Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Friday, May 20, 2016

WAYE SANADI?? 15&16

adsense here waye-sanadi.jpg

[7:58AM, 5/20/2016]
Ábbā-Gãñå WAYE SANADI?

15


MUH'D*ABBA*GANA
09039016969

www.abbagana.pun.bz

tunda muka shiga mota bance kala ba har muka je kabuga safiya kin yi shiru ko kina kewar baba ne kaina ke ciwo ban cika son magana ba,nafi bukatar kwanciya a wannan lokacin,na juyar da kaina.wani tafkeken gate naga mun nufa bayan mun shiga layin runfar shehu gidan horn din da yayine ya dawo dani daga duniyar tunani ina kallon wani yazo ya bude gate din tunda muka shiga nake kallon aljanar duniya sannu da zuwa alhaji yauwa magaji ya aikin.safiya fito mu shiga sai a samo miki maganin ciwon kan,a sanyaye na fito ina binsa a baya har muka shiga gidan babban walo ne muka shiga.daddy sannu da zuwa wata yarinya ta fada tana murmushi,"sannu maryam ina umma? tana daki,daddy ina bakuwarmu "safiyya shigo ki zauna ai daddy tana bayanka aunty sannu da zuwa haka kawai naji ina jin haushin yarinyar dakyar na taushi zuciyata nace yawa na juyo ina kallonsa yana ta faman murmushi ina ummata? safiyyya ki zauna yanzu zata fito nanunan dakinta sanin halina yasa yace ta so muje a cikin falon naga mun shiga wani dan siririn loko sai gamu mun fito wani lafiyayyen falon ya sha kujeru gefen dakuna guda biyu.safiyya ga dakin ki wannan kuma na ummanki da fatan dan gidan nawa ba laifi" na juya na nufi dakin da yace na umma ta ne bbu ko sallama na tusa kai tana zaune a kan sallaya tana gani na ta taso da sauri tana dariya"oyoyo nanata kwana bakwai kamar shekara dubu na ganta wajena ina tunaninki sannu" sai da muka karasa bakin gadonta ta zaunar dani yaushe ya jeya dauko ki? umma kinyi kyau dan haka kika nace sai kin aureshi ashe dadi kika gani,amma ni vaba take min bakin ciki nima nazo na dandali arziki. shigowarsa ce tasa nayi shiru "rukayya na cika alkawari ga safiyyar mu nan na dauko mana tazo gidanmu da fatan zaki zauna da ummanki,please safiyya duk abinda akai miki ki gayan zan dau mataki safiyya na dauke ki a matsayin yata. rukayya baki kawo mata komai ba kuma tace kanta yana ciwo na bawa khalifa key yaje ya karbo mata magani in tasha sai ta kwanta dan ta huta,khalifa da abba sun yi miki sannu da zuwa sun zo ganin ummanki gobe zaki koma bakin karatun nagaya musu kanki ke ciwo gobe zaku hadu gun break bayan fitarsa umma ta juya tana kallona yanzu abinda kike kin kyauta mutumin nan yana yi mana hidima amma baki taba budar bakinki kin masa godiya ba,


Abbagana hausa novels@ facebook.
[8:00AM, 5/20/2016] Ábbā-Gãñå: WAYE SANADI?

16


MUH'D*ABBA*GANA
09039016969

www.abbagana.pun.bz


in yayi miki magana sai ki nuna kamar ba dake yake ba,gaskiya in kina so mu shirya to ki gyara halinki,kai umma har mutumin ya mallake miki zuciya kin daina sona kuma da ki kace yana ta hidima damu to ni nasa shi ko kiransa nayi dan haka bbu abinda ya dame ni da nayi masa godiya"na mike umma zan tafi tunda bakya bukatar gani na,mijinki ya fini.haba nana ina kuma zaki ya riga ya dauko ki kin riga kin dawo nan kawai dan na fada miki gaskiya sai ki tafi ki barni
"umma wannan ba gaskiya kika gayan ba,kawai kin nuna bakya son ganina a gidan nan kuma wallahi in har na bar gidannan ba gaida zani ba sai dai na shiga duniya inda har abada ba zaki kara ganni na ba ina fadar haka na juya zan fita naji umma ta rike hannuna cikin sanyayar murya tace kiyi hakiri nana insha Allahu bazan kara miki fada ba tati ta lallashina har na sauko naci abinci na sha magani umma tace to kije dakinki kwanta kyafi sakewa umma kin san tare muke kwanciya dan haka auranki bazai hanamu kwana tare ba na juya na kwanta.washe gari bayan na idar da sallah na koma na kwanta a hankali umma naji tana bubbuga kafata na bude ido nana ki tashi lokaci yana kurewa kuma tun dazu su abba suke shigowa zaku gaisa.umma sai kace gaisuwar dole ce "haba nana daure ki tashi kin ga zaki makaranta kada lokaci ya kure sai lokacin na tuna da makaranta na tashi na shiga toilet gaskiya rayuwar hutu itace rayuwa Allah kayi mana arziki,abinda na fadi kenan bayan na shiga toilet naga umma tana zaune tana kallona a zuciyarta addu'a take Allah yasa kada na bata kunya.nana in kin shirya kizo muje mu gaisa umma dawa zamu gaisa? nana ai kinsan gidan bamu kadai bane gaskiya umma ba inda zani dole ne sai mun gaisa nifa ban cika sonyin magana,dasu bashi ba na gaya masa bbu ruwana dasu ba" nana yanzu ban isa na saki abu kiyi ba ai ko dan darajata kya je ku gaisa dan Allah kar ki ban kunya ace daga zuwanki har kin fara haka"Allah umma in dai naje yau bazan kara zuwa ba na yarda nana Allah yayi miki albarka taso muje na mike nabi bayanta duk kansu suna falo muka karasa umma kin fito kanwarmu sannu ya bakunta murmushi nayi musu na juya ina kallon maryam aunty an tashi lafiya? lafiya maryam aunty taso muje muyi break a,a,


Abbagana hausa novels@faceebook. adsense 2 here
Share:

8 comments:

  1. inajin sai nadaina karatun littapinga saboda abin yana bani muguntakaici

    ReplyDelete
  2. Wannar ita ake kira goyon kaka

    ReplyDelete
  3. fatima ibrahim ummu faruqMay 20, 2016 at 11:36 PM

    haba ita kuma karta kwafsa mana

    ReplyDelete
  4. Gsky Idan Haka Zata Yi Bata Haduba

    ReplyDelete
  5. Littafin nan akwai abin takaici whl

    ReplyDelete
  6. Sannu jarumin marubuta.
    Keep it up!

    ReplyDelete

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *