Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Saturday, November 28, 2015

KAUNA CE SILA***26---30

adsense here kauna-ce-sila.jpg

[5:03PM, 11/25/2015] Bana: KAUNA CE SILA 27





MUHD-ABBA~GANA





a haka na kara kwarewa kuma na samu wayewa da abin haduwa ta da maryam yanzu tayi wahala tunda ni bana zama da ita ma ga makaranta sai dai mukan yi waya lokaci zuwa lokaci samari sun fara takura min da zummar suna sona wasu aiki zanje gurin sai kaji ance bani number ki ina sonki gaskiya ina fada musu cewa bana saurayi ina samun masu fahimta inda zaka ji sunce kila tana da mijin aure ne nakan yi murmushi wasu kuma sai kaga sunyi dariya wasu kuma suyi min kallan banza kawai su kyaleni ni dai abin dana sani ba soyayya naje yi ba a wannan yanayin ne da ake ciki wata rana mun sauko da zainab zamu tafi sai ga wani dan gurin mu mai suna rabiu yace min mamaa kizo in ji wancan sai na kalli inda yake nuna min ban san shi ba ko a fuska nan zainab tace masa meye yace taje mana taji na dan yi shuru kamar baxa ni ba sai kuma naje yace min ina gajiya nace lafiya yace sunana salisu nima dan vocal ne amma kwanan nan na koma kasuwa shi yasa baki sanni ba amma idan naxo ina ganinki bamu taba magana bane amma ni gaskiya ina sonki kawai sai na juya nace ina da miji baice komai ba dana sami zainab nafada mata sai tace rabu da shi dan Alhaji karki kula shi duk maza mayaudara ne{ amma wallhi bandani } nayi dariya nace to wa zai yaudari ai na fada mishi bana soyayya tun daga wannan ranar salisu ya takura rayuwata kuma abaya tashi zuwa sai ya fuskanci mun kusa tafiya gida kawai sai dai naga ya biyo bayanmu yana magiya





MUHD-ABBA~GANA




www.abbagana.pun.bz
[5:11PM, 11/25/2015] Bana: KAUNA CE SILA 28




MUHD-ABBA~GANA




wani lokaci ma a titi muke tarar da shi idan yana surutun shi bana ce masa komai kai rannan dai salisu har da hawaye kawai na tsaya ina kallon shi naji yana cewa wallahi ina sonki kuma dan Allah bazan cutar da ke ba ki bani dama ban san lokacin da bakina ya furta masa cewa nima ina sonka gaskiya yaji dadi dan fuskarshi ta nuna hakan anan ya karbi number ta dan dama yace shi baza zai karba a gurin kowa ba har sai na amince dashi da kaina an kafe mana sakamakon mu na jarabawa da muka yi yayi kyau ba laifi amma duk mu ukun muna da gyara wato reciting inji bature wanda sai mun gyara zamu tafi ajin gaba ni zan gyara maths and physics husna kuwa maths da chemistry in da ita kuma maryam zata gyara maths kawai mum yi recieting cikin sa'a da mun ci kuma har mun gama registration na shiga aji daya ND 1 mun fara lectures kamar darusan da aka yi mana an kara sosai haka lokaci tashi a yanxu muna tashi biyu na rana amma duk da haka ban daina zuwa studio ba soyyarmu da salisu a halina yanzu tayi nisa dan har gidan mu yana zuwa tun ina boyewa umman mu waye shi karshe dai dole na fada mata gaskiya al'amari dan a gaskiya bana so na dinga yi mata karya dan ta yarda dani kuma tafi so na dinga fada mata gaskiya a kan ko meye irin yanda salisu yake kula dani yasa na fada a soyyarsa kusan kullum ka'ida ne sai ya yi min waya sau uku a rana zai kira ni da safe kafin na tafi makaranta haka da rana haka da daddare koda kuwa yazo ya tafi ne yakan zo gidan mu sau uku a sati koh hudu tun da zuciyata ta amince da salisu sai na kara tsare kaina koda a wani gurin ne akace ana sona bana bada fuska.






MUHD-ABBA~GANA




www.abbagana.pun.bz
[8:41PM, 11/25/2015] Bana: KAUNA CE SILA 29





MUHD-ABBA~GANA





wata rana ina shirin tafiya gida da yamma sai fiddausi tace dan Allah na raka ta wani studio a kusa da gidan dan asabe nace mata muje mun shiga an bude kofar da take kallo inda nake ashe editing room ne nan naga mai fitowa wani shahararran mawaki ne da duniyar waka take yayin shi a wannan lokacin ya iya waka dan ko nima ina bala'in son wakokin shi amma ba abinda ya ba taba hadamu muna hada ido sai naji wata muguwar faduwar gaba nace masa ina wuni sai ya tsaya yace lafiya ya garin nace lafiya dama littafi ne a hannuna na hausa sai naga ya karba ya duba sunan sai ya miko min yayi ficewarsa yana fita sai naji wani dadi ya rufeni da fiddausi ta fito muka sauko tare nayi gida ita ma ta tafi bayan kamar kwana biyu da muka tashi daga makaranta sai na wuce kasuwar sabon gari dan ina so na siyo man shafawa da kuma takalmi dana gama siyayyata sai na nufi zoo road ina hanya sai naji ana kirana dana daga sai naji wani yace ina nan laila studio kizo kiyi min amshi sai nace ban gane me magana ba sai yace sunana umar a gurin nake sai nace to gani nan ina zuwa zan shiga sai muka yi kicibis da Ahmad shi kuma zai fito sai na dan kauce ya fara wucewa sai naga ya bude baki da alamun mamaki wanda nake tunani dan ya ganni da kaya ne niki niki a hannuna na gaishe shi ya amsa sai yace min zo nan na dan bishi sai yace min kina da number ta sai nace masa bani da ita sai yace to bani wayarki ina mika mishi ya saka min number ni kuwa nayi saving narubuta masa YAYA AHMAD.




MUHD-ABBA~GANA




www.abbagana.pun.bz
[8:47PM, 11/25/2015] Bana: KAUNA CE SILA 30





MUHD-ABBA~GANA




dana koma gida sai bayan sallar isha'i na kira number ya ahmad ta fara ringing kamar baza a daga ba can naji yayi magana sai nace hello yace ina ji wake magana nace nice mamaa sai yace ih mamaa vocal ko ya gida nace masa lafiya yace number ki kenan bara nayi saving nace to muka yi sallama ya kashe wayar shi ya barni ina kallon waya ta ina ta mamakin kaina wai ya ahmad ya sanni kai amma naji dadi wata rana ina zaune a vocal sai ga kiran ya ahmad bayan mun gaisa yace min dan Allah kzo studio da muka hadu ranar zakiyi wa wani yaro amshi dan unguwar mune yana so neya yi waka nace masa to sannan lokacin da naje gurin ban samu ya ahmad ba amma nayi aikin bayan na gama na fito na tafi tun daga wannan lokacin mutunci mai kyau ya shiga tsakaninmu da ya ahmad ina yawan kiran shi a waya mu gaisa mukan dan taba hira shima yana kirana amma yafi kirana da safe wanda yawanci ina makaranta ina matukar jin dadin mutunci da muke yi da ya ahmad dan gaskiya ina jin shi a cikin raina ina daukar shi kamar uwar mu daya uban mu data a wannan shekaranne aka yi hira da ni a gidajen radio har biyu gaskiya a halin yanzu na zama cikakkiyar mawakiya wadda nake alfahari da kaina salisu ma yana nan yana ta kokarin nuna min kulawa dan mutane da dama sun san mu tare duk da bana bashi fuskar muyi hira a gurin aiki ko da mun hadu sai dai mu gaisa yace in sai ya zo gida na ce masa toh.




MUHD-ABBA~GANA



www.abbagana.pun.bz adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *