Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Sunday, July 19, 2015

BAYANI AKAN KISHI.

adsense here pict0182-1.jpg

DOMIN KE DA MIJINKI.
««fitowa ta 1»»BY ABBA-GANA
ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮﺣﻴﻢ
ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﻭﺳﻠﻢ
Kishi wani abune mai kyau idan aka saka shi a
wurin daya dace, yakan zama mummuna idan ya
zarce yadda ake buqatarsa, kamar yadda ake
sarrafa dawa akeyin kamu da ita asha, idan aka
jiqata kwanakin suka wuce sai ta zama giya, ko
ruwan kwakwa da yake zama bammi da
sauransu.
kishin maza zaizo a wajen Miji na Qwarai bayan
nagama da Matata Gari.
Mace tagari takan nisanci mummunan kishi
domin yakan rage qaunarta a zuciyar mijin batare
da ta saniba, wata matar takan yi kishi da uwar
mijinta, wata har da 'ya'yan da ta haifama bawai
'ya'yan kishiya ko ita kanta kishiyar ba.
Irin wannan kishin yakan 6ata gidane gaba daya,
ya 6ata rayuwar aure data maigidan da 'ya'yansa
har da ita kanta matar.
A dan iya shekarun da nayi, naga matar data
kashe kanta saboda kishi, wai bazata zauna da
kishiya ba.
Naji wacce tanemi ran mijin Allah ya qwace shi.
Naga wacce tanemi sabautashi maqwabta suka
kai masa dauki.
Sannan naji wace ta zubawa kishiyar da
'ya'yanta fetur zata saka wuta Allah ya qwacesu.
Naga wace ta saka aka kori mijin daga wurin
aikinsa.
Naga wace take addu'ar Allah ya talautar da
mijin don karya iya aure.
Wata tasa an kashe kishiyar.
Wata tanemi an haukatar da ita.
Wata tanemi sakin matar.
Wata ta sayar da lahirarta gaba daya don kawai
wani dadi maras tushe a duniya.
kai ni naga wace ta saka 'ya'yan kishiyarta a
gaba, bata qaunar jin alherinsu.
Wai dacewa duk wadannan suna ganin abin da
sukeyi daidai ne.
Irin wannan yasa magabatanmu Allah yasaka
musu da alkhairi maganarsu a ranar budar kai
tafi qarfi wajen hana mummunan kishi.
Shiyasa Abdullahi bn Ja'afar (R.A) yayiwa 'yarsa
nasiha a ranar kaita daki dacewa:
"Inayi miki kashedi da kishi domin mabudin saki
ne.
Kul da yawan zargi don yakan kawo qiyayya.
Kisaba da tozali"
Kishi yakan wargaza gida ne.
Shiyasa yazama dole a wajen mace tagari ta
nesance shi.
Macen data kamu da wannan cutar ta kishi zaka
riske ta kullum a cikin tsoron cewa wata zatazo
ta qwace mata shi.
Shin me wancan take dashi da ita bata dashi ???
Me wancan takeyi da ita bata iya ba, ko kuma
bazata koya ba ???
Idan budurci ne shekara Daya tayi yawa zaku
zama uwaye.
Idanma ke kin sanshi samada ita, kin gaje gidan
da 'ya'yan farko, ashe itace zatayi kishi dake.
Meyasa kike kishi da ita ?
Haqiqa kishi ba qaunar miji bane, kawai shakka
ne da tsoro na rashin mijin.
Wato galibi mata basu da sakankancewar zuciyar
mijin a kansu, don haka zasu kadaita hankalinsa
akansu koda arziqi koda tsiya.
Matan Annabawa da sahabbai sunyi kishi, amma
nason ace mijin ya amfana dasune kawai, na
neman yardar mijin ne a lahirance, kowa tana
qaunar samun lada.
Shiyasa wata ta iya kyauta da kwananta, don ba
shine matsalarta ba, aljanna take nema tareda
manzon rahama, ko kin fahimci Hausata ???
Ku biyoni a darasi na 6.
Insha Allah. adsense 2 here
Share:

1 comment:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *