Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Sunday, July 19, 2015

NASHA NONON MATATA MENENE MATSAYIN AUREN MU ???

adsense here clickmaster20dady-1.gif

MALAM NASHA NONON MATATA MENENE
MATSAYIN AUREN MU ???
Don Allah malam ya matsayin mutumin da yasha
nonon matarsa, ya aurensu yake ?
(Daga Hamza Sa'eed).
AMSA:
======
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.
Allah madaukakin sarki ya halatta maka jin dadi
da dukkkan bangarorin jikin matarka, in banda
dubura ko kuma saduwa da ita lokacin da take
haila.
Saboda haka ya halatta ka tsotsi nononta
mutukar babu ruwa aciki, amma idan akwai ruwa
aciki, to malamai sunyi sabani akan halaccin
hakan zuwa maganganu guda biyu kamar haka:
1. Ya halatta, saboda kasancewar nonon da yake
haramta aure shine wanda aka sha kafin yaro
yacika shakaru biyu, saboda fadin Annabi (S.A.W)
.
“Shayarwar da take haramtawa, itace wacce yaro
yasha saboda yunwa”
Kuduba Sahihul Bukhari hadisi mai lamba ta
:5102.
Ma’ana.
Lokacin da ba zai iya wadatuwa ba daga nono,
saboda shine abincinsa, shi kuma wannan ya
farune bayan mutum ya girma don haka ba zaiyi
tasiri ba wajen haramta aure.
Wannan ita ce maganar mafi yawan malamai.
2. Bai halatta ya shaba, saboda koda yaushe
mutum yasha nonon mace tota haramta a
gareshi, domin Annabi (S.A.W) ya umarci matar
Abu-huzaifa data shayar da Salim, don ta
haramta a gareshi, kamar yadda Muslim ya
rawaito a hadisi mai lamba ta: 2636, tare da
cewa a lokacin Salim yariga ya girma, wannan sai
yake nuna cewa idan babba yasha nono to zai yi
tasiri wajan haramcin aure.
Zancen da ya fi karfi shine ya halatta miji ya sha
nonon matarsa, saidai rashin shan shine yafi,
saboda fita daga sabanin malamai yana da kyau,
don neman Karin bayani kuduba:
Bidayatul-mujtahid mujallady na 2\67.
Allah shine mafi sani. adsense 2 here
Share:

1 comment:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *