Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Tuesday, July 21, 2015

MUTUNTA DANGIN JUNA.

adsense here bana2.jpg

DOMIN KE DA MIJINKI
««fitowa na 4»»
ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮﺣﻴﻢ
ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﻭﺳﻠﻢ
A duk lokacin da na wayi gari naga matata tana
matuqar qaunata tana girmamani, tana yimin
biyayya daidai gwargwadonta, toba shakka bani
da wata abokiyar rayuwa wace ta wuceta, itace
abokiyar shawarata saboda amincinta, itace
asusuna saboda amanarta.
Amma idan na wayi gari naga cewa ni kawai
takeso ba ruwanta da iyayena da 'yan uwana,
haqiqa komai nata zai fado qasa, haka zan dena
ganin girmanta kamar yadda ta dauki iyayena, ba
yadda za ayi na girmama nata, ni ta wulaqanta
nawa, halin namijin qwarai kenan a jiya da yau.
Mace itace wace kullum take fatan ganin farin
cikin maigidanta, daci gabansa, sabo da hakane
'yan uwansa suka sami albarkacinsa.
Mace ta qwarai tana son dangin mijinta yara da
manya, takanyi musu kyakkyawan zato idan
sukayi kuskure, takan taimaka musu daidai
iyawarta, ta girmamasu, ta wadata su da abinci,
da kyaututtuka, tariqa zuwa sha'anoninsu gaba
daya na haihuwa dana mutuwa, ta dage sai taga
maigidanta yana taimaka musu, wannan zaisa su
soshi sosai, itama su saki jiki da ita, har ma idan
suna neman wani abu sai kiga sun biyo ta
hannunta.
Uwarsa kuma baza taji nauyin shiga gidansa ba,
don tasan yana da mata ta qwarai.
'Yan uwansa duk zasu sota.
Da yawa zaka taras mace ta qwarai tana bawa
mijinta shawara yayiwa 'yan uwansa da
mahaifansa alkhairi, ya ziyarce su, ya tambaye su
ko suna son wani abu, ba wace take korar 'yan
uwansa tana kawo nata ba, tahana iyayensa ta
kaiwa nata, taqi girmama iyayensa tace shi kawai
take aure ba iyayensa ba.
Wannan shine sikelin da ake auna mata tagari da
matar banza.
Wannan uwace, ta haifi da da cikinta tasha
wahalar renonsa, ta qaunace shi, ta san komai na
rayuwarsa da tsaraicinsa, wannan qaunar tana
girma kamar yadda shima yakeyi.
Farat Daya sai zuciyarsa ta rabu da ita ta koma
kanki, yadena cin abincinta sai naki.
Ya dena sirri da ita saike, hatta murmushinsa da
ita ba kamar naki ba, yana yaro ne yake kwana
da ita a gado daya, yanzu sai dai ke ki shigar
dashi wani dakin kija qofa ki kulle.
Kenan kin qwace mata komai daga hannunta,
ashe wannan bai isa kiyi mata hanzari ba idan
tana cutar dake.
Idan kuma batayi ki saka mata da wahalhalunta ?
Haba 'yar uwa, Kiduba kigani, kin qwace komai
daga hannunta da mijnta da sauran 'yan uwansa
ya kamata kiyi tunani.
Duk namijin da yaga matarsa tana son iyayensa
da 'yan uwansa yakan saki jiki da ita, kuma
shima zai riqa kyautata wa mahaifanta, ya
girmama su.
Idan kuwa ta wulaqanta iyayensa da 'yan uwansa
tariqe nata, haqiqa ta janyo masa baqin jini daga
'yan uwansa.
Hatta maqwabta da sauran jama'a sun dunga
zaginsa kenan.
To ina soyayyar asalin take ?
Aure ba gidan kasuwanci bane da za a riqa
tunanin riba, aure wajen neman lahira ne ba
duniya ba, wajen neman qaunar abokin rayuwa ne
daci gabansa da daukakansa.
Sai mun hadu a darasi mai zuwa.
Insha Allah. adsense 2 here
Share:

2 comments:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *