Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Thursday, January 28, 2016

BANA KAUNARKA!!! 10

adsense here bana-kaunarkajpg.jpg

BANA KAUNAR KA!!!





10





MUHD-ABBA~GANA


bayan kwana biyu da yin maganar ina zaune dainmu ina karatun wani littafin addu'o'i ya shahid yai sallama na amsa ciki-ciki'domin yanzu haushi yake bani ya zauna kusa dani bai magana ba sai da ya shafe kusan minti goma sannan ya kalle ni 'ba ki iya gaisuwa ba ne ?na dago " sorry na manta ka tafi lafiya? gani nan lafiya ba lafiya ba lafiya nan da sauki wahida ina son muyi wata muhimmiyar magana okey ina jinka wahida kin san ina sonki ko? what nikake so? wahida me yasa kike son wahalar da dan uwanki...? ban gane nufin ka ba kin san mahida ta zabi dan uwana a matsayin abokin rayuwarta ina so kema ki sauke ra,ayin son karatu ki amince min billahillazi nayi alkawarin barin ki ki ci gaba da karatunki nai murmushi shahid kenan na fada maka bani da lokacin soyayya kwata-kwata ba zan iya hada karatu da soyayya ba shikenan zan iya jiranki ko nan da shekara goma ne no ka nemi wata kawai wahida kin san kuwa irin azabar da nake ji? oho kai kaso ka don haka bbu abinda ya demeni domin na fada maka gaskiya wahida nifa dan uwankine wahida me yasa ba kya sona in wani hali nake dashi wanda ba kya so dan girman Allah ki fito ki fada min kaga na farko bbu abin dana tsana irin shan taba kai kuma kana shan taba,maganar gaskiya ina zarginka da abubuwa da dama shahid ko ba haka ba dama ance sojoji suna shaye shaye kuma suna neman mata wa'iyazu billahi yace tare da mikewa ya cillo min kati gashi nan na baki cikakken sati kiyi bincike a kaina bayan taba me take sha tabar ma koki ka sank sha amma insha Allahu daga yau na barta har abada yana gama maganar ya fice jiki babu kwari.tunda wannan lokacin na shiga bincike kan bom boy har har sati biyu amma ban ga wani aibunsa ba in ban da da yake samu gun jama,a da dama sai dai wani abu ko kadan bana jin sonsa sai ma hausinsa da nake kara jiba kamar in na tuna shi soja ne kuma mugu ne na karshe domin bana mantawa ina karama mugun tsoransa nake innai abu aka ce za a fada wa shahid na kanyi kuku domin ban bashi da wasa gashi da girman kai rashin son magana yanzu ne fa da yake sona yake sakar min iska ni na san yana aurata zai daina sakar min fuska koda dama ance matar soja sai hakuri.kamar kullum ina zaune ya shigo da sallama tun kan ya karaso kamshin turaransa ya cika dakin kai gaskiya ina son turaransa haka nan kamshin kan sani farin ciki ko da kuwa ina cikin bacin rai gashin ban san sunan turaran ba bare in siyo gashi ina ganin kamar zubda ajine in tambaye shi sunan turaransa,kamar kar in amsa sallamar sai kuma na tuna girman sallama da darajarta sai na amsa ciki ciki na janyo remote na kunna T.V domin ta taya shi hira na mike domin in bar masa dakin suyi hirar da T.V caraf ya kamo hannuna sai naji hannunsa dumi ga wani irin taushin ji nai kamar in kwace hannun don wani irin sanyi dadi naji yana ratsa zuciyata na daddage na tofa masa yau a hannu ya daga hannun a tunanina mariina zai ko ya goge min yawun a jikina amma sai naga akasin haka domin ganina yasa harshe ya lashe yau din yace baki san yawunki yafi ice cream ba a gurina na yamutsa fuska ashe kai kazami ne??


MUHD-ABBA~GANA

www.abbagana.pun.bz adsense 2 here
Share:

1 comment:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *