Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Sunday, July 19, 2015

BAYYANA KWALLIYA.

adsense here wpeaceanimated1.gif

img-20150106-105303-1.jpg

ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮﺣﻴﻢ
ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﻭﺳﻠﻢ
'Yar uwata karki karaya, wallahi ke kyakkyawa ce
mai dadin kallo, mai dadin qamshi, mai dadin
murya, mai dadin mu'amalla, komai naki dadine
dashi.
Haka Allah yayi ki, duk daya saka miki rauni qasa
da namiji, amma fa raunin nan naki shine qarfinki.
Domin babu wani da namiji da zai gagare ki, sabo
da Allah yabaki sirrin juya zuciya kamar yadda
yabawa namiji sirrin juya wani da qarfi, don haka
babban taimakon da zaki yiwa kanki shine kiyi
nesa da girman kai, kisan cewa kinada wannan
qarfin koda yaushe.
Son suna da alfahari yana tafiyar da mutuncin
mace.
Shiyasa in tanada sha'ani take binciko qasan
akwati, amma a gida sai daurin qirji, ko tsohon
riga wanda in za a shayar da yaro nono kota
wuyan rigar ana iya finciko shi.
Idan mijin yanason yaga lalle a jikinta to yayi
fatan sha'ani ya taso.
Buqatarta kowa yace tayi kyau alabashi mijin
karya gani, idan ta qarasa wajen sauran matan
tace:
"Su wane da wane sun cika kallo, saisu Qura
maka ido har karasa yadda zakayi tafiya"
Bayan kuwa tagama hado shika-shikan tayarda
hankulan maza, kuma tace ita wallahi ba tallar
kanta take yiba.
Duk macen data kamu da irin wannan matsalar
ba abin da zata iyayi domin mai gidanta, kuma
zuciyarta zatayi nisa qwarai daga tunanin irin
shigar da zata yiwa mutum Daya kacal alhali idan
tafita mutane ne dayawa zasu yaba, mazansu da
matansu.
Ashe mijinta tunda shi Daya ne sai a saka masa
na maneji, ko kwalliyar ma ba dolene yariqa gani
ba.
Mace tagari dukiyarta da iliminta da shekarunta
basa hana tayiwa mijinta hidima, ina sha'awar
matar da wata zatace:
"Mu sayi kaza"
Ita kuma tace
"Maigidana bayaso"
Ba wai tace
"Tabdijan zansha fada kuwa" .
Manufa ba tsoron fadansa take yiba, tsoron ta
sayi abinda ransa bazai soba.
Yakike ganin Khadija (R.A) data auri mai gidanta
(S.A.W) sai abin da yace za ayi!
Yakike ganin biyayyar da tayi masa duk da
kasancewarta mai kudi shi talaka, amma ta
saukar da kanta domin yi masa hidima har ta
amsa kiran Rabbana ?
Yakike ganin saye zuciyar da tayi masa da har
tsufanta zuwa rasuwarta bai da kamarta a
zuciyarsa ?
Ke me zaisa bazaki kwatanta ba ?
Idan aka ajiye maganar daraja agefe guda.
Me Allah yabata a jikinta wande ke bai bakiba ?
Tafiki matsayi, amma ki karanta tarihi kiga
qoqarin da tayi da zuciyarta da jikinta wajen
tabbatar da mijinta a surar data rasu ta barshi.
Yi amfani da duk abin da Allah ya hore miki
wajen biyayya ga mijinki.
Kiduba kigani Allah yayi miki halitta ta ban
sha'awa wace dole a kalla, toki nuna masa,
Yamiki murya mai dadi, toki jiyar dashi, Yabaki
damar yin kwalliya kala daban-daban toki bar
masa shi kadai, karki yarda wasu su riqa haduwa
dashi a kanki.
BAN DA GIRMAN KAI.
Kiyi qoqari ki manta duk sifofin gidanku ko naki
na kanki, kiyi tunanin irin sifar da kikeso mijinki
ya sifantu da ita, da irin matsayin da kike so
yakai.
Allah yabamu ikon yin aiki da abin da muke
karantawa.
Sai mun hadu a darasi mai zuwa.
Insha Allah. adsense 2 here
Share:

1 comment:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *