Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, September 7, 2016

TANA TARE DANI...56--60

adsense here tana-tare-dani.jpg


TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 56
BY MIEMIEBEE


Wani irin tausayin daya jima be mata irinsa ba ya soma jimata yau, azabarcaccen kuka take na hak'ik'a daga ya gwada tab'a koda hannunta ne sekuma ta tsala ihu tana had'asa da Allah. Toh wannan wace erin mafarki ne? Ya tambayi kansa. Kasancewar akoi d'an haske d'akin be damu ya kunna wuta ba, wajen dispenser ya nufa ya tsiyayo mata ruwa a cup cike da tashin hankali. "Fannah gashi sha kinji?" Ko kallonsa batai ba se b'ari da take tana hawaye, "Fannah mafarki ne bawani mutumi anan kinji? Sha ruwan ki koma bacci." Hannunsa daya aza kan bayan ta taja jikin nata baya da wuri. "Dan Allah kayi hak'uri Mami please kizo wallahi gashi nan." Cup d'in ya ajiye bisa side drawer tare da finciko ta da hannu seda ta fad'a a jikinsa, gagam ya matse ta a jikinsa me k'amshin bala'i dakuma d'umi, ta hanyan hugging nata. Ihu ta saki sosai tana b'ari a yayinda kukanta ya tsananta sekuma had'a sa da Allah da take tana k'ok'arin k'watan kanta amman sam ta kasa. "Dan Allah kayi hak'uri ka sakeni, kar ka k'ara dan Allah..."

"Shhh! Fannah is okay, stop crying kinji? Bawani mutum anan Anas ne kawai, stop fighting it keep calm, I'm here for you bar kuka kinji?" Anas ya sanar da ita cikin wani irin salon da be tab'a using ba, hab'ansa na akan kanta. A hankali ta dena fad'an da takeyi na k'watan kantan sede kukan da take har yanzu bata bari ba.
"Is okay kinji? Mafarki ne, I'm here, bar kukan." Hijabin ta daya jik'e jak'af da gumi yayi yunk'urin cire mata wata ihun tasake tsalawa.

"Fannah ba abinda zan miki you are sweating, duk kin jik'e tsaya in cire miki hijabin kinji?"
"No banaso dan Allah kayi hak'uri, karka k'ara."
"Ba abinda zan k'ara kawai cire miki zanyi, you're sweating." Sam tak'i yarda yacire mata shiko ya dage seya cire saboda irin zufan datake ta had'awa duk wuyan hijabin nata ya jik'e. Da k'ak'ani k'ak'a yasamu ya cire mata hijabin tana manne a jikinsa har yanzu. Sunyi kusan minti goma a haka se daddad'un kalamu yake fad'a mata yana shafa bayanta a hankali, hankalinta yana kwanciya, nan ne tasamu tabar kukan sede numfashinta be dawo saiti ba har yanzu. Bacci sosai Anas yakeji, "Fannah" ya kira sunanta a nitse. Cike da tsoro ta amsa kanta manne a k'irjinsa. "Uhmm" tace.
"Ba wani mutumi mafarki ne ba?" Ya tambayeta.
Kai ta giad'a a hankali.
"Good toh lets go back to sleep, nasan kema kinajin bacci." Hannunsa daya zagaya a bayanta ya zaro wani tsoro taji ya sake ratsa ta atake batasan lokacin da ta zagaya hannayenta bibbiyu a jikinsa ba gagam ta matsesa not letting go. Wani erin sparks Anas yajiyo within him.

"Dan Allah kar ka tafi wallahi mutumin ze dawo."
"Fannah I'm here bare dawo ba, ba tafiya zan ba kinga ina chan, ba mutumin da zezo kinji?"
Kai ta girgiza "please kar ka tafi wallahi zezo."
"Fannah we need to sleep, bacci nakeji."
"Anas please..." Ta rok'esa cikin sautin kuka.
"Okay okay naji barin tafi ba amman lets sleep kinji? Barin d'auko pillow na se mu kwanta." Nanma kai ta girgiza da k'yar ta sakesa ya d'auko pillow ahakan ma binsa take hannunta nannad'e cikin nasa. Bayan ya ajiye pillow'nsa kan gadon yace, "oya hau ki kwanta."
"Ina jin tsoro."
"Fannah I'm here." Ture pillows datayi katanga dasu a jiya yayi a k'asa sannan ya kwanta tana tsaye a kansa se b'ari take. Hannunsa ya bud'e mata "come here." Ba musu bale gardama ta haura kan gadon itama, hannunta yaja a hankali ta fad'a kan k'irjinsa, kanta ta daidata ta kwanta comfortably a jikinsa, da rabin jikinta akan nasa se b'arin take har yanzu. A nitse ya zagaya hannunsa a bayanta yana shafawa a hankali.

"Yi bacci kinji ba mutumin daze zo." Kai ta gyad'a a hankali tare da yab'a hannunta kan cikinsa ta zagayesa gagam. Ganin bata bar had'a gumi ba har yanzu ya d'an k'ara k'arfin AC'n. A hankali bacci me uban nauyi yayi gaba da Fannah, jin nauyinta a jikinsa ya k'aru ya tabbata tayi bacci. Cike da dabara ya gwada mai da ita wajen kwanciyarta sede anytime ya gwada motsi seta sake matsesa a jikinta. Sau biyu ya gwada janta daga jikinsa amman tak'i sakesa agarin haka ya since mata ribbon. Uban gashinta ya bayyano kamar wadda zeyi kuka ya gwada packing mata gashin amman ya kasa gashi anytime ya gwada janta daga jikinsa seta sake matsesa.

Ahaka shima wahalellen bacci yayi gaba dashi da gashin Fannah duk yabi ya cika masa fuska.
Asuban fari Fannah ta tashi a hankali ta soma bud'e idanunta har ta bud'e duka ganinta tayi kwance jikin na miji da hannunta zagaye kan cikinsa ihu tayi niyan sakarwa sewani abu ya dakatar da ita. Hannun nata taja daga kan cikinsa da wuri tana d'ago kanta taga Anas ne, meh hakan? Meya kawosa kan gadon? Me takeyi a jikinsa? Bata gama nemo amsoshin tambayoyin nan ba ta tab'a jikinta taji ba hijabinta me zata gani? Gashinta baje a fuskarta da jikinta gabad'aya. Ihun da tayi niyan yi d'azu ta bud'e baki zatayi yanzu, chak tunanin mafarkin da tayi ya fad'o mata akai ya dakatar da ita.

Se a yanzu take tuna duk wani abinda ya faru a daren. Kunya taji sosai inta tuna Anas ya ganta da 'yar kayan dake jikinta dakuma yadda ta riga matsesa a jikinta jiya. Ribbon nata ta lalimo a garin haka ta farkar da Anas tun idanun nasa suna kafewa har ya bud'e su gabad'aya. Idanunsu na had'uwa tayi saurin kawar da kanta bedsheet ta soma ja tana kare k'irjinta. K'aramar tsuka yaja tare da juya mata baya dan cigaba da baccinsa. Ribbon natan take k'ok'arin miyarwa amman takasa batada ma k'arfin kamawa batasan lokacin da tasaki wani wahalallen k'ara ba take Anas ya juyo yakusan minti yana kallonta tayi nan tayi chan amman takasa kama gashin ya tashi ya zauna. Hannu ya mik'a mata da nufin bani. Itako sam bata gane meyake nufi ba. Hannu kawai yasa ya amshi ribbon d'in daga hannunta cike da tsoro ta gwada matsawa baya ayayinda yajawota ta fad'a jikinsa. Uban gashin nata ya soma packing nasu gu d'aya a yayinda take k'ok'arin fisgo jikinta. "Stop it Fannah" yayi warning nata. Ba tare da b'ata lokaci ba ya kama mata gashin a daidai tsakiyar kanta yabar jelan na yawo. Bayan ta d'ago daga jikinsa ta tuttusa jelar ta nannad'e waje d'aya. "Thank you" ta fad'a masa kanta sunkuye.

Bece mata komai ba illa observing nata da yake, nan ya gane hijabinta take nema hannu ya mik'a ya d'ago a k'asa tare da mik'a mata. Hannu tasa ta amsa da wuri ta miyar jikinta sannan ta mik'e tashiga bayi, bayan tafito tayi kan Anas taga har ya koma bacci.
"Anas" takira sunansa a hankali. Idanunsa kawai ya bud'e be amsa taba.
"Asuba tayi ka tashi kayi muyi Sallah." Bayan daya gama sauraronta seya sake rufe idanun nasa ba tare da ya amsata ba. "Anas kaji?" Ta fad'i.
"Naaji!" Ya fad'a a d'an fusace. Mik'ewa yayi daga kan gadon daga shi se nickers nasa, k'are wa jikinsa kallo tayi nan 'yan seconds sannan tayi saurin kawar da kanta. Ko ta kanta beyi ba ya nufa bathroom kafin yafito ta shimfid'a musu dadduma tana zaman jirar fitowarsa.

Bayan ya fito ya zaro wata milk jallabiyansa sabo pil ya zira sannan ya nufa inda tayi musu shimfid'an, ganin ze fara sallan ba ita takira sunansa. "Anas."
"Meh?" Ya amsata a fusace.
"Ba tare zamuyi sallan ba?"
"Kowa yayi nasa" ya amsa ta a takaice.
"Anas but Sallar jam'i yafi lada."
"Da a gida keda su wa kikeyi?"
"Dasu Afrah."
"Naji lets pray then."
"Uhm amman se munyi Rakatainul~fajir ba?" Ta sanar dashi kanta a sunkuye.
Raka... Rakatainul~fajir? ya nanata a zuciyarsa. "Me kuma rakatainul~fajir?" Ya tambayeta a fili.
"Raka'a biyun da akeyi gabanin k'etowar al~fijr."
"Ohhh! Fannah!" Ya fad'a rai ad'an bace tare da sa hannu cikin gashinsa yana hargitsawa. "Ke komai ne sekin had'a masa concussion? Sallan Asuba ma se anyi rakatainul~fajir ne ko meh?"
"Anas hadisi ne fa ingancecce, yin nafilar yafi duniya da kanta dakuma duk wani abinda ke cikinta"
"Toh naji raka'a nawa ne?"
"Biyu ne kacal, a first raka'ah suratul~kafirun na biyu kuma ikhlas." Kai kawai ya giad'a mata yajasu. Ita Fannah bata zata ma Anas ya iya Sallah kamar yadda yajasu ba, ta d'au ko sallan ma seta koya masa. Bayan sun sallamesa yajasu Sallar Asuban, duk wani k'aidojin karatu taji yana karewa, duk wani hukunce hukunce yana biya, a takaice sautin k'ira'ar sa ya burgeta ba kad'an ba saboda yadda yake da zak'in murya, sosai yayi impressing nata ashede ba jahili ta aura ba.

Bayan sun sallame ya mik'e ze koma ya kwanta.
"Anas" ta dakatar dashi da wuri.
"What now Fannah? I want to sleep please."
"Babu kawai so nake na fad'a maka qira'arka tamin dad'i."
"Naji" yace sama sama yana k'ok'arin cire jallabiyar. Chan k'asa k'asa tace, "aini ban zata ka iya karatu bama." Sekuwa yaji ta.
"Kafiri ne ni ai dole kice baki zata na iya karatu ba. Toh in baki sani ba barin sanar dake yau cikin izu sittin na Qur'ani nayi talatin da biyu, kin gane? Ba jahili ne niba."
Mamaki sosai tajiyo, 32? Ta nanata a ranta. Amman shine bai aiki da ilimin Qur'anin nasa? Kuma besan hukunce hukunce ba a addinin muslinci.
"Anas amman shine baka aiki da ilimin naka?"
"Me ruwanki? My life is not your business, kuma ai ba ce miki nayi islamiyya nayi attending ba hadda ne, zallan Qur'ani da tajweed kawai akeyi sesa kiga ga bansan sauran religious stuffs d'innan ba time daya kamata nashiga islamiya nak'i ban shiga ba." Sekuma yayi shiru "why am I even explaining these to you? Kin ga dama kice ban san komai ba game da addini keda kika sani sekita bragging dashi be damen ba kuma bare damen ba, allow me to sleep now, will you?"

"Anas I'm sorry ba abinda nake nufi ba kenan also in aka idar da Sallan Asuba dama kowani Sallan ba direct akeson mutum ya tashi ba. Akwai morning azkar da akeyi wanda yake da falala sosai shima."
"Ohhhh!" Ya sa hannu cikin gashinsa a fusace yana hargitsawa. "Fannah please, please nace nan ba islamiyya bane kince inyi rakatainul~fajr nayi be isheki ba yanzu kuma azkhar kikeson sani yi? for goodness sake jiya bansamu nayi bacci ba, wannan mafarkin da kikayi duk ya bi ya tadda min hankali, haka kika hana ni bacci yanzu kuma dayakamata in kwanta shina kice barin yi ba?" Ya tambayeta a tsawace. Bata san lokacinda ta soma hawaye ba.

"I'm sorry, Allah baka hak'uri." Ta fad'a tana tare hawayenta. Kallonta yayi na 'yan seconds tare da kawar dakansa, nan yacire jallabiyan ya haura kan gado. Sautin kukan tane ya hanasa sukuni, ya d'au pillow ya rufe kunnuwasa amman still yakasa bacci gashi kuma ita tak'i yin shiru besan ina ze kaita ba. Mutum da an masa magana se kuka sekace 'yar yarinya. Ganin ba ubangiji se Allah ya taso daga kan gadon tare da zura jallabiyar sa, gabanta ya tako ahankali ya zauna tana azhkar nata da hisnul muslim nata ahannu tana kuka a hankali ko d'aga kai ta kallesa batai ba. Zama yayi a gefenta yana fuskantar ta.

Littafin ya k'wace nan ne ta d'ago idanunta da suka soma canza launi. 'I'm sorry' yakeson fad'a mata but he can't saboda girman kai instead yace, "they came out wrong, I don't mean any of those words, kinji? Stop crying." Yi tayi kamar bata ji sa ba "kabani littafi na" tace ba tare da ta d'aga ido ta kallesa ba. Shi mesa baya cewa sorry? Ita abu kad'an tayi masa zata ce sorry amman shi sede yace they came out wrong.
"I said they came out wrong, ba haka naso su fito ba ko bakiji ba?"
"Naji kabani littafi na toh."
"No zanyi Azkhar d'in." Batasan lokacin da fuskarta ta sake ba, "zakayi?" ta tambayesa cike da jin dad'i.
"Yes zanyi, show me the page." Nan ya mi'ka mata bayan ta bud'e masa daga farin ta nunnuna masa. Kai ya gyad'a tare da amsa ya somayi. Kallonsa ta tsaya yi, ba k'aramin dad'i taji ba, a rayuwa batada burin da yafi ta shiryar da Anas, kuma alhamdulillah a hankali yana shiryuwan. Ya d'anyi nisa seya dakata tare da d'ago kansa nanne ya kama Fannah na kallonsa. 'yar murmushi ya saki. "Kefa bara kiyi ba? Gashi gama seki bani, I'll wait for you."
"No karka damu na iya a ka zanyi just use it." Kai ya giad'a mata tare da mayar da hankalinsa kan littafin. Koda ta gama nata bata tashi ba seda ta jira ya gama shima sannan suka tashi atare. Jallabiyar yakuma cirewa ya haura kan gadon. So take tace masa ya koma wajen sa na jiya sede kuma ta tuna batada iko. D'ayan b'angaren ta nufa ta d'an ajiye pillows uku a tsakaninsu sa'annan ta kwanta itama daga chan nesa nesa.

A hankali ya juyo yaga tana fuskantar d'ayan gefen ga kuma jera pillows d'in data sake a tsakaninsu. Kai kawai ya kad'a. "Da hijabin zaki kwanta?" Ya tambayeta.
"Eh" ta basa amsa.
"Yayi kyau." Ahaka duk suka koma bacci ba su suka tashi ba se chan k'arfe 11:30AM nanma Anas ne ya tashi, idanunsa basu sauk'a a ko ina ba se akan kyakkyawar fuskar Fannah, tad'an gangaro kad'an zuwa wajen data yi katanga tsakaninsun. Wayarsa ya d'ago ya soma d'aukanta hoto yayi kusan guda ishirin yaga ta motsa k'afa da wuri wuri ya miyar ya cigaba da kallon ta. A lokaci d'aya kawai ta bud'e ido se karo taci dana Anas a kanta kunya yaji sosai a lokacin da ta tare fuskar tata da hijabi. Se k'arya ya mata wai; "ace warki kallon ki nake ne? Wannan uban minsharin da kiken ne ya tadani in the first place."

Fuskarta cikin hijabin tace, "ni bana minshari."
"Nikuma ba k'arya nake ba" yana kaiwa nan ya mik'e, towel da jakar wankansa ya ciro ya nufa toilet. Se ayanzu ta fiddo fuskar ta. Wajen akwatinta ta nufa ta ciro jakar wankanta da towel nata itama, takaici tajiyo data ga 'yar tsawon towel d'in, ko gama kai tsakiyar cinyarta beyi ba, se yanzu ma take dana sanin d'auko towel nata na gida wanda yakai kusan guiwarta.

Wayarta ta ciro takira gida suka gaisa da kowa da kowa se tsiya Afrah kemata amarya ansha amarchi, ya first night. Tsuka taja tare da kaste wayar. Bada dad'ewa ba Anas yafito tunda Fannah ta kafa idanunta akansa ta kasa d'aga wa. Ya d'aura towel d'in daidai iya V line na k'asansa, packs nasa da suke nan 'yan daidai suka sake bayyana. Wani k'aramin towel ne kuma rataye a wuyarsa wanda da d'ayan jelar yake goge gashin kansa daya jik'e jak'af yana sheqi. Wani haske skin nasa ya k'ara da d'igo d'igon ruwa kwance akai. Gashin jikinsa duk sun kwanta luf-luf, da fuskarsa ya bayyana kuwa, ruwa ke d'iga daga tip na hancinsa. "Kallon ya isa." Yace da ita wani irin kunya taji kamar ta nitse k'asa wato tun d'azu ya karanchi kallonsa take kenan. Ya Salam!! Tace a ranta.

"I get it I'm your husband you can stare at me amman banda irin kallon nan yayi yawa." Fuskarta kawai ta rufe da hijabinta ta bi ta gefensa ta shiga bathroom d'in. Nan da nan ya shirya cikin sirinsa na safiya akullum ¾ wando da vest, gashin kansa yayi styling mekyau ya feffeshe da designer turarukansa tare da sa Bouzet agogonsa ya dake kan gado yana 'yan latse latse a laptop nasa.

"Ya Salam!" Fannah tasaki k'ara a cikin bayin kasancewar hijabinta daya fad'a tsundum cikin bathtub, kafin tace zata cire yariga yasha ruwa ya jik'e liqis. Kuka ne kawai batayi ba yanzu ya zatayi tafita da wannan gajeren towel dake jikin tan? Matsewa tatayi amman ina its not at all helping, tasa a haka kuma tana tsoron pneumonia nata karya tashi dan ba wai magani tasha ya mutu ba gabad'aya. Ganin ba ubangiji se Allah ta shanya hijabin a bayin, d'ayan k'aramin towel d'in ta d'aura a gashinta data wanke. Ta iso bakin k'ofar ta sake kallon jikinta kai bara ta iya fita haka ba gaban Anas, tsirecin yayi yawa ta baya kam ma inta tsuguna za'a iya ganinta. "Anas" ta kira sunansa daga cikin bayin ta yadda ze iya ji inhar yana cikin d'akin.
Juyowa yayi yana kallon k'ofar. Me kuma takeso yanzu? Ya tambayi kansa. K'in amsawa yayi.
"Anas are you there?" Nanma shiru yayi. Hamdala ta saki a ranta shikenan bayya ma d'akin barinyi sauri inje in zaro wani hijabin insa kafin ya dawo.

Karap ta bud'e k'ofar tare da rufewa tana juyowa kawai taga Anas mik'e kan gado, mutuwar tsaye tayi a wajen...

© miemiebee

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 57
BY MIEMIEBEE


Kallonta Anas yake wane ze had'iyeta, ko kyafta ido ya kasa, numfashinsa ma gabad'ai yankewa yayi, in ya d'auka daga k'afafunta seya kai kanta ya tsaya sannan ya sake d'aukowa daga k'afafun nata. Yasha kallon mata kan bikini(pant da bra) amman ba wacce ta tab'a birkita masa lisafi kamar Fannah, she is just different in her own ways. Itako kasa koda motsi tayi she still can't believe Anas ya ganta da towel. Idanunsu na had'uwa ta yi saurin sunkuyar da kanta a yayinda Anas ya soma faking tarin tsiya shi a dole wai ya shak'e ganin ta ba kaya disgusts him. Alokaci guda kuwa hankalinta ya dawo jikinta k'ofar ta soma jijjigawa ta baya tana k'ok'arin bud'ewa amman ta kasa dan yadda ta rikice.

Idanunsa da ya kawar ya sake maido su kan ta a lokacin da take k'ok'arin bud'e k'ofar da sauri ta juya masa bayanta, data murd'a handle na k'ofar da k'arfi kuwa se ya bud'u. Kansa ya girgiza dan kawar da image na Fannah da towel daga k'wak'walwarsa.
Wani takaici taji ya rufeta data sake kallon jikinta. K'ofar ta sake bud'ewa kad'an ta lek'a, k'afafunsa ta hango yana nan kan gadon har yanzu. Tunanin ya zata d'auko hijabinta take ganin batada wata mafitan dayafi ta kira Anas ta rok'esa kawai ta rufe ido ta kira san. "Ermm Anas." Yana jinta yayi shiru har yanzu se yawo hotunan ta da towel yake masa akai.
"Anas please nasan kana jina."
"Meh?" Ya tambaya a fusace.
"Please hijabi na zaka ciro min cikin medium size akwati na maroon d'in."
Idanunsa ya miyar kan maroon akwatin nata sannan yace, "barin iya ba."
"Anas dan Allah kayi hak'uri please."
"Kifito ki d'auka da kanki."
"Anas banida kaya a jikina shiyasa please kayi hak'uri."
"Toh aini ba kallonki zanba."
"Nasani kawai ka taimaka please." Kamar wanda bare tashi ba ya mik'e akwatin nata yaja ya bud'e to his suprise yaga na inner wears nata ne, ba komai banda bras da panties ciki. Daidai nan Fannah ta tuna ashe inner wears nata ke ciki, a red d'inne hijabanta ke ciki.

"Anas hold on please kar ka bud'e bashi bane." Inaaa aikin gama ya riga ya gama. Ko sauraranta beyi ba seda ya k'are wa inner wears natan kallo sannan yace, "nafasa kifito ki d'auka da kanki."
"Anas I'm sorry dan Allah cikin jan ne yana nan a gefe, please kaji?" Banza da ita yayi se chan daya ga dama ya bud'o jan ya ciro mata d'aya daga cikin hijaban nata. "Fito ki amsa gashi."
"Anas na d'au zaka kawo min ne fah."
"Cemin kikayi in ciro miki ba inkai miki ba, so kizo ki karb'a."
"Hausan nawa ne baka gane ba, ka mik'o min please." Seda ya gama wasting mata lokaci sannan ya nufa wajen bathroom d'in tare da mik'a mata be jira ta gama karb'ewa ba ya sake k'iris ya rage ya fad'i a k'asa. "Thank you" tace masa a yayinda yayi banza da ita bayan tasa hijabin tafito kanta a sunkuye, akwatin inner wears natan taga a bud'e ga bressiers nata duk a k'asa duk Anas yayi watsi dasu. Shima kallon bressiers natan yake atare suka d'ago ido suna kallon juna cike da kunya ta kawar da kanta, a kunyace ta tsuguna tasoma tattara abinta duk inda ta nufa Anas na binta da kallo. Se guna guni take "kawai da ancewa mutum ya taimako da hijabi seya hargitsa wa mutum kaya."

"An hargitsan nan gaba seki na shiga da hijabinki in bakison ana ganin jikinki." Shiru tayi batace masa komai ba, bayan ta gama had'a kayakin nata ta rufe, man shafawanta ta ciro tunanin ya zata shafa take chan ta juya taga Anas na kallonta mik'ewa tayi da nufin shiga bathroom ta yafe zataje ta shafa man acan. K'aramar tsuka yaja, "dawo ki shafa manki, I'm not interested in looking at your body." Yana kaiwa nan ya tattara wayoyinsa ya fice ko ina zeje se Allah.
"Tafi nono fari" tace chan k'asa k'asa yadda bare jita ba. Bayansa tabi ta sa lock a k'ofar, nan ta cire hijabin nata cikin kwanciyan hankali ta shafa manta ta bud'o akwatin kayakinta takaici ne ya rufeta kap ba atamfa english wears ne zalla ciki. "Afrah wallahi zan sab'a miki, seda nace miki karkisa min english wears ciki. Mschww!"

Haka ba yadda ta iya ta ciro wani red highwaist skirt da white blouse had'ad'd'e ta ajiye a gefe, bayan tasa inner wears nata ta jawo skirt d'in bata gama sawa ba Anas ya murd'a hannunn k'ofar, jin a rufe ya fusata. "Fannah me na rufe ni a waje? Daga baki privacy seki kama kiyi locking d'akin?"
"Toh ai na d'au ko fita zakayi."
"Toh ba fitan nayi ba, open the door."
"Barin sa kaya."
"Wai me zan kalla a jikinki? Open it." A ranta tace ai wallahi sena gama sa kayan zan bud'e hakan kuwa tayi ignoring nasa seda ta gama sa kayan nata ta bud'e masa. Masifeta yayi niyan yi amman ganin yadda kayan jikinta ya mugun mata kyai seya fasa, yaji bayason sata kuka. Matsa masa tayi ya wuce ba tare da yace mata komai ba. Wajen kayakinta ta nufa ta since towel dake kantan a hankali take taje kanta har tagama da k'yar anzo wajen tayi tayi ta kama ta kasa koda ta kama se ya sake fita. Kamar wacce zatayi kuka ta juyo tana kallon Anas, kallon nata yake shima ganin ta juyo yayi saurin maida kallonsa kan wayarsa.

A hankali ta tako zuwa gabansa ta tsaya "Anas help me pack my hair please." Banza yayi da ita "kaji Anas please?" Nanne ya d'ago blue eyes nasa yana kallonta, irin kallon data tsana kenan, kanta ta sunkuyar chan ta d'ago ta ga still kallonta Anas yake ko kunya ya kawar da kansa ma be ba. "Anas kabar kallo na haka mana, in ni ke kallonka seka ce na fiye kallo dayawa, nima banason kallon ya isa please ka kama min. Kaji?" Nanma bece mata komai ba. Ganin baida niyyan kama mata ta juya zata tafi hannunta yajawo seda ta fad'o jikinsa nauyinta kan cinyarsa, hannunta ta zagaya a wuyansa dan balancing kanta. K'ara ta saki take ya aza hannunsa kan lips nata "shhh!" Shirun tayi kum. Kallon cikin idanun juna suke na kusan minti biyu sannan ta d'aga kanta daga jikinsa, murmushi ya saki ta gefe d'aya saboda yasan yadda d'an wannan abu yayi affecting Fannah. Hannunta ya rik'i kafin ta fice, "tsaya mana ko bakiya so in kama miki gashin ne?"
"Banaso I'll manage sakemin hannu Mr. Fauzi." K'in sake mata hannun yayi, wayansa ya ajiye tare da mik'ewa. Hannunta me ribbon d'in ya kama shima tare da zare ribbon d'in. Fannah kad'ai tasan irin shock da takeji, akoda yaushe Anas ya tab'a ta wani erin electrification takeji a ajikinta wanda battaso. A hankali ya sake duka hannun nata ya soma packing gashin natan, a hankali har ya kama waje guda. Hannunta tasa zata tattare jelar a yayinda ya kama hannun nata "kibarshi haka kinfi kyau."

"But An-"
"Lets not argue haka yafi kyau, karki tab'a kinji?"
Kai kawai ta gyad'a masa tareda k'watan hannunta a hankali, binta da kallo yake har ta nufa wajen kujera ta zauna jin idanunsa akanta tak'i d'aga kanta. Chan da zaman shirun ya isheta tace, "Anas ba breakfast ne?"
"Jiya danace kici abinci me kika cemin? you are not hungry koba haka ba? Ba bareakfast 'cause bana jin yunwa ni se lunch." Fuska ta maraice "Anas yunwa nakeji."
"Kijira zuwa anjima se muci lunch." Bata sake ce masa komai ba ta mik'e kan 3 seater'n tare da juya masa baya. Yunwa sosai takeji har wani kuka cikinta yakeyi. Knocking akayi bisa k'ofar nasu nan ya mik'e abincinsu aka kawo musu bayan ya amsa ya ajiye kan table d'in har ayanzu Fannah batasan meke faruwa ba. Plate natan ya b'oye k'ark'ashin gado. Yana bud'e nasan k'amshin sardine sauce da chips d'in ya cika d'akin, Fannah bata san lokacin da ta juyo tana kallon sa ba, har d'igan miyau takeyi gawani kukan da cikinta keyi. Seda ya tabbata tana ganinsa yakai spoon d'aya baki se exxagerating dad'in abincin yake.
"Anas ni banda ni ne? Ina nawa?"
"Babu" yabata takaicaccen amsa.
"Kamar ya babu?"
"Jiya danace kici abinci ba k'in ci kikayi ba?"
"Anas ba ya wuce ba? Nan gaba barin sake ba, please ina plate d'ina?"
"You promise? Nan gaba nace kici abinci zakici?" Kai ta gyad'a a hankali. "Good" hannu yasa k'ark'ashin gadon yaciro mata plate natan. "Come over lets eat." Ba musu ta tashi taje ta samesa bayan ya mik'a mata plate natan ta zauna gefe dashi ahaka suka samu sukayi breakfast nasu.

Kallonta yake yadda take ta cin abincin ba makawa gaskia yunwa yacita da yawa, bayan da ta gama ya tambayeta "a k'ara miki?" Kai ta gyad'a a hankali plate nasa ya mik'a mata. "Kaifa ka k'oshi?" Kai ya gyad'a mata nan da nan ta d'ura nasan cikinta se ayanzu ta jita dam. Lokacin Sallah ya riga yayi nan ta fad'a bayi tayi alwala shima haka sannan ya jasu Sallah bayan da suka idar ya sake feshe jikinsa da turare binsa kawai take da kallo seda yazo fita takira sunansa ganin baida niyyan fad'a mata inda zasa.

"Anas." Chak ya tsaya "wani abu ne?" Ya tambayeta bayan ya bud'e k'ofar. "Nace ina zakaje?"
"Toh wifey kishi ne ya motsa?"
"Nifa ba kishin ka nake ba."
"Toh why asking? Ka
I thought ko zaka sauk'eni a gida ne.
Kin tab'a ganin inda amarya ta fita?
Anas zaman nan d'in ba dad'i.
Wani murmushin tsiya ya saki, just say it you are gonna miss me, karki damu I won't take long yanzu zan dawo. Bejira jin me zatace ba ya rufe k'ofar. 'Yar tsukar ta taja tare da hayewa kan gadon, game na candy crush ta hau yi batans seda bacci yayi gaba da ita ba.

40 minutes later...
A nitsr ya bud'e k'ofar kamar ko yasan tana bacci. Ledar chocolates da ice cream daya siyo musu ya bud'e fridge yasa ciki sannan ya nufa kan gadon inda take kwance bayan ya zauna gefenta ya zura mata ido. wayarta dake kwance a gefenta ya zaro yayi quitting game d'in. Hannu yasa a fuskarta a hankali ta yadda bare farkar da ita ba, gashin dake kwance kai ya d'ad'd'aga sannan ya jawo bargo ya rufeta.

**
Seda La'asar ya tada ta suka idar da Sallah tare da musu ordering abinci, suna cikun ci aka yi knocking get it yache mata ba musu ta mik'e ta bud'e kad'an daga photo album na bikinsu ne. Bayan ta amsa ta masa godiya. Mugani Anas yace.
Nima ingani mana.
I'm your husband yiu follow my instructions so bani. Kallo ta galla masa awww ni kike harara?
Bafa harararka nake ba. Nan ta mik'a masa. Na english dinner'n su ya bud'e wow! Tace cike sa jin dad'i ganin yadda tayi kyau a hoton.
Wow me or you?
Ni mana, ni ba kai nake kallo ba.
Da banga idanunki kan fuska na bane seki fad'a min maganan banza.
Nide ba kai nake kalla ba. Ignoring nata yayi suka cigaba da kallon pictures d'in se anzo page dayaga tayi kyau se ya wani wuce da wuri wuri in akazo inda yayi kyau kamar ba gobe kuma seya tsaya yana admiring kansa. K'ananun tsuka take ja.

Toh Anas a wuce page d'innan mana munfi minti uku fa muna kallo.
In kun gaji seki tashi, thank god I'm handsome and admit it you enjoy looking at my handsome face.
Nide I don't enjoy. D'ayan page d'in ya juya ganin tayi kyau yayi sauri ya juya Anas ka tsaya mana muga nan d'in.
Keda wa? Page d'in beyi kyau ba bara'a kalla ba. Bata sake ce masa komai ba ya juya next page d'in. Babban hotonsa da Fannah ne kad'ai a page d'in wanda tabar wani duk abinda takeyi tana kallonsa zallah. Munya taji sosai ita kanta bata san ya akayi hakan ta faru ba. Hannu tasa ta rufe. Me haka? D'aga hannun mana.
A'a Anas dan Allah ka juya.
Nak'i ni nace ki tsaya kallo na awajen d'aga hannun. Kinga I can't touch you saboda a contract namu ba body contact, d'aga hannun ki.

Tana d'agawa ta bar wajen. Dariya yakeson yi amman bayason ta raina sa. Tana kallonsa ya d'au hoton a wayarsa.

***
Bayan sun idar da Sallan Isha sukaci abinci bayi Fannah ta fad'a ta watsa ruwa a cikinsa ta canza kaya tana fitowa kamar jiya ta jera pillows tsakaninsu. Kallonta kawai yayi tare da kad'a kai bayan data kwanta yaje ya watsa ruwan shima. Pillow d'aya ya zaro ya koma kan cushion daya kwanta jiya ya mik'e kai bada jimawa ba shima yayi bacci. Kamar jiya yau ma ta farka da ihu nan shima Anas ya tashi. Kukan da takeyi yau kamar ma yafi na jiya. Kamar jiya haka ya samu yayi calming nata da k'yar tabar kukan sede b'arin da take har yanzu.


Toh sakeni zan koma in kwanta.
A'a dan Allah Anas karka tafi wallahi mutumin ze dawo.
Bare dawo ba, sakeni toh. Gangamesa ta sake tana girgiza kai.
Haka kikeson mu raya daren a zaune?
A'a nide kawai karka tafi dan Allah ta rok'esa cikin sautin kuka. Ka kwanta anan.
A'a achan zan kwanta ba kece sarkin yin katanga da pillow ba? Kwanta abinki zan kwana achan nima.
A'a zan cire dan Allah karka tafi Anas.
Nifa barin kwana nan ba sekin cire pillows d'in da kanki.
Naji zan cire hannunsa ta kama gudun kar ya gudu tayi watsi da pillows d'in. Nacire dan Allah don't leave me, inma zaka barni ka kira Mami tazo.
Naji I won't leave you barin d'auko pillow na.
A'a ga nawa dan Allah kar ka tafi. Murmushi ya saki. Toh matsa ciki ba musu ta matsa kan pillon nata ya kwanta. Azaune zakiyi baccin ne?
Kai ta girgiza. Kicire hijabin waj bakiya jin zufan da kikeyi ne?
Nanma kai ta girgiza fine zan koma kan kushion na kwanta.

Anas dan Allah karka tafi har yanzu bata bar b'arin da take ba. Toh kicire you are sweating. A hanakli ta yaye hijabin ta shiga kare k'irjinta. Kansa ya kawar daga gareta sdki kwanta. Pillow d'aya taja ta matso dashi kusa da nasa duk tsoro yabi ya ratsa ta. Bayan minti biyar Anas ya juya aga har yaznu batai nacci ba se b'ari take tana had'a gumi sekuma ta basa tausayi. Kin kasa bacci neh? Ya tamnayeta.
Kai ta gyad'a a hankali. I'm here kinji? Ba mutumin daze zo, ina zuwa. Hannunsa ta rik'o Anas ina zakaje?
Bathroom ya amsata.
Dan Allah kar ka tafi please.
Fannah I want to use the bathroom ba tafiya zan yi ba, kibani just a minute. Ai sam tak'i sake hannun nasa. Haka har bakin bathroom d'in tabi sa tana jiransa se waiwaye take kar mutumin yazo. Anas kayi sauri dan Allah kaji? Se buga k'ofar takeyi sam tak'i barinsa yagama biyan buk'antansa. Yana fitowa ta kama hannunsa ahaka suka isa kan gadon suka kwanta. Ta sake masa hannu ma tak'i.

Ahaka har tayi bacci, hannun nasa ya gwada cirewa daga nata amman gam ta matse cikin nata bibbiyu...

© miemiebee

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 58
BY MIEMIEBEE


Cikin baccin tace, “Anas dan Allah kar ka tafi please.” Alokaci guda kuma yaji wani irin tausayinta ya kamasa, bacci take amman idanunta basu bar zuban hawaye ba. D’ayan hannunsa yasa ya share mata hawayer. “Bar kuka kinji? I’m here.” Hannunsa ya raba da nata na k’arfi ganin yadda ta kama nasa gagam. Firgit ta tashi tana hawaye “Anas please don’t go.”
   “Ba tafiya zanyi ba Fannah” ya sanar da ita a lokacin dayake k’ok’arin kwantar da ita kan k’irjinsa. Bayan ya kwantar da itan ya soma shafa bayanta yana kwantar mata da hankali.
   “I’m here ba tafiya zanyi ba kinji?” Kai ta gyad’a cikin tsoro. Chan yaji nauyinta ya dad’u a kansa, beyi yunk’urin d’agata ba, barinta yayi ta cigaba da baccin gudun kar ya tayarda ita.

    Tunanin me yake sata mafarki haka yake. Waye mutumin? Mesa take kuka? Me ya tab’a mata? Me kuma take tsoron ze sake yi mata? Mesa kullum take irin mafarkin? For how long take erin wannan mafarkin dayake mugun tsorata ta haka? Me wannan mutumi ya mata? Har bacci yayi gaba dashi besamu amsoshi ga wad’annan tambayoyi ba.
    Asubar fari Fannah ta tashi a hankali ta bud’e idanunta, hannunta taja daga kan cikin Anas a hankali. Ta rasa meke sata mafarkin mutumin kullum kwana biyu, a da ne da abin yafaru take mafarkin kullum but as days passed by tadena yi kullum setayi kwana uku ma wani sa’in batayi ba amman tunda tayi aure takeyi kullum yanzu, kuma na yanzu yafi nada kayan ban tsoro. Me dalili? Bata kawo wani tunani a ranta ba ta miqe tayi alwala har a yanzu tsoro takeji mafarkin jiya yafi kowanne abin tsoro bayan tafito ta yi musu shimfid’a sannan ta tada Anas.
    Sun idar da Sallansu sunyi Azkhar suka koma kan gado. Pillow’nta ta matsar baya daga nasa tare da duk’unk’unewa cikin hijabinta tana kallon d’ayan side d’in. Anas ya karanchi hakan, yagano har yanzu tsoro takeji ga rashin maganar da takeyi yau kamar ba ita ba. Tausayinta yasake ji ya kama sa making him so anxious jin labarin mafarkin nata.
 
      “Fannah” ya kira sunanta cikin wani irin salo.
    “Na’am” ta amsa ba tare da ta juyo ba.
    “Are you still scared?”
   Kai ta girgiza masa tana matse ‘yar k’wallarta batadamu ko yana kallonta ko a’a ba.
   “I’m here for you kinji? Kibarjin tsoro ba mutumin da ze zo.” Yayi assuring nata. Kai ta gyad’a.
   “For how many months now kike mafarkin?” Bata masa k’arya ba tace, “7 years now.”
   7 years? Ya nanata a ransa, Allah sarki poor Fannah. “Turn and look at me.” Ya buk’ace ta. Ba gardama ta juyo hawayen da take ta k’ok’arin matsewa ne suka soma gangara. Hannunsa ya bud’a mata “come.” Matsowa tayi kusa dashi cije da tsoro, kanta ya aza a kan k’irjinsa. “Everything is going to be alright kinji? Stop crying.” Hannu yasa ya share mata hawayen. “Do you want to talk about the dream?” Kai kawai ta girgiza masa.
  “Even now that I’m your husband?” Ya tambaya cikin wani irin demanding salo. Kuka ta fashe da, “Anas nima bansani ba anytime na kwanta kawai se inji wai wani mutumi yazo yana bina ze gudu dani.” Ta masa k’arya dan battason sanar dashi sirrinta.

   “Shhhh! Is okay bar kukan, lets sleep.” Hannunta ta zagaya akan cikinsa ayayinda yake ta shafa bayanta har tayi bacci.

  **
    Da misalin k’arfe 10:00AM Fannah na zaune shiru kan cushion, game data saba yin ma tak’iyi yau. Yanzu suka gama breakfast da Anas. Observing nata yake tun da suka tashi haka take ta acting strange, ya rasa me ze mata koda ya mata magana amsarta befin ‘eh’ ko ‘a’a’. “Fannah” ya kira sunanta a nitse. “Na’am” ta d’ago kai tana kallonsa. “Kinason kifita yau?” Kai ta girgiza masa da nufin a’a sekace ba ita ba..
     “In kaiki wajen Mami?” Batasan lokacin da ta saki murmushi ba “eh” ta basa amsa cike da jin dad’i. “Lets go then.” Dama abaya ne a jikinta, gyalenta ta d’auka tayi rolling tare da feffeshe jikinta da ture haka shima Anas d’in.
   
    Hannunta rik’e cikin nasa suka fice motan ma shiya bud’e mata da kansa ya rufe bayan ta shiga. Zaman tsit suke cikin motar chan da shirun ya masa yawa yace, “mesa bakisha ice cream naki ba? Bakiya son flavour’n ne?”
    “Inaso.”
   “Mesa bakisha ba toh?”
   “In muka dawo zansha in shaa Allah” ta amsa sa a takaice. Shiru ne ya sake ratsa su chan yace, “I miss your coffee” sincerely. Kuma hakan ne rabuwansa da coffeen ta he can’t even remember.
    “Muje office naka ko painthouse in had’a maka.” tace. Duk wannan magana da suke bata juyo ta kallesa ba shiko fuskarta yakeson kalla dan tayi kyau sosai, maroon jan bakin data sa ya mugun amsarta dukda kuwa fuskarta yad’an kumbura dan kukan data sha jiya dakuma yau da safe.
 
    “Fannah look at me.” Ya buk’ace ta ba musu ta juyo. Murmushi ya saki mata daga heart nasa, “kinyi kyau.” Murmushin ta mayar masa “thanks and you too.”
    “Nikam ai kullum ina yin kyau” ya gwada janta da surutu.
   “Yes Anas, kullum kanayin kyau.” ta fad’a tare da miyar da kallonta gare da windon. Daga yadda take maganar ya karanchi batason surutu. Be sake tuhumarta ba dan bayyason tak’ura mata, abinda ke damunta kad’ai ma ya isheta. Enterprise nasa suka nufa ya bud’e mata k’ofar dan neman magana ba rik’e hannunta yayi ba wannan karan. Hannun nasa ya zagaya a waist nata tsam ya matso ta jikinsa suna shaqan k’amshin turaren juna. Ko uffan batace masa ba, duk abinda zeyi yayi atleast sunada aure yanzu ba zunubi. Tun shigarsu cikin Enterprise d’in ake ta congratulating nasu. Bayan sun shiga office nasa ya zauna kan couch a yayinda ta ke had’a masa coffeen ba abinda yake banda binta da kallo, flask dam ta cika masa tare da sa masa cup ta kawo masa. Hannunta yaja ta zauna gefensa.

     “Thank you” yace da ita. Murmushi tamayar masa as a reply. Bayan ya kurb’e rabi yayi pausing. “Kefa zakisha?” Kai ta girgiza masa. “Why?” ya tambaya.
    “Toh ka tab’a min tayi neh?” Ta amsa tambayarsa da tambaya, abinda ya tsana kenan.
    “Da biyu kikayi hakan koh?”
  “Meneh?” Ta juyo tana kallonsa.
   “Again! Aswering my question with another question.”
   “I’m sorry Mr. Fauzi na manta rules naka ne.” Cup nasan ya mik’a mata da ragowar coffeen ciki. “Shanye lets go.”
     “Se wanda kasha zaka bani?”
  “Admit it Fannah kidena so kina kaiwa kasuwa, tunba yau ba kike kallona in ina shan coffee kinason sha daga cup d’ina. Na baki yau so kisha.”
   “Oh please Mr. Fauzi girman kanka yayi yawa wallahi, I pity duk wata macen dazata aureka.”
  “Kema haka I pity duk wani mijin da ze aureki, kisha lets go.”
   “Ni barin sha ba” ta fad’a stubbornly.
   “Okay shikenan tashi mukoma hotel namu toh, da rabon bakison ganin Mami.”
    “Haba! mana Anas me had’in shan coffee na da kaini gida gun Mami kuma?”
    “Nima bansani ba all I know is that sekinsha zan kaiki.” Harara ta watsa masa aiko yaganta.

    “Ni kike harara ko me ake kiran abun?”
    “A’a nifa ba harararka nake ba abu nagani agashin ka” ta masa qarya, nan tasa hannu cikin gashin nasa seyi take kamar tana cire abu. Chan taciro hannun nata. “Ina abun?” Ya tambayeta.
  “Na yasar.” Yasan sarai k’arya take kawai ya mata murmushi. Coffeen ta kurb’e tas ashe de da dad’i. Zata iya irga so nawa take shan coffeen befi sau uku ba dana yau kenan, gaskia she have been missing. Harshe taciro ta lashe lips nata. Kallonta yake in a cute manner.
   “Zaki k’ar” Sarai yasanta da ci zatace eh aikuwa ta gyad’a kai.
   “Toh baraki k’ara ba ai nawa ne tashi mutafi.”
   “Toh Anas I will make another one.”
   “Zaki b’ata min lokaci mutafi.”
   “Anas please.”
  “Fannah please lets go.” Haka Anas ya hanata shan coffeen. Ahmad yasa ya sauk’o masa da coffee machine da flask nasa ta yadda zata na had’a masa coffee always.

    Bayan isarsu gidansu Fannah ta ruga a guje tashiga da Mami ta soma cin karo hugging nata tayi har tana hanata nishi. Bayan sun zazzauna Mami ta kawo musu d’anwake me rai da lafiya yasha had’i kam. Bajewa Fannah tayi taci kamar ba gobe sekace wacce batayi breakfast ba kallonta kawai Anas yake ko tab’a nasa beyi ba saboda he is not a fan of d’an wake be iya ci ba, inma zeci sede ya tsotse zak’in kawai.
    “Baba na ya baka cin naka?” Mami ta tambayesa.
    “Bakomai Mami kawai ban iya chi bane, I'm sorry.”
   “Su Mr. Fauzi ajebo, gaba takaini” Fannah tace chan k’asa k’asa yadda Anas kad’ai dake kusa da ita ya jiyota. Ignoring nata kawai yayi. Plate nasan taja ta soma chi bayan data k’are nata.
   Afrah da Mami kam baki suka bud’e suna kallon ikon Allah. Cike da kunya Mami tace, “haba Fannah taya zaki d’au nasa kuma.”
   “Mami bakiji me yace bane? Cewa yayi baya ci, ajebo ne shi.” Cike da mamaki Mami ta bud’e baki zata masifeta. Da wuri Anas ya katse ta, “A’a Mami barta please, chi abin ki kinji?” Taci morethan half of plate nasa sannan tajita dam.
    “Mu tafi koh?” Ya tambayeta. “Mami zamu koma inason mu gaida su Ummie ma.” Kafin Mami tayi magana Fannah ta rigata. “Tafiya kuma Anas? Na d’au fa zaka ajiye ni ne kayi tafiyarka se anjima kadawo ka d’aukeni.”
   A ransa yace dake driver’n kine niba?
 
    A fili yace, “Fannah sweetheart kinsan zamuje mu gaishe dasu Ummie fah, ba time.” Ganin zasu fara muse-musen ma’aurta Mami tayi excusing kanta tare da jawo Afrah ma suka basu space.  
  Ganin haka yace, “Driver’n kine ni ai da zaki sani jeka ka dawo, tashi mutafi, aikinga su Mamin.”
   Fuska ta maraice “ayyah amman banga Baba ba fa yana bacci. Yi hak’uri please kabarni in wuni anan wallahi chan ba dad’i.”
    “Ohonki tashi mutafi, ina ni kike cema ajebo kina zagina, stand up lets go.”
   “A’a I take that back dan Allah kayi hak’uri.”
   “Nak’i tashi mu tafi.”
   “Anas please” ta shakwab’e fuska tana murza ido. Yasan sarai zata iya fashe masa da kuka anan. Nanne mami ta fito daga d’akin. Ganin ta cika hawaye a idanunta yasa hannu tare da rik’o fuskar natan, “muga yafita?” Iska ya hura mata a idon “sannu ko?” Kai ta gyad’  “eh ya fita.” Chan k’asa k’asa tace, “ka yarda?” Harara ya galla mata tare da gyaran murya.

    “Uhm Mami zan tafi , zan bar Fannah anan I’ll be back in d’auketa.”
   “Toh toh yayi kyau sannu ko Baba na?” Dad’i sosai Fannah taji sebinsa da kallo take har yasa takalmansa. “Adawo lafiya baby.” Juyowa yayi tare da sakar da best smile nasa. “Thank you” sannan ya fice.
   “Soyayya ruwan zuma...” Cewar Afrah tana gyad’a kai. “Su wani baby kuka samu sara?” Banza da ita Fannah tayi seda Mami takoma d’aki bakin Fannah ya bud’u. “Amman ke mena cemiki? Bance karki samin english wears cikin akwatunan da zan tafi dasu ba?”
   “Toh meh? Ai naga da english wears ake amarchi” nan ta kewaya taga ba Mami “Ya Fannah ya first night d’in? Kinyi kuka?”
   “K’asaran ki maras kunya kawai nima bansani ba.”
   “Heheh!” ta sheqe da dariya, “Toh Allah kawo zuriah d’ayyiba yasa du sharpshooters ne” nan iphone nata yayi k’ara alaman shigowar message. Tana bud’ewa taga airtime ne na dubu biyu hot baby nata yamata sending. Bayan tayi replying nasa tace a fili “Allah bar min kai yau akwai flexing a instagram da kallon stories a snapchat.”

      Har yanzu Fannah ta kasa rufe baki a iya sanin ta de Iphone 5s ce wayar Afrah how comes take rik’e 6s plus yanzu?
    “Ke ina kika samu wannan k’aton wayar? Waya baki?”
    “Wanne wai?” ta tambaya cike da tsiya. “Awww Iphone d’ina? Hot baby ya siya min wallahi, yayi kyau ko?”
   “Hot baby wa kenan?” ta kuma tambaya cike da rashin fahimta.
   “Wa kuwa inba Shettima darling ba, business nasa se bunk’asa yake wallahi.”
   Dariya sosai Fannah ta sheqe da dan tasan ina yake samun kud’in daya ke kashe mata. “Shi business d’in kenan?”
  “Eh mana abin hassada ne kuma?”
  “A’a babyn Shettima Allah barku tare ni taho ki tayani in shirya atamfofina gu d’aya dasu zan koma.” Afrah ta bud’e baki zata kuma wani zancen Fannah ta katse ta “a’a banason bayani muje.” Suna hira suna shirya kayakin har suka gama.

11:30AM

    Daidai nan Anas ya dawo d’aukanta beso sake shiga ba se kawai ya kira ta ta waya alokacin wayar tata na d’akinsu itako tana d’akin Baba se hira suke bazawa kamar ance ta mik’e tace bari taje d’aki. Tana shiga taji rurin wayarta nan ta d’aga tare da duban waye. ‘Anas’ taga tubuce kai. K’in picking tayi dan battason sake komawa hotel nasun nan its so boring. Se a karo na biyu ta d’aga nanma seda ya kusa tsinkewa.
    “Kifito I’m waiting for you.”
   “Anas mana please, bamu had’u da Aiman bafa, tana school se 1:00AM zata dawo kaji? In jira?”
   “Banji ba kuma baraki jira ba, Fannah kifito don’t let me repeat myself.” Karap ya katse wayar, tsuka taja. Aiko ya fad’a kunnen Mami. “Keda waye ne?”
  “Erm.. Ermm...” kafin ta had’o k’arya Mami tace, “keda Anas ko? Fannah tun ba’ayi nisa ba kin soma masa rashin kunya, iyyeh? Me dalili?”
   “Mami waifa har ya dawo infito mu tafi.” ta fad’a tana turo baki.
   “Toh se meh? Out!” ta nuna mata k’ofa. Dake kafad’a tayi. “Fannah zan sab’a miki fa!” Haka kamar wacce zatayi kuka taja akwatinta ta fice ko sauraron Afrah batai ba. Bayan fitarta ta bud’e gidan baya tasa akwatin yana kallonta bece komai ba. Tana shiga ya kunna motar ba wanda yace ma wani ko uffan. Bayan isarsu gida suka gaggaisa, Ummie kamar ta cinye Fannah. Besamu ya had’u da Amal ba dake tana school haka Shettima ma.

     “Kuyi sauri ku gama gaisawan ku zan d’au abu cikin d’akina ne yanzu mukoma.”
     “Kai Babana daman ba yini kuka zo mana ba?”
   “Yini? A’a fa Ummie gaisuwan minti biyar ne kacal.” Yana kaiwa nan yashige d’akinsa. “Oh! Fannah kinga halin mijin naki ko? Yafiye rowa dayawa.” Murmushi cike da kunya ta saki tana kare fuskarta.

     Bayan shigan Anas d’akinsa ya nufa wajen safe dan ciro kud’ad’ensa wanda ze buk’ata to his suprise yaga  an kwashe kusan rabin kud’ad’en. Dubawa dakyau ya kuma yi yaga eh fa kud’in nasa ne babu to waye ya masa wannan d’anyen aiki? Rufewa yayi tare da dawo wa cikin parlon “Ummie” ya kira sunanta.
    “Kin d’au abu cikin d’akina?”
   “Kamar ya abu kuma Anas?”
   “I mean my money morethan half of it are gone.”
   “Wai! Wai! Ka duba dakyau kuwa?”
   “Eh jeki duba kiga” nan ta mik’e ta nufa d’akin nasa. Ganin haka Fannah ta b’arke da dariya har rufe bakinta take, ashe nan ne business na Shettima yake bunk’asa tunda Anas bai gida. Kallon ta Anas yake ya rasa dalilin dariyar tata. Ummie tagama dube dubenta ba kud’ad’en, ko kad’an Anas be kawo aransa Shettima neba.

***
    “Bari in yaran suka dawo zan tambayesu halan sunkai wani wajen daban.” Cewar Ummie dake tsaye bakin k’ofa ayayinda Anas ke k’ok’arin kunna mota. “Okay in Abuu ya dawo ki gaishe min shi.”
   “Toh, amaryar mu semun shigo ko? Mungode.”
  “Yawwa Ummie se anjima” Fannah ta amsata. Acikin motan ne Anas ya juyo yana kallon Fannah. “Dariyan me kuke d’azu?”
   “Da yaushe?” Ta tambaya pretending as if bata gano inda ya dosa ba.
   “Fannah banaso answer me.”
   “Babu kawai daga yin dariya yazama matsala.”
    “Bari zakiyi mafarki ma ai yau zamuga waze zauna dake, infact seperate d’aki ma zan kama.” Jin haka tace, “a’a zan fad’a maka.”
  “Good ina jinki.”
   “All I know is business na Shettima ya bunk’asa.”
  “Kamar ya kenan?” ya katse ta.
   “Oho nifa kar azo ace ina had’a munafirci.”
   “Just tell me.”
  “Promise barakayi reacting akai ba?”
  “I promise.”
   “Nide naga Afrah da 6s plus kuma tace Shettima ya siya mata.”
   “6s plus?” Ya tambaya tare da juyowa yana kallon ta cike da mamaki.
   “Anas kalli gabanka please kar ka bugamu ko mu fad’a rami.”
   “Wato da kud'i na aka sai wa Afrah 6s plus d’in koh? Da kud’in mijinki shine kike dariya. Da kyau zamu had’u dashi.”
     “Toh me zanyi? Shida kud’in yayansa. Plus a’a Mr. Fauzi kaga you promised you won’t react.”
   “So kike inyi shiru in zuba masa ido? Ya kwashe morethan half of kud’in dake cikin safe d’ina fa.”
  “Hak’uri zakayi he is in love kuma dan baida aikinyi ne, let them be please, kaji Mr. Fauzi.”
   “You really wants to annoy me ko Miss Aleeyu?”
   “A’a Anas toh, nide kar ka masa magana.” Chan k’asa k’asa yace, “barin masa magana ba kamar yadda barin canza masa motar sa ba kuwa”
   “Yafi amman dekam karka masa magana.” tache.

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 58
BY MIEMIEBEE


Cikin baccin tace, “Anas dan Allah kar ka tafi please.” Alokaci guda kuma yaji wani irin tausayinta ya kamasa, bacci take amman idanunta basu bar zuban hawaye ba. D’ayan hannunsa yasa ya share mata hawayer. “Bar kuka kinji? I’m here.” Hannunsa ya raba da nata na k’arfi ganin yadda ta kama nasa gagam. Firgit ta tashi tana hawaye “Anas please don’t go.”
   “Ba tafiya zanyi ba Fannah” ya sanar da ita a lokacin dayake k’ok’arin kwantar da ita kan k’irjinsa. Bayan ya kwantar da itan ya soma shafa bayanta yana kwantar mata da hankali.
   “I’m here ba tafiya zanyi ba kinji?” Kai ta gyad’a cikin tsoro. Chan yaji nauyinta ya dad’u a kansa, beyi yunk’urin d’agata ba, barinta yayi ta cigaba da baccin gudun kar ya tayarda ita.

    Tunanin me yake sata mafarki haka yake. Waye mutumin? Mesa take kuka? Me ya tab’a mata? Me kuma take tsoron ze sake yi mata? Mesa kullum take irin mafarkin? For how long take erin wannan mafarkin dayake mugun tsorata ta haka? Me wannan mutumi ya mata? Har bacci yayi gaba dashi besamu amsoshi ga wad’annan tambayoyi ba.
    Asubar fari Fannah ta tashi a hankali ta bud’e idanunta, hannunta taja daga kan cikin Anas a hankali. Ta rasa meke sata mafarkin mutumin kullum kwana biyu, a da ne da abin yafaru take mafarkin kullum but as days passed by tadena yi kullum setayi kwana uku ma wani sa’in batayi ba amman tunda tayi aure takeyi kullum yanzu, kuma na yanzu yafi nada kayan ban tsoro. Me dalili? Bata kawo wani tunani a ranta ba ta miqe tayi alwala har a yanzu tsoro takeji mafarkin jiya yafi kowanne abin tsoro bayan tafito ta yi musu shimfid’a sannan ta tada Anas.
    Sun idar da Sallansu sunyi Azkhar suka koma kan gado. Pillow’nta ta matsar baya daga nasa tare da duk’unk’unewa cikin hijabinta tana kallon d’ayan side d’in. Anas ya karanchi hakan, yagano har yanzu tsoro takeji ga rashin maganar da takeyi yau kamar ba ita ba. Tausayinta yasake ji ya kama sa making him so anxious jin labarin mafarkin nata.
 
      “Fannah” ya kira sunanta cikin wani irin salo.
    “Na’am” ta amsa ba tare da ta juyo ba.
    “Are you still scared?”
   Kai ta girgiza masa tana matse ‘yar k’wallarta batadamu ko yana kallonta ko a’a ba.
   “I’m here for you kinji? Kibarjin tsoro ba mutumin da ze zo.” Yayi assuring nata. Kai ta gyad’a.
   “For how many months now kike mafarkin?” Bata masa k’arya ba tace, “7 years now.”
   7 years? Ya nanata a ransa, Allah sarki poor Fannah. “Turn and look at me.” Ya buk’ace ta. Ba gardama ta juyo hawayen da take ta k’ok’arin matsewa ne suka soma gangara. Hannunsa ya bud’a mata “come.” Matsowa tayi kusa dashi cije da tsoro, kanta ya aza a kan k’irjinsa. “Everything is going to be alright kinji? Stop crying.” Hannu yasa ya share mata hawayen. “Do you want to talk about the dream?” Kai kawai ta girgiza masa.
  “Even now that I’m your husband?” Ya tambaya cikin wani irin demanding salo. Kuka ta fashe da, “Anas nima bansani ba anytime na kwanta kawai se inji wai wani mutumi yazo yana bina ze gudu dani.” Ta masa k’arya dan battason sanar dashi sirrinta.

   “Shhhh! Is okay bar kukan, lets sleep.” Hannunta ta zagaya akan cikinsa ayayinda yake ta shafa bayanta har tayi bacci.

  **
    Da misalin k’arfe 10:00AM Fannah na zaune shiru kan cushion, game data saba yin ma tak’iyi yau. Yanzu suka gama breakfast da Anas. Observing nata yake tun da suka tashi haka take ta acting strange, ya rasa me ze mata koda ya mata magana amsarta befin ‘eh’ ko ‘a’a’. “Fannah” ya kira sunanta a nitse. “Na’am” ta d’ago kai tana kallonsa. “Kinason kifita yau?” Kai ta girgiza masa da nufin a’a sekace ba ita ba..
     “In kaiki wajen Mami?” Batasan lokacin da ta saki murmushi ba “eh” ta basa amsa cike da jin dad’i. “Lets go then.” Dama abaya ne a jikinta, gyalenta ta d’auka tayi rolling tare da feffeshe jikinta da ture haka shima Anas d’in.
   
    Hannunta rik’e cikin nasa suka fice motan ma shiya bud’e mata da kansa ya rufe bayan ta shiga. Zaman tsit suke cikin motar chan da shirun ya masa yawa yace, “mesa bakisha ice cream naki ba? Bakiya son flavour’n ne?”
    “Inaso.”
   “Mesa bakisha ba toh?”
   “In muka dawo zansha in shaa Allah” ta amsa sa a takaice. Shiru ne ya sake ratsa su chan yace, “I miss your coffee” sincerely. Kuma hakan ne rabuwansa da coffeen ta he can’t even remember.
    “Muje office naka ko painthouse in had’a maka.” tace. Duk wannan magana da suke bata juyo ta kallesa ba shiko fuskarta yakeson kalla dan tayi kyau sosai, maroon jan bakin data sa ya mugun amsarta dukda kuwa fuskarta yad’an kumbura dan kukan data sha jiya dakuma yau da safe.
 
    “Fannah look at me.” Ya buk’ace ta ba musu ta juyo. Murmushi ya saki mata daga heart nasa, “kinyi kyau.” Murmushin ta mayar masa “thanks and you too.”
    “Nikam ai kullum ina yin kyau” ya gwada janta da surutu.
   “Yes Anas, kullum kanayin kyau.” ta fad’a tare da miyar da kallonta gare da windon. Daga yadda take maganar ya karanchi batason surutu. Be sake tuhumarta ba dan bayyason tak’ura mata, abinda ke damunta kad’ai ma ya isheta. Enterprise nasa suka nufa ya bud’e mata k’ofar dan neman magana ba rik’e hannunta yayi ba wannan karan. Hannun nasa ya zagaya a waist nata tsam ya matso ta jikinsa suna shaqan k’amshin turaren juna. Ko uffan batace masa ba, duk abinda zeyi yayi atleast sunada aure yanzu ba zunubi. Tun shigarsu cikin Enterprise d’in ake ta congratulating nasu. Bayan sun shiga office nasa ya zauna kan couch a yayinda ta ke had’a masa coffeen ba abinda yake banda binta da kallo, flask dam ta cika masa tare da sa masa cup ta kawo masa. Hannunta yaja ta zauna gefensa.

     “Thank you” yace da ita. Murmushi tamayar masa as a reply. Bayan ya kurb’e rabi yayi pausing. “Kefa zakisha?” Kai ta girgiza masa. “Why?” ya tambaya.
    “Toh ka tab’a min tayi neh?” Ta amsa tambayarsa da tambaya, abinda ya tsana kenan.
    “Da biyu kikayi hakan koh?”
  “Meneh?” Ta juyo tana kallonsa.
   “Again! Aswering my question with another question.”
   “I’m sorry Mr. Fauzi na manta rules naka ne.” Cup nasan ya mik’a mata da ragowar coffeen ciki. “Shanye lets go.”
     “Se wanda kasha zaka bani?”
  “Admit it Fannah kidena so kina kaiwa kasuwa, tunba yau ba kike kallona in ina shan coffee kinason sha daga cup d’ina. Na baki yau so kisha.”
   “Oh please Mr. Fauzi girman kanka yayi yawa wallahi, I pity duk wata macen dazata aureka.”
  “Kema haka I pity duk wani mijin da ze aureki, kisha lets go.”
   “Ni barin sha ba” ta fad’a stubbornly.
   “Okay shikenan tashi mukoma hotel namu toh, da rabon bakison ganin Mami.”
    “Haba! mana Anas me had’in shan coffee na da kaini gida gun Mami kuma?”
    “Nima bansani ba all I know is that sekinsha zan kaiki.” Harara ta watsa masa aiko yaganta.

    “Ni kike harara ko me ake kiran abun?”
    “A’a nifa ba harararka nake ba abu nagani agashin ka” ta masa qarya, nan tasa hannu cikin gashin nasa seyi take kamar tana cire abu. Chan taciro hannun nata. “Ina abun?” Ya tambayeta.
  “Na yasar.” Yasan sarai k’arya take kawai ya mata murmushi. Coffeen ta kurb’e tas ashe de da dad’i. Zata iya irga so nawa take shan coffeen befi sau uku ba dana yau kenan, gaskia she have been missing. Harshe taciro ta lashe lips nata. Kallonta yake in a cute manner.
   “Zaki k’ar” Sarai yasanta da ci zatace eh aikuwa ta gyad’a kai.
   “Toh baraki k’ara ba ai nawa ne tashi mutafi.”
   “Toh Anas I will make another one.”
   “Zaki b’ata min lokaci mutafi.”
   “Anas please.”
  “Fannah please lets go.” Haka Anas ya hanata shan coffeen. Ahmad yasa ya sauk’o masa da coffee machine da flask nasa ta yadda zata na had’a masa coffee always.

    Bayan isarsu gidansu Fannah ta ruga a guje tashiga da Mami ta soma cin karo hugging nata tayi har tana hanata nishi. Bayan sun zazzauna Mami ta kawo musu d’anwake me rai da lafiya yasha had’i kam. Bajewa Fannah tayi taci kamar ba gobe sekace wacce batayi breakfast ba kallonta kawai Anas yake ko tab’a nasa beyi ba saboda he is not a fan of d’an wake be iya ci ba, inma zeci sede ya tsotse zak’in kawai.
    “Baba na ya baka cin naka?” Mami ta tambayesa.
    “Bakomai Mami kawai ban iya chi bane, I'm sorry.”
   “Su Mr. Fauzi ajebo, gaba takaini” Fannah tace chan k’asa k’asa yadda Anas kad’ai dake kusa da ita ya jiyota. Ignoring nata kawai yayi. Plate nasan taja ta soma chi bayan data k’are nata.
   Afrah da Mami kam baki suka bud’e suna kallon ikon Allah. Cike da kunya Mami tace, “haba Fannah taya zaki d’au nasa kuma.”
   “Mami bakiji me yace bane? Cewa yayi baya ci, ajebo ne shi.” Cike da mamaki Mami ta bud’e baki zata masifeta. Da wuri Anas ya katse ta, “A’a Mami barta please, chi abin ki kinji?” Taci morethan half of plate nasa sannan tajita dam.
    “Mu tafi koh?” Ya tambayeta. “Mami zamu koma inason mu gaida su Ummie ma.” Kafin Mami tayi magana Fannah ta rigata. “Tafiya kuma Anas? Na d’au fa zaka ajiye ni ne kayi tafiyarka se anjima kadawo ka d’aukeni.”
   A ransa yace dake driver’n kine niba?
 
    A fili yace, “Fannah sweetheart kinsan zamuje mu gaishe dasu Ummie fah, ba time.” Ganin zasu fara muse-musen ma’aurta Mami tayi excusing kanta tare da jawo Afrah ma suka basu space.  
  Ganin haka yace, “Driver’n kine ni ai da zaki sani jeka ka dawo, tashi mutafi, aikinga su Mamin.”
   Fuska ta maraice “ayyah amman banga Baba ba fa yana bacci. Yi hak’uri please kabarni in wuni anan wallahi chan ba dad’i.”
    “Ohonki tashi mutafi, ina ni kike cema ajebo kina zagina, stand up lets go.”
   “A’a I take that back dan Allah kayi hak’uri.”
   “Nak’i tashi mu tafi.”
   “Anas please” ta shakwab’e fuska tana murza ido. Yasan sarai zata iya fashe masa da kuka anan. Nanne mami ta fito daga d’akin. Ganin ta cika hawaye a idanunta yasa hannu tare da rik’o fuskar natan, “muga yafita?” Iska ya hura mata a idon “sannu ko?” Kai ta gyad’  “eh ya fita.” Chan k’asa k’asa tace, “ka yarda?” Harara ya galla mata tare da gyaran murya.

    “Uhm Mami zan tafi , zan bar Fannah anan I’ll be back in d’auketa.”
   “Toh toh yayi kyau sannu ko Baba na?” Dad’i sosai Fannah taji sebinsa da kallo take har yasa takalmansa. “Adawo lafiya baby.” Juyowa yayi tare da sakar da best smile nasa. “Thank you” sannan ya fice.
   “Soyayya ruwan zuma...” Cewar Afrah tana gyad’a kai. “Su wani baby kuka samu sara?” Banza da ita Fannah tayi seda Mami takoma d’aki bakin Fannah ya bud’u. “Amman ke mena cemiki? Bance karki samin english wears cikin akwatunan da zan tafi dasu ba?”
   “Toh meh? Ai naga da english wears ake amarchi” nan ta kewaya taga ba Mami “Ya Fannah ya first night d’in? Kinyi kuka?”
   “K’asaran ki maras kunya kawai nima bansani ba.”
   “Heheh!” ta sheqe da dariya, “Toh Allah kawo zuriah d’ayyiba yasa du sharpshooters ne” nan iphone nata yayi k’ara alaman shigowar message. Tana bud’ewa taga airtime ne na dubu biyu hot baby nata yamata sending. Bayan tayi replying nasa tace a fili “Allah bar min kai yau akwai flexing a instagram da kallon stories a snapchat.”

      Har yanzu Fannah ta kasa rufe baki a iya sanin ta de Iphone 5s ce wayar Afrah how comes take rik’e 6s plus yanzu?
    “Ke ina kika samu wannan k’aton wayar? Waya baki?”
    “Wanne wai?” ta tambaya cike da tsiya. “Awww Iphone d’ina? Hot baby ya siya min wallahi, yayi kyau ko?”
   “Hot baby wa kenan?” ta kuma tambaya cike da rashin fahimta.
   “Wa kuwa inba Shettima darling ba, business nasa se bunk’asa yake wallahi.”
   Dariya sosai Fannah ta sheqe da dan tasan ina yake samun kud’in daya ke kashe mata. “Shi business d’in kenan?”
  “Eh mana abin hassada ne kuma?”
  “A’a babyn Shettima Allah barku tare ni taho ki tayani in shirya atamfofina gu d’aya dasu zan koma.” Afrah ta bud’e baki zata kuma wani zancen Fannah ta katse ta “a’a banason bayani muje.” Suna hira suna shirya kayakin har suka gama.

11:30AM

    Daidai nan Anas ya dawo d’aukanta beso sake shiga ba se kawai ya kira ta ta waya alokacin wayar tata na d’akinsu itako tana d’akin Baba se hira suke bazawa kamar ance ta mik’e tace bari taje d’aki. Tana shiga taji rurin wayarta nan ta d’aga tare da duban waye. ‘Anas’ taga tubuce kai. K’in picking tayi dan battason sake komawa hotel nasun nan its so boring. Se a karo na biyu ta d’aga nanma seda ya kusa tsinkewa.
    “Kifito I’m waiting for you.”
   “Anas mana please, bamu had’u da Aiman bafa, tana school se 1:00AM zata dawo kaji? In jira?”
   “Banji ba kuma baraki jira ba, Fannah kifito don’t let me repeat myself.” Karap ya katse wayar, tsuka taja. Aiko ya fad’a kunnen Mami. “Keda waye ne?”
  “Erm.. Ermm...” kafin ta had’o k’arya Mami tace, “keda Anas ko? Fannah tun ba’ayi nisa ba kin soma masa rashin kunya, iyyeh? Me dalili?”
   “Mami waifa har ya dawo infito mu tafi.” ta fad’a tana turo baki.
   “Toh se meh? Out!” ta nuna mata k’ofa. Dake kafad’a tayi. “Fannah zan sab’a miki fa!” Haka kamar wacce zatayi kuka taja akwatinta ta fice ko sauraron Afrah batai ba. Bayan fitarta ta bud’e gidan baya tasa akwatin yana kallonta bece komai ba. Tana shiga ya kunna motar ba wanda yace ma wani ko uffan. Bayan isarsu gida suka gaggaisa, Ummie kamar ta cinye Fannah. Besamu ya had’u da Amal ba dake tana school haka Shettima ma.

     “Kuyi sauri ku gama gaisawan ku zan d’au abu cikin d’akina ne yanzu mukoma.”
     “Kai Babana daman ba yini kuka zo mana ba?”
   “Yini? A’a fa Ummie gaisuwan minti biyar ne kacal.” Yana kaiwa nan yashige d’akinsa. “Oh! Fannah kinga halin mijin naki ko? Yafiye rowa dayawa.” Murmushi cike da kunya ta saki tana kare fuskarta.

     Bayan shigan Anas d’akinsa ya nufa wajen safe dan ciro kud’ad’ensa wanda ze buk’ata to his suprise yaga  an kwashe kusan rabin kud’ad’en. Dubawa dakyau ya kuma yi yaga eh fa kud’in nasa ne babu to waye ya masa wannan d’anyen aiki? Rufewa yayi tare da dawo wa cikin parlon “Ummie” ya kira sunanta.
    “Kin d’au abu cikin d’akina?”
   “Kamar ya abu kuma Anas?”
   “I mean my money morethan half of it are gone.”
   “Wai! Wai! Ka duba dakyau kuwa?”
   “Eh jeki duba kiga” nan ta mik’e ta nufa d’akin nasa. Ganin haka Fannah ta b’arke da dariya har rufe bakinta take, ashe nan ne business na Shettima yake bunk’asa tunda Anas bai gida. Kallon ta Anas yake ya rasa dalilin dariyar tata. Ummie tagama dube dubenta ba kud’ad’en, ko kad’an Anas be kawo aransa Shettima neba.

***
    “Bari in yaran suka dawo zan tambayesu halan sunkai wani wajen daban.” Cewar Ummie dake tsaye bakin k’ofa ayayinda Anas ke k’ok’arin kunna mota. “Okay in Abuu ya dawo ki gaishe min shi.”
   “Toh, amaryar mu semun shigo ko? Mungode.”
  “Yawwa Ummie se anjima” Fannah ta amsata. Acikin motan ne Anas ya juyo yana kallon Fannah. “Dariyan me kuke d’azu?”
   “Da yaushe?” Ta tambaya adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *