Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Tuesday, July 21, 2015

KIGYARA KANKI

adsense here baana.jpg

Yanda Amarya ya kamata ta kasance. ranar da
za'a
kaita dakin Angonta
*************************************
Yanada kyau Amarya tayi fesss da ita tayi kwalliya
sosai tayi tsaf-tsaf
Sannan tayi duk wata Addu'a da ta iya don kare
kanta daga shidanu
Musamman ya kamata Amarya ta karanta
Qulhuwallahu Ahad, da Falaqi da Nasi, da Ayatul
kursiyyu, da Amanarrasulu da sauransu
Bayan duk ta karanta wadannan a gidansu kafin a
kawota gidan miji da niyyar kariya daga shaidanun
mutane da aljanu!, to yanada kyau ta daura Alwala
irin ta sallah sannan A rankayo zuwa gidan
mijinta,
Bayan duk tayi haka da anzo da ita kofar gidan, to
ta shiga gidan da qafar dama tare da (isti'aza da
basmalah don neman tsari) sannan tayi sallama in
zata shiga gidan koda kuwa ba kowa
Haka kuma ta shiga da dakin nata da sllama in
zata
shiga wanda zata zauna a ciki
To shi ango fa?
______________________________
Shima yakamata ya caba Ado wanda yasan ze
qayatar da Amaryarsa sannan shima ya shigo
gidan
da qafar dama sannan yayi mata sallama ya shiga
Amma fa Ango kar ka manta ba hakanan zaka
shiga ba ba wata 'yar leda a'a yana daga cikin
tsarin musulumci ka shiga da wani abu na ci Ko
nama, ko kifi, ko Naman kaza, ko tsire, da dan
kayan tsotse-tsotse me dadi wanda za'a ci a sha
ayi Nishadi ayi hira irin ta masoya
Amma fa kafin ayi wannan ciye-ciyen da shaye-
shayen A tsarin Musulumci bisa koyarwar Manzo
(s.a.w) Ango da Amarya zasu fara yin Alwala ne
suyi sallah raka'a 2 ta nafilah don godewa Allah
idan suka idar sai ya dafa kanta yace; Allahumma
inniy As'aluka khairuha wa khairu ma jabaltaha
alaihi wa a'uzu bika sharraha wa sharru ma
jabaltaha alihi
Fassara (ya Allah aina roqonka Alkhairinta da
Alkhairin da ka ginata akansa, kuma ina neman
tsarinka daga sharrinta da sharrin da ka ginata a
kanshi)
Anan zamu tsaya se a darasi na gaba zamu dora
daga inda muka tsaya da yardar Allahu
Allah yasa mu dace Ameen
Daga Zamantakewar Aure ga ma'aurata/whatsap adsense 2 here
Share:

5 comments:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *