Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, September 28, 2015

Mijina yanayin kwai.

adsense here banaio.jpg

MIJINA YANAYIN KWAI.
Ko akwai darasi acikin wannan labarin ???
Wata rana wani mutum ya auri sabuwar
amaryarsa, suna cikin fira sai dadin fira ya
kamashi.
Sai yace da wannan amaryar tasa.
Nagaya miki wani sirri nawa bazaki gayawa
kowaba ?
Sai amarya tace Eh angona.
Sai yace da ita:
Nifa inayin kwai kamar yadda kaza takeyi.
Sai amarya ta gyara zama tace da gaske kake ?
Sai yace Eh amma dan Allah kada ki gayawa
kowa.
Sai tace to.
Wata rana wata qawarta tazo wajenta suna cikin
fira sai tace da ita:
Zan gaya miki wani sirri amma dan Allah kada ki
gayawa kowa.
Sai tace to.
Sai amarya tace mata mijina yanayin kwai.
Sai tace mata ke banason karya sai tace:
Wallahi shine ya gaya mini yace kada na gayawa
kowa.
Sai tace to shikenan kada kisami damuwa.
A karshe dai wannan kawa ta gayawa kawarta
har zance yaje kunnen sarkin garin.
Sai yasa aka kirawo wannan mutumin yace masa:
Wane Labari nakeji acikin gari cewa kanayin kwai
menene gaskiyar wannan maganar ???
Sai kunya takama mutuminnan yarasa abinda
zaice.
Daga can yadago kai yakalli sarki yabashi amsa
da cewa:
Ranka yadade Matata nakeso na jarraba shiyasa
na tsokaneta da haka:
Gaskiya amana tayi karanci a wannan zamani.
Allah kabamu ikon kame bakinmu. adsense 2 here
Share:

3 comments:

  1. Dan Allah akwai yadda zamu iya downloading novels from this blog

    ReplyDelete
  2. Dan Allah a karanta mana sireena 3

    ReplyDelete
  3. @hajia, akwai contact me via whatsapp zan miki explaining

    ReplyDelete

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *