Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, July 22, 2015

WACE CE*******ITA? 72

adsense here computerimages1.jpg

WACE CE ITA..?? 72
Na ABBA~GANA
Tana ganin yabar gurin dama driver yana gurin
tamai waya tace yayi sauri ya dawo da mota
gida yayi gudu sosai farhaan kam traffic ya tsare
shi a hanya ga uban go slow ya biyo ta PZ shi
kuwa driver ta by pass yabi kamin farhaan ya
kawo tudun wada tuni an dawo da motar gida
yana shigowa gida yaga motar, yana huci Kamar
kasa tana zaune a Palo ta saka fura gaba
tanasha yana xuwa yasa qafa yayi ball da furar
gaba daya ya finciko gashin kanta ya wurgata
saman kujera, yazo Dai dai da ita zai kasheta da
mari ta wani riqe hannunsa da qarfi, tayi tsaye
saman kujerar wallahi idan ka mareni ba mijina
bane ko waye kai sai na rama...
A fusace yace ke Dan ubanki ubanwa kike yiwa
kwalliya kina kina fita?
Ta watsa mai harara tace ubanda ya
chanchanchi na yiwa kwalliya shi nake yiwa.! Ya
daki iska ya juya yana huci iffaat ni kike yiwa
rashin kunya?? mi kike zuwayi a Zaria hotel? Mi
kikiye achan?? tsaki ta masa ta diro daga
kujerar ta kama hanyar dakinta ya biyo ta
kinsan Allah wallahi idan bakiyi magana zan iya
kashe ki iffaat wallahi xan sallantar da
ruwuyarki..!!
tashin hankali lallai farhaan yafi iffaat kishi
hadda zancen kisa ta bala'en jin tsoro ta juyo ta
kalleshi taga yanda yayi wani iri dashi, tayi sauri
tabi gefensa ta fita bata tsaya ko inaba sai
Gidan su farhaan tana zuwa ta fada jikin umma
tana kuka... Akayita tambaya amma ba amsa
umma ta kira farhaan tace maxa yaxo tana
Neman sa ya kuwa zo, umma ta fara tambayar
sa mi ya mata haka duk ta firgice shiru yayi ya
kasa magana umma ta dakamai tsawa ya mata
bayanin komai tsaki tayi, rudadden banxa wai kai
mi yake damunka ne? Ko kunya bakajiba Dan
Allah kace ka ga mota amma baka gantaba
kuma ka dawo ka tarar da ita gida, haba wane
irin shirme ne wannan umma wallahi har
kwalliya fa takeyi.! Umma tace to mace a Gidan
mijinta batayi kwalliya idan batayi kwalliya ba mi
kake son tayi kaji shiriritar banxa, kai waya gaya
maka haka ake kishi da hauka, ka bari sai ka
tabbatar sannan ka yanke hukuncin waima kai
uban me kakeyi a Zaria hotel? Da har kaje kayita
ganinta? Ya Sosa kai iffaat data narke jikin
umma ta dago ido ta saci kallonsa ya duqar
dakai, yace umma baqi nake saukewa a gurin.
Tayi tsaki wallahi ka shiga taitayinka. kada ka
qara daga mata hankali da haukarka kaji na
gaya maka sannan duk abinda kakeyi ka bari sai
ka tabbatar sannan ka yanke hukunci farhaan
kam ya rasa bakin magana umma ba fahimtar sa
zatayiba tonon asiri ne ma zai yiwa kansa idan
yace zaiyi ma umma bayani har ta gamsu,!!
akace ta tashi ta bishi ta sa kuka ita bazatajeba
dole umma tace ya tafi gobe ya dawo ya tafi da
ita,
Na gaya muku iffaat fa taji tsoro matuqa taji zai
kaita lakhira...
Dole ta chanxa wata hanya...
Muje zuwa muji hanyar da zata komawa.

by
muhd abba gana adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *