Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Friday, November 20, 2015

KAUNA CE SILA*** 4---5

adsense here kauna-ce-sila.jpg

[8:26AM, 11/21/2015] Bana: KAUNA CE SILA 4












MUHD-ABBA~GANA







bayan taci abinci tayi sallah na fada mata ina so don Allah naje gidan yayarta nayi kamar sati daya Zan gaishesu na kuma fada musu na gama lafiya tace to bakomai bayan kwana biyu da dawowar mu mahaifinmu ya dawo ya sauka a gidan mun yi murna sosai daganina sannnan shima yayi min nasiha mai ratsa jini.lokacin ne ma yake fadamin cewa dama y ahanani sauraran samari ce don ban kammala karatuna ba amma yanzu ina da dama kula duk wanda nake so amma ba hakan yana nufin na kawo masa kare da doki gida ba na kula sosai don nasan halin shi ya kuma cewa sakamakon ku yana fitowa zan nemar miki gurbin karatu sai ki zama cikin shiri nace to na gode har na tashi zan tafi sai yace ga wannnan naki ne na karba ina godiya ina shiga daki na bude sai naga wani kwali mai kyau karami ashe waya ce mai kyau kirar panasonic gaskiya wayar tana da kyau sannnan da layi n glo na bude ina ta murna umma tace lalle to an gode sai ayi mata caji tukunna koh nace to bakina yaki rufuwa dan murna wai nice da waya yau a wannnan ranar ne mauna zaune nida umma a tsakar gida muna hira naji sallamar wani yaro dan makotanmu yana cewa wai ana sallama da mamaa nace inji ea kuma sai yace jibirne nace wa umma kai da alamar ban ji dadin kirana ba sai umma tace tashi kije ai gaisawa zaku yi na tashi don nemo mayafin kayan jikina jibrin wani dan layinmune daya dade yana cewa yana sona tun ina makaranata na sha ji ana fada idan nazo hutu a bacin yan unguwa wai yana cewa ni zai aura ni dai sai dai nayi murmushi yau ya kai yi min kwanta idan yaga ina siyen abu a...








MUHD-ABBA~GANA






www.abbagana.pun.bz
[8:31AM, 11/21/2015] Bana: KAUNA CE SILA 5








MUHD-ABBA~GANA





Waje ko shago haka bana kawo komai idan nayi la akari da yanda yan layin mu muke zaune kamar uwa daya uba daya na fito na sameshi a kan dakalin makwaftanmu nayi masa sallama ya amsa da fara a yace min mamaa ina wuni nace lafiya daga haka ban sake cewa komai ba yayi dan jan numfashi kadan yace mamaa kamar bakiji dadin zuwana ba ko nace a'a me ka gani yace najiki shiru ne nace to mai zance yayi dariya yace dama nazone na miki murna sannnan na kara jaddada miki ra ayina akan ki gaskiya ina sonki kuma in Allah ya yarda aurenki nake so nayi a take naji gabana ya fadi ba tare da nasan daliliba amma ban bari ya gane ba nace Allah ya mana zabi mafi alhairi yace ameen nace masa kaga hadan kamar ruwan za a fara bara na shiga gida yace min to ga wannnan ya miko min leda nace ka barshi na gode yace wallahi sai kin karba na karba ina masa godiya ina shiga na tarar da umma tana t tattare kaya don har an fara iska da alamu yayyafi na shiga na ajiye na fito ina tayata da safe da muka tashi ranar juma'a ne t fito zata tafi nace mata ga abin da ya bani jiya tace me yasa kika karba? nace wallahi rantsewa yayi tace shi kenan amma gaskiya bana so ki saba da karbar abin samari dan haka hatsair ne babba nace mata to zan kiyaye da yamma nayi wanka nayi kwalliyar juma'a nayi kyau gaskiya sosai don wata atamfa na saka mai ratsin purple a jikina










MUHD-ABBA~GANA


09039016969



www.abbagana.pun.bz adsense 2 here
Share:

2 comments:

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *