Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Saturday, January 25, 2020

Dijah Qaya Complete Hausa Novels

adsense here
Dijah Qaya Complete Hausa Novels
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
   

*MY* *NATION* 🇳🇳🇬

*ISLAM MY RELIGION* 😘🕋




 _wata rana an atambayi Manson (S. A. W) "Mene ne  Hak'uri ? Sai manzon  Allah (S. A. W) yace "  juriya kan bak'in ciki, yin raha ga mak'iya, Barin mummunan zato, cire Girman kai, karb'an uzuri agun da Kasan babu gaskiya, hak'uri a inda kakeda karfin ramawa, yafiya ma Wanda ya cuce ka, kyautatawa ga Wanda ya kyautata maka_ _(ya ubangiji kabamu ikon yin aiki da dai dai Ka gafartamana kura kuranmu)_


🌈 *KAINUWA WRITTERS ASSOCIATION* ..........✍🏻


           *page* 5⃣



Tuk'i yake cike da nitsuwa yana bin k'ira'ar sheikh Abubakar shad'iri cikin suratul Namli, har ya iso gida, kai tsaye pert d'insa yanufa,


Akan wani kujera da akayi da sumunti wandayake farfajiyan waje ya hango Sani yana kishingid'e,


Cikin takunsa na isa da izza yak'araso wajensa, yasa hanu ya d'aga hulan da ya  rufe fuskansa dashi "kai bacci kakemin anan? D'an k'aramin tsaki Sani yayi " dole kace hakaman tunda ka shanyani anan, murmushi kawai Kabir yayi yashige falonsa


Wanka yayi ya shirya cikin riga da wando na wani yadi milk mai laushi ya fito da hanu yayi ma Sani alamun yazo,  suna daf da shiga pert d'in Mami Sani yace "wlh kunyan yanda kake sani muke  k'arya  ma mami nake ji


Haba oga meye amfanin kadinga hanamu fita dakai alhalin mami bata saniba,


 

Kabir yace "to wai Sani mezaku tsaremin ne? Duk Abunda Allah ya k'addara zai faru dani bawani mahaluk'i da ya isa ya hana,




Ni ka ganni kullum cikin Addu'a nake ba abunda zai samen insha Allah,


Ba wai cewa nayi zamu hana wani Abun yasamekaba amma ai atleast zamu kula da motarka dalilin da yakawoni garinnanfa kenan gadinka pls oga kabari mudinga take ma baya ko bakomi da muzaburar da mak'iyanka,




Murmushi kawai Kabir yayi batare dayace komiba suka shiga falon Mami,


Afalon suka tarar da Habib da Mum d'insa tare da Mami,


Mum tana ganinsa  tace "yauwa Kabir gwanda da Allah yadawo da kai tun bantafiba, zoka zauna anan tanunamasa gefen da Habib yake zaune, nan yazauna yana sunkuyar da kai yana murmushi

Sani ya tsuguna ya gaidasu yafita mum takalli Kabir da Habib dasukayi tsilli tsilli da ido tace " kukuma  abunda kukaje kuka aikata kenana?


Daga turaku zance  sai kuje kuyi rashin arzik'i? Kuje kusa yarinya agaba kuna mata dariya da rainin hankali?


Mami da bata san me yafaruba, cikin rashin fahimta takalli mum zance kuma?



Nan mum ta zayyane mata duk yanda akayi Mami tahau tafa hanu tana salati mai had'e da dariya,



ai hajiya don bakisan waye Kabir bane shiyasa kikasashi cikin wannan hidima ai koda bakinsu ba d'aya bane indai da Kabir akaje to zance ya b'aci ba abunda ya iya kinganshinnan,  sai shirme,

Mum tace "ai bakinsu d'ayama "yar wajen Aminiyatace hajiya sadiya naturasu dama Akwai wata k'awarta kusa dagidansu yarinya mai hankali shine nace dagana kuma suje kabir ya ganta

Shinefa uwar Amira tak'irani take shaidamin yanda akayi

 Tam yanda kuka je kukayi shirirta haka zaku koma kuje ku gyara saurankuma inji wani abu nida kune       Tafad'a tana mik'ewa bari mu wuce daman zani can gidan yaya ne nace barinzo mu gaisa kwana biyu


Naji dadi sosai, har bakin mota tarakota.


🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴
 Alhaji Ya'u ne k'anin mahaifin Kabir ne wanda suka had'a uba da shi, zaune atanka memen falonsa, tunaninsa d'aya shine yazayyi ya kawar da Kabir aduniya don ya mallake tarin dukiyan da mahaifinsa ya rasu yabar masa.

   Tun Alhaji mahmud na Abba naraye k'anin nasa yake farautar dukiyansa duk da kawaici da kara gami da kyautatawan da yake masa, sosai yasha Alwashin ganin k'arshe yasha kai ma rayuwansa hari Amma Allah bai k'ddara mutuwansa ta hanunsaba.

   Alhaji mahmud haifaffen jahar mai dugurine hark'an kasuwanci ne ya kawoshi jahar Adamawa, wanda Anan Allah yahad'ashi da Fatima bafulatanar asali ba b'ata lokaci  akayi musu aure don dama Alokacin tagama karatunta, 


  Bayan shekaru uku da aurensu Allah yabasu da'nsu muhammad kabir, alokacinne ya dauketa ya kaita garinsu mai duguri don t mahaifiyarsa tace ya kawota tayi wankan gidan awajenta.

 To awannan lokacinne ya'u yanuna sha'awan bin d'an'uwansa  su dawo yola dazama, mahaifinsu malam Rabi'u wanda su kadai Allah ya baiwa don tun bayan haihuwan mahmud mahaifiyarsa bata ka'ra haihuwaba, mahaifiyar ya'u kuma tun bayan haihuwarsa ta tarasu ta barshi ahanun kishiyanta bata masa rik'on d'an kishiyaba tamishi rik'o tsakani da Allah.





  Bayan sun dawo Adamawa dashine yasahi ahark'an kasuwancinsa inda ya bashi manajan kamfanoninsa sannan ya mishi aure ya bashi k'aton gid.


   Tofa tundaga wannan lokaci da Alhaji ya'u ya fara tashen kud'i yaji yana son kawar da wansa don ya mallake duka dukiyansa kafin d'ansa ya taso kullum planing d'inda suke k'ullawa da matarsa kenan yanda zasu kau dashi aduniyan ma baki d'aya.


 (Kai d'an Adam Allah yasa mufi k'arfin zuciyarmu, idan kabi ye ma son duniya ba abunda bazaka aikataba)



  Mahmud bawan Allah shikuma duk tunaninsa shine yanda zai k'ara taimaka ma d'an'uwansa da dangin mahaifiyar sa, ahaka Allah yakarb'i ran mahaifinsu malam Rabi'u.





 Fad'in tashin hankalin da suka shiga bazai yiwuba bayan sati bayanda Alhaji mahmud baiyiba akan yadawo da mahaifiyarasa kusa dashi fir tak'i tace yabarta kusa da "yan'uwanta,


  Haka yadawo yabarta sai dai yana yawan ziyartanta akai akai.



  Kabir yana da shekaru takwas Allah yaba Mami ciki, ai randa Balki matar ya'u taje ta gani ba k'aramin tashin hankali ta shiga tana dawowa ta sanar da mijinta ai shikamma kasa bacci yayi shawara tabashi akan suje gidan boka su sa ya zubar da cikin , sosai yaji dad'in shawaranta ba b'ata lokaci washi gari sukaje aka gama  komi boka ya basu magani yace lalli susa mata a abunci bama zata sake haihuwanba.


 (Iko sai Allah duniya abun mamaki)


    Bayan Kabir yagama secondary ne Abbansa ya kaishi England anan ya karanci medicine alokacin Alhaji ya'u yana da yara biyu Aminu, da Nafisa yawanci idan yazo hutu anan yake samun Nafisa tazo wa Mami hutu Allah ya had'a jinin Nafisa da Kabir sosai tun alokacin duk dashi ba wani mai sake da yawa bane.


  Bak'aramin kulawa da gata gami da soyyaya Kabir yake samuba  awajen iyayensa, wanda hakan ba k'aramin k'iyyaya yak'arama Kabir ba awajen Alhaji ya'u


 Sosai Alhaji mahmud yaci buri akan tilon d'ansa,

  Wani hutun Kabir da ya k'arene Abbansa da kansa yatuk'ashi yakaishi air pot bayan ya masa "yan Nasihohin da yasaba masa ako da yaushe inzai koma makaranta sukayi sallama kowa da Abun da yake sak'awa aranshi na alhinin rabuwa.


  Ahanyansa na dawowa yafito kwanan unguwansu kenan kasancewan gun ba mutane da yawa kawai yaji tayarsa ta sace, gangarawa yayi don yaga mai ke faruwa kafin ya bud'e motar  yaji anrigashi wasu matasa ne su hud'u fuskokinsu a rufe suka bud'e suka shiga d'aya ya zauna agba ukun suka zauna abaya gaba d'ayansu suka saitashi da Bindigogi wanda yake zaune agban yace "Alhaji aikomu akayi mu kasheka amma kaga mu kud'i muke nima ba ruwanmu idankaga zaka fanshi kanka da kud'i sama da wanda Aka bamu mukasheka shikenan sai mubarka da ranka inkuma bazaka iyaba ashirye muke mu Bindige ka anan muyi tafiyarmu.




  Murmishi yayi sosai saida hak'oransa suka bayyana yace "yanzu nid'innan har akwai wanda natsole ma ido?
Zai iya ba da kud'i akasheni?
Wanene wannan?
Don Allah ku gayaminshi,
 Me nacimasa?
   Me rayuwata ta tsaremasa?
  Me yake nima da bazai samuba sai in bana duniya?


Alhaji kana b'ata mana lokaci da tambayoyin da bamu san Amsosinsuba,  kafad'amana zaka bamu kud'inne?
Ko mu kasheka muje mukarb'i nashi?

  Ajiyar zuciya ya sauk'e sannan yace "zan baku Amma don Allah kugayamin wanda ya aikoku?.


 Tsawa ogansun yadaka mishi bazamu fad'a maka wanda ya yaturomuba, 
"ok to nawa kuke so?
50 million atake ya d'auko chek ya rubuta ya basu,


  Bayan tafiyansu yajima zaune acikin mota yana   mamakin wannan Abu,  daga bisni ya ja motar jiki ba k'arfi yanufi gida,


  Afarfajiyan gidan yatarar da Alhaji ya'u yanata lissafa yanda zaishiga cikin d'akinsa ya d'auko decument d'insa na kadarorinsa, don jira kawai yake amasa waya ace masa gashi antsinci gawan d'an'uwansa.


  Afirgice ya k'uramasa ido lokacin da aka bud'e masa gate ya shigo da mota har yayi perking ya fito ya nufoshi bai saniba tsaban firgici don yagama taget a yau zai mallaki dukiyansa gaba d'aya "Ya'u lfy kuwa naganka haka? Muryansa ta katsemishi tunani, 

  "A'a ba komi har  ka kai Kabir d'inne? Eh kawai yabashi Amsa,  "mushiga mana,  "a'a zan wuce ind'uko yara a makaranta yau drivernsu bayanan yafad'a yana shiga mota,



  Alhaji mahmud yaso ya fad'a wa matarsa abunda yafaru saidai baisan yadda zata d'auki abunba gudun kar yatayar mata da Hankali yasashi yin shiru da bakinsa bai fad'a ma kowaba sai dai ya duk'ufa da Addu'o'i ba dare ba rana.


"Allah sarki rayuwa,   duk yadda ka kai da jindad'i ko wahala a duniya wata rana zai  wuce, haka duk yadda ka kai da  so ko k'in mutum watarana sai awayi gari  bakanan ko shi bayanan.


Ahaka cutar ajali takama Alhaji mahmud yayi jinya na tsawon wata uku, sannan ya Amsa k'iran mahaliccinsa,

 innalillahi wa inna ilaihirrraji'un Allahumma ajirni fi musibaty hazih wakhlifni khairan minha, 
Abunda Mami take ta fad'a tana maimai tawa kenan lokacin da take rungume da gawan mijinta hawaye na d'iga d'is d'is akan fuskansa  yana daga cikin wasiyyan da yamata kar tayi kukan da yasb'a ma shari'a bayan yabar duniya.


 Mutuwar Alhaji mahmud ta girgiza  illahirin garin Adamawa da kewayanta, don mutumne da ko  had'uwa kukayi ahanya  zaka bada lbrn nagarcaccen halinsa Akwaishi dakyauta, da tausayawa ma nak'asanshi aranan mutanen maiduguri suka iso har da Ayye mahaifiyarshi wayyo karkaso kaga koke2 agidan .


  Yana da kwana uku Amininsa Alhaji jamil ya tafi England yazo da Kabir, tun ajirgi Zuciyan Kabir yake ta harbawa  duk da dabara da tsarin da Alhaji jamil ya mishi,  lokacin da suka shigo gidan komi yagama kuncemasa, hanun Habib abokinsa yakamo wanda yake d'a ma Alhaji jamil d'in cikin tashin hankali yake magana pls Habib tellme meke faruwa da mahaifana? Ina Dady da Mami na?  Alhaji jamil yarik'oshi ya kaishi har gaban Mami kallo d'aya yayi ma Mami ganin yanda tadawo bak'aramin tashin hankali yaje fashiba,
Yadurk'usa ya kamo  hanunta


 Idonsa  sunkad'a sunyi jazir "Mami Dady ne, ko shine yatafi ya barmu? Mami yanzu Dady ya.....  Cikin kuka tasa hanunta ta rufe masa baki ta shiga masa nasiha mai ratsa zuciya.


 Sai da Kabir yayi wata biyu, kafin yakoma da rad'ad'in rashin mahaifinshi.



            *Mundawo lbr*





 Yajima yana tunani sannan yak'ira wayan yaronsa kila,
 bayan sun gaisa, yace "kila inason kazo muyi magana na k'arshe akan yaronnan, nagaji da wasa da hankalin da yaranka suke min,


 wancan karon kud'i na baku mai yawa amma kuka kasa kashe shi.


 kila yakece da dariya haba dai oga ba kasa kasheshi mukayiba,
 bom d'inne yayi saurin tashi da motar tunkafin yashiga,
 amma wannnan karonkan namaka Alk'awarin baza'a samu matsalaba,


















*tofah wai shi taya d'an Adam zaiyi mawani bawa abunda mahallicinsa bai masaba kodayake komi yana da sanadi wai ina lbrn Dijah k'ayah ne*

*Kubiyoni UMMU FATIMA🇳🇬😘*
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
            *DIJAH QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
   *BY ASMA'U GALADIMA* 🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿           
 
🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋




*OH* *ALLAH* *HELP* *MY* *COUNTRY* 🇳🇬
  *AND* *MY* *RELIGION*🕋




      *PAGE*⏯1⃣


*DASUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JINQAI*


    Likita! Likita!! Likita!!!
 Wani dattijon Bafulatani ke fadi, sanye yake da Riga da wando "yar Shara light green irin wanda mazan fulani ke sawa  da hulansa malfa wanda akasaka da kaba bakin takalmine kwafta na roba akafanshi yana rataye da Goran ruwansa a wuyansa da sandansa ahanunsa farine shi kal har yana Kore Kore kyakykyawa dashi, kallo daya zaka masa ka fahimci tsananin damuwan da yake ciki

gudu gudu yakaraso jerin dakunan ganin likita yana kokarin kutsa kansa sai dai cincirindon mutanen da ke zaman bin Layin ganin likitan ne yasa shi yin turus awajen yana kalle kalle

Daga dan gefe ya hango wani daki guda daya bai da layin mutane sosai ahanzarce ya nufi dakin baiyi wata wataba ya murda handle din ya shiga, wani matashi ne zaune akan kujera yana sanye da jeans  blue da shirt light pink da lapcoat asamanta da fari kal din glass manne a idonsa matashin dan kimanin shekaru 27 fari ne shi amma ba kalba yana da kyau sosai, Rubutu yakeyi, gefenshi wata nurse ce tana shirya files
 agabansa,

yakaraso gabanshi yana fadin
Likita likita "yata zata mutu don ALLAH kataimaka min kazo ka dubata,


Dasauri likitan yadago kai yana kallonshi ganin yanda jikin sa yake barine yasashi yatashi ahanzarce yana kokarin fita daga cikin kujeran zamanshi yace " ina take? Da yatsa ya nuna masa hanyan waje tana can jikin mota Doctor, Don Allah ka taimakeni kar in rasa ta bata ko iya tsayuwa,

Doctorn ya dubi nurse din da take shirya folder yace " sister jeki shigo da ita, cikin girmamawa tace " Ranka ya Dade ba nan ya kamata yakawo taba G O P D zai kaita in suka duba suka ga case din yafi karfinsu sai suturosu nan,  "no problem sister shigo da ita kawai ya fada yana kokarin zama,

 ta karasa ta dauki well chair tafita gudu gudu dattijon yake binta har suka isa inda yarinyan  take kwance agalaibaice take batasan inda take ba,

 Shi yadagata yasata aciki nurse din ta turo har office din,

 nan ya umurcesu dasu kwantar da ita akan gadon da yake office din,
Ya jawo kwalin hand glovs yazari guda biyu yasa ahanunsa sannan ya karaso gadon yafara dubata kusan minti biyar yana dubata sannan yaja jininta yazuba a "yar  kwalba ya mika ma nurse din yace" sister akai aje amana test yanzu mukeson answer tadan rusuna ta karba tafice, ya dauko srinji yaja ruwan Allura yamata yazare glovs din yazuba a dosbin sannan yakarasa wajen fanfo ya wanke hanunsa yagoge sannan yadawo yazauna sai lokacin yadubi dattijon

yace"  bismillah Baba zauna anan yanunamasa wurin zama, yazauna yana ajiyan zuciya, sabon file yadauko ya bude yayi dan Rubuta sannan ya kalleshi,
Baba meye sunan Mara lafiyan? Yace sunanta Dija Bukar, Doctor yayi dan murmushi

yace Baba Dija ba suna bane, kafadamin asalin sunanta,

haka  muke kiranta yaro, Doctor yakara dan murmusawa  Yace Baba na Asalin sunan ai KHADIJA ne, ko?

Eh hakane asalin sunanta khadija Abubakar, "yauwa Baba adinga cikamata sunanta yafi, "hakane dannan  amma tafi gane Dijan yayi murmushi yace" Meyasa metane Baba? Wlh ciwon cikine yake damunta sannan wani lokaci da daddare sai  jikinta yayi zafi kamar wuta kuma tana yawan kukan ciwon kai ga amai komi taci sai tayi amai, yadanyi rubutu sannan yadago ya kalleshi yace "tun yaushe ta fara Baba?,

"kusan wata kenan tana fama, "wata? Likitan ya fada yana zaro ido "haba Baba wata guda tana ciwo anma ba kukaita asibitiba? " mun kaita wani asibiti can gaba da ruganmu sati d'aya suka sallamemu muka koma gida ba sauki shine muka sake komamusu shine suka turo munan,


Sai da yagama Rubuce Rubucensa, sannan ya kalleshi duk ya diririce sai zufa yakeyi tun kafin yaye magana Baban ya rigashi, araunane yace" Likita me ke damunta? Zata tashi kuwa? Doctor ya gyara zama yace "ka kwantar da hankalinka insha ALLAH zata tashi bansan damuwanba tukun sai ankawo saka makon gwajin sai asan abin yi, daidai lokacin nurse din tashigo ta mika masa result din
Bayan yagama dubawa ya jawo takarda yayi rubuce rubucensa ajiki ya mika masa, yace "Baba wannan magungunan za'asayo, yakarba yana Dubawa " a'ina ake sayarwa? Doctor yayi jim "Baba kaikadai kazone bakazo da wani wanda zai sauna da itaba?  Ni kadaine Likita ba damuwa zan kula da ita Doctor Yadago ya kalli nurse yace" sister hadashi da cleaner ya nuna masa phermercy Baba kazo da kudi? "Eh nazo da kudi sosai ko nawane zan iya saye. Insha ALLAH, "ok to kabi wannan zata hada ka da wanda zai nuna maka wajen da ake saida maganin, tana kaishi ga dawo, tadan  rusuna tace "ranka yadade kana da petaint guda biyar da suke da appointment naganinka yau, yadan lumshe ridonsa yabude, yace " bazan samu daman ganinsu ayauba amma  kidauki files dinsu ki kaima Doctor Habib yadubasu, tadan juya idonta Doctor bakwai guda daya da yake da bukatan ganinka bazaiyuwu yaga waniba sai kai, ok bani filedinsa naga meye Case dinsa? Saida ya duba shi sannan ya tashi yace" , inaso amai da yarinyannan world yanzunnan yafada yana fita, kai tsaye word din Ya nufa yana duba wasu da yakwantar  bayan yadan dubasu yadawo jikin gadon da da'aka kwantar da ita, har yanzu bata cikin hayyacinta, dai dai lokacin baban yashigo da magungunan

Drip ya daura mata sannan ya samata magungunan, yajuyo yana cire gloves din hanunsa yana kallon Baba da ya dogare sandansa ya harde kafafunsa ya kurama diyar tashi ido, saida ya wanke hannayensa sannan yafita can sashin Cosmo ya nufa,

Tunda mama jummai ta hangoshi ta tasi da saurinta tana washe baki don tasan abun nima yasamu, duk lokacin da taga Doctor KB yazo wajen da Duke tasan kakanta ta yanke saka don ba karamin kudi yake bataba ta kula da peteint
Sannu Doctor tafada dai dai lokacin da ta iso wajensa yadan murmusa cikin girmamawa yace "mama karki gaji Dani don ALLAH wani datijjone yazo da "yarshi, anbata gado kuma shi kadai yazo baizo da kowaba,

Da saurinta ta katseshi Lah bakomi likita za'a kula dasu yanda yadace ALLAH dai yasakama da khairan irin wannan taimako da kakeyi,
Baice komiba yajuya ta rufa masa baya

Zaune suka sami Baban yarafka tagumi ya tsura mata ido ,

Doctor KB yace" sannu Baba yadora da zaka iya tafiya yanzu, kaje kayi sallah kahuta ga mama zata cigaba da kula da ita in akwai abun da kake bukata kuma kasanar dani, Baba yadago yana dubanshi yace" bana bukatan komi likita nagode sosai da karramawan da kamin Allah ya maka Albarka, mama jummai ta amsa da Ameen, Doctor KB yajuyo da kallonsa ga nurse ita ma shi take kallo tana mamakin Doctor KB aduk lokacin da wasu daga Kauye sukazo da Mara lfy muddin case din ahanunsa yake sai ya dauki dawainiyansu wasu kamma kacokam din maganin shi zai ke saya yana musu amfani dashi

Sister hadashi da baba Garba yanuna mishi dakin da zai zauna aciki yajuya ba tare da yaji daga garetaba,

Kai tsaye office dinshi yanufa bayan yakammala abunda zaiyi yafito ya nufi word anan ya samu Doctorn da zai karbeshi,

Yafara mishi handing over har suka iso kan Dija da zuwa yanxu ta farfado bacci takeyi Doctor na'im yace " wanna yaushe aka Admitting dinta? KB yazura hannayenshi a aljihu yana kallonta

yace" Da safe aka kawota kuma case dinta serious ne typhoid ne yamata chronicHar yana shirin taba heart dinta ga malaria shima yayi mata munmunan kamu kasan mutanen namu San basa son zuwa asibiti saida ciwo yagama mata illa aka kawota,

 yafada yana shafa sajensa ransa a dagule amatsayinsa na cusaltant Sam baiji dadin ganin result din yarinyanba,

Doctor na'im yagirgiza Kansas cike da takaici yace "ba FULANI bane sam bansan yaushe zasu daina irin wannan haliba, yanzu me yakamata amata? Yajuya yana fita yace" yanzu saidai gobe in Allah yakaimu,

Yana bude motansa ya hango Baba zaune duk hankalinsa yatashi katuwar darduma yadauko abayan motansa yakaraso inda Baban yake agefe ya shinfida masa "yace Baba ga gurin zama nizan tafi gida insha ALLAH zanzo da dare, "likita yaza muyi inkatafi? Yadan murmusa "Baba kanaji  da wannan"yar taka gaskiya
" Ayyah Likita mamatace fa awajen,

Murmushi likatan yayi yace "karkadamu na damqata ahanun wani likita zai kula da ita, yajuya yatafi sai godiya yake masa,

Tun kafin yayi horn masu Gadi  suka wangame gate ya shigo idonsa akan Mami sai sintiri take atsakar gidan dama yayi tunanin za'ayi haka murmushi yayi ya bude Motan da sauri ya nufo wajenta atsakiya suka hadu tayi saurin riko hanunsa cikin damuwa saida takaishi har cikin falo sannan takalleshi da damuwa "Haba Kabir meyasa ? Meyasa ka koro body gaurd dinka? Ka zauna kai kadanka tsawon wannan lokacin awaje? Kasan damuwan da kasani kuwa? Nakasa samun nitsuwa gashi ka kashe wayoyinka Kabir kamanta abun da yafaru abayane?


Yakamo hanunta yana murmushi" bakomi Mami kafin infita sai da nayi Addu'an Safiya da maraice sannan nayi Addu'an hawa abun hawa nakumayi na barin gida ba abinda zai sameni ina da bodyguard din gaske ajkina Mami pls banison kidinga daga hankalinki innafita ni kadai ta sauke ajiyan zuciya "nasanka da sakacine kabir don ALLAH kadinga tayani kulawa dakai, tafada tana shafan Kansa Insha ALLAH My luvly mami
Yamiqe zai fita Mami tace "

ga Abinci fa yana jiranka eh zanyi wanka ne Mami aifa ko kwado haka  yaganka yabarka Indai wanka ne sauran daganan kuma inji shiru nayi magana kacemin aidaga fitowankane bacci ya kwasheka Baka saniba, yajuya  yana dariya har zai fita yadawo yace" Mami akwai wanda za'a kaiwa Abinci Asibiti

"to yau kuma wa kasamo ko mutanenkane?

"no wa incan an sallanesu wani dattijone Mami shi da "yarsa bafulatanine wlh

 yadanyi karanin tsaki yana shafa Kansa Mami tace " meyafaru kuma?

 "tausayi mutumin yabani yana matikar son "yartashi gashi kuma zata mutu tabarshi

arazane Mami tazaro ido "kamar yaya zata mutu ta barshi kabir?

Yadan furzar da numfashi Mami sunriga da sunbarta agida ciwon ya mata illa zaiyi wuya ta tashi,

cikin damuwa Mami tace "wannan na ALLAH ne kabir karkasake fadin haka aqidankune kawai na likitoci amma tsananin ciwo bai kawo mutuwa,

yadaga kafadanshi alamun shikenan yana tafiya yana fadin Mami da ALLAH ashirya akai musu yanzu mama jummai tana wurin "ok yanzu za'akai,

 yashiga part dinsa yana balle maballan rigansa akayi knocking yabada izini aka shigo sai da yazanme rigan sannan yajuyo suna hada ido da sani yaballamasa harara, yana dariya ya karaso har gabanshi yace" haba KB me kuma nayi?

Cikin dakewa yace" Haka mukayi da kai? Bance karkabari Mami tagane kunbarni a can kundawoba? Shine har da cemata na koroku ko?
"No bahakabane KB akwai matsalafa sosai cikin barinka kai kadan, yadora hanunsa kan bakinsa "shiittt Sani kudaina wannan tunanin abunda yafaru ya wuce kuma ma wancan lokacin da akasa bom amotana ai ba a asbiti bane kamanta can wajan meting din campani ne? " To inbanda KB kasan daga ina aka biyoka? Ai ko ba komi xamu kula da motanka yanda baza'a samu daman samaka wani abunba pls kaba Mami hadin kai wajen kiwon  lfynka

, "mmnhh naji jeka zanyi wanka ne kai dama ba aikin soja kazaba da low kayi dan kafi dacewa dashi parrot kawai, yafada yana shiga bed room Sani kuma yajuya ya fita yana dariya,

kusan minti talatin yafito sanye cikin fara kal din lallausan jallabiya mai gotun hannu, Fallon Mami yashiga tun kan ya iso kamshin sa ya iso,

Ahankali tadago tana kallonshi ta lumshe ido ta bude aranta tana gulmata kyau da Gayu irin na KB matsalansa. Daya dan banzan jin kai da izza,

Tana matikan son KB tun ba yauba shiyasa fir taki zaman London wajen Abbanta kusan kowani qarshen watanni uku sai tazo Nigeria, wani alokacin har sai Abbanta yayi ta waya yananumata bacin ransa kafin ta koma NAFISA kenan " yar kanin Mahaifin KB

Sam bai lura da ita ba har saida yazo tsakiyan Fallon tayi dan gyaran murya Yadago suna hada ido ya sakar mata harara ya wuce dakin Mami murmushi kawai tayi tabishi da ido ya murda handle din qofan ya leqa da kanshi yace "Mami na "tadanyi gyaran murya abayan gida maida qofan Yayi ya rufe ya dawo fallo ya nufi dining yazauna, ya dago wayansa yana danne danne,

Nafisa ta taso tazo tajawo kujera daf dashi ta zauna tana. Kallonshi  barka da dawowa mijina, yadanyi murmushi gefen baki  "kinimi mijinki tun dare bai mikiba Kaine mijina insha ALLAH hade rai yayi batare da ya kuma tankawaba, tadan ya mutsa fuska "yinwa fa nakeji KB "toni meye nawa aciki dakike gayamin?  Dai dai lokacin Mami ta iso " sai yanzu kagadaman fitowa? Ka wani shanya mutane suna jiranka "I'm sory my Mami " Nafisa samishi Abinci yadan yatsine fuska yace "Mami kina arhantar dani da yawa nidinfa mai tsadane, yaza'ayi ace wannan abarce zata samin Abinci Nafisa ta kaylkyale da dariya Mami "tace ina wani tsada ga gouron da bai da mata?  "to ai Mami ke kika ki auraddani, gashi sa'annina daga mai da daya sai mai biyu ya fada cike da zolaya don kalman da mamin take yawan gaya masa kenan,

Ta balla masa harara " tace af kar kadamu kwanannan zan auradda kai inaga ma. Kafin hutun nafisa ya kare za amuku aure Inyaso saita karashe karatun da aurenta Mami tafada cike da  tsokana tana gimtse dariyanta don tasan tagama kunnashi 

Nafisa ji tayi kamar ta Goya Mami tsaban farin ciki  dariya take qasa qasa tana kallonshi yayi kicinkicin da fuska yana danna wayansa har tagama zuba wa ta tura masa gabansa ta zauna Mami tajawo nata tafara ci tana dan murmushi, nafisa ta sunkuyo dai dai kunnensa tace" my luv ko inbaka abakine? Dan gajeren tsaki yayi yajawo abincin yafara ci "Mami ankai Abincin Asibitin ne? Eh dazu nafisa sunkai ita da driver, tabe baki baki yayi yace mhmm ALLAH yasa dai ba'amusu raahin kunyanba,

Nafisa ta yamutsa fuska wa za'ayima rashin kunya?  "Yan qauyan? Mami tace "CI Abincin ki nafisa baki sabo da halin kabir,

Dadauri sauri yake shiri yana duba agogo yasan yanzu haka Mami tana tasintiri tana jiran shigowanshi, tsaf yagama shirinshi cikin wando cinos brown da  shirt millk colour sai takalminsa sau ciki brouwn da farar safa aciki ya manna farar glass a idonsa ya dauki brief case dinsa brown yarataya akafadansa yana daura agogon hanunsa mai Cain din silve wayassa tahau ruri dan murmushi yayi yadauka yakara akunnensa "Hello Mami gani nan zuwa nagama, aqofan sashinsa ya taradda securitynsa suna jiransa hanu yamika musu daya bayan daya sukayi musabaha, yawuce sashin Mami tana tsaye jikin dining kamar yadda yazata  nafisa kuma tana kan kujeran dining din, hannayensa biyu yahada waje daya yadaga yana kallonta da dan murmushi afuskansa yana juya  kanshi "I'm sorry my Mami ta matsoshi tariqo hannayen ta zaunar dashi kan kujera tana fadin kar kadamu kabir nasan maganinka kwanannan zanyayeka in huta kaikenan kullum latti zan samarmaka mai hanaka wannan baccin, tana magana tana zuba mishi a falate shikuma sai murmushi yake yana kallonta, ta turomasa dumamen tuwon shinkafa miyar danyen kubiya  don tasan shine fevourite dinsa ta zuba masa kunun gyada ta turomasa tana kallonshi shima din ita yake kallo Mami waye zai hanani baccin? Inna aurad dakai dakafara "ya"ya ai shikenan bakai ba baccin safe yadan murmusa yadauki spoon yafara cin abincin,  Nafisa ta lumshe idonta ta bude tana kallonshi ko Rabin baibciba yature yana shirin tashi Mami tace " yanzu ko kununma bazaka shanyeba? Yadan shafi cikinsa "wlh Mami na qoshi  ta tabe bakinta kawai tabishi da kallo,

Bayangidan Fallon yashiga ya kurkure bakinsa yafito briefcase dinsa yahango rataye akafadan nafisa baikobi takantaba yafara sallaman Mami, Addu'o'in datasaba mishi tashiga mishi har sai da tagama yace" ameen mamina nafisa tamiko masa briefcase dinsa, yaharde hanunshi aqirjisa yana kallonta "da ahanuna kika samu?  tadanyi farr da idonta "dannabaka ahanunka ai balaifi nayiba yajuyo da kallonshi ga Mami "yace Mami yarinyannan ta rainani kiga ko gaisheni batayiba, tazo yanzu zatamin rashin kunya Mami tace"ni na isa shiga tsakaninku? " Mami wlh in nagaisheshi kin amsawa yakeyi  "shikenan Mami kinbani dama intattakata kenan? Mami tazaro ido waje ni inbaka daman kataka matarka!? Afusace yafinciki briefcase dinsa yafita yabarsu agun,

Sam bayason Mami take hadashi da nafisa amaganan aure yafison suyi mu'amala da ita matsayin yaya da qanwa don duk familyn Su bawanda yafi shiri da ita irin nafisan

Tunda yafito daga cikin mota yake gaisawa da mutane har yashiga office, sister Amina yatarar tana shirya folder yaja kujera yazauna tadan rusuna tana makale murya tagaisheshi ko kallonta baiyiba ya amasa aggagauce yana duba wani file, kimanin Awanni hudu yadauka a office din ya shiga word a bakin qofa sukayi kicibus da Baba, "sannu likita da murmushi ya amsa da "sannu Baba ya maijikin dai? a wlh jiki Alhadulillah "ta tashi ne? "Eh ta tashi likita har tana dan cin Abinci, nagode likita wlh har bansan mezance makaba sai dawainiya akeyi damu tunjiya ake takawo mana Abinci Niki Niki ALLAH ya maka Albarka kaida iyalanka, "Ameen Baba ALLAH yaqara mata lfy munje inganta, 

 Yana gaba Baban nabiye dashi har jiki gadonta, bacci take amma yaga alamun sauqi sosai afuskanta, yajima yana kallonta yana nazartan yanayin fitan numfashinta yanadan rubuce rubuce, kafin yakai dubanshi ga mama jummai yace "jiya da yaushe tafarka? "Kusan magriba taci Abinci alokacin? "a'a  maltina kawai tasha amma yau da safe tadan ci, ya gyada kansa "baccifa tayi da daddare? "Eh tayi  sosai ma, sai da yagama "yace idan ta farka za'azo akaita can wajen masu xray,  yazaro kodi mai yawa yamiqa wa mama jummai takarba sai zabga godiya take yajuya ya fita zuwa yanzu kam Baba yafara tsananin mamakin likitan dama anasamun irin wa'innan mutanen abirni? 🤔 yatambayi kansa

Sai can bayan la'asar tafarka da sauri mama jummai ta tariketa tana tambayanta zaki zagane? ta girgiza kai gyaramata Zama tayi dai dai lokacin Baba Garba yashigo da katan din maltina da kayan tea wai gashi inji Doctor KB Dija kam gyara zama tayi tana kallonsu suna magana tana tambayan kanta to ko sudin suwaye? Tunda tafarka taga mama jummai tana ta hidima da ita datayi motsi zata matso ta tambayeta me takeso?

TOFA MUJE ZUWA MASOYA AKWAI MAGANA AGABA

TAKU UMMU FATIMA 😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MAY* *ALLAH HELP OUR COUNTRY NIGERIA*🇳🇳🇬

*ISLAM MY RELIGION* 😘🕋



         




           *page* 2⃣


Allah Allah takeyi Baffa yashigo ta tambayeshi, mama jummai ta matso kusanta maclean tasa abrush tamata barush ta wankemata fuska acikin Dan bucket

Tahado mata tea mai kauri tazo tana bata abaki da kyar tadan sha kadan tafara Amai

Riqeta tayi harsai data gama ta mata sannu tagyara mata jikinta ta kwantar da ita tana gyara wajen Baffanta yashigo sannu baiwar Allah mungode da dawainiya Allah yasakamuku da khairan; Ameen tace sannan ta fita

Yajawo kujeran da yake gefe yazauna daf da gadon yana kallonta cike da kulawa "sannu mamata yaya jikin?
"Dasuki baffa, inna batazoba? Bata zoba Dija, aiba tasanma awani asibitin muke ba, tadan turo baki ai da Bintu ce da tazo wajenta,
Dariya yayi Yariqo hanunta "kar kidamu uwata kedai kiyi Addu'an Allah yabaki lfy mukoma gida Abun Mu ,

Baffa wacece wannan dinnan da muke kwana tarennan?

Gyara zama yayi yana kallonta yace "wlh likitan dayake dubakinnane yaro Dan mutunci duk wannan hidima shiyake hatta da Abincin da ake kawowa daga gidansa ne bani da bakin masa godiya sai Addu'a yaqarasa maganan yana jinjina kai

Zaune yake shikadansa a office din yanaduba photon zuciyan da akayi ma Dijah yajima yana nazari akan photon,

Yatausaya mata sosai ya tausayawa iyayenta duk da anashi ganin sakacine yasa hakan tafaru don yana ga da sunkawota asibiti da wuri da ikon Allah da Abun bai kai hakaba 

Juyi yake tayi acikin kujeran daga qarshse ya ajiye photon akan table din ga banshi yahade yatsunsa ya tallafi habansa yana Dan juya kansa ahankali

Dr Habib ne yaturo qofan yashigo kai tsaye kujeran dake gefenshi ya ja yazauna yana kallonshi man yadai? Ya fada yana taba kafadansa Dr kabir yaja dogon numfashi gami da cire hanunsa yana kallon sa Dr Habib yadauki photon dake gabansa yana Dubawa

Gajeren tsaki yayi ya ajiye "KB wai meyasa kakesa kanka cikin case din petaint hakane?

Bayan yawancin case din yara haka sakacin iyayensune don ciwo ba ajikinsu yakeba sai Suyi burus harsai yaro yagama galabaita sai sukawoshi, KB yasauqe ajiyan zuciya yace "duk dahaka dole da tausayi kuma Abun da yafi damuna mahaifin yarinyan yadamu sosai inason in masa bayani don sukula da ita sosai saidai bansan yazai dauki abunba

Kasan irin wannan sai shima zuciyarsa ta buga ,

Habib ya nisa yace "to ya za'ayi dole haka zaka mishi bayani sai ya kiyaye gaba

Kasan meya kawoni? Habib yafada yana shafa kansa "wlh mum ta matsa akan sai naje wajen yarinyannan don Allah yau zanzo da daddare muje,

KB yazaro ido da daddare? Cab mezai kaini wajen Yar mutane da dare?
Mhmm kaima kasan mamina bata barina zuwa ko ina da dare inba masallaciba

Habib yatabe baki "to babyn Mami sai kafadi time din da zamuje

"Towai kai bazaka iya zuwa bane sai dani?

 Habib baicemasa komiba yatashi yafita 
Shima lab coat dinsa yasa yafita suka tafi round shida qananun likitoti da nurses

Yanzuma dayazo jikin gadonta tana bacci saidai ya lura ansamu cigaba anumfashinta bakaman yanda yagani da safe bayan sungamane ya buqaci ganin baffa a office din sa

Sai da yagama rubuce2 sannan yafara masa bayani cikin hikima da tausasawa saidai Baffa bai daga hankalinsa sosai kamar  yadda Dr KB ya zataba

Asanyaye Baffa yace "to likita bazata warke ba kenan?

"Zata warke Insha Allahu Baba kaidai kukula da bata magani sannan kuguji abunda zai sata bacin rai had tayi kuka  in ankiyaye wannan ba komi insha Allah

Baffa yace "insha Allah za akula likita nagode inamaka fatan Alkhairi kaida zuri'anka gaba daya
To Baba nima nagode Allah yabata lfy


Sannu ahankali sauqi yake samuwa ma Dijah satinta daya yanzu hartakan fita waje Tasha iska kuma takan danci Abinci

Da daddare tana zaune Abakin gado Baffata yana zaune agefenta Mama jummai kuma tana zaune akan kujera

Hiransu sukeyi da fulatanci a nitse Dijah tana dan dariya tahango Nafisa tana zuwa, riqe take da basket cike  da kayan Abinci

Tana sanye da riga da sket na roba jah tayi rolling da farin mayafi komi najikinta abayanne yake,

Tunkafin ta iso take musu kallon da tasaba had ta iso ta ajiye Basket din sai wani yatsine fuska takeyi har da rufe hancinta da mayafinta,

Bawanda yasamu arziqin gaisuwa awajenta saima wani wualqanceccen kallon da take binsu dashi Baffa ne yasauqo daga kan gadon sai sannu yake ta mata gami da godiya

Dijah kuma mamakin halin nafisa takeyi yayinda wani bangare na zuciynata kuma yacika dason ganin wanna likitan mai taimako Dan basu taba haduwa dashiba duk zuwansa tana bacci, 
Tafe yake cikin takunsa na izza yana sanye  da farar t shirt da wando jeans blue da farin glass a idonsa sai qamshi yakeyi hanunsa dauke da manyan ledodi guda biyu jikin gadon wani datijjo yafara zuwa bayan yagaishesu ya tambayi jikinsan ya ajiye masa Leda daya da magunguna da yasiyo nan suka hau masa godiya murmushi kawai yayi ya wuce gadon Dijah kallo daya yayima nafisa yahade rai ya qarisa jikin gadon cikin girmamawa yagaida Baffa ya tambayeshi mai jikin cike da fara'a Baffa yace "yanzu kam jiki Alhamdulillahi likita kuna ta dawainiya damu Allah yasaka maka da gidan Aljannah

 Dan murmushi yayi Yadawo da kallonsa wajen Dijah da itama shi take kallo yatsuntsa biyu yasa yashafi goshinta yaya jikin naki? Bai jira tacewantaba yakalli mama jummai "mama Akwai wani matsalne? "a'a bakomi jikinta da sauqi sosai "OK tana zazzabi cikin dare? "a'a gaskiya yanzu batayi ya gyada kai ya dauko magungunanta yaduba, ya ajiye; hanunsa zube cikin aljihunsa ya kebinta da kallo tsawon minti 3 sannan ya musu sai dasafe sukatafi,

Binbayansa tayi da kallo tanason tuno wannan fuska amma Sam yakwanta mata tamanta inda tasanshi haka tayi ta tunanin ta bata tunoba

"KB wai ya maganan zuwa gidansu yarinyannanne? Don Allah kazo mutafi wlh mum ta matsamin juyawa yayi ya kalli nafisa sai danne danne takeyi awayanta hankalinta baya garesu, murya qasa qasa yace" karufamin asiri ba abunda zai kaini wajen "yar mutane adarennan wani Abu ya bullo daga baya ace dani aciki ,

Habib ya balla masa harara "wai me kake nufine KB? Mhnm kasan me nake nufi ai sarai nidai ba ruwana ehe,

Habib yaja dogon tsaki "to sauqeni anan "kabari muqarasa gidanmana "no akwai abunda zanyi ananne perking yaiy agefe Habib yasauqa suka qarasa gida,

Tare suka jero da nafisa har cikin fallo kai tsaye dining ya haye kusa dashi nafisa ta zauna tana fuskantansa  "wai me namakane KB tun acikin asibiti na lura fushi kake dani bai ko kulataba ya cigaba da danne danne awayansa

Ya kara wayan akunne "eh Mami mundawo gani a daining

Langabar da kai ta qara yi pls KB say something, wai meyasa kake min hakane? Don kaifa nake zuwa gidannan Amma sai kadinga wulaqantani, sai alokacin yadago kai ya kalleta ,

"Bakison awulaqantaki? Amma ke kike wulaqanta wasu? na luara da ke ba akan Wa innan kadai ba duk lokacin da aka kai ma wasu bayin Allah Abinci kindinga musu kallon banza da yatsina kenan, bafa finsu kikayba, bawanda yafi wani awajen Allah sai Wanda yafishi tsoronsa

To amma meyasa ke duk lokacin da mu'amala ta hadaki da wasu sai sunyi kuka dakene?

Jiyama inajinku da mai aikin Mami kina ta mata shouting why?? Yaqarsa maganan ahankali

Ajiyan zuciya ta sauqe tana kallonshi "to is ok KB zan gyara insha Allah amma banijin dadin irin rashin kulawanka akaina pls wlh ina sonka ta fada kamar zatayi kuka plate yajawo batare da yatnkamataba yafara zuba Abinci dai dai lokacin Mami ta iso taja kujera ta zauna tana kallon plate din abincin Su jin bai mai maganane tasa ta kau Dashirun da fadin "yaya yarinyan da jiki?

"Mhmm da sauqi sosai gobe in Allah yakaimu zan sallameta,  "ya Baban nan kuma danashi "to shine dai yanzu yake Dan jin jiki Amma dai shima yau naga yadanji sauqi to Allah yaqara musu lfy

Ta dawo da kallonta ga nafisa "nafisa ya dai? Murmushi kawai tayi  batare datace komiba ta fara cin Abincin ta


Tun yana wanka yakejin wayansa na ruri sarai yasan Mami ce kekiranshi don haka yakara sauri akan Wanda yakeyi da

kimanin minti 20 yafito da sauri ya nufi sashin zaune yasameta Kan kujera tana daurin Dan kwali tana ganinsa ta miqe tana sa hijab "kabir so kake kasani latti ko? So nake mufita tare in ajiyeka kafin In wuce wajen aiki

Fitowanta kenan daga bayan gida taji wata nurse tana ce ma mama jummai yau Dr KB yace zai sallameta ba qaramin farin ciki tajiba








Mmmn temah  ce😘 😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
 

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 2⃣2⃣


   
     Batarufe Baki ba sukaga wasu k'arti sun kewayesu da bindigogi zata kurma ihu Kila yadaka mata tsawa,

"Yimana shiru Munafuka inkink'i yanzu infasa wannan k'aton kannaki,

Cikin takun isa da izza ya k'araso gaban Alhaji ya'u da yaransa suka kewayeshi da bindiga,

K'afansa yad'aga yad'ora akan cinyansa, yana kallon fuskansa   "kace kasan maganina ko? To gani  nazo kayi maganina gani agabanka,


Kai wlh kacika d'an Rainin wayo inmaka aiki ka k'i biyana? Sannan kanimi ka gayamin maganan banza?

Cikin zafi Alhaji ya'u yace  "Nabaku kud'inku kad'anne yarage ba gana biyankuba, Amma aikai ka ha'inceni kasan baka kashe Kabir ba kazo kacemin ka kashe yanzu Haka daga gidansu nake, da idona naga Kabir haba wannan abu dame yayi kama?  Shekara nawa ina farautan wannan yaro abu ya gagara kumama yanzu sai dana gama asaran dukiyata kafin ya b'ullo baziyuwaba!!! Yak'arasa maganan cikin k'araji yana taune Hak'ora,

Kila yarik'e hab'a yana ksllonsa cike da kamaki, "ya'u bansanka da shaye2 ba nadai san ka k'ware wajen son kud'i,

Anya ko dai kayi gamone?

Kabir d'in da na fatattakasu da bindiga shi da drevernsa Sannan a idona suka afka cikin k'atuwar Gada wlh ko akan laya yake kwana bai isa fitowa har yataka doron k'asa ba,

"Wlh dagaskene Kila uwarsafa bak'araman shu'uma bace yanzu haka wani tsatsubenta  tayi masa kafin yafita me zai hana kuma kufara bin Bokaye kawai akashe shi da Magani,  inji Rabi,

Shiru Kila yayi yana nazari tabbas ya yarda akwai  sihiri acikin wannan lamari inba hakaba Kabir basu isa su tsiraba,
 
Alhaji ya'u ya mik'e yana zagawa a Falon cikin tashin hankali ya k'araso gaban Kila, "yau nine ka d'ibo yaranka zaku kasheni? Bismillah ku kasheni koma na huta fa wannan bak'in ciki, dai ga Nasara sai asamu fail!! Why???  Yak'arasa cikin shouting yana jijjiga Kila,

Rabi ta k'araso ta dafa kafad'ansa,  "ka kwantar da Hankalinka Alhaji badai kace yasamu matsalan k'wal'walwaba?  Aini inagama angama wannan, ta matso fa bakinta dai2 kunnen Kila ta mishi maganan da shikad'ai yaji, wani mahaukacin Dariya yayi yadafa kafad'an  Alhaji ya'u "Dama kana da mace irin wannan agidanka kasamu muke tashan wahala?  Bani 2 days,  daga haka ya juya yaransa suka rufa masa Baya,

🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴

Washi gari Kabir suna zaune a garden shi da Habib daSani mafi yawancin Hiran  Su biyu ne sukeyi jifa jifa ne Kabir yake ansawa yafi maida hankalinsa kan Lap top d'in dake gabansa,  Sani yana ta latsa wayansa cikin sa'a yasamu no. Da kusan Kullum  sai yanima yajita akashe, harsaida yakusan tsinkewa kafin aia d'aga, bako sallama yace "waye?
"kai lro baka iya sallanaba, to Sani ne  meyasa Kullum inna k'ira inji akashe?

"Ayyah Sani wlh  kuwa inazuwa gona ne shiyasa nake kasheta in ajiye agida, dariya Sani yayi sosai sannan yace "to da  Allah ka kaima Fatima wayan,

"to barin kaimata kuna lfy ko?
  Ya Likita yak'ara ji da jiki?
"Alhamdulillah yanzu yatashi daga gurgu yadawo mai k'afa yafad'a yana dariya yana kallon Kabir da yanayinsa ya canza,

 Cikin sanyin murya suka gaisa da Bintalo, sai janta da magana yakeyi tana sharewa,  "ok tunda kin k'i muyi Hiran ba ma Khadijah mugaisa,

"Dijah bata da lfy tana kwance amman dai barin kaimata,

"Subhanallahi meya sameta?
"wlh wai ciwontane yatashi,

Asanyaye yake Amsa gaisuwan ta jin yanda Muryanta yake fita, yad'ago yana kallon Kabir da yake kallonsa bako k'iftawa,

Yace "to ga mutuminki barin bashi kugaisa, yakara masa wayan akunnensa,

Zuciyan Kabir sai bugawa yakeyi da sauri2 amon Muryanta nazagawa duk sassan jikinsa, Hello kalman da take ta fad'a kenan,

Dak'ya ya iya cewa ke kincikamin kunne da Allah kiibawa Fatima wayan, shiri yaji tayi sai sautin numfashinta da yake fita ahankali,

Sani yacire wayan a kunnensa yana magana jin baiji amsabane yasahi ya kashe, Habib kam saibin Kabir da Ido yakeyi yana son fahimtan wani abu,

Kusan minti biyar gurin yayi shiru can Kabir yace ma Sani wai waye Ba lfyn?

"Khadijah yabashi amsa tak'aice, shiru yayi sannan yace "Wai meyasa meta?

"gaskiya ban saniba,
"k'iramin lron kace yaba ma Fatima muyi magana, cikin sa'a da yak'ira Bintalo ce ta d'auka ya mik'amasa,

"Hello mamata kina lfy?
"lfy Likita ya Mamo?
"lfynta k'alau wai tun yaushene yarinyannan bata da lfy?

"takai Sati akwance, 
"Ankaita Asibitine?
"Eh, shiru yad'anyi ya sauk'e ajiyan zuciya,

"ciwontannane? Ko wani abunne?

"Eh naji Baffah yana cewa wai ciwon tane,

Cire wayan akunnensa yayi batare da yakuma cewa komiba, ya mik'a ma Sani yacigaba da opreting system d'in dayake gabansa,

Cike da zolaya Habib yace "Gurgun birni wai waye ba lfy naga duk kawani diririce, Anyah kuwa Gurgu baka shiga tarkon *Dijah k'aya* ba kuwa?

Afusace Kabir yad'ago yana masa wulak'anceccen kallo, "Look Malam kar kagayamin maganan banza kanaji?

"Sory man meye maganan banzan? Dan nace ka kamu da soyyayan Khadijah sauran muje musha biki kawai,

"God for bit ko kamanta he is my petient, daga Haka ya mik'e ya tafi don ua lura inyaci gaba da zama agun zasu b'ata masa rai don yanaga ko mata sunk'are badai Dijah bakam.


Yana dab da k'ofan Falo ya cikaro da Nafisa, wani wawan tsalle ta daka zata hau jikinsa yayi ta maza ya kauce ya bata guri da wowa tayi tana k'ok'arin mannewa ajikinsa yana nunata da yatsa, "hey stop! Haba Nafisa yaushe zakiyi hankaline?  Swagwb'ewa tayi kaman zayayi kuka haba Kb kabarni inyi murna na watanni nawa rabon da inganka? Kaga halin danashiga na rashinka?

D'azu nadawo kawai naji su Dady da Mamanmu suna magananka duk da ban gane me suke cewaba na fahimci ansamu lbrnkane, shine nazo inji awajen Mami yanzu takece min wai kadawo kana gaden,
Ganin bazata gama surutunba ane yasashi bin ta gefenta ya wuce ya shige ta rufa masa baya sukaje suka k'arasa agaban Mami,
Washi gari yakama Ranan Asabar aran ne kuma zasuyi tafiyansu aggagauce ya shiga kasuwa ya sayi magun gunan Khadija ya dawo yaba ma Sani yace lallai yakaimata ayau Don yak'ira Baffa jiya ya mishi bayanin jikinta nan sukayi sallama shikuma ya wuce air pot, misalin 12:00 na Rana, jirginsu Kb ya d'aga zuwa England sai muce ayi seminer lfy,

   Bayan tafiyan kabir da kwana biyu akasa bukin Bintalo da Sani sati biyu cif akasa,


Muje zuwa......


*Ummu Fatima ce* 😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MAY* *ALLAH HELP OUR COUNTRY NIGERIA*🇳🇳🇬

*ISLAM MY RELIGION* 😘🕋

🌈 *KAINUWA* *WRITTERS* *ASSOCIATION*
         
Girma, daukaka, Imani, zaman lfy, Allah ya qaroshi awannan qungiya mai Albarka, .................. *Dashen* *Allah* 👆🏻



           *page* 3⃣


Mama jummai ta mik'omata wani dogon Riga da Baffa yasayomata ak'ofan asibiti, rigan fari ne yana da manyan zanen flawowi ajiki jajaye,

Tafito shar da ita ko karyawa kasa yi tayi don dokin yau zata tafi gida, tana zaune abakin gado, likitoci sukafara round kallonsa takeyi bako k'yafta ido, itadai tabbas tasan wannan fuskan sai dai takasa tuna  a'ina tasanshi,


Cikin nitsiwa yake zaga gadanje sanye yake da suit bak'ak'e da bulue shirt ta ciki bak'ramin amsan sa kayan yayiba Kaman irin black American d'innan, wani sassanyan k'amshi nafita ajikinsa,

Yana daf da gadon ta tafara tunoshi ahankali Abun da yafaru atsakaninsu  yadawomata,


Mutuminnanne Wanda bai San darajan D'an Adam ba tabass shine, zuciyanta ta jaddada mata wani kallon tsana tabishi dashi,

Cikin taku d'ad'd'ai ya k'araso gadonta shikad'ansa sauran suna d'ayan gadon suna rubuta report,

Gwiwan hanunsa yasa ya dogara da jikin gadonta ya harde kafansa hanunsa d'aya na  cikin aljihun wandonsa, 

Yad'an ran k'ofo kad'an yana kallon dara daran idonta yace "yajikin naki?
Yanzu inane yakemiki ciwo?

Wani mugun kallo tamasa ta sunkuyar da kanta batare da tace komiba yasaka yatsansa d'aya yatallafo  hab'anta yana kallon fuskanta "waike kurmace? Baki jine? Ko maganane bakiyi?

Kwace fuskanta tayi tana zabga masa harara kaman idonta zai fado
 mamakine sosai yabayyana afuskanshi, tomeye daliln masa wannan kallon? Meya mata? Da ya cancanci wannan kallon awajenta? tambayan dayake ma  xuciyansa kenan dai dai lokacin Baffa ya shigo,

Bayan sungaisa Baffa "yace likita wai yau za'a sallamemuko?
 Gyara tsayuwa yayi yana shafa suman kansa dayayi luf kaman hula akansa,
 indonsa akan Dijah yace "na tambayeta ko Akwai wani matsala bata ban Amsaba inaga batashirya zuwa gidan bane, Baffa ya juyo da kallonsa wajen Dijah

 "Dijah kiyi bayanin inda yake miki ciwo
 "nifa na warke Baffa,

Da sauri Dr KB ya dago kai ya kalleta jin muryanta a'ina yasan wannan muryan? Yatambayi xuciyansa

"Barinje Baba inta shirya yin magana zanzo inji inta canacanci a sallameta sai assalametan,

Yana fad'an haka yajuya ga likitotin da suka iso gun da kai ya musu Alaman Su wuce gado nagaba

Wani irin takaici taji kamar ta zunduma ihu wannan Dan rainin wayon wato anan ma sai ya  Wulak'antani ko?


Yana gamawa yashige 0ffice dinsa, yatattara duk abubuwansa,

Tafe yake cikin motansa shikad'ai don tun fitowansa yasallami Budy guards dinsa suka tafi Gida shikuma yanufi gidansu  Amininsa,


Idonsa sai tariyo masa yarinyannan yakeyi kallon rainin data masa sosai Abun yabashi mamaki "Yar k'araman yarinya da rashin kunya haka?  Bama wannan ba meyamata? Meye tsakaninsu? Wani bangare na zuciyansa kuma na jaddadamasa muryanta tabbas kamar yataba jin wannan voice d'in,

Tsaki yaja ya doki sitiyarin motan gami da furzar da numfashi "natsani raini da rashin kunya,

Yafada a fili dai2 lokacin dayake Shiga kwanan gidan,


Afarfajiyan gidan ya tarad dashi da alamu fita zaiyi,

 Kallo daya KB ya masa yakau da kai yana k'unshe dariyansa ya shige ciki aransa yace wai fushi yake dani,


Nana ya Tatar a falo tana danne2 waya tana ganinshi ta tashi tazauna tana dariya tace "welcome bros, "I don't like yace da ita ya zauna a kujeran gefenta,  freich ta bude takawo masa drink ta zauna bros meyasa baza ka amsa gaisuwata ba?

"Saboda ba abunda nazoyi kenan ba right ?

Tadan Langabar da kanta "bros inna k'iraka awayafa ba kad'auka wlh shiyasa nadaina k'iranka "cab yaushe kika koyi k'arya bansa Niba?


"Where is my mum?
"Tana sama let me call her tafada tana hayewa sama,

Tare suka fito da mum tunkafin tazauna  tace " mnnmm kun gama raina min hankalinne yau? Kunga dama? Dai2
lokacin Habib yashigo yana yima KB kallon ka iya ma bakinka,

Mum tace " inkunje dama akwai wata k'awarta kusa da gidansu yarinya mai hankali kabir kai kuma sai kaje kaganta Ku dai2 ta tunda Ku kunkasa zabar ma kanku Nina zabar muku,

Bazaiyiwu  azuba muku idoba sa'aninku daga masu "ya"ya 2 sai masu shirin yin na uku, ku ko kunya ma bakwajii;

Kabir yayi k'asa da kansa yana sosa k'eyansa yace" mum ba mugaisabafa, "bazan amsa gaisuwanka ba har sai kunje kun dawo naji sakamako;

Mik'ewa sukayi dukansu zasu fita Nana tadan rufe bakinta tanakallonsu tace "Bros kugai damin Su Aunty Amiran da k'awanta Aunty ...... ai Bata kai k'arsheba Habib yayi kanta zai doketa, da gudu tayi bayan mum tana dariya mum tace kadai je,

Har sunshiga mota, KB yace ma Habib " da wannan kayan zakaje? Pls sunyi skuizin kaje kasa wasu wlh tunda ga kayanka zamu fara failing bai kulashiba don Dama yasan yanason ya kulashine yasamu nayi 

Sund'au hanya KB yasake cewa amma baibkamata muje hakaba, kamata yayi mud'an sami abinda za mukaimata ko?

"Zamu kaimata ko zamu kaimusu? Karfa kamanta yanzu tafiyan mutane biyune da Amira da k'awanta  Habib yabashi Amsa yana dariya donyaga yanason yarainamasa hankali dayawa;

KB baisake cewa komiba har suka isa

Da Alama dama ansan da zuwansu daga  irin tarban a kamusu
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MAY* *ALLAH HELP OUR COUNTRY NIGERIA*🇳🇳🇬

*ISLAM MY RELIGION* 😘🕋

 

🌈 *KAINUWA* *WRITTERS* *ASSOCIATION* ✍🏻
         

_karkadaina Addu'a domin itace makaminka duk Abunda yasameka duk'ufawajen rokonmahllincinka domin shine maiiyawa. akankan komi_

_katuna mala'iku suna rubuta maganganunka don haka kakiyaye harshenka karlittafinka yacika damaganganu marasa amfani_



           *page* 4⃣


Abinci kal2 Nuratu k'anwar Amira ta gabatar musu;

Ko ruwa basu shaba, had tafito Riga da sket ne ajikinta na atamfa, da hijab d'inta har gwiwanta,


Balaifi tana da kyau dai2 gwargwado,

Tunda tayi sallama tazo tazauna, batace komiba, kallon kallo sukashigayi tsakanin Kabir da Habib Kabir yad'an dunguri Habib Alamun wai yayi magana shima dungurinsan yayi wai shi yafarayi,

Kabir yasaci kallonta  da gefen idonsa ta takure gefe guda kanta ak'asa ya kalli fuskanta tasha kwalliya sosai,

Hanunsa yasa yatab'o Habib k'asak'asa yamishi nuni da fuskanta, Habib ya d'ago ya kalleta gaba d'ayansu suka kwashe da dariya,

Amira da batasan meke faruwaba sosai ta tsorata har tafara tunanin to kodai ba dai2 sukeba

Kabir yayi gyaran murya yana kallon ta yace "sannu "yanmata ba gaisuwane? Sai alokacin tad'an nitsu ta kallesu ina wuninku, dariya suka kuma yi yanzu kam ta fahimci rainin hankali suke mata don haka ta d'aure fuska tana kallon hanyan waje

Kabir yayi gyaran murya " mnnnh dama dai munzone wajenki da niman aure ba wasaba don gaskiya kinyi Wa Abokina,

Shiru yakuma baya suka kalli juna sanna yace so yanzu dai munmiki? Ko ba Mu mikiba? Ma'ana kina son Abokina?

Wani irin haushi ne Yakama Amira wannan wasu irin shashashu ne? Afuska gashj anaganinsu anga wayyayu masu aji,
Amma sumata irin wannan shirmen maganan tun yaushe akabar irin wannan  Hiran?


D'an gajeren tsaki tayi a iya lips d'inta
"Pls say something mana "yan mata muryan Habib ya katsemata tunani

'Kara sunkuyar da kai kawai tayi don bataji aranta zata iya maganaba,

Zaman kurame sukayi tsawan 5 minutes Habib yace to tunda kin kasa mgana Mu zamu tafi, ai bai k'arasaba ta mik'e tafara tafiya
Habib. Yace "mnnm kituro mana k'anwanki da sauti tad'aga labule ta fita kicib'us sukayi da k'anwanta gefenta tabi ta wuce ta tafi ita kuma tashiga da niyan gaidasu,

Bayan sungaisa Habib yace "wai Akwai wata k'awan Amira kusa daku nan ko? tace "eh tana gidannan ma, "yauwa yimana magana da ita "OK to tafita,

Kabir yayi fuska yace "kai karfa ka rainamin hankali wlh  ba ruwana da wata yarinya dai2 lokacin ta shigo da Sallamanta ita ma irin shigar k'awantan tayi, bayan sun gaisa ba b'ata lokaci Habib yagabatar mata da Abokin sa amatsayin manimin aurenta Asaba'in ta kallo KB jikinta har b'ari yakeyi aranta tana Ayyana irin sa'anta ita da haryanzu bata da k'wak'wk'waran saurayi Ace mutum kaman KB yazo niman aurenta? ita koyau Ina zata saka kanta Dan murna,

Cikin rashin sa'a tad'ago kai tana murmushi sukayi  ido biyu da KB ya mata kallon baki da hankali, Habib sai dariyan mugunta yakeyi, KB ya tashi yana kallon Habib inkagma zuban naka kasameni a waje daga haka ya fita,

Asanyaye Aliya ta kalli Habib tace "Anya kuwa dagaske  yana sona Habib ya mik'e yana fad'in karkidamu haka halinsa yake tun Muna yara, ba'a gane abun da yakeso da Wanda bayaso Amman dai kiyarda dani yana sonki bari Mu wuce zamu dawo,

Tare suka fito alokacin KB yana shirin fita Habib yayi wuf ya bud'e motan ya shige,

🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴
Shiru yayi yana sauraran muryanta duk da ba filatanci yakejiba amma ya fahimci akanshi take magana cikin nitsuwa ya k'araso inda take zaune hanusa rik'e da Bakin Allurai, ya kalli Baffa yana murmushi yace "Baffa sai Alluran ne bataso?  "Hahh Dijah da tsoro Allura daga gani a hanunka shine take magiyan kar amata Baffan yafad'i haka don bazai iya fad'amasa Abun da ta ke fad'a akansaba,

Murmushi yayi cike da zolaya yace "wannan ba Allurankibane Amma tunda kina so zansa amiki d'aya,

Cike da tsiwa ta murgud'a baki "nidai wlh baniso na warke ba Alluran da za'amin,

Tsayawa kawai yayi yana kallon bakinta ahankali yafara tunota yarinyannane  marar kunya Wanda suka tab'a had'uwa arugan juma ta mishi rashin mutunci, tabbas biri yayi kama da mutum tunda tafarfad'o take masa kallon kamar tasanshi, wato shine data ganeshi take masa kallon raini haka? Tuno maganan da wani saurayi yagayamasa arugan yayi 

*Dijah bukar med'ori kenan yarinyace maihankali sai dai akwaita datsiwa inkashiga hark'anta gashi bata da hak'uri, bata manta abu komi Kamata saita rama ko ta d'au fansa* 

tsaki yaja yajuyamata baya ahankali yace k'arya ne yarinya kinyi kad'an baki kai kiyi wasa daniba yaushema aka haifeki? Ko can dakikamin nabarki, gani nayi bakikai intsaya yi da ke bane;


Baffa ya matso gaban Dr kB yace "likita don Allah kasallamemu  tunda taji sauk'i  murmushi yayi yanashafa k'irjinsa  "OK Baba yau d'innan za'a sallameku insha Allah, yajuyo da kallonshi ga Dijah ya na mata dariyan mugunta gami da kallon zakisani,

Yakalli Alluran da yake hanunsa ya kuma kallonta yace "za'a k'arasa mata Alluranta "to kawai Baffa yace sannan yafita Dan yin sayyayan da yakesonyi yatafi dashi  gida Cikin takunsa na izza ya matso daf da ita yahad'e fuska Yana kallon tsakiyan idonta, ya lashi lips d'insa meye ma sunanki? *Dijah k'aya* ko? Sunan da "yan k'auyenku suke k'iranki da shi, ya jijjiga kansa "kinga ikon Allah ko? kin tuna alokacin da kikamin rashin kunya a k'auyenku? Yau gashi Allah ya kawoki hanuna, ya juya ya fita Jim kad'an ya dawo da Allura ahanunsa, ina hannunkinan da yamin B'arna mik'o shi yafad'a yana zabga mata harara,


 Dijah  tuni ido ya raina fata Sai b'ari takeyi amma idonta bai huta da hararansaba, sai b'oye hannayenta takeyi tsakanin cinyoyinta, shi kuma yana tsaye k'yam kallonta kawai yakeyi


Ahaka Baffa ya traddasu, "yau likita anmata Alluranne ya tab'e baki tak'i amata kuma bazai yiwu asallameku ba amataba, Baffa ya matsota yadafa kanta haba mamata akamiki baunda yafi Allura zafi, bare Allura kiyi hak'uri amiki ya wuce muyi Mu tafi yau zaki ga innanki insha Allah, taso tasanar da Baffanta cewa Alluran zalunci zai mata bana gaskiya ba sai dai tasan Baffa bazai fahimcetaba don haka kawai ta fashe da kuka ya jima yana rarrashinta sannan ya kalli Dr KB da yake tsaye yana mata wani irin kallo "bismillah likita yimata mutafi matsowa yayi yana mata Alama da tabashi hanunta bayan da ta iya ta mik'o hanunta yana totson lips d'insa yace "atafin hanun za'ayi, Baffa kanshi Abun yabashi mamaki Allura a tafin hannu?


Bai kawo komi aranshiba ya zauna kan kujera yana kalle2 sauran marasa lfyn da suke sauran gadaje,


Cike da mugunta da son ganin gudun ruwan ta ya cakka mata Allura a tafin hanunta har waje biyu sannan ya koma gefe yana kallonta,


Azuciyansa yace bake baki da kunyaba? Kuma wai komi akamiki sai kin ramaba? Tom ina jiranki, ya jawo foldernta yayi rubuce2 aciki yace "shikenan Baba Akula da shan magani da dokan da akamata zata warke insha Allah, daga haka yafice batare da yaji daga Bakinsa ba,


Mama jummai ta shigo da sauri ta k'arasa wajen Dijah tadafa kafad'anta "haba Dijah keda yau zakije kiga mamanki meye naki na kuka? Kiyi shiru abinki maza zo muje kiyi wanka, tajata suka fita,



Kayanta da tazo dashi ajikinta tasaka Riga da zani farare  k'al irin na fulani Baffa yana tsaye abakin k'ofa suka iso ita da mama jummai, sallama ta musu da fatan samun k'arin sauk'i

Baffa yace mata ta nuna ma Dijah office di'n likita ta mishi godiya, don d'azu yazo mata sallama tana wanka, taso tak'i zuwa sai dai bata saba yima Baffa musuba  don haka tabita, da hanu mama jummai ta nuna mata office d'in ta wuce abunta,



a tsorace ta tura k'ofan ta shiga sai zaro ido takeyi yana zaune a cikin kujera yana aiki da lap top kallo d'aya yamata ya dakamata tsawa "ke "yar k'auye meya kawo ki nan wani irin harara ta bishi dashi batare da tace komiba,  a fusace yafara danna k'ararrawan k'ira wasu masu sharane guda biyu suka shigo kufitar min da wannan abar anan sercatif problem ne da ita Ku mai data can layin mahaukata inaga daga can ta k'wace tazo, ai asaba'in suka d'auketa cak suka fita da ita sai tirje2 takeyi tana kuka amma sai da suaka kaita,



Wata nurse suka samu awajen tana zaune tana ganinsu ta mik'e tazo wajen tana tambaya, dayan matan tace "daga nan tafita garin yaya kuke barinsu suna fita  office d'in Dr KB tashiga, nurse d'in ta kalleta cike da tausayi tace "gaskiya bansan da yarinyannan ananba inaga tun banzoba tafita,  juyawa sukayi suka tafi abunsu, cike da tausayi nurse ta jawota itakuma sai kuka takeyi tana tirjewa, akan wani kujera ta zaunar da ita ta jawo ruwan Allura zata mata,



Cikin matsanan cin kuka ta durk'usa ak'asa hanunta na bari tace "don Allah sister kiyi hak'uri wlh ni ba mahaukaciya bace sharri akanmin wlh niba mahaukaciya bace, cak ta tsaya tana kallonta, Dijah ta rik'o hanunta Allah dagaske niba mahaukaciya bace Baffa na yana waje yana jirana,  "kintabbata? dagaske kikeyi, wlh dagaskene sister inbaki yardaba muje kiga Baffa na zai miki bayani,


Nurse d'in tana rik'e da hanunta suka fito fuskanta sharaf da hawaye, Abunda ya bama Dijah mamki shine hango Baffa da Dr KB datayi, harshine ma yake nunama Baffa ita da alamuma yataya Baffan nimantane nurse dince tayi sallama tun kafin Su Amsa sallaman Dr KB yamata kallon don't say any thing, don haka shiru tayi batare da gane komiba,



Baffa ya kamo hanun Dijah yace " haba mamata da baki gane office d'in likitanba bazaki dawoba? Sai kije ki shige wani wuri kisani adamuwa? Ina ta nimanki,


Ya kalli nurse d'in yace "mungode ko, "bakomi tace sannan ta juya batare da tace komiba, tunda anyi waning nata


Dijah kan ko kallon inda KB yake batayiba ta wuce tayi gaba nan tabar Baffa sai godiya yakeyi ma Dr KB




*tofa wai kan meye tsakanin Dr KB da Dijah ne? Shin wani mataki yanzu Dijah zata dauka tunda ance ita bata barin ta kwana?*


*ku biyoni*


Taku *ummu fatima* 😍😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MAY* *ALLAH HELP OUR COUNTRY NIGERIA*🇳🇳🇬




*inamik'a ta'aziyana gareki FA'IZA (ANFA) Marubuciyan sweet novel d'innan D'AN FASHI Narasuwan Mahaifnki da ",yar'uwarsa ALLAH Ya gafrtamusu yasa Aljannace makomarsu ALLAH ya tallafi iyalansu dasu kabari ALLAH Yak'aramuku hak'uri da juriyan rashi*🙏🏼😭😭

       

*🌈KANUWA WRITTERS ASSACIATION* ...........🖊



           *page* 6⃣


Cikin k'ank'anin lokaci kila ya iso kai tsaye fallon Alhaji ya'u yawuce.


   Zaune  yasameshi ya had'a hannayensa biyu ya tallafi hab'ansa da su.


       Yana ganinshi yatashi cikin taku d'ad'd'aya yana goye da hannayensa a bayansa  ya matsoshi, cikin  dakkakiyar murya yafara magana,


   "Shekaru masu yawa ina mafrkin na mallake Dukiyar ya Mahmud, tun bayan mutuwansa nake fad'i tashin ganin markina ya tabbata.


  Ya furzar da iska, sanan yacigaba, "nabi hanyoyi da dama ciki kuwa harda son Auren fatima don insamu abun da nake buri cikin sauk'i batare da nasalwantar mata da D'anta ba amma fir tak'i Amincewa, Ba hanyar da banbi ta  Aura masa "yata Nafisa don mu had'a kai da ita  amma sunk'i

"shekaru biyar kenan  da baka contract d'in kashe Kabir nanma ya gagareku,  inbazaka iyaba kawai kasanar dani innimi wanda zai iya.



   Kila yayi wani mahaukacin dariya ya karkace kai yana kallon Alhaji Ya'u da yake masa kallon kashiga taitayinka,

Yace Ranka ya dad'e kashe Kabir ba abu mai sauk'i bane saboda irin tsaron da Mahaifiyarsa tasa masa da sojoji yake fita masu muggan makamai, duk wani motsinsa sunatare, kaga kuwa kasheshi sai anshirya sosai.


  Amma ina da shawara aganina kashe Kabir shikad'ai bashi bane mufara da wannan seceurytin sannan Sani,  daganan sai akau da Uwar tasa shikenan in anyi haka angama dashi,

Ahankali yake taku har sai da yazauna akan sofa yakalli Kila "wannan ai long prosses ne nikuma  da gaggawa nakeson ayita tak'are  Don haka jeka kawai zan san abunyi, Matsoshi kila yayi yace "No my Boss kabani nan da one weak zakaje ma fatima ta'aziyan mutuwan Kabir,  Dasuri Alhji Ya'u yad'ago kai yakalli kilman dan jin kalman da yafiso yafuto Abkinsa, baiga Alamun wasa afuskan Kila,


 Wani nannauyan ajiyan Zuciya ya sauk'e  don yasan Kila idan ya  aminci zaiyi abu zaiyi Sannan kisa awajen Kila bakomibane ya shek'e wa inda suka fi Kabir ma tsaro.


   Hanu Kila ya mik'omasa Alamun inji dumus Dariya yayi sannan yashige d'aki ya fitomasa da kud'i Aleda "kafara da wannan namaka Alk'awarin indai Kabir yabar Duniya zaka mallaki abunda yafi wannan,

 "Ranka ya dad'e ahad'a har da uwar tashi kawai  "no kabarta  kawai ita wannan ba kowa bace kan dukiyan batasan komiba,  sannan ina gudun kar asamu matsala hara mutane sugane.


   Sosai yaji dad'i aransa har yafara lissafa yanada zai dawo millonian nanda sati  d'aya yayi wani dariya  ya mik'e yana fad'in barima inje ind'auko Nafisa ta koma makarantanta.



🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴
 Tun acikin bacci yake jin gumzan kukanta  arazane ya tashi yana mutstsuke idonsa Durk'ushe ya ganta a gefen Gadonsa ta kifakai a bakin gadon cikin kad'uwa yace  "ke Nafisa lfy?  Meyafaru?  Waye ya mutu kuma? D'ago kanta tayi ta kalleshi da rinannun idonta sukyai jazur  asanyaye yazamo da k'afafunsa k'asa "pls Nafisa gayamin meyafaru? Matsoshi tayi tad'ora kanta akan k'afanshi  tana shshshek'a  "Dady ne yazo wai lallai sai na koma school agobe  wani irin ajiyan azuciya ya sauk'e yasa hanu ya d'ago kanta suka zuba wa juna ido hankacif ya d'ago akan bed side ya mik'amata share hawayen ba musu ta karb'a tashare tas sannan ya nunamata stool  tazauna suna fuskanta juna,

  "Haba Nafisa yanzu akan wannanne yasaki iri wannan kuka kinsan yanda kika d'agan Hankali kuwa?  Karatunne bakiso?

 Langab'ar da kanta tayi  "har yau bansan matsayina agunkaba duk tsawon zamana da nayi sa agidannan KB sabo da kai  nayishi saboda niman soyyayarka, duk da Mami tace min kana sona amman zuciyata tana waswasi KB  wlh inasonka inna rasaka bansan yanda zanyiba  ta k'arasa da muryan kuka,  KB kan k'uramata ido yayi yanzu kam ta daina bashi haushi mamkinta yake ji gami da tausayi wai abunda take fad'a har ranta take fad'a? Shidai yanaji anace so amma bai san yaya ake jinsaba, amma dai ko ma yayane yanaganin amatsayinta na "ya mace bai kamata  ta nuna har hakaba,  bai yi auneba sai jinta yayi  ajikinsa tana wani sabon kuka " pls KB kar kabari sonka ya illatani ahanzarce yacireta ajikinsa "stop it Nafisa is ok kije zan fito zamuyi maganan pls yafad'a gami da mik'ewa sake rik'oshi tayi ganin tana niman tajefashi awani hali yasashi daka mata tsawa  "leave me mana Nafisa  k'ara rushewa da kuka tayi ta kuma shegewa jikinsa,

  Gaba d'aya yarasa yanda zai da ita dai dai lokacin Mami tashigo dama tun da dadyn Nafisa yace mata lallai gobe zata koma tasa kuka tayo part d'in Kabir Hankalin Mami yayo wajen duk datana kyautata zato ma d'annata hankalinta bai kwantaba don tasan sharrin keb'antuwan namiji damace, ganin shirune yasa ta biyo baya, sosai ta girgiza da yanda taga Nafisa manne ajikin Kabir wani irin kallon tuhuma tabishi dashi dukda ya cire Nafisan ajikinsa bata daina masa wannan kallonba  Hanun Nafisan kawai takama tafita da ita batare da tace komiba,  jikin Kabir bak'aramin sanyi yayiba me Mami zata d'aukeni? Meyasa takemin wannan kallo?

Ganin baida Amsane yasa yashige bayi yayi wanka yayi Allolan zuhur yashige masjid bashi yashigoba sai da akayi la'asar nanma Mamice tamishi waya lallai yazo yaci Abinci,


Bayan sallahn isha ne Mami ta tarasu batare da taji daga garesuba tace Nafisa tashirya gobe ta koma in Allah yasa Kabir mijinta ne tana dawo wa wani hutu za'amusu baiko  daga haka ta umurci kowa yawuce makoncinsa
🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴 "Dijah! Dijah!!
 "Na'am   ta amsa sannan ta nufi inda ake k'iranta, agefe ta tsuguna inda "yar'uwanta take tsugune

  "gani Inna, inna ta harareta "wai meyasa kika raina Bintalo ne,

 shin ba yar ki bace? Ta turo baki tace "inna fa nariga tad'aukan tulun,

" kinrigata d'auka bayan kowa da nasa, meyasa bazaki d'auki naki ta d'auki nataba? 

 "inna fa nawan ya tsufane wlh ni banasonsa, wannan nakeso,

 cikin sanyi Bintalo tace "inna nabar mata nawan zan dinga d'aukan natan,   da tun farko ma tace tafison nawan dana bata

"bazaki bataba inma kin bata kwanannan zatace kisake bata wannand'in, tashi kitafi abunki, in Ruwanne bazata d'ibo tabarshi kawai,
Bintalo ta tashi kenan Baffa yashigo,

 ai Dijah tana ganin Baffa tasa ihu da sauri ya k'araso inda take yana kallon inna

 " mene ne kuma? Me kukamta saboda Allah ku kunfison kullum yarinyannan tayi ta kuka kumafa kunsan illan kukantannan fa Lamindo na gayamiki,

inna ta tab'e baki sannan tayima Baffa bayanin yanda akayi Baffa yace
" assha indai akan tulu ne karkidamu mamata maza jeki wajen Barde kizab'i wanda kikeso inna fito zanbashi kud'in ai bai rufe bakinsa ba tadaka tsalle ta tashi ta je dai dai fuskan Bintalo ta zaro harcenta da k'arfi tanamata woooo woooo wululu ta fice daga inna har Baffa sai da sukayi Dariya, Baffa yadafa kafad'an Bintalo yace "nasan kina hak'uri da Dijah kiK'ara kinji ummata? Murmushi Bintalo tayi ta gyad'a kai ta da'uki tulun ta tafita


Su hud'u suka jero Bintalo da ma'u  sai Dijah da Aminiyanta jebu k'anwar ma'u, kowacce d'auke da tulun Ruwanta, haka suke ko dayaushe inzasuje rafi d'ibo Ruwa tare suke zuwa sai dai randa Dijah ta k'wayance, shine zasu tafi daban daban.

Dijah ta lakato jebu sukayi baya alamun zasuyi magana "ke bakiga nayi sabon tulu bane? Nan tabata lbrn yanda akayi Baffa yasayamata suka k'yalk'yake da dariya har su Bintalo suka juyo suka kallesu  jebu tace "ai kafin in iso rafi lado ya tareni ya fad'amin da sauri Dijah ta juyo ta zaro ido takalleta lado? Yaushe yaganni? "Yace min yaganki lokacin da kikaje wajen Barde saya,

Jebu batayi auneba sai ganin Dijah tayi ta sauk'e tulun tazauna akai tasa hanunta tarufe bakinta, tana son tuno mema tayi lokacin da taje wajen Barde, jebu ta kwashe da dariya ke dalla kitashi mutafi, kunya Dijah taji kamar k'asa yatsage tashiga shikenan tabari saurayinta yaganta tana gudu  tsaki taja tad'auki Ruwanta taja bakin gyalanta da tasha d'amara dashi tarufe fuskanta, jebu kuwa sai dariya takeyi Dijah tace "yasin yau bazan je Dandaliba, "kai Dijah matsalata dake kenan abu kad'an ki k'i zuwa dandali Alk'ur'an innaje dandali bakinan sam bani jin dad'i  "ai sai kiyi tundanace bazanjeba kema kin san bazanjeba, "to shikenan muje gidan jummala Amarya,
 "cab wlh bazanjeba jummala ita da Mijinta "yan iskane, ba abunda sukeyi agidan  inba iskanciba wlh da k'yar imba asasu awutaba, ni wlh natsani d'an iska arayuwa, jebu tace "ke ancefa haka akeyi in anyi auren, wani dogon tsaki Dijah taja "wlh k'arya ne, da haka suka iso kowa tashige gidansu Lokacin da Dijah ta shigo gida tasamu Bintalo tayi wanka har tana  kwalliya,  "Bintalo harkinyi wankane?
"Iyi bakun tsaya Hira ahanyaba?  Harnazo nayi wankana, zakije dandaline?  "Bansaninba tafad'a tana murgud'a baki ko kyauma bakiyiba Aljana akwaba, murmushi kawai Bintalo tayi ta tashi tasa kaya ba irin tsokanan ta da Dijah batayiba amma tak'i kulata, dan Bintalo akwaita da Hak'uri duk abun da Dijah zata mata bata tankawa sai dai intak'urota nan kuma intarik'eta jibganta takeyi  son ranta, da Baffa kuma yaji zai hauta da fad'a duk dayasan niman tsokana irin na Dijah da hak'urin da Bintalo takeyi da ita,

Haka ta  k'araci murgud'e murgud'en bakinta tafita batare da Bintalo ta kulataba, ak'ofan d'aki taci karo da inna da tafito daga wanka,  "inna kinga kirabani da  Bintalo  kallonta kawai inna takeyi batare da tacemata komiba ta wuce tana d'an k'unk'uni wlh wataran sai nafasa ma yarinya Baki inna ta girgiza kai tana d'an murmushin gefen baki ahankali tace Allah ya shiryar dake Dijah am,


Muje zuwa
~ummu fatima~ 🇳🇬
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MY NATION*🇳🇳🇬

*ISLAM MY RELIGION* 😘🕋

*jinjina gareku group d'in DAMATA (3) BATUL'S NOVEL* 🤝🏻👍🏻 inajin dad'in zama da ku sosai Allah yabar k'auna😍😘



*sis Sameena Aliyu* 😍😘
*sis Batul Adam jattako* 😍🙇🏼‍♀ 
         
_Inayinku sosai don haka nabaku kyautan wannan page baki dayansa_
  *ALLAH yabar k'auna*🤝🏻

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 7⃣



Tunda ta fito daga wanka tayi sallahn azarhar, tazauna da madubi ahanunta tanata d'ige 2 duk ta fente fuskanta da janbaki da kwalli, sai kallon fuskanta takeyi a madubi ta zaro ido ta murgud'a baki anjima kuma ta kece da dariya abin da takeyi kenan har akayi k'iran la'asar tana zaune agun tana wannan shiririta,

  Ahaka jebu tashigo ta sameta turus tayi tana kallon Aminiyar tata, don kuwa tsawon zamanta da Dijah bata tab'a ganin makamancin hakan afuskantaba idanma taga masuyi ta dinga tsokanansu kenan  tana dariya, agefenta ta zauna tana kallonta "Dijah yau lfy kuwa?


 Cigaba tayi da zanen fuskanta abunta ko kallon inda jebun take batayiba "irin wannan kwalliyan Dijah ko zamuje Dandalinne?

wlh kar kiga  yanda ya cika da jama'a lado ma yanacan yasha kwalliya sai nimanki yakeyi, kusan sati ukufa kenan baki lek'a dandaliba,   Don Allah kizo mutafi karkato da madubin Dijah tayi dai 2 yanda suke kallon fuskan juna,  Harara Dijah ta galla mata sannan ta jinjina kai alamun ki kiyayeni, sannan tacigaba da kwalliyanta, 


jebu ta riga datasan halin Dijah tunda batayi niyan maganaba tasan bazatayinba,

  haka tasan Dijah bata cika zuwa dandaliba dan acewanta duk randa taje sai kanta yayi mata ciwo, 


   Saidai yanda lado ya matsamata akan maganan Dijah ne yasa tace bari tagwada  sa'anta tagani,

 gashi tazo tasamu Dijah akan tsini tunda ko arzik'in magana bata samuba,

Sada ta gama don kanta ta shiga niman kayan da zata sa wani riga da zani tad'uko pink mai hoton taurari blue ajikinsu dariya tayi lokacin da take ware kayan don ranta yanason pink colour,

Har tagama shirinta tayi sallah jebu tana zaune tana jiranta, tare suka fito sukashiga d'akin inna, sosai inna takebinta da kallo,  sannan tayi magana Dijare am yau kece da wannan kwalliyan haka?  Ina zuwa? Dariya tayi tace "inna zanje gaida goggoji ne "to kice ina gaisheta,

   Suna fita Dijah tarik'o hanun jebu "ke kan tudu zanje can waje larito don jiya amakaranta ancemin tayi gulmana, cike da tsoro jebu takalleta don tasan fad'an Dijah ba abu mai sauk'i bane, intafar batajin zata daina, wani hikimane yazo ma jebu, "wai me tace miki? Wai cewa tayi ni masifaffiyace,

  "kinsan Allah k'arya akamata don kawai anga kuna shirine shiyasa za'ahad'aku fad'a cewa tayi tanasonki da k'awa inbaki yardaba kuma zo muje dandali ki tambayeta tanacan,

  Dijah ta tab'e baki nifa nacemiki bazan je Dandaliba zo kawai muje mu gaida goggoji,



  Acan dandali kuwa Lado yayi jiran tauraruwan tasa har yagaji,  yana tsaye yana kallon Abokansa kowa da budurwarsa,  ga "yan mata dayawa wa inda suka fi Dijah girma suna sonsa amma shi Dijah kawai yakeso, dik da har yanzu bai gane inda  ta dosaba, shin tana sonsa koba tasonsa, bata yarda suyi hira ko yaje k'ofar gidansu gudunsa takeyi,

Duk dahaka ya kasa rabuwa da ita don Dijah one in townce kykkyawace na bugawa amujalla duk rugan juma ba "yar data takaita kyau, tana da fasali mai kyau sosai, samaruka da yawa sunyi yunk'urin niman Dija saidai basu samun fuska ladone kawai daya nuna yana sonta bata balbaleshi da masifa, 


  Lado d'an gidan Hard'on garine Hard'o afualatanci yana nufin sarki, lado yayi zaman Birni dan haka kaf Rugansu ba saurayin da yakishi gayu dawayewa,  shiyasama Dijah takesonsa don tanason d'angaye arayuwanta, saidai shiriritanta, yahana lado ya gane tana sonsa, Dondai Dijah ba dai shiriritaba,
 

   Washi gari da dafe Dijah tunda ta idar da sallah take takiciniyar ayyukan Gidansu kamar yadda tasabatayi sharanta fes ta ttara wanke wanke tayi tana kife kwanuka  Baffa yashigo da keke da jarkan ruwa akai da gudu tanufoshi tarik'e masa keken tana ta jero masa sannu sai k'ok'arin sauk'e jarkan takeyi Baffa yace "a'a mamata barshi bazaki iyaba, "Allah Baffa zan iya "to barin kama miki, tare  suka kama suka juye aranda, ya juya yana kallonta da wutsiyan ido, yana d'aure jarkan ajikin keken tazo tarik'e kamar zatayi kuka

Baffa dan Allah karka koma zamu je mud'ibo ni da Bintalo,

 murmushi yayi daman yasan za'ayi haka, sam indai Dijah tana gida bata barin Baffa yayi komi ko itace saitace zasuje suyi shikuma tausaya musu yakeyi amtsayinsu na "ya"ya mata baya son suke wannan wahala,

 shiyasa tunkafin tatashi daga barci sai yaje yadebi ruwa yayo iatace, inta tashi tayi tamitan batason yake wahala sunanan.

  Cikin sigan Rarrashi ya dafa kafad'anta karkidamu mamata sawu d'aya zank'aro  kinga fa zaku tafi makaranta, inkince sai kun d'ebone zakuyi latti amuku bulala, a'a Baffa kabarshi wlh bazu d'ebo ganin tan shirin yin kukane yasashi ajiye jarkan, dai dai lokacin Bintalo tafito donyi musu abun kari, ita kuma Dijah ta d'auki tulu ta tafi d'ibo Ruwan, 

  Tafe  suke cikin Unifoam Riga da wando da hijabi Blue du hud'u kamar yanda suka saba ko ina zasuje Bintalo da ma'u dune agaba Dijah da jebu suna baya hiransu sukeyi harsu ka iso gida su jebune da yarta ma'u sukafara shiga gida sai su Dijah tunda tacire unifom take kwance, inna ta shigo tasameta  "Dijah kifita kuci Abinci tund'azu Bintalo take k'iranki kinyi burus, ta yatsina fuska "inna mekika dafa? "Shiinkafa da miya,  "nidai nak'oshi tafad'a tana turo baki "mhmm dama nasan za'arina inna tafad'a tana fita,

 
     Sai da tagama kwanciyanta tafito anan tasamu Bintalo tana zaune gefenta kwanon Abincine arufe tabud'e kwanon taga Abici ta kalli Bintalo ina Aaabincina? gashi naci nabarmiki, wani mugun kallo tamata ninema zakici abinci kibarmun dankinrainani, wlh bazam yarda ba kibiyani Abincina, "kefa kikace bazakiciba kuma aigefe naci baduka na tab'aba, "wlh nidai bazanci k'azantankiba saida kika jagwalgwala zaki barmin? Nanfa Rigima  yakaure tun Bintalo batakulata har tagaji ta amsa mata ganin da gaske Dijah fitina take nima yasata tashi da  niyar barin gurin da sauri Dijah tasha gabanta bainda zakije sai kin biyani Abincina "Dijah kinga kifita ahanyana zan marekifa, wani kallo  raini ta mata "basai kimaranba wlh yarinya barganin kinfini tsayi ai baki fini karfi ba, dai2 lokacin inna ta fito daga  d'akin Baffa, tana tambayansu  Bintalo tamayar mata dayanda akayi

 inna ta rik'e Hab'anta da hanunta "Anyah Dijah meyasa kk da fitinane damman tun shigowanku nagano rashin arzik'i a idonki to inda gaske abincin zakici kije kitchin akwai akula kid'iba ta turo baki inna ni wlh nawakawai zata biyani,

  Inna takalli Bintalo "kinga  wuce kiyi tafiyaanki kibarta tak'arata Baffa dayake d'aki yakejinsu yayi saurin fitowa don in akwai abunda yatsana to kukan Dijah ne

 yasan yanzu zata fara don daga jin yanda case d'in yake fitina kawai take nima don  inba fitina take nimaba in anyi shinkafa dayake ranta bayaso yawanci gunsa take zuwa yabata gassasun zabi taci da madara ko nono musamman yake ajiyewa sabo da ita,

  Hanunta yakamo kai tsaye sai d'akinsa sai da yararrsheta, sannan yabata taci,

  Bayan tagama ci yabata wani magani  " Dijah karb'a kije

 can wajen masu karaya Akwai wacce nayima d'ori dasafe kije kishafamata yanzu kizo muje can gida musa matanshi takarye ke zaki d'orata.


?🌴🌴🌴🌴

       *A BIRNI*
 Dr Kabir na gano zaune a office d'insa ganin baida abunda zaiyi yanzune yasashi duba wasu tsofffin files da suke cikin drower yajima yana duba wani file guda d'aya dayasha bamban da sauran files d'in watanni kusan 10 kenan daganin mara lfyn case d'inta sereous ne da yakamata ace yanaganinta akai2 to amma gashi sau d'aya kawai yaganta meyahanasu dawowa? To ko mutuwa tayi ras yaji gabansa ya buga daida lokackin sister mena tashigo, tazuba masa ido har ta matsoshi, file d'in yanuna mata "kinsan wannan mara lfyn? Karb'a tayi tana ta dubawa nad'an lokaci tace "Eh naganeta yarinyan bafulatanin nan dasu kazo mai cronic typortdi'nnan ka tuna? Shiru yayi na tsawon lokaci amma bai tunotaba,  " sir yarinyannan dai wanda mama jumai tazauna da ita acan E P U, "Gaskiya ban tunataba haka tak'arashi kwatancenta, yakarb'i file d'in yana dubawa, *Khadijah Abubakar maid'ori*



Hahh muje zuwa Dr Kabir 🤣👍🏻


*Ummu fatima* 🇳🇬  😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MY NATION*🇳🇳🇬

*ISLAM MY RELIGION* 😘🕋



         

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 8⃣



  Mai mai ta sunan yake tayi abakinsa ahankali yafara tunota

"ok yarinyannane mara kunyannan wai suna ce mata *Dijah k'aya* tabbas yatuno sabida tsaban haushinta ma baice ma Babanta yadawo da itaba,

Wani dogon tsaki yaja ya ture file d'in gefe cikin takaici yana tuno abunda yarinya k'arama ta masa abunda yakasa mantawa,

Bazaitab'a manta wannan ranaba don tamasa abunda bawanda ya tab'a masa arayuwansa,


 Wataranan lahadi da rana misalin 1:00 yana dawowa daga wani Ruga can gaba da Rugansu Dijah, 

  Inda suke kiwon dabbobinsu tun mahai finshi yana raye yana da garkunan shanu a garin,


  Bayan Rasuwansa ne Mami takesa Kabir yaje yadubo su jifa2 awekend,


Tun Ranan monday Mami tace zaije awannan wekend d'in don haka yashirya tun safe yatafi don yana son yadawo da wuri,

 bayan yagama duk abunda yakaishi yakamo hanya,


   Yana dawowa Da misali  11:00 Ruwa ya tareshi ahanya gangarawa yayi, yayi perking a gefen hanya harsai da Ruwan ya d'auke kafin ya kamo hanya.

   Adai2 Rugan juma ya wara idonsa yana kallon garin sosai yanayin garin yamasa musamman ma dayaga yara "yan makaranta suna wucewa har aransa yaji dad'in wannan cigaban da akasamu na karatu a Rugagen fulani,

 yana ta kallonsu wasu suna tafiya wasu suna dawowa,

 Ahaka ya iso kusa dasu Dijah ita da k'awarta jebu sanye da Unifom da Alama su sai yanzu suke tafiya, suna k'ok'arin tsallakawa,

  Dijah batayi auneba Kawai sai jin Ruwan kwata tayi duk jikinta har fuskanta anwanketa dashi, d'ago idonta da tayi ta sauk'esu akan wata dank'areriyar mota,

 sai sharara gudunsa yakeyi hankali kwance baisanma yayi wani Abuba,

 Donshi baima san ya wuce su Dijah agunba Bin motan da kallo tayi,

  Cikin takaici batasanma mezatayiba ji take kamar tabishi da gudu,


  Cikin sa'a taga yatsaya ajikin wani shago  dake gefen titi zai sayi Rechart cad,


  Gyad'a kanta tayi ta nufi wurinshi da sauri Jebu ta kamo hanunta, "Don Allah Dijah kiyi Hak'uri kirabu dashi kingafa
Wannan d'an birnine irinsu ne masu shan jinin nan kirufa mana asiri karkijawomana wani fitinan,

 Afusace Dijah tak'wace Hanunta tana masifa "wlh koma wayene shi sai naji dalilin watsamin kwata da yayi,

  Alokacin data isa yana loda card awayansa, tasaya agefensa tana kallonsa, tace "Malam kaga yanda kab'atamin Jikina?

 Allah sarki Kabir, hankali sa yana kan wayansa sam baima lura da Dijah ba,

  juyawa tayi afusace,

 Saida yagama abunda yakeyi awajen yanufi inda motarsa take,

  Batare da b'ata lokaciba Yakama handle d'in motan da niyan bud'ewa yaji ya cab'a hanunsa akan wani Abun dasauri yabi gurin da kallo kashin  shanune da yahad'u da kwacab'in tab'o gabad'ayan murfin motan da glass d'in anshafe dashi cikin matsa nancin  mamaki yakebin wuraren da kallo ahankali yad'ago ya kalli gefen damansa,  Dijah ce tsaye rik'e da kunkumi tana jijjiga bai kawo komi aransaba ya kalli hagunsa ba kowa awajen sake maida hankalinsa yayi wajen da Dijah take tsaye Dariya tayi tace "kaima kaji inda dad'i, cikin rashin fahimta  yanunata da yatsa "kina nufin kice min kece kikam wannan aikin? Cikin isa tace "eh Ramukon Gayya, motarka ai baifi jikinaba  tafad'a tana nuna jikinta da Ruwan kwata ya b'ata, cike da tsiwa tayi maganan,

  Binta kawai yakeyi da kallo baki bud'e ko k'yafta ido bayayi, ta juya tana tafiya yaji andafashi,


  "Ranka yadad'e kayi hak'uri, wlh yarinyan sam bata da dad'i, cikin wani irin fushi had'e da takaici yabi saurayin da kallo, sannan ya kalli hanunsa da yake dumu dumu da k'azanta, yasake kallon saurayin zuciyarsa sai zogi yake masa ganinsa har d'aukewa yakeyi tsaban b'acin Rai,

  Muryansa har b'ari yakeyi yace "waye Uban wanna yarinyan?
Me ta taka?
Metake tink'aho dashi?


    Saurayin yace "kayi hak'uri yallab'oi kar kasako uban mahaifinta mutumin kirkine wlh da zaiga  abunda tayi sai yayi kamar ya had'iye ranshi dan haushi,


  "wai ni mahaukaciya ce  ko Aljana? KB yayi tambayan azafafe,

*Dijah Bukar maid'ori kenan yarinyace mai Hankali sai dai Akwaita da tsiwa inkashiga hark'anta bata da hak'uri komi kamata sai ta Rama ko ta d'auki fansa* 

  Inaga tayan  motan kane ya watsa mata kwata dan naga jikinta duk kwata zaiyi wiya ta maka wannan abun batare da wani daliliba gaskiya,


   Wani irin tsawa KB ya daka masa, "kai kacikamin kunne,
 wace ce ita? Dahar zakazo kanamin bad talk akanta?


   Dai dai lokacin mai shagon dayake bakin hanyan ya iso da bokitin Ruwa da omo,

  "kayi Hak'uri malam zan wanke maka motarka,  Nandai sukayi ta lallb'ashi, ya wanke Hanunsa,  ya je gindi Bishiya yazauna suka farawanke motan,


   Yana zaune awajen yayi tsaki yafi abunda yafi, zuciyansa sai rad'ad'i yake masa amon muryanta, da fuskanta ne yake tamasa kai komo,

  Wayarsa datafara Ringing ya d'auko *Mami na* yagani akan wayan ya d'auka sallama kawai yayi ta fahimci yana cikin b'acin rai 

   Cike da damuwa tace "yadai Kabir?
Me ke faruwa ne?
Kana inane ?


    "wlh Mami ina wani Rugane, "mekakeyi ?

  Na had'u da wata Nonses yarinya ce nan yabata lbrn yanda abun yafaru, sauk'e ajiyan zyciya tayi,

   "Wlh na tsorata danaga har yanzu baka dawoba,
    Shiyasa nasamo maka sojojin da zasu dinga fita da kai dan tsaronka fir kak'i, kaga dasu na wajen ba yanda za'ayi tasamu daman tab'a motarka ,

   Allah  Mami yau sainasa anyi maganinta,

   Atsorace Mami tace  "Rufa min asiri Kabir banyardaba kasan halin fulani kuwa?

Kar kayardaka kafara,

  Barin turo azo a dawo dakai,

   Yamik'e yana fad'in no mami basai kinturo kowaba ganinan dawowa,

  Duk da sunwanke motan tas harda blech baidaina jin yankyanin motarba

  Kud'i ya ciro mai yawa yabasu bai saurari godiyan dasuke masaba ya finciki motan da gudu yabar wurin,

   Tunda yake aduniya wani mahaluk'i baitab'a b'atamasa rai irin yauba,

    Kodaya iso gida Mami tasha wahala wajen rarrashinsa da k'yar yasaki ransa,

    Yanagama tunanin nonses girl d'in inji da fad'a yad'aga file d'in yamayar yadawo yazauna acikin kujera cike da haushi, kamrayanzu abunyake faruwa haka yaji.

   Ahaka yaji ana nocking yabada ixini ashigo wani cosmone yashigo "Tanka yadad'e kana bak'o,  "ok tambayeshi wayene? Jim kad'an yadawo, "wai yace ace maka Alhaji ya'u ne k'anin Alhaji Mahmud, dukda maganan yabashi mamaki da kansa yatashi ya bud'e k'ofa cike da girmamawa, yace  "Bismillah Dady shigo,


     Cikin isa da izza yashigo Kabir yajawo masa kujera ya zauna,  "Sannu Dady lfy kuwa kazo da kanka? Madadin kamin waya inzo?

    Da wutsiyan ido yakalleshi, "k'iranka kuma na nawa?
   Nak'irka yafi abunda yafi,

    Kabir yada'uko wayan yana dubawa "i'm sorry Dady ina wordne banashiga da waya word,

   Tab'e Bakinsa Dadyn yayi "naga ka rufe acount din Campanin nanne gaba d'aya  komeyasa?
 

    KB yagyara zama yana fuskantansa, "satin da ya wuce naje nad'anyi bincike  akan cigaban da campanin yasamu abun takaici sai na tar da b'arnan da akayi acampanin yazarta na kullum da akeyi,  a iya binceken da nayi akai bansan wayee yafitar da kud'ad'e masu yawa hakaba

    Cikin zafi  Alhaji ya'u yafara magana


" lallai Kabir na yarda cewa niba kad'aukeni abakin komiba,

     Ace campani yana hanuna amma karufe acount batare da kasanar daniba?

    Dame za'a biya ma'aikatan?
   Dame za'a sayi duk abubuwan da campanin yake buk'ata?

     Tun mahaifinka yana raye nike gudanarda duk wani abu na campanin nan, bai tab'a samin ido akaiba,

    Tunda yafara maganan kan KB yana k'asa yana nazartan kalamansa d'aya bayan d'aya,
     Sosai yayi mamakin k'anin  mahaifin nashi campani na hanunsa? Amma baisan yaciri wani kud'i dan developing campaninba?
  Kuma kenan yana sane da b'arnan da akeyi a campanin?
    To meyake nufi?
Yanasane da irin kud'ad'en da shima yake wawusa amma yayi kaman bai saniba, muryanshine yakatse masa tunani,
   "kayi gaggawan bud'e acount d'innan   nagayama,
   Ajiyan zuciya yayi yad'ago ya kalleshi
  "zan bud'e insha Allah amma sai na dawo daga tafiyan da zanyi,
   "ina zakaje?
   
      "zamuje Abuja wani seminner ak'arshen satinnan,
     Wani dariya KB yaga  Alhaji ya'u yayi da baisan ta mece ce ba, sai dai ya fahimci jin dad'i sosai acikin dariyan,

   "dayaushe zakuyi tafiyan?
      "Da safe,
  Gyad'a kansa yayi alamun anzo wurin,
  Tashi yayi batare da yak'ara cewa komiba, yafita gida yakoma kai tsaye tun ahanya ya k'ira kila yace yasameshi agida,

    Sai kaiwa da kawowa yakeyi a falonsa kamar wanda yakai mai haihuwa asibiti,


   Bai ko ji shigowan kila ba sai muryansa yaji abayansa

   "ya akayine Boss? Tunda naji kamin irin wannan k'iran nasan tasamu,

     Da sauri ya juyo ya dafa kila,
       "Kabir zai tafi Abuja ran asabar, banaso asamu wata matsala kila kasan duk yanda zakayi ka hala yaronnan acan kar yadawo,
    Kila yafashe da dariya anzo wajen Boss namaka Alk'awari baza'a tab'a samun matsalaba,
     Gobe juma'a don haka gobe zamuje da yarana zamu rarraba kai acikin Daji mujira zuwansa wlh sai dai wani ba Kabirba yafad'a yana datse hak'oransa,


  Kud'i mai yawa yabashi yace su sha mai da haka kila yafita zuciyan Ahaji ya'u fari tas don yana ganin mafaekinsa zai zamo gaskiya,



*Allah sarki Dr Kabir shin yaza takayane*?
*Ku biyini*












*ummu fatima*  😘😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     


*DAMATA!  DAMATA!! DAMATA!!!  LITTAFIN YA FAD'AKAR YA GAMSAR YA MA'ANAR  _SIS BATUL JIN JINA GAREKI 👍🏻👍🏻 NATAYKI MURNANA KAMMALA WANNA K'AYATACCEN LITAFI MAI SABON SALO ALLAH YAK'ARA BASIRA_*
Muna jiranki asabon buk karkidade kinji😰


🇳🇬

         
 

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 1⃣6⃣


   
 Dr Kabir  Yabi hanyan da ta shige da kallo yana murmushi,
   Yadawo da kallonsa wajen   Lado da Jebu da alamu Complain yakeyi akan Dijahn,
    Tab'e bakinsa yayi ya mai da hankali ga wayansa da yake hanunsa,

    Sunjima suna tattaunawa kafin suka jero da Lado inda   Kb da Sani suke Lado ya gaidasu Sani ne kawai ya amsa, Kabir kam sai wani hura hanci yakeyi haka kawai yaji Ladon yana bashi haushi, 
         Nika nace  "toko don yatsani Dijah ne?🤔

    Ganin irin shan k'amshin da yakeyi yasa Lado yin sallama ma Jebu   ya wuce yabarta nan suna magana da Sani,
         Kb kuwa yacigaba da latse2 wayansa jifa2 kuma yana kallon masu wucewa,
     Can ya hango
      Bintalo da Ma'au sun fito cikin kwalliya, suna tafiya suna tad'awa,  ganin Kabir zaune cikin kekensa ne yasa Bintalo k'arasawa da murmushinta ta masa sannu, Shima cikin murmushi da sakun Fuska ya Amsa mata,

      "Mamata wai yau me akeyine haka agarinnan naga kunsha kwalliya kuna yintanan yanuna Inda yaga "yan mata da samari suna yawan yin gurin da yatsansa, tana murmushi tace
 "Dandali ake zuwa, Kabir ya marairaita Fuska kaman mai shirinyin Kuka "mamata shine baki gayyaci d'ankiba, zaki tafi kibarashi

     Dariya Bintalo tayi mai sauti ta zaga tabaya tafara turashi  "bansan kana son zuwaba ne da bazan tafi inbarkaba,   


Sunzo daf da Sani zasu wuce yatare keken da k'afansa yana kallon Bintalo "ina zaki kaishi?

Kabir ya Harareshi "Dalla can malam kabamu hanya muwuce Dandalo zamuje muyi rawa, Jebu ta kwashe da dariya har tana rik'e ciki, "Inane kuma Dandalo?

     Sosai Kabir yaji haushin dariyan datakemasa, donshi baima lura cewa bai fad'i sunan Dandalin dai2 ba tunaninsa itama "yar rainin Hankalice kaman k'awata shiyasa sam baya sakemata Fuska,


     Cikin zafi yace ma Sani Remove ur Leg, matsa musu Sani yayi suka wuce Ma'u tanabiye dasu,
       Suna tafiya suna tad'i duk abunda yagani sai yatambayeta Wani lokaci tabashi Amsa wani lokacinkuma Ma'u tabashi Amsan

    Ahaka harsuka kai Dandali Nesa da gurin yasata ta'ajiyeshi agindin wani Bishiyan d'orawa,


     Suna tsaye awajen Sani da Jebu suka iso, ganin Sani yazo ne yasa Bintalo tace ma Kabir tana zuwa, dama Ma'u kam tuni tashige dandalin,

  Taku d'aya tayi ana biyu Sani yasha gabanta, yana mata wani irin kallo,
    "yanzu duk tarin samarukanki da suke zuwa gida basu ishekiba? Harsai kinbiyosu nan? 

     Cike da mamaki Bintalo tazaro ido tana kallonsa,
    Yad'an had'a fuska,  gami da d'aga gira yace "yes abunda kuke zuwa yi kenan,

    Cikin takaici Bintalo tace "duk wanda yacemaka abunda muke zuwa yi kenan yamaka k'arya kaje ka gani wasanni akeyi kala2 sannan kuma "yan wasu rugagen da basu kaimuba sukanzo ayi zumunci,

   Had'e rai Sani yayi yace "to bazakijeba, waro ido tayi sosai ta kalleshi babu alamun da wasa yayi maganan, 

    Turo baki tayi ta kalli Kabir dayacika da tsananin mamakin Sani harwani karkace kai yayi yana lek'a fuskansa,

   Dawowa tayi daf da Kabir tatsaya tace Likita inason inje wajen wata k'awatace "yar Rugan lelam,

    Murmushi Kabir yayi yace Fatima kinason Sani?

 Wara idonta tayi tamasa kallon kaima haka zakamin? 

     Murmushi yayi ya d'an sassaita muryansa "pls mamata  Dagaske nake tambayanki, banison atakuraki inkina da wanda kk so Dole ya hak'ura,


    Ahankali Bintalo tafara ja dabaya sannan tajuya cikin nitsuwa takama hanyan Gida, "Fatima!, Kb yak'irata ko juyowa batayiba, Sani ya juya zai bita Kabir ya rik'o hanunsa yace "kai sam baka da kunya wlh,

    Sani ya langab'ar da kai yana kallon Kb "kenan tana nufin bata sona?

   Kabir ya Harareshi "to meye imbata sonka?

Kaman zaiyi Kuka yace "pls Kabir kataimakeni wlh I really Love her,

    Gajeren tsaki kb yaja yace "shikenan kaima kazamo d'an iska irinsu Habib,

     Sani ya shafa gashin kansa yana kallon Jebu da take zuwa wurinsu rik'e da leda ahanunta, yace "Kb duk yanda zangayamaka bazaka fahimtaba amma wlh ina sonta sosai,

   "Nidai nagaya maka ka daina mun irin wannan magana,  inbanda iskanci ba abunda kuka iya kutak'ark'are kuyi ta maganan banza akan k'ananun yara wai kunason su,

  Dai dai lokacin Jebu ta iso,
    Ledan daya ke hanunta tamik'a ma Sani, ya bud'e yaga Rogo ne yana dariya ya d'auki guda d'aya "Nagode Zainabu har da tsarabane haka?

 Murmushi kawai tayi ta mik'a ma Kabir d'aya ledan, kafe Ledan yayi da ido sannan ya tab'e baki yace "baniso d'azu ma wa kk dariyan Rashin kunya,

     "Ayyah kayi hak'uri dandalo dakacene yabani dariya, gyad'a kanshi yayi yace nibana cin wannan abun jekici kayanki,
   Yad'an lek'a bayanta "Kunyi fad'a da Aminiyanki ce? Naga banganku tareba,
    "ai bama fad'a kuma bama rabuwa da Dijah sai awajen zuwa dandali,  bata zuwa sai randa taga dama, 

       Ya tab'e baki meyasa? 

"Ra'ayinta ne hakan sam bata jituwa da mutane daga inda mutane suka fi biyar to ita zama acikinsu matsalane awajenta,

    Shiyasa ko biki taje bata wuce minti goma awurin zata koma gida,

     "Mhmm ai saboda tsaban masifantane shiyasa bazata iya zama da mutaneba hatsabibancinta yayi yawa,

    Jebu tace  "aifa Dijah ba masifasiffiya bace saidai in mutum bai fahimcetaba,  ita dai bata da hak'urine kawai amma bata shiga sabgan mutum,   hararanta Kb yayi yace "Eh aibazaki fad'i laifintaba tunda kina tsoronta harkarb'a mata fad'a kkyi,

    Sani dai yana jinsu amma bai tankamusuba, harsaida suka gama

    Kb yace ya maidashi gida kafin suka dawo,


      Ak'ofar Gida suka samu Dijah tana zaune Akan Dutsi tana rik'e da k'ananun duwatsu tana cillasu sama,

    Tundaga can nesa Kabir yake k'aremata kallo harsuka iso, da ace wata yarinyance mai mutunci sai ya yaba ma kwalliyanta don shi yanason dressing d'in fulani yana masa kyau sosai,

     Kayan fualanine irin farare tas  d'innan Riga da zani  anmishi ado  da ja da green d'in zare tajera abun wuya farare sur wuyanta ga wani ta ke waye kanta dashi  ya sauk'o har goshinta gashinta yasha gyara saidai har iyau fuskanta ba kwalliya,

  Sani da yake atabayansa yana kallon irin kallon dayake wa Dijah itakuwa ta wutsiyan ido take kallonsu,

 azahiri zakace batasan da wanzuwansu agunba, da gayya Sani ya turoshi gab da ita, dagangan ta d'ago wani k'aramin dutse kaman zata cafe shi yanda takeyi, kawai ta k'wala ma Kb  a idon sawunsa,


Ya salam! Sani ya fad'a yana kallonta zabura tayi kaman da gaske ta kalli fuskan Kabir da yaciza lip d'inshi nak'asa dan ba k'aramin zafi yajiba,  hanunta biyu ta had'a cike da shak'iyanci tace "dan Allah kayi hak'uri Gurgu d'an birni ban gankabane, 🙏🏼😰

  Cikin zafin nama ya mik'o hanu da nufin damk'ota sai dai ina tuni ta mik'e har ta isa dai dai k'ofan da zai sada ta da cikin gida, ta juyo ta kalleshi ta kece da dariya har tana sunkuyawa k'asa tana rik'e cikinta, 🤣


   Sai da tayi mai isanta, sannan ta fara tafa Hanunta tana fad'i "Eh walale walale walale wa aka jefa wa yayi jifa Gurgu d'an birni, waya tab'o?
Dijahn  Baffa waya gayamaka za ka iya?   Eh jama'a kuzo kuga gurgu d'an Birni wai shi zai jah da Dijahn Baffa, kugayamasa yayi kad'an,
Tak'arashe wak'antan da wani irin  dariyan shak'iyanci tana zaro harce😝

    Duk yanda Sani yakai da son danne dariyansa dan kar yak'ara fusata Kabir abun yaci tura sam shi baisan  shak'iyancin Dijah yakai hakaba sai yau,


       Kanta Sani ya nufo kaman zai kamata ta arce cikin Gida aguje caraf  Inna ta kamo Hanunta cike da tsoro da mamaki don sam bata tab'a tsammanin akwai wani abu tsakaninsuba, sam batayi tunanin Dijah zata musu Rashin mutuncintaba, kasancewansu bak'i agarinma baki d'aya, donko da tajiyota tana wak'a batagane dasu takeyiba sai da Bintalo ta gayamata,

      Janta takeyi har sai da ta kaita gindin Bishiyan lallen da yake gidan tana k'ok'arin ciran bulala, don wannan karonka batajin zata k'yaleta duk irin abun da takeyi takan zuba mata ido,

       Cab d'i Sai dai inaga dad'ewan da Inna tayi bata kama Dijah da sunan duka ba shiyasa ta mance halin Dijah awajen duka, sai dai yanzu tana ta tunamata, don kuwa wani iri k'ara da ihu da Dijah takeyi nema ya hana innan katab'us gashi ta rik'e bulalan, sai kururuwa takeyi don Allah inna kiyi hak'uri inna bazan sakeba wayyo na shiga uku wayyo idona wayyo wuyana wayyo jama'a innata zata kasheni inna kiyi hak'uri,

      Alhalin ko kallon banza innan bata fara mata tukun,  sai tsalle takeyi duk wanda yaji irin kukan da takeyi zai d'auka ana gab da kasheta tsaban duka,


   Haka yake gasu Kabir da suke k'ofan gida duk irin haushin da tasa Kabir aciki jin irin tsalle da ihun da takeyi ba k'aramin tausayamata yayiba, gaba d'aya yaji jikinsa yayi sanyi musamman tunawa da yayi akan abun da tamishi innan take suburbud'anta duk sai yaji kunya takamashi,


     Tofah kankace kobo mak'ota sun fara cika gidan inna sai dai duk wanda ya shigo sai yaga inna rik'e da hanun Dijah d'ayan hanun kuma tana rik'e da bula Dijahn kuma ta rik'e bulalan tana tsalle tsayawa kawai sukayi suna ba inna baki wasu kuma suna dariya inna kam ba abunda tace kuma bata saketaba dan tasha Alwashin sai ta suburbud'eta ahaka innansu Jebu ta shigo kai tsaye gurinsu ta nufa taje ta k'wace hanun Dijah acikin na inna, dai dai lokacin Baffa ya iso k'ofan gidan ai bai san lokacin da yayi wurgi da kekensa ba ya shige cikin gida ahanya sukayi kicib'us,

       Cikin tashin hankali Baffa ya kwato hanunta ya koma ciki da ita abaranda ya tarar da inna,

        Ko kallonta baiyiba yashiga d'aki  da ita abakin gado ya ajiyeta yafara share mata fuska tayi jajazur da ita kallo d'aya zaka mata kazata tasha bugu har da na A'uzubillah, sai ajiyan zuciya take gaba d'aya ran Baffah ya jagule bayajin zai yima innan afuwa wannan karon donji yake kaman yayi kuka ya huce shiyasama  ya wuto da ita d'aki don inyatsaya agun innan yasan baza'ayi mai kyauba,

     Ruwa yabata arandan k'asa mai sanyi tasha sannan ya lakato zuma ayatsansa yasa mata abakinta talasa haka ya tayi mata har tayi bacci ya gyramata kwanciya ya fito,

   Tofah inda yabar inna anan yasameta gefenta Bintalo ne k'irjinta sai bugawa yakeyi

  ( *domin da iyayenmu bak'aramin shakkan mazajensu sukejiba kodakuwa suna da gaskiyane basa nitsiwa in sungansu cikin b'acin rai sab'anin mu ayanzu dagangan zakiyi abu dan kib'ata masa rai kai wasu kama har sa insa sukeyi da miji "yar'uwa ko badon ki mallaki mijiba kibishi don shid'in Ajannanki wlh sai kin bishi kafin kishiga aljannah shi namiji yana da wani abu wlh zai iya rufe ido yaci mutuncinki akan abunda shi kansa yasan bayi da gaskiya akai ammma inkinyi hak'uri tun aduniya zakiga sakamako Allah yabamu ikon yin hak'urin bin mazajenmu*🙏🏼😭)

  Tun kafin ya iso cikin dabara ta aiki Bintalo gidan Goggoji

 ( *don bai daceba kuyi magana na b'acin rai agaban yaranku*)

     Cikin b'acin rai yafara magana wato Karimatu ni ban isa in hanaki ki hanuba? Sau nawa ina miki magana akan yarinyannan? Shine dan kin rainani zaki kama kimata irin wannanduka? Fad'a yakeyi ta inda yashiga batanan yake fitaba, har sai da yayi mai isansa kan inna yana k'asa badon batajin zafin kalamansaba don dai koda Dijah "yar rik'oce ba ita ta haifetaba  bai kamata ya dinga mata hakan akantaba,
Daga k'arshe yace "ki kwantar da hankalinki tunda kin tsaneta zan d'auketa inbayar da ita agunda za'arik'emin ita da amana ba cutarwa, ai da gangan kike matsa mata dan kinga sunan uwa tace meyasa baki matsa ma Bintalo haka? Saboda sunan uwanki ce da ita, daga haka yajuya yafita, sam b'acin rai ya rufema Baffa ido yamanta da banbancin hali dake tsakani Bintalo da Dijah,

        Bintalo takasance mai nitsuwa da hak'uri
        Yayin da Dijah takasance mai tsananin fitina tun tana yarinya ga k'iriniya ita dai sauk'inta batacikayi ma babba Rashin kuntaba amma sam Dijah bata da dad'i,

       Inna tajima awurin tana Addu'an yayewan bak'in ciki don maganganun sun batamata rai dayawa, 

     Tunda ta idar da sallahn isha'i taketayiwa Dijah Addu'an Allah ya shiryeta, ahaka har tajiyo shigowan Baffa tafito alokacin Dijah da Bintalo suna zaune ba mai cewa komi,


   Da sallama tashiga alokacin yana zaune bakin gado kallo d'aya yamata yakau da kai duk da kwalliyanta yaburgeshi don  inna ta iya kwalliya na hankali, wani lokaci inta tsara kwalliya bazaki tab'a cewa arugan fulani takeba,

    ( *nikam nace inna kodai kwalliyan ban hak'uri da Rarrshine?*) 😍

   Ak'asansa ta zauna daf da k'afanshi  ta jiye mishi damammen fura ta kalleshi malam ga fura ko har yanzu fushin kakeyi dani? To inma fushinne kayi hak'uri na tuba ka yafeni, tafara janmasa yatsun k'afansa

    Janye k'afan yayi alamun har yanzu bai huceba ta marairaice to Malam inbaka hak'uraba kamin hukuncin da zakamin Amma don Allah kadaina fushi dani,  ahasale yace hukuncin kenan bazaki sake ganin Dijah a idonkiba, tunda ba ki k'aunanta, murmushi tayi tace haba Malam ya za'ace bani k'aunan Dijah ai koban k'aunaceta don tana "yata ba zan k'aunaceta don kana sonta nikuma ai masoyiyarkace,


    Don Allah kar son Dijah yasa katake gaskiya kasanfa irin hak'urin da nakeyi da yarinyannan tun bata kai hakaba, kafin kayankemin hunkunci Bincike yakamata kayi,


      Saida tagayamasa maganganu masu dad'i sannan tagayamasa abunda Dijahn tayi ta d'aura da kuma wlh ko bulala d'aya banmataba duk wannan karad'in datayi,

 Shiru kawai yayi najin kunyan matannasa amma sai ya wayance da aini dama kukantane banaso kinsanfa tana da matsala, don Allah kidinga rabuwa da ita kawai daga nanan dai saiga ma'auratan suna dariya daga baya kam ai sai zance yasauya tsakinn inna da Baffa nikam nace barin 🏃🏽‍♀







   *Ummu fatima ce* 😍
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MY NATION*🇳🇬
          _Sis safiyya nayarada da soyayyanki gareni wlh nima ina sonki Dijah tana gaisheki_
  *ALLAH yabar k'auna*🤝🏻

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 9⃣


Tun bayan fitan Alhaji ya'u Dr KB yake zaune agun kaman andasashi tunani kala2 yakeyi akan k'anin mahaifin nashi, baifitoba saida akayi k'iran sallahn la'asar, daganan gida yawuce kai tsaye,
   
        Yau yakama Asabar shine ranan da Dr KB zai tafi Abujah, tun dawowansa daga sallahn Asuba yazauna afalo yayi karatu Alk'ur'ani sannan yayi azkhard'in da yasaba, sannan yafito,

  Kaitsaye sashin Mami ya nufa yana k'ok'arin shigewa bedroom yaji motsi akitchen yadawo da baya  ya lek'a Mami yagani tana had'a break yak'arasa ya langab'ar da kanshi haba Mami keda yakamata aganki akwance shine kika shigo kitchen,

    Mami tad'an zaro ido Akwance kuma Kabir? a haba ai tunda akayi sallahn asuba bacci kuma yak'are ai ko ka manta Hadisin manzo Allah (s a w) da yace baccin safe yahana arzik'ine

  Kuma   ma ai ba asan mace da Baccin safe ba,

"Mnnmm duk da hakadai is too early Mami,

  Ina early d'ana zaiyi sammakon barin gida?

     "Kina son wannan d'anaki da yawa Mami  Mezan miki insa ka miki da wannan soyayyan ya fad'a yana nad'e hanun rigansa,

  "kayi aure Kabir kazauna da matanka da Aminci ka hayyayafa inga "ya"yanka aduniyannan kafin inmutu, inkayi haka kasakamin Kabir, cikin sanyi jiki yake kallonta har yagama nad'e hanun rigannasa ya matso yakarb' firan dankalin da takeyi,
    Yanad'an murmushi yace  "insha Allah Mami zan cikamiki burinki,
    Tayaya kenan Kabir d'ina?   Anata gumu dakai ga mata nan suna sonka kai baka sonsu? Tafad'a tana lek'a fuskansa da yake ta sinne shi k'asa yana matik'ar jin kunyan wannan lamarin aduk lokacin da Mami ta d'ago Maganan wai ace Mamin sa mai sonsa da k'aunarsa  amma yakasa yin abunda takeso,


    Cikin jin kunyanta yace Mami to ke waccece ta kwantamiki arai?
        "Nikuma?  Haba dai Kabir nizan zauna maka da ita ? Kazab'i wacce kaleso dai acikimsu,

     "yand'anyi mumushi yana kuna gas yakalli Mami da take tace gyad'an kunu fuskanta k'unshe da murmushi yace "Mami ai indai dan sone zanyi aure bazan tab'ayiba don inaga bayan son ki Mami innace inason watama k'aryane yak'arasa maganan yana d'ora mangyad'a akan gas,

     Shiru Mami tayi tana nazarin maganansa, Kabir yajima yana fad'an wannan kalma, saidai ita takan alak'anta hakan da yarantace,

    Murmushi tayi tace " To shikenan nizan auramaka wacca nakeso dama jiya yarinyannan Aliya ta zo tagaisheni,
     Ahaka sukacigaba da hiransu irin na d'a da uwa harsuka gama, Mami tana zubawa shikuma yana kaiwa daining yana shiryawa, yana gama jerawa ya wuce  sashinsa dan shiryawa, 

    Da waya kan wayan da Mami take ta masa yasamu yashirya cikin suit bak'ak'e da farar shirt taciki takalmansa ma bak'ak'e da farar socks aciki, idonsa manne da farin glass agogon hanunsama na bak'in fatane Sai k'amshi yakeyi kaman sabon Ango Afalo yatarar da Sani yana had'a masa abubuwan dazai buk'ata,
   "Sani ya kalleshi cike da zolaya "Mami tana ta mita wai ita kam ta gaji da halinka kullum sai ta tsaya akanka kake shiryawa kaman k'aramin yaro ita kam aure zatamaka ta huta,
   Da k'afa Kabir ya wurgoshi da wani cup, Sani yakauce da sauri yana dariya
Atsaye yasamu Mami tana kallon agogo, tana ganinsa tazabga masa harara, kansa ak'asa yana murmushi yak'arasa wajen dining yaja kujera yazauna, tana zuba abincin tana tura mishi gabanshi, tana mitan k'in yarda dayayi yatafi ajirki, "mmn Mami nifa nafison intafi amota indai k'asannane, yafad'a yana mik'ewa to Allah ya kare  Kabir kayi Addu'a kuwa?
  " Eh nayi,

  Tana rik'e da hanunsa kaman wani yaro d'an shekara uku, har sukafito Sani yana tsaye rik'e da murfin mota, cikin kulawa Mami ta amsa gaisuwansa, tad'ora da Sani kunyi Addu'ah? "Eh Munyi Mami, tajuyo tana kallon KB da shima ita yake kallo ko k'yafta ido bayayi ta rik'o hanunsa taturashi cikin mota tana takoro musu Addu'a, moto ci  biyarne hud'u cike da sojoji biyu agaba biyu abaya na Kabir a tsakiya Sani yana tuk'awa harbakin gate Mami ta rakasu tana kallonsu harsai da suka b'ace ma ganinta, ta koma cikin gida, ji tayi gidan yamata fad'i dayawa gashi yauba aiki, dahaka ta k'ira wayan Hajiya Rabi matar yayanta da suke uwa d'ya uba d'aya tace ta turomata yaranta su rage mata zaman kad'aici,

      🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴

Cike da nishad'i suke tafiya suna hira suna tuna zamanin yarantansu  jifa jifa suna dariya,

   Wannan na d'aya daga cikin abunda yake k'arasa Sani k'aunan KB da respecting d"inshi sam bai d'aukeshi matsayin wanda yake aiki k'ark'ashinsaba, dagashi har Mami,

  *Bari muje waye Sani*
Sani dai ada mak'ocin  su Kabir ne tare suka taso suna primary Allah yayi ma mahaifin Sani Rasuwa,


. Mahaifiyarsa ta d'aukeshi suka koma Gombe da zama kasancewan dama yar can ne, anan yacigaba da Rayuwa har ya kammala duk karatunsa daganan yafad'a aikin soja  Sai kuma wata jarabawa ta fad'omasa Gwamnati ta dakatar dasu sakamakon wani matsala da  a kasamu  Sojoji dashi, bak'aramin damuwa Sani da mahaifiyarsa sukayiba, ana haka Allah yakawo Kabir garin Gombe duba wani campani dayakeso yasaya, kwatsam Allah ya had'asu ba k'aramin murna sukayi da ganin junaba nan sukayi ta hiran bayan rabuwa anan Sani yake gayama Kabir halin da yake ciki ba k'aramin tausayasa masa Kabir yayiba, Baiyi k'asa agwiwaba,  daya tashi tafiya ya tafi dashi dazummar nima masa aikinyi, tofa alokacinne kuma Alhaji ya'u yad'aura d'amaran ganin k'arshen Kabir tahanyoyi da dama da ya ajiye motarsa za azo asama sa bom, bak'aramin tashin hankali Mami ta shigaba, ahakane tanima masa masu tsaronsa ciki har da Sani wanda yakasance ogansu kuma shine drivern Kabir duk inda zaije duk da wani lokaci Kabird'in yakan k'i fita dashi,


     🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴
   "Hello Kila Kabir fa yataso ina fatan dai kuna cikin shirinku, pls kila wannan karon kar kabari asamu tangard'an da yaronnan zai kub'uta bai mutuba,
      "Ka kwantar da hankalinka Boss gamunan adaji muna jiran shi yau kam Kabir saidai uwarshi ta haifi wani,
     Cikin jindad'i Alhaji y'au yace "Gud Kila nasan zaka iya dahaka sukayi sallama,
   

      Allah sarki Kabir sai hiransu sukeyi shi da Sani Habib ya fad'o masa arai ya k'irashi  yana d'aga wayan yace "Hello Man ya kake? Ya hanya? "mhmm daban k'irakaba ai baza kasan ya nakeba,
     "Haba karkace haka wlh nayi ta nimanka bana samun ka,
      "Ok inaga matsalan network ne,
    "kunyi nisane?
    "ba muyi wani nisaba,
       "Ok to Allah yakare,
       "Ameen daga haka suka ajiye  wayan,
     Bai wani d'auki lokaciba wayan Mami ya shigo inbai mantaba wannan shine wayanta na hud'u tun fitowansu yayi murmushi yad'auka "Hello Mami na,
       "na'am Kabir kuna inane?
          "Gamunan Mami mund'anyi nisa, banijinki sosai Mami ki kashe inna isa zank'iraki,
      Yana fad'an haka yakashe wayan, tafiya kad'an suka k'ara suna dai dai kan wani tafkeken Gada sukaji k'aran bindiga y akarad'e wajan da sauri Kabir ya zuge glass yana kallon motocin masu tsaronsa yanda suke musayan wuta da wasu gungun matasa ga wasu motocin kuma sunjuyo sai gudu sukeyi, cikin firgici Sani yajuya kan motan, ya k'ure mata gudu cikin zafin nama Kila yaraka musu baya harbi yakeyi ba k'ak'k'autawa tun Sani yanaji har ji da ganinsa ya d'auke tuni motan tafara wulagigi akan titi ahaka motan ta hantsila cikin gada😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭

Wayyo Mamin Kabir
Babu wani tsaro da wani ya isa yabaka sai wanda ubangijinka yabaka😭


Kullu nafsin.......

*Ummu fatima ce* 😘
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿󟰾񲰼󟰾񲰼󟰾񲰼󟰊                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     




  *ALLAH yabar k'auna*🤝🏻

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 1⃣0⃣



Cikin farin ciki da jin dad'i kila ya faka motarsa yafito yatsaya akan gadan yana kallon yanda jininsu KB yake gudu akan Ruwa, motarsu kuwa tuni idon  Ruwa yajata ya afkar da ita wani tafkeken rami,

      Busar da wani iska mai zafi yayi yaciro waya a Aljihunsa ya k'ira Alhaji ya'u,

    Alokacin Alhaji ya'u yana tsaye da waya ahanunsa k'irjinsa sai bugawa yakeyi, tsoronsa d'aya kar asamu matsala  wajen kashe KB don yasan wannan shine damarsa ta k'arshe,

  aiyana ganin k'iran Kila hanunsa har b'ari yakeyi ya d'auka murya na b'ari, yace "kila yadai?
Wani mahaukacin dariya kila ya fashe da shi sai da yagaji dan kansa yafara magana

"Boss kayi yanda kakeso yau aduniyannan, kafin kaima naka wa'adin yacika,

 cike da tsoro yace "banganeba Kila?, 
  "matsiyacinnan yabak'wanci lahira, nagama dashi,

 "Dagaske kakeyi Kila?!!!

   "ai bamu tab'a wasa irin hakaba, 

     Cike da nishad'i da jin dad'i Alhaji ya'u yafara masa Alk'awura da haka suka ajiye wayan, yau jinsa yake duk duniya bawanda yakaishi farin ciki, don yasan ya mallaki dukiya angama don yagama target dama da ya kashe Kabir zai je wajen boka yamasa aiki akan Mami ta amince ta aureshi, shiyasa ma baiyi shawaran kisan Kabir da matarsaba, donkar kishi ya d'ibeta bayan aurensa da mami ta tonamasa asiri, dariya yake tayi shi kad'ansa afalo cikin nishad'i,

can kuma yazabura yamik'e

   Makullin motarsa ya sura da sauri da kanshi ya tuk'a kansa bai tsaya ko inana sai gidan Mami a falo ya sameta ita da uncle Musa da yakawo mata yaransa da tace akawosu su d'ebe mata kewa kasncewan dama yanason zuwa don ya kwan biyu baizo sun gaisa da k'anwar tashiba, cike da girmamawa da mutunta juna suga gaisa Mami ta k'walawa sauda k'ira da tun zuwansu suka shige kitchen wannan na d'aya daga cikin abunda yasa yaransuke son zuwa gidan Mami ta kanbarsu su shiga kitchen suyi ta jagwalgwalon girkinsu su dafa wannan su dafa wancan, tanakallonsu,

   Da saurinta ta iso Mami ta umurceta data kawo ma Alhaji ya'u abun motsa baki,

   "Dadyn su ziyarace haka da Ranannan? Saida yahad'iyi Ruwan da ya kurb'a sannan yace "zan wuce ne nace barinzo mugaisa kwana biyu ban lek'oba, "aikuwa ka kyauta d'azu kuwa mukayi waya da "yata tace wai yau sam baka k'irataba nace k'ila kana busy ne,  "mhmmm Rabu da Nafisa darunta yana da yawa kullum inban k'irata sau hud'uba ta dinga mita kenan, dukansu sukasa dariya,

       "Ina Kabir ne?  Inason muyi magana dashi akan sabon sakataren sannan da yakawo sam ban yarda da yaronba,  Mami takalli yayanta sannan ta kalli Alhaji ya'u Amma kuma ai Abdul yaron kirkine d'an k'anin  mahaifiyar muce, uncle Musa yace "tabbas bana zaton za'a samu Abdul da aikata mummunan Abu, cikin diriri cewa  Alhaji Musa ya kallesu yanacewa "to kun san sha'anin mutane nima tseguntamin akayi shiyasa ma nace sai nasamu shi Kabir d'in munyi shawara

   "Eh yana da kyau kuyi shawaran ma, bayanan ai yatafi Abuja Dady yad'an had'e rai oh narasa meyasa sam Kabir bai d'aukeni matsayin da na d'aukeshiba, yanzu ace yaronnan Zaiyi tafiya amma yakasa sanar dani?,  to ai shikenan Allah ya dawomin dashi lfy 

 Mami cikin rashin jin dad'in abunda Kabir d'in yayi tace " kayi hak'uri Dadynsu sam narasa meke damun Kabir da irin wannan Halinsa
   "ba komi ya wuce da yaushe ya tafine?
    "Tun da safe ya tafi ina tak'iran wayansa ma layinsa bayi aiki tafad'a tana  k'ok'arin k'ira,

 Rass taji k'irjinta ya buga kiran yana fara tafiya ya katse ba tare da ance komiba,

    Atsorace Mami ta kalli uncle Musa "yanzu kanma kwat2 layin baya fita sab'anin d'azu da'ake cewa ba Network, tak'arasa maganan da matsanancin damuwa,
K'asa2  Alhaji ya'u yakemata wani kallo aransa yace lallai da sauran rina akaba ko yaya zakiyi lokacin da kika samu lbrn mutuwar d'annaki ohi?

  Uncle Musa yace "inaga dai matsalan Network ne kinsan hanyan Akwai Qauyukan da basu da service,
    "Amma fa yaci ace yanzu suna cikin Abuja yaya ,

     Alhaji ya'u ya amsa da cewa kinsan halin Kabir da sha'awan k'auyuka yanzu haka sasu tsayuwa yayi awani wuri  daba network
asanyaye Mami tace "Eh zai iya yiwuwa, saidai fa d'azun can munyi waya, 
      "ki kwantar da hankalinki Insha Allah bakomi, ni zan wuce yafad'a yana mikewa
 "to Allah yasa nagode agaida mutan gidan
 "zasuji,

     Baijima da fitaba Uncle Musa ma yamata sallama yana cemata ta kwantar da hankalinta,
  To kawai tace masa amma kar ga Allah tanajin ajikinta kaman d'annata ba k'alau yakeba,



Saidai fa tun fitansu Mami take zaune awajen kamar andasata duk jikinta ba k'wari k'afafunta sai rawa sukeyi sai niman wayan Kabir, da Sani takeyi amma maganar bata canza zaniba, 

  Har akayi sallahn isha Mami bata daddaraba kowani bayan seconds tana k'ira amma shiru sosai yanzu kan ta tsorata da jin shirun d'annata,
  Wasa2 Har Mami tayi shirin kwanciya ba wani canji,

   Da haka ta yanke shawaran k'iran yayanta tasanar dashi koda tagayamasa shima ya tsorata, amma kasancewanshi na miji sai kawai ya share ya dinga k'rfafa mata gwiwa,
   Haka dai yalallab'ata dacewa lfy ne yake kawo shiru, Da k'yar bacci b'arawo ya d'auketa sai dai wasu irin mafarkai marasa dad'i ne suka addabeta ak'arshe dai hak'ura da kwanciyan tayi,

   Tun lokacin data saba yin nafilanta baiyiba taje ta d'auro Alola tazo ta tada sallah,

🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴
*Rayuwa kenan duk Abunda Allah ya k'addara ma bawa ba makawa sai ta sameshi saidai Addu'a yana rage k'arfin mummunan k'addara, shiyasa yana da kyau "yar'uwa da kin idar da sallahn asuba kar kitashi awajen har sai kinyi Addu'an safiya da maraici irin wanda Annabin mu ya koyar damu basai lallai kin Haddaceba kinimi Hisnul musulum d'inki kina kaeantawa kada kibari yaranki sufita baki karanta musu wannan Addu'an da da Annabi yake karanta wa Hassan da Hussainiba ki dafa kansu kikaranto musu kaman haka _u'izukuma bi kalimatullahi tammatan min kulli shaid'anin wahammatan wamin kulli ainin lammah_ inkika dafa kansu kikamusu wannan magana ta k'are basu ba kambun baka basu ba kidnaping wane maye wane matsafin da yake tsafi da yaran mutane *Ya Allah ka karemu da kariyanka*

Duk yanda kaso da k'in mutum baka isa kasheshiba sai wa'adinsa yayi,

    Da k'arfin gaske ruwan yake gangarawa da bayin Allahn da basujiba basu ganiba har ya kawosu bakin Gab'a anan suka kwana basu ko san inda sukeba,har garin Allah ya waye alokacin d'ai d'ai kun mutane suka fara fitowa a k'auyen wasu sun fito d'iban Ruwa wasu kuma itace,

    Hakan yake awurin Malam Bukar mai d'ori da k'aton jarka ya fito da igiya abayan kekensa, sauri yakeyi ya gama tunkafin Dijah tafito donyasan indai tafito waje bazata barshi ya d'iba,
   Agefen Rafi ya ajiye jarkansa sannan yanufi cikin jeji yin itace agefe ya kafe kekensa yana shirin haye Ruwa,

   Nanfa idonsa ya sauk'a akan samaruka guda biyu kwance cikin halin mutuwa ko rayuwa, sosai ya tsorata duk da halin jarumta irin na malam Bukar,
 yazuba musu ido yana nazari Abunda ya d'aure masa kai shine ganin d'aya da kakin soja d'aya da bak'ak'en kaya cikin jarumata irin nashi ya k'arasa har inda suke bakinsa d'auke da Addu'a ba k'aramin tsoro da tausayibane yakamashi lokacin da yaga harbi ajinkinsu cikin gaggawa ya hau kekensa bai tsaya ko inaba sai police station,

          Nannfa yasanar dasu abunda idonsa yagani ba b'ata lokaci suka garzaya da maotansu wajen cikin jagorancin Malam Bukar mai d'ori,



   *tofah magana nagaba ina lbrn Mami? Ina Alhaji ya'u? gadai Kabir da Sani zasu mutu ko zasuyi rai sai Allah shi yabar ma kansa sani rayuwa kenan sai naka yakasheka bare kuma ya taimakeka mmm muje zuwa



Ummu fatima ce 😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MY NATION*🇳🇬
         
  *ALLAH yabar k'auna*🤝🏻

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 1⃣2⃣


       Ranan juma'a shine Ranan da za'akai KB Rugan Juma,

       Basu samu flight ba sai wajen k'arfe uku,
 a airpot suna sauk'a dama sunyi bucking Amubulance kasancewan k'afan bayi ko lank'wasuwa,

Basu suka isa cikin Rugamba sai da aka idar da sallahn isha'i,
 suna shiga cikin Garin suka tambayi Gidan *Malam Bukar Maid'ori* ba wani b'ata lokaci aka kaisu,
 ak'ofan Gida suka sameshi sunacin Abinci shi da mak'ocinsa Baban Jebu,
 Uncle Musa ne ya musu sallama Hanu biyu suka karb'eshi hami da bashi wajen zama,

     Bayn sun gaisa Uncle Musa yace "Munzo wajen Malam Bukar ne,
  "Ayyah nine Malam Bukar, nan yasanar dashi  abun da ke tafe da su,  Mik'ewa yayi da sauri yashiga Gida "Dijah! Dijah!!
     "Na'am ta Amsa da sauri ta fito,
      "Maza d'ibi taburmai kije can d'akin Bak'i ki shimdid'a ankawo mara lfy yana fad'an haka ya juya yafita

  a jikin mota yasamu Uncle Musa yana tsaye, "Bismillah kushigar dashi Habib da Driver da Abban Habibne suka d'aukeshi,
  Uncle Musa da Malam Bukar suka rufa musu Baya dama Gidan k'ofa biyu yake dashi d'ayan K'ofan shine zai sadaka da cikin Gidan inda su inna suke,
   sannan akwai k'ofan da zai sadaka da d'ayan side d'in ananne Baffa yake kwantar da marasa lfy,
  kasancewan akwai wanda suke zuwa daga nesa, 

     D'akine ciki da falo wanda akayi da bluck d'in k'asa aka maasa Rufi da ciyawa irin dai d'akunan k'auye sai dai wanna yasha flasta sosai da flu na siminti uwar d'akinkuma har da Gadon k'asa a falo aka shimfid'a taburman
    Suna ajiyeshi Habib yayi sauri yaje yad'auko blancket ya shimfid'amasa yasa pillow suka taimaka masa ya kwanta nan suka zauna aka sake sabon gaisawa Baffa yace sai  in Allah ya kai rai da safe zamu fara aiki,

    Shiga cikin yayi yasa aka kawo musu Abinci,
     Habib ya matso kusa da Habib yana kallonsa  "KB me kk son kaci?
    "Nothing,
    "to barin Had'ama tea
     " bazan shaba kabarshi kawai
     "naga kaman bakaso zuwannan ba kayi hak'uri insha Allah daka samu lfy shikenan, 
   "Gaskiya ni bana iya zama a duhu wannan shine kawai matsalata, wlh yanzu jina nake kaman a kurku,
   "a'a baza abarka aduhuba ka kwantar da hankalinka,

  Yauwa KB pls kayi magana da yarinyannan mana tadamu taji voice d'inka  wlh tadameni seriously,
 tsaki KB yayi ya kalli inda su Uncle Musa suke suna Hiransu,         
"ko zamuyi magana badai yauba sai ka bari da safe, daga haka ya mai da kanshi  ya kwanta,

    Washi Gari tunda safe Baffa yafara had'a magungunan da zai masa d'auri,
    Bintalo da Dijah ne suka musu abun karya, Doya Baffa ya sayo akasoyamusu aka dafa musu Ruwan shayi da yasha kayan k'amshi, Inna ta jere ma Dijah a k'aton tray takaimusu, a falon ta samesu dukansu KB da Habib suna kwance Uncle Musa da Abban Habib suna zaune suna Hira, cikin kunya irin nata ta gaidasu dondai duk tsiwan Dijah takan ji kunya maza sosai, Uncle Musa yace meye Sunan ki "yanmata?  Dijah tafad'a tana mik'ewa, "a'a asai dai uwatace guda awajen, sannu ko uwata ita dai murmushi kawai tayi tafita,

   Abban ya d'aga su KB ya gabatar musu da abun kari,  sunaci suna Hira KB kan Shayin kawai yasha, sosai yaji dad'in Ruwan shayin don Haka yasha sosai,

   Baffa yana gama karyawansa, yafito, yashiga wajensu tunda ga nesa KB yake kallon Baffa har yashigo yasamu guri yazauna, KB yana mamakin yanda hakan yakasance, ikon Allah,  Baffa ya Gaisa dasu Uncle Musa sannan yajuyo wajesu  KB, Baffa kam sake baki yayi cike da mamaki yana kallon sa "Likita!  Ikon Allah Dama kaine Mara lfyn? 
     Allah Sarki D'annan meyasamekane haka? Ya fad'a yana kallon k'afan da ya kumbra suntum,  Uncle Musa yace "Ayyah acnce mana kuma kai kasamesu abakin kogi ka k'ira Hukuma "innalillahi wainna ilaihirraji'un kanason kacemin Likitane na tarar dasu abakin kogi jinajina?  "Eh haka dai police d'in yagayamana, ikon Allah asai kasanshi,
    Baffa yayi ajiyan zuciya cike da tausayi "wannan yaro ai bazan tab'a mancewa dashiba,
  Ya kwashe duk abunda KB ya musu lokacin da yakai Dijah Asibiti,
     "Rayuwa kenan da kakai masa mara lfy, yau gashi shima ankawo maka shi amatsayin mara lfy,
   Shiyasa arayuwa akeso kazama nakowa saboda bakasan yanda wataran zaka kasanceba, cewan Abban Habib,
    Baffa yajuyo da kallonsa ga Kabir da shimad'in shiyake kallo yana murmushi, KB yace "Ashe anan kake? ai inayawan zuwa tanan,  "Allah sarki shiyasa kasan mutuncinmu kasan mutanenmu sam basa mutunta fulani, 
     Dukansu suka sa Dariya "ai dole yasan darajan fulani don Uwarsama bafulatanace, inji Uncle Musa Baffa ya matso Kabir yana cewa a kace bazamu samu matsala wajen aikin k'afanba tunda ya had'a zuriya da fulani, kasanmu akwai dauriya, Habib ya kwashe da dariya "ah Baffa kar ka zugashi don naciro wayata zan masa vidio, kabir ya harareshi " yaro ancemaka ni kaine? Allura mafa inza'amaka sai katara mana mutane,

    Baffa yana dariya yakamo k'afan Kabir yafaramasa aiki, sosai Baffa yatausaya masa don har da tsagewan k'ashi ak'afan gashi yayi tsami,
    Kabir kuwa tunda Baffa yakama k'afanshi yakamo lip d'insa na k'asa yana tsotso ya rufe idonsa gam sai zufa yakeyi, duka d'akin bawanda bai tausaya masaba,
   Har aka gama duka biyun bai ko bud'e idoba, yanajin Angama ya kwanta tuni bacci yayi gaba dashi,

Godiya suka mishi sosai, Uncle Musa yanisa "to Malam nawane kud'in aikin?

    Baffa yad'anyi murmushi yace "ai koda bani namishi aikinba nizan biya amishi Balle kuma ninayi, wlh tun zuwana Asibiti abunda yaronnan yamin nake jinsa kaman d'an dana haifa,

    Inzakuyar da kubarni da Kabir zan masa duk abunda yakamata fatana dai Allah yabashi lfy,

     Godiya suka masa sosai sannan Abba yace "mu yau zamu koma zamu barshi da d'an'uwansa,
   Saidai kayi  Hakuri zamu saka Generator agidannan don munga ba kuwani samun wuta sosai,
    "A'a wannan bawani abun damuwa bane, yafad'a yana mik'ewa, "nizan d'an fita sadai inaga zan dawo kafin kufita,
  "to Allah ya kare muma zamuje cikin gari midawo, tare suka fita, suka koma cikin gari donyin sayayya,

       Inna tana zaune agindin murhu tana Raba Abinci Bintalo tayi sallama, ta Amsa mata tana kallon bayanta, ina Dijah?  "mhmm Dijah suntsaya can ita da Jebu wai zasu daki wata yarinya, inna rafka salati tana rik'e baki yanzu duk fad'an danayima yarinyannan Shekaranjiya batajiba, kenan nayi asaran yawun bakin? "Mhmm inna waifa akan lado ne, wai ancemata anganta da Lado adandali shine tunda akatashi a makaranta suka sha d'amara ita da Jebu ba irin maganan da ba mumusuba nida Ma'u basu kulamuba, cikin takaici Inna tace maza kije kice mata tazo injini intak'i kuma ranta zai b'aci,

     Bintalo kan tsayawa tayi cike da mamki tun isanta gun,

     Dijah ta haye kan wani itace ta hard'e k'afa tanagani k'awayenta Jebu da Har, da sude suna ta  dambe da larito da k'awatanta,

    Cikin zafin nama ta cafko jebu tana mata fad'a "yanzu fisabilillahi Jebu ku wasu irin marasa hankaline,  Dujah ta maidaku sakarkaru, tanimo fad'a tabarku da dambe ita masifa ga tsoron tsiya, kukuma ga k'arfiko?
    Dijah ta jawo hanun Jebu daga cikin na Bintalo, ta hankad'ata cikin fad'a,
     " Jebu har yanzu bakin Larito baiyi jiniba kifasa mata baki sai mutafi, tafad'a tana zabga ma Bintalo harara
     "wlh BIntalo nasha gayamiki kifita ahanyana bafa tsaoronki nakejiba,
    Cike da talaici Bintalo tace "sai ki wuce mutafi Inna tana k'iranki,
    zaro ido Dijah tayi tana kallonta, "sharri kikaje kikamin?
   Bintalo batace mata komiba,
   Ta rik'o hanun Jebu "zo mutafi ta kalli Larito wlh karki aza kin tsirane zan kamaki,
     Suna tafiya tana ta surutu ma Bintalo      ko kulata Bintalo batayiba har suka shiga cikin gida, arumfa suka samu inna ta rafka tagumi,
     Asanyaye Dijah ta iso ta tsiguna agefe,
       "wai Dijah meyasa ne baki jin magana, ban hanaki tsayuwa bayan kuntaso daga makarantaba?  Wai yau harkece da fad'a akan saurayi Dijah? Yaushema kk kula Lado? Yaron da sai yazo yayi aika so goma baki fitaba, naga ko sunansa aka fad'a sai kin b'ata rai, shine don tsaban iyawa harda tare "yar mutane akanshi,
     Wani irin kunya mai tsananine ya rufe Dijah, ji take kaman k'asa ya tsage tashiga ada tasan Bintalo takan rufa mata asiri, kotayi wani abun awaje batacika fad'a agida ba tabbasa da tasan Bintalo zata mata haka bazata bari taji ba, wani irin zufa taji yana bin jikinta, tsaban takaici sai kawai tasaki kuka,
     Sosai Bintalo tayi nadaman fad'a ma inna da tayi, musamman ma yanda taga Dijah tana kuka, ba makawa tasan bashi taci awajen ta sai dai fatanta Allah yasa kar Dijah ta mata mummunan ramuwa,
    Kuka takeyi bil hak'k'i ahaka Baffa ya shigo yasameta dasauri, ta tashi ta rik'e kekensa "Sannu da dawowa Baffa tagad'a tana share hawaye, Ran Baffa bak'aramin b'aci yayiba, Don in Akwai Abunda Yatsana kukan Dijah ne,
     Tana sauk'e kayan Abincin da ya shigo dashi akan keke tana kukanta, har tagama sauk'ewa,
     

        Hanunta yakamo rai b'ace yanufi inda Inna take,
       "me kukayi mata? Ya tambayi inna yana mata wani irin kallo, aza bure Dijah take kallon inna tana juya kanta, inna ta fahimci Dijah bataso Baffa yaji, murmushi tayi "katambayeta tayi maka bayani da kanta, Bak'in halintane inaga ya motsa,


  Nan dai yayi ta fad'an dayasaba sai da yayi yagaji don kansa, 

     Ya shiga d'aki Inna tace "ki wuce kije kicire kayan makarantan kizo ki kwashi Abincin Bak'innan kikai musu,


    Su biyune ad'akin  Kabir da Habib,  suna Hiransu Habib yana rik'e da Hanun KB yana d'an matsamasa, 

    Ta shigo da tray d'in Abinci tunda ta shawo kwanan d'akin Kb yake Kallonta, sallama tayi Habib ne kawai ya Amsa, ta dire tray d'in a gefe ta d'ago ta kalli Habib akunyace tace ina wuni, lfy Beatiful girl yana murmushi,
   Ta juyo ga kabir "inawuni, caraf idonsu suka had'u, Dam taji k'irjinta ya buga ta tsaya baki bud'e tana kallonsa yamurtuk'e fuska yana hararanta, yace "Malama Kallon ya isa haka ko, ai sai kitashi ki k'ara wuta, dama d'an k'auye ako ina sai yanuna k'auyancinsa, bandahaka meye Abun kallon?, mtss yaja Dogon tsaki, cikin zafin Nama ta mik'e saida tafita tasa takalmin ta tayi taku Biyu ta juyo Rik'e da kunkuminta, ta zabga mishi Hararan sama da k'asa sannan taja tsaki ta tafi, Habib ya kece da dariya har yana rik'e ciki shi kuma gogan ji yake kamar zuciyansa tafito din takaici, arayuwansa  yatsani raini,






   *Tofah Anya KB kasan waye Dijah kuwa? 🤔    ka takalota kuma kace bakason raini?* 😳







Ku biyoni


*Ummu fatima* 🇳🇬
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MY NATION*🇳🇬
         
  *ALLAH yabar k'auna*🤝🏻

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 1⃣1⃣


 A gefen Hanya suka faka motan suka shigo wurin da k'afa da hanu Malam Bukar ya nuna musu inda su KB suke,

     Bak'aramin kad'uwa police d'in sukayiba musamman da suka lura Ba k'ananan mutane bane,

  Ogansu da kansa yaja mota ya tafi asbiti suka taho da ambulance akatafi dasu,

     Nan likitoti suka rufu akansu sukaciremusu harsashi ajikinsu, Sani kusan bulet hud'u aka ciremasa, ga raunukan da yaji yayin da akacirema KB d'aya, sai dai ansameshi da karaya aduka k'afafunsa,

       Har la'asar ana abu d'aya akansu, sai daf magriba suka kammala agajiye Doctors d'in suka fito, har lokacin police d'in sunanan babban likitanne ya mik'a ma police d'in hanu, suka gaisa, "yadai likita ansamu nasara?


     "Eh to mundaiyi musu aiki amma dai ba wanda ya farfad'o acikinsu,
   
 Police d'in ya mik'a masa ID card  wannan a aljihunsa muka samu, ya karb'a ya duba
*Kabir Mahmud tugga*  yagani ajiki da sauri ya d'ago ya kalleshi "oficer ai wannan Babban likitane kuma d'an shahararren d'an kasuwan nanne Alhji Mahmud Tugga, 


   Kai police d'in ya jinjina yace "shiyasa nanumaka kagani kasan jiya anyi taron manyan likitoti a Abuja, maybe can yanufa masu hamayya dashi kokuma "yan fashi sukamishi wannan aika aikan, so yanzudai zamu d'aukeshi mukaishi National Hospital Abuja, Inyaso kuyita treting d'in seceuritynsa anan inya d'ansamu releif sai amai dashi cikin Adamawa.


   🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴

Gidan Mami na lek'a bak'aramin kad'uwa nayiba lokacin da na hango Mami zaune abakin gado ta jingina kanta ajikin gini, tanajiyo hargowan mutanen da suka cika gidan wasu "yan'uwanta ne wasu kuma "yan zuwa jajene, yau kwana uku kenan ba Kabir ba labarinsa, ko ataron da akayi na Abuja ma lbr yasamesu Kabir bai halacci taronba, bincike iya bincike kullum yinsa akeyi amma ba lbr,

 hanunta tasa tashare hawaye k'waya d'ayan da yagangaromata  Zuciyanta sai zogi yakemata, ahankali take tuno Abumda mijinta yagaya mata ranan da zai Rasu, *Fatima kikula min da Kabir Don nasan duk mainiman yaga bayana yanzu hankalinsa zai koma kan Kabir shima za'ayi k'ok'orin ahalakashi kamar yanda akaso amin abaya shiyasa akecewa dukiya fitinace, don nasan abumda suke nima kenan awajena dukiyata gashi kuma yanzu zai koma hanun sa*

   "Kabir ta fad'a tana share k'walla dai2 lokacin akayi nocking sauda ce tashigo tad'an rusuna "Mami wai kije inji su Dady, sai da tashiga bayan gida ta wanko fuskanta sannan ta zira Hijabinta tafito acan babban falo tasamesu, su biyune Uncle Musa da Abban Habib, tazauna daura dasu suka gaisa cikin k'arfin Hali, ta kalli yayan nata "yaya har yanzu ba wani lbr?
    Ko boudy guard d'innasa ba'asamu lbrnsuba?
    Uncle Musa yad'ago ya kalli Abban Habib, ya sauk'e ajiyan zuciya, dai2 lokacin wayan Mami ya hau ruri,
 Nafisa sunan da yabayyana akan wayan kenan, d'auka tayi tasa ahans free cikin matsanancin kuka Nafisa tafara magana "Mami ashe ankashe yaya KB tun ran Asabar amma ba wanda yagayamin? Cikin tashin Hankali Mami tace "waya gayamiki wannan magana Nafisa?
    "Dady ne yak'irani yanzu yake gayamin wai ahanyarsa ta zuwa Abuja aka kashwshi, kuma wai bai yarda inzoba wlh sai nadawo ko zai kasheni nabar England har Abada, Mami kam kusan suman tsaye tayi awajen, idonta taf k'wala, ahaka wayan yasulale yafad'i ta zube akan kujera tanayima yayanta kallon tuhuma,
    "Yaya meyasa kuka b'oyemin Mutuwan Kabir?  Bani na halliceshiba don me za ab'oyemin mahaliccinsa ya karb'eshi? Uncle Musa ya katseta da fad'in Fatima ki kwantar da Hankalinki wlh bamu samu lbrn mutuwan Kabirba amma bari muk'ira wanda akaji abakinsa, yalalub'o no. Alokacin Alhaji ya'u suna zaune da su Kila awani tafkeken Hotel suna pertyn samun nasara ganin mai k'iranshinne yasa shi tashi awurin dayake ya canza waje, bayan sungaisa Uncle Musa yace "Ashe kasamu lbrn mutuwar d'anka KB? Shine bakasanar damuba? Cikin firgici  Alhaji ya'u yace "ni ni kuma? Ta ta ina kennan?
     "mhmm yanzu "yarka Nafisa tayi waya take sanardamu kuma tace kai kagayamata,
    Arud'e yace "no no bata fahimceniba bahaka nagaya mataba,
  Kallon Kallo Uncle Musa da Abban Habib sukayi  sannan yakashe wayan yana kallon Mami data zuba masa ido, dai dai lokacin Habib ya shigo bako sallama yazauna yana kallonsu "mmn  Dady nasmu lbrn KB na yanzu  akak'ira asibitinmu akasanardamu KB yana Yana national Hospital Abuja ai gaba d'ayansu mik'ewa sukayi suna k'ara tambayansa Mami kam sauk'ar da kanta k'asa tayi tana kirari ma mahaliccinta tana hawaye, bata majin mesuke fad'a ita dai taji yayanta yana waya murya k'asa2 

  "Fatima kitashi kishiga ciki yanzu zamu Je Asibitin garinnan muduba Sani daga nan kuma zamu wuce Abujan ajirgi  sannan kuma ki iya ma bakinki, karkisanar da kowa cewa ansamu lbrn Kabir harsai mun gano masu hanu akan son salwantar dashi,
  Asanyaye tace "wasune ko? Suka mishi wani abun? 

  "Ranan lahadi da azahar masu tsaronsa suka zo gidana suka shaidamin wasu sun tsaresu ahanya sun kashe mutum biyu acikinsu sauran sun kub'uta da k'yar da raunuka wasu kuma ba raunuka, amma basuga uban gidan nasuba shiyasa bazasu iya zuwa gidannan ba shine sukazo su sanarmin,  nikuma nasanar masu Ibrahim, yanzu haka wanda suka samu raunin suna asibiti muna kula dasu sukuma ma matan munje ga iyayensu munsanardasu munmusu ta'aziya harda d'an ihsani,

Cikin tashin hankali Mami tace muje tare inga Sanin,

Tumdaga nesa da Mami ta hango Sani ta rud'e, kallonta yakeyi har ta matsoshi, sai mirmushi yake mata ta dafa jikin hadonsa tana kallonsa harsu uncle Musa suka gaidashi da jajan tawa, sam Sani baiji dad'in ganin hawaye afuskan Mami asanyaye ya k'irata tad'an sunkuyo tana kallonsa "laifin Kabir yashafeka ko Sani sunyi niyan kashe Kabir kaima sun nakasaka duk wannan gurbin harsashine haka ajikinka? Ta k'arasa maganan cikin kuka,   Sani ya ya marairaita fuska yana kallonta yace "Haba Mami don ALLAH kidaina kukannan dagaske oga KB yana raye? Yafad'a da muryan kuka, Habib yadafa kansa yace "ka kwantar da hankalinka Sani nacemaka yana raye bak'arya namakaba yana Abuja yanzu haka wajensa zamuje, "Don Allah inkaje kak'ira wani da kasani a asibitinnan yabani wayan kahad'amu inji muryansa, "insha Allah zanyi yanda ka fad"an Allah yabaku lfy "Ameen mami ta amsa Abban Habib yace mata tazo amaidata gida tunda akwai masu kula da Sani, tak'i tace anan zata zauna, ahaka suka tafi suka barta har dare tana wajen sai wuraren 1:00 ta koma gida,

Awannan dare kam sam Mami bata rintsaba juyi kawai takeyi akan gado data rufe idonta Hoton Kabir take gani, gashi tun da rana a Asibiti tayi ta k'iran su uncle Musa Amma wayansu baya shiga sosai ta k'ara razana, washi gari kuwa tun safe tagama shirinta taje taduba jikin Sani daga nan tawuce air pot, tana shiga Abuja kai tsaye Hospital ta wuce,

    Gadajen word d'in take bi da kallo can tahango sojoji da police ajikin wani gado k'ura musu ido tayi, abayanta taji ance Fatima tana juyowa ta ido biyu da yayanta yana dariya yace "kin kasa hak'uri ne?  Duk da k'in nimanki danayi awaya, to zo muk'arasa ga gadonsa can jami'an tsarone ke gadinsa, suna k'arasawa da uncle Musa yagabatar da ita amatsayin mahaifiyarsa gaba d'aya suka watse suka basu guri, ahankali Mami take d'aga k'afa kaman wanda k'wai yafashe ma aciki, Kabir kuwa sai k'ok'arin k'ak'alo murmushin k'arfin Hali, yana kallonta duk yanda Mami taso ta daure abun ya gagara hawayen da taso b'oyewane suka hau sintiri afuskanta ta dafa goshinsa da d'ayan hanunta tana share k'olla da d'ayan tace "Sannu Kabir irin jarabawan da mukuma aka jarrabe mu dashi kenan, juya kanshi yakeyi ahankali ya d'ora Hanunsa asaman hanunta kaman zaiyi kuka yana kallo idonta, yace "Pls Mami ko mutuwa nayi bai kamata kimin kukaba, Addu'anki nake buk'ata Mami wlh wannan hawayankin yafi min raunukan jikina Mami,

    Cikin sheshshek'an kuka Mami tace "wayene Kabir? Waye yake son ganin bayanka? Meka musu Kabir?
       Kabir ya tura hanunsa ya jawo kujera yasaka mata ta zauna tana shafa gashin kanashi,

 "araunane yace Mami wlh bawanda ya isa ya kasheni sai kwana na ya k'are, 

Da son ransune da yanzu bana nan, amma kinga da Allah bai soba gani araye pls kikwantar da hankalinki Mamina yafad'a yana sharemata hawaye,

   Mami ya lbrn Sani?
     " yana Asibiti jikinsa da sauk'i har yafi naka,
     "su Bala fa?
       "Duk jikinsu da sauk'i, sai Alokacin Mami ta kalli su Habib da Abbansa suka gaisa,
         



     Sannu sannu Su KB suke samun sauk'i da ikon Allah,

      Acikin watanni Biyu duk wani raunuka ya warke Sani kam tuni har Ansallameshi Uncle Musa ya d'auleshi yakaishi Gombe campanin KB yace masa yazauna anan don haryanzu mutane basu san Ansamesuba,


     Alokacinne kuma aka kunce karayan KB amma wani abun tashin hankali shine sam karayan bai d'oruba ba k'aramin tashin hanlali suka shigaba,

       Ahaka aka sake wata d'aya aka kunce Amma baiyuwuba, ganin haka yasa Uncle Musa yace Asallamesu kawai zasu kaishi amasa na gida haka Kuwa aka sallamesu aranda zasu tafi police d'in da case d'in yake hanunsa yazo, cike da girmamawa yagaida Mami, ya tambayeta jikinsa,

     Mami ta jinjina kai "jiki da sauk'i saidai karayanne bai gyaruba shiyasa zamu koma gida agwada na gidan agani ko Allah zaisa Adace, shiru yayi nad'an lokaci yace "kunada wanda ya iyagyarane? 
       "a'a gaskiya saidai zamu bincika
        "acan k'auyen da nake aikinnan kuwa akwai wani datijjo wanda yazo yasanar mana lokacin da yagansu acikin mummunan halinnan ya iya gyaran karaya sosai don naji ance har daganan akan kaimasa masu karaya, ko zaku gwada kukagani?
     "Abban Habib yakarb'e da cewa "Eh sai kawai mukaishi can awani garine? Wani Rugan fulanine can k'arshen Adamawa sunan Rugan Juma sunan mutumin kuma *Malam Bukar maid'ori* nan yagaya musu tanda akayi kafin akawo KB nan Mami tajinjina kai to Allah yasa Adace,

    Uncle Musa yace "Ameen, tunda hakane kawai sai mufasa zuwa gidan ke Fatima Gobe in Allah yakaimu sai  ki koma gida mukuma jibi sai mushirya mukaishi,


*Tirk'ashi masu kartu ga Dr KB fa yana shirin zuwa gidansu Dijah k'aya abokiyar Hamayyansa cab ga Shi wai ita Dijah bata mantuwa wai wani wainan za'a totane?*








*Ummu Fatimace* 😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MY NATION*🇳🇬
         
 

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 1⃣3⃣


 Sai bayan la'asar sosai, su Uncle Musa suka dawo,

K'aton Generator suka sayo Da kayan Electronic, irinsu, fanka, frich Tv, lokacin da motar ta tsayane wani d'an makocinsu Saurayi mai suna Iro yazo ya dinga shigar musu da kayan sannan yatayasu gyara wajen, capet suka malala d'akin sanna suka sa k'atuwar katifa Gado huta da kujerun Roba guda Hud'u, Basu bar garinba saida aka gama shirya komi,

     Har makanike aka k'ira ya had'a Generator yasa Tv yasa Dish, aka  kunna frich Iro ya jera Ruwan faro aciki da sauran Drinks kala2, 

     Tuni Gurin yayi fes kaman ba acikin Rugan juma ba, Iro kam sake baki yayi yana bin d'akin da kallo aranshi yace "lallai Ni'ima na birni, jinyanma bazai iyayi hakaba  sai sunmayar da d'akin irin nasu,


     Sai wajen Daf Magriba,  suka musu sallama sukatafi,


     Saida akayi sallahn Isha'i suka isa uncle Musa  wajen Mami ya  wuce kai tsaye,

   Nafisa ya samu a falo ta kifa kanta ajikin kujera,  sallamansa ne yasa ta d'ago kanta, tagaishi tace "barin k'ira Mamin, da kai ya amsa mata ta haye sama jim kad'an Mami tazo,  "Yaya shigowan dare kukayine?  "wlh kuwa nasan kin matsu kiji lbrn d'anki, dariya kawai tayi
   Shima dariyan yakeyi yazauna suka gaisa, "ya me jikin dai? "jiki Alhamdulillahi,
  Nan ya gayamata duk yanda akayi, sannan  ya d'ora da "wannan kaman "yar wajen Ya'un nanane ko? "Eh Nafisa ba itace,  "inafatan baki sanar da ita ansamu  Kabir ba "Bangayamataba amma yanda tad'aga  hankilinta   naso ingayamata "to kar kifara nagayamiki akwai binceken da mukeyi,       abunda yasa nace inkundawo inason magana dakai,
      "Dama Alhaji Ya'u ne ya matsamin akan maganan Campani Wai anrufe acount d'in Campanin kullum yana gidannan jiya karkaga irin Haukan dayamin yau kuma tun safe yazo wai Nafisa ta koma gida tunda tak'i karatu nayi ta bashi hak'uri bai saurarenba ita kuma tak'i ta koma,  dariya yayi yana gyad'a kai yace "yasake tambayanki Kabir?
 "cemin yayi yabayar ayi istihara indai Kabir na raye nan da sati zai bayyana inkuma bai bayyanaba, to ya mutu,
  mik'ewa Uncle Musa yayi yana Dariya, yace inyasake miki maganan campani kice yasameni da maganan, sannan maganan yarinya, baruwanki in yamatsa takoma naki ido, duk da Mami bata fahimci komiba, ta karb'i shawaran yayan nata don ta lura kwanann Alhaji Ya'u yana nima yacanza Hali,

  Washi Gari da safe Mami ta fita ta shiga side d'in KB, zama tayi akan kujera sannan tak'ira wayan Habib alokacin ya ciro sabuwar wayan Kabir acaji yana samasa layi,  yana d'auka gaisuwa kawai sukayi yaba ma Kb, jin muryan Mami ne yasashi ya lumshi ido ya bud'e jiyake kaman ya rufe ido ya bud'e yaganshi agaban maminsa, ba k'atamin kewanta yayiba, jin sauk'an nunfaahinsane yasa tayi dariya, "Helo Kabir murmushi yayi yace  "Mamina kina lfy?
       "Lfy lau Kabir ya jikinnaka?
       "Alhamdulillah Mami na,
         "to Allah yabaka lfy Kabir d'in Mami,
       "Ameen  wai jibi za'a kunce Mami kisani a Addu'a Allah yasa akunce a sa'a,
       "To Kabir Addu'a kam kullum yinta mukeyi sai dai ak'ara,
     Wai yaushe Habib zaidawone?
        "wai yace sai nan da sati biyu, 
      "a'a yaushe za'ayi haka kai baka zuwa aiki shima bayazuwa?
       Munyi waya da Sani zaizo ya karb'i shi inyaso inya dawo sai yadinga zuwa a weekend yana dubaka,
       "to Mami Allah ya kaimu Nagode,

Dahaka sukayi sallama ya mik'a masa wayan yayi masa bayanin yanda sukayi da Mami,

      Sallama sukaji anayi, Habibne ya amsa ta d'aga labulen tashigo cikin nitsiwa ta tsuguna tagai dashi, ta kalli Kabir "ya jikin? Yana murmushi ya Amsa da Alhamdulillah,


    Ta mik'e zata fita yace "Mmn nace ba, dawowa tayi ta tsuguna tana kallonsa, Meye Sunanki ne?
      "Sunana Bintalo,
        "Bintalo kuma? Wani irin sunane haka?
           "Fatima, zaro ido yayi waje yana kallonta asalin sunanki kenan  tomeye alak'an wannan Babban suna da Bintalo, Fatima  sunan Mamatace, Habib yace "Daga Fatima suka mayar dashi Binta daga Binta kuma shine akasake cewa Bintalo,  Kabir yace  "Ayyah mai sunan Mami ta kar ki sake cewa Sunanki Bintalo kinji
  Sunanki  Fatima Babban sunane dake, to tace ta mik'e tana tattara kwanukan dasuka karya fasu, Habib yace "ina k'anwan kinnan? Meye sunanta? "Dijah, tana gida  "ok inkinshiga kice ina gaisheta,  "to daga haka ta fito awajen wanke wanke tasamu Dijah ta kad'a kumfa sai shek'eshi takeyi fa cup kaman mai sai saita shayi,
   Bintalo ta zauna agefe tana kallonta dama inzasuyi wanke wanke Dijah ce take wanke wa Bintalo tana d'aurayewa, don kozatayi ya Dijah bazata bata wanke wanba,
     Ganin bata da niyan fara wankewan ne yasa tace  "Dijah ki bar wasannan haka ki fara wankewa zamuje d'ibo Ruwafa, 
   Dijah ta Murgud'a baki "Bazanyinba ina Ruwanki dani?
      "Da Ruwana inbazakiyiba kibani Inyi nawa intashi, Hararanta kawai Dijah tayi tacigaba da wasanta, ganin haka yasa Bintalo ta d'auko omo ta kad'a kumfanta zatayi wanke waken, Dijah kuma tace bata iya jiba,

Da k'afanta tabuge kumfan tazubar, Bintalo tajawo wanda take wasan dashi zatayi wanke wanken, Dijah ta d'auke nandai kokuwa ya kaure, kai kai, suka jiyo muryan Inna abayansu, Rik'o Hanun Dijah tayi tana tambayan meya had'asu, Dijah tana hak'i tace "wai don tace min zata aikeni wajen Ila nace bazan jeba shine kawai ta dakeni, cikin tashin Hankali Bintalo ta zaro ido ta dafe k'irjinta,  "Ni? Ni zakiyima sharri?
     "Eh mana ba sharribane jiyama inaji dayazo Hira kinace masa kina sonsa cikin zafin nama da b'acin rai Bintalo takai ma bakinta bugu, kokuwa suka sake kaurewa dashi Inna ta Rabasu Bintalo ta fashe da kuka tana kallon Inna "wlh Inna k'arya takemin
       "Ba karyabane Inna rananma har wasik'a ta rubutamishi yanzu haka yana jakanta,

 wayyo Bintalo kaman tayi hauka tsaban kunya gami da takaici uwa uba tanaganin kaman inna tana mata kallon shikenan kinzama "yar iska,

 tana share hawaye tace "Wlh Inna sharri takemin

 Inna tace "wuce kitafi abunki kibarta tayi wanke wanke ita kad'ai,  inna takalli Dijah tana jijjiga kai Dijah Allah dai ya shiryar dake Addu'an danake miki kenan kullum nabaki minti biyu kacal kiyi ki tashi awurinnan ku d'bo Ruwa, daga haka ta wuce d'akinta,


    Sauri sauri Dijah tayi tagama, ta shiga d'akin kwanansu ita da Bintalo,  alokacin Bintalo tana Assigment d'inta da aka basu,  Dijah ta tsaya mata akai

 "kitashi muje d'ibo Ruwan, Bintalo bata kulataba tasake magana,  Bintalo ta zab gamata Harara bazanjeba, uwarmarasa kunya, Da k'arfi Dijah tace "Inna ga Bintalo tana k'irga k'waryan tarunta, wai tace ita da guda goma sun mata kad'an,

azuciye Bintalo ta tashi ta Cafko Dijah, Inna tana jinsu tayi kaman bata jiba,

     Sarai tagane cewa Dijah tana rama  Abunda Bintalo tazo tafad'a ne randa ta tare Larito akan Lado,

   Inna rik'e hab'a tayi
"oh ni jikan Adamu naga takaina ayi yarinya da nacin fad'a, wai ba'a isa ayima Dijah abu ta hak'uraba sai ta rama? Aidai Baffanki mai goyamiki bayan bayanan bari dai inbarki da Bintalon yaukam kin k'urota,
     Tanajin tana ihu amma har yanzu bakinta bai mutuba, sai k'ara wasu sharrin takeyi, 

    Ahaka kuma take k'iran sunan Inna
      "bazan zoba
Dijah saikin ji jiki, ke ba k'arfin kobo sai tsiwa da karad'i

    Saida Inna ta fahimci Dijah taji jiki sosai tukun taje rabiya, don dai Dijah ko agun sa'anninta bakintane ke cetonta, indai k'arfine to bata da na ko sisi,

      Ahakanma da k'yar Inna ta fitar da ita ad'akin don kafewa tayi da magana wai sai ta rama.

      Har ga Allah badun Inna tana tunanin kar Baffa ya shigo yanzuba da tabarsu ta d'an k'ara dakata don ta lura har yanzu bakinta bai mutuba, kuka tayi kaman zatayi yaya har sai da Inna ta koma rarrashinta ta kwantar da ita akan cinyanta da k'yar tasamu tayi shiru ahaka Barci ya d'auketa,  Inna ta kalleta sai jan zuciya takeyi, ta girgiza kai tana murmushi,               .      "Dijah am Allah ya shiryeki, anan ta zamar da kanta ta kwantar da ita ta tashi,


       Yaune Kabir yake da sati Guda d'aurinsa,
   Bayan Baffa ya shigo gida ya shiga shashin su Kb da niyan gaishesu kaman yanda yasaba,

     Bayan sungaisa ne Habib yace ma Baffah,  yau zai koma bakin aikinsa Sannan suna sa ran ayaune Sani zai zo Baffa yace "To Allah yakiyaye hanya shima yau za'a kunce d'aurin,

       Ya kalli Kabir yana mik'ewa Yace " anjima Dijah zata zo ta kuncemaka d'ori nizanje can wani k'auye gaida Abokin mahaifina,

      "Ah Baffa itama Dijahn ta iya hark'an d'orine Habib ya tambya don ya kula Kabir ya harzuk'a sosai da jin Wai Dijah ce zata kuncemasa d'ori
    Baffah yace "Eh ai takanyi d'orinma ta iya sosai wano lokacinma nata yakan fi nawan kyau, daga Haka Baffa ya fita
    Habib ya saci kallon Kb sai wani had'a rai yakeyi sai k'unshe dariya yakeyi,
      "yadai kb?
    Kb yaja dogon tsaki wanna "yar rainain hankalinne zata kuncenin k'afa?


     " Kai dai wlh kad'au zafi da yarinyan nanne nibanga matsalantaba wlh ni inajin dad'in hira da ita, wani uban hara kb ya masa Habib yafita  yana dariya         "barin sayo kati abakin hanya,

   Wanka tayi ta fito cikin doguwan Riga na atamfa yellow d'nkwali kawai ta d'aura,  tafito tasaka hijabi ta d'auki maganin da Baffa yabata tashafa ma Kb,

     Da sallama ta shiga d'akin aciki ya ansamata, tunda ta shigo yake mata kallon wulakanci,

     "wai ke baki san k'aidan sallma bane? Dakin yi salkam baki jiran abaki izini, mtsss yaja tsaki,
     Turo bakinta tayi ta tsuguna agabanshi,  "Baffa ne yace inkunce maka k'afa kallonta kawai yakeyi baice mata komiba, ta ajiye maganin ta matso, da k'arfi ta rik'o k'afan
      Ahsh ya furta yana rintse idonsa ta fara kuncewa k'afan sai b'ari yakeyi, ta d'ago ta kalleshi, "af ashe kai ragone? Kodayake wannan kad'anne  da aikin "yan birni ba abunda suka iya sai raki da ragwantaka,
   Inkasan zaka b'atamin lokaci kawai inje unk'ira gardawa jaruman "yan k'auye su ruk'eka,

    Tunda ta fara maganan kallonta kawai yakeyi baya ko rintsawa,

 Ji yake kaman ya kifamata mari da gangan tafara jan igiyan da d'an k'arfi bai san likacin da ya dafe hanuntaba ta d'ago suka kafe juna da ido wani abu kb yakeji namasa Yawo tunda ga d'an yatsansa,

     Zame hanunta tayi ta fita sai gata tadawo da wasu k'atti bak'aramin mamaki Kb yayi ba to wainnanfa?

 Aibaigama tunaniba yaji tace ku damk'eshi sosai Don Allah sama da sati biyu kenan ankasa kuncewa, amma fa sai kunyi dagaske,

    Kb baiyi auneba sai ji yayi su rirrik'eshi ta baya, suna masa sannu Dijah tayi murmushin Mugunta, ta tsuguna tafara kuncemasa ahankali,

    Haka Kb yanaji yana gani da yad'anyi motsi k'attinnan zasu sake damk'eshi ahaka har tagama kunce duka k'afafun, dai2 lokacin kuma  su Habib suka shigo shida Iro,

     Cikin mamaki Habib yake binsu da kallo, Dijah tace musu "shikenan mungode,
   Suka sakeshi sai sannu suke jeromasa gamida Allah yabada lfy,
    Tsananin takaicine yahana Kb yin koda motsine binsu yakeyi da kallo har suka fice sannan yadawo da kallonsa ga Dijah da take gaida Habib cike da ladabi kaman da gaske binta yayi da kallo har tafita, sannan ta dawo da baya tana masa wani kallon rainin Hankali "inka d'an huta zanzo inshafamaka wannan maganin daga haka ta fice,

  Habib ya matsoshi yana kallon k'afan
     "Man wai sai da aka rik'ekane aka kunce?
    Haba kai kuwa katsaya aka d'aurama balle kucewa?


🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣

 *ummu fatimac* 🇳🇬
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MY NATION*🇳🇬
         
 

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 1⃣5⃣


    Kai to amma inda mayene ai daya cinyeni tun a Asibiti,

  Toko dai haka jikin maza yake? Tafad'a afili tana zaro ido, zufane taji yana keto mata, indai haka jikin maza yake  sud'in abun tsorone,

    Haka taji tsikan jikinta yana tashi,

   Tadad'e acikin irin wannan yanayi har Jebu ta shigo tasameta anan

    "Dijah lfy kuwa? Naga idonki yayi jaa?
    Taja d'angajeren tsaki "wlh kaina naji yana d'an minciwo,

     "wai kizo inji ya Sani,
       Dijah tad'an zaro ido me kuma zanmasa?
       "Nidai yace ink'iraki ne kawai, 
      Tashi Dijah tayi har yanzu jikinta ba k'arfi ak'ofan d'akin suka sameshi yana rik'e da k'aton flaks,

 Sani ya mik'o mata flaks yace   "Khadijah oga na yanason shayi mai kayan k'amshi pls kitaimaka kidinga masa koda yaushe ba sai da safeba shi har da rana da dare, sai yasha,

    Tad'an ya mutsa fuska waye oganka?
    Mara lfynki,
Yafad'a yana kallon idonta
      Dai dai lokacin Bintalo tashigo da tren kayan Abinci, tana gaisheshi Dijah ta karb'i flaks d'in tafita,

     Tunda Kb yad'ago suka had'a ido da Bintalo yasakarmata murmushi, itama murmushin tamasa ta ajiya kayan Abincin agefe tanamasa yaya jiki, cikin sakun fuska ya amsa natsuwanta da ladabinta  yana burgeshi sosai kana uwa uba kunya yana son mace mai kunya sosai,


    Mamata ya Inna? Lfynta k'alau, d'azu kin gaidamin ita kuwa?
      "Eh tace tana Amsawa, yanzuma tace agaisheka tana maka yaya jiki,  "Nagode k'warai dai2  Lokacin Sani ya shigo ya zauna kan katifa gefen Kb ya tank'washe k'afa yana kallon Bintalo bako k'iftawa, kallon dayake mata ba k'aramin d'aureta yayiba har takasa bawa Kb Amsan tambayan dayake mata,


      Ahankali Kb yad'ago ya kalleshi lfy kuwa malam?

     Sani yad'an yamutsa fuska "da akayi yaya? Nalura wannan bata gaisuwa, "to ina Ruwanka da ita akan me zata gaisheka? Dallah can Malam kafitar mana anan Kb ya runtse idonsa yabud'esu akanta,
     Yace shikenan inma kace ba Ruwana, Nidai nasan da Ruwana, kuma dole arink'a gaisheni, kamar yanda ake gaisheka,
    Yak'arasa maganan cike da kwaikwayon yaranta,


    Kb yaja k'aramin tsaki, ya kalli Bintalo datake ta b'oye Fuska, "Mama ta jeki abunki,  Da daddare kizo muyi  Hira kinji? Da sauri ta mik'e ta fita, tana gyad'a kai,

   Sani yace Gaskiya Oga ba kyautaminba, Haka kawai ka koreta,

Yad'an gyara zama yana fuskantan Kb an
     Gaskiya yaran Garinnan suna da kyau sosai kb,
    Yad'an shafa sajensa yana lasan lips d'insa mai zai hana mud'auki d'ad'd'aya? Ni ind'auki ita wannan Babban kai kuma ka d'auke k'araman don naga naku yazo d'aya sosai wlh ni har kamannin ku nake gani, 

     Wata wayan caja dake gefen Kb ya d'auka yasaiti dai2 bakinsa ya wurgeshi da sauri Sani ya sunkuya cajan ta wauce ta bugi bango ya d'ago yana kallon Kb dayake Huci kaman macen zaki, Sani ya langab'ar da kai yana Murmushi, "Haba oga Kb? Meyayi zafi?

   Kabir yaja dogon tsaki ya had'a giran sama dana k'asa  "kar ka sake kasake Alak'antani da wannan  fitinanniyan yarinyanba, ka iyama bakinka,
      "Shikenan My friend nidai inason Fatima pls kataimaka min wlh jiya danaga tana Hira karkaji yanda naji, Kb ko kulashi baiyiba donyariga yab'atamasa Rai don daya had'ashi da wannan yarinyan gwanda yazageshi yafi mishi sauk'i,

 
   Yau da gobe asaran mai Rai, cikin watanni hud'u Kafan Kb yastmu sauk'i sosai ayanzu har yana iya tsayuwa, ahaka wani zuwan dasu Mami sukayi sukazo masa da wail chair,

  Yau juma'a ga Al'adan Mutanen Rugan Juma "yanmata da samaruka sukan sha kwalliya suje dandali, don ganawa da masoyansu, 


      Kabir nagano Zaune kan wail chair ak'ofan d'akinsu yasha kwalliya cikin fara k'ald'in shadda wanda Mami takawomasa da zata zo shadan sai maik'o takeyi da d'aukan ido yasanya Hula Ruwan k'asa da akamasa kwalliya da farin zare takalmansa half shaoe Ruwan k'asa bak'aramin kyau Kb yayiba jikinsa yayi lufluf sakamakon Hutu darashin  shiga rana dayasamu arugan juma  farin fatansa maid'aukan ido ga d'an siririn sajansa da yakwanta afuskansa gwanin sha'awa yau yafito a Dr Kbnsa badun rashin k'afaba, gawani fitinanen k'amshi dayake fitowa ajikinsa,
        Yayi shiru ya k'urama Iro dayake wankemasa iner waers ido,
         Dijah ce itada Jebu suka shigo tana rik'e da falaks ahanunta,  daga  Dijah har Jebu kusan suman tsaye sukayi daganin Kb dontunda yazo basu tab'a ganinsa cikin manyan  kayaba, kallo d'aya yamusu ya d'auke idonsa, yana kallon Iro dayake shanya,


      Dijah ta lakato Jebu, tana dariya k'asa2 tace "ke kalli Gurgu k'afa yafara samuwa, dukansu suka shek'e da dariya,  yajisu sarai amma yayi kaman baijisuba yana sane da sunan da Dijah  tasamasa kenan jifa jifa yakanji,


tagefenshi ta wuce  d'akin  ta'ajiye flaks d'in,  tafito tana sa Takalmi wasu manya2 k'adangaru guda biyu suka fad'o daga sama,

arazane tayi tsalle takoma gefe dai 2 lokacin kuma suka razana sukaje jikin k'afan Kb Cikin zafin nama yasako k'afa ya wurgo k'adangaren jikinta, yafad'i akan kaf'anta, wani Razanannen ihu tasaka shikanshi sai  da tabashi tsoro,

 jin k'adangaren yana shirin hauramata ne yasa tayi kansa cikin kid'ima, tana tsala mahaukacin Ihu,  da sauri yasa hanunsa ta baya yasuk'e wani k'arfe keken yayi baya dashi, agefenshi ta tsuguna ta kifa kanta akan gwiwowinta tana kuka, shi kuwa goganna ka ko ajikinsa saibin Jebu da take shirin fita yakeyi da harara har ta b'ace ma ganinsa,

    Dai2 alokacin Sani yafito daga ba bayangida  rik'e da bucket ahanunsa kallon KbYakeyi har ya iso ya ajiye Bucket d'in, aranshin kuwa mamaki yakeyi yarasa meyasa In Kabir da Khadija suka had'u sai ansamu Abu irin Haka ko tamishi ko yamata,



Matsota yayi yafara k'iran sunanta Khadija khadija nan ya sauk'e idonsa akan k'afanta yanda farcen k'adangaren ya. Karjeta sha'aninka da farar fata d'ansiririn jini ya gangaro ya taru atakani yatsunta, kallon Kb yayi yana danne2 waya, d'ki yashiga ya d'auko first aid box ya ajiye agabanshi yana gyaran murya Kabir ya kalleshi yana yatsina Fuska, da ido ya nunamasa K'afan Khadijah


    Ya d'an tsorata daganin jinin wata zuciya tace to incizonta sukayifa mezakagaya ma iyayenta da suke d'awainiya da kai?

   Ohonta ai ita tajawo, wata zuciya tabashi amasa,

    "Pls Kb kayi treating k'afan kagafa jinine yake fita,  Sani ya fad'a yana tura kekensa Gaban Dijah, kaman baziyiba sai kuma ko meya tuna? Ya d'auki auduga yasa hydrogen Dijah tana cikin rafsa kukanta taji wani Sabon rad'ad'i, afirgice ta d'ago tana tsala wani ihun,

    Batasan lokacin data  kama Hanunsaba da sauri KB ya fauce hanunsa yanamata kallon baki da hankali,

    Sani ya tsuguna agefe yi hak'uri Khadijah awanke miki saboda jinin yatsaya, ko kallonsa batayiba taci gaba da kukanta,

    Kb yasake miko hanu zai samata ai asab'in ta mik'e ta d'aga kwalban hydrogen d'in ta watsa masa ajikinsa ta bar wajen sai da taje k'ofan da zai sadata da sashinsu ta juyo tana share Hawaye tace "Gurgu kawai wlh ban yafeba,
 

       Da sauri Sani yashige d'aki don ya fitar da dariyan da yake k'unshewa, anan yatarar da Iro ma yana k'yak'yata nashi,


      Tafe suke shida Sani da yake turashi jifa jifa suna hira sosai yanayin garin ya burgeshi kasncewan yanayin farkon shigan daminane Hadirine ya had'u agarin ya baje sai yabar iska mai dad'i da k'amshin k'asa,

   
    Jifa jifa kuma "yan mata da samari masu zuwa dandali suna wucesu Kabir yakan shagala sosai da kallon tsarin kwlliyansu musamman na "yan matan wani lokacin har yakan d'an murmusa, ahaka suka iso k'ofan gidan, agindin bishiyan dake k'ofan gidan yasa Sani ya ajiyeshi sabo da yanda yake jin dad'in iskan da yake kad'awa, yau cike yake da kewan Maminsa yagaji da raahin ganinta dukda yawan wayan da sukeyi akowani Rana,

    Dafe hab'ansa yayi yana tuno Rayuwa step by step,

       Hayaniya yaji abayansa ahankali ya juyo yana kallonsu "yan matane guda uku Dijah ce ta Hud'unsu ga dukkan Alamu fad'a sukeyi kuma ayanda ya fahimci fad'an Dijah ce ta arangamo sannan taja gefe tana bada umurnin yanda za'ayi,

      Sani ne ya k'arasa wajen bayan yarabane ya tambayi Dijah abunda ya had'asu,

     Abunda ya k'ara ba kb da yake sauraronsu mamaki shine ji Da yayi Dijah tace batasan ma me ya had'asuba  sosai ya ware ido yana kallonsu agefe d'aya kuma yana mamakin Halinta ga iyayenta dukansu masu Hak'uri da sanin yakamata amma Su sun haifi hatsabibiya fitinanniyan yarinya,

   Ajiyan zuciya yayi gami da gajeren tsaki ji yake inama ace a familyn Su take? Tabbas da yajima da karairayata, da b'ab'ballata,


      Jerowa sukayi ita da Jebu da wata yarinya dukansu fuskansu yasaha fente2 kala2 banda Dijah don bako d'igon kwalliya afuskanta tun tana mitsila Dijah ta tsani kwalliya yanzu kuwa da ta girma intaga masuyi wani lokacinma dariya take musu, sai dai fa ran da ta tashi da iya shege takanyi haukan kwalliyan da yafi na kowa muni daf da zata shiga Gida taga Su Jebu sunwatse juyowanda zatayi da niyan tambayansu Ina zuwa?, caraf idonta sukayi karo da na Lado, yana murmushi yasha kwalliya sosai irin na gayun Rugan Juma dogon Riga yasa na wata yadi Ruwan k'asa da wando na jeans ya cusa Rigan tagaba acikin wando tabayan kuma yana reto da Hulansa da ake k'ira Rabin hula Kore mai hoton wata da tauraro,

   Ga wani matsiyacin kambus da yasa jajazur fuskanshi sai k'yallin mai yakeyi Tabbas Lado yana d'aya daga cikin manyan gayun Rugan Kuma, wannan yana d'aya daga cikin abunda yasa yayi nasaran samun matsayin zamowa saurayin babban yarinya Dijah,


     Don acikin Rugan juma samaruka da dama sun gwada sa'ansu agurinta amma basu daceba,


    Dijah kam rasa yanda zatasa kanta tayi Don Lado yagama kamata ba halin gudu itakuma ba babban Abun kunya awajenta shine taganta face to face ita da Lado da Ranan Allah gwandama inda daddarene wataran intaga dama takan saurareshi,

    Shikuwa Lado ji yakeyi yau ba Wanda yakaishi sa'a gashi ga abar sonsa, sai murmushin farin ciki yakeyi, kamo bakin mayafinta tayi ta rufe gefen fuskanta ta inda yake tsaye sai wasa da yatsunta takeyi kanta a sunkuye shikuma sai lek'o fuskantan yakeyi yana magana,


     Kb kam duk yanda yaso ya mayar da dariyansa ya kasa Dan haka ya tallafi hab'anshi da bakinsa yana kallonsu ta gefe,


      Sosai yacika da mamakin wannan Rainin Hankalin na Dijah yanda yanzu2 ta dawo kamar mutumiyar kirki,

     Don bawanda zai kalleta bayi tunanin da gaske tana da  kunyaba, wani k'arin dariyansa shine dressing d'in Lado sannan yagama marairaicewa shi adole yana gaban budurwa,


     To wai saboda Allah wannan yarinyan har ta isa tsayuwa da saurayi? Yatambayi kanshi sannan yaja gajeren tsaki, "ai ko saboda tsaban rawan kantama zata fara tsayuwa da samaruka, ya fad'a aransa,



       Duk maganan da Lado yakeyi Dijah bata amsa ko d'ayaba kanta yana k'asa Su na ahaka Jebu ta iso wajen ai ganin hankalin Lado ya koma wajen Jebu tasa Dijah tayi wuf tashige cikin gida,







*Ummu Fatima ce?*
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MY NATION*🇳🇬
 *Dijah k'aya Fans Group* _jinjina gareku mai tarin yawa bazai yiwu ink'ira sunayenkuba sabo da yawanku saida gaskiya inajin dad'n coments d'inku,_😍
 
*Ummu Fatima convwrsation gruop* _jinjina gareku all musamman Mmn Imam Da Aminiyar Dijah K'aya Momyn Sadiq Dijah tace agai sheki_🤝🏻😍
         *Nasadauk'ar da wannan page gareku dukanku*😘

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊






           *page*1⃣4⃣

 Duk maganan da Habi yakeyi kan Kb na k'asa yana tuna randa yasa nurses su d'auki Dijah sukaita d'akin mahaukata,

    "Kenan hakan yana nufin taramane?

    "Tarama me? Sai alokacin ya fahimci maganan afili yayishi,

     Ahankali ya fesar da Iska, yajingina da pillow yana tunani tabbasa zai koya ma yarinyannan hankali, duk da ya naganin ta mishi k'ank'anta yayi wannan game d'in da ita saidai yanda tayi yanzun ya gwada masa cewa, fitsaranta yakai yanda yakai,

    "waima aina tasamo wa innan k'attinne? Habib yatambaya,

      Iro yace "Baffa ne yasasu sudinga danne mata yara inzata musu d'ori ko in zata kuce indai sunyi gardama,

    Saidai abunda yaban mamaki shine bantab'a ganin sun danne babbaba,

   Kabir kam ko kallon inda suke baiyiba, don wani irin takaici da yake ji,


    Dijah kuwa tun fitanta tafara ayyukanta na Gida da tasaba, cikin farin ciki tayi shara, tazo tafara wanke wanke,
Bata ko nimi Bintaloba dondai indai wajen aiki ne sam Dijah bata da matsala, komin yawan aiki intaso nanda nan zatayi ta tashi,

   Saidai Randa Fitinanta yake gaban goshintane, zata tubure saidai suyi da Bintalo,

    Tana wanke wankenta tana wak'a cikin Fulatanci,

  Tabaya taji anrufe mata idonta,

   Tana Dariya, tace Jebu naganeki,

   Jebu ta k'yalk'yale da dariya tazago ta Gabanta ta'ajiye tulunta agefe ta tsuguna, suna fuskantan juna,

     "Yau sai yanzu kk wanke wanke Dijah?

      "ke wai bakisan ankawo wani mara lfy bane agidannan?
      "Nasani mana inace wainnan "yanbirnin nan?
        "Eh, to shine na kunce masa d'aurinsa yau, shiyasa banyi wanke wanken da wuriba,
     "mhmm Dijah Don Allah kikaini ingansu, kinsan Allah inason inga kalansu kullum sai Raben Gidanmu yaban lbr wai wanda yakaryan kykkyawane , sosai har yafi bak'in dasu ke zuwa Gidan  maigari,

    Dijah taja tsaki "kin tuno mutumin da yatab'a watsamin Ruwan kwata ahanya muna dawowa daga Makaranta?
   "Eh,  Dijah ta tab'e baji,
   "Toshinefa,
    Jebu tazaro ido,       "Dan Allah,? 
  "Zan miki K'aryane?
    "a'a nadaiyi mamaki ne,


Jebu ta sassauta muryanta tana kallon Dijah
    "Lado ne fa ya aikoni wajenki,  Dijah  wai Don Allah meyasa kk masa hakane? 

    Wlh na fuskanci baki sonshi, Da sauri Dijah ta rufe bakinta tana kalle2 kar ko wani yaji,

   Tayi k'asa da muryanta "Kibari sai munfita D'ibo Ruwa, sari sauri suka gama, Dijah ta lek'a Bintalo datake gyaran d'aki Ma'u tana zaune agefenta , dama tunshigowansu da Jebu kowa yayi gabansa,
.
 tace "Bintalo munyi gaba,

   Daga haka suka fito saida sukayi nisa, Jebu ta dafa kafad'anta, "Dijah Lado yace baki sonsa, Dijah tazaro ido wayaga yamasa?  "mnmm ai basai angayamasaba, yaushe rabon da kije dandali ? Kuma yace jiyama da yazo k'in fita kikayyi,
    "ke Baffane yakenanfa,
     "Baffa yahanaki hirane? Kawai inbaki sonsane kifad'amasa,
     "kenifa bance banasonsaba, inason.... Sai kuma ta rufe fuskanta da mayafinta tana dariya  ....
      "Gaskiya Dijah wlh kinason bamu kunya agarinnan duk sa'annimu anbayar dasu wata shekara za'ayi aurensu,  so kikeyi sai anfara samu awak'a dukanmu, don kinga muntsaya jiran sai kinfitar da gwani,
    Dijah kam shiru tayi tana sauraran Jebu har suka isa Rafi,
    "Jebu ta Had'a fuska watoma kin barni ina ta zuba kinshareni ko ?
    Dijah ta d'an Murmusa, "Ke Inasonsafa, Amma don Allah karki gayamasa, inkika gayamasa,  Allah nadaina fitowa kenan,

Jebu ta kwashe da dariya lallai Dijah Randa akamiki aure da Lado bansan yanda zakiyiba, d'aki d'ayafa zaku kwana, Dijah ta dafe k'irji Nashiga uku,

     Jebu ta dinga dariya har tana rik'e ciki tana kallon yanda Dijah ta diririce  sai zaro ido takeyi, ahaka Su Bintalo sukazo sukasamesu, Dijah ce ta ciccikamusu abun Ruwan nasu duka sai wani b'oye fuska takeyi kamar mara Gaskiya, Bintalo ta d'ago Fuskanta tana kallonta lfy kuwa Dijango?  Kwace fuskanta kawai tayi tana dariya,

    Ahaka suka d'auki Ruwansu suka jero suna tad'i Jebuce agaba sai Dijah abayanta, 

   Sunyi tafiya kad'an Jebu ta hango Lado zaune akan wani itace, yana hangosu ya fara smiling, don tun fitowansu gida yake binsu abaya yazauna agun yana jiransu,  Jebu sai k'unahen dariya takeyi, "Jebu dariyan me kik.... Ai bata k'arasaba idonta yasauk'a akan Lado,   
     Sake tulun tayi ak'asa ta juya aguje jinhaka, Jebu ma tasaki nata tabi baynta,  Ma'u da take shirin tambayan Dihjah lfy? Ganin Jebu tabi bayanta yasa itama arazane tasaki tulunta ta kwasa aguje, Bintalo ne ma ta juya da nata akanta tana binsu da gudu ganin dagaske suke gudun zasu tsere mata yasa itama tasaki tana awajen ta k'ara k'arfin gudun tana "yau mun boni, Ma'u Hab'e kuka gani ko yau zasu halakamu, jin haka yasa wasu "yan mata ma dasuka d'auko Ruwan suka juya aguje, kan kace meye wannan sai ga wurin d'iban Ruwan ba kowa, kowa yayi ta kansa, Ma'u kam da tafisu tsoro har wani guntun fitsarine a silmiyo mata,

     Ahaka suka shiga  Gida Dijah agaba Jebu abaya sai ma'u bayanta Bintalo, shigowan Goggoji kenan Maman Baffa tana ta rafka sallama lnna tana bayangida ai tana ganin Su Dijah aguje ga fitsari yana bin k'afan Ma'u Itama ta afka d'akin lnna bata ko tsaya maganan cire takalmi ba, ta mai da k'ofa ta rufe,  akan katifan d'akinsu Dijah ta dire sai murmushi takeyi sab'anin su Ma'u da tsoro da tashin hankali ya bayyana afuskansu, sai mai da numfashi sukeyi dai2 lokacin lnna ta d'ago labule tana karanta fuskansu domin ita kam ko ajikinta bata damuba duk da tana bayangida tanajin yanda suka afko gidan da gudu, don tasan indai da Dijah acikinsu za'ayi abunda yafi haka don iyashegen Dijah ya wuce nan ganin yanda Dijah take ta sunkuyar da kai tana muusawane ya tabbatar mata da Zarginta nacewa gudun nasu bashi da tushe ita abun da yafi damuntama Goggoji da ta shige tasaka sakata,

   Jebu ta kalli Dijah tana haki "wai Dijah me kika ganine?
     Bintalo ta zaro ido ta kalli Jebu kina nufin kice dama Dijah ce tasamu wannan Uban gudun?

      Dijah ta kalli Jebu tace "don Allah yaganni? " Wlh Dijah baki da mutunci yanzu kawai dan kinga Lado shine kika sami mukayi asaran tulunanmu gaba d'aya koginnan ba wanda bai yar da tulunsa ya guduba,

    Inna ta rik'e hab'a cike  da takaici tana kallon ma'u da kunya yagama rufeta fatarinta ajiki aharaf, tace "Banma san me zan k'irakuba, yau kuke tare da Dijah? Sai kace baku san halintaba? Shine dankunga ta yarda tulu tasa gudu zaku rufa mata baya, mtss taja tsaki tasake labulen, Bintalo tace "wlh nidai Allah zai sakamin dan ni danaga Jebu agaba nazaci ita tafara gudun danasan Dijah ce wlh ba'abun da zai sani gudu,  Ma'u kam jitake kaman ta zunduma ihu, murya na b'ari ta kalli Dijah da Jebu tace "Tsakani na daku Allah ya isa wlh ban yafeba, tafita tayi gida Bintalo ta watsamusu harara tafita, Dijah kam ko ajikinta batamasan me suke cewaba tunanin Lado takeyi yamata kyau sosai yasha aski irin wanda takeso fuakansa sai k'uyallin mai yakeyi,
    Tad'an kwanto ajikin Jebu tana murmushi tace "wlh yamin kyau sosai ina ga Askin shago yayi bana wajan Baba wanzam, cike da takaici Jebu ta ture kanta ajikinta, dalla can matsamin kinsa munyi asaran tuluna ni yanzu ban ma san me innarmu zatace b, gaskiya nima banyafeba, daga haka tafita,
     Dijah kam gyara kwanciyanta tayi awurin cike da nishad'i tana jiyo muryan Goggoji atsakar gida tana bambami sabo da Allah takwarace zata saku irin wannan gudu? Ai kuma fita sajarci ni danaganku nayi zaton Hab'ene suka shigo wlh,

         Murmushinta take tayi har Bacci ya d'auketa,
       Har akayi azahar acikin baccin taji ana dukan k'afanta, ta bud'e ido Bintalo ta harareta wai kizo inji Baffa da sauri ta tashi ta fito aabakin gadonsa tasameshi yana tofa Addu'o'i acikin magani tazauna daf dashi sai daya gama tamasa sannu da dawowa, yauwa sannu mamata yana baki magani kishafa ma likita in kinkunce masa d'ori, baki shafa masaba?

    "Nabarshi ya hutane fa Baffa, Baffa ya kalleta hutu kuma? Hutum me kenan mamata?
     Ga wannan anjima da yamma kije kishafa masa kinsan bani samun zama ne yanzu shiyasa nake baki don Allah ki kula shiyasa na koyamiki tun baki kai hakaba sabo da wani lokaci bancika samun zamaba,

      Tunda tayi sallahn la'asar ta shiga gidansu Jebu akan tabarma tasamu lnnansu agindin bishiya ta zauna agefenta ta kwanta akan cinyanta tana dariya tace lnna ina wuni,
   Kunnenta lnnan takama gam "dama nimanki nakeyi keda Jebu sam bamsan yaushe zaku girmaba yanzu saboda Allah abunda kukayi da safe kub kyauta? har kukasamin uwata fitsari ajikinta
    Me Dijah zatayi inba dariyaba tace "lnna don Allah fitsari tayi? Nifa bansan gudun me sukeyiba,  oh hakama zakice? To barin aika ak'ira mun Lado yazo intambayeshi shikan ai yasan gudun da sukayi, wuf Dijah ta tashi tashige d'akin su Jebu tabat inna anan tana dariya,

    Jim kad'an Jebu suka fito ita da Jebu suka shige Gidansu,
     Dijah ta d'auko Roban maganin Da Baffa yabata tashafawa kabir,  suka shiga sashinsu,  Sani ta hango da Iro suna zaune ak'ofan d'aki, aka kujerun Roba suna Hira, tun shigansu Sani ya zuba musu ido har suka iso ta d'an gefensu suka tsaya suka gaisa,  Dijah tace "Iro ina ya Habib ? "yatafi gida ga wanda ya maye gurbinsa ya nuna Sani da yake ta kallonsu yakali fuskan Dijah ya kalli na Jebu, fuskan Dijah ba ko d'igonn wani abu wai shi kwalliya yayinda  fuskan Jebu yasha fente2 da zane2
    Dijah tace masa Sannu da zuwa, yana murmushi yace "sannu k'anwata ni sunan Sani kefa?  "Dijah Nice name k'awarkifa?  "Sunanta Jebu,  "nagane Dijah Khadijah ne to Jebunfa? "Zainab,  Iro ya bashi Amsa,
   Gud Khadija and Zainab, lro yace "d'azu Baffa yazo yayi fad'a wai meyasa baki kisa maganinba, "Eh gashi ai yanzu zansa,
    Sani yace "ok kece mai sa maganin? "Eh
    "haba Khadija tun d'azufa muke jiranki, yafad'a yana mik'ewa, yad'aga labulen d'akin alokacin Kabir yana zaune da system agabansa, yana browsing, yasanar dashi zuwan Dijah tare da  Jebu suka shiga, Jebu tagaisheshi ta masa ya jiki aciki ya Amsa yana kallon fuskanta data sha kwalliya abun yabashi dariya, to amma jin ance k'awar mutuniyarsace Dijah yasa shi yin fuska don bayason raini,
     Ganin yanda yake b'ata raine yasa Jebu tafita wajensu Sani,
      Dijah tada'ga labulen ta d'ora akan k'ofa ya yamutsa  fuska yana kallonta, "Malama sauk'emin labule kizo kiyi abunda yakawoki kiyi Gaba, yanayin yanda tayi maganan ne yasata sauk'e labulen dan bataga wasa a fuskansaba, 
     Zama tayi agabansa ya ture system d'in gefe dama amles ne fari irin na "yan kollo ajikinsa wandon kuma tree quater ne, 
       Yasa hanunsa yaye k'afa wandon sai da yakai shi har cinyansa, gashi dayake cinyoyinsa suka bayyana sunkwanta luf luf,
     Dijah ta d'ibo magni tanashirin mulkamasa idonta yasauk'a akan cinyoyinsa,  Dam taji gabanta ya buga, da sauri ta maida hanunta cikin roban maganin sai damawa takeyi, Kb kuwa ya zuba mata ido cike da mugunta sai lasan lips d'insa yakeyi, tsawon lokaci tana ahaka, takasa d'ago  kai takalli inda take, yad'anyi gyaran murya yadai Jarumar  "yar k'auye?
    Jirankifa nakeyi kigama don inada abunyi,
     Cike da tsoro tasake lakato mai d'in zata shafa masa Hanunta na b'ari ta mayar har sai da tayi haka so uku, ya juya kai yana kllon hanunta da take tadama shi da maganin kaman tasamu lalle, 
    "to inkinkasa ki kai ma wanda zai iya Ashe duk jarumtakankin na k'aryane?  Yaja tsaki yana gyara k'afan wandon nasa yad'an sauk'o dashi k'asa kad'an, "malama maganafa nake miki kiti abunda zakiyi inada abunyi kinji? Juyowa tasakeyi ganin yad'an sauk'o da wandonne yasa tafara k'ok'arin shafamasa hanunta sai b'aei yakeyi tana ta kau da kanta gefe shikuma sai bin hanunta da fuskanta yakeyi da kallo, haka take d'an sakamasa da yatsa,  batakai ko inaba ta mik'e tsaye ya finciko hijabinta tadawo tazauna atsorace, sai zaro ido takeyi jikinta ko sai b'ari   "Haka dama  akesa maganin? Wai ya kikayi shirune?
 Ashe dama rashin kunyan naki na k'aryane? Ai nazaci cewa kejarumar gaskene wanda bata hakuri bata mantuwa mairama duk abin da aka mata ashe ba bahakabane,

  Da iya k'arfinta ta finciki Hijabinta ta tashi tsaye tana mishi wulak'anccen cen Kalo ta murgud'a baki tafita,

  Shima wulak'anccen kallon ya rakata dashi yaja tsaki aransa yace nazaci Raishin kunyanki yakai nan ashe ke k'aramar mara kunyace, 

   Dijah tana fita wucewa tayi kai tsaye bata re da ta yi magana ma Jebu

   Tana shiga d'akinsu kan katifa ta zube haryanzu jikin ta b'ari yakeyi haka ta kwanta data rufe idonta  cinyoyin Kb take gani anya ma kuwa mutumne shi? Tunda take arayuwanta bata tab'a ganin wani mutum hakaba amma duk dahaka tana ganindai shi dabanne acikin mutane kai dagani wannan mayene, tafad'a aranta






Tofah😆

*Ummu fatima ce*😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*Ummu Fatima*🇳🇬
         
 

Don Allah mabiya Novel d'innan kuyi Hak'uri najin shiru dakukayi kwana biyu kumin uzuri kowani d'an Adam yanada uzuri,🙏🏼🙇🏼‍♀


Wa irnda sukabini prvt damsu min text a inbox kai Maman Nabil kamma k'irata tayi, wai yataji shiru itafa tamatsu Dijah tashiga Hanun Dr Kb 😍

Kowa yacemata Dijah tana shakkan Dr kb? 🤔😝

Kai Dukanku ina muku fatan Alkhairi acigaba dagashi insha Allah yanzu ba tsayawa🤝🏻


🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 1⃣7⃣


   
             
     Washi gari da safe  Dijah tazogaida Baffa kaman yanda tasaba,
 Kallonta yaketayi
Haryanzu idonta akunbure yake sam baiji dad'in ganinta hakanba,

Har tamik'e yak'ira sunanta tadawo tazauna cikin lallashi yace "Mamata wai meya had'aki da Kabiru ne tun a Asibiti na fahimci kaman dawani abu tsakaninku sai gashi jiya Innan ku tagayamin abinda kikamasa,

  Turo bakinta tayi tace Baffa shinefa ya wurgomin k'adangare jikina,

  K'adangare kuma? Baffa yatabaya da mamaki,
    Yayi murmushi "kenan kin ramane?
   Ta gyad'a kai,
Jijjiga kansa yayi yace "inaga baisanibane Dijah bansanki da fitina da manyan mutane hakaba, karkisake kinji?  Ta gyad'a kanta, alaman to,

   Baffa yace "maza jeki kaimusu abun karyawansu, kizo ga wankina dakike tafitinan nabaki,

Ince kinyi musu? Tace "Eh nayi,   Baffah kaciro wankin duka zan iyayi wlh kuma zaifita tas,


  Ak'ofan d'aki tasamu Kb yana zaune akan kujeran Roba, yana Rik'e da Littafin Hisnul Musulum kallo d'aya yamata ya d'auke kansa,

   Aransa yana tuna irin Ihun datayi jiya, sai yau da safe Bintalo take cemasa Innan badukanta tayiba, shidai yana manakin Halin yarinyan, Anyah bata da matsalan k'wak'walwa? Yatambayi kansa,

Tagefensa tabi tawuce tashige d'akin bayan ta ajiyemusu abun karin sunjima suna Hira da Sani awajen

 har saida Kabir yashiga tamik'e tana mamakin ganin sa yana dogara sanda yana tafiya, yaushe ya warke haka? Tayi tambaya azuciyanta, tana ficewa,


Wanki takeyi nakayan Baffanta mai had'e da wasa, saida ta zauna tagama wasa da kumfan sannan ta tashi tacigaba, haka tayi tayi har tagama tana shanya taji ana rafka sallama tad'ago tana Amsawa tana kallon mai sallaman,

Wata Matace fara k'al da ita kyakkyawa, daka ganta kaga Bafulatanan Asali,
 doguwar rigan  shaddace lemon green ajikinta dayasha aiki tundaga Sama har k'asa da Babban mayafi kalan zaren da akayi aiki ma rigan golden  takalmi da jakanta ma golden ne tana sanye da farin glass a Idonta, Mamy kenan, itanma kallon Dijahn takeyi fuskanta d'auke da murmushi Beutiful baby, tafad'a tana matso Dijah ganin haka yasa Dijah k'arasowa ta karb'i d'ayan trolin datake ja tana fad'in sannu da zuwa haryanzu Mamy murmushin takeyi, Dijah tanufi d'akin inna kicib'us sukayi da Inna lokacin tana fitowa da kaskon turaren wuta ahanunta ganin Mamin yasa ta ajiye kaskon da sauri abakin k'ofa tana d'an tafa hanu "Lale maraba da zuwa Hajiya sannu sannu kece da tsakar ranan nan? Tabarman Roba ta shinfind'a mata atsakar d'akin tana jeromata sannu,


Mamyn sai amsawa takeyi cike da fara'a,


 Dijah kuwa tana fita batatsaya ko inaba sai shagon ilu ta dawo fa peur water mai sanyi ta shige kitchen ta d'auko plate ta juye takai gaban Mamy ta durk'usa ta'ajiyemata, Mamy tana murmushi

 takamo hanun ta "Meye sunanki? "Dijah, tabata Amsa tana d'an Murmushi "Allah Sarki Khadijah tul kubra,
 Kina zuwa makaranta kuwa? Ta gyad'a kai tana murmusawa, ajinki nawa?
"Ss1, very Gud islamiyyafa?
"ina islamiyya4 Haddah 3

"to Khadijah Allah yataimaka ko, daidai lokacin Inna tashigo da dammamiyar Fura da soyayyun zabi ta'ajiye agabanta, tana fad'in "Bismillah Hajiya karkibiye ma wannan surutacciyan, Dijah ta tashi tafita Mami tana dariya tace "Ayyah Inna kingg koremin ita, Ifna takwara tace?

"Mnn Bitalo ce tatafi kitso, d'azunnan,

"Ayyah ita nasani bantab'a samun Khadijah agidaba, duk zuwana biyunnan,

"Eh wlh baku had'uba kam, dake akan k'afanki kk komawa, Amma yaukam kwana zakimana ko?

"Eh inaga zan kwan in Allah yakai Rai gobe sai inwuce,

"to Allah yasa muna raye, Kici Abinci Hajiya Dan Allah,

Mik'ewa Mami tayi tana Ffad'in barin lek'a Marar lafiyannan tukuna indawo,

Can gindin Bishiya ta hango Dijah tana carafke tayafatota da Hanu, dasauri Dijah ta tashi tana kad'e Hanunta ta isota, Mami ta kama Hanunta "Haba Khadijah ba'asan student da wannan wasanba, Inna da take fitowa ad'aki tace "ai wannan student d'in sai ahankali, Mami tayi dariya tace "muje kimin Rakiya,


Tana rik'e da Hanunta suka shiga pert d'in da sallama Mami tad'aga labule, alokacin Kabir yana zaune  da Lap top agabansa, Sani da Habib suna gefensa,

Suna Hira cike da Nishad'i Kallon Mamin yakeyi Fuskansa d'auke da bayyananne farin ciki, sam Habib bai cemasa tare da Mamin sukazoba,

Kujeran Roban dake gefen Kb Mami ta jawo tazauna, ture system d'in yayi gefe ya Matso ya d'aura kansa a gwiwowin k'afanta yasauk'e Nannauyan ajiyan Zuciya, Kaman uwar da taga d'an daya b'acemata tsawon lokaci,


Yakamo hanunta ya d'ora akansa, Dariya sosai Mamy takeyi tana shafa kanshi "My luvly son ya kk? Ya jikin? Wani farin ciki yakeji yana ratsashi gashi ga Mamin sa yad'ago yana kallonta "Mami da ga safe zuwa yanzu munyi waya yakai 3 times bakicemin kina hanyaba Why?
    "dama naso inmaka suprise ne,
Amma naji dad'in ganinka my Son kayi kyau sosai, gaskiya Sani kana kula dashi da kyau, Sani yana dariya yanuna Dijah da ta daskare awajen dan mamaki aranta ko sai gulma takeyi "k'ato dashi yana ta wani sakalci itakuma sai biyemasa takeyi, "ga wacce take kulawa dashi nan Mami tadafa mishi wannan tadafamishi wancan ba dare ba Rana, yak'are maganan yana kallon fuskan Kb da yake hararansa, Mami ta dafa kan Dijah datake zaune ak'asa gefenta, tace "Ayyah Khadijah yarinyan kirki, bani da bakin musu godiya sai Addu'a,

"Mami ina su uncle ne? Kb ya tambaya don son b'atar da zancen,

"suna nan sunce ingaisheka, ba last weak sunzoba,

Nafisa fa baka tambayeni itaba karkaga yanda duk ta lalace wlh Kabir, kasan Yaya yahana asanar dasu cewa kananan har yanzu akan ba asan inda kakebane,


  Kabir yad'anyi Murmushi yace "Mami kodai Sangaya zakiminne? Auren mata biyu lokaci d'aya, wancan yarinyanma kusan kullum sai ta k'irani, kuma tace kekabata no. na,

"Hakanma zaifi wlh Mami a auramasa su dukansu kinga ma shikenan wlh nanda nan zai taro sa'anninmu da sukajima da aure harda "ya"yan nan, Habib ya fad'a cike da zolaya, 

Kb yabishi da harara "dallacan Malam wayasaka bakinka anan, Sani yace "to ai naga duk suna sonkane kb wazaka ki acikinsu ai kawai hakan shine mafita a auramaka su kawai rana d'aya musha Biki 😁

Murmushi kawai Mami tayi dan ta lura sun maida abun sakarci tace "karku damu koma dai ba amuku sangaya ba nasan yanda za'ayi, daku dashi ai duk kanwan jace,

Tamik'e rik'e da Hanun Dijah, Kabir ya Marai raice fuska Mami ina zaki je kuma? Kofa gaisawa bamuyiba,


Zanje mugaisa da maigidan Kabir ina dawowa,

Mami kam ba k'aramin yaba wa Baffa da iyalansa tayiba irin nanda nan da sukeyi da ita don tunda Baffa ya dawo yaganta Yake ta fita da shigan kawo wanan kawo wancan,

  Da Daddare bayan Mami ta idar da Sallah ta je pert d'insu kb a waje ta samemesu zaune akan darduma tunda suka gama cin Abinci basu tashiba,

  Itama agefensu ta zauna, Dijah ma tazauna agefe sun d'antab'a hira Habib yace ma Sani yazo sufita suga gari,

Sukafita yarage daga Mami sai kb da Dijah, kabir ya kalli Dijah yanda ta nitsu kaman wata mutuniyar kirki, had'e fuska yayi cikin tsawa yace ke dalla kiba mutane wuri, sunkuyar da kanta tayi tana shirin tashi Mami tarik'eta tana masa wani irin kallo, "yahaka Kabir? Me tatsaremaka anan?
"Mami zamu yi magana irin na d'a da uwa, "itama "yata ce Kabir ashe haryanzu kana nan da halinka, baka canzaba, ba ason ransaba Dijah tazauna agurin suna Hira, itama Dijah hakanan tajita kaman akan k'aya sosai takejin nauyin Mamin,

Sunjima suna tattaunawa Harsaida Mami taga Dijah tafara gyngyad'i sannan tajata suka shiga ciki,

Lokacin Bintalo tagama ma  Mami shinfid'a a d'akin da yake gefen nasu, tare suka kwana da Dijah,


Washi gari da safene tabasu tsaraban datazo dashi kayan kwalliya sosai ta had'a wasu Dijah sannan tayi d'inki ma Inna da Baffa Harda buhun shinkafa, taliya da sauransu sosai Baffa yayi fad'a nacewan shibayison tadinga d'awainiya haka duk abunda zaiyi na Kabir Don Allah yamasa,  itama tace badon Kb takawo musuba,

 Yau Mami ita kad'ai ta shiga sashinsu Kb sunjima dukansu sun shan Hira takalli Sani tace "yarona naga kaman bakinka akwai magana ya sunkuyar dakai yana dariya sannan yadago ya kalli Kabir "mnn dama yace zai gayamiki,

"Zaigayamin me?  Mami ta tambaya tana kallon Kb Kabir ya kwashe da dariya yace "wlh Sani baka da kunya ko kad'an,

Mami waifa yarinyan gidan nan yakeso tunjiya yadameni wai ingayamiki kisanar da iyayenta shine yakasa Hak'urin yajira infad'a miki,

Mami tace "Alhamdulillah naji dad'i sosai daga ke shirin "yanta kanka da kanka tun banmaka na dole ba

Khadijah yake so? Yarinya mai Hankali ga nitsuwa,

Kabir yad'an Had'e rai "Haba dai Mami mezaiyi da wannan Mahaukaciyan yarinyan? Fatima yake fad'a

Mami tarik'e hab'a Khadijahn ce Mahaukaciyan? Kabir Allah yanunamin gwananka aduniyannan, ta kalli Sani "Insha Allah zan nimamaka izini awajen mahaifinta daga haka ta fice,

Koda tasami Baffa da maganan Fatima yayi farin ciki sosai saidai yasanar da ita tana da manemi zai samu magabatansa da maganan yaji,

Kwanan Mami biyu ta koma duk da Kb ne yasata tak'ara d'ayan amma datazo tafiya bak'aramin damuwa yayiba, haka tayi ta lalkabashi kaman wani jariri,


Ahankali cikin ikon Allah K'afan Kb yasamu sauk'i sosai dan yanzu da k'afansa yake fita yaje masallaci yadawo, saidai d'an d'ingishi dayakeyi, Ganin haka yasa Sani yatafi gida duba Mahaifiyarsa, anan yabar Kb dagashi sai Iro, 

Muje zuwa masoya Dijah k'aya yanzufa aka fara




*Ummu Fatima ce*😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MY NATION*🇳🇬
         






🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊



           *page* 1⃣8⃣



   
 Abun Duniya duk ya taru ya dami Alhaji Ya'u yarasa inda zaisa kansa har yanzu mafarkinsa yak'i yazama gaskiya,


Bashi da buri aduniya daya wuce ya mallaki Dukiyan Kabir amma abun yaci tura, ada yana ganin kashe Kabir shine masalaha saidai yanzu yana ganin yayi wauta dayawa,

ayanzu dai gashi ya halaka Kabir Amma Haryanzu burinsa bai cikaba, baisamu koda takarda d'ayaba  na dukiyan, sannan Mamin da yakeso ya aura aikin boka yak'i tasiri akanta Ga yaranshi guda biyu dayaci burin suyi karatu Su zamo Abun kwatance  abu yagagara, Aminu kam yagama lalacewa da shaye2 ga Nafisa tak'i karatun dayakashe mak'udan kud'i dantayi yanzu tazama saidai wannan samarin ya d'auketa wancan yad'auketa, wani abun Haushinma akan idonsa,

Inyace tafito da Miji tace KB take jira tunda haryanzu ba aji labarin mutuwansaba.

  Wani hucin iska ya furzar, zuciyansa kaman wuta, dan  takaici,

Wayansa yad'auka yayi d'an danne2 sannan yakara akunnensa,  cikin fad'a yake magana, "Nacuceka ko kacuceni kai kace zaka samomin Boka yamin aiki danaje  wajen Fatima duk abunda nace tayi zatayi,

 kasani naje nasameta nace takawomin duk wani duccument na Kabir, sai gashi yayanta yashigo maganan har da shirin makani akotu,  shiru yayi na d'an lokaci Sannan yace no yanzudai kawai so nake akashe Alhaji Musa yayanta inkungama dashi Fatima bazata gagareniba tunda angama da Kabir daga Haka ya ajiye wayan yanajin k'warin gwiwa,

  🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴🌴

  Yau take Alhamis, matasa maza da Mata suna ta shirye shiryen Gobe juma'a Ranane da aka tanadar da wasannin Al'adun FULANI kala kala, Wanda k'ak'anan Rugan dasuke kewaye dasu suke zuwa ayi dasu.


Tun jiya Iro yakeba KB labarin yanda ake gudanar da wasan.

Kud'i sosai KB yabashi don yin nashi.


Tun da aka dawo daga Masallacin juma'a Kabir yake zaune akan kujeran Roba a k'ofan gida cikin kwalliyan shadda sky blue, Da Bak'ar Hula da tasha kari, bak'aramin  kyau yayiba, shiyasa yawancin Masu Wucewa suke shagala da kallon sa.


Shikam Kallon yafara isansa don Haka ya mik'e da nufin shiga Gida,

Dai dai lokacin Baffa ya iso akan  kekensa.

Da sauri Kabir ya matsoshi yana masa sannu.

Cike da fara'a Baffa ya amsa, yad'ora da "naji dad'in ganinka anan Likita,

Yanzu mukayi waya da Hajiya, take cemun wai ka matsa akan wai zaka koma asatinnan,

Cikin girmamawa Kabir yace "Wallahi kuwa Baffa Asibitin danake aiki Suna da buk'ata na Sosai kasancewan gaba d'ayan Asibitin babu Wanda yakaranci fannin dana karanta,
Tun barina wajen ba Wanda yamaye Gurbina Har yanzu  saidai afita waje,

Shiyasa nakeson inkoma tunda naji sauk'i,
.
  Baffa ya jinjina kai bank'i makaba Kabir sai dai zuwan Kawunka na kwanan nan yatabbatar min da cewa zaka d'an zauna anan dai dai agama gano masu Hanu cikin abumda aka maka,

Kayi Hak'uri kaji nasan dole kagaji kodon yanayin Rayiwanku tasha banban danamu.

Meya hana d'an'uwanka dawowane?

  "Mahaifiyar shi ce bataji dad'iba, Anma da sauk'i inaga Gobe ko jibi zai zo insha Allah.

   Baffah yace "Ayyah Allah yabata lafiya.
    Dai dai lokacin Dijah tafito zata shiga Gidansu Jebu, Baffa yace "yauwa Ga Dijah  kuje ta nuna maka Gari, inaga zaman waje d'ayane ya dameka,

Daga haka ya shige ciki yabarsu anan,

 Kabir Sam baiji dad'iba aransa, Dan baya k'aunan abunda zai had'a Inuwansu da Dijah,

Itakam sosai tashagaltu da kallon kb ba k'aramin kyau yamataba, Ahankali Kabir yad'ago ya kalleta,  ya maida idonsa k'asa,  ga yarinya har yarinya kyau da kyan fasali, duk Allah yabata Ga sweet voice,  Sai Hatsabibanci,

Sake Binta da kallo yakeyi kayan FULANI ne ajikinta dark blue fuskanta ba wani kwalliya daga powdar sai kwalli sai d'an jam bakin da tashafa.

Cikin kasallaliyan Murya tace masa "Mutafi,  sake kallonta yayi jin voice d'in datayi maganan dashi,

 wuce wa tayi yabi bayanta,  ajere suke tafiya ahankali kaman masu niman wani abu ak'asa.
 

Sund'anyi tafiya kad'an ya zauna akan Dutsi agindin wani Bishiya,  danshi sam baiyarda da Dijah ba yasan k'aramin aikintane ta cusashi wani gurin.

 
    Saida tad'anyi nisa sannan ta lura da baya bayanta.

Can tahangonshi zaune yana Kallon masu wucewa, "Lallaima wannan gayen ya rainani wallahi badon kar yab'ata Baffa yamin fad'aba da tafiyana nayi, tafad'a tana dawowa, agabanshi ta tsaya tana mishi wani kallo, Ganin bai ko kalli inda take bane yasata matsoshi,  tace "katashi mutafi wallahi ko inyi tafiyana, kab'ata ba Ruwana dondai nan ba birnibane,

 ai bata rufe bakiba ta hango kuliya yana zuwa inda suke wayyo Allah na!! Tafad'a atsorace ta juya zata gudu, cikin zafi ya cafkota yadawo da ita gabanshi, jikinta na b'ari tace "Don Allah kasakeni intafi wallahi banison kule, ta juya tana kallon kullen har yanzu gun yake zuwa, ta juyo ta kalli Kabir Murmushi yakeyi alamun zai mata mugunta, tahad'a Hununta Biyu tana matsan k'olla "Don Allah d'an Birni kayi hak'uri kasakeni in tafi, wani Murmushin muguntan yakumayi
"Waye d'an Birni?
Bakisan sunana bane? Ko rashin kunya?,

 Kayi Hak'uri Don Allah Likita,  tajuya daf da ita taga kullen yanashirin tab'ata wani k'ara tasake tayo kanshi Ganin tana shirin Hawa jikinsane yasa yad'agata cak ya d'orata kan wani k'aton Dutse, ya matsa da baya yana kakkab'e Hanunsa yana kallonta sai b'ari takeyi tana d'angale k'afafunta, Arayuwan Dijah kokun kulle taji sai hankalinta yatashi bare taganshi ido da ido, batayi auneba kawai taga Kb yad'auki kullen ahanunsa yana nufota, ihu tasaka tana shirin fad'owa akan Dutse da sauri ya tareta da hanunsa d'aya, yagyara mata zama yana rik'e da damtsen hanunta, d'ayan Hanunkuma yana rik'e da kullen,  daga ita har kullen sai zare ido sukeyi

Cike da tsoro tafara magiya
 "Don Allah yaya Likita kayi Hak'uri,

Saketa yayi ya Ajiye kullen ak'asa yana Dariya mai sauti "ta ina nazama yayanki? Dani yayanki ne Khadijah dana jima da b'ab'b'alaki,

 Yazaro hankachef a Aljihunsa yana goge Hannayensa yana kallonta kuka takeyi tsakaninta da Allah, hankalinta bajikin kullen da takwanta luf ajikin dutsin tana wasa da takalmin Kb da yake k'afansa,

Yaja tsaki ke ga shegen tsoro kamar farar kura ga kuma rashin kunya, yanzu duk ina wannan tsiwanki yaje?

Tasa bayan hanunta tanashare hawayen da yake ta zirya akan fuskanta tace "Kayi Hak'uri yaya Likita wallahi bazan sakeba don Allah kakoreshi intafi gida Bacci nake ji,

Yana dariya yace to goge hawayenki tas inkinason inkoreshi ba musu takama bakin Hijabinta ta goge fuskanta, ya kalli fuskanta yayi jazur yace
 "Meyasa ne ke bakya kwalliya kamana na "yanmatan garinnan?  Shiru tayi tana sheshshek'a,
"Inbaki ban Amsaba zan d'aukota insamiki acikin Riganki,

Da sauri tace "nikawai bani son kwalliyane bayi burgeni,

Yatab'e baki "Ok masifa da Rashin kunyane kawai yake Burgeki? 
Talangab'ar da kanta tace "
Nifa bana Masifa,

"to meyasa agarinnan ake cemiki Dijah k'aya?

  "Nima haka naji suna fad'amin tun ina k'ara amma ba a fad'a a idona sai abayan idona, tad'an had'e rai wallahi duk yarinyan da tacenin Dijah k'aya sai nafasa mata baki.

Don Allah yaya kakoreshi intafi bacci nake ji tafad'a cikin sanyi murya,

Ya kalleta duk takoma kalan tausayi haka kawai yaji wani iri a zuciyansa,

"Niba yayanki bane nagaya miki Sunana Kabir inbaki saniba, kuma ba gida zamu komaba can wajen wasannan zamuje inason ganin wasan da za'ayi,

Gyad'a kanta tayi da sauri tace to yaya bazan komaba, dariya Kabir yayi har yana d'an sunkuyawa,  jiyake kaman su tabbata ahaka ganin yanda takoma sosai game d'in yamasa.




*Tofah 😆🤔 yau Dijah ce daba Kb hak'uri? Hardace masa yaya?  Gashi tace masa bazata sakeba anya kuwa dagske yaci bulus kenan? Kubiyoni danjin yanda zasuje dandali* 😂

*Ummu Fatima* 😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*Ummu Fatima*🇳🇬
         
 

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 1⃣9⃣


   Juya bayansa yayi yad'anyi taku biyu sannan yajuyo yana lasan lips d'insa yana Murmushi, 

Yana kallon yanda gaba d'aya jikinta yake b'ari ga wani zufa da yakebinta Ganin bayi da niyan koran kulen ya sauk'o da irtane yasa ta daddage iya k'arfinta tasaki wani irin k'aran dayasa kulen ta tashi ta arce,

 Cikin hanzari ya iso gabanta tana shirin fad'owa yacafeta yamayar da ita, zata sake k'walla wani k'aran yasa Hanunsa ya rufe mata baki,

Yanunata da yatsa kika kuskura kika k'ara min ihu ahanan ba abunda zai hana ban wurga magen nan cikin bakinkiba, ya cire hanunsa daga  Bakinta, yana hararanta,


"Don Allah yaya kayi Hak'uri ka saukeni Mutafi, nagayamaka bazan sakeba Allah daga yau nadaina duk abunda nakeyi,

"Tam maza share hawayanki da zufan gaba d'aya, yafad'a yana sauk'ar da ita,

Ya mik'amata Hankachef takarb'a ta goge fuskanta suka tafi,
             
  Daga d'an nesa yatsaya yana hango abunda sukeyi a filin, ba irin wara idonsa da baiyiba amma bai hango Dijah ba, hayaniyan gurinne yamasa yawa danhaka ya juya tacan bayan fili yatafi,

tundaga Nesa yahango Dijah ita da Lado tana tsugune ta tusa kanta atsakanin cinyoyinta ta danne Hijabinta dak'afafunta, Lado kuma ya d'an rank'wfo yana mata magana.

Dogon tsaki kabir yaja aranshi sai mita yakeyi ta yaya za'abar yarinya k'arama kaman wannan tana sauraran namiji?  Ba dolema tarink'a rawan kaiba, wata k'ilama su suke koyamata abunda takeyinnan, yasake jan tsaki ya juya haka kawai yaji zuciyansa namasa zafi,  gangarawa yayi can bakin kogi ya zauna akan wani itace, yana wurga k'ananan duwatsu acikin Ruwa.

Daga ta bayansa yaji motsin k'afa ahankali ya juya suka had'a ido da Dijah da Jebu, dawo da kansa yayi kan abunda yakeyi harsuka k'araso, 

Aciki ya amsa gaisuwan Jebu, ko kallonsu baiyiba, harsuka gaji suka koma, yajima agun yana zaune daga bisani yad'auko wayansa a Aljuhu Sani yakeson yak'ira don d'azu yaga text d'insa Wai may be yadawo ayau,

Yana shirin k'iransa Wayan Mami ya shigo sai da yamurmusa ya d'auka bayan sun gama gausuwa tace "zakabari zuwa next Month d'inko?

 Yad'an shagwab'e murya yana kwantar da Murya pls Mami aduba uzurina, kinsanfa akwai cus d'in da zanyi a England kuma inaga tafiyanmun bazai wuce nanda da three weaks ba pls Mami yafad'a in a cool voice.


"shikenan Kabir bazan hanaka dawowaba insha Allah ina zuwa asatinnan mudawo tare,


Wani ajiyan zuciya ya sauk'e mai nauyi yace "To my Mum nagode sosai dakika fahimceni, Allah yakaimu,

"yauwa sai maganan Sani da yarinyannan na tambayi mahaifinta awaya akan maganan damukayi dashi nacewa zai  tintub'i iayen yaron fa yake nimanta, yanzu yace ba matsala kawai aturo, kai yanzu me kagani?

Kabir ya zaro ido kaman yana gabanta yace "Mami batayi k'aramaba kuwa ace yanzu za amata aure?

Mami tace "Matsalana dakai kenan Kabir mantawa nayi namaka maganan yo ai ko Khadija k'anwar Fatima batayi kad'anba amata aure balle kuma takwarata.


"Habadai Mami kidaina sa wannan yarinyan alisaffi,

"to shikenan Kabir nidai yanzu zan gayama su Yaya sukai musu Sadaki kawai kuma kai zaka bayar,

 yayi Murmushi "karkidamu Mami hatta kayan auren da gidan dazasu zauna nad'auki nauyi zanbayar,  "To Allah yasaka maka da Alkhairi,

Daga haka suka ajiye wayan, mik'ewa yayi dashirin tafiya yahango Dijah zaune jikin bishiya

Ta jingina kanta da bishiyan tana bacci, d'abi'an Dijah kenan indai zatayi kuka to tabbas zatayi Bacci, taso tatafi gida sai dai tana tunanin kar ta tafi Kabir yakasa komawa Gida 😆

Ragowan Dutsen dayake Hanunsa ya wurgeta dashi, firgit ta tashi tana sosa wajen ya harareta "oya tashi mutafi,  daga haka ya juya ta tashi tabi bayansa,


"Khadijah taji ya k'ira sunanta ahankali tad'ago ta kalleshi,

 shid'inma itan yake kallo,  ya tab'e baki yace "wai mekike gaya ma samarukanki insun zo Hira wajenki?

 Mai da kanta tayi tana kallon k'asa batasake d'agowa ta kalleshiba,  shima bai kuma cewa komiba,

can anjima yaga ta kalleshi tayi murmushin da baisan nameyeba,  Sannan yaga ta sunkuya ta d'auki k'aton Dutse a hanunta sam bai kawo komi aransaba,  duk da Murmushin dayaga tanayi ahaka harsukazo kusa da gida, 

da sauri Dijah ta k'arasa Jikin wata k'atuwar Bishiyan Kuka ta tsaya awajen tana dariya,  kallonta kawai yakeyi har yak'araso wajen yana shirin tambayanta kotasamu matsalan k'wak'walwa ne,

 Dutsen da yake Hanunta ta saiti Gidan Zuma da yake kan Bishiya ta wurgesu dashi,  ta tsula da mugun gudu tashige cikin Gida,  haba ai kan kaceme zuma sun taso gadangadan wajen Kb suka yo ga  wani adabbaben turaren dayake tashi ajikinsa, ga k'afansa har yanzu batagama dawowa Normal ba,
Tashin Hankali🤔

 Gudu yafara mai kama da sassarfa, Sake fitowa tayi daga cikin gidan tatsaya abakin k'ofa tana tafi "Gurgu sai katsere, Gurgu sai katsere,

dai dai lokacin Motan sani tafaka awajen ganin haka yasa ta juya ta koma batare da yagantaba.

 cikin zafin nama Sani ya Bud'e motan Kabir yashiga ya rufe baiyi auneba yaji Harbin ahanunsa Runtse ido yayi yana yarfe Hanun ya jingina kansa ajikin seat d'in motan yanajin yanda harbin yake ratsashi Sani ya had'a hannayensa yakashe zuman k'waya d'aya data biyoshi, yana kallon Kabir, yace

"Sory garin yaya Kb? Tunda nazo garinnan bantab'a ganin zumannan sun tashiba,  ko turaren kane yad'agosu? 


Bud'e idonsa kawai  yayi ta glass d'in Motan yake ganin yanda zuman suke  shawagi awajen batare da yace komiba,


Ahaka Baffah yafito daga cikin gida zai shiga gari dukansu suka fito Kabir yana goye da Hannayensa abaya suka k'arasa suna masa sannu,


"a Sani kadawone? Ya kabaro mai jikin?

"a jiki Alhamdulillah,

"to Allah yak'ara mata lfy
"Ameen,

Kallon Kabir yayi "yace Kabir har kundawone?

 "Eh Nadawo ind'an hutane ya fad'a yana shafa kanshi,

 "to barka inace dai ba wani matsala?

Sani yace Zumace ta harbeshi Baffa,

 "Subahanallahi garin yaya Kabir?  Yarane suka tab'osu ko?  Dondai basu tashi hakanan,

Sunkuyar da kansa yayi tabbas da yasan Sani zai fad'a daya kwab'eshi,

 Yana d'an murmushi ya kalli Baffa "nad'an zaunane ak'asan Bishiya watak'ila k'arfin da turarena yake dashine yasa,

"Ayyah to sannu barin dubomaka magani kashafa.


Tundaga wannan Rana Kabir yayi saranda wa Dijah yayarda da kirarin da mutanen garinsu suke mata, ya k'ara mata matsayi sosai awajen Hatsabibanci, yak'udura aransa bazai sake shiga sabgantaba,

To ab'angaren Dijahn itama hakane saida takoma gida gaba d'aya taji kunya yakamata sam taji bata ji dad'iba can kuma taturo baki ita kad'ai tace "to shima wayace ya shunamin Mage? Wlh inyasake nima Ramawa zanyi, ko da dare yayi bata yarda takaimusu Abinciba Bintalo ce takai tea d'in sama da tadafa wa Jebu tabayar takai masa wasan b'uya suka dinga yi sosai.



*Rayuwa kenan* yau take Alhamis ayaune Mami ta diro Rugan Juma da niyan komawa da Kabir.

Bak'aramin tarba Inna tayima Mami ba, dukda tamusu zuwan bazata,  bayan ta hutane ta tambayi Su Khadjah,  Inna tace sunje can gidan kakar su Goggoji, 


Ayyah KB fa zai tafi yabar Dijah to ko yaya zata kasance
Kubiyoni


*Ummu Fatima ce* 😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*UMMU FATIMA*🇳🇬
         
  *Don Allah kuyi Hak'uri my Fans najina shiru da kukayi, Blood sister nane akamata cs ancire twins acikinta ina ta d'awainiyan asibiti Sam bana samun zama,*


🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 2⃣0⃣


    Washi gari da safe Mami tashiga d'akin Baffa Bayan su Gaisa ta gyara zama tana kallonsa  anitse tace "Baffa Bani da Bakin godiya agareku na irin d'awainiya da kukayi da Kabir, sai dai Addu'an Allah ya muku sakamako da Gidan Aljannah,


 sannan ina k'ara Godiya game da Babban kyautan da akamana na amincewan Bamu auren Fatima, masu kawo kud'in aure sunkoma suna san barkan  irin tarban da akamusu, naji dad'i sosai Allah yak'ara Girma,

 "Ameen Baffa yace sannan yad'ora da "Hajiya Kabir yafi k'arfin Komi awajena sam babu godiya tsakaninmu, Haka banso Rabuwa dashi duk da dama nasan jinyane yakawoshi inyaji sauk'i zai koma amma Sam naji babu dad'i,

Mami tad'anyi Murmushi "a'a Baku Rabu da Kabir ba, Allah ne yahad'amu Baffa Insha Allah Muna tare,

Ya jinjina kai yace to "Allah ya taimaka, nagode sosai, kukuma haka Allah yayiku? Wasu na k'yaman 'yank'auye ku kina k'aunansu,

"a haba wazai k'yamaci tushensa? Mami tafad'a tana murmushi,

Baffa ya gyad'a kai yace "hakane ga mai tunani,
maganan auren Bintalo kuma Hajiya duk lokacin da kuka shirya kuzo kawai insha Allahu baza'a sammu wata matsalaba,


Mami tad'an k'ara muskutawa tana kallon shi tace "to Baffah nagode Allah yabar zumunci,

Shiru ta d'anyi sannan ta d'ago ta kalleshi, Mnnm Baffah karka gaji dani, nakuma zo da  k'ok'on barana har iyau, inaso  kataimaka kabani Khadijah intafi da ita, taci gaba da karatunta, don naga yarinyan tana da k'ok'ari sosai kuma tana son Karatu, ta k'arasa tana kallon idonsa, shirune yabiyo baya, sannan ya nisa yana jinjina kai ya d'an tura Hulansa baya yana shafa fuskansa, yace "to Hajiya Bank'i mikiba,  sai dai kinsan munan karkakra bakaman Birniba, can rayuwa ne na kowa ya iya Allonsa ya wanke, ba Wanda zai sama ka ido cikin lamuranka, sab'anin Mu nan da duk abunda kayi idon wani na kanka, yanzu ina d'aukan Dijah inabaki, to ina mai tabbatar miki m da fita kuma sai dai inzan sa Abu intoshe kunnena,  kowa da irin Abun da zai dinga fad'a akaina,  nabbata akwai wa inda zasu iya cewama na turata karuwanci don dama idon kowa nakan Dijah, Kiyi Hak'uri Hajiya Ba hanaki Dijah nayiba sai dai ina gudun gutsiri tsoman jama'a,

Mami tad'anja numfashi, tace "to  ai karatu zataje tayi kaga yanzu bai wuce saura wata d'aya da wani abuba tagama secondary kuma anan babu makarantan da zataci gaba  inaga kaman hakan ya ishemu Hujja,

"Nasan aranki zaki tsammaci nine baniso, wlh karatun nand'inma karkiga yanda ake zagina akai,  kawai dai na toshe kunnena, ayanzu koda auren Dijah nayi abirni sai nasamu masau zagina agaefe don komi indai akan Bintalo zai zo da sauk'i, sab'anin Dijah.


Shiru Mami tayi na lokaci sannan ta Nisa tace "to yanzu kana ganin ba wata hanya ko wata dabara da zammuyi? Tunda ga 'yar'uwanta basai in anyi bikin Fatima sai sutafi tareba, inyaso daganan sai tacigaba da karatunta,

 Baffa kam rasa irin bayanin da zaiyi ma Mami ta fahimceshi yayi don haka sauk'e kanshi k'asa kawai yayi batare da yace komiba.

Aranshi yana tunani yaza'ayi ya d'auki 'yarshi mace yabada ita atafi da ita sannan ba dangi iya bare na Baba haka, duk da dai baya zatonsu da wani mummunan abu, bazai iyaba,

Ta hanyan aure ne kawai zai iya yarda yarabu da Dijah, bahaka kawaiba,



 Mami tayi shiru aranta tana tunani tabbas tasan abune mai wahala dama Baffa ya amince yabata  Dijah  cikin sauk'i,

Don Haka ta nisa  tace "karka damu Baffah zamu samu mafita insha Allah barinje inga Marar lfyn naka, tafad'a tana mik'ewa, sashinsu Kabir ta shiga kai tsaye.

Kabir yana zaune cikin kujeran Roba ya zuba k'afafunsa  ackin guda dayake gabansa ya manna bayansa acikin kujeran kansa yana kan saman kujeran yana kallon Sani da yake taramasa abubuwansa masu amfani acikin akwati yanata masa shak'iyanci kala2

Shikuwa Kb kallonsa kawai yake bako k'ifta ido batare dayace komiba,

Jin motsi abayansane yasashi juyowa, yasauk'e idonsa akan Mami, Murmushi yayi har hak'oransa suka fito,
Yasauk'e k"afafunsa yana kallonta, "Welcome My Mum tun d'azu nakesa ran ganinki Mami,

Murmushi tayi ta juya tana kallon sani, tarik'e hab'a "Wai duk d'okine hakan yasa kukafara shirya kaya tun yau? Kabir ya langab'ar dakai "Mami inacefa yau zamu tafi,  "Haba Kabir sai kace d'aukan wuta, sai mun k'ara sati nangaba, tayi maganan da zolaya, Sani yafito daga d'aki yana dariya,

Yaja kujera d'aya yazauna yana fuskanta Mami,

"Wlh Mami tun jiya yad'agamin Hankali daga jin isowanki yasani nafara perking sai kace yak'i,

  Ni wlh yanzu garin yafaramin dad'i yafad'a yana shafa kansa,

Kabir ya wurgamasa Harara "to wayace dole sai katafi? Kayi zamanka  tunda yanzu kazama mara kunya kaci gaba da rashin kunyanka, daga Haka yajuyo yana magiya ma Mami, dariya kawai take.




Tun bayan fitan Mami Dijah take zaune awajen gaba d'aya jikinta ba k'arfi tarasa meya kashe mata jiki ko aikin da ta sabayi yau kasawa tayi,

Ahaka Mami tazo tasameta agun ta zauna agefenta tace "yadai Khadijah? Dariya tayi tace "babu,  sannan ta tashi tafita,

    Tulu ta d'auka ta lek'a d'akin inna  tece mata ta tafi d'ibo Ruwa, tana fita tashiga gidansu Jebu suka fito suka tafi Rafi suna dawowane Jebu ta rik'o gefen Mayafinta "wai Dijah meye yasameki ne yau naganki kaman baki da lfy?

"lfy na k'alau ta amsa atak'aice tana cigaba da tafiya Nima haka kawai tun jiya najini bani dai2


"To Allah dai yasa lafiya inji Jebu yauwa yau da safe naji Iron gidanmu yana cewa d'an birni zasu koma garinsu, dagaskene?

Dijah ta sauk'e ajiyan zuciya, "Haka dai jiya Mamin sa tagayamin, kinsan meye? Wai tace tanason tafiya dani, nasan kuma Baffa bazai tab'a yardaba nima kuma wlh tsoro nake ji,

Jebu taja ta tsaya agun tana kallon Dijah cikin damuwa tace Dijah tafiya zakiyi kibarni?

"yaushe Baffana zai yarda? Wlh nasan bazai yardaba,

Jebu ta yi ajiyan zuciya tace "wlh inason kije Birni ko don wata ran inje wajanki sai dai bani son kitafi ki barni inkin tafi shikenan bani da k'awa,

Dijah inason zuwa birni ban tab'a zuwaba inason inje inga yanda ake lbrn birni,

Duk maganan da Jebu takeyi hankalin Dijah baya wajen ta lula wani Duniya da bansan inabane,

Sosai Kabir ya tasa Sani da iro agaba sai da suka gama had'a masa duk wani abun da zai tafi dashi kafin suka kwanta Bacci,

Washi gari kan kace me sai gashi har Kb yagama shirinsa fes cikin k'ananan kaya blue jeans da farar shirt mai layin blue mai gajeran Hanu, bak'in socks yasaka da bak'in takalmi sau ciki, sai baza k'amshi yakeyi,

Duk tsokanan da Sani yakemasa ko ajikinsa, Burinsa kawai yaga Mami tashigo cikin shiri,

Yanatsaye Hanunsa d'aya na cikin aljihun wandonsa yad'aga d'ayan Hanun yana duba agogo mai cain d'in silban da yake d'aure ahanun,

Dai2 lokacin suka shigo ita da Dijah datake rik'e da flaks tana binta abaya,

 Kallonsa takeyi har suka iso shikuma idonsa yana kan Mami, zai yi magana kenan, Mami ta dakatar dashi tana nuna masa flakcs d'in hanun Dijah "karb'a ka karya kafin kafaramin wani coplain,

Bin inda ta nunan yayi da kallo,  sosai yayi mamakin yanda yaga Dijah so silent kaman wanda k'wai ya fashewa aciki take abu, jan kujera yayi yazauna ahankali ta durk'usa agabansa ta'ajiye flacks d'in dai2 lokacin Bintalo ma tashigo da kulan soyayyar doya da kw'ai ta ajiye tana gaisheshi,

Mami tace "Khadijah d'auko cups kizo ki had'a masa tea,

Tana had'a tea d'in shikuma ya tallafi hab'ansa yana kallon Hanunta,  bai tab'aganinta cikin nitsuwa hakaba, saidai yasa aransa tana da dalilinta nayin hakan, watak'ila wani iban Albarkan takeson yi masa,

Tana mik'a masa ta had'a ma Sani sannan ta juya ta tafi, Haka Mami ta tasashi gaba har sai da Yaci ya k'oshi sannan ta koma sashin Inna alokacin Dijah tana zaune akan itace ta Rafka tagumi,  "khadijah je ki tattaro abun da sukayi break d'in ki shigo dashi, tana fad'an haka ta shige toilet, don watsa Ruwa,

Zaune ta sameshi a inda ta barshi yana rik'e da goran Faro yana sha anitse gefensa Iro ne yana zabga godiyan irin kayan da Kb ya taramishi,

Kallo d'aya yamata ya kau da kansa, har ta iso bai kuma kallon inda takeba,

  "Khadijah taji muryansani daga d'aki, amsawa tayi ta shiga da sallamanta duk da labulen ad'age yake,

Kallonta yayi yana Murmushi "K'anwata yadai naganki haka?
Ko kinajin Rabuwa da mutumin nakine Abokin fad'anki?

Turo baki tayi "wayene Mutuminan? Da bakinsa ya nunamata Kb, da Harara ta kalli inda Kabir d'in yake yayi dai2 da lokacin da yajuyo yana kallo cikin d'akin, shima Hararan yasakarmata, atare suka janye idonsu,

Sani ya kwashe da dariya, ya jawo wata Leda ya mik'a mata "Ga wannan wayan kiba wa Fatima kice mata tahad'a zank'irata, 

Gaskiya zanyi Missing naku Khadijah, don Allah inma tak'i karb'a kihad'a zan k'ira,

Dijah ta gyara tsayuwa tana juya ledan ahanunta, "Yaya Sani ai dagani Har Bintalo ba mu isa karb'an wannan kyautaba,
Saidai ka kaima Baffah inya karb'a to, Amma nasan innina karb'a zaimin fad'a tak'arasa tana ajiye masa wayan akan akwatinsu,

 Kai ya jinjina aransa yana k'ara yabama Tarbiyan Baffah

   Afili kuma yace "Naga dai ni yayankune Khadijah yanzufa munzama d'aya,

"Duk dahaka wlh Baffah zai yi fad'a sosai,

"Ok to badamuwa  zanbashi,

Tabi d'akin da kallo tace "Bayau zaku Kwashe kayanku bane? Cikin zolaya yace

"Kabir yace yabar miki duk kayan d'akin, har frich d'in ki dinga shan Ruwan sanyi,

Ta tab'e baki tace "baniso daga haka ta juya tafita,

Cups d'in gaban Kabir ta sunkuya tana kwashewa dagangan ya saiti Fuskanta ya matsa Goran Faron dake Hanunsa, Ruwan ya tsartu ya wanke mata Fuska, tana d'ago kanta ta juya tafita batare da ta kalleshiba, d'an Murshin Gefen baki yayi yarakata da ido,


Misalin 11:00 na safe suka fito kusan gaba d'ayan "yan unguwa sun Hallara ajikin Mototinsun,  Sosai sukaji Rabuwa da Dr Kabir domin ba k'aramin amfana sukayi da zaman nashi, musamman wajen kula da lfynsu don tun kafin k'afansa ta fara warkewa duk wani mai cuta inyazo wajensa  zai dubashi ya rubuta masa magani inkuma akwai awajensa zai d'auka ya bashi ya shashsha aikan Sani ya sayo masa magunguna acikin gari don mutanen wannan yanki,

Tsaraba kam Kabir har yagaji da karb'a daga masu bashi zabbine, k'wai ne fruit ne kai har da masu bashi naira d'ari, d'ari biyu, Baffah kam Saniya yasa aka yanka aka sa ad'ayan motan seceurity,

Sosai ya matsu Mami tafito su tafi, k'asa2 yake ta tsaki Gashi ko yak'irata bata d'auka, ahankali wasu suka Fara Raguwa, ahaka ya hango Mami rik'e da Hanun Dijah gefensu Bintalo ce da Ma'u da Jebu,

Har suka iso bakin Motan yana kallon Fuskan Dijah ko ba'a fad'a masaba yasan tayi Kuka sai dai bai san dalilinta na Kukan ba,

Kwantowa Mami tayi dai dai Kunnenta ta gayamata magana sannan tasake Hanunta ta shafi gefen Fuskanta ta shige Mota,  ahankali ta tako kusa da Kabir da yake k'ok'arin Bud'e Murfin Mota,  murya k'asa2 tace masa "Yaya Kabir Allah ya kiyaye hanya ku gaida gida,

Kai kawai ya jinjina yana kallon k'wayan idonta, ya shiga Mota, gafen Sani ta Matso tace "yaya Sani Allah ya kiyaye hanya,

"Amen k'anwata Baffa yak'i karb'an wayannan anma zan k'iraku da na wajen Iro. Yafad'a yana kallon Bintalo datake ta b'uya abayan Ma'u

Ta gyad'a kai tana juyawa, Motansu ta fara juyawa zata tafi  kenan sukaji ana buga Motan alamun su tsaya,  Goggoji ce ta k'araso wajen, ganinta yasa Kabir saurin zuge gals yana dariya, "kai tsohuwa yau danafi bamu ganaba danamiki saki tara, 
"waneni Kabiru wlh natafi can waje gyatumace tarik'eni da tad'i, zaka tafi baka bani magani naba Kabiru,

"na isa?  Ai nabama Fatima ta kai Inna ta ajiye miki zata miki bayanin yanda zaki sha inya k'are kigayama Iro yagayamin awaya zanbayar akawomiki wani, Gogoji takamo Hanunshi tace Kabiru Allah yamaka Albarka yabaka zuri'a  mai Albarka  ta kunce bakin zaninta ta ciro gudan naira Hamsin tasa masa ahanunsa, da zobe mai kyau na azurfa  "wannan Zoben ka adanashi duk lokacin da Allah  yasa ka auri matan da kake sonta kaba ta wannan zoben nima Mijinane Allah yajik'an Rai yabanishi adaren amarcinmu,

Kabir yana murmushi yace to Goggoji na gode sosai Allah yasaka, Hamsin d'infa? Kasha Ruwa ahanya, daga haka ta juya ta tafi, motansuma tayi Ribas tafara tafiya tacikin madubi yake kallon Fuskan Dijah da yake ta ambaliyan Hawaye, d'ad'd'aikun Mutane dasuka saura agun sai d'aga musu hanu sukeyi har suka bar wajen,

 Kwantar da bayansa Kabir yayi yana murza Zoben da Goggoji tabashi yana tunani magananta,  yad'anyi Murmushi a fili yace "indai don so ake aure to har abada bazanyi aureba Goggoji don bawata mace dazan so har abada, bayan Mami ta.





Tofah masu karatu kunji furucin Kabir🤔

Wai ya zata kaya gadai Kabir zai koma gida ga kuma Alhaji ya'u babban mak'iyinsa waishin yazaiyi randa sukayi ido hud'u da Kabir??...     
Kubiyoni

*Gamasu buk'atan comments ko gyara ma wannan labari k'ofa abud'e take ga no. ta :08065091824: sai naji ku taku Ummu fatima* 😍
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
 

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 2⃣1⃣


   
             
 
 Sani yayi kamar bai jishiba aransa yana addu'an Allah ya nunamasa randa zaikama Kabir da wannan furucin dayadad'e yanayi,


 Kwanciya yayi luf acikin sit d'in yana kallon motan  Mami da yake tafiya kaman bazai tafi, Don sam Mami bata yarda ayi agudu da ita, shiyasa har yau tak'i canja tsohon drivernsu,  juyawa d'ayan gefen yayi yana kallon motan seceurity sum airin tafiyan sauran motan sukeyi, yaja d'an gajeren tsaki afili yace "Wlh na matsu inganni acikin d'aki na gaskiya nayi missing Bed d'ina over,

Sani ya kalli agogon Hanunsa,  ka kwantar da hankali Minti goma kacal ya rage insha Allah,


Wai Kb wani mataki zamu d'auka akan Alhaji ya'u ne?

"kafa iya ma bakinka nagaya maka banison Mami tagane cewa yana da Hanu cikin maganan har sai kungama binciken ku kun gano kome.

Sani ya d'an kalleshi "kana nufin har yanzu baka gamsu bane? Duk hujjojin dana baka basuyi bane? Najima ina zargin Alhaji ya'u cikin son ganin yaga bayanka, sai gashi zargina yazamo gaskiya yanzu da abunnan yafaru wlh ranan da suka tsare motocinmu da idona naga gayannan lokacin da yabi Motanmu yana Harbi sannan kuma da idona yanzu nake ganinsu tare da Alhaji ya'un,


Sannan naji da kunnena suna hiran bayan maganan da Nafisa tagayamin yagaya mata,

Bai kamata azuba masa idoba Kabir yakamata ada'auki mataki,

Kabir yad'an Murmusa yana kallon waje yace "Tun kafin ka gayamin wannan magana nida Habib munsan komi, sai dai inason abi komi ahankaline, ko bakomi ubanane shi sannan kuma ina sa ran auren "yarsa don inason cikama Mami ta Burinta, don bata da Burin da yawuce haka.

 Tunda mai gadi ya wangame Gate d'in gidan, Kabir yake ta murmusawa har suka faka aka bud'e masa k'ofa yafito pert d'insa ya shige kai tsaye,  komi na part d'in agyare yake fes dashi har yanzu k'amshinsa yana nan kaman koda yaushe, afili yace "wannan aikin Mami tace, uwa ta gari Allah yabani daman cika miiki burinki koda Hakan yana nufin Bak'in cikinane, indai ke zakiyi farin ciki shikenan,

 Yana shiga Bed room ya zube akan gado ya lumshe ido yana shak'an iskan dake shiga da fita ad'akin, photon Dijane yazo masa idonsa siraran Hawayenta da yake sintiri akan  fuskanta yake gani da sauri ua zabura yatashi ya zauna afili yaja tsaki yace "stupid girl, ya mik'e yana k'ok'arin rage kayan jikinsa aljihunsa yaji abu ya ciro zobe da Hamsind'in da Goggoji ta bashine yayi Dariya yana girgiza kai ya zubasu akan Mirrow,   ya shige toilet,


       *Bayan sati d'aya*


Zaune yake akan kujeran k'ofan shiga part d'insa ya d'ora k'afansa d'aya akn Table d'in dayake gabansa yana waya da abokan aikinsa, kan yanda tafiyansu zata kasance, nan da sati biyu,  Motoci ne guda biyu suka shigo gidan kusan ajere, d'aya nasu Abban Habib ne da uncle Musa d'aya kuma na Alhaji ya'u maida kansa yayi yaci gaba da wayansa batare da yakalli fitowansuba,

Yana gama wayan ya tashi yashiga lambun gidan yana zagawa,  jin wani abu yakeyi aransa mai kama da kewa,  Sannan wani sashi na zuciyansa yana kamomasa photon irin shak'iyancin da Dijah takeyi yarasa meyasa hakan ke damunsa, yana cikin wannan Tunani yaji wayansa tana Ringin yana dubawa yaga Mami ya kara akunnensa, "kasameni afalo ta fad'a atak'aice sannann ta kashe batare da taji me yaceba,


Zaune suke su biyu akujera d'aya Alhaji ya'u yana fuskantansu, yayin da Mami take tsiyaya Ruwa agaban Alhaji ya'u, ta koma ta zauna shikuma ya d'auka yafarasha yana d'an mata wasan da suka saba (wasan k'anin Miji, ) dai2 Lokacin ne kuma Kabir yashigo da sallama,  har ya iso tsakiyan Falon Alhaji ya'u yana shan Ruwa, Kabir yasami guri ak'asa daf k'afan Mami yazauna, tas sukaji k'aran fashewan cup agurin gaba d'ayansu dama shi suke kallo ban da Mami da take kallon Kabir, Gaba d'aya ya dirieice har yafara tunanin ko magarki yakeyi, wani irin zufane yake ketomasa ta ko ina, jiya2 yagama narka mak'udan kud'i wajen canja takardun cpanin Kabir d'in yana mafarkin campani yazamo nashi sai gashi yayi mafarkin ganin mai campanin, 

Cikin tashin hankali yanuna Kabir "Dama kanan ataye?

Kallon2 Abba sukayi shi da Uncle Musa, Mami tad'an Nisa tafara magana "kayi Hak'uri Dadinsu tun randa muka dawo da Kabir nake k'iranka awaya, dama nafidon sai kazone gaka gashi inshaida maka yanda akayi, Kabir yana raye bai mutuba dam..

Dasuri Uncle Musa ya katseta ganin zata ruguza musu plan,  "Eh tabbas Kabir yana raye Dama hatsari yayi ahanyan Abujah likitoci suka tsinteshi kasancewan sun sanshi yasa suka rik'eshi agunsu basu sanar da kowaba, kodayake sun kaffa hujjan hakan dacewa yasamu matsalane ak'wak'walwansa,

Har saida sukaga yafara warkewa suka sanar damu, tunda aka dawo dashi aka k'ira akan kazo kaga d'anka yana raye bai mutuba, baka samu zuwaba sai yau.


Cike da mamaki Mami ta kalli d'an'uwanta dan batasan dalilinsa na b'oyema Alhaji ya'u zancenba, a ganinta ko za'a b'oye ma wani shi bai cancaci a b'oye masaba.


Shikuwa tsaban Rud'anin da yashiga daga farko bai ji abunda akecewaba, sai kalman k'arshe yaji wato Karbi nada matsalan k'wak'walwa,

Ganin irin kallon dasuka shiga masane yasa yawayence cikin k'arfin Hali yafara fad'a ta inda yake shiga banan yake fitaba, ya tashi yana fad'in shikenan tunda kunnunamin niba kowabane awajen Kabir saidai kurik'e aranku ina da rana zaku nimeni komin jimawa, haka yafice ko gani baya yi da kyau, yana karad'e hanya ya isa Mota,


Kan Kabir nak'asa yanajin yanda Mami take complain d'in sam basu kyauta masa ba sosai suka fahimtar da ita cewa hakan duk a rarrashin kar yad'auka da zafi ne,


  Bayan sungama ne Mami tasanar dasu Waliman da take shirin shiryamasa in ya dawo daga tafiyansa,



 Da dare Kabir yana zaune afalon Mami suna Hira  Habib yashigo da sallama Mami ce ta amsa cikin fara'a tanamasa Sannu gefe ya zauna suka gaisa, ya kalli Kabir da idonsa yake kan T.v yace Wai kai har yanzu baka canzaba? Yanzu dirowana garinfa nazo dubaka kana wani shanmin k'amshi,


Kabir ya harareahi yana tab'e baki, "tom ni nak'ira kane? Kona ce kazo ka dubani?

 "kadai ji dashi gurgu kawai, yafad'a yana mai da dariyansa,  ya mik'e yana kallon Mami da take musu dariya,  "Mami yau me aka dafa agidannan? 

Kabir ya manna bayansa da jikin kujera yanata murmushi, ta wutsiyan ido Habib yake kallonshi yana cin abinci.


Ikon Allah ne kawai yakai Alhaji ya'u gida dan baimasan irin tuk'in da yakeyi ba,  ko gama perkin baiyiba ya bud'e murfin Motan ya fita   a fallo ya tarar da Matarshi tana ganinsa ta mik'e cikin damuwa take tambayansa,

Ko sauraranta baiyiba ya ciro waya bugu d'aya kila ya d'auka,

"Kai Kila nagaji da rainin Hankalin da kakemin dama baka kashe Kabir ba kacemin ka kasheshi?,

 "What? Meka ke nufi Alhaji?  Kodan baka gama bamu kud'inmu bane yasa kafito tanan?  Kamar yadda nagayamaka ai Kabir saidai uwarshi ta haifi wani, amma shikam yayi nisa,

Cikin zafi ya katseshi da kai kar kawomin maganan banza zanyi maganinka, daga Haka ya katse wayan, ya zube kan kujera,

Rabi ta k'araso tazauna gefensa tana tambayansa, nan ya gayamata komi,

Tad'an kalleshi to Alhaji ka kwantar da hankalinka mana kuyi magana na fahimta kai da Kilan wlh nikaina na matsu ayita ta k'are muci dukiya musha dukiya mu kwanta akan dukiya,


*Oh Allah Duniya budurwan Wawa Allah yasa mufi k'arfin zuk"atanmu*

Kar kugaji kubiyoni har yanzu ba afaraba,😂

*Ummu Fatima*

Comments /corection 👇🏻
 .08065091824.
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
  *Jinjina Gareku My Fans wlh inajin dad'in Addu'o'inku gareni ba kad'anba Allah yabarmu tare*

   *Don Allah inkuji wani kuskure kumin gyara k'ofa abud'e take zaman tare kenan in d'an'iwanka yai ba daidaiba ka guaramsa,  Nagode sosai,* 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 2⃣3⃣


   
             
  Dijah!  Wai gashi inji Baffa ki k'arasa shan maganinki,

Dijah da take kwance akan k'atuwar katifan da ta gada awajen Kb 😆 yitayi kaman batajiba, dataga Bintalo zata matsamata sai ta d'aga k'afanta kaman irin agigin Baccinnan ta d'oramata awuyanta,


Bintalo ta ture k'afan,  Dijah tasake d'agawa ta d'oramata akanta, 

Afusace ta saiti cinyanta ta d'akamta duka "iyi kinga kin fara farfafad'owa Rashin mutuncinki yafara dawowa aifa banmanta abun da kikamin d'azuba.

Azabure Dijah ta tashi tana sosa wajen, ta tak'ark'are ta k'walla uban k'ara,
"Wlh bazan yardaba sai na rama tana kuka takama Bintalo da kokuwa,

Nanfa kokuwa ya kaure, tun Bintalo tanabiyemata ta maida abun wasa har ta gaji tafara Bata hak'uri,

"Kiyi Hak'uri Dijah na kinga baki gama warkewaba, "Nidai sai na Rama ko kuma inje ince ma Baffah jiya naji kuna iskanci a waya keda yaya Sani.

"wai ke Dijah meyake damunkine?    Don kawai nace nima inasonshi shine iskancin?

"A'uzubillahi sake maimaitawa kikayi? 😳  narantse sai nafad'a tunma bakije birninba kin fara iskanci, ta fauce Hanunta acikin na Bintalo zata tafi Bintalo ta rik'ota kiyi Hak'uri Dijah ki rama dukan ince shikenan,  "nafasa Ramawa zanje kawai ingayama Inna kar akaiki Birni kije ki kwaso abun kunya.

Dariya Bintalo tayi sosai har tana sunkuyawa, kije kifad'a nima sai nafad'amata Hiran da naji kunayi keda Jebu jiya, daga Haka tafice tabarta agun.

Gyara kwanciya Dijah tayi akan katifa ta d'ora kanta akan pillow tana shak'an k'amshin turaren Kb dayazamo mata jiki, Don tun tafiyan su Kabir tamayar da d'akin wajen zamanta kwanane kawai batayi a wajen k'anshin turaren da yake fesawa har yanzu yana d'akin kaman yanzu ake fesawa itakuma a duniya k'amshin yana mata dad'i.


 Tun ana biki saura kwana Biyar Mami sukazo da kayan sayan baki dakuma d'inkunan da Amarya zata saka dasuran abun buk'ata kafin akaita, don dama Baffa yace a ajiye mata lefenta acan tunda nan za'a kawota.


Tun Randa Mami ta dirk'o take fafatawa da Baffa akan yabata Dijah sutafi fir yak'i amincewa.

Suna zaune da Dijah tana nunamata sakamakon Karatunta tafara wani tunani itadai tanason yarinyan aranta, tanason ta taimaka mata tasamu karatu mai inganci, "khadijah kinason kicigaba da karatunki?

 Dijah ta d'ago tana kallonta, tace "Eh inason incigaba Hajiya wlh inason in zamo mai aiki gidan T.v Mami tad'anyi Murmushi tace nifa Mamin kece ba Hajiyaba, kinji?

Ta gyd'a kai,
"Kinason intafi dake kije kiyi karatunki acan?

 Dijah tazaro ido "Eh inaso amma Baffana bazai yardaba, "Karkidamu nasan Hanyan dazanbi lnsha Allah zai yarda dake za'azo bikin Fatima kinji?

Kayan da tazomata dasu ta bata sannan ta nunamata yanda zatayi amafani da wasu.

Washi gari Mami da zata tafi tashiga wajen Baffa tajima kafin tafito jiki ba k'wari, Dijah tana ganin haka tasan Baffanta bai aminceba.

Ahaka tamusu sallama Har jikin mota suka rakata tafi.


  *Ranan Juma'a* shine Ranan da Baffa yasaka d'aurin auren Bintalo awannan Rana mutanen Rugan Juma sunga Abun Mamaki dayawa wasu kam sun sadauk'ar cewa Baffa yasayar da "yarsa mai Hankali yabar Mashiririciya agida sakamakon  Irin Motocin dasuka shigo garin wanda tsawon Rayuwansu da yawansu idonsu bai tab'a Ganinsuba, gasu fa tsaban yawa nanfa akafara gutsiri  tsoma hatta matan dasuke cikin Gida lbr yakaimusu haka wasu sukazo sunayima Bintalo kallon k'arshe kallon muhad'u a darussalam,  wasu  sai lbrai sukeyi wata wani yazo daga birni ya kashe kud'i mai yawa  ya aureta asai ba'asanta d'an yankan kaibane ana kaitan shikena haryau shekaru kaza ba lbr.

Ire2 labarun da akeyi kenan agidan bukin wannan tanagamawa wancan taba dana ta,  Inna kam yitayi kaman batasan me suke nufiba dondama tasan za'afad'i abunda yafi haka.


Hakadai har 'yan kai Amarya sukafara shiga motoci, nanma ba kowa bace tayarda tashiga don sunce basu shirya kai kayikansu ma 'yan Birniba.

Sai Daf Magriba suka isa Gidan Mami aka kaisu kai tsaye,  wani k'aton pat aka ajiye Amarya da Bak'inta, Hidiman da aka musu ba'a magana, Mami tana idar da Sallahn Magriba ta shiga pert d'in Bintalo tana ganinta ta lullub'e fiska dariya tayi tace kwantar da Hankalinki Amarya ba gunki nazoba nazo niman 'yatace, tazauna agefe suka gaisa da jama'a annantace musu Ina Khadijah? Can ta hangota suna zaune dasu Ma'u Taje ta kamo Hanunta suka fita, bata ajiyeta ko inaba sai part d'inta,

Wani d'aki dayake cikin Falon k'asa ta kaita da alamu kayan ciki basufi sati dasawaba komi sabone dal ad'akin abakin k'ayataccen gadon dayasha gyara ta zaunar da ita,

Ta jawo stool d'in Mirrow ta zauna tana fuskantan ta.

"Haba Khadijah uwata!! Kinzo konimana bakiba kinacan cikin 'yan'uwanki kin shareni nikuma inannan ina d'okin ganinki,

 Murmushi Dijah tayi tana bin d'akin da kallo zuciyanta sai Harbawa yakeyi da sauri2 Haka kawai yau kuma taji wani iri game da Mamin Anyah kuwa Maganan mutanen garinsu bazai tabbataba irin wannan Gida? Ashe haka suke rayuwa shine har suke iya zuwa Rugansu suna zama.

Gaskiya itama yaukam tana ganin sayar dasu za'ayi dukansu,

Mami ta kamo hanunta kaman tasan abun da take tunani tace "ki kwantar da Hankalinki Khadijah Bazamu tab'a cutar dakuba insha Allah.

 kusa aranku kowa da yanda Allah ya tsaramasa Rayuwansa wannan shine banbancinmu daku ba wani abuba, kinji ko? 

Dijah ta gyad'a kanta tana cigaba da kallon d'akin a tsorace Mami tace ina zuwa ta fita Dijah ta tashi tana k'are ma d'akin kallo ahankali tana taku, har ta iso gaban Mirrow ta lek'a azatonta taga fuskanta sai kawai taga wata matashiya atsaye ta hard'e Hanunta tana kallonta gefenta kuma watace atsaye amma bata ganin fuskanta, arazane tasa tafin hannayenta ta Rufe Fuskanta ta tsala ihu mai tsanani da sauri Mami da sauda sukayo kanta  Mami ta rik'ota "Khadijah menene?

"wayyo Allah na don Allah amaidani wajen Baffana wlh bazan sakeba Don Allah ku maidani,

"wai meye kimin bayanimana khadija??

Aljanu nagani acikin Madubi don Allah kukaini Baffa yamin Ruk'iya.


  Mami ta dad'a rik'e Hanunta "ba Aljanu kika ganiba Khadija mune,

"wlh banyardaba waima kud'in ta ina kuka shigo waiyo na shiga ukuna.

Duk maganan da takeyi idonta arufe takeyinsa cikin kuka,

Sauda ko me zatayi inba dariyaba,

Dak'yar Mami ta shawo kan Dijah har ta yarda ta bud'e idonta, "Munshigo munsamu kina kallon d'kinki Khadijah shiyasa muka tsaya muna kallonki, Mu kika gani a madubin ba Aljanuba kinga wannan tanumata Sauda ita kikagani a mdubin ko ba itaba?

"itace to amma ta ina kuka shigo?

"ta k'ofa muka shigo Khadijah ki kwantar da hanakalinki,

Nan d'akinkine ke kad'anki na kawomiki k'anwanki ta gwada miki yanda zakiyi wasu abubuwane, kallon sama da k'asa tayima Sauda sannan ta kalli Mami "Wannan gundu memiyance k'anwata? 

"Af Addanki ce na manta, Sauda ki nunamata yanda zatayi amfani da bayan gidan tayi wanka ga kayanta akan gado intafito tasa sai kuzo muci Abinci, daga Haka ta juya ta fita.

Sauda tana Murmushi tace  "zomuje Beutiful girl kina da kyau Amma don Allah karkisake yin irin wannan k'aran daga gani kinsaba da shine ko? Kanta ta girgiza har yanzu atsorace take cikin 'yan mintuna kad'an, sai ga Dijah ta koma Khadijah tare suka  fito suka tarar da Mami akan Dinining suna waya da Kabir,

*Kuyi hak'uri Fans bayawa wlh inacikin damuwa pls pray for me*  🙏🏼😭
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
  *yau filin nakune masoya*😍👇🏻
*My Hannah gaskiya inasonki ba  karya*😘
*My Aminiya (Khady pinky) Masoyiyar asali*
*My Hanun bra* *(Hassana dan larabawa)*
*Ayi fada ayi dadi kina burgeni sosai* 😜

*Aunty Xee*
*Mmn zee*
*Mmm Ikram*
*Mmn lman*
*Hauwa*
*Momyn sadiq*
*lndon Huguma* 😍😜😘🤝🏻
*Ummi Rabi'u*
*Inayinku sosai Gys Allah yabar k'auna*

*_JAMILA ABDUL'AZIZ NA UMMI & AYSHA GROUOP NIMA INAYINKI NAGODE SOSAI SIS ALLAH YABAR K'AUNA_*




*DON ALLAH 'YAN'UWA KUYI HAK'URI ANSAMU ERROW SOSAI A PAGE D'IN DAYA GABATA HAR AWAJEN NUMBERN PAGE ZANSA 2⃣4⃣ sai nasa* 2⃣5⃣

Afuwan yanzu  ga 25 d'in👇🏻

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 2⃣5⃣


   
             
  Juyawa tayi zata koma inda tafito har takai bakin k'ofa  taji ankamo Hijabinta,  ta juyo ta kalleshi bakaramin zabura tayiba  Don ita a garinsu aga namiji yamaka haka ai har a wak'a sai asaka,

Ganin yanayinta ne yasa yasaketa ya had'a hannayensa biyu yana kallonta Sory sister Sunana Auwal nine Class Rep. Naga abunda yafaru tsakaninki da Nancy bahaka yakamata tamikiba amatsayinki na New comer, kiyi Hak'uri barin had'aki da wata, da Hanu ya yafato wata 'yar matashiya dabazata wuceta da abun kirkiba, tana zuwa yace "Jamila ga k'awa kuzauna pls ki gwadamata inda aka mata nisa, kibata duk Assigment d'in da akabayar tayi sai kukawomin inmata submiting,  Asanyaye Dijah ta d'ago takalleshi, tace "Nagode,


Murmushi yayi Har wushiryansa ya Bayyana, ya lumshe Idonsa yabud'e ya kalleta, itama shagala tayi sosai da kallonsa, "Nima Nagode yafad'a yana fita daga Class d'in, 

Ta dawo da kallonta ga Jamila data Hard'e Hanunta tana kallonsu, Jamila tad'anmata Murmushi takama Hanunta muje ko,

Suna zama Jamila tace meye sunanki?

  "Khadija Abubakar"
"Ayyah Khadijah ba gulma ba amna kar kidinga shiga sabgan su Nancy wlh basu da Mutunci basu ganin kowa da gashi sabida tana Gadara Mamanta Malama ce yasa take Rashin kunyanta  yanda taga dama, shashashun k'awayenta suna maramata Baya,


Nan tadinga nunamata  Abunda akayi batanan,


Sai wajen Biyar Dijah tadawo Gida a mugun gajiye tashige Fallo a lokacin Nafisa tana zaune akan kujera tana canza tasha da remot, Kallo d'aya Dijah tamata, k'irjinta yabada Rasss, da bata san daliliba,

  Tana k'ok'arin shiga d'akinta taji motsin Mami akitchen tadawo da baya, tashiga kitchen d'in, lokacin Mami tana zuba Abinci a kula,


Tana ganinta tasaki fara'a  "a'a Student yanzu nake tunaninki araina kindawo?,

"Eh nadawo Mami sannu da aiki.

 Sannu Khadiija ya Karatun dai? Ince ba matsala?

"Ba komi ta fad'a tana d'aukan Kulan da tagama zuba Abincin aciki,


Mami tace "da kinbarshi Khadijah keda kika dawoyanzu,  kije ki Huta Zan kwashe,

Murmushi kawai Dijah tayi tacigaba da Kwashe Kayan Abincin,

Tsab tajere komi akan dining Sannan tashige d'akinta,

 wanka tayi ta sa dogon Riga mai guntun Hanu, ta haye gado takwanta kenan, K'iran Mami yashigo wayanta tana d'auka Mami tace "khadijah Kifito kici Abinci,

Zaune tasami Mamin da Nafisa suna Hira, da Alama wani magana sukeyi mai muhimmanci, don har da guntun Hawaye a idon Nafisa,

Ak'asa tazauna kusa da k'afan Mami,

Mami tadafa kanta "Khadijah kije kid'ibi Abinci kici, basai kinjiraniba, ni agida na wuni,


"Mami wannan yar waye? Nafisa ta tambaya tana yamutsa fuska,

"yatace,  Mami tabata Amsa agarce,

Sake yamutsa fuskanta tayi kaman taga kashi,  tace "Amma daga  K'auye aka kwota k0? 

Mami tad'an Rage fara'an dake Fuskanta, tace Eh ai tushenmu kenan Nafisa,

Shiru tayi don Rashin samun fuskan Mamin, Tana cigaba da bin Dijah da wani Kallo,

Mami takuma kallon Dijah, Khadijah tashi maza kid'ibo Abinci kici,


Mik'ewa tayi tanufi dining, Nafisa tace "kifara d'ibowa kikawomin kafin kid'ibo naki,


Har Mami zatayi magana sai kuma tayi wani tunani tayi shiru tana Nazartan Fuskan Dijah datake d'iban Abinci,


Tare ta d'ibo danata tazo ta'ajiye mata agabanta, tajuya danata zata wuce d'akinta, cike da Raini da wulak'anci Nafisa tace ke menace miki?


Bance miki sai kinkawo min nawaba?

Kafin kid'ibo naki angayamiki ni sa'arkice?  Dazaki d'ibo mana Atare?


"A'a Nafisa banson Haka bafa 'yar aiki bace ita,  kin aiketa amatsayinki na wanda kika girmeta, wannanbis ok,

 Amma ba huruminkibane kisata tafara kawo miki tukun, inhaka kikeso sai ki aiki su Indo,


Pls wannan k'anwarkice bani son wani Hayaniya,


Wannane k'anwata Mami?, wlh Allah ya kiyaye inhad'a..... Sai kuma tayi shiru tana huci, tana cigaba da zabga ma Dijahn Harara.


Mami takalli Dijah da Hawaye yacika mata ido taf, tace "ke wuce kiyi tafiyanki,

Sauri2 Gudu2 tashige d'akinta ta mai da k'ofan ta rufe,  atsakar d'aki ta dangwara Abincin tazauna ta jingina da gado ta d'ora kanta akan gwiwan k'afanta, tasaki kuka mai ciwo arayuwanta abu mafi tsana awajenta shine a wulak'anta ta, Wannan d'in wacece? Meye matsayinta agidan?


Itadai tun zuwanta tana ganinta agidan jifa2 sai dai har yau bata san matsayinta  agidanba,


Sannan duk lokacin da sukayi ido biyu da ita sai taji k'irjinta yabuga, kodon irin kallon da Nafisan take matane? Oho,


Yaune Rana ta farko da tafara kuka dan wani yamata wani abu,  Maganan da Goggiji take yawan fad'amata idan tayi tsokana tashigo aguje ya dinga mata yawo akanta, kewan Baffanta da Innanta yadawo mata sabo, Anya zan iya cigaba da zama agidannan wannan yarinyan tana wulak'antani? Ta Tambayi kanta tana k'ara rushewa da kuka,


Har akayi sallahn lsha'i Mami bataji d'uriyan Dijah ba don haka tana idar da shafa'inta ta shigo d'akin da sallamanta, akan sallaya ta tarar da ita,  kallo d'aya tamata ta gano irin Kukan da taci,


Shiru tayi tana kallonta sannan ta kalli Abincinta dayake tsakar d'aki,


Taso ta Rarrasheta sai kuma tayi Nazari, indai ta Rarresheta to  ba Gata tamataba, Lallai yazama Dolle ta ankarar da ita Halin Rayuwa,


Don ta lura Akwai sakalci da shagawab'a ajikinta,


Amatsayinta na 'yamace kuwa Sam baidace da itaba, ace komi aka mata zatashige d'aki tayi kuka, ita da zata zauna da Namiji,

Wanda mata suke masa kirari kala2,

Wanda yanzu zai saki dariya anjima kad'an yasaki kuka?


Sannan akance bashi da Tabbas, ma'ana ba lallai kurayu iya kedashiba watak'ila yace daku biyu ko uku ko hud'u yake son Rayuwa,


Kenan inhakane Ba kukane Mafitaba,


Tana tunani idonnta akan Dijah har ta idar da shafa'inta ta ninke sallahyan, kusa da Mamin tazo ta zauna tana k'ak'alo Murmushin k'arya afuskanta,


Murya adishe tace "Mami nazaci kinyi baccine,  Murmushi Mami tayi tana kallon idonta dasuka Kumbura suntum.


"kinzaci Nayi Barci Khadijah ko kuma fushin yashafeni?


Tad'an gyara zama, tace "wannan shine makaminki Khadijah?

Dahaka zaki ke k'watan Kanki?  Kuka shine Maganin matsalanki?


Gaskiya amatsayinki na Mace wacce zata zauna da wani da wata bai kamata ace kimai da Kuka maganin matsalankiba,


Nalura wannan shine karo na Biyu  kina Kuka ma Nafisa, indai hakane to lallai kitanadi Hawaye dan bakima faraba, Kenan kina da ma k'aton aiki agabanki.



Inkuma bahakaba yazama Dole ki koyi Hak'uri da Juriya,  sannan kizamo mai maida Ma Mutum Aniyansa, inharkin fahimci tamiki Abune don kiji Haushi to kinunamata dad'i  kika ji,  karkibari ta fahimci damuwanki ko kad'an,



Don Ko kishiyace kikaga tanason tozartaki  ba kuka, da yajin cin Abinci, ko fushi yakamata kiyiba kiyiba,


Allah yasa kin fahimci inda na Dosa Khadijah,

Tashi kid'auki Abibcinnan kifita dashi ki d'ibomana wani yunwa nakeji,


Kaman Kazan da k'wai ya fashewa Aciki ta nufi Dining,

Itadai sam bata Fahimci inda maganan Mamin  yadosaba, Meye had'n  Nafisa da wani maganan Aure?  Turo Bakinta tayi tana tuno wani hiran da taji matan Auren Ajinsu nayi, Afili tace nibazanma yi aureba har Abada,



Mahakurci mawadaci kubini ahankali zaku fahimci komi



Ummu fatima ce 😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
  *Masoya masu k'irana sumin Addu'a da masu min massage na gode sosai kuma Allah ya biya muku Buk'atunku na Alkhairi nagode sosai Ummu Fatima taku ce* 🤝🏻🤝🏻

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 2⃣5⃣


   
   Sauda ta jawo mata kujera ta zauna tafara saving nasu, sai da tagama zuba na kowa ta zauna dai2 lokacin Mami ta gama wayan ta kalli Dijah ta ke takure acikin kujera "Kici Abinci Khadijah,  nanfa gidankine kidaina d'ari2,


Haka suka ci Abinci Mami tana musu Hira jifa2 takansako Dijah aciki dak'yar tad'an saki  jikinta,


Rana  ta farko arayuwan Dijah data kwanta dasunan Barcin dare ad'aki ita d'aya  gaba d'aya jitayi d'akin yamata mugun girma Allah sarki Bintalona ta fad'a tana share guntun Hawayen da yagangaromata, juyi ta dinga yi ahaka har bacci yayi gaba da ita.


Washi gari akaci gaba da shagalin buki yayinda Mami tad'auko masu Gyaran Amarya nagaske  duk abunda akyi   wa Amarya Mami tasa anyima Dijah,

Kafin yamma inkinga Amarya da k'anwanta bazaki ganesuba gaba d'aya kamanninsu ya canza, aharaban Gidan aka gudanar da tsararren Walima daya d'ibi maza da Mata,

Angoda da Amarya sai Haska waje suke kaman wasu taurari, sai daf Magriba aka tashi,

Duk abunda akeyi Dijah tana takure akan kujera dama ita ba gwanan shiga taroba, gawani Kwalliya da akamata gaba d'aya tana jin fuskanta yamata nauyi, tun daga nisa tajiyo Muryan sani yana k'wala mata k'ira ta tashi ta isoshi sai Kallonta yakeyi yana murmushi "Khadijah kece haka gaba d'aya banganekiba? Murmushi kawai tayi tace " ya Sani kaima ka ganka kuwa da muryanka kawai naganeka,

 Kai da Bintalo sai kace ansakemu ku wani k'ira. Sani yad'an had'e rai "ke Daga yau nasoke wannan Sunan Aunty Fatima zaki dinga cewa ba Auntynki bace ba,

Dijah ta k'yalk'yale da Dariya "ok dariya ma nabaki? Insake jin sunan abakinki,




Zo muje kigaisa da su Hajiyata, yana tafe tana binshi abaya suka shiga pert d'i n da 'yan'uwansa suke, sosai Hajiya taja Dijah ajiki, tajima awurin suna Hira,

Harsaida Mami tanimeta.

Bayan Walima ba abunda aka kumayi awajen don Mami tace Albarka ake nima baza'ayi abunda yasab'a ma shari'a ba,

Sai washi gari aka kai Amarya gidanta tare da Rakiyan 'yan'uwata, Bakaramin kokari Mami tayiba

Wajen tsara gidan Amarya komi yaji saidai fatan Allah yaba da zaman lfy,

Washi garin kai Amarya ne 'yan'uwanta da 'yan'uwa Ango sukayi shirin komawa Garinsu, lokacin dasukazo tafiya and'an fafata da Dijah don tace sam Baffanta bai Amince ta zaunaba,

Harsai da Mami ta k'irashi awaya aka bata yace mata ta kwantar da Hankalinta zai zo ganin d'akin Amarya daganan sai su dawo tare  (kamar yanda yake a Al'adan garunsu bayan Amarya tacika Sati Bab🙏🏼😭
anta yakanje ganin d'aki,)

 Da kad'an kad'an Dijah tasaki jikinta da Mami sosai yanzu take jin dad'inzaman gidan haka tafannin abubuwa Sauda tana koyamata Sosai, tare suke shiga kicin da Mami suyi Abinci kasancewan dama Dijah bata da son jiki shiyasa ta dage kafin tacika wata uku ahanun Mami tuni ta goge ta iya abubuwa da dama, time to time takanbi Sauda suje gidansu nanma bak'aramin Experians take samuba,  Mahaifiyar sauda tana bata kulawa sosai don haka tazamo bata da matsala


  Dijah tana da wata Hud'u cif Mami tasamamata gurbiny karatu a Polytechnic,

Ita da kanta tad'auketa a mota takaita har cikin makaranta wajen Aminiyanta da take koyarwa a wajen takaita Malama Sadiya, a Office tasameta ta tareta da fara'a suka gaisa,

''yau wata Rana Hajiya Fati kece a Office d'ina?

Gaskiya baki da kirki gaba d'aya kingujeni,

Mami tayi dariya tace "yanzumma bahaka kawai nazoba nakawo miki Amanar 'yatace, gatanan tana nan Depertmen d'in Mass communication,

Malama Sadiya ta kalli inda Dijah take "Masha Allah Hajiya Fati 'yar waye?

"yatace pls don Allah inaso asamata Ido kinga Bak'uwace batasan kowaba kar abarta da k'awayen Banza,


"Ok bakomi akwai 'yata Nana zanhad'asu surik'a zama tare,

To nagode Mami ta fad'a tana mik'ewa dukansu tare suka fito suka tsaya ajikin Motan Mami,

Malama Sadiya tak'ira wayan 'yarta,  ba'a jimaba sai gata tazo wajen, kallo d'aya tayi ma Dijah tahau yatsina fuska saidai tagai da Mami cikin girmamawa,

Nan mahaifiyarta tagabatar mata da Dijah amatsayin Sabuwar k'awa sannan ta gargad'eta  da kar tabarta tayi k'awance da wasu shashashun k'awaye,


Mami tadafa kan Dijah tace "Khadijah kikula kinji? Kiyi abunda yakawoki, inkuntashi Driver zaizo ya d'aukeki akwai no. sa awayanki sai kik'irashi, cikin girmamawa tace mata "to"


Nana tana gaba Dijah tana baya ahaka suka isa ajin,

Nana tak'arasa wajen K'awayenta tad'an sukuya ta musu magana akunne gaba d'aya suka kwashe da dariya suna kallon Dijah suna nunata da yatsa,

Wani irin malolon bak'in cikine ya ziyarci Dijah.


*pls Karku manta dani cikin Addu'o'inku inkayi ma d'an'uwanka musulmi Addu'a mala'iku zasu maka kutaimaka 'yan'uwana* 


*Nagode Nagode Nagode*🙏🏼



Mmn temah 😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
  *Gaisuwa Gareki* *Maik'rago* 😍
*Maryam Tijjani*
*My Bysty Mmn Hydar*
*Mmn*✌🏻
*Balkisu* mai gadon Zinare🤓
*Kemxee* 😁😍😜

*Allah yabar k'auna*
*Hajara sarkin complain ai ban isa inyi tuya inmanta Albasba kema kina nand'ina* ❤

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 2⃣6⃣



Ab'angaren Nafisa kuwa, bayan Dijah ta shiga d'aki Mami ma ta haura Sama,

Afusace Nafisa ta tashi batare da taci Abuncinba, ko jakanta bata d'aukaba,  haka tafice batako bi takan Motan da yanzu ta matsa ma Dadynta yasayamataba, don batason Mamin ta fahimci tayi Fushi asiyasa take sonbinta,  okada ta hau ya sauk'eta har cikin Gidansu, ko kud'insa awajen mai Gadi yakarb'a dam batako bi takansaba tayi wucewanta,


 Afalo ta tarar da iyayen nata kowannesu yayi tagumi, kowa danashi damuwan jikin Mamanta tafad'a tasaki kuka mai tsanani.


Tunkafin su tambayeta cikin Kuka tafara magana.


"Mama banagaya mikiba wlh Mamin Kb ce tahana shi ya Aureni, Duk son da datake nunamin na k'aryane yanzu abu kad'an sai tanimi tab'atamin Rai nidai wlh inban Auri Kb ba Mutuwa zanyi zankashe kaina.


Afirgice dadynta ya taso yazo kusa da ita "a'a Nafisa kidaina wannan furuncin ke d'aya yanzu nake gani inji sanyi araina Anyi ma d'an'uwanki Asiri inaji ina gani yanzu yamin Nisa,



Kidaina furta zaki kashe kanki, Waye Kabir? Da Har zaki kashe kanki akansa,  Muddin yadawo k'asannan bashi da mata sai ke ninagayamiki wannan.


"gayamin me Maminsan tamiki yanzu? Mamanta ta tambayeta, cikin b'acin Rai.


K'arya da Gaskiya Nafisa tafad'amusu afusace Maman ta tashi tana surfa Bala'i "Barinje insameta,  lallai Fatima tasamu waje, Duk zuri'ansu bawanda zata kawo ya fiki gadara da wannan gidan keda Gidan Ubanki, shine har zata d'ora wata kucakan k'auye akanki dan samun wuri.


Yau za'ayita ta k'are Kabir kuwa kinma aureshi angama ko tak'i ko taso.


Tana yafa gyalenta zata fita Alhaji ya'u ya kamota, "Karkiyi haka Rabi kefa kika shirya komi ko kinmantane?


Kiyi Hak'uri har plan d'inmu yagama shiryuwa, k'iris yaragefa.


Wani Dogon tsaki taja tace "Wlh daka barni naje naci mutuncinta tukun, naga batasan kawaiciba.


Kunnenta ya matso yagaya mata magana, komawa tayi tazauna tana Murmushi tajawo Hanun Nafisa da ta baza ido da Kunne tana sauraransu.



"kiyi Hak'uri Nafisata kwana kad'an yarage Mafarkinki yazama Gaskiya zaki Mallaki Kabir yanda kikeso Kinji?


Ta gyd'a Kanta Alaman Eh sannan takalli Maman,  "Wlh Mama sai Naci Uban wannan yarinya "yar k'auyen tun Randa nafara ganinta naga tanamin Kallon Raini, Natsaneta Kuma wlh sai na gyaramata zama.


"Eh karkiyarda wata 'yark'auye takawomiki Raini, keda Gidanki, ayanzu kinmafi ita Fatiman Gadara da Gidan da kin Auri Kabir Magana ta k'are Gida yazamo Naki.


 Wani Murmushin Farin ciki tayi don Aduniya ba abunda kesata cikin farin ciki irin ace da ita Matar Kabir.

Dahaka ta tashi takoma dan dama da shirinyin kwanaki taje Gidan.




Sannu Ahankali Rayuwa take nisa ma Dijah.

Rayuwa takeyi cikin Aminci a gidan Mami dan ba k'aramin kulawa take samuba ta kowani  ab'angaren Mami tazamomata katanga sosai  Dijah ta Kile tawaye, ta ko'ina, ab'angaren karatuma sambata da matsala tanasamun kulawa tanan fanni awurin Jamila da Auwal dayagama macewa a Son Dijah tun yana  iya b'oyewa har yafito dashi fili itama tun tana sharewa Har tabada kai bori ya hau, ma'ana   yanzu acikin school  bawanda  bai san da soyayyan dake tsakaninsuba.

Yau Juma'a shine Ranan da suka kammala jarabawansu na karshen 1semester.


Ajere suka Jeru da Jamila suka fito bakin gate suna tafiya suna tad'awa d'an Gefe suka samu suka zauna, sai Ga Auwal, tunda Dijah tad'ago ta kalleshi yana mata Murmushi ta sunkuyar da Kanta, yad'an matso, yace "Aunty Jamila Don Allah kitaimaka min Khadijah tak'i ban Adress d'inta Har yanzu, gashi anyi Hutu yakamata ace na isa cikin Gida Ansan dani aiko?


Jamila tayi Dariya "Kar kadamu Auwal a duk lokacin daka shirya kazo zand'auke ka inkaika har Gidansu,

"Kai Jamila Amma wlh nagode sosai banda kamarki, Barinje ana jirana sai munyi waya daga Haka ya wuce,


Dai2 Lokacin driver yazo d'aukan Dijah,
Jamila tace "to Khadijah sai munzo Dijah tana dariya tace "Wlh Jami ni kunya nakeji to inyazo sai ince ma Mami Me?

"Anzo Hira wajenkiman ko kinfison sai ya turo yafara Zuwa?


"Zandai yi shawara pls karki wani kawoshi, zanyi magana da Sauda tukun.


"to sarkin kunya Inajiranki Dariya kawai tayi tashige Mota.



Tun shigowansu Dijah take bin Gidan da kallo  bak'aramin Gyara akayi ma Gidanba ad'an fitanta daga safiya zuwa yanzu har Anfente gidan tsaf ga gyaran Da 'akayiwa furanni abundai ba acewa komi.


Ak'ofar dazata shiga ciki tayi kicib'us da Nafisa, kallo d'aya zakamata ka fahimci tsantsan Farin cikin datakeciki,  ta gefe Dijah tarab'a zata wuce,  cikin zafi Ta fincikota tayi baya da ita,  tana zabga mata Harara,

"ke wai me kika takane?  Gidan na Ubanki ne? Dahar zakizo ki bugeni ki wuce?

Indan nace bazaki shigaba kin isa kishigane?

Taja dogon tsaki ta d'ora da Banza 'yar k'auye kawai, tajuya fuuu ta shige tabar Dijah awajen tayi sakare tana kallon Hanyan databi.


Kusan Minti biyu sannan tashige ciki,  kai tsaye d'akinta ta shige da Abu biyu aranta na farko abunda Nafisa tamata na biyu tana mamakin yanda Gidan yakoma hatta Falon ancanza masa komi.

Tashige d'akinta komi na d'akin ancanza zu yasha gyara komi fes2 sai k'amshine ke tashi ga Mamakinta har suturanta ancanza mata sabi tun daga English wears, Harsu Atamfofi.

Kan mirownta cike da kayan kwalliya iri2


Ta fito daga wanka kenan taji ana Nocking  ba k'ak'k'autawa, da sauri ta tashi tanufi k'ofan, ta bud'e.


Tsohuwace fara fat doguwa da ita kallo d'aya zaka mata kasan data zuba kyau da gayu alokacin K'uruciyanta,  wayayyiyace sosai da sosai Sannan Hutune ya ainihin b'oye shekarunta, don Azahiri ta manyanta da yawa.


Irin Kallon da Dijah take binta dashi ne yasa tsohuwa d'an had'e Fuska,  Tace "kebaki iya tarban bak'oba ko?


Ko dayake lefin Uwankince data Aiko batazo da kanta tace kije ki gaida Uwar gidankiba.


Barinje inturo miki ita.
Daga haka ta juya, Murmushi Dijah tayi sosai ta tuno mata da Goggoji.

Tana shirin Rufe k'ofan kenan Mami ta iso.

"Khadijah tund'azu naturo Nafisa tak'iraki Kizo ki gaida Iya bakizoba har tagaji ta biyo sawunki.

Kame2 Dijah tashigayi don ita ko idon Nafisa bata ganiba balle tace tazo.

"Maza shirya kizo Kugaisa, inajiranki anan to tace,

Sannan tajuyo tana dariya gami da d'an yarfe Hanu Mami Sabbin Kayan wadrop d'innan duk nawane?

"Eh Nakine Khadijah duka, wasuma suna Gun d'inki, cike da Murna tace Nagode Mami Allah yasaka da khairan.

Ameen Shiga kisako kayan kisameni ad'akin dake gefen nawannan, kar iya tayi Fushi Mahaifiyar Dadyn Kabir ne yau da safe tazo taryansa.

Af na manta bangayamikiba, Gobe insha Allah Kabir zai dawo zasu taso da Asuba.


Daga Haka Mami ta wuce tabarta tsaye awajen Kimanin Mintuna 2 Dijah tana tsaye a wajen tarasa mema zata Tuna dan ita azahirin Gaskiya ta Manta da Kabir.


Cikin mutuwan Jiki ta zira douwar Riga na Material fari mai Jajayen flawowi tayi Rollin da jan gyale, tafito Shar da ita Fuskanta ba Kwalliya ta nufi d'akin da Mami tagayamata.



 Tun shiganta iya take tamata tsiya kin wani saka jan mayafi sai tashin Tirare kikeyi ancemiki zaki tsoratanine?

Itadai Dijah Murmushi kawai takeyi suka gaisa nanfa Hira ya kaure dandai Iya badai Tad'iba kam, Gata da saurin sabo, da Mai da d'an wani nata, tana da dattako da kara, sosai Dijah taji dad'in Hiran nasu tasake da ita sosai tare sukaci Abinci.



Da dare yayima anan Dijah tace Mami tabarta su kwana.


Labarai kam Dijah tashasu duk yawancin Labarin na zaman takewanta da Mijintane,  Dijah kam daga baya lbrn kunya yake bata dan haka tayi bacci ba shiri.



Dukda dogon Hiran dasukayi bai Hana Iya tashin yin Nafilanta datasaba Na dareba,  har aka fara kiran sallah Asuba sannan tad'aga Dijah, tare sukayi Salatul fajri Wanda Manzon Allah (S A W) yace yafi Duniya da Abunda ke cikinta.


Bayan Sun ldar  sukayi karatun k'ur'ani tare.

Sosai Dijah tayi mamakin yanda tsohuwan take Fitar da Kartun k'ur'ani mai Girma.


Shida dai2 Dijah tafito gaida Mami bak'aramin Mamakin ganin Mamin a kitchen tayiba awannan lokacin.

Bayan tagaisheta tace "Mami Da Asubannan kika shiga kitchen?  Yaufa Asabat ne pls Mami kije ki huta.


Da Dariya Mami ta kalleta tana tuno complain d'in Kabir duk lokacin da yaganta da safe haka.


"yau Kabir zai dawo Khadijah shiyasa nashigo dakaina inshiryamasa Abinci yanzu haka yana jirgi.

 
Jinjina Kai Dijah tayi tana Mamakin irin wannan Soyyaya na d'a da uwa.

Tare sukayi komi suka gama, Dijah da Indo mai aiki suka shirya komi akan Daining, bata jira komiba ta wuce d'akinta tahaye gado dan tsaban bacci take ji taso tayi wanka amma ina Bacci yaci k'arfinta.



Wajajen Goma dai2 ta dinga jin hayaniya acikin bacci tashi tayi tazauna tana mutsikke  ldo, Sai da ldonta yad'an washe ta yaye labulen Windown tana lek'a inda taji Hayaniyan yafi yawa, jibga2 Motoci ta gani aharaban Gidan sai sceuirity dasuka kewaye wata mota guda d'aya,

 Cikin Isa yasako k'afansa yafito Fuskansa d'auke da Murmushi da Farin Ciki sai Hanu yake basu suna Gaisawa,

 bata iya Hangoshi gaba d'aya Amma tayi Mamakin yanda yakoma.


Wucewa Gaba yayi Rataye da suit d'insa awuyansa, nan suka Rufa masa Baya, sauri yakeyi kaman zai tsaga k'asa Burinsa kawai yaganshi agaban Maminsa, ldonsa suga Mami ji yake kaman ya shekara goma baigantaba.



*Ummu fatima* 😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     
*Fatan Alkhairi gareku Manyan mata*
*Maryam Ahmad paki*
*Fauxia m Bala*
*Ummu Nabil*
*mrs Makama*
*Mrs Mansur*
*Jidder*
*Aysha Bagudo*
*Maimuna matan Abdoulaye*
*Munira*
*Officail sa'adatu Alk'ali*
*Aysha Machika*
*Aunty Fauza*
*Matar tsoho*👴🏽 *yar Mutan kagara*

*Allah yak'ara muku Basira da Hazak'a* 🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼


*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
 
🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 2⃣7⃣


   
             
  Dai2 k'ofan shiga Falon Mami seceurityn suka tsaya, shi da Sani ne wanda yake rik'e da Breaf case d'insa suka k'arasa ciki  a lokacin Mami tana zaune akan Sofa cikin koriyar atamfan Super Englsh Riga da zani, sai Murmushi takeyi tana Raba ido ta ina zata fara ganin Tilon d'an nata?


Zuba masa ido tayi bako k'iftawa Kabir!! Ta fad'a cike da Mamaki D'aya biyu uku ta fara k'irge da yatsunta azuciyanta, wai tanason ta tuno watanni nawane Rabonsa da ita? Da har ya canza irin haka, fatarsa ta murje tayi wani Haske na daban yad'an yi cika kad'an gashin jikinsa ya manne akan fatansa kaman irin larabawan Kuwait d'innan.



 Agabanta ya durk'usa ya d'ora kansa akan gwiwan k'afanta yana Murza goshinsa akan k'afanta, yanajin wani irin so da k'aunan Mahaifiyartasa, Duk irin boren da Mami taso tamasa na jimawan da yayi bayan bai gayamataba kafin yatafi duk yakawu,

Farin cikin Ganinsa yamantar da ita komi, 


Ta dinga shafa kansa tana Murmushi tsawon lokaci suna ahaka kafin yad'ago yana kallonta, ahankali ya furta "Mami!!.

Saikuma yasaki murmushi ya zauna dirshan kaman k'aramin yaro agabanta, Mamina Nayi missin naki.


"Nima Haka my lovley Son, daga wata uku saigaka kanason zarta wata shida Kabir?


Sunkuyar da kansa k'asa yayi yana Murmushi "kiyi Hak'uri My Mum wlh badaganibane.


"To shikenan ai tunda gaka Allah yadawomin da kai lfy Alhamdulillah Allah ya Albarkaci abunda da kasamu acan.


"Ameeen Mami na"

Sai alokacin Mami tad'ago ta kalli Sani da yake ta kallonsu yana Murmushi,  Gaisheta yayi Ta Amsa cikin kulawa, 

"Ya Fatima tana nan lfy? Mun kasa zuwa muga Gidan naku.

Kodayake ku kuka Hanamu zuwa sabida yawan sintirinku bakwa sati baka kawotaba,  Amma ikon Allah so d'aya suka had'u da "yar'uwanta, duk zuwanta tana Makaranta,


Amma yanzu sun samu Hutu Insha Allah zankawota tamuku ini,

Yauwa ni yabatun karatuntane kullum Inason tambayanka sai inmanta yakamata kamaidata makaranta taci gaba da karatunta.

Sani yad'anshafi kansa "Eh dama wai Nursing school takeso, to kinsan yanayin makarantan bamusamu Form di'nbama to amma tunda Allah yadawo da oga zamu samu yanzu.


"Assha meyasa baka gayaminba ai dana samomuku tuntuni, Shikenannan yanzu kam tunda gashi aiko ba Admission za'asata a Aji, Nigeria kenan tafad'a tana dariya.

Kabir yad'an had'e Gira yana kallon Sani

"Malam tashi kafita kajirani awaje ina fitowa.

"Kabir yazaka koremin d'a?  Bayan katafi Kabarni shida Habibne suke d'ebeminn kewanka, kullum suna tare dani.

"Shiyasama nace yafitan Mami Kusan kodayaushe inmuna waya yakancemin gashi Agidanki.


Yanzukuma yawani zo yasaki agaba da maganan matansa shi Adole ga mai Mata, Ni ansani agefe.


Sani yana dariya ya suri breaf case d'in yakalleshi "To inmutum yaji Haushi shima yayi matanmana.

"Gayamasa dai Sani Ga Amininsa Habib dai za'amasa Auren Dole wata mai kamawa.

Da Harar Kb ya raka Sani dayaketa Dariyan Maganan Mamin, har ya b'ace ma ganinsa,  sannan yadawo da kallonsa ga Mami.

 Dai2 lokacin Nafisa tafito daga d'akinta cikin Riga da sket English wears maijikin Roba ya matseta cif ajikinta tasha kwalliya kam afuskanta kamar Aljanna turare sai tashi yakeyi ajikinta kaman acampaninsa take.

Kallo d'aya Ya mata yad'auke kansa aransa yana tir da wannan shiga hak'ik'a yadawoda niyan Auren Nafisa don cika Burin mahaifiyansa, Amma sai ya d'auki Mataki akanta don yalura yanzu d'abi'unta suncanza, yanasane da Randa zai bar gari ahanyarsa ta zuwa air port yaganta amotan saurayi.

Cikin shock naganin yanda Kabir yadawo tak'araso zata fad'a jikinsa, Da dabara yad'anyi Zillo yakoma gefe ta fad'a jikin Mami mik'ewa yayi Hanunsa zube cikin Aljihun wandonsa yana d'an Murmushi  "waike bakya Girmane? Nafisa kodayaushe Halinki irin nayara, ai yanzu kinwuce min Irin wannan oyoyo d'in.


Turo baki tayi ta kalli Mami, "Mami kinji irin Abundayake fad'ako?

Mami da Gaba d'aya kunyan furuncin Kabir yagama kamata Dariya tayi tana Kallonta Talura ita ko ajikinta bata ma Fahimci abunda yake nufiba.


"Rabu dashi danma yaga an damu dashine.


D'an tattaki kad'an yayi acikin Falon yanabin ko ina da Kallo yace "Mami Falonnan yayi kyau saidai kujerun Daining d'innan sunyi k'anana,

Tasowa Mami tayi tana kallon kujerun "kaidai kafi son Manyan Kujerune irin na pert d'inka amman wa innanma  Sunyi Kabir,  Kansa ya gyad'a zai sake magana.


Ta katseshi da kashiga kagaida Iya tukun sai kazo muci Abinci,

Murmushi yayi cikin jin dad'in tunamasa datayi  tsohuwa Iya tana gidan,


"Barinje inwatsa Ruwa Mami kafin inzo kinsan Iya da surutu, yanzu sai ta rik'eni anan har dare banyi komiba.

"To kadai Hanzarta kar tayi fad'a dan tuntuni take tambayan ka.



Fitowan Dijah daga Wanka kenan, taji wayanta na Ruri ta d'auka tanasawa akunnenta baiko jira jin Sallamantaba yace "Ina waje inajiranki 'yanmata,

 ajiye wayan tayi a fili tace yaya Sani kenan, sai kuma ta jinjina kai tana tunani wai ace suna Gari d'aya da Bintalo Amma su d'auki wannan lokaci basu ga junaba, tanason tace ma Mami zataje saidai batasan yadda Mamin zata Fahimci zancenba, shiyasa tayi shiru da bakinta.


Doguwar Rigan Atamfa tasaka blue mai had'e da bak'i da pink, Fuskanta ba kwalliya kasancewanta ba ma'abociya Kwalliya ba, Pawder ne kawai sai Lip glow da tashafa, ta d'auki bak'in mayafi mai stones Golden ajiki plat takalmi tasa bak'i tafito Hanunta Rik'e da wayanta tana tafiya kamar bazata taka k'asaba, ahankali tana dube2 ta inda zata ga Sani.


Yayi dai2 da Fitowan Kabir daga Falon Mami da niyan watsa Ruwa, ahankali idonsa ya sauk'a abayanta, Zuba ma Bayanta ido yayi cikin Rashin Sani yake k'arameta kallo karo na farko arayuwansa dayasa mace agabansa yaji yana sha'awan ta juyo ya kalleta, wa iyazubillah ya furta ahankali yana gargad'i ma zuciyansa, to idan matan Aure ce fa?  Ai Hak'k'in zai maka yawa, wata zuciyan tagayamasa, Amma haryanzu yakasa d'auke Idonsa ba Abinma dayafi jan Hankalinsa irin tafiyan da takeyi.


Addababben k'amshin turaren dayak'i fita ahancintane tsawan lokaci tana mafarkin wannan turare shine ya ziyarci hancinta azahira, ahanakli ta juyo Bayanta, cikin sauri ya sunkuyar da Kansa, dan inyabari taga yana Kallonta yaci baya aganinsa koma wacece ita tayi kad'an yasaci Kallonta.



Itakuwa tana sauk'e idonta akan Fuskansa wani Jiri yaziyarceta dan Haka dasauri ta matsa ahanya cikin d'aukewan Numfashi tabashi Wuri.

 shikuwa cikin zafin Nama ya wuceta batare da yako sake Kallon inda takeba, aganinshi wanda yayi d'azunma kuskure ne da sharrin Shed'an.


Binbayansa tayi da kallo zuciyanta sai harbawa yakeyi da sauri da sauri, har ya bud'e pert d'inshi ya shiga, yab'ace ma ganinta, tad'an jingina da wani Pilah awajen tana mai da Numfashi, 


Sani ta hango ya bibayansa jimawa kad'an kuma ya fito dama shikam yaganta tun fitowanta, Gunta yak'araso kai tsaye,



Yadai Khadijah? Badai Bacci kk jiba dan tun zuwana nake tambayan Mami take cemin kina Bacci,



"Ba Bacci nakejiba to yana ganki haka? Ko jikin ne?

Ta sauk'e ajiyan zuciya,

"Nothing ya Bintalo? Bayan Hanunsa ya juya zai Buge bakinta ta zille tana Dariya,  "Duka kuma yaya Sani?

"Iyi tunda Kunnenki bayajin Magana ai sai jikinki yagayamiki, sonawa na hanaki fad'an wannan Sunan?

"Oh sory Wlh mantawa nakeyi ya Aunty Binta?

"lfynta k'alau tana nan kullum sai tayi jajanki,

"Ayyah duk zuwanta bama had'uwa, yanzu ai Munyi Hutu zanzo muku kwana,

Kwana? Yafad'a yana zaro ido

"ke wayace miki ana kwana agidan Amare?

Bamu gayyacekiba, ininma dai kar muk'ine ace muna da bak'in Hali, 

Dariya kawai tayi dan sam ba ta fahimci zancenba,

Dai2 lokacin Nafisa tafito k'amshin tirarentane yafara musu sallama kafin ta iso wani wulak'ancaccen kallo tabisu dashi, kafin ta wuce. Da ido Dijah ta Rakata.


Sashin Kb ta bud'e tashiga, Dijah ta tab'e baki ta kalli Sani shima Hanyan da Nafisan ta wuce yake kallo,


" Waini wannan wacece agidannan?

Sani yana Dariya yace "Gaskiya Kafin kayi fad'a da mutum kasan shi waye tukun, kinyi Tambaya me kyau.

Tahad'e Fuska ninace maka fad'a zanyi da ita?

"No tunda dai kinyi Tambaya kitsaya abaki Amsa

"Inajinka
"yauwa ita dai wannan d'in Sunanta Nafisa,

"Eh inaji ana fad'a

"yauwa 'yar k'anin Mahaifin Kb ne kuma mai niman  Aurensa,


Zaro Ido Dijah tayi sosai tana kallonsa bako k'yaftawa, har ya sunkuyar da kai yad'ago tana cigaba da Kallon fuskansa.

"Yadai ko kina cikine?

Turo baki tayi kaman mai shirin yin kuka, tace "Allah yasauwak'e magananne dai yamin wani iri dama mace tana niman aure?

"Eh gashi kuma kingani,

"Kana nufin kacemin dama abinda yake kawota gidannan kennan?

"Iyi tsawon Lokaci tana binshi ya aureta yak'i Amma yanzu ya Amince zai Aureta, Nan yabata lbrn tun farko har zuwa yanzu.

Zuba ma k'ofan Ido Dijah tayi cike da Mamaki mai kashe jiki,

sai surutu Sani yake mata Amma bata fahimtan Komi, ta k'urama k'ofan Ido kaman maison Gano wani Abun.
Aranta kuwa ji take ta tsani Nafisan dama duk wata Mace mai Hali irin nata ita kam tanaga ci bayane Mace tabari Namiji ya fahimci wai tana sonsa. "mtssstt taja dogon tsaki.

Ganin bata cikin Nitsuwantane yasa ya sallameta ya tafi,

Tsawon Lokaci tana tsaye awajen tana abu d'aya.

 cikin Rashin K'arfin gwiwa ta shige ciki d'akin Iya tashiga.

Alokacin iya tana Rik'e da k'ur'ani da k'aton Glass a idonta wanda yake k'aramata karfin ganin Rubutu daga dukkan Alamu ta idar da Sallahn Walhane, kan Gadonta ta haye jifa2 Kuma tana lek'a d'akin ta Window ko zataga Nafisan tafito amma shiru.

Aranta kuwa tuni tabasu wani matsayi na daban dan haka ta tashi zaune  tana lek'e tana d'an mita aranta,  guntun tsaki taja batare datasan  yafitoba tace "Ashema 'yar lskace kike yi ma mutane kallon banza.

Tana shirin sake labulen kenan ta hangosu sunfito ajere, kowannensu Fuskansa d'auke da Murmushi, Nafisa tana magana shikuma gogan Murmushin kawai yakeyi kansa ak'asa da Alama ma Wanka yayi yana sanye da Jallabiya cottin mai guntu Hanu Ruwan k'asa kansa sai k'yalli yakeyi wani.

 Dogon tsaki taja ta sake labulen ta koma ta kwanta.

Tana kallon slim taji sallamansu da sauri ta gyara rufan gyalenta ta juya musu baya.


*Ummu Fatima* 🤝🏻😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
  *Jinjina Gareku da fatan Alkhairi*👍🏻🤲🏻

*Halima Mk*
*Nasiba Gawo*
*Ummi ontop*
*Hadiza isyaku*
*miss Ayyush*
*Maman Aysha*
*Nafisa*
*Allah yak'ara Basira da d'aukaka* 🙏🏼

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 2⃣8⃣


    Fuskanshi d'auke da Murmushi mai cike da Farin ciki ya zauna agaban lya yana Fuskantan ta.


Rufe k'ur'anin tayi ta ajiye a gefe gami da zare Glass d'in Idonta tana kallonshi,  Tana Murmshin farin ciki.

Photon d'anta ne yadawomata sak Kabir yake kama da Mahaifinsa,

"Tsohuwa Irin wannan kallonfa?

Ko kinzaci Malam ne yadawo,

"Kai kama isa ka kamo k'afan Malam, wayacemaka kallon ka nakeyi? 

"OK to barin koma Inda na fito yafad'a yana k'ok'arin tashi.


Caraf lya takamo k'afansa tana Dariya "Yi Hak'uri Mai Gidana na Kaina,  ai Yanzu Kaine sanyin Ido na  Muhammad Khabir kai ka maye Gurbin Mahaifinka aguna ka maye Gurbin kakan ka Malam.

Muhammadu Kabiru Muhammadu mai suna dayawa, Muhammdu sunanka yafi K'arfin Arne,

Barka da Gani na Barka da Nasara Kabir, ta'ajiye Maganan a Raunane.


Murmushi Kabir yake tayi, cikin Tausayin Kakartasahi, ya kamo Hanunta irin wannan kirari Haka Iya Tukuicinki Umra Insha Allah dake zamu Umrannan,


"Kai nasamu Tukuici Mafi Girma Allah yayimaka Albarka yabaka mace tagari da zuri'a mai Albarka,


Nafisa maza k'iramin Uwanku inmata Albishir wannan Abun farinciki, kwanan nadawo gashi zankuma komawa tafad'a tana sharan k'walla, tana Kallon Nafisa da take d'an shan K'amshi.

"Gani nanma iya tun daga kitchen nake jiyo Addu'an ki meke Faruwa ne?


Kedai zauna kiji Fatima Kabiru zai mai dani Umra,

Mami ta zauna tana Dariya "ai wannan Dolensane ma Iya tun ba yauba yake saki ki taho wai kinzo tarbansa sai kizo yak'i dawowa.


Kabir ya gyara zama yana kallon Mami  yace "to Mami wai me takeyi a Maiduguri? Wlh ni sonake ta dawo nan muzauna, nasha k'iranta awaya ina rok'onta tsohuwannan fir tak'i pls Mami kisa baki yak'arsa maganan da sigan rok'o.


Tun kafin Mami tayi magana lya tace "ai nagayamaka kabari sai kayi aure tukun sai inkoma gidanka na lna d'an d'ebe ma matarka kewa,

"Ok shikenan Yanzu sai bazaki komaba sai kijira in nayi Auren sai mukoma Gidan gaba d'aya.

"To yaushene Auren naka?

Ya sunkuyar da kai yana susa k'eya "ki Tambayi Mami Itace zatamin auren.

"lya Rabu dashi kawai Wai yana ba'a ne Amma ba'ansa zai tabbata Very soon.

Shida Abokinsa sunkasa tsayar da hankalinsu sufitar da mata suyi aure, shi abokin yanzu Auren Dole za'amasa kwanan nan.

Iya tace shima ai dakunbi nawa tuntuni da hakan kukamasa,  Amma yanzuma bata b'aciba sai ahad'a dana Habibun kawai.


"Yauwa lya hakanma za'ayi indai yana son ki dawon, Mami tafad'a atak'aice. Nan suka fara magana akan maganan Auren nasa.

Kabir dai kansa yana sunkuye yana Duba massages d'insa na email.


Sallahn Azahar da aka k'irane yad'aga shi yatafi Masallaci.


Bashi ya dawoba sai da aka idar da sallahn lsha'i  yana can yana fama da jama'a kala2 wayan Da Mami take tamasane yasa yashigo, shi da Habib, Dr Na'im da Sani, Mami tanazaune akan kujera.


Yana shigowa baiyarda sun had'a ido da Mamin ba, kai tsaye ya wuce Daining don yasan k'iran kenan.


Sune suka k'arasa suka gaidata sannan suka Haye Dainingd'in.



Kwanan Kabir Uku da dawowa, Dijah bata tab'a yarda sun zauna inuwa d'ayaba, duk yanda Mami taso sudinga cin Abinci a tare ta ware Kanta Dan Haka kawai take jin wani Haushinsu shi da Nafisa.


Ahankali ta lura Nafisa irin Matannane marasa kamun kai, la'akari datayi da irin Mannemasa da takeyi gashi Sam batasan girmama Nagaba da itaba,

Don Ko zuwa gaida lya batayi inka ganta ad'akin lya to tabi KB ne, Itama lyan tunda ta lura da halinta ta d'ibeta tawatsar acewanta Barewa batayi gudu d'anta yayi Rarrafeba.


Ko yauma tana Hango Su daga kitchen tana aiki Suna karyawa k'ok'arin bashi Abincin Abaki takeyi shikuma yana kaucewa,  k'asa2 yake kallon Mami datayi kamar batasan da wanzuwansu agunba,

Ak'asan Ranta kuwa mamakin Halin da Nafisan ta koyo takeyi dondai tuntuni tasan irin son datakeyi ma Kabir amman dai bai Rufemata ldo har hakaba,


Gudu2 Kabir ya kamalla ya mik'e Dan so yake Yau ya lek'a wajen aiki,

"Mami Barin je
"To Allah ya kare
Nafisa ta tashi Itama tanayi ma Mami sallama wai zata gidansu sai da yamma tadawo.


"Khadijah! Mami ta  Rafka mata k'ira,

Daga kitchen d'in ta fito tana Amsawa,
"Gani Mami,

Mami ta jefeta da Harara, ai sai kizo ki karya tunda Dodon naki ya fita.


Tad'an marairaice Fuska "Mami fa na k'oshine,

"OK munfara sa'insane bansani ba?


Jawo kujera tayi ta zauna ta d'ibi chiefs ta fara ci, Mami ta kalleta "Wai Meye tsakaninki da Kabir ne? Tunda yadawo naga kincanza kullum kina kitchen dakinga zamu ci Abinci sai ki tsiri wani aikin?


Turo Bakinta tayi tana yatsina Fuska "Mami wlh ni haka kawai na tsani 'yan iska, shiyasa bani son ganinsa shida wannan 'Yar Rainin Hankalin.

Zaro ido Mami tayi gami da rik'e Hab'a, 'yan iskafa kikace Khadijah iskancin me sukeyi?

Had'iye dankalin Bakinta tayi ta kurb'i Tea tana kallon Mami alamun zatayi Magana mai muhimmanci.

"Wlh Mami lskanci sukeyi baki Gani Harda ido sunayi, inayawan lek'asu ta Window Har maganan lskanci Sunayi Rananma inaji tanace masa wai kowani Numfashinta da sonsa takeyi shikuma yace mata wai Shi har Mafarkin Ranan aurensu yayi yana ta d'oki har antaru za ad'aura sai kuma aka fasa aka aura masa wata yarinyan da bai santaba.
Kinsan meye Mami?

Mami da har yanzu take Rik'e da Hab'a ta Girgiza kai.

Dijah tahad'iye yawu cike da takaici alamun Abun yabata Haushi sosai tace "Sokuwar kawai sai ta fashe da kuka takama Sambatu, Dijah ta mak'ale Murya ta dafe kanta tana koyon yanda taga Nafisan tayi, cikin Muryan Kuka "waiyo My Luve banji dad'in wannan mafarkin nakaba, Wlh da zai tabatta kowacece sai naga k'arshenta ina mai tabattarmaka zan iya kashe koma yar uban waye, duk wanda Ubanta yayi sakacin aura mata kai wlh yayi ban kwana da 'yarsa sai alahira su had'u  dansai naga Bayanta,

Kawai sai yaciro Hankaceif ya mik'amata, cikin muryan 'yan iska yake mata magana nidai banjiba, daga nan na sauk'a agun Nabarsu,

"Oh! Ni Fatima Khadijah har Akwai wani Muryan 'yan lskane?

"Eh Akwai Mami dandai ban iya bane danamiki kinji, insun sakeyi zan koya sai inzo inmiki, Shinema yake yawanyin irin Muryan.

Kuma Rananma Naganasu a k'ofan pert d'insa sunason suyi irin lskancin Abunda su Salame sukeyi a garinmu ita da Mijinta, saura k'iris suyi sai yamatsa basuyiba,


"Mami datayi mutuwar zaune tace yayane lskancin gwadamin ingani,

Sunkuyar da kanta k'asa tayi tana jin kunyan fad'a sai kuma ta tuna dama tanason Tona musu asiri, ldonta arufe ta  Rungumo hanunta ak'irjinta tace Haka,


Mami tajinjina kai Aranta tana tunanin yaranta irin na Dijah tayi tunanin yanzu tadaina ashe dai baizobane kawai,


"Wai Runguman juna kikaga sunyi?
 
"Eh amma dai ya matsa da Baya basuyiba amma wlh sauran kad'an suyi, Inagama Hala suntab'ayi.


Mami tasauk'e ajiyan zuciya "kibarsu zanyi maganinsu

Aure za'a musu kwanan nan,


"Ko anmusu auren ma, lskancinsu zasu cigaba dayi Mami,

Wlh sam Nafisannan bata da Kunya, Tafad'a tana d'aure Fuska.

"Hakane Amma dai kidinga Amfani da abunda ldonki yagani, Zargi ba kyau Khadijah,

Kidaina Zarginsa Sannan kidinga Gaisheshi, kina girmamashi, yanada matsayi Mai Girma awajenki,

Tayatsina Fuska tace "awajena kuma Mami?

Awajen Nafisa dai,  Ni wlh banison gaisheshi, Nafasan Likita yanada jinkai da Kallon Banza.

Mami tad'anyi Murmushi "To ai Umurnina zakibi Khadijah, Ba Halinsaba.

Zata kuma magana Mamin takatseta

"Gama karyawanki Khadijah kije yau ke zaki mana Abincin Rana,


"Mami inason lnje Gidan Uncle kwana biyu Sauda batazoba,

"To jeki in kingama sai kije Amma ba kwana zakiyiba,

Ad'okance ta tashi tashiga kitchen.

Sai Misalin 1:00 tagama ta shirya komi a daining tashiga wanka tana fitowa tayi sallah Doguwar Rigan Shadda dark pink tasa wanda yasha aiki da bluen zare tayi Roling da bluen mayafi fuskanta bawani kwalliya mai yawa daga pawder sai kwalli da tazizara a idonta sai pink Jambaki da tasa, ta saka falat shoe blue da jakansa sai ta manne idonta da glass mai farin kwalba hanunsa pink agogonta ma fatansa pink, Best Colournta kenan.

 Ita kanta sake baki tayi tana kallon kanta a madubi don sam batasan tana da kyau Hakaba,  turare ta fesa mai Sanyin k'amshi ta d'auki wayanta tafito.


Yayi dai2 da Shigowan Kabir  Caraf idonsa ya sauk'a akan Dijah da sauri yad'auke ldonsa ya nufi gun Mami da take kan daining tana jiran fitowan Dijah,  komawa d'aki  tayi kaman mai niman wani abun can kuma ta fito ta matso Mami ahankali tace "Natafi,

Mami tajawo Kujeran da yake kusa da Kabir ta turamata,
"Zauna kici Abinci tukun inba hakaba kifasa fitan,

Badon tasoba ta d'auki plate tad'iba ta tsiyayi Juice tafara tsakuran Abincin,

Cikin Mutuwan jiki Kabir yake cin Abincin yana satan kallon yatsunta da suka sha lalle sunyi jaa mai kyau,  aransa yana son Sanin wai wannan d'in Wacece? Atunaninsa lya ce tazo da ita, can dai zuciyansa ta kwab'eshi, dan haka yanitsu yamaida Hankalisa ga Abincinsa,  wayarsa tafara Ruri.

 *My Lovely wife* sunanda yabayyana akan screen d'inkenan, Dijah data d'auki cup d'in Juice zata kai bakinta ta d'an lek'a Wayan, dai2 lokacinkuma takafa cup d'in abakinta,  Wani irin tarine yasark'eta Juice d'in data kurb'a ya watsu aka fad'an sa Na Hanunta da yake B'ari kuma yazube masa  ahanun Riga, ad'an zafafe ya d'ago ya sauk'e Idonsa akan fuskanta.

Cak ldonsa yatsaya akan Fuskan ta.



*Ummu Fatima* 😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

  *YAU (24/4/2018) AYAU NE FATIMA TA TACIKA  SHEKARA GUDA DA RASUWA,*
😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭

*FATIMA TA YI DOGON JINYAN CIWON ZUCIYA NA TSAWON SHEKARA GUDA KAFIN ALLAH DAYAFINI SONTA YA KARB'I KAYANSA*😭

*FATIMATA 'YA MACE K'WAYA D'AYA DA ALLAH YABAMU KUMA YA JARRABEMU DA SOYAYYARTA DA KUMA LALURANTA DA KUMA ZAFIN RABUWA DA ITA SHEKARA GUDA KENAN AMMA ADUK LOKACIN DANA TUNA SAI ABIMYAZAMO TAMKAR YANZU YA FARU*😭😭

_ina masoyan Ummu Fatim ina baran Addu'anku Allah yabani lkon cin wannan jarabawa Allaj yayi ma Fatima Rahma yasadamu da lta agidan Aljannah_

_nayi anfani da wannan dama na saudauk'atr da wannan page ma duk wata mai suna *FATIMA* BABBA KO YARINYA_

_INA FATIMOMI NA NA GROUPS MASU K'IRANA DA MOMINSU NASADAUKAR DA WANNAN PAGE GABAD'AYANSA GAREKU KUYIMA TAKWARANKU ADDU'AH_
😭😭😭😭😭😭

*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
 

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 2⃣9⃣


   
     Ji yayi kaman Mafarki yakeyi, Tabbas saboda tsaban iya shegen da yarinyan tayi tamasa lokacin da yake Gidansu, shiyasa yake yawan Mafarkinta abacci, Amma ba a irin haka yake  ganintaba, Sannan Bai tab'a Ganinta a ldo biyu ba saidai yayi tunaninta aransa,


Kau da kansa yayi gefe ya kalli Mami da ta kafeshi da ldo, sai kuma yaasunkuyar da kansa yanajin yanda tarinta yake k'aruwa,

Nan wayan tasake d'aukan Ruri, juya wayan a hanunsa yashigayi Mamaki Biyu a zuciyansa na farko, Khadijah yaushe tazo gidansu? Meyakawota?

Ad'ayan b'angaren kuma yana Al'ajabin Sunan daya fito akan wayansa asaninsa bawata mace datasamu wannan matsayin awurinsa,  yaushe aka samasa Sunan?

Sory! Sory!! Sory Khadijah Kalman da Mami take fad'ane yadawo dashi gurin,

Sake Kallonta yayi alokacin tarin yad'an tsagaita tana ta gyaran Murya sabo da yanayin da takejin cikin Mak'ogwaronta, d'agowanda zatayine suka sake had'a ldo saurin janye ldonta tayi,

Nan wani tarin yakuma tasowa, ahankali take buga k'irjinta, sai kuma ta mik'e da sauri ta nufi d'akinta tashiga bayan Gida,

Mai da Kansa yayi yacigaba da juya spoon d'in Hanunsa acikin Abincin kunnuwansa suna jiyomasa irin tarin da takeyi,

Dogon tsaki yaja yakalli Mami da take masa wani Kallon da yakasa banbance nameye..


Mik'ewa yayi "Mami Wannan Stupid Girl d'innane ko?

Kallonsa kawai takeyi batare da tace komiba,

Yad'an yatsina Fuska "tana da Matsalan Heart shine take irin wannan tarin?

Kodayake najima da ajiyeta a ajin Mahaukata first Class,

Mik'ewa Mami tayi ta wuceshi batare data kalleshi ko tace wani abunba d'akin Dijahn ta shiga ta tura k'ofan toilet d'in tashiga, alaokacin tasamu tad'anyi Amai tarin yafad'amata, "Sannu Khadijah Mami tafad'a tana kunna Ruwa ta wankemata baki ta rik'ota suka fito ta zaunar da ita abakin gado,

Tsaban ta galabaita ko zamanma kasayi tayi sai Mamine tarik'eta, tarasa mezatayi no. Kabir ta lalumo awayanta,

Yana d'auka cikin fad'a tace "to ai sai Kazo kadubata, tunda dama kaine Likitanta, batajira cewansaba takashe Wayan bai b'ata lokaciba ya tura k'ofan yashigo,

Kansa ak'asa yace "Mami kina da Bak'i, suanajiranki afalo.


"Tom sai kazo karik'eta ina Zuwa, 

Jiyayi abun yamasa banbarak'wai, amma bayanda ya iya ya iso Hanunsa nab'ari yarik'eta,  Harara Mami tabishi dashi har tafita.


Afalo ta tarar da Bak'intan su Ukune Maman Habib ce sai d'ayan Dattijuwa da kaganta kaga Kamilan mace mai Dattako sai kuma wata 'yar matashiya, tazauna suka gaisa cikin kulawa,


Maman Habib ce tafara magana,


"Mominsu munzo miki dawani magana ne mai marik'ar muhimmanci.

kintuna da yarinyannan Aliya wacce Natura su Kabir wajenta?

"Eh na santa, Mami ta fad'a agajarce.

"Yauwa to wannan kakartace kin ganeta Randa mukaje Gidan da daddre ad'akinta Muka sauk'a,


Cikin damuwa Mami tace "na tuna,

"Yauwa narakota wajenkine,

Mami ta gyara zama  tana Fuskantan Dattijuwan,

Saida tayi Gyaran Murya tace "Dama nazone akan Maganan da mukayi na Auran yarannan kinsan mu mutanen da dason cika Alk'awari bakamanku ba, tunda mukayi Magana anhanata sauraran kowa dama Akwai wani yaro da yake niman Aurenta tobayi da aikinyi, shikuma yamtsa, da mahaifinta yaga sunason junansu shine yace zaibashi aurenta ko bai kawo komiba anma yaje yanemo sadaki,

To yaron irin mutananne masu tsatstsauran ra'ayi, fir yak'i wai abarshi zaiyi komi da kansa bayason ta rainashi, intak'aicemiki yanzu dai har abun yana niman ya haifar da fitina tsakanin lyaye.

Shine Mahaifinta yaturoni wajenki yace kawai kuzo a satinnan dazamushiga ayi auren basai ankawo komiba,  Burinmu kawai akau da zancen wancan d'in.

Wani lrin zufane yaketo ma Mami dan ita kan tunda dataga Kabir yak'i Nafisane yabata zab'i kan cewa ta zab'a mishi da kanta, shiyasa taje kan maganan Aliyan sabida tayi tunani intamatsamishi akanNafisan za'a iya samun matsala abun zai sahfi Zumunci.


"Yadai naga kaman kinshiga rud'u?
Dattijuwan ta Tambaya,

Mami ta nisa, nan takora mata bayani kancewa yanzu Tunda yadwo yace zai Auri Nafisan,


Dattijuwa tayi dariya "indai wannan ne Ranan Juma'a me zuwa kuzo ku karb'a ma Kabir Auren Aliya, inyaso duk lokacin dayashirya wajen zamanta sai yazo yad'auki Matansa, ai Kabir Mijin Mata Hud'u ne.

Sannan duk lokacin da ya shirya sai ya Auri ita 'yar'uwar tashi bayan tama ai yana da sararin k'ara wasu Biyun.

"Hakane Hajiya mungode  da wannan Karamcin, Allah yak'ara Girma insha Allah kujirayemu awannan Rana.

Kakarshi tana d'aki muje sai ku Gaisa.

Tana tafe sunabinta Abaya Har d'akin lya sai da Mami ta warware ma iya komi sannan tabasu wuri dan su tattauna yanda abun zai kasance, kaman yanda lyan ta buk'ata.


Afalo tabar su maman Habib tashiga d'akin Dijah don duba Wainan da ake toyawa.


Ak'ofan d'akin ta tarar dashi sai share gumi yakeyi agoshinsa kaman wanda yayi dambe ko tsere, ldonsa sun kad'a sunyi jajazur.



 "Lfy Kuwa? Mamin ta Tambayeshi.


 D'an tab'e Fuska yayi "lfy Mami Jirana akeyi ina da Bak'o a part d'ina.


"Tom ka bata magani ne?

"Mhmmm zanturo muku dashi Mami,
Inagama kaman ba ciwontanbane Don naga tayi Amai, daga Haka ya wuce dandama Allah Allah yake ya wuce yanaga kaman Mamin ta d'ago Halin dayake ciki,



Azaune ta samu Dijahn ta jingina bayanta da Gado Daga ita sai towel, dan tana gama aman, tafad'a bayi tayi wanaka sam tamanta da wani Kabir da akabashi jiranta har sai da ta zauna taji yaja dogon tsaki ya tashi ya fita.


Sannu Mamin tamata ganin tadawo Hayyacinta, barin zo khadijah tafad'a, sannan ta koma gun bak'inta,


Afalon tasamesu dukansu sai zabga godiya kakan Aliya takeyi ma lya, da Alamun sunyi magana mai k'arfi sosai Har jikin mota mami ta musu Rakiya.


Afalo tadawo tasamu Khadijah sanye da Riga da sket na atamfa wannan karon Hijabine ajikinta,

Agefenta  Mamin ta zauna ta d'an shafi kumatunta,

"Khadijah ki hak'ura da zuwan gidan Uncle d'in kinnan, barin k'ira miki Saudan tazo, kedama bason Hayaniya kikeyiba ba zaman Gidan zaki iyaba dan nasan yanzu bak'insu na nesa sunfara zuwa, gashi ba dad'i kikejiba.


Kwantawa Dijah tayi a ciyanta "Ayyah Mami na warkefa,  dama Wlh Juice d'inne ya wuce ta layin Abinci,

Mami tasaki dariya "to yanzu yadawo layinsa kenan?

Ki Hak'ura da fitannan Khadijah, Munyi Waya da Wata mai gyaran Jiki zatazo tafara miki gyaran Jiki kafin lokacin Bukin su Sauda, lansin kifito sodai amatsayinki na wacce ta zab'eki ababbar k'awa, ko bakyaso?

Sam Dijah bata son musu ma Mami shiyasa kawai tace
"Inaso Mami.

"Yauwa yanzu zata iso kufara.

 "To barinje wajen wancan tsohuwan, Kafin ta zo.

 Wajen la'asar mai gyaran jikin tazo,

Tsawon sati guda anayima Dijah gyaran da ita kam sam batasan ma'ana ko amfaninsaba, Hasalima gani take anyimugun takura mata,  fitowanta daga  Wanka kenan tana shafa mai taji Sallama nan ta bada izinin ashigo Wurgi tayi da Kwalban man tazo ta Rungume Jamila tana Murna abakin gado tamata masauk'i,  tana dariya Jami idon ki kenan? Ta zira Hijabi ajikinta, sannan ta fita samo mata abun motsa baki.


Jerin Akwatuna tayi tozali dashi A falo, kallo tayi tabinsu dashi, sannan ta kai dubanta ga Mutanen falon, Mutum na farko data fara tozali dashi Alhaji ya'une zaune gefensa Abban Habib ne da Uncle, sai Mami da wasu mata biyu da batasansuba, da Alamu sune zasu kai kayan Aure, Dammm taji da wani Furucin da yafito abakin Abban Habib  "bayau akasaba yin auren Mata Biyu lokaci d'ayaba kedai matsalan shine Rashin sanar dashi da akayi, Baikamata ayi ma na Miji irin wannan aurenba, da  kin sanar dashi, na tabbata ba za'a sami matsala da Kabir ba yarone mai Ladabi, yanzu shi azatonsa matar d'aya ce gaskiya wannan shine Rashin Adalcin da aka masa,

 sai dai muyi fatan Allah yasanya Alkhairi.

Cikin b'acin Rai Alhaji ya'u yace "kaidai d'ane inka haifeshi baka isa dashiba, amma inba hakaba ai da duk hakan bata kasanceba, saidai inason inrok'eki Fatima kibarni da Nafisa ni nasan ta hanyan dazanbi in sanar da ita wannan magana don nasan son da takeyima Kabir in tasamu wannan labari zuciyanta zai iya bugawa itakenan min k'waya d'aya Aduniya in haka ta faru ni aka cuta, nabarku lfy daga haka ya tashi ya fice.


Jikinta sai b'ari yakeyi ta k'arasa ta duk'a ta gaishesu Sannan ta d'auki abun da ta fito d'auka tabar wajen,


 "Jamila  nakai sati lna niman wayanki bayashiga, Dijah ta fad'a cikin sanyi lokacin tana ajiye Drinks da takawo mata.

"kedai bari wlh wayan ce tasamu Matsala, ke tare da mutuminkifa mukazo amma ya koma yadai matsane sai da yaga gidanku wai kina ta masa wasa da hankali,


Murmushin k'arfin Hali Dijah tayi jikinta ba k'arfi sam batasan meyake damuntaba yanzu yanzunnan tajita haka.

"Kahdijah wai wannan duk Hutun da akayine haka kinganki kuwa? Jamila ta fad'a tana k'aremata kallo, "Jikinki yayi wani fresh kaman ka tab'a jini ya fito, sai wani shining kikeyi ga wani k'amshi dake fita ajikinki na daban.


 "Kai Jami kema baki ga yanda kika canzaba wlh kinyi k'iba da yawa, kinyi Haske, tafad'a atak'aice, dan batason zancen yaja dayawa, saboda yanayin ya da take jinta.

Jamila ta k'yalk'ayley da Dariya "kai Khadijah baki da dama zauna inmiki kwalliya  akan Hanya nake.

Bamusu Dijah ta zauna Jamila ta Resa mata kwalliya, tsayawa kallon Fuskanta tayi a mirrow sai kuma ta kwashe da dariya,

"Kinsan Allah Jami da Aljana nayi kama nikam bazan iya fitaba,

"ke kinganki kuwa yanda kikayi kyau wlh ko amarya sai dai haka nikam zan tafi zo ki rakani.

Riga da wando na pakistan tasaka Yellow bak'aramin karb'anta kayan sukayiba gyalansa tayafa tasaka takalminta flat shima Yellow suka fito,


Wannan karon kam a falo tasami Mami ita kad'anta kuma bataga Akwatinanba, Jamila tayi ma Mami sallama, Har sunjuya Mami tace "Khadijah yaki d'aki ta wuce tafito mata da Ledan kayan Cosmetics, suka fita.

Daga d'ancan Nesa daf da gate ta hango Kb da Nafisa shi yana zaune akan Farin Kujeran Roba, Sanye yake da Blue Jeans da t shirt Yellow, da Hula fesing cap shima Yellow, Nafisa kuma tana tsaye daf dashi kaman zata fad'i akansa, Shadda ne ajikinta Ruwan K'asa da yasha aiki daga sama har k'asa, tasha lalle da kaganta kasan tana cikin farin ciki ba kad'anba,


*Tofaha jama'a wai Kabir mata nawa zai Aurane?* 🤔
 Ku biyoni yanzu aka fara



Ummu Fatima😘
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
 

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊

 
*Godiya da fatan Alkahiri gareku mai tarin yawa bansan yanda zan kwatantamuku irin farin ciki da dad'in danajiba na irin Addu'oinku Ga Fatima da Ummanta da masumin a groups da masumin ta prvt duk nagani saidai inbiku da d'ad'd'aya ne ina Amsawa naga barin muku adunk'ule Nagode matik'a 'yan mata Allah yabaku maza nagari wanda zakuyi zaman lfy da soyyaya ma dawwami yabaku 'ya'ya masu Albarka* 🤲🏻

*Matan Aure Allah yasa Albarka acikin zamantakewanku da mazajenku yadawwamar dazaman lfy acikinku ya Albarkaci yaranmu ya k'aromana da masu Albarka*


Group din Maman Hauwa bansan yanda zangwada muku nima lnayinkuba Gaskiya irin yanda kuke gwadamin. saidai zangayyaceku Ranan Dinnern Kb da Nafisa da Aliya  😜😝😝


           *page* 3⃣0⃣


   
             
  Ta zuba masa ldo kaman ta cinyenshi,  hanunsa Rik'e da waya yana danne2 jifa2 kuma yana d'agowa ya kalleta,  ya mai da Kansa. 


 Kallo d'aya Dijah ta musu ta sunkuyar da kanta suna cigaba da Hiransu da Jamila,  saida suka matso kusa kafin Nafisa ta d'ago sukayi ldo Biyu   Nan danan Fuskan Nafisa yakoma kaman anwatsa mata Gaushi,

Tarasa meyasa tayi mugun tsanan Dijah ko Kallonta batasonyin Musamman yau dataganta cikin Kwalliya jitayi kaman taje ta shak'eta, wani lrin Mugun Kallo take binta dashi ba abundama yafi bata Haushi kaman irin yanda taga tasake agidan kaman gidan Ubanta, har Mutane take taramusu agida dan tsaban samun waje,

  Shirun da Kb yaji tayine yasashi d'agowa ya kalleta ahankali yamaida kallonsa inda take Kallon,

 Dijah kuwa da taga duk wa ita suka zuba ldo sai dai kowa da lrin yanda yake mata nasa kallon,

Nanda nan  kuma taji Dijahn nata sun motsa, ta zunguri Jamila ta nuna mata su sai kuma suka kwashe da dariya, Sanin Halin Dijah da Kb yayine yasa shi janye Idonsa daga Kallonta, yaci gaba da danne2 wayansa,  Wani dogon tsaki Nafisa taja tana Hararanta tace "Dan k'auye be iya wayewaba, d'an matsiyaci bai iya samun wajeba, Tir  da mai Halin Tinkiya.


Dariya kawai Dijah takuma yi ta ja Hanun Jamila suka fita, a bakin gate tasamu mai d'aukanta nan sukayi sallama tashige mota da tarin tambayoyi abakinta,


Lokacin da Dijah tadawo daf da gate d'in tasamu Nafisa tana tsaye tacika fam yau kam tasha Alwashin sai taci Uban wannan 'yar k'auyen ta fad'a aranta,  cikin kakkausan Murya tace "Ke Banza 'yar k'auye y'ar matsiyata dabba Tinkiya, ma wa kk dariyan Rashin kunya.

Wani irin Dariya Dijah takuma fashewa dashi, ta tako ta k'araso gabanta "basai kin sake Maimaitawaba inasane zan baki Amsanki yake 'yar masu arzik'i ai babu matsiyaci aduniya, watak'ila 'ya'yan masu arzik'i basu shiga ajin lslamiyyane shiyasa bakisan hakanba
 Babu wanda yasan Matsiyaci sai Allah watak'ila wanda yake tink'aho da arzik'i aduniya shine matsaiyaci alahira, d'an talakanma kuma zai iya zamowa matsiyacin wannandai Gaibune da Allah shi kad'ai yabar ma kansa sani, Sannan kuma da karya ai gara tinkiya  Hidiman gabanta kawaitakeyi bata Abin tir da Allah wadai, sab'anin karya da take lank'aye da wani duk inda suka gifta ana Tir da ita,

 daga Haka tajuya zata tafi cikin zafin Nama Nafisa ta fincikota takai mata Mari da sauri ta sunkuya ta Mari lska,
 "Dan Ubanki wacece Karyan? Ta tambayeta tana shirin kai mata wani marin "Hey Stop it Nafisa Kabir yafad'a cikin tsawa, yana k'are ma Dijah kallo,

"Kb kabarni inci Uban yarinyannan ni take cewa karya?

"Kece Karya kona fad'a ko ban fad'aba inba karyaba wacece Kullumtana  jikin Namiji ba dare ba Rana abun Haushi ba Miijinkiba, ba Muharraminkiba mtsss taja dogon tsaki ta wuce zata bi bayanta Kabir yace Nafisa nace miki kirabu da ita Wannan indai wajen fad'a da dambene bazaki iya da itaba shugabace wajen Rashin kunya kirabu da ita pls, Cikin zafi tace wai Kabir ita wannan d'in yar gidan Uban waye?  Waye ya kwasota yakawota gidannan?


Had'e Fuska Kabir yayi "ai ba agidana kika gantaba dazakimin wannan Tambayan kije ki tambayi me gidan Itake da Amsan Tambayanki.

Daga haka yashige part d'insa, afusace tashige ciki tana surutu wlh yau sai na yima yarinyannan mugun duka tabar gidannan.


A falo ta sami Mami kai tsaye d'akin Dijah ta shiga bata ganta ad'akinba tafito tana Huci,

"Lfy kuwa Nafisa meke faruwane? Mami ta tambayeta.

"Wannan yarinyan nake nima Mami wlh yau sai na b'allata,

"Wata yarinyafa? Mami ta Tambaya tana Rik'e Hab'a.

Dai2 Tabata Amsa Dijah tafito daga kitchen Rik'e da goran Ruwa zata kawo ma Mami.

Dasauri Nafisa tayi kanta zata  tad'auketa da Mari Mami tayi hanzarin tashi ta rik'eta lfy Nafisa laifi tamiki Mami kibarni in ci uwar ta wlh yau sai tagane ni Karyace, Zaunar da ita Mami tayi akan kujera.

"Metamiki? Gayamin ni nasan mezanyi akai, ban baki Hukunci a hanun kiba Nafisa.

"wai ni yarinyannan takece ma karya shikuma Kabir wai har zai cemin wai indai Dambe da fad'ane ban isa da wanna yarinyanba wlh k'aryane, yau sai namata kafirin duka agidannan,

Mami ta jinjina kai "inna fahimceki kaman Kabir ne yahad'a wannan fad'an, takalli Dijah da tayi tsilli2 da ldo Khadijah jeki ki k'irakimin shi, dasauri Nafisa tace "a'a Mami bashi yahad'aba,

"lnce dai yana wurin? K'irashi Khadijah ayi komi agabansa sai yazamo shaida tunda abun yakasance haka,


Karo na farko da Dijah ta tink'ari part d'in Kabir tundaga k'ofan falo taji wani sassanyan k'amshi natashi gami da wak'an india na  Falgoni, hanunta na b'ari ta k'wank'wasa k'ofan, sai da yarage sautin Kid'an sannan yace "yes come in, Murd'a Handle d'in tayi ta shiga azaune yake akan kujera ya tallafi Hab'ansa da Hanunsa maganganun Khadijah da tagaya ma Nafisa nata yawo akansa, Metake nufi da wannan maganan? shine tambayan da yake tayi ma kansa,

Khadijah kam sake baki tayi tana k'are ma falon Kallo duk Had'uwan falon Mami da har yau bata gajiya da kallonsa yayi baikai wannan ba komi na d'akin Fatine k'al gashi komi bisa tsari yake, daidai da Tv.

 ga wasu flawowi da aka kewaye gaba d'aya dungun Falon dasu.


Kansa asunkuye har yanzu bai d'agoba atunaninsa Nafisa ce tashigo jin batayi maganaba kuma bata zaunabane yasa shi fad'in Baby zo Kizauna kusa dani kiji, sai alokacin Ta kalleshi har ya watsa Ruwa ya sauya kaya Tree Quater ne ajikinsa mai tsantsi da Rigansa amless, wani uban tsaki taja sannan tayi baya "ance maka ni 'yar iskace Mami na ne take k'iranka, da sauri ya d'ago ido yakalleta  wani lrin kallon ashe abunda kukeyi kenan? Take masa cikin zafin nama ya tashi yayi kanta aguje ta juya sai dai kafin takai ga k'ofan ya damk'ota, (kunsa Dijah da k'ara)
wani irin k'ara tasake Har saida Mami tajiyota, sai b'ari takeyi tana k'ok'arin k'wacewa k'ara fizgota yayi ta fad'a jikinsa da sauri kuma ya cireta yana kallonta "inke ba 'yar  iska bace to waye d'an iskan?  Zata sake sakin ihu ya buge mata baki da bayan Hanunsa.

Ganin yana nima yadawomata zaki ne ta sassautar da Murya "Mami ce fa take k'iranka wlh ba k'arya bane, jin ya d'anyi sako sako da rik'ontane ta fauce ta fita aguje, yabiyo bayanta.

duk saurin datayi kusan ajere suka shiga falon, daf da Mami Khadijah ta zauna tana haki shikuma gogan sai sinne2 kai yakeyi yak'i su had'a ldo,

 Mami ta kalli Khadijah "kekuma ihun me kikeyi?

"Shine ai yatab'amin Jiki Mami nagaya miki wlh lskanci sukeyi yanzuma....
 "Ke Khadijah wai meyasa kike da yawan Surutu ne? Iya ta katseta tana fitowa daga d'aki agefen Kabir dayagama jik'ewa da zufan jin abunda Dijah tafad'a ta zauna "Fatima wai meye yake faruwa?

Mami ta nuna Nafisa "Fad'i abun da ya  had'aku,

Nafisa ta tab'e baki Yarinyannan tajima tanamin Kallon banza Nida gidanmu, shine yau wai har dacemin Karuwa mai bin Maza.

Iya ta Rafka salati tana tafa Hanu "Anyah Kuadijah mai yakaiki? Kinkosan Hukuncin Magananki? Irin wannan katob'ara da kikayi, Da Hankalinki? Ai dai koba komi Nafisa tayi k'anwa dake ak'alla sau biyu,

Saida Iya tagama fad'anta sannan Mami ta dubi Khadijah da taketa Zub da k'walla, tace "Meya had'aku Khadijah? Da har kikamata irin wannan Furucin.

 cikin kuka tace "Mami niba Karuwa nace mataba Karya nace mata Saboda Allah ku baku gani kullumfa indai Likita yana gida tana tare dashi kuma wlh sau dayawa ina ganin suna... "Shout up Mami ta tadakamata tsawa, "Abunda yahad'aku kenan?  "ita tafara cemin Tinkiya nan ta fad'i yadda sukayi.


Cikin kuka tace kullum sai tamin gorin gida,  kuma ai nima muna da gidan.

Mami ta kalli Kabir da ya Dafe goshinsa yana kallon k'asa cikin zafi tace "Kabir wace ce mai Gaskiya acikinsu?

 Ahankali ya d'ago yana Kallon su, yasan cewa indai a Gaskiyane to Khadijah ita tafad'i gaskiyan yanda akayi yayi mamakin Nafisa da tafetta k'arya haka, saidai amma tsananin Haushin Khadijah dayake Ransa, daya iya k'arya tabbas da ya k'aryatata, to inyayi haka kuma shima yayi k'arya abunda bai iyaba.


"Ana tambayanka kayi Shiru me kake Nufi? Inji Mami,

Sunkuyar da kansa kawai yayi yace "Kiyi Hak'uri Mami,

"Eh zakace inyi Hak'uri mana kana Namiji yara suyi fad'a agabanka, amma kakasa Yin komi akai,

"Mami bakisan Halin wannan Yarinyanba, Wlh bata da Kunya koda na Rabasu bazata saurarenba.

Iya tarik'e Hab'a saboda Allah Kabir tambayanda akamaka kenan? Kaba da shaida akan Halin Khadijah ko kuma kayi shaida akan fadansu kaifa Namijine Anyah zaka iya Adalci a tsakani Matanka?

Nafisa tazaro ldo mata? Lallai ma lya Allah yasawak'e yatara Mata ancemiki shi irin wancan tshohon Mijin kinnan ne dayataraku ku biyu wlh nikam nid'ayace bawatta banzan da zata shigomin Gida,

Iya tayi Murmushi "To Allah ya taimaka matan mai mace d'aya, ammadai inaga da ba'a k'arin dake ko shi Mijinkinda kikewa Soyayyan ba d'aya acikinku daga haka ta mik'e ta tafi.

Mami takalli Khadijah datake ta resa Kuka cike da tausayi don ko ba a gayamataba tasan Kukan tuna lyayenta takeyi.

Khadijah yi Hak'uri kitashi kije kiishirya ga Malamin Islamiyyanki yazo kije kiyi Kartunki, kar insake jin kincema watama ba Nafisaba Karya, Kinji? Kai ta gyad'a sannan ta tashi ta tafi

Mami tajuyo ta kalli Nafisa da take ta jijjiga tace "Nafisa kema kar kisake cemata tinkiya sannan na rok'eki kimin Kara kidaina Mata Gorin Gida,

 Yarinyannan 'yar gatace agurin iyayenta bak'aramin artabu nayiba akanta, da k'yar sukayarda sukabani, lta don haka kitaimaka kidaina Mata gori inbadai kinason kinunamin cewa ban isa in kawo wata Gidankubane.

Inkuma kinci Gaba to dani kikeyi bada itaba.

Tashi Nafisa tayi ta shiga ciki jimawa kad'an tafito da makullin Mota "Mami Na fita, "to adawo lfy kawai tace atak'aice.

Kabir yatashi Zai fita Mami tace "Kabir zo dama ina da Magana dakai,

 Gyara Zama tayi tana Fuskantansa Sosai Tafara Magana "Kabir inason ka bud'e kunnenka Sosai kaji Abunda  zangaya maka, lnafatan zaka fahimceni fahimta mai kyau,

sake gyara xama tayi tana fuskantansa, Amatsayina na Mahaifiyar  ka Kabir Namaka Aure!!! Ko ince nasa and'aura maka Aure! Bada saninkaba.


Dukda abaya kai kabani wannan daman saidai yanzu naga kaman ka sauya ra'ayi.


*Tirk'ashi wai yaya Kabir d'an gidan Mami zai d'auki maganan da Mahaifiyarsa Maminsa maiso da k'aunarsa tazo masa dashi shin yaya zaiyi da Nafisa gashi dama ra'ayinsa bana mata biyuba* *gashi an auramasa matar da baisaniba*

shin wai meyasa khadijah tamatsa dacewa Kabir da Nafisa 'yan iskane??

Karkumanta Comments d'inku shine yake bani k'arfin gwiwa👇🏻

08065091824
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
 

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 3⃣1⃣


    Shiru ne na Lokaci ya biyo baya,  Wani lrin sanyi mai gauraye da zufane yake ratsa jikin Kabir,

 Yarasa wani yanayi yake jin Kansa, azahiri dai shi bai kawo Aure ma kansa nan kusaba don har yau shi baiga matar data dace dashiba, duk dai dama yasa ma ransa zaiyi Aure ne don d'abbak'a Suna, da son cika ma Mamin sa Burinta, Don yasan inyace don so zaiyi to bazaiyiba Har Abada don shi bai yarda da Akwai wani Abu mai suna Soyayya ba bayan na d'a da Uwa,  sannan awani b'angaren kuma yana son Zab'in Mamin sa, yana son ganin Farin cikinta, saidai bai yi tunanin Dagaske Mamin zata masa Auren Doleba kamar yadda tasha gayamasa asigan Wasa.


"Kabir! Mami ta k'ira Sunasa cikin sanyi da damuwa, aduniya Abu mafi d'aga ma Mamin Hankali shine ta ga Kabir d'in cikin Damuwa.


"Na maka laifi ko Kabir?
  Ban kyauta maka bako?
 Sai kuma tayi shiru tasake d'agowa ta kalleshi shid'inma itan yake Kallo cikin damuwa, "kayi Hak'ur....  "Mami!! Yak'ira Sunanta cikin sanyi Murya cike da  damuwa ya k'araso yarik'e k'afanta "Don Allah Mamina kar kiban Hak'uri Nine fa Kabir d'inkinnan Mami da kikaci kashi da fitsarinsa, kika jure d'auwainiyansa Na miki Kuka.
 damuwata tahana ki Bacci, Mami kinyi dai2 Abunda kikayi Baki b'ataminba wlh ban isa ince kinmin laifiba, Nagode Mami Allah yasa hakan shiyafi min  Alkhairi Duniya da lahira.


Kallonsa kawai Mamin takeyi dukda ta karanci tsantsan firgici a ldonsa Kalamansa sun kwantar mata da Hankali,  Tabbas Tasan Allah yamata Baiwa da samun nagarceccen d'a mai son ganin farincikinta akullum.


"Allah yamaka Albarka Kabir lnsha Allah wannan aure zai zamo Alkhairi garemu baki d'aya kaci gaba da Addu'a Kabir lnsha Allah zakayi farin ciki madawwami da matarka, da yardan Allah kaima zaka samu 'ya'ya Na gari masu biyyaya agareka tashi kaje.


Cikin Sanyin jiki ya fita tsaban wani abu da yake damunsa wanda bai ganeba shin farin cikine ko damuwa, Waje ya fita ba tare da yaganeba, yajima yanatsaye abakin gate yana tunani gami da Tambayoyi ma kansa,  Why Mami ta masa wannan auren? Meye matsayin Auren Nafisa awajensa yanzu? bayan Har yabada sadaki ansa Rana?

"No Mami bazan lya auren Mata Biyu ba pls ya fad'a yana ya mutsa gashin Kansa.

Kimanin mintuna 40 yana zaga wajen daga bisani yashiga part d'insa Toilet yashige don Rage Ma kansa damuwa. 


Kwance take kan Gadonta tanata juyi gami da sharan k'olla, yau abun da yafaru tsakaninta da Nafisa ya tunamata da Baffanta shauk'in su yacika zuciyanta, Baffanta Mai Bin bayan ta kotana Dagaskiya kobata dashi, Burinsa kawai kar yaganta cikin Damuwa,  Bai tab'a yarda ya d'ora wani akantaba sai dai ta Rarrasheta, wayanta ta d'auko ta dinga bin Contacts d'in d'aya bayan d'aya, aranta tana tunanin Meyasa Fir Mami tahanata Numbern Baffanta saidai tak'irashi da wayanta suyi magana agabanta, ko meyasa hakan? Tabbas da tanada Numbernsa  data k'irashi awannan Lokacin.


Ji tayi Karatunma yafita aranta Inna da Baffanta kawai take son Gani,  tashi tayi tashige Toilet tana wanka ta jiyo Muryan Mami gyaran Murya tayi, tacigaba da wankanta, koda ta fito bata Sametaba,  Rigan Bacci tasa mai santsi dayakawo har gwiwanta, ta tufke Gashinta ta D'aure da K'aton Band  tafito, a Falo tasami Mamin ita kad'ai tun kafin ta zauna Mami tace "Haba Khadijah na ko kowa zai gujeni bai kamata kema ki Gujeniba, Nafisa ta gudu agidan gaba d'aya saboda na nunamata kurenta amatsayina na Uwarta, Kabir ma tunda yafita bai dawoba.

 kekuma meyasa kika b'uya ad'aki kika k'i fitowa? Kema namiki laifiko?  tafad'a tana k'are mata kallo.

Akasalance tace  "Bakomi Mami wlh banyi fushi dakeba bakimin komiba.

Ba abin da zakimin Mami inyi Fushi dake.

             
  Cike da Tausayi Mamin tace To shikenan Khadijah je kici Abinci kije ki kwanta Gobe ln Allah yakaimu da safe ki shirya zamuje gidan Fatima, Zanje in kwanta nasha Magani, kitabbatar kinci Abinci kafin ki kwanta, daga Haka ta Haye samanta,


Dijah tajima azaune agun kafin ta tashi ta Haye daining ta duba Abincin gaba d'aya ba wanda yamata, dan haka ta tashi daniyan barin wajen ta shiga d'akinta, Kabir tagani atsaye Hanunsa acikin Aljihun Wandonsa, Fuskansa amirtuk'e sai Binta da Kallo yakeyi, Ahankali yafara takowa yana Nufota, tana ja da baya yana binta Har sai da suka kai dungun d'akin Sanin Halinta ne yasa yayi saurin sa Hanu ya toshe bakinta sannan ya d'agota suna Shak'an numfahin juna, Jawota yayi sai da ya danganata da wani corridor kusa da  k'ofan Fallon yasaketa yana Kallonta gaba d'aya ldonta sunfito waje, amma sabida Hali lrin na Dijah Qaya takalleshi cike da tsiwa tafara Magana "Meye Haka? Malam ina zaka kaini? Kaga baniso ka matsamin ln wuce.

Yatsunsa Biyu ya had'a ya d'ani Lips d'inta, sanna ya kamasu da k'arfi yana kallonta Fuskansa A murtuk'e

"Ma waye kike cewa d'an lska?  Gayamin lnji.


Hannayenta ta d'ago ta d'ora akan nashi tana juya kanta, zame Hanunsan yayi yana yarfewa yana kallonta tasa Hanu tana shafa lnda yarik'en cike da jin zafi.


Zaki gayamin ko sai na cire wannan bakinki mai Faccakala maganan ya fad'a yana shirin sake kamo Bakin,

"Nifa ba d'an iska nace makaba, cewa nayi naga kuna lskanci kai da wancan Banzan kuma wlh nasha ganinku.

Cike da tsoron Furucinta yake binta da kallo ya lura da iya Gaskiyanta tayi maganan.

"Khadijah menene Iskanci?

"ohon maka kai kasani wlh Har maganan lskanci kunayi ai lnajinku kullum abayan Windowna kuke zama.

Kafin ta Rufe bakinta ya kaima Bakin bugu da bayan Hanunsa zatayi lhu yayi saurin Rufe bakin kika sake kikamin wannan k'arankin sai na B'urma miki baki, yarinya k'arama dake kin iya sa ldo da yin sharri.


Bawani lskancin da kika tab'a gani banza 'yar k'auye kuma ma lnkin ganin lna Ruwanki kiyi damuwan gabanki mana sai kin zauna kina terere na agari,  manufarki Dabam Manufar wanda zaiji wannan Furucin abakinki dabam,  kuma lnna sake ji kin Zagamin Mata sai na B'allaki ahasale tace "wlh ba matanka bace tunda ba ad'aura muku aureba,  kuma wayace kudinga cewa wani l luve u a l missed u kuma kullum sai ta shiga d'akinka ai wlh da agarinmu kuke sai an muku wak'a,  sake baki yayi yana kallonta har sai da ta kai Aya gani yayi inba da gaske ya mataba baza ta daina shiga Rayuwansaba.

Ya fara k'ok'arin ciro Belt d'insa ganin Haka yasa ta fara shiga Hankalinta don tasan zai lya jibganta awannan lungu kukanta abanza.

"To ai Mami ma tace kar insake fad'a kuma nace bazan sakeba kaban hanya lnje in kwanta bazan sakeba.


"kidai cigaba da min tsiwan dakika saba kawai.

"Allah Likita bazan sakeba, kayi Hak'uri nikamma na daina lek'aku.

Mai da Belt d'in yayi ya gyara tsayuwa yana kallonta "karma kidaina lek'amu ki cigaba da lek'enki amma dai kidaina min sharri inma zakiyi gulman to kinimi sani akai kafin ki fad'a lnkink'i sai na farfasa wannan bakin kin.

Kafin ya Rufe baki ta shige ta osinsa ya juyo suka had'a ldo ta tab'e baki "wlh nikam innaga anyi abu fad'a zanyi lnkuma ba'ason lnfad'a sai dai abari, ai ko auren ma kukayi nasan abunda zakuje kunayi kenan k'afansa ya d'aga da sauri ta juya ta shige d'akin lya da gudu, alokacin lya tana kallon labarai tana gyangyad'i taji anruntumo d'akin firgit ta mik'e tana nima wurin b'uya "Lfy Khadijah meye ya biyoki? Ko kinyi mafarkine? Sai da ta zauna akan gado kafin tace Likita ne lya ki Rufe k'ofan.

Iya ta zaro ldo Likitan ya dawo abun tsokananki ne?

Anya Khadijah ki mai da Hankalifa ni matsamin ln kwanta Bacci nake ji gara ke, lnkin gama ki rufe min k'ofan.

 tana tsaye awajan Har lya ta fara Bacci, ta gefen labule ta lek'a bata hangoshi afalonba tayi Dariya ta rufo ma lya k'ofa ta fito tasha kwana zata shiga d'akin ta kena ta ji ta bugu da mutum a tsorace ta d'ago suka Had'a ldo dagashi sai singlet da dogon Wando Hanunsa Rik'e da goran Ruwa da cup da Alama a kitchen ya d'auko.

 juye2 ta hau yi yatsaya yana kallonta ganin ba hanyan guduwane yasa ta juyo ta kalleshi tana zaro ldo muryanta na d'an sezing tace "Sannu da dawowa, ina Wuni, ta gefenta yabi ya wuce batare da yace komiba da gudu ta shige d'aki ta maida k'ofa ta rufe.


Washi gari da sassafe Dijah ta shige kitchen don yin abun karyawa kaman yanda tasaba wani lokacin suyi tare da Mami wani lokaci kuma kafin Mami tafitoma tuni tagama.

Yauma hakan Akayi kafin k'arfe 8:00 tuni ta gama duk abunda yadace tashiga wanka tunda tafito take kan Mirrow,  duk da bawani shafe2 tayiba bak'aramin kyau tayiba, swiss less tasa Lemon green mai kwalliyan zare Orange sark'a da d'ankunnen ta  dasu warwaro duk orange ta saka, takalmi da jaka Lemon green ta yafa mayafinta orange mai stones ba k'aramin kyau tayiba tafito sai baza k'amashi takeyi a falo ta sami Mami itama cikin shiri take karyawan ta kenan ta tashi zata shiga ciki,

cak Mami ta tsaya tana kallonta har tak'arasota ta duk'a tace ina kwana Mami d'agota mamin tayi tana Murmishi lfy 'yar Mami kinganki kuwa?

Kinyi kyau sosai kamar 'yar sarauniyan Engla, Duk na zuwa gidan Fatiman ne? Ai nazacikin manta tayi maganann da zolaya Murmushi kawai Dijah tayi.

"kin karya kuwa? Nasan ma baki karyaba, kikarya inkingama ina sama daga haka ta wuce.


Tea kawai ta had'a zallan sa ta dawo kan kujera a falo ta zauna, dai dai lokacin Kabir ya shigo cikin Riga da wandon dark blue d'in Jeans Rigan kuma shirt ne mai dogon Hanu light blue, kallo d'aya yamata ya zarce d'akin Maminsa, Abakin gado yasameta tana duba wani takarda, d'an gefenta ya zauna Fuskansa d'auke da Murmushi, ya gaisheta ajiye takardan tayi ta dawo kan kujeran da yake kusa dashi ta dafa kafad'ansa  "ka Huceni?  Kabir abun har da yaji?


" a'a Mami kinsan shirin  bikin Habib mukeyi abunda yasa kika ga bandawo da wuriba kenan, muna can wajen tsara Venue,


"To meyasa ka kashe wayarka?

"Wlh Nafisa ce take son takura min shiyasa nakashe.

"Nayi zaton ko don  auren kanne Kabir kamin yaji,


"Bahaka bane Mami yafad'a yana sosa kansa,

Kallonsa tayi da Alama da magana a bakinsa,

Murmushi tayi wata k'ila kanason sanin yanda akayi aka maka aurenko?

"Bahaka bane Mami Nafisa nake tunani yanzu za'a ajiye maganan Auren tanne?

"Meyasa za' ajiye? Ai in anmata haka ba ayimata Adalciba tsawon lokaci tana jiranka. 

"Mami nasani zamu sha artabu da itane sam banson tashi hankali,

"Kabir kad'auki wannan aure naka a wani babban al'amari da Allah ya hukunta kasamwta kasanar da lta bayin ka bane.

"Mami to wai wacece yarinyan kuma yaushe aka d'aura Auren nazacima  Nafisan tasani amma jiya maganan da tamin na fuskanci bata saniba, Mami mata Biyu basuyi yawa ba kuwa?

Murmushi Mami tayi sarai ta fuskanci lnda zancen nasa ya nufa.


"Kar kadamu Kabir zakasan matan lnlokaci yayi, aure kuma  ma bakanan aka d'aura lokacin kana England.


Wani mashiriri cun Murmushi Kabir yayi jin maganan yayi kamar a tatsuniya cikin son yabasar yace "kai Mami  ashe najima da angoncewa ma ni bansaniba, kaman zaki fitane ko?

"Eh zanje gidan Sani "ok lnkin shirya muje inkai ki.
"Khadijah nake jira ka dubota lntagama sai mutafi.


"To yace sannan ya fita bai sameta a faloba, D'an dube2 yashiga yi a kitchen yaji motsin Ruwa yashiga a lokacin tana jikin famfo tana wanke kup d'in da tasha tea, bayanta yatsaya yana k'are mata kallo, ta juyo da niyan ajiye cup d'in kawi taga mutum Wani lrin razannane k'ara tasake, gami da wurgar da cup d'in Da sauri ya matsota zai rik'eta Mami ta fad'o kitchen d'in a tsorace "lfy Kabir mai kamata? Tayi tambayan tana rik'o Hanunta.

Ya Harare Dijah da take ta muzurai Ba abunda namata Mami juyowa kawai tayi ta ganni.

"Gaskiya Mami yarinyannan tana da sercatref problem yakamata akaita Abinciketa, Hanunta kawai Mami takama suka fita.


Uziri pls kuyi Hak'uri da wannan 😰




UMMU fatima
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
         
 

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 3⃣2⃣


   
      Bayansu yabi sai wurga mata Harara yakeyi,  aransa yana Mamkin Halin yarinyan sam lhu bayamata Wuya yanzu ta tatarama Mutane ba wani Abubane awajenta.

Afalo Mami tasake Hanunta, tace ta d'auko mayafinta taje wajen Motan tajirata.


Saida taje tayi ma lya sallama sannan tafito.

Atsaye tazo tasami Kabir ya jingina bayansa da Motan yana hard'e da Hanunsa ak'irji, d'an nesa dashi kad'an ta tsaya tana Amsa waya,  zubamata ldo sosai yayi yana kallon yanda take Lumshe ldo da Alama tanajin dad'in Maganan datakeyi.

Cikin taku Na kamala da Nitsuwa Mami ta iso, tundaga nesa da Dijah ta hangota ta'ajiye Wayan ta nufota ta karb'i jakan Hanunta,

 Baya Mamin tashiga sannan tamata Umurni da shiga gaba, suna tafiya jifa2 Kabir yanayi ma Mami tad'i har suka iso.

A k'ofar Gidan yayi perking, Mami ta kalleshi "meyasa kayi perking anan Bazaka shigaba?  Yad'an yi Murmushi  "Mami ince  yanzu Zaki shiga ki fito, yafad'a yana Langab'ar da kai..

 Murmishi kawai  tayi suka shiga  Khadijah tana Gaba  Mami na biye da ita, a k'ofan falo Dijah tayi Sallama wajen sau biyu ana Ukun ne Bintalo ta Amsa ta fito tana Bud'e k'ofan Falo tayi tozali da Dijah ihun Murna sukayi gaba d'aya suka Rungume junasu.


 gefe Mami taja zuciyanta cike da tausayin yaran dakuma tuhuman Kanta na Rashin Kawo Khadijah wuri "yar'uwanta, Tasani ba k'aramin kawaici tayiba dai2 da Rana d'aya bata tab'a nuna Alamun tanason ganin 'yar'uwan nataba.

"Mami kishigo Muryan Bintalo ya katsemata tunani, Murmushi tayi ta kalli Bintalo da take ta nok'ewa saboda Cikinta da yad'an fara Ture Riga,

K'asa tasakeyi da Kanta tace "Bismmillah Mami kishigo.

"kingama Murnanne Fatima? So kike ki karyamin 'ya ko? Tafad'a tana kutsawa ciki, Sai da tazauna akan Kujera kafin Dijah ta zauna ak'asa daf da ita,  Bintalo tashiga Bed Room ta sako Hijabi, sannan ta shiga kitchen ta cika musu gabansu da kayan ciye2 da shaye2.


A gefe Bintalo ta zauna cike da Girmamawa tagaida Mami,  "Kuna lfy ko Fatima?
"Eh lfy k'alau.
"To Alhamdulillah kina waya dasu Baffankin ko?
"Eh d'azunma muka gaisa.
"To yayi inda wata matsala dai nagaya miki Fatima kar kiji nauyin sanarda ni ko wace irice kuwa, kid'aukeni tamkar lnnan ki kinji?
Bintalo Ta gyad'a kanata tana wasa da yatsunta.

"Sannan shi zaman Aure Hak'uri yafi yawa acikinsa kaman yanda nake gaya miki kullum, Kibi Mijinki sosai Fatima duk da dai nasan ke yarinyace mai ladabi to kik'ara akan nna da.

Ya Makarantan dai lnce ba wata matsala?

"Babu Mami wlh Malam dakika had'ani da itannnan tana kirki sosai, tana taimaka min a kan karatuna.

"Ayyah nasan zatayi ai Hajiya Ameena ba laifi.

Mami ta kalli Agogon da yake mak'ale a hanunta Sannan ta kalli Dijah "Ni zan tafi Khadijah inada Meeting, sannan daga nan zan wuce gidan Uncle d'inku zuwa yamma zan turo ad'auke ki,

"To Mami kigaimin da Umma da Sauda.

"zasuji.

Tana k'ok'arin mik'ewa Bintalo ta langab'ar da kai "Mami bakici komiba fa zaki tafi,
"Sory Fatima Sauri nakeyi ta fad'a tana d'aukan goran Ruwa d'aya, ta mik'ama Dijah kaima Kabir nasanshi da shan Ruwa naga kuma  bai d'aukoba,

 "To, tace Sannan ta d'auka tafita yana zaune akan Mota yana waya da Nafisa,  baya yabata dan haka sam bai gantaba, har sai da yagama, daga bayansa yaji Muryanta adak'ile "Likita wai gashi lnji Mami, wurga k'afansa kawai yakeyi daga saman Motan batare da ya juyoba, tad'an wuto gabansa tamik'amasa zuba ma k'irjinta ldo yayi batare da ya karb'i Ruwanba, cikin dakewa yace lna mayafinki? D'an juyawa tayi ta kalli k'ofan gidan "yana ciki.

"Yamiki kyau yafad'a yana maida kallonsa ga wayansa, ta turo bakinta "ba zaka sha Ruwanbane in maiyar?

Ya had'e Rai "zo ki bani  abaki,  ta karkace kai tana mishi wani Kallo ance maka ni 'yar lskace irin Wancan Banzan Nafisan?

 Wlh ma ka jawo makanka, sai nafad'a Mami abunda naji yanzu kafad'a awaya wai ku had'u a aroma Hotel kaceko?

Cikin zafin nama ya dirk'o asaman Motan ai asaba'in ta yarda goran Ruwan ta arce da mugun Gudu, abakin gate sukayi karo da Mami, Mami tana shirin rik'eta tayi saurin komawa bayanta tab'uya,  tana lek'owa.

"Lfy kuwa? Bintlo da tayi Rakiya ma Mami ta Tambaya tana kallon Kb dayake jingine da jikin Mota, Hanunsa soke a cikin Aljihunsa, barakatab'a cewa dashi Dijah take wannan gudunba.

Mami ta matsa gefe tana kallon su takalli Diijah ta kalli Kabir, badin sanin Haliba sai tace Dijah ita kad'ai ta kwaso wannan gudu.

"lfy Khadijah? Inji Mami.

Turo baki tayi Shine ai wai ln bashi Ruwa abaki.
D'an gajeren tsaki Mami tayi ta wuce ta shiga Mota.


Bintalo ta d'an Harare Dijah murya k'asa2 tace "Mai Hali dai baya fasawa, Allah ya shiryeki, Sannan tak'arasa bakin Mota,  suka gaisa da Kabir d'in alokacin yana shirin tada Motan.

"Ya Kabir shine kak'i shigowa ko?
"Jiya fa iwar haka inacikin gidankinnan Mamata kokin Manta?
"jiya daban yau daban ai.
"kar kidamu Yau da daddare zan zo ind'auki aron Mijinki yamin Rakiya, yafad'a da zolaya, Dariya kawai Tayi ta kauce masa yaja Motan.

Suna komawa ciki Bintalo ta kamo Hanun  Dijah tana k'aremata Kallo, tarik'e Hab'a "Dijah Haka kika dawo? Wlh banda namiki kyakykyawan sani bazan ganekiba, kinganki kuwa?


Dijahn kam da Mamaki take kallonta "yanzu Har zakicemin Na canja Bintalo? Toni Har yanzu kokonto nake anya kuwa kece?

Kinyi k'iba sosai ga wani Fari da kika k'ara Bintalo Meye wannan acikinki? Tafad'a tana zaro ldo gami da tab'a cikin.

Bintalo ta buge Hanunta tana Dariya    tashige Bed Room.

Jim kad'an tafito "Dijah wai lnji Honey yana gaisheki, zaro ldo Dijah tayi "waye kuma Honey?
"yaya Sani man.

Jinjina kai tayi "dama yana ciki Shine yayi likimo yak'i fitowa?

"yafita waya mukayi nace masa kinzo mana kwana lnce kwana zakiyi mana.

"cab shida yace ba a kwana agidanku, ba abunda zai sani inkwana.

Bintalo tana dariya tace to sauko kici koda friut ne.

Sauk'owa tayi suka baje awajen suna Hiran abunda ya wuce suna Dariya, can Dijah tad'an yi shiru, Bintalo tace yadai?

Nan danan Hawaye suka fara zarya a fuskan Dijah "Binatalo Baffah na inason ganin Baffahna wlh inason inkoma gida.

Shiru Bintalo tayi aranta tana tunani ba ita kad'aiba hatta su Baffah insunyi waya sukan nuna mamakinsu na yanda Dijah tayarda ta zauna tsawan wannan lokaci a wani gurin.

Tayi abunda ba wanda yatab'a tunanin zatayi.

Bintalo ta nisa cikin son kawar da zancen tace "To indankuma kika shiga d'akinki na Aure fa ya zakiyi?

Rabuwa dasu ai yazamo miki Dole Dijah tunda Allah ya hallitoki Mace ba na Mijiba.

Tasa Hanu ta goge Hawayenta tanakallon Bintalo "ni bazanyi Aure awani Gariba, gani ga Baffa da lnnata kullum lna tunani yanzu waye yake d'ebo ma Baffana Ruwa?
Wa yake tayi lnna aikin gida?

Bintalo tayi wani Murmushi mai ciwo cike da tausayin lyayen nasu dan lrin tunanin da Dijah takeyi itama takeyi musamman yanda Rayuwa ya canza mata tana  cikin jindad'i ga ababen More Rayuwa kala2 Bata da wata matsala, Rayuwa takeyi irin wanda bata tab'a Mafarkinsaba( Allah kenan) kullum kwad'ayinta inama ace lyayen nasu suma haka suke.

"Tace Dijah ki kwantar da Hankalinki indai wannan ne aidai dama da d'iban Ruwan da aikin Abincin duk dan muna nanne yake yawa, yanzu kuwa duk zai zo musu da sauk'i.

Wlh cikin k'oshin lfy suke duk lokacin damukayi waya sundinga Tambayana lnce dai bama cikin wata Matsala?

Dijah tace Don Allah kibani no. Baffah kinji?

Bintalo tayi shiru tana tunanin maganan dasukayi da Mami bayan ta koreta da wayon takaima Kb Ruwa.

"Mik'omin wayan gashi can abayanki ink'irashi Kugaisa kafin kitafi zan baki no.

Dasauri ta mik'o mata ta kalleta "Kimin Alk'awarin bazaki fad'a musu wani abunda zai b'ata musu raiba  kuma ki share fuskanki kidai daita Muryanki inba hakaba bazan k'iraba.

Me Hali baya fasawa saida tad'an Harareta ta murgud'a baki kafin tace "wlh gaisawa kawai zamuyi.

Tana k'iranshi bugu d'aya  yad'auka.

Jin Muryan da baiyi tsammani bane yasa shi sakin lallausan Dariya cikin farin ciki yace
 "Uwata ta kaina
 Uwata tafi ta kowa
 Uwata maganin Kuka na.
Saida ta sauk'e ajiyan zuciya, tace
"Baffana lnason lnganka Baffah kullum sai nayi Mafarkinka,

"Zaki ganni Dijah na indai ina raye kina raye zamu ga juna dayardan Allah,

Hajiya tace min inkin sake samun wani Hutun anan zakiyi mana, ki kwantar da Halinki mamata kiyi karatunki kinji?

"To Baffah ina lnna ta? Innan ki tana gida nina fitane,

"Kaje d'ibo Ruwane ko Baffah? Ko lta ce? Tayi maganan araunance.

Baffah yayi dariya mai sauti "ki kwantar da Hankalinki Dijah bana Ruwa bana l tace.
.Baffah ina Jebu na? Tafad'a cike da shauk'i.

"Ayyah Jebunki ai kullum itake d'ibo mana Ruwa iro kuma ya d'ibo mana itce kullum tana wajen lnnanki tare suke aikin gidan bata da magana sai naki.

Cikin son Aminiyan nata tace lnka koma gida Baffa Zank'iraka ka had'amu da ita.

"To Dijah na Amna kin min laifi baki tambayi Takwarankiba, Goggoji ita kuwa kullum tana magananki,

Rufe ido tayi kaman tana gabansa tace Kayi Hak'uri Baffah wlh nayi Missing Goggoji na sosai ba kad'anba in munyi magana da Jebu zance takaimata.

Daga Haka Bintalo ta karb'e wayan suka gaisa, daga bisani sukayi Sallama ta kalli Dijah datake ta Murmushin farin ciki, "Ki tashi mushiga kitchen yau ke zakimana Abinci, Honey ya Huta tsaki Dijah taja daida Lokacin Sani yashigo.

Da Murmushi yake Kallon Dijah
"yau Khady Baby ce agidan namu? Lallai yau muna da babbar bak'uwa, yafad'a yana zama agefen Bintalo sannan ya kamo Hanunta yana Murzawa "Sweety yau Baki Har kunne gaki ga Khadijahnki.


Rintse ido Dijah tayi aranta tana tunani Dama haka aure yake duk wanda yayi sai yazama d'an lska?

"Khadijah yaya Gida?
 "lfy ta Amsa kanta na k'asa dariya yayi sannan ya mik'e sweety Barin zo naga wannan Bak'auyuwar k'auyanci nata ya motsa,  lna zuwa yanzu,  yana fita Dijah ta dallah ma Bintalo Harara.

 dai2 lokacin Mak'ociyarta Aysha ta shigo, da Sallamanta tazauna Kusa da Dijah tana kallonta tace "Aunty Fatima wannane Khadijahn ki ce ko?
"Eh itace,
"kai naga kama amma dai tafiki kyau.


"kai Aysha kiduba da kyau dai ta fini kyau? Ko tafini Fari?
"ah wlh kyau d'inma tafiki, lna sonki Mai kyau kusan Kullum sai Aunty Fatima ta bani labarinki kullum lna Allah2 inganki sai yau ya mutanen gidan?
"Lfy k'alau, tana gulmana dai ko?
"ah sam wlh tana dai bani lbrn kine kawai.


Aysha ta kalli Bintalo, "Aunty Fatima kinga jiya baki gannibako? Wlh  sweety na ya rik'eni fir yahanani fitowa kin san jiya anyi d'an sanyi bai fitaba bai barni na fitaba, wlh ko Abinci sai da na lallab'ashi yayi bacci na d'ora ai yana farkawa aka faka girgi agefe, ta k'are maganan tana mik'amata Hanu suka tafa.

Nanfa Hiran matan Aure ya b'arke a tsakaninsu.

Saida sukayi mai lsansu Aunty Aysha ta mik'e barinje ingama ayyukana zan dawo intafi da Mai kyau Gidana.

Dijah dai tana zaune awajen kaman andasata ji take kaman ta nitse awajen Harara kuwa   ta musu ba Adadi daga k'arshema tashi tayi tashiga kitchen.
Anan Bintalo ta sameta har ta kunna Gas tana fere Doya tana dariya tace "oh Khadijahn Mami sakwara za'ayi mana ne?

Barin dafa ma  Honey  indomie, mutuminki yak'irashi wai zasu lek'a Campaninsa  Dijah ta tab'e baki tana mita

"wlh Bintalo kinshiga Ukunki daga zuwa Birni kinzama 'yar iska, nikam ba Ruwana kin had'u da wa incan matan sun koya miki lskanci,

Saida ta d'ora ta kalleta Ayyah Dijah am wanna matan abun ki mata godiyane zuwana gidannan kinsan ba abun da na iya ko Abinci mai kyau ban iyaba haka take shigowa ta koyamun komi da yanda zanyi amfani da komi Hatta zama da Mijin ma ba k'aramin jahadi tayi daniba

Ke wlh bani da bakin mata godiya sai Addu'a ta d'aukeni tamkar 'yar'uwanta.

"Eh daganan kuma sai ta koya miki Rashin kunya da maganan banza ko

Bata rufe bakiba sai ganin Sani tayi ya shigo ta baya ya rungumo matarsa Sweety zan tafi fa kinzo kinbiye ma Khadijah kin mantani.

"ah Honey na gashima yadafu ta juye a flate suka fita tare


 Dijah kam mutuwan tsaye tayi taja gefe tana jinsu har yanzu bata daina mamakin Bintaloba aranta tana tunani inama ace a ldon lnna da Baffa take irin wannan abun tasan da sun tsinemata angama.

.

Sai da yamma Mami ta dawo gida lokacin Kabir da Habib suna zaune a Farfajiyan gidan kusa da pert d'insa magana sukeyi har Mami ta iso gurin basu luraba, saida tace "Sannunku kafin Suka kalleta, Kabir yace "Mami waya dawo dake?
"Ni da kaina nadawo, yad'an zaro ido yana kallon Motan, da kanki Mami? Yanzu kuma mukayi waya bakice min inzo in dawo dakeba "ah ai tunda kace min kai da Habib ne nace to barin barka kayi danna k'irjin da kyau.


Kabir yana dariya yace "Mami ashe Sauda ce Amaryan? ai dama baku b'oye mana wacece matarba.

Habib yad'an lakaci Kabir yana masa ldo.

"kingani ko Mami wai kar in fad'a Munafukai dama suna Soyayyansu a b'oye, lskancine kawai yasa basu nunaba inagama su Uncle sun ganene yasa suka had'a Mami tayi dariya mai Sauti tace "Ashe shiyasa sukayi shuru 'yan bad'o har anata yabonsu wai suna da ladabi, basuyi tawayeba.

Habib yayi k'asa da kansa yana Dariya "Allah Mami k'arya yakemin ni bansantaba.

"To Allah dai yasanya Alkhairi tafad'a tana Duba l.V cards d'in dayake gabansu.


"Mmmn yauwa Kabir kaje kad'au komin Khadijah da Allah yanzu dare yayi, tafad'a tana shiga ciki.

Dukansu suka mik'e Kabir yace  "Habib muje gidan Sani daganan ka rakani  wajen wancan fitinanniyan, wai ltama yau zata dawo gidannan, Jiya Dady yadawo.

"ka manta ne tun d'azu Abbana yake min waya zanje inji, wai ni yaushe ne aurenkune kai da Nafisan?

Hararansa kawai yayi ya Shige Motan ya rigashi Fita.

K'wank'wasa gate d'in gidan yayi ya koma gefe ya tsaya can Dijah ta lek'o tana fad'in "waye?

Ganin Kabir ne yasa ta fito tana kallonsa wa kake nima?

Dogon tsaki yaja "lnkin ga Dama kizo in mayar dake inada abunyi,

Jujjuya ldonta tayi sannan tashiga can kuma sai ga Bintalo Bayan ta masa sannu da Zuwa tace "yaya Kabir na zaci zata kwanane, inyaso Gobe sai muzo tare.

"nifa Mami ce ta aikoni duk basan wannanba, inzata zo tafito ina da Uzuri.

"Ok bari tafito, tana shiga Dijah ta fito ta d'an tsaya tana langab'ar da Kai "Ayya Likita da kabarni da safe sai mudawo tare tsayawa yayi yana bin bakinta da kallo duk ta inda ta motsashi,

Ya Kalleta inkimgama sai kishigo mutafi karkiyarda ki b'atamin Rai wlh.

*Cab Nasan yau da magana* 😳😳😳😳😳😳😳😳😳😳


Ummu fatima ce
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
                  *DIJAH* *QAYA*
 
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
       *BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿

🦋                    🦋
            🦋                       🦋                           🦋                        🦋
     

*MY NATION*🇳🇬
         
  *ALLAH yabar k'auna*🤝🏻

🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊


           *page* 3⃣3⃣


    Bud'e Motan yayi ya shiga ya kifa kansa akan siriyarin motan yana jiranta, yana jinsu suna magana da flatanci, da Alama fad'a Yartata take mata.

Har saida ya k'osa aransa yana Mamaki wai shine yau yake jiran wata ba Maminsaba? Kodayake hakanma Umurnin Mamin ne.

Yana ji ta Bud'e ta shiga bata gama Rufe motanba ya figeta a guje dan ta gama k'uroshi.

Sai da ya hau titi kafin ya tsagaita Gudun.

 Sun Nisa sosai akan Titin Dijah tasake Salati gami da d'ora Hanunta akai,

Agaggauce ya sauk'a akan Titin yana kallonta, tun kafin yayi Magana cikin Muryan Kuka tace Likita Don Allah kamai dani na Manta ban karb'i no.ba ka maidani inkarba ko ka ajiyeni in koma.

"a'ina ne zaki karb'i no.?
"awajen Bintalo.
"no. Meye?
"Numbern Wayan Baffah na.
Wani dogon tsaki yaja ya Figi Motan aguje, yana fad'in nazaci maganan naki mai Muhimmanci ne.

Buga k'afa tafarayi,
 Sanin da yayi kad'an da aikintane ta tara masa jama'a, yasa ya sassauta Murya, "indai Numbern Baffah ne in munje Gida Mami zata baki..

"Bazata baniba Lilita ka ajiyeni kawai inkoma.

Yad'an Lashi Lips d'insa cike da takaici wai yanzu indai yana son zaman lfy amotannan sai ya lallab'ata? Shi da Motansa? Sannan shima ba tuk'a kansa yakeyiba, Amma ya d'ukota, Ga mari ga tsinka jaka ke nan.

Tajjuyo tana sharank'olla tace "Likita!
"Khadijah kiyi Hak'uri inma bata bakiba zan baki, Dan Allah kibarni Haka.

 "Kayi Alk'awari? Ta tambaya tana Rausaya kanta.

Yad'an ciji Lip d'insa yana furzar da lska yace "Eh. Atak'aice

"Kuma kishare Hawayennan ba abunda namiki wai meyasane halinki yazamo wani irine?

Mai da Bayanta tayi ta kwantar ajikin seat din Motan tana share Hawayen.

Yad'an kalleta da wutsyan ido ahankali yace Silly Girl.

Tuk'insa yaci gaba dayi cikin Nitsuwa Ba sautin komi amotan, sai na Numfashinsu kowa da abunda yake nazari, sunyi Nisa Wayansa  tafara Ringing, d'auka yayi ya kara a kunnensa "wai kungama Dinner ne? Yanzu kina Hotel d'inne? Ok gani zuwa daga Haka ya ajiye wayan, yana shirin juya kan Motan yaji anja Dogon tsaki abunda yatsana arayuwansa, wani irin Burki yaja sai da Dijah  ta tsorata, ya juyo suka had'a ldo mawa kikayi wannan tsakin?
 "Nikam ka maidani gida kafin kaje duk inda za kaje wlh ni ba wani Hotel da zanje ta k'arasa maganan da Muryan kuka,
"Inkuma ban mayar dakeba fa akwai wani abunda zakiyi?
Kin ishenifa.
 Kikasake kikasake kikamin wani Rashin kunya Ranki zai b'aci, bamani zaki dinga sakarcinkiba.

"to ni kamai dani Gida kawai.

Jan Motan yayi ba tare da Ya kuma kallontaba,  abakin Hanya ya Hango Nafisa ita da k'awayenta, tana ganinsa suka nufo Motan tana isowa ta bud'e inda Dijah take kasancewan Bak'in glass ne sam bata ga mutumba,wani d'an tsalle tayi ta matsa baya kaman wacca taga abun tsoro, Ta fara Wurga mata Harara ta yatsina fiska "Kabir wannan fa?

Ya kalli Agogon Hanunsa "Nafisa shiga Mutafi sauri nakeyi,

"wah inhad'a Hanya da wannan Abar wlh k'aryane, tasake Murfin Motan, tatsaya agefe tana jijjga.

 Cikinb'aci rai ya kalli Dijah "Ke Rufemin Mota, tun kafin ta ida Rufewa ya finciki Motan yayi Gaba, suna daf da lsa wayanta ta Hau Ringing a Fuskan wayan taga Auwal da kamar bazata d'agaba sai kuma ta d'auka, "Hello Khadijah gani a k'ofan Gate d'in Gidanku, tad'an Murmusa kajira gani zuwa daga Haka ta kashe, ta gefen ido Kabir ya Kalleta ya tab'e Baki, suna isowa a lokacin Auwal yana Zaune akan Machin d'insa, tace "Sauk'e ni anan, wani irin takaicine ya ziyarci zuciyansa, aransa yana tunanin irin rainin da yarinyan tamasa sake kan Motan yayi gadan gadan yayi kan Auwal wani lrin lhu ta sake tana kallon yanda Auwal d'in yadira yayi gefe, Kabir kuwa ko ajikinsa saima  Huci da yakeyi yana Horn, masu  gadi suka wangame k'ofan yana perking tafara kiciniyar bud'e Motan amma ta kasa sabo da Rufewa da yayi,
"Meye tsakaninki da wannan kucakin yaron? yafad'a yana tsareta ldo.

 "saurayi na ne, ta amsa azafafe, wani lrin bugu yakai ma Bakinta, yana Huci "kundace dashi Sosai, Amma ba a gidannanba wlh kika kuskura ki ka fita saina karyaki sai kibari sai kin koma can k'auyenku yabiki.
 Cikin kuka tace wlh sai na fita kuma k'auyen mu ai... Bata k'arasaba ya fincikota bai tsaya da ita ko inaba sai gaban Mami ya wurgata gefe yana huci Mami ta dafe kai,

"Oh ni Fatima wlh tuntuni lna zaune anan ina tunanin wata wainar ake toyawa mancewa nayi nace kad'auko ta, na had'a Wuta da Auduga, Haba Kabir meyasa ne kake biye ma Yarinya k'arama haka?

Zama yayi a kujeran  dake gefen  Na Mamin, "Mami bana biye mata da ina biye mata da tuni na karyata.

Wano k'azamin yarone yazo wai Saurayinta wannan ai zubar da Mutuncine takeson yi ma Mutane, 'yar wannan yarinyan yaushema aka haifeta gata da sakarci Mami wannan ba wuya wani ya yaudareta yajefata wani hali, bata da wayo ko kad'an, ta bari sai ta koma can k'auyansu, sune suke aurar da jarirai inyaso tayi duk yanda taso Amma ba agidannanba.
Ya k'arashe magannan yana nunata da yatsa, wani lrin zafi darad'd'i yakeji ak'irjinsa shi kansa bai san Daliliba jiyake yanason ya tattakata, Dam Dam Mami tajii k'irjinta yana bugawa, karfa tayi gurguwar dabara.


Ta Kalli Khadijah da take ta sharan Hawaye sosai kalamansa suka k'ona mata Rai.

Asanyaye Tace "Khadijah a'ina kikayi saurayi?
Ina kike fita da har kikayi Saurayi?

"Mami a school d'inmu yake, kuma...

Bata kai ga fad'in abunda zata ceba suaka jiyo karad'in Nafisa da k'awarta Meena a falon,

 "Wlh Kabir yau sai kagayamin Matsayin wannan kucaka k'azaman yarinyannan agidannan, tun safe na maka waya zan dawo bayan mungama Dinner n k'awata a aroma Hotel.

tunda a kagama nake ta k'iranka baka zoba sai da ka b'atamin lokaci sannan katashi kazomin da wannan Banzan?

 Mintunanka nawa da dawowa? Shine ka shanyani acan?
Yau sai nasan waye Uban Wannan Banzan ta fad'a tana Nuna Dijah cike da Wulak'anci.

A fusace Dijah ta mik'e itama tana mata Wulak'ancaccen kallo, "Sam bani Mamakin lrin lafuzan da suke fitowa a bakinki, Innayi la'alari da watsatstsen tarbiyanki, yo ai wanda yake da Tarbiyan mutunta iyayensa ne yake tunanin Mutunta na was...


Kukan kura Nafisa tayi takai mata shak'a, cikin Zafin nama Mami ta finciki Nafisa tayi baya da ita,

"Mami wlh yau sai na kashe yarinyannan kuma sai ta koma gidan Ubanta indai anason zaman lfy, inji Nafisa


"Naga kema dai ba zumuncin gidan d'an'uwan Ubanki bane yake kawoki,

 yawon lskancine da tab'ara yake kawoki kinzama bishi zai zai kizo kugama lskancinku... Dijah bata rufe baki ba Nafisa ta k'wace da k'arfin tsiya tayi kanta, itama kantan tayo,

A fusace Kabir ya jawo Dija ya yarfa mata Mari ya nunata da yatsa yana kallon Mami da kamanninta yagama canjawa dan ji tayi kaman Fuskanta ya Mara.

Pls Mami kimai da yarinyannan garinsu Ni kaina abun ya d'auremin kai bansan meya kawota gidannan ba bansan zaman me takeyi agidannanba,

For giveme Mami bayanda za'ayi ahana Nafisa zuwa gidannan, Sannan bazasu tab'a zama wuri d'ayaba Wlh bani son tashin Hankali Mami yanzu Haka kaina ciwo yakemin bazan iyaba, ki mayar da ita Gidansu yak'arasa zancan Kaman zaiyi Kuka, Zuciyarsa cike da tsoron Kallon b'acin rai Kwance Afuskan Mami,


"pls Mami kiyafeni Fitinnan da Hatsabibancin yarinyan yayi yawa.


Cikin matsanancin b'acin Rai Mami tayi taku ta zo gaban Dijah da takifa kanta akan gwiwowinta tana kuka mai tsima Rai ta kamo Hanunta ta wurgata kan k'irjinsa,

"Kasheta Kabir! Kasheta!! Daga nan sai amai da gawanta ai lbrn zaifi tafiya yanda yadace.


Kuna son Sanin Matsayinta ko?
Kanson Sanin zaman me takeyi agidanku ko?
Kanson Sanin Meya kawota ko?

To ku bud'e Kunnuwanku da kyau kuji,

Ta sake kamo Hanun Dijah da tazame a jikin Kabir ta tsuguna tana cigaba da Kuka,

"Wannance Ka k'ira Da Hatsabibiya Kabir Zaman da Khadijah takeyi agidannan Zaman Aurene Kabir, Aure ne ya kawo Khadijah Gidannan Khadijah Matarkace Ta Auren Sunnah Matar kace kake k'ira da Hatsabibiya.

Cikin Matsanancin Rud'u Kabir yace "Mami Mata nawa zaki auramiin? Kince lna England kinsa an d'auramin Aure da wata, Sannan Kince zan Auri Nafisa, Mami lnaga kaman sun isa basai ank'aramin ba.

Mami ta kalli Nafisa da tayi suman tsaye cikin Rashin Fahimtan zancen.

 ta koma kan Kujera ta zauna Ta Kalli Kabir da ya bud'e kunne da baki yana Kallonta.

"Khadijah itace Matar da aka d'aura muku Aure da lta lokacin Kana England Kabir ka Nitsu abun yana da sark'ak'iya bata haka naso sanar daku batunba, saidai Naga Abunne yana niman yazamo wani Abu daban Ba haka kawai lyayenta suka d'auketa suka bani itaba har sai da lgiyan Aurenka ya hau kanta, da Aurenta tazo gidanku, Aure kuwa shike raba kowace mace da gidan Ubanta ta dawo gidan Uban wani.


Sai yanzu Nafisa tasamu daman d'aga k'afa ta iso gaban Mamin ta tsuguna, dan sam Har yanzu bata fahimtaba, ta dafa k'afan Mami, "Mami baki tab'a mana irin wannan Wasanba.

Ni kad'aice Matar da Kabir zai aura bayana ba wata macen arzik'ima bare wannan Kucakan ta nuna Dijah da tazama mutum mutumi.

Mami kidaina fad'a kar 'yan Amin su Amsa bazan iya zama da kishiyaba Mutuwa zanyi.

Mami tadafa kafad'anta Nafisa Kidaina wannan Furucin Matan da suka fiki Daraja Matan Manzon Allah (S. A. W) da Matan sahabbai sun zauna da kishiya Kada kiyi jayyaya da Abunda Allah ya Halalta.


Khadijah Matar Kabir ce Ke bakisan komi game da lyayentaba, Amma kai Kabir kasan irin kara da karamcin da suka maka, dan haka naso Rama musu ta wajen son d'aukan Khadijah dan ln bata lngancaccen llimi Musama lura da nayi yarinyan tana da Hazak'a da baiwa.

Bayanda banyi da Mahaifintaba akan yabani ita fir yahanani ita har Manyan garin  nabi ta hanunsu surok'anminshi yabani ita, yace bazai tab'a bada 'yarsa Mace atafi da itaba, koda kuwa ma 'yar'uwansace, ban tab'a sha'awan ace ina da wani d'a na miji bayan Kabir ba sai awnnan lokaci  dan sam ban kawo had'a auren da Shiba saboda sanin Halinsa na nuna ko oho akan auren, naji araina da ina da wani d'an dana nima masa auren ta dan nasan tahanyan aurenne kawai zai bani ita.

 ammadai tunda nadawo na duk'ufa da Addu'ah da istihara akan abun kullum sai inji lnak'ara son hakan danhaka nayi shawara da Yayana da Abban Habib, suka bani goyon baya d'ari bisa d'ari kan aura ma Kabir Khadijah.

Nan dannan suka wuce gaba bak'aramin daga akashaba lokacin da suka sami Baffanta da Maganan, kasancewan Khadijah ta dabanne awajensa.

Ahaka dai da Allah ya k'addara akayi, Rana d'aya aka d'aura dana 'yar'uwanta aka kawosu tare saidai na rok'i lyayenta kar su sanar da lta kasancewanta k'araman yarinya ko dasu suna aurar da yaransu da wuri Dai tayi k'ank'anta.

Ahaka aka kawota amatsayin tayi ma 'yar'uwanta Rakiya ankawo amarya da ita.

Tad'an Nisa takalli Kabir da zufa yake ta d'iga daga goshinsa,  "Abban Habib shine Waliyinka lnkana niman k'arin bayani kaje gurinsa zakaji.

Da Rarrafe Dijah ta matsota "Mami kin mantane kiiyi Hak'uri bani bace naji da wanda aka musu Aure Aliya Sunanta Ranan naji kin fad'a wlh bani bace tafd'a tana fashewa da kuka.



"Wancan auren bai yiwuba zanbaku lbrn yanda abuun ya kasance.


Sai Alokacin Nafisa tasamu daman k'wallah k'ara tafita  a guje kamar Mahaukaciya sabuwar kamu




*Tofah inajiran Comments d'inku zafa ayita* 😳😂


MMN Temah😘

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *