Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, October 7, 2015

KARANTA WANNAN QISSA KUJI MAKIRCIN SHAIDAN.

adsense here green.jpg

KARANTA WANNAN QISSA KUJI MAKIRCIN
SHAIDAN.
Wani mutumi ne yatashi tunda wuri yashirya tsaf!
Ya canza tufafi yayi alwala domin zuwa masallaci
yayi sallar asuba.
Yana kan hanyarsa tazuwa masallaci, kwatsam!
Sai ya
fadi, tufafinsa suka lalace.
Sai yatashi ya kakka6e jikinsa ya koma gida ya
canza kaya, ya sake alwala, ya kuma nufi hanyar
masallaci.
Yana isowa inda yafadi dazu sai yasake faduwa!!
Tufafinsa suka sake lalacewa ya kakka6e ya
koma gida ya canza wasu tufafin, yasake alwala,
ya kuma kama hanya zuwa masallaci.
Koda ya iso inda ya fadi harsau 2 dinnan kawai
sai yaga wani mutum rike da fitila, dasuka gaisa
sai mutumin yace dashi:
"Dazu naga kafadi har sau 2, akan hakane nazo
domin in haska maka".
Suka kama hanyar masallaci su 2, sai da suka
isa, sai wanda yafadi dazu yashiga masallaci,
yakuma kira wanda yake haska
masa yashigo suyi sallah tare; amma yaqi
yashigo,
Yayi~yayi yashigo masallaci amma yaqi !!!
Daga qarshe sai mutumin yace masa:
"Da farko dai ni shedan ne.
(sai mutumin yaji tsoro dajin wannan magana).
Yaci gaba da cewa:
A lokacin daka fito zaka masallaci nine na kayar
dakai akaro na farko.
Sanadiyar faduwar dakayi baka damuba kakoma
kashirya kasake dawowa.
Sai Allah ya gafarta maka zunubanka gaba daya!
Akaro nabiyu nasake kayar dakai.
kakuma yin hakuri kasake dawowa baka yanke
shawarar yin zamanka a gidaba.
Sai Allah kuma ya gafartawa iyalanka
zunubansu!!
Shiyasa naji tsoron idan nasake kayar daka Allah
zai gafartawa mutanen kauyenku zunubansu gaba
daya.
Shiyasa nayi musu hassada da bakin ciki, domin
kada agafarta masu nafito da fitila har
na tabbata ka isa masallaci lafiya batare daka
fadiba, balantana
agafartamasu, ni kuma ina baqin ciki naji
UBANGIJI yayiwa bawansa gafara)"..
Tofa kunji irin Qiyayyar da Shaytan yakeyi mana.
Yaa Allah kasamu a cikin masu Rinjaye akansa. adsense 2 here
Share:

1 comment:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *