Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Sunday, July 19, 2015

JURIYAR MACE TAGARI

adsense here 29321-5.jpg

ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮﺣﻴﻢ
ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﻭﺳﻠﻢ
Mace tagari fa tsayayyiya ce, tasan yadda zatayi
maganin matsalarta da kanta, a maimakon
neman a saketa ko kuwa lallai wata ta fita, zatayi
bakin qoqarinta ne domin taga rayuwar aurenta
taci gaba ta hanyar warware matsaloli da sa6ani.
Takan jure bushewar zuciyar mijinta, ta daurewa
daukar kura kuransa, domin kar gidanta ya6aci.
Mace tagari takan lura da duk canjin da tagani
daga mai gidanta, don haka sai tafara binciken
yadda zata warware matsalar.
Bana mantawa a rayuwar makaranta nata6a
zama da wata 'yar ajinmu wace aka gaya min
wani abu maras dadi game da ita, nayi qoqarin
6oye mata, amma da muka hadu saida tagano ni
duk kuwa da dariyar dana riqa yi, wannan abu
yajawo hankalina na tambaye ta yadda tagane,
sai tace min itafa MACE ce kuma tana tare dani,
kar nazaci surutu kawai takeyi dani batasan
komai daya shafe niba.
Sai nayi mata nasiha akan abinda aka gaya mini.
Don haka nake ganin ba macen da zata zauna da
namiji batasan abin da yake sakashi fushi, murna,
tunani, sha'awa ba sai bankaura.
Mace tagari takan zauna da maigidanta a lokacin
sa6ani don gyara baya, takan manta da
MUGWANCIN da yayi mata idan ta tuna da irin
wahalhalun da yakeyi da ita da 'ya'yanta, takan
gano cewa saki ba shine mafita na farko ba, sai
an rasa yadda za'a yi tukun.
Annabi (S.A.W) yana cewa:
ﺃﻳﻤﺎ ﺍﻣﺮﺃﺓ ﺳﺄﻟﺖ ﺯﻭﺟﻬﺎ ﺍﻟﻄﻼﻕ ﻓﻲ ﻏﻴﺮ ﺑﺄﺱ ﻓﺤﺮﺍﻡ
ﻋﻠﻴﻬﺎ ﺭﺍﺋﺤﺔ ﺍﻟﺠﻨﺔ .
Duk macen data roqi mijinta saki haka kurum to
qamshin aljanna ya haramta gareta.
Ahmad,Abu Dawoud, Tirmithiy, Ibn Maja da
Darimiy suka fitar.
Ya Inganta.
Kaga kenan mace tagari takan nemi sakine a
lokacin da kowa ya tabbatar da cutarwar da yake
mata, amma ba don kawai tagaji da zama dashi
ko batason wani abu da yakeyi ko don yaqi cika
mata wani alqawari ba.
Aure sunna ce da Annabawan Allah duk sukayi, ya
kamata mugaya matansu suka zauna dasu ???
Bai dace ba kowane mutum ya riqa jin matsolinki
da mijinki, sai in abin yafi qarfinki.
Mace tagari mijinta shine komai, koda bai iya
soyayya ba.
Bata zama a gabansa ko gefensa saida yardarsa,
takan cika da ladabi aduk inda yake, takan nuna
masa qauna sosai ta gaskiya ce ko qirqira ce
kawai.
Idan zai fita qafarsa-qafarta, idan taji yashigo ta
tarbo shi cikin fara'a da annushuwa, nan da nan
tafesa turare ta shafawa lallenta mai yafito sosai
ta danyi kwaskwarima, ta canja murya tareda
yawan murmushi da fari.
Idan zai fita addu'a, in yadawo godiya da murna
da farin ciki.
Mace a kullum mai sanyaya raice ba mai jiran a
sanyaya mata ba, farin cikin maigidanta shine
nata, komai yabata takan gode, ga fadin yi haquri
kamar nunfashinta.
Tana fama da baqin ciki amma tayi dariya,
tanajin zafin abin da mijin yayi mata amma tayi
tunanin yadda zata faranta masa rai.
'YAR UWA IN KINA BIYAYYAR AURE DON MIJINKI
NE TO KITSAYA HAR SAIYA GODE, IN KUWA
KINAYI DON ALLAH NE TO YANA GANIN ABIN DA
KIKEYI BAZAI WATSAR DA AYYUKANKI BA.
Allah kabamu ikon yin amfani da abinda muka
karanta.
Sai mun hadu a darasi mai zuwa.
Insha Allah.

favicon.ico adsense 2 here
Share:

2 comments:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *