Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, October 7, 2015

Qissar wani mahaukaci mai suna BAHLU wanda yarayu a zamanin sarki HARUNA Ar-RASHEED

adsense here sabo.jpg

Qissar wani mahaukaci mai suna BAHLU wanda
yarayu a zamanin sarki HARUNA Ar-RASHEED
(Abu Ja'afar Bnul Mansoor Al-Khaleefatul
Abbasiy).
Wata rana Bahlul yana zaune abisa kabari, saiga
Sarki Harun Rasheed, zai wuce a bisa doki tare
da masu bashi tsaro, sai sarki Harun ya kalli
Bahlul yace masa:
"Yaa kai Bahlul yaa kai wannan mahaukaci wai
yaushe zakayi hankali ???
Sai Bahlul ya sauka daga kan kabarin, yahau can
kan wata doguwar bishiya, sannan yadaga
muryarsa sosai yana cewa:
"Yaa kai Harun yaa kai wannan mahaukaci
yaushe zakayi hankali ???
Tirqashi in banda mahaukacin da anriga an san
cewar mahaukaci ne, wanene a zamanin ya isa
yadubi Sarki Abu Ja'afar yace masa
mahaukaci ???
Sai sarki Haruna ya zaburi dokinsa yakara
kusantar bishiyar da Bahlul yake akai, yadaga
kansa mai dauke da ado na sarauta, ya kalli
Bahlul a sama a zaune yace masa:
"Yanzu nine mahaukaci lo kuma kai da kake
zaunawa a kan kabari ???
"TIRQASHI"
Sai Bahlul yace:
"ina ai ni inada hankali"
Sai Haruna Ar-rasheed yace masa:
"Tayaya kuwa haka zata kasance ???"
Sai Bahlul yanuna yatsansa zuwa ga gine- ginen
benayen fadar Harun Ar-rasheed.
Yasake bashi amsa da cewa:
"saboda ni nasan wadancan masu karewa ne"
Ya cigaba da cewa:
"Wannan kabarin kuwa shine tabbas, shi yasa na
rayashi, kuma nadawo natare a wajensa, kai
kuwa sai ka ruguza naka kabarin kagina benaye a
duniya, shi yasa baka son zuwa inda naka yake,
kariga ka rusa shi!!!"
Bahlul ya karasa maganarsa da cewa:
"To kafadi mini wanene mahaukacin tsakanin ni
da kai?".
Harun yayi kuka har saida gemunsa yajike da
lema, sa'ar nan yace:
"Wallahi kafadi gaskiya".
Sai yace:
"kara mini wani wa'azin yaa Bahlul".
Sai yace masa:
"Littafin Allah Al-Qur'ani ya isheka wa'azi".
Harun yana jin ya fadi haka sai yace:
"To kana da wata bukata in biya maka ita ?"
Sai Bahlul yace:
"kwaraima kuwa, buqatata guda uku ce"
Bahlul: 1. Kakara mini shekaruna na duniya.
Sarki Harun: Wallahi bazan iyaba.
Bahlul: 2. Ka kareni daga mamayar mala'ikan
mutuwa.
Sarki Harun: Wallahi bazan iyaba.
Bahlul: 3. ka sakani a aljannah ka nisanta ni
daga wuta.
Haruna: Wallahi bazan iyaba.
Sai Bahlul yace masa:
"To wallahi kasani kai kanka abin mulkane, kai
bamai mulki bane, don haka kasani bani da wata
bukata a wajenka.
Tofa kunji mahaukaci mai hikima.
Wanne da darasi kuka dauka acikin wannan Qissa
gameda shugabanninmu na yanzu ??? adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *