Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, September 7, 2016

TANA TARE DANI...16--20

adsense here tana-tare-dani.jpg


ANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 16
BY MIEMIEBEE



*ASSALAMU ALAIKUM MASU KARATU, INASON INYI AMFANI DA WANNAN DAMA IN FAHIMTAR DA MASU K’ORAFI KAN LITTAFI NA, NACEWA INA YAWAN SA TURANCI CIKI. RIGHT FROM THE START NASO DAMA IN YI MAKING IT CLEAR KAN ZA KUNA YAWAITA GANIN TURANCI CIKIN LITTAFIN NAN AMMAN KUMA SENA FASA. GANIN ANASON A MAIDA ABIN SUBJECT OF DISCUSSION YAZAMA DOLE INYI MAKING IT CLEAR YANZU. IN KUKA LURA BAWAI NA K’WARE A HAUSAN BANE, KOYO NAKE HAR YANZU, BA BAHAUSHIYA CE NIBA ‘YAR MAIDUGURI CENI, YOU GUYS KNOW RIGHT ‘YAN MAIDUGURI BA’A SASU CIKIN JERIN HAUSAWA. INDA NA K’WARAI A HAUSAN AI BARIN NA SIRKAWA DA TURANCI BA. KUGANE PLEASE KUNA MIN UZURI. MOREOVER, A CHAPTER’N BAYA CHAPTER 15 KENAN, NAGA SHINE NASA TURANCI SOSAI SABODA A OFFICE SUKE, SANIN KANKU NE MASU K’ORAFI BA’A CIKA YIN HAUSA A OFFICE BA, ENGLISH UNIVERSAL LANGUAGE AKE SPEAKING. INA FATAN DAGA YAU MUNYI SOLVING WANNAN ISSUE. THANK YOU SO MUCH, I LOVE YOU GUYS HAVE FUN READING!!!*

   
         Ba tare da ya kalleta ko yace da ita komi ba yacigaba da abinda yakeyi cikin laptop dake gabansa. Tafi minti biyu tsaye sannan ya ciro wata paper daga drawer ya ajiye kan table d’in. “Here is the coffee description, sugar should be minimum.” K’arisowa tayi ta d’aga paper’n lallai ma d’an wannan order’n ne bare irga min ta waya ba seya sa nazo all the way here.
 
           “Sir is that all? Naga ai irin wannan orders muna d’aukawa ta waya.”
           Ba tare da ya kalleta ba daka tsawa “just shut up and leave please!” Har tsakiyar kanta tajiyo wannan tsawa rabuwanta da a daka mata tsawa haka tun barinsu Bama. Take tajiyo hawaye na ciko wa idanta daman ita ba me daure masifa bane, batare da tace komi ba tajuya ta kama tafiya tana share hawayenta nan ne ya d’ago kai yana kallon bayanta har ta bud’e k’ofar ta fice.

       Da misalin k’arfe 3:50PM su Fannah suka iso conference hall d’in komai is in place. 4 on the dot su Anas suka hallaro hall d’in. Fannah na ganin sun shigo ta fice ko sa Anas a ido batai ba, bata masan wani kalan kaya yake sake da ba, se sanda za su soma serving coffee’n ne ta dawo kanta a k’asa take tafiya dan karta jawo attention, haka table by table take bi tana ajiye coffee’n. Table nasu Anas takai k’arshe a hankali ta d’aga kai dan sasa a ido saidai ba direction nata yake kallo ba ya juya yana magana da d’aya daga cikin mutanen kan table nasun. K’eyarsa kawai tagani yadda yayi styling gashin kansa me tsawo wane na bature.

    Bayan ta gama ajiye musu tajuya zata tafi kenan taji familiar voice ya kirata da “waitress” gam ta rufe idanta a hankali ta juya “yes sir” lokacin kuma Anas ya juya yana magana da wasu, k’arisawa tayi ta tsaya daga gefensa “yes sir!” Ba tare da ya kalleta ba yace, “take this away I don’t take coffee.” Kallo ta k’are masa sannan ta d’aga ta fice. Mamaki ne yacika ta wai waye wannan Anas ne ko me sunan san yake feeling like.

      Bayan taron ya watse suka raba kud’in da suka samu sannan ta dawo gida d’aki ta wuce direct. Afrah tasamu se faman chatting take bayan ta mata sannu dazuwa seta karinci kamar wani abu na damun Fannah. “Ya Fannah lafiya?”
          “Wani irin lafiya? wallahi wannan d’an Alhj Muh’d d’in ji da kai ya masa yawa. Bakiji yadda yake ma mutum magana ba ke ko kallon mutum ba yayi.”
      “Kina nufin Anas Ibrahim Fauzi?” Cewar Afrah.
      “Eh wai haka naji sunan nasa amman ya akayi kika sani?”
       “Yanzun nan aka nuna sa a NEWS nake gama meeting d’inda kuka jen ne. Yasa black suit da white shirt da black necktie ko?” Cike da mamaki Fannah ke kallon Afrah. “Eh haka” ta amsa ta.
      “Ya Fannah baki ga kyansa ba wallahi kamar bature.”
     “Toh ai kyansa be amfana sa ba tunda baida hali me kyau.”
      “Ya Fannah waya keta hali? Ke bakiga fuskarsa bane?”
         “Bangani ba kuma bansan gani, ni mubar maganarsa ma he is so arrogant. Barinje inyi wanki kafin Maghrib yayi.”

      Wankin ta takeyi hankalinta kwance tajiyo kiran Afrah daga d’akinsu Baba. “Ya Fannah! Ya Fannah! kizo da sauri.” Nan ta bar abinda take ta ruga a guje ciki acewarta kowani abu ne yasami Afrar dan su Mami basu gida takai Baba asibiti Aiman ta rakata. “Afrah lafiya?” Ta bankad’o labulen d’akin zaune tasamu Afrah gaban TV “Ya Fannah gashi nan! Anas d’in” kafin  Fannah ta kai dubanta kan TV’n har ya juya sede taga kamar ta ga fuskarsa kamar kuma bata gani ba. “Mstw tun d’azu nake kirar ki gashi ai har ya kau da kansa”

       “Yanzu Afrah fisabilillahi akan ganin wannan Anas d’in kika kirani all the way here nafa d’au ko wani abu ne ya same-”
      Bata k’are maganar ba Afrah da hankali ke kan TV tasomsa sabon ihun “gashi nan! gas-” karap NEPA suka d’auke wuta. “Oh damn it! NEPA bakuyi ba.” Tsuka Fannah taja sannan ta koma ta cigaba da aikin dake gabanta.

     
      Wattani da dama sun shud’e...

         Rayuwa ta cigaba da kasance wa Fannah daidai ba abinda ya sake had’ata da Anas. Tana zuwa gun aikinta kullum. Baba kuwa magunan da aka basa a asibiti cikin ikon Allah yana samun sauk’i sosai. Tsoron Fannah d’aya ne rananda magunan zasu k’are bata san ina zata samu kud’i asake sai masa ba. Kullum cikin add’ua take.

   
      Ta b’angaren Anas kuwa abu sunan yadda suke shaye shaye dakuma breaking up da ‘yan mata kullum yana kan yi. Saidai ba kamar da ba, d’an watannin baya da suka wuce sam yadena mafarke mafarken daya saba na Ummimi da kuma yarinyar dayayi raping but kwanan nan sede be kwanta ba seyayi mafarkin yarinyan dayayi raping d’in wai ta dawo garesa. Syrup nasa yake kwankwad’a bayan kwana biyu yasake tashi da mafarkin ji yake yarinyan is somewhere close to him. To kode tana d’aya daga cikin ‘yan matan daya tab’a breaking up dasu ne? Kai! A’a da k’yar ai ita wancan a Bama take. To ina take??

      Shettima dake tsaye a kansa ne yayi ihu dagangan dan tsoratar dashi. “OMG!” cewar Anas da hannu dafe kan k’irjinsa. “K’aniyanka kasan yadda kaban tsoro kuwa!” har yanzu nishinsa be dawo dadai ba. Dariya sosai Shettima ke “hahaha! Kaga fuskarka kuwa? Anyways tunanin me kake har na shigo d’akinka baka sani ba.”

         “Kajima anan ne?” Anas ya tambaya yana k’ok’arin daidaita numfashinsa.
    “Yup about 2 minutes ago” cewar Shettima.
    “Babu, ba tunanin da nakeyi.”
     “Oh common! Ya Anas kama dena min k’arya kasan ko lokacin da ka b’oye min lamarin abinda kama wancan yarinyar a Bama nagane so just tell me what is it now?”
      Tasowa yayi ya zauna, shima Shettiman ya zauna kusa da wansa “tell me ina jinka.”
    Nishi Anas yaja “kasan wani abu ne? Its been long banyi mafarkin wannan yarinya ba but yanzu anytime na kwanta tunanin ta kawai nake ji nake kamar _TANA TARE DA NI_ I don’t know whats wrong kullum cikin tunaninta nake Shettima I can feel it yarinyar bata mutu ba.”

      “Toh fahhhh” cewar Shettima dan ko besan me zaice ma wansa ba he is speechless.
    “Fad’a min Shettima what are you thinking?”
        “Well, Anas maganar gaskia bansan me zan ce maka ba. Yarinyar nan fa a Bama take theres no way zata dawo Maiduguri kuma kai da bakinka kace she was 15 time da abin yafaru who knows ko bata rayu bama an-”
   
        Katse sa Anas yayi “No Shettima I can feel it, bata mutu ba” hannu yasa cikin gashinsa “I don’t know what to think anymore, inasan ganin yarinyar in nemi gafararta Shettima.”

     Kafad’arsa Shettima ya dafa “komai will turn out perfect karka damu, wayasani ko ta kasance d’aya daga cikin ‘yan matan da kake wasa dasu. Saboda baka san fuskarta ba.”
        “But I’m sure ita tasan nawa ai, in ta ganni zata gane ni tunda ita ba’a buge take ba time d’in.”
 
          “Tsab ko zata iya mancewa da fuskarka Ya Anas, katuna da dare ne ranan kuma ruwa akeyi, in har ta rikice beyond imagination alokacin sosai tsab zata mance da kaman ninka. Allah desa bata kasance d’aya daga cikinsu ba.”  “Ameen” Anas yace sannan ya koma ya kwanta tare da zura wa ceiling ido. Wayarsa ya soma k’ara yana kai dubansa yaga family doctor’nsu ne, ba tare da b’ata lokaci ba ya d’aga “Hello Dr Mansur?”
     “Hello Anas kabar duk abinda kakeyi  kazo gidan Babanka yanzu.” ya fad’i cike da tashin hankali sannan karap ya katse wayar.
     “Hello..? Hello...?”
   Zabura yayi yajawo jacket nasa yasa tare da d’auko key’n motarsa ya fice a 360. Bayan ‘yan mintuna ya iso gidan Mr. Muh’d. Sama ya haura direct zuwa d’akin Mr. Muh’d can yasamu Dr Mansur tsaye a bakin k’ofar. “Dr Mansur whats wrong? Meya samu Baba?”

       “Anas is about time kasan gaskiya Babanka yata b’oye ma gaskia saboda bayasan ya saka cikin tashin hankali amman yanzu da lokaci yariga ya k’ure I have to tell you.”
    Take idanun Anas ya cike da hawaye “meke faruwa Dr. Mansur? Meya samu Baba?” ya tambaya murya na rawa.
     “Anas calm down tunba yau ba Baba ke suffering da cutar cancer.”

      “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” Anas ya saki salati. “No thats not true please karka ce haka Baba baida cancer.” Kuka yasoma yi sosai.
      “Anas thats why nace maka you need to calm down yanzu ba lokacin musu ko kuka bane addu’a zaka masa. Kasan shi matsalar cancer ba’a cika discovering na sa da wuri ba bale ayi maganinsa saboda bai da symptoms cin jiki yake sosai the moment ya kama mutum. Haka yasamu Baba ma, yau shekara kenan yana fama da cutar a iya sani na kenan. Duk sanda kaji Baba yace maka zeyi tafiya to ciwon nasa ne yatashi.”

     “Dr Mansur niba wannan ba dan Allah” yasa hannu ya share hawayensa. “Do something to save him please.”
    “I’m so sorry Anas but its too late, saisa nace maka addu’a zamu masa yanzu lokackin Baba yayi, be a man please, kai kad’ai Mr. Muh’d keda bayida wani family bayan kai, you have to be strong.”
       Inaaa Anas se kuka sun shak’u da Baba sosai wane Abuu. Kuka yake sosai Dr. Mansur na basa hak’uri ganin ba mahillici se Allah yasa ya share hawayen sa a hankali ya bud’e k’ofar d’akin Mr. Muh’d. Kwance yagansa rai a hanun Allah wani kukan yasake faso masa jiki a sanyaye ya k’arisa gaban gadon nasa ya tsuguna tare da rik’o hannunsa yana kuka.

          “Baba dan Allah kar ka tafi kabarni, kar ka tafi kabar Enterprise naka we need you.” Magana ciki ciki Baba yace, “shhh Anas, bar kuka ni zan tafi amman na bar musu kai. Kai na mallakawa Enterprise d’ina da duk wani abinda na mallaka”
      “Noo... Nooo please Baba” Anas ya katse sa.
      Baba yacigaba “na riga nayi signing komai under your name Anas, kamar yadda nasan ka da hankali da hardworking ka cigaba da kula da Enterprise d’in koda a bayan raina, naka ne yanzu banida ikon in fad’a maka abinda zakayi dashi, just do what is right. Ban samu naga su Abuu da Amal ba tell them am sorry.”

      “Baba please kabar magana haka in shaa Allah zaka tashi baraka mutu ba please.”
      Wani irin numfashi Baba yasoma yi da k’arfin gaske.
      Gamgam Anas ya rik’e hannunsa yana ihu “No! No! Baba dan Allah karka tafi Dr. Mansur! Dr. Mansur!” a guje Dr. Mansur ya shigo saidai shima ba abinda ze iya tsayawa yayi daga gefe d’aya yana kallon yadda Baba ke nishi. “Dr. Mansur do something to save him please karka bari ya mutu.”

        “Anas I'm so sorry amman ba abinda zan iya masa, lokacinsa ne yayi.”
      “La ila ha illallah muhammadur-rasulillah salla-” be k’are ba numfashinsa ya yanke kap. Ihu Anas ya k’urma “Noooooo! Baba you can’t die please” hugging Baba yayi yana kuka yana jijjik’asa Dr. Mansur ne yazo yana k’ok’arin d’aga sa daga jikin gawan Baba amman ya kasa haka ya zuba wa Anas yana kukan cire rai yana basa hak’uri. Sun musan minti talatin sannan Anas ya tashi a garin yin haka wayarsa ta fad’i kasa “Ina zakaje Anas?” Cewar Dr. Mansur.
    Idanunsa sunyi jazir wane barkono blue eyes nasa sun k’ara shiga. Batare da ya kalle sa koya ce dashi komi ba yafice be tsaya ko inaba se bar (gidan giya) inda yaje ya bugun buguwa. He can’t take it mesa Baba ze mutu ya barsa?

      Wayarsa Dr. Mansur ya d’aga ya kira Abuu ya sanar dashi halin da ake ciki salati kawai kukeji. Bayan ya ajiye wayar ya rufe gawan Baba sannan ya fito a ranan aka ma Baba wanka aka sallace sa aka bisine sa. Kuka sosai kowa yake, ‘yan Maiduguri sun mugun jin mtuwan Mr. Muh’d. NEWS na ranan kap Mr. Muh’d aka yini ana nunawa.
     Ba inda ba’a nemi Anas ba an rasa ina yashiga se Allah, gashi wayar sa bata gunsa. Ranar de ta kasance a very bad day wa mutanen Maiduguri all in all.

     Se washegari da safe Anas ya dawo gida Allah yaso daya dawo Abuu da Ummie basu nan Shettima kad’ai a gida shi ya kula da Anas. Sosai Anas ya bugu ko d’aga k’afa bai iyawa Allah kad’ai yasan ya yadawo gida lafiya. Bayan Shettima ya tayasa rage kayan jikinsa ya kwantar dashi tare da rufe sa da bargo. Bacci sosai Anas yayi se shabiyun rana ya tashi. Shettima yagani zaune a gefensa yana karatu.

     Kansa ya rik’e yana k’ok’arin zama. Nan ne Shettima ya jiyo ya kallesa cike da tausayi. “How are you feeling Ya Anas?”
       Kallonsa kawai yayi ba tare da ya amsa sa ba.
     “Ya Anas hak’uri zakayi Baba lokaci yayi, zuwa gidan giya ka bugu is not a solution. Ba abinda ze amfanar da Baba kamar yadda bare amfanar dakai ba kaima. Addu’a ya kamata ka masa.”
 
         “No Shettima bara ka gane ba, baraka tab’a ganewa ba. Why is my life always like this? Se lokacin dana soma jin dad’i Baba ze tafi ya barni da burden na Enterprise nasa. Baran iya ba Shettima I can’t manage his company.” A hankali ya soma kuka kamar d’an yaro.

 
    © miemiebee

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 17
BY MIEMIEBEE


 
      “Oh common please Ya Anas, kowa yasan how you must be feeling, hak’uri zakayi ka d’au wannan ma wata k’addara ce.” Cewar Shettima yana shafa bayan Anas dake kuka. Daidai lokacin su Abuu da Ummie da Amal suka shigo kan gadon Anas Amal tayi. Ganin wanta na kuka itama tuni ta fara “Ya Anas bar kuka kaji? In shaa Allah Baba is in a better place yanzu.” Rungumosa tayi yana kuka ajikinta kamar d’an yaro.

          “Anas hak’uri zakayi, munsan yadda kaji mutuwan Alhj Muh’d amman yazama dole kayi tawakalli ga Allah kayi masa addu’a lokaci ne yayi. Yabar duk wani prperty’nsa maka inda hali zuwa anjima ‘yan jaridu sunasan magana dakai dangane da faruwar wannan abu.”

       “Noo Abuu please, ni baran iya kula da enterprise na Baba ba baran iya ba, kabawa ‘yan press hak’uri baran samu zuwa ba. Ni Enterprise nasan ma baran iya handling ba, I can’t.” Ya sake fashewa da kuka.

     Ummie ce ta k’ariso ta karb’esa a hannun Amal, “yes you can Anas, zaka iya. Babanka bare ji dad’i ba inda ze dawo yanzu yaji abinda kake cewa, ya bar maka company’nsa ne saboda ya yarda da kai da abilities naka, he is sure zaka iya cigaba da gudanar da lafiyar conpany’n saisa yabaka karka basa kunya Baba na. Kayi hak’uri kukan nan baida amfani gacan abinci na had’aka maka kaci kaje mutanen suna jiranka a TV station ko muce suzo ne?.”

     Kai ya kad’a yana kuka sosai. Bayi ya fad’a dan yin wanka amman wankan ma yakasa damuwa sun masa yawa shower kawai ya kunna ruwan nata zuba kansa kusan na minti ishirin sannan yafito yasa kaya yafice zuwa dining inda Amal ke zaune tana jiransa itama idanun nata sun kumbura sunyi ja. Serving nasu abincin tayi kamar yadda suka saba a plate d’aya sukeci. Sede ko kad’an yau Anas baici. “Ya Anas kayi hak’uri dan Allah kaci, karka zauna da yunwa.” cewar Anas.

        Hawaye taga na cikowa idanunsa, hannu tasa ta tare “Ya Anas kasan baran iya jure kukan kaba please kayi hak’uri.” Be iya yace mata komi ba hannu kawai ya aza kanta tare da mata murmushin dole sannan ya kai spoon d’aya baki bayasan jin Amal na had’asa da Allah kwata kwata spoon biyar yayi yace mata ya k’oshi. Yabari su Abuu su raka TV station d’inma yak’i yana isa wajen ‘yan press tunda ga waje suka soma binsa har sanda ya shiga ciki.

    Bayan an basa kujera ya zauna suka soka jero masa tambayoyi wanda kad’an daga ciki ya amsa sauran kuwa kuka suka sa sa haka fa kamar d’an yaro Anas ya bud’e dandalin kuka a TV station su kuwa se recording suke direct ana uploading a news Nigeria’s most youngest billonaire.
      Ba’a gama interview d’in bama yatashi yafice dan yadda kuka yafi k’arfin sa. He wanted to be strong amman ina bare iya ba, besan dawani damuwa ze fara handling ba, na Ummimi ne ko kuwa na ‘yar dayayi raping ko na mutuwan Baba kokuwa na managing babban enterprise da Baba ya bar masa. Yakasa tunani giya kawai ne in yasha ze warkar masa da wannan damuwa gidan giyan ya koma ya sake buguwa sannan yafito ya kwanta cikin motarsa har bacci me nauyin gaske ya iske sa.

    ****
        “Ya Fannah yi sauri kizo kiga abin tausayi, hurry!” Afrah ta danna wa Fannah dake kitchen kira. Wanke hannu tayi tafito da wuri.
      “Kiga yadda d’an Alhj Muh’d ke kuka, Allah sarki.” cewar Afrah. Fannah na kai dubanta kan TV’n taga Anas zaune kan kujera da hanky rik’e a hannayensa biyu ya rufe fuskar sa dashi se kuka yakeyi kamar d’an yaro se kace besan da camera kota ina a gaban sa ba. “Allah sarki!” tace “Allah jik’an Alhj Muh’d, yasa k’arshen wahalarsa kenan.”

     “Ameen” Afrah dake jin kamar tayi joining Anas suyi kukan tare. “Kinsan kuma me worse part d’in? Fannah ta kad’a kai. Akace a idan Anas d’in Baban nasa ya rasu, yana ji yana gani mutuwa ta musu katanga, Allah sarki!”

     Tausayi Fannah taji yabata jibi yadda yake kuka sekace bashine mara mutunci me gasa wa mutane magana ba, sekace ba shine me uban jijji dakai ba Allah sarki rashi. Dan yadda Anas ke kuka yasa ta fito daga d’akin ko fuskarsa yakasa bari agani tasan sarai ta k’ara minti d’aya a d’akin kuka zata soma dan hawaye bai bata wuya ga kuma uban tausayi...

        Haka fa tun daga ranan rayuwar Anas ya lalace yafi na da worse ba aikinsa se shaye shaye barin gida ma gabad’aya yayi ya kama hotel yadda yake shaye shayensa hankalinsa kwance.

       Safe, rana, yamma, dare Anas na rik’e da bottle na giya a hannu yana sha. Da rasuwan Baba yau sati biyu kenan amman Anas ji yake kamar yau yau d’innan Baba ya rasu sau kusan kullum yake kai ziyara gidan Baba, masu aiki ya nemo dasuna kula da gidan, a rana se anyi shara da mopping sau biyu wane akoi mutum ciki. Tun rasuwar Baba kuwa ya rufe company’n har yau ba’a bud’e ba masu aiki a wajen ba yadda basuyi dashi ba ya bud’e su koma aiki amman yak’i shi a tunaninsa bare iya handling ba bayasan ya b’atawa Baba koda k’wayan zarra ne cikin company’nsa. Allah kad’ai yasan wahalar dayasha kafin yasamu ya gina wannan sky scrapper saboda haka yake jin tsoro sosai kar yayi wani abu yayi ruining abu ciki.

Kusan sati uku ake nema yau Anas yak’i bud’e company ga on going projects dayawa nan barkate. Daga k’arshe sanda ‘yan manya manyan wajen suka je suka ma Abuu bayanin komai sannan ya ce musu zema Anas d’in magana. Bayan tafiyar mutanen, Ummie dake taya Amal tsifa tace, “Ya Ibrahim wallahi Anas tausayi yake ban, ba laifinsa bane yaro yake har yanzu dudu shekarunsa 24 nefa, he is still young.”
    “Saisa yakamata ya bud’e office  d’in, yayi hak’uri ya rungumi k’addara k’in bud’e company’nsa ba taimakasa masa zaiba kin deji abinda masu aikin nasa sukace akoi on going projects dayawa  kuma koba dan wannan bama yau ace Alhj Muh’d na raye ai bareyi farin ciki da abinda Anas keyi ba. Kowa ya tausaya masa shiima yayi hak’uri ya tausaya wa kansa.” Shiru Ummie tayi ta giad’a kai. Amal kuwa idanta tuni suka cike da hawaye rabuwanta da sa Ya Anas a ido har tamanta tun da yabar gidan kota kirasa wani sa’in ma bai d’ agawa yadda zakusan lallai Anas yashiga wani erin yanayi kenan. Ace Amal ma gabad’aya yak’i picking call nata. Allah sarki!

 
         Anas na zaune k’asan carpet a hotel room nasa da giya hannunsa se sha yake ba makawa, gashin kansa ya tarwatse wane na mahaukaci, d’akin duk warin giya yake. Ko ina kwalb’an giya kuke gani ko masu giara sunzoyi bai barinsu su shiga. Kan gadon ne kawai kenan tsatsaf shima d’in saboda ya k’aurace wa kwanciya kai ne a k’asa yake kwanciyarsa yanzu. Wayarsa dake kan gado ya soma ringing haka yana ji amman yakasa koda d’aga k’afa bale yaga kowaye. Haka ya d’aga giyan hannun san yakai baki sanda ya kurb’e tas sannan ya wurgar a k’asa kamar yadda ya saba. Bajewa kawai yayi a k’asan tare da zira wa ceiling ido. Can wayar tasan ta soma ringing again nanma yanaji be d’aga ba se a karo na uku yayi rarrafe ya d’aga idanunsa wani dushe dushe suke gani mai yama kasa gane wake kira kawai picking up yayi ba tare da yace komi ba.

      “Hello Anas?” Cewar Abuu shirun dayaji yasa yasake fad’in “hello? Anas baka ji ne? Hello?”
      Ai kawai Anas ya fashe da kuka cin wayar kamar d’an yaro. Hankalin Abuu in yayi dubu be tashi ba gashi basu san wani hotel Anas ya kama ma. “Anas! Anas until when zaka koyi rungumar k’addara ne wai? Kasani Babanka ya riga y rasu duk wannan abinda kakeyi ba dawo dashi zeyi ba. Haba! Mana Anas sekace bana miji ba, man up please. Kap kowa jira yake ka bud’e company’nka amman kak’i se yaushe wai? Iyye?”  Shiru kukeji ba response ko kukan ma yadena ji. “Hello? Anas!” Aikam tuni Anas yayi hanging up call d’in se kuka yake ba makawa. Shi har yanzu be yarda cewa Baba ya tafi ya barsa ba, Baba yatafi yabar masa company’nsa daya kula dashi. Yana cikin kukan Shettima ya kira yanaji yak’i d’agawa kusan missed calls biyar sannan ya d’aga nanma shiru yayi bece komi ba.

      “Hello Ya Anas” muryan Shettima ya jiyo. “Ya Anas kana ina?” Shiru yayi be amsa saba. “Ya Anas dan Allah kana ina? Wallahi duk mun damu ka fad’amin inda kake.” Amsar wayar Amal dake kuka tayi “Ya Anas yanzu seka tafi kabarmu dan Allah ka dawo gida” ta kuma fashewa da kuka. Jin kukan Amal yasa sa magana bayan ya daidaita muryarsa dan kar tagane a bige yake. “Shhh! Kinji Angel bar kuka, zan dawo amman ba yau ba.”
“Toh kana ina?” Ta tambaya.
      “Ina nan cikin Maiduguri.” Amsar wayar Shettima yayi “Ya Anas tell me ina kake inzo in sameka.”
     “Nooo bareyi kazo ba right now am drunk banasan su Abuu da Ummie suzo...” Aiko ya fara magana kamar zararre “kar su zo sugan ni ahaka sukamu da cancer” bama ciwon zuciya ba. Yad’anyi dariya “wayasani ko suma su mutu.”

         “Ya Salam!!!” Shettima ya fad’i. “Me ya same sa Ya Shettima?” Amal ta tambaya tana  kuka. “Ba komai” Shettima ya mata k’arya “jeki ina zuwa.” A sanyaye ta tashi ta fice. Tana fita Shettima ya dawo kan wayar.
        “Ya Anas what are you saying? Yanzu fisabilillahi tun tafiyar ka can kata shaye shaye? Ina kake yanzu.”
     “Chill little bro! Karka damu am somewhere safe.”
       “Ya Anas ka fad’amin inda kake inzo in duba ka please kaji?”
      “Saboda kazo dasu Ummie da Abuu sugane ina shaye shaye?” Anas yafad’i idanunsa suna kakkafewa besan sanda yabada address d’inbama kawai ya zarce bacci. A gurguje Shettima ya fito ya samu su Abuu a parlour duk hankalinsu ya tashi. “Ya haka? Ina zuwa?” Abuu ya tambayi Shettima. “Wajen Ya Anas zani Abuu.” yabasa amsa.

       “Tsaya muje tare toh mana.”
       “A’a Abuu please kayi hak’uri yace inje ni kad’ai bareji dad’i ba in ya ganmu duka kubar damuwa Ya Anas is somehwere safe.”
        “Anya kuwa Shettima?” Cewar Ummie cike da damuwa. “Kabari muje duka mu gansa dan Allah.”
      “Ummie please kar mu fara ce in ce, Ya Anas made it clear to me ni kad’ai yakeson in je kuyi hak’uri.”
    “Bakomai Shettima Allah kare kakuma isar masa d sak’on.” Abuu ya fad’i.
       “Toh Abuu” nan ya ja mota ya fice. Daidai ya isa harabar hotel d’in yafito bema san room number’n da Anas ke ciki ba, ko daya tambayi Anas d’in kuwa shima ce masa yayi besani ba tsantsan yadda ya bugu kawai.

     Reception ya wuce yayi tambaya k’in fad’i masa tayi acewarta ko yazo cutar dashi ne. “‘kaninsa ne ni can’t you tell? Bakiga muna kama bane?” ya daka mata tsawa. “Now tell me his room number.” Kallon fuskarsa tayi a tsorace sannan taga eh fa suna kama “I'm sorry sir room 21 CEO’n Flames Enterprises yake.” Da gudu ya haura sama zuwa room 21. A bud’e ma ya tarar da k’ofar yana sa kai warin giya ya masa sallama. Salati kawai yake yana bin d’akin da kallo kwalb’an giya sekace na siyarwa. Toshe hancinsa yayi tare da rufo k’ofar akan gado ya tsinci Anas yayi ruf da ciki se bacci yake. Kwata kwata singlet ne a jikinsa seda short nicker. Gashin kansa daya tarwatse ya rufe kad’an daga cikin fuskarsa. Juyar dashi Shettima yayi tare da kiran sunan sa. Shiru kukeji ba amsa. “Ya Anas! Kana jina?”
     “Uhmmmm” ya fad’i idansa rufe yana bacci. Giara masa kwanciya Shettima yayi tare da rufe sa da bargo sannan yakoma k’asa yakira masu aiki suka kimtsa d’akin tsaf aka sa room freshner me uban k’arfi da dad’i dan kora warin giyan.

    Baccin awa uku Anas yayi sannan ya farka a hankali ya soma bud’e ido ya saukesu kan Shettima. K’ok’arin zama yake Shettima ya taimaka masa.
      “Ya Anas how are you feeling?”
    “Yaushe ka shigo nan? Ya kasan ina nan?” Tambayar da ya masa kenan.
       “Kai kafad’a min, but it doesn’t matter. Ya Anas this has to stop. Ya isa fisabilillahi me damuwarka ne? kai bakasan meh k’addara bane a rayuwa? Kashe kanka kakeson yi kwalaban giya kusan 30 a d’akinka hauka ne kuma abin?”
      Ba tare da ya amsa saba yace, “inasu Abuu kataho dasu ne?”
       “Ban taho dasu ba amman believe me ina komawa gida zan sanar dashi da Ummie wannan halin naka na shaye shaye tunda you are not ready to change. Ina ka tab’a jin dan an ma mutum rasuwa seya soma shaye shaye haka? Haba mana Ya Anas.”

         “I’m sorry” ya fad’a a hankali cike da jin haushin abinda yayi. “Shettima I’m sorry, giyan ne kawai in nasha nakejin problems d’ina sun tafi. Shettima kubar ganin laifi na please abubuwa ne sun min yawa I'm just 24 baran iya managing babban Enterprise kamar na Baba ba. Baran iya ba, it is beyond my will.” Sekuma ya fashe da kuka. Da had’in Allah da Annabi da kuka sannan Shettima yasamu yayi convincimg Anas kan bud’e company’n.

       Wanka yasa sa yayi yana fitowa ya masa ordering abinci sosai Anas yasamu yaci. “Thank you Shettima, bansan ya zanyi ba without you.” Hugging nasa Shettima yayi “me too brother dan Allah ka rage shaye shayen nan kar alcoholic level naka ya haura yazama toxic, dan Allah.” Hugging nasa back Anas yayi “in shaa Allah zan rage.” Bayan sun sako juna Shettima yace, “lets go ga kayakin ka nan duk na shirya maka.”

     Tare suka sauk’o bayan Anas ya biya bills nasa suka dawo gida cikin motocin su. Amal na zaune bakin k’ofa tun d’azu tana jiran dawowarsu gate taji an bud’e da sauri takai dubanta ganin motan Ya Shettima k’aramar benz C230 yasa ta koma baya ta zauna tana sake juyawa kawai taga motar Ya Anas tsalle ta daka tayi wajen parking da gudu yana fitowa sukayi huggibg junansu sosai. “I miss you Ya Anas” tace tana hawaye.

© miemiebee

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 18
BY MIEMIEBEE


     “I miss you too my Angel, bar kuka barin sake tafiya ba, I’m back forever.”  “Yeyy!” tasake hugging nasa. Bayan sun shigo su Abuu da Ummie duk sukayi hugging nasa sun mugun jin dad’in dawowansa. “Sannu da zuwa Baba” na cewar Ummie, “kar ka sake tafiya dan Allah.”
       “In shaa Allah Ummie.” Anas yayi assuring nata.
      “Erm Anas I’m sure Shettima ya sanar dakai halin da ake ciki koh? Ma’aikatan company’nka har gidan nan sukazo suna rok’o na in maka magana sukoma office.”
     “In shaa Allah monday zan bud’e Shettima ya fad’a min komai. I’m sorry baran sake barin gidah ba. Problems ne suka min yawa Abuu bansan ta ina zan fara solving ba.”

         “Anas just know we are here for you running is never a solution.”
        “In shaa Allah Abuu barin shiga daga ciki.” Amal dake mak’ale kan cinyarsa ta tashi tare da k’ara mak’ale hannunta a nasa. “Kekuma Amal ina zaki?” cewar Ummie. “Zanbi Ya Anas d’akinsa.”
   “A’a kinga Ya Anas ya gaji yana neman hutu da bakin kinnan zaki damesa.”
     “Ummie mana, barinyi surutu ba” tafad’a tana bubbuga k’afa.
     “Don’t worry Ummie, taho muje my Angel.” Gwalo Amal tama Ummie sannan tabi Anas d’akinsa.
 
    Bayan ya rage kayan jikinsa ya haura gado tana zaune kan couch “Ya Anas ina kaje daka tafi?” Ta tambayesa.
    “Hotel Angel.”
    “Ohhh! kasan kowa yayi kuka daka tafi, tunba ni ba we all miss you blue eyes.”
Ido ya zaro “Amal ina kika san sunan nan?”
    K’arya tayi “babu kawai ni na had’a.”
      “Yau ni kike ma k’arya? Saboda kinsan password d’ina kika fara min shisshigi a waya ko?” ya tambayeta.
      “A’a fah Ya Anas ranan ne wata ta turo message lokacin ina game a wayan shine... Shine..” Sekuma tayi shiru.
     “Shine kika bud’e kika karanta koh?”
     “I’m sorry Ya Anas please karka canza password d’in.”
    “Toh naji barin d’an kwanta koh?”
     “Okah ba-bye” nan ta mik’e ta fice.

        Washegari...

Yau ta kasance Monday da safe Anas ya tashi ya shirya cikin black suit, black shirt da white necktie wanda yamun masa kyau bayan yayi  breakfast yaja benz na sa ya fice zuwa office. Daidai k’arfe takwas ya isa mutane turum ya tarar bakin k’ofar duk shi suke jira yana fitowa sukayi kansa suna gaishesa da “Boss” bayan ya bud’e office d’in ya shiga  elevator zuwa last floor inda new office nasa yake. Kallon office d’in kawai yake se gani yake kamar Baba ze shigo ya zauna kan office. Ba abin arzikin dayayi ranan inbanda  tunanin daya tayi seda signing papers da ake ta kawo masa. Sosai su Kacallah da Yunus suka yi condoling nasa kamar yadda duk sauran ma’aikatan suka masa. Sam be saba ba in suna kiransa da Boss. Aranan akayi renovating office d’in yakoma komai na ANAS IBRAHIM FAUZY.

     Office ne babban gaske me ciki biyu wanda harda d’aki ciki. Fridge, California bed, TV ba abinda babu ciki.
     Da yamma da misalin k’arfe 4:00PM daidai lokacin da suka tashi bayan Anas ya tattara stuffs nasa Kacallah ya shigo. “Uh sorry Boss bansan har ka tashi ba, wallahi seda aka tashi Ahmaz investment daga Kaduna suka kawo wannan kuma gobe zasu koma. “I’m so sorry please.”
   “Bakomai” Anas ya fad’i yana murmushi “kawo inyi signing.”  “Thank you Sir! You’re so kind.” Nan Anas ya zauna bayan yayi signing Kacallah ya sake masa godiya yakai da bakin k’ofa Anas yace, “uhm Kacallah are you free?”
     “Yes Sir wani abu ne?”
      “Ba abinda zanyi yau nace ko zakazo mud’an fita maybe muje muyi having snack tare I need someone to talk to.”
     “Oh yes ofcourse Sir barin kai wannan kafin su tafi.” Kai Anas ya giad’a masa “thank you”
    “The pleasure is mine sir.” Nan yafice bada dad’ewa ba ya dawo suka shiga elevator tare. A motan Anas suka fice, “so ina kakeso muje?” Anas ya tambayesa.
 
       “Duk inda kace will be fine Sir.” Cewar Kacallah cike da girmamawa.
    D’an murmushi Anas yayi “in mu bibbiyu ne kana cemun Anas kawai.”
      “I’m sorry sir amman baran iya ba, girman ka yayi yawa ace na kiraka da sunan ka. I’m sorry please.”
    “Tun da haka kace fine, so ina zamuje.”
     “Muje Fahmaz coffee shop Sir.”
   “Fahmaz Fahmaz...” Anas ya tsaya nazarin abu “ohh sune wanda in an kirasu waitresses nasu basua magana a wayan nan koh?”
   “Ahha Sir nakega basu gane ko kai waye bane. Muje chan d’in please you’ll like their services.” Ba musu Anas ya tuk’asu zuwa coffe shop nasu Fannah.

    Bayan yayi parking suka fito suka shiga tundaga bakin k’ofa aka fara tarerayar su Anas anga Nigeria’s most youngest billonaire. A special table suka zauna. Ya suleiman ne yazo ya musu sannu dazuwa da kansa sannan ya d’auki order’n su. “Mr. Fauzy is my honour having you here at my coffee shop what can I get you?” Ya fad’i yana washe 32.
   Kai Anas ya giad’a masa sannan ya dawo da kallon sa kan Kacallah. “Me zamuyi ordering?”
     “Sir nikuma zan mana ordering please do, ni ai duk abinda ka mana ordering I’m fine with it.”
    “No Kacallah I insist ka mana ordering. Feel free with me please.”
        “Tunda kace haka sir OK. Akawo mana caf`e lat`e.”
     “Unfortunately bana shan coffee.” Anas ya fad’a yana kad‘a kai.
     “Ohh sorry sir but da ka gwada gaskia nan coffee shop suna k’ok’arin yin coffee.”

     “Yes Sir” cewar Ya suleiman “ka gwada coffee’n mu I’m sure you will not regret it, please.”
       “Tunda kunyi insisting okay. Get us two caf`e lat`e.”
      “Thank you sir” sannan ya fice yana shiga ciki ya soma k’olla wa Fannah kira. Nan tafito tana daidaita hijabinta. “Yes Boss!” Ta fad’i cike da gatsine. “Yawwa yau zo ke zaki had’a coffee’n nan. Inason ki had’a coffee’n da baki tab’a had’awa ba.”

        “Tohhh d’an shugaban k’asa ne yazo coffee shop namun?” Ta tanbaya tare da d’age gira.
     “You will find out in kika kai musu. Two cups, ki had’a yayi kyau please Fannah give it your best. Table 03.”
   “Okay Sir” tace tana dariya. Nan ta hau had’awa bayan 3 minutes ta gama ta aza kan tray sannan ta fice. Kanta a k’asa tana kaiwa zuwa table 03 ta gaishesu tare da ajiye wa a gabansu.
 
     “Thank you” Kacallah ya fad’i nan ne ta d’aga kai ta kallesa “you’re welcome” ta masa murmushi jin d’ayan bece komi ba yasa ta juya ta kallesa lokacin kuwa hanky Anas ya cire yana goge fuskarsa se bata samu ta gansa ba. Tana ajiyewa ta fice.

      Anas na kai coffee’n baki yaji k’amshi sosai. Dayasha kuwa yaji dad’insa sosai tunda yasan kansa be tab’a shan coffee me dad’i ba kamar na yau ba last time dayasha a London kwata kwata be masa dad’i ba sesa yabar sha ma. Be cire cup d’in daga bakinsa ba sanda ya kurb’e duka. “Wow! coffee’n nan yayi dad'i sosai, this is the first time coffee yamin dad’i. In ba damuwa inason in k’ara.”
   Murmushi sosai Kacallah yayi “I told you sir. Waiter!” Ya kira wani na miji me uniform “caf`e lat`e zaka k’aro wa Boss d’ina.”
     “Okay” ya fice nan da nan yaje ya had’o ya kawo saidai da Anas ya tab’a ya ji na d’azun yafi dad’i. Da kyar ya had’e dan yadda ya yamutsa fuska yasa Kacallah tambayan ko lafiya.
    “Sir are you okay?”
    Ajiye cup d’in yayi “ba wannan nasha d’azu ba. Irin na d’azu nakeso.” Anas yace.

     “Sir” cewar waiter’n. “Caf`e lat`’n daka buk’atan nefa kalan na d’azu.”
   Tsawa Anas ya daka masa “No!” “nace ba eri d’aya bane kaje ka sake had’o min irin na d’azu.”
  “But sir-”
     “I said now.” Anas ya sake daka masa tsawa. A tsorace yabar wajen.
    “Sir I'm so sorry please” cewar Kacallah. “Is okay ba komai.” Anas ya tabbatar masa.

    Shigar waiter'n ciki yasamu Ya Suleiman. “Ya akayi Harauna?” Cewar Ya Suleiman.
    “Ya Suleiman CEO’n Flames Enterprises ne yace na had’o masa caf`e lat`e na had’o masa kuma wai ba irinshi yakeso ba, wai ba irinsa yasha d’azu ba.”
     “Omg!” Ya Suleiman yayi exclaiming.
  “Ina Fannah? Jeka kirata ita ta had’a masa kace tazo ta barinje in basa hak’uri” da “toh” suka rabu. Isan Ya Suleiman cikin shop d’in yayi kan table nasu Anas. “Sir please kayi hak’uri anje kiran yarinyan data had’a na farkon ne yanzu zata zo kayi hak’uri dan Allah.”

      “Make it quick inada abinyi please.” Cewar Anas nan Haruna yafito “Ya Suleiman Fannah bata nan ta tafi yanzu Asma’u ke fad’a min.”
    “What!?” Cewar Ya Suleiman. “Taya zata tafi? This is the first time take barin nan bata fad’a min ba.” Nan ya kewayo da kallonsa kan Anas.
    “Mr. Fauzy I’m so sorry please yarinyar data had’an ta tafi gida nakega emergency ne yataso but akoi wata itama ta iya had’awa sosai barin mata magana.”
   
      Ran Anas tafasa yake, “then make it quick!” Yafad’a a tsawace.
    Bayan ‘yan mintuna Asma’u tafito da coffee’n Anas. Tana ajiyewa ya d’auka yayi sipping nan ma taste d’in be masa ba wurgi ma yayi da cup din coffee’n ya zube a yayinda cup d’in ya tarwatse b’ari Asma’u ta soma. “Wai ace nan cofee shop amman ba me iya had’a coffee?” Ya Suleiman ne yafito yana ganin irin b’arnan da Anas yayi shi bama wancan ba kar Anas yasa ayi sueing coffee shop nasu.

    Hak’uri ya soma basa. “Mr. Fauzi wallahi wanda ta iya had’awan ne ta tafi gida.”
    “Wacece ita?” Anas ya tambaya rai b’ace.
   “Fannah ce Sir Fannah Aleeyu.”
    “Koma wace ita call her now kace mata ta dawo and make me coffee.”
      “Yyesss sir” Ya Suleiman ya amsa baki na rawa. Wayarsa ya ciro ya kira Fannah har ta tsinke bata d’aga ba se a karo na biyu. “Hello Fannah ina kikaje? Ki dawo please is urgent.”

      “Ya Suleiman jikin Baba ne yatashi yanzu haka asibiti zamu kaisa bareyi in dawo ba.”
   
     “Fannah dan Allah su Mama barasu iya kaisa ba? Nasan lafiyan Babanki means alot amman you are needed here rashin zuwanki ze iya jefa lafiyar coffee shop in mu cikin matsala please.”

     “Ya Suleiman if only I can come, baran iya barin Baba ba dan Allah kayi hak’uri I have to go” karap ta kaste wayar. Fuskar Ya Suleiman kad’ai amsa ce ga tambayar Anas. “So?” Ya tambaya

     “Sir we are so sorry amman yarinyar barata samu zuwa ba.”
     Kallonsa Anas yake “kasan ko ni waye ne? Nace ka kira Fannah take ko meh and tell her tazo ta had’a min coffee.”
       “Mr Fauzi mahaifinta ne ba lafiya saisa barata iya zuwa ba.” Anas najin ance mahaifinta yaji ya hak’ura. “Okay” yace tare da ajiye musu N1,000 kan table d'in yaja jakarsa a yayinda Kacallah yabi bayansa.
      Mamaki ne yacika Ya Suleiman da Asma’u daga jin ance mahaifinta kawai ya canza mind nasa ga kuma dubu d’aya daya ajiye musu ba tare da ya amshi chanji ba. Shide gode wa Allah yayi.

   _Wahsegari..._

     Da misalin k’arfe uku da rabi Anas ya zo coffee shop nasu Fannah shi kad’ansa. Tun jiya ya kasa bacci dan kwad'ayin coffee’n dayake tayi. Sam yarasa meke masa dad’i duk abinda yasa a bakin sa bai masa dad’i shi coffee d’in kawai yakeso duk ya k’osa yasake sha. Bayan yashigo aka karb’esa da girmamawan daya cancanta, nan yayi ordering caf` lat`e. Bayan yaron ya juya Anas ya kirasa “and kace Fannah... Fannah Aleeyu ce ta had’a and no one else okay?”
   “Okay” yaron yace masa. Yana shiga yasamu Fannah zaune tana buga gamw a wayarta yakai mata order’n ba tare da ta kallesa ba tace, “wai nikad’ai kake gani anan ne Boy? Ga Asma’u da Allah ka kai mata kaga game nake yi hak’uri.”

     “Ya Fannah shi wanda yabada order’n ne yace ke zaki had’a.”
   Baki wangalau Fannah ta bud’e lallai ma “yaushe aka fara wannan sabon salo? Coffee ba coffee bane waikam. Koma waye ne yayi hak’uri barin had’a ba tunda ba shift d’ina bane, Asma’u da shift nata ne ta had’a.” Daidai lokacin Asma’u ke shigowa cikin kitchen nasun. “Yawwa gara ma da kika shigo. Gashi caf`e lat`e zaki had’ama wani kiyi sauri.”

     “Waye ne?” Asma’u ta tambayi yaron. “Nima bansan sunansa ba.”
   “Ya yake? Fari ne yanada blue eyes?”
 
     “Eh” yaron ya giad’a kai. “Fannah dan Allah kiyi hak’uri ki had’a masa wallahi shine wanda yazo jiyan.”

    “Wai waye shi duk kika bi kika tsure haka?”
     “Fannah wallahi shine, Mr Fauzi d’an marigayi Alhj.  Muh’d.”
    “shi???” Fannah tafad’i tare da zaro ido.
      “Fannah dan Allah wallahi naki kawai yakeso, jiya nida Haruna muka had’a masa coffee wulli yayi dashi, please Fannah” ta k’are maganar kamar zatayi kuka.
    “Chabdi!” Cewar Fannah “ai gara ke ni da kike gani nannan wallahi banasan abinda ze sake had’ani da Anas d’innan ranan har kuka sanda yasani.” Daidai lokacin Ya Suleiman yashigo ransa b’ace “wai Fannah meke damunki ne? Bakisan da abinda kikeyi zaki haddisa mana problem ba? Wuce ki had’a masa coffeen kinsan ko waye shi?”

      “Ya Suleiman amman shift na Asma’u ne fah.”
   Katse ta yayi “amman kuma ke Mr Fauzi yakeson ki had'a masa off you go.” Zata k’ara magana ya daka mata tsawa “now!” hawaye taji na ciko mata a sanyaye ta mik’e ta had’a masa takawo gaban Ya Suleiman ta ajiye. “Gashi.”
      “Aww nikuma zan kai masa? Kikai masa yana san miki magana.”
     “Ya Suleiman dan Allah kayi hak’uri kaba wata ta kai masa wallahi banasan magana dashi dan Allah.”

     “Fannah I can’t say no to him kawai kije ki rufa wa coffe shop namu asiri.” Zata sake magana ya fice juyowa tayi ta kalli Asma’u da take ta kau da kallonta elsewhere. Miyau ta had’iye sannan ta fice kaiwa Anas kujerun ta duba sannan can ta hangesa dukda bata ga fuskarsa ba amman daga farinsa ta ganesa. A hankali ta k’arisa kan table d’in ta ajiye a lokacin yana kan waya yana kallon window. Tana ajiyewa ta juya zata tafi holding wayar yayi “Boss naki be fad’a miki inasan miki magana bane?” Ya fad’i authoritatively ba tare da ya kalleta ba. Cak ta tsaya tare da kewayo wa...

    © miemiebee

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 19
BY MIEMIEBEE


Wayar da yakeyi ya cigaba da, tafi minti uku tsaye sannan yayi hanging, ba tare da ya kalleta ba ya d’au coffee’n ya kai baki be cire ba sanda ya kwankwad’e tas mamaki ne ya cika Fannah datayi mutuwan tsaye tana kallonsa cike da mamaki waiko d’umi d’umin coffeen ma baiji? “I will appreciate it in zaki bar kallo na haka kinemi waje ki zauna.” cewar Anas. Miyau ta had’iye wai shi ya yake gane mutum na kallonsa ne? A kunyace taja kujera ta zauna d’an nesa dashi har yanzu be d’ago kai sunsa juna a ido ba. Bayan ta zauna ya d’ago kyakkyawan fuskansa ya aza blue eyes nasa kan Fannah.

      Idanunsu na had’uwa Fannah ta saki salati. “Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!” tare da dafe k’irjinta. Kallonta Anas yake cike da mamaki. Kallon cikin ido suke ma juna shide baya manta fuska yau ya soma sa Fannah cikin ido mesa take kallonsa kamar ta sansa? “Hey!” Ya fad’i da kallon ya ishesa. “Are you okay?”
     Shiru har yanzu tayi tana kallonsa tana tuna ina ta tab’a kallonsa, wannan idanu tasan ta tab’a sata cikin idanunta amman takasa tuna a ina. Tayi tayi amman takasa. Table d’in ya buga firgit ta kyafta idanunta tadawo reality. “Aljani kika gani neh?” Ya tambayeta. Kai ta kad’a masa. “Better” ya fad'i relieved.
     “So kece kike had’a wannan coffee?” Shiru tayi bata amsa ba se kallonsa take wanda har yafara feeling uncomfortable. “Please na kiraki nanne to give you an offer bawai ki tsaya kina kallo na ba, hold it after natafi you can admire me.”

    Kut lalle ma wannan Anas, jijji dakai ya maka yawa, well kanada kyau amman ni ba kyanka nake kallo ba cewar Fannah a zuci. “Ba kallonka nake ba” ta fad’a tare da kawar da kanta daga ganinsa. “Allah sa you mean what you said just now. So ke kike making coffeen nan?”
    Kai ta giad’a. “See Fannah kike koh?” Nanma kai ta giad’a.
      “Damn it!” Ya buga table d’in a tsorace ta d’ago kai tana kallonsa. “I hate it in ina wa mutum magana yana using body signal, kimin magana as I do you, clear?” B’ari take ta giad’a kai take tace “eh.” “Good” yace sannan ya cigaba “maganan gaskia I like your coffee.”
    “Thank you”+ tace a hankali.
      “And inason ina sha kullum like safe rana yamma dare all the time.”
     “Sir but coffee shop namu k’arfe shida muke rufewa kuma ni 2:00PM -3:30PM ship d’ina yake k’arewa.” Tafad’i tana kallonsa
     “Exactly! sesa na taho miki da offer yau. And for the last time kidena kallo na will you?”
     Kau da kanta tayi da alqawarin barata sake kallonsa ba so take ta tuna ina ta tab’a ganinsa sarai tasa wannan blue eyes nasan sede ta rasa a ina ta tab’a ganinsu.

      “So kinsan ni waye ne ba sena fad’a miki ba Anas Ibrahim Fauzi CEO’n Flames Enterprises inason inyi offering naki better job a company na kina making min coffee 24/7 meaning duk lokacin da nakeson shan coffee I’ll give you a call and komin me kikeyi a lokacin zaki bari kizo ki had’a min abinda kawai zaki na min kenan and zanna biyanki ko wani k’arshen wata da salary me kyau. So what do you say?”

        “Mr. Fauzi nagode da wannan dama but am sorry baran iya karb’a ba saboda as you can see ina da aiki a nan kuma am satisfied with it. In zakayi excusing d’ina zankoma aiki.” Tana k’ok’arin mik’ewa ya daka mata tsawa “sit! This should be the last time, ba’a dismissing d’ina sede inyi dismissing mutum clear?”
      “I’m sorry” tace “now sit.” Ba gardama takoma ta zauna ita bata ga mesa zesa tama wannan arrogant mutumin aiki ba, ita tausayawa masu aiki k’ark’ashinsa ma take. Mutum kullum cikin tsawa da masifa ba dariya? Chabdi!
      “Nawa ake biyanki anan? I mean whats your salary?” Tambayarsa ne ya dawo da ita daga duniyar nazarin data fad’a.
   
     “Mr. Fauzi me zakayi da albashi na, naga kamar its personal.”
    “Zaki fad’a min salary’n kine kokuma sena sa an rufe coffee shop nakun?”
     Zaro ido tayi wai wannan wani irin mutum ne? “N10,000 (dubu goma) ne.”
    D’an murmushi yayi baki rufe wanda kawai dimple nasa ne kad’ai ya lotsa. “N10,000 kad’ai salary’nki? Work for me I’ll pay you double.” Zaro ido tayi. “Ko ya kasa? N30,000 then.” K’ara ciro ido tayi waje “N40,000 toh.” Kai ta sosa “induk yakasa miki toh N100,000 inshima ya kasa tell me ko nawa kikeso I’ll pay you as long as zakina making min coffee.”

     Mamaki ne yacika Fannah lallai wannan Anas baida matsala jibi yadda yake irga kud’i sekace dutse?
    “So, you accept my offer?”
    “Mr. Fauzi kayi hak’uri inasan aiki na anan dukda albashin bame yawa bane amman Allah nasa min albarka kuma i’m satiafied.”
   “Oh common Fannah karki yaudari kanki dubu goma bare rik’e ki har na wata ba, dubu goman da ake kashewa in just a minute? accept my job ko nawa kikeso I’ll pay you.”
       “Mr. Fauzi I’m sorry please, nagode zan tafi.”
     “Kiyi tunani Fannah anytime kika canza mind naki you can call me” hannu yasa yaciro card nasa tare da ajiye mata kan table d’in. “Koda zaki kira karki kira around k’arfe 5:00PM to 8:00PM.” Be jira me zatace ba ya d’au jakarsa ya fice.

     Hararan card nasan tayi, ta ja tsaki sannan ta d’aga ta karanta, phone numbers nasa biyu tagani kai. “Aiko nasha giyan wake barin kira ka ba, bana buk’atan dubu d’ari d’arin ka mschww” d’aga katin tayi da nufin yagawa karap Asma’u tasa hannu ta wabce. “Ke bani!” cewar Fannah.
      “Nak’i barin bayar ba. Ke yanzu Fannah Mr. Fauzi gabad’aya yabaki card nasa shine kike k’ok’arin yagawa? Meya sa yabaki?”

     “Oho! kiya tambayesa ni bakisan wani abu ba tsoro yake bani wannan da blue eyes nasa kuma kinsan wani abu? ji nake kamar na tab’a ganin sa awani waje kuma kamar yadda muka had’u bawai irin yamin mutunci bane kamar... Sharri” Tayi shiru tana kad’a kai “ya Allah a ina nasan wannan bawan naka?” Ta tambayi kanta.
         “Kefa Fannah anyi mutum yanzu Mr Fauzin ne harzaki wani tambayi a ina kika sansa ko kika tab’a ganinsa? Abinda har office nasa kin tab’a zuwa aikunsha had’uwa.”

     “A’a Asma’u duk had’uwar mu dashi bamu taba had’a ido dashi ba se yau kuma ayau d’in naji na tab’a had’uwa dashi wani wajen amman nakasa tunawa.”
   “Kide tuna” cewar Asma’u. “Seki tashi lokacin tafiyar ki yayi.” A sanyaye Fannah ta mik’e, Asma’u tabi bayanta. “Ina jakarki Fannah?” Akoi wayata ciki in cire.
    “Yana chan kan counter a kitchen please kifito min dashi” murmushi Asma’u tayi sannan tafice zuwa kitchen chan ta d’au jakar Fannah ta bud’e daman bawani wayarta ciki, card na Anas tasa cikin jakar cikin wata zip sannan ta rufe takai wa Fannah.

        Isar Fannah gida keda wuya ta tarar da Afrah kad’ai a gida har su Mami sunkai Baba kenan ta fadi a zuciya. “Sannu da zuwa Ya Fannah ya haka kuma yau? Tun shigowarki kinyi shiru.” Bayan ta zauna kusa da Afrah tace, “wallahi Afrah wani abu ke damu na.”
     “Wani abu kenan Ya Fannah?”
    “Yau Mr Fauzi yazo coffee shop namu-”
     Katse ta Afrah tayi “dan Allah!? Omg! Kunsamu kunyi magana? Wayyo Allah!”
        Marinta Fannah tayi a hannu “da Allah kimin shiru. Kinaji ba?” Afrah ta giad’a kai Fannah ta cigaba; “I mean jiya ma yaje shagon namu to da yasha coffee na seyace wai yamasa dad’i yau ma yadawo na k’ara had’a masa.” Afrah zatayi magana Fannah ta katse ta “please kiyi shiru kiji ni.”  “Ina kaiki, bayan na kai masa...”
Nan ta kwashe labarin komi tabawa Afrah sosai Afrah tasha mamakin erin sokancin da Fannah tayi. A yadda suke shan bak’ar talaucin nan ne har za’a bata aikin dubu d’ari tace battaso? Lallai kam.
    “Afrah kinyi shiru.” Cewar Fannah

      “Saboda kin ban mamaki ya Fannah at thesame time kuma kin ban haushi yanzu har a baki aikin dubbai kice bakiso? Seyau nasan bakisan Baba yasamu lafiya gaskia.”

    “Afrah wace erin magana kike haka? Baki tsaya kinji dalilin dayasa nak’i aikinsan ba fah.”
    “Toh ina jinki wani dalili ne haka?”
   Hannunta Fannah ta rik’o. “Wallahi Anas baida mutunci kinfi kowa sanin yadda nake tsoron masifa da tsawa banasan amin masifa shiko Anas ba aikinsa se ma mutum masifa wallahi ko yau danne zuciyata nayi banyi kuka ba daya daka min tsawa. Bayan haka kuma kinga ai bareyi inbar aiki haka kawai da su Ya Suleiman ba, bareji dad’i ba mun saba najima ina aiki dasu kawai dan an bani aiki me kyau se na mance dasu? Na kyauta kenan?”

       “Haba Ya Fannah mesa masu aiki suke barin gun aikinsu in sun samu me kyau? shi kansa Ya Suleiman inhar yana sanki murna ze miki dan wannan promotion. Dan Allah Ya Fannah ki karb’i wannan aiki, for once a rayuwarmu muma muji dad’in da akeji, Baba yasamu lafiya.”

     Kad’a kai Fannah tayi “Afrah niba wannan bama. Afrah inada wrong idea da feeling akan Mr. Fauzi yau na soma sasa a idanu na amman kuma ji nake kamar natab’a ganinsa wani waje kuma kamar had’uwan mu sharri ne, Afrah bansan meke damuna ba.”

      “Lallai! Ya Fannah ai dama kin sha kallonsa mana, ko kin manta shi kikaje office nasa ranan?”
     “A’a Afrah believe me wallahi duk had‘uwar mu dashi bamu tab’a had’a ido hud’u dashi ba.”
     “Toh in banda abinki ranan ai na nuna miki shi a TV.” Shiru Fannah tayi tana nazarin abu..
    “Kuma fa haka ranan kin nuna min shi a TV lokacin da Babansa ya rasu” zata k’ara magana sekuma tayi shiru “amman fa kaman bangansa ba ma ranan na tuna bangansa ba”

    “A’a Ya Fannah kituna dakyau kin gansa koda kad’an ne, kinsan dama wani sa’in ai haka ne sekaga kamar baka ga mutum ba amman ka gansa next in kuka had’u kuma seka ta wondering ina kuka tab’a had’uwa. In bahaka ba ina ke ina had’uwa da Anas d’an billonaire ko kin manta a ture can London yayi rayuwarsa. Bansani ba ko kema kinje London d’in a mafarki” Afrah ta fad’a taja dariya.

    Maketa Fannah tayi “LOL kuma fa kinyi gaskia nakega hakan ne a TV na gansa ranan in bahaka ba kam ina zan had’u da mutum kan Anas.”
    “Yawwa ‘yar garin so yanzu zaki karb’i aikin?”
    “Eh” tama Afrah k’arya dan kar taji haushinta amman kam har cikin ranta bata san amsar aikin, kuma bataga abinda ze sa ta amsa ba. Gara ta soma neman sabon aiki datayi aiki k’arkashin Anas, mutum ne kullum cikin masifa baya murmushi bale dariya. Sekace dodo!

      Da daddare da misalin k’arfe tara bayan su Fannah sun idda sallah suna shirin kwanciya wayarta ya soma ringing tana kai dubanta taga Ya Suleiman cike da mamaki ta d’aga dan kuwa be tab’a kirarta warhaka ba se addu’a take Allah sa ba magana ze mata gameda Anas ba.
     “Assalamu Alaikum Ya Suleiman.”
    “Ff... Fannah!” Se jin muryar tasa tayi na rawa.
     “Ya Suleiman meya faru? Wani abu ne? Ya muryarka ke rawa?”
   “Fannah shagon mu... Shagon mu Fannah!!”
   “Ya Suleiman dan Allah meya sami shagon namu please tell me” hankalinta tashe take maganar. Afrah dake gefenta itama ji tayi zuciyarta na bugawa.
     “Shagon mu yakama da wuta Fannah k’urumus ya k’one ba abinda aka samu aka cire. Wutan NEPA ne yasoma gobarar kafin akira fire service k’urumus komi ya k’one.”
      Salati Fannah keyi ba makawa. “Innalillahi!” take idanunta suka cike da hawaye “Ya Suleiman kayi hak’uri mud’au wannan a matsayin jarabawa dole kayi hak’uri ka rungumi k’addara innalillahi! Gobe in shaa Allahu zan fito dare yayi yanzu dana fito am so sorry kayi hak’uri dan Allah.”
    “Nagode Fannah” ahaka sukayi sallama.
   
       “Ya Fannah meya faru?” Cewar Afrah.
     “Afrah shagonmu ya k'one wutan NEPA ne yasoma gobarar.” Salati Afrah tayi sannan tayi calming Fannah dake hawaye down. “Daman kinada niyyan barin aikin segashi dalili kwararre ya zo ayyah, Ya Fannah da rabon Allah baisan kiyi witnessing a day without a job.” Kallonata kawai Fannah take cike da damuwa ita shikenan nata ya k’are mesa hakan ze faru da shagonsu? Yanzu ya zatayi da kud’in asibitin Baba? Dole a gobe taje tasoma neman aiki.”

      Washegari da sassafe ta tashi taje ta shagonsu  k’urumus komai ya k’one abin tausayi. Ya Suleiman da Babansa da angansu anga wanda suka kwana suna kuka. Condoling nasu tayi gashi dama k’arshen wata yayi jiran albashi take ta k’arisa biyan kud’in asibitin Baba gashi yanzu da abinda yafaru ba su ba albashi dan koda za’a bata ma barata amsa ba da wannan masifar daya same su.

    One week later...

      Yau k’imanin sati kenan Fannah na neman aiki ba rana ba dare amman har yau ba labarin aiki, abin har kuka yake sata ga kud’in asibitin Baba ‘yan asibitin sun dameta harda cewa in bata k’arisa biya ba zasu kaita gun ‘yan sanda. Abinci ma yasoma k’arewa masu agida abinde ba kyau. Ita nadaman mesa ta yasar da card na Anas ma take ta hak’ura da duk walak’anci da masifan da ze mata inhar ze bata kud’i tabiya kud’in asibitin Babanta. Kuka tasha a waje sannan tashigo ciki. Mami da Baba da Aiman suna d’akinsu. Tana k’arisawa d’akinsu da Afrah ta tare ta zaune kan gado yau ko chatting d’inma battayi dan ba kud’in kati.

      “Afrah ba magana ne?”
      “Ya Fannah me zance miki? Nariga na gaya miki abinda yakamata. Kinada halin da zaki warkar damu daga wannan hali amman kika k’i. Kalli yadda kowa yake shan wahala haba Ya Fannah dan Allah.”
     “Afrah wallahi ba haka bane na miki k’arya dana ce miki zan karb’i aikin da Mr. Fauzi yabani wallahi tun a ranan daya bani card nasan na yasar bansan ya zanyi ba yanzu. Afrah nayi nadamar yin hakan ban zata shagon mu ze k’one ba kuyi hak’uri ina kan neman aiki har yanzu kuyi hak’uri dan Allah.”

     Afrah bata ce mata komi ba. Jakarta ta zazzage kan gado dan tattara credentials nata. Fitsari ne ya matse ta, bayan ta shige bayi Afrah ta lalimo kan gadon tana duba papers d’in dan ko bata yarda da abinda Fannah tace mata ba nacewa ta yaga card d’in. Kap ta duba bata ga komi ciki ba har ta hak’ura se kuma ta d’au jakar ta, dudduba zip nacikin jakar take can tajiyo takarda tana cirowa taga card d’inne daidai lokacin Fannah tafito “Afrah me kike min da jaka.”

    “Ya Fannah me wannan?” Da sauri Fannah ta hauro kan katifar ta amshe card d’in, baki ta bud’e wangalau “aina kka samu?”
    “Ina kuwa? Cikin jakarki? Dama baki yasar ba kenan dan bakisan karb’an aikin ne kika min k’arya kin kyauta.”
   “Wallahi tallahi Afrah kinji rantsuwan muslumi kenan bansan ya akayi abin nan ya dawo jakata ba aida nansan da zamansa da na kirasa tuni nida ake threatning d’ina kan za'a kaini gun ‘yan sanda?” Shiru tayi tana nazarin wani abu can tace, “aikin Asma’u definately ita tasamin cikin jakata” nan taba wa Afrah labarin komai.

  10 minutes later... Dadai k’arfe 5:30PM

    Fannah ce zaune kan kujera d’ayan hannunta katin Anas ne d’ayan kuma wayarta a kunne tana jiran Anas ya d’au wayar. Zuciyarta se bugawa yake bababam! Babam!

© miemiebee

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 20
BY MIEMIEBEE


Ringing wayar yake amman ba response, bayan ya tsinke ta sake gwadawa nan ma haka har ta tsinke Anas be d’aga ba.
         Anas na kwance kan gadonsa yana ganin wayan na ringing ko yunk’urin d’agawa beyi ba danko baya d’aukan waya within time d’innan inba wai familiar number yagani ba. D’ayar number’nsa ta zuba nanma two missed calls duk be d’aga ba. Anas na gani nanma yak'i d’agawa. Fuksarta cike da disappointment tajuyo ta kalli Afrah. “Afrah be d’aga ba 4 missed calls na masa be d’aga ba. Omg!” Wayarta ta duba taga lokaci pass 5. “Oh no! Se yanzu na tuna sanda yace min kar na kirasa within 5 to 8.”

     “Toh seki bari se anjiman ai ki gwada.” Kai Fannah ta giad’a mata.

**
     Sosai Anas yayi missing coffee’n Fannah, bayasan shan komi inba coffee’n Fannah ba. Tun ranan da suka had’u yake jiran kirarta amman shiru. Bayan kwana biyu yaje ya duba coffee shop nasun yaga k’urumus komi ya k’one a tunanin sa wai a ranan ko washegari Fannah zata kirasa ta amshi aikin daya offering mata amman ina har yau shiru, k’ok’arin mancewa da coffee’n yake tunda basamu zeyi ba. Inda kuwa yasa a binciko masa ita da a ranan ze sameta amman kuwa girman kai irin nasa bare barsa ba.

     Washegari da safe da misalin k’arfe tara bayan Fannah tagama shiri tasaka atamfa ne ja da baki seda bak’in hijabi wanda yamugun sake fidda hasken ta. Ba makeup kamar yadda ta saba, daga kwalli se kwalli da lipgloss a baki ta d’au credentials nata tana shirin fita zuwa company’n Anas tunda bata samesa ta waya ba zataje ta samesa in person. Koda ta sake kiran sa ajiyan around pass 9 be d’aga ba acewarsa wai ko irin mata masu kiran san nan ne danko kirar yayi yawa.

      Isarta company’n keda wuya. Wannan shine karo na biyu da take sa Enterprise d’in a ido. Bayan tashiga ciki ta tsaya raba ido dan bata ma san ta ina zata fara neman Anas cikin wannan babban building ba, ita bama wannan ba karya ganta ya cicci mata mutunci yanzu danko baida mutunci. Reception ta hango ta k’arisa wajen da fara’arta ta gaishe da receptionist d’in wani kallon bakwai saura kwata ta mata “how can I help you?” Tace da Fannah tana tauna chewing gum bakin nan yasha jan janbaki.
       “Uhm Mr. Fauzi nazo gani please.”
     “Mr. Fauzi?” Cewar receptionist d'in tare da d’age gira. “Ked’in zaki ga CEO? LOL” ta k’yalk’yale da dariya.
       “Eh kwanakin baya ya tab’a offering d’ina aiki yace kan duk sanda na yi making up mind d’ina in zo in samesa. Ki kaini wajensa please.”
      “Ya sunanki?”
    “Fannah Aleeyu.”
    “Kina da appointment dashi ne? Yasan da zuwanki? Is he expecting you?”
     “Actually no amman in ya ganni ze tuna please ki kaini wajensa please.”
     “Uhm Fannah kinga Boss d’ina is a very busy man bareyi in kaiki wajensa ba, ba tare da yasan da zuwanki ba in zaki zauna kijira in masa magana yaso ko zuwa gobe ko jibi se a had’a muku appointment seki dawo.”
     “Ma’am please kiyi hak’uri dan Allah I need this job so badly mahaifina ba lafiya ki taimaka please wallahi ya ganni ze gane ni.”
    “Fannah kinga kiyi hak’uri ki fice daganan dan nan ba gidan bada taimako bane.”
    “Ma’am please.”
     “Security!” Receptionist d’in takira “kuzo ku fita da wannan ‘yar please.” Nan security sukayo wajen suna tambayan meya faru. Daidai lokacin elevator yake bud’uwa Anas ne ya bayyano yana sanye da navy blue suit da blue sunglasses a fuskarsa, gashin nan anyi styling nasa masha Allah, fuskar nan nasa tamk’e ba alaman murmushi. Wani na miji ne a bayansa wanda ga dukkan alamu PA’n sa ne.
   
     Taku yake magestically cike da k’asaita yana duba agogon hannunsa da alaman meeting zasa, tafiya yake kai a sama yakaida wajen su Fannah ta kira sunansa “Mr. Fauzi” cak ya tsaya sannan a hankali ya juya ya kallet
adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *