Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Sunday, November 22, 2015

KAUNA CE SILA***12---15

adsense here kauna-ce-sila.jpg

[9:36AM, 11/22/2015] Bana: KAUNA CE SILA 12











MUHD-ABBA~GANA





dan shiga gida na rasa me yake min dadi gashi dai ba son jibrin nake ba amma a hakikanin gaskiya ban ji dadin irin sallamar daya zo ya min ba duk da nasan ba laifinsa bane mahaifina ne bai amince dashi ba ina kwance har aka kira sallan magariba ina ta tunani iri iri na tashi nayi alwala dan yin sallah ina idar da salla sai na tsinci kaina da addu'ar Allah yasa haka shine mafi alhairi kuma wai sai gani ina hawaye ina addu'a a ban san kukan me nakeyi ba abin dai dana sani ko bana son jibrin mun saba dan shi kuma yana nuna kulawarsa a kaina wani ikon Allah tun daga wannan ranar na manta da al'amarin jibrin na ci gaba da harkar gabana duk da nakan ji abin da yake ciki kamar ranar daya kai kudi da ranar da aka sa masa rana da sauransu MAMAA nidai sunana sa'adatu i muhammad an haifnine a tarauni kkuma nayi primary school dina a nan tarauni na fara karatuna na secondary a unity college kachako bayan nayi shekara uku na zana jarabawar science na tafi girks science college garko na karasa inda na gama a can matan mahaifina biyu ummanmu ce ta farko sai antinmmu amma ba gida daya suke ba( dan gudun barna) ummanmu tana tarauni kishiyar ta kuma tana kundila mahaifiyata mu biyu ta haifa daga ni sai kanina abubakar sadiq ita kuma kishiyar ummmanmu tana da yar uku salima,salim da salis anfi sanina da mamaa dan da shi ake kirana saboda sunan mahaifiyar babbanmu aka saka min niba baka bace ba zan kuma saka kaina a layin farare ba amma ni nasan kala ta tana da kyau dan gaskiya irin chocolate colour din nan ce dukk man da na shafa sai dai yasa na yi kyau dan bana amfani da mayukan kara fari don bana son abinda zai bata min fiska balle ma rayuwata.











MUHD-ABBA~GANA







www.abbagana.pun.bz



KAUNA CE SILA 13










MUHD-ABBA~GANA







dan bani da kuraje ko kadan a fuskata baza a kira ni kyakkyawa ba amma ina da shi daidai nawa ina da diri bani da tsayi amma ina da jiki ba can ba na iya kwalliya dan duk kayan da na saka sai ance nayi kyau ina da fara'a da yawan wasa da dariya ina da idanu masu kyau da daukar hankali dan na sha jin mutane suna fadin cewa irin idanuna ne ake cewa sexy eyes wasu kuma sunce na iya kallo na sanya nutsuwa to ni dai abin da na sani nima na yarda idanu na suna da kyau, ina da matukar hakuri amma ina da saurin fushi da kuma saurin sauka don ana yi min abu zan nuna bacin raina amma dana nuna ya wuce don bani da riko ba kuma na iya boye abu a zuciyata ba kuma ni da rufi ina kuma da saurin sabo da saurin yarda da mutum wannan kenan.


haka muka cigaba da rayuwa cikin farin ciki da nishadi har sakamakon mu ya fito yayi kyau ba laifi anabln muka siyi forms maryam ta sayi legal ni kuma babanmu ya kawi min na kano state polytechnic haka muka cike muka mayar muka zauna jiran admissiion a haka dai kusan kullum muna tare da maryam ko dai a gidani su ko a gidanmu maryam tana da samari sosai amma tafi son wani dan film din hausa mai suna sani tana matukar sonshi shima yana nuna mata kauna don kusan kullum in dai yana gari to sai yazo wani lokaci tare suke zuwa gidanmu muyi hira tare nima samari su kan ce suna sona amma tunda na rabu da jibrin hankalina duk ya bar zauce su yanzu nafi tunanin karatu dan shine a gabana wata rana muna zaune a dakin maryam muna ta hira sai nace mata kin san meye? tace a'a nace nifa waka nake so na fara tace kamar ya? nace waka dai ta film da kika sani.







MUHD-ABBA~GANA







www.abbagana.pun.bz


KAUNA CE SILA 14









MUHD-ABBA~GANA







tace ke mamaa dan kina dan yin waka a makaranta shine kike ganin zaki iya to wai ma yaza kiyi da karatun naki baba ma zai barki ne nace mata ai addu a nake kuma duk hadawa zan yi tace lallai abin naki babba ne nace mata ni dai malama idan zaki hadani da sani yayi min hanya to tace ba damuwa idan yazo zamuyi magana nace da kin kyauta muka yi dariya na tashi na ce mata zan tafi tace to ta rakani na hau mashin na nufi gida a wannan ranar da daddare bayan sallar isha i muna zaune a tsakar gida sai naji sallamar maryam ta shigo suka gaisa da ummanmu sai naja ta daki nace ya aka yine? tace uhum kya sani dai yana mota yana jiranki kije yayi miki interview nace kai na zaro idanu sai naga tana dariya tace au kin fasa zama mawakiyanne? nace to shi ne har da wani interview kamar wani akin gwamnati ko aikin kudi tace lallai yarinya wasa kikeyi nace mata ni dai gaskiya ba zanje ba tace ke wasa nake mamaa Allah na fada masa shine yace muje ya ji dai daga bakinki nace to muje amma fa gabana faduwa yake kuma maryam ta gane duk da ban fada mata ba a mota muka same shi yana ta danna waya yana ganinmu ya ajiye nace masa ina wuni yace lafiya hajiya mamaa ya hutu nace hutu sai ku.











MUHD-ABBA~GANA






www.abbagana.pun.bz
[9:41AM, 11/22/2015] Bana: KAUNA CE SILA 15


MUHD-ABBA~GANA



yayi yar dariya yace to mun gode Allah kawarki tace min kina so ki fara waka haka ne? nayi shuru maryam tace shiru ko ba haka bane? nace haka ne cikin wata murya mai nuna akwai tsoro a tare da ni yace toke me yasa kike so ki fara waka? nace kawai ina so don ni mawaka suna burgeni ina so naji ina son wakokin su yace to shikenan niba harka taba ce duk da kusan duk daya ne amma kanina yana yi sosai xan hada ku zakiyi insha Allah komai zai zo miki da sauki nace masa to na gode yace ba damuwa ai ke babbar kawarmuce ya kalli maryam da yana yin tsokananta maryam tace bara mu tafi za ki ji ni a waya nace mata sai da safe ki gaida mama tace zataji suka juya suka tafi duk abin nan da ake ciki ba wanda ya san halin da nake ciki daga ni sai maryam munyi kamar kwana biyu bamu hadu ba kuma ba muyi waya ba ranar wata juma'a sai ta kirani a waya tace to ki shirya dan ifan yace yaushe kike da lokaci da zai fara koya miki waka sai nace ni ai ko yaushe sai tace to shikenan tunda gobe asabar ba aiki zance masa ku hadu a gidan mu da yamma amma fa ki zo da wuri kar ya riga ki zuwa nace mata to ina kashe wayar sai naji wani nishadi da karfi yazo min kawai sai nake ganin ai kamar ma na riga na iya.da safe na tashi naji ni ina ta jin dadi bayan mun gama komai na al'adar gida da......




MUHD-ABBA~GANA


www.abbagana.pun.bz adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *