Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, April 11, 2016

BANA KAUNARKA!!! 46

adsense here

bana-kaunarkajpg.jpg

BANA KAUNAR KA

46

MUHD-ABBA~GANA DA AMRAH

A daren ranar haka na kwana jiki babu qwarie, ko baccin kirki ban samu nayi ba, da zarar bacci ya daukeni sai in tuno da abnda idona ya gane min, dakuma abnda kunne na yajiye min. Tabbas na cuci rayuwata, na yaudari kaina, idan masoya sukaji labarina na tabbatar da zasu shekara dubu suna tsine mun. Washe garie tunda safe na shirya cikin riga da skirt na atamfa mai manyan flowers red, hijab na dauko shima red madaidaici na saka, na jawo flat shoes suma red ina qoqarin sakawa mom ta shigo dakin mu tace "Wahida wai me kike ne da har yanxu baki fito break fast ba?" Nace "mom am ok fa" "Kamarya kin qoshi? Me kika ci tunda safen nan", "Mom banci komai ba, kawai dai bana jin yunwa ne", Karki 6oye mn komai Wahida, nasan dole akwai abnda yasa kika qoshi", Neman wuri tayi ta zauna tukuna tace dani "Wahida! Ya kamata ki fada mn damuwarki, kinga dai ni mamanku ce, baki da wacce tafini idan kuma akwai sai inji", Kai kawai na gyda mata alamar "a'a", Batace komau ba ta fice daga dakin nabita a baya ina fadin "mom na tafi skul", A parlour na samesu da Dad yana braekfast yace "auta har anyi shirin skul din kenan?", "Ehh dad na fito ken...", ban gama maganar ba naji sallamah, na dago kaina ina shirin ansa sallamar, wa zan gani? Bom boy ne tafe bayanshi da wannan mummunar matar rashi mai zubin kilaki, da qyar na iya ansa sallamar, dad fuskarshi da annuri yace "aahhh mutane lagosi sannu sannu, yaushe a garin?", Bom boy yace "wlh dad yau kwanan mu uku kenan", Mom ta 6ata rai tace "au yau har kwananku uku amma sau yau zakazo mana? Munyi fushi a koma", "A'ah mim ayi mana afuwa, wlh mun dawi a gajiye ne, jiya kuma munje gidan Mahida ne daga can muka wuce gidan farouk, daman dan mu kankare laifin mu ne yasa nace mata muyi sammakin zuwa yau, sai dare mu tafi", Dad yace "tou sannunku da hanya, amaryarmu an same mu lafiya?", Cikin kisisina tace "lafiya qalay dad" har qasa ta duwa tace "Gud morning ma'am", "Morning too dear, ya mutanen gida ya baqunta?", "Alhamdulillah mom", Sai a lokacin Bomboy ya kalle ni yace "sister Waheeda ina kwana?" Mom tace "yanzu ke wahida bakiji kunya ba? Ace yayanki shine zai gaishe ki?", Nace "mom banfa ganshi bane", fita nayI ko bankwana ban masu ba, zuciyata cike da qunci da nadama, a raina ina fadin "ashe sama su dad sun san Shahid zayyi aure shine suka qi su fada mun?" Dan guntun tsaki nayi nace "tou kuma ai bai zama dole su fada mn ba, tinda sun san BANA KAUNARSHI, da wanann tunanin naja mota ta na kama hanyar skul.

ABBA GANA

AND

PRINCESS AMRAH

adsense 2 here
Share:

11 comments:

  1. IMAM IBNKATHEER ZULQARNAYNApril 11, 2016 at 8:09 AM

    Super brozs......muje xuwa,muna biye da kai

    ReplyDelete
  2. IMAM IBNKATHEER ZULQARNAYNApril 11, 2016 at 8:13 AM

    Super brozs.........muje xuwa

    ReplyDelete
  3. IMAM IBNKATHEER ZULQARNAYNApril 11, 2016 at 8:13 AM

    Super brozs......muje xuwa,muna biye da kai

    ReplyDelete
  4. gaskiya hoton nan nake so

    ReplyDelete
  5. ayya plss abba a dan kara yawan posting nan in da hali. tnx

    ReplyDelete
  6. hoton gaskiya sai ta whatsapp

    ReplyDelete
  7. insha Allahu za,a kara

    ReplyDelete

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *