Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Tuesday, July 21, 2015

Allah kuwa matan wannan zamani kuna biyayya ga mazajenku na aure ???

adsense here bana3.jpg

DOMIN KE DA MIJINKI.
««fitowa na 3»»
ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮﺣﻴﻢ
ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﻭﺳﻠﻢ
Biyayya ga miji ba mai iyawa sai mace ta tagari.
Da yawa mata suna so ace sune wadanda Annabi
(S.A.W) ya sifanta dinnan da (Nagari) saidai
biyayyar itace tayi qaranci, ko za ayi saidai a
gabansa, idan ya matsa an watsar kenan.
Wallahi na taso na taras ada iyayenmu mata
magabata suna kwatantawa.
Furaat bn Sa'ib yake cewa Umar bn Abdil'Azeez
yacewa matarsa lokacin daya ganta da wani
jauhari da ubanta yabata.
"Ki za6i Daya cikin Biyu, kodai ki mayar dashi
baitul mali ko kuwa kibani damar rabuwa dake!
"Tace"A kan mene ?
Nafi sonka sama da ninkokinsa"
Sai yasa aka mayar, yayin da yarasu dan uwanta
Yazeed yahau karaga sai yace in tana so zai
dawo mata dashi, sai tace:
"Wallahi sam!
Mijina ya hanani amfani dashi a lokacin da yana
da rai sai bayan yarasu zan dawo dashi ?
"To mace kenan tagari a gidan miji na gari.
Asma'u bnt Kharijatul Furaziy take cewa 'yarta
ranar budar kanta cewa:
"Yanzu fa kinfita daga sheqar da aka qyanqyashe
ki zuwa shimfidar da baki santa ba, da abokin
rayuwar da baki san shiba, ki zamar masa qasa
sai yazamar miki sama, kizamar masa shimfida
zai zama miki turaku, ki zamar masa baiwa, zai
zama miki bawa, kar ki nace wajen neman
abubuwa domin karya gujeki, kar kiyi nisa dashi
domin karya manta dake, idan ya matso, ki
kusance shi, idan yaja jiki, kema ki dan ja da
baya, amma ki kiyaye hancinsa da kunnensa da
idonsa, karya shinshini komai a wurinki sai
qamshi, kar yaji komai sai kyakkyawan abu, kar
yaga komai sai wanda zai burge shi.
Mace tagari takan yi qoqarin tazamar wa mijinta
aljannarsa ce, batason taga gazawarta a
idanunsa, don haka takan yi farin ciki idan taga
murmushinsa, takan damu matuqa in taga
fushinsa koda bada ita yake ba.
Bata jinkiri a wajen abinci, kuma ta iya dafawa
batare da almubazzaranci ba, itace amintacciyar
abokin shawararsa, mai iya riqe masa sirri, bata
yarda wani yasani ko waye kuwa, sannan ga
taimako.
Allah sarki!
Wani mutum yatashi tafiya hajji yana tunanin
abin da zai barwa iyalinsa, sai matar tace karya
damu ga masara can a gidan wane, buhu 12 ta
saya.
Sai yayi mamakin inda ta samo kudin, tace masa,
wanda yake bayarwa ne, in akayi aikin gida kudin
yaragu sai ta 6oye saboda tunanin gaba, yau
kusan shekara 7 kenan ko fiye, da faruwar hakan,
gashi yau sunyi mana rana.
Allah kuwa matan wannan zamani kuna biyayya
ga mazajenku na aure ?
Matsayinka na namiji idan kasami mace irin
wannan wane yanayi zaka tsinci kanka ???
Sai mun hadu a darasi mai zuwa.
Insha Allah. adsense 2 here
Share:

1 comment:

  1. hmm gara aringa tunasarwa dn mata mafiya yawa anshagaltu da dny mungode sosai da tunasar damu dakukeyi dn sanin mhimmanci maxajen mu.

    ReplyDelete

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *