Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Sunday, July 19, 2015

INA YA KAMATA NA KALLA A JIKIN BUDURWATA

adsense here wpeaceanimated1.gif

INA YA KAMATA NA KALLA A JIKIN
BUDURWATA ?
Tambaya:
Malam koya halatta na kalli gashin macen da
nakeso in aura ???
Ko kuma don Allah malam ka taimaka kaimin
bayanin abunda ya halatta in kalla a jikin macen
dazan aura kafin muyi aure.
Nagode.
Allah ya gafarta maka.
(Daga abba gana)
AMSA.
=====
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.
To dan'uwa ya halatta ka kalli macen da kakeso
ka aura.
Kamar yadda yazo a cikin hadisi, inda Annabi
(s.a.w) yake cewa:
"Idan dayanku yana neman aure, to in yasami
damar kallon abin dazai kira shi zuwa aurenta,
toya aikata hakan"
Abu dawud a hadisi mai lambata: 2082.
Amma malamai sunyi sa6ani akan wurin daya
kamata mutum ya kalla a jikin mace lokacin da
yaje neman aure:
1. Akwai wadanda sukace zai kalli fuska da tafin
hannu ne kawai, saboda tafin hannu yana nuna
ni'imar jikin mace, kamar yadda fuska take nuna
kyau.
Saboda haka sai a takaita akansu, wannan itace
maganar mafi yawan malamai.
2. Nabiyu kuma sukace, zai kalli duk abin yake
bayyana a jikin mace, don haka bayan fuska da
hannu zai iya kallon duga-dugai da wuya.
3. Malamai na uku sun tafi akan cewa:
Zai kalleta a kayan da take sawa a cikin gida, ta
fuskace shi ya kalle ta, sannan ta juya baya ya
kalleta.
Wannan ra'ayin shine yafi dacewa, saboda ta
haka mutum zaisan yanayin matar dazai aura,
yadda ya kamata.
Saidai ba'a son yawaita kallon saboda duk abin
da aka halatta saboda bukata, toya wajaba a
tsaya a gwargwadonta.
Wannan yasa yawaita zuwa zance da yawaita yin
waya, zai iya zama haramun saboda yana iya
tayar da sha'awa, sha'awa kuwa tana iya kaiwa
zuwa barna.
Wal iyazu billa.
Saboda haka matasa ku kula dan kunji ance ya
halatta, kada mutum kuma ya wuce gona da iri a
wajen kallon.
Mai neman Karin bayani, yaduba:
Al'insaf 8\15 da Muhallah 9\161.
Allah shine mafi sani. adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *