Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, February 3, 2016

BANA KAUNARKA!!! 14

adsense here bana-kaunarkajpg.jpg

BANA KAUNAR KA!!!







14







MUHD-ABBA~GANA



zagewa nai na wanke toilet din nasa turare sannan na hada kayan wanki na bayar na cire zanin gadon na sa wani na share na goggoge ko ina nasa wa dakin turaran wuta ina sallah haidar yai sallama ita kuma tana kwalliya bayan na idar na gaishe shi na fice a zuciyata nace da haka zai zo ya samu dakin kamar bola? ina kwance a falo bom boy ya fito daga dakin yaya al'amin ya karaso ya tsugunna gabana wani kallo nai masa tare da nace lafiya dai ko? yace lafiyar ce ta kawo haka please ki taimaka min in taimaka maka da me? so? ya furta nace so menene kuma so? kina son sanin menene so? look at me na mike domin na san ba zan iya abin daya sani ba caraf ya kamo hannuna a fusace na juyo tare da tofa masa yau ina daga idona muuka hada ido daya al,amin gabana yai wani mumunan faduwa shi kenan ta faru ta kare an yiwa me zani daya sata wata irin harara ya wullo min ai da gudu nai dakin mom na fada jikinta mom ki yiwa bom boy magana nace bana sonsa bana kaunarsa! meye zai dinga takura min?,yakike so in yi masa wahida? so kike in tare shi ince kar ya kara kula ki? in kin yi tunani koba komai shahid ai dan uwankine da mahaifiyarsa da ubanki cikin su daya haba auta kiyi hakuri ki sassauta wannan bawan Allah ni wallahi nafi miki sha'awar shahid ko kina da wanda ya fishi,gaskiya mom ku hana shi zuwa gidannan in ba haka ba sai in bar masa gidan in koma katsina mom inaji ana cewa soja akwai zuciya shi kuwa wannan ba shi da zuciya mom tace ai so daban zuciya daban kuma wallahi na amince da son da shahid ke miki na mike na fita don bana son zancan daki na koma dakin bbu kowa da alama sun tafi yi musu rakiya na kwanta sai ka na mike na shiga toilet nai wanka gidansu wata yar class dinmu tun muna primary ina kallo yaya alamin ya shigo fuskarsa bbu walwala yace wahida duk irin rashin kunya da cin mutuncin da ake cewa kina wa bom boy ban taba yadda zaki aikata ba sai yau ashe baki da kunya a gabana kika tofa shahid yau na zumburo baki nace to yaya ai shi ne bashi da gaskiya dan me zai dinga rike min hannu ni kuma na dau alwashin muddin zai taba ni sai na tofa masa yau amma komai ya mike keki kaja tunda kin san yana sonki wahida ya kamata ki sassauta wa shahid ki dinga fada masa kalamai masu kwantar da hankali ko ba kya sonsa bai kamata ki dinga yi masa abin da kike masa ba yaunzu ki taso muje ki bashi hakuri tabdijan gaskiya ba san iya ba ni dai na fada miki kai don Allah yaya kana gani na ci kwalliyata gidansu da yar ajinmu zani yai tsaki ni dai nace ki jira ni in shirya ya fice nai zaune ina mamakin yaya al'amin naga alama so yake inji kunya yanzu ba kunya sai inje in bawa ya shahid hakuri hum'um ai ba zata zabu ba ina nan zaune ya shigo yayi kyau sosai ya rankwafo ta mudubi na kalle shi yaya kana kama fa da bomboy ainun wahida bom boy bai fini kyau ba no haske kawai ya fika amma kamarku har ta baci na dauko hijabina muka shiga dakin mom,





MUHD-ABBA~GANA





www.abbaganw.pun.bz adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *