Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, July 20, 2015

WACE CE******ITA? 58

adsense here computerimages1.jpg

WACE CE ITA..?? 58
Na ABBA-GANA
Ta sa hannu tana qoqarin kwacewa amma ta
kasa ya qara janyota da qarfi saigata saman
qirjinsa, ta daga kai tuni idonta sun cika da
kwalla Dan tsabar azabar da takeji, da qarfin
hali, tace, so bansan kacika wayayyeba sai ka
aikata abinda kake da niyyar aikata wa aikana.!!
yanxu ya gane manufarta tuni ya saketa yayi
tsaki ya fada bayi ya kulle kansa cike da baqin
ciki da nadama, a duniya ba wacce ya raina
kamar iffaat amma itace take gwadamai axaba,
iffaat kuwa tana samu ya saketa ta fita da sauri
ta wuce gida tana zuwa ta fada dakinta ta kulle
tana kukan takaicin rayuwa da mutum irin Yy
farhaan ta daga kai taga hoton Yaya Suhaila da
Yy farhaan sun rungume juna suna dariya tayi
tsaki,ta tashi ta cireshi ta saka a drawer ta
dawo taci gaba da tunaninta har barawo bacci
ya dauketa, bayan ta tashi taje gun mama..
Ah ah yaushe kika dawo?
Tayi murmushi wallahi tun dazu na dawo nasan
kina bacci lokacin shi yasa banma zo natayar
dakeba, okay suka yi tadi mama tana tanbayarta
ta gyara Gidan dakyau kuwa? Dan tasan son jiki
ya mata yawa
Laaa mama kin manta nayi aikatau suka saka
dariya gaba daya, Yaya Ameen ne yazo da Yaya
Ali suka zauna akayi tadin dasu suna cikin
magana Yy Suhaila ta kira...
Sister sorry na sakaki aiki da yawa,!laa kinji dai
Yy Suhaila wane aiki kuma idan ban mikiba
mawa xan yiwa, ta fara godiya, wallahi idan
kinamin godiya zan kashe wayata, to nabari yi
haquri, kin tarar da farhaan a gida?? Wallahi
Naso nace idan yananan ki masa Dan girki,
Tseeeet tayi kamar ruwa ya cita qirjinta yake
bugawa, lokaci daya ta tuna abinda ya faru
tausayi Yy Suhaila ya kama ta Amma bazata iya
fada mataba, hello kinajina kuwa sister? Tayi
xumbur ta dawo daga dogon tunanin da ta tafi..
Inaji Yy Suhaila, to ki bawa mama wayar na
miqawa mama ta tashi tsaye, Yaya Ali ya kamo
hannunta..
bayan sun qare yace wani abokinane yakeson ta
kinma sanshi Nurane mama tace nikam ko
sunansa banaso bare shi na tsani wannan yaron
akwai shegen rawar kai, iffaat tace wallahi nima
mama na tsani Nura kamar me nima dai jabo ba
abarni a bayaba gun tsanar sunan Nura mugu.
Duk aka saka dariya kowa ya tsani Nura Allah
sarki har ya bani tausayi......
**
Goben ranar tinda safe Suhaila tayi waya da iffat
ta gaya mata sun kamo hanya
Guraren qarfe 11 iffat na zaune da mama dasu
yaya da yake yau Saturday, wayar iffat tayi qara
laaaa yy Suhaila hatman sun iso, hello Yy
Suhaila kuna ina? Kun kawo hala?
Taji namiji yace ke sister din Suhailar ce ??
Tace Eh kai waye?
Sorry Dr ne daga Chika, yayar Ki sun sami
accident Allah ya mata cikawa driver kuwa
gashinan kwance ya kakkarye?
Iffaat wata irin qara ta saka ta fadi
sumammiyaaa.... adsense 2 here
Share:

1 comment:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *