Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Thursday, September 8, 2016

TANA TARE DA NI...68---69

adsense here
tana-tare-dani.jpg


TANA TARE DA NI... PAGE 68
BY MIEMIEBEE






     Kasa koda amsashi tayi wani kunya taji ya rufeta, she can’t believe abinda ta aikata sede kuma chan cikin zuciyarta tana miradi da abinda tayi atleast tayi proving masa tana sonsa bare sake kokwanton san da take masa ba. Hannunsa ta sauk’e daga hab’arta tare da juyawa kafin ta soma tafiya yasa hannu a kunkuminta ya juyo da ita tare da matse jikinta a nasa. “Flower look at me” har a yanzu tak’i d’ago kai su had’a ido. “Flower baraki kalleni ba?” Kai ta kad’a masa. “Then look at me” kai ta sake kad’a masa kunya bare barta ta kallesa ba.
     “You love me right?” Ya tambayeta. Kai ta gyad’a masa. “I want to hear it again Flower.” Hannunta ta zagaye a bayansa tayi hugging nasa “I love you Anas, I love you so very much My Lion” shima a hankali ya zagaye hannayensa a bayanta pulling her closer to him. Gashinta yayi kissing “I love you so much more Flower.” sosai yaji dad’in sunan data kirasa dashi •°LION°• it means everything to him.

       Sun d’au tsawon lokaci suna atsaye sannan a hankali ya raba jikinsa da nata tare da jawo hannunta suka zauna kan kujera. Hannyensu ya had’a duka waje d’aya cikin sanyin murya a hankali yace, “Flower fad’amin mesa kikayi shunning d’ina jiya? Nasan kina da qwararren dalili koh?” Kai ta gyad’a “then tell me kinji? Karki b’oye min tell your husband” Innocent eyes nata data k’ayatasu da kajol ta d’ago a hankali ta azasu akansa.
      “I’m afraid Anas tsoro nakeji” ta sanar dashi cikin cracky voice.
     “Tsoron meh Flower? Kin d’au zan miki wani abu neh?” nan ma kai ta gyad’a. “Don’t be kinji? Ba abinda zan miki seda yardan ki I will never do anything to you ki saki jikinki dani kinji?”
        Batasan lokacinda hawaye yasoma ciko mata a ido ba cikin sautin kuka tace, “for how long Anas? For how zaka ta zama haka? For how long zanta toye maka hak’k’in ka?”
     
     “For as how long it takes Fannah ni ban damu ba I love you so kema kibar damuwa kinji?” Kai ta kad’a “Anas dole in damu saboda na miji ne kai dole wataran sha’awah ze taso maka and saboda bakason kayi forcing d’ina seka hak’ura ka tauye wa kanka hak’k’i saboda matarka batason baka hak’k’inka? In hakan ya faru kasan me mala’ikum Rahma zasu min? Anas tsine min zasuyi, zasu tsine min...” ta fashe da wani irin matsanancin kuka. Duk tabi tasa Anas rikicewa a rayuwa ba abinda ke tada masa hankali kamar kukan flowersa. Matso ta yayi ajikinsa yana bubbuga bayanta “Flower kibar kukan nan please I can’t take it please kibari kidena.” Pecking gashinta yayi “stop crying kinji? Ba tsinuwan da za’a miki in shaa Allah ni nayi deciding I won’t touch you se in rananda kika yarda so kibar kukan kinji?” Kai ta gyad’a masa a hankali tasoma shanye kukan nata.

     Seda ya tabbata tayi shiru ya d’ago ta daga jikinsa yana kallonta “Flower but what are you so afraid of? Mesa kike tsoro haka? Saboda kin ganni kind of large?” Ya tambaya tare da d’age gira. Murmushi kad’an ta saki tana kad’a kai danko yabata dariya shi ya d’au wai tsoronsa take amman ko kad’an. “Tsoro na kikeji flower?” Kai ta girgiza masa “mesa zanji tsoron ka Cherie Pie?”
     “I don’t know kodan kinga inada builded body kinga muscles all over my hand kike tsoro I might destroy you on bed kekuma gaki ‘yar k’arama” Dariya sosai ta tsaya tanayi harda rik’e cikinta. “Anas I’m not small kadena cemin small.”
      “Yes you are Baby and thats why kike tsoro.”
      “Ko kad’an ba haka bane Doodle bug matsalar ba daga gareka bane...” Sekuma tayi shiru take mood nata ya canza.
    Hannunta ya rik’o “ba daga ni ba Flower? Bani kike tsoro ba?” Kai ta gyad’a masa “toh daga waye ne Flower?” Take idanunta suka ciko da hawaye “Anas daga ni ne, matsalar daga ni ne...” Sekuma ta fashe da kuka. Hankalin Anas in yayi dubu be tashi ba kamar ya daga ita? Me take nufi? Mesa take kuka haka? Is she lacking something as a woman? Subhanallah!

     Kwanto da ita yayi a kan k’irjinsa yana fad’a mata dad’ad’d’un kalamu masu kwantar da hankali. Duk yabi ya k’osa yaji dalilin dayasa take tsoron had’a kwanciya dashi. Seda ya tabbata tayi shiru ya d’ago ta tare da rik’o fuskarta da hannayensa bibbiyu.
      “You don’t have to be afraid anymore, Flower ko a yaya kike I love you koda you are lacking something as a woman I still love you ahakan ina sonki nake tsakani da Allah badan wani abinda kike dashi ba.” Idanunta taji suna sake cikowa da hawaye “Anas koda... Koda...” sekuma ta sake fashewa da kuka. Haka ya sake rungumota seda tayi kukan me isarta sannan ta taso da kanta, hannunsa ta rik’e cikin nata tana kallon cikin idanunsa da kumburarrun idanunta da sukayi ja “Anas I’m insecure of your love gani nake kamar I’ll lose you, gani nake kamar in na fad’a maka sirrina zaka gujeni ka nisanta daga gareni ka kuma tsane ni, abinda baran iya jurewa ba kenan, I don’t want to lose you My Lion.”

      “Flower I will never hate you kibar fad’an haka, I will never leave your side koda kuwa wannan sirrin kin is as worse as kisan kai God forbid I will never leave you Fannah. I love you for the sake of Allah and nothing more ki d’au wannan sirrinkin k’addara ne a rayuwar aurenmu kinji? And stop saying zakiyi losing d’ina kinji na rantse I will never leave you, never.” D’an sanyi taji a ranta duk da cewa kuwa bata gamsu ba acewarta Anas na fad’in hakan ne dan besan ba cikakkiyar budurwa ce ita ba.
      “So can you tell me? Zaki iya fad’amin dalilin dayasa kike tsoron wani abu ya shiga tsakani na dake? trust me koda mene barin tab’a barinki ba Flower _INA TARE DA KE”_ kai ta gyad’a masa tsili-tsilin hawaye na gangarowa kan kumatunta wanda yasa hannu ya share. “Anas kayi hak’uri dan Allah kasani bawai nayi hakan bane dan cin amanarka, I just can’t bring myself to tell you I’m.. I’m not complete as your woman I’m lacking something. Anas banida... Banida...” sekuma kuka yafi k’arfinta.
     
     Zuciyarsa yaji ya buga tsoro shi kansa ya somaji. “Shhhh is okay” yayi hugging nata “ya isa you can’t talk right now ya isa kinji? Mubar maganan” sosai hankalinsa ya tashi shima yarasa meke masa dad’i me Fannarsa ta rasa? Mesa da zaran ta tuna abin take kuka? Ko kad’an be kawo a ransa wai ko nufi take batada budurci ba saboda yasan hankalinta ya yaba da tarbiyyan ta yasani barata tab’a siyar da budurcinta ma kowani k’ato ba. Seda ya tabbata tayi shiru yace da ita “tashi muje d’aki ki kwanta kinji?”
     “Anas I’m sorry trust me I really want to tell you, wallahi inason sanar dakai I can’t-” katse ta yayi “I trust you My Flower shikenan don’t bother kinji? Mubar maganan I trust you ko baki fad’a min yau ba you will some other day ko ba haka ba?” Kai ta gyad’a. “Shikenan tashi muje d’aki.” Tana manne ajikinsa suka k’arisa d’aki ya kwantar da ita ajikinsa har a yanzu nishinta be dawo normal ba yana bubbuga bayanta har tasamu tayi bacci.
     “Flower” yakira sunanta. Jin shiru yad’an lek’a fuskarta yaga tayi bacci. Hannunsu ya had’a “Fannah I love you kinji? Banga abinda zesa in barki ba no matter what *INA TARE DA KE* forever” ahaka shima yasamu ya kwanta da tunanin Fannah a ransa.

   *****
        Seda Maghrib Fannah ta tashi a hankali ta raba jikinta da nasa ta fad’a toilet bayan tagama duk abinda zatayi tafito tayi kan Anas cikin wani irin romantic salo ta tayar dashi daga bacci yayi alwala shima yajasu Sallah. Bayan sun idar suka ci dinner, kallo kad’an suka tab’a suna hira suna tambayan junansu questions about likes and dislikes nasu dakuma age da sauran abubuwa da dama. Sosai shekarun Anas ya bata mamaki ashede mijin nata yaro ne ko 25 be cika ba gashi kuma ajebo abubuwa dayawa bayya chi. Haka suka tayi har zuwa 10:00PM sannan suka koma d’aki shi da kansa yaciro mata rigar baccin dayakeso tasa.
      “Babe wannan?” ta tambaya tana zaro idanu waje “Ai wannan ba marabansa da babu jibi fah.” ta d’aga shimen sama.
     “Flower shi nakeso.” Wani daban taciro “zansa wannan.”
    “A’a flowor ni wancan nakeso” zata sake magana yace, “zanyi fushi in baki sa ba” da sauri ta katse sa, “a’a karkayi zansa.” murmushi ya saki yana binta da kallo ta shige d’akinta ta koma tasa tare da k’are wa kanta kallo jikin mirror. Kai ta kad’a no gaskia yayi tsireci dayawa wata zuciyar ce tace mata toh ai mijin ki ne bawani gardi ba. Sam ta kasa fita da kayan hijabi ta b’urma akai tana kai k’ofan d’akinsa ta tsaya daga bakin k’ofar a nitse ta bud’e k’ofan kad’an nan ya maido da kallonsa wajen. “Come in Baby” ya buk’ace ta. Ido ta rufe ta cire hijabin da k’yar ta iya shiga cikin d’akin kanta a k’asa se murza hannayenta take duk kunya yabi ya cinyeta kallonta ya tsaya yi wane yau ya soma sata a ido ji yake kamar ya had’iyeta ko kyafta ido ya kasa why is she so damn beautiful? Abinda yake ta nanatawa a ransa kenan. Da kallon ya isheta seta fara k’ok’arin miyar da hijabin nata kamar a kyaftawan ido ya k’ariso gabanta tare da k’wace hijabin.

      “Anas kabani please.” Murmushi ya saki me k’ara masa kyau. “Flower you are damn beautiful” hannu yasa ya zagaye a kunkuminta ya matso da ita kusa dashi. “Kiss me” ya buk’ace ta. Yi tayi kamar bata jisa ba. “Flower I said kiss me.” Kai ta d’ago ta k’are masa kallo sannan tayi d’agel ta yi pecking nasa a kumatu. “There bani hijabi na toh.”
      “Are you kidding me? Kiss me like you did d’azu.”
     “Barin iya ba” ta fad’a stubbornly.
    “Nima barin bada hijabin ba.”
    “Anas please kabani.”
    “Kiss me first.”
    “Okay naji sakeni toh.” Kafad’a ya buga mata. “Ka sakeni toh I will kiss you.”
    “Are you sure?”
   “Yes My Lion.” Ba musu ya saketa hannunta ta zagaye a wuyansa sannan ta k’are wa light red lips nasa kallo seda ta tabbata ya shagalta yana jiran tayi kissing nasa tasa hannu ta fisge hijabin ta ta haye kan gado a 360 tana mai dariya. Murmushi ya saki ya juyo yana kallonta se faman dariya take masa. “Kin min wayo koh?” Abinda yace da ita kenan. Dawowa yayi ya haye gadon shima tare da k’wace hijabin hannun nata jawota yayi ya haye kanta se faman chakulkuli yake mata itako se dariya take harda hawaye tana basa hak’uri ya dena sam yak’i chan zuwa shad’aya suka kwanta a gajiye dan wasan da suka tayi sukayi bacci.

    7:42AM
        Yanzu su Fannah suke gama breakfast. Yau breakfast d’inma a plate d’aya suka yi har suka gama tana zaune a kan cinyarsa, tabashi ya bata ahaka har suka gama karyawan. Tayasa tayi ya gama shiri sannan ta rakosa har bakin k’ofa ta miqa masa lunch pack nasa.
     “My Handsome” ta kirasa.
    “Yes Flower.” murmushi ta saki masa;
    “Yau in ka dawo I’ll reveal my secret for you. Kai mijina ne be kamata ace ina b’oye maka wani sirri na ba zan fad’a maka komai”
    “Are you sure Babe?” ya tambayeta.
   “Yes I am, na yarda da kai dakace baraka barni ba koda kaji wannan sirrin nawa so zan fad’a maka My Husband Baby.”
    Taku d’aya ya k’ara ya rufe gab dake tsakaninsu. “I will never leave you Flower I love you” yayi pecking nata a goshi. “I love you too My Lion take care of yourself for me kaji?”
     “I will Baby.”
    “Me kakeso in dafa maka yau?” Ta tambayesa tana gyara masa necktie nasa daya d’an gauce.
    “Anything yummy” ya kashe mata ido.
    “Okay toh I will cook your favorite”
     “Kina nufin pounded yam da Eghusi soup?”
    “Yes Baby off you go I love you.” Kai ya girgiza mata cike da rashin fahimta ta tambayesa “why?”
    “You don’t love me” yace da ita.
    “Ofcourse I do My King I love you kadena fad’in haka zuciya na bare iya d’aukawa ba.” Hannu yasa ya taro fuskarta.
     “Flower bakiya sona, in har kina sona be kamata ace zan fita office baraki bani ko d’an goodluck kiss ba.”
    Murmushi kad’an ta saki “dalilin dayasa kace bana sonka kenan Baby?” Kai ya gyad’a. ‘Yar murmushi ta saki “wannan bare kawo fad’a ba My Lion.” D’agel d’in k’afa tayi tare da zagaye hannayenta biyu a wuyansa sannan tayi kissing nasa passionately ba kamar jiya da tanayi zuciyarta na bugawa ba, kissing nasa take fiye da yadda tayi jiya duk sun zurfafa cikin abinda sukeyi daga bisani tayi pulling out. Kallon idanun juna suke suna murmushi peck ta manna masa a duka kumatunsa one-by-one sannan tip na hancinsa tayi tayi ta masa a goshi amman takasa dukda d’agel d’in k’afa da tayi. Daya gano haka seya sa hannu ya d’aga ta sama nan ta manna masa peck a goshin sannan ya sauk’e ta.

     “Here are goodluck kisses seka dawo koh? I love you.” Hugging nata yayi “I love you too Flower” daga nan sukayi ba-bye wa juna ya fice. Kan kujera ta fad’a se blushing take tana fad’in “love is the sweetest thing” a ranta “His lips are sweeter than everything and his eyes? OMG!” throw pillow taja ta rufe fuskarta dashi. Shima Anas yana tuk’i amman hankalinsa na akan irin kiss da sukayi sharing da Fannah, “your lips are probably the most sweetest thing I’ve ever tasted Fannah.”

   _3:25PM_
      Fannah tagama duk wani aikin da zatayi, abinci na nan ready ajiye kan dining wanka ta sakeyi tasa wata black lace me torches na pink wanda ya bala’in tafiya da surar jikinta. D’aurin network ta kashe me kyau ta tsara kwalya sannan ta feffeshe jikinta da turare masu k’amshin bala’i. D’akinsa ta shiga ta bud’e wardrobe nasa haka kawai taji bari ta gyara masa dukda kuwa a gyare yake neman abinyi kawai take.
      Drawer’n under wears nasa ta bud’e ta zazzagosu acikin haka diary nasa data soma karantawa da jimawa ya fad’o. A nitse ta d’aga ta miyar ta soma ninke masa boxers da shorts nasa kap ta gama se fad’a mata zuciyarta ke ta bud’e diary’n ta karanta ai matarsa ce ita abinda zata sanar dashi sirrinta itama yau toh se meh dan ta karanta nasa? Hannu tasa wane ana ganinta ta zaro diary’n kwad’o tagani datse a jiki nan tashiga neman key’n cikin inda yake adana cufflinks nasa tasamu ta bud’e. Flipping first 3 pages d’in tayi saboda ta tab’a karantawa. A page 4 d’in taga heading an rubuta da manyan bak’i
 
    THE UNFORGETABLE INCIDENT (THE GIRL)
     Wani irin kishi taji ya gulleta wani girl yake nufi? Dama Anas nada wata bayan ita? So she is not his first love as yadda ya fad’a mata jiya? Bata hankara ba taji hawaye na cikowa a idanunta (Toh fa Fannah uwar kishi) tsuka taja tare da juya pegin ita a dole kishi barata karanta ba. Kujera tanema ta zauna ta soma karanta rayuwarsa na London tana murmusawa tana jin wani sabon sonsa me d’anko yana sake k’aruwa a birnin zuciyarta da zaran taga wajen daya rubuta yasha barasa sekuma ta had’e fuska.
      Dogon tsuka taja sanadiyar ganin mafarke-mafarken yarinyar datake da tabbacin itace wanda yake nufi a page 4 na littafin. Wato ma itace yarinyan dayake mafarkinta time to time yana ce min *_TANA TARE DA SHI?_* Koh”
       “Wallahi Allah kawo ka Anas gaskiya barin yarda ba, waima wace wannan yarinyan?” Duk wannan magana da take a fili take yinsu. Page 4 d’in ta koma ta bud’e tasoma karantawa kamar haka...;


     *© MIEMIEBEE*

TANA TARE DA NI... PAGE 69
BY MIEMIEBEE






Saturday evening Bama, Maiduguri Borno.
 
     Dakata karatun tayi mamaki shimfid’e karara a fuskarta “dama Anas yayi zaman Bama? Wow! Tsaya tukuna ko achan na tab’a ganinsa? Yes definately shiyasa rananda muka sake had’uwa dashi anan Maiduguri naji natab’a ganinsa somewhere ashe a Bama ne. Wow!” Murmushi ta saki ta cigaba da karantawa.
     
    _It pains me writing this, I can’t forgive myself for what I did to this 15 years old girl. I’m so so sorry, I was drunk I didn’t know what I was doing. I blamed everything on her nayi blaming nata akan laifin da ba ita ta aikata ba I’m so sorry I hope we meet in the future saboda in nemi gafararki. Tun rananda abun ya faru na rasa sukuni a rayuwa, I’ve been living a life of guilt. Kullum cikin mafarkin ta nake I don’t know ko tana raye ko ta mutu saboda sautin kukan ta da suke min yawo akai har a yau. Bansan wani erin k’uncin rayuwa na tusa ta ciki ba, believe me wallahi I had no intention of doing so to your precious life. I was densed, stupid and young lokacin my past kept on hunting me sanadin abinda Ummimi tamin my own MOTHER._
     _Da yammacin ranar Asabar, 23rd March 2012_

       Dakata karatun tayi “Innalillahi wa inna ilaihi raj’un!” ta furta cike da rashin yarda tana kad’a kai take idanunta suka cike da hawaye rawa jikinta  ke sosai yana bata wai itace wannan yarinyan da Anas yake nufi itace wacce _TAKE TARE DA SHI_ a kullum “Ya Allah karka tabbatar min da abinda nake zato 23rd March shine ranar da aka k’wace min budurcina aka rabani da martabana na k’arfi da yaji.” Hawayenta ne ya d’iga kan page d’in a yayinda tayi k’arfin hali ta cigaba da karantawa.
 
       _I wrecked a 15 years old girl, nayi raping ‘yar yarinyar da bansan wace ita ba, bansan ya take ba bansan kotana raye kota mutu ba yanzu. Her words are forever stocked in my head._
   
   _“Dan girman Allah bawan Allah kayi hak’uri I beg of you please. Bawan Allah dan Allah kayi hak’uri I'm just 15 ba abinda zan iya baka have mercy on me please dan Allah.”_
       
        Rufe littafin tayi cike da tashin hankali a yayinda hawaye ke ambaliya a fuskarta kanta yana wani irin juyi ga kuma wani jirin da ta soma ji yana neman d’ibanta tabbas bara tab’a mancewa da wad’annan kalamu ba. Kalamun data ta nanata wa mutumin dayayi raping nata haka tata rok’ansa amman haka ba imani ba tsorom Allah ya danne ta yayi raping nata. Kasa rik’eta k’afafunta sukayi ta sauk’a k’asa se “Innalillahi wa inna ilaihi raj’un” take ta nanatawa. Wani irin k’ara ta saki “Wayyo Allah! Anas... Anas ne mutumin, I married the man who raped me, I fell in love with the man who raped me, mutumin danata had’asa da Allah karya k’wace min budurcina amman yak’i koda tausaya min haka ya danne ni ya amshe min martaba. I married the man who made my life miserable, mutumin daya juya min rayuwa ya raba dani da first love d’ina AHAMD bawan Allan da yasoni tsakani da Allah, na auri mutumin da yayi sandanin rashin lafiyan mahaifina, mutumin daya jefa min rayuwa cikin k’unci da bak’in cikin rayuwa, mutumin daya sani cikin tsoro kowani dare sena tashi ina kuka ina mafarki ze dawo ya sake azabar dani kamar yadda yayi a baya. Innalillahi wa inna-” bata k’are salatin ba wani erin masifaffen kuka cike da azaba ya rufe ta, ihu take sosai wasu irin zafaffun hawaye suna ambaliya a fuskarta se juyi take kan rug d’in (k’aramin carpet) ji take kamar ranta ze fita, wannan wace erin rayuwa ce?
   
      “No this can’t be Ya Allah kasa mafarki ne wayyooo!! this can’t be happening mesa ban tab’a gane shine wanda yayi raping d’ina ba? Am I that stupid da har na fad’a soyayya da mugun mutumin daya cuceni har abada? Taya tun rananda naga wancan babban ciwon dake hannunsa na kasa gane a ina na tab’a gani? Taya nakasa recognising blue eyes nasa Why am I stupid?” Kai take kad’awa a yayinda kukan ta ya tsananta har wani sama sama nishinta yake tafi minti talatin tana kuka kamar wacce ta zare, idanunta sunfi jan kala shiga rabuwanta da tashin hankali irin wannan tun lokacin da abin ya faru. A sannu a sannu ta rarrafa wajen drawer’n ta miyar masa da littafin ciki har ayanzu kuka take ba makawa da k’yar ta ja kanta d’akinta tasa key ta rufe sannan ta baje kan gado, d’aurin kan nata ta sinche tasake k’urma wani irin balad’ad’d’en ihu tana jan bedsheet na kan gadon tana duk’unk’unewa a hannunta. “Anas mesa zaka min haka? Mena maka? Mesa seni? I thought I could trust you Anas why does it have to be this way? Wayyo Allah wayyo kaina.” ta rik’o kanta dan wani erin ciwon fitan hankalin da yake mata. “I married a monster. Ya Allah tanan ka kamani akan qaryan danayi ma iyaye na nasasu suka amince auren soyayya mukayi da Anas? Ya Allah na tuba kayafemin badan hali na. This is a dream ba reality bane it can’t be it just can’t be.”
 
      Kuka Fannah ke kamar zata cire ranta har cewa take a ranta ina ma Allah ya d’auki ranta kawai ta huta dukda tasan yin hakan haramun ne, amma kuma da living irin wannan rayuwa gara mutuwa, bayi ma Allah shisshigi ba amman mesa rayuwarta take haka? Daidai lokacin data sama wa zuciyarta sukuni ta fara son Anas hakan ze faru why? Why? Kuka ta cigaba da yi ciwo kanta yake mata kamar ze tsage amman still tak’i barin kukan tun hawaye na zuba har hawayen nata ma yayi seizing, shima muryan nata ya d’auke dan irin ihun data riga yi amma haka tacigaba da kukan ba sauti saboda rashin tausayawa kanta. Wannan wace erin jarabawa ce? Ka auri mutumin da yayi raping naka ba nan kad’ai ba har ka soma son meshi. Wace erin k’addara ce haka?

        “Zama na a gidan nan ya k’are barin iya cigaba da rayuwa da mutumin daya rabani da farin cikin rayuwa naba, barin iya cigaba da rayuwa da kai ba Anas.” Murmushin takaici ta saki “mesa ma nake son sanar dakai sirrina bayan kafi kowa sani? Bayan kafini ni karan kaina sanin wannan sirrin, nayi sakaci da sallolin dare da addu’o’i na shiyaza har na aureka ban gane kaba. Anas abinda kamin is UNFORGIVABLE ka dawo ka sallameni kawai inkuma barakayi ba in tattara kayakina inbar maka gidanka I can’t continue living you with Allah kad’ai yasan abinda zaka iya min nan gaba.”

   
4:21PM
   
    Daidai nan Anas yake dawowa daga office cikin jin dad’i ya miyar da k’ofar ya rufe, he can’t wait ya sa Flowersa a ido. Flasks yaga suna masa sallama kan dining table wanda kobe bud’e ba yasan favorite nasa ne ciki ba abinda yakeyi aransa banda sawa Fannah albarka besan ya rayuwarsa zata kasance ba Flowersa ba. Kitchen yauma yasoma lek’awa beganta ba daga chan yayi d’akinsa. Murmushi ya saki danko yanada tabbacin a d’akinta take. Bayan ya rage kayan jikinsa ya nufa d’akinta sede tun daga nesa yakeji kamar sautin kukan mutum... Kukan mace... Kukan Fannah OMG! “Flower” a rikice ya kira sunanta ya k’arisa k’ofar d’akin ya gwada bud’ewa suprisingly yaga a rufe da lock. Tana jin k’ara ta miyar da kallonta kan k’ofan.

      “Fannah! Fannah! Open up please mesa kike kuka? Dan Allah stop it kitaso ki bud’e min k’ofan please.” Kukan nata ne ya tsananta daga jin muryarsa. “OMG! Fannah whats wrong? Why are you crying dan Allah ki bud’e” yayi stating cike da tashin hankali bare iya jure kukan flowersa ba meya sameta? Meyasa take irin wannan matsanancin kukan? Bubbuga k’ofan yake da k’arfin da Allah yabasa amman yakasa b’alla gun lock d’in dake security door ne.

        Tana tsugune a k’asa se kuka take sha kamar ba gobe.
     “Dang it!” Ya buga k’ofar a fusace se a yanzu ya tuna da akoi spare key a 360 ya wuce d’akinsa yaje ya binciko ya ciro da sauri ya dawo yasa ya bud’e k’ofar. Da gudu ya nufi k’asa inda ya ganta ko d’ago kai ta kalle sa batai ba tsugunawan yayi shima a gabanta cike da tashin hankali da tsantsan tausayi. “Flower” ya kira sunanta cikin sanyin murya cike da tausayi. “Flower dan Allah kibar kukan nan please ya isa dan Allah” ya sanar da ita muryarsa har shaking yake dan tausayi. Ko d’ago kai ta kallesa batai ba se kuka take ba makawa hannu yasa ya dafe kafad’arta hannunsa na tab’a ta ta d’ago kai a firgice ta matsa baya sekace taga aljani. Beso sake ganin fuskarta ba dan yadda ya kumbura gakuma wani irin mahaukacin jan da idanunta sukayi besan seda idanwansa shima suka cike da hawaye ba.
 
     “Fannah why are you crying like this? Meya sameki?” Hannunta ya gwada rik’ewa a firgice taja baya tana matsawa baya daga garesa ganin haka yace, “Fannah Anas ne ba mutumin ba, kinji?” gabad’aya yagama zato ko mafarkin mutumin data sabayi ne tayi take irin wannan wahalallen kukan. Kai kawai take girgiza masa. “Its me Anas your husband bawani ba come kinji?” kai ta kad’a masa  ike da tsoro daga gawani irin kallon da take masa. A guje ta ruga bayi tasa key ta rufe a gujen shima yabi bayanta cike da tashin hankali. “Fannah meya faru dan Allah?” Jikinsa ne ya soma basa ba mafarki tayi ba to mene neh? Ko rasuwa akayi mata? Amman ai in rasuwa ne da shima za’a kirasa a sanar dashi.

      “Fannah I beg of you dan Allah kibud’e please.” Sautin kukanta ta tsananta tana tsugune k’asan bayin se kuka take kamar zata cire ranta. K’ofar yake ta bugawa ba yadda beyi ba dan b’allawa amman ya kasa besan lokacin da hawaye tsili-tsili suka soma gangaro masa kan kumatu ba. Da kukan Fannah ya gommaci yarasa duk wani abinda ya mallaka a duniya.
      Daga k’arshe ma kasa rik’esa k’afafunsa sukayi sauk’a yayi har k’asa hannun sa dafe jikin k’ofar “Fannah koda baraki bud’e k’ofan ba please kibar kukan dan Allah kibari I can’t take it please I beg you.”
     Har ayanzu batajin zata iya dena kukan ba. “Fannah dan Allah fa nace kibar kukan please ya isa haka nasan kinada qwararran dalilin dayasa kike haka becuase I trust you Fannah and I love you please come out kinji? Barin bar nan ba sena gankin Flower” ba irin rok’ar duniyan da be mata ba amman sam tak’i bud’e k’ofar. Ga wani irin masifaffen yunwan dake cinta rabuwanta da abinci tun breakfast gara shi Anas d’in yachi lunch a office. Har Maghrib suna nan ahaka ganin lokacin Sallah ya shiga yayi k’arfin hali yace, “Fannah kifito kiyi Sallah kinji? Nasan koda zan had’a sama da k’asa bara ki bari in ja muba so kifito kiyi naki nima zanje inyi nawa, I love you.” Yana kaiwa nan ya fice seda ta jiyo k’aran rufe k’ofa sannan ta dage ta yi alwala har wani dashi dashi take gani dan ciwon kai dakuma tsantsan yunwa. Cike da tsoro ta bud’o k’ofan bayin kad’an ganin baya cikin d’akin ta d’an taka da wuri ta zaro spare key ta bayan k’ofar ta sake locking abinta yadda bare iya shigowa ba again.

       Yin Sallan kawai take badan tasan me take karantowa ciki ba dan tashin hankali ko raka’a uku tayi ko had’u tayi bata sani ba se Allah shima Anas ta b’angaren sa haka ne. Yana sallamewa ya d’ibi hanyansa back to d’akinta nanma yaga ta kuma rufewa gashi ta zare spare key d’in. Kai gaskia ba lafiya ba what is wrong with Fannah? why is she acting thsi way? Ko an mata wani abu ne? The real question is ko nine na mata wani abu bisa rashin sani. Tsayawa yayi yana nazarin abubuwa sam bai tunanin da akoi aami abinda ya mata wanda za’a ce shi yayi hurting feelings nata haka. Barin maganar zucin yayi a haka “Fannah nasan kina jina I don’t know what got into you sabida ban tab’a ganin ki a yanayi irin na yau ba ko abinci kink’i chi tun d’azu nake miki magana amman kink’i tankani I can’t take it anymore. Please in wani abun na miki wanda yayi hurting naki haka I’m sorry kiyi hak’uri dan Allah ki sanar dani na zauna nayi tunanin duniyan nan amman na kasa tuna koda abu d’ayan dana miki da zesa ki shareni haka yau har ki rufe kanki a d’aki. I’m sorry I’m truely sorry ko abinchi ne kifito kichi not for my sake but for your health’s, I love you.” Ya sanar da ita cikin cracky voice yana kaiwa nan ya wuce d’akinsa ko maybe intaji alamun ba motsinsa zata fito.

      Kalamunsa masu narkar mata da zuciya taji bata k’aunar sake sauraronsu ko k’arfin kuka batada. 20 minutes later bayan ta tabbata baya bakin k’ofar ta mik’e tana dafe dafe har ta isa bakin k’ofar ta bud’e a hankali, leqawa tayi da kyau bata ganshi ba sannan ta sa kai tajeta dining area ta d’ibo abinci kad’an kan plate ga yunwa har yunwa amman ba tajin zata iya chin abincin ma. Ruwa ta cido daga fridge d’in takama hanyan komawa d’akinta gabanta ne yayi mumunan fad’i ganin Anas da tayi tsaye jikin k’ofar d’akinta, data kallesa seta gano yayi kuka shima. Toh kukan meh kuma zeyi bayan abinda ya mata shekaru had’u koma tace biyar da suka wuce. Kai ta soma kad’awa take hawayen ta da sukayi seizing suka soma sauk’owa. A hankali take ja da baya baya wane taga aljani.

       “Fannah please why are you doing this?” Ya tambayeta cikin wani irin salo. “Mesa Flower? Meya faru? In ni na miki wani abun I’m sorry dan Allah ki sanar dani mistake nawan se in gyara kefa kike cemin a baya silence is never the solution to a problem amman kuma kikeyi yau please talk to me.” Kai still take kad’a masa ga wani irin b’arin data soma yi hawaye se ambaliya suke kan kumatunta. Taku ya soma yana nufanta.
      Takasa furta koda ‘A’ se baya baya take har ta isa jikin bango bebar binta ba alokacin da ya rage saura befi taku uku tsakaninsu ba nishinta ya soya tsabagen b’arin da hannunta suke batasan lokacin da ta sake plate da gorar ruwan a k’asa ba. “Tata tas!!” kukeji k’aran fashewar glass.


© MIEMIEBEE
adsense 2 here
Share:

13 comments:

  1. Hmm! Sirrin ya bayyana koya xai kasance in tafada me cewar itace!

    ReplyDelete
  2. Hmm! Sirrin ya bayyana

    ReplyDelete
  3. Thanks lov dis novel

    ReplyDelete
  4. Pls next chapter we re enjoyin

    ReplyDelete
  5. sai ta yi hakuri ta zauna da shi ta kuma mishi uzuri

    ReplyDelete
  6. luv story so sweet pls go on

    ReplyDelete
  7. Allah yakara basira

    ReplyDelete
  8. Sir toh ya ake karkewa tsakanin flower da Anas

    ReplyDelete
  9. I LIKE DIS NOVEL

    ReplyDelete
  10. the novel also lyk u

    ReplyDelete

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *