Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Thursday, September 24, 2015

KALLO***DAYA-3

adsense here kallo-daya.jpg

KALLO DAYA

3


washe gari hanadi ce rikeda umma dake murkususu a tsakar daki tana kuka saboda ciwon umma daya tashi gashi yaya jafar bayanan umma tayi wani irin mika nan take ta suma a gigice hanadi ta fita da gudu tsabar rudewa ma ko dan kwali babu a kanta ballantana nikab tabi layin gidansu neman taimako, karaf taji ta bangaje wani tayi taga taga xata fadi yayi saurin rikota jikinshi a gigice tace Kati hakuri bansan da mutum ba cikin sanyin muryarta mai dadin saurare dago kanta tayi sai karaf idanuwansu suka sarke ana juna a ranshi tasbihi yayima Allah wanda ya halicce wannan kyakkawar fuska ba wani bane illa ya HYDAR kafin ya dawo daga dunyar tunani ya nemta sama da kasa ya rasa nan take xuciyarshi ta kamu da wannan yarinyar da yayima KALLO DAYA tak! A fili yace kodai aljanace sbd kyaun yarinyar gashi kuma y nemeta sama da kasa ya rasa. Cikin tsaananin sanyin jiki ya juya
A bangaren hanadi Kuma gida ta koma anan ta taradda yaya jafar da umma zaune ciwon ya lafa cikin farin ciki ta rungume umma tana hawayen farin ciki umma tace auta kuka ya kare koh tayi murmushi kawai ta tashi ta dauko nikab dintah ta daura xamanta keda wuya saiga yaya hydar yayi sallama cikin husky voice dinnan nashi a take taji gabanta ya fadi ta sunkuyar dakai kallo daya yayi mata ya dauke kansa a ranshi yanajin muguwar tsanarta tareda tunanin aljanar yarinyarda yayima kallo daya .a ranshi yace munafuka suka gaisa da umma tareda tambayarta ya jiki da amsa da kulawa daganan ya ajiye mata manyan ledodi guda biyu cikeda kayan dubiya umma tayimai godia tareda sa albarka suka fita tareda ya jafar domin xuwa masallaci kasancewar magriba ta kawo kusa itama hanadi ta mike tareda mamaki a ranta na irin tsanarda ya hydar ke mata gaisuwace kadai ke hadasu koshi ba kulllum bah tabi baki tayi a fili tace kaika sani.
09039016969 adsense 2 here
Share:

2 comments:

  1. Dan allah ka taimaka min 1da2 na daga kallo daya

    ReplyDelete
  2. dan allah ka posting 3 na kallo daya

    ReplyDelete

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *