Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, July 22, 2015

WACE CE******ITA? 66

adsense here computerimages1.jpg

WACE CE ITA..??66



by

muhd- Abba~Gana



Taci pizzar sosai suna dan labari sama sama
chan ya sako zancen auren ta da farhaan irin dai
yana son ta amince ya nuna mata illar fushin
iyaye akan yayansu, jiki a sanyaye tace mishi ta
amince, Dan murna baisan lokacinda ya tashi
yayi rawaba ya juya itama abin ya bata dariya
nima abba abin ya bani dariya, yana ta saka
mata albarka, yaje jikinsa na rawa ya gayawa
mama da Yy Ali sun ji dadi ko ba komai sun
yanke shawarar idan taqi aminta za'a bar
auren..
*************
Magana ta kowane ban qare ta kan kama iyayen
sai murna suke sunata shirye shirye, amma
amaren kam ko a jikinsu, ana saura kwana biyu
daurin aure saiga goggo da dijee da rukayya
sunzo, koda sukazo iffaat tana skull Dan ita
wannan shirye shirye bai hanata zuwa
makarantaba,
Koda ta dawo bakin qofar dakinta taga wasu
takalmi Masu kama da kito amma dai na
matane, ta shiga dakin saiga su dijee anyi arshe
arshe tsakayar daki da yayanta biyu rukayya ko
yarta daya da ciki ta kallesu ta kwashe da dariya
harda durqusawa qasa Dan dariya, tayi dariya
saida ciknta yayi ciwo suko sun tsaya kallon
ikon Allah ta dago ta qara kallonsu nan ma ta
kwashe da dariya dijee tace ke bamusun iskanci
Dan kin zama Yar birni zaki ijiyemu kina mana
dariya kamar Kinga tutu...!!
ta harareta ta zauna da kyau tana dariyar tace
wallahi mamaki nakeyi wai dijee da Yara har
biyu! Ta qara saka dariya dijee ma sai ta dara,
ta kalli yayan tace amma dai dijee kina dukansu
ko? Rukayya tayi charab ta chabke tace ai
yanzu duk bala'en dije akansune Dan har danbe
tanayi da uwayen yara akansu, dijee tace ke
rukayya banason sharri da zuwa ko gaisawa
ba'ayiba zaki fara mini sharri, nan dai qawayen
suka yini suna tadi suna dariya duk da qauyanci
su bai sa ta gyamacesuba tunda itama chan aka
fito sun cire mata kewa matuqa kuma bata bari
suka gane cewa auren nata sai a hankali bane..muhd-Abba~Gana adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *