Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, February 3, 2016

BANA KAUNARKA!! 12

adsense here bana-kaunarkajpg.jpg

BANA KAUNAR KA!!!







12







MUHD-ABBA~GANA



ya janyo ni ya rungume tsam yana fidda wani irin numfashi nace ka manta na hana ka taba ni? juyo dani yayi ya zubo min mayatattun idanunsa duk na dabarbace da kyar na ture shi nace ashe dama ba sona kake ba sha'awata kake yace what? na hankade shi da gudu yasha gabana wallahi sone ba sha'awa ba ce kauna ce na ce cikin tsawa kai dallacan rufe min baki ya finciko ni tare da doke min baki ya kara yi min wawuyar runguma anyi sha'awar taki ba a kaunarki za'ayi sha'awarki stupid kawai,nace ashe ai ban san kai dan iska bane.....yau ai kin sani nan gaba zaki karasa ni kin gane, yawu na tofa masa nace mara zuciya kawai kamar jira yake ya lashe yawun da sauri na fice.tana fita ya fadi a gurin yana numfashi sama sama me yasa wahida bata sona me nai mata ko dai hakura zan yi da ita kai ba zan iya hakura da ita ba ba zan iya ba ya fada cikin karaji da gudu haidar ya shigo ya rike shi kayi hakuri bom boy ya fincike haidar fada min me nake dashi wanda ban cancanci a soni ba? ka cancanci aso ka bom boy kana da kyau kana da aji kaine yammata ke rubibi a kanka ne zai hana ka hakura da wahidar nan ka nemi wata ba zan iya ba small ina so wahida so bana wasa ba.....tobya zaka yi tunda ita bata sonka kana ganin irin rashin kunyar da take maka kai dana sonka da zuciya kana gani fa har yawu take tofa maka kawai ka share ta no ba zan iya ba small ina sonta zan jure duk wani salon kiyayyar da wahida zata nuna min.
wannan shine takaitaccen labarina amma ku biyo ni don jin ci gaban labarin.mamy ce ta dawo dani daga duniyar tunanin da na shiga tace wahida mun shiga uku me kika yiwa bom boy na tashi zaune wani abu yace miki nai masa a,a yanzu naga dan uwansa ya kamo shi ya fita dashi hannunsa kan kirjinsa ko meke damunsa na tabe baki Allah ya kyauta atu tai sallama tace lafiya na ganki cirko cirko umh wai bom boy ne ba lafiya subahanallahi ba muga ta zana ba meke damunsa mamy ta nuna itace wallahi atu wahida yake so ita kuma take gara shi ta kalleni cikin fada tace kin san Allah muddin jikana ya mutu akan sonki wallahi mun kulla kun san duk cikin jikokina nafi son shahid nace ai sai ki aure shi tunda kin fi sonsa ni dai bana sonsa amma fa a zuciyata a fili kuma nace inma ya mutu shi sayo ni kan ko a kaina da gudu ta wawuro tsintsiya ta bini.



Ranar litinin al,amin ya dawo bayan ya huta sai kiran mahida yace mahida ina wahida? wallahi ai tun ran daka tafi ta bar gidan....saboda me? dan ya furuq yai mata duka shine ta tafi abba yace inje in taho da ita amma tace in munga ta dawo gidannan to dan uwanta ya dawo al,amin ya mike dakin faruq ya shiga ya finciko shi wai kai wanne irin mugune azzalumi me wahida taimaka faruq yaja shaka yace yi hakuri big brother ba zan kuma ba so nake ka fada min abin da tai maka da har ka raba tada gida faruq ya fada masa duk yadda akayi tsaki yayi ya juya ya fita bai zame ko ina ba sai gidan atu ina sharar tsakar gida yai sallama nai ciki datsin tsiyar na rungume shi ya dago ni ya dunguran goshi me ya rabo ki da gida nai raurau yaya in baka nan ab tsaneni kullum cikin duk ni kuma na baro musu gidan yace min fa rashin kunya kike masa ni ba rashin kunya nai masa ba wai dan nace ba zan cewa mahida anti ba to shikenan ki shirya mu tafi ya wuce dakin atu.





MUHD-ABBA~GANA





www.abbagana.pun.bz adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *