Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, October 26, 2015

RAYUWAR***FAUZIYYA-10

adsense here rayuwar-fauziya.jpg

10RAYUWAR (FAUZIYYA) Part (10) Cigaba 10.
Kwana 4 da Auren Fa'iza Nuraddeen ango
yakoma khairo wai akwai abinda zaiyi yadawo
bazai dadeba. Tunda akayi auren tsahon wata 2
banta6a zuwa gidanba sbd Mama tacemin
batason zirga-zirga sbd karna kashe mata aure
amma fa su suna zuwa musamman da sukaga
mijin baya gari, yadda Fa'izan naga tanamin
waya akan yaushe zanzo yasa nafad'awa Mama
duk ranar da zasu ina neman izinin binsu ta
amince, munje tanata murna da ganinmu
musamman ma ni gsky nayi Mamakin Fa'iza
azuciyata nace dama Fa'iza zata iya nutsuwa
haka? Lallai aure yafi 'karfin komai. Gidanta
yayimin kyau sosai na yaba 'kwarai har santin
nawa yafito fili, mun ci mun sha harda guzuri
muka taho gida. Nura ya shafe kusan wata 3
akhairo kafin yadawo gida, nadad'e ina mamakin
Tuzuru kamar Nura amma aure kwana 4 kabar
amarya, idan yazama dole tafiyar meya hana su
tafi tare? Nasan yana da kud'in dazai iya yiwa
mutum 20 visa lkc d'aya, kuma bayan
dawowarsa zaman gida be dameshi ba kllm yana
waje 11-12amyake dawowa gida tun 8am, idan
yazauna agida to yana tare da abokai inzasu tafi
ya bisu, narasa meye ma'anar hakan gaba d'aya
abin yafara damuna, magana bata 6uya wata
'kawata tashaidamin wai wata 'yar uwar su Nura
taji tana maganar cewa "Yayi mamakin Fa'iza
don ya tabbatar da tayi harka da maza awaje"
abin yad'auremin kai nace ko dalilin da yasa
yake wnnn yawace yawacen kenan, nidai nabar
magana ban fad'eta ga kowa ba nasan wata'kila
sharrine towama zan fad'awa. Babban abin
tashin hankali da mamaki ba afi wata 5 da
Aurenba Fa'iza tayomin wani txt kamar haka:
"Fauziyya kitaimakamin aduniya bani da 'yar uwa
kamarki, ko mama akwai sirrina da zaki sani
bata sani ba, mijina yana mu'amala dani ta inda
ALLAH ya haramta, na amince masa don gudun
6acin ransa wllh yanzu wajen ya kumbura sosai
jini da ruwa yake fitarwa bansan yazanyiba, 'yar
uwa kitaimakamin karki bari kowa yaji hatta
Mama ma wllh ina cikin mawuyacin hali
Nagode." adsense 2 here
Share:

1 comment:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *