Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, January 6, 2016

NA DAINA SO!! 26 & 27

adsense here na-daina-so.jpg

[8:19PM, 1/4/2016] abba gana: NA DAINA SO 26






Muhd-Abba~Gana






kin tabbata? shakka bbu na tambaye ki mana Allah yasa na sani sai da ya dan yi jin kafin yayi magana tun yaushe kika fara son yusuf? gaskiya an dade tun lokacin da kuke karatu a birni amma ya akayi ban sani ba? ba tare da ya shirya ba kawai ya ji yayi wannan tambayar saboda yawanci a hanya muke haduwa kin tabbata kina sonshi sosai? ina son shi fiye da yadda nake son rayuwata a zuci taso ta furta hakan amma muryarta taci amanarta yaya kabir ina so ka taimake nina auri yusuf domin ina kaunarsa fiye da yadda kake zato ina alfahari da kai na san cewa bani da dan uwa kamar ka mai kaunata kuma mai kaunar abinda nake kauna don haka ka taimaka ka tsaya kai da fata don ganin cewa yusuf ya zama mijina don idan ba yusuf ba.......' kasa karasa maganar tayi to amma alamun da kabir ya gani a fuskar mairamu ya taimaka masa wajen karasa maganar a zuciyarsa .....idan ba yusuf ba zan taba yin aure ba idan ba yusuf ba ba zan taba jin dadin rayuwar nan ba ...........idan ba yusuf ba mutuwa zanyi"" kabir baya son ganin rayuwar kanwarsa cikin tashin hankali a bisa wannan hujja ne kabir ya fasa bayyana wa mairamu sirrin dayayi niyyar fada mata game da rayuwar yusuf.







Muhd-Abba~Gana






www.abbagana.pun.bz
[8:19PM, 1/4/2016] abba gana: NA DAINA SO 27





Muh'd-Abba~Gana






yana fatan Allah ya shiryi yusuf duk wanda ya rufawa wani asiri to shima Allah zai rufa masa kuma mairamu na matukar son yusuf mairamu kin tabbata shima yusuf din yana sonki sosai? kwarai kuwa wani irin tausayi ne ya lillibe kabir tausayin mairamu rashin sani yafi dare duhu inji yusuf a zuciyarsa da ace mairamu ta san ko wane ne yusuf bala........ da ace mairamu tasan dilin da yasa aka kori yusuf bala daga jami'a lokacin da suke tsakiyar karatu...da ace......... a lokacin da mairamu ta bayyana cewa yusuf take so haka kawai mutanen gida suka ji basa son saurayin haka kawai ni saurayin bai kwanta min a rai ba mahaifinta ke fadawa mahaifiyarta saboda me? yana da wani abune? yana ma daga cikin samarin da ake yabawa da halayen su tun da tare da kabir sukayi karatu a birni.





Muhd-Abba~Gana





www.abbagana.pun.bz adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *