Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Tuesday, September 15, 2015

MENENE HUKUNCIN YIN SAMARI GUDA UKU GA BUDURWA ?

adsense here abbagana.jpg

Salam, dan Allah malam ina neman karin bayani
akan maganar danakeji a bakin mafi yawan iyaye
suna cewa yarinya budurwa sai ta samu manema
3 kafin ta zabi guda 1.
Abisa fahimta ta malam ina ganin bai dace mace
ta tsaya jira ba har wai sai tasami samari 3 da
zarar ta samu 1 wanda aka yadda da addininsa
da halayensa kamar yadda musulunci ya tanadar
sai a tsayar da magana akansa.
Amma a wannan lokaci zakaga yarinya budurwa
suna tare da saurayi kimanin shekara 1 sannan
hakan bai hanata kula wasu ba shi zaisa a ransa
ya samu matar aure sun gama fahimtar juna
amma da zarar wani yafito sai kaga iyaye suna
cewa ai dama mace addinin yabata damar
sauraren manema 3 kafin ta tsayar da guda 1 a
ciki basa duba waccan dadewar dana bayan yayi
yana nema.
Awasu lokutan ma har manya sun san da
maganan daga both side koda dai ace ba'a kawo
kudin aure ba ko sa rana amma ni ina ganin still
haka din bai dace ba.
Dan Allah malam yaya abin yakene ???
Nagode ka huta lfy.
(Daga Amina Nana)
AMSA
=====
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.
Eh babu laifi domin mace samari da yawa sunce
suna sonta.
Amma shari'a bata bayar da dama akan ta tsaya
dasu gaba dayan suba.
Ita macen zata iya sanya wani dan uwanta yayi
mata bincike akan wanda hankalinta yafi
kwanciya dashi a cikinsu.
Addini yabayar da za6i akan cewa:
Zaka iya auren Mutun mace ko namiji domin
abubuwa kamar haka:
1. Addini.
2. Kyau.
3. Nasaba.
4. Dukiya.
5. Tarbiya.
Amma daga Qarshe sai akace yafi kyau ku aura
domin addini da tarbiyar, saboda sune kan gaba.
Bai kamataba ga iyaye su amsa maganar wani
mutum a shafe samada shekara guda yana
soyayya da 'yarsu daga baya suce zasu rabasu
batareda wani dalili mai Qarfiba, Hakan
cutarwane.
Idan basu yarda dashi ba meyasa suka amshi
batunsa tun farko ?
Sannan idan akace baza'a auri kowaba sai mai
addini to sukuma sauran mutane yaya za'ayi
dasu ???
Yakamata mudinga yin aiki da lura.
Allah ka aurar ga matasanmu ga ma'aurata
nagari.
WALLAHU A'ALAM. adsense 2 here
Share:

4 comments:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *