Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Saturday, April 16, 2016

BANA KAUNARKA!!! 48

adsense here

bana-kaunarkajpg.jpg

BANA KAUNAR KA

48

MUHD-ABBA~GANA Da Amrah

Ganin banda niyyar fada mata ne yasa tace "Wahida talk mana", A hankali na share hawaye nace "Mahida tabbas idan nace bana son Bomboy nayi qarya, tun dama can da nake ce maku BANA KAUNARSHI wlh qarya nake, kawai dan ina tsantsar son yin karatu ne, ina ga kamar idan na yarda na auri Bomboy zai hana ni karatu na, sai yanxu nake ta faman da na sani, ina zagin kaina, yanzu da nasan banda mafita, saboda ya riga da yayi aurenshi"... Sosai nake kuka dan ba qaramin tausaya mn Mahida tayi ba, ta rasa abnda zata fadi sai runguma ta da tayi tana share min hawaye.

A hankali muke jin qarar taku kamar ana tafiya, ban dai daga kai na kalli masu tafiyan ba, saboda qarar tafiyar tafi karfin ta mutun daya, muryar dad mukaji yace "Assalamu Alaikum", "Wa Alaikumus salam" Mahida ta fada. Tuni na gama kidimewa dan a tunani na dad ya gama jin zancen da mukeyi. Ban gama kidimewa ba sai dana dago kaina naga jerin mutane sun qura mn ido cikin tausayi suna kallo na. Cikin dattako dad ya qaraso ya zauna kusa dani ya rungume ni, tsam nima na rungume shi hawaye na na sauka a jikin shi, yace "Wahida ina so ki sani qaddara ta riga fata, duk abnda kika ga ya faru to daman can Allah ya gama tsara shi. Ni nasan kina son Shahid ko dama, kawai dai rudin zamani ne yake dibarki da kuma son karatu da kikeyi. Zainab da kike gani yarinya ce mai hankali da sanin ya kamata, ina so ki sani zata dauke ki tamkar kanwarki ta jini, bazata taba yin kishi dake ba domin kuwa ni nasan halinta sosai saboda ni na hada aurensu da Shahid".

Zumbur na miqe tsaye cikin rashin fahimtar furucin dad, naji yana maganar Zainab bazata iya kishi dani ba, tunda niba matar Bomboy bace ba dama ya za'ayi tayi kishi dani? Ya akayi dad ya aurawa Ya Shahid mata ba tare da na sani ba?", Ban gama tunani ba naji dad yace "zauna duka zan baki ansar tambayoyinki", Ashe maganar zucin da nakeyi ta fito waje, zama nayi cikin son jin labarin na fuskanci Dad.

"Labari ne mai tsawo Wahida, tun kafin Shahid ya tafi Lagos ranar da yake shirin tafiyar, Small yake fada mn wai Shahid yana shirin tafiya kuma wai bazai dawo ba sai da mata, nayi baqin ciki sosai a lokacin da naje gidan har ya tafi, numbern wayarshi a kashe, sau uku ina neman wayarshi bai kunna ba, ganin haka yasa na rubuta mashi text kamar haka:

Assalamu Alaikum Son, Naji labarin tafiyarka a bakin Small, amma lokacin danazo gida har ka tafi, ina ta kiran numbernka kuma shiru, kuma kace bazaka dawo nan ba sai kayi aure, to ni kuma gaskiya kusan duk ban yarda da matan Lagos ba musamman na bariki, akwai wani abokina dake zaune Lagos da iyalinshi, yana da 'ya'ya duka 'yan mata, zan mashi magana sai ka zabi guda daya a ciki saboda yaranshI suna da tarbiyya, amma bazan mashi magana ba sai ka kirani dan in tabbatar da kaga text dina. BISSALAM.

Bayan kamar sati biyu naga kira da wata sabuwar number, na dauka nayi sallamh najI muryar Shahid, munyi magana sosai kuma ya amince da za6i na, yaje gidan amini na wato baban Zainab, ya za6i zainab saboda tafi duk sauran yaran hankali, ba'a dauki lokaci ba aka daura aure".

ABBA GANA AND

PRINCESS AMRAH

adsense 2 here
Share:

1 comment:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *