukane, ko, </p><p> Yaushe nabar gida da har zan haifi wanan "yar</p><p>Aisha, Diyar wata abokiyar zaman mu ce, a saudiya, </p><p> Tabani ita ce, tun tana yar karama nake tare da ita shine dazan dawo tace in zo da ita kada zumun cin mu ya yanke,</p><p> Uwarta na saudiya ubanta kuma mutumin Sudan ne, ya dade da rasuwa ko,</p><p> Shiru dakin yayi kowa da abinda yake sakawa a cikin, zuciyar shi,</p><p> Shin ko ma minana anty fadima ,am hakuri na zamuyyi , kawai,</p><p> Tun da har Allah yamaido muna dake gida lahiya,</p><p> Shin mi rage kuma, </p><p>Duk uban daka magana shi tai shitayi shiyajiwo</p><p> Shi an nan,</p><p> Dauri da suka cewa saishe ki na ankayi hwa,</p><p> Ko yanzu da suka tururuwan tahowa inda ki ke da sunan sun taho maki barka da sauka,lahiya, walleh duk karya na sukai,</p><p> Da ijjiyan ga nau nagga sanda Tumba ka nuna ma Dije wagga diyan da kunka taho ita,</p><p> To, mi suka nuhi da hakan hafsi, ,</p><p> Hafsi tace Su,dai sunka sani ,wallah,</p><p> Duhuwar mutum mai kosai,</p><p> Ina jin su amma ban ce masu komai ba sai ma shirun da nayi kawai a lokacin </p><p> Ina nazarin ko yaya zasu fassara wanan cikin da ke a jiki na yanzu,</p><p> Saboda gashi da ga irin hali na mutanen kauye saboda gulma har suna daukar Aisha a matsayi diyata,</p><p> Yaushe har nabar garin da zan iya haihuwar kamar Aisha yar shekara kusan tara,</p><p> Shiru nayi kawai ban kara cewa komai daga hakan,</p><p> Wanan rana ta kasance mara misaltuwa a gareni don duk wani abu da nake yi tankar mafarki na ke ga shi,</p><p> Wai yau nice a a gaban mahaihaifiyata da yan uwa na kuma a kasata ta haihuwa,</p><p> Babu wani fargaba ko shakkun korar kare da akewa mutane saboda rashin galihu, in badon taimakon da nasamu ga sheriff ba,</p><p> Gabana ne yafadi dam saboda tunawa da nayi da zancen sheriff,</p><p> Tunda na iso sai yanzu na tuna da sheriff, </p><p> Saboda farin cikin da nayi na kasancewa ta a gida, tare da kowa nawa</p><p> Mun kusa raba dare muna hira da yan uwa na da mahaiyar mu,</p><p> Barci ya kaurace wa idanuwar mu dan murnan wanan ranan</p><p> Suna bani labarin abin da yafaru bayan tafiya ta</p><p> Dariya muka dinga kyale kyalawa,</p><p> Saida inna tai masu maganar cewa su bari in kwanta in huta saboda ina tare da gajiya a jikina , gobe ma ranace tunda ina garin,</p><p> Mariya ce ta gyara min inda zan kwanta wai saman gadon inna tare da Aisha,</p><p> Nasan cewa ba zanji dadin kwanciya hakana ba saboda ,karantar gadon ,</p><p> Don haka sai na dan wayance da cewa a,a zan kwanta a kasa, kusa da inna ta ne, yau,</p><p> Ke mariya kije ku kwanta keda Aisha kawai,</p><p> Wanan ranan kusa da mahaifiyata na kwanta inda ita da hafsi suka sani a tsakiyan su,,</p><p> Saboda mijin hafsi ya barta takwana gida yau don murna,</p><p> Haka mu ka gwamatsu dukkan mu cikin dan karamin dakin inna na laka,</p><p> Duk yadda nake a gajiye hakan bai bani damar yin barci ba, a wannan daren,</p><p> Sai juyi nakeyi saboda tunane da farin cikin yau nice a dakin inna kamar a farki,</p><p> Ban wani dade, da fara,barci ba naji anfara, kiraye kirayen sallar asuba </p><p> Saboda sabawar da nayi na zuwa yin sallah asuba a,massijid </p><p> Yasa nakasa komawa barci mikewa nayi tsam da ga kwanciyar da nayi da, niyar zuwa in dauro alwala,</p><p> Don inzo inyi nafila</p><p> Saina ga ashe har inna ta ta rigamu tashi,, saboda zaune naganta tana tasbihi,</p><p> Azuciyata nace Allah sarki inna ashe tana nan da wanan yawar ibadan nata, da nasani,</p><p> Koda na idar da salla ban bar lazimi ba har kusan karfe bakwai na safe,</p><p> sannan na mike kai tsaye na fita waje inda inna ta da hafsi ke kokarin dama koko da kuma zuba ruwa a cikin wani plask , don shan tea,</p><p> Ina kokarin zama in gaida inna da hafsi ne naji muryan inna ta na fadin fadima </p><p> Mi, da kin kahito, wuri yanzu </p><p> Dauri ki koma wanki, barci ai,,, ,</p><p> ke fa san cewa, kan ki ya na iya imiki, ciwo,</p><p> Nace wallahi inna naso in kara yin barci saidai na gan ku a waje kuna aiki ne,</p><p> Sai wani hamma yazo min nakarasa zancen cikin yin hamma,</p><p> Da sauri inna tace maza tashi tai zuwa daki ,ki samu wuri ki dan huta ke jji ya,,,</p><p> Ke san doguwar tahi na kin kayi, wallah ,</p><p> Hutuwa, dai ,ki ka bukata,</p><p> Ba,musu na juya dan gaskiya a gajiye nake dama,</p><p> A nutse na tashi na koma daki nadan samu guri gefe guda na dan kwanta,</p><p> Kafin wani lokaci sai barci, yadauke ni mai nauyi kuwa,</p><p> Kusan barcin minti talatin da biyar nayi, a cikin baracin, lokacin sai nadinga ji kamar ana kiran suna na a lokacin natashi zubar,</p><p> Kawu salihu ne tare da mai gari suka shigo har cikin gidan inna yi min barka da zuwa tare da wasu dattijan gari kusan su goma sha,</p><p> Daganin su kasan cewa tun, da suka tafi, masallaci wurin sallah asuba basu koma gida ba,,</p><p> A ho yar kulu,</p><p> Yar kulu bar kadai da,wagga,arzikin, ke ji,,</p><p> Ashe fadima andawo gida,</p><p> Tace, awo rankashi Allah sabbanani,,,</p><p> Allah yayi dawo war ta,</p><p> Sannu da arziki ke ji,</p><p>Wagga diya Allah yai mata arziki tunda ya, maido muna da ita gida lahiya,</p><p> Daidai lokacin nafito cikin wata doguwar rigar da na,zurawa jikina, </p><p> Cikin ladabi na durkusa har kasa ina gaishe su,</p><p> Kusan bakin su guda suna fadin ingwaiyya, agaisheki ke ji,</p><p> Barka da arziki ke ji,</p><p>Fadima ho, ke taho lahiya, yaya kin ka baro su can,</p><p> Ina ta karbawa ina fadin lafiya kalau, na samay ku lafiya ,</p><p> Wanan ya leko ya ce mi fadima ho,</p><p> Maigari yace min fadima a she saudiya an ka tai da ke,,</p><p> Saida baya munka jiya duk mun shiga cikin, wani hali da kin ka bata,</p><p> Allah da annabi nai sunyi gaskiya wallah ,</p><p> Komi kabar ma Allah insha Allahu kana ganin sakayyanai,</p><p> Ke ga dauri duk mun ta da hankullan mu cewa sai, she kina Gajiye ttayi,</p><p> Saiddah bayana mun,kajiya cewa kina saudiya gurin Alhj Ayuba da kin ka ba sako yakawo ma tsuhuwan ki,</p><p> Sannu ke ji sannu da shan wagga duniyar,</p><p> Yar kulu ho, agaishekki, barka da wanga arziki ke, ji, walleh anyi arziki kan, inji sauran yan tawagar hakimi suke fadan hakana,</p><p> Duk maganar da sukeyi ina gefe na tsuguna nadukar da kaina kasa cikin ladabi da biyyaya,</p><p> Ba su dauki wani dogon lokaci ba sukai muna sallama suka tafi,</p><p> Daki na shiga da sauri na bude wani jakkan nafiddo masu da tasbaha da yan turare masu kamshi,</p><p> Sai jallabiyar maza mai kyau na ba maigari, </p><p> Mariya ce ta,sheka da gudu ta kai masu saboda har sun dayi nisa kadan da gidan mu ko,</p><p> Abin karin kumallon safe aka dinga aiko min da shi daga gidan jen yan uwa da abokan arzikin innar mu,</p><p> Kamar su,masa koko da kosai, sai tuwon shimkafa da aka lema miya aciki, ,</p><p> </p><p> Wata sabuwa zance kuma da ya bullo min shine,</p><p> Duk da inna ta bata gane cewa ina da ciki a jikina ba amma sai da Tumba makwabciyar mu,ta gane cewa akwai ciki a jikina hakan</p><p> Saboda tsabar gulma ko yaushe Tumba tana gidan mu zaune wai tana taya mu karban yan zuwa min barka da dawo wa,</p><p> Mai mako ta fadawa inna ta kai tsaye,</p><p> Ai sai kawai ta wuce don gulma gidan Dijen yabo,</p><p> A,a Tumba ta at, tahe yanzu da wagga uban ranan,</p><p> Nita ke dai Dije, am</p><p>Kudin adashen ki na nattaho in kawo nauwa zubin,</p><p> Aiko sau,biyu ni, aika inda kike, ankace min wai ketahi unguwa shin,</p><p> Bari kedai Dije ina can inda wagga bakuwa ta makkah ina kare mata, kallon mamaki,</p><p> Mamaki shin , mi, ar na mamaki kuma,</p><p> Shin ina Dije ta ce gani tumba am,</p><p> Ke taba jin inda "ya mace, ta tai yawon duniya ta dawo gida lahiya lumi,</p><p> Shin , a, a diya ttah,, taka tahiya tsawon wagga shekaru ,ace wai tadowo gida lahiya </p><p> Walleh karyata, </p><p> ke ga wata yar diya dattataho da ita yar diyan larabawa shi,,</p><p> Sai kuma ta dan yi shiru ta fidda goron da ta daure a gefen zani ta tadan balla ta tauna ,</p><p> Sai ta dan matso kusa da inda Dije take zaune ta na gyaran ganyen soborodo,</p><p> Ta dan tausa, murya ciki ciki tace wai ko kesan fadima cikina aggare ta,</p><p> Ke tumba bari wagga maganar, dan Allah dai wane irin ciki kuma,</p><p> Don ke ga tayi dan magurjin jiki, tai kyau,</p><p> Babu karya cikin magana na ta, Dije am,,,</p><p> Uwar diyan ma bata san da wagga zancen ba da ni ka hwada maki,</p><p> Don ko da su shatu,, mai kitso sunka taho taron ta</p><p> suna cewa wai fadima tayi kyau, sai cewa uwan tayi wai ai shekarun girman ta na ,</p><p> take yanzu shinassa, tai kyau haka,</p><p> Dije tace to ke Tumba shin,a,a kinka gane cewa cikina a,ggare ta,</p><p> Walleh Tumba ki bar boni (bala,i)shi kwana, in ba so kikai a kan maki ba,</p><p>(akama ki ba)</p><p> Yau ko ga Dije, inji Tumba,</p><p> Sottdiya,i gwalmadiya,i, shin ni na kuma ban san ciki ba Dije am,</p><p> Don gudun wagga irin tuhum yassa saida ni binkcika da kyau,</p><p> Sanda anka kawo mata tuwo ashe anzuba man shanu a cikine,</p><p> Saida duk ta amaye dan abin da ta ci, </p><p> Ni da kaina nibbata dan goro ta tamna,</p><p> Salati Dije ta sa tace tabbasa tumba ke san ciki wallah,</p><p> Yanzu waga diya dama yawon balaguro na takai a can kasa mai tsarki,</p><p> Kedai Dije am hwadi, yanzu zuwa nikai, duk yan tarkacen tsaraba da anka bani maisuwa nikai,</p><p> Don walleh ban son kayan zina</p><p> </p><p> Wanan maganar ta Tumba itace ta bazu cikin kauyen mu cewa yawon bin maza na yi a saudiya nadawo da cikin shege har da yar diyar shege na zo,</p><p> Hafsi ta far jin wanan labarin gurin mijinta ,</p><p> Bai boye mata komai da ake fadi gamay da ni ba a cikin gari,</p><p> Da kukan ta, wi,wi hafsi tashigo muna gida musalin karfe sha biyu da,rabi na rana,</p><p> Ina zaune tare da inna ina bata labarin zamana a kano, mariya ta na bakin murhun tana ma inna girki,</p><p> Ganin da mukai mata cikin tashin hankali yasa mu fitowa daki da sauri gaba dayan mu </p><p> Cikin rikicewa muke tambayar ta ko lafiya duk a rude muke,</p><p> Cikin kuka take nuna ni da, dan yatsarta tace shin fadimaa wagga batu da mukajiya a gari shin gaskiya na ko ,</p><p> Inna ta ce mi kun ka jiya shin,</p><p> Fadima wai da ciki tta taho, kuma wai wagga diyan ta,tatah,,,,tana mai nuna Aisha dake zaune tana ta wasa da kasa gefe guda,</p><p> Kafin inna tai magana mariya ta cabe zancen tace,</p><p> Yau ,ko kuji min wani zance </p><p> A,a duniya na ta rugumo ba ciki ta,taho dashi ba,</p><p> Banyi magana ba daki na koma kawai na zauna sai naji wasu hawaye na zubu min masu zafi, </p><p> Ba komai yasani hawaye ba sai nasan </p><p> Saboda nasan cewa cikin jikina zai sheganta ga bakin mutane gari ke nan,</p><p> Hafsi tacigaba da fadin fadima mi da kin, kai muna haka shin</p><p> Ke san halin mutane garin ga sarai da sa, ido mi da zaki taho da ciki ,cikin wagga gari,</p><p> Dakin suka shigo su uku lokaci guda , ganin da sukai min ina kuka yasa su yin kukan su ma alokacin,</p><p> Inna ce tai karfin hali tace min,</p><p> Shin fadima da gaskiya na ciki na aggare ki,</p><p> Ban iya bata ansa ba sai kukan da nakara sawa wi,wi,</p><p> Shin inna ko dai mi na,na tun da har Allah yasa ta dawo gida ai sai ai hakkuri da shiya ko,,</p><p> To mi da baki hwda muna ba tunda kin ka taho,</p><p> Ai ke ga sai musan nayi ko </p><p>A hankali nadaga kaina nakalli hafsi na ce mata hafsi nifa ba shige nayi ba,</p><p> Cikina yana da uban sa na halak,,</p><p> Ke jiya ko cikina kuwa da gaskiya,</p><p> Wagga diya ke kashe mu wallah</p><p> Mi za mu wa cikin garin ga shim,</p><p> Daga haka ban kara cewa komai ba sai nai shiru,</p><p> Maganar hafsi na kona min rai,</p><p> Mariya ta ce oho shina suke ta,dawo muna da duk wani tsaraba da anka ba su,</p><p> Oho sunyi wa kansu, don su ka shirin jin kunya wallah,</p><p> Shigowar Abdull yasa su yin shiru, ga zan cen su,</p><p> Saida ya zauna yake cewa mariya wai yanzu ya gama fada da wasu yara sun ce mai yar shi ta dawo yawon karuwanci saudiya da yar shegiya da cikin shege,,,</p><p> Halan mi kace masu in ji mariya,</p><p> Hafsi ta tare zance da cewa mi zaicewa kuwa tunda ba karyana sunka hwadi ba maganar su dutse na,</p><p> Shim mika damunki na hafsi,,,,,</p><p> Da wani zamuji da zancen ki ko da ta mutane shin,</p><p> Inji innar mu tace wa hafsi hakana,</p><p> Fushi tayi batare da tai muna sallama ba tabar gidan cikin fushi ,,,,</p><p> Kallon mamaki duk muka bita da shi,</p><p> Mariya tace yanzu haka muna hukan gidan su na sun ka zugo ta,</p><p> Ita ko ta taho tana ma mutare bori,</p><p><br /></p><p> 🐎 ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI* ✈✈✈ </p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 8⃣0⃣</p><p> BY </p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,,</p><p> </p><p><br /></p><p>Tunda Amal tagane cewa, fadima bata gidan hankalinta yafara tashi,</p><p> Gidan Salimat suka fara zuwa don su bincika ko tana can,</p><p> Sai Salimat ta nuna masu cewa ai itama jin da tayi shiru bata ji motsin su sun laiko ta ba yasa take zancen zuwa gurin su, don ta bincika,</p><p> Hankalin su duk ya daga, saboda rashin sanin halinda fadima take ciki,</p><p> Maman Omar ta nuna cewa fadima ta wuce da Aisha batare da sanin ta ba,</p><p> Don haka Salim da kan shi ya tafi garin makkah don ya diba ko mun tafi can ne,</p><p> Saida duk inda yasan cewa fadima na zuwa yatafi don ya diba ,</p><p> Haka yadawo gida madina jiki ba kwari yai masu bayanin cewa bai samu koda labarin wanda zai ce ya ganta ba,</p><p> Hankalin Ummi duk yatashi sosai da jin cewa nabatane,</p><p> Aziza gari na waye ta fito falo don tayi break fast takuma yi abinda ta niyar yi a zuciyar ta,</p><p> Takai minti arba,in zaune gurin bata ji koda motsi na bane,</p><p> Tashi tayi zuwa ciki don ta ganewa idon ta abinda ke faruwa da ni har ya hana ni fitowa yin break tare da kowa,</p><p> Ganin da Amal tayi kamar tana cikin wani uzuri yasa hankalin amal ya koma wuein ta,</p><p> Aziza tana zuwa ta murda kofan dakin da nake ciki sai tagan shi a bude </p><p> Kutsa kai tayi ciki batare da fargaban komai ba </p><p> Saidai yadda taga dakin tsab alamar ban kwana a cikin sa, ba yasa ta zargin ba,a gidan na kwana ba,</p><p> Fitowa tayi da mamaki ta nufi gurin mama Umar tana tambayar ta ko ina fadima, ta, tafi, yau,</p><p> Maman umar tace ita ma dai bata gan ta ba, tun da gari ya waye,,</p><p> Amal na biye da ita duk wanan sintirin da take yi kamar mahaukaciya,</p><p> Wanan abin yasa suka gane cewa itama din bata san inda na nufa ba,</p><p> Sai dai suna zargin cewa akwai nasabar batana da ita,</p><p> Amal tana mamaki taya zan bar gida batare da sanin ta ko kuma salimat, </p><p> Ga sanin da taimin duk abinda zan yi sai na fada mata saboda daukar ta da nakeyi kamar elder sister di ta ,</p><p> Salim ko da yaushe yana shiga cikin massalaci koda Allah zai sa ya ganni a can,</p><p> Tun tafiya na da kwana biyu aziza ta shirya tabar gari cikin bacin rai don rashin samun aiwatar da nufin ta a kan ciki jiki na,</p><p><br /></p><p> Rashin sanin abin da zasu fada wa sheriff indan yaji cewa na bata, ummi tace kada kowa ya fada mai su bari ya karasa aikin da ya kai shi, ai,duk inda yake ai zai dawo gida,</p><p> Tuna nen da ummi ke yawan yi, a gamay da ni,</p><p> ya nuna mata cewa, sheriff ne kawai zai san inda na tafi,</p><p> Saboda shi yasan kasar saudiya da kyau fiye da su Salim,</p><p> Don haka suyi shiru da bakin su, har yadawo,</p><p> Za ya gane duk inda nake, kuma tace masu ita zuciyar ta yana bata cewa ina gurin mai kyau ba wai mugu hannu kamar yadda su ke tuhuma ba,</p><p><br /></p><p> Duk wani abinda Sheriff Ahmad keyi hankali sa na gurin iyalin shi musan man fadima wace tun kusan zuwan shi kasar spain da kwana biyu rabon da suyi waya da ita,</p><p> Abin yana damun shi so sai a ran shi </p><p> Sai yake ganin cewa fushi fadima ,takeyi da shi, saboda ya wuce batare da wani cikakken bayani ba, </p><p> Shima dai tafiyan haka tazo mai ba shiri daga Riyadh tafiyan takama shi sai suka wuce daga can,</p><p> Amal ce, yakira yau don ya tan baye ta, yaji cewa ko lafiya fadima take saboda baya samun wayar ta,a</p><p> Sai dai Amal din ta boye mai zancen tafiyar fadima,</p><p> Sai ce mai tayi wayar fadima ya ,bata </p><p> Kuma fadimar bata zama a gida sosai saboda tana zirga zirgan hada jarabawar ta,</p><p> Bawai sheriff ya gamsu da bayanin Amal din bane, kawai dai baida yadda zaiyi ne, saboda nisan da,yayi da saudiya,</p><p> </p><p> Yau a gajiye yadawo gida saidai kuma lokacin tashi daga meeting din da suka shiga bai yi ba, saidai kawai ya kama jin ba dadi a ransa, don haka yafito abin shi zuwa masaukin shi,</p><p> Yadai dawo ne kawai saboda yau sam baya jin dadin jikin shi,</p><p> Yana shigowa masaukin shi ya aje yar briefcase din shi gefe kawai ya haye kujera ko takalma ya kasa cire, wa,</p><p> Nan waje barci ya kwashe shi kawai batare da wani bata lokaci ba,</p><p> Duk da barci bai yi nisa ba amma sai wani mafarki mai firgitarwa ya sa,shi farkawa a firgice yana mai yin salati da istigfar, </p><p> Gaban shi ne yakama faduwa saboda duk second sai yatuna da mafarkin da yayi,</p><p> Fadima ce yagani zaune a tsakar daji saman wani dutse, gurin duk ciyawa ne kore shar,</p><p> Saidai tana dago kai sai yaga duk cikin damuwa take da fargaba, ga hawaye jagab a fuskarta,</p><p> Wanan mafarkin ya tsaya mai a zuciyar shi, </p><p> Sai tunane yake yi anya kuwa, ba wani hali Fatima take ciki ba, </p><p> Tunda yasan cewa ta na cikin barazanar Aziza a ko wani lokaci,</p><p> Duk yadda,yaso mafarki yafita mai a rai ya kasa, duk abinda yake yi ,</p><p> Wanan mafarkin da yayi yake tunawa, abin har yana,son zama mai kamar fever,</p><p> A dadafe gari yawaye mai saboda duk ya matsu ya zo saudiya, hankalin shi a tashe yake,</p><p> Jirgin farko da ya sauka a saudiya daga Spain dashi a cikin sa,</p><p> Bai ko tsaya zuwa gidan shi na Riyadh ba,</p><p> Shatar mota ya dauka zuwa madina, shi kadai, ne a cikin, motar,</p><p> duk gudun da driver ke yi gani yake yi kamar baya gudu,</p><p> Karfe biyun rana suna cikin garin madina, direct gida ya dosa,</p><p> Duk wanda ke gidan saida yai mamakin ganin sheriff </p><p> Saboda ba su san da zuwan shi ba, a wanan ranar,</p><p> Gaba dayan su, duk sun shiga cikin rudanin ganin shi cikin wanan lokacin,</p><p> Kowa da ke gidan, yazo yi mai sannu da zuwa a daidai wanan lokacin,</p><p> Karba masu kawai yake yi yana dibar hanyar da zaiga na fitowan fadima,</p><p> Abinci mama umar ta gabatar mai a saman dinning table,</p><p> Kasa daurewa ya yi yace ma Amal wace ke zaune gefe guda duk a takure, </p><p> Fadima fa,</p><p> Amal kallo ta kaiwa ummi, don ta bada ansa, tambayar da yai mata,</p><p> Yadda yaga Amal na nunawa yasa shi mikewa tsaye a lokacin,</p><p> Kamar may rada yace may yafaru da Fatima Amal ,</p><p> A hankali Amal tace ba komai, yayan mu, kawai dai sai kuma tai shiru ta dukar da kan ta kasa,</p><p> Muryan ummi ce yaji daga bayan shi tana fadin ka kwanatar da hankalinka ka ci abinci tukun kafin ai maka bayanin komai,</p><p> Da sauri ya juya gurin da Ummi take tsaye cikin wani irin murya yace dan Allah Ummi ku fada min abinda ke faruwa da Fatima,</p><p> Ummi tace kayi hakkuri ka zauna insha Allah komai zai zo da sauki,ai</p><p> Girgiza kan shi yayi yace ban fahinta ba ummi, har yanzu ina fatimar ta ke ne wai,</p><p> Muryam salim yaji ta bayan shi yana cewa wallahi ta bata muna,</p><p> Da sauri ya juya gurin Salim ya riko hannu shi yace What,</p><p> Ta bata kamar wata dabba can, tun yaushe ta bata da baza,a fada min ba,</p><p> Har saida nagani da ido na,</p><p> Shiru duk sukayi, </p><p> Ba abinda yake nanatawa a bakin shi sai innalillahi wa,ina alahim raj,un, kawai yake ta fadi</p><p> Dan dir dir ya yi na rashin sanin abin yi sai kuma yasamu guri ya zauna yadafe kan shi da hannayen shi,</p><p> Nanda nan idon shi suka kada sukayi jawur, kamar garwashin wuta,</p><p> Duk suna tsaye tsarma tsarma suna kallon yadda ran yan maza ya baci yau,</p><p> Salim ya kalla yace mai kai min bayanin komai pls </p><p> Don insan ta inda zan fara bullowa zancen,</p><p> Salim ya fada mai dan abinda yasani gamay da batar nawa,</p><p> Amal ta karbe zance da yi mai bayanin duk abinda ya faru tun wucewar shi, sai kuma maman umar da ta bada nata bayanin ita ma,</p><p> Wani irin mugun kallo yai masu a lokacin cikin jin haushi da ta kaicin su,</p><p> Bai ce komai ba yasa kai kawai yabar gidan, cikin zafin rai,</p><p> Salim na ganin haka ya mara mai baya suka fita tare kusan lokaci guda,</p><p> Da farko gidan Salimat suka, nufa </p><p> Ita madai bayanin duk yadda fadima ta firgita da Aziza tai masu, amma ta kare zancen da cewa sun yi da ita cewa washegari zata dawo gidan ta ta zauna da ita har sheriff yadawo,</p><p> Sai kawai taji shiru kuma daga baya sai ga Amal ta bugo mata tana fada mata cewa fadima bata gida,</p><p> Shiru yayi nadan wani lokaci yana nazarin zancen ta,</p><p> Daga gidan Salimat gurin ja,mian tsaro ya nufa kai tsaye,</p><p> Batare da bata lokaci ba suka fara aiwatar da aiyukan su,</p><p> Dawowar sheriff da kwana daya su Salimat suka bar kasar saudiya ita da mijin ta,</p><p> Saboda ta kare karatun ta, dama karatu ta, tafiyi ga shi Allah ya nufa har ta kare,</p><p> A ranan bai kwana a garin madina ba Makkah ya wuce kai tsaye,</p><p> </p><p> Washegari duk wani bincike da zaiyi yayi saidai babu labarina sam,</p><p> Babu ma wanda yace mai yagan,ni a garin, makkah </p><p> Hankalin sheriff yakara tashi sosai don ya rasa ko ta ina zai fara binciken,</p><p> Shin ta Aziza ko ta Alin, zai fara, wata zuciya tace mai duk kan su,</p><p> A bokin shi doctor kamal ne ya bashi shawaran su fara bincike akan Alin tukun,</p><p> Duk iya binciken su sungano cewa Alin baya zuwa saudiya har yanzu tun lokacin da yai yunkurin sace ni,</p><p> Sai suka dawo kan Aziza, kuma,</p><p> </p><p> A Dubai ya samayta inda ya buda mata wuta akan cewa lalai sai tayi mai bayani akan abinda taje yi saudiya bayan tasan cewa baya kasan a lokacin,</p><p> A lokacin Aziza ta dauki zancen da wasa so sai dan bude baki tayi tace mai </p><p> Amma dai tana da right din zuwa duk lokacin da taga dama ko,</p><p> Ko saboda yayi auren yar kwaila zai zo ya damay ta</p><p> To bari ta fada mai indai akan fadima zai zo ya tayar mata da hankali sai tayi maganin su shi da ita,</p><p> Kafin ta fadi wani kalma wani irin wawan mari ne ya sauka a fuskan ta saida ta gigice,</p><p> Ya shake mata wuya da hannu guda ya ce ki fada min ina kika kai diyar mutane ,aziza,</p><p> Fadima ta bace a saudiya ba wanda yasan inda ta tafi,</p><p> Ido ta waro waje don jin kalamin shi</p><p> Ta ce ta bace fa kace ya dan sasauta shakan da yai mata ya ce kwarai kuma ke muke tuhuma da bacewar ta,</p><p> Nan ya koro mata duk abinda Amal da maman umar suka gani a gamay da ita, lokacin da tasa fadima a gaba,</p><p> Ta yi mamakin jin cewa a wanan lokacin da tai ta sintiri a kofar fadima a ganta,</p><p> Harda yunkuri zuba Meagan da zai zubar da cikin fadima datayi,.</p><p> Cikin sanyi murya tace wallahi ba ita ce ta sace fadima ba san da tayi cewa gurin hukuma za a kaita kara </p><p> Indan kuma anyi karanta kasar Dubai zasu dawo da ita kasan haihuwar ta ne ba zasu kara barin ta shiga masu kasa ba,</p><p> Tai wani yunkuri don ta mike shiya sanya shi dan ne mata kafa da tasa</p><p> Yar kara ta saki ta ta dibe shi da sauri, sai taga ya canza mata ba Ahmad din da tasani bane yau,</p><p> Muryanta na rawa tace wallahi bani na sa aka sace taba,</p><p> Ni yunkurin zubar da cikin da ta yaudare ni ne kawai nayi,</p><p> Wani irin mugun shaka ya kara kai mata ya saida idon ta yafito waje don azaba,</p><p> Tunda take ba,a taba gwada mata azaba irin wanan ba,</p><p> Duk yadda taso ta motsa ko ta kwace kanta ta kasa </p><p> Wani zogi da radadi ya ratsata, </p><p> Kallon ta yakeyi yana nazarin irin rudewar da yagani a idon ta,</p><p> Can tace wallahi Ahmad ka yarda da ni ban san komai a gamay da batar fadima,</p><p> Cikin wani irin zafin rai ya sake ta yana huci yace barin fada maki aziza muddin bincike ya nuna cewa da hannu ki a cikin wanan zancen wallahi bazan raga maki ba ko kadan,</p><p> Bai kara koda second ba ya juya yabar gidan cikin fushi,</p><p> Nan Aziza ta rushe da kuka mai tsuma zuciya tayi da tasani ga shirin da tayi niyar ai,watar wa a kan fadima,</p><p> Wani abokin su ne ya basu shawaran su koma saudiya su kara bincike duk yadda akayi zaau gane inda fadima take,</p><p> Su Amal sun rasa gane kan dan uwan su tun da wanan abin yafaru,</p><p> Ya koma masu kamar wani mahaukacin zaki, sai jami,an tsaro ke masu sintiri a gida,</p><p> Wanan lokacin duk wqni wanda ke tare da shi yasan irin kaunar da son da yakewa fadima,</p><p> A nacikin wanan halin aka bugo mai waya daga Nigeria cewa jikin hjy tsohuwa ya tashi,</p><p> Gabadayan su suka zo Nigeria dan diba jikin nata,</p><p> Kwanan biyu ya koma saudiya don ci gaba da bincike,</p><p> Nasir abokin doctor kamal ma aikacin yan sandan ciki ya basu shawaran zuwa ma aikatar tafiye tafiye don adiba masu,</p><p> Sheriff yace yasan cewa fadima bazata iya kai kanta gida ba saboda tun tana yar karama akabar Nigeria da ita,</p><p> Don haka da wuya ta iya komawa garin su, </p><p> Ganin cewa Nasir din ya nace ne yasa su zuwa maaikatar tafiye tafiye na kasar saudiya,</p><p> Sunayen wa,yanda sukayi tafiya a wanan date din zuwa yanzu aka fitar da photos din su ,</p><p> A madina suka fara bincike basuyi nasara ba sai suka tafi jidda,</p><p> Ganin ko a jidda ba suyi nasara ba yasa yace masu su bari kawai don shi dama ya san ceqa ba zan iya komawa gida ba,</p><p> Doctor kamal yace sam sai sun tafi Riyadh sun karasa bincikawa,</p><p> Binciken farko ya nuna masu photo nadana Aisha a ranan da mukabar gida ranan nabar kasar saudiya zuwa kasata ta haihuwa Nigerian,</p><p><br /></p><p> 🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 8⃣3⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p> </p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,,</p><p><br /></p><p> </p><p> Bincike ya nuna cewa Fatima ta bar kasar saudiya, tun ranar da tabar gida </p><p> Kuma jirgin Nigeria ta bi zuwa gida Nigeria,</p><p> Amma tare da taimakon wata mata yar kasar Nigeria din,</p><p> Duk iya binciken da za,ayi anyi don a gano ko, da wace, ce fadima ta zo airport, a lokacin da zata wuce Nigeria amma ba,a gane ba,</p><p> Haka suka hakkura su ka koma makka cikin bacin rai,</p><p> Zaune yake saman kujera a falon shi, laptop din shi ke gaban shi yana searching din wasu kayan aiki da su,ke bukata a company su,,,</p><p> Saidai gaskiya a zahiri ne yake aikin a cikin system din shi,</p><p> A badili kuwa tunanen fadima ne fam a cikin zuciyar shi,</p><p> Yaso ace yana a Nigeria daidai wanan lokacin,</p><p> Amma hakan bai samu ba saboda tsaida shi da doctor kamal da Khalid sukayi akan cewa yadan dakata masu har su dan samu leave,</p><p> Ture system din yayi gefe guda, ya koma bayan kujerar ya jingina jikin shi akai, hannayen shi na rike da habar shi,</p><p> Wani irin iska mai fushi ya furzar daga bakin shi,</p><p> Yakara dan rintse idon shi , fadimar ce ke mai gizo a zuciyar shi,</p><p> Abuna farko da ya tuna dashi shine farkon ganin da yafara yi mata,. </p><p> Tana wasa da ruwa a cikin gidan shi na birnin Riyadh,</p><p> Sai kuma lokacin da ta tsinci wallet, din,shi a cikin shagon shi da suke gyara,</p><p> Yadan shafo sumar kan shi a hankali yakara furzar da iska,</p><p> Kuka takeyi sosai bayan irin wulakancin da Nafisat tai ma lokacin jiyar Ummi,</p><p> Mikewa yayi buzur daga inda yake zaune, ji yayi kamar a lokacin take kuka yake ji,</p><p> A hankali ya furta sunan ta yace fadima Y,? Y ? Why d u leave me?, fadima,</p><p> May yasa zaki tafi gida ke ka dai duk tsawon wanan lokacin da kika dauka baki gida,</p><p> Kawai sai ga yan maza yau hawaye na zubuwa daga cikin idon shi,</p><p> Ta dalilin tunawa da irin wahalal da yar karamar yarinya kamar fadima tayi a duniya,</p><p> Gashi yau ta koma gida tare da lalurar ciki a jikinta da kuma bacin ran rashin mutuncin da Aziza tai mata,</p><p> Kamar mai tuna nen wani abu da sauri ya haura zuwa sama bed room din shi ya bude cikin sauri,</p><p> Yana shiga ya nufi bayan wani da side drower dake gefe gudan dakin,</p><p> Yajawo shi a hankali wani drower ne yadan bullo bayan bangon dakin </p><p> Da alamar a manne yake jikin bango wanda ba kowane yasan da wanan drower, a gurin,</p><p> Wa su yan lambobi ya dan danna a jikin bangon sai wurin ya bude,</p><p> Yana budewa wasu irin gwala gwalai ne na mata masu matukar tsada da kuma kyaun gani,</p><p> Da guda guda yadinga daga su ya na dibawa , ya na maida su, inda suke cikin dan kit din su,</p><p> Saida ya gama ganin su tsab yakuma gamsu da irin kyaun su,</p><p> Sai yai wani irin ajiyar zuciya kawai,</p><p> Saman gadon shi ya koma yadan kwanta rigingine yana kallon rufin dakin </p><p> Daganin shi kasan cewa baya cikin hayacin sa,</p><p> Saboda harda wani dan kasunba ya aje a fuskan shi a kwanakin nan,</p><p> Wayar shi da ke gefen shi, ya jawo ,, yadinga bidan wasu lanbo bi,. </p><p> Bayan kiran da ya dan nawa dayan layin kamar second guda sai dayan bangare a kadauki kiran nashi,</p><p> Sallama tafara yi tare da gaisuwa duk a cikin lokaci guda,</p><p> Cikin larabci yake magana da matar mai suna Ma,issha,, </p><p> Yai mata bayanin cewa yana son ta shiga shagunar da ke cikin Garin da take masu kayan kware da kyau da tsada ,ta sayo mai kaloli masu kyau wanda zai yi pitting din mace mai chucuklet colour</p><p> Matar tace mai ba matsala yabata kwana biyu,</p><p> Yai dan ajiyar zuciya gami da lumshe idon shi, </p><p> Ya dan furta kadan yace fadima dole inyi duk wani abinda zai wanke ni da ga kowace irin zargi daga gare ki har ma da saurar yan uwan ki,</p><p> Haka,dai ya koma kamar wani ta ba be a wanan lokacin,</p><p> Allah ya taimaki sheriff Ahmad a wanan lokacin saboda ,duk wani process da yake yi a kan Company nin su yasamu karbuwa, so sai a idon duniya,</p><p> Hakan yasa Abu Abdallah yai mai kyauta ta musan man akan wanan gaga rumin cigaba da suka samu acikin wa yan nan shekarun da suka fara sana,a da Sheriff Ahmad,</p><p> Ashe wanan tafiyar da yayi har fadima tabar kasar saudiya saboda farautar rayuwar ta da Aziza ke yi mata,</p><p> Sheriff yasa hannu jari a wasu kamfuna, na Abu Abdallah,</p><p> Hakan ya janyo masa samun riba mai girma a ajiye ,a bankin kasar Dubai, al,amarin da cikin dan kankanin lokaci yasa shi bunkasa,</p><p> Hakan yasa yakara dadewa a she a wanan lokacin don yaga cewa komai ya kammala kafin yadawo saudiya </p><p> Saboda yaba son yafita ya shiga don ganin cewa shima ya kafa nasa company na,urar sadarwa a kasahen bakaken fata,</p><p> Ga damar tasamu gare shi don komai da yake bukata yanzu yasa mu </p><p> Sai gashi kuma wani fanni da yake gani na farin cikin sa ya gushe masa a lokaci daya,</p><p> Yaso ace wanan labarin da yasa mu na kammaluwar company sa fadima ta kasar saudiya a,yi gagarumin walima ,</p><p> Sai gashi komai ya tsaya mai cikin lokaci guda,</p><p> Duk yadda Almustapha yaso su ci gabada aiwatar da aiyukan su hakan bai samu ba saboda yarasa gane kan shugaban nashi sam,</p><p> Don haka dole yagaji ya kyale shi, har yaga farincikin sheriff din</p><p> Jin labarin cewa da akayi natafi kasar Nigeria yasa suka ga dan sasauci ga sheriffudeen nasu,</p><p> Yau ma kamar kullun Sheriff ne ke jar motar da kan shi, zuwa </p><p> Haram Saboda hakan da bi,ar sa ce dama, indai har yana a cikin gari duk ranar jumma,a ,</p><p> A massallaci mai girma yake yini sai dare yake dawo wa gida bayan ya idar da sallah isha,i</p><p> Zaune yake inda yasaba zama don yafi zama a kofar Sayidina umar A,s,w,,,</p><p> Yana dawo wa daga dawa fi sai yadan fito waje don yadan kewaya,</p><p> Wata yar karamar yatinya ce yagani yar takari ana ta faman yin artabu da ita da wasu mazan larabawa </p><p> Sungane cewa yariyar ba nakassa,sa bace dabara ce kawai ta neman kudi yasa ta daure hannu ta baya tankar wata musaka ,</p><p> Sun kewaye ta sai dangwarar ta sukeyi suna mata ihu </p><p> Yariyar nata famar kuka a tsakiyar su, tausayi taba sheriff </p><p> Bai san lokacin da ya je gurin yadinga ba wa mutanen hakkuri ba </p><p> Saboda ganinta yasa ya tuna da fadima a lokacin da take irin wanan harkan ta yawon bara don naimar wa hjy abin duniya,</p><p> Sai gashi duk wahalar da hjy tasa diyan mutane yi, an wayi gari daga karshe komai bata tsira da shi ba,</p><p> A wahalce ta koma gida da dinbin ciwon zuciyar da takwasa a sanadiyar damfar ta da akayi kashi kashi akasar saudiyar,</p><p> Tausayin yariyar ya kara kama sheriff din yakara kutsawa cikin jama,ar ya dinga ba su hakkuri</p><p> Kallon da sukai mai suka gane, cewa bawai tare da ita yake ba </p><p> Balle ya yaudare su iya kadai kila don suna launin fata guda ne yake son ceton ta,</p><p> Hakuri sukayi suka kyale yarinyar kowa ya watse kudi ya ciro daga aljihun shi yamika mata yace ta kaiwa shugaban ta,</p><p> Yatafi yin abinda yafito da shi daga cikin massalaci ran shi a bace </p><p> Yana tir da Allah waddai da masu dauko yan hara kanani hakan nan zuwa bautar wa da sunan wai neman kudi,</p><p> Arziki idan Allah ya nufe ka dayinta koda a cikin ramin kura kake sai kayi shi,</p><p> Har dare sheriff na cikin massallaci yana rokon Allah sauki da kuma yiwa fadima fatar sauka lafiya</p><p> Yana mai rokon Allah da yaba su zuria, mai albarka,</p><p> A hanyar shi ta komawa gida ne daddare ya dinga ganin matan takari a gefen titi suna boye boye wai suna gudun yan bagaladi su gansu, su kama su,</p><p> Kowace da kayar saidawa a gefenta wasu kuma sun rike a hannu suna nunawa mutane masu wucewa,</p><p> Ya girgiza kanshi cikin takaici, ya natir da Allah waddai da masu irin wanan halin kwadan,,,</p><p> Koda yadawo gida duk a gajiye yake saboda tun safe da ya karya bai kara cin komai a yinin yau ba,</p><p> Sako yasamu daga doctor kamal cewa su shirya zuwa wani sati sutafi Nigeria </p><p> Ba karamin dadin hakan yaji ba don dama duk hakkurin shi yaso karewa ga jiran su,</p><p> Tundaga wanan ranar ya, fara shirin tafiya Nigeria,</p><p> Shirin da bakowa yasan irin tanadin da yayi mata ba,</p><p> Sai dai abinda ke damun sheriff a zuciyar shi ita ce </p><p> Shin a Nigeria a ina ne zai je nemar fadima, </p><p> Sanin dayi cewa kida a cikin garin kano take abu ne mai wuya kafin yagane ta,</p><p> Tau yanzu shin ya ya zai yi, waye ya kamata ya fara tambayar inda zai zakulo Fatima a cikin Nigeria,</p><p> Maman umar ce ta fado mai a rai don haka washe gari itace yafara tambayar ko tasan garin da fadima take a Nigeria,</p><p> Tace wallahi duk zaman su da fadima bata taba sani ko yar wani gari bace,</p><p> Tace ai ita ta dauka cewa ko yar garin kano ce ita,</p><p> Jin dayayi cewa bazai gane komai a gurin ta ba yasa shi sallamar ta,</p><p> Tunane yake tayi to yanzu gurin waya kamata ya binciki labarinta,</p><p> Duk wani gurin da yakamata yatafi har gurin hjy laila yatafi ,</p><p> Itama dai ce mai tayi wallahi haduwar su da hjyar mu a nan saudiyace kawai bawai sun san juna bane dama,</p><p> Tundaga wanan lokacin yakara yin tir da Allah waddai da masu hali irin nasu hjy,</p><p> Yana mamaki taya mutum zai shigo cikin duniya batare d yabar wata sheda da za,a iya gane cewa ga asalin mutum ba,</p><p> Duk wanda yashigo cikin duniya indai bahaushe, ne saidai yace ai daga kano yake,</p><p> Yakara jan dogon tsaki yakara karkata motar shi zuwa tsohon uguwar da muka zauna kafin mu dawo gidan shi,</p><p> Ga mamakin shi duk bakin fuska ne agurin duk wani bayani da ya yi a gamay da mu ba wacce ta gane mu, daga cikin su,</p><p> Haka yadawo gida ga gajiya ga bacin rai duk atare da shi,</p><p> Bayan kamar kwana uku da yawon nai manta da yaketi bai gane komai ba , yasa yafara shiga cikin wani sabon damuwa,,</p><p> Yau yana zaune da dare bayan ya gama komai,</p><p> Cikin rashi ba wani dafi a tare dashi,</p><p> Salim ne ya kira shi dan su gaisa da yayan nashi,</p><p> Inda yake tambayar shi ko anji labarin fadima din,</p><p> Cikin rashi wallawala yace mai tana Nigeria saidai yarasa ko a wani gari take a can din,</p><p> Salim yace yatam bayi Amal ko tasan inda nake kasancewa zaman da mukayi tare da kuma irin shakuwar da ke tsakanin mu,</p><p> Sheriff yaji dadin wanan shawar so sai don shi sam ya manta da zancen tambayar Amal,</p><p> Kiran Amal din yayi bayan yar vaisuwar da sukayi ne </p><p> Itama din taje tambayar shi labarin fadima ya sheda mata cewa tana nan a Nigeria </p><p> Saidai bai san a kowani state take ba, kuma duk yatambaya amma ba,a samu wanda yasan garin su ba,</p><p> Shiru tayi a lokacin tana tuna wani hirar da muka tabayi da ita,</p><p> A likacinda muke kallon lambobin da yan makaran tar su suka bata,</p><p> Inda naga sunar wata yar class dinsu na nace mata akan wai sunan yar garn mu ce </p><p> Nace mata sai ta buga min wayar ta muji ko tasan iyayyena,</p><p>Duk iya buga wayar da mukayi bamuyi sa,a mai lanbar wayan ta dauka ba,</p><p> Tun ina tambayar ta akan tabuga min idan mun buga ba mu samu yasa har uka daina</p><p> Shirun da sheriff yaji tayi ne yasa yace mata ya, naji kin shiru Amal,</p><p> Nan tadan bashi wanan labarin a takaice,</p><p> Cikin zakuwa yace mata may ye sunar yariyar da nake son takira min a lokacin wace nake ganu kamar yar garin mu ce,</p><p> Tace mai murja dogon daji,</p><p> Yakara maimaita sunar yace murja dogon daji,</p><p> Dogon daji a wani state yake tace gaskiya brother ban sani ba wallahi,</p><p> Amma dai a lokacin ita wanan murja din a kano take zaune,</p><p> Shiru yayi yana nazari ko ba komai yasan cewa zai dan samu wani dan aarin haske a wanan labarin, insha Allah,</p><p> Amal tai sallama dashi akan cewa ita ma zata kara kokartawa ko zata samu layin wanan murja din,</p><p> Yai mata godiya so sai kamar ance mai ai an gane garin da nake ne ma ko,</p><p> Duk wani bincike yabar shi ahannu bashir kafin su shigo kasar Nigeria din</p><p> Bashir din yai mai alkawari ya kwantar da hankalin shi insha Allah indai har a cikin kasar Nigeria nake za,a gane inda nake,,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎[11/25, 9:42 PM] 80K: ✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 8⃣4⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Duk wani bincike da yakamata Bashir yayi akan wanan garin da suke tuhumar cewa fadima ta na can ya yi shi,</p><p> Da kyat da sudin goshi yasamu wani bawan Allah mutumin kano yace lalai ya taba jin wanan sunan abakin wani abokin sanar shi,</p><p> Sai dai yana tuhumar cewa garin yana can cikin jahar sokoto ne </p><p> Hakan yasa suka bidi wani mutumin jar sokoto da ke cikin kasuwar wuse </p><p> Don jin ko yasan wanan sunan gari , sanan ta ina ne garin yake dan Allah,</p><p> Dan dattijon malam iliya yai yar dariya yace kwarai kuwa ba shakka nasan wanan garin a can cikin jahar mu ta sokoto take , garin baida wani nisa sosai da cikin garin sokoto so sai,</p><p> Dattijon ya kara yar dariya irin ta manya yace Dogon Daji mai rijiyar Biri zam,zam ke nan,</p><p> Yace ai gari ne mai tsohon tarihi, acikin yakin sokoto ga arzikin noma da kiwo Allah yaba mutanen wanan garin,</p><p> Bashir yaji dadin samun wanan labarin dayayi</p><p> Saboda bai son wani abinda zai sa dan uwan shi cikin tashin hankali,ko kadan,,</p><p> A hanyar shi ta komawa gidan shi ne yai wa Sheriff text a waya akan cewa an gama komai, ko,</p><p> Sheriff shima da alokacin yana hanyar madina zuwa makkah yai yar murmushin jin dadi tare da shafar suman kanshi,</p><p> Har cikin zuciyar shi yaji dadin wanan sakon na Bashir don gani yake yi kamar har ya isa garin su fadima ko,</p><p> Yasan kowa ye Bashir dama shi yasa yake kara son shi yasan tun suna yara Bsshir yana damuwa da damuwar shi,,,</p><p> Yai yar ajiyar zuciya yace fadima i will surprise u, insha Allah,</p><p> Duk inda kika shiga cikin duniyar nan zan iya tono ki, </p><p> Yai dan murmunshi da saida fararen hakoran sa suka baiyyana waje, yace,,,</p><p> Ke tawa ce ni kadai fatima, bazan iya rabuwa dake ba, duk ritsi bazan barki ba,</p><p> Tun a wanan lokacin yaji kamar yai tsuntsuwa yaje Nigeria,</p><p> Sai yaji kamar an sauke mai wani nauyi ne a kan sa, </p><p> </p><p> Shigar safiya su kaiwa garin kano su biyu ne a tafiyar tasu Khalid bai samu biyo su ba, kamar yadda yaso, sai Al, mustapha da ke tare da Sheriff din shi akoda yau she,</p><p> Tafiyan su ta zanto tamkar kamar ta official ne, don jirgin ba wai wasu passenger ya kwaso ba masu yawa,</p><p> Daga Riyadh Abuja jirgin ya sauka, bayan duk wani bincike da ya dace ai masu angabatar</p><p> Motocin company su Ahmad ne har guda hudu Suka zo don taron su inda aka lodawa hilux kaya masu yawa a bayan ta,</p><p> Sai a lokacin doctor kamal yaga irin kayan da Ahmad ya jibgo don tafiyan,</p><p> Cikin mamaki ya juya inda Ahmad din ke tsaye yana kokarin bude kofar mota,</p><p> Bayan sun zauna ne Doctor yace wanan uban kayan fa da ka dauko,</p><p> Murnushi yayi lokacin yana kokarin ciro wata yar karamar system din shi new model don binciken wani karfe,</p><p> Yace wa Doctor duk kayan fadima ce Doctor,</p><p> Cikin yar zarar idon mamaki yake kallon shi,</p><p> Shiko cikin ko in kula yace yes </p><p> Da da farko ba,a gaban iiyayen ta, na nemi auren ta ba duk wani abin da yakamata ai wa fadima ban mata ba, </p><p> Wancan lokaci kasani kai aure ne kawai na wani manufa,</p><p> But yanzu ko ta riga ta zama wani sashe na jiki fiye da yadda nake tsamani,</p><p> Shiyasa zan tafi mata da wanan kayan a matsayin lefen ta, a gurin iyayen ta na aini fi,</p><p> Don su ma in basu hakkin su tare da hakkuri, da duk wani kuskure da aka tafka alokacin na rashin bidan yardan su,</p><p> Murmushi doctor yai mai don gane hikimar yin hakan </p><p> Yana son Ahmad wurin bawa kowa hakkin shi komai kan,kanta abu </p><p> Yace wanan kuma fa gaskiya ne Ahmad, hakan nada wani fa,ida so sai, </p><p> Musan man ga mutanen mu hausawa da suka maida kayan lefe kamar wani sunna babba,</p><p> Zakaga koda yaro baida halin su kamar dole sai ya nemo su ya kai gidan yarinya,</p><p> Wasu ma don jahilci har rainawa sukeyi, agaban yan uwan yaro,,,</p><p> Sannu a hannkali motocin ke tafiya a bissa titin cikin garin Abuja,,</p><p> Saidai yar go,slow da suka samu a hanyar don gurin yadan cike da abin hawa,</p><p> Doctor kamal sai yaba garin Abuja yake yi, ga irin girman da takara acikin yan shekarun nan,</p><p> A zuciyar shi yana fadin cewa a gaskiya gwainatocin Nigeria suna iya keep karin su dosai wurin inganta rayuwar al,uman su,</p><p> Babu gwaunatin da zata hau mulki da baita wanin abin ci gabar al,uma ba akasar </p><p> Duk wacce ta hau sai tayi iya kokarinta ga jama,ar ta,</p><p> Suna tafe suna hirar su, Ahmad na fada mai cewa shima yana son yabar kasar saudiya yadawo kasarsa da zama,</p><p> Saida har yanzu gwaunatin saudiya sun ko sake shi ,</p><p> Koda yaushe kokari kara mai ci gaba sukeyi a gurin aikin shi. </p><p> Ta yadda ba zaiyi tuna nen dawowa kasar shi ba, saboda amfanar da sukeyi dashi,</p><p> Maitama suka ga an rubuta baro, baro a titin shiga layin uguwar,</p><p> Agaban wani kyakyawan gida suka tsaya, inda mai gadin kofar gidan ya wagale get motacin suka shige ciki gaba dayan su</p><p> Gidan Ahmad na maitama, ke nan, wanda bai ko tare a cikin sa ba,</p><p> Sabone shiya gina abin shi tun lokacin da yafara aiki a kasar yai tunanen yin wannan ginan don gaba,</p><p> Don ita Nafisa tana zaune A so Rock, a gidan shi da company su na nan Nigeria ta gina mai ,</p><p> Don haka a can maitama ya yanke shawar sauke doctor,</p><p> Saboda Doctor ya huta yasa su zuwa maitama direct,</p><p> Doctor kamal yayi mamaki kwarai da wanan katafaren gidan da Ahmad yagida a kasar shi ta haihuwa,</p><p> Saidai mamakin nasa ba wani mai tsawo bane saboda sanin da yai,wa Ahmad din ,</p><p> Akan irin kudin da yake samu a kowani wata, daga guraren aikin shi da kuma masana,artan su ta Abu Abdallah, dake Dubai,</p><p> Dan ma Ahmad din ya kasance mutum mai son taimakawa addinin sa , </p><p> Yana yawan taimakawa kasa shen musulumai baka ken fata da tallafi, da kaso nai tsoka daga cikin dukiyar shi akoda yaushe,,,,</p><p> Sun samu Bashir ya aiwatar da komai da yakamata don taron baki a gidan, </p><p> Saida ya tabbatar da cewa, doctor yasamu natsuwa daga gajiyar da suka kwaso ne,,</p><p> Sai yai mai sallama da niyar wucewa gidan shi da nafisa take zaune a ciki,</p><p> Al, mustapha ya bar mai, don kauda shiru agidan shima kuma mustapha din agajiye yake a lokacin,</p><p> Sam nafisa bata da masaniyar cewa Ahmad zai zo yau saboda ta san cewa yafi shigowa karshen wata, duk da bawai ko wani wata bane yake samun shigowa Nigeria din,,</p><p> Duk da rashin shigowar shi time to time bai sa tadamu da rashin zuwan na shi ba,</p><p> Ita dai gurin ta ta zauna a matsayin matar shi a rayuwar ta don gani take yi kamar babu sauran namijin da yakai Ahmad din ta komai yanzu,</p><p> Don haka tasa wa ran ta yin hakkuri da zama dashi ko ta yayane, zata iya jurewa da shi din,</p><p> Don haka babu wani tanadin da tai mai na shirin zuwan nashi Kamar yadda ya kamata duk wata, mace ta tarbi mijin ta a duk lokacin da zai ziyar ce ta,,,,,</p><p> Nafisat ta canza halinta so sai yanzu ba kamar da ba , duk wani shaye shaye ta daina shi yanzu,</p><p> Zaune take a cikin tanga may,may falon ta tana waya yar aikin ta na gefe guda ta na dan goge gogen kayan cikin falon,</p><p> Duk da safiya ne yanzu, bai hana nafisa ta tsara kwaliyar ta ba tankar wace mijinta ke a gari, zaune,,,</p><p> Da sallamar shi ya shigo cikin falon nasu, duk da gidan shi ne, amma shi akidar shi ce yashigo da sallama,</p><p> Ganin da taimai girshi sai da gabanta ya fadi, cikin nuna yar faduwar gaba tace Ahmad ,</p><p> A yar razane ta mike tsaye daga zaunen da take, </p><p> Tana mai sannu da zuwa cikin mamaki, </p><p> Inda take yadan nufa yadan sunbaci tsakiyar goshinta kamar yadda larabawa kewa matan su ko diyan su,</p><p> Kaine tafe babu ko sanarwa, batare da ya dakata ba ko ya dan tsaya ya wuce kai tsaye zuwa hawan stairs ,</p><p> Binshi tayi da kallo tace a zuciyar badai, miskilanci ba Ahmad,</p><p> Itama saman ta haura tabi bayan shi,</p><p> Koda ta shiga dakin ta samay shi yana cire botton din rigar shi,</p><p> Zuwa tayi don taimaka mai cikin kissa irin ta yan duniyar mata,</p><p> Duk da yagane nufin ta hankalinshi bai wani daga ba ga duk wani kisi,sinanar da take ai,watar wa,</p><p> Kara tanbayar shi tayi ko lafiya ya shigo batare da fada mata ba, zai shigo ba</p><p> Jaye taye daga gaban shi kadan, ya nufi hanyar bayi,</p><p> Daidai kofar shiga toilet yace mata, batafiyan ki nayo ba shi yasa ban sanar da ke ina hanya ba, yashige bayi abinshi,,</p><p> Ta yar murmushi kamar ta mugunta tace aiko nice mai tafiyar ba aiki ba,</p><p> Bayan yafito ne ya shirya ta kara shigowa dakin cikin kwalliyar da yafi nadazu, kyau,</p><p> Abin breakfast ta gabatar mai duk da ya danci wani a abu acan gidan da suka fara sauka da doctor </p><p> Hakan bai hanashi karban tayin da tai mai ba na abincin don ya fitar mata da hakkin ta,</p><p> Kasa stair ya sauko don ya ci abincin,</p><p> yafara cin abincin da ta sa aka shirya mai a saman dinnig, a hankali saboda sam bai jin cin komai a halin yanzu,</p><p> Kunun cookeroth yadan kurba, kadan sai wayar shi tai kara alamar kira,</p><p> Bashir ne a layin inda Sheriff ke sheda mai cewa ai ya iso ko tun dazu kuma yana gidan nafisat,</p><p> Aiki ne yataso maku haka ba shiri kashigo a gagauce,</p><p> Nafisat ta kara tambayar shi a karo na biyu,</p><p> Kai tsaye yace mata a,a aikin kaina ne wanan karon,</p><p> Mata, ta ce nabiyu , shiyasa kika gan ni a wanan lokacin,</p><p> Duk da maganar yadan daki zuciyar ta amma sai ta daure don kawai alkawarin da ta daukar wa iyayen ta,</p><p> Tai dan murmushi tace Aziza ce sai ka biyo ta har nan wacce ba wani zama takeyi ba a kasar da har zai sa ka biyo ta,</p><p> Daidai lokacin da yake mikewa tsaye yace Aziza kuma, </p><p> Ai Aziza ba sai na biyo ta har Nigeria ba tunda ba,a nan take zama ba,</p><p> Kafin wanin su yai wani magana ne Bashir ya shigo falon cikin sallamar shi,</p><p> Dan rugumay juna sukayi bayan misa bi,ar da sukayi,</p><p> Bayan gaisuwa da kuma tambayar sauran jama,a</p><p> Sai suka zauna a lokacin Ahmad ke cewa Bashir to ya mutumin da zai gwada muna hanyar garin ya shirya tafiyan ko,</p><p> Sai a lokacin nafisa da ke tsaye ta sandare cikin mamakin maganar da Ahmad ya fada mata, tun dazu,</p><p> Tadan gyara zaman ta don jin zancen takeyi kamar ta almara har yanzu,</p><p> Bashir yace a gaskiya ba karamin kokari yarinyar nan tayi ba, da ta kamo hanya ita kadai tun daga saudiya har wanan gari da akace yana da nisa sosai,</p><p> Ahmad yadan yi, ajiyar zuciya ,cikin muryan tausayi,yace ba komai ke kara tayar min da hankali ba kamar cikin da ke ajikinta, Bashir,</p><p> Banason ace min wani abu yasamu cikin nan don duk wani hope nawa a yanzu bai wuce kawai inga ance min an haifi abinda ke cikin cikin nan ba,</p><p> Ido waje Nafisa ta kara kallon shi , </p><p> Ta mai,maita a zuciyar ta tace ciki fa,</p><p> Wace matar tashi keda ciki wacce ban sani ba,</p><p> Kai wanan dai kila matar wani ne can suke zance,</p><p> Shiko bai ko san cewa tanayi ba ma,</p><p> Don haka cigaba ya yi kawai da zancen shi, batare da yako kula da wani zaran ido da nafisat keyi ba,</p><p> Bashir ne yadan kulada halinda take ciki a lokacin don haka ce mata yayi,</p><p> Kina mamaki ne ke ma ko Nafisa, a ce mace ta baro saudiya da ciki zuwa nan kasar aiba gaskiya bane koma dai may ne ai zata bari har ta haihu ai ko,</p><p> Nafisa tai karfin halin bashi ansa tace watakila wani abin ne yabata mata rai har yasa ta tafiya mai nisa haka,,</p><p> Ahmad yace ma bashir cikin murmushi </p><p> You know she is still young,</p><p> Bawai wata babba ba ce, barazanar Aziza ce yasa ta firgicewa a lokacin, don yadda taga Aziza tana farautar rayuwar ta dole ne ta firgice da ita,</p><p> Don a ranan Amal tace sintiri ta kwanayi a kofar na ta,</p><p> Tabbas kuwa ba aziza din bace inji nafisat ke wanan zancen acikin zuciyar ta,</p><p> To wa ce ce wanan mai cikin wace har kira da wai matar shi, don dai gaskiya ita a iya sanin ta bayan Aziza da ya aura a bayanta bataji yakara wani aure ba,,</p><p> Sunda dade nan gurin suna hiran su shida bashir don daga karshe duk kusan rabin hirar na hjy tsohuwace,,</p><p> Fitar Bashi keda wuya Ahmad ya mike da niyar ya shiga dakin shi yadan kwanta,</p><p> Nafisace tace mai wai wata matace kake zance Ahmad don ban fahinci maganar taku ba sosai,</p><p> Matata, Fadima wace kika sani a saudiya mana,</p><p> Fadima gabanta yaba da wani dam dam,</p><p> Takara nanata sunar a hankali ta ce fadima yar takaru,</p><p> Yace mata kwarai kuwa ita, </p><p> Matar kafa kace kuma harda ciki,</p><p> Cikin mamaki ya kalleta yace kina nufin kice duk tsawon shekarun nan bakisan na auri fadima ba ko may,</p><p> Zaune takai daga tsayen da take duk da sanyi A, C dakuma dan sanyin garin bai hana Nafisa fidda wani zufa ba a goshin ta,</p><p> Cikin rawar murya tace nasan za,a rina fadima nasan cewa zaki iya yin haka wallahi ko,</p><p> Wani irin kallo yai mata cikin rashin fahintar maganar ta</p><p> Yadan kalle ta kawai sai ya wuce nan yabar ta da dinbin tambaya a zuciyar ta,</p><p> Duk wani zagwadin kasan cewa da mijin ta da takeyi sai taji ya fice mata aran ta</p><p> Wayanta ta dauko ta dan na lambar mahaifiyar ta, kira na biyu tadaga wayan,</p><p> Cikin tashin hankali take magana da maifiyar nata,</p><p> Tace mama na shiga uku ashe Ahmad yana da wata matar bayan nida Aziza,</p><p> Wai har matar nada ciko a jikin ta, </p><p> Yanzu haka ma zancen da nake maki ma yana cikin kasar nan wai matar tashi ta gudo daga saudiya,</p><p> Saboda Aziza da tasata a gaba akan sai taga bayanta,</p><p> Sai da uwar taji ta idar da zancen ta ce maya nafisa ki kwatar da hankalinki ki natsu ki saurari abinda zan fada maki,</p><p> Kada ki manta yadda kika koma gidan Ahmad wallahi duk kikayi wani abin da ki ka jawo wa kanki matsala ba ruwana a ciki,</p><p> In ba abinki ba tunda ma har Aziza ta nuna cewa bata kaunar wanan matar ke mai zai hana ki nuna kulawar ki akai ta yadda Ahmad din zai kara amincewa da natsuwar ki,</p><p> Kafin uwar ta ce wani abu nafisa tace mama wanar yar iskan yarinyar yar aikin namu ce fa fadima nake nufi ya aura,</p><p> Uwar tace ina ruwanki aikowa da halinsa yake zama a gidan miji,</p><p> Badon taso ba uwar har taci karfin ta tai nadama, da zancen,</p><p> Washegari ne tafiyar su zuwa dogon daji,, motoci ukune kamar ta jiyan na hudun su hilux ce mai dauke da kaya ,</p><p> Motar farko wanan mutumin da zai gwada masu hanya ce tare da security guda biyu,</p><p> Mota ta biyu Sheriff ne tare da doctor kamal a, baya sai driver da ke jan su,, tare da Shehi a gaban motar</p><p> Mota ta uku Bashir ne ke jan ta, sai Al,mustapha da salim a ciki a tare da shi,</p><p> Bayan su kuma hilux ce dauke da kaya sai security ma,aikatar su a cikin motar,</p><p> Ba karamin gudu suke yi ba duk da kasancewar hanyar ba kyau ke gareshi ba,</p><p> Gudu kawai suke yi abinsu,</p><p> Doctor kamal ya,dan kalli Ahmad wanda ke ta , dajin da ake ta wucewa, tun dazu,</p><p> Cikin kada kai yace wa aminin shi, ya ce kadiba fa irin wanan nisan har a ce wai wanan yariyar ta biyo shi ita kadai,</p><p> Ahmad yadan nisa kadan ya gyara zaman shi, yace ma doctor, kamar kasan abinda ke acikin zuciya na wlh, </p><p> Yadda wanan matar tadauki yar karamar yarinya tun daga nan har zuwa kano da ga kano kuma wai har saudiya,</p><p> Wai bidar kudi kawai,</p><p> Kai mutane ba imani wallahi, doctor,,</p><p> Karfe uku daidai na rana su na cikin garin sakoto saboda uban gudun da sukayi,</p><p> Kasan cewar motocin su duk lafiyyau ne, </p><p> </p><p> Yau tunda safe da na tashi sai kawai naji raina ya na baci don haka ba wani maganar kirki nakeyi ba,</p><p> Dama mariyace abokiyar zancen nawa sai ko innar mu da muke yawan zama tare, duk da wani lokaci Tumba takan shigo gidan mu hira wurin innar mu ,</p><p> Amma ni sam har yanzu ban sake jikina da ita ba sam don matar batai min ba,</p><p> Saboda mariya ta ji cewa wai zuwa takeyi dan taga ko wani irin launin da zan haifa,</p><p> Saboda tagane cewa dan larabawane ko bakar fata,,</p><p> Don taji dadin zuwa ta yada a gari, don gulma</p><p> Ganin da mariya tai min yau, shiru shiru ne yasa ita ma baitai wani damuwa na da surutu ba,</p><p> Bayan mun idar da sallah azahar ne innar mu ke ce min indan kokarta in tashi muje mu diba lafiyan kawu salihu</p><p> Wanda yai fama da gudawa yan kwanakin nan,</p><p> Duk da ba son fitar nakeyi ba amma ban iya cewa inna mu ban jin dadi jikina, yau, haka na daure na fita</p><p> Nashirya nida mariya muka fita, zuwa gidan kawu salihu,</p><p> A kan hanyar mune muka hadu da musa mijin hafsi, tare da malam Basiru, </p><p> Da alamar gidan kawu suka fito su ma don yar kwarkwadan da zata sada mu da gidan kawu ne muka hade da su,</p><p> Cikin girmamawa malam Basiru ya gaishe mu, </p><p> Sai kawai musa yace amma dai Basiru anyi mutumin kawai ,,,</p><p> Karasa wacce zaka duka ka gaida sai wacce ta fito yawon bariki, </p><p> Malam basiru ya dauka da farko ko wasa ne musa ke muna,</p><p> Saida yaji maganar da musa ya ci gaba da fada min ne, yagane cewa ba wasa bane wanan zance, ta shi,</p><p> Musa yaci gaba da fadin,</p><p> Don isa ma har yawon nuna sheda takewa mutane a cikin gari,</p><p> Ni wallahi su baba ma sun cuce ni da suka hana inturo masu yar uwar su,</p><p> Tun batazo nima watarana ta haifa min mugun iri a gida ba,,</p><p> Idan mace tana jin cewa kudin yawon duniyar ta na iya ruda musa ne wallahi tayi karya, </p><p> Dan ban ga wanin abin arzikin da aka zobda shi duk wanan uban dadewar, da akayi a uwar duniya,</p><p> Yai wata yar dariya irin ta yan iska, yace,</p><p> Dan musan gaskiyar komai wallahi, duk gumama ne aka tsira da shi, kawai,</p><p> Mariya ce ta,yi kokarin tsayawa dan ta bashi ansa </p><p> Duk da na, hana </p><p>mata hakan cikin tsawa hakan bai hana ta cewa idan baka sako hafsi ba yau daga gidan ka musa lalai uwar ka da zina ta haife ka,</p><p> Kokarin shirin dukan ta yayi saida malam Basiru ya tare shi ya ce mai baka da gaskiya musa,</p><p> Don dai yaran nan basu ce muna komai ba banda gaisuwa,</p><p> Malam basiru ya juyo inda muke yana mai bamu hakkuri,</p><p> Nasamu naja mariya muka shige gidan kawun mu </p><p> Mariya tana ta bambamin ta,</p><p> Jin muryanta da kawu yayi ne yasa su fitowa don jin komai ke faruwa,</p><p> Nan mariya ta kwashe komai ya faru ta fadawa kawu, salihu,</p><p> Kawu ranshi ya baci so sai yace aiko musa zaka ji kunya wallahi,</p><p> Dan daukar alhakin wanan yariyar da kukeyi a garin nan yai yawa wallahi don nagane cewa bakomai bane hassada ne yakawo hakan</p><p> Saboda kawai anga cewa yar kulu da yaranta Allah ya rufa masu asiri,</p><p> Bayan mun gaisa da kuwun mu wanda nasamu da kyat ya hakkura yai shiru, da fadan da yakeyi da musa,</p><p> Dan yace sai yai karar musa gurin maigari akan irin wulakancin da yake min, </p><p> Bawai wani dadewa mukayi ba agidan nakawu sai mukayi sallama da su mukabar gidan,kawu salihu </p><p> Don mariya na son zuwa gaida wata kawarta da bata da lafiya,</p><p> Saboda nasan yariyar sosai tana yawan zuwa gaida ni ko kuma ta dauki Aisha zuwa gidan su tai mata kitso har da kumshi,</p><p> A gidan su yariyar nasamu taron arziki sosai shine gida na hudu da nataba shiga tunda nazo dogon daji,</p><p> Gidan mu gidan kawu salihu, saiko gidan su hafsi inda akai muna mugun wulakanci saboda kawai hassada,,,,</p><p> </p><p>🐎ZEEE MAKAWA</p><p>[11/25, 9:47 PM] 80K: ✈✈✈TAKARI✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣 </p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 8⃣5⃣ </p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost True Life Story,,,</p><p><br /></p><p> A, jere motocin suka gan gara cikin garin na dogon daji lokaci guda,</p><p> Duk wani wanda waje a lokacin yaga shigowar su cikin garin,</p><p> Wasu mutane ne maza mutum biyu ke tafi a gefen hanya gudan mutumin yana ta faman sababi ,da alamar fada yakeyi,</p><p> Motar da security ke cikine yadan tsaya a gaban mutanen biyu dan tambaya,</p><p> Bayan sallama da sukai masu gudan ya karba masu ne sai na cikin motar yake tambayar su dan Allah suna tambayar gidan mai gari ne,</p><p> Kwatace malam Basiru yai masu na inda zasu bi zuwa gaidan mai gari,</p><p> Gefe suka dan rabewa motacin don su wuce, sai dai duk suna bin motocin da kallo </p><p> Ta yadda za,su iya ganin wa,yanda ke cikin motar zaune,</p><p> Mota tabiyu ce tafi daukar hankalin musa so sai,</p><p> Yace kai mutumi kaga wani hadaden guy cikin wanan motar da ganin shi shege, naira ta zauna mai boko ya ratsa ko ina,</p><p> Har motocin suka shige kwanar gidan mai gari suna tsaye suna masu kallon kurullah </p><p> Basiru yace kila wasu jami,an vwaunatine suka shigo yin wani aiki,</p><p> Sai musa yace ka ko ga wanan motar ta bayan da alamar kaya ta dauko acikin ta,</p><p> Kawai gara mu isa kada aba mu labari,</p><p> Suka bi bayan motocin cikin sauri kamar zasu tashi sama,</p><p> Duk wanda yaga motar sai shima yabi don zuwa ganin ko may ke faru ,</p><p> Irin dai yadda kauye ke samun abin gulma duk akewaye,</p><p> Bayan security sun fito sukai saurin shiga wurin mai gari don naiman isa tare da jagorar malam illa,</p><p> Batare da bata wani lokaci ba fadawar maigari suka gyara masu guri zama,</p><p> Nan da nan mai gari yasa akawo masu ruwa mai sanyi da abin sha na gwangwani,</p><p> Inda aka masu masauki kafin suga maigari aji abinda yakawo su garin </p><p> Sallah suka fara gabatar wa,tukun acikin jam,i</p><p> Suna gama sallah saiga wasu yara sun shigo da furar shimkafa yaji nono da kan kara </p><p> Wanan irin taron da maigari yasa akai masu duk da bai san ko su suwaye ba, </p><p> Yasa sunji dadin hakan gaba dayan su ,,,</p><p> Cikin zuciyar Sheriff yace yanzu yafara ganin inda nadauko sanin darajan mutane,</p><p> Iso akai masu har cikin zauren maigari inda securities suka tsaya wajan zauren,</p><p> Sauran jama,an gari duk suna daga gefe sunyi cirko cirko dan jin ko wani irin sako aka zo dashi,</p><p> Malam illa ne yafara yiwa mai gari bayan dan abinda yasani na cewa daga Abuja yazo dasu don suna cigiyar garin shine yai masu jagora,</p><p> Bayan maigari yai masu barka da zuwa ne sai Shehi ya dauki zancen da cewa mai gari,</p><p> Lokacin ne Kawu salihu yazo wajen da niyar karar musa wurin maigari don sherin da suke kulla ma fadima yai yawa,</p><p> Kawu na zama daidai lokacin Shehi yaci gada fadin,</p><p> Mun shigo wanan garin ne a saka makon nemar wata yarinya da mukazo </p><p> Wace muke zaton cewa yar wanan yakin ce daga saudiya ta fito batare da sanin mijin ta ba lokacin da ta bar saudiya saboda yan wasu dalili lai nata,</p><p> Kafin Shehi yaci gaba da bayani, sai kawai muryan </p><p> Kawu Salihu ya cabe maganar yace ko fadima, cikin razana Sheriff da sauran suka shakka babu itace,</p><p> Ai sai kawai wuri yadauki salati, </p><p> Inda har nawaje suka shiga leken ko may ke faruwa da har ake salati haka,</p><p> Saida wurin yadan natsu ne maigari yace wanene mijin nata cikin mamaki </p><p> Da sauri Bashir ya nuna Sheriffudeen da hannun shi,</p><p> Cikin jin kunya Sheriff ya dan noke kan shi kasa don nauyi da kunya da suka kama shi a lokacin,</p><p> Maigari yace ma wani daga cikin mutanen shi ya tashi Sheriff yadawo nan,</p><p> Kawu salihu da sauran jama,a suka dauki murna da kuma shewa kamar yadda dattawa kan yi indan sunji dadin abu,</p><p> Kawu ya ce akan zancen ta ne nazo wanan gurin yanzu wallahi alheri ne ke kirana ban sani ba,</p><p> Ai, nan da nan maigari ya nuna masu kawu a matsayin kawuna kuma uba na dan shine mai kula da duk wani lalurar mu,</p><p> Kasancewa uban mu baida rai tun muna yan kana,na,</p><p> Gaida kawu suka karayi cikin ladabi, </p><p> Wani bafade maigari ne yadaga murya sama dan sauran mutanen dake waje suji saboda leken da suke tayi ,daga waje,</p><p> Yace Allahu akabar zato ko zunubi ne danko yau Allah ya wanke yar kulu da diyar ta fadima ,</p><p> Allah yakawo mijinta uban cikin ta har gida,</p><p> Yau zargi yakare ga munahukai yan hana ruwa gudu,</p><p> Ai kafin ace kwabo wajen fadar mai gari yadauki zancen cewa mijin fadima yazo daga saudiya </p><p> Wa, Sukuma su ce kila dai sheri nayi aka biyo ni daga saudiya,</p><p> Amma ina fadima ina wa yan nan mutanen haka,</p><p> Sun dai boyene, kawai, </p><p> Kai mutum baka iya sa wallahi, sai Allah</p><p> Batare da bata lokaciba maigari yasa a,kaisu gidan mu dan su tabbatar ko ni ce,</p><p> </p><p> </p><p> Masu karatu nadai fada maku irin fasalin gidan mu tun farkon labarina,</p><p> Dan haka gidan mu gidan laka ne mai dauke da dakuna biyu na laka saman dakin mu jinka ne,</p><p> Gidan mu an kewaye shi da zana ne da kuma karar marasa,</p><p> Yan kayan aikin mu suna a tsakar gida gefen darni inda muke girki,</p><p> Sai yan dabbobin da inna ke kiwo a gidan raguna guda biyar da awaki sun kai hudu,</p><p> Sai kaji, da kuma tantabaru, da Abdull ke kiwon su,</p><p> Don haka da zaran ka aje wani abu yanzu kiwon nan na inna zasu far ma abin da ci ko tono,</p><p> Shiyasa bamu aje komai a fili duk cikin daki muke aje kayan mu,</p><p> Tafiya sukeyi da kafa sai jama,a dake bin su a baya mata harda leke sukeyi a darni gidan su dan ganin zahiri,</p><p> Sheriff sai waige waige yakeyi yana nazarin irin gidajen da ke gare mu a kauyen,</p><p> Yana tunane a ranshi cewa a wanan irin gidar fadima ke rayuwa aciki,,</p><p> Ganin da sukayi kawu ya nufi wani dan tsukarken gida </p><p> Wanda a,ganin su bai fi daki daya ba,don kilama ba filin gida acikin shi,</p><p> Anan kawu ya tsaya kofar gidan yana kwada sallama,</p><p> Kawune akofar gidan innar mu yana kwada sallama, Abdull da Aisha dake wasa ta tsakar gida suka amsa mai </p><p> Innar mu dake fitowa daga daki tace mai ,</p><p> Koni am shigo mana Salihu sai kace wani bako can,</p><p> Yace aida bakina muke shinassa</p><p> Bakin shim to lale marhabin da bakin mu inji inna,</p><p> Tace mai shigo dai ni,daita agidan, </p><p> Sheriff da doctor sai bashir dake bayan su duk suka kutso kai cikin gidan na inna bayan ison da Kawu yai masu,</p><p> Ganin datayi bakin sam ba suyi kama da mutanen kauyen mu ba yasa inna saurin jan zanin da ke daure a sanan wanda ta daura dama kusan da bi,ar mutanen kauye ne daura zani biyu,</p><p> Ko kuma a aza guda a saman kai </p><p> Aisha da ke ta zagayan gida wata yar akuya karama tana kora akuyar sunata faman guje guje </p><p> Daga kan da Aisha zatayi sai kuyi arba da sheriff,</p><p> Wani irin ihu tayi don gani da taima cikin mamaki tana fadin Abu,Abu,, </p><p> Ware hannayen shi yayi tafada mai ajikin shi karamar yarinyace sai kawai tasa kuka,</p><p> Duk wanda ke gurin saida hannkalin shi yatashi dan yadda Aisha ke kuka,</p><p> Daki inna tai masu shimfida, a samar wata tabarmar kaba mai ruwan ja da shudi,</p><p> Bayan fitowar mu gidan kawar Mariya bamu tsaya ko ina ba sai gida,</p><p> Abinda na dan lurada shi ,shi ne yadda yau nake samun gaisuwa ga yan kauyen mu ,</p><p> Koda ban san mutum ba zai ce min fadima ho, </p><p> Mariya ce ke cewa ingwaiyya,,</p><p> Duk da ganin mutane dani kofar mu hakan ban kawo komai a raina ba illa saurin da nakeyi kawai in shige cikin gidar mu </p><p> Kaina yana a duke har muka shige batare da na tantace ko suwaye a waje ba,</p><p> Ashe salim na kallona da shi da Almustapha acikin su, </p><p> Ganin da sukayi mun dukar da kai a kasa yasa suka kyale mu </p><p> Wai sun dauka ko al,adar garin mu ce hakana,</p><p> Uwar,Tunkiyar inna ce ke fitsari samar takalmar sheriff takalman da akalla zasu kai dubu saba,in indan ankiyasta da kudin Nigeria,</p><p> Mariya na kokarin cewa inna ga wasu mutane fa akofar gidan mu tsaye, </p><p> Sai kawai hancina ya shar min kamshin da bazan taba mance mai amfani da wanan irin turaren ba arayuwata,,</p><p><br /></p><p> Hakalina a tashe na furta a hankali na ce Sheriff,</p><p> Sheriff mariya ta maimaita abinda nace ina mai nuna mata kofar dakin innar mu,</p><p> Ta, waiga da saurinta ta isa kofar mutum uku ne zaune sun cika muna daki da kamshi sai innar mu da ke can ta kuryan daki rusun,ne,</p><p> Cikin sauri ta isa kofar tana kokarin lekawa, cikin dakin,</p><p> Sandarewa nayi tsaye inda nake don sam bantaba zaton cewa Sheriff zai biyo ni har kauyen mu ba,,</p><p> Nadauka cewa mun rabu ke nan har abada, dashi, </p><p> Don ban zaci cewa kamar sheriff zai tsaya bata lokacin shi ga yar aiki irina ba,</p><p> Waigiwar da sukayi dan jin muryan mariya yasa su hango ne tsaye cikin mamaki,</p><p> Doctor kamal ne yai min larabci yace min inshigo, mana,</p><p> Ganin da yayi kamar ban motsi a tsayen yasa ya fadawa sheriff, </p><p> Cikin sauri duk suka nufo inda nake tsaye sandare ina dogon tunane,</p><p> Jin muryoyin su da na yi a kusa dani yasani dawowa a cikin hayaci na,</p><p> Cikin sauri sheriff ya rike min hannu na muryan shi naji gab dani ya na ce min in zauna tukun,</p><p> Zama naji bisa dan turmin dakar inna da ke kife a gefe na,</p><p> Kaina nakama jin ya na wani juya min a lokacin dan haka sai nadan dafe kan da hannu na guda,</p><p> Mariya ce tazo da saurin ta ,ta dan dafani tana fadin anty fadima may ya samay ki pls</p><p> Har yanzu na kasa magana sai ido nake dan binsu dashi cikin mamaki da fargaba,</p><p> A hankali duk suka karaso inda nake daidai lokacin innar mu tasa mariya tafito da tabarmar a waje,</p><p> Cikin damuwa nadan daga kaina da kamar wacce zatai magana sai kuma na kasa na kara dukar da kaina kasa,</p><p> Inna tace wa mariya ke maza kuna sunka taho, </p><p> Sai mariya ta washe baki saboda jin dadin zancen inna </p><p> Tace Allah mungode ma,</p><p> Da na rasa abinda zanyi sai kawai nasa masu kuka kamar yadda Aisha tayi,</p><p> Sheriff yace min cikin larabci Fatima may yasa kika barni may yasa kikai min haka,</p><p> May zai sa ki wahal da kanki da baby na,</p><p> Fatima ba kya gudun wani mugun abu yasamay a hanya </p><p> Kin ko san irin kasadar da ki kayo haba Fatima,</p><p> Sai na kara sautin kukan da nakeyi,</p><p> Sunana yakira a hankali, </p><p> Yace min ya rokeni Allah indaina wanan kukan </p><p> Kada mutane na su dauka ko wani mugun hali yake min acan,. </p><p> Yadan langabe kan shi alamar maganar shi ba wasa acinkinta,</p><p> Batare da kalle shi ba na mike a hankali da niyar in shige dakin mu,</p><p> Duk wanan drama a gaban su inna da kawu har da tumba wace ta shigo gidan da niyar gulma </p><p> Batare da yadamu da mutanen da ke wajen ba ya dan jawoni kadan zuwa jikin shi </p><p> Nai sauri na gwauce da ga rikon da yai min,</p><p> Yace haba fatima aiko doctor dai kya tsaya ku gaisa da shi ko </p><p> Ga kuma Almustapha da salim a waje har da Shehi,</p><p> Da sauri na waiga dan in gaskanta zancen shi aiko Shehi ne tare su </p><p> Suna shigowa cikin gidan mu,</p><p> Da sauri na mike zuwa wurin shehi mutumi da nake jin shi kamar mahaifina </p><p> Kuka kawai nasa mai agaban shi kamar wata yar karamar yarinya, </p><p> Yace fadima bana son inga kin kara wanan kukan ,</p><p> Ba kuka yakamata kiyi godewa Allah yakamata kiyi,</p><p> Duk yadda na so inyi shiru abin ya faskara kukan kamar kara min shi ake yi,</p><p> Nakasa yin magana dakowa daga cikin su,</p><p> Har nadan wani lokaci,</p><p> Bashir ne ya fita tare da su almustapha da salim da niyar zasu tafi cikin garin sokoto don suyi booking din hotel </p><p> Inda zasu sauka gaba dayan su, anjima, saidai sun bidi taimakon wanda zai masu jagora hakan,</p><p> Mariya ce tasa aka kira malam basiru wanda dama yana kofa atare da sauran securities din da suka zo da su,,,,,,</p><p> </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 8⃣6⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost True Life Story,,,</p><p><br /></p><p> </p><p> Idon sheriff na ga cikin jiki na kyam don ya tabbatar </p><p> Cikin ya wani turo wa kamar wacce zata hai hu a lokacin</p><p> Duk na rasa inda zan sa kaina a wanan lokacin nauyi da kunyar bakin mu duk ya cika min ido,</p><p> Zaune nake a gefe guda duk zullumi ya cika min ciki, sai tuna ne nakeyi ya akayi suka san garin mu har suka zo,</p><p> Ganin da nayi hankalinsu na gurin masu zuwa sokoto, ana muhawaran ko wasu su tsaya nan garin ne,</p><p> Sai na mike tsaye a hankali,nadan sulala na shige cikin dakin mu,</p><p> Sheriff da duk wani tako nawa ya ga idon shi yana lura da ni, </p><p> Ganin da yayi na shige cikin dakin innar mu yasa shi,</p><p> Biyo bayana ganin mutum nayi kawai a cikin dakin </p><p> Kokarin rike ni yayi alokacin ,</p><p> Iya karfi na nasa nadan ture shi baya kadan , murmushi yadan yi min kawai </p><p> Ya ce min fadima nan fa gidan mu ne banga abinda zaisa ki kokarin hana min abin da ya halat a,kaina ba,</p><p> Ina son inji lafiyar ki ,ina son kuma inji dan dumin baby na da kika hana min ji, </p><p> Ya fadi hakan cikin muryan da dole ya ba mutum tausayi a lokacin,</p><p> Kaina nadan dukar kasa saboda na kasa hada ido da sheriff sam, duk yadda yasa mu hada ido da shi na kasa,</p><p> Ganin da yayi ba zan saurare shi ba </p><p> Yasa ya kara tausa muryan shi kasa,kasa yace min</p><p> Fadima fushin ki a gare ni yanzu tankar wani barazana ce mai kokarin rushe duk wani tubalin da zuciya ta ta gina akan ki,</p><p> Fatima banyarda da zuciya ta ba da farko sai lokacin da ki ka bar saudiya, batare da sani na ba ko wani nawa,</p><p> A lokacin nasan cewa son ki da kaunar da bi,un ki sun min illa acikin rayuwa ta,.</p><p> Fatima kin taimaki rayuwa ta fiye da duk yadda zan fada maki, </p><p> Dan zaman rayuwar da nayi da ke yasa na fahinci wasu abubuwar a zaman duniya,</p><p> Wanda ada sam ban dauke su wani abu ba can mai muhin manci a,rayuwar mutum,</p><p> Kin sadaukar da rayuwar ki akaina, kin kuma bada duk wani lokaci naki akaina, </p><p> Alkawarin da nayi a kan mace, a,da</p><p> A,yanzu duk na jaye shi araina saboda ke nagane cewa mata suna suka tara,</p><p> Fatima ki sani duk wani abinda da namiji zai bukata a gun mace kin tara su a yanzu kyau ,hali, ilimi, </p><p> Duk Allah ya baki su a lokaci guda , taya,ya kike ganin zanyi sakaci da kuma sa,ar da Allah yabani akan ki ya wuce a banza,</p><p> Yazama wajibi a gare ni duk inda kika shiga cikin wanan duniyar in bideki ,</p><p> Banyi aune ba saiga namijin duniya kamar sheriff mai jin kan sa wanda yasha gwagwal maya da larabawa kala,kala da turawa har ma yan china,</p><p> Mutum mai ji da kansa ya zube min a gabana gwiwa biyu, biyu, </p><p> Yana kuka a gaban yar karamar yariya kuma cikin dakin uwa ta, a cikin ginan laka,</p><p> Ban san lokacin da na mike tsaye da sauri na tallabo shi tsaye ba </p><p> Saboda sanin dani kowaye sheriff da kuma sanin darajan shi a idon al,uma,</p><p> Ban san lokacin da na kankame shi ba ina mai kuka cikin sauti mai ban tausayi nace mai ,</p><p> Daraja ta da kimata bai kai har ya rusun na min ba kada ya manta da cewa ni ce fadimar nan yar aikin gidan shi har yau,</p><p> Hannu yasa kafin in fadi wani kalma ya toshe min baki na yace daraja na da kima na tun farko yafi karfi yar aki a gare shi,</p><p> A yar uwa yadauke ni, ba yar aiki ba ko da can,</p><p> Shigowar mariya dakin yasa mu ka dan jaye jiki a na juna badon naso ba ni ma,,</p><p> </p><p> Sai alokacin yake ma mariya magana cikin harshen turanci saboda ba hausa sheriff ya iya ba sosai daga harshen su na kanuri sai ko turan ci sai kuma idan yaci sa,a mutum najin larabci harshen da ta zauna mai a baki daram kamar itace yaren shi ta gado,</p><p> Murmushi mariya tayi mai tana dan bashi ansa a cikin dan turacin ta wanda bai nuna ba,</p><p> Lokacin sallah magrib da yagabato ne yasa shi fita daga dakin na inna,</p><p> Din shi duk abinda yake yi hankalin shi na ga ibadar shi,</p><p> Sai bayan fitan su sheriff ne wanda kamar bai fita ba saboda kamshin da suka bar muna acikin gida </p><p> Inna ta samu yi min magana,</p><p> Tace min fadima kada kiyi wasa da damar da Allah ubangiji ya baki akan rayuwar ki,</p><p> Naga kamar shedan nason ya rude ki kiwa wanan bawan Allah wulakanci,</p><p> Duk da ban san komay yahadaki da shi ba ina mai kara horon ki a rayuwa da kizama mai hakkuri da yafiye, aduk al,amari,</p><p> Taci gabada fadin fadima idan har kinyi fushi dashi banga amfanin </p><p> Lokacin da na kwashe wurin koyar da ku tarbiya mai inganci, </p><p> Nace inna aiba fushi nakeyi dashi ba ,</p><p> Tace fushi kikeyi mana tunda baki yi dibaiyar cewa sun fito daga wata uwar duniya zuwa nan gurin ki ba,</p><p> Ai da kamata yayi a ce kin tare su da hannu bi,biyu tunda har suka zo mahaifar ki,</p><p> Ba saboda komai ba sai saboda darajar ki,</p><p> Ga alama fa bake ka daice a gurin shi ba kamar yana da wata matar,</p><p> Amma ya iya biyo ki har kauyen ki kuma yazo batare da yanuna muna wani kyama ba ko raina kama,</p><p> Tace mu mata sauda dama muna wasa da damar da Allah ya ba mu gurin nuna jayayya da hukuncin ubangin jin mu,</p><p> Barin fada maki duk abinda yai maki har kizo nan yanzu da alamar ya jaye su,</p><p> In ma har wani barna ne kinsan abin barna shiga rai ke garesu,</p><p> Daga lokacin da akace wanan abin baida kyau ko kuma adaina shi,</p><p> Haramun ne mutum zai ji yana son aikatasu, fiye da komai arayuwar shi,</p><p> Shiyasa aka ce an zagaye wuta da abubuwan kawatawa, na ban sha,awa,wanda zuciya keso </p><p> An,zagaye aljanna da abubuwa ki wanda zuciya bata so,</p><p> Duk wanda ya kama hanyar aljanna zai ta haduwa da abubuwa da zuciya bata so, haka wanda ya kama hanyar wuta zai ta haduwa da abubuwan da zuciya ke so,</p><p> Shiya sa akace daga cikin hakkurin da akeson mutum yayi a cikin rayuwar shi harda hakkurin biyayya ga Allah da manzon sa kuma mu mata da hakkurin zaman gidan aure ma,ana biyayya ga mazan mu,,</p><p> Yin fushi da mutum ko a kaurace mashi baya hanashi, aikata abin da yasaba sai dai ma ya kara,</p><p> Amma jan mutum ajiki shike sa mutum ya tuba daga abinda yake aikatawa, </p><p> Don haka matakin da kika dauka bayan zuwan su har nan ,</p><p> Nakin kula su ba zai raba ku da mijinki ba,</p><p> Sai fa in har kin tsaya kin kwanatar da hankalinki har kowa ya fahinci may ye matsalar da har tasa ki ka fito daga dakin ki bada sanin mijinki ba ki ka zo nan,</p><p> Kinga ta hakane har zaku fahinci juna a sulhunta tsakani, inko ba haka ba damuwa da kuma shakku ba zai kare ba a tsakanin ku,</p><p> Inna tana kawai na ta wuce ta dauki buta da niyar zuwa tayi alwala, ta bar mu nida mariya a tsatsaye tsakiyar daki cirko, cirko,</p><p> Mariya ce ta kalle ne tace min anty fadima yazama dole ki daure ki fadawa su inna damuwar ki dan asan ta inda za a bulluwa maganar </p><p> Dan kinga da tun farko kin fada masu komai da duk kafin suzo ansan abin yi,</p><p> Dan damar zancen ma da hjy umma tazo tadan walwale ma su kawu dan kadan daga zancen,</p><p> Kallon mariya nayi yar karama da ita ta iya wanan zancen haka,</p><p> Sai kuma natuna da cewa ai ba abin mamaki bane,</p><p> Don mu yaran kasar sokoto komai kankantar yariya tasan iya zama da jama,a </p><p> Koda aure aika mata da shekara goma zata iya zama da irin mutanen da aka kaita cikin su,</p><p> Zaka gansu kamar kauyawa amma wallahi da wayon su fam, kauyanci daine kawai</p><p> Sallah muka gabatar gaba dayan mu ,</p><p> Saidai na lura da cewa duk inna ta rude ta rasa may zata bakin mu na abinci,</p><p> Sallama mukaji ashe mai gari ne ya aiko masu sheriff da abinci cike, cikin wasu manyan cooler rubo guda biyu,. </p><p> Godiya inna tayi so sai dan ice darbejiyan dake kofar gidan mu wanda mahaifin mu ya shuka tun yana da rai ,</p><p> Nan mariya tai masu shimfida a samar wani katon tabarma guda biyu wanda ta anso gidan Dije,</p><p> Zaune nake gurin da na idar da sallah zuciya ta sai sake sake take min dan a,gaskiya a halin yanzu in har sheriff yace zai koma da ni saudiya nasan cewa zai dauko magana dan ji nakeyi bazan kara barin inna ta cikin wanan rayuwar ba ni in koma cikin daular duniya,</p><p> Sallamar hafsi ne yadan katse min tunanen da nake yi,</p><p> Jin muryanta nayi yau kasa,kasa ba kamar yadda tasaba ba,</p><p> Tana cewa innar mu ashe baki ankayi, inna ta ce mata eh,</p><p> Tace shina ankaki aika min,</p><p> Akan mina za,a aika miki inji mariya ,</p><p> Dan mutanen gidan ku suji dadin kulla muna wani sheri,,,,,</p><p> Bata karasa ba ni da inna mukai mata tsawa, amma sai da tace</p><p> Ta ce walle, andai ji kunya,</p><p> Allah ya tona asirin mahassada, </p><p> Ta wuce fuw, hafsi tace ke dai kin ka sani,</p><p> Inna da ta lura da cewa na idar da sallah tace min,</p><p> Fadima tunane ni kai ko mutanen ga za su iya cin abincin mu,,</p><p> Nacewa innar mu za su ci ai , kila, </p><p> Sun kuwa ci din don kaji ne dakwale har kusan guda bakwai mai gari yasa aka gyara masu shi irin gashin kauye na ainihi ba wai na oven ba,</p><p> Sai kuma fura stuwon shikafa danya da miyar yakuwa, da alaihu yaji man shanu, sai kamshi ke tashi,,</p><p> A gaskiya ban da abinda zancewa maigari sai dai godiya kawai, da fatar gamawa lafiya,</p><p> Hafsi dai tana zaune shiru gefe guda sai duk tausayin ta ya kama ni,</p><p> Ce mata nayi ta bari a kira mata sheriff su gaisa, dashi,</p><p> Sai inna da mariya suka ce a,a ta in,bari kawai ai basai yazo ba,</p><p> Aisha ce naiwa larabci ta tashi taje inda suke zaune tafada mai cewa ana magana dashi,</p><p> Batare da bata lokaci ba ya shigo ciki rike da hannun Aisha,</p><p> Yana mai sallama cikin muryan nan tashi mai taushi da dadin sauraro ko yaushe,,</p><p> Da larabci na fada mai cewa ga yayata nan wacce nake bi wa, </p><p> Tazo gaishe shi, cikin girmamawa yafara gaida hafsi da hausar shi da ba ganewa akeyi ba dan ni ban ma taba jin yai hausa ba sai yau,</p><p> Da larabci yake fada min cewa zasu koma sokoto su kwaba duk da shi yasa ya kwana a garin </p><p> Saidai saboda doctor bazai tsaya ba dan kada ya barshi shi kadai, </p><p> Yai ma innar mu sallama dasu hafsi mariya ce tabi bayan shi suna magana ,</p><p> Daidai lokacin innar mu ke ce min bazan bishi in mai rakiya ba,</p><p> Ashe bansan cewa rakiyar bako har kofan gidan yana da falala ba ga Allah,</p><p> Tashi nayi da kyat zuwa inda suke da hafsi suna magana ina kawowa naga yafito da kudi masu yawa yana mika mata,</p><p> Cikin sauri nake tambayar mariya ko kudin may sai tace min cewa yayi abawa inna ai masu breakfast, da safe,</p><p> Na sheda mai cewa akwai kudi a hannu na ai zai isa ai masu komai batare da ya saurare ni ba wuce kawai yana mai muna saida safe,</p><p> Nabi bayan sheriff da kallo sai naji yabani tausayi,</p><p> Dan nasan cewa bai saba da wanan wahalar ba sam, gashi a dalilina ya shigo kauyen mu yau,</p><p> Bashir wanda yadawi yanzu daga cikin garun sokoto,</p><p> Shine kuma mariya taiwa sako akan yakoma tare da su yasayo mata duk wani abinda zasu bukata goben,</p><p> Ashe , sheriff yabawa Basiru kudi, yakaiwa maigari kamar yadda yabawa inna mu,</p><p> Mai gari yaji tsoron yawan kudin dan har dubu dari biyu ya bashi a lokacin,</p><p> Bayan mariya ta gama ba malam basiru sako tadawo dan ta kidaya sauran kudin ssi naji tayi dan ihu </p><p> Duk hankalin mu sai ya koma gareta </p><p> Tace inna har dubu dari biyu yabayar fa,</p><p> Duk sai naga sun rude hankalin su ya tshi,</p><p> Dan murmushi nayi nacewa innar mu kadan ke nan daga aikin sheriff nan nadan fara ba innar mu labarin</p><p> Ko, waye,Sheriff, dan daga halinsa nadan fada mata ,</p><p> Mariya tace ai naga alama anty don naga duk mutanen nan dayazo da su shine ogan su,</p><p> Hafsi tai muna sallama, mukai mata saida safe ta wuce har kofar shiga gidan mu nadan rakata nadawo,</p><p> </p><p> Washegari kafin mu fara aikin abinda zamuyi sai ga mai gari ya aikowa innar mu cewa kada mu aiwatar da komai shine zai masu komai,</p><p> Kuma innar mu tabar wahal da kanta har su tashi yadauke mata dawainiyar su,</p><p> Munji dadin wanan zancen so sai don maigari yana nuna muna kulawar shi ko yaushe,</p><p> Misalin karfe goma na safe, sai gasu sun dawo wanan karon da karin motoci a tare da su,</p><p> Tare da maigari da kawun mu suka shigo inda muka ga a nata aune aune filaye da kuma zanen a takarda,</p><p> Ashe wai sheriff yadauko masu aikin gina irin na company daga sokoto sune zasu gyara wa inna gidan ta,</p><p> Mamaki hakan yabani sai kace sheriff ya shiga zuciya na,</p><p> Dan nima naso hakan tun da nazo amma jin danayi ana cewa yawon banza nayi a saudiya yasani fasawa dan zasu ce ai da gaske ne tunda gashi na samo kudi har ina aiki,</p><p> Ashe ma barin shine alherina dan wanan aiki da sheriff ya bada ayi yafi wanda nai niyar yi sau,dubu,,,</p><p> Abin mamaki saiga musa wai yazo gaida sheriff, </p><p> Yar magana mariya har ta shiga zuba bakar magana sai nai saurin tare ta naiwa sheriff baya nin ko shi waye,</p><p> Hannu ya mika mai sundan, dade yana rike da hannu musa yana mai godiyar kula mai da matar shi da sukayi, </p><p> Mai gari ne ya sa aka shigo muna da akwatinar da sheriff yakawo min a matsayin kayan laifen da bai kawo tun farko ba agaban iyayye na ba,,,,, </p><p> Ai ko kafin kace may gari yadauki zance a gidan kawun mu inna tace akai kayan can aka tafi da su,</p><p> Duk wanan abin wayancewa kawai nake yi dan sam bana jin dadin jikina ina dai daurewa ne kawai, </p><p> ,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 8⃣7⃣</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost True Life Story,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yau gidan cike yake da mutane masu shigow a zuwa gaida bakin mu,</p><p> Babu kunya musa ya shige cikin su sheriff ana ta faman aune aune filin da za,ai ma innar mu gina,,</p><p> Yana ta wani nuna concern din shi ga al,amarin,</p><p> Duk da da nasan cewa banda abokin fada a rayuwa ta , wanan karo nasa wa raina cewa sai na rama duk sherin da musa ya kulla min koda narana daya ne,,</p><p> Zaune nake a cikin yar rumfar da ke cikin gidan innar mu, duk da rumfar na da iska mai dadi sai kawai ya kasan ce yau ban jin iskar sam,</p><p> Duk na rasa abin da ke min dadi,a jikina sai zufa nakeyi kamar wace tai wani aikin zafi,</p><p> Duk da munga juna da Sheriff shigowar su na farko da safe, </p><p> Amma na san cewa yan zu haka ya na son mu kebe dan yaji lafiyata,</p><p> Nima dai din naso mu kebe din dan in ba shi hakkuri kamar yadda innar mu tace min,</p><p> Da nai nazari sai nagane cewa maganar innar mu da hajiya umma, gaskiyace,</p><p> Fita nayi daga gidan miji na batare da yai min komai ba saboda sherin kishiya na dauko wa kaina zunubi,</p><p> Ina cikin wanan tunanen ne sai naji wani irin abu kamar an dan tsikare ni ,, dai,dai lokacin da,</p><p> Mariya ce tazo inda nake zaune,tana wadar lemo, da hannunta,,</p><p> Saida takai wanda tafara wadewa a bakinta sannan tawade mun wani ta miko min ,</p><p> Kai kawai na iya kada mata alamar a,a bazan sha, ba,</p><p> Tana dago kai ta tambaye ni komay yasa bana sha,</p><p> Sai taga inna ta hada zufa,duk jikina yana wani makyar,kyata kamar a na ka da ni,,</p><p> Kyat na iya bude bakina nace mata bana, jin dadi jikina na ne yau,</p><p> Yaran da ke tawasa su na ihu, acikin gidar mu mariya ta dakawa wa tsawa</p><p> Tace kai ku tai zuwa wargi, waje kun taho nan duk kun cikawa mutane kun nuwa,</p><p> Inna da ke can gurin dabbobin ta tana gyara masu guri taji abinda mariya ke fadi,</p><p> Ta ce kai wagga diya ke kan ana tausar kai , kulun kamar kara ki na akai,</p><p> Kafin inna ta kara cewa wani abu sai ga hafsi ta shigo gidan mu, tare da yaran gidan su,</p><p> Yaran suna dauke da wani, langa babba a kan su guda biyu,,</p><p> Gurin innar mu ta tura yaran ,</p><p> Sai inna tace su aje a rumfa inda muke nida mariya kafin ta zo, </p><p> Yar katsalandar mariya tasa hannu ta bude langar, dan gani ko may ye a ciki,</p><p> Fura ne na shimkafa fari tasa manya manyar curi har guda hudu, </p><p> Anyi mai aikin kwarai don yana iya kai kwana biyar ko shida bai baci ba furar saboda dakar hannu ne akayi mai,</p><p> Kafin innar mu ta karaso sai mariya tace wa hafsi aida baki wahal da kanki ba,</p><p> Don maigari na ka daukar nauyin bakin ga ke san shi maigari mutumin kirki na baida kyamar mutum kowane irina shi tarbone shi kai,</p><p> Daidai lokacin innar muta iso gurin ta kai wa mariya rankwashe a kai tana cewa wagga kan bakinta bai samu farsa ba,</p><p> Tace to Inna gani niyyi gidan su musa a,wa, basu da ta, idon na, da zasu kalli anty fadima da shi tunda duk wani sheri da ankai mata garinga can na adda mafari ne,</p><p> Dakuwa Innar mu tai mata gami da ran kwashi a kan ta,</p><p> A dadafe na gasai da hafsi wace ke kokarin cire hijab din jikin ta,</p><p> Shiru tayi tana kallo na, lokacin da idon ta ya kai kaina,</p><p> Murmushin karfi hali nai mata a lokacin dan ban masan nai mata ba,</p><p> Hafsi tace wa Innar mu shin Inna wai ko yau diyar ki lahiya take,</p><p> Inna da ke can gefe tana gyaran inda zata aje langar furar da hafsi ta shigo wa baki dashi,</p><p> Tace ma hafsi mi kik gani , halan,</p><p> Inna tai dan taki har inda nake zaune sai taunar baki nake yi,a lokacin ina daurewa,</p><p> Nai wa Inna murmushin karfin hali, tayadda zata dauka ai bakomai,</p><p> Juyawar Innar mu yayi daidai da wani uban murdan marar da yazo min kamar in kwala ihu na ji,</p><p> HAfsi ta fada dakin Innar mu ta dan gyara shi da kyau duk da mariya na iyakar kokarinta, da dakin yawa dai mukayi wa dakin kawai,</p><p> Tans fitowa muka hada ido sai nai mata wani guntun murmushi wanda baiko kai ciki ba,</p><p> Tace min sannu ko in kawo maki kunu ki sha ne fadima,</p><p> Kai kawai nadaga mata cikin karfin hali a cikin wani kula ta juyo min shi yanada dan zafi na sha</p><p> Aiko kamar na sha ,wa kaina fitina ne, dan ko cup ban aje ba naji wani irin ciwon mara ya turnuke ni a lokaci guda,,</p><p> Cikin hikima hafsi tasa ni tashi zuwa cikin dakin Inna mu,</p><p> Kamar wace ake jira ta shiga daki kawai a lokacin,</p><p> Gaba daya naji duk ko ina nawa ya dauki rawa kamar an min wani allura,</p><p> Mariya naganin yadda na shiga dakin mu da kyat sai hankalinta ya tashi so, sai a lokacin, </p><p> Cikin sauri ta nufi waje inda su sheriff ke tsaye ana nuna masu yadda plan din ginar zai fito,</p><p> Cikin tashin hankali take mai bayanin cewa banda lafiya, </p><p> Baisan lokacin da ya wurga da takardan dake hannu shi ba yai cikin gida da sauri inda mariya ta dafa mai baya,</p><p> Ganin haka doctor kamal ya mara mai baya dan kusan lokaci guda suka shigo cikin gidan,</p><p> Ganin da sukayi kofar dakin Inna a rufe yasa yin cirko, cirko,</p><p> Ko minti daya basuyi da tsayuwa ba kukan jariri duk ya karade gidan na Inna</p><p> A,lokaci guda suka dauki kalman shahada, gami da hamdala ga Allah, ubangiji,, subbahanallah,</p><p> Sheriff ya kalli gidan inna da kyau kamar a lokacin ya fara shigowa gidan, sai yadan lunshe idon shi kadan yace, Ya, Subbahanallah,,,</p><p> Mariya suka shigo cikin gidan ita da Tumba wace ke tafiya cikin sauki kamar, zata tashi sama,</p><p> Docto kamal ya kalli, Sheriff ya ce mai, is a baby boy,</p><p> Dan murmushi kadan Sheriff yayi a lokacin, don hankalin shi na nan, a kofar dakin inna, mu,</p><p> Ji nayi a wanan lokacin kamar ancire min wani kaya ajikina,</p><p> Ina gefe guda nadan rakube a bakin gadon Inna sai wani lunshe, idona, </p><p> Inna ce da Tumba acikin dakin tare dani sai dan jaririn da ke saman tabarma, yanata tsala ihu,</p><p> Doctor kamal yace wa kamal su dan fita daga waje kafin a rarage komai,</p><p> Inna tace indan daga daga inda nake kadan,</p><p> Aiko ina dagawa sai naji kamar wani abu zai kara fito min ashw ko hakan ne,</p><p> Da sauri na kai tsugune yun kuri guda nayi sai ga yar baby a kasa tareda uwar tafiya lokaci guda suka fito,</p><p> Duk suka karade gidan Inna da ihu, </p><p> Su doctor da suka kai kofa shi da sheriff zasu fita sukaji kukan kamar na mutum biyu,</p><p> Doctor yace masha Allah twins babies, insha Allah,</p><p> Ido sheriff yafitar waje dan jin abinda doctor yace sai kuma yadan yi murmushi yace, all 4 me,</p><p> Ina jin muryoyin su Inna sama ,sama a lokacin, saidai bazan iya cewa ga abinda suke fadi ba,</p><p> Su kan sai murna sukeyi abin su batare da su, lura da halin da ni,ke ciki ba alokacin,</p><p> Inna ce tafara ganin yadda,,na sake a lokaci guda ga jini na zuba min kamar famfo,</p><p> A, sama sama nake jin kamar ana kiran suna na, duk yadda nai karfin halin ansawa ko in bude idona nakasa yin hakan,</p><p> Kuka mai karfi irin na tashin hankali Tumba sa, saida duk wanda ke kofar gidan mu yaji ihun ta,</p><p> Sheriff da doctor da suke tsaye a,waje, sukayo cikin gida cikin tashin hankali,</p><p> Dakin suka fada sai gani na sukayi a kwance ko motsi banyi,</p><p> Cikin wani irin murya Sheriff ke kiran suna na a cikin tashin hankali, </p><p> Doctor ya dan auna ni ya ce cikin tsawa a dauko mai mota da sauri,</p><p> Nan da nan idon sheriff suka kada sukayi jawur a lokaci guda,</p><p> ,Addu,a kawai suke min ban kosan anayi ba shehi da sheriff sai matar kawu salihu,</p><p> Gaban shi sai wani mugun faduwa yake yi a lokacin dan ji yakeyi kamar ya karbi tukin motar, dan gani yakeyi driver bai sauri ko kadan,</p><p> Asibitin gawon nama suka kai ni watau Uduth, inda doctor kamal ya nuna masu katin shedar aikin sa,</p><p> Yakuma fada masu dalilin shigowar shi wanan kasar ta Nigeria </p><p> Ba suyi wani bata lokaci ba gurin ansa na kuma sukayi min duk wani abinda ya kamata a lokacin,</p><p> Duk jama,an da suka kawoni jungum suke a tsatsaye babu mai wani kuzari, </p><p> Tsayin lokaci babu wanda yake iya wa wani magana,</p><p> Doctor yafito da dan murmushi makale a fuskan shi murshin da dagani bai kai ciki ba, yana dai yine dan ya wayance,</p><p> Yanayin maganar shi kawai ya nuna cewa akwai sauran zance, yadan dafa kafadan sheriff yace mai dole sai mun yi mata karin jini,</p><p> Saboda tayi loosing din jinin ta da yawa, tana bukatar jini,</p><p> Lokacin su Inna suka iso tare da Tumba,daga kauyen mu,</p><p> Subbahanallah kawai sheriff ke iya fadi a,lokaci sai wani daci da bakin shi keyi,</p><p> Duk angwada jin su har da na Bashir da kamal ba,a samu wanda zaiyi min ba,</p><p> Hankali a tashe kowan su yake agurin,</p><p> Caraf wanan zance ya fada a kunnen Innar mu aiko sai ta kasa daurewa bata san lokacin da kuka ya zi mata ba,</p><p> Hakuru matar kawu salihu da tumba suke bata,</p><p> Cikin kuka inna ke magana tace dole ne tai kuka saboda irin haka mahaifin yaran nan yarasu, </p><p> Gurin bidan jinin da za,a kara aka rasa wanda zai mai har ya rasa rayuwar shi, </p><p> Tumba ma wacce ke dan sharar kwalla alokacin tace ma Inna insha Allah tashi zatayi</p><p> Duk inda kowa nawa yake a cikin asibitin hankalin su ya tashi, </p><p> Sosai dan dai an auna har da wasu daga cikin security din sheriff ba,a samu ba,</p><p> Shehi ne yace wa Sheriff a gwada nasa ko zai yi daidai a diba, sai sheriff yace a,a yabari kawai a gwada na sauran yaran agani ko zaiyi,</p><p> Gani shehi ya nace akan sai yaba da nashi gudun mawar yasa su, yarda inda aka gwada nashi da na salim zasu iya taimaka min ,,</p><p> Batare da bata lokaci ba aka fara diban na shehi sai kuma na salim,</p><p> Doctor yabada umurnin kada a,tashe ni har sai in na farka da kaina,</p><p> Hakan yasa Sheriff ya sallami kowa yace suje su huta, hakana Saidai Bashir da Basiru sunki zuwa ko ina ,</p><p> Zaune suke da sheriff acikin yan kujerun da aka ajewa masu jinya a tsakiyar yar corridor dake gaban dakin da nake kwance a ciki,</p><p> Daga inda suke kukan yar jaririyar duk ya karade dakin har waje inda suke, zaune suna ji tankar a gurin take,</p><p> Da sauri ya fado dakin idon shivakan yan yaran da ke dunkuke a cikin zani,</p><p> Sai yanzu ya sauke idon shi akan yan jariran wa,yanda tunda aka haifesu bai sa su a ido ba sai yanzu,</p><p> A hannu tumba mai kukar take gudan kuma yana hannu matar kawu salihu,</p><p> Hannu ya mikawa Tumba alamar ta miko mai baby din,</p><p> Duk da mamakin da takeyi akan yai rashin kunya a gaban su zai zo yace abashi yar shi,</p><p> Yakarbi yar da bissimillah, Abin ,Al,ajabi gami da mamaki, sune suka lulube kowa adakin, </p><p> Don yarinyar na shiga hannu ubanta sai kawai tai shiru kamar wace akasawa nono abakin ta,</p><p> Kowa dakun sai da yai mamakun hakan, sai a lokacin yake karewa yar kallo wace tankar kaki yayi tafito,</p><p> Dan murmushi yayi wanda ba baiyanane ba, yadan dagata yai mata ikama kamar yadda addini yakoyar,</p><p> Sa kuma addu,an neman tsari daga kariyar duk wani sheri ko bala,i dai yai mata,</p><p> Ganin da yayi tayi barci sai ajiyar zuciya takeyi a cikin barcin yasa shi aje ta a saman dan gadon jarirai dake dakin,</p><p> Abin mamaki koda da jin ta saman katifa aiko sai ta tsala wani ihu saida kowa ya firgita,</p><p> A razane ya sureta ya hau girgizatadon ta koma barci, saida matar kawu ta karbe ta ta sata a baya,</p><p> Da namiin ya karba dafa hannu Tumba shi kan yana ta barcin shi hankali kwance, yai mai addau,a maka mancin wanda yai wa macen,</p><p> Dan motsawa nayi kadan sai nani muryan sheriff yana dan kiran suna na,</p><p> A hankali na dan ansa tea suka hada min saidai ba mai zafi ba kanar yadda likita yabada umurni,</p><p> A hankali yadan ta dani yabani kadan na kurba na koma na kwanta ,saboda barcin da ya rinjaye idona,</p><p> Kusan a zaune sheriff da su bashir suka kwana dan barci kadan sukayi, </p><p> Cikin ikon Allah sai naji sauki zuwa safe don da kaina natashi da niyar zuwa toilet,</p><p> Amma sai matar kawu ta kamani dan dan jirin da nake gani ,</p><p> Nai wanka nafito tsab dani nadan zauna a bakin gado nai tagumi sai a lokacin ido na yakai ga yaran da ke barcin su a hannun su Gwago matar kawu,</p><p> Kofar dakin aka turo a lokacin sheriff ne tare da su Doctor kamal wanda yai farin cikin ganin yadda nai saurin samun sauki,</p><p> Bayan yan aune aune sai doctor ke tambayar lafiyan yaran ida aka sheda mai cewa lafiya lau suke,</p><p> Waau magani yarubuta yace asiyo su ai min allura,</p><p> Annan ne yake mun sallamar cewa shi zaitafi, zai koma saudiya tunda na rike mai abikin tafiyar shi,</p><p> Dan murmushi nayi da ga kwancen da nake nace mai Allah ya kai ahi lafiya nagode,</p><p> Sai tumba ce take ce mai a,a diyan ku dai ne sukari ke shi,.</p><p> Sheriff na gefe yana jin mu sai wani dan murmushi yake yi,</p><p> Tare suka fita zuwa raka doctor zuwa airport don zuwa Abuja, tare da, Almustapha wanda zai koma shima dan cigaba da aiyukan su,</p><p><br /></p><p> Washegari da rana aka sallame mu zuea gida,</p><p> Alhmdullahi don naji sauki sosai a wanan lokacin,</p><p> Matsala ta guda shine bawa yara nono,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p> </p><p> ✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 8⃣8⃣</p><p> BY</p><p>🐎 *ZAINAB*IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p> </p><p><br /></p><p> Almost True Life Story,,,</p><p><br /></p><p> </p><p> Muhawara so sai akeyi a tsakanin Shehi da kawu, akan cewa sai su wuce da ni da yara,</p><p> Inda kawu yace sam ba,zai yiyu ba sai dai kawai, </p><p> Su barni a nan har yara suyi kwari tukun, Sheriff a zuciyar shi ko haihuwar da nayi a dogon daji baiso ba sam,</p><p> Amma da yake mutum ne mai saurin tawakkali ga ubangiji sai yai tuna nen cewa aiko ni a garin aka haife ni har kuma na girma cikin koshin lafiya,</p><p> Wanan tunanen yasa shi ya kawai da duk wani damuwa da fargaba dake cin zuciyar shi tun farko,</p><p> Shiyasa ko yanzu da ake wanan muhawarar bai ce komai ba sai dan murmushin da yakeyi dan ganin manya na ta takkadama atsakanin su,</p><p> Ajiyan zuciya yasaukar a hankali tare da kara gyara zaman shi, yana mai murmusawa kawai,</p><p> Yadanyi gyarar murya yace cikin muryan tashi mai taushi, </p><p> Malam nima naso a ce natafi da su kodan in kai fadima asibiti dan akara diba min lafiyar su acan,</p><p> Amma tunda kawo ya nuna cewa yafi son abarsu a nan din ba matsala, sai mutafi kawai mubar su har zuwa lokacin da za,a bamu su mutafi,</p><p> Ya juya inda Bashir ke zaune yace sai kayi duk wani shiri da yakamata ai masu kafin mu wuce, </p><p> Musa da ke gefe guda zaune kara kwalalo idon shi yayi waje,</p><p> Yace a zuciyar shi watau dai wanan mutumin ba karamin mutum bane ,</p><p> Bama shine zai tsaya shirya komai ba wai sawa kawai zaiyi ai mai, hmm lalai, </p><p> Mikewa sheriff yayi daniyar shiga cikin gidan Inna dan yai sallama da mu, </p><p> Hakan yai daidai da zuwan maigari, </p><p> Cikin girmamawa yagaida maigari yadan samu wuri gefe guda ya zauna cikin ladabi,</p><p> Saboda duk irin wa yan nan abubuwa yau sun zama mai bakon al,amari saboda ba sabawa da shiga mutane haka yayi ba,</p><p> Maigari ne yai yar gyarar murya a lokaci guda </p><p> Yafara da sallama irin ta addinin musulunci,</p><p> Inda maigari ya ce wa kawu da shehi, duk suyi hakuri ga sabanin fahintar da basusyi wa juna ba,</p><p> Nan maigari yai makowan su bayanin cikin kyakyawan fahinta ta yadda kowa zai fahinci uzurin dan uwa,</p><p> Maigari yakare zance da bawa kawu salihu hakkuri akan ya bari kawai su wuce da italin su,</p><p> Saboda yanzu sun fi su iko akan su, sosai, ka ga cewa wai ta tsaya har yara suyi wayo duk bai taso ba,</p><p> Tunda can asibiti ne zasu kai su akara diba lafiyan su dakyau, kabari kawai su tafi da abin su,</p><p> Jin bayanin maigari yasa kowa dake gurin shiga cikin natsuwa a,lokacin,</p><p> Dole badon kawu yaso ba ya hakkure da zancen tafiya da mu, </p><p> Duk da bani isa,shen lokaci yake da shi ba hakan bai hana yace abari da safe tunda rana ta yi yanzu ,</p><p> Zuwa lokacin kuma yana ganin duk mun gama shirin da zamu yi,</p><p> A haka taron yawatse, alokacin a kan zamu tafi da safe,</p><p> Kawu salihu ya shigo cikin gida yana bawa inna labarin duk yadda zancen ya kasance a waje ,</p><p> Dakuma akarshe an yake cewa zasu tafi da ni da yara,</p><p> Inna tace ai ba matsala Allah yasa hakan shine alheri agare mu,</p><p> Allah kuma ya raya yara yasa masu albarka arayuwar su,</p><p> A gagauce aka fara shirin tafiyar mu, inda sheriff yace jirgi zamu bi zuwa Abuja ,</p><p> Jin cewa tare da ni za,a tafi yasa hankalina yadaga sosai saboda a gaskiya bazan son tafiya inbar mahaifiyata cikin wanan halin ba,</p><p> In koma cikin daular duniya ita ko tana cikin wanan kangin rayuwa a halce,</p><p> Jin bayanin da kawu yai min ne ta karshe da yace gobe zan koma gidan miji na kamar yadda suka bukata,</p><p> Jikina a mace nadan mike daga zaman gurfanan danayi ina mai kallon kawu salihu nace, agakiya kawu ni bazan tafi tare da su ba a yanzu </p><p> Kawu ya katse ni da fadin saboda may fadima ai an riga an gama zance ko ,bawai shawar ki nazo nema ba ina fada maki abinda aka zantar ne kawai,</p><p> A tsorace na karasa mikewa tsaye na ce cikin murya dishi,dishi, </p><p> Inna kiyi hakkuri wallahi,,,,</p><p> Ban karasa ba Inna tai sauri ce min fadima ai kinji abinda kawun ki yace maki ko umurni aka baki akan ki shirya kutafi da mijinki,</p><p> Jin kalamar Inna yasani tsayawa tsaye sororo sai kawai naji wani hawaye na zubo min </p><p> Duk hankali na yata shi sai tunane nakeyi taya zan koma dauke da yara har biyu haka ba kwari kuma ni kadai sai kace wata mara galihu,</p><p> Kawu ya tashi yafita zuwa gida dan ya dan lalubo abinda zai ba mu,</p><p> Anan ne kuma shehi yatare shi yana fada mai cewa suna son su san koda suwa zan tafi,</p><p> Indan kuma saidaga baya za su biyo ni to, kawu salihu yace bari ya koma cikin gida don sukara shawara tukun,</p><p> Ko da kawu ya shigo yasamau ni cikin tashin hankali ina ta kukan akan cewa bazan tafi ba,</p><p> Shawar da kawu ya kawo ne yasa nadan tsagaita kukan nawa dan ji koda suwa zamu tafi,</p><p> Inna da kawu suka yanke shawar a tafi da daya daga cikin matar maigari sai kuma gwago matar kawu,</p><p> Ina jin haka nacewa innar mu gadkiya da mariya zan tafi, </p><p> Sai inna tace anyi yawa kada suga rashin hankalin mu ,</p><p> Wani sabon kuka nasa alokacin, mariya ma wace ke zaune dauke dan jariri a hannu ta tasa kuka,</p><p> Sai kusan zuwa yamma sheriff ya shigo cikn gidan mu,</p><p> Kaina na,duke kasa a lokacin har suka gaisa da matat kawu mu,</p><p> Ta fita dakin ta barni nida shi sai mariya dake kokarin gyara min kayana,</p><p> Kallon mariya yayi sai ya lura daga ni har ita babu wanda ke cikin walwala, </p><p> Ya dan tako har inda nake zaune ga wani kwano ancika min shi da kunun kanwa sai kamshin kayan yaji ke tashi,</p><p> Ganin shi duke yana karewa kunun kallo yasa nadan daga kai na kalle shi,</p><p> Yai daidai da dagowar shi da ga tsugunin da yayi,yakarewa irin kunun da nake sha kallo,</p><p> Ido muka hada kawai sai nakawar danawa cikin sauri,</p><p> Cikin sanyin murya yace min bakya iya sha ko kai nagirgiza mai ,alamar zan iya mana,</p><p> Sai ya juya gurin mariya yace ma mariya idan mutafi can ashe kece zaki dinga yi mata wanan din ko,</p><p> Da sauri na kalleshi murya na min rawa na ce wai bada ita zamu, ba,</p><p> Cikin alamar tambaya yace saboda may baza,a da maman babies ba,</p><p> Ya ce haba no,no no yakamata inna tayi hakkuri a tafi da ke mana,</p><p> Yunkuwa yayi ya mike gaba daya yana fadi tare da ke zamu tafi gobe insha Allah ,</p><p> Sai a lokacin nadan yi murmushi tun zuwan sheriff dogon daji, </p><p> Ido ya zuba min yana nazarin irin son da muke wa juna nida mariya,</p><p> Dan ina jin cewa da mariya zamu tafi gashi har yaga murmushi a fuska,na,</p><p> Fuskan da tun da yazo garin yake daure kamar wace akaiwa mugun, sako,</p><p> Yana mikewa yace min zanbar wa inna da maigari kudi suyi bukin sunan su a nan duk yadda yakamata,</p><p> Sanan zuwa suna zan sa a shirya wasu suzo gurin mu dan ayi suna dasu,</p><p> Ya miko min wasu kudi yace in baiwa inna tayi nata taron sunan a nan yadda al,adar mu ya tanada,</p><p> Gaba daya sai jikina yai sanyi so sai dan ganin irin yadda sheriff ke kokarin ganin ya farautawa yan uwa na rai,</p><p> Musanman mahaifiyata wace ke cike da kewa ta da kuma zullumin rabuwa da ni ko wani lokaci,,</p><p> Dan murmushi yayi yaja baya yace ki karba ba wani abu yasa nabata ba sai dan kawai ta yi wanan hidimar dasu,</p><p> Har yafita dakin ina nan yadda yabarni, cikin zulumi da kuma jimamay yadda abubuwan zasu kaya muna,</p><p> Bakaramin kokari maigari yai muna ba a,wanan tafiyar namu gaskiya dan harda dan rakiya ya hada mu dashi namiji wanda zaije ya ga garin su Sheriff, da yan uwan shi,</p><p> Kawu ya kawo ma su sheriff tsaraba zuma don itace sana,ar shi pure one har gora biyu,,</p><p> Kilishi mai yawa da shi da maigari suka basu tsarabar shi,</p><p> Sai kuma dakuwar ayya da fura da nono tsaraba irin ya yan kauye shi akaiwa su sheriff,</p><p> Aisha ce ke wasa da wani tsohon photo a hannu ta a cikin akwatin karfe inna ta dauko shi lokacin da inna ke fitar min da,wasu yan zoben azurfa tace in sa wa a hannun su,</p><p> Har waje Aisha ta fita da photo a hannunta tana ta wasa dashi, gurin sheriff taje ta zauna a jikin shi, </p><p> Karban photo yayi kura mai ido, yana kallo har wani lokaci, kamar may son ya gane wani abu aciki,</p><p> Gefe yadan aje photon daniyar ya dan gyara Aisha da ta zauna mai,</p><p> Sai sheriff ya mika hannu ya dauki photo ai tun bai karasa kallo ba yadan mike dan mamaki,</p><p> Saboda shi dai yasan cewa iyasanin sa baizo da nashi photo nan garin ba, to ina wanan yafito,</p><p> Cikin mamaki yake kallon photo ya ce wanan ai photo dan uwa nane </p><p> Da mamaki sheriff ke kallon shi yana jin abinda shehi ke fadi kamar al,mara,</p><p> Sheriff ya nemi jin bayani gurin shehi nan yai mai bayanin cewa, Photo shine shida kanin shi, lokacin da suna yara amma dai dan uwar nashi yabar gida har yau basu da labarin shi,,</p><p> Wata sabuwa dan sai yanzu yake tuna zan cen inna a asibitin sokoto inda take mai godiyar jin da yaba fadima tace mai ai jin su yanada wuyar samu dan hakana mahaifin su yayi da yayi accident sai, akai bidan jinin da zaa kara mai ba,a samu ba har Allah ya karbi ran shi,</p><p> Zubur ya mike ya na mai fidda kwalla a idon shi yace, </p><p> Tabbas wanan dan uwan shi ganin shehi da gaske yakeyi yasa su duk zuwa gurin mai gari,</p><p> Bayanin tun zowar su mahaifin fadima garin zuwa sayen fata da suke har takai shi da zama garin,</p><p> Shehi yace watau Dangiwa mai fata shine ya wuto masu da dan uwa har nan, amma akayi ne man shi akarasa kuma bai fada masu cewa yana tare da shi suna sana,ar jima,ba alokacin,</p><p> Nan wani sabon kuka yazo wa yan family mu dan kukan murna da farin ciki a lokaci guda,</p><p> Yau gori ya karewa hafsi a gidan mijin ta dan duk inda fada ya hada ta da yan gidan sai suce ai ita ba,a san asalin su ba </p><p> Mahaifinta yawon duniya yazo yi har ya auri yar kulu a lokacin, </p><p> Kuma ai kwadai yasa inna ta auri bako dan tagan shi mai sana,a ne,bai noma,</p><p> Kafin ace haka labari yafara karade gari cewa dangin mahaifin su fadima yazo an gane shi,</p><p> Shehi yai kuka sosai don jin cewa dan uwanshi ya rasu ya fada masu irin gatan da mahaifin mu ke ciki amma rana guda aka nemay shi aka rasa,</p><p> Murna a cikin murna ke nan a gurin innar mu dan ba karamin dadin hakan yai mata,</p><p> Ba dan gori da hattara yaranta sun ji shi ga jama,ar gari so sai wallahi,</p><p> Hira akayi so sai tsakanin mu da malam.shehi ko in ce wan mahaifin mu ,</p><p> Inda ya jajanta mu na rasuwar mahaifin mu,</p><p> Yakuma ya ci gaba da muna nasihar rayuwa,</p><p> Yace ya jin jina ma irin rayuwar da inna tayi da mu shiyasa ake cewa amana tana hannu hagun mutum,</p><p> Gaskiya gaskiya tana nan a damarka da sune mutum zai tsalake siradi ranar lahira,</p><p> Haka nan idan baka da dasu koda kataba tsamanin zakaci ribar rayuwar duniyar da ta lahira,</p><p> Yakare da cewa ina mai jinjina maku tare da mahaifiyar ku wace ta iya rike gaskiya da amanar ku,</p><p> Duk munyi shiru mun natsu muna sauraren nasihar da Shehi ke muna,</p><p> Yace yau gaskiya da amana yasa duk kun kai ga samun nasarar rayuwar ku,</p><p> Haka akai wani lokaci cikin kulawa da kuma kara kaunar junan mu,,,</p><p> Tunda safe motocin da sheriff yazo dasu suka Parker kofar gidan inna akai masu loading tafiya inda mu da su gwago da matar maigari zamu bi jirgi zuwa Abuja,</p><p> Cikin irin shigar da nasaba yi a saudiya yau shine a jikina ,</p><p> Yan kauyen mu sun fito tab dan yi min fatar alheri da kuma kara taya mu farin ciki,</p><p> Tun cikin dare innar mu tai ta min nasiha ajan zaman duniya da kuma koyi da sunnan ma,aiki, S A S W,</p><p> Harda maigari wanda yake min kamar uba cikin masuyi mun rakiya zuwa airports,</p><p> Karfe sha biyun rana har angama muna checking din komai mun shiga motocin da za su kai mu Maitama gidan Sheriff,</p><p> </p><p> </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 8⃣9⃣</p><p> BY</p><p>🐎 *ZAINAB**IDRIS**MAKAWA*🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost True Llife Story,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Mota guda muka,shiga nida sheriff sai kuma wata doguwar mota mai kama da kifin ruwa, ita su gwago da matar maigari suka shiga </p><p> Mariya da yaran suna tare da,su,</p><p> Kusan tun ranan da sheriff yazo kasar mu ban mutaba kebewa ba sai yau,</p><p> Driver na tada mota alamar zamu bar airport din ke nan sai kawai naji sheriff yadan lalubo hannu na,</p><p> Ya danke cikin nasa gami da sauke wani irin ajiyar zuciya,</p><p> Yace min fadima kiyi hakkuri ki daina wahal da rayuwar mu hakana pls,</p><p> Sai naji jikina yai sanyi da kalaman shi, sai naji kawai ya bani tausayi,</p><p> Dan gaskiya sheriff bai can canci haka ba daga gareni,idan har nai la,akari da irin taimakon da sheriff yai min a,rayuwa ta,</p><p> Musan man wanan na karshen da yai min nataimako akan inna ta, wacce nafi damuwa da al,amarinta,</p><p> Ban san lokacin da na dan kwantar da kafada na saman nashi ba, ina mai a,jiyar zuciya,</p><p> Dan kokarin kallon fuskana yayi a lokacin, sai yaga hawaye nakeyi kawai, </p><p> Dan murmushi yayi yace min may kuma na kuka yanzu tunda ga ki gani ni nai maki alkawarin ba, Aziza ba kowani irin ma,sherancin abu bazai kara zuwa kusa da ke ba,</p><p> Kaina yana a kafadar shi still ina dan she,shekar kukana </p><p> Nadan dago kaina ina mai kallon shi cikin murya maiban tausayi na ce mai amma dai ba zaka kara barin mu zauna guri guda da ita badai ko,</p><p> Batare da ya juyo ya kalleni ba yace min kin riga dai kin tsorace da al,amarin Aziza ne kawai ba abinda da zata iya yi maki,</p><p> Kara narkewa nayi a jikin shi kamar zan shige mai, kaina na saman kafadar shi still nace ba tsoro bane,</p><p> Kawai dai ina tsoron ta rabani da mijina ne kawai, uban diya na,</p><p> Shiru yayi bai ce min komai ba a lokacin saidai yar sautin murmushi, shi dana ji,</p><p> Ashe har mun,kawo gidan nashi na maitama ban sani ba,</p><p> Jin muryan masu gadin gidan dake muna sannu da zuwa ne yasani gane cewa mun shigo gidan ko,</p><p> Badon naso ba nadaga da kafadar sheriff ina mai gyara Mayafin kaina da kyau, ta yadda ba za,a iya gane fuskata ba sosai,</p><p> Gidane na gani tsantsarare ginan zamani don tsaywa musalin shi zai bata min lokaci ,hawa guda ne,</p><p> Sama da kasa kawai, amma fadin gidan yakai wani tsayi mai tsawo gaskiya,</p><p> Yadan kalle ni bayan yasan cewa na zauna da kyau a sit din yace ina fatan ginar gidan zai maku,</p><p> Idan akwai abinda bai maki ba sai kiyi min bayani in sa a gyara maku,</p><p> Cikin mamaki na bude baki da zumar in mai godiya sai kawai yasa yar yatsar shi a bakin shi ya ce min shiiiiiiiiiii alamar inyi shiru,</p><p> Dole na rufe bakina ba shiri tunda an hana ni furta komai,</p><p> Kofar motar a ka bude muna, a lokaci guda, mukafito, daga ciki,</p><p> Yan officer din su ne na nan Abuja suka zo tariyar mu da kuma taya ogan su samun karuwa,</p><p> A hankali nake takawa kamar maijin tsoron kasa bakina fam da duk wani addu an da yakamata in yi a lokacin,</p><p> Sai kallo nakeyi yadda Naira ya sha kashi anan, a gaskiya na tsinke da al,amarin sosai sai naga kamar wanan ginan duk ya cuna ma gidajen Sheriff,</p><p> Wanan irin ginan na sheriff ya tamfsa abin abin kallo ne gaskiya, </p><p> Sai a yanzu na tuna cewa su gwago da yaran basu karaso ba, dan haka dan dakatawa nayi dan su iso mushiga gabadayan mu,</p><p> Isowar su naci gaba da tafiyana a hankali suna biye dani rungumay da yaran a jikin su,</p><p> Sheriff yadan tsaya nisa dani kadan yana muna wani irin kallo cikin so da kauna,</p><p> Don ji yake tamkar a lokacin ya rungumay ni don wani irin so da sha,awar mu dayake ji kamar ransa zai fita don so na da yaran,</p><p> Azuciyan shi mamaki yakeyi waiyau shine keda wanan baiwar na diya biyu a lokaci guda,</p><p> Ya lumshe idon shi yadan karasa takowa muka shige cikin gidan atare dashi lokaci guda,</p><p> Sai da nakarewa ko ina kallo da ido tunkun na sai nadan waigo nakalli inda sheriff yake tsaye ,</p><p> Alamar godiya nai mai da ido ta yadda bakowane zai fahinci may mukayi wa juna ba,</p><p> Duk a falo muka sauke yar gajiyar mu inda masu aiki suka gabatar muna da abinci,</p><p> Ganin su gwago a gajiye suke yasa shi yi min magana cikin harshen larabci, ya zai tafi yaga inda yakamata mu sauke bakin mu, kai kawai na gyada mai,</p><p> Sai a lokacin su gwago suka dan sake jikin su suka fara mamakin irin abincin da aga jib ga agaban mu, wai mu kadai,</p><p> Hassan nai yai dan motsi wanda ke ta faman barci tun a jirgi, gwago ta miko minshi wai in bashi nono yasha,</p><p> Saida gabana yafadi a lokacin, </p><p> Sai nace mata barin da kewaya kafin in zauna tare da mariya muka shiga daya daga cikkn dakunar da ke kasan ,nadan zagaya ban daki, dan inji dadin zama,</p><p> Dakin ba laifi dan haka muka zauna ciki dayani nida mariya,</p><p> Ganin nafito daga bayi yasa mariya fita dan ta dauko min hassan din kusan a kofar dakin suka hadu da gwagon mu,matar kawu dauke da hassan wanda ke ta faman mutsitsiri a cikin showell</p><p> Mikon min shi gwago tayi ,daniyar inba shi nonon </p><p> Baki na turo dan in akwai abinda banson ji yanzu shine ace yaran zasu sha nono,</p><p> Dan har ga Allah bana son jin wanan bada nono da gwago ke damuna dashi,</p><p> Muryan gwago naji tana cewa , oh ni Salamatu kun gamin yarinya </p><p> Nafa lura da take taken ki sarai bakya son jin zancan shan nono,</p><p> Indan baki badu nono suka koshi ba may kike son aba su </p><p> Bayan ga abincin su Allah ya hore masu wadataccen nono bawai babu ba,</p><p> Baki nakara turo idona yai ja kamar may shirin yin kuka,</p><p> Gwago ce ta gyara min yadda zan rike yaron da kyau dan yaji dadin shan nono,</p><p> Daidai na daga riga na kenan zan sawa yaron nono a baki sheriff ya shigo dakin da sallamar shi,</p><p> Cikin sauri na sake rigar ina mai gyarawa sa kyau dan kada yaganar min nono na,</p><p> Gwago dake tsaye sai abin yabata mamaki tace shin wai mi kika nuhi na fadima,</p><p> Yaro najin yunwa kuma ke bi nono duk kin lulubi shi rub,</p><p> Wani mugun haushi gwago tabani alokacin ya take son inyi, agaban sheriff take son in bude nono ko kuwa may take nufi,</p><p> Cikin mamaki yake kallon mu tsakanin ni da gwago dan jin may ke faruwa,</p><p> Yadai daure yana kallon gwago yace ko madara za ,a sai masu ne,</p><p> Cikin sauri gwago tace a,a wallah, mizai sa atai zuwa sayen madara bayan wanga da Allah yabba su, ya wadatar da suwa,</p><p> Gwago tace yanzu kam dai ai ga uban su nan in kin gadama sai ki yi wadda zakiyi, </p><p> Tasa kai tafita dakin tana fada so sai dani, ina ganin tafita nai wani ajiyar zuciya kamar wace aka cirewa kaya alokacin,</p><p> Yaron yaci gaba da tsala ihu sosai ,</p><p> Cikin sauri sheriff yakaraso inda muke yace haba dai abashi nono yasha mana,</p><p> Ki daure ki bashi nasan ba dadi amma pls kiyi hakkuri ki basu abincin su ,</p><p> Cikin jin kuya ga kuma idona har sun kawo kwalla alokacin,</p><p> Nadan daga rigana kadan natura wa yaron nono, abaki,,</p><p> Ganin cewa yaron ba iya kama nonon zaiyi ba ni kuma bawai na iya bane gashi kuma gwago tayi fushi tafita,</p><p> Yasa sheriff ya gyara daga rigar nawa sama da kyau yace bari kiga yadda akeyi,</p><p> Cikin jin kunya nai sauri kama rigar da niyar in gyara rufewada sauri ya kamo nono yaturawa yaron abaki nan da nan yakama yafara tsotso, yana wani ajiyar zuciya,,,</p><p> Wani irin masifar zafi nake ji lokacin da yaron ke ta zukar nonon,</p><p> Ban san lokacin da na fara rintse idona ba saboda wani irin masifa da nake ji,</p><p> Da zafin yai min yawa ai ban san lokacin da nakai kwance saman jikin sheriff ba ina wani irin dan ihun zafi,</p><p> Wani reaction yaji a jikin shi lokacin kamar an mai wani, shock, yaji,</p><p> A haka har yaron ya koshi ya sake nonon da kan shi, ganin yaron yai barci ya sake nonon yasa sheriff ya dan kwantar da yaron a gefe guda,</p><p> Ji kawai nayi sheriff ya rungumoni so sai zuwa jikin shi,</p><p> Kasan cewar mundade hakan bai faru ba a tsakanin mu yasa na kyale shi,</p><p> Fuskan shi ya yi kokarin hadawa da nawa, mukai ido hudu lokaci guda,</p><p> Sai naga yai yar murmushi kawai yakau da kan, shi gefe guda,</p><p> Daurewa nayi dan nasan cewa shaukin so ke diban shi a lokacin,</p><p> Sai nasa hannu na a fuskan shi nadan shafo fuskar a hankali sai naji yai yar ajiyar zuciya,</p><p> Sajen fuskan shi nadan kama shafawa a hankali cikin murya mai taushi na ce mai</p><p> Kayi hakkuri da abinda nai ma ka yafe min pls bazan kara yin wani abu batare da sanin kaba in sha Allah,</p><p> Bai iya maganana ba alokacin kuma bai iya hanani ba dan saboda ji yakeyi kamar yau ne farkon fara kebewar shi da mace a duniyar nan sai yadinga ji dama a haka zasuyi tazama daga shi sai fadima da yan diyan su,,,</p><p> Karar wayan shi ya dakatar da shi daga tunanen da yakeyi a lokacin,</p><p> Ganin mai kiranshi a wanan lokacin yasa shi yadan, mike zaune da sauri yana mai man,na wayar shi a kunnen shi,</p><p> Cikin girmawa yake ansa mai tankar yana ganin shi a fili,</p><p> Bayan sun gaisa da Abban yake tambayar shi ko har yanzu yana garin namu ne,</p><p> Ya ansa mai da a,a mun dawo Abuja yau din nan, Alhaji,Lawal Zanna yakara tambayar shi msi haihuwar fa ya ansa mai cikin ladabi yace har da su,</p><p> Hamdallah Abban yayi da yaji hakan, ya cigaba da fadawa sheriff' cewa hjy tsohuwa ta tayar masu da hankali, akan cewa sai taje garin da yaran suke ta gane su da idon ta,</p><p> Yar dariya yayi yace zankira gida akai mata waya muyi magana da ita duk yadda mukayi zan kira in fada ma</p><p> Sukayi sallama da Abba din lokacin sheriff yadan mike zaune da kyau yabini da kallo dai dai lokacin da nake kokarin gyara daurin dankwalin kaina,</p><p> Yace cikin larabci hjy tsohuwa tana son dauko mai wata sabuwar rigima kuma,</p><p> Murmushi kawai nayi dan nasan kowaye hjy tsohuwa na kuma san fitinar ta sosai,</p><p> Bayanin yadda tsarin dakunan gidan suke sheriff yai min inda yace min,</p><p> Zamubar wa su gwago da sauran baki dakunar kasa inda dani dashi zamu zauna cikin dakunar dake sama,</p><p> Dan haka idan motar kayan mu sun iso sai asan inda za akaiwa kowa kayan shi,</p><p> Yadda yai min bayani naiwa su gwago amma sai suka su dai abar su suzauna daki guda ya ishe su,</p><p> Mariya da Aisha kuma suka zabi guda su ma, inda zasu zauna, ciki, duk da na so Aisha tazo mu hau sama tare amma kuma saina kada abar mariya ita kadai </p><p> Mamaki kawai mukeyi irin wanan gidan da sheriff ya kwankwatsa acikin Abuja,</p><p> Dagani Naira tasha kashi so sai, agurin, dan irin gida haka kai kasan sai wani da wani,</p><p> Don a gaskiya yafi na saudiya tsaruwa sosai, dan komai na gidan abin kallo ne, sabo new murder ne aka zuba ciki,</p><p> Sai kusan la,asar masu motocin mu suka iso, garin Abuja bisa jagirancin Bashir,</p><p> Wanda dama duk wani al,amarin sheriff a hannun bashir din yake, kusan kowa yasan wanan tundaga gida har ma,aikatar su,</p><p> Abin mamaki sai ganin malam Basiru nayi cikin matafiya, ana shigo da kayan mu sai gashi,</p><p> Ina zaune falo yazo ya zauna kasa gefe na yace hjy barka da gida mun samay ku lafiya ko ,</p><p> Duk kan mu munyi mamakin ganishi tare da su </p><p> Gwagoce mai kokarin tambayar shi tafiyar harda shine daman za a zo tafiyan murmushi kawai yai mata,</p><p> Ya ce ai daga bayane aka yanke, tafiya da shi saboda yazo yaga gurin da muke dan masu zowa sunna,</p><p> Duk yadda yakamata aiwa bako haka nasa aiwa bashir saboda a gaskiya tausayi yake bani sosai,</p><p> Nasan shi tun ina yar karama yana da kirki, matar shi kuma yar uwar su Gajiye ce, ,</p><p> Duk gida ya kici may da baki yau kala kala, don kusan kowa na gidan yau ne farkon zuwan mu wanan tankamaymay gidan na sheriff </p><p> </p><p> Duk wani kulawa a gaskiya su gwago da matar maigari suna iya kokarin su wajen kula da lafiyana da na yan yaran,</p><p> Duk da yaran bawa ni fitina ke gare su ba ko dayaushe cikin barci suke,</p><p> Tun ranar da mukazo da yamma, Sheriff ya wuce gidan nafisa dan acan zai kwana, </p><p> Sai a,lokacin yake sheda mata zancen haihuwa na,</p><p> Tadai yi kokari ta danne kishin ta kamar yadda mahaifiyar ta ta umurce ta tayi kokari nunawa sheriff jin dadinta so sai na samun wanan karuwar da akayi,</p><p> Har take tambayar shi yau she zata tafi sokoto, ta dibo yaran, </p><p> Yace mata ai yaran da uwar duk suna nan cikin Abuja </p><p> Tayi mamakin jin cewa muna cikin garin kuma ba,a gidanta ba,</p><p> Sheriff yace mata muna maitama, gidan shi na can, </p><p> Cikin zaro ido take ce mai a sabon gidan shi zamu zauna ke nan,</p><p> Yabata ansa da eh dama saboda mu yagina shi dan kada muzo Nigeria bamu da gurin sauka,</p><p> Duk yadda taso ta taushi zuciyar ta ta kasa wanan karon kuka ta samai sosai akan cewa bai mata adalci ba dan itace yakamata ace ta koma can in yaso mu sai mu dawo nan inda take,</p><p> Da mamaki yake kallonta don tayi mugun bashi mamaki sosai saboda abinda tace </p><p> Azuciyar shi yace shin ko batasan matsayin fadima agurin shi bane da har zata furta wanan kalamin,</p><p> Shi wanan gidan damay yafi wancan da zata ce wai itace ya dace tashige,</p><p> Ganin idan har ya tsaya sauraren ta ranshi zaifi nan baci, yasa shi shigewa dakin shi yabarta nan tana kukan bacin rai,</p><p> Maman ta takira tai mata bayanin duk yadda sukayi dashi,</p><p> Uwar tace Nafisa ban san lokacin da zakiyi wayau ba shin wai har kin manta yadda muka samu kika koma gidan shi ,ko,</p><p> Fada sosai mahaifiyarta tai mata kuma taja mata kunne akan ta tabbatar da ta tafi, ganin yaran da aka haifar mai dan haka zai sa yadan wanke zargin da yake mata,</p><p> Haka ko akayi dan washegari, ya shirya musalin karfe tara na safe da ganin shi tasan cewa can zai tafi,</p><p> Dai steps din din karshe take ce mai ai mata kwatancen gidan don taje ta dibo yaran,</p><p> Kallon mamaki yai mata tare da zargin wani abu daga gareta dan haka yace mata tabarshi kawai basai ta tafi ba ,</p><p> Tagane nufin shi amma sai tace indai dan abinda yafaru ne jiya dan Allah ya yi hakkuri aikin shedan ne, insha Allah bazata kara maka mancin haka ba,</p><p> Allah ya kyauta kawai yace yasa kai yafita inda Bashir ke jiran shi awaje,</p><p> Har sun dan fara hanya kiran Amal ya shigo a wayar sheriff bayan sun gaisa ne Amal ta tambaye shi lafiyan mu sai kuma tace mai ga hjy tsohuwa da ma itace ke son magana da shi,,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE. MAKAWA🐎</p><p>👏👏👏👏👏👏👏👏</p><p> ✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 9⃣0⃣</p><p><br /></p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost True Life Story,,,</p><p><br /></p><p>Muryan hjy yake saurare yana murmushi kawai dan yasan cewa wani sabon fitina take son kirkirowa kawai,</p><p> Jin yai shiru yasa hjy ta tambaye shi ko yakashe wayar ne cikin harshen kanuri take tambayar shi,</p><p> Cikin sauri yace ina sauraren ki hjy ina jiran ki gamane </p><p> Sai kuma ta fara kuka kamar kulun tana kwararo mai addu,a tana mai sa mai albarka, da neman mai tsari a,rayuwar shi,</p><p> Jin kukan zai kashe mai zuciya yasa shi saurin kashe wayan,</p><p> Ya lunshi idanun shi a hankali, tare da ajiyar zuciya </p><p> Can bude idon yana kallon shimfidaden titin da suke tafiya akai,</p><p> Bashir ne ya ce mai tazo dawani sabon zance ko,</p><p> Hmmm kawai sheriff ya ce mai yace ban ma santa inda zan fara wanan zancen ba ,</p><p> Yadan juya inda Bashir ke zaune yana jan mota yace </p><p> Wai akawo ta Abuja taga yara, dan tana son ta zauna da su,</p><p> Bashir yace aina san za,arina wallahi wai waya fada mata, aida sai an yi sunna kawai a fada mata,</p><p> Ido kawai sheriff ya lunshe yana murshin jin kalaman Bashir, </p><p> Dan daga shi har Bashir din kowa yasan halin hjy tsohuwa,</p><p> Kawai shi fatan ako dayau she yasa mu su rabu lafiya da yar tsuhuwar duk shima yasan cewa duk cikin jiko kin ta, tafi ji da shi,</p><p> Idan kuma har ya furta cewa kada tazo gaskiya komai ma zai iya faruwa </p><p> Shiko bazai so ace ansamu wani akasi daga gare shi ba,</p><p> Dariya Bashir yai mai yana mai cewa rigimaman mata kawai duk fitina take bida,</p><p> Daidai lokacin yakarya kwanar shiga gidan mu ya ce wa sheriff ka shereta kawai idan ta, tambaya kace mata ni ne naki zuwa dauko ta,</p><p> A lokacin aka wagale masu get din gidan, mlm Basiru da ke zaune waje saman wata farar kujerar rubo ya taso zuwa inda suka Parker motar su dan ya bude masu kofa,</p><p> Bashir ya cewa sheriff wanan mutumin wallahi tausayi yake bani so sai ,</p><p> Batare da sheriff yabashi duk ansar maganan shi ya bude kofar motar ya fita, zuwa cikin gida_</p><p> </p><p> Zaune nake a kasan carpet tsakiyar dakina, ina shan perpper soup din kan rago wanda yasha kayan yaji,</p><p> Sai kunun kanwa wanda gwago ta dama min ,yar aikin gidan ce tagwadawa gwago yadda zatai amfani da gas din duk da haka gwago bata yarda ba saida ruwa yai zafi aka bata ta dama min tana ta mamaki,</p><p> Yar aiki wata Bunufiya ce badai za,ace mata tsohuwa ba matar, </p><p> Saidai gaskiya tana da kirki so sai ga ladabi kamar may, dan har kasa take rusun,nawa mutum,</p><p> </p><p> Yau atamfa ce a jikina cikin wanda salimat ta dinko min a sokoto, </p><p> Atamfar ja ce sai fararen flowers da akaimata hade dan kallan kore mai haske,</p><p> Zani da rigane dinkin ya karbi jikina so sai ya zauna min dan dagwas ajikina,</p><p> Da sallama shigo dakin, dakin da keta kamshin turaen wuta mai dadi cikin wanda salimat taimin tanadi tun a saudiya , ne tace idan na haihu inyi amfani da shi,</p><p> Kamshin turen wutan da na room fresh ya hade da kuma dan karnin jego da duk yadda akayi sai andan ji shi,</p><p> Idon shi ya sauka a kan a miyar da ke gabana kamar wace akasa sha dole ashe ita dan dai tunda na haihu bakina gaskiya baida test ko kadan,</p><p> Gwagoce ta tursasa ni sai nasha shi,</p><p> Idon shi ya sauka a kaina daga inda yake tsaye a kofar dakin, yana min wani irin kallo,</p><p> Sai kunya duk ya kamanu a lokacin don tunda nake sheriff bai taba ganina hakaba don bantaba sa atamfa yagani ba,</p><p> Inda naje zaune yanufo yadan duka yana mai rage tsawon shi, </p><p> Alokacin nace mai inna kwana cikin wata irin murya mai kasala,</p><p> Hannu na dake dauke da cibin da nake shan pepper,soup yadanko yakai cibin da miyar abakin shi,</p><p> Dan danon kayan yaji yadaki harshen shi da sauri ya hade ,yadan kalleni cikin tsusayi sai ya mike tsaye zuwa wurin gado inda yaran ke kwance suna barci tun da su gwago sukai masu wankan safe suke wanan barcin,</p><p> Yai ma kowanin su addua, ya shafa masu sannan yajuyo yadawo inda nake zaune,</p><p> Cikin wata irin murya mai rauni yace min Fatima,</p><p> Sai naji duk wani irin kunyan shi ya kamani har nakasa koda motsawa in sha soup dina,</p><p> Shima din wani irin kallo yake min wanda har nakasa koda daga kai in kalli inda yake tsaye,</p><p> Ji yake yi duk wani kasala ta lulubeshi lokaci guda,</p><p> Fadima ce mace da duk duniya zai kalla yaji wani sha,awarsa ta motsa mai a lokaci guda,</p><p> Yarinyar da tun tana yar karama komai nata shawa take bashi saboda idan ka kalleta zakaga komai nata anmatashi dan dagwas zabban sha,awa, yadaure,</p><p> Yace Fadima, yana mai jawoni zuwa jikin shi ,jinayi yana mai sun,sunar wuya na har zuwa kaina,cikin wani irin sallo,</p><p> Fatima ni kadai nasan irin wahalar da rashinki kusa dani ya jawo mani, a gaskiya nasha wahala, daki ka wuto kika barni ni kadai, </p><p> Jin yace shi kadai yasa nadan daga kai nakalle shi, dan dai nasan cewa ga mahaifiyar shi da kuma yan uwan shi har da matar shi,</p><p> Ya ce yes of course, ina fatan bazaki kara bari na ba irin haka,na,</p><p> Mukasan ce atare har mutuwa insha Allah, barabuwa a tsakanin mu,</p><p> A hankali na furta mai insha Allah nima fatana kenan,</p><p> Cikin sauri yakara jawo ni ya manne ni gam ajikin shi yace may kikace,</p><p> Ganin yadda yanayin sheriff din ya sauya lokaci guda yasa wani irun tsoro ya bakunci zuciya,na,</p><p> Daganin shi yana cikin wata irin yanayi na muguwar sha,awa a lokacin</p><p> Jin da yayi bazan kara bashi ansa ba yasa kara dan matse ni kadan yana may lunshe idon shi yana wani sakin ajiyar zuciya,</p><p> Munkai wani dan lokaci a hakan can naji ya dan sasauta rikon da yai min yace,</p><p> Godiya ta, tabbata ga Allah Fatima har kullun ina may kara gode ma Allah ubangiji da yabani ke a matsayin matata kuma uwan 'ya'yana,</p><p> Ina mai gode ma Allah da duk irin baiwar da yai min na mallakar mace kamillah kamar ki ,</p><p> Jin wanan kalaman na sheriff yasa na kara narkewa a jikin shi ina mai jin dadin irin wanan yabon da yai min a lokaci guda,</p><p> </p><p> Saida naga cewa shetiff yadan samu natsuwa sai na dan zare jikina cikin nashi, a hankali daga rugumar da yai min wani irin ajiyar zuciya naji yayi a lokacin,</p><p> Tausayin sheriff yakamani so sai dan na tabatar da lalai yana tare da sha,awa sosa, kuma yana kewata dan kusan wata uku kenan yanzu rabon shi dani,</p><p> Yadan dade zaune a bakin gado na ,dafe da kan shi har zuwa wani lokaci,</p><p> Sai naga ya mike tsab daga inda yake zaune yadogo kai yakallr ni, </p><p> Idon shine suka kada sukayi jajir duk kasala ta sauko mai dakuma wata irin sha,awa,</p><p> yai hanyar fita waje, batare da yakara kallon inda nake ba,</p><p> Ido kawai nabishi da shi cikin tausayi da kuma fargaba,</p><p> Kamar mariya tana jiran yafitane ta shigo dakin tana ce min zasu tafi kasuwa ne da wata yar makwabciyar mu sheriff ne zai aike su,</p><p> Shiru nadan yi ina nazari can nace ma mariya ta kula da kanta to amma ya suka san cewa akai wata a makwabtar mu har zasu aike su,</p><p> Bankara ganin sheriff ba sai bayan sallar azahar ya shigo </p><p> Har zuwa lokacin su mariya basu dawo ba,bayan na gaishe shi cikin girmamawa </p><p> Sai kuma na,dan dukar da kaina kasa ina mai tambayar shi har yanzu su mariya basu dawo bane daga gurin aiken,?</p><p> Shiru yayi yana kallo na cikin mamaki yace ai bashi ya aike su ba,</p><p> Waya yazaro yana tambayar Bashir ,bashir din yace shiya aike su sayen wasu kayan mata da bai san masu kyau ba,</p><p> Amma yai waya dasu yanzu zasu dawo, don suna kan hanya,</p><p> </p><p> Sai bayan sallah magrib nakira wayar hjy umma muka gaisa natambayi lafiyar su dakuma su safiya,</p><p> Tace min duk lafiya suke, jin nai shiru batare da nai wani magana ba yasa,</p><p> Umma cewa kodai an hai hu ne fadima , shiru nayi kawai wanda yanuna mata cewa an haihu din,</p><p> Dan in kauda zancen umma na ko,karin tambayana sai ce mata nayi abani safiya,</p><p> Mamaki tayi wai ace cikin wanan zamanin ansamu mai kunya irin na mutanen da,</p><p> Bayan mun gaisa da safiya take tambayana ko may aka samu sai kawai naji ban iya fada mata,kai tsaye,</p><p> Amma dan tagane sai ce mata nayi ga sunan dai suna jiran zuwan ki,</p><p>Ke uwar su,</p><p> Cikin sauri da mamaki tace har guda nawa fadima nakara ce mata kizo ki gane su mana,</p><p> Inajin suna murna kamar a fili su je murmushi nayi dan jin dadin yadda suke kulani tamkar wata yar uwar su ta jini </p><p> Saida daga karshe nake sheda ma safiya cewa muna Abuja,</p><p> Tai wani tar karan murna tace min kina nufin dady babies yazo Nigeria, kenan,</p><p> Ina gama waya da su sai nakira Salimat nafada mata inda tai murna sosai danjin cewa na haihu </p><p> Itama dai tambayana tayi ko may na hai fa nace mata baby As,amau, dai tasa mu kan,ne ,</p><p> Ihun murna tayi tai ta hamdala ga Allah tace fadima dama na fada maki auren ki da Sheriff akawai wani baiwa da Allah yai ma wanan auren naku da sheriff,</p><p> Dariya kawai nakama yi mata dan jin taci gaba dayi min nasiha,</p><p> Rugaiyya, kan fada takama yi min akan gaskiya ban kyauta ace har kwana kusan hudu da haihuwa ban fada mataba sai yau take ji,</p><p> Nabata hakkuri tace min ita gaskiya tayi fushi saidai tazo dan sheriff da yaran shi amma badan ni ba,</p><p> Nace mata aiko hakan ma angode,ba laifi,indai har zaki zo din,,</p><p> Ita ko Amal tunda shehi yakoma madu da sabon labari take ta farin cikin kasancewar hakan </p><p> Tasan cewa ashe ba son banza muke wa junar mu ba ta alakace babba,</p><p> Duk da ba wani shakuwa mai karfi ke tsakani da sheriff ba tun farko, </p><p> Nasan cewa i,zuwa yanzu akwai fahitar juna so sai a tsakanin mu,</p><p> Wanda har yaka indan uwa na cikin wani hali zanan yau da gobe dole guda ya gane komay ke damun shi,</p><p> Kusan kwana ukun da mukayi a garin Abuja zan iya cewa akwai abinda ke damun Sheriffudeen din mu azuciyar shi sai dai yakasa furtawa,</p><p> Dan haka tunda dare na kulla araina cewa yau zan tunkare shi dan jin komay ke damun shi arai,</p><p> Kafin ya shigo gidan na tsantsara kwaliya irin na jan hanjalin maigida, tayadda bazai iya aiwatar da komai ba idan munyi ido biyu,</p><p> Hakako akayi dan cikin yar damuwar tashi yashigo ko yau din ma, bayan yadan yi hugging din na nadan wani lokaci ,</p><p> Sai ya sakeni ya koma bakin gado yai zaune yasa hannun shi yarike habar shi dashi, </p><p> Sai naga alamar yau damuwar har yafi na kullun yawa ma,</p><p> Nakuwa ci sa,a yaran na wurin su gwago tun da suka sha nonon safe, kuma nasan cewa zasu dade suna barcin safe,</p><p> Kofar dakin nakoma nasawa key, nadawo nasamay shi inda yake saidai wanan karon ya mike kafar shi,guda </p><p> Dayar kuma tsayar daita, ya yi yasa gwaiwar hannunshi akai don yaji dadin dafe goshin shi da tafin hannun shi,</p><p> Matsawa nayi jikin shi nadan jingina kaina da kafadar shi nasa hannu na guda nazagaya ta bayan shi, tayadda har muna jin bugun zuciyar junan mu,</p><p> Wani irin kallo yake min a cikin mamaki idonshi kar acikin nawa,</p><p> Nakalleshi idoncikin ido nasakar mai wani irin lalausar murmushi,</p><p> Nayi mai hakane don in samu damar aiwatar da nufina akanshi,</p><p> Don kawai in san may ye damuwar mijina, da har baida kuzari a kwanan gabadaya acikin damuwa yake,</p><p> Cikin wata irin murya nace narasa komay ke damun Sheriff dina acikin kwanakin da yakamata ace yana cikin farin ciki da walwala a rayunshi,</p><p> Sai nakara kallon shi karo na biyu nasakar mai wani munafukin murmushi,</p><p> Dan kuwa yau nayi niyar rike mijina da a hannu akan komay ke damuwar shi zan tayashi warwarewa insha Allah,</p><p> Cikin wata murya naban tausayi ne yadan daga ni kadan yagyara muna tsayin mu</p><p> Can yace min fatima bakomai ke damuwa na ba sai abinda da yan uwan haihuwa na suka sani aciki kawai,</p><p> Yanzu yadace ace duk cikin su koda mutum guda yakasa kirana mu gaisai </p><p> Balle har yai min murna samun karuwa fadima may narage masu da zasu dinga yi min haka,</p><p> Duk al,amarin su kusan nawa ne ,bada sanin Abba ba nake zuwa inda suke in masu alheri daidai gwargwadon hali,</p><p> Kusan sune nafarko danafarayi wa text batun haihuwar nan,</p><p> Amma wai ace har yau bawanda ya ko kirani ko kuma text din,</p><p> Wani iri naji azuciya nasan lalai sherif na cikin wa i hali don agaskiya dan uwa yabaka baya bakaramin tashi hankali bane,</p><p> Dan amin irinshi nani zafin shi na kumasan irin halin da mutum ke shiga,</p><p> Nace mai kayi hakkuri sheriff kamar yadda kasaba yin hakkuri da su insha Allahu wata rana zasu gane gaskiya su dawo hanya ai,</p><p> Murmushi yayi kadan yace bazaki gane bane,ai har in hjy mama tana raye ba,amu taba shiryawa da su ba saboda mugun akidar da take cusa masu, </p><p> Dazaran taga cewa muna dan shiri da gudan su ta shiga zariya kenan sai taga ta yi nasaran raba mu da may shi,</p><p> Murmushi nayi nace may idan har hjy mama ta hana yan uwanka mu amula da kai baga mu ba nida su Amal da Salim,</p><p> Ko bamu isheka ba, nafada ina mai kara tabbatar da ansar tambayana a idon shi,</p><p> Hancina yadan ja kadan yace aiku yan uwanane na na shakikai,</p><p> Amma su yan uwan haihuwana ne na jini kin ga ai dole indamu da rashin kulanin da basuyi,</p><p> Yace Anya fatima ko maraya yafini sanin rashin sanin zafin mahaifiyar mutum idan bata agida,?</p><p> Nakalle shi cikin natsuwa na ce mi,shi kadai fi su gata,,</p><p> Yakalleni yace min anya kuwa,?</p><p> Kware da gaske nace mai rashin mahaifi ko mahaifiya daban taka matsalar daba ai</p><p> Ganin danayi cewa yana cikin damuwa har yanzu yasa na sako may zancen wasa,</p><p> Nace kaida keda hjy tsohuwa a hannu ina kai ina maraici,</p><p> Murmushi mai yar sauti yayi man jin na anbaci hjy tsohuwa </p><p> Natare shi da fadin halin alherin da ta koya ma shi zakaci gaba da gabatar masu duk abin da sukai ma wanda ba daidai ba , kansu sukayi wa,</p><p> Nace nasan halin mijina da mutunci da kuma son kyautatawa na bayadashi,</p><p> Haka kada ma ka nuna masu cewa rashin tayaka murna da basuyi ba yadamay ka,</p><p> Kai mutum ne mai daraja da dauka musaman ga duk kan yan uwa,</p><p> Wanda harci ka ga yan uwa har yanasa amanta da wata hjy mama da zurian ta can,</p><p> Balle yanzu daga ka zama mai iyali, kan ka fiye dasu, da su aje iyali ba, </p><p> Kaga kenan kafi su koga idon jama,a, a addinan ce ma kafi su daraja,</p><p> Ban taba zaton zan iya tsayawa agaban sheriff in furta koda kalma daya ne mai tsawp ba sai gashi yau nice mai dogon sharhi irin haka,</p><p> Don haka sai naga maganar nawa ya shige shi da kyau, abida kuma dama nakeson gani ke nan,</p><p> Fatima ya fadi sunana cikin wani yanayi sai kuma naga yaja bakin shi yai shiru, </p><p> Wata kila yarasa abinda zai furta min ne,</p><p> Ganin hakan dani sai na furta cikin wata yar sauti na ce ina son ka sheriff kuma ina kaunar ka,</p><p> Jikin Sheriff sai yadauki rawa alokacin tankar wanda yasha wani abu</p><p> Hakan yakara bani damar kokarin cusa bakina acikin nashi saboda in kara mallake zuciyar mijina dan kawai in fitar mai da damuwar shi,,, </p><p> Lokaci mai dan tsawo muka dauka nidashi cikin wani irin yanayi da ba zai iya kwatantawa ba,</p><p> Sannu a hankali yayi karfin halin cire bakin sa a cikin nawa</p><p> Yai yar gyaran murya wanda ya tabbatar min da alamar yasamu natsuwa, so sai kamar yadda nake bukata,</p><p> A haka ya man na min kiss a goshi kamar yadda larabawa ke ma junar su sallama,</p><p> Idon na,bishi da shi yana tafiya cikin natsuwa har ya murda handle din kofar sai kuma yaja ya tsaya, </p><p> Batare da ya waigo ni ba yace min hjy fa ta dauko muna sabon rigima,</p><p> Dan tace wai sai anzo da ita nan ta zauna da yara,</p><p> Jin nayi shiru ban yi magana ba yasa shi dan waigo da idanun shi rinanun da suka dan fara watsakewa,</p><p> Shiru nayi nima alokacin ina sauraron shi don jin karshen maganar shi,</p><p> Ganin ya waigo yasani ce mai tasamu lafiya ke nan ko, da har zata iya zuwa,?</p><p> Dan murmushin nan nashi wanda baikai ciki ba yayi, </p><p> Yace still on bed bansan may zato tayi masu ba,</p><p> Sai a lokacin namike zuwa inda yake tsaye nace mai zatazo ganin jinin jikanta ne,</p><p> Wani irin sanyi ya sauka cikin ranshi da nafadi hakan,</p><p> Gaskiya bazan so ace tayi wani tafiya ba ahalin yanzu, dan gudun tashin ciwon ta,</p><p> Ce mai nayi may zai hana mu mutafi can idan har yin hakan zai fi,</p><p> Shiru yayi kamar mai nazari sai yace a gaskiya ina ganin kamar wahala zai ma yaran yawa don at,list suna bukatar hutu by now</p><p> To amma kuma hakan shine daidai don bazan bar hjy tazo nan in a long journey ba gaskiya,</p><p> Insha Allah zuwan mu bazai sa wani abu yasamu yaran ba,har muje mudawo,</p><p> Wani irin sanyi ya sauka cikin ran shi, don duk problems din shi fatima ta walwale mai su a,lokaci guda,</p><p> Yace zamu tsaya nan har ai seven days idan mutanen dogon daji sun koma sai mutafi can wurin ta tayi nata buki,</p><p> Ina fatan hakan yayi maku dai,</p><p> Wani irin farin cikin jin cewa yan uwa na zasu zo suna nan garin ,</p><p> Saidai a fili nace mai au har sai sunzo kuma bayan bamu dade da dawo ba,</p><p> Ido yazaro min yace bakya son azo ai muna farin ciki dakuma fatan alheri ga yaran mu,</p><p> Yaran mu daya ce shi ya bani ku ya sai nakasa tsayawa yakarasa zancen shi,,,,,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 9⃣1⃣</p><p> BY </p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost True Life Story,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Ban tsanmani arai na cewa hjy umma zata zo abuja ba saiga ta tare da yayan malam Abu driver ne yakawo,su,</p><p> Hjy Umma mutumiyar kirki macen da tasan ciwon kanta ga kuma riko ga addini,</p><p> Tazo ma yara da kayan sawa masu kyau da sai kuma ni da tazo wa da irin din yan Senegal din shaddace taci kwaliya har kasa, dogon riga,</p><p> Da ga ita har yaranta sunyi mamakin ganin irin gidan da nake ciki a matsayin gidan mijina,.</p><p> Dan sam basu zaci cewa arkin Sheriff yakai can ba murmushina yi masu dan nasan cewa basu san kowa ye sheriff ba,</p><p> Da Allah zai kai su saudiya da sun tabbatar wa kan su ba sai na fada da bakina ba,</p><p> Basu zauna suka fara gudanar da al,amarin buki,</p><p> Awa daya tsakani Salimat ta iso tare da sisters din ta su uku, </p><p> Nayi murna kwarai da zuwan su,Salimat, </p><p> Don zuwan na,su ,yai muna amfani sosai, saboda sun hade da su hjy umma suna ta arranging din abinda za,aiwa baki,</p><p> Sai zuwa dare Antyna Rugaiyya ta iso uwar gaiyyar aiki,</p><p> Dan ko Rugaiyya ta nuna mi ita ita din ce a gareni,</p><p> Tazo min da duk wani kayan snacks da ake yi a gurin buki tankar yadda al,adun mu na kasar sokoto yake, </p><p> Duk wani abinda uwa ko ya zataiwa yar ta shi Rugaiyya ta hado min ,</p><p> Mota guda suka ciko da kayan gara, irin yadda ala,adar mu ta hausa take,</p><p> Ban samu bakin da zan mata godiya ba don abin ya wuce lissafina,</p><p> Sai zuwa dare sai ga mutanen dogon daji sun iso, mota biyu na mata guda na maza,</p><p> Kawai sai naji aiduk na rude ban iya ai,watar da komai Salimat da Anty Rugaiyyane sukai kasafin guri sauke kowani bako yadda ya kamata,</p><p> Maza yan dogon daji mun kai su boys Quarters,</p><p> Mata kuma sai duk aka rabasu a sauran dakunar gidan,</p><p> Nida Salimat da Safiya da sister ta muka koma dagin sheriff sai mukabar hjy umma da Rugaiyya da hafsi dakina,</p><p> A gaskiya ban taba zaton haka ba sam a rayuta ashe jama,a dadi gare su,</p><p> Duk yadda dangi na suke yan kauye a cikin mu sai naji kawai hankalina yafi karkata gare su, don komai su nake fara sa akawai, ko,aimasu,</p><p> Ban bada wani kafan da za,araina min yan uwa ba sam,</p><p> Sai cikin dare so,sai mutanen Maiduguri suka iso ,hurjanjan duk sun gaji,</p><p> Sam bamu san da zuwan su ba alokacin sai dai ganin su mukayi, kawai,</p><p> Da gudu Amal tazo ta rungumay ni cikin missing din juna muka dan dade a hakan,</p><p> Can kuma sai naji ta ture ni baya kadan ta canza fuskanta ,</p><p> Cikin larabci ta fara zazagami ruwan bala,i akan gudun danayi na basu,</p><p> Inda take ce min wai na guda batare da na fadawa Ummi matsalata ba kuma ma na raina da Ummi ne aida ban rainata ba da ban gudo na barsu a cikin tashin hankali ba,</p><p> Shiru nayi kawai sai yar murmushin da nake mata,</p><p> Suko yan uwan su da basu san ni ba sai kokarin zuwa sugan ni suke yi,</p><p> Nan da nan falon ya kaure da larabci tsakanin Salimat da Amal da Anty Rugaiyya sai ni dake dan jefa masu baki </p><p> Hjy umma tace wa safiya kin gani ko keda nacewa kitafi saudiya karatu kika ce min ke bazaki ba yai maki lokal,</p><p> Tace yanzu dan Allah hakan bai baki sha,awa ba sai kawai duk mukasa dariya,</p><p> Nan Amal tace ai karatun saudiya nada amfani so sai wlh musan mam ma ga matasan mu mata, don duk wani akidar alheri da ake so uwata samu har ta tarbiyartar da yaran ta dole tasamo shi a can koda ko batayi niyan koyon hakan ba</p><p> Don al,adun su kawai zaisa mutun yaje koyi dasu har ya dauki halayyan su ya dinga yi,</p><p> Ta ce ai rashin sani ne kesa iyayen tura ditan su karatu har kasa shen turawa bayan ga inda ya kamata iyayye sika yaran su don koyi da sunna ma,aiki SAW,,,</p><p> Wata daga cikin yan maiduguri baidai yarinya bace kamar mu ta cabe zancen da cewa ai mu mun ga faidar hakan so sai ba sai an fada muna ba,</p><p> Don ko mai wanan gidan da muka taru don shi abin musaline kawai,</p><p> Dan yan uwan shi da aka fara turawa kasan turawa karatu akwai daga cikin su wanda har yau baiko leko kasan nan ba, </p><p> Gudan ma da yazo wani lokaci da kitso fa yazo muna har kauyen mu dashi, shiko guda da baturiya yazo ganin gida sai kuma akidar sa wando a sabule shi ta baya wai duk cikin wayewa ne,</p><p> Shiko Amadu don hassada akasa a lokacin wai akaishi karatu saudiya saboda wai basu da karfin ilimi kamar kasar turai,</p><p> To kin san abin Allah sai gashi shi wanda Allah ya nufa ya take daga cikin su,</p><p> Su yanzu suna can ba wanda yasan ma halin da suke a ciki, </p><p> Garama da da Abba ke zuwa dibasu wani lokaci har yadan tsawata masu akace duk da uwar su na boye wa duniya sherin su, batasan cewa ba,a boye magana ba yanzu,</p><p> To yanzu ma Abba girma ya kamashi ba ko,ina yake zuwa ba,,</p><p> Allah ya kyau,ta inji hjy umma takarasa zancen dashi tana fadin Allah yasa iyayye su gane su daina tura diyan su kasa shen da babu akidar addinin musulunci acikin ta </p><p>Kowa ya ansa mata da Ameen, a lokaci guda saboda duk jikin mu yayi sanyi ga bayanin ta, dan sai a lokacin nadan fahinci cewa ashe hjy mama hassada takeyi da Sheriff ,</p><p> Shiyasa yan uwan shi basu kaunar ci gaban shi sam,</p><p> Nace inko hakane gaskiya akwai aiki so sai nan gaba dan dai dole a sheriff's yasamu support dan kara mai karfin gwiwa, saboda yasa su aran shi, ,</p><p> Sai daga bayane nake jin cewa ita wanan matar mai magana diyar dan uwar Abbane, </p><p> Kakansu guda da sheriff hjy tsohuwa itace ta haifi mahaifinta,</p><p> Ke nan ba karami zumunci ke tsakanin su da shi ba don haka na sa araina cewa zan ja ta ajiki sosai , </p><p> Saboda duk abinda mace zatayi ya kasance taja koda mutun guda ne daga cikin dagin mijinta ajiki so sai wanan zai sa yan uwan miji so so mutun kodan dole,</p><p> Kamar yadda wa su baruwan su da dangin mazan su kan su kawai suka sani da yan uwan su, </p><p> Duk yadda miji ke kyautata masu su basu damu da nashi yan uwan ba,</p><p> Tundaga waban lokacin na dinga kafa,kafa da ita dan kusan duk abinda za,ayi sai ince akira hjy falmata,</p><p> Hakan yasa ta tun ba,akai ko ina ba tafara yabona agaban yan uwan su ,</p><p> Washegari aka radawa yara suna a babban masallacin dake cikin maitama suna,tare da kwararo madu addu,a,</p><p> Kusan duk wanda yazo sallah asuba aranan ya sheda wanan abin don sun koma gida dauke da gift da su malam Basiru da Bashir suka tsaya daga kofa suka bayar as a sadaka,</p><p> Yara sunci sunan, hjy mama, da kuma Abba lawal zannah,</p><p> Sheriff da kanshi yasa shehi yai masu huduba da wanan sunan </p><p> Saboda hjy mamatasan cewa ita uwace a gurin shi ko yau she,</p><p> Agida kan bukin suna akayi sosai kamar yadda mata ke taruwa yan uwa da abokan arziki ayi ,</p><p> Dagani har yaran kwaliya kawai muke ta dan dasawa wanda mai photo da kuma video ke tadaukar kowa gurin,</p><p> Yan company din su dake nan Nigerian Mobile sun yi kokari sosai don sun shirya wata liyafa taban girma ga shugaban nasu,</p><p> Wanda dama jama a bsdu sanshi ba sosai sai a wanan lokacin, aka waye shi tunda ba Nigeria yake shigowa ba sosai,</p><p> Mariyata tayi mugun kyau cikin yan kwanaki kadan din da mukayi da barin kauye dan tare da safiya suka fita inda takai saloon akai masu gyara na musn man,</p><p> Abdull kanin mu hafsi tazo da shi kayan yan kati na ma,a suka fita da salim yasaya mashi su kalakala masu kyau, dakudin shi,</p><p> Nai magana akancewa zan bashi kudin yace min ina ruwa na ko nafishi son shi ne ? nai shiru naja bakina,</p><p> Walima suka shirya wanda suka gaiyato mashuriyar malamar na mai ma mata wa,azi, watau malama Zuwaira, tare da wasu sairan malamai mata biyu,</p><p> Da musalin karfe hudu na marance za,ai wanan walimar,</p><p> Sai musalin karfe biyun rana lokacin ina cikin shigar wani material green colour ,mai tsada wanda tun a saudiya da nake da ciki salimat tasani muka siya don wanan ranan taba mijinta yazo dashi Nigeria adika min,a kano,</p><p> Wasu matane sukayi sallama a falon su hudu daganin su kasan cewa kosassun matane don shigan su kawai yawadatar ga may ganin su,</p><p> Ga wani kamshi duk ya kaure gidan, da suka shigo da shi kowace taci ta koshi,</p><p> Duk wanda ke falon ba su san ko suwaye ba,</p><p> Kasancewar mu duk muna sama,</p><p> Hjy umma ce zaune tare da Rugaiyya suna fasalin abinci hatta anty falmata bata san su ba,</p><p> Gurin zama hjy umma ta basu cikin mutunci tasa akawo masu abin tabawa ,</p><p> Cikin wani irin murya da sauti irin na yan duniya wata daga cikin su ta dakatar da wace umma ta turo dauko abincin,</p><p> Text naji ya shigo min alokacin kamar kada indauki wayar sai dai na mika hannu na nadauka dan inga ko text mai amfani ne gareni,</p><p> Salim ne dake waje zaune cikin taron mazan dake kofa ya hango shigowar su gidan alokacin da kyat ya iya sheda ta, ma,</p><p> Abinda ya turo min shine ga, Aziza ta shigo maki gida sai ki san yadda zaku tare su,</p><p> Gabana yai dam, cikin mamaki na furta afili na ce Azazi kuma by now,</p><p> Da sauribkowa ya kalloni cikin mamaki dan jin abinda nace a bakina,</p><p> Cikin kidima Salimat tace tana ina ? nace masu cikin murya mai rau,ni tana falon kasa wai,</p><p> Amal tace barin fita kafin ta fara wa mutane iskanci,</p><p> A,falo kuma su Aziza da hindu suna can sun fara yiwa mutane iskanci ko,</p><p> Cikin ya tsunar fuska suke wa mutane magana,wai a kawo masu jarirai su gani dan dama su shi yakawo su ai,</p><p> Amal daga step tana saukowa ta basu ansa tace </p><p> Akan wani hujja za a,dauko maku, jarirai haka kawai kai tsaye,</p><p> Aike kinfi kowa sanin cewa ina da hujjan yin hakan ko</p><p> Don dole in diba don inga dawa sukati kama don har yanzu bawai na saduda bane, dama wanan damar nake jira dan in tabbatar da cewa ko da kwana akai wanan cikin ko kuma da nasu ne kawai,</p><p> Yan rakiyan nasu na cewa kwarai kuwa dan gani yakori ji,</p><p> Cikin harshen kanuri Amal taiwa yan maiduguri magana,</p><p> Tace masu matar Ahmad ce ta Dubai tazo ne dan ayi bala,i kawa, tace dan Allah su figita ta so sai ,</p><p> Haba Hindu dake wani tanar cingun kas,kas jin wasa yuka kawai tayi a bayanta, karrrrrr karrrrr ta waiga da sauri aiko,</p><p> Anty Falmata ce ke wasa yuka sai wasu sauran yan uwan su cikin dangin mahaifin yaghana da suka zo ga tsaga yaba yaba a fuskan su suma sukace dawa Allah yagama mu bada kuma ba,</p><p> Tashin hankali aisai gasu duk sun mike atsaye Allah yasa Amal ta rufe kofar duk shiga gidan </p><p> Aikafin ace haka sai hindu ta dauki waya jiki na rawa ta kira wani wai hello Kura kana ina ne ku shigo kawai akwai matsala, fa,</p><p> Allah ya taimaka Salim ya farga da mutanen tun zuwan su yai ma duk securities din gbayani akan akulada su,</p><p> Sai da aka bari sun shigo tsakiyan sai kawai fitina yatashi tsakani su da security, dakuma su salim da mlm Basiru wanda tun gida sunci maganin tauri,</p><p> Yanka guda yakawo wani security sai Basiru ya tare aka samay shi ganin gurin bai yi jini ba yasa gudan cewa Wlh muyi ta kan mu kura kada rana ta baci muna yau don da alamar yau ba nasara ga aikin nan</p><p> Duk yadda su kura suka so suyi yun kurin gudu security da su malam Basiru sun hana su ga kuma wasu yan sanda da Bashir suka turo su ma sun iso gurin</p><p> Cikin gida kuwa yau su Aziza sunga Barebarin asali sun kuma ga aikin su </p><p> Daya daga cikin kawayen Aziza da tai tsauri mike wa dan gudu taga cikin masu tsagar na ta nufota da yuka tsirara ai,sai kawai ta fara kurma ihu ,,</p><p> Tana bidan ceto, daga waje, duk sun tsorace gawayar su Kura ana kiran su basu daga ba,</p><p> Nan fa hankalin hindu ya kara tashi kamar ta ce gara da bata zo ba,</p><p> Aziza tace wa Amal Amal nizaki sa aiwa wanan rashin mutuncin haka,</p><p> Amal tace au ke mutunci kikazo yiwa mutane ko may,</p><p> Amal tace yara suna nan lafiya lau amma kisan da cewa babu jiniki cikin ko dayan su,</p><p> Dan Allah yafiki yafi sheriki, dan bakiso koda ahaifi su din ba tunda kikaso kashe su tun a cikin ciki,,</p><p> Allah ne ya kare fadima har takai ga haihuwar su lafiya batare da kin yi galaba akan su ba,</p><p> Haba sai Azuza tafara cewa ni duk wanan zancen wallahi ban san dashi ba Amal </p><p> Amal tace ai yau takare dai tunda ke kika kawo kanki don sheri, wai har zaku shigo kunawa mutane wulakanci a cikin gida,</p><p> Amal takara wa matan nan yaren kanuri aiko sukayo kan su Aziza da yuka tsira gadan,gadan kamar zasu yanka su da gaske haba sai ga Hindu a kasa ta daga hannu biyu tana fadin aimata rai,.</p><p> Aziza saida na fada maki kada muzo ki ka nace akan son kai yau gashi kin jawo muna bala,i a filin Allah,</p><p> Matan na suka samu su Aziza suka murje su da kyau, sai sun baka tausayi,</p><p> Kofar da ake duka ne kamar za,a balle shi yasa suka dakata da bugun su, kin bude kofar akayi,.</p><p> Saida Bashir yai magana da karfi aka bude kofar, </p><p> Shi da sheriff ne tare da wasu yan sanda suka shigo cikin gidan cikin tashin hankali suke kallon kowa don ganin mutane cirko cirko,</p><p> Kallo guda Sheriff yai wa Aziza ya kau da kai cikin yare yai wa Amal magana ta juya da sauri ta hau sama,</p><p> Ina zaune cikin tashin hankali ta fado dakin cikin sauri take magana tace wa safiya ta dauko jaririn guda ta biyo ta zuwa falo,</p><p> Ban san lokacin da na mike tsaye ba dana ji haka</p><p> Ido waje nake tambayar ta ko ina za su kai min yara,</p><p> Batare da Amal tabani ansa ba ta sakai zuwa downstairs da yar baby a hannuta safiya na binta da dayan a bayan ta,</p><p> Duk kan mu falon muka fito cikin rudani rashin sani may za,ayi wa yaran,</p><p> Ganin Aziza da kawayen ta zube saman ties, yasa duk muka tsaya tur tsaye da mamaki,</p><p> Daya bayan daya yadinga daga yaran yana nuna mata kamanin su da kyau,</p><p> Duk halin da take ciki bai hanata yin ajiyar zuciya ba alokacin,</p><p> A hankali na tako zuwa har inda suke nadan tsuguna daidai saitin inda Aziza take </p><p> Nace mata hjy dan Allah kiyi hakuri kifita harka na da na diyana hakana,</p><p> Allah yagani banda amanar ki shi yasa lokacin da kikaso cin amana na Allah bai baki ikon akaina ba,</p><p> Duk cikin larabci nake mata magana don tana fahinta saboda zamanta a Dubai,</p><p> Hakan yaba duk wace ke gurin dama masu jin larabci muka shiga za,aga masu maganganu cikin bacin rai,</p><p> Saida sheriff ya tsawata muna cikin bacin rai sannan muka kyale su,</p><p> Banko tsaya ba na, juya cikin kuka nabar falon cikin bacin rai, da tashin hankali,</p><p> Bayan dogon shehin da yai matane yan sanda suka wuce da ita, zuwa tare da kawayen ta,</p><p> Abinda mutane suke iya shedawa kawai shine kishi yakawo ta dan haka akai mata wanan mugun wulakancin da tazo da niyar ita taiwa mutane sai gashi reshe ya juye da mujiya,</p><p> Ba wanda muka fadawa yadda zancen yake akabar shi arufe,</p><p> Karfe hudu duk angama wani shiri akan walima, jiran isowar malamai kawai akeyi,</p><p> Walimar yayi armashi so sai malama Zuwaira tai sherhi akan hakkin uwaye akan diyan su da kuma yadda tarbiya ke farawa tun yaro na shan nono, har zuwa girman shi,,</p><p> Ana tsakiyar walimar Nafisat ta iso gurin tare da yan uwanta su kusan shida inda suka mara mata baya,</p><p> Cikin shigar su ta yan gayu suka shigo wurin kowa idon su na akan su saboda irin yanayin shigar su,</p><p> Duk da sundan rufa yan gyale a kan su kamar ba matan aure ba,</p><p> Don daga kasan cewa ba,a tunanen mutuwa zata iya riskan mutun anytime, an shagala da duniy kawai, ba a tunanen gamuwa da ubangiji </p><p> Kallo guda nai mata daga inda nake zaune naga tadan kara kiba sama da sanin da nai mata,</p><p> Amma banda shi tanan bakar ta bata shafa man da matan zamani ke shafawa ba dan suyi haske,</p><p> Daga inda akai masu mazauni muka hada ido da ita, duk da nike yarinya na hago ki shina karara a cikin idon ta,</p><p> Nasan ko ba komai bane sai ganin yadda na sake lokaci guda na canza daga fafima yar takari zuwa Fadimar Sheriff Ahmad Lawal Zannah,,,</p><p> Taro ya,watse cikin jin dadi da annatshuwa inda aka raba wasu manyan traveling bags dake dauke da showel da su sabulai da kuma kayan snacks a ciki da su sweet kalakala,</p><p> Yan dogon daji da sukazo zasu koma gida matan su kowace turmin zani da dubu biyar mazan su kuma shadda da dubu biyar, ga kuma kayan buki kalakala,</p><p> Hakanal yan maiduguri su ma kyauta iri guda akai masu da yan dogon daji,</p><p> Naso hafsi ta tsaya saidai kuma saboda tafiyan mu maiduguri yasa na bari tabi sauran yan uwar mu zuwa gida,</p><p> Su hjy umma wace take zama min kamar uwa yanzu takara min nasiga sosai akan zaman duniya inda ta lurar dani yadda sherin mutanen zamani yaje da kuma yadda zan zauna da mijina a cewar duk kishiyoyina ,suna da matsala atare da su,</p><p> Da zu tafi kamar kada su tafi su barni nake ji don duk kusan lokaci guda suka wuce bayan alherin da Sheriff yai masu ta bajinta tare da yi masu godiya,,,</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>,✈✈✈ *TAKARI*✈✈ </p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 9⃣2⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost True Life Story,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tun cikin dare bayan tafiyan bakin mu, muka soma shirye, shiryen tafiya, zuwa maiduguri,</p><p> Natambayi sheriff ko a nan zamubar su gwago da su mariya yace mi aida su zamu tafi,</p><p> Shiru nayi saidai a zuciya sai ina gani kamar mun yi yawa ga tafiyan ace duk yan uwana har kusan mu biyar </p><p> Zamu je masu bakun ta a,gaida a gaskiya ina gudun abin magana saboda ban san irin rayuwar mutanen can ba,</p><p> Duk wani abinda ya kamata mudauka dan bukatar mu mun dauka , dan ba musan abinda zamu tarar ba acan,</p><p> Tunda sheriff yafita da yamma baidawo gidan mu ba saidai a waya ne mukai magana da shi, inda yake sheda min cewa tafiyan safe zamu yi,</p><p> Sai da safe ya shigo gidan mu a cikin shirin shi tsab </p><p> Duk da mun shirya karyawa kawai yarage muna muyi a lokacin, </p><p> Ina zaune bakin gadona ina baiwa ummibanan nono ya shigo dakin mariya dake tsaye gabana tanawa Abbazannah wasa tana jiran dayar tagama shan nono ta miko min shi tai niyar fita dakin,</p><p> Da hannu sheriff yadakatar da ita ta tsaya abin ta ba zama zai yi ba,</p><p> Inda nake yazo ya kai min dan sunbata a gaban goshi cikin larabci yake tambayar lafiyar mu na ce mai kowa kalau masha Allah,</p><p> Yace min duk wani gifts da yakamata arabawa mutane sa acan yasa Bashir ya tanadar min zan samay su acan ko, </p><p> Nai mashi godiya tare da yimai addu,oi da fatan alheri akoyaushe,</p><p> Sai kuma ya ce min duk da bai san ko kwana nawa zanyi can ba yana son dan Allah duk abinda muka gani dani da su gwago muyi hakuri da shi,</p><p> Nace mai duk abinda za ai muna insha Allah bazamu dauke shi komai ba tunda bashi yai muna ba,</p><p> Ankawo min abinci har dakina muka karya tare da shi don irin sakkon dayayi zuwa gidan mu nasan cewa baici abinci ba,</p><p> Yana cin abincin yana kara yi min bayanin cewa har gurin ummi yake sonmuje mudan kwana biyu</p><p> Na nuna mai murna na afili wanda hakan yasa shi jindadi sosai aranshi,</p><p> Duk mun fito cikin shirin mu tare dasu gwago inda ,</p><p> Suna rugumay da yara niko Aisha ce kawai na rike da hannu na zuwa bakin get,</p><p> Dan ni azato na da mota zamu tafi ashe jirgine zamu zuwa can, saidai wasu kayan mu za,a biyo mu dasu,</p><p> Cikin kwaliya muke na gani na fada saboda nasan cewa Sheriff mutum ne mai son yaga matar sa acikin shiga na kwarai na alfarma da mutunci,</p><p> Shima hakan ne dan wasu yadi yasa na maza na India Pakistan, yadin yana da kyau so sai kuma dinki kusan irin nasu ne,</p><p> A hanyar muta airport ne muna zaune a bayan motan nida sheriff nake tanbayar shi, </p><p> Amma dai shi ba dadewa zaiyi a can bako zai koma gurin aikin shi,</p><p> Saida yadan murmusa min kadan yace har kun gaji da gani na ne ko kuwa,</p><p> Cikin sauri na ce, mai haba wa ,ai bana fatan ranan da zangaji dashi a duniyar nan,</p><p> Yace to kina tsoron kar in bar ku can ne ku kadai,</p><p> Wani murmushi na danyi, </p><p> Sai nadan matsa kusa dashi kadan na kwantar da kaina saman kafadar shi,</p><p> Nai magana acikin tausa murya kamar mai rada na ce ba tsoron nake ji ba sheriff,</p><p> Indai son mijina a kusa dani ne kawai, bana son mu ni,santa da junar mu ko kadan,</p><p> Shiru yayi batare da ya ce min komai ba,</p><p> Saidai ni nasan cewa shirun shi na nufin wani ansa ce hakan nan , dole in sa ido in fahinci ansar maganata nan gaba,</p><p> Muna isa airport muka samu time din tashi har ya kusa batare da bata lokaci,ba muka shige sai tafiya,</p><p> Tayi ce mai dan nisa sosai mukayi wanan karon din yafi wanda mukayi daga sokoto zuwa Abuja nisa,</p><p> Wani tunane yazo min acikin jirgin ina tuna yadda zan je in bakunci wasau mutanen da ban saba rayuwa da suba acan baya,</p><p> Kuma gashi da alama ba sajin hausa akasarin su duk yare suke yi,</p><p> Ban san ko ya mahaifin sheriff zai tareni ba kasancewa ta yar talkawa, badiyan masu arziki ba</p><p> A yadda naji su Amal na hiran arzikin shi da kuma irin rashin ko in kula da yakewa yan uwan shi,</p><p> Uwa uba kuma irin yadda zan riski hajiya mama,</p><p> Tuna ne sosai nayi har zuciya ta takoma min tunanen irin matan sheriff da zan yi zaman kishi da su arayuwa na,</p><p> Sai dai kuma wata zuciya na ce min ina ruwa na da su suda suke gidajen su mai zai hada ni da su ,</p><p> Alokacin naji dadin tunanen da nakeyi har nakai kaina a makarin kujerar da nake zaune dan inji dafin tunane,</p><p> Nace nadai ji manya na fadin Namiji ba dan goyo bane, watau ke nan koni in yi hankali da Sheriff kenan arayuwana, dan zai iya zuwa wata rana ya juya min baya,</p><p> Na ce hmmm ni ko asani na ai namiji shi mafi darajan mutum wanda ke haska mace komai mukamin ta ko arzikinta ko mulkinta, ko kuma kyau,</p><p> Dazaran baki da aure duk wanan daular yatashi a free dan baki taba daraja a idon duniya,</p><p> Sai kawai a zuciyana nasa aikoda anan gaba sheriff zai juya min baya zan ita hakkuri da shi badon wai abin hannu shi ba ko kuma kwadan zama dashi, </p><p> A,a saidai kawai dan bazan taba mantawa da irin mutuncin da yai min ba arayuwa ta san nan kuma ga zuria, a tsakanin mu, </p><p> Nakara dan lunshe ido na nakara cewa acikin zuciya na,</p><p> To ai shi sheriff ma dole mace taso shi saboda irin hakkurin da Allah ya bashi ga kuma kyautatawa a tsakanin shi da mace,</p><p> A haka naita nazarin rayuwa ta da na sheriff a cikin zuciya na ni kadai keyi kuma ni kadai keba kaina ansa,</p><p> Jin sheriff dake zaune a kusa dani ,nayi yana dan murza min hannuwa na yace min batare da ya kalle ni ,ba yace, may kike tunawa haka kike ajiyar zuciya,,,</p><p><br /></p><p> Mun isa lafiya Inda motocin gidan su Sheriff sukazo taron mu kusan guda hudu,</p><p> Tun a airport naga irin taron arzikin da mutane ke muna sai sambarka sukeyi wa sheriff,</p><p> Duk da rana yadan yi a lokacin da muka isa don haka kai tsaye vidan mahaifin shi muka wuce direct,</p><p> Wani bangare guda daga cikin gidan aka bude muna nida su gwago,</p><p> Duk wurin idan kagan shi zaka dauka cewa ba isa,shen fili ashe idan ka shi gida sukutun a guri don da kunoni ne kusan guda shida acikin plat din,</p><p> Batare da mun huta ba ko tsayawa cin abinci nasa muka tashi zuwa cikin gida gaida su Abba,</p><p> Alokacin yamma har yafara yi , don haka dakin hjy mama muka fara shiga,</p><p> Mun samay ta zaune falonta tare da wasu mata su uku, sai masu aikinta,</p><p> Durkusawa nayi kasa nakai mata gaisuwa, tana saye da wani farin,glass a idon ta,</p><p> Ina kokarin gaisheta ito idonta na ya na kan zanin dake jikina , tana kokarin tantance ko super ne daura ko kuma yar kwaikoyo, ce nadaura,</p><p> Gwagona kokarin mika mata yaron dake hannuta still idon ta na kaina,</p><p> Ganin haka yasa na dan gyara da kyau dan taga zanin dakuma zobban gold da na jera a hannu na,</p><p> Saida ta ware ido da kyau lokacin da taga wa yan nan zobban na hannu na,</p><p> Da kyat ta iya ce min ashe kuna tafe,</p><p> Ai mu bamu da labarin cewa zaku zo nan dauka muke yi acan za kuyi ta sha,anin ku kawai,</p><p> Na yar murmushin gefen kumatu nace haba dai ai muzo neman albarkan ku,</p><p> Shiru tayi kamar bata jini ba ,,,</p><p> Nai,dan murmushi nace mun samay ku lafiya da kyat ta ansa min tace lafiya kalau banda shi ba wanda yakara magana daga cikin mu,,,</p><p> Shiru ne ya,biyu dakin ba wanda yace komai kowa na maganar zuc Daidai lokacin sheriff ya shigo dakin shi ma,</p><p> Fuskan ta ba yabo ba fallasa aciki, yadda nayi haka shima din yayi a kasa ya zauna ya gaida hjy cikin girmamawa,</p><p> Tana daga kishingide take ansa mai da kyat tace ashe kana Nigeria har yanzu,?</p><p> Tambayar taba shi mamaki sosai ,sai kace wace batasan ai mai haihuwa ba take mai wanan tambayar,</p><p> Basar wa yayi yace mata tare da nuna mata yaran da hannu yace ga wa,yanda suka hanani komawa nan,</p><p> Ga su ankawo maki su kigan su, </p><p> Sai cewa tayi a,a kun dai kawo wa hjy tsohuwa ita da ke ta damuwar mutane da zan cen sai kace bata taba ganin anhaihu ba agidan</p><p> Daidai yana mikewa yake ce mata mama kin san wanan daban ne dana ko yau,she shiyasa ta damay ku,</p><p> Kafin ta bada ansa yakai waje kofa ko,ganin yafita yasa ni mikewa nacewa wasu gwago suzo muje ,,</p><p> Bayan shi mukabi zuwa shiyan da hjy tsohuwa take ciki tana jin ya tare da yan jikokinta biyu daga can kauyen,Auno,</p><p> Hjy tsohuwa tana zaune da chasbaha a hannun ta ja tana dan gyangyadi daga zaune, </p><p> Yin sallamar mu yasa tamike tana fadin </p><p> Alhaji karami koba shi bane,</p><p> Yace nine hjy Amaduna zo nan zo in ganka, </p><p> Ina kashige nake ta ma aike kazo katafi dani baka zo ba,</p><p> Ina fatan kazone mutafi ko, ina yaran naka, ?</p><p> Duk a cikin kanuri take mai magana yace mata hjy ai tare da su muke,</p><p> Gasu nan nakawo maki su ki gansu ai ba sai kin zo ba hjy,</p><p> Sai kokarin mikewa takeyi, daidai lokacin muka shigo katon falon da take zaune a ciki. </p><p> Hjy tanan kamar yadda nasan ta sai dai ta dan kara tsufane kawai </p><p> Dakin yana ta kamshin turaren wuta don har yafi dakin hjy mama kamshin dadi,</p><p> Tana kokarin gyara lafayan ta tana kuma kokarin miko hannu dan karban yan jarirain da ake mika mata alokacin,</p><p> Dole tabar gyaran lafayan takarbi yan yaran tana ta washe baki cikin farin ciki da jin dadi,</p><p> Sai kuma ta,hau yin hamdala ta aa dauko addua dake bakinta tana tofa wa yaran,</p><p> Saina kula da cewa ko su gwago sunfi jin dafi dakuma sake jiki a gurin hjy tsohuwa, fiye da dakin hjy mama da muka farq zuwa,</p><p> Nan da nan yan matan nan suka kawo muna Birabisko, da kunun gyada,</p><p> Hjy na fadin (uno biri yo biski ) </p><p> Mudai murmushi kawai mukayi, nan muka baje a shiyan hjy tsohuwa abin, mu, har bayan sallah magrib mu,na nan sai lokacin </p><p> Sai musalin karfe tara na dare ,sheriff yai min waya yana sanar dani cewa mushirya akawo gurin Abba, mu gaida da shi,,</p><p> Yana zaune saman wani ddaduma mai laushi da kuma sulbi sai ya'yan itace dake a gaban shi da alamar su yake ci a lokacin,</p><p> Cikin murna da farinciki Abba ya tare mu yana ta fara,a da zuwan mu, aka mika mai yaran dadauka daya bayan daya yana sa masu albarka yana mai nuna faricikin shi,</p><p> Yajiyo yana tambayana mutanen garin da yan uwana suna lafiya ko, acikin ladabi dakuma kunya na bashi ansa da suna lafiya kalau,</p><p> A,lokacin hjy tsohuwa tashigo falon tana wani busan iska tawuce zuwa inner room fuuu, can kuma takara fitowa kamar bata gan muba,</p><p> Nima ban kara gaida ita ba duk wulgawan da takeyi agaban mu,</p><p> Sai alokacin ta dawo tadan zauna tana ce min, duk wa yan nan tare kukazo da sune ? ko kuwa, ?</p><p> Duk da tambayar nata yai min zafi amma sai nadake kawai, araina nace mata eh,</p><p> Wanan gwago tace wanan kuma matar babana ne,</p><p> Abbane ya karba da fadin masha Allah haka yati kyau mungode kwarai da kulawar ku,</p><p> Allah ya raya muna yaran yasa masu albarka, kowa dake wajen akace amin, bandani da na karba a cikin zuciyana, ba,a fili ba,</p><p> Ba muwani dade ba muka taso zuwa falon hjy tsohuwa don muyi mata saida safe, saboda gaskiya a gajiye muke,</p><p> Wai ashe duk zaman da nayi falon hjy bata gane ni ba saida Sheriff yai mata bayanin, ko wace ce ni,,</p><p> Ina shigowa naji tace min U,ro, Uro,</p><p> Tana min alama da hannu inzo gurinta tanace min ashe abokiyar zuwa dawafi na ne ban gane , </p><p> Kece haka kika girma masha Allah , sai kuma tasa kuka kamar yadda tsofafi keyi indan sunji dadin abu,</p><p> Nace mata ta daina kuka dan Allah ai yanzu mun zama daya ba inda zani, kuma muna tate muyi ta zuwa dawafin mu atare,,,</p><p> Koda muka koma shiyan da aka ba mu mun samu wayan nan yan matan sun gyara muna shiyan da aka sauke mu sai kamshi yake yi,</p><p> Aiko su gwago sukace indai harda sheriff a shiyan zai sauka sam su baza su zauna ba saidai su koma gurin hjya,</p><p> Sai ko ga wayan shi yana sheda muna cewa shi ya wuce gurin da zai kwana gidan Baban, Bashir, acan wqni unguwar Bulama,</p><p> Jin haka muka sake jikin mu mu kadai saidai duk daki guda muka kwana saboda sam gwago tace ita bata yarda da hjy mama ba,</p><p> Hakana muka kwana acikin daki guda, gabadayan mu,</p><p> Washegari gashi dai munyi wanka mun shirya tsab, amma har zuwa goma da rabi na safe ba akawo muna abin karin kumallo ba,</p><p> Gashi cikin jegone mun tun ina daure wa gwago nata masifar fada tana cewa gaskiya wanan abi da niyya akai haka,</p><p> Mai aikin hjy mamace tashigo da sallamar ta dauke wani dan kula abinci wanda, ko mariya da Aisha ba zai kosar ba ,</p><p> Kwaine soyyaye da dankalin tura har yayi sanyi, wai hjy ce tace akawo muna ,</p><p> Har takai kofa sai gwago tace mata, tazo ta dauka tamayar tace ai mun koshi,</p><p> Naso in magana tai cikina da fada so sai tace da wanan cikin jegon naki za,a kawo muna wanan dan abincin haka,</p><p> Ganin munkai har rana yasa kawai naiwa sheriff text nace muna jiran abin breakfast,</p><p> Cikin mamaki yakirana yana tambayana nan na sheda mai duk yadda akayi kuma na fada mai gwago ta ce amayar mata dashi,</p><p> Ba afi minti ashirin ba sai ga take away na wani restaurant ankawo muna gudan mai yawa mukaci har muka koshi,</p><p> Sheriff yazo yabawa su gwago hakkuri, tace ita abinda yasa tace amayar saboda idan mun karba ko gobe haka za,a kawo muna kuma ba mai sani ,, </p><p> Naji yace masu saboda zuwan mu komai yasa ankawo don bukatar mu </p><p> Gwago tace barta kawai munsan irin wanan </p><p> Muda muka fito hausa muza,agwadawa barkado,</p><p> Kuma muna nan bamu wucewa sai mungama abinda yakawo mu,</p><p> Sheriff yaji nauyi sosai amma dayaga su gwago madu yi ne sai yaji dadin hakan don yasan zasu iya maganin mama,,,,</p><p><br /></p><p>✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 9⃣3⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost True Life Story,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Kafin karfe biyu duk wani simple stock an tanadar muna shi a side din da muke zaune a cikin gidan Abba,</p><p> Sau biyu ina zuwa side din hjy mama dan mu,gaida ita amma gurin yana a kulle,</p><p> Saida mariya tagama gyara muna ko ina san nan muka kwasa muka koma side din da hjy tsohuwa take ciki,</p><p> Mariya da yan manta sukayi muna abincin da zamuci ,</p><p> Sai bayan sun kam,mala komai ne suka zubowa kowa a inda yakamay, </p><p> Falon hjy tsobuwa muk banje muka fara cin abin cin mu hankali kwance,</p><p> Hakan bakaramin dadi yai min ba dan dama duk a tsorace nake da hjy mama,</p><p> Dan kada tabar mu da yun wa, gashi tare da su gwago muje bamu kadai bane, duk da sun san halin irin wasu matan a gurin kishi,</p><p> Banyan mun gama cin abinci mu kazauna nan falon hjy tsohuwa zaman hira,</p><p> Sai a lokacin Ummibanan ta farka daga barci tana ta tsala ihu,</p><p> Ruwa maidan dumi nasa mariya tadan zubo min a cup in bata tasha ,ihun da takeyi yasa gwago ce min kada in koya wa yaran fitina man,</p><p> Yaron da baya kuka indan aka kyaleshi yana kuka har zuwa wani lokaci zai koyi kukan banza daga wanan lokacin,</p><p> Har uwa tarasa gane kan yaro saboda yawan kukan da yaro zai dinga yi,</p><p> Hjy tsohuwa dake gefe guda tana jin abinda gwago ke fada tace min,</p><p> Dan Allah Fatima ki kula da wa yan nan yaran kinji, kinga uban su abin tausayi ni a duniya </p><p> Saboda shi shikadai ya tashi batare da sanin dadin yan uwa ba ,</p><p> Tanuna kofar side din hjy mama tace kin gata can bata da halin kirki ko daya,</p><p> Tunda kurciyar ta, har yanzu da girma ya kamata mugun haline tatare a zuciyar ta </p><p> Hassada da bakin ciki shike cin rayuwar ta akan wanan yaro,</p><p> Gashi diyan nata da ta nuwa wa so kamar ta mutu duk ba nagari daga cikin su,</p><p> Tun ban san ko wace ce Alhaji karami ya aura ba nake farin ciki da jin cewa wanan karon yar mutunci ce ya aura kuma yar yarinya kamila,</p><p> Nai farin ciki kwarai dajin hakan daga bakin Bashir</p><p> Saboda duk matan shi na farko sai ina ganin kamar daga, sherin hjy ce yake samun su don babu wace ta dace dashi daga cikin su,</p><p> Kawai sai labari naji cewa wai ai matar Amadu na ta haihu, bakaramin farin ciki nayi ba dajin wanan labarin gaskiya,</p><p> Tana nuna min yaran da hannu tace wa yan nan yaran da Allah yabaku kawai sun ishe ku a bin tin kaho a duniya,</p><p> Kwana nawa ne ,in ubangiji Allah yaraya, maku su za su girma</p><p> Kin ga daga wanan lokacin shi kan shi duk wani kwakwan da yakewa yan uwan shi don su shirya dashi zai ragu yadawo ga nashi iyalin,</p><p> Zuri, ar Amina ba zuri ar arzikiba ce wlh, tun farko ban so auren yaron nan da ita ba fin karfina ne kawai akayi da kuma rabon iyali atsakanin su,</p><p> Don haka ki zama mai hakkuri da mijin ki, kibawa diyan ku tarbiya nagari tayadda za su zamo abin alfahari a cikin duniya baki daya,</p><p> Shi kanshi maigidan naki na bukatar kulawar ki sosai don zan iya ce maki duk halaiyar shi guda da mahaifin shi,</p><p> Amma kinga shi mahaifin nashi rashin samun mace ra gari wace zata dinga karamai karfin gwiwa wajen kara habbaka rayuwan sa , bai sa,a da hakan ba,</p><p> Gaba daya ita gurinta shine tamallake komai nasa ita kadai sai iyalin ta,</p><p> Shine yasa kike ganin tana mugun bakin ciki da mijin ki,</p><p> Don ita aganin ta ba,aiwa diyanta , yan uba,</p><p> Wanan son kan nata yasa har ta cuci kanta da kanta diyanta suka lalace,</p><p> Ta girgiza kanta tace Allah ya shirya wa yan nan yaran,</p><p> Kamar yaron nan mai mutunci da sanin ciwon kanshi ace diyan shi sun shigo wanan garin da kitso akan su,</p><p> Tace fafir Amina ta hana akai Amadu karatu kasan turawa saboda hassada wai zai je inda diyanta suka tafi,</p><p> Sai gashi ashe alheri ke kiran shi kasa mai tsarki, don zuwan nashu yanzu yazama duk wani dan uwan mu alheri,</p><p> Don kin ga kusan duk yan uwa yai masu sanadin samun wuri madogara,</p><p> Wanan hassadan na Amina yanzu haka sai kara ruruwa yake yi akan shi,</p><p> Ganin cewa duk diyan ta ba wanda ya kama kafan sa,</p><p> Kwanaki har da sherri ta hada wai aje abincike shi yana saida haranttatun kaya akasar saudiya,</p><p> Salati su gwago suka sa dan jin abinda hjy tace tace kwarai da gaske sai daga baya ne asirinta ya tonu gurin dan karamin dan ta ,</p><p> Yai mata fallasa so sai agaban mutane saboda taki yarda ya auri baturiya ran shi ya baci yai mata tas,</p><p> Tai yar murmushin tsofafi tace ki kula da kyau da duk wani abinda Amina zatai maku keda yaran ki don sherinta yawa gare shi,</p><p> Nima kin ganni nan to zamana duk yakai mata ko ina wurin nan,</p><p> Ni kaina zaman dole ne nakeyi anan dan can kauyen mu yafi mun nan sosai,</p><p> Tace dazun da mijin ki yashigo gaida ni saida nai mai korafi akan yabarni in koma dakina koda ma mutuwa zanyi in mutu a dakina,</p><p> Jin dogon jawabin hjy tsohuwa akan mama yasa duk jikina yakara mutuwa sai tausayin sheriff ya mamaye min zucita a lokaci guda,</p><p> Nace Allah sarki ashe shiyasa yake ta damuwa akan su mama da yaranta watau shi ke son su , su basu kaunar shu sam,</p><p> Inko haka dole in kara jawo mijina ajiki dan in kawar mai da damuwar da yake ciki,</p><p> Washe gari gidan anty Falmata mukaje yini, gabadayan mu harda hjy tsohuwa tun a mota tasa sheriff agaba akan sai ya maida ita gida kafin ya wuce,</p><p> Anty falmata taimin wani irin hadaden miya nadabab tace min wai shi sukewa masu jego kafin suyi arba,in,</p><p> Kazace aka dafa taci kayan hadi da kayan kamshi, sai sauran sake saki da aka dafa su tare, da ruwan rubutu,</p><p> Tace min ko wanan nasamu naci kawai kafin in yi arba,in yawadatar amma in son samu ne sau uku yakamata inci kafin inyi arba in,</p><p> Jin haka yasa na dan faki idon su gwago nace mata tayi kokarin dafa min sauran kafin mu tashi,</p><p> Tai yar dariya tace ai zan dafa maki fadima , yadda kika nuna kina kauna na kuma kina kaunar dan uwan na ai dole ni ma in soki fiye da tsanmanin ki,</p><p> Sha kurumin ki ai kafin kubar nan zan sa aimaki komai daya kamata,aiwa mace mai haihuwar farko kamar yadda muke yi anan kasar,</p><p> Naimata godiya sosai danjin wanan harar cin nata,</p><p> Ashe gwago taji tace ke kisha kurumin ki mu kan ai indai kayan hadine gida kikazo nida kaina zan hada maki walle sai kin bide ni kinmin godiya,</p><p> Duk muka sa dariya a cikin lokaci guda, anty falmata tace ai ki kwantar da hankaliki fadima duk abinda zan yi wa kaunata ta ciki guda inshaAllah zan maki ke ma,</p><p> Saboda naga kishiyoyin ki duk yan bariki ne,</p><p> Ni tausayi Ahmad ma nake ji har ina mamakin ko ina ya gangamo da ire,iren su haka,</p><p> Dan kin ga shi mutum ne salihi wanda bai magana,</p><p> Karar kiran wayana ne ya katse muna hiran, nobar Sheriff ne nagani a wayar </p><p> Nakai wayar a kun,ne na, daidai lokacin da yake sallama a cikin natsuwa da tausa murya,</p><p> Nima dai tausa muryan nayi na ansa mai yace min yana fatan ba matsala dai ko in harda matsala yazo ya kwashe mu zuwa gida,</p><p> Cikin sauri nace mai ba komai gamunan muna ta hira har su gwago sai nani yai yar ajiyar zuciya,</p><p> Alamar yaji dadin jin duk mun sake jikin mu da yan uwan shi,</p><p> Sai kuma yace min zai zo zuwa hudu yatafi damu mu gaida mahaifin Bashir ,</p><p> Dan yana ganin gobe zamu wuce gurin su ummi dan zai koma Saudiya very soon insha Allah,</p><p> Gabana yai matukar faduwa dajin cewa zamu koma saudiya tun yanzu,</p><p> Don dai gaskiya ni nafi son in zauna nan Nigeria abina,</p><p> Duk da bai anbaci cewa dani zai tafi ba nasan cewa mawuyacin abune yabar ni nan,</p><p> Shirun da yaji nayi yasa shi cewa hello, na ansa da naam,</p><p> Ya, Ce ina fatan kin fahince ni ai ko nace mai eh kawai, yace min ok take care,</p><p> Duk hankalin su yana agurina dan ganin cikin dan lokaci kadan na canza fuskana,</p><p> Anty falmata ce may tambayar komay ke faruwa,</p><p> Ban boye mataba na fada mata cewa wai gobe zamu tafi,</p><p> Kuma soon zamu koma saudiya,gaba daya, kuma ni gaskiya bana son komawa can wallahi,</p><p> Tace cikin sauri kada ki fara kice bazaki koma ba, fadima , kituna cewa bake kadai bace fa matar shi,</p><p> Idan har baki je ba sai wata ta tafi, nadan turo baki nace su tafi mana,</p><p> Gwago dake jin mu tun fara zancen tace ke arrr, da wanga hali naki, </p><p> Wasu nason atai da su ke ko wai son zama kikai, inkin zauna zaman mi zakiyi, ke dai,anan,</p><p> Shiru nayi ina jin maganar gwago da anty falmata </p><p> Sai jikina yai sanyi da nasihar nasu don ba yadda na iya dole in bi mijina in koma saudiya kenan,</p><p> Wasu hawaye suka dan silalo min natuna cewa ko hjy maisharwali da takai ni saudiya ta dawo Nigeria abinta, da duk wasu wa yanda mukaje tare, alokacin ,</p><p> Ni kadai kawai Allah yai zamana acan ke nan, cikin dabara nagoge hawayen ahankali,</p><p> Ashe anty falmata ta kuladani, a cikin dabara tajani har zuwa cikin bedroom din ta,</p><p> Tace min fadima may kikewa kuka akan komawar ki saudiya ne ko,</p><p> Ido ta kura min taa jiran ansa na ganin da tayi banda alamar bata ansa yasa tacigaba da maganar ta, </p><p> Tace fadima ki godewa Allah da yabaki Ahmad a matsayin miji, aure, yau kuma gsshi har da zuria a tsakanin ku,</p><p> Sam kada ki dauke ni a amatsayi yar uwar mijin ki, </p><p> Kisan wasu dangin miji suna zama ma mutum abokan gaba da zaran sunga dan uwan su na son ka, sosai,</p><p> Ni tun banganki ba naji kin min kawai don gurin Bashir nake jin labarin ki wanda shima ina ganin gurin Ahmad yake dan samun labarin ki,</p><p> Nai maza nadan dago kai ina mamakin maganar ta , </p><p> Tadaga min kai tace kwarai da gaske hakane ko ki na ganin baki isa yai maganar ki a gyefe bane,</p><p> Ta ce har in ki na shakku ki daina don ni gaunau ce ba jiyau ba don a gaba yake fadawa Abba da hjy tsohuwa irin halaiyar ki, da abinda yasa har ya aure ki,</p><p> Dan haka ki shirya kawai duk lokacin da ya bukaci ku koma ki bishi kawai batare da nuna bacin rain ki ba,</p><p> Shin idan kin tsaya nan may zaki tsinta mijin anan din idan har kin tsaya,</p><p> Daga kai nayi ina mamakin ta, kodai don bata san ko shekara nawa nayi can batare da iyayyena ba,</p><p> Sai naji ansar kuma a bakinta, tana cewa kina yar karama ma ,kin inyi zama batare da iyayyenki ba balle yanzu da kike da aure a kanki,</p><p> Kenan tasan koni waye tun farko wasu hawaye naji sun sulalo min a fuska na,</p><p> Dafa ni tayi a kafada tace ki zama ma jajircewa akoda yaushe don ki lashe duk wani lanbar yabo daga mijinki ,</p><p> Ki zama mai mallake mijin ki ,koya mai yin adalci acikin ku, duk da nasan yana kwatantawa, saboda shi haka ya tashi mutum mai tsoron Allah,</p><p> Kiyi kokari ki tarbiyartan da ya'yan ki cikin hikima da dabara ki hane su ga duk wani abinda zai kaisu ga koyon lalacewa,</p><p> Hakan bazai kai ga samun nasaran ki ba sai kina kusa da mijin ki uban diyan ki, </p><p> Dan haka kada ki kara bata ranki ga wanan tafiyan ki je ki zama mai yi nayi bari na bari kamar yadda aka san ki,</p><p> Daga haka bata kara ce min komai ba sai shirun da yabiyo dakin, ido kawai ta zuba min,</p><p> Sai can nadan yi ajiyar zuciya, na nisa, nadago kai na kalle ta na ce cikin siririyar murya na gode kwarai anty kuma zan yi kokari in koyi da duk abin da kikace,</p><p> Kafin mu fito falo nai ma anty falmata godiya sosai acikin ziciya na kuma ina mai gode ma Allah da ya hada ni da ita ,</p><p> Hudu daidai sheriff ya iso inda suka kwashe mu zuwa gidan su Bashir </p><p> An muna taro na arziki so sai an kuma nuna muna so da kauna na gaskiya,</p><p> Ba mu wani dade ba saboda dare yayi mukayi sallama da su muka dawo gidan Abba,</p><p> Washe gari har hjy tsohuwa muka dunguma zuwa garin su can wani local government ne,</p><p> Ummu ta tare mu cikin jin dadi dakuma murnan ganin yan jikokin ta duk tana kokarin boye wa,</p><p> Nikan sai ince gida nazo don gidan wan mahaifinane nazo,</p><p> Aiko zuwa dare nan da nan yan uwan su Shehi dake zaune agari aka diga shigowa gani na ni da mariya,</p><p> Duk wanda ya gan ni sai ace wai lalai, mun mafi diyan shi kama da shi,</p><p> Hjy tsohuwa tasa fitina akan dole gidan ta da zamu sauka dan haka kwana guda kawai nayi a gidan Shehi na koma gidan hjy,</p><p> Duk da Sheriff yafada madu mun fasa yin kwanakin da mukayi niyar yi anan da farko ,saboda wasu dalilai da suka taso daga gurin aikin su,</p><p> Gyaran jiki sosai akai min dakuma kitso irin nasu na yan maiduguri,</p><p> Gajikin jego dake samun kyakyawan kula ga kuma adon da aka yarfa min a,jikina </p><p> Haba ai sai kawai na ko.a kamar wata bakar balaraba can</p><p> Tunda nazo bamu kebe da Sheriff ba sai yau muka hade a dakin hjy tsohuwa, </p><p> Ina zaune ina bawa Abbazannah nono yashigo tundaga kofa dakin idon shi na akai na duk daga mutane adakin yau sheriff baiji kunyar kowa ba,</p><p> Kallo guda nai mai naga irin kallon da yake min sai da gaba na yafadi sai kuma yabani tausayi,</p><p> Don a gaskiya yana da hakkuri sosai namiji lafiyye kamar sheriff mai mata uku yazauna kwana da kwanaki hakanan,</p><p> Cikin murya kamar ta mai kasala yake min magana yace fadima maganar su gwago ne da man nazo dashi,</p><p> Saboda gobe da mun koma ranar jumma,a da asuba zamubar kasar nan,</p><p> Duk da naso in daure amma sai nakasa nadogo da sauri na kalle shi,</p><p> Murmushi yai min kawai yaci gaba da zancen shi,</p><p> Don haka ko can tare da su zamu tafi tunda maigari da kawu sunce sai kunyi arba,in kamar yadda al,adar hausawa take,</p><p> Don hakane ma tun muna maiduguri na bugawa maigari na sheda mai cewa yayi hakkuri dasu zamu tafi, gabadaya </p><p> Wani irin murna naji ya sauka min azuciya na, wanda banko iya lissafawa,</p><p> Yace saboda agaskiya naji dadin zuwan su tare da mu sosai saboda irin kulawar da suke ba ku akai da kai,</p><p> Azuciya na ko cewa nayi aini nafika jin dadin hakan don ni zama dasu sai jinaje kamar da innata nake zaune,</p><p> Saboda gwago ta canza sosai saikace ba itace mai hattarata ba da ake zaton cikin shege da shi,</p><p> Sam banga laifin su don sona yasa sukai min haka yanzu ko da suka gane gaskiya sun fi kowa farin ciki,</p><p> Muryan shi naji yana cewa ina fatan zaki masu gamsashen bayani ko,</p><p> Godiya nafara mai sai kawai naga yadaga min hannu, alamar bai so </p><p> Ina jin lokacin da Sheriff ke shedawa Ummi zan cen airen Amal yace bazai dade zai dawo dan ayi bukin takoma can </p><p> Naji dadin jin haka don ko ba komai zan samu yar uwata a kusa dani,</p><p> Don haka nafara mata sherin cewa duk tafiyan mu guda nida ita tunda zama kasar mu yagagareni,</p><p> Munyi sallama da yan uwa cikin wani yanayi kamar kada mutafi dan dan sabon da mukayi da jama,a,</p><p> Gwago da mama matar mai gari jin labarin tafitan su sukayi kamar almara,</p><p> Don basu taba zaton haka ba,</p><p> Saiga shi cikin ikon Allah tafiyar yazo masu a cikin sauki,</p><p> Mariya ko ina ga tafi kowa murna dan ina fada mata tai wani ihu ta kankamay ni saboda farin ciki,</p><p> Da kanta taje yiwa sheriff godiya,,</p><p> Kamar yadda yace hakan ne yafaru don da Asuba muka bar Abuja zuwa saudiya,</p><p> Inda muka sauka ta jidda don haka Makkah direct muka nufa,,,,,, </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎</p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 9⃣4⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almost true life story,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Allah yakawo mu gida lafiya cikin dare muma shigarin makkah,</p><p> Mun samu maman Umar a gida tai muna taro na musan man,</p><p> Sai murna take yi daganin mun dawo tare da yar ta lafiya,</p><p> Ba karamin chanji nagani ba a gidan amma dayake nasan halin sheriff, da son abubuwan zamani dan shi bai jin zafin sayen abin rayuwa a gidan shi,</p><p> Sai dai may azuciya wani irin kallo nake wa gidan sai kace yau na fara zuwa ciki,</p><p> Ina tuna cewa a wanan gidan ne fa nasamu cikin da zankira da rabo,</p><p> Murmushi kawai nayi azuciya dan nasan ba,a wasa da ikon Allah,</p><p> Dakina na aini hi na shiga da niyar zama kasan cewa nasan cewa sama na Aziza ne da Sheriff,</p><p> Ina tsaye a tsakiyar dakin ina kallon yadda maman Umar ta gyara min shi, tas,</p><p> Sai naji an banko kofar dakin da karfi, cikin firgita nadan waiga dan gani kowa ye haka,</p><p> Sheriff ne nagani a tsaye yana min wani irin kallon mamaki ,</p><p> A hankali ya karaso har inda na ke, tsaye,,cikin fuskan mamaki yake ce min, sai bangaki adaki ba shiyasa daman nasa rai cewa kina nan,</p><p> To may kuma zaki anan din, don naga kayan ki nan,</p><p> Saida na kai zaune bakin gadona ina kokarin gyara, wani dan kit din yan kunen da na cire a kune na,</p><p> Nace cikin sanyi murya Sheriff ina zan kai kayan nawa to,</p><p> Ina ce nan ne dama dakina a gidan, ko, </p><p> Yar murmushi yace a da ke nan ko Fatima, yanzu kema kin san cewa kin wuce zama a kasa saida sama ko dan kici gaba da kula da Sheriff din ki kamar yadda kika saba ko,</p><p> Murmushi nayi nace aiko anan zan dinga kuka da shi fiye da tsamanin shi,</p><p> Wani irin laulausar murmushi ya sake , yace umurni na bayar bawai fa shawara nazo bayar wa ba, </p><p> Sai kawai yajuya da niyar barin dakin bayan shi na bi da kallo dai dai lokacin shi ma ya juyo gareni,</p><p> Yace min mariya ta dawo wanan dakin ita da Aisha su gwagwa su zauna dakin da Amal ta fita, dan nasan cewa baza su yarda araba masu daki ba,</p><p> Kai kawai na kada mai ina son ince mai idan Aziza tazo fa yaya zanyi zan kara barin dakin ne kamar yadda tai min a madina,</p><p> Kamar yasan tunane na sai yace ko kina ganin a halin yanzu akwai wata matar da zata zo nan tace ki bata daki har ki yarda ki bata kamar yadda kikayi a baya,</p><p> Murmushi nayi don tuno da wanan lokacin da yake magana, don ni kadai nasan irin kukan da nasha a wanan lokacin </p><p> Ga ciki ajikina ga tashin hankalin Aziza,da tasani agaba saboda hauka, </p><p> Murmushi nakara yi na Allah nagode ma da baka sa na biye ma aziza ba, muka dinga hauka alokacin,</p><p> Tashi nayi na nufi kofar daki dan in diba su gwago in masu bayanin inda zasu zauna </p><p> Suna tare da maman umar anata labarin abin da ya shafi cikin garin makkah da kewayenta,</p><p> A cikin larabci nai mata bayani nakuma bukace ta data kai su gwago su yi umurah zuwa gobe idan mun huta,</p><p> Tare da mariya muka hau sama don ganin dakin da aka umurceni in koma ciki,</p><p> Dakin na nan a gyare kamar kulun sai kamshi ke tashi cikin shi, tankar a kwai mutun adakin,</p><p> Wardrobe na fara zuwa na bude dan inga komay ke cikun shi,</p><p> Kayane ciki na mata birjit sababi fil a sheke ko ina dasu,</p><p> Gurin dressing mirrow na nufa abin mamaki kayan shafa ne irin na mata babune kawai babu agurin,</p><p> Mamakin yaushe akai wanan abin ya kamani sosai ,dan dai a,gaskiya abin yabani mamaki so sai,</p><p> Itako mariya sai santin dakin takeyi tana cewa kai anty fafima shine har kika iya barin nan kika gudo zuwa gida,</p><p> Cikin mamaki na kalleta nace lailai ma mariya da sauran ki,.</p><p> Anfada maki cewa akwai inda yakai gida dadina agurin duk wani dan halak,</p><p> Da taimakon ta muka sa komai inda yakamata daga cikin dan abin da mukazo da shi,</p><p> Su gwago duk mamaki da imani yakashe zukatan su,</p><p> Wai ace a wanan kasar nazo tundaga dogon daji yar karama da ni nai rayuwa a cikin ta batare da iyayyena ba,</p><p> Matan maigari mama tace gaskiya rashin sanin yanan kasar yasa har wasu yan sheri sukayi saurin zarga wa wanan yariyar sheri,</p><p> Gwago tace ni wallahi har kunya nake ji idan an tuna wanan maganar, </p><p> Saboda alokacin idona ya rufe sai nake ganin maganar su tumba itace gaskiya kamar yawon bariki ne kawai yariyar tazo yi,</p><p> Tabata muna sunan zuri,a don duk wanda zaiyi magana cewa zai yi ai iyalen gidan mu ne,</p><p> Amma tun wani rana da tazo gidan mu yini a hiran su da kawun ta nagane cewa tana da aure duk yadda akayi </p><p> Saboda duk bayanin ta acikin natsuwa taiwa malam shi,</p><p> Mama tace kedai bari agaskiya zato zunubi ne sosai wallahi,</p><p> Suna cikin wanan hiran sai ga sheriff yace ai sai su fito za akai su suyi umurah,</p><p> Don ba kyau mutum yazo garin makkah har ya kwana batare da yayi umurah ba indai har farkon zuwan mutum ne,</p><p> Fitar su gabada a lokaci guda yasa nagane cewa zaman su a tare da ni yana da matukar amfani,</p><p> Don ni kadai na dinga lalurar yaran kafin su dawo,</p><p> Gaba daya tun fitar su gidan ina sama tare da yaran , duk na rude na rasa yaya zan yi dawainiyar su ni kadai,</p><p> Azatona tare da sheriff suka tafi yin dawafin, ashe shi har yatafi yayi ko yadawo,</p><p> Dakin yashigo daure yake da bath robe, zaune ya samay ni ina kokarin sawa Abba permpers ga kuma ummi tana ta tsala ihu daga kwance,</p><p> Cikin sauri ya dauko yarinyar ya rungumay ta a jikin shi,</p><p> Sai kuma ya koma kallon wanda nake sawa permpers din shima ya fara kuka ,</p><p> Wata irin ajiyar zuciya yayi don har cikin ran shi na bashi tausayi don yar karama dani ya zanyi rainon yara biyu alokaci guda</p><p> Duk da kwazon da yasan ni da shi lokacin ina yarinya so sai,</p><p> A hankali yazo inda nake zaune rugumay da yaron a hannu na ya hada mu gaba daya ya rungumay,</p><p> Kuka na fashe da shi kawai, batare da ya bani hakkuri ba yana nan rike dani har nadan ba kaina hakkuri,</p><p> Yace min Fatima cikin murya mai rauni, baki godewa Allah bake nan ko,</p><p> Allah mai kyauta da kari shine yai maki wanan baiwar a lokaci guda,</p><p> Kina son ki nuna mai cewa baki gode bane ko kuwa,</p><p> Yadan kara mannani ajikin shi yace nasan ki da kwazo sosai na san cewa zaki iya wanan dawainiyar </p><p> Amma kuma nasan cewa a yanzu baki saba da wanan harkan ba yana daga cikin hikimar da nayi don zuwa da su gwago har zuwa lokacin da zaki dan saba da lalurar su,</p><p> Yakare zancen yana mai ce min kikara daurewa, ki kula da yaranki,</p><p> Kiyi kokari cewa duk wani bukatar mu nida yaran mu kin kokarta kin muna shi,</p><p> Idan kin muna haka, ki kingama muna kimai don mun zama yan gata agareki,</p><p> Jin kalaman shi yasa nadan murmusa, kamar banice mai kuka ba yanzu,</p><p> A hankali na ce baku da matsala daga yau insha Allah, </p><p> Yace to ki rikeni amana nida yarana pls,</p><p> Rugumay shi nayi nace in sha Allah zaka samay ni mai rikon ku amana,</p><p> Yadan mike ya lakuto min fuska yace to koke fa ,</p><p> A, hankali na ce nagode da wanan fadakarwan,</p><p> Yace ni dai zan gode maki nida kika yi wa wanan kyautar </p><p> Kin mayar min da gida na kamar yadda kowani magidan ci ke bukatar gidan shi ya koma,</p><p> Kin ingata min rayuwana kullun acikin godiyar ubangina, nake da ya zanto na mallake ki amatsayin mata ta uwar diyana abin alfaharina ako yau,she,</p><p> Dariya maganar shi tabani daidai lokacin na aje yaron dake a hannu na tafi daniyar in karbi yarinyar da tai barci a hannu mahaifinta,</p><p> Ji nayi kawai ya nemo bakina ya manne da nashi, wuri daya,</p><p> Can wata duniya muka tsinci kan mu cikinta, irin duniyar nan mai mantas da mutum inda yake,</p><p> Saida ya gaji dan kanshi ya sake ni ya juya da sauri yabar dakin namu,</p><p> Bayan shi nabi da kallo yana mai bani tausayi don hakkurin shi bai sa ka gane damuwar shi,</p><p> </p><p> Sai dare sosai driver yadawo da su gwago saigasu da tsarabar su him wai sun fara sayen tsarabar da zasu kai gida,</p><p> Alokacin har na fara barci saboda na gaji da zaman motar da mukayi, dazun,</p><p> Jin motsin su ne yasa ni saukowa dan in masu sannu da zuwa </p><p> Ganin su da kayan danayi anata warewa yasani tsayawa turus cikin mamaki,</p><p> Sai kuma abin yabani dariya, nace gwago wanan kayan fa sai ce min tayi wai tsaraba ne suka fara sayi,</p><p> Matsawa nayi kusa da su nace haba gwago indan kun tashi aini da kaina zaikai ku kusayi duk abinda ranku ke so insha Allah,</p><p> Amma ai wanan duk tarkace ne kuka kwaso yan riyal goma goma,</p><p> Cikin mamaki gwago takalleni tace haba fadima ,</p><p> Ina mukaga wanan acan balle kice muna tarkace ne,</p><p> Kedai kawai bari mu fara aje abin mu idan lokacin yayi sai mukara kawai,</p><p> Abinci nasa maman Umar ta kara gabatar masu sanin cewa dani sun shawo wahala acan dole suji yunwa yanzu</p><p> Murnan kayan ma ya hana gwago cin wani abinci,sosai sai kallona tayi tace min wanan matar zata kai mu inda akesa hakuri gobe,</p><p> Ido waje nake kallin maman Umar wace tai masu alkawarin zuwa sa hakorin gwal,</p><p> Nace gwago ai,zaku sa amma ku bari akaiku inda ake sa na kwarai a madina,,</p><p> Cikin sauri mama da tun da muka fara zancen batai magana ba tace aiko na nan a samuna duk dayane ai,</p><p> Ruwan lemo gwangwani gwago takaiwa bakinta saitake ce min wai may yasa baki sa hakori ba duk zaman ki a kasan nan,</p><p> Dan murmushi nayi nace wallah gwago ban taba yin wanan tunanen ba arayuwata,</p><p> Taiwani tabe bakin ta,baki tace wagga diya kan ai halin ta sai ita,</p><p> Ita ko dan kurin nan da matan masu kudi kayi banga tanayi nai ba,</p><p> Dani da mariya duk dariya mukasa mata har da maman Umar wace ke kokarin zuba masu abinci,</p><p> Duk hiran mu a she Sheriff najin su yana zaune inda yake zama don ansan sakwan,nin shi,</p><p> Karar watan shi naji ana kiran shi yasa nagane cewa yana cikin falon ashe,</p><p> Satin mu biyu da dawowa saudiya mun murje mun yi kyau daga ni har yan rakiyar mu ga wani irin kulawa ta musan man da muke samu daga sheriff gaba dayan mu,</p><p> Nida yar kaunata mai kaunata fiye daduk yadda zan yi bayani mariya,</p><p> Tare yau muka tafi wurin gyaran jiki, duk wani abinda za,aiwa mace dan gyara ta an muna shi nida ita,</p><p> Mun yi kyau sosai amma sai naga mariya duk tafi rude ma nawa kwalliyar,</p><p> Tunda muma dawo gida nasa mu yaran sunyi kuka an dan lalashe su,</p><p> Ina zaune falon mu ina basu nono kaina ba dan kwali don tun shigowar mu nacire duk lailaiyar jikina wata yar body hook ce na sa mai ruwan Ashe,</p><p> Sheriff ne yashigo alokacin da alama daga gurin ma,aikatar su na Company maita kasar saudiya yake saboda irin kayan shiga mai katar daban ce,</p><p> Kallo guda yai min sai naga yanayin shi ya canza lokaci guda, </p><p> Sama yahau yana shiga dama ya debo gajiya a jikin shi, wanka ya fada kawai dan yadan ji dama,</p><p> Tashi nayi naje dan in tare shi ganin da nayi ya shiga wanka yasa nadauko mai simple riga doguwar jallabiya na aje mai, da turaren shi da kuma yar hullar shi,</p><p> Komawa nayi dan jin kiran sallah da akeyi a cikin tv nasan cewa zai fito da sauri ya tafi massallaci ne,</p><p> Dakina koma nima dai wanka nashiga saida na gyara jikina, ,</p><p> Nafito don in gabatar da sallah na ina a rakar farko Sheriff yafado cikkn dakin nawa, alokacin cikin mamaki yake kallona don sam baisan nafara sallah ba</p><p> Ganin ina sallah yasa tabar dakin dan yana da online meeting alokacin,</p><p> Maki nai fam a,zuciyar shi tun yaushe nafara sallah ne bai sani ba,</p><p> Inko har nadade dafarawa gaskiya ban kyauta mai ba,</p><p> Bai samu dawo dakin ba har wani lokaci saboda meeting din yadan dauki lokaci a tsakanin su,</p><p> Dan suna son a canza launin aiyukan su na kowani kasa, yanzu don cigaban da ake samu,</p><p> Dole sai sun hadu a Dubai anyi meeting na face,to face,</p><p> Zuwa gobe insha Allah,</p><p> Mariya ta kwaso min yaea saboda dama karfe taran dare, nake shimfede yaran,</p><p> Bayan ta kwantar min dasu ne take ce min ita zata shige kenan don duk agajiye take yau , saboda dadewar da mukayu a wurin gyaran jiki,</p><p> Tabarni ina sa yar rigar barci na mai ruwan pink da yar adon duwatsu bakake, amma ba ainihin stone bane,</p><p> Kamshin jikina ko daga nisa kake zaka iya shakan shi, dan man baki na shafa ina kokarin in je in, ma yara addu,a naji an turo kofar daki na,</p><p> Mamaki naji dana ganshi sama a yanzu don nasan cewa sai kusan shadaya da wani abu yake baro falo koyau saboda tarin aiyukan dake gaban shi,</p><p> Cikin mamaki nake kallon shi har ta iso inda nake zaune gaban mirror</p><p> A saman mirror ya dan jinki na jikin shi,tadan baki baki,</p><p> Sai nai dan dum saboda ban sam may yakawo shi ba awanan lokacin,</p><p> Magana yafara yi cikin yanayin damuwa da kuma tausayi,</p><p> Yace haba maman twins, tun yaushe kikafara sallah ban da labari,</p><p> Gabana ne yai wani irin dam don ban tsanmaci wanan maganar zai min ba sam,</p><p> Kasa magana nayi sai kuma wani irin rudanin da nashiga cikin lokaci guda,</p><p> Shirun da taji nayi yasa yakara maimaita tambayar shi, </p><p> A hankali nace mai tunda muka dawo da kwana hudu,</p><p> What, ya fada cikin zaro ido sai kuma naji yace subbahanallahi,</p><p> Yai shiru nadan wani lokaci,</p><p> Sai ya sake tausasa murya yace haba Fatima baki tausayin dan bawan Allah,</p><p> Shin kiko san halin da nake ciki Fatima, kalli fa yadda na koma na ramay duk na wani lalace, nayi wani irin baki duk saboda rashin tsarkin ki,</p><p> Shim kiko san halin da nake ciki kuwa,</p><p> Yaidan shiru nawa lokaci sai yacigaba yace,</p><p> Allah ma ,yasan nayi hakkurin wallahi, don tun barin ki saudiya rabona da mace,</p><p> Jin wanan kalamin yasa nadaga ido da sauri na kalle shi mukayi ido hudu ya kada min kai yace kwarai da gaske Fatima,</p><p> Cikin yar siririyar a</p><p> a na ce mai yi hakkuri, ban san cewa haka ake yi ba,</p><p> Magana ta dariya tabashi, har ina dan iya jin sautin dariyar da yayi,</p><p> Yace Fatima ni nasan baki san yadda abubuwa suke bane kasan cewar ba agaban inna kika karasa girman ki,</p><p> Amma duk da haka kina kokarinki, shiya sa koda yaushe nake maki fatan alheri, dan kina da saurin fahintar da muta,</p><p> Kiyi hakkuri ki tsimake ni Fatima basai munyi koyi da al,adaba ba kamar yadda su gwago suke nufi,</p><p> Ina bukatar kasancewa da ke Fatima, ako yaushe amma sanin yadda al,ada yake yasa nake kokarin jajir cewa zuciyana,</p><p> Kullun da wanan abin nake kwana araina dashi nake tashi,</p><p> Kaina da ke sunkuye nadaga da sauri na kalle shi danjin yadda muryan shi ke sarkewa alokacin,</p><p> Ban san ya akayi ba sai kawai na tsinci kaina da rugumo sheriff zuwa jikina,</p><p> Wani irin ajiyar zuciya naji ya sake lokaci guda tare da kai hannu shi a saman jikina,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 9⃣5⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost True Life Story,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Yan uwa kutaya mu murna mun samu, karuwar, Sister MAIJIDDA HARZIMI ta huguma group ta haihu jiya mun samu baby girl, Allah yasa mata albarka a rayuwan ta naduniya da lahira,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Sheriff a ranan godiya yai wa Allah dan bai taba sanin mace nada wani fa,ida na musan man ba sai kan Fatima,</p><p> Don farin cikin kasan cewar shi da fatima baya ko misalttuwa,</p><p> Yana rugumay da ita bayan komai yakan,mala, a tsakanin su,</p><p> A hankali yakira sunan ta cikin wani yanayi mai nuna jindadin kasan cewa a tare,</p><p> Idona a lunshe na ansa mai cikin shagwaba,,</p><p> Yace Fatima kin taimakawa rayuwa ta daki yardan min nakasance dake a yau dan da ban san halin da zan shiga ba,</p><p> Kasan cewa dake wani abune tankar rabin rayuwata, </p><p> Duk abinda namiji zai bukata gurin mace Allah ya wadatar maki shi Fatima,</p><p> Idan har zanci gaba da samun kula irin wanan daga gareki , </p><p> Kingama da rayuwata Fatima,</p><p> Dadi yasa ni na kara kankame Sheriff, nai yar murmushi,</p><p> Yace baki ce komai ba to, saida na lunshe idona sai kuma nadan bude nace may zance maka, sheriff,</p><p> Da sauri naji yace min la, la,la bana son sunan Sheriff din nan pls,</p><p> Nace sai may ,yace acanza min pls,</p><p> Yace wanan sunar masu aikina kawai zasu iya kirana dashi,</p><p> Nace ainima har yanzu ina cikin masu aikin ka don haka ina neman izini abarni in dinga fadin haka na pls,</p><p> Nadan marairaice muryana kamar zanyi kuka,</p><p> Ya jawo sosai cikin jikin shi yadan rada min akune na yace wayo kike son kimin ko,</p><p> Yar dariya nai mai nace aigaskiya na fada saboda sunan yana min dadi idan nafada,</p><p> Dan shiru ya,biyo bayan zancen nashi, sai kuma yace yadda kike so, kawai,</p><p> Yace gobe zan tafi Dubai kuma ina sa ran zan dan yi kwanaki acan, insha Allah,</p><p> Inda su gwago basa nan da daku zamu tafi kawai muje can mu huta</p><p> Da sauri nace mai hutu kuma aiko yanzu muna hutawa, nan, ma,</p><p> Hmmm kawai yace dan baki san cewa rashin ki a kusa da ni yana haifar min da wata illa, ce ba,</p><p> Dan haka yanzu sam bana son abinda zaikai har muyi wasu kwanaki bakwa atare dani,</p><p> Haka mukai ta hira wanda zance sai yau muka dan yi magana mai yar tsayi sosai dashi,</p><p> Yana barcin shi agefe na hankalin shi a,kwance,,a hankali nazamay jikina ganin da nayi yaran sun fara motsi alamar zasu iya farkawa anytime,,,</p><p> Wanka naje nayi alokacin , saboda in tsarkake jikina, kada yaran su falka, daga barci,</p><p> Fitowana kuwa ummi ta ,tashi, nadauko tà nafara bata nono,</p><p> Ina zaune ina bawa, ummi nono,,ina karewa sheriff kallo, nai wa Allah godiya da mallaka min sheriff a matsayin mijin aure na, kuma uban diya na,</p><p> Sai asuba yatashi yakoma dakin shi don ya kintsa ma tafiyar su da wuri,</p><p> Karfe bakwai na safe duk komai ya kan,mala ko, yai sallama da su gwago, </p><p> Yadan dade dayaran a hannun shi san,nan ya a jesu yatafi, cikin ran shi yana jin shi cikin farin ciki, da anshuwa, ayau,</p><p> Haka rayuwa, rayuwar mu tacigaba da guda agidan sheriff tare da su gwago na da yan zu kusan watan su biyar kenan tare da mu, acan,</p><p> Sheriff yai alkawarin da zaran an gama aikin hajji na bana za,adawo dasu gida insha Allah,</p><p> Yarana sunyi bulbul da su gwanin ban sha,awa duk wanda ya gansu sai yai mamakin irin girman da sukayi a lokacin,</p><p> Yanzu Sheriff arzikin shi ya bungasa sosai don hannun jarinsa da yasa a cikin company Abu Abdallah ya samu riba a yan shekarun nan mai girma,</p><p> Al,amari da larabawa babu cutarwa aciki don haka su da kan su suka bukaci ya bude company kanshi a kasa shen turawa, da kuma wasu kasa a Africa,</p><p> Don haka batare da bata lokaci ba, yadukufa wurin wanan aikin har Allah yasa komai ya kammala,,</p><p> Cikin dan Lokaci kadan sai gashe ya tsewa wa duk wani sa,an shi,</p><p> Farin cikin mu a kullun kara karuwa yakeyi a gidan mu,</p><p> Matsalata daya shine har yau ina fargaban zuwan aziza a garin saudiya,</p><p> Saidaga baya nake jin cewa ai Sheriff ya saketa tun wancan lokacin da takai muna takaka agida ranan sunan su twins,</p><p> Kuma an mata dokar hana shigowa kasar saudiya tun lokacin har ita ranta,</p><p> Matsalar mu yanzu itace hjy mama kawai da iyalin ta,</p><p> Saidai duk wani sheri da zatayi wa sheri bai ko kawowa gareshi Allah ke kare shi,</p><p> Sam ban san cewa Sheriff ya biyawa su inna makkah ba dan bai fada min ba,</p><p> Sai kawai baki mukayi daga Nigeria ganin bazata mukayi masu,</p><p> Abin yaban mamaki matuka,dan ,daga Inna, da hafsi,da kawu, sai wasu mutum biyar a bangaren mahaifina, maigari, da malam Basiru, </p><p> Wanda wai yazo ke nan da zama shida matar shi wace har yau Allah bai basu haihuwa ba,</p><p> Aiki zaiyi ma sheriff a,daya daga cikin ma,aikatar su, da ke nan kasar saudiya,</p><p> Tsohon gidan sheriff na mai,katar su da muka taso, a can aka sauke bakin mu </p><p> Mutum goma a bangare na goma bangaren shi sai goma side din nafisat,</p><p> Mutum, Talatin cur suka zo sauke farali, daga kasar Nigeria wanda sheriff ya biyawa,,</p><p> Dana zauna nai nazari sai naga cewa aini anawa bangaren nafi su duk jama,a, ai, don ga su gwago da mariya duk zasuyi aikin hajji bana,</p><p> Maman umar tasamo min yan takari mata da maza su ashirin daga fannin girki da gyaran gida da aike duk mun tanadar ma wanan fanin masuyi muna su,</p><p> Tun zuwan su inna da sauran jama,a bamu da hutu agidan mu don haka , nima nai niyar bin yan uwa dan sauke farali, </p><p> Ashe da sauran jama,a atafe don fanin su Ummi suna hanya andan samu matsalar tasowar su, </p><p> Abin yabani mamaki kwarai da gaske dan ban ji zancen aikin hajji gs bakin sheriff ba,</p><p> Saida naga duk wani abinda nakeyi nakuma tabbatar da yarana sunyi barci,</p><p> Cikin shigar wata rigar barci mai kyau dakuma daukar sha,awa nake,</p><p> Sai kamshin turaren dake tashi ajikina don tun yarana suna kanana bazaka taba jin cewa ina karnin nono ba sam, </p><p> Idan baka ga ina shayarwa ba baka ganewa,</p><p> Yana zaune da alamar bai,dade da fitowa wanka ba, yana diban wasu takardu a hannun shi,</p><p> Dan karamin tire ne a hannu na wanda ke dauke da cups guda biyu, sai spoon a,gefen tire din,</p><p> Tun da na shigo dakin ya kafe ni da ido har nakai tire din saman dan stoll din dake gefe na aje,</p><p> A hankali najuyo zuwa inda yake tsaye bakin save din shi,</p><p> Ta bayan shi na zagaya na rungumo shi, inajin lokacin da yai wani ajiyar zuciya, </p><p> Kaina na aza a,saman bayan shi nadan lafe nawani lokaci, inajin shi yana murmushi,</p><p> Can naji yadan kira suna na yace Fatima na ansa, cikin kissa, </p><p> Yace baku kwantaba ke nan,</p><p> Nai yar ajiyan zuciya na zagayo ta gaban shi, still ina rike da shi, </p><p> Nace cikin murmushi ya zan kwanta ban gama hidimar maigida ba,</p><p> Murmushin jin dadin abinda nafada har cikin ran shi yayi,</p><p> Ya girgiza kanshi yace ina alfahari dake fatima na san cewa duk wani lalurana kina kokarin kiyaye wa, duk da wahalan shayar min da yara da kike yi,</p><p> Nadan yi murmushi daidai lokacin da na riko hannun shi zuwa daidai kuguna yarike ni,tsab yana mai sun,sunar wuyana zuwa kaina,</p><p> Nace ai lalurar yara duk kan mu keyi tunda in kana gida kaine mai kula da su,</p><p> A cikin saitin kunne ya rada min yace ai ya kamata ki shirya daukan wasu baby din haka na ko tunda wayan nan sunyi wayo,</p><p> Bansan lokacinda nai kokari kwace kaina dafa rikon da nasa ysi min ba,</p><p> Girgiza kanshi ya kara yi yace cikin kashe murya yana kashe ido yau din nan nake son yi ma twins kanne insha Allah, </p><p> Dariya maganar tabani sosai kafin ince au har ka manta da fadan gwago ke nan ko,</p><p> Yajanwoni zuwa jikin shi sosai kamar za mu hade guri guda yace ai itama abin alfaharintane ai ace mun haifa mata jikoki da yawa,</p><p> Kawai kiyi addu,an Allah yakawo masu albarka ban son raki, idan anzo zace a fake ga gwago, ta ce,,,,,,</p><p> Ina dariya na dan kwace kaina zuwa bakin gado,</p><p> Saida na zauna sosai in fuskantar shi na ce nazo in yi godiya fa,</p><p> Yadago kai da sauri yace namay fa nace na Alhazai da aka kawo saudiya batare da sani na ba,</p><p> Hannu kawai yadaga min batare da nakai karshen zance ba yace nafada maki ba godiya atsakanin mu fadima,</p><p> Shin dakike fadin haka wai,mako kinsan cewa wallahi kunyar inna nake ji haryanzu don narasa may zan mata wanda zai sai taji dadi tabon rashin ki da taita fama dashi,</p><p> Abu guda Bashir yai min dabarar yi shine kada in bari su komada ga ita har hafsat Abdull kuma za,azo min da shi daga Maiduguri, ne,</p><p> Bansan lokacin da jin dadin wanan maganar ya sana furta I love u my Sheriff, </p><p> C ,U ya ce min tare da yar dariya yace ai badan ke nayi ba dan twins nayi hakan don su kara shakuwa da kakan su,</p><p> Wani irin kunya naji da tace haka dan nasan cewa maganar shi gaskiya ne so sai hakan zai sa yara su san inna ce kakar su ta fannin uwa duk da mu talkawane na gaske,</p><p> Tunda naji cewa su inna bazasu koma da sauran jama,a ba yasa na fara murna har ban iya boye jindadi na,</p><p> lnna ce kawai nake jiwa dan nasan cewa za,a kwashi yan kallo kafin ta yarda ta zauna damu,</p><p> Sayayya sosai nai wasu gwago don tafitan su gida,</p><p> Duk kan su an saya masu gadaje acewar su zasu kai wayaran su ne,</p><p> Sai tsarabar riguna jakkuna,da kuma su dardumar sallah masu kyau,</p><p> Sheriff yai kokari sosai gaskiya don kayan su a cargo akai don a auna masu shi,</p><p> A madina muka hade duk kan mu da sauran alhazai, </p><p> Wa yanda sheriff yakai duk agidan mu suke basu gani na akoda yau she, saboda kulun busy suke,</p><p> Kwanan mu goma muka dawo makkah don hawan Arafat,,,</p><p> Motocin maikatar su sheriff guda biyu irin dogayen luxurious din nan dasu mukai ta jigila duk inda zamu,,</p><p> Don haka bawani dogon binciken da ake muna dan ganin tambarin maikatar su da akeyi a jikin motar yariga kuma ya kama muna hema inda zamu zauna,</p><p> Duk inda zamu shida salim ke daukar yaran ko malam Basiru,</p><p> Don haka bazance nawa sha wuya ba a wanan aikin da muke yi, ina manne da innata ko kuma sheriff,</p><p> Munji dadin aikin sosai , don abin yazo muna cikin sauki,</p><p> Alhamdullah anyi lafiya ankare lafiya duk wani wanda yazo karkashin sheriff yasamu kyauta sosai,</p><p> Gashi kuma da dabi,ar zuwa, shi kadai a massalaci yabada zakkah ko kuma sadaka mai tsoka wanda sai mutum ya girgiza,</p><p> Zakkah bana a dogon daji ya aika dasu saboda ganin irin wahalar da mutanen kauyen mu ke fama dashi, </p><p> Ko maigari bai sani ba don yana saudiya gurin mu Bashir ne yakai ma su can kamar yadda sheriff ya bukaci, malam Basiru yai list ,,,</p><p> Waya kawai suka bugowa maigari cikin farin ciki suna sheda mai irin alherin da,akai masu dakuma ragunar layya da aka kaiwa, sauran iyalin su kawu a,gida da na maigari,</p><p> Ina sama ina gyara ma sheriff, daki, mariya takirani a waya, in sauko ina da baki a falon mu,</p><p> Ban bata lokaciba na sauko zuwa kiran da ake min,</p><p> Da mamaki nadan tsaya ina kallon su, su kawune tare da maigari da sauran abokan tafiyan su yan uwan nafisat da Sheriff, din mu,</p><p> Da sauri nasa akawo masu abinsha nakuma bada umurnin ai, masu,abincin cikin sauri,</p><p> Guri, na samu nadan tsuguna daga gefe ina gaishe su cikin ladabi,</p><p> Nasheda masu cewa maividan baigari yatafi Riyadh yau da safe amma zuwa gobe zai dawo, insha Allah,</p><p> Anan mukayi ni da bakin mu ina ta yi masu hidima,,</p><p> Gabadayan su sun yaba da halaiyan mu na girma ma nagaba da mu dagani har maigidan, </p><p> Sukuma sheda min cewa daman sun zo suyi mai godiya suka yi mai barka da saukowa Arafat,</p><p> Naji dadin hakan da sukayi dan haka nima nai madu kyautan da badu zaci samubadaga gareni, </p><p> Ni e sukar suyi wa mutanen gida tsaraba dashi, sunji dadi sosai inda suka shiga samin albarka da fatan gamawa lafiya,,</p><p> Sheriff nadwo wa na sheda mai zowan yan tsofafin gida ai bashiri yasamau su a masaukin su, da kanshi,</p><p> Donshi gurin shi ,shine yakamata ya tafi,gurin su neman albarka,ai,,,,</p><p> Ance sabo turken wawa da kukan mu, muka rabuda su gwago ranan da zasu koma su kuka mu kuka, </p><p> Sai zabga godiya sukeyi wa sheriff wanda ke tsaye yana kallon mu cikin dakewar zuciya dan shima yaji kamar a,ce da mu zasu zauna anan, ba,zasu koma ba,</p><p> Gwago sai washe hakiran gold takeyi abinta wanda yai mata kyau cif a,fuska,,, </p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI* ✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 9⃣6⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA🐎</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Almoy True Life Story,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Wuce wan su gwago yasamu cikin halin damuwa sosai musan man yaran da suka yi wayo a gaban su gwagon mu,</p><p> Duk da ga su Ummi da Inna agidan sai mukaji gidan yai muna wani irin girma so sai, kamar ba mutane acikin ta,</p><p> Mun saba da gwago idan tafara zuba ko ba ka, son surutu sai kayi shi,</p><p> Ita koda karamin yaro magana take yi abinta, hankali kwance,</p><p> Na lura cewa innar mu a takure take agidan bata son dogon motsi,</p><p> Kullun ta na daki ita baka ganin ta waje sam, bakomai yasa haka ba sai kunya da take ji wai idan angata za,ace tazo gidan surikin ta ta zauna,</p><p> Ummi na jin lokacin da take fadar haka sai ummi tace idan har tace haka to itafa,</p><p> Ai ita avidan dan farinta tazo ta zauna, tun tana jin kunyan haka har tadaina, acewar ta,</p><p> Tun lokacin inna ta ta rage, zancen jin kunya a gidan surukin ta,take,</p><p> A kida tace shiga kitchen da kai na dan yin cooking wa mai gida na har mada sauran iyayyen mu,</p><p> Nasan cewa yana gari yau dan haka, abinci mai kyau da kuma abinsha ns hada masu,</p><p> Nasan cewa dare yafi son yaci tuwo kowani iri ne,</p><p> Don tun ina aiki a gidan shi nasan wanar a kidar tashi ta rashin son wani abin da ba tuwo ba da dare,</p><p> Hakan ke sa shi shan wuya idan yai tafiya, zuwa waje,</p><p>Tuwon semovita nai mai da miyar kuka wanda inna takawo, muna lokacin da zasu zo, miyan yaji daddawa da kayan yaji sosai,</p><p> A, leda na kwashe wa kowa nashi mariya dake gefe ita da maman Umar </p><p> Suna tayani aiki suka shiga mikawa mutanen gida nasu don kowa da inda za,akai mai nashi,</p><p> Muna gamawa, da sauri nafada dakina dan in dan gyara jikina kafin sheriff yadawo gida,</p><p> Duk gidan yadauki Kamshi da na turare dana girkin gida,</p><p> Yau atamfa ce a jikina, super wax, doll colour, dinkin zani da riga ce, sheriff baya son dinkin buje da riga, acewar shi, nasan da hakane tun lokacin auren shi da nafisat,</p><p> Wata rana da tasa buje darigar dinkin material sun dawo office da Almustapha a lokacin yako dinga mata masifa yace kada ta kara sa irin su a gidan shi,</p><p> Yace may amfanin kasa kayan da duk tsiraicinka zai baiyyana afili,</p><p> Wai da sunan yin wa maigida kwalliya alhalin bashi kadai ,aiwa adon dashi ba dole ne a fita waje wani yaga ni,</p><p> Muna tsaye gefe muna jin su nida Amal, alokacin,</p><p> Yaci gaba da fadin matar Abdull ghana da ta rasu kwanaki ana bidan zanin da za,a rufa gawan ta dashi duk cikin kkayan ta ba zani,</p><p> Ya ce may yafi wannan abin tashin hankali ace yar musulumai bahausa ba,a samu zani a cikin kayanta ba ai wanan yazama abin ku ya ga mutum tun a nan duniya,,</p><p> Ya ce shi dama bai kaunar yaga mace duk ta matse jikinta a waje koba,a cikin ma,za bane,</p><p> Jin wanan maganar tasu da, nasifit yasa hakan ya zauna min a rai tun wancan lokacin duk abinda zanyi bana sa dinkin da zai mugun matsemin jikina ,</p><p> Balle gidan mu da kusan mutane su na shiga bawai shi kadai maigidan ke shigowa ba,</p><p> Duk su salim da malam Basiru wanda yazu yake tare damu yana zama kamar dan uwana na jini sosai,</p><p> Don gaskiya munji dadin zuwan shi saboda akwaishi da kwa,zo ga rikon amana,</p><p> Ina sauri inj tafi gurin su, ummi indiba ko sun fara cin abinci saboda bana son su zauna basu ci komai ba,</p><p> Dai step na karshe ya bude kofar falon yashigo gida a lokacin,</p><p> Yana rataye da couth din shi a kafadar shi, almustapha da Basiru suna bayan shi dauke da takardu da briefcase din shi mai dauke da laptop din shi,</p><p> Tun daga nisa muka yi wa juna yar murmushin mai aikawa da sakonni, kala kala,</p><p> Inda nagane nufin shi kwaliya ta taimai kyau, nikuma na nuna mai cewa don shi nayi ai,</p><p> Sai yai wani ragwada kai alamar yagode fa,</p><p> Su Almustapha da Basiru dake bayan shi basu gane komai muke yi ba,a tsakanin mu,</p><p> Kayan da su Basiru suka dauko mai nai kokarin karba</p><p> Tare muka koma sama, dashi, muna bacewa wasu Almustapha ya rungumo ni zuwa jikin shi yana mai sun sunar ko ina ajikina a kaukauce,</p><p> Da kyat na iya sabulewa rikon da yai min ina mai gabatar mai da ruwan wanka,,</p><p> Kafin yafito na fitar mai da kayan da zai sa har da plat shoes da zai sa ya fito, </p><p> Ina cikin fesa turare sai naji wani irin abu ya taso min kamar zan yi amai,cikin sauri nabar dakin ,,</p><p> Sam ban dauki hakan komai ba aguri na, dakina ,nakoma nadan kara kallon mirrow dan indan kara burge maigida ,</p><p> Zaune na samay shi a falo yana jirana in zuba mai abinci ,</p><p> Kurrr idon shi akai kamar bai taba gani na ba, </p><p> Direct dining na nufa shima yataso a hankali zuwa bisa tebur din,</p><p> Kululin da ke jere saman tebur din nafara budewa, nadago kai na kalle shi dan inji may zai ci daga cikin abincin da nake budewa,</p><p> Daidai lokacin naji wani irin amai ya zo min duk yadda, na so in daure har in gama zuba mai, abin ya faskara,</p><p> Da sauri na toshe bakina na nufi, toilet, din dake cikin falo,</p><p> Amai nayi sosai har sai da naji jiki, da kyat na samu ya tsaya min, na bude famfo na wanke baki na da fuskana,</p><p> A hankali na dago da niyar in koma in cigaba da zuba mai abincin,</p><p> Ganin shi na tsaye kofar toilet din hannun shi harde, a saman kirjin shi,</p><p> Wani irin kallon tuhuma yake min .</p><p> Zuwa, nayi da niyar indan bi gefen shi, in wuce zuwa cikin falo ,,</p><p> Tambaya ya watso min may yasa may ki fatima,ina kokarin wucewa ya, kara jefo min tambayar,</p><p> A hankali na ce mai ba komai, nima bansan komay yasa may ni ba nai aman,</p><p> Hanya yabani nawuce cikin tuhuma yake kallo na har muka kai bakin dinning din,</p><p> Nai kokarin in kara zuba mai wani abinci, aiko saura kiris in amayo ma sheriff amai a jiki,</p><p> Mikewa yayi da sauri yazo inda nake duke ya rike ni </p><p> Duk wanda ke gidan saida yafito a lokacin saboda irin kakarin aman da nakeyi,.</p><p> Tunda yatsaya min yace mutafi asibiti, amna fafir nace bazan je ba tunda lafiya na kalau,</p><p> Yanzun ne kawai hakan ya samay ni daga jin kamshin abinci,</p><p> Wani kallon tuhuma su Ummi da Inna suke min a lokacin,</p><p> Inna ce tace mai wani asibiti zamu ai saidai kuma in Allah ya rabamu lafiya,</p><p> Sam ban fahinci may inna take nufi da hakan ba dani don haka dagani har sheriff muka hau sama,</p><p> Duk da barcin yamma ba dabi,ana bace yin hakan yasa yau sai gani nayi barci ,don wuya,</p><p> Barci mai nauyi nayi a lokacin dan bakara min jin jiki nayi ba,</p><p> Doctor kamal ne yazo gidan bayan sallah isha,i don ya dibani,</p><p> Amma sai ya gani ,zaune a falo tare da su mariya da su maman Umar munata labarin mu muna dariya,</p><p> Ganin su tare da docto yasa ni dan shan jinin jikina,</p><p> Duk kan su mamakin gani na lafiya sukayi cikon hokima muka wayance zancen batare da doctor yabani koda paracetamol ba,</p><p> Tun wanan ranan ban son jin warin girki musam man mai dauke da tafarnuwa,</p><p> Idan kuma dare yayi sai in kama jin high fever har kusan sallah asubah,</p><p> Yau kamar na wancan ranan ne ina cikin taimakon shi sai kuma ga amai </p><p> Mariya tana gurin yace dole sai muntafi asibiti sn diba ko may ke samuna haka,</p><p> Mariya tace Allah yabar muna yaya Sheriff, shin bakaji abinda inna ta fado na ba,</p><p> Cikina fa take cewa sai randa Allah yasa ta haihu zata daina hakan,</p><p> Aiko hankali mu mida sheriff yai wani mugun tashi da jin kalamin mariya,</p><p> Tambayar mariya yayi ko yaushe inna ta fadi hakan,</p><p> Sai ta kara nanata mai abinda inna ta fadi a ranan</p><p> Tsaye nake amma ban san lokacin da nakakai zaune ba nadafe kai na sai wasu hawaye ke biyo min a fuska suna silalowa kasa,</p><p> Shi ma sheriff zama yayi yadafe kanshi da hannu gida duk yarasa abin yi,</p><p> Mikewa yayi ya nufi inda ake aje makullaiyan motocin gidan,</p><p> Ya hau sama da sauri yadauko min Naifal dina yace intashi muje asibiti,</p><p> Ba musu na shirya muka kama hanya zuwa asibiti,</p><p> Diba guda likita yai min ya tabbatar min da cewa ina dauke da cikin wata biyu a jikina ,</p><p> Ido nazaro dan mamakin jin hakan danayi bani ba har shi saida ya kadu,</p><p> A firgice yacewa doctor muna da babies yan wata takwas fa,</p><p> Likita yai dan murmushi yace ba komai bane hakan kawai za,a rubuta muna magani da kuma irin abincin da zamu fara ba yaran,</p><p> Niduk bayanin da sukeyi kaina yana kasa ina ta sharban hawaye kawai,</p><p> A cikin mota duk yarasa abinda yake ciki saboda gaba daya na birkice mai yarasa gane kaina,</p><p> Yai lalashi na har yagaji banyi shiru ba,</p><p> Ido kwai ya samin zuciyar shi duk bai mai dadi, don shi gani yakeyi ai yaran zasu shiga matsala har yajawo masu matsala,</p><p> Nikuma nafarkon abin da nake tunane a zuciyana shine da,wani ido zan kalli su Ummi da Inna kai har ma da sauran mutane </p><p> Kai gaskiya da sake awanan zan cen namu dole asan abinyi kafin a,san cewa akwai ciki atare da ni,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Dan Allah kuyi hakuri da wanan pls ba yawa bana jin dadin jikina sam,👏👏👏👏👏👏</p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 9⃣7⃣</p><p> BY </p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost True Life Story,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Jin zuciyar shi yakeyi kamar zata tsage mai gida biyu, saboda jin kukan da takeyi kamar ana mai yayafin ruwan zafi ne a jikin shi,</p><p> Burki yataka da karfi saida ta dan razana, don yadda ya taka birkin mutanen da ke gefen titin suka dinga kallon su,</p><p> Shiru yayi yasa ma min idon ina ta faman gumzar kuka, na,</p><p> Ganin yadda ya faka motar da karfi ga kuma mace aciki tana kuka yasa yan bagaladi zuwa inda motar take dan ganin abinda ke faruwa a cikin motar,</p><p> A hankali suka kwankwasa glass din motar dan na ciki su bude masu, </p><p> Katin shedan wurin aikin shi yadauko yafara nuna, masu cikin girmamawa , suke ce mai may ke faruwa ne haka yace,</p><p> Masu ba matsala su wuce kawai, abinsu sai yai godiya yai kick din motar shi, yadau hanya,</p><p> Muna shiga get din gida mu ya dan waigo inda nake yace, idan har ina son su Ummi su san abinda nake cikine inci gaba da kukan da nakeyi </p><p> Dole nadan saita kaina nashare hawaye da tmyai min jagab a fuska, </p><p> Cikin dakiya nadan daure na bude mota zuwa cikin gidan </p><p> Cikin sauri na haye matakalan hawa sama ina mai zub da hawaye ,</p><p> Shiga na da kamar min ti biyar naji anturo kofar dakin a hankali,</p><p> Shiru naji ba ai min magana ba ni kuma ban waiga inga ko waye ba,</p><p> Don ni a zato na sheriff ne wanda yanzu haushin shi nake ji don gani nakeyi shi yai min wayo har aka kai ga haka,</p><p> Muryan mariya na ji cikin wani yanayi tana fadin haba anty dan Allah ya kamata ki daina wanan kukan haka, </p><p> Sai a lokacin nadan waigo kadan , fresh milk ta miko min a cikin wani cup din tangaran maidan sanyi kadan,</p><p> Bamusu na karba don kusan shine abinci na yanzu,</p><p> Duk son da nakewa fresh milk din yau sai naji shi kamar wani guba nake sha ,</p><p> Ko rabi ban sha ba na aje a sidedrower dina na koma ina batun dunku lewa a saman gado,</p><p> Mariya tace wai anty fadima kin san may kike yi kuwa,haka,</p><p> Bafa cikin shege kikayi ba cikine mai uba kuma uban ba gajiyye ba wanda ko kun kai ku nawa ne zai iya kula da ku,</p><p> Anty ko dai ni dake kasa gare ki aibani wanan abin dan nasan cewa ba mai wuce kaddaran shi,</p><p> Balle wanan abin alfahari ne ai agare ki,</p><p> Da sauri na dan waigo ta dan jin abinda tace min,</p><p> Ta ce eh mana, shin ki ko san cewa a kauye duk da talaucin da muke yi har gasan haihuwa suke yi a haka nan,</p><p> Fuska na alamar mamakin maganar ta ya nuna ,karara,</p><p> Taci gaba da fadin a cikin wanan talaucin za suyi ta zuba diya waidan kada kishiya tafi su tara diya,</p><p> Shiko miji ko oho,ho,ho, wata ma da kyat ake samun dan akuyan da za ayanka mata,</p><p> Gashi ba wani wada,ttacen abinci da mace zata ci takara kuzari,</p><p> Hakan bai hana kafin kwana biyu kiji ana fadin ai wance ciki aggareta,</p><p> Kinga sun samu riba biyu kenan gashi sun raya sunnan, ma,aiki (S A W) ga kuma ribar kishi da suka samu, ace ai wance yanzu aurenta shekera kaza ne diyanta kuma kaza,,,,</p><p> Kafin taci gaba sheriff yashigo dakin dauke da ummibanan a hannun shi tana yar fitinar ta da alamar nono take so,</p><p> Cikin ido na yake kallo yaga ko zan karbi yarinyar ko kuma zanki karban ta ,</p><p> Ina karbanta na bude nono na mika mata tai wani irin ajiyar zuciya takama nonon </p><p> Sai faman aje zuciya take yi don jin dadi da alamar tadan dade tana kuka,</p><p> Mariya ya dan kalla sai kawai ya fahinci cewa aikintane hakan,</p><p> Gefen gado yadan zauna batare da kalle ni ba, ,yana fuskan tar kofar dakin,</p><p> A hankali ya ke magana yace min Fatima kiyi hakkuri dan Allah ki shayar da yaran nan har zuwa lokacin da ya kamata a cire su a nono,</p><p> Wani iri naji a cikin zuciya da yace haka dan ban san lokacin da tausayi kaina da na yaran ya kamani ba,</p><p> Wani sabon kuka na sa masu mariya dake shirin barin dakin ta waigo tana fdin Ya Salam,</p><p> Anty fadima wai ko lafiya kike da wanan abin da kike yi,</p><p> Shin kisan cewa Bintu ta haihu da wata uku ta samu wani ciki,</p><p> Duk da kuka nakeyi saida nadan waigo dan mamaki jin maganar yar kaunata mai dabiar manya mata,</p><p> Tace walle ko bata kumayi wani fitina ko shiga tashin hankali ba,</p><p> Iyaka dazata haihu uwar ta ,ta taho, tadauki yarinyar ta farko, anka barta da dan jaririn,</p><p> Takara she zance da cewa to balle ke ga Ummi da Inna damuwa mika damuwan ki banda ki cika ma yaya sheriff gida da yan diya,</p><p> Wani irin harara da bugu nakai mata ta mike tana dariyar keta,</p><p> Sheriff da ke jin mu ya kama muna dariya yana dan murmusawa,</p><p> Fitar ta keda wuya sheriff yadan matso kusa dani kadan yadan sau,sauta muryan shi yace min fatima, kafin yafadi wani magana,</p><p> Nai saurin toshe mai baki , na a,za kaina asaman kirjin shi, nakama kuka,</p><p> Rungumay ni yayi ya na dan shafa min kai alamar lalashi,</p><p> </p><p> Na hana mariya da sheriff su fadawa su inna wanan zancen haka naci gaba da shayar da yara na nono cikin fargaba,</p><p> Sheriff kuma yana kokarin sayo masu duk wani magani da zai sa su karin kuzari </p><p> Ganin da nayi yaran basuyi komai ba yasa nadan fara sake jikina ,</p><p> Ga bukin Amal yana kawo lokaci don yan zu saura wata guda ga lissafin da naji su sheriff da Salim nayi,</p><p> Hakan yasa yanzu ban da wani time din zama gida sosai don muna shirin zuwa sudan can garin iyayyen Almustafa dan gyarawa Amal gidan ta na can,</p><p> Cikin dake jikina duk da yafara girma so sai bai hanna ni yin kuzarin aiyukan da yadace inyi ba,</p><p> Saida muka fara zuwa Nigeria tukun muka kwana uku, gurin shehi, sanan muka dunguma zuwa kasar sudan tare da yan rakiya daga dangin su Shehi mutum guda sai dangin ummi mutum guda </p><p> Abin mamaki saigashi ni a fanni na har mutum shida sheriff ya yarda in tafi dasu,</p><p> Salimat safiyya mariya Rugaiyta, matar Basiru, da hafsin mu,</p><p> Hafsi taiwa Ummi kumshi mai kyau irin na yan sokoto kafar yarinya yai radam yai kyau,</p><p> Mun isa lafiya, ankarbe cikin mutunci, a can muka samu kayan da sheriff yai oda a Dubai har sun iso ko don haka ba bata lokaci muka shiga gyaran gida don yin abinda yakai ,</p><p> Tun a cikin family su Almustapha naga mata da maza suna ta zuwa kallon ummina, da ke dauke hannu matar malam Bashir wace yanzu kusan duk kula da yaran ya koma hanninta,</p><p> Abinda sukeyi bai bani mamaki saida mukaje gurin wasan kamun ango da sukayi da yamman ana gobe zamu dawo Nigeria,</p><p> Naga an kewaye min yarinya anata kallon , cikin tashi hankali na isa gurin da suke a zaune a sasu a tsakiya sai kafan Ummibanan da yasha kushi ake kallo ana mamaki,</p><p> Tambayar su nayi a cikin larabci, harshen larabci ko may ke faruwa suka kewaye min yar diyata,</p><p> Sai ce min sukayi wai kumshi sukaga an mata shine suke mamaki,</p><p> Wai ita da batada miji may zai sa ai mata kumshi yar karama da ita haka,,,</p><p> Mamakin su kwarai nayi dan sai da sukace haka na tuna cewa larabawa basuyi wa diyan su mata kwalliya irin namu wai sai wacce keda miji zatayi irin hakan damu nan muke yi,</p><p> Nai masu bayani cewa mu haka al,adar mu take diya mace za,a iya mata duk wani kwalliya da macen aure zatayi </p><p> Saboda ta tashi da wanan tarbiyar na koyi da sunnar maaikin manzan Allah, SAW,,</p><p> Lokacin da naiwa yan uwa na bayani sai duk mamaki ya kama su su ma, </p><p> Salimat tace min ai lokacin da ta taba yiwa Asamu,u kum shi da taje massalaci da ita a madina wasu larabawan Egypt taruwa sukayi suna kallon ta,</p><p> Tace ai su haka akidar su take wai wa yaro zaiwa kwaliyar burgewa da har za,a bata lokacin yi mai kumshi haka,</p><p> Muka dawo Nigeria abin cikin jin dadi irin karramawar da dangin Almustapha sukayi muna akasar su,</p><p> Gidan buki yafara cika don yanzu aiki har yawa yake muna saboda dangin uban nin mu sun zo daga jimeta,,</p><p> Sungan mu mun gasu inda sukai min korafin rashin zuwa inda suke daban yi ba lokacin da na haihu,</p><p> Hakuri na basu dan ban da gaskiya duk da nasan cewa ba laifina bane barinane da ba,ayi ba shi yasa ban je ba,</p><p> Amma yanzu nai masu alkawarin cewa zan zo insha Allah kafin in koma saudiya,</p><p> Duk wani al,adar da akeyi na bukin aure anyi a wanan bukin na Amal don gaskiya yan uwa da abokan arziki sun zo tako ina don taya mu murna,</p><p> Nafisat ma tazo daga Abuja saidai bata kwana ba tace zata tafi maiduguri ta kwana acan,</p><p> Kuma ko can din wai ba,a gidan Abba ba,ina jin suna fada da sheriff a cikin waya yana ce mata aida bata zo ba hakan zaifi mai sauki,</p><p> Hjy mama ko sakon Allah sa alheri bata aiko wa Ummi ko sheriff da shi ba, har aka ci aka sude,</p><p> Yan uwan Almostapha sun yaba kwarai da irin karancin da akai masu da sukazo don kusan duk abinda sukai muna da mukaje hjy Umma tasa mukai masu ninkin banin kin, </p><p> A gaskiya abin ba,acewa komai a lokacin, a gurin wanan bukin yan uwan mu ke cewa wai a hada mariya aure da Salim </p><p> Ban boye ba na nuna masu cewa hakan bai yu,yuwa sam,</p><p> Saboda ko nasan cewa halin su ba zai hadu ba, za,a bata goma daya bai gyaru ba,</p><p> Sanan shi Salim nafi kowa sanin yanada budurwan, da suka dade tare tun muna karatu a madina,</p><p> Ana gobe za a wuce da amarya kasar sudan inda zasu dan kwana biyu kafin su wuce saudiya,</p><p> Muka wayi gari cikin tashin hankali,don duk mun hada kayan tafiyar mu duk da sheriff yace bazan koma Sudan, ba dan tafiyan yai min yawa, hakana,</p><p> Sai gashi mun wayigari cikin tashin hankali, anyi sallah Asuba, lafiya da hjy tsohuwa ,</p><p> Inda take zaune tana lazimi sai Allah ya karbi ranta agurin,</p><p> Ba wanda yasan da haka sai lokacin da wata jikanta tashigo gurin ta ansar kudin kosai da ake mata sadaka duk safiya,</p><p> Taimagana taju shiru tana kai hannunta taga ta fadi gefe,</p><p> Sai ta sa ihu kawai cikin tashin hankali, lokacin ina dama ma Abbazannah madara ya sha,</p><p> Naji wanan ihun tashin hankali, Sheriff wanda yafito wanka alokacin ya na tsane ruwa a,kan shi,</p><p> Jin ihun yasa shi saurin sa rigan shi yai waje cikin tashin hankali,</p><p> Dauko yaron nayi nima mukayo waje inda yarinyar keta tsala ihu tana nuna falon hjy tsohuwa da hannu,</p><p> Cikin sauri ya fada dakin hjy tana kwance yadda ta fadi har yanzu,</p><p> Da sauri ya isa gurinta yana jijigata koda yadaga hannunta yaga ya biyo shi sharkaf,</p><p> Salati ya, sa,a lokacin yana mai zubda hawaye,a ciki tashin hankali,</p><p> Ina kawowa naga sheriff duke a gaban hjy dake kwance, bashiri naja da baya cikin tashin hankali,</p><p> Wayan sheriff na dauko lambar Bashir nafara kira sai na Shehi, </p><p> Batare da bata lokaci ba saiga,su,cikin gidan hankali a tashe,</p><p> Duk wanda yazo sai ya tabbatar da cewa ai hjy tsohuwa lokaci yayi,</p><p> Shehi ne da kanshi ya kira wayar Abba dake maiduguri ya sheda mai abinda ake ciki,</p><p> Kafin wani lokaci gida yacika fam da yan uwa da abokan arziki,</p><p> Andan jinkinrta ma Abban su Sheriff dan yazo yaga gawar mahaifiyar nasu, shida wasu yan uwan su daga Maiduguri,</p><p> Kulli nafsin za,ikatin,mau, yau muna kallon cikin tashin hankali da kuma jimamay aka wuce da hhy tsohuwa makwancinta,</p><p> Dole aka jinkirta tafiya da Amal wace taci kukan rashin kaka na gari da sukayi,</p><p> Duk shekarun da nayi da sheriff wanan ne karo na biyu danaga yana zub da hawaye arayuwan shi,</p><p> Duk da nasan cewa bakaramin rashi yayi ba na mutuwar hjy,</p><p> Amma kuma hawayen danaga yanayi yasa nakara gaskanta mugun shakuwar da ke tsakanin shi da yar tsohuwar mai mutunci ga zumunci da sanin ya kamata,, </p><p> Abba zanna ya ce lalai dai a wuce da Amal washe gari tunda ko an tsaya ba wai dawowa hjy zatayi ba,</p><p> Amal na kuka muma muna kuka kamar bazamu kara haduwa ba aka wuce da ita,</p><p> Tare da yan rakiyan ta duk da Abba ya hana atafi da yawa daga nan,</p><p> Su hjy umma da Salimat suna cikin yan tafiya, tare da mariya na,</p><p> </p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎[12/12, 9:05 PM] +234 816 295 0551: ✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 9⃣8⃣</p><p> BY</p><p><br /></p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p> Almost True Life Story,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Saida akai sadakan uku, sannan muka fara shirin komawa saudiya, </p><p> Inna kan tace atabau ita bazata koma tare da mu dama zaman can ya ishe ta </p><p> Tace ace mutum kulun yana zaune bai aikin komai saidai aimai duk abinda yake so,</p><p> Gaskiya bazata iya wanan rayuwar ba itakan,</p><p> Ganin cewa inna ta matsa yasa Shehi ya cewa sheriff yasa amaida ita gida,</p><p> Banji dadin hakan ba gaskiya naso ace Inna tai hakkuri mukoma har lokacin da zan haihu amma sam taki yarda,</p><p> Hakan yasa muka dan daga tafiyan mu dan mu kaita gida tukun,</p><p> Wanan karon nasamu taron arziki gurin mutanen garin dogon daji so sai </p><p> Da kaina natafi gidan maigari batare da sanin kowa ba ,</p><p> Nakai makukan matsalata dan ina son in koma tare mama maidakin shi,</p><p> Sam baiji dadin yadda inna taki yarda ta zauna da mu ba a can yace mata ai anbar wanan kunyar da take yi yanzu</p><p> Yanzu koda gidan yar farin ta ne tana iya zuwa ta zauna, tare dasu balle ni da nake yarta ta biyu gurin haihuwa,</p><p> Hakan yasa muka dawo tare da mama matar maigari sai tumba wace ta leke muna da ita zamu tafi kasan cewa dama bata taba haihuwa ba kuma mijin ta yadade da rasuwa,</p><p> Mundawo lafiya saudiya komai yacigaba kamar yadda muka saba ada,</p><p> Mariya zata ci gaba da karatun ta, anan amma sai bayan na haihu,</p><p> Har zuwa yanzu sheriff bai walwale ba daga rasuwar hjy tsohuwa da mukayi abin ya buge shi so sai dan har da yar rama sai da yayi,</p><p> Yau ina daki na ina barci na hankali kwance saboda yaran suna can gurin su mama tun da safe,</p><p> A cikin barci nadinga jin murya sama sama, murya da sam bayi zaton jin shi ba a lokacin,</p><p> A cikin karfin hali na bude idona don in tabbatar bar in ba mafarki nakeyi ba,</p><p> Hjy mama ce tsaye a kaina tayi murtuk da fuskanta da yafara tsufa a,lokacin,</p><p> Muna hada ido ta watso min harara tana cewa saboda samun guri da ki ka yi shine wai har zaki bada dokar cewa kada atashe ki idan kin kwanta,</p><p> Kamar banjitaba nai kokarin saukowa daga saman gadon </p><p> Duk da nauyin da nayi hakan bai hana ni kaiwa har kasa ba ina gaisheta,,</p><p> Itama yi tayi kamar bata jini ba sai cewa da tayi min, </p><p> Samun wurin har ya kai an fara tara mai yara kamar haihuwar bera, agidan </p><p> Don kawai an samu dukiyar banza, ana son a mamaye guri,</p><p> Kaina yana duke akasa zuciya tana fada min in mayar mata da ansar maganar ta ma tun da ba mutumiyar arziki ba ce ita,</p><p> Saida na yaki zuciyata so sai nai mata yar murshi mai nuna alamar sam banji zafin maganar ta ba,</p><p> Nace cikin murmushi mama wanan ai ra,ayin maigidan ne, haka,</p><p> Dan yafi son yaga kowani lokaci gidan shi na albarka wai,</p><p> Namike dai,dai lokacin da nake fadin maganata ta karshe,</p><p> Hanyar fita dakin nanufa batare da na kalle ta nabar mata dakin nawa,</p><p> Don in har na tsaya mukaci gaba da maganar baza a kwashe da dadi ba,</p><p> Falo na sauko da kyat duk da kafa, na sun min nauyi so sai da kyat nake taka su alokacin,</p><p> Abba nagani zaune saman daya daga cikin kujerun falon namu yana , duk yadan ramay da alamar bai da isasar lafiya a jikin shi,</p><p> Cikin sauri na isa inda yake zaune ina kokari rusun nawa dan ingadashi,</p><p> Shima cikin sauri yake fadin ,a a fadima zauna abinki kawai mun samay ku lafiya dai ko,</p><p> Namayar mai cikin ladabi da lafiya kalau, yace gamu munzo kuma ashe maigidan yayi tafiya,</p><p> N</p><p>Cikin mamaki nace bai san da zuwan ku bane ko Abba,</p><p> Yadan kurbi ruwan tare da hade wani magani da ba ya ballo daga gidan shi yace a,a tafiyar namu zuwa jiya da yaune muka shirya shi,</p><p> Dan dama a US zan tafi ganin likitana na can sai kuma ahawara ya sake akan mu zo nan kawai,</p><p> Saida na tabatar da duk wani abinda za,a tanadar masu na ci da bukata an kawo masu, dan da kaina nafada kitchen din dan hada masu ,</p><p> Ko kallon hjy mama ban kara yi ba tun fitowar mu daki,</p><p> </p><p> Doctor kamal nakira batare da na sheda wa sheriff ba wanda nasan cewa yanzun ma koda zamu kirashi ba,za mu samay shi ba ma,</p><p> Doctor ya iso cikin wani dan lokacin da ba mai tsawo ba , </p><p> Sun gaisa da su Abba da kuma tanbayar su gajiyar hanya,,</p><p> Tashi nayi dan inbasu guri saboda doctor ya gana dasu,</p><p> Inda nake zaune mariya ta fito cikin kwaliyar ta kamar wace zata unguwa,</p><p> Kujerar da nake zaune tazo ta zauna a gefen hannun kujerar tadan rankufo da ka ta tana kokarin daukar mu photo da wayan ta,</p><p> Tureta nakamayi ina fadin wallahi mariya zan bata maki rai fa,</p><p> Doctor na tsaye daga kofa dakin da yafito yana muna kallon cikin murmushi,</p><p> Ni na fara ganin shi a inda yake tsaye nace mata tadiba ga doctor yana kallon mu fa,</p><p> Karasowa yayi yasa mu daya daga cikin kujeran inda muke zaune,</p><p> Mikewa tayi tadauko may abin sha takai mai har inda yake zaune,</p><p> Magana mu keyi dashi amma hankalinshi na gurin mariya wace ke duke tana zuba mai drink a cup</p><p> Tana gamawa ta mike tana fadin anty zan tafi gurin su mama, ta wuce abinta,</p><p> Tana bacewa sai na ji yai wani irin ajiyar zuciya ya waigo yana mai shafar kan shi daidai lokacin da ya kwakwadi drink din ya aje cup din a saman stol din yace, min,,</p><p> Fadima ki bani wanan kaunar taki mana pls,,,,</p><p> Jin maganar nayi kamar a mafarki dan ban taba zaton mutum kamar doctor kamal har zai tsaya yace wai yana son mariya ba,</p><p> Kamar yasan abinda nake tuna ne sai ji nayi ya katse ni da fadin,</p><p> Ko nai mata tsufa ko fadima, murmushi nayi nace mai ,a a ni bance ba,</p><p> Ai,gata nan ga ka sai ku shirya a tsakanin ku, ni ba magana ta bace,</p><p> Ido yadan tsura min don ya tabbatar da magana ta ko da gaskiya ce,</p><p> Can ya, mike ya na fadin shi ke nan insha Allah zan gwada sa,a ta, in gani </p><p> Amma sai kin bani nobar ta dan in fara tanan in gani,</p><p> Ina dariya na fara karanto mai noban nata yana loading a wayar shi,</p><p> Yai min sallama tare da fada min gobe insha Allah za,a kawo Abba asibitin su,</p><p> Godiya sosai naima akan zuwan da yayi cikin lokaci yace haba ai nima mahaifina ne ko,</p><p> Sai bayan da mukayi sallah magrib nakoma shiyan da su Abba suke dan mu kara gaisawa da su,</p><p> Cikin ladabi na gaishe su amna sai Abba ne kawai ya karba min gaisuwar tawa, a lokacin,</p><p> Jin shirun da yayi mama bata karba yasa Abba fadin ana gaishe ki fa </p><p> Sai cewa tayi aina karba ko indai kuwa zan ma yar mulkin naku ba,</p><p> Murmushi nayi kawai dan dama nasan cewa za,a rina </p><p> Don tunda nashigo dakin take watso min harara,</p><p> Nakara yiwa Abba bayanin akan yadda doctor kamal yai min na cewa tun da safe kada ya karya akai shi asibiti don awo,</p><p> Cikun murya kamar mai masifa mama tace ba yariga yai muna bayani ba </p><p> Ko aiko ki yayi kikara fada muna,</p><p> Abba ne ya tare da fadin nagode kin ji fadima Allah yai maki albarka keda zuri,ar ki,</p><p> Na ansa da fadin Ameen Abba na gode Allah yaba ka lafiya,</p><p> Yai dan murmushi yagyara daga shingidar da yayi kadan yace kayya fadima Allah dai ya kyauta kawai kin ji,</p><p> Daga haka bayan Ameen din da nace na mike jiki ba kwari na bar dakin ina mai masu saida safe,</p><p> Wayan sheriff ne ke kirana a lokacin, </p><p> Bayan mun gaisa ne nake sheda mai zuwan su Abba,</p><p> Har yaso yatayar da hankalin shi sai nake sheda mai cewa ai doctor kamal yazo diba shi , dazun nan,</p><p> Yaji dafin hakan so sai dan har da godiyan yaso yai min na ce mai bana son haka na pls,</p><p> Mukayi sallama bayan mun dan taba hira dashi,ina zaune lokacin a daki na,</p><p> Mikewa nayi tare da kulle kofar shiga dakina,</p><p> Nafito nafara zuwa gurin su, mama da Tumba don indiba yaran,</p><p> Sai na iske har mama ta basu abinci tai,masu wanka har sunyi barci, ko, daga can bayan mun dan taba hira kadan, dasu,</p><p> Dakin mariya nafada kuma,don duk dare kafin in kwanta sai na bisu naga halin da suke ciki, zaune suke ita da Aisha har da maman Umar suna hira ga wayar ta na wakar hausa, a gefe,</p><p> Direct wajen wayar na nufa nakashe ta dariya takama yi min tana fadin ai dama tun da na shigo tasan zan kashe wayar ne,</p><p> Zama nayi a bakin gado muka fara hira da su hiran ,bukin Amal suke muna na zuwan su, Sudan kai amarya,</p><p> A cikin gatse na ce masu saura mukai wa yan Niger tasu amarya su kuma muga yadda za suyi muna ko,,</p><p> Har suna saurin hada baki suna fadin cewa wace ce za,a kai Niger kuma,</p><p> Ce masu nayi watace nan makwabciyar mu ce ,</p><p> Maman Umar ta kalleni tana dariya tace min ai ina ga kamar bukin suna za mu fara sha kafin na makwabtar ko,</p><p> Dan murmushi na yi na ce mata har da ke cikin yi min sheri ko,</p><p> Washegari duk yadda naso Abba yai sakko hakan bai yu,yuba saboda kofar dakin su yana a rufe alamar basu tashi ba ke nan gashi rana, har ya soma fitowa a lokacin, </p><p> Sau biyu sheriff yana bugo min waya don yaji ko an tafi asibitin,</p><p> Saida taga dama don kanta ta bude side din, kafin su fito sai da aka dauki wani dan lokaci,</p><p> A raina nace lalai wanan matar takai muguwar gaske, dan ciwon ba a jikin ta yake ba, shi yasa tai haka ko,</p><p> Tana fitowa tazauna cin abinci Abba yana zaune cikin jallabiyar shi fara,</p><p> Na,zo har inda yake na gaishe shi da kwana tare da sheda, mai cewa driver yana jiran shi tun dazu doctor kamal ya kira waya, tundazu,,</p><p> Bayan fitan su na bi bayan su dakallo cikin tausayin Abba wanda sai yadda hjy mama tayi da shi saboda hakkurin shi,</p><p> Babu abinda ke damun Abba sai hawan jinin da yai mai kamun kwarai ,,,</p><p> Gashi kuma ba wani kulawa yake samu a gurin hjy mama ba</p><p> Wace ita ta kanta takeyi yanzu duk karfin haline kawai ya rage mata,</p><p> Tare suka dawo da doctor kamal , yazo dauke da maganin da yake son adora Abba akai</p><p> Mariya ce yakira yace itace yake son ta dinga ba Abba maganin har kwana uku,</p><p> Kafin akara yi mai wani awon, fuskan hjy mama na kalla dan ganin ko zata yarda da abin da doctor yace ,</p><p> Ya tsunar fuskan take yi kamar mai jin kashi ko warin mutane,</p><p> Wasu takardu doctor ya miko min ina dibawa nai dariya a lokacin ina biye a bayan doctor nace mai,African people's</p><p> Takardun shedar haihuwan su twins ne akayi da sunar a saudiya aka haife su,</p><p> Da yamman ranan su sheriff suka dawo daga US </p><p> Direct gurin Abba ya nufa dan gane ma idon shi halin da Abban yake ciki,</p><p> Sai da yagama tambayar Abba lafiyan jikin shi tukun sannan ta juyo ya gaida hjy mama,</p><p> Ta ansa mai cike da basarwa, da kuma takaici a zuciyar ta dan ganin yadda Sheriff yakoma cikakken mutun mai fada aji,</p><p> Yana shiga side din shi ya samu har na hada mai ruwan wanka ko,</p><p> Saida yadan rungumay ni na dan wani lokaci tukun sanan ya sake ni ya fada bayi,</p><p> Abinci yaci daidai lokacin da yake gamawa doctor yakira shi dan jin ko ya iso lafiya,</p><p> Saida na kwashe duk kayan da yaci abinci na gyara gurin </p><p> Lokacin yana yar dakilar system din shi, saidai duk rabin hankalin shi na akaina,</p><p> Yana ganin na gama muka wuce bedroom lokaci guda,</p><p> Saida na koma side dina na gyara jikina da kyau,</p><p> Sannan na isa gurin maigidan ,</p><p> Duk da bawani dadewa yayi ba acan din duk da haka duk kan mu kowa na kokarin nunawa dan uwansa yadda yai missing din sa,</p><p> Bakaramin soyayya sheriff ya nuna min ba aranan kamar wanda yai shekara baya tare da ni,</p><p> Saida koma ya kamamala a tsakanin mu yadan jawo ni zuwa jikin shi kamar mai min awo, yace,</p><p> Kin ko tafi awo, fatima, saida naji wani dam don sam ni ban son harkar awon nan ,</p><p> Kaina nadan kwantar a saman kirjin shi sannan nace mai a,a banjeba gaskiya,</p><p> Saboda may tafadi cikin karaji,</p><p> Nace kai nake jira kadawo mutafi tare, hanci na ya ja min yace ban san may yasa bakya son zuwa asibiti ba fadima,</p><p> Gaskiya gaskiya hakan zai iya kawo muna matsala tunda naga ke baki damu da lafiyan ku ba ke da baby,</p><p> Dan haka gobe indan Allah ya kaimu ki shirya tunda safe, mutafi ki ga likita,,</p><p> Hakan akayi dan wanan karon har E,D,D an rubutamin ko,</p><p> Don yanzu watana bakwai ke nan nake ciki, ina kallon yadda sheriff ke jin dadi a ranshi, har saida ya baiyyana afili,</p><p> A hankali nadan sasauta murya na na ce sai a rage bani wahala pls,</p><p> Yar dariya yayi yakamo hannu na ya matse acikin nashi gam,</p><p> Ce ai likita bai ce haka ba kin ga kenan likita ma kila so yake in kara kaimi fiye da da,</p><p>,,,,,,,,,,,,,,,,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE. MAKAWA🐎</p><p>[12/13, 9:24 PM] +234 806 371 4187: .✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈ </p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 9⃣9⃣</p><p> BY</p><p><br /></p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAW🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p>Almost True Life Story,,,,,</p><p><br /></p><p> Allah yadawo da su Amal saudiya lafiya daga hutun da Almustapha yatafi na aure a garin sudan</p><p> Tana sanye cikin lafaya duk ta rufe jikin ta lif da shi,</p><p> Dama sa lafaya ba bakon abu bane agurin ta don su ma garin su shi suke sawa saidai ace ba dukka ba,</p><p> Kallon ta nayi sai na tuntsire da dariya duka takai mun a baya Sheriff dake kawo wa ya ce cikin daga murya Ke kina da hankali kuwa,</p><p> Tace yayan mu baka ganin itace ke min dariya dariyar naci gaba dayi nace ashe ba dadi ko,</p><p> Kin manta a madina lokacin ,,,,,</p><p> Bankarasa ba tace min ai wancan ya wuce kamata yayi ki tausaya min fadima,</p><p> Ina can kasan mutane ina ta kewan ku, ashe ke ba ki ma damu dani ba,</p><p> Nace mata ni na isa acan ban kewar yar uwata </p><p> Auren ne kawai naga yai maki kyau shi yasa nake dariya kai,</p><p> Bayan mundan zauna na gabatar mata da abin rabawa a baki, ne sai fira yaushe rabo ya fara a tsakanin mu,</p><p> Take sheda min cewa tawuce da mutuwar hjy tsohuwa a cikin zuciyar ta fam,,</p><p> Nace to ya za,a yi sai hakkuri dan hanyar kowa ne mutuwa,</p><p> Sai zuwa rana kadan lokacin da zan kaiwa Abba abinci Amal tabini zuwa gaida su,</p><p> Kamar yadda hjy mama tasaba yi wa duk wani wanda ya shafi fanin Sheriff ko Abba wulakanci,</p><p> Yanzuma da Amal tashigo hakan ne yafaru da ita,</p><p> Don ko kallon inda Amal din take hjy batayi ba ,</p><p> Abba ke yar hira da Amal din yana tambayar ta labarin mutanen saudiya,</p><p> Cikin takaici Amal ta kali gefen inda hjy take zaune tana faman wayar karya tace,</p><p> Tace Allah dai ya kyauta Abba Allah yakare muna kai daga sherin masheranta har kullun,</p><p> Hjy ta dago idon ta jajaye ta kalli Amal dasu wace a lokacin take shirin tashi,</p><p> Dakina muka koma muka kara bajewa saman gado muka hau sabon fira,</p><p> Acikin firar tane na fahinci cewa Almustaph mutum ne wanda bai dagawa mace kafa ko kadan</p><p> Ita kuma Amal din wanan abin yana damun ta so sai alokacin,</p><p> Saida nadan nisa nace mata cikin nuna maganar da zanyi mai ma,anace </p><p> Amal yanzu duk yadda kika samu Almustapha dole ne ki daure da halinsa </p><p> Saboda rashin sabo ne ke damun ki ke kin a sannu idan har kin saba bazakiyi wanan korafin ba, ai,</p><p> Shiru tayi tana nazarin zance na can ta nisa tace amma gaskiya duk yadda naso in daure na kasa daurewa fadima,</p><p> Tunda har ki kaji nai maki complaint kin,san abin nadamu na,</p><p> Tausayi tabani a cikin zuciya ta, dan nasan cewa ta hadu da wani sabon yanayi ke nan,</p><p> Zuciya tace to amma ko ai mustapha bai yi kama da masiffafun maza ba,</p><p> Nace ma kaina kajini da wani zance taya dama ake gane namiji mai wanan irin rayuwar,</p><p> Hakana dai nai ta bata hakkuri da yan shawar,wari yadda za,tayi,</p><p> Nakara mata da nuni da yarda da kaddara komai kan,kantar shi ko girma,</p><p> Addu,a tana rage girman mumunar kaddara ga bawa, akoyau she kamar yadda sadaka yake riga kafi ga mumuni,</p><p> Abinda duk kagani arayuwar ka mukaddarine ka dogara ga ubanginin ka kar kayarda zuciyar ka ta, raya maka abin da ba daidai ba,</p><p> Wata nacan tana neman kwatan kwancin wanan rayuwar bata sanu ba,</p><p> Hakan da ubangiji yai maki shine mafi alherin da koyau she iyayyen mu ke rokar muna ga uban gijin mu,</p><p> Ranan mun kai wani lokaci munata hiran duniya ,</p><p> Har zuwa lokacin da Almustapha yazo daukan ta don su tafi,</p><p> Bawani nisa bane sosai a tsakanin mu da su,don kusan unguwa guda muke,</p><p> Har kusan fita gida na raka ta nida mariya da Aisha,</p><p> Ina dawo,wa na shige wanka dan ko zanji dan dama ajikina,</p><p> Tare da alwala nadauro nazo nagabatar da sallah, </p><p> Ina idar wa marita tashi dakin dauke da Abba zannah a hannu ta </p><p> Gefen gado ta samu ta zauna sai faman murmushi take min</p><p> Ina kokarin gyara pillow na ne nake ce mata, wai may ye naga kamar bakin ki akwai zance ,</p><p> Yar dariya tai min tace may kikagani halan? nace sanin halin ki mana,</p><p> Tace Anty ke nan sai ina da magana zan yi irin haka ,</p><p> Daidai lokacin nakai bayana saman gado ina mai kiran sunan Allah tare da neman tsari ga shedan,</p><p> Nace mata to nikan sai kuban guri indan rintsa ko kadan ne pls,</p><p> Wani kallo taimin cikin shagwaba tace zuwa na fa biyu da niyar in fada maki sai na iske ki kuna magana da anty Amal, in koma,</p><p> Nadan kalle ta nace mata, ainace kina da magana kince min tak,</p><p> Tayi ma,za tadan gyara zaman ta kamar mai rada tace dama nazo in fada maki ,,</p><p> Yau kwana biyu ke nan doctor kamal ya na bugo min waya ,,</p><p> Ido nazaro nace waya fa,? mariya ina dai lafiya ko,</p><p> Tace a,a fa anty dama wai ya na son zaizo gurinane,</p><p> Kallon tanayi cikin tuhuma sai tai saurin cewa ,aa fa bani nace yazo ba,</p><p> Shiru nayi kamar may nazari nace mata toke may kikace sai tace min, ce mai nayi sai na fada maki tukun,</p><p> Nace o kika daure ni ko mariya,</p><p> Tana yar dariyar kunya tace a,a wallahi nace ne kawai sai in anyardar min ,</p><p> Na nisa a hankali daidai lokacin nagyara hular kaina nace mata, sai ki bari har in fadawa yayan ki ko,</p><p> Tai maza tamike tsaye tana daukar yaron tace shike nan zan fada mai idan ya bugo,</p><p> Bayan ta nabi da kallo ina mamakin karfin hali irin na mariya kamar ta har zata tsaya kula kamar doctor kamal wanda kilama ya kusa haihuwan ta in har za,a bibiya,</p><p> Amma wai shine har take tsayawa dashi hirar soyayya ,</p><p> Naiwa sheriff bayanin duk yadda mukayi da doctor kamal tun farko ,</p><p> Da kuma yadda muka yi da ita mariyan yau,</p><p> Batare da ya kalleni ba yai yar murmushi kawai yace Allah sa alheri a ciki na kuma yiwa mariya murnan dace da mutun nagari kamar kamal,,,</p><p> Mariya wace ke Allah Allah taji ko sheriff ya amince saidai bata da yadda zatayi ne tai shiru,</p><p> A daki nasamay ta nai mata bayanin abinda yace kasa boye murnan ta tayi a gabana,</p><p> Tun wanan lokacin doctor kamal ya fara zuwa zance gurin mariya,</p><p> Don haka duk wani plan na sheriff akan karatun mariya ya tsaya,</p><p> Cikina yanzu ya shiga wata na takwas kenan, saboda haka yai min dan tsawo a gaba duk wanda ya ganni sai ya tausaya min,</p><p> Sheriff zaune akan saman wata yar kujer office irin mai juyawan nan, , hankalinshi na gurin system din shi </p><p> Da alamar duk abin da yakeyi mai muhin manci ne so sai don harda Ummibanan taso yadauke ta amma yadan lalashe ta tai barci, </p><p> Doguwar rigace fara,kal,ajikina mai shara,shara mara nauyi, sai hular da nasa akaina ,</p><p> Duk jikina kamshin turaren alrahab ke tashi, sai yar lipstick dana dan zizara a bakina,</p><p> Fresh milk na dauko mai sanyi kasancewar zafin da akeyi a yau din, </p><p> Komai sanyin A,C sai kaji dan dum kadan zaune yake na nufi gefe nadan aje mai milk din duk cikin rashin sanin na iso gurin,</p><p> Kamshin turare na ya shaka hakan ya nu a mai cewa ina kusa da shi, </p><p> Daidai lokacin da zai dan juyo a lokacin na kwanto mai a bayan shi,</p><p> Wani irin sanyayyan ajiyar zuciya yayi har sai da na dan daga mai ajikin shi,</p><p> Aje aikin yayi ya juyo inda nake muna fuskantar juna nida shi,</p><p> Hannu na namika najawo mai cup din milk din na nufi bakin shi dashi,</p><p> Babu musu ya bude bakin nafara bashi yana kurba a hankali yana mai lunshe idon shi,</p><p> Saida ya kusa shanye cup din milk din yai min alama da kai ,ya ishe shi hakana,</p><p> Namaida cup din sama dan stol din na aje, </p><p> Zama nayi wanan karon a saman ciyar shi ina mai wasa da sumar kan shi,</p><p> Hannun shi yadauka yasa daidai saitin cikina kamar mai son jin motsin baby alokacin,</p><p> Aiko bai kai ga cire hannun shiba yaji wani bul,bul alamar motsi a cikin,</p><p> Cikin razana yai saurin ya cire hannun shi kamar wanda za,a rike,</p><p> A hankali yadan dago kai yakalle lokacin ina mai dariyar irin reaction din da yayi,</p><p> Na kalle shi cikin natsuwa, nace mai nifa wanan karon jinake kamar ma banda ciki pa,</p><p> Da sauri yace min a hakan na dan rausaya kaina nace mai kwarai ma, kuwa,</p><p> Kowancan ma nasu twins sai da na kusa haihuwa ne kafin intafi Nigeria yafara dan damuna,</p><p> Yadan sasauta murya kamar mai rada yace min ashe sai in ci gaba da,,,,,,,</p><p> Cikin sauri na rufe mai baki yadan kai min cizo kadan a hannu, cikin sauri na cire,</p><p> Namike da kyat ina fadin barin barka ka karass aikin ka kada in damay ka da surutu,</p><p> Yace kamar kin san bincike nakeyi akan wasu kaya na Abba wa yanda suka bace ,</p><p> Ashe su, Suraj ne suka saidasu ba tare da sanin Abba ba,</p><p> Har da wasu daga cikin filayen shi da gidan jeshi,</p><p> Suna sayarwa suka gudu suka koma inda suka fito batare da sanin Abban ba,</p><p> Hankalina na mayar dan jin wanan labarin mai cike da tashin hankali,</p><p> Batare da natashiba saman jikin shi yaci gabada fada min cewa,</p><p> Ai,yau babu komai don duk sun kashe kudin har sun fada cikin rikici, </p><p> Yace yanzu haka shi babba an harbe shi a kafa agidan rawa yana jinyar kafar ne,</p><p> Shiyasa uwar tace ma Abba yazo nan don kada su tagi can yagani hat yaji ba,asin hakan,</p><p> Shiko suraj ya auri wata baturi wace suka dade tare har sun ma haifi diya buyu kafin ai auren,</p><p> Ido na waro waje kamar mai shirin ihu,</p><p> Yace yes, yanzu nasa aimin bincike akai in har yayi auren ta yadda yadace zan yi kokari in tallafa mai,</p><p> Nace mai to shi gudan fa,ya ce min yana can wata kasa suna waka a Jamaica,</p><p> Innalillahi kawai na kama maimaitawa ina cewa subbahanallah Allah ubangiji ya shirya muna su,</p><p> Yace min Ameen Fatima, nace ya Allah ka shirya muna zuriar mu ta hanyar alheri,</p><p> Duk sai naji banji dadiba wallahi jiki ba kwari natashi daga jikin shi ina mai yin addu,a abakina,</p><p> Duk sai naji tausayin Abba ya kamani ace yara uku sun zama bala,i alokaci guda,</p><p> Allah ka shirya muna kai muna jagora mafi alheri,</p><p> Daki na nakoma nasamu guri na kwanta jiki ba kwari,</p><p> Har sheriff ya shigo dakin yasamay ni a kwance haka,nan cikin damuwa,</p><p> Hannu shi yasa saitin fuskana yana dan waven kamar mai maganar kuramay,</p><p> Yana shirin zamane yake ce min yana son muje shopping a kasar Turkish,</p><p> Banko bari yakarasa zancen shi ba nace mai gaskiya ba,zan je ba ,</p><p> Cikin mamaki yake kallona nace mai gaskiya duk abinda zamu bukata za,a samay shi a nan saudiya insha Allah,</p><p> Nakarasa da fadin kaga sauran kudin sai kakara ma masu zuwa sauke farali a wanan shekarar ko,</p><p> Yaji dadin wanan maganar tawa so sai don ido kawai ya zura min yana min kallo cikin sha,awa,</p><p> Bayan kwana biyu sai ga masu dicoretion din gida sun zo a wanan lokacin muka koma wanan can gidan mu na farko,</p><p> Kafin sati guda, har sun gyara ko ina sun kuma kwashe nafarkon sun tafi da shi,</p><p> Subawa mabukata don bamu da yan uwa da zamu bawa anan,</p><p> Tundaga get din gidan har zuwa cikin shi an gyara muna komai gwanin ban sha,awa,,</p><p> Kwanan mu guda da komawa gidan muna cikin murna sai ga kiran Abba cikin gagawa yake bidan Sheriff,</p><p> Duk da Alwashin dayayi cewa bazai kara fita waje ba sai bayan na hai hu ,</p><p> Wanan karon sai gashi yaza mai dole yafita, zuwa ansa kiran Abba,</p><p> Don a yadda yaji muryan Abban a waya hankalin shi ya tashi sosai gaskiya Allah Allah yake yi gari ya waye yai process din tafiyan shi,</p><p> Ina tsaye daidai lokacin da nagama rufe mai, zip din yar traveling bag din shi ,</p><p> Ya na tsaye ya na waya cikin fada, fada saidai da harshen turanci yake wayar </p><p> Hankali a tashe yazo inda nake tsaye cikin damuwa yai dan hugging dina yakai min sun bata daidai tsakiyar goshina ya ce min take care of ur selves pls,</p><p> Kafin duk in sauko in biyo shi har yakai bakin kofa dan gudu gudu yake tafiya,</p><p> Tsayawa nayi ina mai addu,a daga inda nake ina mai fatan Allah yadawo dashi lafiya,</p><p> Tashin hankali ya iske agidan don dai gida babu dadi </p><p> Saboda yaran mama sun sayar da duk wani abin da Abba ke tunkaho dashi ,</p><p> Ashe tun zuwan da kamal yayi sa,an shiga har cikin turakar Abba ranan jumma,a lokacin Abba na massalaci ya kwashe duk ka documents din yatafi dasu,</p><p> Abba yana hawaye yake sheda wa sheriff, wanda alokacin shima hawaye yake yi dan ganin hawaye tab a idon mahaifin shi,</p><p> Cikin kuka Abba keba sheriff hakuri murmushi sheriff yayi duk da hawayen dake idon shi ya ce ma Abba ai shi yadade da sanin haka </p><p> Yadaiki fada wa Abban ne kada ran shi ya baci, amma Abban yayi hakkuri dan Allah yabar su da duniya kawai itace zata koya masu darasi,</p><p> Abba na kuka yace duk sun wawashe komai Ahmad may zan bar maka kaida iyalinka nan gaba,</p><p> Murmushi yayi yagyara zaman shi yace ma Abba shikan Alhamdullahi gaskiya don ko ayanzu yana da abinda iyalin shi har ma da yan uwa zasu amfana,</p><p> Yakumace yana ma Allah godiya da yabashi Abba a matsayin mahaifi har ya tsaya mai yaga cewa yai karatu wanda zai amfane shi,</p><p> Kuka mai tsuma zuciya Abba yasa dan jin kalaman sheriff zuwa gare shi,</p><p> Yana mai bidan yafiya ga dan nashi wanda ada yamayar kamar bashi yahaife shi ba,</p><p> Hjy mama tana daga waje tana jin maganar su babu dama tashigo saboda warning din da Abba yai mata da dakin shi ,</p><p><br /></p><p><br /></p><p>🐎ZEEE MAKAWA🐎✈✈✈ *TAKARI*✈✈✈</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 👣👣👣👣👣</p><p> 1⃣0⃣0⃣</p><p> BY</p><p>🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎</p><p>🐎HUGUMA GROUP🐎</p><p><br /></p><p>Almost True Life Story,,,,</p><p><br /></p><p><br /></p><p> Tausayin mahaifin nashi duk ya sa jikin shi da zuciyar shi sanyi a lokaci guda ace mutum kamar Abba yana zub da hawaye, haka,</p><p> A ranshi yace tabbas ciwon mahaifin nasu nada nasaba hannun hjy mama da diyan ta,</p><p> Sai da sheriff yatabbatar da Abba ya kwantar da hankali so sai san nan yabar maiduguri zuwa Abuja,</p><p> Yana da kwana biyar a Nigeria doctor kamal yazo ya samay shi suka dunguma zuwa gurin inna,</p><p> Maigari yace ma su aiyanzu tunda angane inda yan uwan maihafin mu suke dole can za,a tafi neman auren mariya,</p><p> Sheriff yaji dadin irin aikin da ya iske anyi wa gidan innar mu </p><p> Saboda aikin ya kawatar da shi so sai wallahi, don haka yanzu yasan cewa koda tafiyan zuwa gida yakama mu baida wani shakku akan hakan kuma,</p><p> Yasa aka daukar wa inna yan aiki mata biyu duk da inna ta nuna bata son hakana zata iya yiwa kanta komai,</p><p> Amma saida sheriff yasa aka samo mata mutun biyu ya umurci Bashir duk wata ya dinga aika masu da albashi da kuma duk wani abin bukata da inna ke so,</p><p> Ita kuma hafsi ya sa aikai mata wurin buga pure water, sai engine din nikan gari har guda biyu, don ta samu madogara,</p><p> Allah ya taimake su Shehi ya bugowa maigari waya yace ya bashi baki akan ya gudanar da komai gamay da mariya,</p><p> Maigari yaji dadin wanan girmamawan da aikai mai sosai,</p><p> Don haka bata lokaci akai komai har sadaki saida aka yanke mai dubu hamsin da abinda Allah ya hore mai,</p><p> Saida suka bada sadakin suka dawo zuciyar su fam da dinbin mamaki acikin sa,</p><p> Lokacin komawar Abba check up yayi don haka sheriff baibar kasan ba sai tare da mahaifin shi,.</p><p> Don hakan ma yafi kwantar mai da hankalin shi,</p><p> Kwanan sheriff uku da dawo,wa kasar, shi da Abba nakuda yakamani cikin dare mariya nakira a waya nace ta kiramin maman Umar,</p><p> Zuwan maman umar baifi minti uku ba ba san balo dan yaro na yana ta tsala ihu,</p><p> Maman Umar wace duk ta rude lokaci guda dan bata ,zaci hakan ba don ita kokari takeyi na mu nufi asibiti,</p><p> Gefe na koma ina kokarin maida nunfashi, saboda sai naji ni sakat dani,</p><p> Sheriff nadaki yaji kukan jariri kamar a mafarki lokacin yafito kenan dagawa wanka yanashirin zuwa dakina yadiba ni don yaji shiru,</p><p> Akofan dakin sukai karo da mama Umar cikin rudewa take sheda mai cewa na haihu ai,</p><p> Mamaki ya kamashi so sai dan baifi minti talatin ba da muka rabu wurin cin abinci dashi,</p><p> Amma baiga wani alamar nakuda ba atare da ni lokacin,</p><p> Anyake wa yaro cibi har nai wanka saina kwanta saboda ciwon ciki da yadan murde ni lokaci guda,</p><p> Kiran doctor kamal yayi ya sheda mai abinda ke faruwa,</p><p> Murmushi doctor yai mai yace ai akwai irin wa, yan nan matan da basu wani dogon nakuda saidai kawai aji haihuwar su,</p><p> But sai dai still suna shan wuya sosai nadan lokaci guda saboda komai gaba daya yake,zo masu,</p><p> Doctor yazo tare da nurse guda biyu sukai min yan aune aune tare da yiwa jariri shi ma,</p><p> Sai allura da sukai min, sukace zuwa kwana biyu muzo asibitin su,</p><p> Sun fita da kamar minti biyar iyakar su bakin get din mu dai,</p><p> Ina cikin barci naji wani irin uban naguda yazo min wanan karon yafi na farkon zafi da ciwo sosai ,</p><p> Allah yatai make ni mama da mariya suna zaune gefe suna maganar a bugawa inna waya asheda mata cewa na haihu,</p><p> Sai gani na sukayi na sauko kasar gado da sauri nayarda bargo da na dan rufe jikina da shi,</p><p> A saman bargon dan yafado tare da uwar tafiya lojaci guda ,</p><p> Mikewa tsaye sukayi lokaci guda duk sai bari jikin su keyi,</p><p> Kamar ba zaiyi kuka ba sai kawai ya callara wani irin ihu, lokaci guda </p><p> Maman Umar da sheriff da ke tsaye adan falon mu na sama tana rike da jariri ta, sai ta kama waige waige don dai taga cewa ga jaririn dai a hannun ta sheriff nabashi zuma da zam,zam,</p><p> Har suna karo da juna gurin sauri tsakanin mama dake shirin fita dan kiran likita da nurse su dawo,</p><p> Itakuma maman Umar na kokarin shigowa dakin dan taga ko may ke faruwa, a ciko,</p><p> Salati duk suka sa lokacin da mama ke fadawa sheriff ai nakara haihuwa,</p><p> Doctor dake shirin shan kwanar uguwar mu dole ya juyo da motar shi cikin al,ajabi ,</p><p> Yaran biyu dukka maza ne wanan karon gaba dayan su,</p><p> Kuma gasu da gani identically twins, ne don harda dan digon da sheriff ke dashi shida Abba junior suma suna dashi daidai inda na sheriff yake,</p><p> Hakan yasa kowa kallon su tsab ko za,aga inda suke da ban banci don adinga gane su,</p><p> Har Abba yau saida yashigo har dakin da muke ciki saboda dakina bai shiguwa yau,</p><p> Hakan yasa na canza dakin dan agyara wancan din,</p><p> Wani irin barci nayi mai nauyi dan sai kusan sallah asubah nafarka, dawani irin yunwa,</p><p> Yunwa nake ji so,sai a lokacin, Allah yataimakeni maman Umar ta dama min kunu shina sha so sai aloacin,</p><p> Wanan karon dayake a saudiya na haihu na kara agurin yan black din mu so sai,</p><p> Don duk wa yanda sheriff ke hurda dasu da kuma yan uwan su sunzu muna murna,</p><p> Kamar kullun yau ma wasu kun,giyar yan ghana tare da yan Benin, suka shigo kusan lokaci guda </p><p> Masu abincin taron baki sun tanadar masu da konai har da su ruwan aiteard dake saman wani dan abin garwashi </p><p> Sai kuma, sai seashe, kalla da aka jera dai inda maza ke zaune saman wani jan carpet mai laushi,</p><p> Kusan kowani gidan balarabe zaka samu irin wanan dan wurin yin picnic din a gefen gidan inda zai dinga zama da iyalinshi su shan iska ko baki,</p><p> Duk wanda yazo za,abashi jariri yadinga kwararo mai addu,a idan zai mikawa wani zai aje mai kyautan, da yazo mai dashi,</p><p> Kusan duk Union din da sheriff yake sunzo muna wanan yar walimar bawai sai anjira ranar suna ba,aa duk lokacin da Allah yabada iko sai kazo,</p><p> Don haka mun tara kyauta mai dinbin yawa daga al,uman Annabi,</p><p> Don har larabawa sun zo muna barka saboda shaharan sheriff a cikin su,</p><p> Shi kan shi sheriff yayi mamakin irin jama,an dake zo mai murna,</p><p> Mutane Nigeria sun zo saidai bada yawa ba gaskiya,</p><p> Daga antyn mu falmata sai anty shuwa, yayan su Amal wace ke biwa sheriff, sai kuma antyna hafsat da safiya, sai Salimat,</p><p> Su kawai sukazo dan canjin yanayi da kasa tasa mu yanzu,</p><p> Yaran anbar su da sunan su hassan da husaini,</p><p> Hjy mama sai daga baya take nin cewa ai na kara haihu diya biyu kuma, </p><p> Hankalinta yatashi duk ta kidemay tashiga cikin wani yanayi </p><p> Wai ace har sheriff yakai ga tara iyali haka ita babu ko yaro guda daga cikin diyan ta da yai aure har yanzu,</p><p> Hakan yasa hakalin ta yai mugun tashi har ya kai ga ta bidi hadin kan Nafisat a lokacin don tayar da su hada hannu su san yadda zasu yi da sheriff din,</p><p> Allah ya taimaka nafisat bata abu batare da shawaran mahaifiyar ta ba,</p><p> Don haka babu bata lokaci ta sheda wa mamanta abinda hjy mama tace mata,</p><p> Ita kuma uwar bata lokaci tasheda wa mahaifin nafisat din amin Abban sheriff, </p><p> Kiran hajiya mama yayi yai mata kacakaca ta waya kuma yace sai ya fadawa sheriff da mahaifin shi,</p><p> Zaune muke sherrif na ma yar lelensa ummibanan wasa, don kusan ko yaushe in har yana gida suna like da Ummi, </p><p> Saboda shakuwan shi da ita har ya kai ko barci sai ya lalashe ta take inki baya gari aiki yasamu ke nan da mu dake gida zamu sha kuka agurin ta ranan,</p><p> Wayan shi ce ke ta kara alamar kira na shigowa hannu yasa ya dauko wayar dake gefen shi,</p><p> Da sauri naga ya mike daga kwancen da yake saman dongon kujera, </p><p> A hankali ya aje Ummi a gefe guda, yana mika mata key din dake hannun shi dan tayi shiru,</p><p> Cikin gimamawa naji yana cewa baba mun yuni lafiya yana yi kamar baban na ganin shi,</p><p> Jin danayi yace baba yasani kokarin mikewa dan in bar gurin,</p><p> Saboda mutum guda nasan yana kira da baba watau mahaifin nafisat,</p><p> Da hannu ya nuna min alamar in zauna abina kawai,</p><p> Zama nayi amma agaskiya ban so zama ba dan ban san kowani maganar siri zasuyi ba a,tsakanin su,</p><p> Kai kawai naga sheriff yana dagawa sai kuma kiran innalillahi danaji ya nayi,,</p><p> Jin danayi yana cewa baba nasan cewa hjy mama zata iya aikata koda fiye da hakan, </p><p> Babu kazafi a wanan zancen baba tunda har ita nafisa ta,fadi hakan ayi shine tabbas,</p><p> Daidai lokacin da yadauko Ummi ya aza a saman jikin shi, yake cewa </p><p> Insha Allah Abba zan dauki mataki akai kafin ta aikata wani mugun abin kuma,</p><p> Abba zai dawo Abuja da zama yabarta can zan sa masu security, sosai agida,</p><p> Haka sukai ta zancen su harzuwa wani lokaci ina gefe ina ba yara nono saidai duk hankalina ya daga sosai gajin bayanin su,</p><p> Sukayi salama sheriff din nata wa baba godiya akan fadarkar dashi dayayi,</p><p> Bayan sunyi sallama ne naji yayi ajiyar zuciya mai karfi sai yakama nanata kalman innalillahi,</p><p> Tashi nayi daga inda nake nadawo saman kujerar da suke zaune na zauna gab da shi,</p><p> Saida yanisa yadago ido yakalle ni yace min fatima </p><p> Hjy mamace wai ke son hadin kan nafisat su halaka mu ni da Abba su ci dukiyar mu,</p><p> Subbahanal da innalillah Allah yabani ikon fadi alokacin saida naji cikina ya kada saboda fargaba don har ga ni nake yi ai kamar har sunzu halakasu din ko,</p><p> Kwalla nagani a idon shi yana fita sai kawai tausayin shi yakamani,</p><p> Shifide yaron dake a hannu nayi na danna intercom </p><p> Saiga maman Umar na umurce tada ta dauki yaran zuwa gurin su Tumba da mama,</p><p> Suna bace wa nadawo kusa da sheriff har muna iya jin numfashin junar mu a lokacin,</p><p> Nace mai a hankali may ye a bin yi yanzu sheriff,? </p><p> Yadago idon shi rinanu sun yi ja jar yace min hmmmmm bari Fatima lisafima duk ya kwance min ai,</p><p> Saida na nisa alokacin maman Umar tadawo daukan sauran yaran bin bayanta nayi da kallo har ta bace min,</p><p> Sai wani tunane yafado min arai nace may zai hana Abba yai wani aure ko zai samu kulawa daga matar,</p><p> Wani irin kallo sheriff yai min da idon shi da suka rene sukayi jawur</p><p> Yace aure kuma Fatima kamar Abba za a ce yayi aure yanzu </p><p> Saida na dan kara matsowa kusa da shi sosai na fara mai bayani ta yadda zai gamsu da bayani na,</p><p> Saida yanisa yace fatima Abba fa ba wai yana hurda da kowa bane balle in ce kila akwai wace zai iya aure yanzu,</p><p> Cikin sauri nace mai ga maman Umar nan mu hada tadashi tunda duk mun yaba da irin halaiyar ta mun sani,</p><p> Yamike tsaye yana ce min sai yayi shawara ido nabishi dashi har ya bace min,</p><p> Ba adauki wani lokaci ba wanan maganar ya tabbata ,</p><p> Amma saida shehi yazo da kanshi yaiwa Abba nasiha so sai mai kashe jiki akan karin iyali,</p><p> Ranan jumma,a bayan ankare sallah kamar yadda akeyi </p><p> Aka daura auren Abba da Umma salma,( maman Umar)</p><p> Inda suka tare a tsohon gidan sheriff,</p><p> Zasu dan zaina kwana biyu kafin sheriff yagama process din abin da yake yi,</p><p> Auren mariya a Nigeria aka daurashi, amma amarya nacan saudiya,</p><p> Bamuyi wani wahalan zuwa Niger ko Nigeria ba maza ne kawai suka zo daurin aure,</p><p> Amarya mariya tasha gyara gurin su anty Amal, so sai don abin har saida yabani tsoro,</p><p> Har zuwa wanan lokacin ban fara kwana da mijina ba saboda abubuwa da sukai muna yawa,</p><p> Sai bayn tarewar mariya ne muka samu lokacin kan mu nida sheriff,</p><p> Duk yadda naso in zulle mai saida yasan yadda yai dabara yau yakai gare ni,</p><p> Sai bayan komai ya kammala ne atsakanin mu yadan kalleni yace min fatima na ansa mai a gajiye yace,</p><p> Ya akayi najiki kin wani kara ni,ima haka, shin may sirin abin ne wai,</p><p> Anya kuwa Fatima, zaki barni in ,zauna da wata mace kuwa,</p><p> Har ya gama maganganun shi, ban yarda na ce mishi komai ba</p><p> Nidai nasan cewa anty falmata tayi aikinta ke nan ita da Salimat,</p><p> A ranan sai da dabara nasamu na sauko zuwa kasa dan sheriff gabadaya ban gane mai ba,</p><p> Ba,a dauki wani lokaci ba Abba da amaryan shi su kadawo Nigeria, da ,zama </p><p> Direct Maiduguri suka fara zuwa, saboda Abba yace can zai fara zuwa,</p><p> Haba hjy mama ina wuta tasaka sheriff da mahaifin shi,</p><p> Balle yadda taga maman Umar yariya shar doguwa fara,</p><p> Mai kyau da ita ga kuma wayewa kamar wace tai zaman turai,</p><p> Zuwa kwana biyu suka bar maiduguri zuwa Abuja tare da umar don. AISHA anbar muna ita gunmu,</p><p> Sheriff ya mayar wa wa ya da suka sayi kaddarorin Abva kudi a ka basu abin su cikin ruwan sanyi,</p><p> Bayan kwana biyu muka zo madina don ziyara mu , mika gaisuwar mu ga ma,aikin manzon rahama,</p><p> Shine har Allah ya hada .u dake a masallaci nai maki wanan labarin nawa,</p><p> Yanzun haka yaran mu shida da sheriff maza biyar mace guda,</p><p> Ga harkokin sheriff sai gaba gaba yakeyi akoyau she,</p><p> Kuma ina zuwa gida Nigeria zuwa ziyar yan uwa da abokan arziki,</p><p> Muba nan tare da nafisa wace ke zaune a garin Abuja ita kadai,</p><p> Saidai insha Allah kwanan nan zamu dawk gida Nigeria saboda sheriff ya nan yana kokarin aje duk har kokin shi na can mu ko.a guda yaci gabada business din shi acan,</p><p> Dafatan yan uwa musullumai zasuci gaba dayi muna fatan alheri a rayuwar mu,</p><p> Nagode Nagode Nagode, Da lokacin da kuka bani don sauraren wanan dan guntun labarin,</p><p> </p><p><br /></p><p>Yan uwa anan labarin fadima yar TAKARI yakawo karshe da fatan zaku yafe min duk wani kuskuren da na aikata acikin wanan labarin mai suna TAKARI,,,,, </p><p> Godiya gare ku yan uwa yan huguma groups baki daya da kuma sauran group da ban anbaci sunar su ba,</p><p> Godiya ga Anty Hafsat , ta huguma Mama Farida , anty Mariya SB, da Anty Nafisat,Harzami da sister maijidda Harzami</p><p> Don Allah duk yan uwa da ban an baci sunar su ba ,Ina fatan zasu yi min hakuri, su yafe mindan Allah,,,,,,,👏👏👏👏👏</p><div><br /></div><p><br /></p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-42135220963076616962020-12-05T21:43:00.004-08:002020-12-05T21:43:48.342-08:00SHAHRAZAD COMPLETE HAUSA NOVELS<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-DxNXpjYkppg/X8xvFlM5NSI/AAAAAAAAJc4/rkZmGWLgPJ0yR5fn18MxNO0ii6Ip03HrQCLcBGAsYHQ/s2048/SHAHRAZAD.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="SHAHRAZAD COMPLETE HAUSA NOVELS" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-DxNXpjYkppg/X8xvFlM5NSI/AAAAAAAAJc4/rkZmGWLgPJ0yR5fn18MxNO0ii6Ip03HrQCLcBGAsYHQ/w320-h248/SHAHRAZAD.jpg" title="SHAHRAZAD COMPLETE HAUSA NOVELS" width="320" /></a></div><br /> [4/15, 10:02 PM] +234 806 448 1931: *GODIYA* <p></p><p>Godiya ta tabbata ga Allah (s.w.A) daya bani ikon fara wannan littafin , tsira da amincin Allah su kara tabbata ga manxonshi annabi Muhammadu ( S.A.W) da iyalan gidan sa da kuma sahabban sa.</p><p><br /></p><p> *Tukuici* *GA* </p><p>Sameera aliyu da anas dina Allah ya rayashi ya albarkace shi. Ameen.</p><p> </p><p> *GAISUWA* *GA* </p><p>Dukkan dukkan marubuta littafan Hausa.</p><p><br /></p><p> *KYAUTARWA* *GA* </p><p> Shahrazad dina wannan novel nakine halak malak.</p><p><br /></p><p> *TUKUICI* *GA*</p><p>Dukkan makarantana na ko INA ciki da wajen kasarmu, ban cire kowa ba.</p><p><br /></p><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p> *JINJINA*</p><p>Ga shahrazad my shona pyar zindagi</p><p><br /></p><p>*JAN* *KUNNE*</p><p>A dinga kokarin aje littafinmu a lokutan sallah da aikin gida, da makaranta.</p><p> Na gode.</p><p><br /></p><p>❣ *SHAHRAZAD*❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p><br /></p><p>*By* *NUSNIM*</p><p> </p><p> 1&5</p><p>Ke kam fatima kina wanka kamar mai canxa fata dallah mallama kiyi Sauri, in ba haka ba wallahi mutafi mubarki , ni'imah CE ke wannan mitar .</p><p><br /></p><p>Khausar ta amshe maganar da cewa aikuwa dai don na kosa mu isa gidan aunty shahrazad don a kage nake danaji labarin ta, kun San tace muxo da wuri don labarin da tsayi.</p><p><br /></p><p>Nusaiba dake gefe tana karanta wani story book, ta dago ido ta kalle su race haba sisters kubar fatima tayi wankanta mana. Duk kunbi kun cikata da mit__ __ kafin tagama rude bakinta sai ga fatima tana cewa, rabu dash daughter.</p><p><br /></p><p>Ni'imah ta harareta saboda haushi race munkusa muyi gaba wallahi Mara "m" </p><p><br /></p><p>Fatima ta kallesu a kaikaice , cikin wasa tace " Ku don't kun saba yin jika jika ni ban saba ba " amma banda daughter nusaiba</p><p><br /></p><p>Khausar tayi dariya tayi tafi tace .</p><p><br /></p><p>" lallai ma wannan yarinyar yar rainin hankali CE, an gaya miki mu kaza mai ne? Kalle mu fa ki gani"</p><p><br /></p><p>Tayi Dan murmushi , tace "ai najima da sanin Ku !!</p><p>Ni'imah ta harareta cikin wasa " kefa baki da mutunci , duk uban zaman nan da mukayi muna jiranki babu abundant zaki saka mana dashi sai cin mutunci? Mun gode amma ki sani zamu rama" </p><p> Tayi dariya tace sai dai Ku rame wallahi",</p><p><br /></p><p>Nusaiba tace kunga Ku rufe wannan chapter din naku muyi abunda ke gaban mu , mummy fati sorry yi sauri kishirya , toh baby nuscy.</p><p><br /></p><p>Su nim da khausar suka ce hmmm wayaga uwa da ya, fatima tagama shirinta suka fito haraban gidan su.</p><p><br /></p><p>Yan mata be su hudu masu ji da Kansu , fadimatul zara'u ni'imah , nusaiba Kausar, tafiya suke cikin kasaita kowacce idan ka ganta said ka rantse babu mai damuwa cikin su.</p><p><br /></p><p>Alhalin ba haka bane kowaccen su ta dandana bakin ciki biyu daga cikin su suna da aure.</p><p><br /></p><p>Fatima tana da sure yayinda akayi mata auren dole alhalin tana da Wanda takeso amma shi bai San tanayj ba, iyayen ta sunyi fama da ta fitar da miji amma bata fitar ba , sai dai kullum tacewa iyayenta sukara mata lokaci . mahaifin fatima ya gaji da jiranta akan da ta fidda miji.</p><p><br /></p><p>Shine ya yanke shawaran hadata aure da Dan abokin sa mai suna abubakar , fatima tayi kuka sosai akan hukuncin da abbanta y yanke mata, ba yadda zata iya haka ta hakura ta karbi auren abubakar.</p><p><br /></p><p>Amma zuciyar ta tana wajen najibullah , Gangar jikinta ne ke wajen abubakar.</p><p><br /></p><p>Watan Fatima biyar agidan mijinta ts gudu saboda baza ta iya rayuwar aure da mutumin da bata so .</p><p><br /></p><p>Tashigo motan zuwa Kaduna dama ita yar kano ce acikin mota ne suka hadu da ni'imah.</p><p> </p><p>*kubiyoni* *agaba* *don'* *jin* *wacece* *ni'imah* </p><p>TAKU UMMU RUMAN ( *nusnim*)</p><p>[4/15, 10:02 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p> (Labarin Sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p><br /></p><p> 5&10</p><p>Acikin mota ne suka hadu da ni'imah itama sakamakon guduwan datayi Daga gidan aurenta, ita mijinta muxguna mata yakeyi bai bata abinci sai dai ita taje ta nema.</p><p><br /></p><p>Da hakan ta kai karanshi gdan iyayen ta amma sai suka ki su yarda da ita " saboda su a tunanin su sharri take masa " tunda dama tun asali bata son auren akayi.</p><p><br /></p><p>Daga karshe dai tarasa ya zata yi shine ta yenke hukuncin data gudu , tunda anki sauraronta.</p><p><br /></p><p>Wannan shine takaitaccen labarin auren ni'imah da fatima.</p><p><br /></p><p>Fatima tana zaune kusa da Ni'ima a cikin mota" tayiwa ni'imah sallah tare da mika mata hannu , ni'imah ta amsa mata tare da mika mata itama hannu.</p><p><br /></p><p>Fatima tace baiwar Allah idan bazaki damu ba ina da tambaya? Ni'ima tacs bismillah Allah yasa na sani?</p><p><br /></p><p>Fatima tace nagode da kika bani dama.</p><p><br /></p><p>Dama zan tambaye kine kema Kaduna zaki ? Ni'imah tacd mata eh Kaduna zani.</p><p><br /></p><p>Fatima tace yauwa Ashe waje daya zamu je " ni'imah tayi murmushi , fatima taci gaba da cewa don Allah wani unguwa ne agarin Kaduna Wanda kasuwanci yake da saukin yi aciki Wanda komin kankar tarshi zaka samu abunda kake nema?</p><p><br /></p><p>Ni'imah tayi nadan wani lokaci sannan race eh to dayake nima yau nafara zuwa Kaduna ba lallai bane na sani, amma inba zan manta ba agarinmu suleja akwai wata makociyar my tana cewa , kasuwanci a u/rimi yafi dadi don tayi zaman wajen gasu da girmama mutane da sanin kimar mutane," shiyasa Nima nake son na sauka a u/rimi.</p><p><br /></p><p>Fatima ta numfasa tace inna fahimce ki, kema bakuwa ce again zuwanki na farko kenan?</p><p><br /></p><p>Ni'imah tace eh , fatima tace Ashe tafiyar mu daya dake nima bakuwa ce kuma ma idan munje Kaduna bansan inda zan sauka ba , banda kowa agarin.</p><p><br /></p><p>Sai ga hawaye na zuba a idanun fatima , Ni'ima tayi saurin cewa yar'uwa lafiya naga kina hawaye? Meyasa ki kabar garinku ? Bayan baki San kowa anan Kaduna ba?</p><p><br /></p><p>Fatima tayi murmushi takaici, tace yar'uwa cewa zakiyi meyasamuka bar garin my bayan ba mu San inda zamu ba?</p><p><br /></p><p>Sai ga hawaye a idon ni'imah , Ni'ima taci ni ina da kwakkwaran dalilin barina mahaifata wato suleja.</p><p><br /></p><p>Ni'imah taci gaba dacewa da farko dai yaka mata mugaba tarwa da kanmu junan mu" fatima tace hakane.</p><p><br /></p><p>Fatima tace ni sunana fatima Muhammad kuma ni yar garin kano ce.</p><p><br /></p><p>Ni'imah tace ni sunana ni'imah haruna ni yar garin suleja ce , daga suleja nazo kano sannan kuma na Hau motan Kaduna.</p><p><br /></p><p>Nan fatima da ni'imah suka ba mawa junayen su labarin kan su , duk sun tausaya ma Kansu , kuma sun kills kawance kamar yan uwan juna, fatima tace mubar ma Allah komai "sannan mune ma taimakon sa akan bukatun mu, sannan kuma ya ganar da iyayen mu akan kuskuran su da suka aikata.</p><p><br /></p><p>Ya Allah ka bamu ikon yiwa ya'ya'yen mu adalci kuma kabamu ikon yiwa iyayen mu biyayya ameen.</p><p><br /></p><p>Da haka suka sauka garin Kaduna mai train albarka garin gwamna (center of Learning) Suns kara sowa kawo wani sanyin dadi sukaji y ziyarce zuciyan su.</p><p><br /></p><p>Bayan sun sauka daganan suka Hau napep da zuwa u/rimi " mai napep din ne ya tambaye su dai dai ins zasu sauka a u/rimi sukayi Dan shiru na wani lokaci sannan fatima tace dai dai wajen makarantar nan me Suns Kaduna (state university Kasu)yace to.</p><p><br /></p><p>Ni'imah ta kalli fatima tace fatima me zamuyi amakaranta bayan bamu da kudin Shiva kuma wajen ai, ba wajen Sana'a bane wajen karatu ne.</p><p><br /></p><p>Fatima tace hakane amma inaji ajikina kamar zamu samu irin su photo copy's tunda nasan Baxa arasa acikin school din ba ko kuma shagon provision hakane kam.</p><p><br /></p><p>Sun karaso dai dai gate din Kasu, suka sauka tare da biyan mai napep kudinsa.</p><p> Sun tsaya cirko cirko abakin Kasu Suns tunanin ta INA zasu fara, su saka wannsn su kulla wancan.</p><p><br /></p><p>Da haka Suna wannan tunanin ne suka hango wata yar budurwan yarinya waccd baza ta wuce shekaru 23 ba tana tafiya cikin nutsuwa da alamun zata shiga cikin (Kasu) din ne .</p><p><br /></p><p>Fatima race ni'imah anya bazamu yiwa wannan yarinyar magana ba ko ma samu hanyar shiga cikin Kasu?</p><p><br /></p><p>Ni'imah tace aikuwa kuma da alama tana da saukin kai suna cikin magana ne sukaji ta musu sallama tare da wucewa suka amsa sallamar ta.</p><p><br /></p><p>Had ta gota su fatima tayi saurin cewa baiwar Allah Dan tsaya cak ta tsaya.</p><p><br /></p><p>*TAKU* *UMMU* *RUMAN* ( *NUSNIM*) </p><p> </p><p>Pls duk me novels dina ya taimaka y turon</p><p>Adalilin sonta</p><p>Hanta da jini</p><p>Kuncin rayuwa</p><p>Kutausaya min</p><p>Labarin ni'imah</p><p>Aljana CE ko mutum</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:02 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin Sharrin zuciya)</p><p> *BY* *NUSNIM*</p><p> 10 & 15</p><p>Fatima tayi saurin cewa baiwar Allah Dan tsaya cak ta tsaya tare da juyowa fuskarta dauke da murmushi, fatima da Ni'ima suka karaso inda take , suma fuskar su dauke da murmushi suka gaisa.</p><p><br /></p><p>Fatima da Ni'ima suka fada mata sunan su tace wood mai sunan mamana fatimah " sannun Ku ni kuma sunana nusaiba sulaiman " ni'imah Suna mai dadi.</p><p><br /></p><p>Fatima tace nusaiba Dan Allah inbaza ki damu ba taimako muke nema , mu baki ne agarin nan, mun fito Neman aikinyi ne don mu rufa mawa kan mu asiri , koda iron aikin photo copy's ne tunda munyi karatu Daga secondry har diploma na ( computer school).</p><p><br /></p><p>Nan dai suka mata bayanin Daga inda suke !!! Amma basu fada mata dalilin fitowar su Daga garin su ba.</p><p><br /></p><p>Nusaiba ta danyi shiru na Dan wani lokaci kadan yayin da fatima da ni'imah sai addu'a sukeyi azuciyan su, Allah yasa su sami abunda sukazo nema.</p><p><br /></p><p>Nusaiba ta dago idonta Tamara kallon su da kyau , sannan tace ba damuwa in Allah ya yarda zan taimaka muku iya gwargwado nah!!! Don kaima bakasan nan gaba wazai taimake ka ba.</p><p><br /></p><p>Su fatima sunji dadi sosai sai godiya suke ta mata, nusaiba tace nima aiki nake acikin (Kasu) din fannin photocopys din, nida kawata"" amma yanxu bara na kaiku gidan mu Ku huta tunda kunsha gajiyan hanya, kafin zuwa anjima muga yadda zamu bulluwa al'amarin.</p><p><br /></p><p>Suka ce to mun gode nusaiba.</p><p><br /></p><p>Nusaiba ta tsare musu napep ya kaisu dagel (1) banisa Daga Kasu duk area din u/rimi ne, bayan sun sauka tabiyashi kudin sa.</p><p><br /></p><p>Nusaiba nagaba, su fatima nabinta abaya har suka Shiva cikin gate din, babban gida ne mai flat dayawa aciki akalla zasu kai flat 20 sannan kuma ga mai 1 bedroom with toilet aciki.</p><p><br /></p><p>Wannan mai 1 bedroom with toilet yan makaranta sunfi kamashi sabanin mai flat shi kuma irin masu iyalan nan ne.</p><p><br /></p><p>Su nusaiba suka Shiga bangaren mai 1 bedroom tabude wani daki tace bismillanku daki ne Dan ma dai dai ci da toilet aciki sai gado da akwatina , sai (TV) said kuma kujera guda daya dake gefe , kayan dakin basu cika yawa ba komai dai dai .</p><p><br /></p><p>Fatima da Ni'ima suka zauna bakin gado , nusaiba tace musu tana zuwa , bayan fitar ta da yan mintina, ta dawo dauke da kulan abinci sai ruwa da drinks ta ijye musu agaban su.</p><p><br /></p><p>Ga abinci kuci in kungama ga toilet can koda zakuyi wanna ko wani abun, ni zan koma wajan aiki ne, saboda akwai abunda zanyi amma bazan Dade ba zamu tashi Daga wajen aikin ba.</p><p><br /></p><p>Ni'ima tace OK badamuwa nusaiba sai kin dawo mungode , tace laa bakomai" duk anxama daya Allah ubangiji dai yamana jagora a dukkan al'amuran mu allahumma ameen.</p><p><br /></p><p>Su fatima sunci abinci sungama har suka watsa ruwa , tare da gabatar da sallolin su , bayan sun idar sukaci gaba da tattaunawa akan al'amuran su.</p><p><br /></p><p>Nusaiba ta isa wajen aikinta wata yar matashiyar budurwa wacce baza ta wuce sa'ar nusaiba ba, tace haba nusaiba tun dazu fa nake jiranki, mu karasa aikin nan kin San yau za suzo karba ko, duk ta marairaice fuska kamar zatayi kuka .</p><p><br /></p><p>Nusaiba tace sorry my lovelly sisto wallahi wani abune ya tare ni, nan nusaiba ta labar ta mata abunda ke faruwa , tace Allah sarki har sun bani tausayi.</p><p><br /></p><p>Yanxu abunda yadace muyi don mutaimaka masu shine muyiwa oganmu magana dama muna Neman Karin ma'aikata, sannan kuma sai muyiwa hajiya magana akan makwancinsu , sai aka ma musu dakunanan dake kusa da da kunan mu tunda bakowa acikin su.</p><p><br /></p><p>Sai tabamu hayan daki daya , Daga baya idan sun fara samun kudi sai su kama dayan dakin !! Kinga munzama mu hudu kenan dakunan mu a Jere batare da takura ba.</p><p><br /></p><p>Nusaiba tace yauwa sister gaskiya kin kawo idea mai kyau dama ina tunanin tayaya zamu bulluwa Lamarin, sai ko gashi cikin sauki kin kawo mana bayani.</p><p><br /></p><p>Nusaiba sunyiwa ogansu magana kuma ya amince , sannan kuma sunyiwa hajiya magana akan sun son daki daya, Daga baya zasu bata kudin dayake ta yarda dasu kuma suna bin dokokin hayar gidanta, shiyasa batajin shakkan ta hanasu daki ba.</p><p><br /></p><p>Duk sai da suka gamawa su Fatima komai kafin su shiga gida , bayan sun shigo cikin (compound) din gidan su , nusaiba tace sister bani key din dakin ki in dauko wayata dana jona chaji daxu OK.</p><p><br /></p><p>Bayan ta dauko suka shiga dakin nusaiba sallama sukayi tare da tura kofan , yayin da Ni'ima ke kishingide tace Waalaikumus salam !! Fatima tace a'a nusaiba har kun tashi ? Tace eh wallahi sannunku da hutawa" yauwa.</p><p><br /></p><p>Fatima ta kalli abokiyar tafiyar nusaiba .</p><p><br /></p><p>Tace nusaiba wannan itace kawar taki wadda kikace kuna aiki tare ? Tace eh itace nan dai aka kara gaggaisawa.</p><p><br /></p><p>Nusaiba tace wannan itace kawata khausar ita yar adaamawa ce na yankin (MUBI) ni kuma yar Hadeja ce.</p><p><br /></p><p>Fatima tace allah sarki anan garin kuka hadu kenan? Nusaiba tace eh dukkan mu mun baro gdan iyayen mune saka makon auren dole daza amana , alhalin dukkan mu munada wayanda mukeso .</p><p><br /></p><p>Amma iyayen mu sunki bama damar fidda mijin da muke so , ganin ana shirin yimana auren mukabi shawaran zuciyar mu mukabar garin mu.</p><p><br /></p><p>*kubiyoni* *agaba* *don* *muji* *shin* ya *rayuwa* *yan* *matannan* *zai* *kasance* *star* *dinsu* *tanan* *tafe* *cikon* *tabiyar* *din* </p><p> </p><p>Ina Neman novels dina please</p><p>Adalilin sonta</p><p>Hanta da jini</p><p>Kuncin rayuwa</p><p>Kutausaya min</p><p>Labarin Ni'ima</p><p>Aljana CE ko mutum </p><p>08064481931</p><p><br /></p><p>*TAKU* *UMMU* *RUMAN* (NUSNIM)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:02 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p> (Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 15 & 20</p><p>Shine mukabi shawaran zuciyan mu mukabar garin mu .</p><p><br /></p><p>Ni'imah tace Allah sarki Ashe duk matsalar mu daya " sai dai mu anriga da ammana auren. Don da auren mu muka bar garin my , khausar tace kai garin yaya hakan ta faru?</p><p><br /></p><p>Nan' ni'imah ta labarta masu komai har zuwan su Kaduna " kowaccen su saida ta share kwalla , nan dai suka bamawa junayen su shawara , nusaiba tabayyana musu zancen aikinsu da dakin kwanan su , sunji dadi sosai suka kara yi musu godiya.</p><p><br /></p><p>Rayuwar su shar shar komai ya dai dai ta musu, sai dai Dan damuwan da baza arasa ba wacce bata wuce na kewar gida ba, suna aikin su kuma suna samu da haka har suka kama dayen dakin .</p><p><br /></p><p>Kowaccen tana da dakinta , suna sana'oi da dama shiyasa basu zama " saboda suna da zumar cigaba da karatu.</p><p><br /></p><p>Akwana atashi bawuya wajen Allah har sun samu shiga *Kasu* fatima da nusaiba depertment dinsu daya suna karantar ( biochemistry) yayinda ni'imah da khausar suke karantar (microbiology).</p><p><br /></p><p>Ayanxu haka suna matakin 200 level, rayuwar su shar, anan Kasu suka hadu da aunty shahrazad wajen cin abinci, lokacin itama take lunch" tabayan kujeran da take zaune ne taji su ni'imah suna tattaunawa akan rayuwar su sai taji tana son su kulla kawan ce" ko don ta basu shawara akan biyewa sharrin zuciyar su da sukayi.</p><p><br /></p><p>Duk da ta dan girmemu su , sannan ita matar aure ce kuma tan 300 level itama (biochemistry) take karanta.</p><p><br /></p><p>Shahrazad ta tashi Daga kujeran da take tazo wajen su khausar tare da cewa assalamu alaikum .</p><p><br /></p><p>Suka amsa mata da wa'alaikumus salam, tace sannun Ku fa cikin fara'a " suma suka maida mata da martani tare da bata wajen zama" taji dadin karban da suka mata.</p><p><br /></p><p>Tace ni sunana shahrazad abdulmaleek ina karatu acikin Kasu inda nake karantar biochem. Sannan kuma inada aure da yaro daya me suna *umar* *farouq* .</p><p><br /></p><p>Nusaiba tace woow suna mai dadi khausar tace aunty shahrazad ina son yaronki duk da banganshi ba , amma naji ina sonshi" shahrazad tayi murmushi tace nagode.</p><p><br /></p><p>Tace gaba da cewa dafatan zaku karbeni amatsayin kawar Ku in badamuwa , Fatima tace why not , insha Allah munxama kawaye , amma fa kinzama auntyn mu , tace haba dai kawar Ku nazama.</p><p><br /></p><p>Ni'imah race auntynmu kika zama" tunda kin girme mu gaki da aure harda baby boy !! Kinsan shi aure yana jawowa mutum girma da Kima a idon mutane . shahrazad tace hakane nagode da wannsn girman da aka bani.</p><p><br /></p><p>Shahrazad tace saura Ku ' Ku sanar min da kanku " sun gabatar mata da Kansu kuma ta gamsu.</p><p><br /></p><p>Kawance mai karfi ya kullu tsakanin shahrazad dasu nusaiba " har suna zuwa gdan ta su wuni dayake mijin shahrazad matafiyi ne " gidanta yana nan a malali a halliru Dan turo cresent.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Su fatimah suna jin dadin tarayya da shahrazad , saboda macece mai kirki da Sanin ya kamata " ga hidimomi datake yawan yi musu " alheri kala kala ba wacce basu gani Daga wajen shahrazad " hakan yasa sukayi mugun shakuwa da 'ita , kuma takan basu shawara akan abunda yashige mu su duhu, saboda yadda da sukayi da ita yasa basu boye mata sirrin su ba.</p><p><br /></p><p>Lokacin da shahrazad taji asalin labarin su " ta tausaya musu " sannan kuma taga wawtarsu akan biyewa Sharrin zuciya har suka bar mahai fansu, wannan ba karamin kuskure suka tafka ba.</p><p> </p><p>Shiyasa tace musu da suxo ranar weekend don tabasu labarinta da irin hakurin da tayi" ta mikawa Allah lamarinta .</p><p><br /></p><p>*wannan* *shine* *takaitaccen* *labarin* *wayannan* *gwanayen* *matan*</p><p><br /></p><p>Bayan fatima tagama shirinta su ka fito haraban gdan su, suna tafiya nusaiba tace oh rayuwa kenan gashi wai yanxu har muna 200 level muna tsaka da shiga 300 level kamar ba yau muka fara ba , fatima tace hakane daughter nusy.</p><p><br /></p><p>Wato shi lamarin rayuwa yanxu sai da hakuri da addu'a kafallamawa Allah komai lamarinka " sai kaga yamaka jagora a rayuwarka mu tsarkake zukatan mu " muriqe gaskiya da amana aduk inda muke.</p><p><br /></p><p>Ni'imah tace tabbas kuwa yanxu kufa kalla yaushe muka fara wannan business din takalman da atamfofin nan " sai ganin cigaba mukeyi kuma Dan danan ya kare ankawo wani.</p><p><br /></p><p>Khausar tace lallai kam alhamdulillah " babu abun bautasa da gaskiya sai Allah, Allah mun gode maka.</p><p><br /></p><p>Sun fito bakin gate din daidai hajiya mairo ta fito da mota zata fita sukaci karo da ita"suka gaisheta cikin girmamawa" tace a'a daughters dina sai INA zuwa , suka ce malali zamuje gidan kawar mu.</p><p><br /></p><p>Tace hanyar mu daya kuxo muje inkaiku , ni zani f.j.c ne makarantar su salim " OK hajiya mun gode, tace bakomai har kofar gidan shahrazad ta sauke su , sukayi mata godiya ta tafi.</p><p><br /></p><p>*kutara* *tara* *agaba* *don* *jin* *wainar* *daza* *atoya* *agdan* *shahrazad*</p><p><br /></p><p>TAKU UMMU RUMAN( *NUSNIM*)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:02 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p> (Labarin sharrin zuciya)</p><p> *BY* *NUSNIM*</p><p> 20 & 25</p><p>Sukayi mata godiya ta tafi su kuma suka shiga cikin gidan da sallama, lokacin shahrazad tana kallon TV taji sallamar su , ta tashi cikin murna don tarban su.</p><p><br /></p><p>Oyoyo sisters dina aiko yan xunnan nagama tadinku axuciyata" Ashe dai kuna tafe khausar tace aikuwa dai.</p><p><br /></p><p>Shahrazad tace bismillah kuxauna" suka zauna fatima tace wash nagaji " ni'imah tace aikin me kikayi daza kice kin gaji, ke da ba'akafa kika taho ba , bantala ace gajiyan tafiya ce.</p><p><br /></p><p>Fatima ke raguwa ce Allah " nusaiba tace kai ni'imah Dan Allah kibar min mummy nah ta sarara mana" tun kafin muxo gidan aunty shahrazad kuke ta damunta keda khausar.</p><p><br /></p><p>Shahrazad tayi dariya tace Ku dai Baku rabuwa da tsokana " gaskiya ni'imah da khausar zamu sa kafan wando da Ku akan abunda kukewa fatima duk cikin raha suke magana.</p><p><br /></p><p>Khausar tace kai kai aunty shahrazad abun ma yanxu saniyar ware ake mana" wato kin shigar mawa fatima da nusaiba ko?</p><p><br /></p><p>To gaskiya da sake bazamu yarda ba " shahrazad tace kaina bisa wuya kanwata khausar amin afuwa"" bazan karaba su duka sukayi dariya kasan cewa yadda shahrazad ta marairai ce fuska kamar zatayi kuka.</p><p> </p><p>Tace bara na kawo muku ruwa da lemo, ni'imah tace aunty shahrazad zauna abunki bara naje na dauko bana so ki wahala dayawa, ki kasa bamu labari.</p><p><br /></p><p>Shahrazad tayi dariya kai ni'imah ke kam kina son labari haka" bayan sunsha drinks din su da cake.</p><p><br /></p><p>Sai shahrazad tace to sisters dina yanxu zakuji labarina Wanda nafada cikin ukuban rayuwa aciki saka makon kishiyar mamana.</p><p><br /></p><p>Kamar yadda kuka sani ni sunana shahrazad abdulmaleek " mahaifina Dan garin kano ne a unguwan fage haka mahaifiyata ma yar garin kano ce amms it's suna hoto road ne.</p><p><br /></p><p>Sunan mahaifiyata lubabatu , amms anfi kiranta da hajiya , hajiya lubnah tana yawan shigowa fagge kawo dinki kasan cewa yan fage sun shahara a iya dinki.</p><p><br /></p><p>Anan shagon telanta me suna muntari suka hadu da babana abdulmaleek har suka kulla soyayya mai karfi Wanda ya kaisu gayin aure.</p><p><br /></p><p>Alokacin babana yana aiki a Kaduna " yana da gida a u/kudu anan yake xaune " bayan auren su da wata daya ya dawo da mamata garin Kaduna acikin gdan sa dake u/kudu.</p><p><br /></p><p>Anan suka ci gaba da rayuwar su" har Allah ya albarka cesu da haihuwan da na miji mai suna aminu.</p><p><br /></p><p>Aminu yana da shekara biyar aduniya hajiyata ta sake haihuanwan diya mace , alokacin mahaifina ya ba mawa hajiyata zabin sunan daza asamun.</p><p><br /></p><p>Hajiyata tace tana son asamin shahrazad don ta Dade da son sunan tun kafin tayi aure.</p><p><br /></p><p>Ni shahrazad na tashi cikin so da kulawa " inada shekaru 7 aduniya mahaifina yasake aure " inda ya auri yar'uwarsa me suna indo, Daga azare aka kawota Kaduna.</p><p><br /></p><p>Indo iriin masifaffun matan nan ne" gashi tana nuna mawa hajiyata tafita matsayi agun banana " gata da kishin jaraba ga Neman fada, amma ita hajiyata bata kulata don bata son tashin hankali.</p><p><br /></p><p>Indo tasa min ido bidi bidi tasani aiki Sam bata kaunar taga na zauna lafiya " ga yaranta da ta taho dasu Daga azare, daman ta taba aure acan azaren , auren ya mutu ne shine ta kyalla ido tags banana ta like mai mahaifiyarta da mahaifiyar banana uwa daya uba daya suke" dalilin dayasa kakata taso auren kenan don akara kulla zumunci" nan kuwa basu San wacece indo ba . da sun Santa da basuyi kokarin hada auren ba.</p><p><br /></p><p>Anan Layin mu akwai wani gida daya ke kallon gidan mu " wato gidan tanko soba matarsa daya me suna aunty hauwa , babban Santa sunan sa Khalid said ta biyu amina ana ce mata amingi sannan na ukun shine umar sai auta me suna bilal.</p><p><br /></p><p>Muna mutunci da yan gdan " nakanje gidan don intaya aunty hauwa aiki in amingi batanan matar tana sons.</p><p><br /></p><p>Inada shekara 12 aduniya na shiga secondry school wato j.s.s1 a makarantar government girls scondry school u/rimi , tun ina karamata Khalid ke tsokanana da matarsa ni kuma inajin kunya.</p><p><br /></p><p>TAKU UMMU </p><p>*nusnim*</p><p>[4/15, 10:02 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p> (Labarin sharrin zuciya)</p><p> *BY* *NUSNIM*</p><p> 30 & 35</p><p>Allah sarki hajiya allah ya jikanki da rahma suka ce amin " shahrazad taci gaba da cewa bayan rasuwan hajiyata da wata daya indo ta fara takura min , ta maidani baiwa ga hantara da duka da zagi kullum sai inxauna inta kuka, abinci sai taga daman bani.</p><p><br /></p><p>Wataran sai dai in je gidan su yaya Khalid inci acan , duk nabi na lalace inda nagodewa allah bata hanani zuwa makaranta" ina cika shekara sha biyar da haihuwa samari suka min caa , nikuma duk bani son ko daya, alokacin ne yaya Khalid y danno kai, ranar alhamis ina zaune a kofar dakina , yayi sallama yashigo , lokacin indo batanan " na amsa sallamar sa cikin murmushi sannu da zuwa yaya Khalid.</p><p><br /></p><p>Yauwa matas tayi murmushi tace ya aunty hauwa kwana biyu ban leka na gaishe taba, yace to mayyasa? wallahi karatu ne yasani agaba dayake mun kusa fara exam ayya Allah ubangiji ya taimaka amin.</p><p><br /></p><p>Yaya Khalid yace shahrazad wai yanxu waye saurayin naki ne? tayi murmushi tace ka kosa kaga mijin dazan aura ne" yayi dariya eyye har kin San wani miji" tace kai yaya Khalid wai kana nufin ban girma bane ? Nifa inajin kaina on top fa!! Ya kara kyalkyalewa da dariya woow my shazee anxama big girls haka nake so!! Tace hmmm wai shin kai baza kayi aure bane sai kara tsufa kake" ko ka rasa budurwa ne"" ko dayake baka da kyan da mace zata soka cikin tsokana take wannan maganar.</p><p><br /></p><p>Khalid yace lallai yarinyar nan kece dai baki da kyau tunda gashi kin rasa mashinshine" shiyasa nake son intaimaka maki karki kara tsufa acikin gda duk cikin zolaya yake wannan maganar .</p><p><br /></p><p>Tazaro ido waje tace wa tabdijam akai kasuwa bana so " kai nifa ingaya maka ni irin matan nan ne masu wuyan samu, shazee cute lady</p><p>Shazee Queen of star </p><p>Shazee yar kwalisan yan mata </p><p>Duk Wanda ya ganni sai ya kyasa " kamar kai da kazo yan xunnan nasan kaima Neman shiga kake takarasa maganar cikin yi mishi gwalo .</p><p><br /></p><p>Aiko bata Ankara ba sai taji rankwashi ta marairai ce fuska kamar zatayi kuka" kai yaya khalid da zafi fa Allah sai na rama!! Yace sai dai ki rame " ta juya mashi baya alamun tayi fushi" yace to sorry my kanwa kaina bisa wuya , tace to nayafe maka, yauwa yace shahrazad nazo ne muyi wata magana mai muhimmanci" tace to yayana.</p><p><br /></p><p>Dama ba komai bane illa nazo ne insanar dake son da nake miki Wanda tun kina karamar ki na kamu da sonki, pls shahrazad kibani zuciyar ki , zan zame miki farin ciki arayuwar ki zan zame miki uwa da uba inasha allahu .</p><p><br /></p><p>Please shahrazad karki ce baki sona kamar zaiyi kuka , tunda yafara maganar nan take kallon sa tare da zubda hawaye , saboda taga tsantsan sonta a kwayar idanunshi, kuma tana da tabbacin shi zai riketa amana ya rike maraicinta.</p><p><br /></p><p>Tashare kwallanta tace yaya khalid karka damu na amsa soyayyarka Allah ubangiji yazaba mana mafi alkhairi arayuwar mu baki daya" wani irin sanyi farin ciki ya ziyar ce zuciyar sa " yace wooow am so happy today tanx a lot dear shahrazad ana hubbik tartir " itama tace me too I so much love you khalid.</p><p><br /></p><p>Tun daga wannan lokacin soyayya mai karfi ta kullu tsakanina da yaya khalid Wanda aranar sai mu hadu sau biyar muke iyayin bacci.</p><p><br /></p><p>Nusaiba tace lallai aunty shazee soyayyar Ku ta birgeni "</p><p><br /></p><p>Shahrazad tayi murmushi tace kadan ma kikaji.</p><p><br /></p><p>Ni'ima tace aunty shazee baki fada mana kamannin yaya khalid din ba?</p><p><br /></p><p>Shazee tace eh to yaya khalid baki ne mai irin kyallin nan gashi da dogan hanci da manyan idanuwa sannan kuma shi bawani dogo bane can , kuma ba gajere ba dai dai dai, sannan kuma yanada sajen sa mai kyau fuskarsa dogo ma'abociyar murmushi.</p><p><br /></p><p>Khausar tace woow gsky yaya khalid ya hadu gaskiya ina son inganshi, fatima tace dallah dagajin kyakkyawan mutumi har kina so ki ganshi , yarinya ki maida maitar ki khalid na shahrazad ne, dukan su suka kwashe da dariya .</p><p><br /></p><p>Nusaiba tace gaskya zaku haifo yaya masu kyau ke gaki yar fara mai hanci da beauty point. shi kuma black beauty dashi woow abun yayi , shahrazad dai tana jinsu sai dai tayi murmushi.</p><p><br /></p><p>Taci gaba da cewa lokacin muna tsaka da soyayya yarinyar indo mai suna nafisa ta dawo gidan mu da zama , wulakanci ba Wanda bangani ba wajenta haka indo zata tula min wankin nafisa tace nawanke shi tsaf kuma nafisan bata wuce sa'ata ba , idan na fada mawa babana abunda ake mun sai dai yace mun shahrazad kiyi hakuri kiyi koyi da hajiyarki shikenan abunda yake cemun.</p><p><br /></p><p>Akwai watarana ranar jumma'ah munyi waya da yaya khalid yace mun gashinan zuwa zaiga kwalliyar jumma'ata, aiko natsara kwalliyata mai kyan gaske yazo nafito kofar dakina ina gyara Maya fina " naji nafisa nacewa kayan aro anyima saurayi kwalliya dashi ko kyau bakiyi ba ko kulata banyi ba nafita abuna.</p><p><br /></p><p>Muna cikin hirarmu ta soyayya sai ga nafisa ta fito zata unguwa , har ta wuce mu ta dawo tare da kurawa khalid ido taji aduniyar nan ba Wanda take so sai khalid " shiko kallon ya bashi haushi yace mallama lafiya , tayi saurin zabura tace yi hakuri sannan ta wuce tana tadin zuciya , tabbas nasamu Wanda nake so, tayaya zan sameshi da alama danji da Kaine taja dogon tsaki mtsssssssw , kai ya kamata ingaya mawa mama indo don gaskiya da sake wallihi.</p><p><br /></p><p>Ni nusnim nace tabdi jam , kutara agaba.</p><p>TAKU UMMU RUMAN</p><p>( *NUSNIM* l</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:02 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD*❣</p><p> (Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 25 & 30</p><p>Tun ina karama Khalid ke tsokana na da matarsa " ni kuma nakanji kunyarasa yakan shigo gidan mu suyi hira da hajiyata " kamar abokanai suke da hajiyata.</p><p>Akwai lokacin suna hira da hajiyata atsakar gida yake cewa hajiyan mu niko idan shahrazad ta kara girma zaki aura min ita ? Hajiya tayi dariya tace kai Khalid kace wasa dayawa" yace Allah hajiya da gaske nake ina son shahrazad" Ina son ta kasance matata in Allah ya yarda.</p><p><br /></p><p>Hajiya ta kura mai ido da kyau taga dagaske yake maganar sa. Ta numfasa tace Khalid inaso ace Kaine ka kasance mijin shahrazad " zanyi alfahari da hakan saboda nasan kai waye ne" idan shahrazad itace mafi alkhairi agareka Allah ubangiji ya mallaka maka ita" in ba ita bace Allah ubangiji ya zaba maka mafi alkhairi " Khalid yace allahumma amin.</p><p><br /></p><p>Tudaga lokacin Khalid ya dingajin kunyar hajiyan shahrazad.</p><p><br /></p><p>Akwana atashe ba wuya awajen Allah Allah yayiwa mahaifiyata rasuwa , mutuwan da ta girgizani da sauran mutane, don adaren ranar da hajiyata zata rasu tace shahrazad zoki zauna muyi hira, nace to hajiyata.</p><p><br /></p><p>Na zauna kusa da mahaifiyata " tace shahrazad ina son nan gaba ki zama abun alfahari agun al'umma , ina son kiyi karatu mai zurfi don watarana zai taimakeki " kuma inso da ki rike addu'oi don shine takobin mumini.</p><p><br /></p><p>Idan kin kai munxulin aure ina rokan Allah daya zaba miki miji nagari , Wanda zai iya rikeki " banda ruwan ido irin na sauran mata , nayi saurin rufe ido nace kai hajiya ta " menene kuma na batun aure , nifa ban isa aure ba.</p><p><br /></p><p>Hajiya tayi dariya tace shahrazad kina girma ammah baki San kin girma ba , tace da akauye ne ai da kin dade dayin aure tunda shekarunki sha uku fa , kefa budurwa ce yanxu .</p><p><br /></p><p>Amma bana so kiyi aure yanxu har sai kin gama secondry school dinki in San samu ne , kifara karatu a jami'ah , don yanxu rayuwar ce tazama abunda tazama.</p><p><br /></p><p>Baza ki gane abunda nake nufi ba sai nan gaba , duk randa Allah y daukaka ki Ina son kidinga taimakon Mara su karfi , ki Kasan ce mace mai yawan ibadah da sadaka .</p><p><br /></p><p>Ki rike yayanki sosai shi kadai gare ki , ki rike indo amatsayin mahaifiyar ki , duk abundant zata miki ki dinga hakuri , ko ba komai kun hada jini da'ita.</p><p><br /></p><p>Mahaifin ki ma ki kasan ce mai yi masa biyayya , duk da nasan kinayi ki kara akan Wanda ki keyi .</p><p><br /></p><p>Shahrazad tace hajiyata meyasa yau kike tamin irin wayannan na sihar ? Wlh duk jikina yayi sanyi sai ga kwalla sun fito Daga idanunta.</p><p><br /></p><p>Hajiya tace haba shahrazad menene kuma na kuka , taja hannuna ta daura kan cinyarta ta rungume ni tare da shafa min bayana kamar wata yar yarinya har sai da nayi ajiyar zuciya.</p><p><br /></p><p>Tace my shazee tashi kije ki kwanta Allah y miki albarka, y kare ki Daga sharrin mugayen mutane da aljan, Allah y albarkaci rayuwar ki da zuri'a dayyiba (amin) na kai bakin kofa na juyo na kalli hajiyata tayi min murmushi, nima nayi mata murmushi, Ashe haduwar mu na karshe kenan .</p><p>Kallon mu nakarshe kenan , maganar mu na karshe kenan. </p><p><br /></p><p>Hajiyata tace ga garinku nayi kukan da bantaba yi ba hakama Dan'uwana da babana .</p><p><br /></p><p>Nan shahrazad ta fashe da kuka su fatima kuwa duk fuskar su ta jike da hawaye , nusaiba tace kiyi hakuri aunty shahrazad Allah yafiki son kayan shi, shiyasa ya dauka ni'imah tace hakane.</p><p>Allah sarki hajiya allah ya jikanki da rahmah.</p><p><br /></p><p>*kuyi* *hakuri* da *wannan* *page* *din* </p><p>TAKU UMMU RUMAN</p><p>( *nusnim*)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 35 & 40</p><p>Bayan wuce wan nafisa, Khalid yace my shazee wannan mahaukaciyar daga ina? Hmmm yarinyar mama indo ce mai suna nafisa!! Ta dawo wajen mamanta daza. Khalid yace tabdijam Allah ubangiji yasa karkarta takura miki, afili Shahrazad tace ameen, amma acikin xuciyarta tace na yaushe kuma.</p><p><br /></p><p>Cikin alamar rawan murya Nusaiba tace aunty Shahrazad ina fatan nafisa ba kwace miki yaya Khalid xatayi ba? </p><p><br /></p><p>Shahrazad yayi murmushi tace Nusaiba kenan kedai kici ba da bina cikin labarin nan zakiji komai.</p><p><br /></p><p>Shahrazad tace bayan kwana biyu da haduwata da yaya Khalid , ina zaune ina cin abinci sai naga mutum atsaye akaina, daga kaina nayi inga ko wayene nafisa ce ta rike kwankwaso sai girgije girgije takeyi .</p><p><br /></p><p>Nace nafisa lafiya kika tsaya mun akaina , budan bakinta tace ba lafiya ba, dama Nazo ne in miki kashedi akan ki rabu da Khalid " don shi ba tsaranki bane dani yafi dacewa, in kuma kinki jikinki zai gaya miki , don ba karamin aiki na bane inmiki rashin mutunci eheeen .</p><p><br /></p><p>Haka nabita da kallo daga sama har kasa, cikin zafin nama nace wlh baki isa ki rabani da yaya Khalid ba, kuma inkince zaki shiga tsakanin mu, to wallahi zamu raba abun kunya.</p><p><br /></p><p>Nafisa tace oh haka kika ce? Eh haka nace bismillah shege ka fasa,, haka nafisa take kallona cikin mamaki don bata taba zaton haka nake ba, afusace tabar daki.</p><p><br /></p><p>Sai jin ihunta nayi atsakar gida tana cewa wayyo Allah mama indo Shahrazad ta kwada min tabarya akai, sakamakon jin abunda take fada sai naji gabana ya fadi </p><p><br /></p><p>Don nasan yau kashina yabushe awajen mama indo.</p><p><br /></p><p>Indo ne ta fito da gudu tana nafisa lafiya , nan nafisa ta kora mata karya da gsky, habawa kamar jira takeyi, tafa zunduma ashar tana kwala min kira Shahrazad Shahrazad Shahrazad Shahrazad Dan ubanki kina ina? Yar iskan yarinya mayya kawai.</p><p><br /></p><p>Cikin sauri nakara so inda take har ina tuntube, ban Ankara ba , nafara jin duka ta ko'ina, mama indo da nafisa suka rufeni da duka, gajimun shegiyar yarinya zata kashe mun yata don bakin ciki , haka kawai ki dauki tabarya ki kwala mata akai.</p><p> </p><p>To kema bara kiji inda dadi, nafisa miko min tabaryan in kwala mata taji Inda dadi, ihu nake ina magiya ina basu hakuri amma ina ba Wanda ya tankani, saida suka min lilis sannan suka kyaleni, dakyar nake iya numfashi.</p><p><br /></p><p>Fatima ta fashe da kuka tace wannan wasu irin mugayene haka za suyi kisan kai , amma sai Allah yasaka miki aunty shazee, dukkan su suka goge hawaye, Shahrazad tace Fatima kadan daga cikin muguntan da su mama indo suka min.</p><p><br /></p><p>Tacigaba da cewa.</p><p><br /></p><p>Da kyar na rarrafa nashiga dakina inata kuka ina wayyo Allah na wayyo hajiyata wayyo Khalid dina, yayin da hannuna a kumbure da kyar nake dagashi sakamakon bugamun tabaryan dasu kayi, ina cikin kuka ne baba nah ya dawo yana kirana amma nakasa amsawa"" saboda kukan da ya sarke wuyata, .</p><p><br /></p><p>Dayaji shiru shine ya biyo ni daki, yadaga labulan dakina yana ke Shahrazad lfy kike kuka? Waya tabaki da kyar ta iya fada mashi, ranshi ya bace amma bayadda zaiyi, yace tashi muje agyara miki hannun da alamun targade ne , tace to baba , ya taimaka mata suka fita abakin kofan GDA suka ci karo da Khalid ya fito amota.</p><p><br /></p><p>Ganin masoyiyar shine cikin wani hali yayi saurin kara sowa da gudu duk arude yake , yana baba lafiya.</p><p><br /></p><p>*TAKU* *UMMU* *RUMAN* (nusnim</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 40 & 45</p><p>Yana baba lafiya mai yasa meta haka? baban yace rauni taji shine zan kaita aduba mata hannun nata don kar yayi tsami, Khalid yace baba koma gida kawai zamu kaita nida ameena, wato kanwarsa.</p><p> </p><p>Baba yace to ba damuwa, Khalid ya bude ma Shahrazad mota tashiga, ya dauki wayarsa ya kira amingi , itama cikin sauri tafito, abunka da makwafta banisa tsakanin su!!! Tana kara sowa tashiga mota kusa da Shahrazad, "" cikin damuwa amingi tace shazee waya dake ki haka, Shahrazad ta sunkuyar da kanta kasa tana hawaye.</p><p><br /></p><p>Khalid yana kallon ta , ta madubi yayin da zuciyarshi ke suya , amingi ganin shazee na kuka tayi saurin rungumeta tana lallashinta, sorry my sister stop crying , kukan Shahrazad yakara tsananta.</p><p><br /></p><p>Hankalin Khalid yagama tashi bai San lokacin daya ja burkiba ya tsaya !! Tare da juyo kansa baya , cikin muryanshi mai dadin sauraro, yace Shahrazad Dan Allah waya dake ki? don wannan ba faduwa kikayi ba, alamun duka ne. Na daga rinannun idanuwa ta na kalleshi, zanyi magana, yayi saurin cewa please my d karki boye mun komai kifada mun?</p><p><br /></p><p>Na kura mashi ido ina kallonshi, azuciyata ina fadin shin in fada mashi gaskiya ko kuma sabanin hakan !!! Wata zuciyan tace gara kawai ki fada mashi gaskiya don baki da kamarsa "" daga abbanki sai shi.</p><p><br /></p><p>Amingi tace muna jinki shazee, nan na labarta musu komai , innalillahi yanxu bala'in da nafisa ta kunno dashi kenan, Allah natuba me zanyi da ita, amma ko sai nayi maganinta, sai tasan ta ta baki,"" amma mama indo bata kyauta ba, yana magana yana goge yar kwallan sa.</p><p><br /></p><p>Amingi tayi kwafa tace ba komai Allah na nan shi kadai zaiyi maganin su , kici gaba da hakuri Shahrazad, kuma ki cigaba da mika mawa Allah lamarinki , insha Allah wannan wuyan na Dan wani lokaci ne.</p><p><br /></p><p>Kuma insha Allah ba Wanda ya isa ya rabaki da yaya Khalid, naki ne ke kadai, kinji yar kanwata, nayi murmushi nakalle ta"" nace ba komai aunty amingi ,rayuwace kowa da tashi kaddaran, yauwa yar kanwata shiyasa nake sonki. Allah yabar mu tare amin.</p><p><br /></p><p>Bayan munje wajen mai gyara ta duba hannun tace targade ne , ta gyara mun, amma fa nasha azaba,"" ni'ima tace sannu aunty shazee Allah y saka maki duk Kansu suka ce ameen.</p><p><br /></p><p>Babana yasamu indo yayi mata fada akan abunda tamin , amma indo ta musanta "" sai cewa ma da tayi wai rashin kunya na mata, ba yanda babana zayyi kawai karkade kai kawai yayi, tare da cewa Allah ya shiryeki ya ganar dake gaskiya tace amin.</p><p><br /></p><p>Nafeesa ce zaune shiru tana tunani, tayaya Khalid zai zama mallakin ta "abun duniya duk ya isheta, mama indo ce ta karaso wajenta tana lafiya nafeesa? Kin wani fada kogon tunanin.</p><p><br /></p><p>Budan bakin nafeesan tace ba dole infada tunani ba mama indo, xuciyata tana kokarin fashewa idan ban samu abunda nake soba , mama indo tayi saurin cewa lafiya mekike so haka? Kika kasa sanar dani, fada min yata?</p><p> </p><p>Ko menene sai na mallaka miki shi,komin wuyanshi , nan nafeesa ta washe hakora alamun jin dad.</p><p><br /></p><p>Mama dama ba komai bane illa ina son in mallaki yaya Khalid amatsayin mijina, sai da gaban mama indo ya fadi, tace turkashi, ke nafeesa ki rasa Wanda zakice kina so sai wancan yaron mai taurin rai !!! Kuma kinsan alhaji yasan komai tsakanin Khalid da Shahrazad , don har manya sunshiga magana.</p><p><br /></p><p>Nafeesa ta hade fuska tace ni gaskiya mama sai na aureshi wallahi don inajin idan na rasashi sai zuciyata ta fashe in mutu, mama kawai kice baza ki taimaka mun ba, nan tafashe da kuka.</p><p><br /></p><p>Maman indo ta jawuta jikinta tana lallashi kiyi hakuri na miki alkhawari sai kin auri Khalid kwanan nan, sai dai inba na raye.</p><p><br /></p><p>Shahrazad ta goge hawayenta.</p><p><br /></p><p>Khausar tace lallaima matan nan , yanxu fisabilillahi tsakanin masoya zata Shiga , ko dayake, aibata fada in Allah ya yarda ba, kuma insha allahu baza su sami nasara ba.</p><p><br /></p><p>Ni' ima tace aunty shazee nakosa inji karshen labarin nan, bana so ki rasa Khalid, Shahrazad tace karku damu nakusa.</p><p><br /></p><p>Taci gaba dacewa bayan nadawo gida daga gyaran targade na, na kwanta adakina ina ta tunani , sai ga mama indo ta shigo dakina afusace kamar wacce aka hankado.</p><p><br /></p><p>Nace sannu da gida mama, ta watsa min harara , cikin daga murya tace Shahrazad dama nazo ne inja kunnanki akan yanxu lokacine da yayi zaki rabu da Khalid , gabana ne yayi mummunan faduwa,!!! Taci gaba da cewa, don nafeesa nake son in aura mashi, saboda haka sai ki he gun babanki kice mashi kinfasa auren khalid umurni nabaki ba shawara ba .</p><p><br /></p><p>Cikin kuka Shahrazad tace haba mama indo karkiyi mun haka, kin San kalan soyayyar mu da yaya Khalid tun ina Yar karamata, kuma hajiyata kafin ta rasu , tabashi ni"" wallahi bazan iya rayuwa inbashi ba.</p><p><br /></p><p>To ki mutu mana ni ina ruwana, aini ada dinane ai inkin mutun , tayi ficewar ta, kuka nake ba kakkautawa kozan samu zuciyata tayi sanyi amma ina sai ma zafi danaji tana min.</p><p><br /></p><p>Wayyo Allah, Allah karka bari arabani da yaya Khalid dina.</p><p><br /></p><p>*TAKU* *UMMU* *RUMAN* *NUSNIM*</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 45 & 50</p><p>Allah karka Bari arabani da yaya Khalid, natashi na dauro alwala don gabatar da sallah, nayi addu'oina masu yawa , sannan nashafa na kwanta abuna.</p><p><br /></p><p>Cikin bacci ne naji wayata tana ringing , dauka nayi ganin sunan danayi ajikin wayan , yasa nayi murmushi my D wato yaya Khalid, nasa wayan akunne na tare dafadin </p><p><br /></p><p>Assalamu alaikum</p><p>Adayan bangaren aka ansa min </p><p><br /></p><p>Wa'alaikumus salam , gimbiyar kamshi dafatan kina lafiya , ya karfin jiki?</p><p><br /></p><p>Lafiya lau full option!! Dafatan kamai kananan lafiya?</p><p><br /></p><p>Ina lafiya kamar yadda kike lafiya, amma inba kya lafiya to nima bana lafiya.</p><p><br /></p><p>Haba dai yaya nah ka kwantar da hankalin ka, lafiyata kalau, sai dai kawai zuciyata tana cike da begenka da soyayyar ka!! Fatana mukasan ce a inuwa daya in Allah ya yarda, ina tsoron watarana in rasaka my D.</p><p><br /></p><p>Shahrazad insha allahu zamu kasan ce a inuwa daya tare da farin ciki mai daurewa , fatana ki rike mun alkhawari !!!! Ina sonki Shahrazad ina kaunar ki Shahrazad "" in ina tare dake inajin wani shauqi, Shahrazad kina Jan ragamar soyayyata.</p><p><br /></p><p>Kai yaya nah dadina dakai ka iya lafuzza masu sanyaya zuciya.</p><p><br /></p><p> Shahrazad ikon Allah, karki tabaji a ranki wai shazee ba abin kaunar Khalid bace.</p><p><br /></p><p>Khalid na son shazee 4rever & ever, Khalid naki ne, shazee dukiya ce Dan ko kinfi kudi, gida mota da komai ma, Khalid yace Shahrazad rayuwa CE, taka a sannu taka shazee ga shazee Yar Fulani.</p><p><br /></p><p>Woow yayana duk wannan kalaman ni kadai gaskiya kasani farin cikin Mara misultuwa ina sonka yayana, nima ina sonki babynah, dukun mu muka kwashe da dariya.</p><p><br /></p><p>Nusaiba tace woow aunty shazee gaskiya kuna wuta fa, Fatima tace sai kace masoyan cikin littafin (kutausaya min)na nusnim wato rumana da king laisu.</p><p><br /></p><p>Gaskiya kun burgemu,, Shahrazad sai dariya take, kurufa min asiri ni na'isa mu iya irin soyayyan *rumana* da *king* *laisu*, khausar tace kai aunty kunmafi haka.</p><p><br /></p><p>Shahrazad tayi murmushi kudai kuci gaba da .</p><p><br /></p><p>Washe gari da safe ina zaune adaki sai ga mama indo ta fada dakina, tare da cewa Shahrazad ya maganar da mukayi dake jiya? Kifa ganin ina binki ta ruwan sanyi don ba fin karfi ne kikayi ba, "" don idan naga dama ayau zan iya daura mawa nafeesa aure da Khalid kuma ya zaunu.</p><p><br /></p><p>Kin fada mawa baban Baku abunda na fada maki jiya? Na sunkuyar da kaina kasa nace a'a, to me kike jira? Ba komai, mama kiyi hakuri wlh bazan iya tunkaran baba da wannan zancen ba.</p><p><br /></p><p>Aiko ban Ankara mama indo ta kai mun duka abayana, ja'irin yarinyar insaki Abu kice mun baza ki iya ba to wlh ba a haifi Wanda zaimun haka !! Ke har kin isa , tashi kifi ta kimun aikina.</p><p><br /></p><p>Mama kiyi hakuri don Allah , hakurin ubanki , har tsakar gida ta biyoni tana duka da hauri , tana cikin dukana sai ga kawar ta me suna ma'u, tashigo cikin sallama, tana indo lafiya kike ta masifa? Tundaga waje nake jiyo muryar ki .</p><p> </p><p>Hmm ma'u ba lafiya ba, wai harni zansa Shahrazad Abu tace mun baza ta'iya ba,!! Ma'u tace shin me kika sata ? Nan indo ta labarta mata komai.</p><p><br /></p><p>Ma'u tace ashsha indo Ashe baki da wayau ban sani ba, akwai hanya mafi sauki daza ki raba yaran nan, batare da kinsha wahala ba.</p><p><br /></p><p>Nayi saurin dago kai don inji wani hanya ne ma'u take son fada mawa indo.</p><p><br /></p><p>Indo tace ma'u bangane me kike nufi ba?</p><p><br /></p><p>Ma'u tayi gyaran murya tace kixo muje wajen wani malami dake saman tudu, ya iya aiki sosai shan yanxu maganin yanxu, batare da kanki yayi ciwo ba.</p><p><br /></p><p>Ai ban San lokacin Dana saki wani uban ihu ba ganin za arabani da masoyina, nayi saurin kama kafafun mama indo ina mama ki tainakeni ki mun rai, karki rabani dashi Dan Allah , komai kika ce in miki zan miki amma karki rabani dashi .</p><p><br /></p><p>Indo ta hanka data gefe Dalla mallama yi mun shiru!! Wallahi kinji na rantse sai na ba mawa yata abunda take so , saboda haka kisa ka aranki, sai dai inba indo ba, kuma ki wuce ki karasa min aikina.</p><p><br /></p><p>Jikina ba kwari ga zazzabi dake addabata ga yunwa, nake jibgan aiki ko su tausayamin !! Amma ina , ina aiki INA waswasi , shin ingaya mawa babana da yaya Khalid abunda ke faruwa , ko kuma infada mawa Khalid kawai mugudu muyi auren mu awani wajen, wani bangare na zuciyata ke fada mun haka, !! Gyangyadi ne naji tana diba na!! Har na jingina kusa da bangon kicin dinmu nafara yin bacci.</p><p><br /></p><p>Cikin bacci na naga hajiyata tazo min tana cewa Shahrazad karki biye, mawa *Sharrin* *zuciya* ki aikata abunda zaki dawo kina da kin sani , mafita kawai kici gaba da addu'a, ina cikin hakane naji an watsa min ruwa"" mama indo ce , eyye wato in saki aiki kixo kina bacci, toh na baki nanda minti talatin kingama, muryata na rawa nace to mama.</p><p><br /></p><p> Da daddare ina zaune Khalid ya kirani awaya yace mun yana kofar gdan mu, nace mishi to gani nan zuwa.</p><p><br /></p><p>Mintina kadan na fita wajen shi, nayi sallama ya amsa min, Khalid yace shazee ya naganki wani iri , alamun kina cikin damuwa , nayi saurin kakalo murmushi, tace yaya nah mugaisa tukun na , inayi ni, yasu aunty Hauwa da amingi, yace lafiyan su kalau sunce agaishe ki da jiki.</p><p><br /></p><p>Ina amsawa.</p><p><br /></p><p> Tace yaya Khalid Dan Allah mugudu muje muyi aure awani wajen , Khalid yayi saurin cewa lafiya kike kuwa shazee? haba tayaya zaki ce mugudu bayan iyayen mu sunsan muna son junan mu, kuma zasu aurar damu.</p><p><br /></p><p>To menene kuma na guduwa, nace Khalid baza ka gane bane, nan nafayya ce mishi komai.</p><p><br /></p><p>Khalid yace innalillahi wa'inna ilaihiraji'un, Allah kayi mana tsari da wayan nan mutanan, ta Allah ba tasu ba, !! Shahrazad mu dukufa wajen Neman kariya amma baza mu biyewa sharrin zuciya mugudu ba.</p><p><br /></p><p>Koda mun gudu, idan Allah yayi asiri zai kamamu to tabbas sai ya kamamu ,koda birnin sin mukaje, kinga ko guduwa baida amfani,, !!! Addu'a itace maganin.</p><p> </p><p>Na sauke wani nannauyan numfashi nace hakane, amma ina tsora fa my D,!!! Karkiji tsoro baby nah, to yayana.</p><p> </p><p>To danyi dariya mana, nayi murmushi, yauwa ko kefa .</p><p><br /></p><p>Shahrazad rayuwa ta koya mana cewa so ba qunshe yake da kallon juna ba amma muna kallon bangare daya atare lokaci guda, ina sonki shazee , me too yayana.</p><p><br /></p><p>TAKU *UMMU* *RUMAN* (nusnim)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 50 & 55</p><p>Nagode shazee kici gaba da addu'a, to yayana, to ya kamata ki wuce gida dare nayi kar baba yayi fada toh, yayana sai da safe!!! Yauwa yan matana sai da safe.</p><p><br /></p><p>Washe gari ma'u,takamo hanyar zuwa wajen indo akan maganar da sukayi nazuwa wajen mallam nakan tudu, nafeesa na zaune kusa da indo tana bata labarin kalan soyayyar da takewa Khalid!!! Indo tace karki damu yanxu zamuje gun mallam.</p><p><br /></p><p>Kai amma naji dadi mama indo shiyasa nake sonki, sallamar ma'u ce Takatse musu hirar su !!! Indo tace a'a ma'u har kin karaso ? Eh wlh nakara so, dafatan dai ashirye kike, ashirye naki.</p><p><br /></p><p>To tashi maza muje , sun fito kenan suka ci karo da ni, saida gabana ya fadi tuni nafara karanto addu'a, indo ce tace ke lafiyar ki kike kallon mu?</p><p><br /></p><p>Shin me ma ya kawo ki kofar daki dana , cikin rawar murya nake magana dama omon wanke wanke nazo ki bani, indo tace nafeesa ki ba mawa wannan yarinyar omo, to mama, sannan suka fita.</p><p><br /></p><p>Nafeesa ta jehon omon ajikina tare da cewa mai house girl gashi, karki kara cemun house girl don ni ba sa'ar ki bace!!! Mtsssw ke kika sani , Khalid dai yau sai yazama nawa, sai dai a hadiye zuciya bakin , karya kike ya rinya sai dai ke ki mutu ba niba,"" kuma duk abunda kuka shuka sai kun girba, ta Allah ba taku ba, mtssw nayi wucewa na ina Dan kwalla.</p><p><br /></p><p>Su ma'u sunje gun mallam, mallam yace me kuke so ayiwa yarinyar , so kuke akasheta, Ko kuma so kuke a haukatata, ko amata kurciya tabar gida, ko kuma arabata da yaron yace yafasa aurenta?</p><p><br /></p><p>Mama indo tace so nake yaron da kanshi yace yafasa aurenta, yadda abun zaifi mata ciwo ta hadiye zuciya ta mutu.</p><p><br /></p><p>Ni'ima tace kaji muguwa azzaluma kawai, wato idan yaya Khalid ya furta miki bai sonki abun zai fi miki ciwo , sai kiji gara ki hadiye zuciya ki mutu, Nusaiba tace kin San irin wannan yafi bakin cikin, saboda masoyin da kake so tsakani da Allah kabashi yarda da amana , sannan daga baya yazo yace maka baya Sonka kuma baki da baki, ai sai kinji kamar ki hadiye zuciya ki mutu"" shiyasa mama indo tazabar mawa aunty shazee haka.</p><p><br /></p><p>Kai Allah ya wadaran naka ya lalace khausar tace haka ameen dai.</p><p><br /></p><p>Aunty shazee muna jinki ci gaba toh.</p><p><br /></p><p> Hmm ingaya muka mallam ya ba mawa mama indo magani ta zoba azauren gdan mu inda yaya Khalid ke zama, ki tabbatar kinsa to mallam mun gode, cikin murna indo ta dawo gda , nafeesa ta tare ta da sannu da zuwa mama dafatan andmashi </p><p><br /></p><p>Mama indo ta fadada murmushi eh andace, yanzu kece zaki ka rasa sauran aikin, toh mama ni me zanyi cikin zaro idanu, ke dallah ba wani Abu bane duk kikabi kika tsorata, kinga wannan garin maganin zakije zaure ne, ki barbada a inda Khalid ke zama shikenan"" sannan nafeesa ta sauke ajiyar zuciya tare da cewa yanxu naji hankalina ya kwanta .</p><p><br /></p><p>Da nayi zaton wani abune tunda wannan ne ai Abu mai sauki ne, aiko anjima kadan zanje in xuba mashi, shikenan nakusan mallakar. Khalid , duk Kansu sukayi shewa.</p><p><br /></p><p>Zaune nake adakina na idar da sallah azahar , na dauki alqur'anina ina karanta wa, bani nagama karutun ba sai da aka kira sallah la'asar , sannan nayi sallah na, nacigaba da addu'oina.</p><p><br /></p><p>Da yamma nafeesa ce ta fito cikin sanda alamun kar a ganta , har ta isa zauren , tana zuwa ta rufe kofan zauren ta barbada maganin yadda baza agane ba , bayan ta gama ta fito,"".</p><p><br /></p><p>Ina cikin addu'a wayata tayi kara na dauka nayi sallama yayana y kake ya gajiyan aiki, yace lafiya lau, anjima kadan ina nan zuwa to angona sai kazu , please ka Dan ta homin da lemon tsami, kedai baza ki bar shan lemon tsamin nan ba, kin fi son kina tafiya akayi iska ya gudun min dake ko, haba dai yaya Khalid tayaya iska zai tafi dani? </p><p><br /></p><p>Aiko to inbaki rage shan lemun tsamin nan ba wataran iska zai tafi dake, bakisan yanasa rama ba ko, "" to zanrage my"" dukkan mu mukai dariya, yanxu sai nazo , to Allah ya kawo mun kai lafiya ameen.</p><p><br /></p><p>TAKU UMMU RUMAN (nusnim)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 55 & 60 </p><p>Natashi naje zan debi ruwa arijiya inyi wanka sai ga mama indo, tace a'a Shahrazad me zakiyi da ruwan sanyi yanxu da yamman nan, wlh wanka zanyi, to ga Dan ruwan zafi can atukunya sai ki kashe sanyi dashi, don kin San garin akwai sanyi"" baki nasake cikin mama ki nake kallonta tare da cewa to mama sannan ta wuce.</p><p><br /></p><p>A zuciyata ko sai tunani naka anya wannan mama indo ce " daya bangaren cikin zuciyata yace itace, watakila ta canxa haline? Kawai nakada kaina naje na diba ruwan nayi wanka na.</p><p><br /></p><p>Bayan nafito na daura alwalan magrib nashige dakina, nayi shafe shafe na"" na tsantsara kwalliya ta mai kyau na dauko duguwar rigata kalan blue ba kara min kyau tamun ba Dan kwalina ban daura ba" saboda hijabi zansa nayi sallah yanxu!!! Bayan na idar da sallah ta na karanto addu'oi na Dana saba, nazauna gaban madubi don in daura Dan kwalina.</p><p><br /></p><p>Ta jikin madubi na "" nake hango gaban kofan daki na sai naga kamar ana lekena , nayi sauri na tashi don duba waye ne, bude labulan dazanyi sai naga nafeesa ce," ganina duk tabi ta daburce, alamun Mara gaskiya , don bataji karan tahowa taba da ta gudu, nace nafeesa lafiya me kike nema?</p><p><br /></p><p>Cikin muryan marasa gaskiya tafara cewa dama nazo ne in Dan ara silifas dinki zanshiga bayi ne banga nawa bane, cikin rashin yarda da ita nace mata ta dauka!!! Sannan najuya baciga ba da daurina kamar wata amarya, ni kaina nasan nayi kyau ina kuma ga sahibin nawa idan ya gani!!! Nakara sakin murmushi .</p><p><br /></p><p>Nafeesa kuwa bayan barinta dakina ta wuce sashen su, mama indo na ganin ta , tace nafeesa ya me Shahrazad takeyi , tana daki tana shiryawa da alamu Khalid yana hanyar zuwa, yauwa autana!! Farin cikin ki ya kusan cika, aikuwa mama wayyo dadi kasheni.</p><p><br /></p><p>Bayan nagama daurin dankwalina nafeshe jikina da turare , ina cikin hakane naji karan text yashigo wayata dubawan dazanyi, naga yaya Khalid ne"" ya rubata min,</p><p><br /></p><p>Babynah kiyi hakuri bazan samu zuwa ba, nayi bakine , tuni naji raina ya bace" kamar zanyi kuka, cikin gungunai nafara magana di kai!! Yanxu fisabilillahi yaya Khalid saida natsara kwalliya mai kyau saboda, sai kace mun baza kazoba, ni wlh nayi fushi ma""" </p><p><br /></p><p>Fatima tace kash meyasa yaya Khalid zai miki haka duk wannan kwalliya da kika tsara don shi, yaci aci ace ko lekowa ne yayi agurguje.</p><p><br /></p><p>Nusaiba tace ai rashin zuwan nashi shine mafi alkhairi , kun mata ansaka mashi magani awajen zaman sa, kunga ko idan yazo yazauna awajen , shikenan aunty shazee tayi bankwana dashi, dukkan su suka ce eh kuma hakane fa, Shahrazad dai nata kallon su, batace komai ba"" sukace muna jinki aunty shazee.</p><p><br /></p><p>Murya can kasa sai naji ance karkiyi fushi my D wasa nake miki gani a kofar gdan Ku, tuni na zabura nafara dube dube don inji ta ina nake jin muryan ya Khalid , Ashe nadan na kiranshi ban lura ba , yaji lokacin dana ke magana, yace Ashe ma bakisan kin kirani ba saboda masifa, na kalli wayar dake hannuna!!! Nace haba habibi tunda kamin haka, to nima bazan fito ba, nakashe wayata.</p><p><br /></p><p>Yana ta kirana naki dauka sai dariyar mugunta nake, can kuma naji karan shigowan tex ya Khalid ne yaturo min tare da cewa</p><p><br /></p><p>Allah sarki shazee!!! Kukanki na samun damuwa "" damuwar ki tana bani takaici"" faran cikin ki shi nake so""" shazee tafi kudi, gida, mota, """ Shahrazad duniya ce , I love you.</p><p><br /></p><p>Cikin jin dadi na rungume wayata akirjina ina murmushi, na dauki gyalena na fita banganshi azauran mu ba, nafita waje jikin motarshi naganshi ya kwantar da kanshi Asama.</p><p><br /></p><p>Cikin sallama na karasa yayi saurin waiwayo wa yana ganina na sakar mashi wani irin murmushi tare da kanne ido daya, shima ya maida min da martani.</p><p><br /></p><p>Nakara masa da gwalo tare da cewa nima na rama ai, yace aikuwa kin rama, ido ya Bini dashi kamar zai hadiye ne, nace wannan kallon fa ai saka sa infadi kasa, yasaki murmushi"" kinga kuwa sai intaro ki, nasan zamu bada ma'ana, "" na fashe da dariya tace kai yayana ai sai kajira ranar auren ba yanxu "" sai kasa mutane su mana fassara kuma hakane fa.</p><p><br /></p><p>Shahrazad gaskiya kinyi masifar kyau , uhmn nida banda zolaya , Allah ba zolaya bane da gaske kinyi kyau, kai Allah ka mallaka min wannan Yar babyn nawa amatsayin matata, inhakan tafaru , inaga nafi kowani namiji sa'a aduniya,!! Nace ko yace allah.</p><p><br /></p><p>Na kalleshi nace kaima ya Khalid duk macen da ta sameka tagama morewa ado daukan wanka iya magana , kula da mace , duk kai kadai, nima nayi sa'a yayana, na'am shazee nah</p><p><br /></p><p>You have touched my heart and filled my world with so much love , honey I love u more and more with each passing day.</p><p><br /></p><p>Thank you my D I so much love u, dukkan mu mukayi murmushi, nafeesa dake lekan mu sai tsaki take sakewa alamun bata ji dadin tsaya warmu anan ba .</p><p><br /></p><p>Yayana mushiga zaure mana ko anan yau zamuyi tadin ne, aikuwa sai naji ban San karasawa ciki aiko dole mushiga"" bakaga mutane duk sun zubo mana ido ba,"" to mushiga ina gaba yana bina abaya.</p><p><br /></p><p>Nafisa naganin zamu shigo taruga cikin gida da gudu tana murna.</p><p><br /></p><p>*TAKU* *UMMU* *RUMAN* nusnim</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 65 & 70</p><p>Bayan tafiyar yaya Khalid da kwana uku, mama indo ta kirani tace Shahrazad nikam kwana biyu shiru bana ganin Khalid, ko lafiya?</p><p><br /></p><p>Na danyi shiru na Dan wani lokaci ina tunanin wani kalan amsa zan fada mata, sai naji bangaren zuciyata tana cewa , kawai kice mata kema baki sani kuma inkinkira wayarshi bata Shiga" ilai ko haka na fada mawa mama indo.</p><p><br /></p><p>Cikin nuna alamun damuwa mama indo tace assha ,shine kuma kike zaune maimakon ki leka gdan su kiji ko lafiya, maza dauko Maya finki kishiga gdan"" nace to mama!! Na juya dakina ina tafiya ina sake sake da alama mama indo akwai abunda suke kullawa"" amma ta Allah ba tasu ba.</p><p><br /></p><p>Nashiga dakina na dauko mayafina nafito nace mama na wuce, tace to ki gaida Hauwa""" to zasuji.</p><p><br /></p><p>Nafito kofar GDA ina Dan murmushi na, nace kawai bara nashiga gdan su ummi kawata mudanyi hira"" cikin GDA kuwa su mama indo ne da nafeesa suna ta Hiran su najin dadi, nafeesa tace mama gsky aikinmu yayi, kai nakusa zama amarya, aikuwa dai autana, yanxu dai bara mujira dawowanta" muji mai zata CE!!! Aikuwa.</p><p><br /></p><p>Tunda nashiga gdan su ummi nakira yayana mukaita hira dashi, nafada mai abunda ke faruwa, yayi dariya"" yace shazee akwai abunda mutanan suke kullawa Wanda bamu sani ba," kamar sunyi niyan raba mu ne, shine suke tunanin hakar su ta cimma, nanko basu San , kamar kara manna mu akayi ba, aikuwa dai habibi </p><p><br /></p><p>Yanxu dai inkin koma gida kiyi alamun kamar kinyi kuka kice kinje wajena na nuna ban sanki ba ," na Kore ki na hantare ki!! Muji kuma mai zasu ce "" kai yaya nah ka iya kawo idea.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>To sai anjima in munyi waya to baby nah, bayan mungama waya ne sai nayiwa ummi sallama nace mata na wuce gida ,"" kafin infita daga gidan saida nashafa mawa idona ruwa alamun nayi kuka,"".</p><p><br /></p><p>Da sallama nashiga zauren mu ina gunjin mama indo ta tashi tana lafiya Shahrazad kike kuka me Khalid ya miki, nan nakwashe yadda mukayi da Khalid din na fada mata"" tace kai amma Dan Adam butulu ne, yanxu abunda zaisaka maki dashi kenan, amma ba komai , sai naje har gidan nasu inji dalili"" nayi saurin cewa a'a mama ba sai kinje ba, ki kyalesa da halinsa"" ni barsa da Allah .</p><p><br /></p><p>Mama indo tace ba komai Allah zai saka maki , Shiga daki ki kwanta abinki"" nafeesa dake lekan mun kamar ta zura aguje don murna, bayan na shige daki na fada kan gadona ina dariya ba kakkautawa.</p><p><br /></p><p>Yayin da mama indo da nafeesa anacan ana murna.</p><p><br /></p><p>Lokaci sai tafiya yake yau satin Khalid dina daya a abuja, " mama indo taje ta samu kawarta ma'u tace," ma'u aikin mallah na kan tudu yayi fa, nan ta fayyace mata komai , ma'u tace kinga ai na fada, yanxu kuma menene kuma agaba?</p><p><br /></p><p>Yanxu abunda zanyi zansa nafeesa taje gdan su don tabishi" ko Allah zaisa akara dacewa"to hakan ma yayi.</p><p><br /></p><p>Bayan mama indo ta dawo gida take fada mawa nafeesa ga abunda zatayi, nan nafeesa aka hawan rawan jiki, taje tayi wanka aka tsantsara kwalliya, tace mama nayi kyau kuwa? Eh autana kinyi kyau, nagode mama sai na dawo , mama indo"" tace to sai kin dawo.</p><p><br /></p><p>Duk abunda sukeyi a kunne na , bayan fitan tane na kwashe da dariya, shirmen banxa "" iska na wahalar da mai kaya.</p><p><br /></p><p>Nafeesa na zuwa kofar gidan su Khalid taci karo da kanin Khalid , tace yauwa Umar Dan Allah kadan min magana da yaya Khalid mana" yace ai baya nan yayi tafiya amma ya kusan dawowa ,tace to nagode Allah ya dawo dashi lafiya"" amin.</p><p><br /></p><p>Haka ta dawo gida duk ranta abace, maman ta na ganin ta tace nafeesa lafiya mama wai Ashe yayi tafiya, amma yakusan dawowa, !! To shine kika bi kika tada hankalin ki"" kika sani ko ya tafine don bai son ganin Shahrazad, sannan nafeesa ta saki ranta , yauwa kokefa, yanxu inxai dawo sai ki mashi girki mai dadi, kafin nan na koma gurin mallam na kan tudu na karbo miki maganin mallaka kamar yadda muka karbo Wanda ya zauna akai rannan, yauwa mamanah.</p><p><br /></p><p>Karaf akunne na, hankali na ya tashi, na dawo dakina da gudu, na fashe da kuka"" nace dama abunda mama indo ta shirya min kenan, ai da gudu na tashi naje zauren mu wajen da muke zama!!! Ko zanga alamun maganin, Ina ta dubawa bangani ba kamar ance in waiwayau.</p><p><br /></p><p>TAKU *Ummu* *Ruman* (nusnim)</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p> *BY* *NUSNIM*</p><p> 70 & 75</p><p>Ai da gudu na tashi naje zauren mu wajen da muke zama ko zanga alaman magani , ina ta dubawa ban gani ba, kamar ance in juyo sai na hango wani takarda alungun wajen!! Na karasa nasa hannu tare da bismilla na dauka magani ne, amma kadan ne aciki, da alamun shine maganin da aka zuba mawa yaya Khalid!!! Na kare fashe wa da kuka, ina kiran sunayen Allah da Neman tsari.</p><p><br /></p><p>A haka har na koma dakina inata kuka, daga sama naji muryan mahaifini yana Shahrazad Shahrazad Shahrazad kina ina , nayi saurin goge hawayena tare da fitowa , nace baba gani, yauwa dama zan fada miki ne gobe dangin mahaifiyar ki zasu zo, za akawo kayan sa ranar ki.</p><p><br /></p><p>Don jiya Khalid yasanar mawa baban sa yana so kayi bikin Ku da wuri, saboda nanda wata biyar zai koma abuja da zama, saboda aikinsa.</p><p><br /></p><p>Karaf akunnan mama indo cikin kaduwa tace alhaji me kace"" ya kara maimai ta mata,,, tace alhaji ai wannan maganar banxa ne, bayan yaron nan yaciwa Shahrazad mutunci, yace baya sonta baya kaunar ganin ta, nan yarinyan nan ta dawo tana kuka,, tace ta hakura dashi har abada.</p><p><br /></p><p>Sannan kuma yanxu zaka zomana da wani maganar da baida ma'ana, baba ne yace indo kinsan abunda kike fada kuwa, anya kina cikin hayyacinki kuwa? Kwarai da gaske ina cikin hayyacina.</p><p><br /></p><p>Ai ga Shahrazad din agaban ka, katambayeta kaji gaskiyar maganar "" tunda baka yarda da nawa ba,!!; baba ya juya ya kalle ni, alokacin fuskata duk tagama jikewa da hawaye. Kuma raina abace jin maganganun mama indo.</p><p><br /></p><p>Budan bakina nace abba nah duk maganar da mama indo ta fada maka, duk shiri nane, nayishi akan wani dalili.</p><p><br /></p><p>Cikin zabura mama indo tace mun ke Shahrazad me kike nufi da shirin kine "" karki cemun , duk abunda Khalid ya miki karya ne, babane yace shin lafiyarku menene kuke haka Ku fahimtar dani yadda zangane.</p><p><br /></p><p>Nace baba bara na maka bayani, nan na kwashe komai na fada mashi, amma ban fada mashi mama indo taje gun mallami ba, na rufa mata asiri awannan"" haka baba yayi salati yayi sallallami yace!!! Yanxu indo abunda kikayi yadace kenan, saboda son zuciya da kuma sharrin zuciya zaki raba Shahrazad da Khalid """ sannan kuma ki hada yarki nafeesa da Khalid din.</p><p><br /></p><p>Fisabilillahi atunaninki kin kyauta kenan, amatsayin ki na uwa"" amma kin bani kunya ,, koba ke kika haifi Shahrazad ba ,amma jinin kice ita,"" abunda zaki so yarki dashi yakamata itama kiso ta dashi!!! Tun ba yau ba kike azabtar da marainiyar yarinyannan, inke akama yarki haka zakiji dadi,"" to ina jan kunnan ki akan kishiga hankalinki ki nutsu"" inba haka kuma duk abunda ya biyo baya kekika sani,, ya juya abunsa ya tafi.</p><p><br /></p><p>Bayan tafiyar sa cikin kunan rai mama indo tace wato ina miki kallon shiru shiru Ashe ke babbar muna fika CE"" to ki kwan da sani muddin in ina raye baza ki taba auren Khalid ba,, nafeesa ce zata aureshi , duk Wanda yaja dani kamar yaja da mutuwar sane, tana gama fadar haka, ta kama hanya ta wuce,, yayin da ni kuma azuciyata ta sai cewa nake, ta Allah ba taki ba.</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu</p><p><br /></p><p>Yan'uwan mahaifiyata zun xo, yan gdan su yaya khalid sun kawo kayan sa rana, da kudin gaisuwa , inda suke neman alfarman bada kudin sadaki atare kawai,, kuma sun amince anbada kudin sadaki dubu hamsin.</p><p><br /></p><p>Cikin gida kuwa wata kanwar hajiyata tace niko Shahrazad , Ashe haka kike zama da wannan indon,, nace inna me kika gani, hmm daxu ne naje bayi ina dawowa naci karo da indo, ta wani rike kugu sai girgiza takeyi, tana habaice habaice, har tana fadin ayi dai agama Khalid dai na yatace nafeesa, idan ba abar mana shi Dan Allah ba, za abashshi don wuya, shine abun ya daure mun kai, da alamun akwai Yar tsama ciki,, shiyasa nace bara na tambaye ki, don ko sai antashi tsaye da Neman kariya wajen ubangiji!! Hakane inna.</p><p><br /></p><p>Nan na bayyanawa innatah, yadda muke da mama indo, haka itama ta dinga salati da sallallami, wato Shahrazad shine baza ki kira waya ki fada mun ba, da sai ataimaka maki da wani Abu, don naga wannan matar bata da karki ko kadan don zata iyayin komai.</p><p><br /></p><p>Muna cikin magana ne, autan su hajiyata yashigo Wanda muke ce mashi kawu mamudu</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 75 & 80</p><p>Shahrazad tace karku damu kuci gaba da bina.</p><p><br /></p><p>A kwana atashi ba wuya lokacin bikina sai kara matsowa ya keyi, yan uwa sai shiri sukeyi .</p><p><br /></p><p>Yayinda nafeesa kuma abun duniya duk ya dame ta, kamar zatayi hauka "" ta hana kanta fita ko ina tana daki in banda kuka ba abunda takeyi !!! Mahaifiyar tata tayi lallashi har ta gaji. </p><p><br /></p><p>Mama indo ta kasa zama kullum sai aikin fitan nema mawa yarta farin ciki, amma ina ba sa'a.</p><p><br /></p><p>Yau saura wata daya aurena, innata tazo daukana ta tafi dani,, don za amin gyaran amare.</p><p><br /></p><p>Da kyar babana ya barni, ana gobe za mu tafi, Khalid yazo gidan mu da daddare, ya kirani awaya yace gashi nan awaje nace to yayana.</p><p><br /></p><p>Na Dan gyara fuskata na fita, da sallama ta na isa wajen sa"" yaya nah y kake dafatan kana lafiya,, amaryata ina lafiya" ya shirye shiryen tafiya !! Gashi nan sai yinta muke .</p><p><br /></p><p>To madallah yauwa ga kayan nan Wanda zaki bada dinkin fitan biki, yauwa kaga dasu ma zan tafi, dama kawu babayo yace inkawo zai dinka min, toh shikenan ma.</p><p><br /></p><p>Khalid yace Shahrazad nace na'am yaya Khalid yanxu tafiya zakiyi ki barni !!! Kai yaya nah, bafa dadewa zanyi ba, zafa agyara maka nine, baka son ranar bikin in kara kyau ne,, kai ina so mana,, aidanafi kowa murna ganin amaryata ta hadu, nayi dariya "" to ai nasan sai kafini haduwa yaya nah,, hmm wlh Shahrazad kin iya zolaya,,, ni na isa ki hada kaina da ke!!! Kinsan nesa ba kusa ba, kin fini kyau ,, ke ingaya miki duk fadin unguwan rimin nan banga wacce tafiki kyauba.</p><p><br /></p><p>Wayyo Allah yayana kadai na sa kaina ya kato , eh mana gaskiya na fada my lady to godiya nake my prince.</p><p><br /></p><p>Khalid yace ga 20,000 kudin dinkin ki, wannan kuma 30,000 ne kiyi tsaraba dashi sai dai ba yawa, kai yayana wannan kudin sunyi yawa gaskiya ka rage.</p><p><br /></p><p>Haba shazee ina yawa anan ni awajena ma sunyi kadan wlh, don kinfi komai awajena, to yaya Khalid nagode Allah ubangiji ya kara budi ya dauka ka ka duniya da lahira ameen kanwata.</p><p><br /></p><p>Allah ubangiji ya kaiku lfy ya dawo min dake lafiya, ameen, toh bara nashiga ciki, OK Allah ya tashemu lafiya.</p><p><br /></p><p>Washe gari muka kama hanyar kano, ba karamin murna nayi ba da ganin yan'uwana , nashiga cikin dangi, duk inda nabi ace ai Yar gidan marigayi yace, sai da muka kara kokawa na rashin hajiyata,, nasha gyara ba kadan ba, har wani canxawa nayi.</p><p><br /></p><p>Gida kuwa mama indo sun rasa ya zasuyi duk hankalin su ya tashi, gashi ta sa babana agaba wai sai dai a hada auren mu nida nafeesa,, baba yace indai tasamu miji tsab kuwa zan hadasu aure ita da Shahrazad"" alhaji baka gane nufina ba?</p><p><br /></p><p>Toh me kike nufi,, ina nufin a hadasu su biyun a aurawa Khalid din tunda ita nafeesan tana son sa, haka baba yasake baki yana kallon ta cikin mamaki.</p><p><br /></p><p>Shin wai indo yaushe kika fara haka ne ban sani ba,, Khalid din ne yace miki yana son nafeesa ko kuwa sabagen iskanci ne kika zo min dashi yaja tsaki mtssssw yayi wuce Warsa.</p><p><br /></p><p>Indo kamar tasa hannu aka tace wayyo.</p><p><br /></p><p>Ina kwance kan gadon kakana na dauki wayata nakira angona muna hiran soyayyar mu, yace shazee nah wai yaushe zaki dawo ne "" nayi missing dinki fa, kinga saura sati daya biki fa, kar ka damu my one jibi zamu dawo.</p><p> </p><p>OK Allah ya kawo min ke lafiya amin,, my shazee kinfi kudi, mota , gida, ke rayuwace ,kina Jan ragamar soyayyata, nima haka my prince,, kagama mallakar zuciyar shazee,, shazee taka ce insha Allah da haka har mukayi sallama dashi na kwanta.</p><p><br /></p><p>Yau litinin mun kamo hanyar zuwa Kaduna, tun a hanya nake kiran yayanah , yana ringing amma ba adauka ba" almost 20 misscall ba adauka ba!! Har muka isa Kaduna lafiya, muna shigowa cikin gida naci karo da nafeesa a zauna kan kujera tayi tagumi, tana ganina ta ballamin harara, nayi wuce wata daki, su innama suka karatso.</p><p><br /></p><p>Dama baba yasa angyara dayan dakunan don saukan yan biki"" na diba ruwana naje na watsa tare da dauro alwala nayi sallah, naje dakin babana don gaisheshi amma baya nan.</p><p><br /></p><p>Hmm</p><p>*ranar* *da* *bazan* *taba* *manta* *waba* *arayuwata*</p><p><br /></p><p>Kuka ne ya kwacewa Shahrazad, su fitama da basu San menene ba suma suka fashe da kuka" cikin raunin murya Nusaiba tace aunty shazee mai ya faru pls ki fada mana.</p><p><br /></p><p>Da kyar Shahrazad ta tsaida kukan ta, tace ina cikin dakina, naji nafeesa ta fasa wani uban ihu , maman ta sai lallashinta takeyi, tace kiyi hakuri nafeesa insha allahu Allah zai bayyana mana shi.</p><p><br /></p><p>Nayi saurin kara sawa gaban mama indo, ina cewa mama lfy meke faruwa shiru mama tayi tana kallona, tare da Nuna alaman tausayawa, ta kasa magana.</p><p><br /></p><p>Aunty amingi ne tashigo gidan mu da gudu ta rungumeni, ta baya tana shazee mun rasa yaya Kha___ kafin ta karasa na juyo afusace tare da girgixa ta, nace meye sa meshi karki ce mun ya mutu, don bazan iya jure rashin sa ba, pls kifadan gaskiya, duk nabi na kadu kamar mahaukaciya"" sai jin baba na nayi yana cewa sace Khalid akayi yau kwana biyu kenan babu shi babu alam____ ai kafin baba ya karasa na fadi sumammiya.</p><p><br /></p><p>Khausar tace innalillahi wa'innailaihi raji'u sai tafashe da kuka, gabaki daya yan mata biyar din nan kuka suke.</p><p>Nima anan na ijye wayata don bazan iya ganin bayin Allah nan cikin wannan halin.</p><p><br /></p><p>*TAKU* *Ummu* ( *nusnim*)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 85 & 90</p><p>Allah ka kawo min sauki cikin rayuwata,, ni Shahrazad waye zan fitar amatsayin abokin rayuwana, Wanda zai rike ni da amana, ya kare mun mutuncina da maraicina, oh Allah anya kuwa zanyi auren nan,, don bana jin akwai wani namijin dazan iya kallonsa har muyi soyayya sannan kuma ayi aure, kai banajin hakan zai taba yuwa,, Khalid kadai naba mawa matsayin nan,,,na kara fashewa da kuka nace babana kayi hakuri tunda nake bantaba saba maka dokan kaba """ amma wannan karan bazan iyayin abunda kake so ba.</p><p><br /></p><p>Hmm ni nusnim nace akwai aiki gaba, kucigaba da bina.</p><p><br /></p><p>Shiri nakeyi don tafiya islamiya don na makara, nafito nakama hanyar zuwa misbahul"" ina tafiya ne na wuce wajan dondazon maza, sai naji suna cewa,, tunda masoyin ta ya bata haryanxu taki tayi aure"" gashi shekarunta sai tafiya yake tana kara kwantai"" inbatayi wasa ba me mata uku ko biyu zata aura, don ba saurayin dazai auri wannan tsohuwar, suka kwashe da dariya .</p><p><br /></p><p>Tuni nakara sauri sakamakon hawayen dake zuba da gudu gudu a fuskata, zuciyata kamar zata fashe saboda bakin cikin, nasa hannu na, don goge fuskata, sai naga anmiko min abunda zanshare fuskata, , tare da cewa karbi ki goge hawayen ki , kar mutane su gani.</p><p><br /></p><p>Da sauri na karba ko kallon mutumin banyi ba, yace kiyi hakuri ki dunga addu'a kuma ki dinga saka murmushi afuskarki,, kar agano kina da damuwa, bayan na goge na mika masa abunsa amma ko kallon sa banyiba sai dai nace na gode "" nawuce abuna ina zancen zuci ina Allah wadai da wasu mutanan!! Da haka har nakarasa islamiyan.</p><p><br /></p><p>Shiko mutumin nan yace Allah sarki baiwar Allah, daga ganin ta kaga damuwa atattare da ita"" Allah ga baiwar kanan tana cikin damuwa ka yaye mata, ka kawo mata haske a rayuwarta ameen ya Allah.</p><p><br /></p><p>Su Fatima suka ce aunty shazee amma mutanan nan yan iskane wallahi, sai Allah yasaka makin" waya sani ma ko suna Neman shigane sunga ba fuska shiyasa suka miki haka.</p><p><br /></p><p>Nace sosai ma kuwa dayawa daga cikin su sunsha zuwa wajena da zancen soyayya sai dai nabasu hakuri"" shiyasa suka miki haka, Allah ya miki sauyi da mafi alkhairi ameen.</p><p><br /></p><p>Da aka tashi islamiya na biyo hanyar gidan mu ,, zan shiga gida kenan naji abaya ance assalamu alaikuma ya mu'allima ? Cak na tsaya batare da na juyo ba, na amsa nace wa'alaikumus salam batare da najuyo ba.</p><p><br /></p><p>Yaci gaba da cewa ba mallama inba zaki damu ba ina son yin magana dake ,, gaba nane ya fadi , nasan bazai wuce zancen soyayya ba,, nayi saurin ce mashi mallam ni matar aure ne inada miji" yayi saurin cewa subuhanallah, amatsayinki na mallama bakiyi kama da maiyin karya ba,"" gaba nane naji ya kara fadi.</p><p><br /></p><p>Yaci gaba dacewa ni nasan ke ba matar aure bace, kuma nine mutumin da ya baki Abu daxu da safe kika goge hawayen ki,, cikin xuciyata nace ya ilahi"" me wannan mutumin yake nufi da nine? </p><p><br /></p><p>Yace kar ki damu ba komai nake nufi dake ba sai alkhairi,, na zaro ido waje tare da to she bakina wato yaji zancen zucin danayi.</p><p><br /></p><p>Na bude bakina kenan zanyi magana sai ga babana yazo zai shiga gida, sai washe hakora yakeyi, alamun yana cikin farin cikin ganina na tsaya da saurayi.</p><p><br /></p><p>Nace sannu da zuwa baba yauwa baba ya mika mawa mutumin nan hannu don musabaha,, amma sai ya noke hannun sa ya tsugunna kasa yana gaishar da baban!!! Baba yaji dadi sosai,, ni kuma ganin haka kamar in kwasa mawa mutumin nan mari"" tuni nayi shigewa ta gida, baba yace Dana ya sunan ka?</p><p>Kuma me ke tafe da kai?</p><p><br /></p><p>Wannan saurayin yace baba ni sunana Muhammad sauban, ina zaune a unguwar malali"" to nakan shigo unguwar rimi wajen abokina dake ramat close"" to garin wuce wa nane , nake ganin mallaman nan,, kuma duk sanda zanganta cikin damuwa take"" shine take bani tausayi, na tsinci kaina da son shiga cikin rayuwarta, na kulla alaka mai karfi tsakanin mu, wato ina son in aureta, tazama mata agareni in Allah ya yarda.</p><p><br /></p><p>Baba har cikin zuciyarshi yaji dadi ya kuma yaba da hankalin Muhammad sauban, baba yace Muhammad, naji dadi da jawabin ka "" kuma nayaba da hankalinka!!! Na baka dama ka nemi soyayyar yata Shahrazad"" amma zakayi hakuri da yanayin ta, kamar yadda kace kana ganinta cikin damuwa"" wannan tabbas haka yake sakamakon rashin masoyinta da tayi.</p><p><br /></p><p>Nan babana ya bamawa Muhammad sauban labarina, sai da ya zubar da hawaye sosai tare da kara tausaya min, yaji sona ya kara karuwa acikin zuciyan sa.</p><p><br /></p><p>Yace baba insha allahu zansa mawa Shahrazad farin ciki azuciyar ta, fatana kawai baba kabani ita . baba yayi murnushin jin dadi nabaka ita sauban, amma ka nemi yardan ta, to nagode sai anjima.</p><p><br /></p><p>Niko ina zaune adaki sai safa da marwa nake , saboda naji shiru baba bai shigo ba" ko lafiya?</p><p><br /></p><p>Na kara lekawa inga ko yashigo , cikin zaure naji motsin mutum alamun za ashigo cikin"" nayi sauri nashiga cikin dakina!!! Ina lekansa ta window din dakina,, baba ne yashigo sai murmushi yake shi kadai""" cikin xuciyata nace ko lafiya baba ke murmushi .</p><p><br /></p><p>Koma dai menene intayi tsami maji.</p><p><br /></p><p>Ina ganin mama indo tashiga dakin baba, tace sannu mallam dama Naxo ne muyi magana akan Shahrazad, inajinki mallam ya kamata ace ka aurar da yarinyar nan, tunda taki ta fitar da miji , ya kamata kowaye ne muzaba mata mu bashi, ko ni insamo mata miji, don nagaji da surutan mutane wallahi"" baba yace hakane karki damu insha allahu kwanan xatayi aure don akwai Wanda yazo Neman aurenta yau"'' mama indo tayi kicin kicin da fuska tace mallam yo ni ai har na Mata miji ai, dama Dan gidan kawata ma'u ne yazo wajena yana kuka wai shi inba abashi Shahrazad ba zai iya mutuwa,, mallam yace tofa.</p><p><br /></p><p>Su khausar suka kwashe da dariya suka ce amma wannan matan muguwa CE, gaskiya bata sonki da alkhairi, naga alama mugunta take hada miki!! Nayi dariya nace sosaima kuwa.</p><p><br /></p><p>Fatima yace aunty shazee wai meyasa baki kalla mutumin dayazo wajenki ba, Aida kin bayyana mana ya kamannin shi yake,, wallahi haka nan kawai natsani kallon mazane.</p><p><br /></p><p>Ni'ima tace nikam yamin kuma daga gani zaiyi kusan halin Yaya Khalid, ga sunan shi mai dadi *Muhammad* *sauban* nice name, dukkan su suka kwashe da dariya saboda yadda ta fadi sunan.</p><p><br /></p><p>*taku* *Ummu* *ruman* (nusnim)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p> *BY* *NUSNIM*</p><p> 90 &100</p><p>Washegari ina zaune adakina , naji sallamar wani yaro atsakar gidan mu, mama indo ta amsa mashi"" yace wai ana sallama da Shahrazad awaje!!! Mama indo tace je kace injiwa, ya koma wajen shi , yace" kace inji Muhammad sauban.</p><p><br /></p><p>Ya fada mawa mama indo daidai lokacin nafeesa ta fito zata fita,, mama indo tace yauwa nafeesa Dan Allah jeki duba wani kalan mutumine yake kiran Shahrazad!!! Taya mutsa fuska tare da cewa toh, duk akun nena ake abun,, nafeesa ta fita cikin yanga da yauki kamar mai nemar kai.</p><p><br /></p><p>Yana ganinta ya daure fusaka itama ta daure fuska tare da jan tsaki,, tace dama kai ke Neman Shahrazad, yace eh nine'"" ko ban isa bane? Ta bushe da dariya, injiwa harkayi yawa ma, kai amma naji dadin zuwanka saboda Kaine ka dace da wancan kucan shazee din, takara bushewa dariya, sannan ta wuce cikin gida, xuciyarta cike da farin ciki, saboda kalan na mijin da take so in aura kenan.</p><p><br /></p><p>Mama indo tace nafeesa lafiya naga kin shigo gida cikin annushuwa, ki fada min yaya mutumin yake mai kudine ko talaka, nafeesa tace hmm mama ki kwantar da hankalin ki.</p><p><br /></p><p>Ai ingaya miki talaka ne shi jagab, sannan kuma ustaz ne, gashi bai iya Shiga ba kullum kya ganshi cikin jallabiya,, mama indo ta washe baki tace yauwa, har naji dadi.</p><p><br /></p><p>To amma ke a ina kika sanshi, wallahi alayin su kawata bilki nake ganinshi malali,, gashi yasa mana ido nida ita, ba daman ya ganmu munci ado za mufita sai, ya dinga mana wani wa'azi ,, ko kuma ba dama yaga samarin mu sunxo daukan mu, ya dinga cemana kuji tsoron ,, sai kace munce mashi ba mujin tsoron Allah!! Yacika sa ido.</p><p><br /></p><p>Duk ina jinsu ina Allah ya wadai da halin su,, mama indo naji ta kwala mun kira, nace na'am mama,, kifita waje ana sallama dake nace mata to"" cikin zunburo baki nafita!!! Na karasa wajen shi tare da sallama , ko kallansa banyi ba, yace mallama har nagaji da jira da har ina shirin tafiya, sai nace mashi Aida ka tafi ma"" yayi murmushi yace saboda baki son zuwana ko, bance komai ba.</p><p><br /></p><p>Yace mallama Shahrazad kenen suna mai dadi, nace nagode,, da fari dai sunana muhammd sauban, Ina zaune a malali ,,ina yawan zuwa unguwan nan wajen abokina, nan ya bayyana mun komai kamar yadda ya fada mawa babana,, ina jinshi ban ce mashi komai ba.</p><p><br /></p><p>Yaci gaba da cewa da fatan zaki taimaka mawa xuciyata ki bata matsugunni koyaya ne don Allah!! Wallahi Shahrazad ina sonki ina kaunar ki, kallamanshi sun sa xuciyata zafi tare da hawaye, ban San lokacin da na daga hannu na ba nace dakata sauban!!</p><p><br /></p><p>Wannan Kalmar awajen mutum daya nafiso injishi, awajen shi yake mun dadi shi daya tal"" kuma shine kadai yacika xuciyata, bai bar waje ko kadan ba,, duk yabi ya toshe ramukan dayasan wani Abu zaishiga,, yacinkushi , ya matse, ya manne, sannan yasa Abu mai karfi ya rufe"" shin ka gaya mun ta ina kake son na ijyeka sauban? Ta ina sauban? Ta ina sauban?</p><p>Please tell me sauban, na kara fashewa da kuka.</p><p><br /></p><p>Cikin karayan zuciya yace shazee ki daina kuka please. Kukan ki yana daga mun hankali wallahi, shazee kefa musulmace kuma kin San ance muyi imani da kaddara mai kyau ko Mara kyau"" sannan kuma karki manta fa yau kusan shekaru hudu kenan babu Khalid babu alamarshi , kamar yadda baba ya fada mun, ina so ki nutsu kije kiyi tunani mai kyau,, kiga menene yakamata ki fuskanta ayanxu? menene ya dace da rayuwarki? , Shahrazad kefa ba yarinya bace bafa yanxu. Nidai ki daure ki sama mun matsugunni ko kadan ne !!! Nace uhmm .</p><p><br /></p><p>Yayi murnushin takaici, yarasa ma da mai zaiji, ga rashin kallon sa da takiyi"" ga rashin bashi dama da takiyi "" yauwa shazee ni kam menene alakarki da wannan yarinyar da ta fito daxu, nace yar'uwa tace, sai yace gaskiya kudinga mata fada ta gyara halinta, tana biyewa kawayen banxa alayinmu suna zuwa club, nayi saurin cewa , yanxu abunda nafeesa keyi kenan yace eh wallahi,, duk randa na gansu sai na musu nasiha, kuma su zageni, bashi kuma zai hana gobe inki musu magana ba.</p><p><br /></p><p>Nace Allah ya kyauta, angode da kulawa, ni zanshiga gida, najuya zan tafi yace shazee please meyasa baki son kallona ?ko kamanni na baki saniba fa.</p><p><br /></p><p>Nayi Dan yake, nace mutun daya nake kallo, yace to Dan bani numbern ki, da kamar ta kyalesa, sai b nace bani da waya, yace to ga tawa dayan, na dafa goshina nace kash, wallahi kacika naci, nace ya bani wayan nashi nasaka mashi number Nah, da murnarsa yabada wayan!! Ina gama samashi nayi shigewata cikin gida ko sallama ba muyiba.</p><p><br /></p><p>Yabi bayana da kallo yace shazee iyayen rigima gaskiya zanyi fama kafin na shawo kanta.</p><p><br /></p><p>Fatima tace aunty shazee gaskiya baki kyauta mawa sauban, yaci ace ko yayane ki Dan sassauta mashi, kin San kowa da kalan da baiwar da Allah ya masa,.!! Khausar tace wallahi ya bani tausayi Allah.</p><p><br /></p><p>Shahrazad tace haba Ku kuwa kawai sai, inbashi dama azuciyata, kai da wuya wlh , na Khalid ne kadai Nusaiba tace hmm aunty shazee ance kaso mai sonka fa,, kuma kifada mana dalilin kin kallon fuskan sauban, zakuji anan gaba.</p><p><br /></p><p>Aiko mallam na dawowa mama indo tayi saurin Shiga dakinsa ta zauna, tace mallam da magana fa? Yace Allah yasa lfy indo , lafiya lau Dama zancen makane_____.</p><p><br /></p><p>*taku* *Ummu* *Ruman* (nusnim)</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 100 & 105</p><p>Mama indo tace mallam da magana fa? Yace Allah yasa dai lafiya indo, lafiya lau ba komai bane face maganar auren shahrazad*" yau naji gidan biki, kawai naga anata nuna ni abun ya daure mun kai, nace Niko menayi ake nuna ni?</p><p><br /></p><p>Shine na tambayi wata mata tace, cewa ake kunki aurar da Shahrazad wai kuna jiran mai kudi, mai mota, Wanda zai dinga taimaka mana dawasu abubuwan!!! Har ana cewa wai duk samarin unguwan nan sunxo Neman aurenta ka hana sai mai kudi,, baba nah ya rike baki yana innalillahi wa'innailaihi raji'un"" kai mutane basu San komai sai Allah yayi ba,, tun kafin kazo duniya Allah ya Riga da ya rubuta maka abubuwan da zakayi,.</p><p><br /></p><p>Baka da ikon yin Abu da kanka har sai Allah ya baka iko"" mama indo tace hakane,, amma mallam nikam dazu wani yazo wajen Shahrazad sunanshi kamar saudan ne ko saudin ne, oh dai bansani ba,, mallam yayi murmushi yace sauban sunan"" yauwa shi kuwa, mama indo tace wallahi nayaba da hankalin yaron ,"" kuma da alamun shi da gaske yake zai aureta.</p><p><br /></p><p>Naga babu alamun wasa awajen sa,, gashi yana sonta sosai,, baba nah yaji dadin maganganun mama indo.</p><p><br /></p><p>Baba nah yace tabbas kuwa Muhammad sauban yanada hankali da natsuwa da kuma addini, nima kaina na yaba dashi kuma nayiwa Shahrazad sha'awar auren sa,,, mama indo tace to mallam me zaihana kawai kace ya turo magabatan sa tunda ka gamsu da yaron!!! Mallam yace eh kuma hakane,, amma kafin nan bara nasa amin bincike akansa.</p><p><br /></p><p>Mama indo ta ya mutse fuska, alamun bahaka taso ba, tace acikin zuciyarta bara dai nabi komai a hankali, don karna ruguza shirina, sai nayi yake nace hakane kam"" kayi gaskiya,, Allah ya taimaka ameeen.</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu babana yasa an mishi binciken Muhammad sauban, anfada masa daga gidan mutunci ya fito, iyayen sa, dadtijan kirki ne yaji dadi sosai.</p><p><br /></p><p>Kwance nake kan gadona ina tunanin menene mafita" gashi baba Nah ya takura mun akan sai na fidda miji"" ni kuma duk ba Wanda ya min!!! Ga sauban nan ya takura mawa rayuwata, yahanani sukuni, ya matsamin!! Gashi ni bayyimun ba , bansan kamannin sa ba, ban San halinsa ba,!! Kuma bana bukatan na sani .</p><p><br /></p><p>Wayyo Allah Nah na fashe da kuka, na jawo jakata na Ciro hoton Khalid dina Wanda ya dauka da sallah, ba karamin kyau yayi ba"" andaukeshi yana murmushi , ban San lokacin da nima murmushi ya subuce munba.</p><p><br /></p><p>Na Shafa hoton tare da cewa Khalid sonka Allah ne ya sanya min shi a cikin xuciyata, ya narkan mun dashi yadda babu wata hanya da za'a iya fitar dashi har abada.</p><p><br /></p><p>Abin burina Khalid , Khalid naka sance cikin rashin walwala da nishadi , bani da wani abun tunani sai kai "" shin Yaya zanyi da kaina "!! Kaine tauraro daya mallakin xuciyata, babban ranar bakin cikina shine ranar da narasaka Dan Allah ka dawo gareni"" na fada kan gadona tare da rungume hoton a kirjina, da haka bacci mai dadi ya kwashe ni.</p><p><br /></p><p>*wanene* *Muhammad* *sauban*</p><p><br /></p><p>*Atakaice*</p><p><br /></p><p>Muhammad sauban da ne ga alhaji aliyu, da naja'atu, asalinsu yana garin gashuwa ne, aikine ya kawo alhaji aliyu da iyalan sa Kaduna a unguwan malali laberia raod, babban dansa shine Muhammad sauban, sai Saadiqa sai Yusuf sai Nabila, sannan sai autan su salim, Saadiqa ce kawai tayi aure acikin su, yayin da Nabila take secondary school autan su salim yana j. S.S .1, Yusuf kuma yana jami'a nan kasu,, yanxu haka ana fama da sauban akan ya fito da matar aure sai dai yace had yau baiga wacce ta dace da rayuwar sa ba, ana haka Allah ya hadashi da Shahrazad Inda ya fada tarkon sonta!!! Wannan kenan.</p><p><br /></p><p>Cikin bacci naji wayata tana kara da kyar na daga wayata nasaka akunne na tare da cewa hello"" wato bacci kike ko gimbiyata? Ban San lokacin dana ja tsaki ba tare da cewa kaga ni gaskiya kana takura mawa rayuwata dayawa fa!!! Dan Allah ka kyaleni sauban, tana kiran sunansa ya lumshe ido tare da jin dadin hakan.</p><p><br /></p><p>Naci gaba da cewa haba haba na fada maka gaskiya amma duk da haka kaki ka kyaleni, sai kace ni kadai ce mace, yayi saurin taran numfashina yace tabbas ke kadaice maccen danake gani"" sauran matan ina masu kallon maza ne yan'uwana !!! To ai sai kai tayi kit na kashe wayata, gaba daya .</p><p><br /></p><p>Bangarenshi kuma wani siririn hawayene ya gangaro idanun sa, yace Allah kabani ikon cika wannan alkwarin Dana dauka, ameen.</p><p><br /></p><p>Baba Nah yasa nakira mashi sauban awaya yace yazo yana son ganin shi, gabana sai faduwa yakeyi saboda ban San me baba na zai ce masa ba.</p><p><br /></p><p>Bayan sallar isha'i yazo wajen baba Nah yace mashi yabashi dama ya turo da magabatan sa ayi maganar aure, ba karamin dadi sauban ya tsinci kansa aciki ba"" sai godiya yakewa baba!!!! Baba yace bakomai duk anxama daya,, sauban ko tsayawa bayyi ba sungaisa da shazee yayi tafiyar sa gida.</p><p><br /></p><p>Yana shiga yaga ammin sa azaune ita dasu Nabila da salim, da sauri ya karasa wajen amminsa ya rungumeta cikin murna, tace son lafiya wannan murna haka, ammina anbani shazee ance naturo magaba tana""" Nabila tace wooow bros bravo alaika, gaskiya natayaka murna, salim yace me too bros am happy for you, thanks to you all.</p><p><br /></p><p>Yanxu bara daddy ya dawo sai infada mashi, yauwa ammina, yanxu dai bara nayi wanka sai inzo mu tsatstsara abunda zamuyi, OK son""' sauban nashiga daki ya danna wayansa yakira wani layi, tare da cewa komai yakusan dai daita fa, anbani ita, sai ya kyalkyale da dariya batare da nasan me aka fada masa yasa shi dariya ba.</p><p><br /></p><p>Ina zaune daki babana ya aiko mama indo takirani, muka taho tare, nagaishe shi, yace Shahrazad ba komai bane yasa nakira ki , illa infada miki na ba mawa sauban ke nace ya turo magabatan sa, za 'asa ranar aure, nanda wata daya ko biyu, shine nace bara na fada maki"" kiyi hakuri haka Allah ya rubuta miki, aibansan lokacin da nafashe da kuka ba, nace baba kayi hakuri wlh bana sonshi.</p><p><br /></p><p>Ka kara mun lokaci zanfitar da miji, baba nah ya harzuka ya fara fada"" yace maganar banxa zan zauna ne inxuba making ido kikiyin aure, mutane na zagina a unguwa to wallahi baki isaba kibar ganin ina lallabaki"" mama indo tace shashasha kawai ki godewa Allah kin sami saurayi wanda ke sonki, ba mai mata ba.</p><p><br /></p><p>Da gudu na tashi na wuce dakina tare da tsanar sauban da mama indo, sai surutu nake cikin bacin rai nace wallahi sauban bazan aureka ba," sai dai ka mutu"" bangaren zuciya tane naji tana cewa, aiko in kina gidannan to dole sai kin auri sauban.</p><p><br /></p><p>Shawara kawai ki gudu shine mafita, da Sauri na'aminta da sharrin xuciyata" sai ga murmushi ya kubuce mun, nagoge hawayena, nashiga hada abunda zan bukata nasa ajakata"" nafito gidan mu ba Wanda ya gani, har na wuce kofar gidan su Yaya Khalid " sai nadawo baya na kalli Inda Khalid ke zama, da Inda yake parking din motarsa!!! Kawai nafashe da kuka INA cikin kukane naji andafa ni"" da Sauri na juyo aunty amingi ce cikin murna na rungumeta, nace aunty amingi yaushe kika zo?</p><p><br /></p><p>Tace dazo da rana " ayya da mijinki kuka zo eh wlh,aunty amingi tace shazee meke damunki haka kike kuka, kuma INA zaki haka? nayi shiru ta kara tambaya ta"" naga bazan iya boye mata ba, kawai nafada mata halin Dana ke ciki da kuma Inda zani.</p><p><br /></p><p>Ai bansan lokacin da aunty amingi ta daukeni da mariba sau biyu har sai da naga star.</p><p><br /></p><p>Hmm ana wata ga wata</p><p><br /></p><p>*taku* *Ummu* *Ruman* (nusnim)</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 105 & 110</p><p><br /></p><p>Ai ban San lokacin da aunty amingi ta daukeni da mari har sau biyu sai da naga star.</p><p><br /></p><p>Cikin mamaki na daga ido nake kallonta, ita kuma sai zubar da hawaye takeyi" ta finciki hannuna ta jani gidan su har cikin dakinta, ta jefani kan gado,, sai a sannan na fashe da kuka, itama ta fashe da kuka.</p><p><br /></p><p>Sai da mu kayi mai isar mu sannan mukayi shiru!! Aunty amingi ne tafara cewa haba Shahrazad haba Shahrazad,, yanxu don baki da hankali saboda auren nan zaki bi sharrin zuciyar ki ki gudu kibar gidan iyayen ki?</p><p><br /></p><p>In kin tafi kin San Inda zaki? Kin San me zaki hadu dashi? Kin San hannun wa zaki fada? Mecece ribarki inkin bar gidan iyayenki? </p><p><br /></p><p>Yau mahaifinki ya wayi gari yaga babu ke kin gudu, shin kin San me zaifaru dashi? Kin San kalan bakin cikin da zai kunsa? Kila saboda guduwan ki ya fada cikin mayuwacin hali? Kinyiwa Khalid adalci kenan in kin gudu, na tabbata da zaiji haka!!! Bazai taba barinki ki aikata haka ba.</p><p><br /></p><p>Tunda babu shi to nima bazan taba barin ki aikata haka ba"" haba Shahrazad meyasa har yanxu kin kasa dangana ne, shekara hudu fa kenan babu Khalid babu alamun sa, kinga ko bazai taba dawowa garemu ba.</p><p><br /></p><p>Ni Nafi jin araina Khalid baida numfashi,, nayi saurin cewa aunty amingi kar kice haka"" Khalid dina yana nan kuma zai dawo gareni insha allahu.</p><p><br /></p><p>Amingi tayi murmushi ta karatso kusa dani tana goge mun hawayena, tace shazee ban San wani irin so kike mawa Khalid ba, ko uwar data haifeshi ce sai haka, dake da aunty Hauwa wato(mahaifiyar Khalid) kun kasa yarda Khalid bazai dawo ba,, ina rokan Allah daya cire mukushi.</p><p><br /></p><p>Shazee kiyi hakuri kiyi hakuri" kibi zabin mahaifinki,, gaskiya yake fada miki, kuma shi mai sonki ne, ba zai so wani Abu ya cutar dake ba,," yau da hajiya tana da rai ni natabbata baza ta taba barin kikai haka batare da kinyi aure ba"" nace tabbas maganarki gaskiyace aunty amingi hajiya baza ta bari ba.</p><p><br /></p><p>To kin gani, kinga ko bakaramin kokari baba ya miki ba daya barki bakiyi aure ba, yanxu sai ki mashi biyayya kamar yadda kika saba, kiyi auren" kuma kiyi hakuri, kiyiwa mijinnan naki biyayya kamar yadda zakiyiwa Khalid.</p><p><br /></p><p>Inkinyi haka ba karamun dadi zamuji ba, shima Khalid zaiji dadi sosai!! Na rungumeta nace nagode aunty nah , insha Allah zanyi duk abunda kikace,, yauwa kanwar mu ko kefa.</p><p><br /></p><p>Amma da wai zaki bar gida,, kuma yin haka ba karamin kasada bane,, don yanxu yawancin yan mata haka sukeyi, subar gida, Wanda hakan baida kyau, gujewa umurnin iyaye,, sai kaga Allah ya jarabce ka da masifu kala kala, kabi karasa ya zakayi.</p><p><br /></p><p>Amma idan mukayi hakuri sai muga Allah ya kawo mana sauyi da mafita cikin sauki.</p><p><br /></p><p>Hakane aunty Nah ,, Allah ya bamu juriyan rashin Yaya Khalid, idan yana Raye Allah kayi gaggawan bayyana shi"" inkuma baya Raye Allah kayi masa Rahma ka kai haske kabarin sa ,da ga bakin kofa akayi saurin cewa ameee muka juya kallon kofan aunty Hauwa ce da Umar suka karaso ciki, tare da zama!!! Aunty Hauwa tace duk naji abunda kuka tattaunawa, kuma naji dadi, da Allah yasa amingi kika ga shazee, da badan kun hadu da itaba da ba musan Inda take ba.</p><p><br /></p><p>Nan aunty Hauwa tamun fada da nasiha tanuna min illar guduwa, jikina duk yayi sanyi, kuma nayi Dana sani.</p><p><br /></p><p>Taci gaba da cewa dama dazu alhaji yake fada mun za ayanke bikin ki,, nanda wata daya ko biyu,, naji dadi sosai Allah yasa muna Raye sukace amin.</p><p><br /></p><p>Umar cikin wasa yace aunty shazee, kawai ki aureni tunda muna kama da Yaya Khalid, ga baki dayan su suka kwashe da dariya, nace kai Umar baka da dama.</p><p><br /></p><p>Amingi tace mama yanxu sai ki fara gyara Yar taki tunda baza adau lokaci ba , aikuwa"" yanxu dai shazee tashi ki koma gida don kar aga bakyanan to, natashi na dauki jakata, aunty Hauwa tace ki ijye jakar taki daga baya sai amingi ta kawo miki, toh aunty.</p><p><br /></p><p>Na fito don tafiya GDA abakin titi naga nafeesa anci kwalliya za afita ta gabanta na zo wuce wa nayi kamar banganta ba!!! Sai ji nayi tace haba matar ustaz ko magana babu, tana magana tana dariya .</p><p><br /></p><p>Ban bata amsa ba na wuce azaure naci karo da baba Nah yace ke kuma daga INA, nace naje wajen aunty Hauwa ne , yace to nashiga gida yana kallona tausayina babana yake .</p><p><br /></p><p>Fatima , NI'IMAH, Nusaiba, khausar, duk kan su jikin su yayi sanyi, ko wanne acikin su suna Dana sanin baro gidan iyayen su, yanxu basu San halin da suka sa iyayen suba, khausar ce tafashe da kuka, gaskiya gobe zan koma gida innemi gafaran iyayena, gaba dayan su" haka suka fada, Shahrazad har zuciyarta taji dadi !!! Dama tana so sukoma ga iyayen su, su Neman yafiyar su, Fatima tace, gaskiya aunty shazee Allah ya taimakeki da baki bar gidaba, gaskiya aunty amingi suna sonki sosai.</p><p><br /></p><p>Ni'ima tace wallahi nima nasihar da suka miki, shi yasa ni, Dana sani, da biyewa sharrin xuciyata, gaskiya mun tafka kuakure, Allah ka yafe mana.</p><p><br /></p><p>Cikin kuka Fatima tace mu da auren mu ma muka gudo innalillahi wa'innailaihi raji'un, Allah kayafe mana.</p><p> </p><p>SHAHRAZAD tace Ku godewa Allah da bai kawo muku tsanani ba, bayan barinku gidan iyayen Ku da mazajenku,, Allah yana so kushiryu Ku gane gaskiya, inaga shiyasa ya hadani daku"" Allah kaya femana baki daya ameeen.</p><p><br /></p><p>Iyayen sauban sunzo anyanke biki nanda wata daya, komai ankawo , lefene kawai suka rage"" haka innata suka kara zuwa biki, ni nace bazanyi taro ba, aunty amingi tace ban isaba, tace washe gari tana ban zuwa, dayake a abuja take aure. </p><p><br /></p><p>Aunty Hauwa ta dage sai tsumani takeyi , amingi tazo anshirya komai event daya kawai za ayi, shine Wanda amingi tashirya *sisters* *day*</p><p><br /></p><p>Yau saura sati biyu biki aka kawo lefe baba da innata suka ce agidan aunty Hauwa za akai, , taji dadin karramawan da aka mata,, mama indo tace ba lefen daza taje gani, don tasan bazai wuce akwati daya ba"" don haka nafeesa ta fada mata.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Aranar ma unguwar tama ta tafi"" masu kawo lefen sunxo bakaramin tarba suka samu ba, su Kansu wayanda suka kawo lefen sun raina kan su!!! Akwatuna ne Seti biyu wato gudu shabiyu"" ko wanne kaya ne ciki makil, , su aunty Hauwa suma sunyi mamaki kuma sunji dadi"" mutane yan unguwa sai zuwa ganin gulma suke!! </p><p><br /></p><p>Aiko tuni u/k ta dauka da lefen Nah, anata kananan surutu,, wasu suna cewa yarinyar nan datayi kwantai itace zata auri saurayi kuma mai dukiya, bayan indo tace mana ustaz ne mijin daza ta aura baifi akawo akwati daya ba.</p><p><br /></p><p>Khausar ta kwashe da dariya tace kai mama indo wato ita taje ta baza a unguwa ustaz zaki aura kuma akwati daya za akawo miki kuma yana da mata"" takara fashewa da dariya !!! Yanxu intaji labarin akwatunan da aka kawo ya zatayi?</p><p><br /></p><p>Nusaiba tace aikuwa dai, sai zuciyarta ta fashe, Shahrazad tace ai bara kuji.</p><p><br /></p><p>Tana unguwan da take mutane ke kiranta sukace mata ankawo akwatunan shazee guda talatin, suka kara gishiri Amiya!!! Ai mama indo ta zabura tana karya kuke bayan akwati daya aka kawo ai nafeesa taga akwatin"" taitayi surutai, har ta dawo gida bata yarda ba akwati daya aka kawo ba"" hankakinta atashe.</p><p><br /></p><p>Innata da ta fuskanci haka gun indo bataso nayi auren dadi, sai ta fakaici idonta tace Shahrazad yanxu fisabilillahi kirasa wazaki aura sai ustaz masu kawo akwati daya,, aiko sai ga mama indo ta tashi da sauri"" tace kulu dagaske akwati daya aka kawo, innata tace eh wlh!!! Sai ga mama indo na washe baki ta wuce zaki!! " innata tasaki baki tana kallon ta cikin mamaki"" Niko abunma dariya ya bani.</p><p><br /></p><p>Aunty amingi ne take cemun, shazee nikam ya kukayi da sauban ne game dashirye shiryen biki. Ko zaiyi event ne"" na tabe baki nace ni rabona dashi tun lokacin. Da baba yace nakira masa shi, banma San kamannin sa ba</p><p>.</p><p><br /></p><p>Amingi ta bude baki tace kai to Allah ya kyauta maki shazee, bani number sa, cikin turo baki na mika mata wayata"" tare da cewa nifa karkice yazo "" Dalla rude mun baki.</p><p><br /></p><p>Ringing daya ya dauka tare da sallama nanta yi masa bayanin kanta, da sauri natashi daga wajen don karta hadani dashi.</p><p><br /></p><p>*taku* *Ummu* *Ruman*</p><p>(NUSNIM)</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 110 & 115</p><p>Ringing daya ya dauka tare da sallama , nan ta fara yi masa bayanin kanta"" nayi sauri natashi daga wajen don karta hadani dashi.</p><p><br /></p><p>Daga bangaren sauban yace tuba nake aunty mu na rashin zuwa na"" gimbiyar ce bata son ganina!! Shiyasa" dama ina ta tunanin tayaya zan bada kudin hidimar biki tunda ba sanin kawayenta nasa niba.</p><p><br /></p><p>Aunty amingi tace sai kayi hakuri da kanwar tawa, insha allahu komai zai dai dai ta" yace toh ya tabbatar.</p><p><br /></p><p>Dama zan ce maka ne zamuyi sisters day, ko daga bangaren ka akwai wayanda zasu zo"" yace eh inada kannai mata biyu insha allahu za su zo, OK nagode .</p><p><br /></p><p>Yauwa aunty Dan Allah Dan turo min account number dinki, don zan turowa Amarya sako .</p><p><br /></p><p>OK yanxu zaka gani!! To nagode, ba damuwa.</p><p><br /></p><p>Bayan sun gama waya ta tura mashi account dinta , dayake G.T take amfani dashi, shima haka, yayi mata transfer din kudi mai tsoka taji dadi sosai, takirani take fada mun"" nace ni ba abunda zanyi da kudi aunty amingi.</p><p><br /></p><p>Shahrazad wallahi ki Shiga hankalin ki inba haka ba in saba maki don naga abun naki iskanci ,toh zan gyara miki zama sorry aunty meenatah.</p><p><br /></p><p>Nafeesa ce tashigo dakin su ta ga mama indo sai murna take, tace mama shin lafiya na ganki cikin annushuwa, mama indo ta washe baki tare dacewa ai ankawo akwatin Shahrazad nan dai mama indo ta fada mata komai!! Itama nafeesan taji dadi sosai.</p><p><br /></p><p>Shagalin biki ya kanka ma, ba abunda nake tabukawa, sai sana'a ta na kuka Dana sa agaba"" dayake banda kawaye, kawata ta kusa tayi aure wato ummin A.A kuma taje naija,, shiyasa aunty amingi ta gayyato kawayenta amatsayin kawayena!! Sai dai kawai inbisu da ido.</p><p><br /></p><p>Yaune ranar sisters day din da aunty amingi ta shirya Wanda za ayishi a 17 hotl dake u/rimi kufaina road , ba karamin haduwa yayi ba, ba a iya fadan yadda hall din ya kayatu.</p><p><br /></p><p>Sadiqa da Nabila sai shiri suke , bakaramin kyau sukayi ba,, sauban ne ya karaso wajen su yace sisters gsky kunyi kyaufa, tanx bros!! Sadiqa tace bros kai zaka kaimu ko"" no bani zan kaiku ba Yusuf ne ni akwai abunda zanyi ne ok., suna cikin magana wayarshi tayi kara " yafita daga Inda suke don ansa waya, hello yadai sai naji yayi shiru ban San abunda ake cemai ba a dayan bangaren!! Sai gani nayi yasaki murmushi tare da zubowan hawaye a fuskar sa, yace insha allahu komai zai dai dai ta,, sai ya kashe wayan da tare da sauke numfashi.</p><p><br /></p><p>Aunty amingi ne zaune gabana tana gyara mun dauran Dan kwalina, tace woow sister kinga yadda ki kayi kyau kuwa "" naturo bakina, nace nidai kidaina cewa nayi kyau bana so, sai ta fashe da dariya tace kalle yadda kikayi kamar karamar yarinya"" wata kawar amingi CE tashigo, tace haba amina kunxauna sai hira kuke duk mutane sun gama zuwa Ku kadai ake jira kawai.</p><p><br /></p><p>To gamunan zuwa oya shazee tashi, zainab Ku taka mata abaya toh , da haka har muka karasa cikin mota xuciyata bata min dadi idan na tuno da sauban za ayi auren nan, munkarasa cikin hall din aka sake sauti ma dadi mai tsuma, can na hango yan GRP din </p><p>All dostis of nusfulhayat, su aunty rabi, yayar cool, Fatima, Firdausi, fauziya , Ummu Arfat, da dai sauran su ,.</p><p><br /></p><p>Ba sai na tsaya fada muku yadda sister day din ya hadu ba, wannan na bar muku.</p><p><br /></p><p>Bayan angama kowa ya koma gida da abun arziki don ba karamin Abu aunty amingi tayiba da bikin nan yadda kuka San yayan tah ke aure.</p><p><br /></p><p>Zaune nake cikin dakin Yaya Khalid na kulle kaina sai kuka nakeyi , ina tunanin yanxu haka I gobe nazama matar sauban, ya ilahi, Allah ka kawo min sassauci, da haka har bacci ya dauke ni.</p><p><br /></p><p>Amingi sai nemana takeyi, ko ina ta duba bana nan , ko ina shazee taje ne oho, har ta gota dakin Yaya Khalid sai ta dawo da baya"" ta karema kofan kallo da alamun anshiga dakin ? Ta karasa wajen kofan ta murda taji shi arufe.</p><p><br /></p><p>Ta koma dakin aunty Hauwa ta dauko dayan makullin ta bude dashi, can karshen gado ta hango ni kwance na kudundu ne da bargon Khalid sai kuma hoton sa dake kirjina rungume.</p><p><br /></p><p>Amingi ta fashe da kuka tare da cewa Allah sarki, shazee abar tausayi, har yau dai dai da kwaya dayan son Khalid baifita aranki ba,, shin yaushe zai fita daga ranki " ta daga hannu sama tana roka min Allah daya cire mun Khalid"" tayi mun addu'oi ta Shafa mun , tare da gyara mun kwanciya na, sannan ta fitar tare da jawo min kofa.</p><p><br /></p><p>Washe gari ya kama asabar ranar daurin aure nah da Muhammad sauban , mama indo andage sai aikin abincin biki take, sai wajajen sha daya natashi bacci, kasan cewa bana sallah aranar ,, ni kaina nayi mama kin baccin danayi, kuma ba Wanda ya tasheni.</p><p><br /></p><p>Bayan nayi brush na fito na kulle dakin na karasa dakin aunty amingi, zaune na gansu suna karyawa!!! Tace a'a Amarya kintashi, gaskiya yau kinsha baccin gajiya"" nace aikuwa dai!! Na zauna cikin su muka karya tare.</p><p><br /></p><p>Bayan mun gama ne kowa yayi wanka ya shirya har nima nasa atamfana mai kyau, sai akayi min kwalliya duk inda na gota , to sai nabar kamshi, ni kaina nasan na hadu sosai, kowa sai su yake ya daukeni hoto.</p><p><br /></p><p>Hmmmmmmm</p><p><br /></p><p>Karfe biyu Masallacin misbahul Islam cike yake da mutane yan daurin aure, can Nagano ango sai kyalli yakeyi tare da washe baki ga abokanan sa duk sun mamaye sa , can naji a na cewa an daura auren Shahrazad abdulmaleek da angonta Muhammad sauban aliyu, abisa sadaki dubu hamsin !! Sauban ne ya daga hannu sama yace alhamdulillah , Allah nagode maka daka cika mana burin mu"" ina kuma rokanka da ka cika mana dayan burin mu daya rage.</p><p><br /></p><p>Hmm masu karatu, wai mai sauban ke nufi ne, nifa banyarda dashi ba, koza Ku iya lalubo mana amsan., sai najiku.</p><p><br /></p><p>Kawu mamudu ne yashigo gida yana ina matar sauban ta fito angonta yazo yana son ganinta"" innata tace mamudu nikam har andaura auren ne,, eh Yaya andaura yanxu shazee tazama matar sauban.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Daam naji gabana ya fadi, nace innalillahi wa'innailaihi raji'un, yanxu ni shazee nazama matar sauban kaicona , na fashe da kuka me tsuma zuciya, amingi ne ke lallasha, tana bam baki, kiyi hakuri shazee komai yayi farko zayyi karshe.</p><p><br /></p><p>Bayan isha'i , babana ya kirani daki yayi mun nasiha sosai , hakama baban Khalid, ban San lokacin Dana fada jikin ABBAN Khalid ba na kara fashewa da kuka, yashiga lallashina, da kyar yake iya magana.</p><p><br /></p><p>Su aunty Hauwa da innata sai da suma suka min nasiha, sannan akace Amarya su fito anxo daukanta, dakyar aka rabani da innata da aunty Hauwa.</p><p><br /></p><p>Su mama indo da nafeesa sune kan gaba akai Amarya don suje suga kalan gidan.</p><p> </p><p>An wuce dani unguwar malali inda gidana ke can kasan laberia raod , ana xuwa kofar gidan , mama indo tayi saurin cewa ai ba nan bane gidan, me tuka motan yace hajiya nan ne, ido ta zaro waje takasa magana, yayin da nafeesa ta sandare azaune.</p><p><br /></p><p>Mai gadi ya bude musu get din gidan suka Shiga ciki, tsararren gidane Dan madaidai ci, mai tsari da fasali, ka shokoki kewaye da harabar gida, don haduwa kam gidan ya hadu, mama indo dakyar tafito daga mortar"" tare da sakin baki, kamar wawiya!!! Aka fito dani har cikin dakina aka kaini , kayan dakin , kayan dakin sun tsaro kuma ankashe kudi acikin,, wannan duk aikin iyayen Khalid ne, su sukace dole su zasu min kayan daki da komai na cikin gidan"" ba abunda zan cewa bayin allahn nan sai dai ince Allah yasaka masu da alheri ameen.</p><p><br /></p><p>Bayan kowa yagama ganin dakin Amarya aka watse da kyar aka ja mama indo cikin mota, don ihu take tayi kamar mahaukaciya"" dagani sai aunty amingi sai kawayenta guda biyu.</p><p><br /></p><p>Muna zaune har ango da abokansa sukazo, akayi siya baki, suka ga Amarya bayan sun bada kudi, daza su tafi da kyar aka rabani da amingi na kanka meta sai kuka nakeyi ,, itama kukan take,, ni kadai aka barni adakina sai tsoro nakeji,.</p><p><br /></p><p>Bayan sun tafi sauban yashigo ya rurrufe ko ina na gidan, zai shigo dakina wayarshi tayi kara,ni kuma dake daki duk tsoro ya cikani, shine na fito don ba zan iya zama ba, fitowa ta kenan naji"" sauban na cewa awaya ? zankiyaye .kuma ai alkwari na dauka don cimma buri, gaba nane ya fadi araina nace buri.</p><p>Jin magana abayanshi, yayi saurin jiyowa.</p><p><br /></p><p>Hnmmmmm ana wata ga wata, mai karatu mai ka harsasu a wannan novel din INA kiran comment dinku, in ba haka ba baza kujini ba.</p><p><br /></p><p>Ga mai son ganin sisters day din Shahrazad ya duba dp dina.</p><p><br /></p><p>*taku* *ummu* *Ruman* (nusnim)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 115 &120</p><p> Jin magana abayan sa ya sashi juyowa, nace buri. </p><p><br /></p><p>Wani buri kake son cikawa , cikin takun kasaita ya taku wajenta, ya tsugunna fuskanshi dauke da murmushi,, a zuciya na ko cewa nake masha Allah yayi kyau anan, gsky sauban namijini mai kwarjini da haiba, na kafeshi da ido nima ya kafeni da ido"" kallon juna Muke kowannen mu da abunda yake saka wa a zuciyan sa.</p><p><br /></p><p>Niko gabana sai harbawa yakeyi saboda kallon da yake mun irin na Yaya Khalid Sak, da badan kamanni ya banbanta ba"" to da babu abunda zai hanani cewa Khalid dina ne.</p><p><br /></p><p>Ban ankaraba cak naji andaukeni kamar wata jaririya , ido kawai nake binshi dashi kamar wacce taga wani abun" ya direni kan gadona , na kara jeho mashi tambaya nace wani buri kake son cikawa?</p><p><br /></p><p>Yace burin danake son cikawa shine, in rike Shahrazad tsakani da Allah, inbata kula, in saka mata soyayyata, in share mata hawayenta, toh kinji, na sauke ajiyar xuciyata.</p><p><br /></p><p>Yace toh ke me ya fito dake daga daki, na cinno bakina gaba nace, to ba tsoro naji"" gidan nan ma akwai aljanu Allah, sauban ya kwashe da dariya, yace, Ashe haka kike da tsoro tabdi jam zanyi fama .</p><p><br /></p><p>Yanxu dai bara na dauko plate da cup da gazarki , ya miki kenan nima nayi zumbur na miki , yace lafiya kuma, ni wlh bazaka barni cikin dakin nan ni kadai , tare zamu.</p><p><br /></p><p>Sauban yayi dariya cabdijam lalle shazee akwai Daru, toh muje yana gaba Ina binsa abaya ya dauko, tayashi da wani Abu dazamu dawo ciki, iskace takada kofa, garam kakeji, ai bansan lokacin Dana ruga aguje na rungumeshi sosai , kayan hannu na, na watsar dasu.</p><p><br /></p><p>Sauban ya rikice yace lafiya shazee, idona arufe yake gam, sai da ya girgizani sannan na bude ido "" nace wancan kofan naji anturo da karfi.</p><p><br /></p><p>Kai shazee iskane fa , hadarine ya hadu sosai, ya tattaro kayan muka shige daki , na zauna akasa, shima ya zauna, yabude kazan , yazuba mana milk a cup,, nace nifa akoshi naki !! Yace ai kuwa baki isaba, sai kinci, inba haka ba infita daga dakin; duk abunda zai kama ki ya kamaki, yayi yunkurin tashi, nayi saurin rike mashi Riga nace"" nace yi hakuri kazauna zanici.</p><p><br /></p><p>Bayan mun gama ci, natashi nayi brush dina tare dayin alwala don banyi sallar isha'i ba, bayan na tada sallah tah yayi min wayau ya fita. Dakinsa ya wuce yayi alwalar tare da wanka , ina kan abun sallata ya shigo, nace shine ka gudu ka barni ko.</p><p><br /></p><p>Tuba nake gimbiyata, natabe bakina, yace tashi muyi sallah mu godewa allah, ba musu natashi , amma gabana sai faduwa yakeyi.</p><p><br /></p><p>Bayan mun idar yayi mana addu'oi, da kuma abubuwan ma aurata ke gabatar wa,, zantashi ya rike mun hannu na"" yace ina zaki kuma, zan kwanta ne, ai bayanzu zaki kwantaba hira zamuyi. </p><p><br /></p><p>Hira kuma, yace eh , nifa gaskiya bacci nakeji, cikin muryan mai kama da kuka,, yace kefa baki rabuwa da shagwaba da girman ki, humm"" to Dan Allah zauna akwai maganar daza muyi , na zauna , tare da kallon shi "" yace shazee sai yaufa kika taba kallona , na miki kuwa? Ina cikin tsarin mazajen da kike so? Sannan kina sona kuwa? </p><p><br /></p><p>Na sadda kaina kasa ina wasa da yatsun hannu na"" ina tunanin me zan ce masa,, ya kinyi shiru shazee kibani amsa na mana, xuciyata tace Dan Allah karki gaya mai magana Mara dadi.</p><p><br /></p><p>Nace sauban kayi hakuri da abunda zance ma, kai namiji ne wacce mace zatayi alfahari dashi, duk macen data ganka baza tace bakayi mata ba"" hasalima mata rububinka zasu yi tayi,, sai washe baki yake tayi"" amma kuma ni xuciyata, sai nayi shiru nakasa karasawa.</p><p><br /></p><p>Sauban yace amma kuma ke zuciyarki Khalid kadai take so, shi kadai kike gani, gangar jikin ki na aura amma zuciyar ki tana wajen Khalid,, (kamar na Hanna abubakar imam da uncle haisam) ya cigaba da cewa shazee bazan miki tilas da ki soni ba, amma xansu ki kyautatamin, kimin biyayya a matsayina na mijinki, sannan kuma Dan Allah ko yayane ki koyawa duciyarki sona koda Rabin rabine"" in magana ta ta bata miki rai kiyi hakuri, kalaman shi sun shigeni ya kuma bani tausayi"" kai kayi aure amma matar bata sonka, nace Allah ya bamu zaman lafiya.</p><p><br /></p><p>Yace amin</p><p><br /></p><p>Na tashi na haye gado, shima ya tashi ya haye gadon"" xuciyata ne naji tana harbawa yau gani daki daya da wani namijin, kuma mijina, tare zamu kwana,"" duk yagane a tsorace nake yayi murmushi, ya juya min baya.</p><p><br /></p><p>Da tunani bacci ya kwashe ni, da asuba natashi yin sallah na duba gefen sauban naga baya nan, nace kila yaje masallaci ne.</p><p><br /></p><p>Nayi alwalata nayi sallah, ina cikin karatuna yayi sallama ya shigo, Dana gama karatun, nagaishe shi . </p><p><br /></p><p>Ya amsa min, tare da cewa ya gajiyan biki da tsoro, nasadda kaina kasa nace lafiya to madallah, yace bara yaje dakin sa zai hada wasu takardune ,, nace toh, yace koxa ki rakanine? Nace a'a , xan kwanta, ne OK.</p><p><br /></p><p>Gari yakara haske sai wajajen 10am natashi nayi wanka nayi kwalliya sannan nafito parlo, sauban ne zaune yana kallo nakaraso parlo na zauna , yace Amarya harkin tashi nace mashi eh, to sannu my D .</p><p><br /></p><p>Nayi saurin juyowa tare da zaro ido, nace sauban ina kasan sunan nan? yace wani suna kuma, my d da kace, wani abune? ". Ina nufin fa my darling menene shazee, nace sunan da Khalid ke cemun ne fa, kai shazee wannan sunan fa kowa zai iya fada mawa nasoyin sa, "" cikin gajiya da maganar nace to ya isa, amma azuciyata ina ta tunani.</p><p><br /></p><p>Yace ga breakfast dinmu can , ammi tasa ankawo mana nace to,, natashi na dauko abincin ba zuba mana waina CE da miyar taushe sai kamshin manshanu yake, sai kuma sai kuma soyayyar arish da kwai ga kayan tea , na zuzzuba mana mukaci "" bayan mungama na kwashe kayan nakai na wanke .</p><p><br /></p><p>Sannan na dawo na zauna , muna zaune mukaji sallama, ya amsa tare da zuwa bude kofan, su Nabila ne da Sadiqa,,, sauban yace lafiya kuka zo mun gida da safe,, Nabila tace lallai ma, bros kace wani Abu, don kayi aure shine zakayi mana wulakanci, Sadiqa zo mutafi dama sallama nazo maka"" duk cikin wasa suke magana.</p><p><br /></p><p>Yayi saurin cewa no sister karki tafi mana, nima wasa nake miki fa , dukkan su sukayi dariya, duk ina jinsu!!! Tare suka karatso cikin parlo din " nace sannun Ku da zuwa , suka ce yauwa, nan muka gaggaisa, sannan muka Shiga hira""" can kuma sai ga aunty amingi tazo """ wayyo dadi da gudu naje na rungumeta """ ni sake ni karki karya ni ,, ta karaso suka gaisa da su Sadiqa,, nan hira ta barke,, lokacin tafiyan su Nabila yayi , na hada musu turarur ruka da kayan kwalliya.</p><p><br /></p><p>Intakai ce muku, haka rayuwata taci gaba da tafiya agidan , har nayi wata biyar a gidan sauban, tsakanina da dangin mijinta mutun tawa da girmamawa"" suna sona kamar zasu cinye ni,, nima haka .</p><p><br /></p><p>Mama indo kuwa kamar zautacciya ta dawo kullum sai ta dinga sambatu akaina, wai ina ina baza ta yarda nayi aure gidan kudi yar'ta bataji ba""baba na kallon. Mahaukaciya yake mata!!! Nafeesa kuwa Takara tabarbarewa sai yawonta take iya son ranta.</p><p><br /></p><p>Kullum muna waya da aunty amingi, taitayi mun nasiha akan da inbi mijina inkyautata masa , insoshi, hakama aunty Hauwa fadanta kenan.</p><p><br /></p><p>Har nakai wata goma dayin aure, nida kaina na zauna tunani don yin karatun ta nutsu, akan aurena,, naga bana kyautama sauban , amatsayin sa na mijina ya kamata iyanxu in hakura da wani Khalid, infuskanta gabana!!! Da haka na fara koyawa kaina son sauban amma ba sosai ba"" ranar ya tafi gun aiki, na tashi na gyara gidana yayi kyau, sannan nayi girki mai dadi, duk kamshi ya mamaye gidan!! Sannan naje nayi wanka na tsantsara kwalliya, nasaka Riga da wondo .</p><p><br /></p><p>Wandon ya matseni sosai ya fitar da shape dina, rigana Mara hannu sai igiyan wuya da ake daurewa, wandon baki, rigan red"" ba karamin kyau nayi ba.</p><p><br /></p><p>Yau nayi niyan faranta mawa mijin , na fashe ko ina na jikina da turare, kamshine kawai ke tashi"" har dakin shi na gyara ko ina nagidan saida nasa turaren wuta.</p><p><br /></p><p>Na zauna ina kallon TV can naji karan mota alamun ya dawo yana shigowa hara ban gidan yafara ganin canji"" ya karaso kofan da zata sadaka da parlo, ya kwankwasa, natashi kirjina sai harbawa yake yi ina tunanin tayaya zan iya hada ido dashi ahaka har na rungumeshi, , nakara kallon jikina"" gashi ko bra babu ajikina, Abu a tsaye gashi ana kallon shedan kan kirjina,, kara kwankwasa kofan da yayi"" ya dawo dani daga cikin hankalina.</p><p><br /></p><p>Da sauri na bude kofan , zaiyi sallama kenan ya tsaya cak sakamakon rungumeshi da nayi, kirjina ne ya cakeshi , numfashin sa nason daukewa, jakar hannun sa ta fadi kasa. </p><p><br /></p><p>*taku* *Ummu* *Ruman* (NUSNIM.)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD*❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 120 & 125</p><p>Jakar hannun sa ta fadi, hannu na, nakai tsakiyar bayan shi ina shafawa, zuwa saman Kansa, tare da rada mashi akannu ne, barka da dawowa my zauji"" na kama dayan hannun sa , na saka akan kwankwa so, sannan na jashi zuwa dakin sa.</p><p><br /></p><p>Sauban ya kasa magana duk ilahirin jikin sa sai rawa yake,, bayan munshiga dakin,, nashiga balle mashi botur din rigansa, sannan nacire, na ijye gefe, idon sa aruntse!!! Sannan na kai hannu na kan belt din wandan sa zan cire, yayi saurin rike hannun na, yana sauke numfashi a hankali.</p><p><br /></p><p>Cikin murya kasa kasa yace no shazee bashshi zanyi,, nima nace no sauban ,komai ni zan maka yanxu, please karka hanani!!! Da kyar ya barni nafara cire masa ,dagashi sai gajeran Wando da .</p><p><br /></p><p>Sannan na jashi zuwa toilet, bayan na kaishi na fito naja mashi kofan "" na sauke ajiyar zuciya, duk abun nan danayi karfin haline wlh,!!! Sauban kuwa bayan nafita shima ya sauke ajiyar zuciya, tare da cewa, anya lafiyar shazee kuwa , da kyar inba wani Abu tasha ba.</p><p><br /></p><p>Kai yarinyar nan zatasa na karya alkwari, kai anya zan iya yin wannan aikin,, don gaskiya da akwai wahala da hatsari, acikin"" kalli duk yadda tabi tasa na jike,, hmmm gaskiya da aiki agabana.</p><p><br /></p><p>Na bude wajen ijye kayansa, nafito masa da kaya mara nauyi nashan iska, sannan nima na koma dakina, na saki wanka tare da kwalliya, Wanda yafi na dazu,"" siket nasaka dai dai iya cinyata, sa kuma wata Yar riga mara nauyi , kayan masu kyau, , bakara min kyau nayiba sai nadawo kamar Yar tsana"" ammafa inajin kunyan fita haka.</p><p><br /></p><p>Da kyar nafito parlo, zan Shiga dakin sa kenan sai gashi ya fito mukayi karo ,, na tafi ta baya zan fadi kenen ya taroni,, ni kuma na rike goshina ina wash Allah, cikin muryan shagwaba nace kafasamin goshina ko, cak ya dagani muka karasa cikin parlon muka zauna ina kan jikin sa, cikin kasa kasa da murya yace sannu ko bara naga wajen .</p><p><br /></p><p>Hannun sa yasaka asaitin wajen yana Dan daddan na min, nace wash da zafi fa allah , to sannu ko"" ya kare mun kallo ga santala santala santalan cinya na awaje, azuciyar shi,, yace masha Allah.</p><p><br /></p><p>Nafara kokarin tashi yace ina zaki abinci zan kawo mana , OK to,, haka na tashi ina tafiya ko ina na jikina sai juyawa yake, abunka da dirarriyar mace mai kira.</p><p><br /></p><p>Jikina yabani Ana kallona, na kara sauri,, shi abun ma dariya ya bashi!!! Na dawo dauke da kulan abinci kala kala"" da drinks na kwakwa da kunun aya mai dadi,, tare mukaci abinci yana ci yana santi,, lallai shazee haka kika iya abinci, kai wai da mai da mai kikasa aciki ne, nace kai zauji kodai insa maka waigine? Yayi dariya.</p><p><br /></p><p>Bayan mun gama ne, ya kura mun ido har naji kunya ,, nace kallon nan </p><p><br /></p><p>Yace bakomai shazee princess kinyi kyau, ta lumshe ido tareda budewa, wayar sa ce tayi ringing don hk y mike ya nufi daki,</p><p> Ganin haka yasa ta mike itama ta tattre kayan ta maida kitchen,</p><p><br /></p><p>Bayan kwana biyu,</p><p> Yau Saturday babu aiki,</p><p> Sauban da guri yafita exercise don dama du weekend HK yakeyi,</p><p><br /></p><p>Shazee na kwance yau ko fitowa batayi b, balle ta hada musu breakfast</p><p>Batada lafiya tun Daren jiya takejin ciwon mara kadan kadan to yau kuma ya karu,</p><p>Tun tn daurewa hr takasa Inda tafashe da kuka juyi take itakai saman gado,</p><p> Sauban bai shigo ba sai karfe goma na safe,</p><p> Yana shigowa baiga shazee a falo ba kmr yarda y saba,</p><p>Sai ya Shiga dakin direct inda y hangota kangado tana juyi,</p><p> Cikin sauri ya karaso yn kiran sunanta shazee? Shazee menene, lafiya?</p><p>Takasa mgn illah juyi da take kawai,</p><p>Yaye blanket din yy da sauri ya dagota, hankali a tashe bai San lokacin daya mannata a jikinsa b yana mai girgizata hankali tashe,</p><p> Yace fadamin pls</p><p><br /></p><p>Cikin yanayi najin ciwo tace c cik,,,cikinnaa, tafada cikeda rawar murya,yace subhanllahi tun yaushe? Dama kinayine?</p><p><br /></p><p> Girgiza masa kai tayi</p><p> Kwantar da ita yayi ya mike ya fice, </p><p><br /></p><p>Chemist yaje ya siyo mata mgnin ciwon ciki,</p><p> Yace sannu shazee daure muje kisamu kiyi wanka kidan ci abinci sai kisha magani,</p><p> Koda ya mikar da ita, kasa tsayawa tayi, koda ya lura da hakan sai kawai ya dauketa cak hr bandakin</p><p><br /></p><p> Ya hada mata ruwa, sannan ya Dan mtso cikin sanyin murya yace shazee kidain kuka, bari in taimka miki, cikin tsoro tace zan zn iya kaje kawai,</p><p> Ya kalleta sosai yace are you sure? Kai ta daga mishi,</p><p> Fita yy a bndakin ya rufo mata kofa,</p><p><br /></p><p>Yarasa me zaiyi sai yafara gyra mata gadon yana cikin gyarawa yaga digo digon jini,</p><p><br /></p><p>Kallon wajen yakeyi cikeda tunani,nan ya gano abunda ya haddasa mata ciwon, </p><p><br /></p><p>Yaye bedsheets din yy ya shimfida wani,</p><p><br /></p><p> Nan da nan ya gyara, tana fitowa ta tashirya dakyar take kokarin zama a kasa, yayi saurin karasawa inda take ya sanya hannu ya dagota a hnkli yace sannu shazee</p><p><br /></p><p>Ya kwantar da ita dakansa ya shiga kitchen y hada mata breakfast,</p><p><br /></p><p> Dakansa ya bata abaki, tanaci tana hawaye, ya sanya hannu yana share mata hawayen,</p><p><br /></p><p>Lokacin da cikin ya murda mata juyi takarayi ajikinsa tare da kifa kanta ta tsakanin cinyoyinsa tana kuka, wani shock yaji lokacin da ta daura kanta bisa cinyoyinsa musamman data goge marar sa, yrrr tsigar jikinsa ta tashi,</p><p><br /></p><p> Ganin hanklinsa na kokarin tashi yasa yadan janyeta,</p><p><br /></p><p>Kwantr da ita yayi gefe, inda ya Dan Shiga bubbuga baynt alamun rarrashi</p><p><br /></p><p>Tuni barci ya dauketa,</p><p><br /></p><p> Ganin HK yasa yamike shima wankn yashiga, ya fito ya shirya, sm yakasa cin komi sai ruwan tea, koda yakom falo, du bayan minti biyar saiya leka yg kota tashi,</p><p> Bata farkaba sai wajen karfe biyu,</p><p><br /></p><p> Kalau ta farka babu ciwon bandaki tashiga inda taga ta baci sosai ta kimtsa knt sannan tafito,</p><p><br /></p><p>Masu karatu bari in Dan huta daga nan,</p><p><br /></p><p>Haj ceeymer💁</p><p><br /></p><p> nagaisheki ba adadi Allah yabar zumunci,</p><p><br /></p><p> </p><p>*TAKU* *UMMU* *RUMAN* (Ruman)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 125 & 130</p><p>Bayan ta fito ta shirya tasa kaya ta fito parlo, sauban dake zaune yayi sauri ya tashi don taroni, kamani yayi tare da cewa sannu ko shazee, ya jikin"" nace da sauki, ya zaunar dani kan kujera, tare da cewa ina yake miki ciwo yanxu?</p><p><br /></p><p>Nace babu naji sauki sosai to madallah haka nake son ji , na Dan kura mashi ido, azuciya na nace Allah sarki sauban bawan Allah, kalla duk yadda ya rude akan Dan wannan ciwon danayi.</p><p><br /></p><p>Ya ce shazee wannan kallon fa nayi saurin kakalo murmushi tare da cewa sauban nagode sosai Allah ubangiji ya biya ka, haba shazee godiyan me kike mu? In don wannan kulawar Dana baki kike godemun to ki daina"" saboda yazama dole in kula dake , ke amana ce awajena , alkhawari na daukar musu.</p><p><br /></p><p>Nayi saurin cewa suwa ka daukar mawa alkhawari,, gaban shine yafadi, don baisan lokacin da maganar ta subuce masa ba,, yace su baba mana, ai nace musu bazan bari wani Abu ya tabaki ba.</p><p><br /></p><p>Na zuba mashi ido ina son karantar wani Abu don banyarda da maganar saba, tunda nashigo gidan sauban ,, nafara lura da wasu abubuwa, yana min abunda Khalid ke mun, sannan kuma nakanji shi yana amsa waya, sannan kuma yana boye mun wani Abu"" kaai akwai wani Abu.</p><p><br /></p><p>Wasa wasa nayi shekara daya da watanni agidan sauban wani Abu na auratayya bai taba shiga tsakanina dashi ba"" sannan kuma naga ya canxa mun ,, kullum sai ya dinga zama nesa nesa dani,, ga yawan tunani da yakeyi ,,, duk yabi ya rame tun abun baya damuna har yafara damuna saboda ance ka damu da Wanda ya damu dai.</p><p><br /></p><p>Duk macen data samu sauban a matsayin mijin aurenta, to wlh ta more bata da damuwa, saboda ya iya tattalin mace.</p><p><br /></p><p>yau sati sauban ya wuni adaki bai fito parlo ba,, ganin haka yasa na Shiga dakin sa "" tare dayin sallama, yana kwance idon sa biyu yana kallon silin din dakin,, hawaye na gangara , yana jin motsina, yayi saurin goge hawayen sa cikin dabara don kar ingani.</p><p><br /></p><p>Da sauri na karasa tare da zama kusa dashi na taba jikinsa duk na rude nace zauji lafiya, meke damunka,, kwana biyun nan duk ka canxa, kuma kaki kafada mun damuwar ka,,,kawai sai nafada jikin sa na fashe da kuka me tsuma zuciya.</p><p><br /></p><p>Ya tashi cikin rudewa ya dagoni tare da cewa sorry my Shahrazad ki daina kuka please, don kukanki na daga mun hankali!!! Nace haba sauban tayaya ba zanyi kuka ba, kaki fada mun damuwar ka , kabar ni cikin duhu, sannan kuma ina tuhumar ka da abubuwa masu yawa,,, xuciyata takasa yarda bakai bane Khalid dina, yayi saurin tureni tace shazee kin San me kike fada kuwa.</p><p><br /></p><p>Nima na miki nace na sani,, sauban kai ne Khalid dina, kai ne masoyina ,, Kaine habibi na"' da soyayyar ka na girma"" kuma dashi nake rayuwa har yanxu""wlh bazan iya mantawa da kai ba.</p><p><br /></p><p>Amma why Khalid meyasa zaka boye mun kan ka, kafito min amatsayin sauban,, haba ko baka yarda kai nake soba? Ka zo ne ka gwadani kaga ko zan so wani na miji bayan kai?</p><p><br /></p><p>To bara kaji Khalid wallahi ban taba son wani da namijin arayuwata ba sai kai Khalid, koda kaga ina baka kula amatsayin sauban daka zo min"" to ba so bane yasa nake haka,, kyauta tawa ne, da kuma zamantowar ka amatsayin miji,, inayin hakane kada Allah ya kamani da laifi.</p><p><br /></p><p>Sauban ne ke kuka kamar karamin yaro ya dur kusa kasa, nima kuka nake sosai, nima adurkushe nake "" na karaso wajen shi tare da ,, daga kasa ina share masa hawaye,, nace stop crryiny Khalid , ni naka CE,, kuma babu mai iya raba mu"" kamanta soyayyar da mukayi, kamanta har sashen ka akaina,, to bara na tuna maka .</p><p><br /></p><p>Cewa kake shazee kin fi kudi, kinfi gida, kinfi mota, shazee ke rayuwa ce gabaki daya, shazee ina sonki kuma bazan taba rabuwa dake ba"" my d katuna fa,, na kara rungumeshi .</p><p><br /></p><p>Sauban yayi saurin fincike ni daga jikin sa tare da matsawa baya ,cikin daga murya ya ce Shahrazad karki yaudari kanki"" wlh bani bane Khalid, bani bane Khalid bani ne khalid., ya kara fashewa da kuka.</p><p><br /></p><p>Ni kuma sai girgixa kaina nake, no no no, banyarda ba,, sauban yaci gaba dacewa, shazee zamana dake ya nuna min baza ki iya zaman aure da kowani da namiji ba inba Khalid ba.</p><p><br /></p><p>Son khalid ya miki babban rami azuciyar ki"" Wanda baki ganin kowa sai shi!! Gaskiya na jinjina miki shazee, Khalid yayi dacen mata,"" kidaina yaudaren kanki danine Khalid, no bani bane kuma bazan taba zama shiba har abada,, ni sunana Muhammad sauban kamar yadda kika sani.</p><p><br /></p><p>Nace idan ba kai bane Khalid meyasa zaka dinga mun abubuwan da Khalid ke mun? Kana yawan Nuna min wasu abubuwa irin na Yaya Khalid dina.</p><p><br /></p><p>Na share hawaye na, nace tunda kace ba kai bane Khalid ,, to da alamun kasan Khalid dina , kuma yana kusa dakai"" inba haka ba to bazan taba yarda bakai bane Khalid dina, masoyin asali"" sannan kuma in ba kai bane Khalid, meyasa kwana biyu kashiga cikin damuwa,, kake mun wani irin kallo.</p><p><br /></p><p>Shazee ki fahimce ni da kyau, kin San Allah daya ne ko, to wallahi wallahi wallahi kinji na rantse bakya bina bashin rantsuwa, bantaba ganin Khalid ba,, ban sanshiba,, ban San a ina yake ba, sai ta dalilin ki nasan Khalid kuma a hoto nataba ganin shi.</p><p><br /></p><p>Kuma damuwar nan da kika ga inayi,, inayin sane, saboda ke.</p><p><br /></p><p>Nace ni kuma? Eh kefa, toh mena maka? Ba abunda kika min,, ya juya mun baya yace shazee lokacin rabuwa ta dake yazo"" dama tun asali na aure ki ne amatsayin taimako, turoni akayi"" kuma a lokacin basanki nake ba!! Duk plan ne aka shirya"" na aurekine na Dan wani lokacin"" gashi kuma zan rabu dake ,, a lokacin danaji dadin zama dake!!! Ke macece da duk namijin daya zauna dake bazai so rabuwa dake ba.</p><p><br /></p><p>To nima haka nakeji araina, amma ina rokon Allah da ya musanya mun irinki"" daga yau aikina ya kare"" ban San lokacin Dana zo wajen shi na dauke sauban da lafiyayyun mari ba guda biyu"" saura kadan ya fadi kasa.</p><p><br /></p><p>Na kama rigarsa ina jijjigawa cikin kuka nace waya turo ka ka aure ni"" me na muka daza ku zo neman aurena ,, cikin daga murya nace sauban ka fada mun !! Dama ka shigo rayuwata ne, ka kuntata min, ka Shiga tsakanina da masoyina,, kafada min waya turo ka"" ji nayi ance ni na turo shi"' juyawan dazanyi , na xaro ido waje bakina na rawa , xankira sunan nakasa, hawaye ne yakara gudu afuskata, kirjina kamar zai fashe sai harbawa yake.</p><p><br /></p><p>*Taku* *ummu* *Ruman* (nusnim)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD*❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 130 & 135</p><p>Kirjina sai harbawa yake, kamar zai fito, kafafuwa na sun kasa dauka ta nayi saurin na dafa bakin gado ""da sauri ta karaso wajena don ta kamani"" daga mata hannu nayi sama alamun ta dakata.</p><p><br /></p><p>Taja baya ta tsaya tana tsiyayar hawaye.</p><p><br /></p><p>Nace aunty amingi Ashe dake za a iya hada baki aci amanata"" amina me na miki daza ku min haka,, amingi sai da tazaro ido waje saboda yaune rana na farko da na taba kiran sunan ta kai tsaye .</p><p><br /></p><p>Naci gaba da cewa, Ashe baki son alakata da yayanki Khalid,, Ashe baza ki iya taimaka masa wajen mallakata ba? Ashe bazaki taya yayanki kishin wani ya rabe ni ba!! Haba amingi, why me na miki haka daza kisa ayimin auren mutumin da bana so'</p><p><br /></p><p>Ke kanki kin sani, Khalid kadai xuciyata keso dashi nake sha'awar aure!!! Amma ki kayi ruwa kikayi tsaki, har na auri sauban" haka nayi ta gayawa aunty amingi maganganu marasa dadi.</p><p><br /></p><p>Nace amina daga yau bani bake, har abada, tunda baki son farin cikin yayanki,, amingi ta durkusa kasa sai kuka take yi sosai, tace shazee ki fahimce ni""wlh Nafi kowa son ki aure Khalid, nayi saurin kara sowa kusa da ita na cakumi wuyar rigarta, nace karya kike muna fuka.</p><p><br /></p><p>Fatima da ni'ima da Nusaiba da khausar sukayi saurin mikewa tsaye, cikin tashin hankali" sukace, amma aunty shazee idonki ya rufe ne haka, kikewa mai sonki amingi cin mutunci haka'' hmm Ku zauna kuji kawai.</p><p><br /></p><p>Na ci gaba da cewa wlh amina kinci amanar soyayya,, na daga hannu kenan zan mari amingi,, kawai sai naji saukan mari a fuskata, daga idon da zanyi, naga sauban ne, ya mareni yana hawaye!!! Ya jani gefe tare da jefar dani akan gado, cikin bacin rai ya fara magana kamar haka.</p><p><br /></p><p>Shahrazad wai mai kika maida mutane ne? Kowa kika samu ki Mara, kuma alhalin ba abunda aka miki"" illa taimakon ki ma da akayi!! Amingi bata cancanci haka daga wajenki ba.</p><p><br /></p><p>Matar data dage wajen ne mami ki farin cikin rayuwar ki"" matar da kullum cikin kuka take akanki, matar da kullum ne man mafita take akanki, matar data hana idon ta bacci akanki, matar data hana cikin ta abinci akanki, matar da kullum take yawo akantiti da garuruwa duk akan farin cikin ki.</p><p><br /></p><p>Amma kirasa da mai zaki saka mata sai cin mutunci.</p><p><br /></p><p>To bara kiji ki bude kunnan ki da kyau, don kiji abubuwa da dama, Wanda akarshe nasan sai kinyi da kin sani.</p><p><br /></p><p>In baki manta ba, kishiyar hajiyarki wato mama indo, bata sonki da Khalid,, sai kuma yatta ta kamu da son Khalid, inda mama indo ta dau alwashin rabaki dashi, ta hadashi da nafeesa!!!</p><p><br /></p><p>Tayi asirin farko bai ka mashi ba"" sai a asiri nabiyu ne yayi tasiri.</p><p><br /></p><p>Wato a asiri na biyu, taje gun boka, don abatar mata dake kibi duniya kar aganki" ita da kawarta ma'u sukaje, ya bata wani magani da suje makabarta su Burne, amma tsohuwar makabarta, ya gar gade.</p><p><br /></p><p>Yace idan suka sa a sabuwar makabarta, to ba shakka Khalid ne zai bata, amma idan suka saka atsohuwar makabarta, to kece zaki bata.</p><p><br /></p><p>Wato sai Allah ya mantar dasu, inda suka kuskure suka saka a sabuwar makabarta"' ta dalilin haka Khalid ya bata"" su mama indo basu tashi ganewa ba, sai bayan da akace musu Khalid ya bata!!!! Ba karamin tashin hankali, mama indo tashiga ba"" saboda alokacin tana tunanin wani hali yarta nafeesa zata Shiga ba.</p><p><br /></p><p>Sai daga baya kuma nafeesan ta warke daga damuwar batan Khalid, har ta manta shi, shima ta dalilin mama indo, magani akamata ta manta shi.</p><p><br /></p><p> Shine mama indo daga baya ta dinga Neman hanyar daza a kuntata maki, tunda taga son Khalid ya hanaki tsayawa da kowa"" shiyasa kullum sai taje wajen babanki tayi ta mashi hudubar shaidanu, tace ana xaginsu agari, don sunki aurar dake, shiko babanku abun na damunshi"' shine yayanke shawaran da ki fitar da miji, yaje yasa mu baban Khalid ya fada masa abunda mutanan gari ke cewa.</p><p><br /></p><p>Baban Khalid baiji dadi ba, shima yasanarwa da matarsa aunty hauwa da yarsa amingi"" tundaga wannan lokacin amingi ta dauki damaran taimaka miki, batare da sanin kowa ba, don tasan matsalar gidanku, don tana gudun kar mama indo tabi wata hanyar ta kuntata maki, tunda dama tasan da maganar maganin nan da aka zuba mawa Khalid azauren gidanku.</p><p><br /></p><p>Ana haka, kawar mama indo wato ma'u, ta cewa mama indo me zai hana danta ya auri ki,, bayan Dan nata rikakkan barawo ne, gashi mashayi ne,, aiko ana haka amingi tasamu labarin abunda su mama indo suke shiryawa.</p><p><br /></p><p>Dama a lokacin tazo ganin gidane sai taji mummunar labarin nan,, aiko ko dadewa batayi ba ta koma abuja gidanta, tasaka mijinta agaba sai kuka take, daya taimaka mata, karki fada wani hali.</p><p><br /></p><p>Shine mijinta yace yana da Dan uwa yaron kanin baban sa mai suna Muhammad sauban, (wato ni),, zamu mishi magana akan dayaxo Neman auren ki, kuma yafito amatsayin ustaz, don mama indo ta amince, dama bataso kije gidan Hutu,, amma akwai sharadi a auren, zan dau alkhawarin bazan taba yarda wani auratayya tashiga tsakanina dake ba.</p><p><br /></p><p>Zan zauna dakene, har lokacin da Allah zaisa aga Khalid, in kuma baya Raye, sai afada maki gaskiya, in zaki iya zama dani amatsayin masoyi shi kenan, amma dama shekara biyu. Aka daukar mana a auren mu"" don baza mu cigaba dazama irin haka ba , amingi yaji dadin shawarar mijinta, kuma ta amince"" da haka har suka min magana, ni kuma dayake metausayi ne, na amince, zan dauki wannan kasadar,, don wannan babbar kasada CE.</p><p><br /></p><p>Mukayi mawa iyayena bayani suma suka yarda, don suna son aunty amingi, don macece mai son dangin mijinta.</p><p><br /></p><p>Da hakane har nazo wajenki,, dama kuma nafeesa tana zuwa layinmu, INA ganinta, kuma duk lokacin daza mu hadu amatsayin ustaz take ganina, wannan kuma duk shirin amingi ne,, don yadda zamu samune musa mu Shiga wajen mama indo.</p><p><br /></p><p>Sannan kuma amingi ta Nuna min hoton Khalid, da kuma abubuwan daya ke miki , duk aunty amingi ta fada min in dinga yimiki, don hankali ki ya karkato wajena"" sai Allah ya daurani akan yan gidanku, aka amince dani"" kece kawai kika ki aminta dani.</p><p><br /></p><p>Sai daga baya daza ki gudu, Allah ya taimake mu, amingi ta ganki, da bata ganki ba da bamusan ya zamuyi ba, da haka su amingi da yan uwanta suka shawo kanki kika karbi aurena badan kin soba.</p><p><br /></p><p>Mu kuma muna ta Neman Khalid don har karatu mukasa ake mana, don ance mana asiri akayiwa Khalid"" haka amingi take ta fafutukar nemo Khalid ba dare ba rana,, ko wayar da kike ki nakeyi , da amingi nakeyi, akan na rike amanar yayanta .</p><p><br /></p><p>Yanxu haka danake miki magana mama indo tana can gida cikin tashin hankali saboda yarta ta bace, shine duk ta tona ma kanta asiri"" shi kuma Khalid munganshi,nayi saurin mikewa da kyar na karasa wajen sa, adaburce nace yan yan yan in in Ina bakina sai rawa yake, yace shazee kiyi hakuri Khal___ bai karasa ba nafadi kasa bana numfashi ,"" amingi da sauban sai girgixani suke tare da samun ruwa amma ina ban farfado ba.</p><p><br /></p><p>*TAKU* *UMMU* *RUMAN* (Nusnim)</p><p>08064481931</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 135 & 140</p><p>Sauban ya dauke ni,, yayin da amingi tayi waje da sauri don bude mota, yana zuwa yasaka ni aciki" yashiga amingi ma ta Shiga, sai asibitin garkuwa"" da gudu gudu aka karbe mu don taimakon rai na.</p><p><br /></p><p>Da kyar aka samu numfashi na, sannan akamin alluran bacci, likitan yace nanda anjima kadan zan farfado,, yawan damuwa ne yasa min dogon suma,, Allah ne kawai ya kare ni"" sannan hankalin su amingi ya kwanta.</p><p><br /></p><p>Can da yamma, nafara bude idona, sauban ne ya lura da hakan"" yayi saurin kara sowa wajen, aunty amingi ma tana ganin hakan itama ta karaso"" suna sannu shazee, ido kawai nabisu dashi, alamun mai son tuno wani Abu.</p><p><br /></p><p>Ina kokarin tashi amingi ta taimaka min tasa min pilo abayana na jingina"" sai binsu nake da kallo sunnu suke tace mun </p><p><br /></p><p>Sauban yace ina yake miki ciwo yanxu na girgiza kai na, alamun babu "" nazuba musu ido, ina kallon inda nake"" azuciyata nace mai ya kawo ni asibiti? Can na dan yi shiru na Shiga tunani" tuni na tuno abunda ya faru na rushe da kuka ina cewa shi kenan ya mutu ya barni.</p><p><br /></p><p>Nima yazama dole in mutum" amingi ne ta rungumeni tana bubbuga min baya na" kiyi hakuri shazee, Khalid dinki bai mutu ba"" nayi saurin daga ido ina kallon ta nace da gaske bai mutu ba? Tace eh!! Sai ga murmushi ya kubuce mun a fuskata sai washe baki nake.</p><p><br /></p><p>Amingi tace sai dai baida lafiya yana kwance a gida , amma yakusan tashi tunda an mishi turare, da magungunan Islamic chemist "" don tun barin shi gida , yafita hayacin sa"" sunanki kawai yake kira yanxu , alamun sauki yazo, tunda da baya magana.</p><p><br /></p><p>Nace Allah sarki Yaya Nah. Mai sona, nace aunty amingi tayaya kika Ganshi"" tace akwai watarana, inata mafarkin sa , yana kirana acikin garin kano.</p><p><br /></p><p>Aiko inatashi daga bacci nafada mawa mijina. Yace shirmen yace shirmen nafarki ne,, nikuma nace INA da gaske ne Dan uwana yana Neman taimakona"" shine fa muka shirya muka kama hanyar kano , sai dube dube nake a hanya, da haka har muka iso cikin garin kano, shima inata waige waige ,, kamar ance in waiga hannun dama na.</p><p><br /></p><p>Na hango wani mutum cikin bola yana cin abinci hannu baka" nacewa mijina ya dakatar da motan , nayi saurin fita shima ya biyoni"" mukayi saurin karasawa inda yake "" wazan gani inba Khalid ba, na fadi akasa sai kuka nakeyi"" shiku Khalid ganin mutane agabansa kuma yaga ina kuka,, ya karaso inda nake, yazo yana min dariya hannun sa rike da Leda wai zai share min hawaye"" duk tsorone ya cika xuciyata"" haka ya goge mun hawayena, yana girgixa min kai alamun indaina kuka"" a haka dai muka mashi wayau mukasa shi amota tare da dawowa Kaduna,, kai tsaye wajen mai magani muka kaishi.</p><p><br /></p><p>Sai da aka mai rukiya, aka babbashi magani, yanxu haka yana GDA yana kwance, sati daya baya magana, sai yau da safen nan ,mukaji yana Shahrazad Shahrazad"" sunanki kawai yake ambato" dalilin dayasa nakira sauban na fada masa, daya kawo ki,, sai naji shiru Baku zo, shine nazo da kaina don ganin ko lafiya, sai natarar da Ku cikin tashin hankali.</p><p><br /></p><p>Sauban yace shazee yanxu kin tabbatar da amingi mai kaunar kice ko, kin tabbatar tafi kowa sanki da Khalid ko.</p><p><br /></p><p>Na fashe da kuka, ina aunty amingi kiya fe min Dan Allah, sharrin zuciya CE tasani fada maganganu marasa dadi da kuma son Khalid!!! Kiyi hakuri kiyi hakuri kiyi hakuri ki yafeni!!! Natuba na dinga bubbuga kaina ajikin gadon asibitin.</p><p><br /></p><p>Aunty amingi tayi saurin hanani tare da rungumoni, tace bakomai shazee , wallahi ban rike ki araina ba , nasan bayin kanki bane"" kuma na tabbatar komin rintsi baza ki taba gujewa Dan uwana ba"" gaskiya Khalid yayi dace , kin zama abun alfahari a family din mu"" Shahrazad muna sonki sosai .</p><p><br /></p><p>Nima ina son Ku aunty amingi, bayan mutuwar hajiyata, Ku kuka zame mun uwata, nima ina alfahari da kasan cewa a cikin Ku, muka kara rungume juna muna kuka.</p><p><br /></p><p>Sauban ne ya sulale ya fita waje sakamakon kukan daya ci karfinsa"" yasami inda ba kowa ya tsugunna sai kuka yake sosai"" yana fadin ya Allah!!! Ka cire mun son abunda bai dace dani ba'" ya Allah kana gani taimako nayi niyyan yi tsakani da Allah"" ya Allah kaji tausayi na ka cire mun son shazee ka musanya mun da wata.</p><p><br /></p><p>Kabani hakuri da juriya allahumma amin.</p><p><br /></p><p>Mu kuwa ba musan sauban baya nan ba, saida muka gama kukan mu, har muka Shiga hira, nake tambayan aunty amingi,, yanxu kowa yasan Khalid ya dawo nice kawai ban sani ba sai yanxu "" tace eh ke kadai ne baki sani ba, ance kar afada maki, don yanxu ke matar wani ce"" basu San auren ki, ni na hada ba.</p><p><br /></p><p>Amma yanxu in muka koma gida zan fada masu,, nace dama ance ka gina ramin mugunta dai dai kai"" kuma dama ance abunda ka shuka shi zaka girba .</p><p><br /></p><p>Amma bazan taba yafewa mama indo ba, sai Allah yasaka mana tunda tajefa mu wani hali"" amingi tace , karkice haka shazee Allah yana son mai yafiya, kiya fe mata, tunda gashi Allah ya Nina mata kuranta, gatacan kamar mahaukaciya take" saboda bacewar yarta nafeesa, kuma kinsan duk cikin ya'yanta ba Wanda take so irin nafeesa""" kuma hannun ka baya rubewa kayardar, tunda komin Yaya ne, mama indo jininki CE"" fatan dai kiyi musu addu'a Allah ya shirya su, ya kuma bayyana nafeesa a duk inda take, nace amin.</p><p><br /></p><p>Sauban ne yashigo fuskar sa dauke da murmushin karfin hali, yace dafatan dai kun shirya, suka ce eh suna dariya.</p><p><br /></p><p>Na kalli sauban da kyau nace sauban , ina rokan ka da kaima kaya fe min, don ban kyauta maka ba, kaima ka taimake ni arayuwa, samun irinka yana da wuya, na jinjina maka sauban ba karamin namijin kokari kayi ba , nagode nagode sauban Allah ubangiji ya saka da alkhairi ya baka mata mai kaunar ka,, na fashe da kuka"" yayi saurin kara sowa wajena, har zai rungume ni, sai kuma ya fasa tare da kakalo murmushin karfin hali, yasa hannu ya dago habata muka kura mawa juna ido, yasa Dan yatsan sa ya share mun hawaye na,, yayin da ni kuma nake kallon kaunata cikin kwayar idon sa.</p><p><br /></p><p>Kirjina ne yafara harbawa, na fashe da kuka, amingi tayi saurin barin dakin tana hawaye, tare da fadin ya Allah wayyo ni amina nasaka bawan Allah cikin damuwa , gashi daga gani ya kamu da son shazee,, ya Allah kayi gaggawan cire mishi.</p><p><br /></p><p>Cikin murya can kasa kasa yace shazee bakomai ni ban rikeki da komai ba, kidaina kuka, don bana son kukan nan"" nace to,, na kara kallon sa nace sauban ka kamu da sona ko?</p><p><br /></p><p>Yayi saurin cewa shazee kin San abunda kike fada kuwa ,, ni bantaba ji INA sonki ba ko kadan, hasalima inada Wanda nake so murmushi nayi,, nakalle shi nakuma yin murmushi"" nace shi kenan.</p><p><br /></p><p>Likita ya sallame ni,, muka dunguma sai gidan su Yaya Khalid ko gama tsayawa motar batayi ba, na fito da gudu nashiga cikin gida, ina Shiga parlo naci karo da aunty Hauwa da babana da baban Khalid da mijin aunty amingi sai iyayen sauban, duk suna zaune, nafada jikin aunty Hauwa na saki kuka mai tsuma zuciya,aunty Hauwa Ashe anga Khalid, eh shazee , Allah y bayyana mana shi.</p><p><br /></p><p>Su sauban suka karaso falon, aka gaggaisa , sannan mijin aunty amingi yafara yi musu bayani akan auren na da sauban, ta yadda akayishi,, dukkan su sun girgixa kuma sun jinjinawa amingi da sauban"" tare da tausaya mawa sauban din.</p><p><br /></p><p>Baban Khalid yace amma sauban ba amaka adalci ba idan aka rabaka da MATAR ka, babana ma yace hakane.</p><p><br /></p><p>Sauban yace wlh ba komai, yayi musu karya akwai wacce yake so tana jiranshi yanxu hakan, dama ya barine ya gama wannan aikin , sukace to tunda haka kace mungode, yaciro takardan saki yabani, na karba ina tausayinshi.</p><p><br /></p><p>Yayi musu sallama yace yana da uxuri yayi saurin fita, ni kuma da gudu na tashi na fada dakin Khalid kwance na ganshi nafada kanshi, ina kuka, yayanah, farin cikina my d dina, ina kaunar ka"" kamar daga sama yaji muryan da bazai taba mantawa ba, ya bude ido"" yana sha sha shazee dina, ya idonshi ya bude akaina, wani karfine ya zo mashi ya rungumeni, yana kuka ina kuka.</p><p><br /></p><p>Sauban dakyar ya hau motarsa ya je gida,, dakina ya wuce, ya dauko kayan bacci na, ya rungume, yana kuka sosai , yana tuna ranar danayi ciwo" da ranar dana rungumeshi, kuka yake yana kiran Shahrazad Shahrazad Shahrazad.</p><p><br /></p><p>*taku* *Ummu* *Ruman* (nusnim)</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 140 & 145</p><p>Sauban yace Shahrazad, yanxu shikenan kin tafi kin barni kenan, wallahi ina sonki shazee ina kaunarki, ban San ya zanyi ba"" amma xuciyata bata min adalci ba'' me yasa zata kamu da abunda bai dace dani ba.</p><p><br /></p><p>Sadiqa ce tayi sallama tashigo don ammin su ce ta turo ta, don tace tazo taga halin da yake ciki"" ganin halin dayake ciki yasa takarasa wajen shi,, tana bros please ka daina kukan nan, kayi hakuri ka dau dangana, watarana sai labarin,, Allah na kallon ka bazai taba barin ka haka ba.</p><p><br /></p><p>Yace Sadiqa lallai xuciyata ta kamu da son shazee, cikin lokaci kankani,, gashi yanxu tamin nisa, amma bakomai, Allah ya musanya mun amin bros" zaka sha mamakin kalan matar dazaka aura, Allah ya tabbatar kanwata.</p><p><br /></p><p>Fatima tace aunty shazee gaskiya ni banji dadin rabuwan Ku da sauban ba"" wlh duk tausayinsa ya kamani, nifa Nafi sonki dashi fa" </p><p><br /></p><p>Khausar tayi saurin cewa haba aunty Fatima, karkiyi son zuciya mana" idan aunty shazee ta zabi sauban, to gaskiya batayiwa Khalid adalci ba, kina ga a tasanadiyar ta, ya fada cikin wannan halin"" da baice yana sonta ba, to dahakan bazata kasance dashi ba"" kuma fa yan uwanshi suka dage kan nema mata farin ciki"" dabadan aunty amingi ba, da bamusan wani hali aunty shazee zata fada ba"" gaskiya bakaramin kokari aunty amingi tayi ba, mace kamar namiji"" Allah ubangiji yasaka mata da alkhairi ameen.</p><p><br /></p><p>Ni'ima tace tabbas maganar ki gaskiyace khausar ana barin halal don kunya,, kuma gsky sauban ya masu halacci.</p><p><br /></p><p>Nusaiba tace hakikanin gaskiya sauban yayi jarumta, shekara daya da rabi kana zaune da mace a gida daya, kuma abunda ya hadaku da ita na auratayya"" gskya na jinjina mawa sauban, don ba karamin kasada yayi ba"" sai gani sukayi Nusaiba na kuka" shazee tace Nusaiba lafiya kike kuka, Nusaiba tayi murmushin yake kawai.</p><p><br /></p><p>Nim tace aunty shazee muna jinki cigaba</p><p><br /></p><p>Nida yayana muna zaune kamar zamu hadiye junan mu, sai ga amingi ta shigo da dakin, tana cewa hmm romeo and Juliet anan anfara sana'an ko"" to mudai kar a kona mana gida" dukkan mu muka kwace da dariya .</p><p><br /></p><p>Sai ga aunty Hauwa tashigo ita da Umar , umar ne ya karaso wajen Khalid tare da rungumeshi" yana hawayen farin ciki!!! Yace wato Yaya aunty shazee ta dagaka, da ko tashi bakayi, wato soyayya ta dagaka yanxu.</p><p><br /></p><p>Khalid ya kaimai duka abaya,tare da cewa lallai Umar yaushe kazama hakane, hahaha ya Khalid ni yanxu na girma fa, sanin dda kamin!!! Lallai kam.</p><p><br /></p><p>Nandai aka bamawa Khalid labarin abubuwan da suka faru'' yayi kuka sosai, tare da tausaya mawa sauban,, lallai ya kamata ya hadu da sauban** sannan kuma ya jinjina mawa kanwarsa amingi"" ya tabbatar yasami Yar' uwa mai kaunar sa sosai, ya rungume amingi suna kukan farin ciki"" sannan ya dinga bina da ido ya rasa da mai zai saka min, muna haka sai mijin amingi ya shigo ya, sukayi musabaha da Khalid. Ya mishi godiya.</p><p><br /></p><p>Aunty amingi ne tace intaso mushiga gidan mu, nace mata baza Niba ni anan zan kwana, aunty Hauwa tace, ai zakije ne ki dawo, zaki gaida mama indo da jiki don bata da lafiya,, sai da Khalid yasa baki tukunna na yarda naje.</p><p><br /></p><p>Muna tafe muna Dan hiran mu da aunty amingi har muka karasa , akofan gida naga baba na yana zaune, muka gaisa dashi, yace me kikazoyi an an, ai acan zaki kwana, nace nazo duba jikin mama indo ne,, yace Allah sarki kin kyauta da baki riketa aranki ba"" Allah ya miki albarka, mukace amin.</p><p><br /></p><p>Sannan muka karasa ciki, tana tsakar gida akwance ita da ya'yanta maza sai kuma kanwarta, tana ganina ta fashe da kuka, muka karasa inda suke tare da gaggaisawa, nan mama indo ta rokeni gafara na yafe mata, tare da rokon Allah ya bayyana nafeesa a duk inda take, dukkan mu mukace ameen.</p><p><br /></p><p>Khalid mun hadashi da sauban inda ya masa godiya sosai tare da nuna masa farin cikin sa"" sannan sauban yacewa Khalid da ya rikeni amana" kar yasake ya bari na kubuce masa akaro na biyu, don bakaramin dace yayi ba"" Khalid yace nagode sosai sauban Allah ya musanya maka da mafi alkhairi yace amin, tundaga lokacin Khalid da sauban suka zama aminai""</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tun daga ranar rayuwata tafara canxawa, damuwata ta tafi"" illa Abu daya wato shine, sauban ina so in sama masa mata , wacce zata kwantar masa da hankali, ta zauna dashi tsakani da Allah, amma ina mun kawo masa yan mata kala kala shi yace ba wacce ta masa, shi yasan matar sa tananan zuwa insha allahu, haka nan muka zuba masa ido ba don mun so ba, don da mun so a hada bikin mu tare.</p><p><br /></p><p>Nice zaune da Yaya Khalid a parlo muna hira, yace my d mu godewa Allah, daya kara hadamu akaro nabiyu, lallai Allah na sanmu ,hakane my d.</p><p><br /></p><p>Khalid yace shazee ganin ki kan Kore min duk wani bakin cikin datake dauke da xuciyata, don haka nakira ki da wacce tafi kowa sa'a a duniya!! Ina sonki koma zanci ga ba sonki koda zaki juya min baya.</p><p><br /></p><p>Yayana bazan taba iya juya maka baya ba , sonka ya zamo walwalata , ya zamo Bargon rufata, yayanah bani da aiki akowace rana sai na begenka, bazan iya mallaka mawa wani namiji soyayyata ba inba kaiba.</p><p><br /></p><p>Nagode my xclusive one shazee be loved one queen you are my royal highness, my excellency my lady" fiency love you , my wife to be insha arrahman.</p><p><br /></p><p>Nace tanx habibty Nah ana hubbiq tartir.</p><p><br /></p><p>Akwana atashi ba wuya, an saka bikin mu, nanda sati biyu, sai shirye shirye akeyi" yayin da sauban yake shirin barin kasar don baya so ayi bikin yana kasar, don har yanxu zuciyar sa bata gama warkewa daga sona ba"" mama indo ta Dan sami lfy don da itama ake shirye shiryen bikin, amma tunanin yatta bai saketa ba" a kullum addu'a ake Allah ya bayyana nafeesa, ana gobe bikin mu sauban yazo gida wajen mu ya kawo mana gift din bikin mu"" bayan mun gaisa, dashi, yace min ina angon nawa, nace ya fita, OK kila bazamu samu haduwa ba don gobe zan wuce u.s don akwai abunda zanyi"" na zuba mashi ido Ina kallon sa " nace sauban ni nasan saboda bikin mu zaka tafi, kuma bazan hanaka tafiya ba, amma karka manta ka kasance mai tawakkali, nasan haryanzu kana sona sauban kuma saboda nine kakiyin aure, amma ina kara baka hakuri Dana shigo rayuwarka ban maka adalci ba, kayi hakuri sauban pls karka rikeni aranka.</p><p><br /></p><p>Yayi saurin cewa shazee ki daina damun kanki, wlh ban rike kiba, kuma baki da laifi, ba yadda Allah bayayi, kowa da tasa kaddaran hakane"" yace ka gift dina adinga sakamawa Khalid nasan zayyaba, nakarba ledan ina duddubawa ne, sai da kunya takamani, rigunan bacci ne masu kyau, da turare, sai kuma kudi dubu dari, daya bani"" nayi godiya sosai naji dadi sosai araina.</p><p><br /></p><p>Yace wannan kuma ki ijyewa Khalid, shima turare ne sai agogo mai kyau, nakara masa godiya, sannan na rakasa mota yashiga, yana daga mun hannu nima ina daga masa.</p><p><br /></p><p>Intakai ta muku yau jumma'a itace ranar da aka daura auren khalid tanko soba, da amaryar sa SHAHRAZAD abdulmaleek, , bakaramin dadi masoyannan sukaji ba.</p><p><br /></p><p>Ankaini gidan mijina dake kabala, gidane nagani nafada hadade, gidan sama, tsayawa fadan kyanshi bata bakina, gani da ido shi yafi dacewa,, kannan sauban suna cikin mutanan da suka min kawance don aunty amingi, ta bar musu wannan fannin" haka mutanan dasu ka kawoni sukaita yabon gdan , harda mama indo acikin kawoni gidan mijina, sai hawaye kawai takeyi, tace Allah sarki natauyewa yarinyar nan hakinta, da yanxu tana gidan nan da yaranta, amma nabi sharrin zuciya na aikata abunda bai dace ba. Gashi ya koma kaina.</p><p><br /></p><p>Yan kawo Amarya sun watse, sai Amarya kadai adakinta, Khalid ne yashigo cikin sallama na amsa masa, yasha fararen kaya, ba karamin kyau yayi ba </p><p><br /></p><p>Ya zauna kusa dani, tare da janyoni jikinsa, ya cire mun mayafina yana kallon yace baby kin hadu fa"" yacire Dan kwalina, yana Shafa kaina tare da shinshinawa, yana lumshe ido, ni kuma na kara lamo akirjin sa, yace my d yau ranace ta farin cikin mu, tashi muje muyi sallah mugodewa Allah , nace to, na yunkura zan tashi ya dagani cak, sai toilet dakansa ya min alwala, sannan ya daukoni, ya shimfida mana abun sallah!!!! Mukayi sallah bayan mun Idar yayi mana addu"zaman lfy.</p><p><br /></p><p>Sannan ya tashi ya dauko mana kazar mu da drinks,, ya zaunar dani kan cinyar sa, yana, bani ina ci, shima haka nabashi, da haka har muka koshi, yace my d bara naje na miki wanka"" na zaro ido waje nace habadai sai kace karamar yarinya"" yace to ni sai na maki, bai jira abunda zance ba ya sunku ceni, sai toilet ina zillo tare da kukan shagwaba, nace nidai ka saukeni Allah da kaina zanyi"" da kyar ya kyaleni, ya fita yana dariyar mugunta yace yarinya zaki sani ne ai. </p><p><br /></p><p>Akwatina ya bude ya fito min da rigar barci cikin wayanda sauban ya kawo min, , rigar daidai cinya, kuma shara shara CE" ana ganin komai na mutum wuyanta abude, dai dai cibiya akwai rami zaka iya sa hannu"" sannan kuma dai dai inda kan mamanta zai zauna shima andan mai rami, inkasa zai fito waje"" kallon rigan yayi yana dariya, sannan ya ijye ya fita zuwa dakin sa don watsa ruwa.</p><p><br /></p><p>Bayan nafito nayi Shafa ko ina na jikina sai da na budesa da kamshi,, kayan bacci naga kan gadona, na dauka, Rigan tamin kyau, ballura da hujin dake jikin Rigan ba"" nasaka Rigan, na kalli kaina a madubi nace subhanallah, dai dai kan mamana awaje yake, kamar zai tsole maka ido, dai dai cibiyata shima akwai huji zaka iya sa hannu"".</p><p><br /></p><p>Gaba nane ya dinga faduwa ni gsky bazan iya kallon yayana da wannan kayan jikin nawa ba" na juya kenan naga mutum tsaye saura kadan in sake ihu, da sauri ya manna ni jikin bango yasaka bakin sa cikin nawa yana wasa da harshena, sai aika min sakwanni yake"" tare da Shafa ni, cikin Shafa ni dayake, hannun sa yaji ya tabo wani Dan karamin Abu , ya kara tabawa kan mamanane daya fitowaje, aiko tuni yara murzasu yana gurnani, tureshi nake Amman ina yafi karfina, gashi ya mannani jikin Bango kamar za mushige, ga kunya duk tabi ta hanani sukuni"" da haka har ya sauko da bakinsa kan kirjina, yafara caccaka da hakoransa yana gurnani dayan hannu sa ne yakai kan cibiyata.</p><p><br /></p><p>*taku* *Ummu* *ruman* (nusnim)</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 150 & 155</p><p>Ni'ima tace aunty shazee yanxu ina sauban, shazee tace yanxu ko zaki ga ya shigo bata gama rufe baki ba yayi sallama" ga baki dayan su ido suka tsurawa bakin kofan shigowa" Shahrazad tace wa'alaikumus salam.</p><p><br /></p><p>Tace Dan halak kaki ambato yanxun nan muka gama maganar ka, ya karatso ciki yana murmushi yace wato gulmata kikeyi"" daga sama sukaji murya abayan su , akace haba dai zaujatul da'iman bata gulma, ya karaso yana murmushi, suka rungume juna shida sauban, khalid ne" Khalid yace hmm mutanan u.s wato kaki zama kasan ka ko" to zamu cika taranka"</p><p><br /></p><p>Shazee tace my d duk yadda akayi yan matan u.s ne suka rike shi" sauban ya tuntsire da dariya, yace shazee kin fara ko, bara na kira amingi itace daidai dake, Khalid yace Ashe zamu muku runduna kenan.</p><p><br /></p><p>Fatima, NI'IMAH, Nusaiba, khausar haka suka zuba ido suna kallon 3 star din nan cikin birgewa , sun matukar basu sha'awa, tare da mamaki.</p><p><br /></p><p>Shazee CE tace AF na mance fa, kun sani na shagala ina biye muku, alhalin inada baki" sauban ne da Khalid suka jiyo inda su Fatima ke zaune" tuni idanuwan saban ya sarke danata, yayin da itama haka, tun shigowar sa, gabanta ke harbawa" sai kuma yanxu da sukayi 4eyes " ita dashi sukace ya ilahi azukatan su.</p><p><br /></p><p>Shahrazad tace my friends ga Yaya Khalid dina Angona, sannan kuma ga yayana Muhammad sauban" su Fatima sukayi murmushi tare da gaida sauban da Khalid, suka amsa cikin fara'a, shazee ta kalli sauban da Khalid tace wayannan kawaye nane da muka hadu a skull din mu, sakamakon wani hali da suka fada kwatan kwacin nawa.</p><p><br /></p><p>Khalid yace garin Yaya hakan ta faru, nan dukan su suka zauna shazee ta warware wa sauban da Khalid komai"" sun tausaya musu kuma basuji dadi ba.</p><p><br /></p><p>Khalid da sauban suka masu nasiha da fada, tare da cewa insha allahu zasu taimake su , zasu maida su gidan iyayen su "" sannan kuma zasu dawo gidan Shahrazad da zama, kafin asan abunda za ayi" sauban yace ke Fatima da NI'IMAH, auren dake kanku shine Matsala dole sai mun shigo da iyayen mu cikin lamarinku, don asan yadda za abullowa lamarin"" don wanna. Maganar babbace.</p><p><br /></p><p>Fatima tace mun gode sosai tabbas haduwar mu da aunty shazee alkhairine" da badan itaba da ba Masan kuskuren da muka aikata ba.</p><p><br /></p><p>Ni'ima tace tabbas hakane, yanxu duk hankalin mu ya koma ga iyayen mu , don musan halin da suke ciki.</p><p><br /></p><p>Khausar tace mungode sosai gsky munji dadin labarin Ku mai dauke da darasi, Allah ubangiji ya kara hada kanku,, aunty shazee bamu da kamar ki" kin taimake mu" Allah ubangiji ya barki da Yaya Khalid dinki ,, Yaya sauban kuma Allah ubangiji yayi maka zabi na alkhairi, kai saudaki ne' inama inama?</p><p><br /></p><p>Nusaiba CE ta fashe da kuka yayin da kowa ya juyo wajenta hankalin su tashe, cikin rudewa Fatima da shazee suka ce lafiya Nusaiba meke damunki, ganin kukan na Neman fin karfinta, ta tashi ta fita da gudu waje, tare da toshe bakinta.</p><p><br /></p><p>Su shazee ne zasu bita Khalid ya dakatar dasu yace kukyaleta, kar kubita tana bukatan kemewa, akwai abunda ke damunta.</p><p><br /></p><p>Ni'imah tace tabbas akwai abunda ke damun Nusaiba, tun lokacin da aunty shazee ke bamu labarin ta, tashiga wani hali, Fatima tace tabbas hakane nima ina ganinta ta gefen ido " a lokacin naso na tambayeta kuma sai na share.</p><p><br /></p><p>Shahrazad tace oh ni yasu meke damun Nusaiba, bayan sauban yagama jin su ya sulale ya fita waje, yayin da Nusaiba ta jingine jikin mota, Ashe motan sauban ne, yazo zai Shiga ya wuce gida don yara meke damunsa" rabon dayaji wannan yanayin ya manta, sai kuma yanxu da idonsa yayi arba Dana ta kwayar idon ,zai bude motar kenan yaji shashshekar kuka tare da cewa, wayyo Allah ni Nusaiba, meyasa xuciyata zaki min haka, daga jin labarin sa sai kisa min son sa" wlh ina son sauban ina kaunar Muhammad"" yadda take fadar sunan yaji duk duniya babu macen data iya kiran sunanshi.</p><p><br /></p><p>Nan ta durkusa tana kuka mai tsuma zuciya, yayi saurin bude mota batare dataji ba, ya zagayo inda take, hannun sa yana rawa yasa ya dagota, daga kasa" zabura tayi" don kallon waye ido hudu sukayi"" idon sa jajur, itama haka, sun dau mintina suna kallon juna, yayi mata nuni da hannu tashiga gaban mota ta zauna" ba gardama Nusaiba tashiga.</p><p><br /></p><p>Ta zauna tare da kifa kanta kan cinyoyinta , takara fashewa,, yace ya ilahi,, yace Nusaiba , ta dago tana kallon sa, tare da cewa na'am.</p><p><br /></p><p>Yace meke damunki har kike kuka haka, me aka miki, pls ki fada min kinji, cikin raunin murya yake magana.</p><p><br /></p><p>Takalleshi da kyau tana magana acikin zuciyarta, tana cewa sauban cikin lokaci kankani, xuciyata ta jarabtu da sonka, gashi nikuma ba ajinka bace, , yace injiwa yace ke ba ajinane ba"" Ashe maganar xucin da take yafito fili tayi saurin rufe bakin, tare da zaro idanu waje, yayi mata wani irin murmushi mai mika sako ya juyo dakai, tare da rike hannun ta yace Nusaiba nasan sona kike"", kuma kin Riga da kin samu don shigo wata gidan xuciyata tamin arba da matata uwar ya'yana" nima haka Nusaiba ina sonki ina kaunar ki.</p><p><br /></p><p>Bantaba tunanin zan samu wacce zanso ba bayan shazee sai gashi ban ma taba jin yanayin danakeji ayanxuba.</p><p><br /></p><p>Ya kara rausayar da kansa kasa yace nuscy zaki auri tuxuru, zaki zauna dani, ina kaunar ki nusaiba"".</p><p><br /></p><p>Nusaiba ce ke murmushi tare da rufe fuskarta, ,tana murna, yace ki bani amsa mana.</p><p><br /></p><p>Dakyar ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da ya sunta tace"" a hakan naga tuxuron na haukace ason sa, ina sonka zan zauna dakai har abada, yace promise tace yes promise nusban ever in love.</p><p><br /></p><p>Kawai basu Ankara ba sukaji shewa da tafi, shazee ta rungume Khalid dinta, sai murna suke, Khalid yace lallai Allah ya amsa addu'ar mu"" komai lokacine sai Allah yayi.</p><p><br /></p><p>Nusaiba wani uban kunya taji, shiko sauban ko ajikinsa" su Fatima sukace wato dama Nusaiba ciwon sune ya kamaki, suka kwashe da dariya"" Nusaiba jitayi kamar kasa ya bude ta rufe kanta.</p><p><br /></p><p>Aiko sauban ganin iskancin da suke mata, yayi wa motar key yaja da gudu ya bar gidan, Khalid sai cewa yake kai mallam ba afa daura auren ba daza ka tafi mana da ita.</p><p><br /></p><p>Me shazee zatayi inba dariya ba" khausar tace abun mamaki baya karewa, ni dama nayi tunanin haka"" Nusaiba jin ana tafiya amota ta dago ido tana kallon sa cikin mamaki.</p><p><br /></p><p>To INA zasu</p><p><br /></p><p>*taku* *ummu* *Ruman* muyi hakuri da wannan wlh ban jin dadi ne.</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 145 & 150</p><p><br /></p><p>Dayan hannun sa na kan cibiya ta sai wasa yake dashi shi, yana min tafiyar tsusa, danaga abun na son ya wuce gona da iri wani karfi ya zomin na Dan ture shi kadan, tare da fara kukan shagwaba, shiko duk a wahalce, sai bubbuga kafata nakeyi"" tare da cewa Yaya Nah tsoro fa nakeji" shiko haka ya zuba min ido yana kallona saka makon bubbuga kafan da nakeyi, haka kirjina ya dinga sama yana kasa, ko ina sai rawa yake"" ni shaf na manta ma " kalan kayan dake jikina.</p><p><br /></p><p>Cikin kasa kasa da murya Khalid yace in bakyaso in miki komai ina so kimin tafiya daga nan zuwa bakin kofa in gani"" sai a lokacin na kalli kayan dake jikina"" nayi saurin nasa hannu na don kare jikina" tare da cewa wayyo Allah.</p><p><br /></p><p>Yayi dariya yace na yaushe kuma, ai naga kayana"" yanxu in baki so in kara ta baki to kiyi mun abunda nace miki inko ba haka ba" zaki sha mamaki.</p><p><br /></p><p>Dayake ina tsoro Dan yi shiru ina tunani gani nayi kamar yana alaman tashi , ai ban San lokacin Dana fara tafiya ba " na juya baya ko ina na jikina sai girgixa yake"" shiko sai lashe leben sa yake.</p><p><br /></p><p>Aiko ban Ankara ba naji an fisgoni nafada jikinsa, nace wayyo my pls ka kyaleni wlh tsoro nakeji" yace karki damu baza kiji zafi ba" cikin dabara ya cire mun rigata, yashi ga kissing na ko ina na jikina, hannu sa na sarrafani, Niko mutuwar tsaye nayi, danaji bakina sa kan na Fulani na, tuni na sake masa jikina, wasa yake dani baije ga babban hanya ba"" sai da yasa na jiki na kamu Allah Allah nake ____ ? Uhmm Ku karasa kayan Ku cool shugaba, Yar Mulki rabi'ah, nan kukafi auki.</p><p><br /></p><p>Asuba ta gari, khalid ne yatashi yayi wanka, ya dauro alwala, ya gabatar da sallah "" ya tashe ni, da kyar na bude idona don bacci ne a idona SBD ban samu bacci ba jiya, da kyar na diro kafafuwata kasa zan tashi na sake wata Yar kara, da sauri ya karaso inda nake yace sannu ko my baby, cak ya daukeni, sai toilet y direni cikin ruwan da ya hada mun, shi ya min wankan Niko sai kara langwabewa nake.</p><p><br /></p><p>Ya gasa min jikina, sannan yace nayi wankan tsarki, shi kuma ya fito ya gyara gadon da muka kwanta ya cire zanin gadon ya shimfida wani.</p><p><br /></p><p>Bayan nagama na fito ya taimaka min nasaka kayana sannan nayi sallah, shi kuma ya Shiga dakin sa, bayan ya dawo ne ya ganni akwance akasa ina bacci.</p><p><br /></p><p>Yazo ya daukeni muka hau gado muka kwanta ya jamana bargo bacci mai dadi yayi awon gaba damu.</p><p><br /></p><p>Bamu muka tashi ba sai wajajen sha daya , Donni na rigashi tashi ma, naje nayi wankana, nafito na Shafa mai na tsantsara kwaliyata, "" na zabo kaya mai kyau nasa ka tare da kashe Dauri na feshe jikina da turare, sai kamshi nake </p><p><br /></p><p>Na kalli kaina a madubi nida kaina nasan na hadu"" sai murmushi nakeyi da na tuno Daren jiya nayi saurin rufe fuskata.</p><p><br /></p><p>Ni nusnim nace wannan murmushin menene, ban sani ba sai su hjy ceeymer da cool da Yar Mulki da Sadiya da rabi'ah.</p><p><br /></p><p>Na tashi naje kusa da Yaya Khalid na zauna ina kallon sa, sonshi na fuzgata na saka bakina dai dai kunnan sa ina hura mai tare dasa hannu na afaskar sa ina shafawa" na gangaro kan leben bakin sa sai waiwayi nake masa, karaf kuwa yasaka yatsata cikin bakin sa, yana tsotsa kamar karamin yaro mai shan nono, nayi nayi na kwace hannun nakasa ya bude idon sa yana jifata da wani zazzafan kallo mai kashe jiki.</p><p><br /></p><p>Yasa hannun sa ya janyo ni na fada jikin sa yace my shazee kinyi kyau sosai fa, sai kamshin dadi kikayi , kin tada min da hankali fa,, ya kamata in ya mutsa kwalliyan nan yanxu.</p><p><br /></p><p>Ganin yana kokarin saka hannun shi cikin rigata, cikin shagwaba nace my d yunwa fa nakeji, kuma ni wlh nagaji, ya fashe da dariya yana kwaikwayen muryata, yace nima my baby ina bukatar kine. Yadda yayi maganar yabani dariya, dukkan mu mukayi dariya"" yace bara baje nayi wanka ko tace to , na kara gyara dakin nawa "" na fito parlo,,, na fito ba da dadewa ba, naji Ana kwankwasa kofa, na karasa wajen don budewa.</p><p><br /></p><p>Su aunty amingi ne. Da kannan sauban nabila da Sadiqa, ihun murna mukayi tare da rungume juna, kamar wayanda suka Dade basu hadu ba, sauban ne ya karaso da gudu jin ihun da yayi "" yayi zaton wani abune ya sameni"" yana my d my d lfy mai ya sameki"" baimaga su amingi yazo yana tattabani duk ya rikice ya rungumeni yana bubbuga bayana"" tafi da shewa yaji abayansa ana cewa , wo bros wannan soyayya haka da bata boyiwa, hmm I like that, saadiqa CE barama mu kashe muku hoton"" binsu da ido yayi galala yana kallon su, "" yace yaushe kuka zo?</p><p><br /></p><p>Amingi tace kuna can kuna soyayya tayaya zakusan munzo" to awan mu daya zaune kofar parlon Ku muna jiran Ku"" saura kadan mu tafi shine muka kara bubbuga kofan, sai ga Shahrazad ta bude mana!!! Kunya duk tabi ta ishemu" Khalid ne yayi karfin hali yace ke dama amingi kincika sa idon bala'i mijinki ya Shiga uku wlh, suka kwashe da dariya.</p><p><br /></p><p>Suka shigo cikin parlon shi kuma Khalid ya wuce dakin sa don karasa shirya wa.</p><p><br /></p><p>Amingi ne ta zungure ni tare da daga min gira tana cewa yane matar bros da fatan dai an ba mawa Yaya Nah abunda yakeso ba aja mashi aji ba" Nabila kanwar sauban tace lallai ma amingi, ke tayayan ki ma kike bata Amarya ba"" aji kuwa dole sai anja mashi, don mace sai da aji"" hahaha lallai Nabila wato abun saniyar ware ce ko, to zaki Shiga hannu na, muka kwashe da dariya"" cikina ne yayi kugi, nace wash Allah sukace lfy nace yunwa nakeji"" Khalid ne ya karaso yace kunki ba matata abinci kun sata gaba sai surutu kuke mata"" saadiqa tace bros maida wukan ga abinci can an kawo muku, ya tashi ya dauko ya zuba mana abincin sannan ya janyo ni"" kancinyar shi yafara bani abaki inaci"" abun ya burgesu haka suka Shiga yi mana video da hotona, suna mana kirari kamar agidan sarauta.</p><p><br /></p><p>Rayuwar aure mai dadi wasa wasa har nayi shekara biyu a gidan Khalid muna dirzan soyayyar mu"" kuma ya mai ya cikama hajiya alkwarin cigaba da karatuna , inda aka samamin admission a masu"" lokacin ina da ciki"" sauban ya kanxo gidana muxauna muyi ta hirarmu"" saida yayi da kyar sannan soyayya ta tafiya azuciyar sa"" zaman u.s yasa shi ya kara kyau da kwarjini.</p><p><br /></p><p>Kullum nida Khalid sai mun mishi magana akan yayi aure sai dai yace mana aure lokaci ne in lokacin yayi ba makawa sai yayi"' Sadiqa kanwarsa tayi aure"" haka kazalika nima na haihu na haifi Dana na miji mai kama da Khalid, yaro yaci suna Umar farouq "" Khalid ya rushe gidan babana an gyara yayi kyau"" babana kuma ya auri innata kanwar hajiyata, dayake mijinta ya rasu.</p><p><br /></p><p>Suna zaune lfy da mama indo har yau ba labarin nafeesa ,, har an fitar da rai"" rayuwa mai dadi muke yanxu haka Khalid ne mijina.</p><p><br /></p><p>To kunji labarin"" su Fatima sukace woow aunty shazee gaskiya munji dadin labarin ki mai dauke da darasi da abun al'ajabi, kuma muma munyi da mun sanin barin gidan iyayen mu.</p><p><br /></p><p>Ni'ima tace aunty shazee yanxu INA sauban, shazee tace yanxu ko zaki ga ya shigo aiko bata gama rufe baki ba yayi sallama.</p><p><br /></p><p>*taku* *Ummu* *Ruman*</p><p>(Nusnim)</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 155 & 160</p><p><br /></p><p>Nusaiba jin ana tafiya a mota ta dago ido tana kallon, shiko ya daga mata, yace yane" tace INA zamuje haka , yace wajen ammina zamuje" naga sun saki agaba da tsokana!! Nusaiba tace haban sauban, yanxu ko kunya sai ka kaini wajen ammi?</p><p><br /></p><p>Yace to menene, ai ranar da suke sun gani ne yazo"" nasan ba karamin murna zasuyi ba!! Nace kayi hakuri don Allah kabari ba yanxu ba" tunda kaga ba mu koma gidan iyayen muba!! Kuma ba musan andaura mana aure ko ba adaura mana ba" wani irin Jan birki yayi , kiiiiiiiiiiiiiiiii, sai data tsora ta!! Cikin tashin hankali ya juyo yana kallon Nusaiba, yace ai bazai taba yauwa ba, wannan karan bazan taba yarda ba.</p><p><br /></p><p>Kota halin kaka sai na aure ki Nusaiba, bazan kara yin asara ba""kisa aranki nanda sati biyu insha allahu kinxama matar sauban.</p><p><br /></p><p>Haka Nusaiba ta zuba mishi ido tana kallon sa kamar Wanda ya haukace , sai huci yake, yabata tausayi sosai "" cikin lokaci kankani haka har ya kamu da sonta"" sai hamdala take azuciyar ta.</p><p><br /></p><p>Cikin sanyin murya tace my sauban insha allahu kamar mungama mallakar juna!!! In Allah ya yarda wannan karan baza ka taba kara rashin masoyiya ba!!! Sai a lokacin yaji zuciyar sa ta masa sanyi"" yace nagode Nusaiba Allah ya barmu tare ameen.</p><p><br /></p><p>Yaja motan ya tsaya awani super market , yace mata yana zuwa shi kadai ya Shiga ya jido kayan kwalliya, dasu turarur ruka masu kamshi, wajen Leda 6, kasa mashi abayan mota, ya Shiga motar, sai tudun wada wajen masu gasa gaji yaje *taraba* *suya* wani kam shine mai dadin ji ke tashi awurin, manyan motocine da hamshaqai ke layi awajen, can na gano cool da Yar Mulki sai rabi'ah, suna wanke wanke sai lashe bakisuke, aunty rabice tazo ta Dan gutsuran masu nata data siya.</p><p><br /></p><p>Bayan ya siya suka wuce GDA"" suko su Shahrazad , ankira su aunty amingi da Nabila da Sadiqa ta fada masu, sauban yayi mata fa.</p><p><br /></p><p>Bakaramin dadi sukaji ba, Khalid ne zaune kusa da matars shazee da dansu Umar farouq "" dayan bangaren kuma su Fatima ne , hira suke su duka .</p><p><br /></p><p>NI'IMAH tace oh su Nusaiba shiru fa, SHAHRAZAD tace aikuwa dai , inaga sunbiya wani wajena"" Khalid yace kudaina damun kanku suna can sun samu lambun soyayya sun baje.</p><p><br /></p><p>Sai ji sukayi ance eh wlh mun samu wajen daza mu baza soyayyar mu batare da an samana ido ba"" daga ido sukayi don ganin waye sauban ne ke wannan maganar" sai ya bone kamar bashi yayi ba"" Nusaiba na gefenshi suka karaso ciki" suka zauna kujera daya" dama tun amota sauban yacewa Nusaiba bonewa zasuyi su nuna musu sun fisu iskanci"" inba haka ba toh baza su barsu su zauna lfy ba.</p><p><br /></p><p>Cikin mamaki shazee tace lallai kam kunfi karfin mu, tace my d kallafa kujera daya suka zauna kamar ba yau suka hadu ba, ko irin kunyannan"" Nusaiba CE tace aunty shazee dane ake wannan kamar yadda kukayi da Yaya Khalid gida danci cikin zolaya Nusaiba ke wannan maganar, Khalid yace my shazee wlh muyi shiru don wayannan masoyan sunfi karfin mu, naga Kansu na hayaki kadan ya rage su kona mu fa.""' Khausar tace aikuwa Yaya Khalid, nida nasan Nusaiba da kunya amma yanxu ta bada mawa idanunta toka.</p><p><br /></p><p>Sauban yace inba haka muka muku ba, to baza Ku barmu mu huta ba, xaku samu agabane, shiyasa muka muku haka, gaba ki yansu suka kwashe da dariya!!! Me gadine ya gama shigo da kayayyakin da su sauban suka siyo.</p><p><br /></p><p>Ko wacce ya mika mata leda daya na nusaibace Leda biyu, bakaramin dadi sukaji ba, nan aka Shiga cin taraba suya.</p><p><br /></p><p>Washe gari su Fatima sun kwaso kayan su dake gdajen da suka kama, hajiya tayi kewar su, bataso tashin su ba,, amma sunce mata zasu dinga zuwa gaisheta, taji dadi har ta masu alheri"' sun dawo sunga gidan cike da hayaniya , su amingi da yaranta hudu, sai Nabila da yaranta uku, sai saadiqa da yaranta biyu, cikin sallama suka kara sa cikin parlon"" amingi ta tashi da murnanta kamar ta sansu din nan, kowacce sada ta rungume tare da cewa wellcome my sister, su Nabila da Sadiqa ma haka"" nan aka Shiga gaggaisawa.</p><p><br /></p><p>Sadaqi tace wacece Amaryan Yaya sauban, ni'imah tace, ki cinka mun baki zabi" tace to , suka tsaya suna kallon ta suga wa zata zaba, ta nuna Fatima, amingi tace kai ba wannan bace ta sakiyar Ku CE, wato Nusaiba, shazee ne tace tayaya kika sani.</p><p><br /></p><p>Tayi murmushi tace ai tun lokacin da suka shigo naga take Dan jin kunya tanan Nagano"" Nabila tace Nusaiba muna sonki, don kyau tace ke awajen mu, don kinrudar da yayan mu, dole muma mu soki, gashi kina da kyau.</p><p><br /></p><p>Ai tuni Nusaiba ta bar wajen don kunya, Shahrazad tace Nabila kinga kinsa taji kunya ko"" Sadiqa tace damma ba aunty amingi CE tasa ta gaba ba, Aida inaga sai ta nutse katsa" sukayi dariya, amingi tace kin samun idofa saadiqa keda Yaya Khalid kamar ciki daya kuka fito.</p><p><br /></p><p>Su Khalid sunyiwa iyayen su magana akan su NI'IMAH , anyanke kowacce zasu je gun iyayen ta, haka nan aka dunguma , akace za afara zuwa garin su Fatima, sun kama hanyar zuwa garin ,, gaban Fatima sai fuduwa yake, har unguwarsu sukaje, tunda ga nesa ta hango gdansu , hawayene ya silalo mata .</p><p><br /></p><p>Baban Shahrazad ne yace nan ne gidan Ku tace eh,, sai akace su mata su fara Shiga, da yake da aunty Hauwa aka taho sai Shahrazad dasu Nusaiba" Fatima ke gaba, atsakar GDA ta hango mahaifiyarta na kwashe abinci, sallamar da akayi ne ta dago kai, waza ta gani kamar yarta Fatima, wacce ta Dade da begenta.</p><p><br /></p><p>Aida gudu Fatima taje ta rungume mahaifiyarta tana kuka, itama mahaifiyar kuka take, tana cewa Fati Nah ina kika Shiga kisamu a damuwa munyi Neman har mun gaji, aunty hauwace tace me gidan na nan akwai baki maza awaje, sai a lokacin suka dawo cikin hankalin su"" tace yananan ta masa magana shima cikin murna ya fito dayake da baki awaje shiyasa baibi takan Fatima ba.</p><p><br /></p><p>Aka shigo dasu cikin parlon Gidan intakai ta maku , nan dai aka bayyana masu komai, sunyi kuka kuma sunyi da sun sanin auren dauka mata"" ayanxu , hakama tun bayan tahowar Fatima mijinta ya saketa, ba aure akanta.</p><p><br /></p><p>Komai ya daidaita washe gari suka kama hanyar suleja garin su NI'IMAH, sun bar Fatima a can akan zatayi sati daya ta dawo Kaduna saboda zasu fara jarabawa.</p><p><br /></p><p>Sun iya garin su ni'imah lfy itama andaidaita da iyayen ta, ,, itama bata da aure tuni mijin ya saketa, kwanan su daya suka wuce Adamawa mubi garin su khausar, itama NI'IMAH anbarta a can"" iyayen khausar sunyi murnan ganin yarsu, dama ita ba adaura mata auren ba ta gudu"" nanma kwanan su daya, sai ya rage Nusaiba kadai, tayi kewar yan'uwanta sabo turkin wawa" dukkan su sai da sukayi kuka.</p><p><br /></p><p>Nan akaje jigawa garin su Nusaiba,ita harda Neman aurenta ma"" ita kadaice iyayen ta, suka so bada Matsala don da iyayen ta cewa sukayi dole sai sun mata auren nan da bataso har ta gudu, ganin sauban na kuka yana rokansu shine ya basu tausayi, har suka ammin ce, ba karamin dadi sukaji ba"" baban Nusaiba ya kalli baban Shahrazad yace mallam nikam kamar naso ingane ka wlh, baban shazee yace aikuwa nima, inata maka kallon sani, kamar munyi karatu an an *guri* ko secondry skull din nan na yan maza dake garin hadeja, kaman sulaiman ko, haka kuwa kai kuma abdulmaleek ko , kwarai kuwa, nanfa aka kara gaisawa , yace SULAIMAN yanxu Nusaiba Yar kace, shine kaso kayi sakaci" gaskiya ka godewa Allah da ya hadata da Yar wajena wato Shahrazad"" baban shazee ya kara masa nasiha da bashi shawarwari!!! Yayi godiya sosai.</p><p><br /></p><p>Shazee da Nusaiba sai murna suke sakamakon iyayen su maza abokanaine"" baban Nusaiba ya damkawa baban shazee komai nadangane da auren Nusaiba da sauban, yaji dadi sosai""saida sukayi kwana biyu sannan suka shirya tafiya dakyar Khalid ya lallabe sauban su tafi,"" don yace shi bazai tafi ba, har sai ranar da Nusaiba zata koma sai su koma** saida baban sa ya lallabesa sannan suka wuce kaduna tare sa kawar juna, Nusaiba da sauban harda kwalla.</p><p><br /></p><p>*taku* *Ummu* *Ruman*</p><p>Nusnim</p><p>Ana hubbiq aunty Shahrazad Allah ya barmana ke</p><p>Amarya agun farouq dinta</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 165 & 170</p><p>Najib yace Fatima dama kina nan?</p><p><br /></p><p>Ina nan wlh , ayya ya kk ya kwana biyu, ya yara?</p><p><br /></p><p>Lafiya lau amma banda yara single nake, najib yace da kamar naso naji kinyi aure ko?</p><p><br /></p><p>Fatima tace eh, nayi amma auren ya mutu, yace ashsha Allah yasa shine mafi alkhairi ameen.</p><p><br /></p><p>Yace biki kema kikazo kenan"eh kawata ke aure ayya ni kuma oga nane ke aure " Fatima tace. Sauban kake nufi" yace eh shine, ko shine mijin kawar taki " eh shine.</p><p><br /></p><p>Ayya Allah ya basu zaman lafiya ameen "" su ni'ima ne suka karaso inda take, sallama suk masu" najib ya amsa " Fatima tayi saurin cewa har kungama abunda kukeyi ne? Suka ce eh .</p><p><br /></p><p>Tace naji ga kawayena , ni'imah ga najibullah nagarin mu"" khausar tace woow Fatima shine najib din nan naki?</p><p><br /></p><p>Fatima tayi saurin cewa ke uwar surutu, najib dai sai murmushi yake , yayi kamar baiji abunda khausar ta fada ba ya basar da maganar"" tuni khausar ta bar wajen don zuwa shaida mawa aunty shazee da Khalid, don ga dama tazo kar su bari najib ya subucewa Fatima.</p><p><br /></p><p>Bayan tafiyarta najib yace Fatima ko zan iya samun number ki, "" tace ba damuwa nan ta bashi number ta ya kira layin , number sa ne ya fito akan wayan!!! Khausar tagama fada mawa su shazee suka tsaya nesa da su suna kallon Fatima da najib.</p><p><br /></p><p>Bayan najib ya tafi Fatima ta fara Dan tsallen murna, tare da daga hannu sama tana rokon Allah ya bata najibullah amatsayin mijinta amin.</p><p><br /></p><p>An watse daga dinner kowa ya dawo gida agajiye, nan aka baje da hira ana tsokanar SHAHRAZAD da Nusaiba , tun suna jin kunya har suka daina.</p><p><br /></p><p>Khalid ya sami sauban ya fada masa haduwanta da najib tunda yana aiki akanfanin sauban din,, nan sauban ya nuna murnar sa yace insha allahu bayan biki zan masa magana.</p><p><br /></p><p>Najib kuwa yana can yana zancen zuci tare da tuno maganar khausar ashe Fatima na sona? Indai ko hakane, bakaramin dadi najiba, don ni ma ina sonta.</p><p><br /></p><p>Washe gari aka kama hanyar zuwa jigawa don daurin aure, mutane dayawa sun hallara, anyi biki sosai a jigawa,, dauran aure ya Tara dunbin jama'a sosai, bayan andara da la'asar aka dauko Amarya zuwa kaduna "" kai tsaye aka wuce da ita gidan mijinta dake malali, Nusaiba tayi kukan rabuwa da iyayenta.</p><p><br /></p><p>Gidan Nusaiba mai kyau yadda baza a iya fadan kyawun gidan ba" wannan na barma masu karatu, da kyar su Fatima suka yi mawa Nusaiba wayau suka gudu, taci kuka har ta gode mawa Allah" gidan ya rage sai ita kadai' "" sauban ne yashigo cikin sallama a hankali ta amsa mashi.</p><p><br /></p><p>Sai murmushi yake ya karaso kusa da Nusaiba tare da daga mayafinta yana Amarya kinsha kamshi bakya laifi koda kin kashe Dan masu gida, Nusaiba tace habadai sai dai inban kashe ba, dukan su sukayi dariya.</p><p><br /></p><p>Sauban yace Nusaiba yau gamu amatsayin ma'aurata cikin inuwa daya, gaskiya ba karamin murna na tsinci kaina ba"" yanxu tashi muje mu godewa Allah, sun gabatar da sallah tare da karantu addu'oi na zaman lfy da samun zuri'a dayyiba.</p><p><br /></p><p>Bayan sun gama sunci sunsha, sauban yace yana zuwa bayan fitar shi Nusaiba tashiga toilet don wasa ruwa, bayan ta gama ta fito ta feshe ko ina na jikinta da turare, tasa kayan bacci taga babu maraba da tsirara , tayi sauri ta dauki zani ta daura, ta saka hijabi sannan ta hau gado ta kwanta.</p><p><br /></p><p>Bayan sauban ya gama shirin bacci ya shigo dakin can karshen gado ya hangota ta dukunkune"" yayi murmushin mugunta tare dafadin azuciyar sa, lallai za'ayi fama, tana jinsa ya hau kan gadon ya janyota jikin sa, kirjinta sai bugawa yakeyi .</p><p><br /></p><p>Yace baby nuscy ya kikasa hijabi zai shake miki wuya fa, ko zafi bakya ji cikin murya kasa kasa tace bana jin zafi" yayi murmushi.</p><p><br /></p><p>Yace yi hakuri kicire nifa mijin kine kidaina jin kunyata yau ranace da zamu raya sunna""" Dan Allah karki bare wannan lokacin ya wuce mu, kiji tausayina Nusaiba "" haka yabi ya lallameta da dadin baki , da dabara ya cire hijabin da zanin"" kirjinta ne abayya ne.</p><p><br /></p><p>Ai tuni hankalin sa ya tashi, ya kai masu cafka, kamar wani zaki, da zafi zafi yake aika mata sakonni abunka da mayun waci"" Nusaiba sai kuka take tana bashi hakuri ai ina bai masan tanayi ba,""taga ba sarki sai Allah.</p><p><br /></p><p>Haka nan ta mika masa kanta, sai da ya rabata da komai na jikinta , ko ina saida ya lashe daga sama har kasa , itama tafara biye masa' yaji dadi sosai amma yana Shiga babban hanya ta saki kara , sai da ya toshe mata baki , sun batu yake shi kadai, sauban yaji shi awata duniyar.</p><p><br /></p><p>Hmmm Ku karasa wannan Harkan.</p><p><br /></p><p>Washe gari da Kansa ya mata wanka, ya shirya ta kamar wata Yar baby, breakfast ma shi ya hada masu, don yana kowa yazo da safe don kar a takura su, yazo yana bata ita kuma sai langwabewa yakeyi"" saida sukayi sati daya suna durzan amarci batare da kowa yazo gidan ba. </p><p><br /></p><p>Su Shahrazad ne zaune suna cewa oh su Nusaiba da sauban shiru kake jin su, sun kashe waya, don kar adamesu"" dama duk shuru din mutum kaidai kawai bisu da ido" khausar tace aikuwa, mu ma dai bara muzo muyi auren nan. Muji me akeji haka, suka kwashe da dariya.</p><p><br /></p><p>Bayan sati biyu da auren su Nusaiba sauban ya kira Khalid sukagaisa, Khalid yace woow mutumina an shigo sahun manya , kaje birnin maji dadi, sauban ya kwashe da dariya yace sosaima kuwa"" yanxun ma da kyar na iya kiran ka don yanxu mun kusa dayin harka .</p><p><br /></p><p>Hahaha amma kai Dan iskane fa gskya kafi karfina sai anjima"" ya kashe wayan yana dariya.</p><p><br /></p><p>Akwana antashi babu waya wajan Allah Fatima da najibullah sun hada kai tare da taimakon su Khalid, haka su ni'imah da khausar duk sun fitar da mazajen aure, anyenke biki bayan sun kammala degree dinsu tunda saura wata biyu.</p><p><br /></p><p>Nusaiba kuma tana dauke da Dan karamin ciki, Wanda ya kara mata kyau"" amma kuma ga laulayi" shine aka nema mata mai aiki , wata yar budurwan yarinya bazata wuce shekara ashirin da hubu ba.</p><p><br /></p><p>Amma kana ganin yarinyar kaga alamun damuwa, kuma bata fiye magana ba, kullum cikin kuka take" Nusaiba tayi tambayen har ta gaji, " shine tajewa da Shahrazad da zancen yarinyar ita dai tana bata tausayi gata da girmama mutane" Shahrazad sarkin tausayi da taimako ta shirya tazo gidan Nusaiba don taga mai aikin nata.</p><p><br /></p><p>Nusaiba taji dadin zuwanta, ta kira mai aikin nata don ka mawa aunty shazee lemo, kanta akasa tashigo parlon har gaban shazee ya ijye zata juya .</p><p><br /></p><p>Shazee tace baiwar Allah yarinyar tayi saurin daga kai don gasgata mai muryan nan , ido hudu sukayi, dukan suka razana tare da mikewa tsaye, shazee tace nafeesa dama kina Raye , itama nafeesa tace Shahrazad Ashe zamu sake Haduwa"" suka rungume juna tare da sakin kuka, nafeesa tace kiya femin Shahrazad , nida mahaifiyata munbiyewa sharrin zuciya mun rabaki da masoyin ki,"" sai gashi cikin sauki Allah ya saka maki"" nan nafisa tafara ba mawa shazee labarin ta, Ashe ta Dade cikin hauka inda kullum cikin bola nake zama, da haka har wani Mara tsoran Allah ya min ciki , wajen haihuwa na warke daga haukan wata matace ta taimakeni "" dayake ina yawan zama alayin su har yara na tsokanata , itace takan ban abinci"" data ga zan haihu ne shine ta taimaka min," na haifi diyata mace!!</p><p><br /></p><p>Matar ta tambayeni gidan iyayena nace ban sani ba don bani so indawo gda, da yarinya a hannuna , ace aina nasamu, don cewa karuwanci natafiye Wanda kuma ba asan hauka nayi"" da haka naci gaba da zama wajen matar , ta rikeni tsakani da Allah, dayake bata da karfi shine tasa mamin aiki anan gidan.</p><p><br /></p><p>Shahrazad ta kara fashewa da kuka, nan ta ba mawa nafeesa labarin dalilin haukanta, harda canjin rayuwa daya zo musu.</p><p><br /></p><p>Cikin kuka nafeesa tace mahaifiyata ta cuce ni , talala tamin rayuwa, gashi asanadiyarta na haifi Yar da ban San ubantaba"" dakyar dai aka rarrashi nafeesa akan data yafewa mahaifiyarta.</p><p><br /></p><p>Khalid da sauban sun dawo tasanar dasu komai, aka tafi da nafeesa GDA,mama indo na ganinta ta rugo aguje tana tattabata don ta tabbatar ba mafarki takeyi ba.</p><p><br /></p><p>Suka rungume juna suna kuka , ta rungume baban shazee wato kawunta, tare daneman gafara, nan shazee ta kora masu bayani kamar yadda nafeesa nafada masu.</p><p><br /></p><p>Mama indo tayi kuka kuma tayi da tasani, tunda abunda ta suka shi ta giba tunda gashi harda yarinya nafeesa ta samu, duk ta sanadinta!!!</p><p><br /></p><p>Dakyardai aka kwantar masu da hankali, baban shazee ya kara masu nasiha, yace ita duniya nan fadice gareta, Allah baitaba bari azalunci bawansa batare daya saka masa ba"" a kullum musaka tsoran Allah azuciyar mu, KAR muce ai ba bu me ganin mu inxamu yi mugunta"" ina ba haka bane, Allah na kallon mu" sannan kuma muyawaita istigfari don naiman yafiya, mudaina biyewa sharrin zuciyar mu don zata kaimu ta baru mu"" duk lokacin dakaji zuciyarka ta ayyano maka Abu Mara kyau to ka gaggauta fadin auxubillahi minalshainanil rajeem"" muna rukon Allah ya karemu daga sharrin mugayen mutane, da dabbobi da aljan ameen</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Su Nusaiba naga kasu sun fita da result mai kyau, kowa cikin farin ciki yake, anti auren su Fatima, su Nusaiba da shazee sun taka rawar gani abikin.</p><p><br /></p><p>Bayan biki da sati uku Nusaiba ta haifi kyakkyawar yarta mai kama da sauban, inda taci suna Shahrazad "" bakaramin dadi su Khalid da shazee sukaji ba!!</p><p><br /></p><p>Small SHAHRAZAD tasamu kyaututtuka daya wa" su Nusaiba suna rokon Allah daya bamawa yarsu hali na taimako irin na shazee.</p><p><br /></p><p>Bayan shekara daya nafeesa tasami miji tayi aure, yarta kuma tana wajen mama indo, Allah kuma ya Dora mawa mama indo son yarinyar nafeesa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Itama Fatima ta haihu da namiji yaro yaci sunan babban najib.</p><p><br /></p><p>Rayuwa mai dadi Khalid ne zaune amota da matarsa shazee sai yaransu guda biyu Umar faruq sai Hauwa, sai abdulmaleek shine auta" khaleed yace my d kinga yadda rayuwa ta sauya ko, yau gamu da Yaya harku, Allah ubangiji ya daya mana su amin</p><p><br /></p><p>Ta Dan kwanta kan kafadansa tana murmushi tace Allah ya barminkai my d dina jarumin jarumai, Dan kwalisan matasa, da bazarka nake taka rawa, INA sonka my Khalid.</p><p><br /></p><p>Yasa dayan hannun sa yaja hancina tare da cewa , shazee kinfi kudi kinfi gida kinfi mota, ke rayuwa ce shazee, don kin min babban kyauta har guda uku, ayau da daddare zancika na hudun , suka kwashe da dariya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>*ALHAMDULILLAH*</p><p>Anan nakawo karshen labarin nan, badon naso bamawa ba" amma insha Allah zakujini awani sabon novel dina" inafatan zaku dauki darussan dayake ciki"" in nayi kuskuren ayafemin"" nagode sosai makarantana</p><p><br /></p><p>Group dina na all dostis of nusfulhayat INA kara gode muku da kuka bani goyon baya, cool Yar Mulki fauxiya, rabi'a, aunty rabi, hauwa'u Nuhu" yayar cool , Fatima , Ummu Ilham " Ummu anas da sauran members din NASA kuna raina nagode sosai.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ban manta da kuba Sadiya ta GRP din m Jabo</p><p><br /></p><p>Da ameera , da billy s Fari , da sauranku.</p><p><br /></p><p>Sai kuma Dan uwana, me son novel dina,nagode maka dama kirani , da kuma kullum in banyi post ba, sai ka tambaya nagode sosai..</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Wannan littafi nakine don ke nayi, kina cikin raina masoyiyata, Allah y barmu tare shona Shahrazad dina" </p><p>Ina sonki aunty Shahrazad Allah ya barki da farouq dinki,, much of luv Shahrazad.</p><p><br /></p><p>Kawayena </p><p>Miss zozo</p><p>Hafsat Rano</p><p>Ummu Yahaya</p><p>Ummu Adnan</p><p>Ayusha ilyasu</p><p>Maman Bobo </p><p>Nafi Anka</p><p>My Qurratul ayni</p><p><br /></p><p>Much of luve all</p><p><br /></p><p>Saini marubuciyar.</p><p>*Nusaiba* *SULAIMAN* </p><p>Wacce akafi sani da *Ummu* *Ruman* *nusnim*</p><p>08064481931</p><p>Love u all</p><p>[4/15, 10:03 PM] +234 806 448 1931: ❣ *SHAHRAZAD* ❣</p><p>(Labarin sharrin zuciya)</p><p>*BY* *NUSNIM*</p><p> 160 & 165</p><p><br /></p><p>Fatima NI'IMAH, Nusaiba khausar bakaramin kewar gidajen iyayen su sukayi ba, sunyi da sun sani, sannan kuma sun godewa Allah dayasa babu wani Abu daya faru dasu "" kuma suna kara godewa aunty shazee.</p><p><br /></p><p>Bangaren sauban kuwa ana can ana shirye shiryen biki"" haka Shahrazad ba abarta abaya ba, duk abunda tasan Amarya na bukata shi take Adanawa, don sun kusa dawowa , SBD skull"" Fatima acan garin su take tambayar wata kawarta bilki take ce mata , niko bilki najibulla yana nan kuwa?</p><p>Yayi aure ne?</p><p><br /></p><p>Bilki tace ai najibullah yana Kaduna dazama yanxu, yasa mi aikin gwamnati, sai ya samu Hutu yake zuwa gaida iyayen sa"" amma kuma har yau bayyi aure ba , yace har yanxu baiga wacce yake so ba.</p><p><br /></p><p>Fatima tace Allah sarki najibullah, bilkisu tace Fatima badai har yanxu kina son sa ba, Fatima tace tabbas har yau ina son sa, amma ba zan taba fada masa, har inshi da kansa yace yana sona, kin San ban son raini, don yanxu kika cewa namiji kina son sa, to kin Shiga uku wlh don wata rana sai ya goranta maki, amma zanyi tayin addu'a har Allah yayi min zabi mafi alkhairi"" Donni yanxu ko wani auren akace za asake min ga mutum da banso, tsab zan zauna kuma in masa biyayya irin ta aure" nasan komai mukaddari ne daga Allah, ba abunda Allah bazai jarabce ka dashi ba don yaga zaka karba ko baza ka karba.</p><p><br /></p><p>Bilki tace hakane kawata, gsky yanxu kinyi sanyi , ba dole ba , bilki tace gsky aunty Shahrazad alkhairice arayuwarku, tunda gashi ta sanadiyarta tacanxa min kawata, ta dawo min da ita har gida, Fatima CE ta kaiwa bilki duka abaya, tace kin fara tsokananki ko.</p><p><br /></p><p>Kinga yanxu saura kwana biyu mu koma Kaduna SBD muna da jarabawan Shiga level 4 final kenan , ga kuma bikin Nusaiba da sauban kinga ko hidimace agaban mu.</p><p><br /></p><p>Bilki tace hakane kam nima dai zan daure inxo in ba mawa idona abinci, inga jarumai uku din nan wato Khalid Shahrazad sauban, Fatima tace aiko Dana ji dadin zuwanki.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau lahadi ranan da su Nusaiba zasu koma Kaduna, , khausar tafisu nisa ita tun ranar sati tazo kano gidan su Fatima washe gari kuma suka dauko hanya zuwa Kaduna"" gaba ki dayan su sun hadu a tashan kawo, ba karamin murnan ganin juna sukayi ba , cikakkun mata masu haiba tafiya suke cikin kasaita, kowacce da akwatin ta Tanaja har suka isa gun motar da aunty Shahrazad ta aiko adauke su.</p><p><br /></p><p>Can gida kuwa su amingi dasu bila sunzo gidan shazee don karban baki, gda ya bude da kamshin girke girke, yadda kuka San wasu baki za ayi daga kasashen waje, kuma ina duk sabagen son da SHAHRAZAD ke musane shine ta shirya musu haka.</p><p><br /></p><p>Sun iso har cikin haraban gidan suka fito daga cikin motan shazee ce tafito da gudu gudun ta tare da cewa oyoyo my sister nayi kewarku, duk saida suka rungumeta .</p><p><br /></p><p>Harda su amingima saida suka rungume su, aka dunguma ciki. Nusaiba sai ware ido take taga ko zata ga sauban duk suna lura da ita, shazee ne tace Amaryan mu karki damu yanxu angon naki zaizo, cikin jin kunya Nusaiba ta sunkuyar da kai tare da cewa kai aunty shazee bashi nake nema ba fa, Umar dinki nake son inganshi fa"" suka kwashe da dariya amingi tace rabu da wannan shazee itama ta koyi sa'ido, Khalid ne yace ba irin nakiba da , ya karaso yana dariya, aka gaggaisa" yayi shigewar sa daki.</p><p><br /></p><p>Sauban ma yazo suka kebe da amaryarsa suna hirarra soyayyar su.</p><p><br /></p><p>Wasa wasa su Fatima har sungama jarabawan su, yayin da Shahrazad itama tagama degree dinta, ta fito da result me kyau , sai datayi kukan murna tana inama hajiyata na nan, baban ta ya tayata farin ciki tare dayi mata fatan alkhairi arayuwarta , takara rungumar mijinta tana me gode masa da yatsaya mata har tagama, lallai Shahrazad tayi dacen miji nagari Wanda zakayi alfahari dashi.</p><p><br /></p><p>Saura sati biyu bikin Nusaiba, sauban yazo ya kaita wajen ammin sa, taji dadin ganinta kuma tayaba da hankalin Nusaiba dayake ya'yanta su Nabila suna bata labarin ta, tun bata gantaba tayi na'am da'ita.</p><p><br /></p><p>Khalid da Shahrazad su suka dauki nauyin kayan dakin Nusaiba sun hana iyaye yin komai, dayake yanzo arzikin Khalid sai kara karuwa yake yi.</p><p><br /></p><p>Iyayen Nusaiba har Kaduna sukazo godiya dayake suma rufin asiri gare su,, yadda aka kasa bikin Nusaiba shine, za'ayi sisters day, sai kuma dinner daza ayi, kafin adaura auren, ana kuma gobe daurin aure a tafi jigawa can mahaifan Nusaiba, adaura aure, daga can kuma sai akawota gidan mijinta sauban , dake malali. Haka aka tsara.</p><p><br /></p><p>Har GDA shazee ta kawo me gyaran jiki ta gyara Amarya da kawayenta, bilki kawar Fatima tazo itama, agidan shazee akayi sister day, yasha kayan ado antsara dakyau, dayake babban gidane sai kayi zaton a hall, yadda wajen ya tsaru, ba abar su yan GRP din ne all dostis of nusfulhayat ba , sunzo bawa idanunsu abinci, yayin da guda uku suka zo Neman sauban wato cool da yarmaulki da rabi'a.</p><p><br /></p><p>The next day kuma aka tafi dinner , ,, sauban da Nusaiba sai daukan ido suke motar da suka hauma abun kallo ne, yaro Dan kwalisan matasa mai sabon jin, duk inda ya wuce sai yabar abun magana, kamar king laisu, hannun sa yasa ya kama hannun Nusaiba suna tafiya a hankali don Shiga hall din' sunxo daidai Shiga hall yasa dayan hannun sa akan kwan kwason ta, ya Dan jawota jikinsa kamar wata Yar baby zuka zuba mawa juna ido sai karan daukan hotuna kakeji bakaramin bada style sukayi ba,"" ahaka har suka isa mazaunin su.dije sai wasasu yake, kawar Amarya tazo tabada tarihinta hakama abokin ango, sannan aka saka kida, waje yacika da jikakkun yan gayu, Khalid ne yace shifa adole sai sun fito fili sunyi rawa don taya abokin sa murna, ba musu shazee ta amince, don gwanace wajen rawa haka suka shika shigo fili suna rawa cikin girma, ba irin gajagan gajagan ba, suna cikin rawa ne, amingi tacewa m.c din ya sama wa su Khalid wakan , *kashiga* *raina*</p><p>Habawa ana sawa zancen ya canxa salo jin su suke kamar sukadai ne afili, rawa suka Shiga yi, batare da sun San mutane n wajen ba, haka Khalid ya daga shazee cak yana jujjuyata, yayin da hannu watan biyu, sun dafa kafadan sa, shi kuma hannu sa yana kan kwankwa sonta "" ya daga kai sama yana kallon ta itama tana kallonsa suna aikawa junayen sakonni, aiko tuni kallo ya dawo Kansu, su sauban sukazo suna masu liki amingi ne tasa aka watsa masu abun nan mai kyalli kalli daga sama.</p><p><br /></p><p>Alokacin ne suka dawo hankalin su ya sauketa , ai fuskarta ta boye cikin kirjinsa don kunya" su sauban suka kwashe da dariya, Khalid ma karfin hali yayi, dayake aunty Hauwa tazo itama, agabanta akayi wannan fitsaran"" sauban ya daga mashi gira yana murmushi . amingi ne tacewa shazee ja'ira kamar ba ita bace suka gama soyewa saura kadan fa kuyi kiss, ko kunyi zaton kuna kan gado ne, hahaha.</p><p><br /></p><p>Shazee da ba bakin magana don ta hada ido da aunty Hauwa ,sai tayi mata murmushi. Shiyasa Takarajin kunya, ganin haka Khalid yaja matarsa suka bar cikin hall din.</p><p><br /></p><p>Khausar tace kai yau ana soyayya a dinner din nan , NI'IMAH tace aikuwa aini saida na dauka awayata Dana Nusaiba da sauban Dana Khalid da shazee, sukayi dariya, Fatima natafiya zataje ta dauki drinks kawai aukaci karo da wani har wayanta ya fadi, tace auzubillah ya hakuri bawan Allah, ya tsugunna ya dauko mata wayarta yace LA bakomai nida nafadar miki da waya, dagowan da zayyi sukayi ido hudu , gabanta ne ya fadi ta nusa sa da yatsa tace najibullah, shima yace Fatima, sai sukayi dariya.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Insha Allah inaga gobe zan kammala novel Dina</p><p> *taku* *Ummu* *Ruman* nusnim</p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-45233025336822903892020-12-05T21:38:00.003-08:002020-12-05T21:38:54.404-08:00SIRRINANE COMPLETE HAUSA NOVEL<div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-vu7GT5-Oo7A/X8xt9wJzZFI/AAAAAAAAJcw/F3oxxH1uhWMzJ4Zm0s4BOuSWaPhZb3JagCLcBGAsYHQ/s2048/SIRRINANE.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em; text-align: center;"><img alt="SIRRINANE COMPLETE HAUSA NOVEL" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="248" src="https://1.bp.blogspot.com/-vu7GT5-Oo7A/X8xt9wJzZFI/AAAAAAAAJcw/F3oxxH1uhWMzJ4Zm0s4BOuSWaPhZb3JagCLcBGAsYHQ/w320-h248/SIRRINANE.jpg" title="SIRRINANE COMPLETE HAUSA NOVEL" width="320" /></a></div><p> <br /></p><p>SIRRINA NE</p><p>Ni Benaxir Omar Zaune nake akan kujera</p><p>babu abunda nake tunani sai yanda zan je</p><p>wajen Maryam domin naji labarinta . duk da</p><p>nasan abune mai wahala sosai domin kuwa</p><p>nasan ta da zurfin ciki. Koda yake kawatace</p><p>kut da kut. Bazataban wahala ba gurin</p><p>gayamn labarinta ba. Donhaka namke cikin</p><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p>azama nadau wanka nadaukl mukulln</p><p>motana nagayda umma sannan nace zanje</p><p>gidan maryam tace da sassafen nan/? Nace</p><p>labar zamuyi yau hala nakai dare, na kwash</p><p>kafa ban nufii ko ina ba sai gra. Na y hun</p><p>megadinsu yabudemin gate. Bayan</p><p>shiganane nasamu tana zaune a falo tana</p><p>karatun wani lttafina ikon Allah, tash tayi</p><p>ckn murna da farin cik wayyo besty oyoyoyo</p><p>na murmushi nazauna, ta aika aka kawo</p><p>aman abinci da kayan kwalama, nace</p><p>kawata yau gani da takarda da biro, don</p><p>allah labarnki zakban nida dalbaiana na</p><p>makaranta kowa ta naso tadau darasi, wani</p><p>kallo tamin wanda sa dana hadya yawu, kina</p><p>nufin sirrin nawa zaki gwadawa dunya?</p><p>Nace haba besty darasi rfa zaa dauka, tace</p><p>to saiki gyra zama domin kuwa zaMU kai</p><p>dare , Allah ya taimakeki maigdan baya nan,</p><p>anan nazuba na zomaye tafara kaMAR haka</p><p>Sunana Maryam usman ,haifaffiyar garin</p><p>bauchi mu uku ne agun iyayena mubiyu</p><p>mata saii namji daya, kanwata faiza shekara</p><p>daya nabawa faza, yaya abbakar kuwa</p><p>yaban kusan shekara akwai,muntaso ciikin</p><p>gata don kuwa iyayenmu suna da arziki daga</p><p>baba har mama kowa na aikin kanshi,</p><p>Ina ss2 ,faiza kuwa tana ss1, kanmu daya</p><p>komai daya kuma tare mukayi, inbaka sanmu</p><p>ba zaka zata mu yanuwane,munshaku sosai</p><p>ba ataba jn kanmu, inma kashga saikaj</p><p>kunya,</p><p>Ni irin mATannanne masu tsiwa, inada tsiwa</p><p>sosai haka zalika kuma nada hakuri duk</p><p>sonka kaga bacin raina bazaka ganiba,komai</p><p>bacin rai bana nunawa, hakam yasa nake</p><p>zama dakowa lafya, hatta classmates dina</p><p>.kawata kwaya daya wacce nakeji da ita</p><p>sunanta Fatima abbakar anma anacemata</p><p>adda ummi, a federal low cost take, anma</p><p>mun shaku sosai da ita ,banda tsayi don</p><p>kuwa Fatima tafini tsayi , mutane suna kiran</p><p>kawancenmu tall nd short, inkaganmu</p><p>gwannin shaawa, duk hassadan mutum bai</p><p>isa yace yaga munyi fadaba.</p><p>Zaune nake akan kujera ina chatn a wayana,</p><p>saiga faiza tashigo cikin murmushi tace adda</p><p>maryam ana sallama dake awaje, ko kallonta</p><p>banyiba domin kuwa tasan bazuwa zanyiba</p><p>neman maganane yasaa takirani, nace sai ki</p><p>je a madAdina tunda bazaar ganeba ke dani,</p><p>tayi dariya sosai sannan tace wlh nafki tsayi</p><p>suma masu cewa basa ganemu neman</p><p>magane ga evidence a filli? Ni doguwa ke</p><p>guntuwa, bansan lokacin dana mike nabita</p><p>da gudu ba ,akuwa dagudu ta kwashe bata</p><p>nufii ko ina ba sai dakn momy, taje bayanta</p><p>tana cewa momy ki taimakamin wlh adda</p><p>maryam dukana zatay, momy tahade rai</p><p>sannan tace ke maryam bakyajn Magana</p><p>ko? Naja turus na tsaya sannan nace haba</p><p>momy, guntuwa fa tacemin, momy ta</p><p>kwashe da dariya sannan tace to karya</p><p>tamiki? Najuya ina huci, chatn dina naje</p><p>nacgaba dayi da grup din benaxir na</p><p>whatsapp wato burin ya mace, inajn dAdin</p><p>group din sosai, a hankal ta cuso kanta anty</p><p>maryam kiyi hakuri wallahy bzan karaba ko</p><p>kallonta banyiba dagudu tashige daki, lokacn</p><p>sallah nay namke nadaouro alwala sannan</p><p>na gabatar da sallah, nadauk hjabnna</p><p>nAsaako takalm nafito gun mota na tsaya,</p><p>Ibrahim driver yazo sannan yace hajiya</p><p>mutafine? Nace ae, nashga nazauna harzai</p><p>tayar saiga faiza da hijabi da taKALmi a</p><p>hannu dakuma jakan islamyanmu, tashgo</p><p>tana matsifa haba malam ibrahm tafiya</p><p>zakayi kabarni? Yace kiyi hakuri n azata</p><p>bazakijeba , t ace kana ganin adda maryam</p><p>sannan nmai zai hanani zuwa? Baice komai</p><p>ba sai hakuri daya bata muna tafiya sai tace</p><p>adda maryam laaa kiga shamsu nectarnk,</p><p>jyama yakirani wai kinki daukan wayanshi,</p><p>ckin fushii najuyo nace to mai bakin alllah</p><p>tsine, bakinki baya shiru chiichic chii kamar</p><p>parrot, hakan yasa tayi shru har muka isa</p><p>bata kara cewa komaibSIRRINA NE</p><p>Ni Benaxir Omar Zaune nake akan kujera</p><p>babu abunda nake tunani sai yanda zan je</p><p>wajen Maryam domin naji labarinta . duk da</p><p>nasan abune mai wahala sosai domin kuwa</p><p>nasan ta da zurfin ciki. Koda yake kawatace</p><p>kut da kut. Bazataban wahala ba gurin</p><p>gayamn labarinta ba. Donhaka namke cikin</p><p>azama nadau wanka nadaukl mukulln</p><p>motana nagayda umma sannan nace zanje</p><p>gidan maryam tace da sassafen nan/? Nace</p><p>labar zamuyi yau hala nakai dare, na kwash</p><p>kafa ban nufii ko ina ba sai gra. Na y hun</p><p>megadinsu yabudemin gate. Bayan</p><p>shiganane nasamu tana zaune a falo tana</p><p>karatun wani lttafina ikon Allah, tash tayi</p><p>ckn murna da farin cik wayyo besty oyoyoyo</p><p>na murmushi nazauna, ta aika aka kawo</p><p>aman abinci da kayan kwalama, nace</p><p>kawata yau gani da takarda da biro, don</p><p>allah labarnki zakban nida dalbaiana na</p><p>makaranta kowa ta naso tadau darasi, wani</p><p>kallo tamin wanda sa dana hadya yawu, kina</p><p>nufin sirrin nawa zaki gwadawa dunya?</p><p>Nace haba besty darasi rfa zaa dauka, tace</p><p>to saiki gyra zama domin kuwa zaMU kai</p><p>dare , Allah ya taimakeki maigdan baya nan,</p><p>anan nazuba na zomaye tafara kaMAR hakaSIRRINA NE</p><p>Ni Benaxir Omar Zaune nake akan kujera</p><p>babu abunda nake tunani sai yanda zan je</p><p>wajen Maryam domin naji labarinta . duk da</p><p>nasan abune mai wahala sosai domin kuwa</p><p>nasan ta da zurfin ciki. Koda yake kawatace</p><p>kut da kut. Bazataban wahala ba gurin</p><p>gayamn labarinta ba. Donhaka namke cikin</p><p>azama nadau wanka nadaukl mukulln</p><p>motana nagayda umma sannan nace zanje</p><p>gidan maryam tace da sassafen nan/? Nace</p><p>labar zamuyi yau hala nakai dare, na kwash</p><p>kafa ban nufii ko ina ba sai gra. Na y hun</p><p>megadinsu yabudemin gate. Bayan</p><p>shiganane nasamu tana zaune a falo tana</p><p>karatun wani lttafina ikon Allah, tash tayi</p><p>ckn murna da farin cik wayyo besty oyoyoyo</p><p>na murmushi nazauna, ta aika aka kawo</p><p>aman abinci da kayan kwalama, nace</p><p>kawata yau gani da takarda da biro, don</p><p>allah labarnki zakban nida dalbaiana na</p><p>makaranta kowa ta naso tadau darasi, wani</p><p>kallo tamin wanda sa dana hadya yawu, kina</p><p>nufin sirrin nawa zaki gwadawa dunya?</p><p>Nace haba besty darasi rfa zaa dauka, tace</p><p>to saiki gyra zama domin kuwa zaMU kai</p><p>dare , Allah ya taimakeki maigdan baya nan,</p><p>anan nazuba na zomaye tafara kaMAR hakaa</p><p>Har mukaje muka dawo bance matA Uffanba</p><p>saida nazo natarar momy ta kawo fruts wato</p><p>kuma nasan yau ranana ne da gyra tuni</p><p>nasake fuska nafara murmushi, faiza na ta</p><p>kalleni ta kwashe da da\rya domn kuwa ta</p><p>fahmci abunda nake nufi, wlh adda maryam</p><p>ko, nace aa faiza knga dam azan Gaymiki</p><p>wani srri knga mu gyra sai ingayamikii,</p><p>momy tashigo dasauri jaka a hannunta</p><p>zamuje gombe an aiko aimana ta haihu,</p><p>tsalle muka rinkyi wanda tuni mun manta da</p><p>maganan wanke fruits daman a tsani wankke</p><p>fruits faiza dasauri tamike donta dauko gyale</p><p>nima hakanne , momy dasauri tace to</p><p>mutum daya dole yazauna a cknku</p><p>sArakunan yawo, nayi jim sannan nace faiza</p><p>jeki sannan momy tace lami zata kawo sarin</p><p>damukayi inmuka tafi dukkanmu waxai karba</p><p>, haka kuwa akayi da daddy da momy</p><p>dakuma yaya abbakar suka tafi don taya</p><p>anty aimana murnan aihuwa shekaranta</p><p>goma sha uku bata haihu ba sai yau Allah</p><p>yanufe ta, tsabar murna namanta</p><p>bantambayi me aka Haifa ba, komawa nayi</p><p>nacgaba da chat dinA, tunda suncemn</p><p>washegari zasu dawo, dare nayi nadafA</p><p>indomie sannan narufo kofar nakwanta, a</p><p>whatsapp ne faiza ta turomiiin da hoton</p><p>jarriri tuni nasashi a dp, washegari</p><p>bantashiba sai karfe sha daya wanda kirane</p><p>yatasheni naduba nagani baffa ahmadu ne,</p><p>kanin dadyn mune uwa daya uba daya</p><p>batare da tunaniiiiiiin komai ba nadauka,</p><p>sallamu alaikum yace maryama kiina iina?</p><p>Nace ina gida baffa, yace to barin aiko dreba</p><p>yaxo yadaukeki, nace to, amma haka kawai</p><p>naj jikina yayi sany, nadauki wayata</p><p>zanturawa faiza message ta whatsapp</p><p>sainaga last seen dinta tun karfe 6 na asuba</p><p>nayi mamaki sosai saboda inkaga faiza bata</p><p>online to last seen dinta baya wuce some</p><p>minutes amma bazai taba kai awa dayaba,</p><p>Message dnta nagani wanda ta turomin</p><p>adda maryam kitashi asuba tayi yanxu</p><p>muma zamu dauko hanya iinmun iso lafya</p><p>to, inbamu isobar a yafemu, tsaki naja tare</p><p>dacewa wlhy faiza wani lokacin surutunta</p><p>yawansa har yansa tayi useless Magana,</p><p>wanka nashiga adaidai nan dreban yaxo</p><p>narufo gdan nashiga muka nufi federal low</p><p>cost don anan baffa na yaake, muna xuwa</p><p>nafara ganin motoci tunda kwanan gidan</p><p>baffa, hakan yasa nace to ko don hahuwan</p><p>anty aimanaa ne? anma kuma mazane kuma</p><p>duk sunzauna shiru alamun makoki, ban</p><p>tsaya wani tunaniba nafice a Motan na nufi</p><p>cikin gidan yanuwa nagani daga mai kuka</p><p>saimai tagumi, gabana yafadi rasss</p><p>musamman danaga da suka ganni kawai sai</p><p>aka fara jijjiga kai alamun tausauyina, dakin</p><p>jummare matan baffanmu nashige nasameta</p><p>kukA takeyi sosai, nace umma jummare don</p><p>Allah meye ke faruwa, batacemin komaiba</p><p>sai rungumana datayi tana kuka, aisha yar</p><p>shekara takwas ce tacemin adda maryam su</p><p>baba bauchine da faiza da yaya abbkar</p><p>sukayi hatsari suka mutu, dasauri umma</p><p>jummare take kokarin gwabe bakinta amma</p><p>ina hartafada, ido na zura mata, bansan</p><p>lokacin dana rike kaina ba uku uku nake</p><p>gani, wani ihu na nasa ko ince kara.</p><p>Bude idonayi dasauri narufe sannan kuma a</p><p>hankali nakara budewa, Faiza nagani a</p><p>gefena zaune take amma bandage ne a</p><p>daure a kanta dakuma gefen hannunta kuka</p><p>takeyi takasan makoshi, batasan nabude</p><p>idoba, juyawa nayi a hankali nayi umma</p><p>jummare nagani tana zaune akan sallaya, na</p><p>yunkura zan mike sai naji gum , dasauri</p><p>nadanyi wani kara washhhhhh, hakan yajawo</p><p>hankalin faiza gareni dasauri tamike umm</p><p>Jummare ta farka dasauri umma jummare</p><p>takarasa ta rikoni tana alhamdulila</p><p>alhamdulila alhamdullila, sai tafashe dakuka</p><p>faiza tace bara naje nakira likita, dasauri</p><p>tafice nidai kallonsu nake gakuma mamaki</p><p>daya isheni domin narasa dallili me aka</p><p>kawoni asibiti, to ko banda lafiya ne? to</p><p>amma tun yaushene banda lafiyan? Sannan</p><p>ina momy da daddy dakuma yaya abbakar</p><p>bangansuba sai umma jummare?innalilahi</p><p>wainna iilaihi rajiun, kainane yafara juyawa</p><p>sakamakon tunawa danay da maganan</p><p>fatyma , capko umma jummare nayi , umma</p><p>dagaske ne su daddy sun mutu? Dagaskene</p><p>nadawo marainiya banda kowa? Umma</p><p>dagaskene ni kadai ne yanxu? Wayyo</p><p>nAshga uku, umma ckin kuka tace a a</p><p>maryam kinada gatAnki momy da daddy</p><p>suannan har faiza bakiga faiza bane yAnzu?</p><p>Suna gidan anty aimana ne . nan nayi jum,</p><p>har faiza tashigo da likita anan nakare mata</p><p>kallo tarame ta kode gakuma ciwuwuka nan</p><p>namike xugum na cukumota faiza kigayamn</p><p>karyane su momy basu mutubako, wani irin</p><p>kuka tasake gamiida rike hannuna adda</p><p>maryam sunanan, nace to meya sameki/?</p><p>Duk ciwo ajikinki faiza ina wasa dake, zan</p><p>kamota likitan yajani yawuce dani kan gado</p><p>faiza tabard akin tana wani irin kuka mai</p><p>tsuma zuciya, Allura likitan yamin atake</p><p>kuma bacci ya kwashenii,</p><p>Idonabude ceiling din dakin nake kalla kuka</p><p>nakeji a gefena, dakumA maganganu, wanda</p><p>hakan yasa banyi motsiba don naji mai ake</p><p>fada ,ummma jummare ne tace kinga faiza</p><p>inbakyi hakuri kikayi shiruba tayaya zata</p><p>tashi akan gadon bayan targa tasa zargi a</p><p>ranta, kinsani sarai duk mai rai mamacine</p><p>saikiyi hakuri kinamusu adduan Allah</p><p>yajikansu kefa bakiida lafya amma kinki cin</p><p>abinci , faiza kiyi hakyri haka zaki godewa</p><p>ubangijinki ? bayan kinsan cewa duk cikin</p><p>motan ke kikayi rai? Cikin kuka faiza tace</p><p>umma jummare don allah kibarni nayi</p><p>kukana iyayefa narasa dukkansu biyu da</p><p>yayana, sAlati nafarayii wanda dakarfi</p><p>nakeyinsa dasauriiii suka miko dansuji</p><p>meyene, nace wayyo momy nah wayyo</p><p>momy kiyi hakuri kidawo, sauran yan dakin</p><p>ba abunda sukeyi sai kuka dakumA</p><p>tausayimin yadda rayuwana take, faiza ne</p><p>cikin kuka tace haba adda maryam meyasa</p><p>kike haka? Kedaya kamata ace mun musu</p><p>addua, amma tunranda suka rasu gashii</p><p>gobe zasu cika kwana 23 kullum kina kAra</p><p>jawowa kanki matsala, bafa akanmu aka fara</p><p>rasuwannan ba addua yakamata muy, cikin</p><p>sanyn jiki nace yanxu haka baku barni nayi</p><p>addua wa iyayena ba? Kuka kaisu? Tace to</p><p>adda maryam baki cikin hayyacinki tayaa</p><p>zaki musu? Balle drip din hannuna nayi</p><p>dakarfi wanda hakan yasa jini yake xuba</p><p>umma jummare taxo dasauri anma ina</p><p>harnamike zanbR dakin tAjawoni dakarfi ina</p><p>kuma zakije? Sai na kura mata ido , ina</p><p>tambayan kwalkwata ina zanje ? adaidai nan</p><p>baffanmu yashigo , yazauna yanata kallon,</p><p>sannan yace taci abinci sukaje a a ko minti</p><p>talatin batayiba da farkawa , yace to ku</p><p>rakata tayi brush sanan ku kintsata tasha ko</p><p>tea ne, sannan yamun sannu dajiki yafice,</p><p>faiiiza ce ta taimakamiiin nayi brush nayi</p><p>wanka wanda acewarta yau kwanaana</p><p>ashirin da uku rabona da wanka ko abnci</p><p>banama hayyacina; wani dogon riga nasaka</p><p>sannan tahadaminn tea nasha da ferfesun</p><p>hanta , kwata kwata bnajin taste anma dole</p><p>na nasha saboda umma jummare tasani a</p><p>gabaa, in gamawa suka kira likita yagama</p><p>gwaje gwajensa sannan yace yanxu kwarin</p><p>jkine yaragemin sannan yayi fada akanme</p><p>zaa barni nacire drip sannan baazo</p><p>ankirashiba, dayagma yatafi</p><p>Kwanana uku a asibiti, na warke sosai</p><p>kullum inakan sallaya ina rokawa iyayena</p><p>gafara Allahh yajiknasuuuu gann haka yasa</p><p>likitan yace zai sallamemu,randa ya sallemu</p><p>ranan bafffa yazo da mota aka kwashemu</p><p>bamu nufi ko inaba sai gidansa, nan wani</p><p>sabon kuka yazomin, yanzu shikenan narasa</p><p>family na, dagani sai faiza saikuma</p><p>Allahnmu, gidan baffa mukaje annan muka</p><p>samu wasu dangi anatamin sannu faiza ma</p><p>ankuncemata ciwonta, daki baffa yA</p><p>waremana sannan yace nmun huta zamuje</p><p>gidanmu mu kwaso kayamu don zaa rufe</p><p>gidan, kukanmu mukac sannan muka</p><p>dangnana, faizana duk tayi sanyi itanake</p><p>tausayi kasancewarta yarauta yanxu yarage</p><p>ni ce uwarta ni ce ubanta domin kuwa ni</p><p>narage mata, adaidai lokacin adda ummi</p><p>tashigo kallonta nayi sannan najuya kaina ,</p><p>donna tuna ashe tunda nakwanta batazo</p><p>tagaysheniba, saikuma nace to hla tanada</p><p>dalili barinje , don kuwa adda umm macece</p><p>daban taba ganba saukin kai dakuma</p><p>fahimta ga iya zama da mutnae, ta kalleni</p><p>cikin fuskan tausayi sannan tace besty</p><p>yahakuri nayii murmushi nace lao, banganki</p><p>a asibibtiba, kafin tabada amsa faiza tace</p><p>tunda aka kaiki ita take jnyanmu mu biyu</p><p>saida akayi rasuwa wa kakanta tatafi</p><p>washegari kika farfado, dasaur nAce yahakuri</p><p>besty? Bata amsaba tace besty yahakuri?</p><p>Allah yajikansu yamusu rahama yasa</p><p>sunhutaa, nace amin,</p><p>Anan nima namata taaziya aka kawo abinci</p><p>nidai ban iyaciba.faiza ce dai taci. Anan</p><p>adda ummi tace maryam? Yaushe zaki koma</p><p>makaranta. Wani irin murmushi nayi natuna</p><p>ashe ana boko? Nace wani term ma muke?</p><p>adda ummi tace kai kawata har kin manta?</p><p>muna third term ne. Anan nace hakane fa.</p><p>Mayb nxt week mukoma.sai dare ta tatafi.</p><p>Yan makarantanmi dayawa sunxo sunmana</p><p>taaziya har wanda bansaniba. Waya kuwa</p><p>mutane dayawa sunyi .muna kwance nida</p><p>faixa don washe gari zamu koma makaranta.</p><p>Donhaka nace ta tashi muje gida mu kwaso</p><p>kayanmu. Mukaje muka tattaro komatsanmu</p><p>wanda muke amfani dashi kayansu mama</p><p>duk anrufe dakin munadawowa aka rufo</p><p>gidan aka sallami masu aikin gidan. Nida</p><p>faixa muka zauna tsaf muka shirya dakin</p><p>yayi daidai. Tvn mu dasu dvd har fridge</p><p>dinmu dakuma laptops dinmu akwatinanmu</p><p>kowa hu hudu muka jera kayan kwaliyyanmu</p><p>dakin sai yayi kyau. Kaman nawata amarya.</p><p>Nashare dakin yayinda faixa ta wanke</p><p>bandaki tajera tsaf. Muna kai saiga ummita</p><p>tashigo saan faiza ce. Ta karewa dakin kallo</p><p>sannan tace yayi kyau wlh .faixa ce sarkin</p><p>surutu kuma dayake suna dan wasanninsu</p><p>tace yason ranki. Yafi naki kyau ko? tayi</p><p>murmushi wanda a tunanina na dolene</p><p>sannan tace sosaima. Anma dadin abun a</p><p>kasanmu naku yake.tanafadin haka tafice.</p><p>Banyi tunanin komaiba faiza kuwa tace kujita</p><p>adda maryam daga wasa zata gasamin</p><p>magana. Najuyo sannan nace faiza kinsani</p><p>sarai cewa baffa basu wani shiri da daddy</p><p>haka gydannan. Tunda kaddara ta kawomu</p><p>zama saiki kaudakai. Wannan zolayan naki</p><p>kibari .ki nutsu faiza banso a zo a</p><p>wulakantamin ke. Kuka nafarayi wanda</p><p>itama shitafara muka gama kukanmu sannan</p><p>nace mata faiza tashi kisa mana caji. Anan</p><p>adda ummi tashigo a sanyaye tace kardai</p><p>kucenin haryanxu kukan kukeyi na kauda kai.</p><p>Tanata tambaya shiru nayi faiza ce tamayar</p><p>mata da komi. Ta jinjina kai sannan tace irin</p><p>wannan kananun abubuwan bai kamata</p><p>maryam kina daukaba saboda bai kamataba</p><p>kicire komai a ranki. Nace to. Muka danyi</p><p>tadi kafin tatafi.washegari muka shirya tsaf</p><p>zamu tafi makaranta baffanmu yakiramu</p><p>sannan yace. Dreba zaina kaiku. Mukace to.</p><p>Kullum muje makaranta mudawo lami lafiya.</p><p>Ba hantara bakomai tsakaninmu da gidan</p><p>baffanmu amma benaxir kinsan wani abu?</p><p>sai nazama kamanki aduk lokacin dakike</p><p>tareda mutane. Wato karantansu.karanta</p><p>tsaf nayiwa umma jummare da baffa</p><p>dakuma ummita. Suna janmu a jiki amma a</p><p>zahirin gaskiya cutanmu sukeyi ta kasa.</p><p>Baidamenba kuma bangayawa faizaba don</p><p>nasan saita gayamusu magana. Na fahimci</p><p>hakane ganin kamfanin dady baffa yashiga</p><p>juyawa yana bude nasa kamfanin duk arxikin</p><p>daddy nasan shiga da ficensa hatta</p><p>directorn. Da manajojin kamfanin daddy</p><p>yahadani dasu donhaka nakan kirasu naji ya</p><p>kwanan gun.anan manajan yake gayamin</p><p>baffa yakori duk maaikatan gun yasako</p><p>wasu. Kuma kudin da akesamu ada baassmu</p><p>yanxu don kamfanin biscuit ne. Sannan</p><p>akwai wata rana ummita naji suna tadi da</p><p>umma jummare wai itama amata irin</p><p>dakinmu ko ita datake yar gydan bata da</p><p>abun damuke dashi saimu. Tace mata ki</p><p>kwantar da hankalinki komai yskusa zuwa</p><p>karshe tufkan hanci zamu musu don</p><p>dukiyansu saura kiris tashigo hsnnunmu.</p><p>Manajan nakra donjin ya gun take anan yace</p><p>dama daddy da akayi sighning kamfsnin nida</p><p>faiza ne next of kin dinshi kamfsnin yaya</p><p>abbakar ma nine. Donhaka dasuka tashi fitar</p><p>da kudi kimanin miliyan 23 sai bankin ta</p><p>bukaci sighnature na ko na faiza tunda mu</p><p>akasaka. Jihaka yasa nanemo faiza narufe</p><p>kofan dakin sannan nsmata bayani game</p><p>dajan kunnenta. Kods wasa kar baffa kowani</p><p>ya yaudareki ki yi sighning inkikayi kin gama</p><p>da rayuwanmi. Faiza ta mugun tsorata harda</p><p>kukanta. Ashe su baffa zaman cuta suke</p><p>damu? lalle zamanin yanxu kudi yafi</p><p>xumunci.</p><p>Nikam dai kunne najamata. Karki kuskura</p><p>kowani lallami zaimiki tace to. Nakira</p><p>manajan nace masa najawa faiza kunne</p><p>yakwantar da hankalinsa yanuna bakomai</p><p>sannan namasa godiya. Aranan abun</p><p>yadamen. Nace faiza kiban labari meya</p><p>farune daxuwanku har hatsarinnan. Sannan</p><p>gaskiya zankira anty aimana don naji ya dan</p><p>nata yake. Anan nakira ta muka gaysa</p><p>takaramin taaziya gameda min nasiha sosai</p><p>akan rayuwa. Tace ai gobe ma zamuxo. Tun</p><p>jibi ne arbain. Nace hakane anty aimana</p><p>saikunxo. Bayan nakashe wayan faiza sai</p><p>whatsapp take sannan nace dawa kike chat</p><p>ne haka? tayi murmushi sannan tace anty</p><p>benaxir ne tayi postn a grup dinta shine</p><p>abun yaban dariya muke dan tadi akai. Na</p><p>jinjina kai sannan nace wannan kam ai sai</p><p>ahankali. Kucilan yarinya sai manyancen</p><p>tsiya. Dariya sosai faiza tayi sannan tace</p><p>wlh kar tajiki don yanxu zakuyi rikici. Aiba</p><p>yaro zancen rayuwa da ilmi nace hakane.</p><p>Dafatan zaa amfana .nidai taso kiban labari</p><p>akwai abunda zan binciko manane. Ta taso</p><p>tazo sannan tace. Bayan mun bar gida sai</p><p>mukadau hanyan gombe har muka isa momy</p><p>da daddy na abunda suke sai tadin dan da</p><p>aka haifa da yadda zaayi sunan. Muna isa</p><p>mukaje asibiti don baa sallametaba tana</p><p>gun. Wlh adda maryam dan kyakyawa mu</p><p>yadauko ga hanci ga ido. Haka mukajira ana</p><p>sallamata mukaje gyda bayan munyi sallah</p><p>munci abinci shine nafita nabar momy da</p><p>anty aimana a daki naje falo ina chatn dina.</p><p>Yayinda uncle abu wato mijin anty aimana</p><p>suke zaune da daddy daga baya daddy da</p><p>yaya abbakar suka tafi gida. Wato gidanmu</p><p>na gombe .nida momy kuma muka kwana a</p><p>gydan anty aimana. Karfe tara nasafe daddy</p><p>yace mushirya mudawo donke kadai aka bari</p><p>a gyda. .nikuma dama tunda asuba namiki</p><p>text ta whatsapp akan kitashi sallahn asuba</p><p>sannan gamunan zuwa kimana addua. A</p><p>hanyane wata trailern mai ta yanko ta</p><p>gabanmu daga kwana daddy yayi kokarin</p><p>kaucea amma ina tabi takan motan. Momy</p><p>da daddy ne a gaba saini da yaya abbakar</p><p>abaya hakan yasa tabita gabansu. Ammafa</p><p>kinsan abun mamaki? ko kwarzane babu a</p><p>jikinsu daddy nema jini yadan xuba ta</p><p>kanshi. Nikuma dogon suma nayi da</p><p>ciwuwuka da dama. Ahakadai nafarka</p><p>naganni a asibiti wai ashe nima kwanana</p><p>hudu a asibiti har anbinne. Yaya abbakar</p><p>kuma a kwalbatin daya fadane yasha ruwa</p><p>sosai a yanda aka gayamin wato dai ruwa</p><p>tacishi. Dukkanmu hawaye muke sharewa a</p><p>lokacin datake bada labarin. Sannan tace to</p><p>shinefa dana farfado naga halinda kike ciki</p><p>tuni nawa ciwon ya warke. Bamuyi</p><p>tsammani zakiyi raiba. Ankara miki jini da</p><p>ruwa .abinci sai ta tube ake baki. Allurai ma</p><p>ta drip akesawa da maguna. Numfashinki da</p><p>kyar yake fita. Duk wanda yaganki a lokacin</p><p>saiya tausaya. Na jinjina kai sosai. Sannan</p><p>nace Allah yajikansu yamusu rahama tace</p><p>amin. Sannan nace faiza abunda yakamata</p><p>muyi shine zamu tashi tsaye . Karmu bari</p><p>bayin Allahn nan su cucemu. Faiza nasan</p><p>yarintarki ko bana nan koda wasa inwani</p><p>abu yafaru ko sunsaki wani abu think before</p><p>you act. Use your brain for wat dey are</p><p>meant for .tace to adda maryam insha Allah</p><p>Ahaka mukavzauna a gydan har nagama</p><p>secondry na. Faiza kuma na ss2. Duk</p><p>takunsu ina hankaltansu. Dazaran sun bullo</p><p>tawani gu sainabi na toshe. Duk da dukiya</p><p>kam yanxu suna abunda sukaga dama dashi</p><p>.baffanmu mutum ne mai albuzaaranci</p><p>daddyma daya tara kudin baitaba spendn for</p><p>nothing ba. Nasan kowacce ramadan daddy</p><p>nafitar da buhu nashinkafa gero da flour</p><p>dubu uku uku. Yaraba. Sannan yabada motar</p><p>kalanzir akai massalaci araba. Kayan sallah</p><p>musamman yanayi wani gydan marayi dake</p><p>kasan layinmu. Anma baffa daga xuwa hutu</p><p>wannan kasan sainan. Infact yanxu yadena</p><p>zuwa aiki .dukiyanmu yake fataka dashi. Duk</p><p>da akwai kimanin miliyan 36 a account din</p><p>daddy wanda yakeson fitarwa anma hakan</p><p>ta gagara. Nasa manajan kamfanin ya</p><p>tattara duplicates din files sannan ya ajiye.</p><p>Azuciyana na kudiri zan karanta business</p><p>mngt.duk da nayi niyyan karanta medicine</p><p>anma saboda baffanmu nafara karanta wa a</p><p>atbu . Nayi niyyan kama daki anma gudun</p><p>halinda faiza zatashiga yasa naxauna. A</p><p>yanxu motan da daddy yabamu anma driver</p><p>ke kaimu shine nadauko nake hawa accura</p><p>ce. Randa zan dauko nasamu baffa a falo.</p><p>Na tsuguna na gaysheshi sannan nace</p><p>bappah. Inason mukkulin gida. Ya kallen</p><p>sannan yace mezakiyi dashi? Nace zandauki</p><p>motata ce. Yace kinada motane? Nadaga kai</p><p>sannan nace daddy yaban anma don ban</p><p>iyaba sannan yace bankai 18 ba kar akarya</p><p>doka yasa ake kaini. Ina magananne raina a</p><p>hade. Benazir fuskata kaman taki ne. Inada</p><p>nake gixo sosai. Duk a hanyan inkika ganni</p><p>baki sanniba zaki dau inada girman kai</p><p>sosai.sannan banda sakewa anma idan</p><p>muka saba shikenan.ina yiwa mutane gixo</p><p>wasu nacewa kwarjinine donkuwa duk</p><p>girman mutum idan zan hada rai na yi</p><p>magana to bazai kawo rainin hankali ba.</p><p>Hakan nayiwa baffanmu wanda yayi shiru</p><p>sannan can yace dama akwai wasu</p><p>documents wanda ake bukatar sighning dinki</p><p>kona faiza. Tunda kune magadan marigayi.</p><p>Murmushi nayi. Saboda i was waitn for dix</p><p>moment a year back. Ganin murmushinane</p><p>yasa yace zan hadaki da manajan zaiyi</p><p>directn dinki ga duk wasu files . Na gyada</p><p>kai sannan nace to. Sai na jinjina kai nace</p><p>baffa inbazaka damuba inaso mukoma</p><p>gydanmu dasauri yakallen meyasa? kintaba</p><p>ganin inda yanmata suka zauna sukadai? Na</p><p>girgiza kai sannan nace a a bamu kadai ba.</p><p>Zamu kira umma . Umma kanwar momy ne</p><p>uwa daya uba daya.danta dayane namiji</p><p>yanzu yana moscow yana karatu .aminu</p><p>sunansa tunda mijinta yarasu bata kara</p><p>aureba. Ya girgiza kai yace ba inda zakuje</p><p>ku zauna anan. Namike nafice . Inashiga</p><p>daki nace faiza shirya zamu fita yanxu tana</p><p>whatsapp tace tooo. Tamike tana sa</p><p>kaya.adda maryam ki canjamin waya. Batare</p><p>dana kalletaba nace wani waya kikeso. Tace</p><p>galaxy s4 zoom. Nace muje inmuna</p><p>dawowa. Nadauki atm card dina dakuma</p><p>littafina don zamubi ta makaranta. Dogon</p><p>rigane baki ajikina da ratsin purple desighn</p><p>din yahadu sosai dady ne yasayamin a</p><p>egypt. Tun asali mukam mun saba don</p><p>komai dady acan yake sayomana saimun</p><p>fara amfani da jimawa zamu gani a nja.</p><p>Wayata nadauka tareda cewa adda ummi</p><p>kishirya plx zaki rakani. In black nd purple</p><p>plx. Nakashe ta fahimci menake nufi don duk</p><p>inda zamuje to colour daya muke matchn.</p><p>Gamu farare saidai ni guntuwa ita doguwa.</p><p>Karfa mutum yace guntuwa sosai. A a wlh</p><p>guntancina yakarban sosai. I love it. Munfito</p><p>kenan mukaci karo da ummita dawasu</p><p>kawayenta nikam shigewa nayi yayinda faiza</p><p>ta tsaya suna magana. Inashiga motan nayi</p><p>horn dasauri tazo tashige. Glass dina nasaka</p><p>na kamfanin loius vuitton wanda dubu sha</p><p>biyu nasaya. Munyi matukar kyau sosai</p><p>bannufi ko inaba sai fed.low .cost muna isa</p><p>kofar gydansu adda ummi nakirata. Tana</p><p>fitowa faiza tafita takoma baya. Itama dogon</p><p>rigan tasaka amma nata purple sai fatsin</p><p>baki ajiki. Da glass dinta da purse amma duk</p><p>na gucci yayinda nikuma komai na loius</p><p>vuitton. Muna tafiya ko ina muka ratsa sai</p><p>ankallemu .munyi kyau sosai. Nanufi</p><p>kamfanin inashiga maaikatan kallo suka</p><p>bimu dasu banbi takansuba nace nazo</p><p>neman manajan gun. Dama munyi waya da</p><p>manajana cewa zanje guj manajan da baffa</p><p>yasa duk yanda mukayi zangayamishi. Wani</p><p>mutum ne yace waye asaki zata ga manajan</p><p>namike. Sannan yace biyoni. Nabi sawunsa</p><p>taredacewa faiza da adda ummi ina</p><p>xuwa.munashiga naganshi zaune akan</p><p>kujera anma kujeran tabaya ne donhaka</p><p>nanemi kujera nazauna. Naxuba fuskan. NO</p><p>RAINI .munkai akalla minti goma sannan</p><p>yajuyo. Har yanxu glass dinane a fuskata.</p><p>Batare da ya kalleniba yace. Meke tafe</p><p>dake? banyi maganaba. Naciro card nabashi</p><p>yakalli katin sannan yace alhaji said ne ya</p><p>aikoki? nace ae. Yaciro wasu documents da</p><p>filez yana wani irin murmushi alamun sunyi</p><p>nasara sannan yace gasu dukka zakiyi</p><p>sighnin</p><p>Na kalli files din daya bayan daya.daya</p><p>nafitar dakudine miliyan 23 .wanda banki</p><p>tabukata. Daya kuma na reownation na</p><p>kamfaninne wato komai xai koma hannuj</p><p>baffa hatta suna saisu canja.a xuciyana</p><p>kuwa mamakin jahilcinsu nake. Wani irin</p><p>haukane haka? ga karara dukiyana dana</p><p>kwanta zai salwanta anma don banida</p><p>hankali nayi sighnin? ko an gayamusu</p><p>bansan menakeyibane? lallai. Na bugasu</p><p>akan table din.sannan cikin sanyayyar</p><p>muryata nima batare dana kalleshi ba nace.</p><p>Thers no way i should sighn this. Dasauri</p><p>yajuyo akanme ? kasancewar nasan munada</p><p>duplicate din nida manajana na. Yasa</p><p>nadauki files din kyaaaaaaassssssss na yaga</p><p>na watsa masa kan table din .sannan nacire</p><p>glass dina nace THIS IS A GAME OF CHESS.</p><p>YOU EITHER WIN OR LOSS. DUDE I USE MY</p><p>BRAIN FOR WAT IT IS MEANT FOR. Sannan</p><p>na taba kaina nace I THINK. Namike nabar</p><p>masa office din kallo yabini dashi. Inafitowa</p><p>nanufisu faiza kutashi mutafi. A mota nake</p><p>basu labarin abunda yafaru. Dariya faiza tayi</p><p>tare dacewa oooo naso naga yadda</p><p>fuskanshi zaiyi. Anma adda maryam babban</p><p>mutum ne ko. Nace a a fa. Bai dare shekara</p><p>30 ba. Matashine mai ji dakanshi. Adda</p><p>ummi tace amma kingama dashi wlh. Nace</p><p>ai inyasan wata baisan wataba. Inbanda</p><p>hauka. Niba yar shekara gomaba shekarana</p><p>19 amma wai akawomin files din dukiya ina</p><p>sighning sunbar hannunmu sai inyi?</p><p>stupidity behind its head.atbu muka wuce</p><p>inda naje nayi test . Mundawo dare dare</p><p>bayan mun idda cin abinci namike zanje</p><p>dauko ruwa a falo don ruwan dakinmu</p><p>yakare.adaidai kofan zanshiga naja turus na</p><p>tsaya sakamakon maganan danaji</p><p>anayi..alhaji gaskiya kabar yarannan subar</p><p>nan. Inbahakaba bazamu cimma buriba.</p><p>Yarinyannan maryam basira take dashi</p><p>wayooo . Tana hankalce damu kuma tasan</p><p>arxikinsu mukeci. Kabarsu sukoma gun ita</p><p>gwaggonsu kaga insunyi sighnin kudin muna</p><p>kwasa saimubar kasan. Gwaggon tasu sai</p><p>taji dasi. Yace hakanefa. Anma aimana</p><p>zatayi zargi . Taja tsaki sannan tace kotayi</p><p>zargin akwai abunda zatayine? itada ake</p><p>airenta? yace a a. Tace to kawai su tattara</p><p>suje can. Haka kawai yara kanana zasu</p><p>toshemana hanyan arxiki. Dasauri nakoma</p><p>daki. Wani makulelem yawu na hadiya. Faiza</p><p>na chatn donhaka bata fahimci menakeciki</p><p>ba. Washegari baffa yakiran akan cewa</p><p>yakira umma yamata magana sannan kuma</p><p>yau zataxo donhaka mushirya mukoma can</p><p>gida. Ban gwada masa komaiba nace</p><p>nagode. Namike. A ranan muka tattara muka</p><p>koma gydanmu umma taxo. Haka maaikata</p><p>ankawo mana sabbi . Har dreba wanda</p><p>zainakai faiza makaranta. Tundaga ranar</p><p>nafara rokon Allah yadaurani akan bawan</p><p>Allahn nan. Kar yabashi ikonyi da</p><p>dukiyanmu. Allah yakarenu sannan yajikan</p><p>iyayenmu.baffa yskirani maryam bakiyi</p><p>sighning ba. Nace baffa inaga ba files din</p><p>dakace yaban yabaniba. Wannan fa nafitar</p><p>dakudine miliyan 23 mexaayi dawannan</p><p>kudin? ba ginin masallaciba ba komai ba.</p><p>Sarrafa dukiyan akeyi. Shiru yayi sannan</p><p>yace xanmishi magana basu nace yabakiba.</p><p>Tuki nakeyi dasauri domin kuwa nayi lattin</p><p>lectures ga lecturern inya rigaka shiga aji</p><p>shikenan bazaka shiga ba. Hanya daya ne</p><p>kuma yaxama dole sai kawuce kan maizuwa</p><p>yawuce. Na sako kai kenan shima ya sako</p><p>kai. Raina yabaci to yakoma sai nawuce</p><p>anma naga sai xuwa yake. Hakan yasa nayi</p><p>parkn motata. Shima parkn din yayi. Tun ina</p><p>Allah Allah harna hakura da kectures din.</p><p>Inaso inga wani bawan Allah ne who has d</p><p>guts. Minti goma saiga wani mota yaxo</p><p>tabayana. Yana horn banko kullashiba.</p><p>Hakan yasa yafito yabugamin glas nabude</p><p>don glas din masu duhune. Yace hajiya meke</p><p>faruwa ko notanne yabaci? nace ko kadan</p><p>inajira wancan yaban hanyane. Sai yace to</p><p>bari inmar magana. Bansan yasuka kareba</p><p>yadaeo hajiya kiyi hakuri wlh yaki komawa.</p><p>Nace to inaga saidai kayi hakuri don zaj iya</p><p>kwana a wajennan. Bana acceptn challenges</p><p>agun maza. Ganin motan danake ciki kuma</p><p>lambar motar sunan daddy ne wato USMAN</p><p>duk motoccinmu sunan kenan. Don duk</p><p>wanda yake bauchi yasan alhaji usman.</p><p>Yakoma. Nima saina kunna ac. Nadauko</p><p>wayata nafara chatn.can naji anbuga glass</p><p>nasaukar shima glas ne a idonsa waikibada</p><p>nukbanki zaimi magana kokuma ki janye don</p><p>bakisan koshi wayeba. Glass dina namayar</p><p>narufe yakai minti goma ahaka sannan</p><p>yakoma. Bansan meyace ba. Anma ni</p><p>mamaki nakeyi waye mai motar to? kowaye</p><p>lallai yahadu da gamonshi. . Buga glass din</p><p>akayi sannan naduba aliyu nagani. Aliyu</p><p>klasmate dinane sosai muna shiri</p><p>yatambayeni ko lafiya nace babufa hutawa</p><p>nake . Yace bakije lectures bane. Nace</p><p>wannan aikinne yahanani xuwa. Anma in</p><p>anshiga na 5 ka kirani yawuce tagabanan</p><p>yazo daidai gun wannan motan naga sun</p><p>tsayar dashi ba abunda yazo raina har</p><p>yagama yatafi. Wayana naga ankira. New</p><p>nomber. Nadauka kenan. Naji ance kina ina</p><p>nace bank road. Akace to kixo asibiti ankade</p><p>kanwarki faiza. Cikin rudani naja motan</p><p>najuya nafice nabarsu agun nazo daidai go</p><p>slow naga wannan motan sunbiyoni yawaina</p><p>glass dinsa kasa tare da sauke glass din</p><p>fuskanshi yakalleni yamayar tsaki naja</p><p>donkuwa naganeshi. Wanda nasamu a office</p><p>din baffane wato manajansa. Dasauri</p><p>nashiga asibitin dawata nurse naci karo plx</p><p>anzo dawata yanxu as accident patient?</p><p>Tace a a. Nace thnx nadaga zankira wannan</p><p>numban naji aina suke sainaga call dinsa</p><p>yashigo ina dauka kafin nace komai yace</p><p>baki gantaba ko? nace ae. Yace juyo bakin</p><p>gate ina juyawa nagansu. Shinedai a tsaye</p><p>yaja glass dinshi yana kallona yana</p><p>murmushi sannan yace. THIS IS A GAME OF</p><p>CHESS YU EITHER LOOSE OW WIN. IVE WON</p><p>THE FIRST CHALLENGE yakashe wayan.</p><p>Yaja motarsa yawuce. Bansan lokacin dana</p><p>wurga wayan dakarfiba</p><p>Bakin ciki yasa dana koma motaba ban iya</p><p>tukawaba zama nayi dim ina tunani lallai</p><p>gayen nan ya balain raina mini hankali.</p><p>Amma karyadamu yahadu da daidai shi Lets</p><p>continue the game. Naja way Ina tafiya</p><p>amma hankalina a tashe gamida bacin rai</p><p>wannanma ai rainin hankali ne. Ina xuwa</p><p>nasamu umma a zaune tana karatun wani</p><p>littafin addini. Hakan yasa nashige daki ina</p><p>msi cewa umma yakike yakuma yagyda.</p><p>Tace yanzu faiza tadawo tana tambayana</p><p>ke. Ina shiga nace aikuwa yanxu aka</p><p>gamamin rainin hankali. Dariya tayi saannan</p><p>tace. Kedawaye haka. Nace wani dan rainin</p><p>hankali ne. Inashiga bandaki nasakewa kaina</p><p>ruwan zafi. Sannan nadauro alwala nayi</p><p>sallah. Har yanxu nagagara cire fuskansa a</p><p>tunanina. Gixo yakemun sosai. Haushinsa ne</p><p>kokuma me? Nagagara ganewa anma</p><p>maganan data zauna araina shine tsabar jin</p><p>haushinshi danakeyine yasa hakan. Littafina</p><p>nadauko nadan duba amma kuma shine a</p><p>tunanina. Fuskarsa nake gani. Dogo ne</p><p>launinsa irin fulanin asali gashin kansa ya</p><p>kwanta luf. Ga idanuwa kaman namace. Idan</p><p>ba gixoba nidai yanamun kama da abishek</p><p>abachan. Faiza ce tashigo .dasauri tace</p><p>meyasamu wayanki shiru tun safe? Nace</p><p>kumafa yana kunne meye kaman wani</p><p>zakiban kudi. Tace uhm. Wanine yaxo wai</p><p>manajan baffa. Tuni na juyo meyace?. Tace</p><p>files yakawomin wai nayi sighning shine</p><p>nace mishi a a ke yakamats but yarokeni</p><p>naki. Shine nake kiran numbanki. Nace</p><p>gwara da kika yi haka yanxu haka trackn</p><p>dinsa nakeyi. Tace to si yabada leta nabaki.</p><p>Ta mikomin nabude ksmshin turare ne</p><p>yabushe hancina sannan nace uhm meye</p><p>kuma nafesa turare. Nabude ina karantawa a</p><p>nutse Maryam nasan zakiyi mamaki. Anma</p><p>bakomsi bane yasa narubuto wannan</p><p>wasikan illa inaso nazama shugaban birnin</p><p>xuciyanki.maana inmallake. Amma fa bawai</p><p>shawara bane . Noo dole ne. Dole kisoni</p><p>Wani wawan tsaki naja tare dacewa wannan</p><p>giya yasha lokacin daya turo wasikan</p><p>kokuma bacci yakeyi? Faiza tayi dariya</p><p>sannan tace hahahaha lafiyanshi lao dai</p><p>yabani, na kalli wasikan dakyau sannan nace</p><p>badamuwa wannan wasikan dashi zanyi mar</p><p>reply, dare dare faiza tanadai chat dinta</p><p>nikuwa a kundume a cikin bargo ba abunda</p><p>nake tunani sai bawan Allahn mutumn dako</p><p>sunansa bansaniiba abakacin duk abinda</p><p>yayii yabatamin rai, saikuma naji yana</p><p>burgen, gaskya da sakel, wani haushin kaina</p><p>naji a lokaci guda kuma narinka buga jikin</p><p>gadon faiza ce ta taso adda maryam , eya</p><p>faru? Cikim sheshekar kuka nace faiza wlh</p><p>son mutumnnan nakeyi narasa yazanyi, tayi</p><p>shiru sannan tace yakamata kiyi yaki da</p><p>xuciyankii domin wanda kikeso makiyinmune,</p><p>kuma idan kika bari sonshi yaci galaba</p><p>akanki, to bazamuci galaba akansuba,</p><p>comon saikace ba adda maryam din dana</p><p>saniba? Wacce bata barin rainin hankali?</p><p>Nayi shiru sannan nace shikenan faiza zanbi</p><p>yadda kikace, ahaka muka kwanta anma</p><p>idan nace nayi bacci to nayii katon karya ,</p><p>domn kuwa yadda naga dare haka naga</p><p>safya, nadauro alwala nai sallah tukun ina</p><p>adduiona, namike nashiga wanka domin</p><p>inada lectures karfe bakwai, faiza ma</p><p>jarabawa take dashi donsun fara waec,</p><p>nashiryya tsaf nadauki jakaana nafito</p><p>nasamu umma a falo da kayan karyawa</p><p>agabanta nazauna naci dankali da kwai</p><p>nakora da tea dasauri namke umma sai</p><p>nadawo tace to Allah ya kiyaye hanya, adaidi</p><p>roundabout kawai nahadu da go slow,</p><p>hankalina yatashi sosai, saboda wannan</p><p>sabon lecturer tunda yafara lectures</p><p>bansamu nayi attending ba anma course</p><p>mate dita fatyma matori, tacemin tabbas</p><p>wannan baya murmush sannan inyargaka</p><p>shiga shikenan. Karfe bakwai da kwata tamn</p><p>acikin atbu dakaman bazanjeba sai nace</p><p>barinje dai mugani ko zai barni, mutane</p><p>hudu nagani awaje suna tsaye uku maza</p><p>mace daya , na tsaya gefenta sannan nace</p><p>baya bari a shigane tace ae wlh, nma sai</p><p>naja na tsaya, can kuma wata xucyan tace</p><p>to meye amfann tsayuwana , nakoma mana,</p><p>harna juya nacee barin leka kozanga faty</p><p>mator, nakuwa ganta acan bayan raba danu</p><p>danayi, najuyo kenan adada lokacn muka</p><p>hada iido jakan hannuna ne ya sulube yafadii</p><p>shma littafn daya rike sai ta fadil, gabana ne</p><p>yafadi lallai adanasan wannann ne lecturern</p><p>danazo da shrirna anma yanxunma bata</p><p>baciba, nabata rai sannan najuya nabar gun,</p><p>umarni yabayar da akirani nace sukoma suce</p><p>bazanxoba, hostel dinsu fattyma matori naje</p><p>sannan nazauna akkofan dakin , mnti talatin</p><p>sai gata tadawo , tana ganina tace yanxu</p><p>nake da niyyan inkiraki , ke kin janyoma</p><p>mutane matsifa ,attendance yadauka kuma</p><p>yace gobe zaiyi test wlh duk wnd bajeba</p><p>shiyasani, naja tsaki nace can ta matse</p><p>mishi wlh bazan kara xuwa ba, dasauri tace</p><p>haba maryam aina kka sanshi? Wayeshi?</p><p>Meye a tsakaninku? Nace ba komai jex</p><p>kawai mundanyi rikici dashi a hanyane</p><p>kwanak, tace to wlh kinjawa mutane ,</p><p>kitaimaka gobe kishga sawun wanda zaaje</p><p>neman hakuri kozai hakura, wata tsaki naja</p><p>nace saidai kurkuyi karatun , haba kaata</p><p>bansank8da bakn haliba, nikam wayata</p><p>nadauka nakira adda umm plx kna nane ?</p><p>tace natafi gombe , nace shine tsabar rashin</p><p>mutunci ko sallama babu, tace a a wlhm</p><p>kduba wayank zakga missed calls , nalkrak</p><p>baki daukaba, nace to shikenan , tace ya</p><p>maigidanki? Nace wakenan tace manaja</p><p>namu mana, dasauri nace bulluktu black</p><p>mutuwa, ta kwashe da dariya kun raianama</p><p>mutane hankali waiku game opf chess kun</p><p>tsaya kuna soyayyya aboye, dariya nayi</p><p>sanna nnace ka kawata , tace serous knsan</p><p>sarai cewa bamai karantank kaman n a</p><p>duniyannan,nace hakane ahaka mukadany</p><p>tadi nakashe , fatyma mator kuwa tuni</p><p>tashge dski, tadai rokona take don Allah</p><p>nataamaka nazo gobe koza j kan wasu</p><p>donta lura kaman yana shayna, nace to</p><p>,sannan namke nafto motana nashiga</p><p>adaadai bakn gate gurn dasuke duba mototci</p><p>naci karo dashi zai fice, saisamn hannu yake</p><p>alamun n tsaya anma ina tuni nawuceshi</p><p>yakuwa biyoni , gida na nufa, dasaur a</p><p>hanya nace faiza kn dawone? Tace ae nace</p><p>ftomn da kofin ruwa tace to,</p><p>nashiganasameta atsauye da kofi nakarba</p><p>nadauko takardan letan dayamn na kwaba</p><p>ack ya kwabu sosai kaman tuwo, sagashi</p><p>yashigo, hun yayi alamun naje da kofin a</p><p>hannnuna nataka nakarasa gareshi nadan</p><p>sauko da fuskana sannu ko, na kalleshi</p><p>batare da bash amsa ba, na debvo kullun</p><p>papern dana dama nan, nashafa mish a</p><p>fuska sumul har nagama shafawa bsi motsa</p><p>ba sannan bace koamk ba, sannan nace</p><p>gobe ka kara biyoni muhallina zan maka</p><p>abinda yafi haka da muni, yayi dariyan keta</p><p>sannan yace nagode bazna cireba sai na</p><p>tabbaata yabushe, dasi zan mki replyn</p><p>amsan chess dink, ya figi motanshi kaman</p><p>zai kadeni dasauri na kauce , wata irin</p><p>dariya yayi sannna nuyawuce</p><p>Cikin gida nawuce koba komai naji relief.</p><p>akan tsiyan dayamin. Washe gari karfe</p><p>bakwai fatyma matori tafara kirana a waya .</p><p>Maryam kidubi girman Allah kixo wlh bawan</p><p>Allahn nan zaiyi mana tsiya. Kaman nace</p><p>saime saikuma natuna wlh in fatyma ce</p><p>saitarama ko tayaya. Hakan yasa nace mata</p><p>to ina zuwa. Sanin zamuyi tsiya dashi yasa</p><p>nasa dogon riga baki. Nayi rolling da baki</p><p>nasa snickers dina vincci shima baki.</p><p>Nadauko glass dina. Namaka. Don karma</p><p>yatukamin tsiya naji kunya. Ina isa yauma</p><p>nayi latti . Kuma naga hall din acike da</p><p>alama wato yabada test din. Ina shigowa</p><p>yace Keeee ina zaki?!!! Na batarai kaman</p><p>tunds Allah yayini bantaba dariyaba sannan</p><p>nacire glass din fuskan tawa don yaga bacin</p><p>rai na. Kur yamin abunda zaa rainani.</p><p>Donkuwa bazaiji da dadi ba. Bance komai</p><p>ba. Kallonshi kawai nakr. Shima kallon nawa</p><p>yake amma da alama dariya ta tirkeshi yine</p><p>kawai bahalinyi saboda mutane. Anma ni</p><p>nasan halin abuna. Yamikomin paper kije</p><p>kirubuta yanxu kiyi summiting.kuma Kinyi</p><p>laifi biyu. Kibiyoni office kisameni ko na</p><p>cancelling miki papers. Koda kuwa exams</p><p>ne. Cikin rashin damuwa nace ohkay no</p><p>problem.nakarasa gunshi daniyyan in karba</p><p>kawai yaja yace anma bakida kunya. Ki</p><p>tsaya agun. Har nagama abunda zanyi kuma</p><p>kikayi ksrambannin tafiya to kin yanke</p><p>zamanki a atbu.nasan kadan daga cikin</p><p>aikinshine donhaka na tsaya. Akalla nakai</p><p>awa uku agun. Har kowa yagama test ya</p><p>watse anma yadda kikasan gunki ko</p><p>waiwayata baiyiba. Bansan lokacin da</p><p>hawaye suka zubominba. Yace ki leta</p><p>zakimin na apology ki kaeomun karki manta</p><p>full leta. Dayazo wucewa kaman zai</p><p>bankadeni anma haka na gauce.dakinsu faty</p><p>matori nawuce. Fatyma wlh yuv disgraced</p><p>me. Laifinki nagsni bana kowaba. Tunda</p><p>nazo duniya ive neva felt humilated like dix.</p><p>Wannan si rashin mutunci ne. Tabata rai</p><p>itama sannan tace kinga maryam wlh</p><p>banson rashin mutunci. Karkuma ku raina</p><p>mun hankali daga ke har ahmad din. Kunsan</p><p>juna kuma yu both knw y yu do ol dix</p><p>nonsense. Ina doubtin akwai abu a</p><p>tsakaninku. Nace waye kuma ahmed ? tace</p><p>haba maryam yazakina mayar dani under</p><p>15? nace uhm wlh bansan sunansaba. Tace</p><p>wlh fa kikace? nace ae wlh</p><p>Cikin gida nawuce koba komai naji relief.</p><p>akan tsiyan dayamin. Washe gari karfe</p><p>bakwai fatyma matori tafara kirana a waya .</p><p>Maryam kidubi girman Allah kixo wlh bawan</p><p>Allahn nan zaiyi mana tsiya. Kaman nace</p><p>saime saikuma natuna wlh in fatyma ce</p><p>saitarama ko tayaya. Hakan yasa nace mata</p><p>to ina zuwa. Sanin zamuyi tsiya dashi yasa</p><p>nasa dogon riga baki. Nayi rolling da baki</p><p>nasa snickers dina vincci shima baki.</p><p>Nadauko glass dina. Namaka. Don karma</p><p>yatukamin tsiya naji kunya. Ina isa yauma</p><p>nayi latti . Kuma naga hall din acike da</p><p>alama wato yabada test din. Ina shigowa</p><p>yace Keeee ina zaki?!!! Na batarai kaman</p><p>tunds Allah yayini bantaba dariyaba sannan</p><p>nacire glass din fuskan tawa don yaga bacin</p><p>rai na. Kur yamin abunda zaa rainani.</p><p>Donkuwa bazaiji da dadi ba. Bance komai</p><p>ba. Kallonshi kawai nakr. Shima kallon nawa</p><p>yake amma da alama dariya ta tirkeshi yine</p><p>kawai bahalinyi saboda mutane. Anma ni</p><p>nasan halin abuna. Yamikomin paper kije</p><p>kirubuta yanxu kiyi summiting.kuma Kinyi</p><p>laifi biyu. Kibiyoni office kisameni ko na</p><p>cancelling miki papers. Koda kuwa exams</p><p>ne. Cikin rashin damuwa nace ohkay no</p><p>problem.nakarasa gunshi daniyyan in karba</p><p>kawai yaja yace anma bakida kunya. Ki</p><p>tsaya agun. Har nagama abunda zanyi kuma</p><p>kikayi ksrambannin tafiya to kin yanke</p><p>zamanki a atbu.nasan kadan daga cikin</p><p>aikinshine donhaka na tsaya. Akalla nakai</p><p>awa uku agun. Har kowa yagama test ya</p><p>watse anma yadda kikasan gunki ko</p><p>waiwayata baiyiba. Bansan lokacin da</p><p>hawaye suka zubominba. Yace ki leta</p><p>zakimin na apology ki kaeomun karki manta</p><p>full leta. Dayazo wucewa kaman zai</p><p>bankadeni anma haka na gauce.dakinsu faty</p><p>matori nawuce. Fatyma wlh yuv disgraced</p><p>me. Laifinki nagsni bana kowaba. Tunda</p><p>nazo duniya ive neva felt humilated like dix.</p><p>Wannan si rashin mutunci ne. Tabata rai</p><p>itama sannan tace kinga maryam wlh</p><p>banson rashin mutunci. Karkuma ku raina</p><p>mun hankali daga ke har ahmad din. Kunsan</p><p>juna kuma yu both knw y yu do ol dix</p><p>nonsense. Ina doubtin akwai abu a</p><p>tsakaninku. Nace waye kuma ahmed ? tace</p><p>haba maryam yazakina mayar dani under</p><p>15? nace uhm wlh bansan sunansaba. Tace</p><p>wlh fa kikace? nace ae wlh</p><p>Nan tayi tsit saikuma takoma lallashi.</p><p>Maryam nasanki da taurin kai. Shima taurin</p><p>kai. Kinja igiya shima yaja mexai faru ?</p><p>saiku tsinka. Anma idan yaja saiki hakura.</p><p>Nace uhmmm lallai. Ai ni ko duk abinda</p><p>nsmiji zaimin to karya shiga hurumina. Its a</p><p>big shame nazauna namiji yayi winning dina.</p><p>Over my dead Body. Its either naci kokuma</p><p>shi yakura. Tace to Allah yabaku saa. Nima</p><p>na sungumi. jakana ban nufi ko inaba sai</p><p>gyda .a daren baffa yakirani maryam gobe</p><p>zanxo karkuje ko ina. Nace to. Washegari</p><p>faiza nadawowa daga paper nace mata</p><p>karkifita baffa yace zaixo. Karfe biyar na</p><p>yamma yaxoshi yasamemu da umma</p><p>yataramu a falo. Maryam kinsan xuriarmu</p><p>bama barin mace tayi shekara uku a jamia.</p><p>Daga shekara biyune. Anan gabana yafadi</p><p>wlh tsaf nagama mancewa nan kuma nsji</p><p>wani bakin ciki. Ya kulleni. Sai yaci gaba</p><p>kina da tsayay? Nace</p><p>Banni dashi baffa. Yace to alhamdulilah.</p><p>Akwai wani yarona zanhadaki dashi yanada</p><p>biyayya sosai. Dan mutunci. Tunda yafada</p><p>wannan kalman brain dina yabani cewa to</p><p>tabbas duk acikin game dinne wato zai</p><p>hadani dawani nakusa dashi don</p><p>acucemu.cewa yayi kin amince? batareda</p><p>nasan sauran meyace ba. Nace ae baffa</p><p>zabinka shine nawa. Ba umma ba hatta faiza</p><p>saidata gitgiza wani kallon tuhuma tamin</p><p>irin nasanma menakeyi kuwa? umma kuwa</p><p>zuramin ido tana murmushi Allah sanya</p><p>alheri. Baffa kuwa kaman wanda akace ga</p><p>aljanna kashiga yarinka samim albarka</p><p>hakan yadada tabbatar min dacewa tabbas</p><p>da niyya biyu yahada duk dabansan waye</p><p>ba. Daya tashi tafiya yace zai aikoshi</p><p>kugana sosai .zaayi komai a watan gobe.</p><p>Nace to. Haka yatafi. Yana tafiya faiza tace</p><p>adda maryam? kalanki. Hannu nasa a bakina</p><p>nace mata shhhhhhhhhhhh. This is a game</p><p>of chess. Use your brain for wat they are</p><p>meant for THINK.. Zuramin ido tayi alaman</p><p>tunani can kuma ta zaro ido. Kardai yanaso</p><p>yahadaki dawani nakusa dashine duk akan</p><p>dukiya. Nayi murmushi sannan nace yauwa</p><p>kanwata haka nakeso kizama. Think think</p><p>A satin magayawa kawayena kowa zanyi</p><p>aure . Bawacce batayi mamaki ba. In</p><p>antambayeni kuwa sai nace bansanshiba.</p><p>Adda ummi ta tsorata sosai hakan yasa</p><p>takanas daga gombe tayi dropping lectures</p><p>dinta tazo. Mungama cin abinci kenan tace</p><p>kawata? nace naam. Tace to dalili ne</p><p>yakawoni. Nangane kina cewa zakiyi aureba.</p><p>To dawa zakiyi? kinada saurayine? na</p><p>murmusa sannan nace a a fa. Baffa ne wai</p><p>zai. Hadani dawani yaronshi. Adda ummi</p><p>tace kekuma saikikace me? sai nace masa</p><p>to. Saboda duk game muke playn ko</p><p>kinmantane. Ta girgiza kai tace kawata</p><p>kinada taurin kai. Haba ki hakura mana.</p><p>Kefa macece. Na kalleta sannan nace kina</p><p>nufin inzauna azzulumai sumana kwasan</p><p>arxikin uba ? ni dama ta hanyar halaq zai yi</p><p>amfani dashi baxai damenba. Anma nasan</p><p>halin baffa sarai. Gaskiya dadi bazai zauna</p><p>yatara arziki ta halaq wasu suxo su barnatar</p><p>ta haram ba. Tace hakane. Anma kinsan</p><p>aurefa yawuce tunaninki. Shigane na</p><p>dimdimdim. Nace hakane. Anma kin manta</p><p>da cewa duk abinda aka gina shi da yaudara</p><p>da mugunta da karya bata tasiri? kisamun</p><p>ido. Ayi mugani aurene ina? zanyi. Bata</p><p>karacewa komai ba. Saidai nidai kiyi a</p><p>hankali. Ina guje miki wayonsu da dabara.</p><p>Nace Allah nanan dashi na dogara.. Ahaka</p><p>muka danyi tadi gameda shirye shiryen bikin</p><p>nidai ba abunda zanyi adda ummi tace to</p><p>zasu hadamun sisterx eve da ita da faiza.</p><p>Numban wayana aka kira naduba numban</p><p>sannan naga bakon number. Inadauka akace</p><p>maryam usman ce? nace ae. Sai akace to</p><p>kixo dept dinku ina nemanki. Gabanane</p><p>yafadi donkuwa tunda naji haka bakalau ba.</p><p>H.o.d. Dinmune. Washegari 10 a makaranta</p><p>tamin bayannakai faiza gyda akan zata wuce</p><p>gombe da rana. Inashiga office din</p><p>nagausheshi cikin sanyin murya. Yace lafiya?</p><p>nace maryam usman. Kace kana nemana.</p><p>Yace v.gud. An layn mana complaint daga</p><p>gen. Lecturer ku. Tuni nafara basa hakuri.</p><p>Yace yanxu kije ki ku sassanta dashi yayi</p><p>miki sighnin ki kawo. Kokuma ki fuskanci</p><p>hukunci. Nace to. Hostel na nufa. Bansan</p><p>lokacin da hawaye suka zubominba. Wannan</p><p>rainin hankali har ina. Ai gwara nabar</p><p>makarantan da akan inje gun wannan mugun</p><p>neman gafara. Fatyma kam zama tayi sai</p><p>waazi take. Kinga malaminkine koba komai</p><p>kibashi wannan darajan inkunbar nan saiku</p><p>karata awaje. Kicire girman kai. Kije. Na</p><p>kalleta da kyau sannan nace bakisan rayuwa</p><p>ba har yanxu wlh. Infact zan iya barin</p><p>makarantan nan inhar sai nanemi gafararsa.</p><p>Zaro ido tayi sosai. Sannan tace gaskiya</p><p>nanji dadiba ko kadan . Kin gwadamin nayi</p><p>kadan ingayamiki magana kiji. Nace ayya</p><p>kema kinsan kece second besty ta</p><p>matotooooo. Habawa tabiyoni dagudu na</p><p>tsare. Intakaita dai dakyar fatyma matori</p><p>tasamu na hakura akan zata rakani muje</p><p>tare. Muka shirya tsaf muka nufi office dinsa.</p><p>Ahankali tabude kofan tashiga nabi bayanta.</p><p>Sannan tagaysheshi. Fincikoni tayi takasa</p><p>alaman nima na gaysheshi dama tunda</p><p>muka shigo baidago ba balle yagasu waye</p><p>hakan datamin yasa nace evn sir. Bashiri</p><p>yadago kansa aikuwa muka hada ido. Na</p><p>murkuda mar baki. Yace sannunku lafiya.</p><p>Anan fatyma matori tamar bayanin abinda</p><p>ke tafe damu. Yace whos the conplaint?</p><p>tanunani yace then excuse us. Ta zo zata</p><p>fice har zanbi bayanta tayi narai narai da ido</p><p>alamun don Allah in tsaya inji mezaice.</p><p>Najuya na tsaya itakuma tafice. Yajuya kai</p><p>yacigaba da abunda yake nakai minti goma</p><p>kafin nace sighnig dinka zakaban nakaiwa</p><p>H.o.d. Anan yadago yace aibahaka kukayi</p><p>dashiba. Cewa yayi kixo kibada hkr. Cikin</p><p>tsiwa nace Allah sauwaka. Ko kabani</p><p>kokuma kasan halina sarai. I dnt bloody</p><p>care. Zan iya barin makarantannan</p><p>akanka.yayi dariya mai isarsa sannan naga</p><p>yacuro wata paper yayi sighn sannan</p><p>yamikomin. Nawani daka masa harara.</p><p>Batare danace nagode ba nafice. Inashiga</p><p>office din h.o.d namika masa. Kallona yayi</p><p>tare dacewa are you stupid? Nima kallonsa</p><p>nayi alaman inaso inji meye yake zagina.</p><p>Kawai naga papern. A lokacin nalura da</p><p>papern wannan papern dana yi tuwo dashi a</p><p>ruwan kofi. Ita yaje yashanya yasamata</p><p>gum. H.o.d. Yace mena ce miki ki karbomin?</p><p>nace sighnin. Yace to meye wannan? Ina</p><p>karba nakaranta da jan biro aka rubuta I</p><p>LOVE YOU. Kan uba!! nama rasa mexance</p><p>masa. Yace will yu get out of my office.</p><p>black fool!!! Fatyma wacce rabona da ita</p><p>tuna office dinshi ta taho da xummar tajime.</p><p>Hannunasa mata cikin bacin rai matori luk.</p><p>Kibarni .plx ki rabu dani. Ke kikamun causing</p><p>ol dix nonsense. Batace komai ba. Da papern</p><p>a hannuna ina tafiya anma hawayene yake</p><p>xuva. Ina zuwa daidai office dinshi naji horn</p><p>abayana ina juyowa kuwa muka hada ido</p><p>dashi. Yacire glass dinsa sannan yace ive</p><p>moved a step ahead of you in the game.</p><p>Saikin iso. Wayyo Allah. Inama kasa zata</p><p>hadiyeni dawannan bakin cikin.yawuce</p><p>yabarni agun. Ranar ba karya kuka natika a</p><p>gyda ko abinci nakici. Faiza kuwa tuni tafara</p><p>cewa to adda maryam ki hakuramana da</p><p>game dinkun. Ko kallonta banyiba balle ta</p><p>tsammaci amsa</p><p>Baffa ne yakirani a waya. Maryam kishirya</p><p>bakon naki yau zaixo kiganshi kuma ku</p><p>sasanta. Cikin rashin damuwa nace to Allah</p><p>yakaimu. Gidan mai naje don nasa mai a</p><p>motana don umma tace zataje walimansu</p><p>faiza wanda zaayi nagama makaranta.</p><p>Donhaka naje nayi fueling mota. Gidan man</p><p>anyi layi. Don yanxu ake saukar da mai. Na</p><p>bude kofan motan ina dan kalle kalle. Motan</p><p>shi nahango yana tsaye kuma a bakin</p><p>motan. Hahahaha dariya nayi sosai sannan</p><p>nace barin gwada tawa fasahar. Mutanene a</p><p>cike agum maxa da mata gakuma masu</p><p>saye da sayerwa. Akwai wani mai rake agun</p><p>. To yasa weelbirown shi adaidai inda ahmed</p><p>ke tsaye naje na tsaya nayi cinikin na dari</p><p>biyu nasaya.yana juyawa kawai a lalube na</p><p>jefa daya cikin aljahun riganshi. Dake jamfa</p><p>yasa. Dake dan karami ne sai baiji nauyiba.</p><p>Sai najuya naga wata yarinya nakira. Mukaje</p><p>bakin motana nace ingo wannan raken.</p><p>Nabata gudan dubu daya. Nace tunda kinga</p><p>ke guntuwace. Zaki iya abunda nakeso kiyi.</p><p>Ki jefa cikin aljihun mai blue shaddan nan.</p><p>Ahankali. Inkin jefa saiki . Kwalawa mai rake</p><p>kira kice ana kwashema rake. Kinafadan</p><p>haka saiki gudu. Ungo kudinki. Dake karama</p><p>ce. Bata gaza shekara shida ba. Ta je</p><p>ahankali ta tusa tana sawa kawai sai ta</p><p>taba rigan ahmed yana juyowa. Bansan</p><p>metace mishiba. Har gabana yafadi inacewa</p><p>kar yarinyan nan ta nunani harna rufo kofan</p><p>motan kawai sai naga ya ciro rake daya</p><p>zaimayar kawai yarinta ta tsalo ihu mai rake</p><p>ana kwashema rakenka. Habawa shikuwa</p><p>kaman maijiran kyas. Yaxo yafara kwale kan</p><p>ahmad. Naci dariya sosai. Anan mutane</p><p>suka rabasu. Na fito nima na tsaya. Kawai</p><p>sai mutumin yace satamin rake yayi.</p><p>Mutanengun kuma bawan Allah meya faru?</p><p>yace nifa wata yarinyace tacemin tasamin</p><p>rake nacire gameshi. Inacirewa kuma ta</p><p>tsala ihu. Abun yadaure musu kai. Baiyi</p><p>kama da fatarrare ba balle kuma wanda zai</p><p>sace rake. Can yaciri sabbin dari biyu fil</p><p>yabawa mai rake. Ungo anma ni nafi karfin</p><p>rake. Tsaki yaja yashiga motansa nima</p><p>dawuri nashiga. Yazo daidai fita yana jira</p><p>mota suwuce yasa kai. Nawaina glass dina</p><p>na leko. Sannan nace gaskiya kayi kyaufa da</p><p>barayin. Well nima ive moved ahead saika</p><p>biyoni. Bude baki yayi tare dacewa i should</p><p>have known aikinki ne makira</p><p>Nace kadan kenan. Yu beta surrender</p><p>kokuma wlh ka wahala. Yace God forbid lex</p><p>continue playn. Yaja motarsa da karfi</p><p>alamun abun yadamesa. Harnadawo gyda</p><p>dariya nakeyi. Faiza kuwa dana bata labari</p><p>saita fara cewz nikam yanxu yadena bani</p><p>haushi tausayi yakeban. Nace to kuwa zaki</p><p>mutu . Nayi wanka nashirya bayan suntafi</p><p>waliman nikuma nazauna inason naga bakon</p><p>game dinmu wanda zaiyi joining dina ahmed</p><p>muyi playn. Kuma at the same tym mijin</p><p>dazan aura. Ummi mai aiki ce tashigo tare</p><p>dacemin nayi bako. Nace to. Saidana shafe</p><p>minti talatin kafin nasakai nafita. Newspaper</p><p>ne a hannunshi yadaga kafa daya kan daya.</p><p>A zuciyana nace lallai wannanma dan duniya</p><p>ne. Na nemi gu nazauna. Saida muka shafe</p><p>minti goma kafin wayata tayi kara nan</p><p>yasan nashigo falon. Yaja newspapern. Muka</p><p>hada ido. Bashiri namike. Kan balai. Yace</p><p>meye kuma sai kace kinga malaikan</p><p>mutuwa? nace Allah sauwaka na aureka.</p><p>Yace noooo ki fahimceni. Ai idan mukayi</p><p>auren gamedin zaifi tafiya daidai. Zamuyi</p><p>playn sosai koya kikace. Naja tsaki nafice</p><p>nabarshi agun yanata dariya. Wasa wasa</p><p>saura kwana uku daurin aure dangi kam</p><p>kowa yaxo bauchi waisunxo daurin aure.</p><p>Gyran jiki kam anty aimana saiyi takeyi.</p><p>Dake yawanci a gydanmu aka tare harsu</p><p>fatyma matori. Su adda ummi. Su zafyra</p><p>danbaba. Duk sun hallaru kowa yana ta</p><p>murna. Nikuwa ko a jikina ba yabo ba</p><p>fallasa. Fatyma matori kuwa tsiya tayi</p><p>tamin. Kice kunmaidani jahilan karshe</p><p>kunsani a tsakiya ashe shegu soyayyanku</p><p>kuke. To waima yakuka kare da h.o.d nku</p><p>ne. Nace bansan ya akayiba kawai yakirani</p><p>wai karna kara naguji bacin rai. Dax ol. Tace</p><p>yaje yabada hkr on yur behalf ne. Danaga</p><p>neman magana take atake nabarta agun.</p><p>Akayi biki na yayan gata don anan wani abu</p><p>yadauremin kai. Familynsa masu kudi ne</p><p>sosaiii. To meyakeyi a karkashin baffa?</p><p>sannan kuma daga baya na fahimci ashe a</p><p>nnpc yake aiki. To meyake kaishi lecturing a</p><p>atbu? banda mai amsamin donhaka naja</p><p>tsufana nayi tsit Akayi events kala hudu.</p><p>Kuma kowannemu dagani har ahmed kowa</p><p>yabada hadin kai rimi rimi. Anma fa naciki</p><p>naciki. Ji nake kaman imharbeshi. Shima</p><p>nasan hakanne saboda kallon dayakemin</p><p>inya faki idon mutane. Yanamin nima nake</p><p>ramawa. Ashe adda ummi na hankalce</p><p>damu. Taxo daidai kunnena tace yanxu</p><p>game dinkun yadawo ta idone? bansan</p><p>lokacin dana kwashe da dariya</p><p>Da aka gama komai. Nida faiza da adda</p><p>ummi mukaci kukanmu sosai. Don saida</p><p>faiza tafara zazzabi gargadi kuwa da nasiha</p><p>namata sosai. Itama yanxu atbu zaa nema</p><p>mata tafara. Muka dangana. Anty aimana da</p><p>umma suka sani agaba. Inbanda waazi ba</p><p>abunda suke na saduda sosai. Har da</p><p>nadaman meyasa nabari aka daura aure.</p><p>Bayan araina badan Allah nane don wata</p><p>burina nane daban. Saikuma na kawar da</p><p>tunanin Dare dare aka kaini. Dakina. Har</p><p>suka tafi inata kissina mezai faru idan aka</p><p>barmu mukadai. Nikam kurfa yakama yadaka</p><p>kaman yasamu jaka. Na tsorata sosai. Yana</p><p>rufe kofa yawuce side dinsa. Dasauri natashi</p><p>na rufe kofana. Nayo alwala nayi sallah</p><p>natofa a koina sannan na dake kan gadon na</p><p>kwanta. Ina kwance. Ina tsoro har bacci</p><p>barawo ta kwasheni. Da asuba namike nayo</p><p>sallah tare da adduoi na. Sannan karfe</p><p>bakwai nayi nabi lafiyan gado. Sha daya</p><p>daidai nafarka. Yunwa ce kuma ta tashen</p><p>don haka sai na fito da zummar naje kicin.</p><p>Abin takaici da bakin ciki. Kulan abincine da</p><p>flask aka direnin da short note. Nadau</p><p>sannan nakaranta. Matar oya karya kafin</p><p>nadawo Naja tsuka nadauki kulan naje</p><p>naleka naga dakuna uku a jere. Ina tantaman</p><p>wannene donhaka sai nashiga leka idona</p><p>cikin ramin. Naga riga a makale. Hakan ya</p><p>tabbatar min nanne dakinshi Na ajiye agun</p><p>sannan nima nadauko biro na rubuta gashi</p><p>bazan iyaciba. Saboda karen gydanmu ne</p><p>mai cin irin wannan abincin. Nashiga kicin</p><p>nahada lafiyayyen tea na. Nasha tsum</p><p>nadauko remote ina kallo. Adda ummi ne</p><p>takirani. Mukasha tadinmu nanma sai data</p><p>karamin gargadi. Maryam nasan halinki kiyi</p><p>hakuri kishare komai kufara sabon rayuwa</p><p>nace to. Misalin biyu naji alamun</p><p>shigowanshi. Dama gajerar wando nasa sai</p><p>dan vest ajikina. Nazubo gashina ko</p><p>motsawa banyiba kuma dagangan nayi</p><p>hakan. Yaxo baice uffanba yawuce. Yana</p><p>xuwa yadauko kulan abincin adaidai gun</p><p>yakaranta. Yaxo gabana fuskarshi a turnuke.</p><p>Kirasa wani abinci zakice abincin karan</p><p>gydanku? sai best food dina? nabata rai</p><p>sannan nace waka taba ganin yabaza baki</p><p>yaci indomie a matsayin abinci if not</p><p>marmari.ya girgiza kai. Gud i knw yur</p><p>perfect medicine</p><p>yashige yabarni agun. Baikara fitowaba</p><p>hakan yasa nima nashareshi. Munjera sati</p><p>muna kwasan tsiya dashi. Yadaiyi sanyi</p><p>sosai. Don yanxu so yake mushirya nikuma</p><p>nayi kicibis nahana ruwa gudu. Wata rana</p><p>yadauko jaridarshi yana karantawa . Naji</p><p>kawai inbane mi tsokananshiba to ba zaman</p><p>lafiya na dauko wayata nafito falo. Yauma</p><p>gajeren wando na nasa. Anma yau baki. Sai</p><p>tshirt fari. Ina zuwa nasake waka. Yayi</p><p>shiru. Ganin ya shareni yasa</p><p>Hade rai yayi tare dacewa mai napep.</p><p>Malam idan kajata saika kwana a cell.</p><p>Mutumin ya cire mukulli . Nikuwa nafito</p><p>nafara banbani. Bawan Allah lafiyanka? daga</p><p>ganina zakace saika tafi dani? to nafi</p><p>karfinka. Mai keken yace baki sanshibane?</p><p>nace ae mana. Dana sanshi zan tsaya rigima</p><p>ne? tun acikin shago yaketa bibiya ta. Nan</p><p>danan mai keke yatara masa mutane. Anata</p><p>hayaniya na sulale na tsare wani keken na</p><p>nufo gyda.can saigashi yashigo riga duk tayi</p><p>squeexing. Na kwashe da dariya. Nace anma</p><p>kam kayi kyau. Nadauko camera nafara</p><p>dokanshi hoto nace zan wanke insha Allah a</p><p>falon nan zansaka. Baice komaiba yawuce</p><p>daki. Can bayan yayi wanka saiya dawo. fita</p><p>yayi saigashi yashigo da gashashen kaji</p><p>zakici ne yar wajena ? yana</p><p>murmushi.kaman nace ae. Sainace a a.</p><p>Yadauko yaxuba sosai yabaje yanaci yana</p><p>kora juice. Natashi nabar mishi falon don</p><p>yawuna ya tsinke. Naji ina shaawan naman</p><p>nima. Harna shiga dakin nafito nadauko</p><p>roban ice cream nakoma. Yabugamin kofa</p><p>nace waye. Yace kayanki zaki kwasa.</p><p>Nabude mishi nakarba. Na jejjera kayan.</p><p>Sannan na ajiyewa umma da faiza nasu</p><p>dama idan zanje makaranta ne zan biya</p><p>inbasu. Washegari dasafe baffa yakirani a</p><p>waya. Mijinki zai xo dake anjima zamuyi</p><p>magana. Nace to. Bankawo komai a rainaba.</p><p>Illa duk acikin game dinmune. Muna zaune</p><p>agaban baffa sannan yace maryam tunda</p><p>kinsamu kinyi aure lafiya to dukiyan</p><p>mahaifinki ne nakeso kisakarma mijinki</p><p>saboda yana juya muku keda kanwarki. Na</p><p>numfasa sannan nace a a baffa abarshi</p><p>tukun harsaina kammala degreena daman</p><p>fannin kasuwanci nake karantawa gashi</p><p>itama faiza abunda zata karanta kenan. Yayi</p><p>shiru sannan yace kije zamuyi shawara akai.</p><p>A mota bance ma ahmed uffan ba shima</p><p>baice komaiba.kwana yashiga naga yana</p><p>hanyan barin gari. Nace lafiya muda zamuyi</p><p>gra naga kayo nan? yace cinyeki. Zanje</p><p>nayi. Na kwashe da dariya sannan nace mu</p><p>cinye juna dai. Yajuyo yakalleni yace ai baki</p><p>isa ki cinyeni ba .saidai nina cinyeki. Na</p><p>murkuda baki nace abayan raina kokuma</p><p>wata maryam din anma nikam nafi karfin</p><p>tunaninka. Hotel yaje damu .muna isa</p><p>farfejiyar yace toki fito muje. Nafito batare</p><p>da tunanin komaiba. Ina tsaye yaje shi</p><p>reception bansan meyayi ba.sannan yace</p><p>muje inkaiki gun yan kungiyanmu. Nabishi</p><p>batareda ko fargaba ba. Wani daki mukaje</p><p>yabude sannan yace jirani nikuwa harda gyra</p><p>gyale nazauna adole ina jiran yan kungiya.</p><p>Yashigo da drinks a hannunsa. Nakarba</p><p>nakurba ina murmushi. Ina suke? yace suna</p><p>zuwa. Minti goma kawai idona yafara</p><p>juyawa nafara ganin uku uku. Lallaima</p><p>narikoshi. Ahmed rikeni karna fadi. Bansan</p><p>inda hankalina yatafi ba kuma</p><p>Idona nabude a hankali . Nayi kokarin</p><p>motsawa anma wani zafi naji a sassan jikina</p><p>wanda dawuri yasa na nutsu. Nabude idona</p><p>yana tsaye alamun daga wanka yafito yana</p><p>ahare jikinsa da tawul gashin kirjinsa duk ya</p><p>kwanta. Gaba nane yayi mummunan fadi.</p><p>Domin tunanin danayi muna hada ido</p><p>yasakar min murmushi yar wajena ya</p><p>akayine. Nakauda kai wata irin dariya yayi .</p><p>Wanda bansan yazan kimtsataba. Kai anma</p><p>fa kinsan me. Kinyi loosing anan. Domin</p><p>kince sai dai ki cinye ni. Anma kuma ni</p><p>naciki. Auxubillah nake fadi. Tare da kokarin</p><p>mikewa wani kara nasakar tare da komawa.</p><p>Hawayene suka zubomin. Yakaraso guna</p><p>sannan yace xo intaimaka miki. Nace Allah</p><p>sauwaka tareda murkuda bakin yaja yayi</p><p>turus sannan yace wannan karamin bakinki</p><p>sai uban rashin kunya. Kitaso muje namiki</p><p>wanka . Haka ya cincibeni tun ina shureshi</p><p>har nadaina tsabar wata irin damka dayamin</p><p>saidanaji ajikin jijiyana. Bath bowl yasani</p><p>sannan yasa dettol. Yafincike kayan jikina</p><p>nashiga ruruufe jiki. Yace kuji ya. Nizaki</p><p>rufewa jiki? gwara kibude . Na ki duk abinda</p><p>yake bance komaiba. Daga baya nace</p><p>banson iskanci kawice kabarnan habawa ai</p><p>atake yace nidin? Bari kiga rashin kunya da</p><p>iskanci. Benaxir wlh haka bawan Allahn nan</p><p>yatube mukayi wanka inamar tsiwa ya</p><p>damkoni dole na nutsu. ya rufoni yasa a</p><p>tawul sannan yadauko mai zai shafamin</p><p>nanma mukayi bori sosai. Sannan yace</p><p>yarinya jiki kamar auduga kina cewa pit zan</p><p>maimaita . Nasan zai rina anma don dai kar</p><p>yasamu abunfada yace naji tsoronshi hakan</p><p>yasa nace pit pit pit pit nafada kayi abunda</p><p>zakayi. Aikuwa yamike. Wlh haka yakara</p><p>second round. Ihu kuwa har masu hotel suka</p><p>fara buga kofa yabude yace matarsa ce.</p><p>Yarufo abunsa. Tuni na galabaita. Bankuma</p><p>san inda nakeba. Bude idona nayi naganni a</p><p>asibiti .da ruwan drip a hannuna. Faiza ce a</p><p>gefena tayi tagumi. Tace adda maryam</p><p>yajikin nadaga alaman kai cewa dasauki.</p><p>Sannan tace saidanace auren bawan Allahn</p><p>nan matsala ne. Kikace zaki iya gashi anfara</p><p>kawoki asibiti nan gaba kuma yazaayi? nayi</p><p>murmushi cikin muryan marasa lafiya nace ai</p><p>ba abunda yafaru. Juya kai tayi alamun bata</p><p>yaddaba. Adda ummi da fatyma matori ne</p><p>suka shigo. Adda ummi a rude. Meya miki?</p><p>nace babu. Tace a a kam. Duk kasanki a</p><p>lalace? anmiki nakarfi? hawaye zafafa ne</p><p>suka xuba. Namika hannuna alamun su</p><p>mikar dani. Natashi nazauna suka gyrani</p><p>sosai. Fatyma matori itakam abun yadameta</p><p>tagagara ganewa tazata auren soyayya</p><p>mukayi anma yanxu tafahimta cewa</p><p>kowannenmu da nufinshi. Tace kaiku tsaya</p><p>don ubanku kugayamin meke faruwa bazaku</p><p>mayar dani yar iskan tsakiyaba. Adda ummi</p><p>tayi dariya sosai sannan tace laa abunda ke</p><p>faruwan kenan kike gani. Tace serious</p><p>gaskiya kun dauremin kai. Dama basonki</p><p>yakeba kullum yake damuna akanki? nazaro</p><p>ido. Nace banganeba. Tazauna sannan tace</p><p>barin baku labarin komai gameda ahmed</p><p>Ahmed.Modibbo da kwaya daya tal ga alhaji</p><p>muhd moddibo. Hamshaken maikudi sannan</p><p>kuma kowaccenku tasanahi anan. Ahmed</p><p>dan shekara 31 wanda jini yake ji ajika.</p><p>Matashi kyakyawa fari xubin fulani wanda</p><p>kowacce mace take mafarkin samu.</p><p>Saudayawa nakanyi mamakin yanda maryam</p><p>kike tsula masa tsiya bakya considering</p><p>qialities nashi. Namiji ne mai kwarjini. Yayi</p><p>makaranta a moscow yanda yakaranta</p><p>business administration. To bayan yadawo</p><p>ne. Wata rana.mahaifinshi ya aikoshi</p><p>gidanku kasancewar da daddynku da</p><p>daddynsa abokai ne. Nasan kunsan alhaji</p><p>muhammadu. To shime mahaifinsa. Tun.</p><p>Lokacin daya taka kafa yazo gydanku aika</p><p>yaganki. Yaji yana sonki. Hakan yasa yayima</p><p>mahaifinshi magana. Daddy kuwa yace</p><p>yabashi ke. Da alhaji muhammadu yanemi a</p><p>gayamiki saboda kar rikici ta tashi idan anzo</p><p>aure ko kice baki sonsa kokuma kice kin</p><p>tsaida wani hakan yasa daddy yace a a</p><p>yasan yarsa. Zaimiki magana da karki kula</p><p>samari harsaikin yi makarantanki. Hakan</p><p>yasa a ka bar zancen shikuma a lokacin</p><p>yakoma yin masters dinsa. Sanadi yakawo</p><p>muka rasa daddy da momy. Bayan kun koma</p><p>gun baffa. Shine shikuma ahmed yadawo da</p><p>zancen cewa aishi gashi abunda akayi. Baffa</p><p>yace yasanki da taurin kan tsiya sannan</p><p>kinada basira .hakan yasa yace bari abuga</p><p>dan wasa dake. Suka hada plan. Dakyar</p><p>ahmed ya yarda akan yazama manajan</p><p>daddy saboda duk kuke haduwa. Kuma</p><p>kamar yadda aka shiryan hakanne tafaru.</p><p>Ahmed asali a gydan mai na nnpc yake aiki.</p><p>Anma sanadiyanki yanemi aiki a atbu kuma</p><p>aka bashi dalilin qualifications dinsa aka</p><p>bashi wani subject wanda ke baki offering</p><p>ahaka yayi amfani da dukiya mai yawa aka</p><p>canja. Sanadin dayasa yafara lecturing duk</p><p>akanki. Karkiyi mamaki nasan wannan</p><p>labarin nake boye miki. A a wlh. Nima</p><p>sanadine yajawo nasani. Mamansa yar</p><p>mamanane uwa daya uba daya. To wata</p><p>rana bayan anyi aurenku ne yaxo yace</p><p>abashi abinci anan take tambayansa lafiya</p><p>yace babu data matsa masa shine yakebada</p><p>labari anan nima naji. Kuma maganan fidda</p><p>kudinku dazaayi duk plan din baffa ne. Duk</p><p>da a cewar ahmed bappah ya gwada masa</p><p>donke akeyi anma daya lura dashi yaga</p><p>alamun acikin ransa wacce sirrinshi ne</p><p>shiyasani. Dalilin haka yasa baffa yace zai</p><p>daura aurenku duk acewarsa acika alkawarin</p><p>daddynki. Dahaka kuma kika amince. Tohfa</p><p>kinji dalili. Sannan kuma ahmed kullum inhar</p><p>zamu hadu to ba abunda yake bada labari</p><p>illa irin burgeshi dakikeyi wai ke baitaba</p><p>ganin mace mai confidense irinkiba. Infact</p><p>wsi you are hundred percent perfect. Nd</p><p>kuma nazo nan naga alamarin its not the</p><p>same nashare sauran gawayen dake makale</p><p>a fuskana bayan fatyma matori ta idda bani</p><p>labari.faiza ma kuka take adda ummi kuwa</p><p>tagumi tayi. Magana mukaji daga bayanmu.</p><p>Fatyma meyasa kika fada mata? wannan</p><p>sirrinane.</p><p>Baffanki ne ya matsamin nayi wani abu</p><p>nikuma bazan iyaba. Na gyra zama sosai</p><p>sannan nace inajinka. Lokacin danazo masa</p><p>da bukatata ta aurenki dakuma yadda akayi</p><p>alkawari. Yacemun dama akwai aikin</p><p>dashima yake tunanin zaisa ayi. Anma</p><p>tundanazo aikin mai sauki ne. Baffanku naso</p><p>ayi reownin kamfaninku yakoma nashi.</p><p>Sannan acire duk jarin account dinku. Akan</p><p>zaije florida yazauna da matarsa da yarsa.</p><p>Yanxu haka da wasu jarinku yayi gini babba</p><p>a can. Kinsan yadda ginin kasar waje take</p><p>anman haka yaje yayi.to kwanakin nan</p><p>yadameni nasan yadda zanyi kiyi sighnin a</p><p>fidda kudin nan ko kuma yasa a kasheni a</p><p>cewarsa baiga amfaniba. Ke kuma kikazo</p><p>kika wani rufe kanki dawanne zanji?a</p><p>sanyaye nace to shine kake wahalar</p><p>dakanka? yace tohfa cewa yayi nasamiki</p><p>kwaya kifita daga hayyacinki naga bazan</p><p>iyaba. Agun yasa nayi alkawatrin zansa</p><p>miki. Dalilin dayasa nasamiko kenan</p><p>damukaje hotel anma a bakacin nayi abunda</p><p>yasani naga bazan iyaba shine nayi wani</p><p>daban. Naja numfashi sosai nace badamuwa</p><p>nadauko wayata nakira faiza nace taxo.</p><p>Tana isowa namata bayani tace yazaayi</p><p>kafin sukasheshi. Nace zanyi sighning din</p><p>faiza tace adda maryam lafiya? nace ae</p><p>saboda karki manta mu marayune. Hakkinmu</p><p>zata bishi har gadon mutuwansa. Ta jinjina</p><p>kai tace toh shikenan dahaka mukayi</p><p>sallama nace karta gayawa umma.nadawo</p><p>gunshi nace kawo files din. Yace mezakiyi</p><p>nace sighnin. Yace gwara na mutu akan</p><p>inbada dukiyanku. Na zaro ido. Nace nikuwa</p><p>dana rasaka gwara narasa wadannan</p><p>dukiyan.. Mukayi rikici dashi sosai kafin ya</p><p>yadda nayi sighnin. Yashirya yafita</p><p>sannanan ne adda ummi tashigo nace</p><p>madam sai yau. Tadiremin kaya agaba</p><p>nashiga budewa. Ashogbe ne dai a dinke ga</p><p>takalmi da jaka har sarka. Nace nawa kuma</p><p>tayi murmushi sannan tace na aurena.</p><p>Bansan lokacin dana wani tsala ihuba.</p><p>Wayyo abbakar yaji dadi. Tace sosaima.</p><p>Mukayi ta tadi yadda bikin zai kasance.</p><p>Daga baya natashi nadaura girki wa mai</p><p>house. Harta tafi baidawoba. Inajin horn</p><p>dinsa dagudu nafita ina cewa zamuyi auren</p><p>adda ummi. Kallona kawai ya tsaya yi. Na</p><p>tsuke sannan nace meye kuma. Yadago</p><p>hannunsa daidai kaina. Alaman wato yana</p><p>auna tsayina. Najuya nace ahhhhh wlh da</p><p>sakel. Yayi dariya sannan yace guntuwass.</p><p>Nace barni am feeling my guntanci. Habawa</p><p>mexaiyi inba dariya ba. Har muka shivga</p><p>daki yanata dariya. Wai duk yanda mutum</p><p>zaimin nasan amsan dazanbashi nace ehdin</p><p>Watan bikin adda ummi yakama muka</p><p>gwangwaje sosai muka kaita garin gombe.</p><p>Itama tazama amarya. Gama bikin keda</p><p>wuya nafarka washegari natashi da</p><p>matsanancin ciwon ciki. Ahmed na tunkaro</p><p>ni nafara amai sakamakon kamshin</p><p>turarensa. Anan muka nufi asibiti aka</p><p>tabbatar mana inada juna biyu. Ahmed</p><p>lasheni ne kawai baiyiba anma murna kam</p><p>yashata. Muna isowa muka samu su baffa a</p><p>kofar gyda. Nayi mamaki sosai na risina na</p><p>gaysheshi anan yake cemana shida umma</p><p>jummare dakuma ummi zasu koma can</p><p>gidansu. Mukayi sallama sosai. Bayan</p><p>tafiyansu ahmed yace yanxu bakiji wani</p><p>abuba gameda kwashe dukiyan nan? baibar</p><p>muku wani abun arxiki bafa sai miliyan 12.</p><p>Nace wannanma alhamdulilah wasu ko dubu</p><p>darinma basu samuba. Yayi shiru.</p><p>Sannu bata hana ruwa gudu. Faiza tafito da</p><p>miji mukayi aure nagani nafada. Muka kaita</p><p>gyda dubu. Randa aka kaita nima nafara</p><p>nakuda na haifo lafiyyan namiji abuna. Ran</p><p>suna mukasa sunan dadi anma munace</p><p>masa abba.kullum saimunyi waya da adda</p><p>ummi. Umma kuwa zaman kadaici</p><p>yasameta. Ina zauna ina yiwa abba wasa</p><p>waya tashigomin. Nadauka. Cikin tashin</p><p>hankali take maganan . Anma nagano</p><p>muryan ummitan baffane. Nace lafiya meya</p><p>faru. Adda maryam gidanmu ne yakama da</p><p>wuta. Kuma gashi dadi jiya akamar sharian</p><p>daurin rai da rai. Waisun shigo dawasu</p><p>kwaya kuma ankashe har sojoji uku.bansan</p><p>yana kareba. Nadai bude ido naganni a</p><p>tsakiyan mutane dangine surkum. Nakalli</p><p>faixa nace ina ummitan? tace ya ahmed</p><p>daxu yabi jirgi zaije daukota. Anyi jimami</p><p>sosai. Anma irinsu anty aimana cewa tayi</p><p>allah ya kara. Nasha gayawa baffa yahakura</p><p>da dukiyan yara duk sninda zakayi banda na</p><p>marayu. Gashi wa wa kasuwa ta watse? .</p><p>Da kwana uku aka dawo da ummita ts jeme</p><p>ta kode. Cikin kuka take nemsn gafara ws</p><p>iyayen nata. Ahmed yace yasamu ganin</p><p>baffs. Ba abunds yske roka saiku yafe masa.</p><p>Yaso nazo dake. But bayanda muka iya.</p><p>Nida faiza tuni mukace mun yafe. Anan</p><p>ummita takoma zama da umma. Shikuma</p><p>ahmed dasauran dukiysn yafara juyawa .tuni</p><p>muka maida kudinmu. Kudinmu yafito har</p><p>yafi nada. Bamu da ssuran bukata a duniya</p><p>sai dai munemi lahira. Nagodewa Allah</p><p>dayabani ikon karasa miki labarina.Ni</p><p>benaxir sai na saduda kai sannan nace</p><p>barinyi laasar saimu yi magana bayan mun</p><p>idar. Sai nace wannan tarihi naki nadauki</p><p>wani darasi aciki sosai. To ya kuka kare da</p><p>batun game dinku. Tayi dariya sannan tace</p><p>munakai har yanxi. Don bamu dainaba. Naki</p><p>hakura shima yaki hskura.namike sannan</p><p>nace nagode maryam Allah yayi albarka.</p><p>Yakara dankon xumunci barin gudu kafin</p><p>momy ta nemo ni.</p><p>MUHADU A NA GABA DANGIN MIJI</p>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0tag:blogger.com,1999:blog-9014226675773213292.post-88084560395987610582020-12-05T20:43:00.005-08:002020-12-05T20:43:46.017-08:00HAQQI COMPLETE HAUSA NOVEL<p></p><div class="separator" style="clear: both; text-align: center;"><a href="https://1.bp.blogspot.com/-n5xE_N4D_CY/X8xgJ6CyTUI/AAAAAAAAJck/k-XJ2NDkqXckQzGzxCgcu8oTQfSQBFtWgCLcBGAsYHQ/s2048/HAQQI.jpg" imageanchor="1" style="margin-left: 1em; margin-right: 1em;"><img alt="HAQQI COMPLETE HAUSA NOVEL" border="0" data-original-height="1584" data-original-width="2048" height="310" src="https://1.bp.blogspot.com/-n5xE_N4D_CY/X8xgJ6CyTUI/AAAAAAAAJck/k-XJ2NDkqXckQzGzxCgcu8oTQfSQBFtWgCLcBGAsYHQ/w400-h310/HAQQI.jpg" title="HAQQI COMPLETE HAUSA NOVEL" width="400" /></a></div><br /> Compiled by Princess Aysha Muhammad (Humaira) <p></p><p><br /></p><p><br /></p><p>[5/17, 15:33] Umar Dalha: ☠HAQQI☠</p><p><br /></p><p> ✍🏾mr. melody💥 </p><p><br /></p><p> 🌙april-2017</p><p><br /></p><p> </p><p> IT'S PAGE 1⃣-1⃣0⃣ ONLY</p><p> AND</p><p>⇨BEST ON A TRUE LIFE⇦</p><p> </p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p> Page1⃣&2⃣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Dedicated to my beloved sisters ummi-aysha & fatima-bintu👩👧*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>~Actually this what was happened to our elder brother and our friend also, finally he has answered Allah's call already since last two years ago. May your gentle soul rest in perfect peace (muhammad abdullahi) ameeen~</p><p><br /></p><p><br /></p><span><a name='more'></a></span><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>βismillahir rahmanir rahim</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Ranar saturday quarter to 11 O'clock morning na</p><p>tashi daga ghetto nayi shaye-shaye na fitar</p><p>hankali wiwi, madaran suku die, coideen, drugs</p><p>kai in takaice muku zancen duk wani abu da kuka sani</p><p>mai gusar da hankali banda giya sai dana sha shi sannan na</p><p>kama hanyan gida. Tafiya nake ina malangarine kamar akwalan keke yara su kayi dan-dazo suna min ihu suna cewa “yayi marisa ya sha capsule sha" idanu na a rufe suke kuf! kamar mai bacci saboda shawuwan da nayi, nan take na lalubi duwatsu a kasa jifa kawai na fara yi kota ina kamar zararre har na fasawa malam yusuf limamin unguwar mu kai, yaran duk suka watse kowa sai gudu yake ga sabon mahaukaci.</p><p> Saukan bulalai kawai na fara ji a jiki na any how, manyan unguwar mune suka nad'a min na jaki a bisa abunda na aikata na rashin hankali. A</p><p>wurin na fad'i kasa sai bacci ga kwatami da bola</p><p>a gefe. Nine ban farka ba sai bayan sallah'n la'asar ba wanda yazo ya tashe ni balle ya jany'e ni daga gefen kwatamin, sai naji duk jiki na yana</p><p>min zafi da rad'ad'i ga wani uban yunwan da</p><p>nake ji a hankali na lalla6a na tafi gida. Zuciya a dakule na bankad'e kofan gidan na kutsa kai ciki, kasantuwar gidan namu na haya ne duk matan gidan suka shige shashin su da y'ay'an su gudun kada na illata su, kitchen na wuce na shiga</p><p>bubbud'e tukwane kamar wanda yayi ajiya amma</p><p>ban samu koda k'anzo ba hakan yasa na shiga</p><p>kwalawa mahaifiya ta kira a tsawace daso!</p><p>Daso!! Tana kyarma ta fito da tsohon cikin ta</p><p>haihuwa yau ko gobe, “ina abinci na!?" nan ta fara kame-kame “umh umh yi hakuri muh'du,</p><p>wallahi ban zata zaka bukaci abincin bane shi</p><p>yasa na baiwa su fatima d'azu" “me! Abincin nawa?,</p><p>wallahi karya kike, uban ki ne yake nemowa ko</p><p>uba na?" “dan Allah kay...." maganar da ban bari ta karasa ba kenan na wanke ta da mari tas! A</p><p>kuncin ta na hagu na sake d'ago ta da wani marin a kuncin ta na dama nan fa na hau yin ball da ita tana kuka “wallahi yau sai kin</p><p>yabawa aya zakin ta, sai na kashe ki na kuma</p><p>kashe d'an dake cikin ki" wallahi haka nayi ta jibgan mahaifiya ta ko tausayin ta bana ji, nan ta shiga rera kukan neman agaji tana kuka mai cin rai wai ga d'an data haifa nan yana dukan ta instead of ko zagi kada ya jawo mata, wallahi musa ina baku labari duk sanda na tuna abubuwan da na yiwa mamata a rayuwa sai naji kamar na kyastawa kaina wuta ko zan d'an ji sauk'i a cikin zuciya ta, nida aboki na aliyu da ake bamu labarin banda hawaye babu abunda muke yi, gaskiya *HAQQI* ba wasa bane dan wallahi ya zarce tunanin mutum balle aljan, duk wanda ya san muh'd idan ya kalle shi a cikin wannan halin wallahi sai yayi masa kuka, ya kumbura sosai na fitar hankali domin rigan jikin sa sai in an raba shi kashi biyu sannan zan d'au daya a hakan ma zai min yawa, a wannan halin da yake ciki duk da cewa ba wanda yasan gawan fari amma wallahi shi bana tunanin zai wayi gari da rai, duk wanda bai san meke faruwa bama zaiyi tunanin cewa ko yana dauke da wani cuta ne amma wallahi al-hak'i ne kawai ke bin sa. Any where lets back to our normal business, ni kuwa ko a kwalar riga ta balle naji tausayin d'an dake cikin cikin ta sai kace ba ita ta haife ni ba.</p><p> Shovel na dauko na shure ta da kafa ta fad'i kasa na d'aga shovel d'in zan kwad'a mata ta saki kara iya karfin ta hakan yasa ali, hamza</p><p>da dauda shigowa cikin gidan a guje suka bankad'e ni</p><p>gefe nayi tangal-tangal kamar zan fad'i ali ya hauni da masifa “mahaukacin ina ne kai? Wannan ba mahaifiyar ka</p><p>bace Dan uban ka? Ko baka san da ciki a jikin ta bane kayi mata duka haka?" kafin na ankara naji saukan mari on my left cheek tas! Wallahi har sai dana ga star-stars, d'agowa nayi naga hamza ne tsaye a kai na kafin nayi yunk'urin tashi ya kai min a wonderful punch a fuska ta wanda yasa baki da hanci na suka</p><p>fashe. </p><p> Dama hamza ko ransa ba a 6ace yake ba yana cracking sosai during speaking balle a yanzu dana ga ya harzuka sosai zagin ma ya kasa yimin sai bugun da yake ta kai min any how. Dukkanin su</p><p>abokai na ne and also my age mate sai dai yadda nake jin tsoron su bana</p><p>tsoron wani mahaluki a duniya ban san dalili ba, a cikin su hamza ne kad'ai abokin shaye-shaye na amma ali da dauda basu ta6a shan koda tramol ba balle other drugs masu gusar da hankali. </p><p> With hamza's cracky voice yace “kai dan</p><p>uwar ka wannan ba uwar ka bace? Wani irin</p><p>kwaya ka sha yau?" ali da dauda suna can wurin</p><p>mamata data ke rera kuka suna bata hakuri daga karshe suka tattara ta izuwa dak'i. Duk wannan chakwakiyar da muke yi ba wanda ya shigo haka zalika ba matar data fito a cikin gidan. Kamani su kayi suka min d'aurin sweet wato sama d'auri k'asa d'auri da igiyan shany'a sannan su kayi waje dani.</p><p> Garden suka kai ni inda babu wanda zaiji sautin kuka na balle ya kawo min agaji. As always kamar yadda nasan dauda da hamza basa rabuwa da bulalan cable mai baki goma a jikin su, with my big surprise gani nayi sun d'aga riga gami ciro bulalan cabels d'in a kunkumin su, kowa yana rik'e da nasa. Hamza da crackcy voice nasa yace “yau zaka ci uban ka, in</p><p>shaye-shaye ne zaka nuna min ne? yaushe Ka fara shan kwaya ne harda zaka je ka sha wani drugs wanda ko gajiya bazai iya cire min ba zaka zo ka yiwa mamar ka duka?" ihu</p><p>nake yi tsakani da Allah ina basu hak'uri can naga ali ya zame jikin sa ya bar wurin ashe dai shima bulalan yaje tsinkowa, kawai ganin sa nayi ya fito da santalelen bulalan k'aya yana zuge gany'any'akin dake jikin bulalan. Ai kuwa volume na ihun nawa ya dad'u kamar wanda yaga mala'ikan mutuwa saboda yadda naga sun had'e rai suna wani zazzaro min na mujiya nasan dakuwa zanyi na fitar hankali wanda idan aka kaini asibiti sai likitoci sun tambaye ni da damisa nayi fad'a koda zaki.</p><p> Without noticing of anything naji sauk'an duka tun ina ihu har murya na ya dashe sai sautin saukan bulalai kawai ke tashi a wurin, sai da nayi laushi sosai</p><p>sannan suka kyale ni, nafi 2 hours ban san a ina nake ba farkawa kawai nayi na ganni kwance a kan gadon asibiti da drip a hannu na wai ashe har sun kawoni gida mahaifina na yayi ta masifa daga karshe ya kirawo y'an Qato da gora a kayi gaba dasu a kan cewa sai time d'in dana farka zasu bada bailing. wallahi na daku a wannan ranan jiki na ya farfashe sosai ko ta ina kwarzanin bulalan k'ayan ali ne sai kuma fashewan da jiki na yayi wannan kuma na bulalan cabel nasu hamza ne.</p><p> *~*~*~*~*~*</p><p> The following day, 8㏂ mamata ce da kanta taje tayi bailing d'in su hamza daga office na y'an qato da gora suka dawo gida. Ni kuwa bayan likita yazo ya dubani yayi prescribing min wasu medicines d'in da ya aika wata nurse ta d'ebo masa a dispensary sannan ya had'a mana da takaddar sallamar mu tare da yiwa baba na gargad'in cewa kada a sake bari na, na sha kwaya saboda kwayoyin da nake sha sunfi karfin jini na baba na yace “toh zamu kiyaye insha Allahu doctor". bayan mun dawo gida kannena aisha da fatima sun dawo daga tallan awara baban mu yace “ke aisha?" “na'am baba" ta amsa mai “dauko mana tabarma da sauri" bayan ta dauk'o ya umarce ta data shimfid'a min tabarman. Bararrajewa nayi a kan tabarman, baban mu ya shiga kwalawa mamar mu kira “daso?! Daso!?, wai baza ki fito bane?" “Gani nan zuwa" ta fito tana mai cizon le6e da turo cikin ta “yanzu ke maryam ashe baki da mutunci? Baki da hankali? D'an nawa tilo kika zuba ido abokan sa su kayi mai dukan tsiya eyyeh?" “Haba malam? Kai kenan baza ka daina d'aurewa karya gindi ba? yaro yana neman halaka ni y'an albarka suka kwace ni a hannun sa da kyar amma kake wannan furucin?" Ta kare maganar cikin sautin kuka, haushin ta kawai na fara ji take na fara kwarara mata ashar baba na yana ji amma haka ya kyale ni na rinka zagin mahaifiya ta wacce a yanzu ita take kula dani day and night duk da cewa abubuwan da nayi mata a rayuwa are unforgettable and unforgivable ne amma a haka take bani kulawa na musamman, ban ta6a sanin tana sona ba sai dana fad'a cikin wannan bala'in mai tsanani, tunda mahaifiya ta ta haife ni ban ta6a sata farin ciki ba kullum sai nayi mata abunda za tayi kuka amma bata ta6a bud'e bakin ta tace min muh'd Allah ya wadai da kai ba. Musa, Aliyu wallahi na zalinci kaina, ku duba kuga yadda na dawo? Duk wanda ya kalle ni sau d'aya baya marmarin ya sake kallo na amma ga uwata nan wacce na raina wacce na tsana ba tare da tamin komai ba ita take caring d'ina. Nayi kashi, fitsari ta wanke, nayi amai ta goge, idan kayana sunyi daud'a ta wanke min su ta kuma yimin wanka, sai kuma ya fashe da kuka mai tsuma zuciya abun tausayi da shi. Yana shesshek'a yace “yanzu dare yayi musa, quarter to 10㏘ ya kamata kuje gida ku huta zuwa gobe insha Allahu sai mu daura daga inda muka tsaya, hawaye ne kawai ke forming on our both left and right cheecks nida aliyu nace “Allah ya kaimu da rai da kuma lafiya, sai da safe" yace ameen Allah ya nuna mana, ko uffan aliyu ya kasa cewa sai hawayen da yake ta zubarwa muka fice daga dak'in. Mahaifiyar sa ce zaune a kofar dak'in bisa tabarma muna wiping off our tears with hanky nace “toh mama mu zamu wuce sai da safe" “toh musa ku huta gajiya ko? mun gode! Mun gode!! Allah ya saka da alkhairi ya kuma bar zumunci" da kyar aliyu ya iya bud'e baki yace “ameen" “aliyu ka gaida min maman ku sosai da gajiya and you also musa" da “toh" muka amsa mata sannan muka fice...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>😊мr. мεισdγ🍉</p><p><br /></p><p><br /></p><p>[5/17, 15:33] Umar Dalha: *LITTAFI* HAQQI☠</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p> ✍🏾mr. melody💥</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🌙april-2017</p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> page3⃣&4⃣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*Dedicated to my beloved sisters ummi-aysha & fatima-bintu👩👧*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau take sunday ban fita wurin aiki na ba kasantuwar ina hutu, bayan nayi wanka around 9㏂ na kira aliyu a waya not long enough sai gashi yazo muka wuce al-arfat</p><p>shopping complex muka d'anyi sayayyan drinks daga ciki akwai maltina, bitter lemon, exotic, fresh milk da sauran su, a k'alla dai munyi spending kud'i 1k sannan muka wuce gidan su muh'd. Kamar kullum yau ma mahaifiyar sace zaune a gefen sa da kanta take feeding d'in sa break fast da soyayyan doya mai kwai sai black tea. “yau Kune a gidan namu da safe haka?" “hmm eh wallahi mama, ina kwana?" Muka fad'a tare da aliyu yayin da muka durkushe har k'asa “lafiya qalau y'ay'an nan, ya su maman ku da sauran yaran?" “kowa lafiya qalau wallahi mama, ya mai jiki?" “toh ga mai jiki dai, sai addu'ah" “Allah sarki, Toh Allah ya bashi lafiya ya kuma sa kaffara ne" da “ameen" ta amsa mana sannan ta fice ta bamu wuri muka zauna gami da ajiye shopping d'in da muka yo masa a gefen sa. Kallon sa kawai na tsaya yi saboda naga kumburin nasa ya dad'u ba kamar na jiya ba, “sannu muh'd, Allah ya baka lafiya" abunda aliyu ya iya fad'a kenan “ameen aliyu, ina gajiya musa?" “ba gajiya wallahi, kana cin abinci muka katse</p><p>ka ko?" fake smile yayi “no karku damu dama i'm</p><p>platefull kawai dai ta matsa min dana ci ne that's all" ajiyar zuciya aliyu yayi sannan yace “Allah ya kyautata</p><p>karshen mu" mu duka muka ce “ameeen" daga nan dak'in ya dauk'i shiru na wasu y'an dak'ik'u kamar ba halittu a cikin sa duk munyi zugum, chan! aliyu ya nisa sannan yace “anya muh'd zaka iya cigaba da bamu labarin nan kuwa?" “why not?, insha Allahu zan iya don't bother yourself" "toh shikenan muna sauraron ka" na fad'i hakane yayin da nake gyara zama dan</p><p>sauraron labarin da kyau.</p><p> bayan na fara samun sauk'i daga dukan da su</p><p>hamza suka min na d'an fara fita waje dan shan iska, as you know already mahaifin mu jobless ne bashi da aikin fari balle na bak'i, yau shine wannan</p><p>gobe shine wancan da ky'ar yake iya samo mana na abinci balle y'an kud'ad'en da zamu biyawa</p><p>kawunan mu bukatu dasu, duk da rashin da muke fama da shi na talauci amma a haka idan maitana ya tashi wato kwad'ayin shaye-shaye na idan ya motsa tisa shi nake a gaba har sai ya bani kud'i, wani lokacin ya bani 500 wani lokaci kuma 200 saboda ni kad'ai ne namiji babba a gidan mu shi yasa bana tambayan abu na rasa kamar yadda nima bana tambayar abunda nasan yafi karfin gidan mu. Ta sanadiyar wannan gatan da yake nuna min ne yasa na 6aci dan har yau ban iya wani aikin hannu ba infact ban ta6a yin wata sana'a ba kullum mahaifina ne ke bani kudi, shi kuwa idan na tambaye shi kud'in bani kawai yake yi baya tambayata me zanyi dasu ni kuwa sai naje can ghetto na kashe mana kud'in tas! a kan kayan maye tare da abokai na, na banza.</p><p> Wata rana mahaifin mu ya dawo daga gona, gonar</p><p>ma ba tasa bane daukan sa haya aka yi wato</p><p>barema, ko gida ban kyale sa ya shiga ba na tare</p><p>shi a bakin kofar gidan ba tare dana kar6i icen da ya d'auko ba balle nace masa sannu da zuwa. Kai</p><p>tsaye nace “baba bani da kud'i fah kuma ina jin</p><p>yunwa" “toh baka ci abinci bane ko basu girka bane?"</p><p>fuska na 6ata “ni in za'a bani a bani ba wai a tisa ni a gaba da tambayoyi ba, in kuwa baza a bani bane let me know shine kawai ehe!" sai daya d'an 6ata lokaci yana kallo na finally ya d'an karkace ya zaro 1k yace “toh gashi kaje ka kawo min 800 yanzu" kar6an kud'in kawai nayi ba tare da nayi godiya a gare shi ba sai ma y'an kumbure-kumburen dana keyi, reason nayin hakan kuwa shine 200 ya min kad'an. Ghetto na wuce wallahi sai dana ga bayan 200 d'in nan a kan kayan maye sannan na dawo gida.</p><p> Rannan mahaifiya ta tana toya awara wa kanne na a kitchen suna kaiwa godiya private school na diro mata ba sallama shiru tayi min gudan kada tayi magana nayi mata wani abun, matsami na</p><p>dauk'a na kwashi awara a cikin man tuyan na zuba a plate sannan na barbad'a yaji a kai. Duk abubuwan dana keyi bina kawai take da ido “wai ya da kallo hakane? Ko sai na bad'e idanun da barkono ne sannan zaki daina kallo na?" nayi maganan ina mai zare mata ido kai kace da y'ata nake maganar bada MAHAIFIYA TA ba. “yi hakuri ka jeka, babu komai ai duniya ce" doguwar tsaki naja sannan nace “lahira ce ba duniya ba iskanci kawai" ina kaiwa nan na shige cikin dakin ta na zube a kan single couch nata na d'aura plate na awaran bisa cinya ta sannan na hau awaran da chi like there's no tomorrow. Bayan na cinye awaran sai kuma naji kwad'ayin shaye-shaye na ya motsa and my pocket was dried nan fa na shiga chaje mata dak'i da kwanuka amma ban samu koda kwandala d'aya ba, zuciya a dak'ule zan fita kenan sai kuma nayi step backward kasantuwar mahaifiyar tawa uwar adashe ce sai na karasa kan gadon ta na d'aga pillow, wani jaka na gani irin wanda ake daurawa a k'ugu mai d'an girma haka, nan fa zuciya ta tayi haske ban tsaya wata-wata ba na bud'e jakan, dubu-dubu, dari biyar-biyar sai y'an dari bib-biyu na gani a ciki wanda ni kaina ban san ko nawa bane, tattara su nayi kaf! Zan fita dasu kenan sai kuma naji tausayin ta ya kamani “yanzu idan na tafi da kud'ad'en nan ai zata iya rasa rayuwar</p><p>ta ko?" Tambayar da na yiwa kaina kenan, take imani ya ziyarci ruhi na, 200 kachal! na dauka a cikin kud'in na mayar mata da sauran cikin jakan na tura shi karkashin pillow'n kamar yadda yake as before wanda baza tayi tunanin wani ya ta6a mata kud'i ba. </p><p> Ghetto na wuce nayi ta shaye-shaye wanda har sai da zama ya gagara tsayuwa ta gagara, a ghetton ma na kwana tsabakin yadda na shayu na gama ficewa a hayyaci na gaba d'aya. </p><p> Hmm muh'd yayi murmushin takaici sannan yace “wannan fah ina</p><p>baku labarin aika-aikan dana keyi a cikin gida ne</p><p>dan wallahi hatsabibanci na ya wuce nan." Wannan karon ni ko aliyu ba wanda yayi hawaye a cikin mu sai sauraron sa kawai da muke yi, aliyu yace “toh muna sauraron ka muh'd, ka bamu labarin kato6aran</p><p>daka tafka a waje amma kafin nan ga wannan ka d'an sha" yayi maganar ne yayin da ya bud'e ledan drinks d'in da muka taho masa da shi ya d'auko maltinan gwan-gwani ya bud'e sannan ya mik'a masa, kad'an ya sha ya ajiye sauran.</p><p> Sanin kanku ne musa, a daa lokacin ina ji da kaina iskanci babu wanda bana yi, fannin mugunta da cin zali kuma kowa ya sallama min dan ba'a barni a baya ba. Wata rana da yamma muna zaune chamber ni, ali, hamza, dauda, abdullahi da kuma yusuf muna hira sai ga hassan mamar sa ta aike sa shagon abbo siyan flower, yazo wucewa kenan na kira sa “kai hassan zo nan" ya waiwayo ya kalle ni ba tare da yana zuwa ba, “wai baza ka zo bane?" na fad'a a tsawace still yak'i zuwa na tashi a fusace nayi kansa “kai dan uwarka ba kiran ka nake yi ba?" kuka ciki-ciki ya fara yi na zabga masa tafi yasa ihu “dan uwarka kayi kukan da tushe, in uban ka ya kira mu bama zuwa ne?" Da wannan na kyale shi yayi kwana abin sa, sai da yayi nisa kad'an yayi min dak'uwa yana cewa “kaci uwar shege tsinanne munafiki mugu azzalimi kawai" “ni ka zaga?" na fad'a da d'an ihu gami da pointing na kaina “eh kai d'in mugu kawai, kuma wallahi Allah ya isa na" “ai kuwa yaro ka zama nama dan wallahi idan na kama ka sai naci uwar ka" a haka fa na hana yaro zuwa aike, da isar sa gida bai jima ba sai ga mamar sa ta fito dama bata da hakuri idan ka ta6a mata y'ay'a, daru mu kayi da ita sosai finally abun ya bani haushi nace da ita “sai dai in bazai na fita waje ba, amma wallahi muddin na rik'e shi sai naci uwar sa" “au! Rashin kunyar taka har ya kai kace zaki ci uwar d'ana? Lallai yaron nan mahaukaci ne kai" Da kyar su hamza suka bata hakuri ta amince, dan cewa tayi sai ta kira min police su tafi dani, duk da cewa ina tsoron zuwa bayan canter amma sam! ban nuna mata a fili ba sai dad'a kurari nake.</p><p> Haka dai rayuwa ya cigaba da tafiya kullum cikin rikici nake, na daki d'an wannan na daki d'an wancan har y'an unguwa suka kai report wa babana cewa na fita hanyar y'ay'an su ko kuma su dauk'i matakin daya dace, ni dai bana kwa6uwa dan kuwa sai dai ayi ta min surutu amma duk a banza na riga na zama fitinanne na kin karewa idan naje nayo shaye-shaye na dawo gida duk wanda na samu mahaifiya ta ko kanne na sai na jibge su iya son raina baban mu baya cewa komai sai dai idan su hamza ne suka min duka a bisa dukan mamata ko kanne na da nayi. Ina mai tabbatar muku cewa mahaidiya ta, ta kamu da ciwon hawan jini nine ta sanadiya ta. A nan ya fashe mana da kuka yana zubar da hawaye zafafa, in between crying yace “dan Allah aliyu ka kira min *MAHAIFIYA TA* na sake neman gafarar ta" wallahi da wannan furucin nasa ya karya min zuciya ban san lokacin da hawaye suka fara rolling on my both cheeks ba. Kamar yadda ya bukaci aliyu daya kira mai mamar sa not long enough suka shigo tare gaba d'aya hankalin ta ya gama tashi a zaton ta jikin nasa ne ya tashi, a gaban ta muh'd ya zube on his knee gami da duk'ar da kansa k'asa yace “dan Allah dan annabi mama ki yafe min, ki gafarce ni ba dan hali na ba, ban kyautata wa kaina ba ko kad'an, wallahi kaicho na!!" ya kare maganar da kuka mai tsuma zuciya a hankali ya sulale k'asa ya kama kafafun ta yana neman tuba sai kukan da yake yi mai sauti.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>😊мr. мεισdγ🍉</p><p><br /></p><p><br /></p><p>[5/17, 15:33] Umar Dalha: *LITTAFI* HAQQI☠</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> ✍🏾mr. melody💥</p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🌙april-2017 </p><p> </p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> Page5⃣&6⃣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*dedicated to my beloved sisters ummi-aysha & fatimah-bintu👩👧*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Tausayin sa ya dad'a lullu6e mata zuciya bata ma san lokacin data fara zubda hawaye ba. </p><p>Duk'ar da kaina nayi k'asa wasu zafafan hawaye nake tsiyayarwa na d'an ta6a aliyu nufi na ya tashi mu tafi amma sai ya gyad'a min kai alamun a'a ba yanzu ba, ni kuwa zuciya ta baza ta iya jure ganin muh'd da mahaifiyar suna kuka ba, hakan yasa na tashi zan fita aliyu ya rik'o min hannu ba yadda na iya dole tasa na zauna.</p><p> “Muh'd na yafe maka duniya da lakhira, Allah ya baka lafiya ya kuma yima albarka" tayi maganar cikin kuka gami da d'ago sa daga durkushen da yake ta rungume shi shima yayi hugging nata back yana kuka tana bug-buga bayan sa yana cewa “nagode mama Allah ya saka miki da gidan Aljannah, lallai kin cika uwa ta gari" sun d'au lokaci mai tsawo a rungume da juna finally tayi breaking hug d'in a hankali. “mama?" Yayi exclaiming d'in sunan ta da sark'ak'iyar muryar sa “na'am muh'd?" “mama Ina su aisha, fatima da aunty?" Hawayen dake rolling on her both cheeks ne tasa hannu tayi wiping off sannan tace “sun tafi talla, me kake so suyi ma?" “Ba abunda nake so suyi min face gafara, domin na zalince su a rayuwa" ya kare maganar da kuka. Lallai rayuwar muhammad tana k'unshe da darussa bila adadin, wanda mu matasa ya kamata muyi duba ga yadda rayuwar muhammad take a daa can baya, shan kwaya bashi da wani fa'ida kuma ba abunda baya haifarwa, yanzu wani abu da yake damun mu, mu matasa shine wai idan kai baka shan drugs, cigarrete, wiwi, oris da shi-sha (pot) muddin dai baka shan d'aya daga cikin wad'annan haramtattun ababen wai kai baka cika gaye ba, a'uzubillahi, toh kada Allah yasa na cika gayen in dai sai nayi shaye-shaye ne. Wato wani abu d'aya da har yanzu mutane basu fahimta ba shine, turawa sun k'irk'iro shi-sha ne ba dan komai ba sai dan su lalata mana tarbiya wanda iyayen mu suka 6ata shekara da shekaru suna bamu ita. Da farko abunda za muyi la'akari da shi a nan shine: shi-sha da oris duk kamshi d'aya ne dasu sai dai shi oris kamar taba yake a nannad'e, karfa ku manta shi-sha tsani ne wanda mutum zai bi a sauwak'e ya fara shan taba wiwi da sauran su ba tare daya sani ba, kullum ka saba shan shi-sha kana sayan flavor 350 ranar da baka da kud'in sayan flavor'n kuma kana kwad'ayin shan shi-sha cewa za kayi “ba gara naje na saya oris naira goma ba na sha tunda duk kamshi d'aya ne dasu" toh daga ranar da tunanin haka ya fad'owa mutum a rai wallahi tasa ta kare domin shaye-shaye zai fara gadan-gadan kuma dan Allah dear readers ku duba ku gani 80% cikin 100% na mashayan yanzu matasa ne, 70% cikin 100% kuma daga shi-sha suka fara shaye-shaye har suka fara shan wasu kwayoyin, dama shi-sha foundation ne na koyan shaye-shaye wanda turawa suka kafa dan lalata tarbiyan y'ay'an musulmai, yanzu ma abun harta 6aci akwai turare mai kamshin flavor'n shi-sha wai (straw-berry) har mutane suna saya su shafa a jikin su dan rashin hankali, yo! Baka sha amma idan ka had'u da wanda bai san cewa turare bane shikenan kimar ka ta zube a idanun sa, kai bada girki ba amma da warin hayak'i. Allah ka kare mana imanin mu ameen ka kuma tsare mu da muggan abokai domin masu iya magana suna cewa zama da mad'aukin kanwa shike kawo farin kai. Masu sha Allah ya shirye su mu kuma da bama sha Allah ya dad'a tsare mu ameen thummah ameen.</p><p> Da kyar na samu nayi convicing na aliyu ya tashi muka tafi gida da sharad'in cewa zamu dawo by 8pm dan jin karshen labarin kasantuwar yau babu zuwa majalis. Haka kuwa aka yi 8pm bayan munci abinci muka wuce gidan. Kai tsaye muka zarce dak'in nasa wannan karon k'anwar sa fatima ce ke gefen sa a zaune tana taya shi hira. Cikin girmamawa ta gaida mu, muka amsa sannan ta tashi ta fice muka zauna. </p><p> Da fara'a kwance a fuskar sa yace “Sannun ku da zuwa" “yauwa, ya kaji da jikin naka kuma?" a cewar aliyu “hmmm" kawai yayi ba tare da amsa ba “amma muh'd baza ku koma asibitin nan ba kuwa?" Na fad'i hakan ne yayin da nake kare mai kallo dan wallahi babu alamun sauki a tattare da shi saima abunda ya karu. “eh toh abunda yake kaimu asibitin dama magungunan cin abinci ne da kuma irin abincin da doctor yace ina ciki" “haa'ah, kamar ya? Dama basa duba jikin naka ne duk zuwan ku asibitin?" aliyu yayi maganar da mamaki “eh dama tun kafin jikin nawa yayi tsanani likitan ya shaidawa baban mu cewa ciwo na bana asibiti bane kamar yadda binciken su ya nuna bana d'auke da wata cuta daya sa nake wannan kumburin" ajiyar zuciya nayi sannan nace “kun gwada na gargajiya ne?" Ruwan dake gefen sa a cup ne ya d'aga ya d'an kur6a kad'an ya ajiye ya nisa sannan yace “har gombe an kaini amma bamu dace ba, nifa ina ji a jiki na bazan tashi ba" da sauri nace “subhanallahi, bai kamata ka furta wannan kalmar ba, sai kace ba musulmi ba? ka tuna fa cewa ba abunda ya gagari Allah, Allah gagarau ne saboda haka ka cigaba da addu'a muma cikin yima addu'ar muke a kullum kuma insha Allahu zaka samu lafiya" “toh Allah yasa, nagode Allah ya saka da alkhairi ya bar zumunci" nida abokina aliyu muka masa da ameen. “Toh aliyu ne dama ya matsa min akan lallai-lallai muzo ka karasa mana labarin, zaiyu ka karasa mana yau ko kuwa mu hakura sai gobe?" Lumshe idanun sa yayi a hankali kamar mai jin baci yace "gaskya da zaku hakura sai goben da yafi, saboda ina jin kaina yana sarawa ga kuma baccin da nake ji tun dana gabatar da sallah'n magharib" “kash! Subhanallahi Allah ya yaye, ka sha magani kuwa?" aliyu ya tambaye shi “a'a, ban sha ba amma da zarar na samu nayi bacci zan tashi babu ciwon kan" “toh Allah ya baka lafiya, mu zamu wuce gida sai goben in Allah ya kaimu" na fad'i hakanne yayin da muke mik'ewa tare da aliyu “Allah ya kaimu da rai da kuma lafiya, nagode! Nagode!! Allah ya saka da alkhairi ya kuma bar zumunci" da ameen thummah ameen muka amsa masa sannan muka fice bayan munyi sallama da mahajfiyar sa.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>😊mr. melody🍉</p><p><br /></p><p><br /></p><p>[5/17, 15:33] Umar Dalha: *LITTAFI* ☠HAQQI☠</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p> ✍🏾mr. melody💥</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🌙April-2017</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Page7⃣&8⃣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*dedicated to my beloved sisters ummi-aysha & fatimah-bintu👩👧*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Yau take monday muna da general exam na english paper 1-3 Tun 9:30am sai 4:30pm muka kammala. Bayan mun dawo gida so exhausted tare muka ci abinci da aliyu bayan nan ya wuce gida yin wanka nima na fad'a a family bathroom na gidan mu dan watsa ruwa.</p><p> 30 minutes after sai ga shi ya taho sanye cikin kananan kaya white t-shirt ne mai style da y'ay'an beads da ¾ amry trouser ni kuwa jallabiyar makkah na zurmud'a sannan muka wuce gidan su muh'd dan jin karashin labarin nan nasa. Kai tsaye muka fad'a cikin gidan da sallamar mu matan gidan suka amsa muka gaisa dasu sama-sama sannan muka shige cikin dak'in a inda muka tarar da mamar sa tana bashi abinci a baki.</p><p> “Ina yini mama?" muka fad'a tare da aliyu yayin da muke kokarin zuwa kasa “lafiya qalau, sannun ku da zuwa" “yauwa mama, ya mai jikin?" Ajiyar zuciya tayi gami da cewa “wallahi jikin nasa ba wani alamun sauki, jiya iyau koma ince sai dad'uwa yake" na d'ago idanu na, na zuba su kan muh'd wanda tun shigowar mu ya jingine a jikin bango idanun sa a lumshe suke sunyi kanana mini-mini dasu tsabakin kumburin da yayi har za kayi tunanin cewa idanun nasa basa bud'ewa ne. “Allah ya sauwake" cewar aliyu “ameen ya Allah, throughout yau baku zo wurin d'an uwan naku ba sai yanzu, lafiya dai ko?" Murmushin yak'e kawai nayi nace “munje zana jarabawa ne wallahi shi yasa bamu zo ba" “toh Allah ya baku sa'a yasa ku fito da flying colour" da ameen muka bata amsa sannan ta fice. Duk muka yi shiru ba wanda yace koda uffan aliyu ya duk'ar da kansa k'asa kamar me nazarin wani abu, kwallafa idanu na nayi a kan muh'd ina kallon shi cike da tausayawa shi kuwa har yanzu idanun sa a lumshe suke wasu siraran hawaye na gani sun gangaro masa a hankali ya fara yin kuka mara sauti tausayin sa daya min yawa yasa na kasa appeasing d'in sa kamar yadda aliyu ma ya kasa. Yayi kuka mai isar sa ba wanda ya lallashe sa a cikin mu saboda kukan nadama ya keyi bai kamata mu lallashe sa ba, kukan da yayi zai sa ya d'anji sauqi koda kad'an ne a cikin zuciyar sa. Cikin rawar murya yace “sannun ku da zuwa" aliyu ne ya amsa mai da “yauwa" shi d'in ma cikin shesshek'an kuka ne, ya d'aura da cewa “sannu muh'd, Allah yaye ma wannan musiba" kai yake kad'awa a hankali ga kuma hawayen da suke rolling on his cheek “musa baza kayi min magana bane?" Cike da tausayawa na matsa kusa da shi nasa hannu na share masa hawayen da suke sauka kan kumatun sa nace “yi hakuri, sannu kaji? Allah ya baka lafiya ya kuma sa kaffara ne" kukan da nake matsewa ne ya kwace min, gefe na koma na zauna ina matsar kwalla, sai da duk muka saita kawunan mu sannan muh'd ya sauke sassanyar ajiyar zuciya ya kalle ni ya kalli aliyu yace “mu d'aura daga inda muka tsaya jiya ko?" da sauri aliyu ya gyada masa kai gami da cewa “eh". </p><p> Muh'd ya sauke sassanyar ajiyar zuciya a karo na biyu gami da gyara jinginuwan sa a jikin bangon ya fara da cewa “as usually dama bani da wani aiki sai dai naje ghetto nayi shaye-shaye sai nayi d'ub nake shigowa cikin unguwa duk yaron dana had'u da shi dukan sa nake tamkar aiko ni aka yi daga sama jama'ar unguwa su kayi ta min magana amma kota kawunan su bana bi sai ma ashar d'in da nake ta faman kwararo musu, baban su usaini ne yazo ya sameni ina langa6e a jikin bango sai wani lumshe ido nake saboda yadda na shawu over, yazo ya sameni ne akan na lakad'awa inusa duka kanin usaini har sai da na fasa masa baki “kai muh'du yanzu abunda kayi ya dace kenan?" Cikin yanayi na shawuwa na kalle shi da ido d'aya nace “daga yau kada ka sake kira na da muh'du, kana ji ko?" Duk da cewa a shaye nake amma da sane na nake fad'in hakan, “yo! Ai sai kaje ka fad'awa uban ka wanda ya rad'a ma sunan kace baka so, ina mai gargad'an ka daka fita a idona na rufe dan wallahi zan sa a daure min kai a garin nan" kallo tara saura quarter nayi masa sannan na tsartar da yawu nace “sunana john daga yau in kuma ka sake kira na da muh'du zaka gane cewa shayi ruwa ne, dan wallahi sai y'ay'an ka sun kasa shaida ka balle matar ka" ya tafa hannun sa yace “innalillahi wa'innaillaihir raju'un!, yanzu kai haukan naka har ya kai kace kai sunan ka john? sunan kafiri?" Tsaki naja na bar wurin sai wani layi nake sai kace mahaukacin jaki, shi kuwa bina kawai yayi da ido baki a wangale. Haka dai a dolen-dole na koma arne in ka kira ni da muh'd na kwararo ma ashar in kuwa john kace sai mu zauna lafiya. Wallahi har yau wasu da john suke kira na wasu kuma da shi suka sanni abun yana bani haushi matuk'a amma ba yadda na iya saboda *NI NAIWA KAINA*. A nan ya fashe mana da kuka yana cizon le6en sa dan takaici, in between crying yace “wallahi shaye-shaye ba abu bane ma kyau, da ban fara shaye-shaye ba, da duk ban tafka rashin hankali dana tafka a duk tsawon rayuwata ba. Nothing is hurting me more and more! like the way that i treated my only mumy harsly like this" kukan nasa ya fad'ad'a Ya sake cewa “peoples are saying what you sow is what you reap either good or bad, yes of course they are right because i have now started reaping all bad things that i have been sowed since" yana kaiwa nan a zancen sa ya duk'ar da kansa kasa yana wani irin kuka mai karya zuciya yana maimaita astagfirullah! Wa'atubu ilaihi Astagfirullah! wa'atubu ilaihi!!...</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Kai jama'a Allah yasa mu dace, matasa dan Allah mu kiyaye shaye-shaye bashi da wani anfani sai ma cutar da lafiyan d'an adam da yake yi. Likitoci sun bayyana cewa shaye-shayen cigarrete, wiwi ko shi-sha yana ru6ar da huhun d'an adam, yana ta6a lafiyar kwakwalwa sai kaga mutum shi kad'ai yana ta surutai, yana jawo cutar daji wato cancer, uwa uba kuma yana zubarwa da mutum mutuncin sa a idanun al ummah. Su kansu masu company'n me suka ce? Cewa su kayi (the federal of ministry of health warns that smokers are liable to die young) abunda suka rubuta a jikin kwalin kenan, abu mai kyau ba sai an fad'a maka cewa wannan abun mai kyau bane kai kanka ka sani, ai ido ba'a nuna masa bacci. Sanadin shaye-shayen nan kwanaki a damaturu na samu labarin cewa wani matashi da bai wuce 22 years ba yaje sha kwaya ya dawo gida ya hallaka mahaifan sa duka biyu har hoton sa na gani, dan Allah me anfanin shaye-shaye ya y'an uwana matasa? bakwa bukatan karin haske ku kanku kun karanta labarin kunji me late muhammed abdullahi ya aikata, kar kuyi zaton ko fictitious story ne wallahi it is true. Bani da ta cewa sai dai nace Allah ya jikan sa da rahama yasa tuban sa kar6a66iya ce mu kuma Allah ya kyautata karshen mu ameen thummah ameen.</p><p><br /></p><p><br /></p><p>😊mr. melody</p><p><br /></p><p>🍉</p><p>[5/17, 15:33] Umar Dalha: ☠HAQQI☠</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> </p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> 🌙April-2017</p><p><br /></p><p>.</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> ✍🏾mr. melody💥</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p> Page9⃣&1⃣0⃣</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>*```this page is dedicated to you my besty <aliyu garba-ALi baii> ana mugun tare wallahi nawan```*</p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p><br /></p><p>Bayan yayi ta istigfari daga bisani yayi murmushin yak'e sannan yace “a rana mai kamar ta yau monday itace babban ranar nadama a gare ni, kuma babban ranar farin ciki a gare ni domin ta sanadiyar wannan ranar na nema gafarar *MAHAHAIFIYA TA* kuma ta yafe min masha Allah, my only mum may Allah (s.w.a) reward you jannatul fiddaus ameen thummah ameen i really so much love my momma you are one in a billions".</p><p><br /></p><p> “I thought ranar da muke zaune a chamber'n kofar gidan mu tare daku muke zaune ko?" zallan Kai kawai muka gyad'a mai alamun a'a ”no bad yau za kuji komai" ya fad'i hakan ne yayin daya d'an kora ruwan faro saboda an hana shi shan ruwan randa kona fan-fo sai swam ko faro.</p><p><br /></p><p> WAto ranar misalin karfe 8 bayan sallah'r i'sha, kwance muke a chamber muna shan iska kasantuwar zafi ake sosai, wani almjiri ne wanda da kyar ya kai 13 years ya shige cikin gidan mu yayi ta bara yak'i fita ni kuwa abun ya bani haushi sai na harzuka na shiga cikin gidan na fito dashi na wanke shi da gigitacciyar mari take ya fad'i kasa sumamme y'an uwan nasa da suka ga haka sai suka kira manyan su suka tafi dashi makarantar su.</p><p><br /></p><p> Wannan yaron dana mara ba-barbare ne (kanuri) Haka y'an makarantar nasu ma duk kanurai ne harda malaman. Haka dai na kwana lafiya a wannan ranar kamar maye yaci shirwa. Safiya nayi guraren karfe goma zuwa sha-d'aya da y'an kai, zaune muke a chamber muna break fast da fara da mai (garau-garau) wanda mamar su shukura take yi na sayar wa.</p><p><br /></p><p> Garadan makarantar su almajirin dana mara daren jiyan ne nayi tozali dasu sunyo gayya kwannen su yana rik'e da allon sa sun nufo kan mu, ganin hakan yasa na tuno da abunda na aikata jiya. Gida na shiga na biya ta kofar baya na gan-gara kasan kwari na gudu.</p><p><br /></p><p> Da zuwan su chamber'n suka tambayi abokan yaron dana mara d'in cewa “a cikin wad'annan wanne ne ya mari baana?" Yaran duk suka kid'ime suka kasa tunano fuskata sai suka nuna modu, modu na ganin an nufo kan sa da saran allo yasa ihu yana cewa “wallahi tallahi bani bane wanda ya mare sa ya gan-gara k'asan kwari ya gudu".</p><p><br /></p><p> Wani babba daga cikin su yace “ya gudu?, toh wallahi baza mu kyale shi ba sai mun d'auki fansar d'an uwan mu" jama'ar unguwa su kayi chaa! A gun kowa naso yaji meya faru. Many'an unguwa suka karaso jama'a suka bub-bud'a musu suka shigo inda garadan nan suke.</p><p><br /></p><p> “Meke faruwa ne aaramma?" Baban su ishaq ne ya tambayi jagoran nasu, yana huci yace “alan-guro wani yaro a gidan nan ya mari d'an uwan mu daren jiya dan yazo yayi bara, yanzu a haka yaron yana can a kwance ba lafiya toh wallahi tunda ya gudu sai mun d'auki fansa" yana kai aya a zancen sa yace “kai kuzo mu tafi" baban su ishaq da sauran jama'a su kayi ta basu haquri amma ina sun kafe a kan magana d'aya sai sun d'auki fansa.</p><p><br /></p><p> Nine ban dawo gida ba sai bayan sallah'r magharib. A nan ne aka labarta min komai, a cikin daren baban mu ya nemo min kud'in motan zuwa maiduguri akan naje can nayi zama na a gun k'anin sa after magana ya lafa sai na dawo gida saboda idan na tsaya naki tafiya zasu iya dawowa ako da yaushe kuma babu shakka zasu d'au fansar su.</p><p><br /></p><p> Dama banyi kwana biyu da yin d'aurayan kayaki na ba, wad'anda suke da datti baza su wuce set biyu bane a ciki, da asuba na kin-kimi jaka ta na wuce tashar motoci terminors.</p><p><br /></p><p> A maiduguri nayi spending 2 months bayan komai ya lafa harma na manta da rikicin daya koro ni daga garin *biu* jiki na ya fara kumburi da naga cewa abun baya yin sauk'i sai na tattara na dawo gida gudun kada jikin nawa yayi worst bana gaban mahaifana.</p><p><br /></p><p> Abu kamar wasa Duk asibitin da muka je sai ace mana wannan bana asibiti bane, na gargajiya ma idan muka je sai ace mana muje asibiti har muka gaji da yawuce-yawuce, daga nan dai aka yiwa baban mu kwatancen gidan wani malami yana can a unguwar nasarawa muka je, baban mu yayi masa bayanin dukkanin abunda ya wakana malamin ya jin-jina kai ya kalle ni sannan yace “kana d'auke-d'auke ne?.</p><p><br /></p><p> “A'a bana d'auke-d'auke"</p><p>malamin yayi shiru yana nazarin wani abu finally yace “kayi tunani dai, baka ta6a d'aukan kayan wani ba?" Same answer na basa, ya sauk'e sassanyar ajiyar zuciya yace “ba shakka wannan kumburin naka yana da nasaba da wani, amma babu wani abu daya shiga tsakanin ka da wani?" “Allah gafarta malam a gaskiya kusan kullum sai munyi rigima da jama'ar unguwar mu kafin lalurar nan ta same ni".</p><p><br /></p><p> “Toh ya zama dole kaje ka bisu d'aya bayan d'aya ka nemi tuba idan Allah yasa wanda yayi ma wannan d'anyen aikin yaji tausayin ka zai war-ware insha Allahu, bayan kwana biyu in kuka babu wani canji sai ku dawo" godiya sosai muka yi masa sannan muka fice. Haka kuwa aka yi duk sai dana bisu d'aya bayan d'aya na nemi gafarar su, alhamdulillahi duk wanda na tunkare shi da maganar yafiya cewa yake ya yafe min duniya da lakhira.</p><p><br /></p><p> Bayan kwana biyu babu alamar canji sai muka koma gidan malamin. shiru yayi yana nazari, sosai ya 6ata lokaci a haka daga bisani yayi ajiyar zuciya yace “lallai al-amarin nan babba ne".</p><p><br /></p><p> “amma kayi tunani da kyau dai" nayi shiru ni gaba d'aya nama manta da wancan almajirin, ina tunowa da shi naji gabana ya fad'i ras! Take hawaye ya gan-garo min baki na yana rawa nace “ba shakka akwai bare-baren almajirin dana mara kwanakin baya har sai da ya suma, kuma y'an uwan sa sunyi ikirarin cewa sai sun d'auki fansa".</p><p><br /></p><p> “Ba-barbare? Tab! Babbar magana" malamin ya fad'a a d'an razane hakan yasa jiki na yayi sanyi matuka “a gaskiya bani da kokwanto suna da alaka da wannan ciwo naka, kuma in kana son lafiya ya zama dole kaje ka nemi yafiyar su dan wallahi kanuran nan suna iya yiwa mutum abunda yafi naka ma, amma kayi tattaki izuwa makarantan nasu ka nemi gafarar su shine kawai mafita a gare ka" godiya sosai mu kayi masa mahaifi na yayi masa d'an dunkuli sannan muka tafi.</p><p><br /></p><p> Kamar yadda malamin nan ya shawarce ni da naje can makarantar nasu neman tuba, haka kuwa nayi amma da naje tsangayar da mamaki na, naga babu kowa a makarantar alamun sun tashi kenan, zubewa nayi kasa on my knees ina kukan fitan rai dan kuwa yanzu na dad'a tabbatarwa da kaina cewa ciwo na yana da alaka da wad'annan mutanen ne. A garin ba inda bamu neme su ba amma sam koda d'uriyar su bamu ji ba.</p><p><br /></p><p> Gaba d'aya tausayin sa ya shige mu sai tsiyayar da kwalla kawai muke dan wallahi ban ta6a ji ko ganin haka ya faru da wani ba koda kuwa a film ne ballantana a history. “Allah yasa kaffara ne ya kuma yaye ma wannan bala'i shine kawai addu'ar, yanzu dai maghariba ya karato kuma ya kamata mu kyale ka hakan nan kaima ka huta" aliyu yayi maganar yayin da yasa hanky yana wiping off na hawayen sa. </p><p><br /></p><p> “Ameen thummah ameen, nagode! Nagode!! Kwarai da gaske da irin kulawar da kuke nunawa a gare ni, Allah ya saka da alkhairi ya kuma bar zumunci" da “ameen" muka amsa masa sannan muka fice bayan munyi sallama da mahaifiyar sa da sauran mutan gidan. *(Allahu akbar! Ashe dai sallamar mu ta karshe kenan Allah sarki rayuwa, Allah kasa mu cika da imani ameen)*.</p><p><br /></p><p> The following day muna da exam na mathsmatics from 9:30㏂ sai 3:00㏘ muka fito daga hall so exhausted ga kuma wani irin fad'uwan gaban da nake ji tun shigan mu cikin hall d'in har muka fito bai daina ba kuma ban san dalili ba, a haka dai muka tsaya da sauran friends namu muka d'an has-haska pictures, a hanya ma muka idar da sallah'n la'asar sannan muka wuce gida. Muna zaune akan d'an benching dake kofar gidan mu nida amini na aliyu sai muka hango keke napep ya shigo layin zuciya ta, ta buga da karfi mai mashin d'in yana wucewa a gaban mu na saki salati saboda mahaifiyar muh'd na hango tana rik'e da tea flask a hannun ta da tabarma.</p><p><br /></p><p> Not long enough muka jiyo karan jiniyar amblance yana shigowa ashe tun tafiyar mu makaranta aka d'ebi muh'd sakamakon jikin nasa ya tsananta fiye da kima. Salati kawai muka rinka yi har aka wuce da gawar sa.</p><p><br /></p><p> Muka d'ugunzuma izuwa makabarta tare da y'an unguwa, wallahi bakwa bina bashin rantsuwa in dai iri na za'a binne a cikin kabarin wallahi sai dai mutum biyu. Bayan an kawo mamacin ramin yayi masa kad'an ta saman kafad'ar sa sai da aka yi ciko da duwatsu sannan aka jera itatuwa followed by gany'e da kwa6a66iyar kasa da busasshiya sai bayan sallah'r i'sha muka baro makabartan. Allah yasa aljannah ce makomar ka muhammad ameen thummah ameen.</p><p> </p><p>Allah yasa mu anfana da wad'annan darussa ameen. Allah muna rok'on ka da kasa mu fi karfin zuk'atan mu, mu kuma cika da kalimatil *la'ilaha il-lal-laa muhammadun rasulullahi sallallahu alaihi wasalam* ameen</p><p><br /></p><p><br /></p><p>```dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah shi kad'an sa malikil quddus, wanda ya ciyar damu, ya shayar damu, ya tufatar damu, ya isar mana. Na rubuta wannan littafi ne dan isar da sako kuma alhamdulillahi na isar, Allah yasa masu irin halayyar sa su gyara dama wad'anda suke yunk'urin bin wannan hanyar ameen. Ya Allah ina neman afuwar ka gare ni bisa kuskure ko tun-tu6en harshe da nayi a bisa rashin sani a dukkanin lamura na, ka bani ladan abunda na fad'a dai-dai ka kuma karamin kaifin basira na rubuta abunda d'umbin jama'a zasu anfana da shi ameen```</p><p><br /></p><p><br /></p><p> мυsα м sαεεd</p><p> (mr. melody)</p><p><br /></p><p><br /></p><p> *```WABIHAMDULLAH```*</p><p><br /></p><p><br /></p><p>Complied by Princess Aysha Muhammad (Humaira) </p><div><br /></div>Muhammad Abba Ganahttp://www.blogger.com/profile/16412370455028324934noreply@blogger.com0