Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, July 22, 2015

WACE CE*******ITA? 68

adsense here computerimages1.jpg

WACE CE ITA..?? 68






by

muhd-Abba~Gana


Gari ya waye ma amaren farhaan yana jiran
amai breakfast amma shiru har 12 yunwa ta
isheshi ya duba ko ina ba alamar girki sai
hayaniyar mutane, Yakama hanya ya fita abinsha
bai dawoba sai guraren daya na dare bata
damuba cox yan ganin amarya da qawayenta
sunanan sunyi girki sun debe mata kewa, bayan
sun tafi sannan ta fara tunanin ina yaje!? Daya
na dare ya dawo daya shigo tamai kallon
tuhuma tana Palo bai kula da itaba ya wuce
dakinta,
Koda ta shiga ya shiga wanka ta zauna bakin
gado har ya fito ta kalleshi yana goge kai alamar
wankan xxxxxx yayi. Ta fuskanceshi da kyau,
tace ina kaje yau? Gurin abokaina ya bata amsa
yana chire doguwar rigar dake jikinsa dagashi
sai towel bata taba ganinsa hakaba sai yau tsoro
yakamata ta tashi ta koma palo, ranar dai batayi
bacciba zuciyarta cike da tuhume tuhume, sai
guraren asuba bacci yayi awon gaba da ita bata
farkaba sai guraren 12 Subhanallahi yau tayi
lettin lecture dole taje ta nemo abinci ta tashi ta
fita direvan bayanan an ma fita da motar da ake
kaita skull da ita tayi tsaki tafito ta taka sosai
sannan ta sami mai adaidaita sahu ya dauketa
koda taje Al nasiha restaurant abincinda takeso
ya qare aka mata kwatancen wani guri inda zata
sami abincin ta qara tsayawa chan saiga mai
adaidata sahu ta tsayar dashi suka tafi sun isa
gurin tace ya jirata ta fito tana zaune tana jiran
a hada mata abincin taji ance farhaan, wani rass
taji mace ce ta kira Sunansa ta juyo ta kalleta
ga dukkan alamu tasan ta amma ta manta ina
tasanta Dan kamar ta qara fari yanxu, ta kashe
kunne taji tace Tana xuwa yanxu. Iffaat tace ina
xataje oho? Tana fita tabi bayanta Tana kallo ta
tsallaka titi sai taga ta shiga wata villa a gun,
tayi tsaki, ta dawo abinta ta karbi abinchinta ta
shiga adaidata sunxo daidai villa taga motar da
ake kaita makaranta....
Jiki na rawa ta tsayarda mai adaidaitan tace
Tana xuwa qirjinta kamar ya fito Dan tsananin
tashin hankali wata zuciya tana kije wata na
fadin kada kije, haka ta shiga gurin taje gun
Masu coffee ta nuna musu hoton farhaan
mutumin ya gaya mata dakin da yake zama
kullum, taje dakin da qarfin guiwa za'ayi kashin
kai wallahi!
Ta bubbuga farhaan ya taso ya bude mata,
tsaye yayi yana mamakin mi tazo yi anan gurin
ya kalleta mi kikeyi anan ta watsa mai harara
abinda kakeyi shi nakeyi ta shiga dakin ta duba
ko ina ba mace, tazo ta kalleshi karuwar taka
bata Iso bane??
Keeee waike bakida hankaline?? Mutum bai isa
ya fito shaqatawa ba sai ace yaje gun karuwai
wall.......
Sheeee ta katseshi da Dora hannu a lebenta...
da kunnena naji kana waya da karuwarka kana
taxo ka iso tazo kuyi iskancin da kuka sabako??
Ya daga hannu zai wanka Mata mari tuni ta riqe
hannunsa,...

muhd-Abba~Gana adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *