Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Sunday, November 22, 2015

KAUNA CE SILA***6--7

adsense here kauna-ce-sila.jpg

KAUNA CE SILA 6










MUHD-ABBA~GANA








yafa mayafi purple na sake bakin takalmi dama ni bana saka plat sai mai tudu ko don bani da tsayi ne sosai amma dai irin takalma na kenan dana fito nacewa umma ni zan tafi tace to ki gaida mama marayam da maryam din amma kar ki kai magariba don Allah gidan su maryam na nufa na shiga da sallama na ganta a tsakar gida tana karatun littafin hausa nace mata har an fara ta tareni da dariya muka shiga falon su muka zauna t kawo min ruwa na sha muka fara hira tace bari ta zubo min abinci nace mata ai a koshe nake don yau ko abincin dare ma bana jin zanci tayi dariya nace mata yana ji gidan shiru tace min duk sun tafi kamu wata yar uwarmu ni suka bari da girkin dare nace ai gara da na sameki na mika mata wayata ta fara daddannawa tana murna tace yauwa ai yanzu kin zama babba ta dauko wayarta ta saka number ta ta kira naga tana yin sarving anan ne nake bata labarin yanda muka yi da jibrin tace toko shi ya sai miki nace a'a ubana ne tayi dariya tace iyye ashe mun kusa shan biki nace dawa din? nifa bana sonshi tace meyasa? nace nifa kinsan nafi son dan gayu kuma mai ilimi tace au shi ba gaye bane? nace gaskiya ba sosai ba muka tafa tare muna dariya munyi hira sosai da maryam wadda rabi ta samarice har take cemin ina fa wallahi duk tafi son wanda yake wasan hausa nace mata to Allah ya taimaka










MUHD-ABBA~GANA

09039016969





www.abbagana.pun.bz





KAUNA CE SILA 7









MUHD-ABBA~GANA




bayan ta rako min nake fada mata cewa zanje jos gurin yayar ummanmu amma kafin na tafi zanzo muyi sallama tace to zata kira nima nace mata to tace dan Allah ki gaida min umma sosai kafin nazo tace to ranar ne da daddare ummi take fada min babnmu yace na shirya ranar lahadi na tafi jos din nace mata to ina murna,bayan sallar ishai yaro ya shigo yace wai jibrin yana kirana haka naje kmar yanda na saba fuska taba yabo ba fallasa na zauna tare da sallama bayan mun gaisa na dan daure fuska nace jibrin ashe dama kaya ka kawo min har kala uku to gaskiya ni bna so kawai sai ka hau kawo min kayan sakawa yayi yan dariya yace haba mamaa nifa nake fatan zama mijinki idan nayi miki ai kaina nayiwa ko? nace masa eh duk da haka dai yace tro amma fa a min afuwa nace shikenan washegari na fito zanje wanki kawai sai muka hadu da jibrin sai na dan sunkuyar da kai na kasa nace masa ina wuni yace lafiya ina zak haka nace saloon yace muje na rakaki nace a'a ka barshi na gode yace shikenan har ya dan yi gaba sai nace masa au gobe zanyi tafiya zan je jos gurin yayar mamanmu yace amma shine ba ki fada min ba nace kayi hakuri na manta yace ba komai sai nazo da daddare nace to da daddare yazo kamar yanda ya saba haka na karasa na zauna muka gaisa nace masa ga number ta.










MUHD-ABBA~GANA

09039016969






www.abbagana.pun.bz adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *