Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, September 7, 2016

TANA TARE DA NI...11---15

adsense here tana-tare-dani.jpg

 TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 11
BY MIEMIEBEE

Bayan tafiyan Ya Khaleel bada jimawa ba su Mami suka dawo gida, Fannah na d’aki tana kukan cire rai bata ma ji shigowansu ba kawai ganin Mami tayi tsaye a kanta take ta soma share hawayenta “sannu da zuwa Mami, yaushe kuka dawo?”
          “Habibti kukan me kuma kike? D’an mayen can yazo ne?”

        “A’a ba kuka nake ba Mami, inasu Afrah?”
          “Fannah ga idanunki sunyi ja sun kunbura, fad’a min meneh? Keda waye?”
        “Ya Khaleel ne yazo...” Nan ta irga mata duk abinda yafaru tana kuka.
        Rungumota Mami tayi “Shikenan yi shiru in shaa Allahu Kawu da d’ansa barasu k’arisa da duniya lafiya ba, mugayen mutane kawai bar kuka kinji? Akoi Allah Fannah always have this at the back of your mind, in shaa Allah baraki auri Farouq ba.”

     Hannu tasa ta share hawayenta,    “Mami ni nasan zan auri Farouq ba abinda zamu iya Ya Khaleel yariga ya gama komi.”
      “Fannah kin cire rai daga Allah kenan?” Kad’a kai Fannah tayi “toh ki bar fad’in haka, Allah ba azzalimin bawansa bane. Allah da kansa yace a Qur’ani auren mazinaci se mazinaci aikinsani koh?” Kai Fannah ta giad’a “toh kibar kukan ya iso mik’o mai in taje miki gashinki.” A sanyaye ta mik’e ta d’auko mai da comb mama ta taje mata gashinta takama mata gu d’aya sannan ta bata waje tasa kaya. Itakuwa ta fice zuwa d’akin Baba.

Kwance ta samesa, “Malam ya jikin?”
    Baki na k’yarma yace, “da sauk’i.”
          “Sannu, Malam ko kanada labari d’azu Kawu yazo ya cicci mutuncin Fannah? Duk nazo na sameta se kuka take.”
        “Eh..Mam.. Maman Aiman saisa yazama dole in siyar da gwalagwalen da Umma (mahaifiyarsa) ta tab’a bani dana ajiye kan duk sanda Fannah tazo aure se in sayar mu mata kayan d’aki amman tunda ga yadda abu ya kasance dole mu siyar yanzu...” Tari ya tsaya yayi sannan ya cigaba.
        “K’ark’ashin wancan akwatin akoi d’an kunne da sarqa da zobe dakuma warwaro guda hud’u na gwal, da ace ina da lafiya da a gobe zan jeni Maiduguri in siyar amman gajan haka yasa dole seke zaki Maman Aiman.”

    “Ina jinka Malam, in mun siyar me zamu da kud’in?”

     “Gidan nan zamu bari, garin nan zamu bari gaba d’aya mukoma Maiduguri inason bayan kinje kin siyar da gwala gwalen ki kama mana gida me arha koda 2 bedroom ne kawai wanda zamu iya affording, sekuma da essential abubuwan da zamu iya bu-” tari ne ya tsaida sa sosai.
 
    “Malam shikenan ya isa nagane kar jikin ka ya tsananta. Amman Malam bara mu tafi da kayakin mu ba? Inaga zefi mana sauk’i inda hali ma gidan nan se mu siyar.”
 
     Gyaran murya yayi sosai “inaaa... hakan bame yuwu wa bane Maman Aiman mukayi haka ai kamar mun fad’awa duniya zamu bar garin Bama ne kisani no one must know about this. Fannah kawai na yarda ki fad’a mata itanma dan mu cireta daga damuwa ne kuma ki gargad’e ta karta kuskura ta fad’awa Afrah kar da baki taje cikin jama’a ta tona mana asiri. Dan maganan nan na fitowa fili shikenan namu ya k’are dole Fannah zata auri Farouq, ni na fad’a miki.”

        “In shaa Allah Malam, Allah kaimu goben zan wuce Maiduguri dan kasan matsalar samun gida, in bamu soma nema a kan lokaci ba zamu makara har lokaci ya k’ure we have just a month.”

  **

        “Fannah habibti. Fannah!” Kirar Mami dake tsaye daga bakin k’ofa.
    Sanda Fannah takai k’arshen ayan datake karantawa sannan ta amsa “na’am Mami am sorry bansan yanke ayan ne.”
    “Bakomai karatu kike ne?”
    “Eh Mami wani abu ne?”
     “Ina Afrah da Aiman?”
      “Suna can parlour suna assignment.” Fannah ta amsa a takaice.
           “Oh toh magana daman nazo miki.”
         “Toh bismillah Mami” nan Mami ta k’ariso ciki tare da rufo k’ofar tayi joining Fannah kan katifar sanan a hankali ta sanarda Fannah abinda ita da Baba ke da shirin yi. Sosai Fannah taji dad’i harda hawayen nin dad’i.
   
       “Mami dagaske kike? Zamu koma Maiduguri barin auri Ya Farouq ba?”
         “Sosai Habibti ai dama na fad’a miki koda bamuda komai munada Allah, kuma Allah ba azzalimin bawa  bane kamar yadda na fad’a miki gobe zani Maiduguri.”
    “Toh Mami in bi ki mana muje tare.” Cewar Fannah tana share hawayen jin dad’i.

         “A’a Fannah kinsan Kawunki wane bodyguard haka yake kusan kullum seya zo gidan nan inkuma yazo bani ba ke kinsan dole yayi bincike the moment asirin mu ya tonu kuwa kinga dole sekin auri Farouq. Saboda haka ni kad’ai zanje addu’a kawai zakimin Allah sa inje a sa’a in dawo lafiya.”

          “In shaa Allah Mami Allah baki sa’a. Nagode sosai, keda Baba kun gama min komai aduniya Allah biyaku da gidan aljannah.”
 
         “Ameen Habibti barin koma in had’a akwati na.”
    “Toh muje in tayaki shiryawa.”
       “A’a Habibti zanyi dakaina, go on da karatunki.”
      “Toh Mami.” Har Mami takai bakin k’ofa Fannah ta danna mata kira da    
      “Mami!”
      “Na’am Fannah.” Ajiye Qur’anin dake hannunta tayi ta ruga gun Mami da gudu tayi hugging nata “Jazakumullahu bikhairan keda Baba nagode sosai, Allah sak’a muku da gidan Al-Jannah.”
       “Ameen Habibti Allah miki albarka kema.”   “Ameen” ta ce sannan ta sako Mami tana kallonta har sanda ta shige d’akinsu da Baba. Sujjada tayi tana gode wa Allah sannan tashiga bayi tayi alwala tayi nafila raka’a biyu tare da sake gode wa Allah ji tayi kap matsalolinta sun gushe. Kan katifar su ta fad’a se murmushi take.

**
4 days later...

        “Oyoyo Mami! Oyoyo Mami!” cewar Aiman tana daka tsale. “Oyoyo auta ta” Mami ta d’aga ta sama. Nan su Fannah suma sukazo suka mata oyoyo. Kwanan Mami uku a Maiduguri tadawo, tafiyar ta kuwa was a success kap addu’o’insu Allah ya amsa musu. Kud’in data samu bayan ta sayar da gwala gwalen ta kama musu gidan haya 2 bedroom dashi a unguwar jiddari polo, na shekara, seda katifu guda biyu da d’an kayan abinci da kayan kitchen. Alhamdulillah!

2 weeks later...

      Farouq ne tsaye bakin gidansu Fannah shi a dole yazo ganin matarsa nan da sati d’aya da ‘yan kwanaki zata zama mallakinsa tsabagen iskanci ba abinda yake imagining illa first night nasa da Fannah. Wani almajiri ne yazo wucewa take ya tsaida sa “kai shiga nan kace wai inji Farouq matarsa ta fito.” Da “toh” yaron yashiga gidansu Fannah suna zaune tsakar gida suna tsintar shinkafa ita da Afrah.

    Ita kanta Afrah mamakin yadda Ya Fannah ke walwala kwana biyu ke bata kukan data sobayi safe rana dare yamma duk tadena yanzu, dukda batasan reason nayin hakan ba itade tana ma yarta murnan dawowar farin cikinta.

     “Assalamu Alaikum” cewar almajirin. “Wai inji Farouq wai matarsa tafito” dadai lokacin Mami tafito daga kitchen. “Me kace?”
     “Farouq ne ya aiko ni wae matarsa ta fito.”
    “Dan ubansa kace barata fito ba yaushe tazama matartsa? Fice kabani waje.”
      “Almajiri tsaya” cewar Fannah “kace masa ina fitowa.” Kallo Mami ta watsa mata “Fannah baraki fita ba kinsan wannan d’an mayen yanzu seya saki kuka ki zauna.”
        “A’a Mami kibari inje ai ba abinda ya isa yamin a waje a idan mutane, kiyi hak’uri.” Mami zata sake magana Fannah tace, “please Mami.” Da d’aga kan da Mami tamata Fannah ta shiga ciki ta d’au hijabinta sannan ta fice a zaune ta samesa kan benchi da alama yau ba a buge yake ba.

         “Ke zo nan kizauna yaci ace kin saba dani yanzu, nan da ‘yan kwanaki zaki zama tawa.” A zuci Fannah tace, _taka? never! Allah ya riga ya kare ni daga auren mazinaci kamar ka._ Kawai jin hannun sa tayi kan kumatunta firgit ta matsa baya. Yasake matsowa kusa da ita “wai tunanin me kike haka? Kode tunanin first night namu?” Ya d’an murmusa “karki damu I'll take it easy on you” batace dashi komai ba illa kallonsa da take.

        “Ke wai yau azumin magana kike ne?” Juyawa tayi zata tafi ya danna mata kira cak ta tsaya bata tanka sa ba. “Kiyi sha’aninki iya san ranki kimin rashin mutunci iya san ranki amman kisani nan da sati d’aya da ‘yan  kwanaki ni zanna ja miki aji. You can go daman nazo inga kyakkywar fuskarki ne kafin na wuce bayan gari.” Kai kawai takad’a tashige ciki.

      Tsaye ta tarar da Afrah da Mami da damuwa karara a fuskarsu. “Ya haka Mami wani abu ne?” Ta tambayesu

         “Farouq fa inade be miki komai ba?” Cewar Mami.
        “Kai Mami da Allah ki kwantar da hankalinki Mami, kema haka Afrah ba abinda Ya Farouq yamin banda suratan banzan daya saba wai yanzu haka ma bayan gari zasa.”
         “Shege mazinaci” cewar Mami. “In shaa Allahu baraki auresa ba.”
        “Amman Mami yau fa sauran sati d’aya da kwana uku ne bikin anya akoi abinda ze hana aukuwan wannan aure?” Afrah ta fad’i cike da damuwa.
       “Akoi Allah Afrah, always have this at the back of your mind. Jeki huta Fannah nida Afrah zamu gama girkin.”
       “Toh Mami, ina Aiman tazo mu mata tsifa.”

     _3 days later..._
   Ana saura sati bikin Fannah da Farouq. Ya Khaleel ne tsaye cikin tsakar gidansu Fannah. Mami, Fannah da Afrah suna tsaye kansa. “Toh nide nafad’i nawa tun ana wata bikin nan na fad'awa Fannah ta sanar dake batun gadon nan gashi har yau baku sai ba wallahi zakusha mamaki dan kuwa amaryarku kan tabarma zata kwana. Wasu erin matsiyata ne ku? Ace ‘yarku zatayi aure ko gado kun kasa yi mata? Wai ahaka ma dan na d’auke maku nauyin kayan kitchen. Allah wadar in erinku wallahi.”

        “Kawu kayi hak’uri nan da ‘yan kwanaki zan kwashe adashe na se in sai wa Fannah gadon dan Allah ka k’ara hak’uri.” Cewar Mami.

         “Wannan kuma ku ya dama, ko ku sai gado ko amaryarku tayi kwanan tabarma. Ni na tafi.”

    Yana ficewa Mami taja hannun Fannah sukayi d’aki gudun kar Afrah ta fahimce wani abun. Itade Afrah tasoma zargin abu da a da ne Kawu yayi wannan magana definately Fannah zatayi kuka sega yau ko nuna damuwa batai ba.

   Da daren ranan Fannah da Afrah suna zaune d’akinsu Aiman tayi nisa a bacci. Afrah tafi minti biyu tana kallon Fannah har sanda tasa ta tsarguwa. “Afrah wannan kalo haka?” Cewar Fannah tana duba pages nawani Government text book.

    “Ya Fannah kallen.” D’ago fararen idanunta tayi wanda suka sha bak’in kwalli ta azasu kan Afrah. “Na kallekin” tace. “Kina b’oye min wani abu kinsan na sanki fiye da yadda nasan kaina I can tell in kina b’oye min bu.” Cewar Afrah
 
           “Me zan b’oye miki Afrah? Kawai de inajin dad’i ne.”
       “Dad’in me fah? Dad’in zaki aura Ya Farouq??” Ta tambaya tare da d’age gira.
     Dariya kad’an Fannah ta saki “ko kad’an Afrah ina murna ne saboda inaji ajikina barin auri Ya Farouq ba.”

      “Toh Ya Fannah Allah sa, kinsan happiness naki ya fiye min komai a duniya.” Hugging junansu sukayi cike da so da k’aunar juna.

   
**
Ana saura kwana biyu biki...  
Da misalin k’arfe 8:00AM
      “Farouq! Farouq!” Kiran Ya Khaleel yana zaune kan tabarma. “Na’am Baba” Farouq ya amsa yana isowa sannan yasamu waje ya zauna.
         “Ni ya jiya ka had’u da Fannah kuwa? Mahaifiyarta tace mun cikin satin nan zasu kawo gadon gashi saura kwana biyu bikin naku basu aiko ba. Anya mutanen nan lafiya kuwa?”

       “Ni Baba kawai mu share zancen gadon nan kafa san basuda kud’i ni Fannah ta zamo mata ta shine babba ban damu ba ko kan tabarma zamuna kwana bale ma ai ina gado se in tafi mana dashi.”
    K’eyarsa Ya Khaleel ya tand’e “ai dama kai wawa ne, taya mu zamu masu komai tashi muje gidan nasu yanzu.” Ba gardama Farouq yabi bayan Babansa suka fice zuwa gidansu Fannah.

         “Salamu alaikum!” Cewar Ya Khaleel a yayinda Farouq kuma ke knocking shiru kukeji ba amsa “waiko wannan matsiyatan bacci suke ne?” Ya Khaleel ya tambayi Frouq. “Toh ya zansani Baba inba wai shiga zamuyi ba.” Sa kai sukayi a tare Ya Khaleel na sallama sede har da suka iso tsakar gidan ba amsa dan haka Ya Khaleel yayi d’akin Baba yayi knocking nanma shiru hannu kawai yasa ya bud’e k’ofar yaga d’akin wayam! Daga katifa se katifa ba bakunan kaya ba komai. “Tashin hankali!” ya kira a fili. Farouq dake tsaye tsakar gidan yace, “lafiya Baba?”
       “Ba lafiya ba” cewar Ya Khaleel “zo kaga ba kaya a d’akin nan. Tsaya duba d’ayan d’akin yaran tukunnah” nan Farouq yaje ya bud’e same story. “Nan ma ba kaya Baba.”

            “Tashin hankali! Bade Aliyu da iyalansa sun gudu sun bar garin Bama ba.” Y fad’i cike da tashin hanakli. “Amman ai basuda inda zasu ma, through out rayuwarmu anan mukayi, baida ma kud’in biya masu kud’in mota bale ace ya kama masu gida a inda sukaje. Dole suna cikin garin nan suna b’oye cikin wani gida taho muje mu sami kakanka mu irga masa.”

    Bayan sunje sun samu kaka Ya Khaleel ya irga masa komai. Matuk’a Baba yasha mamaki. “Tunda haka d’an uwanka yayi deciding, mu barsa mu ga iya gudun ruwansa. Mun nuna masa halacci ya nuna mana butulci. Ni badan komai na amince da wannan maganar ba dan kar ‘yarsa ta rasa mijin aure ne amman tunda haka yace se mu barsa.”

        “Haba! Baba haka zakace!? Nida na d’au tsine masa zakayi. Guduwa fa yayi Baba ya bijire wa umarnin ka.”
          “A’a Khaleel ba maganan tsinuwa anan fatan mu Allah sa hakan dayayi shine mafi alkhairi garesa da ‘yarsa dakuma iyalansa gaba d’aya.” Ko “amin” d’inma Ya Khaleel be amsa ba shida yagama sa rai Fannah zata haifo masa kyawawan yara ace sun gudu basu gidansu. IMPOSSIBPLE. “Tashi Farouq yau ko shadda suka shiga suka b’uya semun tonosu bayan nagama bazawa a gari zakayi aure se ace amarya ta gudu wallahi k’arya ne tashi nace. Aliyu be isa ba yau duk inda suke a b’oye sena nemo su!” Baba na k’olla masa kira ko a jikinsa yaja hannun Farouq a fusace suka bar gidan.

   *Masu karatu kui hak’uri yau bansamu nayi typing kamar yadda na saba ba, severe back pain ke damuna in shaa Allah gobe zanyi dayawa. I love you guys!*
 
   *©miemiebee*

 TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 12
BY MIEMIEBEE


Da misalin k’arfe 7:30AM su Fannah suka isa garin Maiduguri daga can suka tsara taxi se sabon gidansu. Ba laifi gidan gaskia yayi arha d’akuna biyu ne da bayi biyu dakuma  kitchen. Fannah takasa b’oye murnanta, finally barata auri Ya Farouq ba.

     Ya Kaheel da d’ansa Farouq kuwa haka kaman zararru suka riga bin gida one-by-one a Bama su a dole suna neman Fannah da family’nta sam hankalinsa be basa Maiduguri su Fannah suka tafi ba. Har dare suna neman su Fannah ganin ba mahalicci se Allah yasa suka hak’ura suka dawo gida disappointedly.

     Fannah kuwa yanzu rayuwa yasoma mata dad’i, a hankali ita da family’nta suke settling a Maiduguri hankalinsu akwance basuda wata tsoro yanzu, Government school me kyau Mami tasamu aka zuba Afrah da Aiman. Fannah kuwa ko kad’an bata sa rai kan zata cigaba da makaranta ba se sanda Baba yayi suprising nata kud’in daya kamata abiya akaisa asibiti ya yafe kan Fannah tayi proceeding karatun ta. Admisson aka nemo mata a Polythecnic course na Business Administration.

         Sosai taji dad’i. Koda ta soma zuwa makaranta kuwa kullum cikin hijabi da nik’af take, mazan makarantar su basu ma san ya fuskarta take ba bale ace su gano kyawunta su soma binta. Haka Allah ya cigaba da yima rayuwar Fannah albarka, karatu take sosai ba wasa, Mami tana d’an sayarda irin gwanjon kaya hakan nan dashi suke cafanin gida. Baba kam jiki se worse yake ba kud’in kaisa asibiti a kullum burin Fannah ta gama karatu tasamu aiki ta kai Babanta asibiti.

     Ya Khaleel kuwa koda ya kira Mami a waya bata d’aukawa haka yagaji ya bari. Rayuwa de alhamdulillah...

   
★★★★
        4 YEARS LATER...
★★★★

             Abubuwa da dama sun gudana a both rayuwar Fannah da na Anas. Fannah tanada k’imanin shekaru ishirin a duniya yanzu. Kyanta yagama fitowa, hips nata da dukiyar fulaninta daidai jikinta beyi yawaba kuma be kasa ba masha Allah. Fannah takai mace duk inda ake neman mace,  shekarunta kusan biyu da gama poly tayi graduating under Business admin da excllent result. Sede aiki ne har yau babu ta kasa samu, duk wad’anda ake bata ba related to course nata bane daga baya dole ta hak’ura ta karb’a aiki as a waitress (me serving abinci ko drinks a shago kokuwa wajen taron jama’a) a wani babban coffee shop. Dad’in abin Coffee shop d’in nasu sananne ne sosai cikin garin Maiduguri yawancin meetings kokuma party ko biki da akeyi a Maiduguri a Coffee shop nasu Fannah ake zuwa a d’ibi waitresses kuma duk lokacin da akayi haka kud’i suke samu sosai. Da wannan take samu ta biya kud’in school fees na Aiman dana Afrah, amman de yanzu Afrah itama tagama makarantar tana neman kusan shekara da gamawa.

       Fannah na k’ok’ari sosai dan tasa Afrah a makaranta sede abun ya gagara, jarin Mami ya jima da karyewa lokacin da jikin Baba yatab’a yin tsanani dole ta tattara ribanta da uwarkud’in business natan duka aka kaisa asibiti. A takaice de yanzu Fannah ce breadwinner’n family’nta duk akanta sukayi depending. Allah sarki Fannah ‘yar Albarka Allah cigaba da miki albarka, ameen.

       Samari kuwa ba ta kansu take ba, sau afi a k’irga in aka d’ibesu serving food and drinks a meetings alhazai masu ji da naira suka ganta sesun neme ta amman saboda duk sanda ta tuna da past nata, ta tuna bata da  budurcinta martabarta setaji barata iya k’ara yin soyayya ba saboda definately randa aka gano gaskia ita ba budurwa bace za’a guje ta abinda bataso kenan. Bature yace prevention ia better than cure sesa tun farko ma bata sa kanta cikin soyayyar. Daga wanda zata musu k’arya tace takusa aure se wanda zata ce musu tanada aure.

         Zancen mafarki kuwa har yau bata dena ba kusan kullum setayi mafarkin mutumin dayayi raping nata wai ya dawo ze sake raping nata, Mami kullum ke calming nata in tayi mafarkin rananda Mami batta kusa kuwa haka zata riga kuka tana b’ari har wayewan garin Allah, Allah sarki!

       K’arfe 2:00PM...
      Dadai lokacin tashin Fannah daga aiki kenan kafin ta tsari napep ta dawo gida kuma 2:30PM yayi. Tana shigowa gida Aiman dake carafke tsakar gida tasoma mata “Oyoyo Ya Fannah” cewar Aiman dake da shekara 8 kenan baki kam masha Allah. “Oyoyo Aiman” cewar Fannah tare da hugging nata. “Ina sweet d’ina Ya Fannah?”
    “Laaa kinga yau na mance ban siyo miki ba in shaa Allah zan siyo miki gobe, yi hak’uri kinji?”
     “Ai dama haka kike cewa kullum inda saurayin kine ai baraki mance ba.” Cewar Aiman tana guna-guni.
      “Ya SALAM!!!” Fannah ta zaro ido “ban hanaki maGanan saurayi ba? Ni narasa ina kikejin wanga zance.”
     
        “Sekin tambaya ne Ya Fannah?” cewar Afrah data fito daga d’aki “wannan maras kunyan kuma.”
         “Ai wallahi Ya Afrah ko kiyi shiru ko in fad’awa Ya Fannah batun wancan saurayin dayazo wajen ki d’azu da Mami batta gida.”
    Kai Afrah ta dafe “banza! ai kin riga kin fad’a matan kuma wallahi kisani baran sake baki chocolates ba in yakawo min.”
        “Wait wait wait Afrah saurayi kika soma kawo wa gida bada sani na ba?” Cewar Fannah in a serious tone.
       “Ya Afrah fa ba saurayi na bane munafircin wannan munafukan ne, Ibrahim nefa classmate d’ina na secondary school.”
          “Meaning? Afrah bawai zan hanaki yin samari bane kawai becareful karki yarda da maza so easily zasu kaiki ne su baro ki.”
      “In shaa Allah ya Fannah I'm very vigilant.”

6 hours later...
      Mami da su Fannah ne zaune a d’akinsu suna d’an tab’a hira. “Fannah nace wannan karan se ankai har k’ashen wata za’a biyaku?”
         “Eh Mami” ta amsa da fara’arta “wani abu ne?”
        “Fannah Habibti nasan kina mana sosai in ba ke family'n nan would have been dead by now, mungode sosai Allah cigaba da miki bud’i ya miki albarka kuma.”

        “Ameen Mami dan Allah kidena min godiya, you guys deserve all that I'm doing for you. We are family. Kina buk’atan kud’i ne? Kaman nawa?”

        “San samu dubu biyu kinga Maman-”
    Katseta Fannah tayi “a’a Mami ba sekin min bayanin me zakiyi da kud’in ba” nan ta ciro wallet nata ta irga N4000 gashi jiya mun samu ankai mu wani meeting da akayi na commissoners so anbiya mu kud’i. “Nan N4000 gashi zdmiki aiko?”

        “Fannah N2000 ma ya isheni dan Allah ki rik’e sauran kema kinada buk’atunki ai.”
      “Mami dan Allah ki amshi ai ni na baki.” Hannun Mami tabud’e tasa mata kud’in ciki. “Nagode Habibti Allah miki albarka yakuma k’ara bud’i.”
       “Ameen Mami nagode da addu’arki Jazakillahu khairan. Barinyi sallah in kwanta k’arfe bakwai zan fita gobe akoi meeting da za’ayi muzamuje muyi serving abinci can.”
      “Toh ki huta gajiya nima barinje in samu Babanku. Seda safe.” A tare Afrah da Aiman da Fannah duk sukace “Allah bamu alheri” sannan Mami tafice bayan ta amsa da “Ameen karku manta kuyi addu’a”

     Ya Fannah zan d’an samu d’ari biyun kati ne? Cewar Afrah tana b’oye fuskarta.
     ‘Yar murmushi Fannah tayi “saboda kisamu na kiran samari ba”
      “Haba! Dan Allah Ya Fannah wallahi a’a.”
     “Toh Allah kaimu gobe zan baki, kwanan nan bana spending much muku kuyi hak’uri tara kud’in nake ne Afrah inason kai Baba asibiti kinde san ya jikin nasa yake.”
     Kai Afrah ta giad’a alaman tasani sosai. “Mun gode sosai Ya Fannah Allah k’ara bud’i.” Da amsar “Ameen” suka kashe wuta suka kwanta.

   ★★★★  
ANAS
 
      Sosai Anas ya k’ara kyau, fari da fresh, shekaru sun k’aru yazama cikakken saurayi yanzu me shekaru ashirin da uki (23) a duniya. Jikinsa muscular yake, packs nasa na nan guda hud’u dadai ba guda shida irin na wrestlers ba. Tsayayyen na miji yake yad’an k’ara kauri kad’an kan sirancinsa wanda yasake fito da kyansa. Sede kam hali na nan na shaye shaye dukda cewar har a yau Abuu da Ummie basu san yanayi ba, duk wanda yaji ance Anas na shaye shaye ma bare yarda ba saboda erin hankalin dayake nuna wa mutane, kominsa a b’oye yake. A da se in yayi mafarkin Ummimi ko na yarinyan dayayi raing yake sha amman banda yanzu, haka kawai in ya rasa abin yi ze kurb’a abinsa. Allah shirya.

    A wannan shekaran yagama makarantarsa na London. Tun tafiyarsa be dawo gida ba sanda ya k’are shekaru biyar d’in cur! Cikin ikon Allah kuwa  yafito da excellent result, school nasu sunyi dashi ya soma musu aiki dan iya zanen Anas as an architecture amman sam yak’i saboda san cika burinsa na karya wa mata zuqatansu, yafisan yayi da matan Nigeria kaman sa ba tsinannun turawa ba. Amal tasa ta girma sosai shekarunta 13 yanzu, ba abinda ya rabata da Anas kyau kawai ya d’ara ta da kad’an. Amal an d’an soma wayo amman har yanzu halin autan ta nanan dakuma rashin kunya da rashin shiri da Shettima. Shettima har yau besan ya girma ba shekarunsa ishirin da d’aya da abu a ka amman hakan be hanasa papiro Fannah da gudu in tamasa rashin kunya. Cat and dog Ummie ke ce musu.

         Anas kuwa saide in bai gida sarai fa yasan Amal ce da laifi amman haka zebata gaskia yabawa Shettima laifi se in sun keb’e yake basa hak’uri. Sosai Anas yaya ne me hankali, yana kula da k’annansa ba kamar da ba kuma yanzu in yana cikin family’nsa yana murmushi da walwala sosai seda Amal ne kawai yake dariyan da har za’a ga fararen hak’waransa tas. Su Baana da Kashim ma suna nan sun bud’e ‘yar sana’a tare and alhamdulilah Allah na sa musu albarka. Shettina kuwa yasa san jiki a gaba, sam bayasan yin abu wa kansa yayi depending da Abuu kawai ‘cause yanzu masha Allah Abuu arziki se bunk’asa yake tunanin komawa Maiduguri ma yake sede har yanzu nothing is certain yet.

     A yanzu haka Anas yana garin Maiduguri yazo neman aiki kwanansa uku kenan yau yakeda shirin fara fita neman aikin, Allah bada sa’a.

     Construction industries yasoma bi sede yawancin su se suce basu d’iban masu aiki yanzu ya dawo bayan wasu ‘yan watanni dukda kyan result nasa kuwa haka ya gama yawo a ranar farko besamu aiki ba. Ranar biyu ma haka ya jera kusan sati yana neman aiki kap babu har yayi giving up kan monday ze koma Bama ze huta yanzu a weekends a gidan chairman daya sauk’a.

      Yana kwance a guest room kan gado Iphone nasa yayi ringing yana kai dubansa yaga “My angel” Amal kenan. Da murmushi kan fuskarsa ya d’auka.
       “My Angel” ya fad’i.
   “Na’am Ya Anas d’ina ina wuni?”
       “Lafiya qalau Angel ya kike ya school?”
      “Lafya qalau Ya Anas, yaushe zaka dawo baka samu aikin bane har yanzu?”
       “Ban samu ba Angel ina kan nema har yanzu amman nakega monday zan dawo. Kinasani cikin addu’a ko Angel?”
         “Sosai Ya Anas yanzu ma dana idar da sallah sanda nasaka ciki”
          “Yawwa My Angel ya Ummie toh?”
   “Lafiyarta qalau. Ya Anas kaga Ya shettima d’azu ya mareni.” Ta fad’i kamar zatayi kuka.
     Yana kishingid’e jin Amal tace Shettima ya bugeta yasa ya zauna tare da zaro blue eyes nasa. “Ya mareki? A dalilin meh?”
       “Wallahi ba abinda na masa Ya Anas kawai fa abokansa ne sukazo yace in gaishesu nikuma nak’i saboda hak’ori na na ciwo shine bayan da suka tafi ya mareni a bayana wajen har yayi pink.”
       Sarai yasan Amal da rashin kunya daga ji ba k’in gaishe da abokan nasa kad’ai tayi ba in aka bibiya halan har zaginsu ma tayi.
      “Toh yi hak’uri Angel yanzu zan kirasa in sissilesa na dawo kuma zan rama miki.”
   “Yawwa Ya Anas ba-bye.” Ding! Ta kashe.
 
     Komawa yayi ya kwanta tare da zira wa ceiling ido yana murmushi wa kansa daidai lokacin wayarsa tayi k’ara yana kai dubansa yaga number ke kira, zurawa screen d’in ido yayi yana nazarin wacece can yace wannan number Meenor ce. Sanda ya kusa tsinkewa sannan ya d’aga batare da yace komi ba wata murya ce me zak’in gaske ta soma magana a hnakali dukda cewar cikin tashin hankali kuwa take.
 
     “Haba dan Allah blue eyes, menayi kuma wannan karan? Tun jiya nake ta trying number’nka sarai kana gani ignoring d’ina kawai kake.”

    “Toh nayi, zaki iya yin wani abu ne?” Gatsau ya bata amsa.

     “A’a dan Allah blue eyes kar muyi haka dakai I'm sorry, I love you.”

     “Meenor nomore of that we are done, karki sake kira na please ko kin kira ma barin d’auka ba.” Karap ya katse wayar. Kafin ya ajiye ta soma kira again sa number’n nata yayi a call divert tare da sakar da murmushi hakwaran samansa suka bayyana. “7 of  100 kenan.” ya cize light red lips nasa. Ma’ana cikin mata d’ari daya d’au alwashin ze kariya masu zuciya yaci nasara kan guda 7 wannan ma tun kafin yasamu aiki yazama billonaire kenan!

© miemiebee

 TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 13
BY MIEMIEBEE

washegari...
      Kasancewar yau Asabar bayan Anas yayi wanka yayi breakfast yayi shirinsa na kullum T shirt da pencil trousers ya feffeshe da turare tare da taje gashin kansa yayi styling nasa me kyau sannan ya rataya jakar laptop nasa da credentials nasa ke ciki. D’an fita ganin gari zeyi tunda Monday ze koma Bama.

      Tafiya yake cikin unguwar Old GRA yana d’an kalle-kalle yadda kowa yake aikin gabansa can yaga mutane sun taru gu d’aya se hayaniya ke tashi wajen, a hankali ya taka izuwa wajen shima dan ganin meke faruwa. Yawancin architects ne awajen seda masu construction kuma zane ne babba a gabansu se musu suke sun rasa gane ya zasu gudanar da aikin. Daga wata gefe kuwa wani dattijo ne zeyi erin shekaru 65 d’innan yayi tagumi ya zuba musu ido sunata shirmeh. Kallo d’aya Anas yayi wa zanen wajen ya gano zanen babban gini ne ko erin company ko industry haka. Daya sake kallo kuwa seya gano matsalar da suka samu wajen zanen murmushi yayi sannan yayi giaran murya “may I interrupt?” yace dasu.

     Tas kowa wajen ya juya yana kallonsa, wasu suna admiring kyansa wasu kuma mamakin blue eyes nasa suke kode bature ne? Amman kuma farin sa bekai na turawa ba toh fah. Na zaunen ne yace “sure please” tare da mik’a ma Anas paper’n. Dattijon kuwa har yanzu na zaune yana kallonsu. Amsar pencil da cleaner Anas yayi yad’an goge wani waje a zanen ya giara daga k’asa sannan yayi haka ma daga sama. Yana gamawa ya juya paper’n yana kallon babban nasu na zaunen bayan ya d’an kalla aikuwa sega abinda suke san sucire d’in yafito, building d’in is in perfect position. “Wow!” Yayi exclaiming “saurayi you are incredible! ku tafawa wa wannan saurayi please.”Nan take duk mutanen wajen suka d’iba da tafi suna hailing Anas.

     Dattijon dake zaunen ne ya taso da karar tafiyarsa irin na gayu me kan gwal d’innan ya iso wajen a hankali. Cikin muryar manyanta yace, “meke faruwa anan?” Babba na zaunen ne ya juya da paper’n yana nuna masa “gashi Mr Muh’d toilet da ake buk’ata a last floor d’in yafita building d’in is in perfect position yanzu.” Kai Mr Muh’d ya giad’a a hankali “good.” yace. Babba na zaunen ya cigaba da cewa “wani saurayi ne anan yanzu ya giara yana zuwa kawai ya amshi papern ya d’anyi goge goge kawai ya fitar he must be a genius. Ina kake ne?” Yana dubawa kuwa se ba Anas har ya juya ya cigaba da tafiyarsa.

         “You two” Mr Muh’d ya nuna yaran aikinsa guda biyu “ku bisa ku kira min shi.” A papare suka yi inda Anas yabi suna gudu suna binsa can suka gansa ya tsaida taxi ze shiga “hey! Hey! Bawan Allah ka tsaya” sam be jisu ba gashi basu san sunan saba. Can d’ayan yace, “me blue eyes!!!” da k’arfi cak Anas ya tsaya ya juya yana kallon inda yajiyo kiran. Bada jimawa ba suka iske sa. Hannu d’ayan ya mik’a masa suka gaisa. “Uhm I'm Kacallah wannan co-worker nane Yunus mune wanda kayi saving building drawing namu yanzu. Thank you”

         “Oh!” Anas yad’anyi murmushi, “that was nothing kar ku damu” ya juya ze shiga taxin. Yunus ya tsaida shi “erm dan Allah d’anyi hak’uri ka tsaya Boss na wajen aikin mu neh CEO’n Flames Enterprises babban company’n dake Maiduguri keson maka magana.”
       Zaro blue eyes nasa yayi “me?” Ya nuna kansa cike da mamaki.
      “Eh” Kacallah yace “you! You did what muka kasayi duka for that yanason ya maka godiya and am very sure zeyi honouring naka saboda Mr Muh’d mutum ne me kirki.”
     “Okay” Anas yace... Har yanzu ji yake kamar a mafarki wai CEO’n Flames Enteeprises keson masa godiya, sosai yasan Enterprise d’in kullum cikin NEWS se anyi maganan enterprise d’in yadda suke successful. Shi koda yake neman aiki ma be lek’a can ba a tunaninsa ma barasu kallesa ba bale su d’auke sa.

     Kacallah ne ya katse masa tunani, “blue eyes baka ce komai ba.”
     D’an murmushi Anas yayi “you can call me Anas, suna na Anas.” Kacallah yace, “wow suna me dad’i but still I prefer blue eyes sorry to ask muslimi ne kai?”
       Kallonsa Anas ya tsaya yi daman ina kama da christians ne? Ya tambayi kansa.
      Ganin Anas be amsa saba yasa ya giara zancen nasa “uhm don’t feel offended please bawai kamin kalan arne bane kawai your eyes...” ya nuna idanun Anas da yatsa “nad’au bature ne kai.”
      Sosai Anas yayi mrmushi, “toh ai ban kaisu fari ba” yace.
          “Eh nasani ko irin black Americans d’innan ne kai.”
         “To ka kwantar da hankalinka ni nan da kake gani na kanuri ne daga Bama dangi na kap ba christian.”
       “Ohhhh!” Kacallah da Yunus suka fad’i a tare suna giad’a kai. “Ikon Allah!” cewar Yunus. “Kanuri amman zallah? Baka had’a dawani yare ba?”
      Toh fa an tab’o gogan namu, ya washi yakira yaren Ummimi amman ya ya iya dasu? dole ya fad’a musu ko zasu bar kallon da suke masa.

          “Mahaif-” se zece mahaifiya ta seya gagara dan koda wasa baisan kiran Ummimi dasunan mahaifiyarsa shi Ummie yasani mamansa ba Ummimi ba. Ganin sun zura masa ido yasa kawai yace, “mahaifiyata shuwa arab ce, mahiafina ne kanurin.”
 
      “Aihoooo aiko da alama” cewar Kacallah “sesa kake da kyau haka, masha Allah. Toh blue eyes muje Boss namu nasan ganinka.” Sallamar me taxi d’in yayi sannan ya bisu har gaban Mr Muh’d suka kaisa. “Mr Muh’d gashi nan” suna fad’in haka suka ja da baya duk suka bar wajen ya rage daga Anas se Mr Muh’d.
      “morning sir?” Anas ya gaishesa tare da durk’ushewa har k’asa mutumin be amsa ba illa kallon Anas dayake har Anas ya shiga tsoro daga bisani Mr Muh’d yace, “morning boy, get up please.” Nan Anas ya mik’e yana kallon k’asa. “I will first of all like to thank you for saving my men and company in all.”

      Anas na murmushin dole yace, “ba komai Sir, don’t make an issue out of it.” Cike da mamaki Mr. Muh’d ke kallon Anas jin yayi hausa. “Kanajin hausa kenan?” ya tambayesa.
     Mamakin erin tambayan Anas ke wai dagaske aka gansa bara’a d’au yana jin hausa bane? Dole ya sai black lens (k’wayan ido) a kasuwa ya soma sawa.
      “Sosai inaji Sir d’an nan ne ni ai, kanuri nake daga Bama.”
     Sanda idan d’an dattijon ya warwaru. “Kaid’in?” Ya tambaya in disbelief.
      “Eh sir” kafin Mr Muh’d yasake wata maganar Anas yace, “nasan you must be wondering ya nake da blue eyes haka aka haifeni amman d’an nan ne ni kuma muslimi ne ni my name is ANAS IBRAHIM FAUZY.”

     Kai Mr. Muh’d ya giad’a alamam ya yarda. “Toh masha Allah Mr. Fauzy kanada kyau tubarkallah.” Murmushi Anas ya masa “na gode Sir.”
      “Kana kirana da Baba, I once had a son as you.” Sekuma mood nasa ya canza.
      Nan Anas ya gano rasuwa d’an nasa yayi kenan. “I'm sorry Sir.. I mean Baba.”
     “Bakomai Mr. Fauzy. Aeroplane crash ne ya samemu time da zamuje hutu Paris nida d’ana Sultan da matata sekuma da iyayena, bayan jirgin yayi crashing atake duk suka rasu ni kad’ai nayi surviving a family na dukda nima naji ciwo sosai a sanadin haka na rasa k’afata na hagu anyi aiki sosai amman ina yak’i gyaruwa sesa kaga ina tafiya da stick (sanda).”

     Tausayin bawan Allah’n nan Anas yaji ya kamasa, sarai yasan how it feels to be alone, not to have a family shi Ummimi kawai suka rasa amman rayuwarsu ta tab’arb’are bale shi nasa da ya rasa komai. “I’m so sorry Baba Allah ya jik’ansu da rahmah.” “Ameen Mr Fauzy sede ana nema na awani meeting yau gashi har...” Ya d’aga hannunsa ya kalli agogon hannunsa “8:30 yayi.”

        “Ba komai Baba I’ll sit here in jiraka its my honour meeting with you, nasha ganinka a NEWS you’re such a successful man.” Murmushi kad’an Mr. Muh’d yayi “lets go” cike da rashin fahinta Anas yace, “excuse me?”
     “Lets go to the meeting together.”
     Blue eyes nasa ya zaro “Baba thank you for the offer but I’m not invited kar inje a koreni.”
    “Hahaha!” Mr. Muh’d yayi dariyan manya. “Not in kana side d’ina so lets go?”
      Kai Anas ya giad’a masa. Waya Mr. Muh’d yayi bada jimawa ba wata prado 2016 bak’a tasha wanki har kamar mirror jikinta yake ya zo yayi parking a gabansu. Fitowa wani yayi daga gaba ya bud’e k’ofar baya, hannu Mr Muh’d ya nuna wa Anas da nufin ya shiga a sanyaye ya shiga tare da rik’e jakar laptop nasa daya rataya a kafad’arsa kan cinyarsa, bayan shigansa Mr. Muh’d ma yashiga a hankali driver’n yasoma tuk’i.

     Basu tsaya ko inaba se wata babban conference hall tun fitowarsu daga motar mutane suka soma layi jiran su gaisa da Mr. Muh’d. Mamaki ne yacika Anas mutane kamar su cinye Mr. Muh’d wasu kuwa tambaya suke kowaye Anas amsar dayake basu ne yasa Anas shocking wai “he is my son.”

       Wajen VIP aka zaunar da Mr. Muh’d shima Anas yasamu kujera a gefen sabon Babansa (lol). Tambayoyi sosai Mr. Muh’d ya riga yi ma Anas kan ina yayi karatu? Sheraunsa nawa? Tambayoyi de turum. Daga k’arshe ya buk’aci Anas da ya nuna masa CV’nsa dan yagani Allah yaso Anas kullum yana yawo dashi nan ya ciro yamasa presenting.

      **
      “Fannah! Fannah” kirar Boss na wajen aikinsu. “Yes Boss” ta fad’i bayan da ta iso. “Ga can table na VIP Mr Muh’d ne CEO’n Flames Enterprises.” Ido Fannah ta zaro tare da kewayo wa tana kallonsa ba shakka tana ganinsa a NEWS kap Maiduguri ba wanda yakaisa kud’i.    
       “Kinga saboda kinfi sauran ‘yan uwanki fasali yasa ke zanbawa chance d’innan kije kiyi serving nasa drinks dashi da saurayin gefensa dukda cewar yau na soma ganinsa naji ance wai Mr. Muh’d da bakinsa yace d’ansa ne kinga ko sekije kid’an tatso mana su. Kiyi amfani da kyanki ki ja attention na d’an nasan.”

     Fuska Fannah ta d’aure ko juyawa ma takalli saurayin da akace d’an Mr Muh’d d’in batai ba. “Ya Suleiman wai mesa kake magana haka ne? Nikama b’ata min rai nafasa kai musun gasu Asma’u ka kira sukai masu.”
           “Haba Fannah ke bakisan wasa bane? Ai wasa nake miki. Ungo ga plate nasu na shirya yi hak’uri ki kai musu.” Kallo ta watsa masa sannan ta d’aga ta fice. Murmushi yayi haka suke cikin fad’a kullum shida Fannah sarai yasan batada interest cikin samari shikuwa yata neman taokanarta, in aka ajiye wannan agefe kuwa shida Fannah suna shiri sosai tamakar sister’nsa ya d’auketa. Shine d’an me coffee shop na wajen aikin su Fannah’n. Saboda haka duk wani aikin da akeyi shike bada orders.

     Tunda Fannah ta soma tafiya zuwa table na Mr. Muh’d dan kai masu drinks da d’ansa bata d’aga kai ba. Kanta a k’asa tana isa table d’in ta gaishe da Mr. Muh’d da fara’arsa ya amsa sannan ta ajiye mishi cup nasa, ta mik’a hannu ta ajiye wa Anas nasa shima. A yayinda yake answering call ko d’aga ido ya kalli wacece ma beyi ba kawai “thanks” yace. Fannah itama da kanta ke k’asa bata d’aga kai ta kalle sa ba kawai de tasan waya yake. Ta juya zata tafi kenan Mr. Muh’d ya kira ta da “waitress” cak ta juyo “yes sir.”  “Take this away” ya nuna cup na gaban Anas dake kan waya har yanzu ko kallon direction nasu baiyi “ki kawo masa irin nawa”  “okay” tace sannan ta d’aga tana juyawa taga Asma’u sekuwa gashi kan plate nata akoi erin na Mr. Muh’d nan ta d’aga ta aza kan table d’in. “Here you go Sir” tace sannan ta juya zata tafi dakatar da ita yayi sannan ya zira hannu a aljihu ya ciro bundle na d’ari biyar ya mik’a mata. “Gashi ko mungode.”

     Fannah tasha jin ana cewa Mr. Muh’d nada kyauta bata tab’a tabbatar da hakan ba se yau. Amsa tayi hannu bibbiyu ta masa godiya. “Ba komai wannan nakine bawai na baki bane kije ki kai wa boss naki, wancan na zuwa daban. Keep this”
         Murmushi take sosai “Thank you sir! Thank you” nan ta fice daidai lokacin Anas ya katse wayar dayake yi tare da kewayo wa. “Kai da waye ne?”
         “Nida Abuu ne mahaifina.” Ya amsa a takaice.

          “Okay gashi an canzo maka tunda you are allergic to wancan flavour’n.”   “Thank you” yace “gashi ban samu na bata hak’uri ba nasa ta tayi sahu biyu.”
       “Bakomai don’t worry.” Atare suka sa cup nasu a baki suka d’anyi sipping sannan suka mayar suka ajiye. “So Mr Fauzy naga credentials naka you have such an excellent result, I'm ready to offer you a job a Flames Enterprises as my Personal Assistance (PA) akan albashi N500,000 (dubu d’ari biyar) dakuma weekly allowances N5000 (dubu biyar) kowani sati for a start kenan inhar naga ka iya aiki kana kiyayye komai kuma naji dad’in aiki dakai there will be additional salary for you. So? Will you accept my offer?”

     Anas ji yake kamar a mafarki albashi dubu d’ari biyar? “Yes! Yes Baba nagode sosai, in shaa Allah zaka sameni me kiyaye duk wani dokokin da ka kafa min. This is amazing nagode sosai yau sati na a nan Maiduguri ina neman aiki ban samu ba segashi ka bani wanda ban tab’a zaton zan samu irinsa ba I can’t wait in kira Abuu in sanar daahi. Nagode sosai Baba Allah saka da alkhairi.”
 
     Kallonsa Mr. Muh’d yake yana murmushi he made Anas happy, kawai tunawa yake da d’ansa.

   
     *© miemiebee*
NAGODE LOADS FOR THE WARM CONCERN YOU GUYS HAVE SHOWN ME, I LOVE YOU ALL!
      

 TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 14
BY MIEMIEBEE


      “Hello Abuu?” Cewar Anas ta waya.
       “Anas Baba na ya kake?”
      “Lafiya Abuu I have a suprise for you”
     “Toh inaji Baba na.”
        “Nasamu aiki!” Anas yayi exclaiming.
     “Ahh toh Alhamdulillah a ina haka?”
     “A Flames Enterprises Abuu, kuma as Personal Assistance na CEO’n wajen.”
      “Wai wai! Kana nufin Alhaji Muh’d Muh’d??” Abuu ya tambaya cike da mamaki.
     “Shi Abuu salary na N500,000 da weekly allowances N5000.”
       “Kai Baba na namaka murna barin fad’awa Ummie se add’ua take ta maka.”
      “A’a bari Abuu I’ll call her dakaina banasan Amal tasan she is not the first person I called to tell.”
     “Uh!” Abuu yayi exclaiming “kai da wannan ‘yar takan.”
     Murmushi Anas yayi “Aikam Abuu ina karb’an first salary na shopping zankai Amal.”
     “Toh Allah maka albarka Anas yacigabada bud’i congratulations.”
    “Thank you Abuu se mun sake magana.”
     “So yanzu zaka shigo Monday d’in still?”
    “Eh zan shigo saboda in d’iba kayakina I have untill next week inyi resuming office.”
    “Okay toh yayi kyau, welldone.” Ahaka sukayi sallama.
 
      Anas na cikin searching contact na Amal wayarsa ta soma k’ara number ke kira bayan yad’an zura wa number’n ido ya gano Teema ce. Murmushi yayi sannan ya d’aga batare da yace komi ba.
 
     “Hello angelic blue eyes” cewar budurwar.
    “Yes” ya amsa ba tare da ya nuna damuwa ba.
     “Blue eyes fad’a muke ne? Tun jiya nake expecting call naka shiru.”
    “I have far worth important stuffs to attend to than you Teema.”
    Har tsakiyar kanta ta jiwo wannan zagi amman ta danne zuciyarta. “Blue eyes dama so nake in sani ko you are free zuwa anjima da yamma inason mu fita ne, like a date.”
     “What are you implying Teema? Kina nufin ni bansan abinda yakamata ba se kece zaki bani time da zamu fita date dake?” Ya fad’a a tsawace.
     “Blue eyes please calm down ba abinda nake nufi ba kenan naji kace gobe zaka koma Bama I want to spend some time with you kafin ka tafi.”
     “Huh!” Ya saki numfashi. Tare da jawo kad’an daga cikin gashin kansa yana wasa dashi da wata mirmushin mugunta a fuakarsa. “Nikuma banaso kinsan me Teema? Lets just end it bana sonki anymore lets break up, we are done karki sake kira na ko kin kira barin d’auka ba.”
    “Blue ey-” bata k’are maganar ba ya katse nan take ta sake kira kalan abinda yama Meeno ya mata. 8 of 100 ya murmusa sosai wanda ya mugun k’ara masa kyau.

    Amal nasa ya kira ya fad’a mata yasamu aiki. Tsalle ta riga dakawa haka suka sha hira sannan yace ta kai wa Ummie wayar. Sosai Ummie ta masa. Shettima ne k’arshe ya kira ya fad’a masa aikin daya samu, sosai Shettima uwar san jiki yamasa murna at long last ze soma jin dad’i dan yasan halin Anas be iya rowa ba inba wai dagangan zeyi ba, mutum ne me kyauta amman fa ma wanda yaga dama.
 
    ★★★★

           Da misalin k’arfe 3:30PM Fannah ta dawo gida da ledoji manya manya hannunta siyayya tama family’nta sosai. Mami, Afrah da Aiman duk suna tsaye tsakar gida hankali tashe a tunaninsu ko wani abu ne yasamu Fannah saboda duk sanda zata wani waje daga gun aiki tana kiran Mami ta sanarda ita wanda yau batayi ba.
 
     Tana shigowa Mami tayi kanta tare da rungomata “Fannah ina kikaje? You made us worried sick gashi nata kiran wayarki akashe.”
        “Wallahi game natayi seta mutu, kubar tada hankalinku please in shaa Allah ba abinda ze sameni. Kasuwa na wuce nad’an mana siyayya.”
    Nan Afrah da Aiman suka k’ariso tare da karb’an ledojin akan tabarma suka zauna tare da zazzage kayakin.

       Kitchen utensils ne, food items, seda sweets da chocolates dakuma atamfofi guda hud’u masu kyan gaske seda shadda guda biyu, se sauran k’ananun abubuwa irinsu tissue, toothpick da sauransu. “Fannah ina kika samu kud’i haka ko har anbiyaku albashin ne?”

        “Ko kad’an Mami, ina meeting dana fad’a muku za’a kaimu serving d’insu yau?” Mami ta giad’a kai “ashe harda Alhaji Muh’d Muh’d CEO’n Flames Enterprises.”
      “Haba keh!” Cewar Mami.
     “Ya Fannah kap Maiduguri fa ba wanda yakaisa kud’i!” Cewar Afrah.
    “Ya Afrah shine wanda muke gani a NEWS yawancin kullum?” Aiman ta tambayi Afrah. “Eh shi” Afrah ta amsa ta a takaice.
   
         “Toh shida d’ansa sukaje ni akace na kaimusu drinks nasu bayan nakai nakega se d’an nasa yace baya shan flavour’n drink d’in baban nasa ya kirani na canzo masa nazo tafiya kawai Alhj Muh’d d’in ya kirani ya mik’a min bandir na N500 kyauta bayan da aka k’are meeting d’inkuma da muka raba kud’in da aka bamu na tashi da dubu goma albashi na na wata fa kenan ga kuma dubu hamsin. Daga can na wuce kasuwa namana d’an siyayya dududu kayan dubu talatin ne anan.”

      Aiman mathematician har an buga lisafi “sauran miki N30,000 kenan.”
   Kallonta Fannah tayi tana murmushi “welldone ashe surutun nan naki ba’a banza bane tunda kin iya math haka.”
    “Math d’in ‘yan primary three ba” cewar Afrah tana duba zannuwan. Aiman zatayi magana Afrah tace, “Ya Fannah wannan zannuwa fah?”

      “Namu ne biyu na Mami ta zab’a ciki, guda biyu iri d’ayan kuma naki da Aiman.”
       “Haba Ya Fannah mena siya min turmin zani iri d’aya da wannan maras kunyan.”
        “Yo! Ked’inma ance miki inasan yin anko dake ne? Ya Fannah mungode sede har yanzu banga sweet d’ina ba.” Cewar Aiman.

      Nan Fannah ta bud’o jakarta ta ciro packet na sweet “ungo wannan duka naki ne kika rabawa ‘yan ajinku kuma ni ba ruwa na.” Amsa tayi tana tsalle “nagode Ya Fannah ai ko Ya Afrah ma barin bata bale ‘yan ajinmu masu kwad’ayin nan, wallahi Falmatan nan har k’wai na sanda taci ranan” Zani biyu iri d’ayan ta d’au d’aya tashige d’akinsu dashi. “Ke dawo nan waya ce miki ki d’auka?” cewar Afrah jan d’ayan tayi itama ta ruga tabi Aiman cat and dog kenan.
   
        “Fannah Allah miki albarka, Allah k’ara miki bud’i yaci gaba da kare mana ke. Mungode matuk’a da d’awainiyan da kike mana dukda kuwa ba responsibility’nki bane wannan aiki na ne da Babanku amman kinayi. Kiyi hak’uri.”
     Hannun ta Fannah ta rik’e bibbiyu cikin nata “Ameen nagode da addu’arki Mami amman dan Allah kidena min godiya ba godiya tsakani na daku Mami. Na ware dubu ishirin cikin kud’in gobe seki kai Baba asibiti a duba shi ko magani a basa tunda baramu iya affording aikin da za’a masa ba.”

        “Toh Fannah, sannu da k’ok’ari Allah miki albarka.” “Ameen” tace “barin je in samu su Afrah ciki, ki d’au zannuwa biyu anan shaddojin kuma na Baba ne.” “Toh mungode sannu.”

     Fannah na shigowa d’aki tasamu Afrah da Aiman se dambe suka dak’yar ta rabasu zani de gasu iri d’aya amman ahakan ma se anyi fad’a. Bayan ta rabasu ta kori Aiman dawayo in bahaka ba sun hau wasan habaici kenan. Ana kawo wuta ta had’a wayarta a charging. Kayakinta na cikin wardrobe take shiryawa a yayinda Afrah ke kishingid’e kan gado tana game a wayarta. Can ta nisanta sannan takira Fannah. “Ya Fannah!” “Na’am Ya Afrah, mene kuma yanzu?” cewar Fannah tana ninke kayakinta.

       “Kikace d’azu kinga Alhaji Muh’d Muh’d?” Kai Fannah ta giad’a batare da ta kalleta ba. “Okay da d’ansa kuma kikace sukaje wajen?” Afrah ta fad’i kalma d’ai d’ai.
     Barin abinda takeyi tayi ta juyo ta kallon Afrah “what are you implying?”
    D’an dariya Afrah tayi “guilty concious?? Ni bance komi ba kawai cewa nayi kinga d’an Alhj Muh’d?”
     “Nope ni bangansa ba.” Fannah tabata takaicaccen amsa.
 
     “Wow! Yau me hana mutane k’arya keyi? Hilarious.” Cewar Afrah tana mocking smile.

       “Kuma se akace miki k’arya nake. Allah ban ga d’an nasa ba.”
        “Toh ikon Allah kuma ke fa ke kika kai musu drinks nasu? Kodan had’ewarsa yasa baki gansa ba?”
    “Ke wallahi Afrah suratan banza sun miki yawa. Ni ko zaki samin wuk’a a wuya bansan kalar fatar sa bama bale insan ko kyakkyawa ne ko mumuna. Muryarsa kawai naji.”

      “Haba!” Afrah ta daka tsalle tare da baro inda take ta matso kusa da Fannah. “Ya muryar tasa take Ya Fannah? Fad’amin please kinsan su yaran masu kud’i muryarsu ma daban take.” Shiru Fannah tayi tana nazarin muryar Anas dasuka d’au d’an Alhj Muh’d ne. “Well ba hassada muryarsa nada zak’i irin zak’i ta mazan nan and yana cracking hakan nan. Barin miki bayanin yadda zaki gane kinsan muryar Lancelot nacikin season film Merlin ba?” Kai Afrah ta giad’a sau uku. “Toh haka murayarsa take sede kamar zatafi na wancan d’inma dad’i. Toh kinji, matsa min nacigaba da abin dake gabana.”

      “Iyye! Har kinsa na fara imagining wannan d’an billonaire nasan definately zeyi kyau sesa hakan ma ba’a nuna sa a NEWS gudun kar ‘yan mata su bisa.” Kallo Fannah ta bita dashi “kefa wallahi surutun banzanki sunyi yawa.”

         “Hummm! Afrah taja numfashi “Ya Fannah kenan. Kinsan muryarsa meaning kunyi magana kenan.”
      “Wai meke damunki bamuyi magana ba acewarki yaran da ubansu billonaire suna magana wa mutane anyhow ne? Ko kallona ma beyi ba dana ajiye masa drink d’in kamar yadda nima ban kallesa ba thank you kawai naji yace.”
   “Iyye! Amman daya miki magana fa? Zaki amsa?”
      “Ke qaniyarki, Afrah kika sake maganan wancan saurauyin bake ba kud’in kati se next month.” Tsit Afrah tayi bata kuma cewa komi ba, ahaka Fannah tasamu tagama had’a kayakinta cikin wardrobe.

           _One week later..._
     
           Anas ne tsaye gaban dressing mirror a d’akin da chairman yabasa. Yau ze soma zuwa office he is feeling nervous sosai. Sanye yake da mint blue shirt me long sleeves da cufflinks, seda jean trousers. Simple shiri ne amman yamugun amsar sa he is looking way smart. Jakar laptop nasa ya d’ago yasa laptop d’in ciki da sauran takardu kad’an sannan yasake kallon kansa jikin madubin sannan ya fice bayan ya karya ya wuce office.

       Yana isa gaban building d’in da za’a iya kira da mini sky scrapper ya tsaya. A k’alla floors za suyi 7-8, dogon gini ne sosai wanda jikin bangon yake glass. Building ne babba bakin k’ofar an rubuta FLAMES in caps. Wani button ya danna k’ofar glass d’in ya bud’u yana shiga k’ofar yayi scanning nasa bayan ya tabbatar baya d’auke da makami sannan wata k’ofar ta sake bud’uwa nan ne mutanen cikin ginin suka bayyana. Maza da mata kowa se aikin gabansa yake very organised. Wajen shiru ba hayaniya. Wajen dayaga an rubuta RECEPTION ya k’arisa mace ce tsaye wajen gabanta telephone ne da pack na pencil da biro seda files kuma. Tun kafin ya mata magana tace dashi “Hi” tana washe 32 inta acewarta taga bature.

       “Hello” ya gaisheta back, “erm I want you to direct me to Mr. Muhd’s office, the CEO.”

     “Okay American's most handsome” tace dashi. “Whats your name?”

     “Anas Ibrahim Fauzy.” Ya amsata a takaice. Baki tasake wangalau wai dama ba bature bane?

   “Excuse me, I mean your name. Name.” dan bata yarda muslimi bane.

   “Yes Anas Ibrahim Fauzy. Ko kema kin d’au Joseph ko Andrew ne sunan nawa? My name is Anas for goodness sake.” ya fad’a a tsawace.

        “I'm sorry blue eyes” ta fad’a tare da kashe masa ido. Tsuka yaja tare da kawar da idanunsa daga kanta.

      “Uhm are you two having an appointment with the CEO yasan da zuwanka?”

    “What nonsense? Da inbe san da zuwa na ba zanzo nan ne? Take me to your CEO” yayi demanding ba alaman dariya a tatare da fuskarsa. “Mesa yawancin kyawawan mutane basuda hali ne?” Cewar receptionist d’in a hankali aikuwa Anas ya jiyota harara ya watsa mata bayan d’an dube-duben da tayi a system dake gabanta tace, “I'm sorry Mr. Fauzy seems like ba sunanka acikin wad’ana zasu ga Mr. Muh’d yau maybe next time.”

           “Kinsan wani abu? Tunda nake a duniya ban tab’a ganin senseless mutum kamar ki ba.” Dadai lokacin elavator ya bud’u Mr. Muh’d ya fito daga ciki. Taku d’ad’ai kamar yadda ya saba yayi yatako zuwa gabansu Anas cike da girmamawa Anas ya gaishesa.

        “Ya Anas me kakeyi baka shigo ba har yanzu? I've been waiting for you”
        “Baba wannan receptionist d’ince ta rik’eni wai baran shiga ganinka ba.”
    “No Sir ba hak-”
   Katse ta Mr. Muh’d yayi rai a b’ace “this should be the last time da zaki sake hanasa shigowa nan he is Anas my son, copy that!” ya daka mata tsawa.
   “Yy..yyess sir, my aplologies please.”

     “You apologise to him not me.”
     Kallon Anas take yana mata murmushin mugunta, “Mr. Fauzy I'm sorry.” Harara ya watsa mata sannan yace, “apology accepted.” Nan Mr. Muh’d yaja hannunsa “come lets go in nuna maka office naka.” A floor na k’arshe yakai Anas inda aka rubuta Mr. Fauzy a bakin k’ofar d’akin. Office ne babba da split AC ciki, office kujeru ne manya guda biyu da table d’aya. Akoi telephone da flat screen desktop kan table d’in seda notepad, da pen dakuma pencil pack. Gefe guda kuwa fridge ne seda plasma TV. “This is your office, inda abinda be maka ba let me know se a giara” Godiya sosai Anas ya masa tun daga ranan Anas ya soma aiki.

     He is very punctual, duk meetings da schedule na Mr. Muh’d shi yake maganing kasancewar duk Enterprise d’in ba architecture’n daya kai Anas duk sandq za’ayi zanen project Anas keyi.

  © miemiebee

 TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 15
BY MIEMIEBEE



★★★★★
    5 months later...

               Shak’uwa ne me k’arfin gaske ya shiga tsakanin Anas da Mr. Muh’d, ladabi da biyayya kam Anas ya iya duk wanda yaji ana cewa Anas na shaye-shaye ze k’aryata zancen. Basu tab’a samin matsala da Mr. Muh’d ba aikinsa duk yanayi me kyau tun da yayi joining enterprise d’in abubuwa suka sake improving fiye da da. Family’n Anas a yanzu haka sun dawo Maiduguri da zama a unguwar New GRA. katafaran gida Abuu ya sai masu da taimakon Anas. Gida ne mansion d’aki kota ina. Rayuwa alhamdulillah yanzu, ansa Amal a Ruby Springfield College. Shettima kuwa ya soma attending UNIMAID a inda yake karanta accounting.

     Anas yayi introducing family’nsa wa Mr. Muh’d sosai suka shak’u da juna. Sanin yadda Anas keson Amal yasa shima Mr. Muh’d yakeson Amal sosai, musamman yadda take sasa dariya duk sanda suke tare in su Anal sunyi hutu kullum tana office wajen Mr. Muh’d datake kira da grampa, wane family haka suka zama. A birthday’n Anas Mr. Muh’d ya basa sabuwar mota pil cikin leather k’irar mercedes-benz SLK. Tunda Anas yayi mota walak’anci ya k’aru ahaka yanzu a list nasa yanada mata 33 da yayi breaking hearts nasu. Leaving life nasa yake to the fullest duk sanda su Baana suka shigo Maiduguri kuwa shan giyan ranan na daban ne. Suna waya sosai da friends nasa Abdoul da Musty.

     Yau ranar ta kasance Monday as usual ya soma shirin office, Shettima da ba lectures se da rana se bacci ake sha. Amal da ba office zata ba amman ta riga Anas tashi tare suka had’a breakfast su biyunsu sukaci bayan sun gama ta rakasa har parking lot yashiga cikin sabuwar motarsa sukayi ba-bye da juna sannan ya fice. As usual yashirya wa Mr. Muh’d schedule nasa na ranan yakai masa. “Welldone Anas, kana k’ok’ari sosai nace zanen project d’incan kasamu kayi kuwa? Kasan mutanen daga Ghana zasu zo yau akoi board meeting da za’ayi by 4:00PM zamu masu presenting.”

      “Eh Baba nayi yana nan ajiye cikin shelf a store room floor 2.”

      “Good, se meeting d’in zanbar care d’in a hannunka. Akoi inda ake samun professional waiters a Fahmaz coffee shop (inda Fannah ke aiki) kayi waya da masu wajen kamana booking.
   
    “Okay Baba, I’ll be going” nan ya zarce office nasa inda ya kira number’n me Fahmaz coffee shop d’in.

    ***
     “Ya Suleiman ga call from Flames Enterprises.” Fannah ta danna kira wa Ya Suleiman dake waje. “Ki d’aga kiji meneh, I'm busy here.” Hannu tasa ta d’aga tare da yin shiru bata ce komai ba. “Hello?” Anas ya fad'i cikin muryarsa me tafiya wa kowace mace da imani. “Hello” Fannah ta fad’i in return. This is Fahmaz Coffee shop, how can I assist you?”

      Jin muryar mace ne yasa ransa ya b’aci take. A fusace yace, “ai nasan Fahmaz Coffee shop d’inne saisa na kira so just shut up plus haka aka koya miki wajen aikin naku in kun d’au waya kuyi shiru?”

         “Lalle ma wannan mutum anyi d’an iska” cewar Fannah a zuci “shi ya kira kuma yana jiran nice in soma yin magana?” Dukda bame san magana bace amman taji barata iya hak’ura ba so take ta sa koma waye ne shi in his rightful position sekuma ta tuna wannan business related matter ne she shouldn’t take it personal.

       “I'm sorry. How can I assist you?”
    “Mstchww” yaja tsuka sannan ya cigaba “we need 5 waitresses and 5 waiters from your coffee shop here at Flames Enterprises by 4:00PM.”

     “Okay copied” tace.
        “Bama tolerating late coming you guys should make sure 4 d’in ya muku anan.”
       “Lalle ma wannan mutumin” cewar Fannah a zuci.

        “Ko baki ji bane?” Zatayi magana ya katse dagangan.  Ciro telephone d’in tayi daga kunnenta tana kallon wayar cike da namaki wannan wani irin bawan Allah ne me uban jijji dakai haka? Mstcw taja tsaki daidai lokacin Asma’u ta shigo “yau Fannah ke tsaki? Keda waye ne haka?” Ta bud’e baki zatayi magana Flames Enterprises d’in yasake kira sanda ya kusan tsinkewa sannan ta d’aga “yes.”

       “Don’t use that tongue with me young lady” cewar Anas in a serious tone daya tsorata Fannah kum tayi shiru. “Incase clueless mind naki be baki idea ba, you have to be here now saboda coffee zakuyi serving ba drinks ba. So zakizo in baki details d’in plus don’t be late bana jiran mutum sede a jirani.” Shiru tayi tana mamakin wannan bawan Allah. “Are you there? Cause bana repaeating kaina twice”

        “Yes I’ll be on my way.” Nan ya katse wayar. Tsuka takuma ja “lallai akoi arrogant people dayawa a duniya what is he feeling like? D’an Adam de ba wanda yafi wani we are all equal.” Asma’u dake kallonta tace, “ji yadda kike magana sekace bakisan Anas ba.”

     Fannah tace, “Anas? Waye shi?”
     Asma’u tace, “no wonder sesa kike tada jijiyoyin wuyanki haka, ni rananda ya kira na d’aga bakiga zagin duniyan daya min ba aike yamiki mutunci ma.”
     “Toh waye shi? Whats he feeling like?”
      “Shine PA’n Mr. Muh’d na Flames Enterprises kuma ance Mr. Muh’d nasan sa tamkar d’an cikin daya haifa, cewa ma yake Anas d’in d’ansa ne.”
     “Ikon Allah! Lallai kam.” cewar Fannah cike da mamaki.
     “You better go kafin yasake kira ya balbale ki.” A sanyaye Fannah ta fice bata tsaya ko inaba se Flames Enterprises can akayi directing nata zuwa office na Anas tsaye take a bakin k’ofar office nasan takasa shiga zuciyarta se bugawa take musamman ma data d’aga kai taga ansa *Mr. Fauzy* asaman. Tafi minti biyu tsaye a wajen sannan jiki na k’yarma hannu na b’ari tayi knocking k’walli d’aya tal jin ba’a amsa ba yasa ta k’ara d’aya “come in” taji muryan na miji ya fad’i authoritatively. Tabbas tasan wannan murya shine wanda yace mata thank you rananda Mr. Muh’d ya bata bandir na N500 kawai haka taji zuciyarta na bugawa tarasa dalili.

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *