Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Tuesday, February 28, 2017

Alheri danko ne complete

adsense here hausa novel blog ‹ Home View web version Thursday, 22 December 2016 aisha ummi at 01:08 ALHERI DANKO NE 1-50 mmi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣ Na UMMI A'ISHA JAN KUNNE- duk wanda ya canza min wannan labarin ko ya canja sunan taurarin ciki, ko yayi min editing ALLAH YA ISA BAN YAFE BA. Tafe yake yana cire safar hannun dake hannunsa yana cillar da ita akan tile din dake malale aharabar runfar asibitin, leburorin wurinne suke biyeda shi suna tsince duk abinda ya yar awurin shikuwa sai faman yatsina fuska yake yi sai kace yaune ranar farko wadda yafara karbar haihuwa kokuma yafara operation,ahankali yake tafiya sai kace marar jini ajiki yana sanye da light blue colour din t shirt mai dogon hannu da black din jeans idonsa sanye cikin farin gilashi amma da alama gilashin nasa na gayune bana kara karfin ido bane, duk inda ya ratsa babu abinda kakeji sai weldon sir! Shi kuwa gogan baya magana sai daga hannu domin magana tana mutukar bashi wahala saboda yangarsa da jan ajinsa gashi da iyayi kamar mace amma hakan yana mutukar kara masa kyau kuma da alama iyayi nature dinshine, ayanda na hango fuskarsa zan iya kiyasta shekarunsa bazasu haura 27 ba aduniya,fari ne dogo siriri lange lange kana ganinsa zaka gane baya aikin wahala kuma hutu ya zauna ajikinsa, cikeda yanga ya karasa office dinsa wanda yake jere a rukunin ofisoshin manya likitoci ( consultants) wani office yabude yashiga wanda asaman kofar aka manna wani dan katako aka rubuta DR TAFIDA ajiki da manyan harrufa, ahankali yashiga cikin office din wanda yayi tsananin tsaruwa kamar ofishin shugaban kasa, kan wata doguwar kujera baka yaje yakwanta yamike yatasa kansa da hannun kujerar yafara cire (neck tied) din wuyan rigarsa yacire gilashin fuskar sa yalumshe manyan idanuwansa wanda suke zagaye da bakaken gashi masu mutukar baki sai da yadan huta sannan ya mike a hankali tamkar mace ya isa kan teburinsa yadanna wata kararrawa aguje wasu fadawa guda uku sanye cikin jajayen kaya suka shigo, suna shigowa suka fara zabga kirari, Allah ya taimaki mai girma tafida, dan sarki jikan sarki kuma sarkin gobe da yardar Allah, Allah yakara maka nisan kwana! [6:56PM, 11/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 2⃣ Na UMMI A'ISHA Hannu yadaga musu take sukayi shiru saboda sun gane nufinsa kuma dama can shi baya son yawan magana duk maganarshi atakaice yake yinta itama sai takama mutuka amma in bakamawa tayi ba sai dai yayi umarni da hannunsa, kallonsu yayi yanuna musu kan table dinsa tuni suka zabura suka fara harhada takardun dake kan table dinsa gamida dibar wasu files manya, laptop dinsa da brief case dinsa suna gama harhadawa sukayi waje yayinda shi kuma dr tafida ya sake mikewa a kujerar da yake kai sai da ya shafe sama da minti 20 ahaka sannan yatashi yahau kan kujerarsa ta aiki yajawo drawer dinsa yaciro tabar wiwi (ganye) yadauki ashana ya kyasta yafara busa hayaki, wani dan madaidaicin glass cup ya ajiye musamman akan table dinsa inda yake tara tokar tabar da yakesha kuma da alama yana sha akai akai domin har kofin yakusa cika da tokar tabar, zukar tabar wiwin yaci gaba dayi har ta kare sannan ya kishingida ajikin kujerarsa nanma yashafe fiyeda minti goma sannan yatashi ya dauki phones dinshi da gilashinsa yafita daga office din yana fita fadawansa suka zabura suka nufi motarsa dasauri suka bude masa gidan baya yashiga yazauna suka rufe kofar motar suka runtuma tasu yayinda daya daga cikinsu yashiga mazaunin direba ya zauna yatashi motar ya harba suka bar harabar cikin asibitin. [7:33PM, 11/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 3⃣ Na UMMI A'ISHA Fita sukayi daga harabar asibitin mutane sai kallon motocin nasu sukeyi gamida daga musu hannu amma dan mulkin yana daga kishingide acikin kujerar baya hannunsa rikeda jaridar daily trust yana karantawa da haka har suka isa kofar fada inda anan gidansu dr tafida yake, wani makeken gida nagani gaba dashi kuma filine babba tuni digarawan dake zaune abakin kofar gidan suka mimmike tsaye saboda ganin motar tafida,kan motocin suka kutsa cikin babban gidan wanda yasha zane iri iri da adon kala kala irin na sarakai nidai ummi Aisha tun daga nan nagane cewar gidan sarki nashigo domin gaba daya tsarin gidan namasu sarauta ne, cikeda iyayi da takama hadida kasaita dr tafida yafito daga cikin motar yatasamma cikin gidan wanda akalla sai da aka wuce zauruka sunfi 5 sannan yakarasa wani babban fili mai dauke da part part akalla zasu kai guda 5 kansa tsaye yawuce wani sashe mai mutukar kyau wanda yasha ado da kwalliya, budewa kofar falon yayi yashiga nan nahango wani dattijon mutum wanda akalla shekarunsa zasu kai 65 yana kishingide akan kilisan dake malale acikin falon wanda yawansu zai iya kaiwa guda biyar kala kala gashi jikin bangon dakin yasha zane na sarauta, gefensa tumtum ne wanda yajingina ajiki ga kayan marmari nan agefe dangin itatuwa kamar su inibi, tufa, ayaba, kankana, gwanda, zaitun, ruman, da sauran kayan itatuwa cike cikin wani dan madaidaicin kwando wanda aka tanada musamman dan adana kayan marmari, cikeda alamun gajiya yayi sallama ahankali yashiga wannan al'adarsa ce duk lokacin daya dawo daga office sai yaje ya gaida mahaifinsa da mahaifiyarsa,washe fuska dattijon yayi ya amsa sallamar da Wa'alaikas salam wa rahmatullahi wabrakatu, barka da zuwa ibrahim cikin jin dadi yakarasa inda mahaifin nasa yake yazube akasa yafara kwasar gaisuwa,barka da hutawa mai martaba dafatan mun sameku lfy, ya akaji da jama'a? Cikin jin dadi yace alhamdulillah ibrahim dafatan ka dawo lfy? Lfy lau yafada yana murmushi gamida mikewa yana fadin nabarka lfy ranka yadade, Allah yakara nisan kwana, Allah yaja zamani. 4⃣ Yana fitowa ya gangara izuwa wani sashen nagaba wanda tun daga nesa nafara hango bayi da kuyangu sai faman kaiwa da komowa suke, wasu suna aikace aikacen gida wasu kuma suna ta faman shige da fice tunda tafida yadoso su suka fara zubewa suna dibar gaisuwa barka da dawowa mai girma tafida, takawa lfy dan sarki jikan sarki, tafiya sannu sannu kwana nesa sarkin gobe, hannunsa kawai yake cira musu amma ko kala yakasa furtawa sai dai da alama sun san halin tafidan domin hakan bai hanasu cigaba da gaishe shi ba, ko kallo basu isheshi ba balle ya amsa gaisuwarsu wannan dalilin ne yasa mutane da dama suke kiransa da mai girman kai wasu kuma suce yanada iyayi da wulakanci to koma dai menene da alama iyayin nature dinsa ne [8:36PM, 11/11/2015] Ummi A'isha: Tamkar wani mai ciwon kafa yaci gaba da tafiya har ya cimma sashen mahaifiyarsa hajiya Kilishi wadda yake tangamemen gaske yana shiga kasaitaccen falon nata wanda yasha adon kayan alatu yafara cin karo da bayinta wasu sunata aikin gyaran falon wasu sunata wawwatsa wani abu mai mutukar kamshi kamar turaren wuta suna ganinsa suka durkusa barka da shigowa mai girma tafida! Kai kawai ya gyada yawuce cikin dakin inno kamar yadda yake kiran mahaifiyar tashi, akan wata katuwar darduma ya hangota tana zaune ta jingina bayanta da babban filo kafafuwanta kuma ta dorasu kan tumtum wata baiwa sai aikin mammatsa mata kafafun take, da sallamarsa yashiga yana shiga wannan baiwar ta zabura barka da zuwa yallabai, bai bata amsaba tatashi tafice, agefen gadon mahaifiyar tashi ya zauna wani irin gadone nakarfe mai runfa fentinsa kalar ruwan hoda yasha lallausar katifa da shinfidu na alfarma ga kamshi mai dadi dayake tashi daga cikin dakin, barka da hutawa inno yafada yana wani lallausan murmushi, yawwa barka da zuwa tafida tafada tana murmushin itama, kallo daya zakayi mata kagane cewa mahaifiyarshi ce domin babu ta inda ya barta akama, kamarsu daya dashi kuma da alama tana jidashi sosai, macece mai fara'ar gaske kuma bata tsufa ba dan shekarunta bazasu wuce 45 amma bazaka taba gane hakan ba saboda jikinta bai nuna ba ko kusa, cikeda kulawa tace zakaci abinci ne yanzu? Kai ya girgiza tamkar wani karamin yaro yace a'a inno sai anjima yanzu bacci nakeji, to atashi lfy tafada tana murmushi,murmushi yakuma yi yakwanta akan gadon mahaifiyar tashi yaja filo yatasa kansa dandanan bacci yayi gaba dashi, tashi inno tayi takoma falo tazauna gudun kada azo adameshi yana bacci. 5⃣ Karfe 3:40 yatashi daga baccin da yakeyi yafito idonsa duk yayi kalar masu bacci afalo ya taradda inno tana salla dan haka bai tsayaba yawuceta yafita daga lungunta yanufi nashi yana shiga yafada toilet ya hada ruwan zafi yayi wanka yafito yasaka farar t. Shirt mai gajeren hannu yasa wando jeans baki yafesa turaren FOGG yafito yanufi masallaci lokacin dayaje har anshiga salla, yana idarwa ya fito ya wuce ma 'ajiyar dawakai yasamu an shirya masa dokinsa anyi masa shimfida an gyarashi domin fita kilisa bai bata lokaci ba yahau suma fadawansa wanda suka hada da sarkin fada, sarkin mota, da maja sirdi suka hahhau nasu suka fito daga gidan ahankali suke tafiya tacikin garin har suka fita suka shiga dokar daji, dama idan da sabo sun saba dan kusan kullum sai tafida yafita kilisa, kilisa tana daya daga cikin abubuwan da suke burgeshi a harkar sarauta, tafiya kawai suke suna shakar iskar dake ratsa dajin sannan suka billa tawata hanyar domin komawa gida alokacin mangariba takusa yi har ta kawo jiki, suna zuwa gida ana kiran salla, akasalance tafida yasauka daga kan kosasshen dokinsa yayi alwala yashiga masallaci ana idar da salla yafito adaidai lokacin wata hadaddiyar mota tashigo baka kirar croutoure mai tsananin kyau ajiki an rubuta TAFIDA 1 kallon motar yayi yai tsaki yawuce gaba, agabansa aka yi packing din motar aka fito wani saurayine wanda zai kaishi atsaye kuma ashekaruma bazai fishiba yafito daga cikin motar yana dariya Allah yaja zamanin tafida, batare da tafidan yayi masa magana ba yawuce yafara tafiya shikuma yabishi abaya har suka karasa sashen tafidan suka shiga, afalo suka zauna cikin muryar iyayi tafida yace wai kai faisal meyasa bakada mutunci ne? Motar tawa kadauka katafi yawon iskanci? Dariya yayi wanda aka kira da suna faisal yace haba abokina kaima iskancin nan kana dan tafabawa, fuska tafida ya yamutsa, ni bana wani iskanci kaine dan iska, ok naji ni dan iskane saboda ina neman mata kai kuma dan ganye? Filon kusa dashi tafida yadauka yajefeshi kai dan iska ne idan ni dan ganye ne ai dasauki tunda har yanzu ni saurayine cikakken saurayi kuma, dariya abokin nasa yayi dakyau virgin boy, amma dai abi ahankali banda ganganci,shiru tafida yayi bai kara magana ba domin shi baya doguwar magana idan kajishi yayi magana mai tsawo to da mahaifinsa ne ko mahaifiyarshi ko kuma abokinsa faisal. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [7:23PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE ! 6⃣ Na UMMI A'ISHA Tashi tafida yayi ya shiga daki yahaye gado yakwanta minti kadan faisal yabiyoshi cikin dakin abokina ya zaka kwanta bayan ba mugama magana ba? Kai malam bana son surutu, eh nasani ai shiyasa nake son na sanar dakai cewa na dauki wadannan kudin naka nayi sadaka dasu, tsaki tafida yayi mtwww to ina fata ba iskanci kaje kayi da kudina ba? Murmushi faisal yasake yi wai kai finka laifi nayi? Kaima fa mai laifi ne, kana shan ganye over ni kuma ina neman mata jifa jifa ba koda yaushe ba, murmushi tafida yayi yatashi zaune, to ai ni matan ne ma tsoronsu nake, gaba daya ban san ta inda zanbi ba yanzu haka idan ka ajiye min mace wlh ban san yadda zanyi da itaba, wata irin dariya faisal yayi hahahaha! Ammafa kacika dan rainin wayo, ta ina kake karbar haihuwa? Kaida ka karanci mata kasan yadda suke, karfa ka manta kai likitan matane su kake gani kake dubawa akoda yaushe, dan malalacin murmushi tafida yasaki to sai aka fada maka kuma nasan hanyar? Karya kake kasani mana, dariya tafida yayi kai dan iska ne, wlh duk ranar da mai martaba yasan kana neman mata sai ya tube rawanin da ya daura maka,cikin dariya shima faisal din yace kamar yadda kaima mai martaba zai tube rawanin daya daura maka ba duk ranar da yagane kai mugun dan ganye ne, murmushi tafida yayi ra'ayina shine nasamu cikakkiyar budurwa kamar yadda nake cikakken saurayi, taba baki faisal yayi eh munji kai saurayine amma ai dan ganyene, dariya tafida yayi duk da haka dai nafika,ni yanzu ma ka kyaleni wlh yunwa nakeji sai da inno tace naci abinci dazu nace bacci zanyi amma bari nayi mata waya akawo mana, wayarshi ya dauka kirar yota phone yakira inno yace akawo masa abinci shida faisal ba awani jimaba sai ga kuyangi guda 2 sun shigo hannuwansu dauke da tirarrika na silba manya manya anan suka ajiye suka fita, suna fita faisal ya fara bubbude kwanukan abincin, abinci ne kala kala na gargajiya saukowa tafida yayi suna ci suna hira har suka gama, suna gamawa suka tafi masallaci sukayi salla suka shigo gida afalo faisal yazauna yafara waya da yanmatansa shi kuma tafida yawuce daki yafada kan gado yajanyo tabar wiwi yafara zuka. 7⃣ Washe gari dasafe dr tafida yashirya tsaf cikin shirinsa nafita office bakin wando yasa da bakar t.shirt mai dogon hannu yadora jar jacket asama yasa bakin takalmi cover shoe [7:38PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: Yafesa turaren fogg yafito lokacin faisal yanata bacci kasancewar shi a ministry for local government yake aiki baya fita dawuri shikuwa tafida 7:30 yasaba fita office, yana fitowa sarkin fada da sarkin mota sukazo suka zube suka fara zabga kirari barka da fitowa mazajen fama hadiri sa gabanka inda kakeso, murucin kan dutsi baka fitoba sai da ka shirya, atafe dakyau, atsaye dakyau amma azaune kafi dadin kallo dan ahmadu jikan sani gyara kintsi giwa kinfi karfin waiwaye, kura ko kin mutu kinfi karfin kare, wani kaya sai amale wane jaki, cikeda takama yace barkanku da safiya yawuce cikin gida yanufi dakin inno mahaifiyarshi alokacin har ta harhada masa kayan karyawarshi tsaf ta zuba acikin akushi mai kyau tana jiran shigowarsa, yana shiga yazube agabanta tana kushingide hannunta rikeda carbi tana ja sukuma bayinta har sun fara aikace aikacen da suka saba yi, barka da asuba inno yafada idonsa akasa, barka da tashi tafida, kafito lfy? Lfy lau inno, to Allah yabada sa'a, Allah ya tsareka, Allah yadawo dakai lfy, amin inno nabarki lfy, tashi yayi yafita yanufi sashen mai martaba lokacin shima yana zaune afalonsa yana karatun alqur'ani mai girma, cikin girmamawa tafida yadurkusa barka da asuba ranka yadade, cikin murmushi yace yawwa ibrahim har anfito? To Allah yatsare Allah yabada sa'a, amin mai martaba yafada yatashi yafita inda aka adana motarsa yanufa aka bude masa gidan baya yashiga yazauna cikeda nuna isa yake daddana wayar hannunsa fadawa sai kawo gaisuwa suke yi amma yakasa amsawa,asibitin Rasheed shekoni specialist hospital suka dosa inda tafida yake aiki. [7:48PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 8⃣ Na UMMI A'ISHA Suna zuwa kamar kullum yafito yashiga office dinsa wanda yake jere ajerin gwanon ofisoshin kwararru na asibitin, yana zama wata nurse tashigo tana sanye da fararen kaya,morning sir! Morning ya amsa mata idonsa yana kan laptop dinshi yana daddannawa, sir akwai patient wanda jiya kayiwa operation tofa har yanzu bata farfado ba, cikeda damuwa ya tashi domin shi yana tausayin mata duk lokacin dayaga mace acikin halin rashin lafiya sai yaji kamar zaiyi kuka, maternity yanufa wannan nurse din tana biye dashi abaya ita dai wannan likitan yana burgeta domin yasan aikinsa matsalarsa kawai yanada girman kai ga nuna isa kamar shine sarkin ko dan sarauta ne? Yahadu sosai ga kudi da sarauta ga ilmi ga uwa uba kyau, yana shiga maternity yafara bin patient din daya bayan daya yana dubasu har yagama yakoma office dinsa alokacin yafara ganin marassa lfy wadanda suka zo ganin likita kuma gaba dayansu matane domin shi mata kawai yake dubawa baya duba maza sai wurin 11 yagama ganin marassa lfy yayi breakfast yatashi yashiga round. [8:16PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 9⃣ Na UMMI A'ISHA Yana dawowa daga round yanemi wuri a office dinsa yazauna lokaci lokaci fadawansa suna lekowa domin ganin lafiyarsa, sai misalin karfe 5 yatashi lokacin yafito daga theatre cikin gari suka shiga akan hanyarsu ta tafiyane suka ratsa tawani dan kauye anan yaga wata makekiyar gona wadda akalla zata kai kilo mita 5 anyi shukar shinkafa aciki, shukar tayi kyau sosai sarkin mota ya yiwa magana cewa ya tsaya cikin sauri ya taka birki yaja ya tsaya yabude kofa yafito suma fadawan firfitowa sukayi suka tsattsaya, gonar ya zubawa ido ta kayatar dashi hakika wannan zatayi daidai da wurin da yake nema domin gina business suit dinshi hadida gidan shakatawarsa motar ya koma yashiga ya zauna, fadawansa suka shisshiga suka nufi gida tun da suka shiga yasan cewa mai martaba yau yana fada dan hakan fadan yashiga wacce ta kayatu sosai, mai martaba yana zaune akan wata karagar mulkinsa ta alfarma wadda tasha ado da zinare, gefe daga hannunsa nadama wazirine da galadima ga chiroma, kusa dashi kuma hakimin cikin garine, daga hannun hagu kuma wani dan dattijone zaune wanda shekarunsa zasu kai na mai martaba kusa dashi kuma san turakine wato faisal aminin tafida, cikin sallama tafida yazauna yayi gaisuwa yatashi yashige cikin gida yawuce dakin inno yau bai wani jimaba yafito yashiga dakinsa yayi wanka yafito cikin bakar riga da bakin wando, yanufi lambu wanda yake girke acikin gidan, wurin yasha shukoki na kayan marmari ga wata korama daga tsakiya tana gudana can gefe wasu kujerune hadaddu aka ajiye saboda hutawa kan kujerar yaje yazauna amma ko minti 5 bai yiba yatashi yafita yanufi dakinsa yashiga yakunna tv yakamo tashar kwallo yafara ganin wasan arsenal da man u, wasan yafara kayatar dashi faisal yashigo remote ya dauka yakashe tv din domin yasan yanzu zasuyi fada saboda faisal dan arsenal ne shi kuma tafida dan man u ne gashi ancisu har 2-0 yasan idan faisal yagani yau zai sha tsiya, kusa dashi faisal yazauna. [8:32PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣0⃣ Na UMMI A'ISHA Kusa dashi faisal ya zauna yafara dariya ko kallonsa tafida bai yiba yadauke kansa shikuwa faisal sai dariya yakeyi, haushi tafida yafara ji yace ya isheka haka,dariya faisal yayitayi sai da yayi mai isar shi sannan yace kasan me nake yiwa dariya? Jiya jiyan nan kagama yimun bayanin kaifa bakasan hanyar da zakabi ba awurin mace idanma aka ajiye maka mace bakasan yadda zaka bida itaba to sai gashi yanzu za abaka mace nan da sati 2,kaga ashe kenan ka kusa kasamo hanyar ko? Wani kallo tafida ya watsa masa ni zanyi aure amma ba yanzu ba sai nan da 3years dariya faisal yakumayi kasan Allah? Kai angone kakusa ganin hanya, wai kai waya fada maka aure zanyi ne? Uhm abokina bazaka yarda da abinda nake fada maka ba sai kaji kira daga wurin mai martaba sannan zaka gasgata ni, tsaki tafida yayi insha Allahu kai zai yiwa aure amma baniba,ni daba dan iska ba wa zaiyi min aure yanzu? Kai da kasan mata kake nemansu ai kai yadace ayiwa aure, dariya faisal yayi kasan Allah? Wlh kakusa zama ango kai barima kaji dazu daka zo kasamemu da mai martaba wlh maganar aurenka akeyi kuma nan da sati biyu za ayi, cikeda mamaki tafida ya kalleshi wai dagaske kake yi? Wlh Allah dagaske nake tafida wlh aure mai martaba zaiyi maka dazu akanka mukayi meeting da yamman nan kuma wani abin burgewar ma zaka samu virgin girl kamar yadda kake virgin boy, zumbur tafida yamike ni za ayiwa aure yanzu? Wanne laifin nayiwa mai martaba da zai hukantani ta wannan hanyar? Wa zai aura min? Yaya kamanninta suke? Girgiza kai faisal yayi wlh ban saniba abokina, to nima dai ummi Aisha ban saniba sai muci gaba da bibiyar tafida, masu karatu muje zuwa kubiyo Aisha. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [8:53PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣1⃣ Na UMMI A'ISHA Kallon faisal tafida yayi ai kuwa wlh bazai taba yiyuwa ba nikadai ne da agidan? Akan me za ayi min wani aure yanzu kai ba gaka nan ba haba da Allah wlh bana so babu wanda zai rabani da gidan nan yanzu, kuma wlh duk yarinyar da tayi kuskure ta aureni sai ta raina kanta, dariya faisal yayi wadda takara kular da tafida kaga bani zaka fadawa ba kamata yayi kaje gurin mai martaba kayi masa wannan bayanin amma nidai ina tayaka murna sai dai shawarata agareka itace kasan mai martaba baya yin magana 2 daga yayi magana to yagamata so be careful kar kaje kajawa kanka, kaga mitumin nan nadazu daka samemu afada dashi? Shine mahaifin yarinyar wlh kayi dacen suruki cikeda bakin ciki tafida yace malam banfa tambayeka ba dan haka kayi min shiru banza kawai dariya faisal yaci gaba dayi ganin haka yasa tafida ficewa daga dakin yatasamma lungun inno wadda yake da dan tazara daga sashensa, yana shiga yatarar da bata cikin dakin sai kuyanginta suna gyara dakin kusan ko wanne lokaci dakin nata cikin gyaransa ake, shiyasa koda yaushe yake cikin tsafta tamkar dakin sabuwar amarya, suna ganinsa sukayi waje suka bar aikin da sukeyi, gadon inno ya dale yakwanta idan dasabo kowa agidan yasaba ganinsa akan gadon inno koda wanne lokaci yagadama zai zo yahaye yasha baccinsa akai kamar wani yaron goye. [9:36PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣2⃣ Na UMMI A'ISHA Rufe idanuwansa yayi amma yasan ba bacci zai iya yi ba maganganun faisal ne kawai suke dawo masa jiya jiyan nan kagama fadamin idan an baka mace baka san yadda zakayi da itaba sai gashi nan da sati 2 zaka zama ango an baka mata, zunbur ya tashi zaune jin abin yake kamar a mafarki aurefa? Daidai lokacin inno tashigo taganshi zaune akan gadonta, tafida ashe kana nan? Nima daga wurin mai martaba nake yakira ni yabani wani sako wurinka ras! Gabansa yafadi wato maganar faisal ta tabbata kenan ai kuwa tunda yake da mai martaba bai taba yimasa musu ba amma awannan karon dai zai yi, domin bai kamata ayi masa haka ba, abinda yafi cancanta shine abarshi ya zabi matarsa da kansa tunda sauran yayyensa ba haka akayi musu ba, maganar inno ce ta dawo dashi cikin hankalinsa mahaifinka yace nasanar dakai zai daura maka aure nan da sati 2 da wata yarinya yar gidan abokinsa amma ayadda naji yafada yarinyar ma ba lafiyayyiya bace, cikeda damuwa yace inno kuma ni za aurawa marar lfy? Haba inno yanzu mace ma an daina yimata auren dole balle namiji kuma naga sauran duk ba haka aka yimusu ba agaskiya nidai afasa maganar auren nan idan bahaka ba wlh za aji kunya, cikeda tashin hankali inno tace haba tafida mai martaba kake fadawa haka? Mahaifin naka zaka kunyata a idon duniya? To bari kaji wannan sakon naka yafi karfina sai dai yanzu katashi da kanka kaje ka sanar dashi bazakabi zabin da yayi maka ba, amma kasani mahaifinka ba yayin magana 2 magana daya yakeyi kuma aduk inda yasaka doka a garin nan ana bi balle agidansa dan haka ina baka shawara da kayiwa mahaifinka biyayya kar kajawo abinda zaiyi fushi dakai, shiru tafida yayi ransa duk yagama jagulewa wannan wanne irin abu ne? Shidai wlh wannan auren bada shiba, kallon inno yayi to inno abawa faisal mana amma sai ace ni za abawa? Wlh bana so ni babu auren da zanyi ban shirya yin aure yanzu ba kafin inno tayi magana jakadiya tashigo gafara dai ranki yadade barka da hutawa ayi min izini nashigo, kya iya shigowa jakadiya inno tafada tana kokarin kishingida. [10:49PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣3⃣ Na UMMI A'ISHA Shigowar jakadiya ne yasa tafida dago dara daran idanuwansa yafara kallon jakadiya cikin girmamawa jakadiya ta durkusa ranki yadade barka da hutawa, Allah ya kareki uwar dakina sarki ya aikoni, kallonta ta maida kan tafida mai girma tafida sako daga mai martaba sarkin adalci sarki nakwarai yace kaje yana son ganinka cikeda damuwa batare da tafida yabata amsa ba yatashi yafita izuwa lungun sarki gaba daya jinsa yake kamar a mafarki, yana isa dakin sarki yaja yatsaya abakin kofa sakamakon ganin maga kofa dayayi toge akofar, cikin girmamawa maga kofa yafada dakin sarki yayiwa sarki bayanin zuwan tafida, yashigo sarki yafada atakaice, dasauri maga kofa yadawo yayiwa tafida iso suka karasa dakin sarki sannan maga kofa yafita yabasu wuri sunkuyar dakai tafida yayi Allah yaja zamaninka yanzu na samu kiranka daga wurin jakadiya,eh nine naturata takira min kai, ranka yadade na amsa kira, ibrahim! Mahaifin nasa yakira sunansa na'am, Allah yaja zamaninka, Allah yasa kafi haka tafida yafada kansa yana duke akasa, dalilin kiran da nayi maka shine kayi hakuri da abinda zakaji daga gareni, wato ibrahim aure zanyi maka nan damako biyu, ina fata zakayi dukkan wasu shirye shiryen dasuka dace nan da sati biyun, sannan ina so kayi hakuri da ita matar da zan aura maka domin ba lafiyayya bace kuma ga hotonta idan kana da bukatar gani, kansa akasa yace ya mai martaba ayi min adalci kuma asausauta min dan Allah afasa auren nan domin banida shirin tunkarar aure ahalin yanzu, kai! Wata tsawa mai martaba yadaka masa wadda ni kaina ummi Aisha sai da narazana, bafa shawararka nake nema ba umarnine nake baka, yanzu kai ibrahim har kayi girman da zan fada maka magana kayi min musu? Tuba nake ranka yadade, natuba mai zamani, ayi min afuwa hakika nayi kuskure amma ayafe min, cikin fada sarki yace to aure babu fashi zan daura shi inyaso aranar dana daura kana iya warwareshi ta hanyar sakin matar, ai kuwa zan sakenta tafida yafada acikin ransa. [8:17AM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣4⃣ Na UMMI A'ISHA Tabbas ko wacece sai narabu da ita danme za ayi min auren dole bayan ga faisal nan shi ba ayi masa ba, kuma naga komai mai martaba zai yi tare yake yi mana nida faisal sai a wannan ne za a banbanta mu? Fadan mai martaba ne ya dawo da shi cikin hayyacinsa, sanin kankane ni ba karamin mutum bane bare jama'ata su rainani, bana alqawari in saba sannan bana yin magana biyu dan haka dolenka ka amincewa umarnina domin ba kaine ka haifeni ba nine na haifeka idan hukuncin dana yanke maka yayi maka tsauri to ka mutu kabar duniyar inyaso sai ka huta da auren da zanyi maka, tuba nake ranka yadade, ayi min aikin gafara, tashi kabani wuri mutumin banza mutumin wofi, Allah ya huci zuciyarka ya mai martaba cikin hanzari tafida yatashi yafita gaba daya idanuwansa sun kada sunyi jajawur kamar gauta, ransa in yayi dubu yagama baci, dakin inno ya koma acan yaci karo da momcy bai iya yi mata magana ba yashiga dakin inno yazauna akusa da kafafunta, inno wai dan Allah laifin me nayi muku ne haka kuka tsaneni? Murmushi tayi irin nasu na manya haba tafida na, da daya tamkar da dubu, wlh tafida idan na rantse maka cewa dani da mai martaba munfi sonka fiyeda kowa acikin yayanmu ba zanyi kaffara ba, ni da mahaifinka duk cikin yayanmu munfi nuna maka so da kauna ba wai dan kasancewar ka dan auta ba a'a soyayyar daga Allah take haka nan Allah ya sanya mana sonka fiyeda sauran yan uwanka sannan nasan mahaifinka bazai taba cutar dakai ba, saboda idan kashiga damuwa sai yafika damuwar, dan Allah tafida ka kwantar da hankalinka kayiwa mahaifinka biyayya kaji? Shi wannan mutumin da zai baka yar tasa mutumin sarki ne tun suna yara, yayiwa sarki alherai da dayawa wadanda bazasu lissafu ba to kaga kuwa shi ALHERI DANKO NE! Baya faduwa kasa banza sannan kuma dadi musanye ne, abinda nakeso dakai kawai shine kayi biyayya, cikin kunar rai tafida yace amma inno ga ba faisal nan ba why not shi baza abashi ba? Sai ni za abawa danni aka tsana? Kai rufe min baki marar kunya inno tafada cikin fada dan kaga inata shawo kanka ina lallaminka da kalamai masu dadi shiyasa zaka fada min maganar banza? Anki abawa faisal din kai aka yi niyyar bawa in yaso aranar da aka daura auren ka saketa ko kuma idan ankaita gidan naka ka kasheta kaji? Fitsararren kawai in banda tsabar rashin kunya har sarki yabada umarni katsaya kana ja in ja da umarninsa? To sai gareka karka fasa, tashi maza kafice min daga daki kuma kar nasake ganin kafarka acikin dakina, da sauri tafida yatashi yafita bayi da kuyangu sai mamaki suke domin inno bata taba yiwa tafida irin wannan fadan ba kowa agidan yasan tafida shine dan lelen inno da mai martaba. [8:41AM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣5⃣ Na A'ISHA (UMMI) Tafiya yake ahankali duk da cewa dama haka yasaba tafiya amma tafiyar yau tasha banbam data kullum lungun momcy mahaifiyar abokinsa faisal kuma dan uwansa najini yanufa yana shiga jakadiya tayi masa iso yakarasa dakin momcy tana zaune akan gado wata baiwa tana yimata firfita da muhucin kaba gefenta kuma wata baiwar ce take yi mata labarun ban dariya ko sallama bai iyayiba yashiga take bayin suka bar abinda sukeyi suka tashi suka fita, akan daddumar dake malale acikin dakin ya zauna yadukar da kai barka da hutawa ranki yadade, barka kadai tafida,cikin damuwa yace momcy ko kin samu labarin abinda zai faru dani? Cikin bacin rai tace nasamu tafida dazun nan jakadiya tazo min da labarin kuma inaji banyi kasa agwiwa ba natashi natafi wurin mai martaba domin jin sahihancin labarin anan ya tabbatar min da gaskiyar lamarin sai dai nayi takaici da ba abar min kai kazabi matarka da kanka ba kamar yadda aka yiwa sauran yan uwanka sai amma kirana gareka shine kar kayi jayayya da umarnin sarki domin hakan zai iya janyo maka fushin mai martaba akanka sanin kanka ne kuma fushin Allah yana daga cikin fushi na iyaye wannan hadisine ingantacce saga bakin annabinmu annabin rahma, kayi hakuri kayi biyayya idanuwansa jawur ya dago yadubi momcy dama momcy duk wanda kaji anbawa hakuri ai cutarsa akayi cikin damuwa tace babu komai tafida ni kaina narasa dalilin sarki nayimaka wannan irin aure acikin gaggawa amma babu komai kayi biyayya kawai ni naso ace ma wannan shashan dan uwan naka faisal za ayiwa auren, babu komai momcy nagode, tashi yayi yafita yanufi sashensu shida faisal yana shiga yasamu faisal kwance afalo cikin kujera cikeda damuwa yanemi wuri ya zauna faisal yana kallon fuskarsa yasan ya amsa kiran mai martaba tashi zaune yayi yadafa kafadar tafida abokina ya akayi? Kamar tafida zai yi kuka yace faisal wlh bana son auren nan bana so bana so, cikin damuwa faisal yace wlh tafida dazun nan lokacin da akeyin maganar tun alokacin nafara rokon sarki akan yayi hakuri nasan bazaka so auren nan ba amma yaya chiroma da baba galadima suka hayayyako min da fada wai nida kai mun raina kowa afada bama bin umarnin mai martaba saboda mu yan gata ne nida kai ne kawai sarki zai bawa umarni mu tsaya muna jayayya dashi ganin sun dauki zafi yasa nataso nabaro wurin amma dan Allah kar kadamu kanka, lallashin tafida faisal yayi tayi da kalamai masu sanyaya zuciya tareda nuna masa illar rashin bin umarnin iyaye. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:21AM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣6⃣ Na UMMI A'ISHA Shidai tafida yau rauni yafi gaban ciwo kallon faisal yayi kasan Allah? Ana daura auren nan sai nasaketa kowacece cikin sauri faisal yakatse shi kar kasoma yin haka abokina domin zaka aikata babban kuskure kar kazo kayi abinda mai martaba zaiyi fushi dakai, tashi tafida yayi yashige daki yabar faisal afalo cikeda damuwa domin damuwar tafida ta faisal ce. *********************** Alhaji Ahmad Muhammad sani shine sarki na uku ajerin sarakunan garin misau ta jihar bauchi, garin misau babban gari ne sannan kuma babbar masarauta ce mai girman gaske, sarkin misau nayanzu shine sarki na uku yagaji sarautar ne ahannun mahaifinsa alh Muhammad sani nabiyu, alh Ahmad sani sarkin misau nayanzu yana da matan aure 2 hajiya kilishi (inno) da hajiya mabruka (momcy),hajiya Kilishi wadda akafi sani da inno itace uwar gida sunyi auren saurayi da budurwa ita da mai martaba lokacin baifi dan shekara 23 ba alokacin aka nadashi sarkin garin misau, Allah ya albarkacesu da yara guda 5 duka maza babban dan sarki shine chiroman misau alh Muhammad sani sai mai bimasa marafan misau alh adamu Ahmad sani sai turakin misau alh jamil ahmad sani sai barwan misau alh Mahmud ahmad sani sai kai gaman misau alh mannir ahmad sani daga nan sai dan autansu tafidan misau sannan hakimin disina alh ibrahim ahmad sani, amaryar mai martaba hajiya mabruka (momcy) yara biyu suka haifa da mai martaba babbar yarsu itace hajiya maryam (hajiya daso) sai kaninta alh faisal ahmad sani san turakin misau hakimin dambam, faisal da tafida tare suka taso adaki daya kasancewar babu yan ubanci agidan kowa yana kaunar dan uwansu bazaka taba iya banbance tsakanin dan hajiya inno da dan hajiya momcy ba saboda tsabar hadin kai, gaba daya yaran inno adakin momcy suke tasowa yayinda itama momcy ita ta aurar da hajiya daso kasancewar bata da ya mace, shi kuwa faisal da tafida kusan lokaci daya aka haifesu tsiransu kwana 5 ne atsakani shiyasa suka taso kamar wasu yan biyu sannan suka zama abokan juna dukkaninsu basuda wani aboki sai junansu tun suna yara haka suke kiran junansu kuma wani abin sha'awar shine bazaka taba jinsu sunyi fada ba kullum cikin zolayar junansu suke, gashi suna yar kama duk kuwa da cewar tafida yafi faisal kyau domin shi mahaifiyarsa ya dauko ita kuma bafulatana ce. [10:03AM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣7⃣ Na UMMI A'ISHA Tunda suka taso basa rabuwa tare suke yin komai har suka zama samari shekarunsu daya tsayinsu daya kuma ko amakaranta ajinsu daya, tun lokacin da suka gama primary school suka tafi america acan sukayi karatunsu gaba daya suna gama degree suka jona masters dinsu, zaman da sukayi akasar waje anan tafida ya koyi shan ganye shikuma faisal yakoyi neman mata amma daga nan baya wata dabi'a shima tafida daga shan ganye baya komai mace kuwa babu abinda yake hadashi da ita sai asibiti idan bata da lafiya, tun akasar turai yan mata suke nuna masa maitarsu afili daga turawan har bakar fatar amma bai taba yadda ya kusanci kowacce mace ba neman mata sai dan uwansa faisal, suna kammala karatunsu suka dawo Nigeria kowannensu yakama aiki shi tafida kwararren likitane a fannin mata shikuma faisal auditor ne a ministry for local government, basu jima da fara aikiba akayi musu sarauta shi faisal sarautar sa san turakin misau hakimin dambam shikuma tafida sarautarsa tafidan misau hakimin disina,tun asali shi tafaida bamai yawan magana bane bashida surutu magana bata dameshi ba wannan dalilin ne yasa ake yimasa kallon mai girman kai yanmata dayawa kuma suke masa kollon mai takama dakyau basusan shi haka yakeba naturally. *********************** Tafida yana shiga daki yakifa akan gado zuciyarsa sai tukuki take tamkar zata fasa kirjinsa tafito waje cikin damuwa faisal ya tashi yabishi cikin dakin yaci gaba da bashi baki amma tafida Ji yake kamar ya rushe da kuka, tashi yayi ysdauko ganye yafara busawa shikuma faisal ganin haka yasashi fara tsaki dalla malam kafita waje kagama busa hayakinka acan hararsa tafida yayi kana iya fita kai tunda ba daureka nayi ba dan iska kawai, dariya faisal yayi kaima ka kusa zama dan iskan ai tunda kakusa sanin hanyar da baka sani ba, tsaki tafida yayi yasake xukar tabar ya busar da hayakin ai wannan hanyar ko zan santa ba yanzu ba, kai dan iska ne sau nawa zaka santa? Inji faisal murmushi tafida yayi kaine dan iska amma ni banida hadi da kowacce mace,yanzu ai zakayi hadin da ita faisal yafada yana dariya, hira suka cigaba dayi har karfe dayan dare sannan suka kwanta bacci amma shi tafida bacci gagarar idonsa yayi shima faisal din baiyi dayawa ba yatashi. Kamar yadda yasaba fita yauma haka ya shirya ya dakin inno ya gaisheta dakyar ta amsa fuskarta babu walwala, fitowa yayi ya shiga dakin mai martaba shima hakan take, dakin momcy ya shiga itace ta karbeshi da fara'a ga kayan karyawa ta shirya masa sai data kara yi masa nasiha sannan yatashi yatafi. Yana zuwa asibitin su ya zauna jugum yana nazari wai shi mai martaba zai yiwa auren dole, bayan auren dolen ma marar lafiyace yarinyar, kai ai auren nan bazai dadeba yafada yana bude laptop dinsa. [10:30AM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣8⃣ Na UMMI A'ISHA Laptop dinsa yabude yashiga email dinsa anan yaci karo da wani sako daga kungiyar litocin mata ta duniya ta shirya musu wani course har na tsawon wata 5 kuma har dashi aciki zasu gudanar da course din ababban birnin kasar India wato Mumbai dadi yadanji domin dama garin yayi masa zafi da azamarsa yatashi yanufi maternity domin duba halin da suke ciki. Tunda yadawo daga office yakule adaki shi kadai yafara cike ciken takardun tafiya course dinshi anan faisal yazo yasameshi abokina dama kana ciki, eh gani kaganni kuwa, akusa dashi faisal yazauna me kakeyi? Wlh wani course zan tafi na 5 months, kai dazakayi aure wanne course kuma zakatafi bayan ga babban course zaka samu duka tafida yakaiwa faisal yace zan yimaka rashin mutunci wlh, dariya faisal yayi duk tsiyarka dai ana daura maka aure kazama bazawari,waya fada maka? Wlh karya kake kaine bazawari amma ni virgin ne dariya faisal yayi ai mun kusa muga karshen virgin domin virgin zai koma disvirgin dariya tafida yayi yace ka karaci iskancinka kagama akwai ranar ramuko. Tuni aka fara shirye shirye agidan mai martaba har an hada kayan aure irin na al'ada dana zamani ankai gidansu amarya kullum bushe bushe da raye raye akeyi agarin mai girma tafida zai angwance,ni ummi Aisha hannuna asama nace Allah yaja zamanin mai girma tafida, tunda aka fara shirin biki tafida baya shiga sabgar kowa agidan tsakaninsa da kowa gaisuwa ce daga angaisa shikenan dama can shi ba mai magana ba da faisal kawai yanzu yake magana mai tsawo shima faisal din dan bazai iya fushi dashi bane saboda sun shaku sosai, amma ko inno da mai martaba tsakaninsu gaisuwa ce yadda suke fushi dashi shima haka yake fushi dasu, ana igobe za afara gudanar da biki yafara shirye shiryen tafiyarsa India domin nan da sati 2 zasu fara gudanar da course din mai taken yaki da cutar sankarar mama (cancer),shi dai faisal shine yazama tamkar angon domin komai wanda ango yakeyi shine yayi, shikuma tafida hakan ko ajikinsa tashi yayi yaje wurin mai martaba yayi masa maganar tafiyarsa India maimartaba bai damuba yace babu matsala dama itama amaryar taka karatu takeyi koda tana nanma nace babu maganar tarewarta yanzu tunda bakaso duk lokacin dakaso ta tare nan gaba, dukar da kai tafida yayi yace godiya nake mai martaba Allah yakara nisan kwana yatashi yafita. [8:41PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣9⃣ Na UMMI A'ISHA Yana fita yayi kicibus da faisal kallon faisal yayi yadauke kai domin yafuskanci faisal ya zake akan auran nan, cikeda dariya faisal yaja hannunsa mutumina ya akayi? Shiru yayi kamar baijishi ba cikin zolaya faisal yace wai kai duk dokin zaka samu hanyar ne ya hanaka magana? Sai alokacin tafida yayi murmushi wlh kai wannan yadama ni yanzu ba wannan ne agabana ba, dariya faisal yayi zo muje abokina kaji hannunsa yakama suka nufi cikin gida har dakinsu suka zazzauna faisal ya dubeshi yace dan Allah tafida ka tsaya ka nutsu ka rungumi matarka shifa aure mukaddari ne, cikin jin haushi tafida yace me zai hana kai ka rungumi kaddarar ka aureta? Dariya faisal yayi ai ni ba abani bane amma kai kaga da yake dan gatane aure za ayi maka kasha sha'aninka tsaki tafida yayi yajawo earphone dinsa yajona ajikin wayarsa yafara shan sauti dariya faisal yayi yace kadai kusa ka zama bazawari, jin shiru tafida bai amsa ba yasashi gane cewa bai ji abinda yace ba domin dayaji da sai ya bashi kyakkyawar amsa domin babu abinda yatsana irin yaji yakirashi da bazawari tashi faisal yayi yafita yana dariya. Shirye shiryen biki ya kankama yayinda shi kuma tafida yaketa shirye shiryen barin kasar, ranar alhamis aka sanya amarya a lalle faisal shine yake tsaye akan komai kullum baya samun lokacin kansa daga nan zai yi nan gidan mai martaba kuwa ya cika yayi dam da al'umma garin in banda kade kade da raye raye babu abinda akeyi domin sarki zai aurar da dan autansa kuma dan gaban goshinsa amma shi tafida in banda fushi babu abinda yakeyi gaba daya yadaina walwala yazama marar fara'a gashi kullum sai sunyi fada da faisal, ranar juma'a aka fara niyyar daura auren tafida amma kememe yaki kirshayawa. [9:05PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 2⃣0⃣ Na A'ISHA (UMMI) Babu yadda faisal bai yi da tafida ba kan ya shirya su fita domin da misalin karfe 1:30 za adaura auren amma yaki yarda yatashi ya shirya tun faisal yana yimasa cikin lallami har yafara fada shiru tafida yayi masa bai tanka masa ba, ganin haka yasa faisal yakara tunzura ya hasala yafita daga dakin, lokacin har su mai martaba sun tafi inda za adaura suren, faisal shi kadai yatafi yasha fararen kaya masu tsada yana zuwa lokacin wurin yacika makil amma haka yasamu ya kutsa ya isa wurin mai martaba sarki yana ganinsa yafara tambayarsa ina tafida cikeda damuwa yace ranka yadade bashida lafiya ne bazai iya zuwa ba, cikin fushi mai martaba yace yayi daidai kuma rashin zuwansa bashine zai sani nafasa yimasa wannan auren da nayi niyya ba, hakuri faisal yafara bawa sarki tuba muke ya mai martaba ayi mana uzuri,galadima ne ya matso yace ranka yadade ni ina ganin afasa daura auren nan da tafida abawa faisal, girgiza kai sarki yayi a'a galadima banki ta takaba amma nidai da tafida zan daura auren nan, nan aka fara daurin aure waliyyan amarya sunzo aka daura auren tafida da amaryarsa akan sadaki naira dubu dari, ana gama daurin aure sarki yakira uban amarya gefe yafara yimasa bayani kan cewar amarya ba yanzu za akawota ba sai lokacin da yayi magana gyada kai mahaifin amaryar yayi tareda yiwa mai martaba godiya, ana kammalawa faisal ya koma gida afalo ya taradda tafida kwance yana danna wayarsa dariya faisal yafara yi yamikawa tafida hannu assalamu alaikum mr ango harara tafida ya cilla masa yayi tsaki wata dariya faisal yayi mr ango asamo hanya lafiya amma banda rashin imani dan wlh idan kayi mata takarfi zaka iya kasheta, tashi zaune tafida yayi wlh faisal kar ka kaini bango, ya isheka, murmushi tafida yayi daga fadar gaskiya? Allah yabaka hakuri gyara kayanka baya zama sauke mu raba, murmushi tafida yayi yau kam yazama amma kabari duk lokacin dana nemi hanyar narasa zan nemi taimakonka, zama faisal yayi bawani nan dama can kasan inda take, wai kai sau nawa zan fada maka ne? Wlh Allah ni ban san ta inda take ba kai nifa ko haihuwa idan zan karba bana tsayawa naduba kawai aikina nakeyi dariya Faisal yayi to congratulations yanzu zaka gane ta inda take sallamar jakadiya ce ta katse musu hirar tasu. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:27PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 2⃣1⃣ Na UMMI A'ISHA Har cikin falon jakadiya tashigo tarussuna barkanku da hutawa samarin kwarai tafida ta kalla ranka yadade mai martaba yana kira tana gama fadin haka tajuya tana cewa afito lafiya, tashi tafida yayi yafita shikuma faisal bai bishi ba domin yasan fada zaisha awurin mai martaba yana tsoron kar yaje ahada dashi, tafida yana isa dakin mai martaba yasameshi shida inno da momcy zazzaune gabansa wuri yasamu yazauna gabansa yanata harbawa, cikin fada mai martaba yafara magana ibrahim ka raina kowa agidan nanko? Kanuna mana mu bamu isa dakai ba kenan tunda har za muyi maka umarni amma kasa kafa ka shure, saboda baka daukemu da daraja ba shine zaka ki halattar daurin aurenka ko? To ka kyauta kuma duk abinda kayi daidai ne domin ahalin yanzu sai dai kanemi wani uban amma baniba aure kuma nayi maka shi sai dai zaka iya nunawa duniya rashin matsayina ta hanyar sakin matar, nanfa inno itama tadauka ya saketa mana shiyasani kuma mutumin banza kawai kai in banda tsabar raini har ayi maka umarni ka ki bi? Yaran yanzu bakuda kunya kota sisin kobo muda aurenma basai an tare zakaga matar ba,waye zai tsaya jin ra'ayin mutum, hakuri momcy tafara basu hajiya inno ayi hakuri dai, mai martaba dana yayi kuskure amma ayi hakuri ayi masa gafara ayafe masa kar yashiga cikin wani hali dan Allah aduba kokena, tashi inno tayi tafita tanata fada shima mai martaba tashi yayi yafice yatafi fada, kallonsa momcy tayi tafida baka kyauta ba meyasa zakaki zuwa wurin daurin auren? Cikin kasala yace momcy ni auren ne bana so, 27 years nayi aure? Is too early wlh,murmushi momcy tayi babu komai yanzu abinda nakeso dakai anjima da daddare kuzo kaida faisal kubawa sarki hakuri kaji? Naji momcy, yawwa Allah yayi maka albarka, tashi yayi shima yafita. [9:47PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 2⃣2⃣ Na UMMI A'ISHA Da daddare faisal yasaka tafida agaba sukaje wurin sarki suka bashi hakuri amma sai dakyar suka samu ya sauko sa'arsu daya su yan lelensa ne domin badan hakaba da zai dade yana fushin bai huceba, daga nan sashen inno suka shiga itama suka bata hakuri tsakanin da da uwa sai Allah nan itama ta huce tace tahakura suna dawowa dakinsu faisal yafara bawa tafida shawara, abokina kafin katafi India yakamata kaje kaga amaryarka kayi mata sallama, tsaki tafida yayi naji zanje, yawwa mutumina yakamata kaje. Abangaren gidansu amarya kuwa koda mahaifinta yaje musu da batun rashin tariya dawuri nan dangi suka fara kace nace wasu kuma mamakine ya kamasu wannan wanne irin aure ne kodan anga basuda kudi shiyasa za araina musu wayo? Shidai uban amarya baice komai ba kuma zancen da nake yimuku har yau nidai ummi Aisha banga kalar amaryar tafida ba balle na zayyano muku yanda take, kasancewar sarki mutum ne mai adalci yasa ya aikawa da gidansu amarya kayan abinci kala kala yace arinka ciyar da amarya kuma duk lokacin da yakare zai aiko wani sannan duk wata bukata tata arinka sanar dashi hakan da yayi ba Karamin dadi gidansu amaryar sukaji ba. Tafida shirin tafiya yagamu domin yau saura kwana 2 yabar kasar, wanka yayi ya shirya yadau kwalliya cikin bakin danyen boyel yasa bakar hula takalmin kafarsa ma baki yaafito sai zuba kamshin turare yake take fadawansa suka bude masa motarsa yashiga suka rufa masa baya driver yaja sai disina, suna zuwa suka zarce wani dan madaidaicin gida daga ganin gidan gidan talakawa ne masu rufin asiri, cikeda yatsina fuska tafida yafito daga motarsa yanufi cikin gidan fadawansa suna take masa baya, babu ko sallama yakutsa kai cikin gidan yana rayawa aransa wai dan abin kunya nanne gidan sirikansa kai Allah ya kiyaye, atsakar gida yahango mahaifin matarsa da mahaifiyarta tana hura wuta, kafarsa yasa yayi bol da wata buta ta farin karfe atsakar gidan da alama butar mai gidan ce, dayake gwanine wurin kwallo take butar tawuce tasaman kan mai gidan taje tadaki bango tadawo baya tafadi atsakar gidan ta tankwashe yanda bazata moruba har abada. [10:07PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 2⃣3⃣ Na UMMI A'ISHA Cikin tashin hankali mahaifiyar matarsa tafara magana suwaye ku? Me kukazo yi anan gidan? Cikin yayyatsina fuska tafida yadubi wannan mitumin yace bawan Allah yadda kasa aka daura min aure da yarka to tun wuri kaje kasa awarwareshi domin bazan zauna da itaba kuma bazan taba sonta ba, banda tsabar son zuciya tayaya zaka dauki yarka ka kaiwa mai martaba rallarta har alika min ita, to bana sonta kuma sai nasaketa sai asannan suka gane ashe shine mijin yarsu sirikinsu duk cikinsu babu wadda yayi masa magana kawai tsayawa sukayi suna kallonsa fadawansa kuwa sai fadi suke hutawarka lafiya tafida wannan sako naka ya je inda kakeso yaje, abi tafida a zauna lafiya tafida buhun karangiya ko an zazzage dole sai ya makale, gaba salamun baya salamun dan sarki jikan sarki, gunbar dotse, icen kan kabari titi kafi karfin a tsallakaka dole sai an waiga, takawarka lafiya toron giwa dawisu da ado aka sanka, ragayar dutse namijin fama, juyawa tafida yayi yafita daga cikin gidan fadawansa suka rufa masa baya kai tsaye fadarsa yawuce inda wakilinsa yake, anan ya tambayi wakilin nasa wacce gonace tafi kowacce girma agarin? Cikin washewar baki wakili yace ranka yadade gonar sirikinka malam faduluddeen gonarsa tafi takowa girma cikin rashin damuwa tafida yace ok to inaso nan da sati mai zuwa agyara min domin zan turo masu aiki zasuyi min ginin gidan shakatawata awurin, cikin mamaki wakili yace yallabai sirikinka fa, ka iya bakinka wakili fadawa suka fada lokaci daya, shiru wakili yayi yace tuba nake yallabai tashi tafida yayi yana bawa sarkin fada sallahun ginin da za azo ayi masa, cikeda farin ciki yakoma gida domin yasan abinda yayiwa mahaifan matarsa dole zasuji haushi kuma kila zasu samu sarki suce yasashi yasakar musu yarsu amma abin mamaki shiru yaji ba wani batu alokacin har ansoma fara yimasa ginin gidan da yabada umarni acikin yanayin yashirya yanufi kasar india yana cikeda haushin auren da yake kansa. [10:45PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 2⃣4⃣ Na UMMI A'ISHA Lokacin da tafida ya tafi india ya samu damar mantawa da auren dayake lankaye akansa sai dai kusan kullum idan sunyi waya da faisal yana yawan yimasa maganar amaryarsa dariya kawai tafida yakeyi domin yanzu ya daina damuwa idan faisal yana yimasa tsiya, cikin ikon Allah yasamu yagudanar da course dinsa cikin kwanciyar hankali da nasara wata 5 daidai yayi yafara shiri ysdawo Nigeria. Ranar da yadawo ranar fada ta cika makil da yan sannu da zuwa faisal kuwa sai zolayarsa yakeyi amma yashareshi har sai da suka koma daki sannan yakalli faisal yace mekake cewa dazu? Dariya faisal yayi abokina kayifa kyau sosai kayi fresh kodai kabi hanyar ne? Tsaki tafida yayi kai wai baka da wata magana sai kwaya daya? Ai ni nafada maka ko zanbi hanyar da kake fada to ba yanzu zan bitaba, dariya faisal yayi to malam yakamata fa kasan inda dare yayi maka dan wlh nakusa korarka daga dakin nan? Wazaka kora? Kai zan kora tunda yanzu Kai magidancine so sai kakoma wurin iyalinka, kamanta zurriyya ba iyaliba tafida yafada tareda mikewa yafara cire rigar jikinsa domin shiga wanka. Washe garin ranar da tafida yadawo yakwanta yayi baccinsa ranar bai je office ba sai wurin 11 sannan yashirya cikin suit milk colour yasa milk colour din takalmi yasha turare yafito dan zuwa asibitinsu yana so yaje yakai report, agidan baya yazauna acikin motarsa fadawansa suna tareda shi har asibitin yana fitowa daga mota wasu yanmata wanda zasu kai kimanin su 20 suna sanye da unifoam suka fara kallonsa da alama yan practical ne aka turosu asibitin duk cikinsu babu wadda tafida bai tafi da imaninta ba nanfa suka fara tattauna maganar a tsakaninsu. Sai da tafida yayi hutun sati 2 sannan yafara zuwa office aranar dayaje yana tsaye acikin office dinsa yana daddanna wayarsa wata nurse tashigo masa office akidime pls sir ka taimaka mana munada patient wadda take neman taimakon gaggawa kamar baijiba yayi har saida ta sake maimaitawa sannan yace yaji yabi bayanta har zuwa female ward can gadon karshe takaishi tace gata sir wannan ce, gaban gadon yakarasa wata yar budurwa yagani wanda shekarunta zasu kai 23 aduniya tana sanye da farar riga da bakin dark blue din wando daga gani yar practical ce domin yaganta da unifoam din yan lab science. [11:12PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 2⃣5⃣ Na UMMI A'ISHA Kallon fuskar ta yayi kyakkyawa ce ta daukar hankali shidai yana ganin mata masu kyau amma baiga wadda ta kai wannan kyau ba duk kuwa da cewa baka ce amma bakinta mai kyau ne har wani shining take kallon nurse din yayi me yasameta? Cikin inda inda tace let me go and call her friend she's d one dat brought her here, dasauri tafita Jim kadan sai gata dawata budurwa itama tana sanye da uniform irin na wadda take kwancen kallonta tafida yayi meya sameta? Dr wlh kawai muna zaune mukaga tafadi, sai alokacin yasa hannunsa yatabata amma da bai taba koda hannunta ba ya salam! Yafada saboda jin laushin fatar jikinta, nan yafara jin wani yanayi ajikinsa daurewa yayi yafara checking dinta anan yasamu yagano matsalar tata yayi mata allurai har guda hudu alokaci guda, kallo yabita dashi dama wannan ai dole tasamu matsala saboda tahadu sosai shiyasa takamu da ciwon mara mai tsanani wanda bazata taba warkewa ba har sai tasadu da namiji, fita yayi yakoma office dinsa sai 3 yashiga round yana shiga yan practical suka fara gulmarsa wannan likitan duk asibitin nan yafi kowa kyau, ai duk misau ma babu mai kyanshi inji wata aciki, yana tafiya yana duba patient har yazo gadon karshe inda yanmatan nan suke, waje yace sufita yafara duba patient dinshi wadda har ta wartsake kallonta yayi doguwa ce baka tanada manyan idanuwa da dogon hanci gata da dan tsukakken karamin baki, gashin girarta mai yawane batada kiba dayawa amma tana hips da cikar kirji sosai, yanmata kin tashi? Ya tambayeta, biron hannunsa ta karba da takarda tayi masa rubutu kamar haka, bana jin abinda kafada ni bebiyace kuma kurma ce, mika masa tayi yakarba ya karanta cikeda mamaki ya rubuta mata, ayya sannu, amma ko kin san ke kyakkyawa ce? Mika mata yayi takarba tagani takaranta tayi masa reply nagode amma Kayi hakuri ni matar wanice, karba yayi yai murmushi nima mijin watane, murmushi tayi wlh inada aure, bai gasgata ta ba saboda yaga tana fama da matsalar ciwon mara sperm yataru dayawa a mararta gashi har ya haifar mata da ciwo shi kuma yasan da ace tanada aure da hakan bazata faruba kallonta yasakeyi waye zai mallaki wannan a matsayin mata yatsaya yazuba mata ido yana kallonta? Kai karyane gaskiya budurwa ce cikakkiya kuma. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 2⃣6⃣ Na UMMI A'ISHA Wani tsadadden murmushi tafida yayi mata yace ok koma dai menene bari na rubuta miki maganin dazai taimaka miki, wata yar takarda yadauka ya fara rubutu yana gamawa ya mika mata gashi Allah yabaki lfy, duk wadannan maganganun da yakeyi bata jinshi murmushi yayi mata kinyi min kinyi daidai da tsarina hannunta tadaga tayi mai nuni ma'ana me yake nufi, murmushi ya sakeyi wanda har sai da fararen hakoransa suka bayyana kumatunsa na dama ya lotsa kusan ko magana yakeyi sai yadan lotsa kallonsa tayi taji gabanta yafadi wannan likitan yanada kyau tafada acikin zuciyarta astagfurullah tayi saurin tuba saboda tunowa datayi itafa matar aure ce, fuskarsa ta kalla lokacin da yake yin rubutu ajikin takarda yadan dunkuyar da kansa yanayi yana lasar lebenshi nakasa wanda suke jaja jaja duhu duhu domin tabar wiwin da yakesha tahadu da jan lebensa sai tabada wata irin kala mai kyau kamar yana shafa jan baki gashi farinsa irin mai dan jan nanne kura masa ido tayi kai wannan saurayin yana yimata kama da Seth rollins dan wrestling domin har tsayinsu ma zai zo daya gashi manyan idanuwansa ma irin nasane sak, dagowa yayi yana murmushi yamiko mata takardar yayi mata wani kasalallen murmushi yajuya yafara tafiya ita dai nurse tana tsaye tana kallon ikon Allah domin tunda take acikin asibitin nan bata taba ganin dr tafida yayi irin haka da wata patient ba babu ruwansa da kowa tsakaninsa da kowa gaisuwa ce amma sai gashi yau har dasu bude hakora taf lallai wannan tacika mai nasara. [12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 2⃣7⃣ Na UMMI A'ISHA Yana juyawa marar lafiyar tafara kallonsa yahadu sosai ta kissima aranta sai da yafita tabude takardar da yabata tafara karantawa kamar haka Yake kyakkyawa agaskiya yau idona ya yi duban da be taba yiba hakika banyi kuskure ba idan nakiraki da suna tauraruwa kigodewa mahaliccinki domin ya tsara halittarki irin tsarin da har yau banga wadda takaiki ba, ina sonki zuciyata takamu da kaunarki alokaci guda,ina taredake aduk inda kike luv u! I. T. Tana gama karanta wasikar kawayenta suka shigo dukkaninsu kowacce tana sanye cikin unifoam nanfa wata daga ciki tafara yimata tambaya da hannu alamar meya ce mata murmushi kawai tayi bata fargaba taji sun fizge takardar hannunta karantawa sukayi take kuma bakin ciki ya mamaye zuciyoyinsu domin agaskiya wannan likitan bai dace da ita ba dasu yadace mutum dayace bataji haushin hakanba asalima murna tayi sukuwa sauran ji sukeyi kamar su shaketa dan haushi. Dr tafida yana fita daga female ward yanufi office dinsa zuciyarsa cikeda tunanin yarinyar da yagani sai dai yana jin tausayinta har cikin ransa domin abin atausaya matane gata budurwa har budurwa kyau iya kyau amma dayake Allah alhakimu ne sai ya iyota kurma kuma bebiya, duk da haka zuciyata tana sonki yanmata ni babu ruwana da jinki ko maganarki ke kawai naji ina so, zama yayi yafara kiran fadawansa minti kadan sai gasu kayansa yace su hada masa zai tafi gida babu bata lokaci suka harhada duk wasu abubuwa nasa suka fita,tashi yayi yacire bakar coat din jikinsa yabar iya tacikin wadda take light green mai dogon hannu da neck tie baki da green, ahannunsa yariko rigar idonsa yana sanye cikin farin glass yana tafe yana daddanna wayarsa. [12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 2⃣8⃣ Na UMMI A'ISHA Fadawansa na hango shi suka zabura suka zo suka fara take masa baya suna tafe suna zabga kirari, takawarka lafiya, alafiya dai tafidan alheri, gaba salamun baya salamun namijin fama, babban goro sai magogin karfe, karo da karo sai rago, wani Kaya sai amale wane jaki, buhun kaya kake mai daukarka sai wanda ya shirya, kogi ba ayi maka katanga, kaga katangar sukari kowa ya jingina sai ya lasa, sauka lafiya dan ahamadu jikan sani, farin wata sha kallo, lafiya dai mai dogon zamani, gaba salamun baya salamun,shi dai tafida tafiya kawai yakeyi yana yin waya da faisal amininsa kuma dan uwansa har ya isa gun motarsa suka bude masa ya shiga ya zauna, daliban nan duk akan idonsu hakan tafaru har motar tafida tafita daga cikin asibitin, daya daga cikinsu mai suna sakina itace ta tabe baki wai kuga haduwar wannan gayen amma yarasa wacce zai so sai waccan kurmar,bebiya dukansu baki suka tabe wayaga abinda rai keso inbanda haka me zaiyi da ita kuma kunji ma dan gidan sarki ne ashe, daya daga cikinsu ce ta katsesu haba sakina meye amfanin haka? Ina ruwanku dasu, wannan abun da kukeyi babu kyau hassada ce ita kuma hassada Annabi yayi hani da ita domin akwai wani ingantaccen hadisi da manzon Allah s.a.w yake cewa iyyakum wal hasadu, fa innal hasadu ta akulul hasanati kama ya akulul narul hadabe, ma'ana nahaneku da hassada domin ita hassada lallai tana cinye kyawawan ayyuka kamar yadda wuta take cinye itatuwa ko kuma karare, dan haka wannan abin da kukeyi wlh bashida amfani ko kadan,soyayya ta Allah ce idan kukayi hakuri kuma zaku samu rabonku, tana gama fadin haka tabar wurin takoma cikin female ward, tsaki sakina taja wannan damuwarki ce amma wlh bazai yiyu ace mu masu baki da kunne yakimu yaso kurma ba. Tafida jinsa yake kamar bashiba har yaje gida,shidai bai taba soyayyaba asalima ko budurwa bai taba yiba saboda shi miskili ne nagaske kai kallon mata ma bai dameshi ba, baya hulda da mata ko kadan amma yau yayi gamo, gamo wanda za a iya cewa kyakkyawan gamo. [12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 2⃣9⃣ Na UMMI A'ISHA Cikeda farin ciki ya isa gida sai wata walwala yakeyi marar kan gado domin babu wadda ya saba ganinshi cikin wannan yanayin su kansu fadawansa mamaki sukeyi yadda yau yake cikin nishadi da walwala, suna isa tangamemen gidansu yafito daga cikin mota fadawan dasuke tsaron kofar suka mimmike tsaye suka fara gyara kintsi gaba salamun baya salamun barka da shigowa tafidan zamani tafida ba akawo maka wargi, takawarka lafiya dan toron giwa, dan zaki kafi karfin rainon kura, ko kura ta mutu tafi karfin kare yaja gawarta, namijin dawa kake mai kayan alfarma, barka da shigowa zaki dangin sikari, tsawo dangin rama, takawarka lafiya gaba salamun baya salamun, cikeda jin dadi tafida yadaga musu hannu kamar yadda yasaba yanufi zauren dazai sadashi da lungun mai martaba yana zuwa kansa tsaye yawuce cikin dakin mai martaba yasameshi zaune yana kallon labarai atashar CNN zubewa yayi yafara diban gaisuwa, sannan yatashi yafita yanufi wurin inno itama a falonta ya taradda ita tana kishingide jikin tumtum ga bayi zagaye da ita sunayi mata firfita ka kayan motsa baki a gabanta shiga yayi yazauna a kan kujera bayinta suka tashi suka fiffita anan ya zamo kasa ya gaida ta yatashi yafita yau gaba daya jinsa yake kamar wani sabon mutum dan tsabar nishadi, yana isa dakinsu yashiga toilet yayi wanka yafito yasaka kayan yan kwallo jar riga mai number 1 ajikin rigar da wando dogo,adaki yayi salla yana idarwa yafito yanufi wurin dawakansa yasamu har an daura masa sirdi domin fita kilisa shi kadai kawai ake jira baiyi wata wata ba ya haye dokin shima sarkin fada yahau nasa da alama yau su biyu zasu fita kilisar, tafe suke ahankali kowannensu rikeda linzamin dokinsa har suka isa wasu manyan gonaki, tafida ne yayi yar magana ahankali kamar yadda yasaba, sarkin fada wannan gonar idan baka mantaba nataba fada muku zatayi daidai da tsarin danakeso wurin gina business suit dina, Allah ya taimakeka tafida sarkin fada ya fada,amma yallabai wani hanzari ba gudu ba wannan gonar itama ta sirikinka kace idan ban mantaba, yatsina fuska tafida yayi koma tawaye a cikin satin nan za afara yimin aiki, Allah yaja kwana,Allah yasa kafi haka, sarkin fada yafada amma acikin zuciyarsa cewa yake wannan wanne irin mutum ne ace duk gonakin sirikinka sai bi kakeyi kana karbewa kana gini marassa dalili. [12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 3⃣0⃣ Na UMMI A'ISHA Haka suka karaci shawaginsu suka koma gida lokacin magriba tana daf da kawo jiki, suna isa gida tafida yasauka daga dokinsa a gajiye ya shige gida afalonsu ya zube akan carpet ya kwanta gaba daya ya gama gajiya, jinsa yake kamar yayi wani gagarumin aiki, fuskar wannan yarinyar ya hango take yayi wani murmushi insha Allahu sai na auri wannan yarinyar yafada azuciyarsa domin kyakkyawa ce ajin karshe, amma mamakinsa shine yadda take karatun science alhalin kuma bata ji kuma bata magana hakika ta cika yar baiwa gashi komai nata mai kyaune tamkar ita tayi kanta saboda yadda halittar ta tatsaru sosai, lumshe manyan idanuwansa yayi oh ko meye sunanta? Tsabar yarude yamanta bai tambayi sunanta ba shigowar faisal cikin falon ne yasashi dago kansa yakalleshi abokina daga ina? Zama faisal yayi daga dambam nake kasan garin nawa kullum basa rabo da rikicin manoma da makiyaya, murmushi tafida yayi uhm dakyau hakimi, dariya faisal yayi kaima dai dadinta hakimin ne, murmushi tafida yayi masa wadda har saida faisal yayi masa magana yau naga kana ta fara'a kodai? Murmushi tafida yayi babu abinda yafaru amma nazo maka da albishir nasamo matar aure dariya faisal yafara yi bakada seti tafida yaushe kayi aure da har zaka fara neman wani? Tsaki tafida yayi kaga babu ruwanka malam ni namanta ma wlh da wani auren da mai martaba yayi min, kallonsa faisal yayi to wlh kafadawa yarinya gaskiya tunda wuri ka sanar da ita gaskiyar lamari kai bazawari ne ba saurayi ba dan kanada mata yakarasa maganar cikeda dariyar mugunta,shiru tafida yayi masa bai bashi amsaba amma yatsani faisal[truncated by WhatsApp] [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 3⃣1⃣ Kallon faisal yayi malam banida lokacinka yanzu yana gama fadin haka ya mike yanufi lungun inno zuciyarsa fes domin yana cikeda farin ciki a wannan rana. Daren ranar bacci kadan yayi domin alla alla yake gari ya waye yaje yaga wannan yarinyar, asuba tana yi yatashi yafita masallaci yayi salla yana dawowa ya dauko alqur'aninsa ya buda yafara karantawa har karfe 6 tayi sannan yaje yayi wanka yafito ya shirya cikin suit ash colour hatta takalmin kafarsa ash colour ne yadaura agogon Gucci na azurfa duk wannan budurin da yakeyi faisal yana kwance yana kallonsa sai da yagama shiryawa tsaf faisal yace gaskiya kayi kyau mitumina wlh babu wanda zai ganka yace kai ba saurayi bane kamar ba kayi aure ba, tsaki tafida yayi Allah yasa kaima asatin nan dai ayi maka auren inyaso muga ta tsiya, dariya faisal yayi gaskiya kam gara mai martaba ya taimaka min yayi min aure tunda gashi har Kanina zaiyi mata 2 ina zaune niko daya banyi ba dariya tafida yayi yajuya yafita bai ce komai ba yana fita yashiga gurin inno ya gaidata yafito yaje wurin mai martaba shima ya gaidashi sannan yayi haramar tafiya office lolacin karfe 8 saura minti 20. Yana zuwa office yazauna akan table dinsa yadauki yar farar takarda yayi rubutu yasa agaban rigarsa yafito yanufi female ward, yana shiga nurses suka fara gaisheshi morning sir! Morning kawai yake cewa yawuce, da haka har yaje last bed inda budurwar nan take, kallon kyakkyawar fuskarta yayi yai mata murmushi ita dinma shi take kalllo wata farar takarda ya miko mata takarba yana bata yajuya yafita dama abinda yakawo shi kenan, theatre ya hara dan yanada aiki acan, yana fita ta bude takardar tafara karantawa rubutunsa kyau kadai kamar wadda aka buga ajikin computer, sakon nasa takaranta kamar haka "some people hv a nice smile, some hv a nice eyes,and some hv a nice faces, you u hv all of them & nice heart Good morning & hv a nice day! I. T, tana gama karantawa sai kuma tasoma hawaye wanda nikaina ummi Aisha ban san ko na menene ba. [12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 3⃣2⃣ Na UMMI A'ISHA Kuka take sosai wannan wanne irin abune da aurenta ta rinka son wani mutum nadaban, istigfari tafara yi ba kakkautawa acikin yanayin kawarta zara'u sulaiman tazo ta sameta zama tayi gefen gadon tafara tambayarta da hannu meyafaru? Dakyar tadauki biro zara'u yau zan bar asibitin nan dama kin san acikin satin nan zan gama practical dina gida zan koma idan kingama naki ma hadu a sch dariya zara'u tayi to kijirani zanje nadawo tana gama rubuta mata ta tashi tafita, hawayenta tagoge tadauki takardar taboyeta acikin rigarta, tana nan zaune aka kawo wata mata marar lafiya agadon kusa da ita aka kwantar ta Jim kadan sai ga likitanta yazo wato dr tafida idonsa akanta yaje yagama duba matar nan yabata dukkan taimakon daya kamata sannan yadawo inda take, da ido yayi mata alama wai meya sameta idonta yayi ja, murmushi tayi takada hannu alamar babu komai takarda yadauka yarubuta mata meye sunanki? Da babban baki tabashi amsa sunana HANFA yana karantawa yayi murmushi meye ma'anar hanfa? Dan ni ban taba jin wannan sunan ba, murmushi tayi yakamata ka rinka bibiyar tarihi amma nabaka assignment go and find out d meaning of hanfa murmushi yayi yace zan kuwa baki mamaki domin zan samo miki ayau basai gobe ba yana gama rubutawa yabata yafita daga masu jinyar har nurses din kallonsu suke tayi to kodai sun san juna wannan abin mamaki ya isa domin ada ibrahim tafida (I.t) baya tsayawa yayi magana da patient amma gashi yau yatsaya yanata rubuce rubuce da kurma gulma nurses din suka fara yi agefe daya duk dai sun san ita wannan marar lafiyar yar practical ta hadu ta cancanci hakan. [12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 3⃣3⃣ Na UMMI A'ISHA Agurguje yagama abinda yakeyi ya koma gida abinda bai saba yiba tashi karfe biyu amma yau yayi saboda yana so yasamu damar binciko ma'anar sunan hanfa, yana zuwa gida yasamu sirikinsa yana fitowa daga fada ko kallonsa bayi ba balle yasa ran zai gaisheshi tafiyarsa yayi cikeda takama fadawa suna biye dashi suna takawarka lafiya dan toron giwa gaba salamun baya salamun dahaka yashige gida dakinsu yaje yabaje ya jawo laptop dinsa yafara searching din hanfa sai da yadade yana nema sannan ya samo cikeda farin ciki yatashi yaje dakin inno bata cikin dakin dan haka kan gadonta ya haye yayi dai dai yana tunanin hanfa ba shakka sunanta ya dace da ita kuma ya cancanceta ganin inno bata shigoba yasashi mikewa zai fita daga dakin sai gata kuma ta shigo,a'a tafida dama kana nanne? Kai yadaga mata ina nan inno ai tun dazu nadawo amma sake fita zanyi, to amma dai sai kaci abinci ko? Murmushi yadanyi to inno abani kadan naci dakanta tafita ta hado masa abinci takawo masa harda kayan marmari agefe zama yayi yadanci abincin kadan yatashi yafita yakoma dakinsu yayi wanka yafito yashirya tsaf cikin blue colour din jeans da riga dark brown mai gajeren hannu yana fitowa yahadu da faisal ya yau da wuri zaka fita kilisar ne abokina? Faisal ya tambaye shi, no zanje asibiti ne amma bazan wani jimaba zan dawo, ok sai kadawo faisal yafada yawuce ciki shi kuma tafida ya fita, yana zuwa su sarkin fada suka bude masa kofar mota ya shiga ya zauna sai asibitin kwararru na rasheed shekoni wanda yake da xango acikin garin misau. [4:08PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 3⃣4⃣ Na UMMI A'ISHA Suna isa asibitin ya nufi female ward yashiga nurses din dake ciki sai fadi suke welcome sir! Last bed ya hanga amma babu kowa cikin rudewa ya tambayi daya daga cikin nurses din ina patient din dake last bed? Ahankali tace dr dazu tatafi, ahargitse ya kalleta are you mad? Danme zaku barta tatafi ban sallameta ba, meye amfaninku agurin? Wannan ya nuna min cewar baku san aikinku ba, sai kun karbi query saboda sam bakuda hankali hakuri suka soma bashi we are sorry sir! Ko kulasu bai yiba yafice daga cikin ward din, to shi yanzu ina yanufa? Tunda bai san inda yarinyar nan takeba sa'arsa daya yasan sunanta, fita yayi yashiga motarsa fadawansa suka rufa masa baya, ransa abace yake yau sanadiyar rashin ganin hanfa da wannan bacin rai suka karasa gida yana zuwa dakinsu ya fada akan gado ji yake kawai kamar ya fashe da kuka, tabar wiwi ya janyo ya kunna ya fara zuka nan fa ya turnuke dakin da hayaki kamar salansar babur, faisal dake kwance kusa dashi yana bacci ya bude ido yafara kallonsa dan ganye ka fara zuke zuken naka ne? Shiru tafida yayi masa domin bacin ran dayake ciki baxai barshi ya iya yin magana ba tabarsa yaci gaba da busawa batare da yace komai ba tuni idonsa ya kada yayi jajawur kamar jini ganin abin bana kare bane yasa faisal kwace sauran wiwin ya boye yana cewa kai meyasa wani lokacin baka da saiti ne? Sai kaje kajawa kanka wata cutar, kana likita amma baka san abinda zai illataka ba, dakyar tafida ya iya bude baki yace faisal ban ganta ba, wacece? Faisal ya tambayeshi yarinyar da nace maka nahadu da ita a asibiti, to kuma shine zakazo kayita shan wiwi? Ai kamata yayi katsaya ka nutsu ka binciko inda take amma baka zauna kayita bunkawa cikinka hayaki ba lumshe idanuwansa tafida yayi yace nagode abokina insha Allah zan kokarta kwanciya yayi yafara hango kyakkyawar fuskar hanfa, Allah sarki kowa da yadda Allah yake jarrabarsa ita kuma haka Allah ya halittota kurma sannan kuma bebiya amma ya tsara halittarta yadda bazai kwatantu ba, dan tsaki yaja ni ba muryarta nakeso ba kuma ba jin maganarta nakeso ba ita kanta nake so kuma insha Allahu sai na mallaketa. [5:09PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 3⃣5⃣ Na UMMI A'ISHA Zama jugum tafida yayi yana ta sake sake acikin ransa gamida tunanin yadda zai nemo sahibarsa hanfa daren ranar bashida wata walwala har gari ya waye, shiryawa yayi yadda yasaba cikin suit bakake yasa bakin takalmi yasa glass dinsa fari dan siriri yafito agurguje ya leka wurin mai martaba yafito yashiga wurin inno yana fitowa yanufi asibiti koda yaje tuni har ma'aikata sun firfito manyansu da kananansu, gakuma yan attachment suma duk sun fito, yana zuwa yawuce office dinsa yafito yashiga maternity jim kadan yafito yashiga female ward nanma bai fi minti biyar ba yafito yana fitowa yashiga antenatal,yana fitowa yadaga yan yatsunsa guda biyu yashiga office take dogarawansa suka furtsa aguje suka nufi office dinsa nanfa yan practical suka fara kace nace wato wannan daga yatsun dayayi ashe fadawansa yayiwa magana lalle sarauta sai me ita,basu farga ba sai ga wani bafade guda daya yazo inda suke yayi musu sallama yace wacece zara'u acikinku? Gani zara'u ta amsa, to kizo mai girma tafida yana son ganinki, hanzarta yanmata, tafida ikon Allah tafida mai jan doki, dasauri zara'u ta tashi tanufi office din dr tafida yayinda dogari yake biye da ita yana fadin takawarki lafiya yanmata, gyara kintsi bakuwar tafida alafiya dai gaba salamun baya salamun, ita dai zara'u gaba daya atsorace take domin bata san me zai biyo baya ba, yayinda kawayensu suna can suna ta gulmarta ita da hanfa to ko yanzu zara'u zai ce yana so? Inji wata acikinsu kudai jira muga dawowarta tukunna sakina tafada, zara'u suna zuwa office din tafida bafade yabude mata tashiga abinka ga jinin sarauta akishingide ta sameshi yana jiran zuwanta tana shiga yayi gyaran murya take fadawan sukayi waje suka ja musu kofa. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [6:39PM, 11/17/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 3⃣6⃣ Na UMMI A'ISHA Fadawansa na fita ya kalli zara'u yana daga kishingide yace hv a seat zarah, babu musu ta zauna akan kujerar dake nesa dashi, kallonta yayi ina hanfa take? Hanfa tatafi gida, a ina gidan yake? Ya tambayeta, acan disina gidansu yake, dagaske ne ita kurma ce? Daga Kai zara'u tayi tace dagaske kurma ce sannan kuma bebiyace, murmushi yayi wanda yasake bayyanar da zahirin kyansa afili to yanzu ki taimaka min kibani address dinta zanje gidansu na sameta amma kuma naji tace min wai ita matar aurece hakane? Girgiza kai Zara'u tayi wlh bani da masaniyar hakan amma nima tabbas ta taba fada min cewar ita matar aurece amma ban yarda ba gaskiya, murmushi yayi hakane metake karanta a makarantar? Lab science take karanta, a school of nursing & midwifery dake cikin garin nan amma asalinsu yan garin disina ne, ok to ke tun wanne lokaci kika santa? Sanina da ita baifi shekara daya ba lokacin da muka shiga makarantar nanne kuma tunda muka fara kawance da ita har yau babu abinda ta taba yi min na bacin rai har gidansu naje itama taxo namu gidan, ok good yanzu ki rubuto min address din ki kawo min nagode amma zan kara nemanki idan bukatar hakan ta taso,daga kai zara'u tayi babu komai tashi tayi zata tafi murmushi tafida yayi nagode zarah amma agaskiya ina son kawarki sosai kuma zan aureta, murmushi zara'u tayi tace Allah ya tabbatar da alheri amin tafada tareda ficewa daga office din. [6:56PM, 11/17/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 3⃣7⃣ Na UMMI A'ISHA Zara'u tana fita tafida yayi kishingide yazama tilas agareshi gobe yaje disina yabinciko gidansu hanfa, tashi yayi yafito daga office dinsa yanufi motarsa nan da nan su sarkin fada suka tattaso suka fara bin bayansu daidai lokacin zara'u tazo tamikawa tafida address din gidansu hanfa ko dubawa bai yiba yasaka takardar acikin aljihunsa ya wuce yana cewa thank u, ita kuwa zara'u tana komawa wurinsu sakina sakina tayi farat tace wai zarah me wannan gayen yake so awurinki ne? Dariya zara'u tayi address din budurwarsa ya nema kuma nabishi, dakyau sakina tafada cikeda bacin rai. Tafida yana zuwa gida yayi dukkan abubuwan da yasaba yi yafita kilisa yau kilisar tasu daga shi sai faisal, suna tafe ahankali akan dawakansu tafida yace abokina gobe zanje disina, me zakayi a disina? Akwai abinda zai kaini, ok to ko gidansu matar taka zakaje? Eh can zanje tafida yafada ahasale, dariya faisal yayi Allah yabaka hakuri abokina abin bana fada bane daga tambaya? Eh daga tambayar tafida yafada yana harararsa kasan Allah tafida? Ka nemi matarka ku sasanta tun wuri, tsaki tafida yayi haba faisal wayace adaura min auren da banine na bukata ba, wlh babu wani sasanci da za ayi ni yanzu ma aure zanyi wanda duniya zata san nayi aure amma wanccan auren ai na mai martaba ne murmushi faisal yayi to kuwa sai Allah ya tambayeka domin nauyin yarinya yana kanka tun daga ciyarwarta da shayarwata ga uwa uba hakkinta na aure tunda ita macece mace kuwa kasan tanada rauni, kuma duk duniyar nan kai kadaine zaka iya yi mata wannan domin babu wanda zai bata sai kai, uwar me zan bata? Tafida ya tambayeshi kafini sanin abinda zaka bata to ai kuwa sai dai ta mutu wlh dan banida lokacinta, dariya faisal yayi yace Allah ya shiryeka abokina, da haka suka juya suka koma gida. [7:18PM, 11/17/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 3⃣8⃣ Na UMMI A'ISHA Suna komawa gida tafida yashiga dakinsu ya zauna yafara bincike acikin laptop dinsa wanda ni kaina ummi A'isha ban san me yake nema ba sai da ya dauki tsawon lokaci sannan yarufe laptop din nasa yanufi masallaci yana dawowa yadora daga inda ya tsaya yaci gaba da bincikensa har faisal yazo ya sameshi yafara yimasa hira amma shi tafida sama sama yake jinsa duk hankalinsa ya tattara akan binciken da yakeyi. Washe gari da misalin karfe 11 nasafe tafida yayi shirinsa tsaf cikin wani tsadadden boyel fari yasa hula yasha turaren fogg ya daura agogon azurfa kirar kamfanin omega yasa farin takalmi cover shoe yafito yayiwa mai martaba da inno sallama cewar yatafi disina duk babu wanda yasan abinda yatafi yi sai faisal amma su mai martaba basu tambayeshi me yatafi yiba kasancewar sun san garinsa ne shine yake mulkar garin, wata jibgegiyar jeep yashiga wadda akalla zata iya daukar mutum goma ita yashiga yazauna agidan baya sarkin fada yashiga gaba yazauna yayinda sarkin mota shikuma yazauna a mazaunin driver yaja suka tafi, tafiya sukayi ba mai nisa dayawa ba suka karasa garin disina, address din da zarah ta basu sarkin fada yarinka bi har suka isa wata unguwa mai suna gangare, anan sarkin fada ya tambayi wani yaro ko inane gidan su hanfa? Wancan mai koren fentin ne yaron ya nuna musu shidai tafida yana zaune abaya kishingide ajikin kujera yana latsa wayar hannunsa, adaidai kofar gidan sarkin mota yayi packing din motar yafito shima sarkin fada fitowar yayi ya isa bakin kofar gidan yafara kwada sallama sai da yayi sau wurin biyar sannan wani yaro yafito, yana amsa sallamar, yaro nanne gidansu hanfa? Eh nanne,tana ciki? Eh tana nan to kaje kace ana sallama da ita, to yaron yafada tareda juyawa cikin gidan da gudu, Jim kadan kuma sai gashi yadawo wai ance inji wa? Kace inji tafida, dagudu yaron ya sake komawa can sai ga wani mutum yafito daga cikin gidan waye yake nemanta? Mutumin yafada cikin fada, daidai lokacin tafida yafito daga cikin mota wazai gani? Sirikinsa yagani mahaifin matar da mai martaba ya aura masa. [7:50PM, 11/17/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 3⃣9⃣ Na UMMI A'ISHA Bata fuska tafida yayi yasauko dakyau ya tsaya yana kallonsa dama shima sirikin nasa kallonsa yake, cikin murtukewar fuska mutumin yace, lfy kuka zo min gida? Cikeda isa tafida ya kalleshi amma baiyi magana ba sarkin mota ne yace barka da safiya dama yallabai ne yazo gurin yarinyar gurinka hanfa, wata harara mutumin yayi musu sai yanzu yasan da ita? Da lokacin da aka daura auren ya nemi inda take balle ace ya ganta, tunda aka daura auren nan bai san cinta ba bai san Shanta ba bai san sutturarta ba uwa uba bai san lafiyarta ya takeba dan haka nidai nayi dana sanin aura maka yata kuma nayi bakin cikin auran yata da kayi domin kai ba mutumin arziki bane bakada wata kama ta mutanen kirki,dan haka ina mai shawartarka da kadauki sahunka a likkafa tun dare baiyi maka ba kabar kofar gidana sannan kuma yazama tilas, dole ka saki yata domin bazan hada zuri'a da mutumin banza ba irinka dama na aura maka yatane dan mutuncin mahaifinka to yanzu nafasa, yana gama fadin haka yakoma cikin gida tareda doko kofar gidan da karfi, sai asannan tafida ya iya motsawa daga mutuwar tsayen da yayi dama hanfa itace matar da mai martaba ya aura masa? Wata zuface ta fara karyo masa kamar an kwara masa ruwa ga kafarsa tayi wani irin nauyi marar misaltuwa, ahankali ya zare gilashin dake idonsa yafara tafiya ahankali tamkar kazar da kwai yafashewa aciki, batare da tsoro ba yatura kyauren kofar ya shiga gidane na talakawa babu yabo babu fallasa komai na cikin gidan irin na talakawa ne,yana shiga ya fara sallama tamkar mai yin rada, zuruf masu gidan suka fito daga daki baban matarsa ne yataso cikin fada, waye yayi maka izinin shigowa cikin gidana? Kai kafita daga idona yanuna shi da yatsa nadade da sanin kai marar kunya ne kuma bakasan mutuncin nagaba da kai ba, kafitar min daga cikin gida tun kafin nayi maka kamun kazar kuku, cikin rawar murya tafida yace baba zan fita amma sai ka bani matata, kar ka kuskura kasake kirana da baba domin baka daukeni uba ba kuma nima duk cikin yayana babu mai wulakanta mutane wanda bai san darajar mutane ba, kayi hakuri baba amma dan Allah kabani matata tafida yafada tamkar zai fashe da kuka, wai wacce matar yake fada? Wata mata ta tambaya cikin fada, wannan akwai marar kirkin yaro, sai yanzu kasan da matar taka, yau auren naka yafi wata 6 ko sau daya baka zo kaganta ba saboda kana gadarar kuna da sarauta? Kai gaka dan gata to mu bamu da sarauta amma Allah shine gatanmu, nuna masa hanya baban hanfa yayi fice min daga cikin gida marar kunyar banza marar kunyar wofi, cikeda rashin karfin jiki tafida yajuya yafita yayinda mahaifin hanfa yabiyoshi yayi masa korar kare, dakyar tafida yashiga mota yacewa su sarkin fada sushiga su koma misau take suka bi umarninsa. [8:28PM, 11/17/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 4⃣0⃣ Na UMMI A'ISHA Gudu sosai sarkin mota yayi amma tafida gani yake kamar ba tafiya sukeyi ba alla alla yake yaga sun isa garin misau, wani jiri yaji yana daukarsa wannan abin al'ajabi da yawa yake, tun farko dayasan wannan kurmar ce matarsa ai da ya amince, to ai sai da mai martaba yabaka hotonta amma kaki gani, shiyasa aka ce komai idan aka bishi a sannu yafi armashi zuciyarsa tafada masa, gefen kansa yaji ya sara kamar wanda zai tsage gida biyu, da sauri yasa hannunsa ya rike, sai yanzu yasan wulakanci bashida rana gashi yanzu yanaji yana gani yataho yabar hanfa batare da yaganta ba, amma da ace alheri yayiwa mahaifinta tun farko da bazai yi masa wannan cin mutuncin ba domin shi ALHERI DANKO NE! Baya faduwa akasa banza ko baka samu alokacin ba to agaba zaka dauki abinka watikil ma harda riba, wayarshi yadauka yafara kiran number faisal bugu biyu faisal yadaga abokina ya? Kana ina faisal? Ni gani a office kaifa kadawo daga disinan ne? A'a nakusa zuwa dai yanzu gamu acikin azare dan Allah kadawo gida nafi son da nazo nataradda kai agida pls abokina, ok dama nima nagama aikin da nakeyi yanzu zan koma gida, Allah yadawo daku lfy amin faisal, tafida yafada yakashe wayar, kansa yadafe yana ji kamar zai bar jikin wuyansa dakyar ya iya mikewa ya kwanta akan kujerar da yake, gudu sarkin mota yakara dan danan sai gasu acikin disina, suna isa gida tafida yatashi yafito anan yabar gilashinsa da wayoyinsa, sai sarkin fada ne ya dauko masa, yana shiga dakinsu yasamu faisal zaune yana waya kusa dashi yazauna faisal yagama wayar ya jiyo gareshi yace abokina kadawo? Kai tafida yadaga yace nadawo sai dai yau nayi dana sanin aikata kuskure da sharri arayuwata faisal hakika nayi kuskuren aikata sharri hakika faisal sharri jakada ne maishi yake dawowa yayinda shikuma ALHERI DANKO NE bazai taba faduwa abanza ba, kallonsa faisal yayi wai meya farune? Cikin damuwa tafida yace faisal yarinyar da nake baka labari ashe itace matar da mai martaba ya aura min sai yanzu da naje gidansu na tabbatar da hakan, dariya faisal yafara har da saukowa kasa daga kan kujera nan ran tafida yakara baci sai hawaye sharr! Cikin sauri faisal ya daina dariyar yace haba abokina be a man mana, ya zaka rinka kuka kamar mace, faisal ina sonta nd i can't do with out her! Hannunsa faisal yarike yace maza tashi muje wurin mai martaba mu rokeshi yabaka matarka, tashi tafida yayi yabi bayan faisal har suka isa fada kuma fadar acike take makil da alama sarki yana ganawa da yayun su tafidan ne, turakin soro shine yayi musu iso wurin mai martaba, a kasalance suka isa cikin fadar nan suka matsa gaban mai martaba suka yi gaisuwa caraf fadawa suka cafke,sarki ya gaisheku samarin alheri, sarki ya amsa gaisuwarku mazajen fama, tafiya dai sannu sannu kwana nesa. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:52AM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 4⃣1⃣ Na UMMI A'ISHA Cikin fargaba faisal yace ranka yadade akwai abinda yake tafe damu, gyaran murya mai martaba yayi nan da nan fadawansa suka fice daga cikin fadar sai iya su chiroma da galadima da sa'i kawai aka bari awurin,cike da jin nauyi faisal yace ranka ya dade dama tafida ne yace yatuba yanzu yagane abinda yayi bai kyauta ba shine muka zo mu nemi afuwarka ayi hakuri abashi matarsa, cikin fada sarki yace kai! Idan ku shashasu ne to ni ba shasha bane, dama wannan ce maganar da ta kawo ku? Maza kutashi kubar wurin nan tun kafin raina ya baci, hakuri faisal yafara bayarwa yayinda shikuma faisal yakasa furta koda kalma daya in banda fararen idanuwansa da suka rine sukayi jajawur, cikeda fushi galadima yace kai! Akace kutashi ku bawa mutane wuri marassa kunyar banza, tashi faisal yayi yaja hannun tafida suka fice daga cikin fada, suka tafi wurin inno, afalo suka tarar da ita tana zaune kuyanginta zagaye da ita, rai abace tafida ya zauna kallonsu tayi ya akayi naganku duk kunyi wani iri, inno bukata ce take tafe damu inji faisal, kuyangunta ne suka tashi suka fita,meya faru? Inno ta tambaye su, inno daga wurin mai martaba muke dan Allah kisa baki adawowa da tafida matarsa ai abinda ya wuce ya riga ya wuce, au dama wannan ce ta kawoku? To maza ku tashi kubar min dakina kuma kar ku kara tunkarata da wannan maganar kunji dai na fada muku marassa kunya kawai, tana gama fadin haka ta mike tashige dakinta nanfa tafida yaji kansa ya sara, jan hannunsa faisal yayi taso muje wurin momcy bai yi musu ba yabi bayansa har fannin momcy, suna shiga lokacin tana kokarin fitowa ganinsu yasa takoma ciki suka bi bayanta, tafida me yafaru? Ta tambayesu faisal ne ya iya yi mata bayanin abinda ya faru nan tafara kwantarwa da tafida hankali, kar kadamu tafida insha Allahu komai zai zo da sauki kaji, kayi hakuri zanje nasamu mai martaba saboda dama yanzun nan wurinsa zanje jakadiya tace min yafito daga fada, kujirani naje nadawo yanzu, tashi tayi tafita zuwa sashen mai martaba. [9:53AM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 4⃣2⃣ Na UMMI A'ISHA Koda momcy taje wurin mai martaba hakuri tafara bashi akan maganar tafida ai kuwa nan mai martaba ya rufeta da fada baji ba gani, cikin fuskar alhini momcy tace to ranka yadade ni kayi min izini gobe sai naje disinan da kaina nataho masa da matarsa, hajiya mabruka muddin kikaje to wlh bada yawuna ba kuma babu hannuna aciki,aure dai ai nine nayi masa ko? To babu ruwanku aciki ku zuba min ido kawai, tashi momcy tayi tana fadin Allah yahuci zuciyar ka ranka yadade amma mai martaba sai fada yake ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba, tashi momcy tayi ta koma sashenta tana shiga tasamu su faisal suna zaman jiranta, cikin damuwa tafara magana, nayi duk iya kokarina amma mai martaba bai saurareni ba asalima cewa yayi idan naje disina to bada yawunsa ba, amma abinda nake so dakai tafida shine kayi hakuri mujira muga nan da gobe ko Allah zai sa ya sauko, kai kawai tafida ya iya dagawa yamike faisal yabishi suka fita, suna zuwa dakinsu tafida ya zube akan gadonsu yafara fitar da numfashi mai zafin gaske shikuma faisal ya zauna yafara bashi baki, wunin ranar nan tafida yayi shine kawai amma acikin bacin rai yake shi kansa a matsayinshi na likita yasan bp dinsa yahau sosai ba kadan ba dan yaji alamun hakan ajikinsa, gashi ko ruwa bai sha ba bare yaci abinci har dare yayi. Wurin misalin karfe 10 nadare tafida ya kalli faisal yace abokina dan Allah kayi min wani taimako, ina jinka fadi injishi, so nake gobe katafi disina gidansu hanfa kasamu mahaifinta kuyi magana ta fahinta kaji ko ahaka aka haifeta da lalurar kurmanci da bebanci, idan ba haka aka haifeta ka dauketa ka kaita asibitin tafawa balewa teaching hospital akwai likitan kurame acan kuma insha Allahu akwai taimakon da zai bata, cikeda tausayawa faisal yace dama kurma ce? Kai yadaga wlh faisal kurma ce kuma bebiya bataji kuma bata magana amma tahadu fiyeda yadda baka zato gata da hazaka domin ahakan take karantar nursing, girgiza kai faisal yayi Allah sarki Allah yabata lfy ya daidaita tsakaninku, amin faisal sa'ar danayi ma da ban saketa ba tun da farko da matsalar da zan shiga sai tafi haka, kayi hakuri dai tafida ka kwantar da hankalinka tunda kasan illar saka damuwa acikin zuciya daga kai tafida yayi yashiga duniyar tunani har faisal yayi bacci amma shi faisal yadda yaga rana haka yaga dare ga wani azababben ciwo da kansa yake yi masa dakyar yatashi ya dauko brief case dinsa ya bude yadauki abin auna jini yafara auna jininsa nan yaga yahau fiyeda zatonsa ahankali ya mayar yakoma ya kwanta, alla alla yake gari ya waye dan faisal ya tafi disina. [9:54AM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 4⃣3⃣ Na UMMI A'ISHA Wayewar garin ranar faisal yashirya ya tafi disina alokacin tafida ko tashi zaune baya iya yi, lokacin da faisal yaje gidansu hanfa tarbar arziki mahaifanta sukayi masa, bayan sun gaisa yace baba dama zuwa nayi naji ko dama hanfa haka aka haifeta da wannan lalurar? Cikeda alhini mahaifinta yace wlh faisal da bakinta da kunnenta muka haifeta har ta girma ta xama budurwa, haduwarta da lalurar shekaru uku baya ne da suka wuce tayi wata rashin lafiya mai tsanani tun daga lokacin tadaina magana tadaina ji, amma da lafiyarta lau yakarashe maganar yana kwalla, ayya Allah ya rufa asiri faisal yafada yanzu tana ina? Tana ciki, dama ina sone zan kaita asibiti likita zai dubata, cikeda farin ciki mahaifinta yace Allah saka da alkhair madallah madalla nagode, tashi yayi ya shiga ciki bai jima ba sai gasu sun fito tare da ita kallonta faisal yayi agaskiya kyakkyawa ce sosai shiyasa tafida ya rikice da hannu suka gaisa ya bude mata mota tashiga yayiwa mahaifinta sallama suka tafi, suna zuwa asibitin faisal yafita yaje yabude mata polder aka nuna masa inda zai ga likita sannan yakoma yataho da hanfa suna zuwa tabi layi tazauna wurin ganin likita basu fi su biyar ba, tana nan zaune har layi yazo kanta suka shiga tare faisal, likitan da zai dubata bature ne nan yafara bincikarta yana wasu yan rubuce rubuce, tare da dauko wani zungureren almakashi yadauki audugu yatura a kunnen yafito dashi nan yacewa faisal gado zasu bata, za ayi mata aiki zasu biya kudi dubu dari bakwai da hamsin tashi faisal yayi yafita yaje banki ya ciro kudin yazo ya biya jifa jifa tafida yana kiranshi awaya yana tambayarshi halin da ake ciki, bayan ya gama biyan kudin ne yatafi gidansu hanfa ya sanar musu abinda zai gudana nan da nan mahaifiyarta tahada kaya suka nufi asibiti sai da faisal yagama yi musu komai sannan yayi sallama dasu yakoma misau sai yamma lis ya isa gida yana zuwa yasamu tafida kwance adakinsu ga ledar ruwa nan ana kara masa ashe duk wannan wayar da yake yimasa karfin hali kawai yakeyi shima yana kwance, sannu tafida yau likita ne dakansa ake kara masa ruwa? Murmushi tafida yayi faisal ya kukayi da hanfa? Cikin fara'a faisal yace an bata gado aiki zasuyi mata nan da kwana 3 fatan dai Allah yasa adace amin faisal nagode Allah yabar zumunci, haba tafida duk abinda nayi maka ai kaina nayiwa Allah yabaku lafiya, tashi yayi yafita saboda tsabar tausayin dan uwansa da ya shigeshi. [9:54AM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 4⃣4⃣ Na UMMI A'ISHA Acikin kwanakin kullum sai faisal yaje garin disina yayinda shikuma tafida yana nan akwance yana jinya jininsa ne yahau over gashi tunda yake bai taba yin hawan jini ba sai a wannan lokacin, ranar da za ayiwa hanfa aikin aranar faisal yatafi da sassafe dama duk abinda suke bukata shi yake kai musu, yana zuwa asibitin ya samu za ashiga da ita dakin da za ayi mata aikin ga iyayenta agefe ko wannensu zuciyoyinsu babu dadi haka shima faisal yatsaya suna nan tsaye har tsawon awa 2 sannan aka fito da ita kai daga ganinta kasan tawahala mutuka wani daki aka zarce da ita amma da alama ba ayi nasara ba, sai bakar wuya da tasha domin sai da aka fara yimata fanfo sannan aka yimata wankin kunne kai wuya dai kala kala tashata amma bata samu lafiya ba domin sauki daga Allah yake nan mamanta tafashe da kuka shi kansa faisal ji yake kamar yayi kukan domin bai san halinda tafida zai shiga ba idan yaji cewa bata warke ba, tashi yayi yashiga office din likitan dan neman karin bayani anan likitan yake sanar dashi cewa sunyi iya bakin kokarinsu amma ba adace ba kuma amma kunnenta lafiya lau yake dan haka agobe ma zasu iya tafiya gida godiya faisal yayi masa yafito yazo yasamu iyayenta yayi musu bayanin abinda likita yace, babu komai Allah yasa haka shine yafi alheri mahaifin hanfa yafada alokacin faisal yayi musu sallama yakama hanyar misau yana zuwa ya tarar da tafida yana jiransa nan ya zauna yafada masa dukkan abinda ya wakana, cikin damuwa tafida yace babu komai ni dama ita nakeso ba wani abu nata ba amma yanzu abinda nakeso dakai faisal dan Allah kaciri kudi gobe kaje kasiya musu gida mai kyau ka zuba musu furnitures kasiya musu kayan abinci domin babu amfanin ni ina zaune awuri mai kyau ina cin mai kyau amma matata tana cikin kuncin rayuwa kai faisal yadaga hakane Allah yakaimu goben. Acikin kankanin lokaci faisal yaje garin disina yasiyawa su hanfa hadadden gida mai kyau wanda yadace da zamani yazuba musu furnitures dama unguwar ba unguwace mai hayaniya ba babu bata lokaci suka koma gidan nan iyayenta da ita kanta suka shiga yiwa faisal addu'a domin duk atunanisu shine yake yi musu wannan hidimar, lokacin da faisal yadawo gida ya sanar da tafida ba karamin dadi yajiba anan yake sanar da faisal cewa an hadashi da wani malamin addini wanda yake taimakawa mutane dan haka zaije ya duba hanfa ko Allah zai sa adace, hakan kuwa akayi faisal yaje yadauki malami suka tafi gidansu hanfa, suna zuwa malamin yace taje tadauro alwala sannan ya bukaci da abashi ruwan zamzam original ba jabun ba nan faisal yatashi yaje wani Islamic chemist anan cikin garin ya siyo yakawo, ruwan zamzam din malamin yajuye acikin wani koko yafara addu'a yana watsawa akan fuskar hanfa take tafadi akasa, cigaba da watsawar yayi yanayi yana addu'a har aka kwashe tsawon lokuta alokacin yafara yiwa su faisal bayanin cewa hakika hanfa tana fama da matsala ta jinnu kuma kurame ne gashi sunfi wahalar sha'ani amma aci gaba da addu'a, nan faisal ya zauna agarin bai tafi misau ba sai dai suna yin waya da tafida. Kwana uku malamin nan yayi yana yiwa hanfa magani amma shiru sai akwana na hudune Allah yabada nasara jinnun sukayi magana amma da hannu suke nuni da haka malamin yace sufita daga jikinta amma da yake masu taurin kaine sai da suka sha wahala sannan suka fita. [9:56AM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 4⃣5⃣ Na UMMI A'ISHA Sai da malamin yaja musu kunnen cewa su sakar mata kunnenta da bakinta kafin su fita, suna fita tayi wata irin atishawa mai karfin gaske, Allahu akhbar hakika sauki da rashinsa daga Allah suke tuni tafara wani bacci mai nauyi, malamin ne yajiyo gasu faisal yace wato abinda yafaru shine ruwan zafi ita wannan baiwar Allah ta zuba musu to shine suka shiga jikinta amma insha Allahu yanzu tasamu waraka farin cikine ya mamaye zukatansu asannan mamanta tayi magana tace dama lokacin taliya tadafa tana tacewa tashekar da ruwan shikenan tun daga lokacin tafara jinya, girgiza kai malamin yayi shiyasa ba aso azubar da ruwan zafi akasa dan haka sai akiyaye nan suka zazzauna suna jiran farkawarta sai da ta dade tana bacci sannan ta farka bakinta dauke da addu'a nan fa ta kalli mamanta tace mama! Wato masu karatu ni ummi Aisha sauran kadan nasaki wayata tafadi taci screen saboda tsananin zakin muryar hanfa danaji wata irin zazzakar murya ce da ita shi kansa faisal ji yayi kamar wata balarabiya balarabiya tazama maida kallonta tayi ga faisal tace nagode Allah yasaka da alheri tana gama fadin haka tatashi hawaye suna bin kumatunta tashiga daki tayi alwala tafara salla domin nuna godiyar ta ga Allah yayinda shi kuma faisal yadauki malam suka koma misau suna zuwa yafara yiwa tafida albishir ai tafida bai san lokacin da yadiro daga kan gado ba yazo ya rungume faisal tuni yaji jikinshi yaware nan yafara tambayar faisal nawa za abawa malam? Yace duk abinda yasamu domin shi bai yanke ba, ok to zan bashi dubu dari biyar da mota daya da gida guda daya take shima tafida yafada bathroom yadauro alwala yazo yafara nuna godiyarsa ga Allah. Bayan hanfa ta warware ne tafara shirin komawa makaranta nanfa tafida yayi siyayya mai tarin yawa yabawa faisal ya kaimata duk abinda yasan zata bukata sai da yasai mata kayan kwalliya da kayan abinci da drinks kala kala hatta pad sai da ya siya mata ga turarruka masu tsada nan iyayenta da ita suka shiga godiya bayan tafiyar faisal mahaifinta yake ta yabon faisal sannan yabata labarin cin mutuncin da dan uwan faisal din yayi masa wato mijinta tafida tun daga nan taji ta tsani tafidan tun kafin ta ganshi. Ranar Monday ta shirya tadawo makaranta nanfa yan makaranta suka shiga mamaki jin hanfa bebiya tawarke yayinda wasu kuma suke cewa ai babu mamaki da sha'anin Allah, ranar data dawo makaranta ranar tafida yafara zuwa office bai dawo ba sai 5 tunda yadawo yaci abinci yayi wanka yafita shida babban zaginsa da sarkin mota yana daga baya azaune yace musu school of nursing zasuje haka kuwa minti kadan sai gasu acikin makarantar suna shiga suka fara tafiya ahankali har sukaje gaban wani hall inda dalibai ke tsattsaye group group da alama daga lecture suka fito nanfa daliban suka fara bin motar tafida da kallo wata babbar jeep ce kirar kamfanin crotoure baka mai bakin gilasai an rubuta tafida 4 ajiki, ba aganin wanda yake ciki, ido tafida yafara budewa yana kallon daliban can ya hangota da uniform ajikinta da dan karamin hijabi iya kafadarta tayi wani kyau sosai tana tsaye cikin maza sunfi biyar da modern biology a hannunta da alama bayani take musu nanfa yaji ransa ya sosu, babban zaginsa ya cewa yaje yakira masa ita koda yaje hanfa bata kulashiba sai ma gurmuda baki da tayi duk abinda tayi akan idon tafida yana kallonta ta glass din motar dan haka koda babban zagi yadawo bai jira bayaninsa ba yabude motar yafita nanfa kallo yakoma kansa yatsuke cikin bakar riga mai gajeren hannu ajikin rigar an rubuta big guy da jan fenti yasa jan trouser da jan takalmi irin nasu na sarauta hatta belt din da yadaura ja ce yadora bakar jacket asama ahankali yafara tafiya yana zuwa yajiyo da ita yaja hannunta nanfa tafara turjewa ganin haka yasa tafida fizgota jikinsa ya rungumeta nan fa su babban zagi da sarkin mota suka fito da gudu suka zo inda suke suka baza babbar rigarsu sukayi musu runfa suka lullubesu ahankali tafida yadago kanta yasa bakinsa akan nata yafara zagaye lips dinta da harshensa,tofa muje zuwa dai masu karatu. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [5:39PM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 4⃣6⃣ Na UMMI A'ISHA Cikin sauri hanfa ta bude idanuwanta ta fara kallon fuskarsa bakinsa kan nata gashi ya wani kankameta duk kamshin turarensa na fogg ya cika hancinta ras! Taji gabanta ya fadi, jan hannunta yayi yakaita cikin mota yabude gidan baya yasata shima yashiga sukuma su babban zagi suka zauna daga waje, yayinda dalibai suka yi cirko cirko suna tattauna wannan lamari da ya afku wasu kuma ba karamin burgesu tafida yayi ba, suna shiga cikin mota hanfa tafara matsawa yana binta, tana matsawa yana matsowa har taje jikin kofa daidai lokacin ya karasa matsowa kusa da ita kallon fuskarsa tayi yawani rankwafo jikinta, jikinsa yana gogar nata hatta numfashinsa akan fuskarta yake sauka, tunani tafara yi, yana yi mata kama da faisal sosai sai dai yafi faisal kyau, komai nashi ya tsaru sai kace shi yayi kansa dan kyau, to kodai shine tafidan? Duk yadda akayi wannan shine tafida mijina sannan kuma still dr din da ya dubani a asibiti tafada acikin ranta, hakika taji dadin kasancewarsa a matsajin mijinta amma kuma sai ta wanashi ta nuna masa kuskurensa na ciwa mahaifinta mutunci da yayi domin tana son ta nuna masa cewa iyayenta suna da martaba da kima a idonta, iska ya hura mata akan fuskarta take tajiyo wani kamshin strawberry me hade da splash ya fito daga bakinsa, ahankali kamar meyin rada yace kin gama gudun? Kallonsa tayi tadauke kanta tafara kiciniyar bude kofar motar amma bataga wurin budewar ba saboda tsananin tsaruwar da motar tayi, hannunsa mai mutukar laushi yasa yajiyo da fuskarta madam! Kijiyo kiji abinda zan fada miki, ko bakya ji? Well dama ni basai naji muryarki ba tunda nasan kina jina shikenan, nayi mutukar farin cikin kasancewarki mata ta hakanne ma yasa nayi alqawarin kyautata miki domin na nuna godiyata ga mahaifinki akan aura min ke da yayi, wannan dalilin ne yasa nima na himmantu har sai da kika samu lafiya tareda taimakon dan uwana, abokina, aminina faisal, wanda banida kamarsa aduniya, dam taji dama shine yasa faisal ya yimata dukkan abinda yayi mata? Shiru tayi tana sauraren taushashshiyar muryarsa tun da take bata taba jin muryar namiji mai dadi kamar tasa ba. ALHERI DANKO NE! 4⃣7⃣ Na UMMI A'ISHA Mahaifinki yayi min alheri mai yawan gaske shiyasa nima na daura aniyar yi masa alheri ta hanyar sama miki lafiya domin shi ALHERI DANKO NE sai alokacin ta kalli fuskarsa idonsa tarr akan fuskarta, yatsina fuska tayi takawar da kanta, meyasa kika shiga cikin maza kika tsaya? Ko baki san ina kishinki ba? Shiru tayi bata bashi amsaba amma tajiyo takalleshi daidai lokacin da yake lasar lebenshi wanda ya kasance ja kamar ya shafa jan baki mai duhu, juya kanta tayi ta kalli window ahankali taji yakama hannunta yatsun hannunta ya zubawa ido fatarta bakace amma ga gashi nan kwance sai kace jikin namiji, kallon hannun nata yayi yai murmushi ai bakar mace tayi arayuwa dama shi can bakar mace yakeda ra'ayin aura, dayan hannun nasa yasa yafara shafa gashin hannunta, wani irin shock tafara ji amma sai ta maze, ahankali yace haka kike da gashin nan duk jikinki ko iya hannun ne? Sai alokacin tayi masa magana dubawa zakayi sai kaga, wani darr yaji acikin kunnensa saboda jin sautin muryarta. [6:13PM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 4⃣8⃣ Na UMMI A'ISHA Kamar wani sakali haka tafida ya zuba mata ido yana kallonta ashe tasan muryar ta tahadu shiyasa tatsaya ja masa aji sai da tagama yangarta sannan tayi masa magana, wani sanyin dadi yaji acikin ransa hakika hanfa tana daya daga cikin matan da Allah ya horewa baiwar murya zazzaka, kallonta yayi ya lumshe manyan idonsa ya budesu akan fuskarta, kafar wandonta yakama yadago kafarta yadan janye shi sama nan yaga gashi kwance mamakine yakama hanfa shi wannan be san gatse ba, dan tace yaduba yagani shine zai duba din, hannunsa yasa yashafa kwaurinta nanma akwai gashin har cinyarki? Shiru tayi hannunsa yadauke daga kwaurinta ya ajiye kafar tata akasa yafara kokarin saka hannunsa acikin rigarta nanfa tayi caraf tarike hannunsa me zakayi? Cikinki zan duba naga ko nanma akwai gashin, to babu tafada tana buntsira baki, ni kika buntsirawa baki? Kefa kika ce dubawa zanyi sai nagani kuma ya zan duba zaki hanani? Bata bashi amsaba, kin san me nakeso dake daga yau kar nasake ganinki acikin maza kin gane? Buntsira baki tasake yi, yana ganin haka yakai bakinsa kan nata yahada yatsoti lebenta. ALHERI DANKO NE! 4⃣9⃣ Na UMMI A'ISHA Bakinta ta kwace ta tofar da yawu tasaka bayan hannunta tafara goge bakinta wannan wanne irin kazanta ne haka? Tafada tana hararsa aranta kuma tana cewa wato kai ga mai mata ko shine harda wani biyoni school, kallonta ya danyi kyankyami na kike yi? Wannan abin ne kazanta? Zakiga kazanta kuwa wannan ba kazanta kika gani ba, yana gama fadin haka yajanyota jikinsa ya fara kokarin saka bakinsa cikin nata amma taki ta damke bakinta yanda bakinsa bazai shiga nataba, murmushi yayi wlhi ko ki bude bakinki ko kuma nayi maganinki yanzu, hannunshi yazira cikin rigarta ta baya bashiri ta yi magana, meye haka? Dan mitsitsin bakinta yakalla ga fararen hakoranta siri siri ajere gata da yar wishirya nan da nan yaji yawunsa ya tsinke, bakinsa yahada da nata yakama harshenta yarike yafara dura mata yawun bakinsa mutsu mutsu tafarayi tana tuttureshi amma yaki cikata, haka tarinka shanye yawunsa yana dura mata wani sannan yafara lasar harshen bakinta yana tandar lips dinta sai da yashafe samada minti 20 sannan yasaki bakinta, hannunta tasa akan bakinta tana tofar da yawu tuf tuf, dariya tafida yayi wadda har saida beautiful point dinsa yafito fararen hakoransa suka bayyana, yarinya zancen yaushe kuma ai kin riga da kinsha yawu na sai dai kiyi hakuri ki kiyayi gaba amma yanzu kan kin ga kazanta iya kazanta ko? Harararsa tayi mugu kawai, ni kike cewa mugu? Zakiga muganta yarinya. [8:30PM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 5⃣0⃣ Na A'ISHA (ummi) Baki hanfa ta murguda kawai saboda tsabar kazanta zaka wani bani yawunka nasha, wannan ai kazanta ne, wani malalacin murmushi tafida yayi mata ai dan kinsha yawuna ba wani abu bane tunda zan zuba miki abinda yafishi ajikinki, wa? Allah ya kiyaye tafada tana harararsa tareda fara idonta wai nanfa ta kara saka tafida a wani yanayi, hannunta ya kama shidai hannunta yana burgeshi gashi da tsananin taushi kamar auduga ga laushi da tsantsi, farcenta yafara murzawa sannan yakai hannun bakinshi yayi kissing dinsa yasa dan yatsanta abakinshi ya fara lasar farcenta yana tsotsar dan yatsan, cike da mamaki ta kalleshi hannun hagun ne fa, to meye? Kece kike kyankyamina ni bana kyankya minki kanta takawar daka kallonsa, sai alokacin idonsa yakai kan agogon hannunsa dake daure akan tsintsiyar hannunsa karfe 6:20 har anfara kiraye kirayen sallar magrib sannan yawancin daliban dake harabar area classes din sun tattafi hostel sai daidaiku, dan yatsanta yadan ciza duk da taji zafi amma bata nuna masa ba, cire yatsan nata yayi daga bakinsa yace kije kitafi hostel amma ga zarah can nahango ta ki turo min ita, shiru tayi aranta tana cewa gaskiya kam kai dan sarauta ne ace magana tarinka yiwa mutum wahala kanata yimin magana kamar me yin rada kana magana dakyar,ni ummi A'isha nace dan hanfa bata san tafida bane amma ahakanma ita dakarfi yake yi mata magana, wani abu ya taba take kofar motar tabude, hannunta ya saki ba dan yasoba yace kitafi sai dasafe amma gobema zan dawo, bata bashi amsa ba tafice tanufi inda su zahara'u sulaiman suke tsattsaye tana zuwa tace zarah kije yana kiranki, dasauri xarah tatafi inda yake, tana zuwa yasauke glass din motar tafara gaisheshi, cikin sakin fuska ya amsa yace zarah ga amanata nan nabaki ki kular min da ita fiyeda yadda zaki kula dakanki, compliment card dinsa yamika mata ga wannan akwai phone number dina ajiki idan da wani abu sai ki kirani domin ita bazan bata phone yanzu ba. hausa novel blog ‹ › Home View web version Thursday, 22 December 2016 aisha ummi at 01:26 ALHERI DANK'O NE 51-END [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [8:20PM, 11/20/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 5⃣1⃣ Na UMMI A'ISHA Murmushi zarah tayi insha Allahu zaka sameni mai tsananin rikon amana, yawwa zarah nagode ai tafada miki nine mijinta ko? Murmushi zarah tasake yi wlh tafada min kuma nayi murna sosai Allah yabar kauna, amin zarah nagode juyawa zarah tayi tatafi sukuma su babban zagi sukazo suka shiga motar sarkin mota yaja suka tafi. Zara'u tana zuwa inda su hanfa take tasamesu tsaye hanfa tana yi musu bayanin wani zanen skeleton dake zane ajikin littafi nan zarah tajirata tagama domin hanfa akwai brain kusan tafi kowa ja a yan lab science, kuma wani abin burgewar mahaddaciyar alqur'ani ce dan da ka take dori batare da ta buda alqur'anin ba wow inama ummi aisha ce, tana gama yi musu bayanin suka tafi hostel itada zarah, cikeda zolaya zarah tace hanfa mijin nan naki dan love ne dan naga ko kunyar dalibai baiji ba yawani rungumeki, dan karamin tsaki hanfa tayi ai kibari kawai zarah namiji bai san kunya ba yanzu dan Allah in banda rashin kunya meye nashi na hugging dina agaban mutane? Ai kuwa kinyi sa'ar miji dan ni ina son namijin da ya iya soyayya, um hanfa tafada aranta kuma tana cewa idan wannan ne ai har ya isheki ma dahaka suka karasa hostel suka shiga room 2 kasancewar nanne dakinsu kuma komai nasu ahade yake su 2. ALHERI DANKO NE❗ 5⃣2⃣ Na UMMI A'ISHA Shikuwa tafida tsintar kansa yayi cikin farin ciki marar misaltuwa gaba daya hanfa yau tagama tafiya da imaninsa ko yaya ya lumshe idonsa ita yake gani da wannan tunanin suka je gida abakin gate suka hadu da mutuminsa faisal kowannensu ya fito daga cikin mota, suka bawa juna hannu dai dai lokacin suka shiga cikin gida anan suka hango mai martaba yafito daga gida yashiga masallaci dariya faisal yayi abokina yakamata fa mu koma wurin mai martaba musake bashi hakuri ko Allah zai sa ya hakura abaka matarka, dariya tafida yayi wlh babu inda zan sake zuwa badai matata ce ba ai ni hakan yayi daidai tunda gashi sun turota makaranta sun manta da batun aurena akanta to wlhi nima sha'anina kawai zansha tunda ai ba haramun bane nida za tasamu cikima dasai nafi jin farin ciki, duk wadannan maganganun acikin zuciyarsa yayisu afili kuma yacewa faisal kai rabu dasu yanzu idan sun kawo min itama banida abinda zan bata, kaji tsoron Allah faisal yafada yana dariya wlh kanada abinda zaka bawa mata huduma ba daya ba, dariya tafida yayi an fada maka ni wahalallene irinka? Banida lokacin mace yanzu malam, karya kake wlh irinku masu shiru shirun nan kunfi jaraba, dariya tafida yayi yadauki buta yafara alwala yana cewa kanka akeji, shima faisal butar yadauka yafara alwalar yana fadin kanmu akeji dai. [8:46PM, 11/20/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 5⃣3⃣ Na UMMI A'ISHA Masallaci suka shiga sukayi salla suka fito tun acikin masallacin suka tsaya suka debi gaisuwa wurin mai martaba sannan suka wuce cikin gida suna shiga dakinsu tafida ya fada kan kujera ya lumshe idanuwansa ya budesu agaskiya babu abinda yafi soyayya dadi ya ayyana hakan acikin ransa, faisal ne yakatse masa tunaninsa ta hanyar cewa abokina ina matar taka ne? Yanzu tunda kagane itace wacce kakeso ai sai kaje kanemo hanyar, murmushi tafida yayi yace kaifa dan iska ne, kasan abinda nadade ina son na tambayeka? Jijjiga kai faisal yayi sai kafada, wai faisal ya akayi naga gidansu hanfa yakoma wani wuri alhali da ba acan nasansu ba? Cikin fuskar tausayi faisal yace wlh korarsu mai gidan yayi shine suka tashi suka bar unguwar, girgiza kai tafida yayi batare da yace komai daidai lokacin wayarshi tayi ringing, yazaro ta daga aljihunsa yakara a kunnensa yayi shiru domin shi aka'idarsa idan yadau waya baya magana sai dai yayi shiru, muryar zarah sulaiman yaji tana cewa hello ranka ya dade yagida,murmushi yayi lfy zarah ina amanata? Gata tana jinka,ok bani ita zanyi magana da ita, mikawa hanfa wayar zarah tayi tareda tashi tafita daga cikin dakin. ALHERI DANKO NE❗ 5⃣4⃣ Na A'ISHA (ummi) Karbar wayar hanfa tayi takara ajikin kunnenta tayi shiru, murmushi tafida yayi wadda har sai da tajiyo shi acikin kunnenta tafida badai dadin murya ba tafada acikin zuciyarta, hello madam kina jina? Yafada ahankali tamkar me yin rada dan hatta faisal dake zaune acikin falon baya jin abinda yake fada asalima bai san da wa yake wayar ba, madam yasake fada ahankali ko muryar ma sai nasiya? Babu mamaki tafada ahankali itama wannan jan aji har ina inji ummi aisha, ok to kin san ai zan iya siyar duk abinda zaki sayar min, nawa ne hajar taki? Bata sayarwa bace, kagama ni karatu nake son nayi, gobe inada txt din chemistry kuma banyi karatu ba, karfe nawa zaki shiga txt din? Sai lokacin da malamin yazo kawai, ok tom zan barki kiyi karatu amma dole gobe sai nazo ganinki, Allah yakaimu tafada tana yatsina fuska kamar yana ganinta, to sai nazo madam yafada tareda kashe wayar ba dan yaso ba, murmushi yayi shi kadai ai da bai samu hanfa ba Allah ne kadai yasan halin da zai shiga, wayar ya kashe suka cigaba da hira shida faisal amma kowanne lokaci fuskarsa dauke take da murmushi saboda yawan tuno hanfa da yakeyi. [9:16PM, 11/20/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 5⃣5⃣ Na UMMI A'ISHA Daren ranar tafida kwanan farin ciki yayi washe gari yagudanar da dukkan abubuwan da yasaba yafita office amma yakira zarah yafi sau goma yana tambayarta ina matarsa, tun abin yana bawa zarah mamaki har yadawo bata dariya. Bai tashi daga office ba sai around 5 yatafi gida yayi wanka yaci abinci yashirya yafito dogarawansa suka take masa baya yace su kaishi school of nursing tun ahanya yakira zarah tana dauka yace zarah ina matata? Dariya zarah tayi tace tana area class nikuma ina hostel, ok to zan ganta acan yafada tareda kashe wayar cikin sa'a suna shiga sai ya hangota tana fitowa daga cikin hall hannunta rikeda question paper da alama daga txt din ta fito, sarkin fada ya tura ya kirawota tana tsaye dayake ita ce tafara fitowa sarkin fada yazo yafara yimata kirari barka da fitowa gimbiya, gaisuwa nake sannan kuma mai girma tafida yana kiranki dafatan zaki iso lfy yana gama fadin haka yajuya yatafi, juyawa tayi tahango motar tasa batajiya bace domin ta yau Prado ce ja amma kuma mai bakin gilasai ce, sanin zai iya biyota yayi mata irin ta jiya yasata nufar inda motar take tunda tafara tahowa tafida yafara kallonta tana sanye da wata atamfa ja anyi doguwar riga mai hannun shimi ansha rigar daga kirji daga kasa kuma tabaje tasaka bakar riga aciki mai dogon hannu sai rigar tabada style kamar english wear tayafa jan karamin mayafi akanta, tana zuwa sarkin fada ya bude mata kofar baya ta shiga yamayar kofar ya rufe suka koma gefe, tana zama tadauke kantakusa da ita yauma ya matso yafara kallon fuskarta, har tsawon minti 5 sannan yace babu gaisuwa? Ina matsayin mijinki amma bazaki gaisheni ba? Kallonsa tayi yana sanye cikin shudiyar t shirt da dark blue din jeans sai faman kamshi yakeyi, question paper hannunta yakarba yafara dubawa sannan ya wurgata baya, kallonshi tayi amma batayi magana, hannunsa taji yadora akasan kirjinta wannan kayan bai dace kisa su ba jifa yadda breasts dinki ya bayyana, banza tayi dashi ganin haka yasashi fara zana dan yatsanshi akan kirjin nata kalli nan yadda yafito, kalli shatin bra dinki sai alokacin ta ture hannunsa to meye ruwanka? Da ruwana akan me zaki rinka saka kaya irin wannan? Hannunsa yasa akan botir din da akayi wa rigar amaimakon zip yaja botir din yafincike shi, wai ya haka? Tafada cikeda gatsali ok yauma rashin kunyar zakiyi min? Hannunta yaja yarungumo ta jikinsa yafara shafata sai alokacin idonsa yagano masa gashin kanta mai tarin yawa nanfa yarude ya nemi nutsuwarsa ya rasa shi bai ma san ta inda zai fara ba, bakinta ya laluba yasaka cikin nashi yafara tsotsa duk yagama rudewa, wata yar na'ura yadanna abin mamaki sai kawai kujerar tabaje tazama kamar katifa, ahankali yafara fitar da numfashi, kirjinta yafara shafa wanda sukayi mutukar gigita shi, nan yafara fita daga hayyacinsa. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:59PM, 11/20/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 5⃣6⃣ Na UMMI A'ISHA Shinfidar da ita tafida yayi akan bajajjiyar kujerar yafara bata kiss ta kowanne sashe na jikinta tareda lasar lips dinta, hancinsa ya goga akan nata yadora hannunsa akan kirjinta yafara fincike botiran gabar rigar tata ai hanfa najin haka jikinta yafara rawa, acikin kunnenta yarada mata whats wrong? Idonta cikeda kwalla tace kabari pls, murmushi yayi ya lumshe idonsa dama duk wannan tsiwar taki ke matsoraciya ce? Kinga kuwa bazan bari ba sai nayi abinda nayi niyya, duk da cewa a tsorace take dashi amma sai ta fuske ta murguda masa baki tace kar Allah yasa kayi hakurin ai nasan duk abinka dai ba mutuwa zanyi ba, bakinta ya cafka yafara tsotsar harshenta yana shafar wuyanta har ya gangaro kan na fulaninta baiyi wata wata ba yazame hannun rigarta yafara kokarin tura hannunsa cikin kirjinta amma kuma sai rigarta da bra suka yimasa cikas, gashin kanta ya fara shinshina wanda yake ta faman kamshi mai dadi ahankali yafara lasar wuyanta kamar wani sabon maye sai da yagama jigata ta sannan yahakura yakama hannunta ya matse cikin nashi ya lashi lebenta muje kirakani unguwa mudawo. ALHERI DANKO NE❗ 5⃣7⃣ Na UMMI A'ISHA Gabanta ne yafara faduwa karfa yaje yayi min aika aika yanzu batare da na shirya ba, tafada aranta,zaune yatashi yafara gyara wuyan rigarshi yaja hannunta tashi ki gyara mutafi tashi tayi tanada gyalenta amma kuma duk gaban rigarta abude yake yacire mata botiran gaban rigar, ganin yana kallon kirjinta yasata janyo gyalen tarufe jikinta murmushi yayi acikin zuciyarsa yace zakiyi bayani yarinya, gyara kujerar yayi tadawo yadda take ya zuge glass din setinsa yadagawa su sarkin fada hannu sai gasu aguje sunzo ranka yadade, kushigo mutafi, jikinsu narawa suka shiga motar sarkin mota yaja suka fara tafiya, hannunta tafida yariko tareda matsawa jikinta sosai ahaka suka je kofar fada anan yace sarkin mota yayi packing, yana tsayawa yace ku karasa gida nizanje unguwa firfita sukayi daga motar shi kuma yadubeta madam fito kidawo gaba kin san ni ba driver bane, baki ta buntsira tabude tafito batare data kalleshi ba saboda nauyin hada ido dashi take ga wata kunyarsa dataji ta saukar mata kai gaskiya al'amarin nan akwai kunyafa, fitowa shima yayi yazauna a mazaunin driver yakunna motar yayi ribos yajuya kan motar, suna hawa kan titi yajiyo ya kalleta tadauke kanta takalli titi hannunta yakama yarike yayinda yake driving da dayan hannun, kaga yadda kacire min botiran jikin rigata ko, murmushi yadanyi eh saboda bana son kisake saka rigar ne, yanzu kiga yadda ta takurani ta hanani taba......... [8:53PM, 11/21/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 5⃣8⃣ Na A'ISHA (ummi) Kanta tadauke bata tanka masa ba, kinga wannan rigar bata kamace ki ba madam nahadaki da Allah kar ki kara saka rigar nan kinji? Shiru tayi masa sanin bazata amsa masa ba yasashi matsa dan yatsanta dakarfi wash! Tafada hadeda runtse idonta gaskiya ka iya mugunta,murmushi yayi zakiga mugunta yanzu bakiga komai ba sai ranar da kikaji nauyi na, nanma shiru tayi amma aranta tana cewa dama ai nasan da mugunta zaka yi min wlhi, daidai wani shopping plaza yayi packing yasaki hannunta yace ina zuwa, fita yayi yashiga wani babban boutique ya lodo mata arabian gown kala kala da after dress bakake masu kyau da tsada da turarurruka domin shi yana son kamshi sosai tana nan zaune ya shigo motar da babbar leda ya ajiye abaya yatashi motar,fita suka yi daga shopping plaza yace zakisha ice cream? Girgiza kai tayi nagode, hmmm to tunda bazaki sha ice cream ba nasan abinda kike son sha kuma zan baki ita dai hanfa bakinta gum bata ce masa komai ba har suka shiga school of nursing, lokacin an fara kiraye kirayen sallar magrib. ALHERI DANKO NE❗ 5⃣9⃣ Na UMMI A'ISHA Daidai bakin gate din hostel dinsu yayi packing yajiyo ya kalleta yana murza dan yatsan hannunta, madam ga kaya nan su nayarda kisaka ako da yaushe mutukar ba uniform zaki saka ba, kallonsa tayi fuskarta dauke da alamar tambaya wanne irin kaya? Idan kinje zaki gansu, bana son nasake ganinki da irin wannan rigar da kika saka yau, sannan wannan dan motsitsin hijabin da kike sakawa amaimakon sa na siyo miki wanda yafishi girma kinji? Naji tafada ahankali, hannunsa yasa yadago fuskarta lumshe idanuwanta tayi bata kalleshi ba ahankali yakai bakinsa kan nata yahada yafara tsotsa, abin da yabashi mamaki yau batayi gardama ba amma idonta arufe yake gam ganin haka yasashi niyyar tsokanarta yafara zuba mata yawunshi nanma bata yi masa irin najiya ba haka yakaraci neman maganarshi yagama sai da yaji an shiga masallaci sannan yacikata yace dauki kayanki, sai da safe hannu tasa tadauki ledar tace nagode ta bude kofar motar tafita tsayawa yayi yana kallonta har tashige hostel sannan yatashi motarsa yafita daga cikin makarantar. [9:20PM, 11/21/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 6⃣0⃣ Na UMMI A'ISHA Fita yayi daga cikin makarantar yanufi gida yana tafe yana tunanin abar kaunarsa hanfa. Koda yaje gida ma yana cikeda tunaninta acikin ransa, washe gari mai martaba ya aikesu kano shida faisal inda zasu kaiwa sarkin kano katin gayyatar bikin zumunta wanda aka saba gudanarwa bayan kowacce shekara uku domin yaukaka dangon zumuncin dayake tsakanin sarki da talakawansa. Basu dawo ba sai karfe 6 lokacin agajiye suke lis washe garima suka sake tafiya jihar jigawa inda suka rinka shiga gari gari suna kaiwa katin gayyata domin dama wannan biki da za ayi bikine na al'ada da aka saba gudanarwa sannan kuma jama'a daban daban ne suke halarttarsa, aranar da suka dawo daga jigawa ma bai samu ganinta ba sai dai yana yiwa zarah sulaiman waya yaji lafiyarta,sai da yayi sati 1 bai ganta ba saboda kullum akwai inda zasuje aranar da suka dawo daga darazau ne yace komai dare sai yaje yaganta, wurin 5:30 ya isa makarantar dama shi kadai ne yau bai tafi da fadawan nasa ba, yana shiga a kofar hall din daya saba ganinta ya hangota zaune da wasu maza daga can gaba kuma zarah ce zaune ita da wata, tsaki yayi yafara kiran zarah awaya, daga inda take tadaga hello yallabai,zarah yakike, lfy lau, kituro min matata gani ina kallonku murmushi tayi angama ranka ya dade, tashi zarah tayi taje inda hanfa take tace kije tafida nakiranki, yana ina? Gashi can acikin mota, tashi hanfa tayi ta nufi inda motarsa take gaba tabude tashiga tazauna ta dan kalleshi yana sanye da farar shadda wadda tasha dinkin sarauta kansa babu hula, kallonta shima ya tsaya yi tana sanye da riga da skirt na atamfa da dan madaidaicin farin hijab, wai ke ban hanaki zama acikin maza ba? Shiru tayi ba amsa, wlh idan kikayi wasa bazaki gama karatun nan ba sai da ciki ajikinki tunda gashi nan kayan da nace kirinka sakawa ma bakya sawa saboda kin rainani, kallonsa tayi ciki? Waye zaiyi min ciki? Tunda nasan kai dai baka isa yin ciki ba, oh ashefa akwai maza rampantly a makarantar may be sune zasu yi min ciki, kallonta yatsaya yi batare da yace mata komai ba yakunna motar yatadata yayi ribos yafara kokarin fita daga cikin makarantar. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [8:18PM, 11/23/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 6⃣1⃣ Na UMMI A'ISHA Cikeda mamaki hanfa ta kalleshi yasha kunu kamar bai taba dariya ba,ina zaka kaini? Lecture fa zan shiga ta physics, sai alokacin ya kalleta to yau ko lecture din me zakiyi sai dai ki hakura saboda babbar lecture zakiyi, pls dan Allah kar kasa nayi missing din lecture din nan, hmm kin san Allah? Yau ba zakiyi wannan lecture din ba yau mai rabani dake sai Allah saboda reni zamu je mu raba yau zaki gane shayi ba komai bane face ruwa, yau sai kinsan ni ba sa'anki bane da har zaki dubi idona kice wai ban isa yi miki ciki ba, saboda baki daukeni namiji ba ko? Sannan wai harda cewa a school dinku akwai maza rampantly sai dai idan sune zasu yi miki ciki? Da auren nawa akanki zaki rinka zancen maza zasuyi miki ciki? To kafin suyi miki gara ni nayi miki dan naga alamar kin fara sha'awar maza amma banga laifinki ba dan kinyi kokari shekara 23 ai dole ki nemi namiji akusa dake, nanfa gaban hanfa yafara harbawa ta tsorata ashe haushi yaji dan tafadi wannan maganar? Itafa tafada ne kawai saboda yayi fada domin adan zaman da tayi dashi ta fuskanci bai iya fada ba saboda bashida yawan surutu amma idan itace yana dan kokar tawa yajata da zance sannan kuma tana jin dadin voice dinsa Mai mutukar zaki da taushi. ALHERI DANKO NE❗ 6⃣2⃣ Na UMMI A'ISHA Tunaninta ne ya tsaya lokacin dataga sun isa wani gida wanda babu gidaje da yawa a unguwar, ginin gidan wani bene ne aka dora ba agama ba amma ankai hawa na shida da alama business suit ake ginawa awurin gefe kuma ga gate nan wanda za ashiga cikin gidan, abakin gate din yatsaya yafara horn nan da nan mai gadi yazo yabude gate din, kutsa kan motar yayi suka shiga cikin gidan wanda yake katoton gaske sannan yasha fenti da alama ma ba adade da gama ginin gidan ba, suna shiga yayi packing ydubeta fito madam, kin motsawa tayi, kinga idan baki tashi ba wlh daukarki zanyi,ahankali tabude kofar motar tafito aranta tana karanta ayatul kursiyyu domin neman tsari daga tafida, fitowa yayi yashiga gaba tana biye dashi abaya tana rarraba ido kamar wata marar gaskiya, da haka suka shiga falon gidan wanda yayi mutukar tsaruwa bai tsaya anan ba yashige wani babban daki amma ita sai taki shiga ta zauna afalon Jim kadan sai gashi yafito ok ba zaki shigo bane? Shiru tayi take idonta yaaciko da kwalla dan Allah kayi hakuri kar kayi min haka, murmushi tafida yayi tareda cije lebenshi na kasa, kinga kar ki wahalar da kanki kisa na wahalar dake tashi kawai muje, ai nafada miki yau raba raini zamuyi. [8:25PM, 11/23/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 6⃣3⃣ Na UMMI A'ISHA Nanfa hanfa taji hankalinta yatashi innalillahi kawai take kira acikin zuciyarta, ganin ya nufota yasata saurin mikewa tsayawa yayi to ki shigo salin alin tun kafin nakamaki dan idan kika bari na kamaki sai nayi miki kaca kaca yau, jin haka yasa hanfa ta daure tace ahakan? Ni nafi so ko zakayi min kaca kacan kabari sai ka zama namiji tukunna dan har yanzu da sauranka, murmushi yayi ai shiyasa nake son yau na nuna miki nadade da zama namijin da kike magana, bude baki tayi da niyyar yin magana amma takasa saboda ganinsa da tayi yaxo inda take, baiyi wata wata ba yakamata yafara janta tana turjewa ganin zata bata masa lokaci yasa yadauketa cak akan kafadarsa yayi bedroom din da ita, yana shiga ya ajiyeta akan gado tareda zare hijabin jikinta, kiga dan hijabin dakike sawa bayan nasiyo miki babba amma shine saboda tsabar kin gama rainani bazaki saka ba, rigar jikinta yafara kokarin cirewa, yau zan saita miki zama yadda nan gaba bazaki sake tsallake maganata ba, yana cire rigarta yaga ko bra bata saka ba nanfa yafara matsarsu yana lugwigwita su, kuka hanfa tafara, oh har kin fara kuka tun yanzu? Yarinya zaifi miki kyau da kiyi shiru saboda hawayen zasuyi miki amfani anjima, yafada cikin tausashashiyar murya, wasa yaci gaba dayi baji ba gani da dukiyar fulaninta wanda take jin kamar cire mata kansu zai yi dan azaba, wata kwalla ce tazubo a idonta mai zafi wai tun daga nan kenan tun ba aje ko ina ba, juyata son ransa yaci gaba dayi yana jan na fulaninta tareda bata zafafan kiss ako wanne lungu najikinta wanda sai da yakwashe fiyeda minti 25 asannan ne yafara kokarin zame skirt din jikinta da yake tagama jigata bata iya yunkurin hanashi ba amma fa ta fashe da wani wahalallen kuka wanda yasa ummi Aisha jin tausayinta. ALHERI DANKO NE❗ 6⃣4⃣ Na UMMI A'ISHA Kuka tafasa masa amma tafida bai kulata ba sai da ya rabata da komai najikinta sannan yafara neman hanyarsa ita kuwa hanfa najin haka ta saddakar da cewa yau tafida bazai barta ba sai yayi mata kaca kaca kamar yadda yace, tafida tsintar kansa yayi cikin farin ciki domin bai samu hanyar ba gaba dayanta jinta yayi babu kofa komai kankantar ta hakan ya tabbatar masa da hanfa cikakkayir budurwa ce kamar yadda yayi tunani amma duk da haka bazai barta ba sai ya nemo hanyar sa saboda gaba basai yazo yana wahala ba nanfa yashiga bulayi wai bara akufai ita kuwa hanfa tunaninta ne yatsaya cak jin tafida yanata laluben inda hanyar tasa take amma bataji ya samu ba, nan tafara murna domin hakan ya tabbatar mata da shima cikakken saurayi ne domin bazata manta hirar dataji wasu matan aure sunayi ba a room 5 [8:33PM, 11/23/2015] Ummi A'isha: Alokacin taji suna cewa indai namiji saurayine shima ana ganewa saboda idan yazo sai yasha wahala kafin ya samo hanyarsa idan kuma dama yataba yi to yana zuwa farat daya zai nemo hanyarsa, tana jinsa yanata neme nemensa amma bai samu ba haka ya dauki tsawon lokaci amma bai samuba sai da yafara kokarin kyaleta ne yafara jin alamunta amma koda yaduba yaga ba ita bace zancen zuci yafara yi anya kuwa wannan yarinyar tanada kofa ajikinta? Tana jinsa ya hakura yaci gaba da mutsuttsukata har na dan wani lokaci gaba daya jikinta yagama yin tsami tun anan tasan tafida namiji ne domin tun kafin mai afkuwa ta afku har tafara raina kanta,jin jikinta take kamar tayi wani gagarumin aiki ga duk gabobin jikinta sunyi tsami, kyaleta tafida yayi yafara maida numfashi har tsawon minti 5 sannan yasake shiga jikinta yafara jan albarkatun kirjinta, hawaye yana bin kumatunta tace pls kabari wlh zafi suke min, bai kulata ba yaci gaba da jajjansu tareda cafkarsu zuwa bakinsa sai da yayi yadda yake so da nashanunta sannan yakyaleta yatashi yashiga bathroom ita kuma tana nan kwance tanata kuka saboda radadin da dukiyar fulaninta suke yi mata. ALHERI DANKO NE❗ 6⃣5⃣ Na A'ISHA (ummi) Yana fitowa ya sameta kwance inda ya barta rigarshi yadauka wadda tagama yin squeezing kallonta yayi cikeda tausayawa amma sai ya fuske yace kitashi ki shirya kifito na maida ki makarantar yana gama fadin haka yafita yana kokarin saka rigarsa, yana fita tatashi dakyar ta jawo kayanta tasaka duk idonta yayi hulu hulu kamar wadda yayiwa mai gaba daya, tsaki tayi wlh bazan ma shiga ko toilet din ba idan nakoma school nayi wankan, hijabinta tadauka tasa ta tashi tana cewa ko haka ka barni nayi hankali daga yau bazan kara rainaka ba kuma bazan sake kin bin umarninka ba, afalo tasameshi yana zaune yana shan lemo tsayawa tayi har yagama yace zaki sha lemon? A'a bazan sha ba tafada, tashi yayi yace to zo muje, bin bayansa tayi suka fita ya bude motar suka shisshiga suka zauna sannan ya tada motar sai da suka fita da gate din gidan sannan yace bana son nakara ganinki cikin maza, to tafada tun kafin ya rufe bakinsa har abin yaso bashi dariya saboda yadda yaga yanzu tafara tsorata dashi alhalin shi kuma ba wani abu nakuzo ku gani yayi mata ba, hannunta yakama yasarke cikin nasa, ki rinka saka dogayen rigunan nan kinji? Eh naji zan rinka sawa, kissing din hannunta yayi. Ayshkaus oasis yanufa yayi packing yafita yashiga Jim kadan yafito hannunsa dauke da leda yashigo ya zauna ita dai hanfa mamaki tafida kawai yake bata dan binsa da ido take tayi duk abinda yayi burgeta yakeyi, kuma yanzu ta gane tafida gwarzo ne ba kadan ba, school of nursing yashiga ya tsaya akusa da gate din hostel,kusa da ita ya matsa nan idonta yayi tsuru tsuru kirjinta yashafa yace nifa ba komai zanyi miki ba, daga yau ina jin bazan sake shigowa ba sai nan da bayan 2 weeks saboda munata shirye shiryen bikine, ki kula da kanki kinji? Kai ta daga insha Allah, ledar ya mika mata yace kigaida zarah, zataji tafada tabude motar tafita tashiga hostel tana shiga hostel ta shiga dakinsu lakacin duhu yayi dan har isha'i takusa, tana shiga ta ajiye ledar ta fada kan gado kallonta zarah tayi mrs tafida lfy? Lfy lau hanfa tafada tareda tashi ta dauki bucket tafita taje tuka tuka tadebo ruwa tadawo tazo tacire kayanta tadaura zani tasa hijab tadauki soup case ta kinkimi ruwan tanufi bathroom dariya zarah tafara yau dai duk yadda akayi tafida yayi babban aiki, wanka tayi tai alwala takoma daki tafara shiryawa nan zarah tafara tambayarta wai me kika kawo mana ne? Duba kiga zarah dan nima ban san menene ba, ko sallar magrib banyi ba, sallaya tashinfida tayi sallah sai data idar sannan zarah tafara kokarin bude ledar wadda nikaina ummi na kagu naga abinda ke ciki. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:01PM, 11/23/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 6⃣6⃣ Na UMMI A'ISHA Tana budewa taga drinks kala kala da fresh yo milk, da snacks dangin su miet fie da cake da spring rolls, da sauransu ga robar ice cream nan guda 2 da gasasshiyar kaza katuwa, nanfa ummi Aisha taji yawun bakinta ya tsinke, murmushi zarah tayi kawata irin wannan kaya haka? Lallai yau duk yadda akayi kin jiyar da tafida dadi dan naga kina dawowa da wanka kika fara, harararta hanfa tayi kin manta, ato ai gaskiya ce tunda ni dai nasan ba mensuration kikeyi ba kalau kika fita yanzu kuma gashi kina dawowa kin fara da bath, zarah tafada tana dariya murmushi hanfa tayi zarah kece abar dariya amma bani ba domin ni yanzu nafara sanin rayuwa ke kuwa babu abinda kika sani amma ina addu'ar Allah yakawo aurenki nan da wata 3 yadda kema zaki dandana kiji yadda naji, dariya zarah tayi amin ga kayan dadinki kizo kici, fara ci ina zuwa. Tafida kuwa yana zuwa gida yawuce dakinsu lokacin faisal yana nan yana shiga yawuce toilet yayi alwala ya fito yahau kan dadduma yatada kabbarar salla, sai da ya idar faisal yace mutumina yau da wa kukayi dambe ne? Naga kayanka sunyi squeezing,dariya tafida yayi bakada mutunci ni banyi kokawa da kowa ba tunda kasan ni ba dan iska bane, dariya faisal yayi zaka fadi gaskiya shiru tafida yayi yafara tunanin kodai yafadawa faisal yarasa hanyar ne? Ai faisal dan uwansa ne kuma amininsa babu abinda bazai iya fada masa ba, kallon faisal yayi, abokina wai a ina hanyar nan take? Dariya faisal yafara yi harda kwanciya sai da yagama kular da tafida sannan yace amma kai yarone wlh nan yafara wata dariyar tashi tafida yayi yahau kan gadonsu yajawo laptop dinsa yabude yafara binciken female reproductive system, shi kuma faisal sai aikin dariya yake, tsaki tafida yayi yadauki wayarsa yakoma falo yafara kiran zarah, tana ganin shine ta mikawa hanfa wayar, ahankali hanfa tayi magana hello! Hello yafada yakike? Lfy lau, ya gajiya? Shiru tayi tafara murmushi, ok dama kira nayi nai miki sannu, kinyi kokari sannu kinji Allah yayi miki albarka yanzu ki kwanta ki huta, to nagode hanfa tafada ahankali, I luv you yafada, nagode tafada takashe wayar. [2:52PM, 11/25/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 6⃣7⃣ Na UMMI A'ISHA Tun daga lokacin tafida bai sake zuwa makarantar su hanfa ba saboda kullum yana busy bashida lokacin kanshi kullum suna hanya shida faisal mai martaba yana aikensu sukai invitation amma kullum sai ya kirata yaji lafiyarta, tunda bikin zumunta ya rage saura kwana 3 tafida da faisal suka tafi kasar Morocco inda suka iyo siyayyar kayan da za ayi hawa dasu. Kwanansu daya suka dawo suna zuwa suka samu garin misau yacika dam da baki mahalatta bikin zumunta ga gari ya rude da kide kide da bushe bushe gamida raye raye nanfa su tafida aka fara tsare tsaren yadda bikin zai gudana. Ranar asabar da misalin karfe 3 shine lokacin da aka fara gudanar da bikin dukkan hakimai sun harhadu kowa yahau dokinsa da yan tawagarsa, gidan sarki kuwa yawan mutanen dake ciki ba agano adadinsu alokacin sarki yafito daga cikin gida yahau dokinsa, shi kuma faisal tawagar tafida yabi, lokacin da aka fito daga gidan sarkine aka hau titi da niyyar zagaya garin missau gaba daya kaf domin sarki yagana da talakawansa. Hanfa tana kwance adaki zarah sulaiman tashigo tace mrs tafida tashi mutafi bakin gate kallon hawa ance tana nan zasu wuce, shiru hanfa tayi azahirin gaskiya tayi missing din tafida sosai kuma tana son ta ganshi, tashi tayi tacire kayan jikinta tasaka wata Arabian gown blue tasa dan madaidaicin hijabi suka fita, abakin titin kofar makarantar suka tsaya inda daliban duk suka firfito kwansu da kwarkwatarsu domin kallon sarki kai harma da baki wadanda ba yan makarantar bane, tuni wuri ya rude da ihun dawakai da kide kide da algaita, tawagar chiroma ce tafara wucewa sannan sai ta sa'i dukkaninsu yayun su tafida ne, sa'in misau yana wucewa sai ga tawagar tafida nanfa yan mata suka hau shewa harda masu yin guda domin yawancinsu shi sukazo kallo,tafida kam yasha kyau tun daga kan kwalliyar dokinsa wadda ta kasance anyita da jajayen yadika masu kyalkyali, sirdin dokinma Jane komai dai najikin dokin ja akasa masa, shima tafida fararen Kaya yasa yadora jar alkyabba asama aka nada masa jan rawani takalmin kafarsa ja ga wani bakin glass dayasa gaba daya fuskarsa arufe take saboda rawanin har fuskarsa aka nade gashi yakawo bakin glass yasa kar kuso kuga yadda tafida yayi kyau kamar shine sarkin yayinda yan tawagarsa suka sha kwalliyar kaya maroon ga faisal agefensa shi kuma yayi shigar fararen kaya. [2:56PM, 11/25/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 6⃣8⃣ Na UMMI A'ISHA Faisal ne akusa da tafida ga wasu kuma akasa rike da kaskon turaren wuta sai budade mutane suke yi da kamshi, bude ido hanfa tayi tana ganin tsaruwar da tafida yayi wai dagaske mijinta ne? Kwata kwata bata taba zaton zata samu kamarsa a matsayin miji ba, hayaniyar wasu yanmata ce ta katse mata tunani, lah muniba ga mutumin naki, ok bani wayar nan nayi masa picx wadda aka kira da muniba tafada tana yatsina fuska, gaskiya yayi kyau nabashi 100 marks, nan tazaro iPhone dinta baka tafara zooming din tafida tana yi masa picx, ai insha Allahu sai na auri tafida, ai hanfa najin haka hankalinta yayi mutakar tashi, da duk maganar da suke yi bata damuba amma tana jin an anbaci sunan tafida taji hankalinta yayi masifar tashi, idonta ta daga ta kallo tafida yana kan dokinsa yarike wani mashi ahannunsa na hagu hannun damansa kuma sai dagawa mutane yake yana amsa gaisuwar da suke yi masa, kallonta tadawo da shi kan wadannan yan matan sun hadu iya haduwa kai da ganinsu kasan sunsha naira sun koshi da hutu ga tsabar kyau dan tamkar larabawa suke, sai picx suke yiwa tafida basu kadai ba ma duk yan matan dake gun daukar tafida suke a waya ko ina ka duba flash ce ke haskawa da karar daukar hoto kas kakas kas, take hanfa taji zaman wurin ya dameta yafita daga ranta ko zarah bata yiwa magana ba tajuya tanufi cikin makaranta tana zuwa hostel tashiga dakinsu tafada akan gado tafara kuka wanda ita kanta bata san ko na menene ba balle kuma ummi Aisha wadda ta kasance yar kallo, kuka take sosai domin jin zuciyarta take tana yi mata wani zil zil kamar zata faso kirjinta ta fito ga wani kishi dataji ya turniketa, ga haushin tafida taji tanaji alhalin shi kuma bai san ma abinda yake faruwa ba nan tayi kukanta ta more na tsawon wani lokaci, zarah kuwa bata dawo daga kallo ba sai wurin 6 lokacin hanfa tagama kukanta ta wartsake. [2:59PM, 11/25/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 6⃣9⃣ Na UMMI A'ISHA Hanfa bin zarah tayi da kallo lokacin da ta shigo dakin, murmushi zarah tayi mrs tafida ya akayi na nemeki na rasa ne? Eh kaina ke ciwo shiyasa na taho, amma shine babu sallama kikayi tafiyarki? Ai da kin tsaya kinyi picx da angon naki, amma ga wani da na dauko miki nasa shi daya, kin karba hanfa tayi saboda bata son ganinsa yanzu, ki bari anjima zan gani, cikeda mamaki zarah tace tafidan naki? Tsaki hanfa tayi ta tashi tafice daga dakin. Shi kuwa tafida duk ya gama kaguwa yaga matarsa domin yayi missing dinta yana bukatar yaganta amma bai samu dama ba domin ranar da suka fara hawan zumunta babu lokacin dazai samu yaje ya ganta kuma ma ai ganin da zai yimata na musamman ne, sai da aka kwashe kwana 3 ana gudanar da bikin da yasamu halattar dunbin jama'a tun daga kan sarakuna da hakimai da dagatai da masu unguwanni kai harda sahibar ummi Aisha cwt kausar luv, ana gama gudanar da bikin kuma aka fara shirye shiryen sallamar baki wanda wannan ma yadauki lokaci. Ranar da aka gama bikin ranar tafida ya kira zarah don yana son yaji muryar hanfa sai taki karba haka zarah ta karaci abinta amma taki karba dole ta hakura ta kyaleta, ita kuwa hanfa har yau jin zafin tafida take sai kace shine yace yan matan su daukeshi a hoto. Wasa wasa sai da akayi sati tafida yana iyo waya amma hanfa tana kin karba ganin haka yasashi shiryawa washe gari ya nufo makarantar. [3:02PM, 11/25/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 7⃣0⃣ Na UMMI A'ISHA Washe gari da safe wurin karfe 10 hanfa ta shirya cikin bakar doguwar riga after dress aciki kuma tasa dogon wando da yar body hug aciki, bata yiwa fuskarta kwalliya ba iya powder kawai tashafa tasa lipglow tafesa turaren night feelings da unforgettable me, tadora bakin karamin hijab asama domin yanzu kayan da take sawa kenan tun ranar da tafida ya koya mata hankali, kallon zarah tayi wacce ke kwance batada lfy, zarah bari naje nasiyo mana kerosene din nadawo sai nadora mana girkin, to sai kin dawo zarah tafada, daukar galan hanfa tayi tafita, tana zuwa gate din da zata fita gari taga wata bakar mota mai bakin glass kirar vibe dauke kanta tayi tawuce amma sai motar tadawo aka fara horn bata kula ba saboda tayi zaton ko irin samarin nanne yan iska ita kuwa da auranta, ta saitinta motar tazo tatsaya aka zuge glass tafida tagani yana mata dariya, tagefensa takoma ta bude kofar tashiga, kallonta yayi haba madam irin wannan shariya haka ana ta yimiki horn, to da auran nawa za ayi min horn natsaya? Murmushi yayi yanzu kin yarda kinada auren kenan? Kanta ta sunkuyar kaga kerosene zanje nasiyo fa, ok to bari muje suna fita yadauki titin unguwar rannan nan hanfa taji gabanta yafadi kallonsa tayi yana sanye da jan wando da brown din t shirt yayi aski sumar kansa sai sheki take, gaban hanfa ne yaci gaba da faduwa har suka sha kwanar gidan, kallonsa tayi ina zamuje ne? Wani malalacin murmushi yayi karki damu kawai nuna miki zanyi ni ba yaro bane nadade da girma, to naga rannan ka nuna min, a'a ai na yau daban ne daidai lokacin suka shiga gidan, babu yadda ta iya dole tabishi suka shiga ciki har bedroom din rannan amma fa duk tagama tsorata dashi kana ganin yanayinta zaka san a tsorace take, kofar dakin yasawa key ya isa inda take agefen gado yajata suka zube yafara kissing din bakinta nan da nan kwalla tazubo a idonta, hijabin datasa ya zare yacire after dress din data saka nan yatsaya kallon surar jikinta yadda tafito acikin kayan data saka, kokarin cire body hug din datasa yafara, yana cirewa yaji jikinta dumi tun alokacin yagane period take nan yaji haushi yakamshi yau yazo with full confidence zai bi hanyarsa amma kuma babu dama mensuration ya bata masa shiri, haka ya hakura yafara wasa da kirjinta har na tsawon wani lokaci, sai da yadanji dama dama sannan yayi magana cikin narkakkiyar murya yaushe zaki gama? Banza tayi dashi jin haka yasashi dora hannunsa akan mararta har tsawon minti 5 sannan ya dauke hannunsa yace da baki fada min ba nagano kwana 7 kikeyi yau kuma kwananki 2 da farawa kinga kenan nan da kwana 5 ni angone dan ranar bazan barki ba komai kukanki. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [6:43PM, 11/25/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 7⃣1⃣ Na UMMI A'ISHA Murmushin mugunta hanfa tayi azuciyarta tace zaka dade domin ni next week zan tafi gida kuma idan na tafi bazan dawoba sai nan da sati 3 tunda an kafe mana time table din exam lokacin, ci gaba da shasshafata tafida yayi har yasamu nutsuwa yadda ya kamata sannan ya kyaleta yayi hugging dinta ajikinsa sai da ya danyi bacci ahaka sannan yatashi yana kallonta sai wani murmushin mugunta take yi masa tsaki yadan ja ni kike yiwa dariya ko? Hmm ki gama dariyarki yau yarinya yana gama fadin haka yatashi yafita yana cewa ki zo na maidaki inda na daukoki saboda yau amfaninki kadanne, yana fita ta tashi ta shirya tafito lokacin har ya fita daga falon yashiga motarsa, motar taje ta shiga suka tafi, in banda tsaki babu abinda tafida yakeyi domin yau gaba daya ya gama sa rai da samun hanfa, dariya hanfa tayi aranta tace bakayi tsaki ba sai ranar da kaji nabar misau na tafi disina, hannunta ya kamo kamar yadda ya saba yafara wasa da yan yatsun hannunta har sukaje wani store inda ake sayar da kayayyaki kala kala, ciki yashiga yasiyo mata dan karamin gas wanda zai ishesu girki har na tsawon wata uku sannan ya iyo mata shopping din kayan cooking daga nan yafito yashiga restaurant yasiyo mata take away da drinks masu sanyi yadawo motar, dan kallonsa hanfa tayi sai kuma taji tausayinsa ya shigeta saboda yadda taga yana yi mata hidima ga kudinsa da yake kashewa akanta, makarantar ya mai data yayi packing a inda yasaba tsayawa dama gaba daya motocinsa gilasan tintac ne sai kace wani marar gaskiya, kinje kallon hawa? Ya tambayeta yana lankwasa yan yatsun hannunta, kallonsa tayi eh naje ananma naga yan matanka ai, dariya yayi har hakoransa suka fito, ni inada yanmata ne? Kodai yanmatan faisal kika ga? In dai faisal shine tafida to yan matansa naga. [7:04PM, 11/25/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 7⃣2⃣ Na UMMI A'ISHA Tafida daban faisal daban amma ni banida wasu yan mata faisal ne mai yanmata, sai dai nima nakusa nayi budurwa acikin makarantar nan, kallonsa hanfa tayi tafara kokarin kwace yan yatsunta daga hannunsa ai ya halatta kayi tunda an baka dama kayi mata 4 babu laifi, sake damke hannunta yayi yace ni bazanyi 4 ba amma zanyi 2 shine ra'ayina murmushi hanfa tayi duk kuwa da cewa kishi ya tuketa, Allah yabaka ikon yin adalci amin uwar gida yafada yana murmushi, kinga wata fine baby can ko da ita zanyi miki abokiyar zaman? Waiwayawa hanfa tayi ta hango mami wata yar room 4 tana karantar midwifery bazata fita a haifeta ba yar kano ce daidai lokacin tazo kusa dasu, sauke glass din tafida yayi yace yanmata ji mana, babu musu mami tadawo tace gani, kallon hanfa yayi tayi kicin kicin ta hade girar sama data kasa, yi hakuri dama sako zan baki amma barshi kawai, ok babu matsala amma da ka fadi sakon naka, ki barshi nagode yafada yana daga glass din sama, kallon hanfa yayi kema haka kike da kishi? Dubawa zakayi sai kagani tafada tana kawar da kanta, to ai gashi naduba nagani kinada kishi, meye abin kishi? Ni indai ta nine ka auro mata 3 banida damuwa, karya kike kawai dai kin fada ne, amma dagaske fa yarinyar nan kyakkyawa ce, da sauri ta jiyo ta kalleshi dagaske fa kace, to ko dagaske auran nata zakayi? Eh ai na fada miki aure zan kara sai ku tare lokaci daya, shiyasa kake so kayi min ciki saboda zakayi sabuwar amarya? Sai kuma hawaye yafara bin kumatunta cikeda mamaki ya kalleta meye abin kuka? Nifa da wasa nake miki jawota jikinsa yayi ya rungumeta yafara lasar lebenta kidaina kuka wlh wasa nake miki kuma duk kyanta kinfita kyau bata da wani kyau ma, ki kwantar da hankalinki ni ke kadai kin isheni rayuwa kuma wlh banida wasu yan mata, dariya tayi bata shirya ba saboda jin abinda yafara yi mata, sakinta yayi yana dariya wannan dan karamin cikin naki yakusa zama babba, fuskarta ta dauke daga kallonsa ta kalli window,idan kinje kiyiwa zarah sannu kinji, zataji hanfa ta fada tana kokarin bude kofar motar, kayanta yafito mata dasu ta dauka ta tafi hostel. [7:22PM, 11/25/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 7⃣3⃣ Na UMMI A'ISHA Juyawa tafida yayi yatafi yana cike da kewar matarsa ya nufi asibiti domin yanada theatre. Ita kuwa hanfa hostel tashiga hannunta dauke da kaya niki niki lokacin zarah har ta dan warware shewa zarah tafara yi dakyau mrs tafida muma mun zama yan gayu mun daina amfani da stove mun dawo girki da gas, zama hanfa tayi tana dariya kwarai kam, ai ke kam kinyi sa'a tafida yana ji dake ban san me kika bashi haka ba yabi ya rude, ke kika sani kuma hanfa tafada tana murmushi domin ita kanta tasan tafida yana sonta saboda abubuwan da yake yi mata kadai sun isa su tabbatar da hakan, lumshe idonta tayi ta fara hango soyayyarsa mai dadi da tsayawa arai, haka tayita gudanar da abubuwanta cikin nishadi da annashuwa amma tun daga ranar tafida bai kara shigowa school dinsu ba saboda wai baya so yazo yaganta tayar masa da hankali zata yi alhalin kuma tana fashin salla ba wani abune zai gudana a tsakaninsu ba, haka yayita daurewa amma kullum yana yi mata waya ta wayar zarah. Ana igobe zata fara salla tashirya tayi tafiyarta disina bayan sun gama waya da tafida amma bata sanar dashi zata tafi gida ba saboda tasan idan tafada masa zaiyi amfani da karfin ikon igiyoyin aurensa dake kanta ya hanata tafiya tunda yanzu a karkashin ikonsa take, haka taware abinta batare da saninsa ba shi kam tafida alla alla yake jibi tayi domin lokacin yasan tagama period yaje ya dauketa amma koda dare yayi yakira zarah yace tabashi matarsa sai zarah tayi mamaki tace bata fada maka dama zata tafi disina ba? Gabansa yaji yafadi yaushe ta tafi? Wlh da safe lokacin da kuka gama waya ta tafi, amma da nasan bata fada maka ba wlh da nafada maka, yaushe zata dawo? Sai nan da 3 weeks wlh, to zarah nagode sai da safe yafada cikeda damuwa. [9:06AM, 11/26/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 7⃣4⃣ Na UMMI A'ISHA Ajiye wayar tafida yayi cikeda bacin rai, har tayi tafiya bata sanar dani ba ina matsayin mijinta? Yayi mata kyau yafada afili nan ya kwanta yana mai cikeda kunar rai ahaka faisal yazo ya riskeshi awannan halin shi dai agaskiya yanada bukatar matarsa dan haka gobe ko jibi zai je disina koda kuwa mahaifin hanfa zai koroshi haka ranar yayi bacci cikin damuwa. Wayewar garin ranar bai samu yaje disina ba saboda patients din da ya wuni yana dubawa dan haka washe gari yashirya tsaf cikin shadda mai tsada fara yasa hula yasha turaren active man yatafi disina shi kadai yatafi bai tafi da kowa ba domin acewarsa sirrinsa zai je yagano. Karfe 11:30 ya isa gidansu hanfa yana yin packing yafara tunanin ta yadda zai tunkari gidan, ta maza yayi sannan yafito yashiga gidan yana sallama baban hanfa ne yafito yana ganinsa ya murtuke fuska yafara tambayarsa me kadawo yimin agida? Ban gaya maka kar nasake ganin kafarka agidana ba? Maza maza ka fice min daga gida kar nasake ganinka agidana har abada sannan kuma ban yarda kasake koda magana da yata ba bare har kabita makaranta, cikeda damuwa tafida yace dan Allah baba kayi hakuri, ka fitar min agida nace kuma ko kofar gidana ban yarda kasake zuwaba, zubewa tafida yayi yafara rokonsa amma bai saurareshi ba haka ya koreshi fata fata nan fa idon tafida yakada yayi jawur yafita yashiga motarsa yatafi, gudu yake shararawa bana hankali ba ga faisal yanata yi masa waya amma bai dauka ba daf da zai shiga garin misau wata tirela tayi gaba da motarsa ji kake taratsatsatsa tafida bai tashi ganinsa ba sai agadon asibiti, gasu faisal da mai martaba tsaye akansa inno kuwa da momcy sai kuka sukeyi, ya bugu sosai ya karye a hakarkarinsa na dama gashi hatta harshensa ma ya tsage gida biyu banda daddaujewa da yayi, wani likita ne ya shigo yaduba shi anan yace ana bukatar za akara masa jini, jinin faisal akaje aka diba aka kara masa, gaba daya kamanninsa sun canja ko magana baya iya yi duk wanda yaga motar daya yi accident din da ita kuwa bazai yi zaton ya rayuba saboda yadda tayi kwatsa kwatsa, shi kansa faisal duk dauriya irin tasa sai da ya zubarwa da tafida hawaye. [9:12AM, 11/26/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 7⃣5⃣ Na UMMI A'ISHA Lokacin da labari yajewa gidansu hanfa iyayenta suka taso sukazo dubashi alokacin baya gane wanda yake kansa hakuri baban hanfa yafara bashi tareda cewa yabashi hanfa ko yau yake son kawota gidansa yaje yadauko ta,har suka tafi tafida bai san abinda ake yi ba, bayan tafiyarsu da kwana 2 iyayen hanfa suka ce tashirya tazo tayi jinyar mijinta babu musu ta shirya ta taho saboda dama kawai dauriya take amma tana cikin damuwa, asibitin tafara zuwa itada zarah sulaiman anan tasamu faisal da mai martaba da momcy, sunyi murnar ganinta sosai tareda jajantawa juna, lokacin dataga tafida kuwa kawai kuka ta fara saboda yana jin jiki. Kwananta 2 a asibitin yafara gane komai har yana dan bude baki yayi magana dayake an cire dinkin da aka yiwa harshensa, zarah kuwa kullum tana zuwa dubashi daga sch, ko abinci ta ruwa ake bashi amma jikin nasa yadanyi sauki. Kwananta 5 yafara magana radau, tana zaune agefen gadon yabude idonsa babu kowa adakin sai su 2 magana yafara yi mata ahankali, hanfa nasan mutuwa zanyi amma ko namutu faisal kawai na yarda ki aura domin shine dan uwana kuma aminina sannan abokina kiyi hakuri hanfa yana fada yana hawaye, cikin hawayen itama tace bazaka mutu yanzu ba tafida insha Allahu ba yanzu zaka mutuba bakinta tasa akan nashi tafara yadda yasaba yi mata duk lokacin da suka hadu wato zagaye lips dinta da harshensa, hanfa mutuwa zanyi nafada miki rungumeshi tayi ba mutuwa zakayi ba tafida ko kamanta da abinda ka fada min? A kunnensa ta rada masa so kake ka mutu ba kayi min cikin ba? Murmushi tafida yayi itama murmushin tafara yi ga hawaye kuma akan kumatunta hannunsa yasa acikin rigarta yafara shafa cikinta zaki haifa min baby? Kai tadaga cikeda jin kunya, ganin wasan nasa zaiyi yawa yasata tashi taje tasawa kofar dakin key tadawo, kokarin cire rigarta yafara yi da hannunsa guda daya mai lafiya, taimaka masa tayi tacire rigar nan fa yafara sarrafata da hannu daya. Sai da ya nishantu sannan ya rabuda ita, jin ana kwankwasa kofa yasa hanfa tashi tasaka rigarta da hijab dinta ta nufi kofar dakin tabude, faisal ne yashigo shida wata bakuwa suna shigowa faisal din yafita ita kuma bakuwar takarasa ciki daidai lokacin tafida yafarka yabude idonsa akan kujerar dake gaban gadon tazauna tana fadin sannu baby, cikin sauri hanfa ta kalleta baby kuma? Hmmm wai nidai ummi Aisha nayi nan. Ausar! Ausar! Naci karo da sakonki, mun gode Allah yabar kauna da zumunci on behalf of hausa novels [truncated by WhatsApp] [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:14PM, 11/26/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 7⃣6⃣ Na UMMI A'ISHA Kallonta hanfa ta farayi daga sama har kasa, farace sosai dogawa mai manyan idanuwa kyakkyawa ce ta ajin karshe kuma daga ganinta yar masu kudi ce, ahankali tafida yabita da kallo amma bai yi magana ba ita kuwa bakuwarsa ci gaba da yi masa sannu tayi, sannu baby ashe haka abu yafaru wlh sai jiya nakira faisal nake tambayarsa me yasamu phones dinka inata kiran ka bana samunka shine yake fada min kasamu accident ne, to yau kuma ban samu flight din safe ba shiyasa, ita dai hanfa tsaye tayi tana jin ikon Allah wannan shine karfin hali wai barawo da sallama agabanta wata tana kiran mijinta da baby abinda ita bata taba kwatantawa ba lallai dole ta daura damara kuma yazama dole tasake shiri na kulawa da tafida, nan fa kishi ya motsa ta bata rai, hannu tafida yadaga mata alamar zai sha ruwa, ruwa marar sanyi ta dauka fuska babu walwala ta isa bakin gadon tazauna babu damar ya tashi zaune kuma idan tasa masa robar ruwan a bakinsa ruwan zai tafi har ta hancinsa, abakinta ta dura ruwan sannan ta hada bakinsa da nata tafara zuba masa ruwan acikin bakinsa ahankali yana shanyewa har yakare tasake guntsar wani ta zuba masa haka tai tayi har ya koshi ita kuwa bakuwarsa har yanzu bakinta bai yi shiru ba sai cigaba da jajantawa take yayinda shi dai tafida yaki magana saboda bai san yadda hanfa zata dauki bakuwarsa ba, domin tare sukayi makaranta da ita a lokacin da suke karatu itama doctor ce kuma tun a makaranta ta nuna tana sonsa amma shi baiji yana sonta ba saboda ko ashekaru ma shekarunsu zasu zo daya gashi babanta shahararren mai kudi ne jin dadi da hutu sun gama baibayeta hakan yasata wayewa sosai shi kuma yafi son ya auri wadda bata wayeba domin yafi son wadda komai shine zai koya mata kamar hanfa babu abinda ta sani sai abinda yayi mata, hankalinsa ne yadawo jikinsa jin hannun nana ajikinsa tana tabashi cikin sauri ya kalleta yace nana meye haka kuma? [8:05AM, 11/27/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 7⃣7⃣ Na UMMI A'ISHA Ayya sannu baby kawai ina sone naji yadda temperature din jikinka take aiki amma naji normal take, kallon hanfa tafida yayi tagama kuluwa kawai kallonsu take, shigowar zarah ne ya sata samun sukuni, duba tafida zarah tayi sannan taja hanfa suka fita suna fita hanfa tafara yiwa zarah korafi tana cewa ita zata tafi gida cikeda mamaki zarah tace saboda rashin wayo ko me? Mijin naki bashida lafiya kitafi ki barshi? Anya kuwa kina sonshi? Shiru hanfa tayi aranta tace lallai zarah bakida seti ai tun ranar da nafara ganinsa nakamu da sonsa kuma tun lokacin da ya nuna min soyayyarsa mai dadi najishi yashiga raina, zama zarah tayi tabata shawarwari masu amfani sannan tayi mata sallama ta tafi. Tunda zarah ta tafi bata shiga dakin ba sai da bakuwar tafida tafito suka tafi da faisal sannan hanfa takoma cikin dakin, tana shiga tafida yakirata madam zo nan, shareshi tayi taki zuwa, idan baki zo ba wlhi ban yafe miki ba jin haka yasata tashi taje inda yake, hannu yasa yajata gefen jikinta ya kwantar da ita yafara yi mata kalamai masu dadi nan taji hankalinta ya kwanta jin tafida ya fada mata ita kadai ce a birnin zuciyarsa, kanta ya shafo fitsari nakeji da sauri ta tashi fitsari kuma? Kaga faisal yafita kuma dama shine yake taimaka maka kayi, to yanzu meye nufinki? Zama zanyi tayi da fitsarin har sai faisal yazo? Kallonsa hanfa tayi to ya za ayi? Kira min nurse din nan ita tasan yadda zatayi harara ta watsa masa tadauko wata ya silba ta bashi tashi kayi yana tashi ta juya baya har yayi yagama madam baki bani ruwa ba ai, robar ruwa tadauko ta rufe idonta tazo ta bashi har yagama idonta a kulle yake sannan ta karbi silbar ta nufi toilet. Zaman hanfa a asibitin nan yasata daura aniyar bawa mijinta soyayya domin kullum yan mata wuni suke suna yi musu zarya a asibitin domin duba tafida, kwanansu 15 aka ce zasu iya tafiya gida in yaso sai arinka zuwa gida ana dubashi nan suka shirya kayansu suka tafi, wannan shine karo nafarko da hanfa zata shiga gidan sarauta tun daga bakin kofa tafara kallon tsaruwar gidansu tafida wanda yake makeken gaske yasha shuke shuken kayan itatuwa su dabino da dogon yaro, shi kansa wurin packing din motar unguwa gudane gashi waje waje lungu lungu, lungun su tafida sukaje wanda yake babban falone da katon daki wanda yasha kayan ado masu kyalkyali da kyau ga shinfidu daki daki, dakin kuwa ba a magana domin wani mulmulallen gadone da jibgegiyar katifa akai ga labulaye nan masu design mai kyau kai abin dai sai wanda yagani. [8:09AM, 11/27/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 7⃣8⃣ Na UMMI A'ISHA Tunda sukaje gidan hanfa take kallon abin mamaki iri iri agidan komai kuyangune keyi kuma alokacin jakadiya tasata agaba zuwa fada inda zata gaishe da mai martaba,suna shiga fada taga fadar mai girma ce ga ado da kwalliya da aka yi mata sannan ga wata kujera mai kamada gado da dan abin dora kafa agaban kujerar wadda aka yita da barawon gold domin in banda kyalli babu abinda takeyi, bayan hanfa ta kwashi gaisuwa ne suka koma lungun inno anan aka yi mata masauki acikin dakin inno ai tuni inno tashiga nan nan da hanfa domin tana sonta sosai ganin yadda take kula da tafida a asibiti. Tunda suka dawo gida ita taci gaba da kulawa da tafidan kuma yanzu alhamdulillah jikinsa yayi sauki hakarkarinsa ne har yanzu bai gama warkewa ba amma kamanninsa sun dawo. Yau tunda yamma tadawo dakin inno tayi wanka tashirya domin ta baro tafida yana bacci, bayan ta shiryane tasake komawa tana shiga taji motsinsa acikin toilet nan ta zauna tana jiran fitowarsa tana nan zaune har yafito yana ganinta yafara murmushi tareda wucewa inda kofa take yatura kofar yasa key yadawo, kallonsa hanfa tayi ya haka? Hannunta yaja yahadata da jikinsa yafara kissing din bakinta,wuyanta da goshinta nan yafara rudata da soyayyarsa tareda janta zuwa gado acikin dabara ya rabata da kayan jikinta nan yafara shakar kamshin dake fita ajikinta, wasannin daya saba yi mata yafara amma na yau yasha bamban dana kullum nan hanfa tafara fita hayyacinta saboda wahala amma yau tafida yarantse sai yanemi hanyarsa yabi, duk kukan da hanfa take yi bai sashi kyaleta ba har sai da yasamo hanyar yabi, hanfa ta jigata sosai ga azabar datake ji ajikinta,dakyar tafida yadan kyaleta ta huta in banda hawaye babu abinda take yi, tana dan hutawa tafida yafara shafarta tareda kokarin maimaita abinda yayi domin hanfa tagama rudashi, nan kuma tafara kokarin hanashi amma takasa sai da yajishi zamzam sannan ya iya hakura amma dakyar ya iya barinta,dakyar tayi masa magana da dasasshiyar muryarta, bani ruwa nasha cikin sauri tafida yadauko mata babbar robar ruwa yabata tana karba tafara sha bata ajiyeba sai data shanye ruwan ciki tas. [8:29AM, 11/27/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 7⃣9⃣ Na UMMI A'ISHA Tana shanyewa ruwan baccin wahala yace muje zuwa take baccin wuya ya dauketa, zuba mata ido tafida yayi yana kallonta hakika hanfa tazama wani sashe na rayuwarsa, Allah sarki yau namiki rashin tausayi hanfa yafada acikin zuciyarsa tashi yayi yashiga toilet yayi wanka yafito yasa riga bakar t shirt da green din three quarter yazauna zaman jiran hanfa ta farka, gefenta ya kalla duk wurin yagama baci kai hanfa yau kinsha wuya yafada yana shafa gashin dake kwance a hannunta ahankali tabude idanuwanta wadanda sukayi ja kamar jini, yana ganin tafarka yatashi yadau wayarsa yafara kiran momcy, tana dauka yace momcy dan Allah ki turo min jakadiya amma kutaho tare cikeda tsoro momcy tace lfy? Momcy kuzo dai kawai yana fadar haka yakashe wayar, ai hanfa najin haka sai kuka, wannan wanne irin abune? Komai daya faru sai ansani, kai me za ayi da gidan sarauta sam babu sirri yanzu wannan abinma sai ansani? Nan tasake barkewa da kuka nidai tafida yagama cutata yarasa a inda zai min wannan abin sai agidansu gidan surukaina agaban iyayensa,ganin tanata kuka yasa tafida fara lallashinta sorry my wife, nine ko? Sannu, bata kulashi ba taci gaba da kukanta,tashi yayi yaje yabude kofa momcy da jakadiya yagani, meya faru? Momcy ta tambayeshi momcy yarki ce batada lafiya, meya sameta? Momcy kishiga zaki gani yafada yana shafa kansa, shigewa su momcy sukayi anan suka ci karo da ta'asar daya aikata kallon jakadiya momcy tayi tace maza tashiga bandaki ta tari ruwan zafi ita kuma tafito ta nufi sashenta tadebo wasu maganguna shi dai tafida yana tsaye afalo yakasa zaune yakasa tsaye, har momcy tadawo ta kalleshi sannu da aiki yarinyar tayi zaman jinyarka a asibiti ko gama hutawa batayi ba kabita da wannan danyen aiki tana fadin haka tashige dakin, ita da jakadiya ne suka gyara hanfa sukayi mata komai suka gasata tashiga ruwan zafi sannan suka fito suka barta tayi wanka tafito lokacin an sake shinfida sabon zanin gado. [8:54AM, 11/27/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 8⃣0⃣ Na UMMI A'ISHA Zama tayi tashafa mai tasaka kayanta tabi gadon takwanta sai da tayi bacci sannan su momcy suka fito daga dakin ita momcy mamakin rashin kunyar tafida takeyi kodan yaga shine auta amma in banda rashin ta ido irinta yaran yanzu yaushe zakayi haka agidanku, yana ganin sun fito yatashi momcy kun fito? Eh idan ta tashi dakina zata zo ba dakin inno ba kaji? To momcy, suna fita yashiga dakin yatsaya yana kallon hanfa wadda ta bararraje akan gado tana bacci, falo ya koma sai ga faisal ya shigo yana ganin faisal yaje ya tare bakin kofa ya tsaya, kan kujera faisal yakarasa ya zauna yace mutumin ashe ka warke na tayaka murna da rabon bazaka mutuba sai ka nemo hanyarka, dariya tafida yayi acikin zuciyarsa yace zancen yaushe kuma nikam ai har nasamo hanyata nabita naje inda zanje nadawo, tashi faisal yayi zai shiga daki cikin sauri tafida yasha gabansa, malam yau dakin nan babu shiga fa saboda nayi ajiya aciki, dariya faisal yayi dalla matsa min laptop dina zan dauko, ok to tsaya nadauko maka komawa faisal yayi yazauna tafida yashiga dakin ya dauko masa ya kawo, nan shima ya zauna lokaci lokaci yana leka dakin yaga ko hanfa ta tashi, ba ita ta farka ba sai karfe 6:30 tana tashi tayi yunkurin saukowa daga kan gadon amma ta kasa, nan tafida yashigo yaganta sannu kin tashi? Harararsa tayi tafara saukowa ahankali kamar wata mai koyon tatata tafara tafiya tazo tawuce ta gabansa tana fita falo kuma taga faisal a hankali tawuce tafida yana binta abaya nan faisal yabisu da kallo, suna fita tafida yadauketa a kafadarsa yayi lungun momcy da ita, akan gadon momcy ya kwantar da ita yace bari nakawo miki magani kisha kinji, fita yayi yakoma dakinsu yana shiga faisal yafara tsokanarsa ashe kai yau garin da baka taba zuwa ba kaje shiyasa kahanani shiga daki shiru tafida yayi yadauko first aid box dinsa yafara lalubar maganin da zai bawa hanfa, shi kam faisal yau yasamu nayi sai tsokanarsa yake, bai kulashi ba yayi alwala yatafi masallaci sai dayadawo sannan ya debi magungunan yatafi kai mata, lokacin daya shiga momcy tana falo amma babu kunya haka ya wuceta yashiga dakin, hanfa ta gama cin abinci kenan yashiga tana ganinsa ta sunkuyar da kanta, sannu madam ga magani nakawo miki kinji yar kaciya, karba tayi tadauki ruwa tasha maganin, to sauranki allura nan kuma tace bata san zance ba, kokawa suka shiga yi ya matseta tsam ajikinsa yajanye skirt dinta yayi mata allura har guda 2 kuka tafara bakinta yafara[truncated by WhatsApp] [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [6:45PM, 11/27/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 8⃣1⃣ Na UMMI A'ISHA Bakinta tafida yafara lasa yana rarrashinta tare da shafa kanta, kukan shagwaba hanfa tafara sai yau nasan baka sona baka kaunata domin wahalar da kabani tunda nazo duniya ban taba shan irinta ba, da nasan haka zaka yimin da banzo ba, hawayen kan kumatunta ya lashe da harshensa haba matata yazaki ce haka? Kiyi hakuri kinji nasan kinsha wahala amma am so sorry pls kuma kin san ni dan theory ne wlh ban taba yin practical ba sai yau shiyasa nakasa controlling din kaina amma kiyi hakuri kinji, jikinta takwace ta kwanta, jikinta yafara kokarin shiga daidai lokacin momcy ta shigo takalleshi to marar kunya tashi ka fita kabarta ta huta marar kunya kawai, saboda tsabar rashin tausayi kaga abinda kayi mata tafiya ma nema take tafi karfinta tashi tafida yayi yafice ya nufi sashensu yana shiga faisal yace kaga ango, zama tafida yayi duk jikinsa asanyaye domin yasan yayiwa hanfa bata nutsuwa ba, wai kai saboda tsabar rashin kunya akan gadon nan kayi komai? Harararsa tafida yayi ban sani ba,gaskiya idan anan kayi ni ka cuceni dan bazan kara kwana agadon ba, kar ka kwana din tafida yafada yana zaro wayarsa daga aljihu dariya faisal yafara yi yaro yau ya girma sai asannan tafida yayi dariya shima yace ai ni dama nadade da girma ita kanta tasani, ai dama ita yau tasan ka girma tunda ka nuna mata, tashi tafida yayi yafita yanufi lungun inno yana murmushi domin yau acikin farin ciki yake. Bai sake komawa lungun momcy ba sai bayan sallar isha amma koda yaje momcy hanashi shiga wurin hanfa tayi tace yafita haka yafita yatafi ba dan yaso ba yana komawa daki faisal yafara yi masa tsiya tun da naga an canja bedsheet nasan aikin gama ya gama tsaki tafida yayi kai in banda lalura ma mai zai sani yin making love da matata a wannan gadon da kagama tsiyarka akai. [7:04PM, 11/27/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 8⃣2⃣ Na UMMI A'ISHA Sai da faisal ya karaci yiwa tafida tsiya sannan ya kyaleshi ya kwanta amma ba baccin yake ba shiru kawai ya yiwa faisal kamar yayi bacci, tunanin hanfa kawai yakeyi shekarunta yanzu akalla zasu kai 23 amma hakan bai sa ta zubar da darajarta a titi ba abinda wasu yan matan sukeyi domin mafi akasarin yanmatan yanzu zawarawa ne shi yasa yayi mamakin yanda hanfa tarike kimarta duk da cewa dama ba ataru an zama daya ba amma shi kam yana alfahari da samun hanfa a matsayin mata saboda arayuwarsa babu abinda ya tsana irin zina bai taba aikata taba kuma bashida sha'awar aikata ta domin ko a hospital tsakaninsa da mata yayi abinda yakaishi yatafi baya tsayawa karewa matan mutane kallo sannan idan ba takama dole ba baya son taba jikin mace wannan dalilin ne yasa mutane da yawa suke ganin kamar girman kai ne yake sashi yin haka, kuma haka yadade yana fatan samun matar da bata taba aikata zina ba saboda yatsani zina arayuwarsa. Har asubha tayi idon tafida biyu baiyi bacci ba kamar yadda itama hanfa takasa baccin ita kawai tunanin abinda yafaru tsakaninta da tafida take lallai wani aikin sai dai maza shiyasa adaren farko dole mace tazama yar kauye musamman agurin mijin da ya amsa sunansa saurayi dan ranar babu abinda bazata ganiba, ita dai tafida ya shayar da ita mamaki domin duk kyansa da kudinsa da sarautarsa bai sashi neman mata ba wadda ko akyauta mace zata iya kawowa tafida kanta amma duk da haka yadaure ya tsaya har Allah ya azurtashi da ita a matsayin mata murmushi tayi tashafi cikinta oh ko yanzu har yayi min cikin ko kuma sai nan gaba, hmm tafida kenan sarkin iya soyayya dariya tayi ita kadai saboda jiyo sunbatunsa acikin kunnenta daya rinka yi mata azahirin gaskiya budurcina shine yancina sunan wani littafi na adda benaxir juyawa tayi ta gyara kwanciyarta Allah ina rokonka daka barni da tafida amatsayin mijina kabamu yara masu albarka masu kamada tafida dan yafini kyau, ya Allah ka kare min yarana daga aikata zina kamar yadda ka karemu nida mahaifinsu, rabbana wa takabbal du'ahh! [9:11PM, 11/27/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 8⃣3⃣ Na UMMI A'ISHA Shiru tayi taci gaba da tunanin tafida da ita kanta a yanayin dazu wani abin idan ya fado mata sai dai tayi dariya wani kuma sai tausayinsu itada tafida ya kamasu dahaka har asuba tayi alokacin ta tashi dakyar tashiga toilet tayi alwala tazo tayi salla tana idarwa takoma gadon momcy takwanta gaba daya jikinta ciwo yake yi mata ga gabobinta duk sunyi tsami dakyar take motsa jikinta dahaka bacci ya dauketa bata tashi ba sai karfe 10:30 nasafe tana tashi tashiga wanka tafito ta shirya tayi simple kwalliya tasa riga da skirt na atamfa dark blue ta shafa turare nan kuyangin momcy suka shigo mata da kayan karin kumallo cikin kwanuka kala kala tashi tayi dakyar tafita falo tagaida momcy takoma dakin duk kunya tagama baibayeta ko inda momcy take bata son zuwa dan kunyarta take ji, abincin da aka kawo mata tafara budewa, soyayyen dankali da kwai da farfesun kayan ciki da ruwan zafi da kayan tea ga kuma gurasa da miya, dankalin tazuba dan kadan tafara ci ahankali tareda hada ruwan zafi empty tafara sha, jikinta ne yabata ana kallonta ga wani kamshi da taji ko ba afada mata ba tasan tafida ne domin kamshin turarensa taji kanta tajuya ta hangoshi tsaye abakin kofa yajingina da bango yaharde hannunwansa a kirjinsa yana sanye da orange colour din t shirt an rubuta you can't see me ajiki, da bakin jeans murmushi tafida yafara aika mata dashi sannan yakarasa cikin dakin yaje kusa da ita yazauna yafara kallonta cikeda sha'awa, good morning madam! Yafada cikin muryarsa mai mutukar dadi, morning tafada ahankali batare da ta kalleshi ba, kallonta yasake yi yajikinki? Kinji sauki? Kin daina tatata din ko har yanzu yar kaciyar ce? Murmushi tayi zaka fadi haka mana tunda kai dai kagama abinda zakayi. [9:35PM, 11/27/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 8⃣4⃣ Na UMMI A'ISHA Kusa da ita ya matsa haba ya zakice haka? Tambaya fa nayi idan baki warke ba sai na sake yi miki wata allurar, dasauri ta dago ta kalleshi um um ni babu allurar da zaka kara yimin, murmushi tafida yayi yasa hannu acikin dankalin datake ci yafara diba shima yana ci, gaskiya ke matsoraciya ce kiga wurinda kika cijeni jiya yadda gun yatashi ko? Kallonsa tayi awannan yanayin idan da abinda yafi cizo ma ai zanyi saboda banji da dadi ba, murmushi tafida yayi yanzu kin gane ni ba yaro bane ko? Ni dama tun jimawa nasan ka girma, shiyasa jiya kika cijeni? Nifa ban cijeka ba, mantawa dai kikayi yanmata amma kin cijeni ki kalli wurin kiga, tashi hanfa tayi tahau gado ta kwanta kaga ni ka kyaleni bacci nakeji bacci zanyi, zakiyi bacci amma sai kinsha magani,nifa ka barni nawarke, murmushi yayi yataso yazo kusa da ita yazauna agefen gadon yafara tsokanarta tafida da nasani da banzo ba, da nasan kasheni zakayi da bazan zo ba wayyo zan mutu, murmushi hanfa tayi naji nayi kuka amma ai kaima kayi kukan, to ai kin cancanci haka, juya kanta tayi takwanta nan ya zauna yaci gaba da tsokanarta har momcy tashigo sannan ta korashi badan yaso ba yatafi yabar hanfa yakoma dakinsu yaje ya kwanta yafara ramuwar baccin da bai samu yayi ba itama hanfa baccin tayi sai wurin azahar sannan ta tashi. Tunda momcy ta kori tafida bai kara shigowa ba sai dare lokacin momcy tana sashen mai martaba yana shigowa ya sameta zaune agefen gado hannunta rikeda littafi mai tsarki tana karanta suratul ankabut, zama yayi akusa da ita, alqur'anin ta rufe ta ajiye tajiyo ta kalleshi tana ganin ya matso ta matsa ya kara matsowa tasake matsawa har taje karshen gado, hannunta yarike yau kuma guduna kikeyi? To kadaina matsowa tafada kamar zatayi kuka, nifa ba komai zanyi miki ba kiketa matsawa, to ai ni bana son karinka matsowa bakinta ya tsotsa yashafi kirjinta yace ke tsoronki yayi yawa wlh yana kokarin daga rigarta momcy tashigo nan tafara fada wai kai wanne irine? Kabar yarinyar nan tahuta dan Allah, ka ga yadda kayi mata kamar kai ba likita bane to tashi maza kafice, tashi tafida yayi yace momcy nida matata amma arinka korata? An korekan maza fice min, to kuma momcy ko hira ba zamuyi ba? [6:32PM, 11/28/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE ! 8⃣5⃣ Na A'ISHA (ummi) Kaci gidanku kai da hirar, kai meyasa bakada kunya ne? So kake ka illata musu yarinya? Yanzu kaga yadda take tafiya dakyar, momcy nifa ba komai zanyi mata ba, to koma dai menene fito ka kama gabanka, fita tafita yayi yana tafe yana kunkuni harda doddoka kafa akasa sai kace wani karamin yaro hakan da yayine yabawa hanfa dariya, ni kike yiwa dariya ko? Wlhi zan kamaki, ka kamata din momcy ta fada tana talle kyeyarsa, haka yafice amma tun daga lokacin yayi zuciya yadaina zuwa dama shi mutumne mai zuciya, yana son yaje yaga matarsa amma kuma yanata daurewa dan yasan ko yaje momcy korarsa zatayi haka yaki shiga lungun momcy har tsawon kwana 2. Duk jinsa yake babu dadi sanadiyyar rashin ganin hanfa amma ya cije har kwana biyu akwana na 3 ne da yamma yafito daga sashen mai martaba zai shiga sashen inno azaure yaci karo da ita zata fito tsayawa yayi yana kallonta inye sai yau kika fito? Kallonsa hanfa tayi daga shi sai thee quarter da t shirt light blue, akan kafadarsa ya sabeta yayi sashensu da ita nan tafara dukansa da hannunta akafadarsa da gadon bayansa har suka shiga falonsu ga faisal azaune yana kallo amma hakan bai sa ya ajiyeta ba sai ma kallon faisal da yayi yace dan Allah ka tashi katafi yawonka zan gana da iyalina ne, kallonsa faisal yayi ai kai dan iskane, kaine dan iska tafida yafada tareda shigewa daki dole tasa faisal tashi yafita daga gidan ita kam hanfa duk ya gama bata kunya suna shiga ya rufe kofa yaje yadireta akan gado, fadawa gadon yayi tareda jawota jikinsa yadorata akansa ya kwantar da ita ke kuma haka akeyi sai ki daina zuwa zaman jinya? Bayan ban gama warkewa ba? Cikeda kunya hanfa tace ka warke mana ai ka dade da warkewa tunda ka nuna min hakan, hannunsa yasaka cikin gashin kanta to ai ke dama jinyata kika zo yi meyasa zaki gudu ki barni? Runtse idonta tayi sakamakon zip din rigarta da taji yajanye ahankali yajuyata takoma kasa shi yana sama numfashinsa na sauka akan fuskarta kwalla tafara saboda tuno azabar data sha rannan da tayi dan Allah nidai kayi hakuri ka kyaleni kar kamin irin na rannan wlhi da zafi hawayene yafara bin kumatunta, rigar jikinta yacire yafara wasanni da sassan jikinta ni ba komai zanyi miki ba iya kacina nan sai alokacin taji hankalinta yadan fara kwanciya,wasa yayi da ita son ranshi wanda ita kanta sai da taji armashi ta nishantu sosai har aranta tace wannan shine mai sweet din amma da anje daya bangaren wuya zan sha, bakin tafida taji akan nata yana wasa da harshensa akan lebenta, madam da na mutu da tuni ban samu wannan garabarsa ba ko? Amma fa acikin zafin ciwo nayi miki waccar maganar,gwara da ban mutu ba gashi na bude hanyata da kaina, hannunta tasa takare fuskarta dan kunya saboda shi tafida sam ba yajin kunyar fada mata kowacce irin magana tun kafin wani abu yashiga tsakaninsu yake fada mata duk abinda yaso, juyata yayi ya kwantar da ita ajikinsa yakama hannunta yarike cikin hannunsa yafara wasa [truncated by WhatsApp] [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [8:18PM, 11/28/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 8⃣6⃣ Na UMMI A'ISHA Cire hannun nata yayi meye abin jin kunya? Ba gaskiya nafada ba, murza dan yatsanta yayi yasashi abakinsa yayi kissing dinshi kallon hanfa yayi madam yaushe zaki koma makaranta? Zan koma amma ba yanzu ba, kice zansha budiri na kafin kitafi murmushi hanfa tayi tace ai tunda ka warke nima gidanmu zan koma, kara matseta ajikinsa yayi yace nasan zanyi missing dinki dayawa amma ke ko damuwa dani ma bakiyi ba, shiru tayi aranta tace ai ina jin son danake yi maka kai baka yimin rabinsa dan ina sonka over, shiyasa abinda kayi min banji zafinka ba amma da ban sonka da Allah ne kadai yasan irin tsanar da zanyi maka, bakinsa taji akan goshinta ya hura mata iska a kunnenta tareda bushe mata idonta da iskar bakinsa tunanin me kikeyi? Babu komai kabarni natafi wurin inno dan Allah, zaki tafi amma sai munyi wanka kallonsa tayi kamar zatayi kuka dan Allah ka taimaka min kabarni natafi, daukarta yayi cancak ya nufi toilet da ita, ita dai duk ya takurata takasa sakewa dashi saboda kunyarsa takeji, shine yayi mata wankan bayan shima yayi yadauketa ya kaita tsakiyar gadon ya ajiyeta, dakyar ya barta tasaka kayanta ta tashi zata tafi rungumeta yayi wai baya son ta tafi tabarshi,lallabashi tayi yahakura ya barta, tana fara tafiya yabiyota tsayawa tayi ina zakaje kuma? Rakaki zanyi, ni basai ka rakani ba kabarni natafi meye naka na rakani salon aganmu tare ace wani abun mukayi, hannunta yaja yahadata da jikinsa to meye ke ba matata bace? Idan kina jin kunyar mutane su ganki da ni to sun kusa ganinki da katon ciki, murmushi tayi ko zasu ganni da katon ciki ba yanzu ba, yarinya naki wasane amma nidai nasan nabaki ajiyata abinda zance miki kawai ki kular min da baby, cikin sauri gami da tsoro tadago ta kalleshi dan Allah dagaske kake? Nidai nafada miki ai, hannunta tazare sai anjima tajuya tafita cikeda kunya, bin bayanta tafida yayi yatsaya yana kallonta har yadaina hangota lokacin data shige lungun momcy. [8:37PM, 11/28/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 8⃣7⃣ Na UMMI A'ISHA Yana nan tsaye yana murmushi hannuwansa cikin aljihun wandonsa faisal yazo ya tarad dashi sannu dan iska faisal yafada yana harararsa,wlh ka kusa barin dakin nan dan banga dalilin da zai sa ka rinka yimin abinda kaso aciki ba, murmushi tafida yayi yadan lashi lebensa wlh kaine dan iska kuma saurin me kakeyi dama ai nakusa barin dakin saboda nafi son nazauna da matata zama na dindindin amma koda yaushe ni atakure ita atakure, dariya faisal yayi yaro wannan karon sai dai kaje wurin mai martaba kai daya amma ni bazan rakaka ba, dariya tafida yayi haba abokina tare zamuje murmushi faisal yayi yaja hannunsa suka shiga falo. Hanfa nazuwa dakin momcy takwanta tafara shafa cikinta dagaske tafida yake har yabata ajiyarsa? Murmushi tayi inama a school nake da nayi test nagani idan hakane amma kuwa indai maganar tafida tazama gaskiya yazama sharp shooter daga yi sau 1 sai in samu ciki, haka tayita raya zancen acikin ranta ita kadai tana yi tana murmushi. Tun daga lokacin tafara shirin komawa disina tunda tafidan ya warke kaya aka harhada mata na alfarma tun daga kan wanda zatayi tsaraba har zuwa wanda yake nata, ana igobe zata tafi tashiga lungun inno babu kowa afalon dan haka takarasa cikin dakin nanma babu kowa sai tafida data hango yana kwance agadon inno yana bacci yana sanye da three quarter ja da bakar Riga,kallonsa ta tsaya yi ikon Allah da girmanka kazo ka kwantawa tsohuwa agado, sadaf sadaf ta karasa bakin gadon, hannunta tasa tashafi sumar kansa ta karkata kanta ahankali ta lashi lips dinsa, bude ido yayi kamar a mafarki yaganta hannunta dake kan kumatunsa ya dafa yaushe kika shigo? Yanzu nashigo naganka kana bacci, kallonta yayi yanzu tafiya zakiyi ki barni? Murmushi tayi kajika sai kace idan natafi natafi kenan, zaune ya tashi yakama hannunta yafara yi mata dabara wai zai taba babynsa yaji lafiyarsa, daga taba babyn kuma yafara yin sama kokawa suka fara dakyar tasamu ta kwace ta gudu. [9:03PM, 11/28/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 8⃣8⃣ Na UMMI A'ISHA Tana guduwa takoma dakin momcy nan ta zauna suka yita hira har dare yayi washe gari kuma tashirya faisal yadauketa sai disina tun ahanyarsu ta tafiya faisal yafara bata labarin cewa yana son kawarta zarah adan zaman da sukayi a asibitin nan har sun daidaita nanfa hanfa tashiga murna tayi fatan Allah yasanya alkhairi, karfe 1 suka shiga disina dayake basu tafi da wuriba ,suna zuwa gidansu hanfa iyayenta taresu da murna tareda bawa faisal kyakkyawar tarba, sai da yayi salla sannan yayi musu sallama yatafi nan kuma hanfa ta shiga maraicin mijinta da dokin ganinsa amma kusan koda wanne lokaci tana shafa cikinta tana kulada ajiyar da yabata. Satinta 2 da dawowa ta tafara shirin komawa makaranta wannan lokacin ma tafida babu abinda bai siya mata ba domin provision yayi mata nagani nafada komai da zata bukata sai da yasai mata ranar dazata tafi kuma yaturo su sarkin fada da babban zaginsa suka dauketa domin alokacin faisal yana yin wani aiki, katuwar mota Highlander baka mai bakin glass ya turo a ita aka dauketa yayinda ita kuma tayi shigarta cikin bakar doguwar riga da dan karamin hijab dayake tafiyar yamma tayi karfe 5 ta isa makaranta, tana zuwa hostel suka rungume juna itada zarah nan tashiga taya zarah murna domin tasan faisal yanada kirki ita da tafi ganin kirkinsa ma fiyeda tafida sai daga baya sannan ta fahimci shima tafidan yanada halin kwarai. ALHERI DANKO NE! 8⃣9⃣ Na UMMI A'ISHA Tunda tadawo bata ga tafida ba shima bai ganta ba sai dai waya da sukeyi awayar zarah yauma zaune take bayan sun gama wayar zarah ta kalleta wai mrs tafida anya kuwa? Dariya hanfa tayi meya faru mrs faisal san turaki? Kallonta zarah tayi kin ganki ne? Menayi? Wlh kinyi kiba kinyi kyau kuma kirjinki sun ciko tashi hanfa tayi taja doguwar riga tasa tace wlh zarah lafiyata lau kawai dai kibari acikin zuciyarta tace ai tafida ne bana wasa bane wlh duk dafin hannunsa ne yasani cikin wannan yanayin, kallon zarah tayi bari naje lab nadawo,fita tayi tana tafe tana tunani gwara yau nayi test dinnan nagani koda gaske cikin gareni, tana zuwa lab tayi test amma sakamako yana fitowa taga bata da juna biyu. [9:34PM, 11/28/2015] Ummi A'isha: Nan tadawo hostel cikeda murna domin tasan da dagaske ne da zata sha kunya duk da cewa ba haramun bane amma da kunya ace baka tareba kayi ciki, zama tayi agefen gado tafara kallon zarah wadda tayi hade hadenta na Karin ni'ima tana sha kallo kawai hanfa take binta dashi har tagama bayan tagama tadauko wani turare wai na matsi ne dariya hanfa tayi zarah kinada hankali kuwa? Meya faru? Kidaina shan wadannan abubuwan kijira kiga yadda faisal zai yi dake tukunna, kallonta zarah tayi malama barni nagyara nayi tsam, kada kai hanfa tayi nabarki amma nidai nan da shekara ma idan kika bani maganin matsi bazan yiba, saboda me? Saboda wahala zarah, zaro ido zarah tayi dan Allah hanfa dagaske da wahala? Dariya hanfa tayi ai zarah ki kaddara tunda kikazo duniya baki taba shan wata wahala wadda zakisha akan wannan abun ba, nidai tunda uwata takawo ni duniya ban taba shan wuya samada wannan ba shiyasa nayi mamakin yanmatan da suke iya bada kansu awaje, tsuru tsuru zarah tayi yau nashiga uku, ai zarah baki shiga uku ba sai ranar tazo, ni saboda tsabar wahala ana gamawa sai da na shanye babbar robar ruwa anan take, saboda tsabar wahala, tofa lallai wahala tayi wahala inji zarah, ai zarah wahalar ta isa wlh danni ranar kasa bacci nayi ga ciwon jiki shiru zarah tayi barni haka karkisa na sume dan Allah kyaleni haka dariya hanfa tayi tace zakiyi bayani. ALHERI DANKO NE! 9⃣0⃣ Na UMMI A'ISHA Yau tunda wuri tafida yataso daga office yataho wurin hanfa amma koda yazo bai samu ganinta ba yadda yakeso domin alokacin ma lecture takeyi haka suka gaisa aguguje ta tafi duk da haka yaji dadin ganinta domin yasameta da shigar da yace ta rinka yi haka yatafi yanata tuninta domin kwalliyarta tayi masa kyau sosai saboda jar arabian gown tasaka tayi rolling duk da bawata kwalliya tayiwa fuskarta ba da tunaninta daren ranar yayi bacci kamar yadda itama tayi bacci da tunaninsa. Washe gari takama juma'a tunda yaje office yaduba patients yanufi makarantar su hanfa lokacin dayaje yayiwa zarah waya yace ta turo masa ita nan hanfa tashirya taci kwalliya dama daga wanka tafito tasha turarenta na night feelings tasa doguwar riga tafita, tun daga nesa tahango motarsa kirar Mazda 6 ash colour mai bakin glass murmushi tayi wai kai wannan kowacce motarka haka take da bakin glass kamar wani barawo, motar tabude tashiga yana zaune yasha farar shadda wadda ta dau dinki irin nasu na masu rawani, ina yini? Tafada kanta akasa lfy maman baby, ya baby na? Murmushi tayi wlh babu wani baby acikina ni dayace, kallonta yayi ban yarda dake ba, tashin motar yayi yana cewa sai munje na aunaki fita sukayi daga cikin makarantar yanufi asibitinsu yana zuwa yace tafito tashiga office dinsa shi zaije round, office dinsa tashiga tazauna tafara kalle kalle oh tafida badai gayuba da daukar wanka, hutunansa manya guda biyu amanne ajikin bango daya yasha rawani da alkyabba daya kuma yasha blue colour din suit, tana nan zaune yashigo yace zaije masallaci yadawo, alwala yayi yafice ita kuma tayi sallarta a office dinsa tana nan zaune tana jiransa yadawo yadauketa ya nufi gidan shakatawarsa da ita, suna zuwa hanfa taji jikinta yafara rawa saboda tasan wuya yau za[truncated by WhatsApp] [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [1:04PM, 11/29/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 9⃣1⃣ Na UMMI A'ISHA Kallonta tafida yayi haba madam irin wannan rawar jiki haka sai kace kinga dodo dan Allah ki nutsu yau bazaki sha wahala ba, ita dai hanfa gaba daya tagama tsorata dashi lallabata yafara yi da haka yayi nasarar shiga jikinta amma fa ji tayi tafi shan wuya fiyeda ranar farko nan idonta yakumbura yayi hulu hulu, sai data sha kukanta sannan bacci ya dauketa tafida na ganin haka yatashi yashiga wanka bayan ya fito yasa kayansa yafita, momys kitchen restaurant & catering services yaje ya siyo mata abinci da drinks da ruwa mai sanyi lokacin daya dawo yasamu har ta tashi daga baccin tayi wanka tana daure da zani tana kwance agefen gado, cikin dakin ya karasa yana kallon fuskarta, sannu maman baby daurewa tayi tai murmushi ta tashi zaune takoma tsakiyar gadon ta zauna, abincin ya mika mata acikin robar take away fried rice da salad da soyayyen plantain agefe, karba tayi tafara ci ba ji ba gani nan tafida ya tsaya yana kallonta yadda take cin abincin babu kakkautawa, robar fresh yo yamika mata da strow ajiki tana karba tafara zuka har ta shanye, ruwa yasake mika mata nan shima ta shanye rabin roba, abincin taci gaba da ci shikuma tafida yaci gaba da kallonta, daina kallona tafada tana harararsa dauke kansa yayi daga kallonta har tagama cin abincin tana gamawa tadauki kayanta zata saka nan tafida ya matso yarike hannunta pls & pls ki barni nadan kara dan Allah kinji, cikin rudewa ta kalleshi yau nashiga uku dan Allah kayi min afuwa dan All.... Bata karasa ba yajanye zanin jikinta nanfa tashiga kuka sosai shidai tafida baya jin kukanta har sai da yasamu nutsuwa, dakyar tasamu ta tashi zaune duk idonta ya rine yazama ja ga muryarta tagama dishewa dakyar take fita, bani abinci naci tafada kwalla duk taciko idonta cikeda tausayawa tafida ya miko mata nasa take away din dama biyu ya siyo tana budewa tafara ci dasauri dan jin cikinta take kamar anyi mata yasa sai kace ta shekara bata ci abincin ba. [2:50PM, 11/29/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 9⃣2⃣ Na UMMI A'ISHA Kallonta kawai tafida yake duk tausayinta yagama cikashi ganin yadda taketa dura abinci acikinta kamar ba dazu tagama ci ba, miko min ruwa tafada tana kallon fuskarsa ruwan ya mika mata da robar madara guda daya, tana karba ta shanye madarar ta dau ruwan shima ta shanye taci gaba da cin abincin, cikin kulawa tafida yace kiyi hakuri kinji wlhi hanfa ban taba aikata zina ba kuma banida sha'awar aikatata shiyasa kika ga nakasa hakuri na kyaleki amma kiyi hakuri banida wacce zan kaiwa bukatata sai ke daya shiyasa, kallonsa tayi tagirgiza kai batace komai ba dan har acikin ranta bataji haushinsa saboda tasan idan ba gunta ba babu gun wadda zaije kuma ma azamanin nan samun mijin daya tsare Kansa kamar tafida ai sai an tona, shiyasa bataji zafinsa ba ko kadan tunda yatsaya ya tsare kansa alhalin yawancin mazan yanzu ba haka suke ba, hakuri yaci gaba da bata har tagama cin abincin, tashi yayi yashiga wanka yafuto yana fitowa yace tazo tayi itama, dakyar ta iya tashi yataimaka mata taje tayi wankan tafito tasa kayanta, takalleshi kazo mutafi, tashi yayi yawuce gaba tana biye dashi abaya amma dakyar take iya tafiya kasancewar yana gaba shiyasa bai lura ba, da suka fito ya tsaya awani restaurant wato ayshkaus restaurant anan yafita yashiga yasake yi mata siyayya yasai mata abinci da ice cream da snacks yadawo tun dataga ice cream din taji yawunta ya tsinke dasauri tadauka tafara sha kallonta tafida yayi sannu madam gaskiya daga gani kin wahala sosai nawahalar dake amma wlh bada niyya nayi ba kinga yadda kika koshi haka nima yadace nakoshi tunda daga yau ba lalle nasake daukoki ba sai wani lokacin kuma, harararsa tayi gashi nan ai kasa sai abinci nake taci kamar wata mayunwaciya alhalin kuma da ba haka nake ba banida cin abinci ko yaya naci ya isheni amma yau sai da nacinye take away biyu kuma duk manya takarasa maganar cikeda shagwaba, hannunta yariko to ai yanzu dole kirinka cin abinci dayawa fiyeda da saboda yanzu ku biyu ne da kuwa ke kadai ce, nifa nafada maka banida ciki, to naji bakida ciki dan sammin ice cream din naki kinga ni ko abinci banci ba, taya zaka ci abinci tunda kagama koshi, murmushi yayi gaskiya kam yau akoshe nake dam amma duk da haka ki dan sammin. [3:11PM, 11/29/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 9⃣3⃣ Na UMMI A'ISHA Acikin dan spoon din ta debo ta mika masa, dauke kansa yayi yamake kafada ni bana so, to wanne kake so ta tambayeshi, ni na bakinki nake so, murmushi tayi aranta tace tafida kaima fa fitinanne ne wlhi nagaske,diba tayi tace to bude bakinka sai nabaka ni nace miki na bakinki zan sha, dole babu yadda ta iya haka tadiba tazuba abakinta sannan tahada bakinta da nasa ta zuba masa haka yarinka yi mata wayo yana ta shan bakinta acikin dabara shi ala dole ice cream yake sha saboda yasan idan ta gane bakinta yake son sha bazata yarda ba gani zatayi kamar sake maimaitawa zaiyi tunda yanzu tariga da tagama gajiya, da wayo da wayo ya tsotsi bakinta son ranshi sai da yaga ice cream din ya kare sannan ya hakura ya kunna motar yanufi school of nursing, suna zuwa yabata kayan tareda yi mata kalaman soyayya masu dadi, yakare maganarsa da fadin i luv u my cwt heart murmushi tayi tace luv u too, dasauri ya kalleta dagaske kike? Kai tadaga yes i luv u too, murmushi tafida yayi nagode Allah yayi miki albarka, fita tayi daga cikin motar ta nufi hostel tunda yaga yanda take tafiya yaji hankalinsa ya tashi domin da alama yauma an kwatanta irinta rannan, haka yafizgi motarsa ya fita daga makarantar. Ita kam hanfa tana zuwa hostel ta tarar da zarah hannunta rikeda key point din chemistry tana karantawa kayan ta ajiye ta kwanta saboda tagama gajiya, sannu da zuwa zarah tafada tana kallonta yawwa sannu zarah dan Allah ki debo min ruwa atuka tuka ki dafa min zanyi wanka cikeda tausayawa zarah tace to ta tashi tadauki bucket taje tuka tuka tadebo mata ruwan tazo ta kunna gas tadora mata ruwan zafi, kallon zarah hanfa tayi ga abinci kizo ki dauka harda ice cream,a'a kifara yin wankan idan kika fito sai muci, ni na koshi zarah kici kawai tashi tayi tajuye ruwan zafin ta tafi bathroom domin yin wanka. [8:15PM, 11/29/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 9⃣4⃣ Na UMMI A'ISHA Shi kam tafida yana can zuciyarsa fes domin jinsa yake wasai sakamakon yau ya samu hanfa son ranshi, sai da daddare yasamu zarafin kiranta suka dan taba hira sakamakon bata jin dadi jikinta har wani zazzabi zazzabi take ji amma bata sanar dashi ba, kullum yana kiranta awaya suna hira amma bai san bata da lafiya ba,nan kuwa tana jin jiki sosai domin ko class bata fita saboda tafiyar ma wahala take yi mata shi dai tafida bai san wainar da take toyawa ba. Ranar laraba kawai da yamma ya shirya yatafi makarantar yana zuwa yahadu da zarah a area class amma bai ga hanfa ba anan yake tambayar zarah cikeda mamaki ta sanar dashi hanfa fa bata da lafiya tun ranar da ya zo yadauketa, hankalinsa yaji yatashi nan ya tura zarah taje ta taho masa da ita, koda zarah taje hanfa dariya tayi tace duk kinbi kin tayarwa da mijina hankali bayan ni kuma nawarke, wayasaki ki cemasa banida lafiya? Kallonta zarah tayi Allah ya baki hakuri, amin hanfa ta fada tazira doguwar riga suka fito, bakisa turare ba zarah tafada, babu turaren da zan sa balle yaji kamshi yakasa hakuri yaje yasake yi min jina jina, dariya zarah tayi mrs tafida kenan, lokacin da suka fito tun daga nesa tafida yake kallon tafiyarta babu laifi yanzu ta dan dawo dai dai amma ba yadda take ba, karasowa tayi tabude motar ta shiga ita kuma zarah ta wuce class, kallon tafida tayi sannu da zuwa,yawwa sannunki da kokari,murmushi tayi me nayi? Shiru yayi bai bata amsa ba wai adole yayi fushi,dauke kansa yayi daga kallonta,kallo tabishi dashi yana sanye da orange colour din riga da dark blue colour din jeans sai kamshi mai dadine yake fita daga jikinsa, hannunsa dake ajiye akan hand break ta kalla yatsunsa zara zara sai kyalli suke faratansa kuwa tamkar ya shafa musu lanfen fari. [8:44PM, 11/29/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 9⃣5⃣ Na UMMI A'ISHA Babban dan yatsansa na tsakiya ta kalla yana sanye cikin zoben azurfa mai kyau, ya daura agogon azurfa a hannunsa ahankali takai hannunta tadora akan hannunsa, wai me nayi maka tafada tana shafa hannunsa nan tafida yaji ta fara rudashi amma dai duk da haka baiyi magana ba, ci gaba da wasa da hannun sa tayi da hannunta, ka yi hakuri idan wani abu nayi maka, shine bakida lafiya amma baki fada min ba ko? Murmushi hanfa tayi takai masa kiss akumatunsa kayi hakuri ai na warke, ban hakura ba to me kake so nayi maka ka hakura? Nidai ban hakura ba kanta tadora akan kafadarsa dan Allah kar kayi fushi dani kasan idan miji yana fushi da matarsa tana rasa rahamar ubangiji tafada kwalla ta ciko idonta, jiyowa tafida yayi yarungume ta nibana fushi dake amma dai banji dadin abinda kika yi min ba dabaki fada min naji miki ciyo ba, ni ba ciyo kaji min ba, to me nayi miki? Ai nawarke shikenan, ban yarda ba yafada yana kissing din goshinta, kin san ma'anar sunanki? Eh babana ya taba fada min saboda tun ina yarinya har nagirma ban taba jin mai sunana ba shine na tambayi babana ya fada min, murmushi tafida yayi kajita yanzu ke din mecece idan ba yarinya ba? Wlh yanzu ni ba yarinya bace na girma, hannunta ya dan matsa nine nasa kika girma ko? A'a kai din da me kafini? Baki sani ba? Na mayar dake babbar mace yanzu, zoben hannunsa ta murza dama can ni nagirma, haka dai kika ce, zan fada miki fassarar sunanki amma sai a first night dinmu, wanne first night kuma? Bayan aikin gama ya gama, uhm waya fada miki? To meya saura? Ai ka rigada ka gama first night dinka tun jimawa kar ki kara fadin haka har yanzu ni saurayine, hmmm kai kam har yanzu saurayine amma ni kagama mayar dani bazawara, dariya tafida yafara yi sannan yace mata wlh kin bani dariya ai kema har yanzu budurwa ce, kafada ne kawai dan naji dadi amma ni kaina ajikina ina jin natashi daga budurwa, to tsaya yanzu yaya kike so ayi? Kawai ka fada min ma'anar sunana kadaina batun sai first night, to zan fada miki amma ba yanzu ba, to Allah yakaimu lokacin tafada tana saka dan yatsansa a bakinta, sai da suka karaci abunsu sannan tafida yay[truncated by WhatsApp] [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [6:11PM, 11/30/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 9⃣6⃣ Na UMMI A'ISHA Tun daga ranar tafida bai dawo makarantar ba saboda exam hanfa zata fara dan haka yayi hakuri ya kyaleta domin tasamu damar yin karatu, amma atakure yake da rashinta, sai dai kullum suna makale awaya, lokacin da zarah zata tafi gida ya aiki babban zaginsa yakai wa hanfa waya hadaddiya mai tsadar gaske nan suke wuni kullum suna hira har ta kammala exams dinta tafara shirin komawa gida aranar da zata tafi ma bashine yakai ta ba fadawansa ya tura suka dauketa suka kaita gida. Bayan tafiyarta da kwana 2 mai martaba yatura jakadiya takira masa tafida da faisal nan suka taso suka taho atare suna zuwa turakin soro yayi musu iso nan da nan fadawa suka fara zabga kirari, barkanku da zuwa samarin kirki sarki ya gaisheku, takawarku lfy gaba salamun baya salamun, cikin girmamawa suka shiga cikin fadar suka zube suka fara gaisawa, murmushi sarki yayi tareda yin gyaran murya, ibrahim, faisal Allah yayi muku albarka yayana, hakika ina alfahari daku acikin yayana musamman kai ibrahim domin ina sane da dukkan abin alkairan da kake yiwa iyayen matarka hakika naji dadi marar misaltuwa kuma hakan da kayi ya nuna min cewa nine na haifeka kuma dama tun farko nasan zabin da nayi maka zai zama alheri agareka shiyasa kaga na jajurce, shi mahaifin matarka yayi min alherin da bazan iya mantawa ba shiyasa nayi burin hada Zuri'a dashi saboda mutumin kirki ne sannan yasan yakamata, a matsayina na mahaifinku ina horonku da ku yawaita aikata ayyukan alheri arayuwarku domin shi ALHERI DANKO NE, sannan duk wanda ka yiwa alheri bazai manta ba mutukar ba butulu bane,magana ta biyu kuma itace nan da sati uku za ayi shagalin bikinku kowa akai masa matarsa, godiya sukayi tareda fadin Allah ya tabbatar da alheri, nan suka taso suka fito kowannensu fuskarsa dauke da murmushi, shi dai tafida duk da mai martaba bai fada masa alherin da baban hanfa yayi masa ba yasan alherin mai girma ne nan yaji soyayyar hanfa tasake ratsa shi. [7:12PM, 11/30/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 9⃣7⃣ Na UMMI A'ISHA Shirye shirye aka fara domin gudanar da shagalin bikin amma tafida yafi kowa zumudi ita kanta hanfa har mamaki yake bata sai kace bai santa a matsayin ya mace ba saboda komai cewa yake sai a first night dinsu zai fada mata. Masu gyaran jiki da kunshi da gyaran gashi aka dauko takanas daga garin nijar nan suka shiga gyara hanfa ciki da waje kafin kace wani abu tuni kamaninta sun sauya jikinta yayi sulbi da taushi gamida laushi har wani santsi yakeyi duk da cewa bawai kalarta ce ta canja ba tana nan a bakarta mai duhu amma tayi kyau, tun daga gashin kanta har kafarta sai da aka wanke aka yi mata jan lalle mai kyau, ga gyaran fuska da aka yi mata, yayinda itama gimbiyar faisal zarah tana can ana gyarata, tsakanin tafida da hanfa wayace amma tun kafin ya ganta yabi ya gama rudewa kamar wadda za akwace masa ita. Yauma hanfa zaune take a makeken falon gidansu kasancewar tafida yabawa babanta gidan da yagina a gonarsa kuma gidan babba ne gashi yasha kayan alatu, daga ita sai daurin kirji gabanta da kaskon turaren wuta tana turara jikinta da turare mai kamshi Wanda ni kaina ummi Aisha sai da naji kamshin ya ratsani, wayarta ce tayi kara murmushi tayi tun kafin ta daga domin tasan tafidane yau tun safe bai ber kunnenta ya huta ba, hello munib tafada ahankali, gaskiya ni ban yarda ba ki canja min suna, dariya tayi kabari sai nazo gidanka sannan zan canja maka sunan, murmushi yayi to shikenan ai saura kwana biyu, dariya tayi anjima zan kiraka, haka suka gama wayar suna cikeda shaukin juna. Washe gari aka zo aka dauki hanfa daga,nanfa ta shiga kukan rabuwa da iyayenta duk kuma sai taji hankalinta ya tashi duk da irin son da take yiwa tafida,dakyar aka banbareta daga jikin mahaiyarta, kuka take kamar me har aka sata a mota, momcy ce tafara lallashinta kiyi hakuri kinji hanfa kowacce mace dole sai haka ta faru da ita hakuri zakiyi dakyar tayi shiru da haka sukaje garin misau nan taga garin yacika dam da mutane babu wurin masakar tsinke, cikin gidan aka wuce da ita kai tsaye dakin momcy aka kaita nan aka zaunar da ita, basu jima da zuwaba sai ga zarah ma an kawo ta nan ta danji sanyi, momcy da kanta ta kawo musu kayan karin ni'ima tabasu wadanda yawanci an hadasu da madara ga kazar amare, dakyar hanfa ta iya ci domin har yanzu kuka take dama dama zarah ita tayi shiru koda aka kawo musu abinci hanfa kasa ci tayi. [7:33PM, 11/30/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 9⃣8⃣ Na A'ISHA (UMMI) Karfe biyu daidai momcy tashigo musu da kayan da zasu sa domin za ayi musu cuda wato bikin al'adar da aka saba gudanarwa indai ana biki agidan sarki, wata mata aka kawo mai kwalliya wadda ta tsara musu kwalliyarsu ta daukar hankali pink din leshi suka saka da gwaggwaro pink da takalmi shima pink sai yar karamar jakar hannu ga gwalagwalai da aka zuba musu tun daga wuyansu har abin hannu, fito dasu aka yi aka kaisu inda za agudanar da bikin wanda iya matane suka halarcin wurin nan da nan masu kidan kwarya suka fara kida suna rera waka, inda aka tanadar musu aka kaisu suka zauna tuni aka fara gudanar da cuda abin gwanin sha'awa sai turare kuyangu suke fesawa awurin nan aka gama aka mayar dasu cikin gida, tunda tazo bata ga tafida ba asalima rabonta dashi tun lokacin dayaje wurinta a makaranta, shi kam tafida yana can bakinsa har kunne sai washe hakora yake za akai masa hanfa gida, gashi yana son yaganta amma yana kunyar shiga cikin gidan saboda yasan acike yake da mata, daki yashiga yadauko iPhone dinsa ya kunna yafara lalubo hotunan da yayarsa daso ta daukar masa na hanfa dan takanas ya bata yace ta dauko masa hotunan hanfa har agama bikin, nafarko yafara gani tana gyara agogon hannunta ta sunkuyar da kanta lokacin acikin dakin momcy ne, wani yasake budewa shi kuma tana yiwa zarah magana sai na uku lokacin har anje gurin cudar, haka yayita kallon hotunan nata kwalliyarta tayi bala'in yi masa kyau komai pink murmushi yayi hanfa kenan komai nata mai kyaune, fuskarta yaci gaba da kallo ajikin wayar duk hotunan babu wanda bai yi masa kyau ba amma yafi ganin kyan wanda ta tsaya afilin rawa sai dai da alama ba rawar take ba, murmushi yayi hanfa tanada kunya yasanta yarinyace mai kunya gata da ganin girman nagaba da ita ya tabbata zasu yi rayuwa mai dadi da ita. Washe gari aka fara shirin tafiya daurin auren faisal da zarah wanda za a gudanar agarin disina, tafida shine akan komai har akaje daurin auren aka dawo lokacin karfe 2:30 ana dawowa aka fara shirin tafiya hawan dawakai da za agabatar wato (kilisa). [8pm, 11/30/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 9⃣9⃣ Na UMMI A'ISHA Yauma kwalliya aka tsarawa su hanfa cikin wani tsadadden material wanda kudinsa nikaina ummi ban san adadinsu ba amma naga sai kyalkyali suke kalarsa golden yasha ado sosai, gwaggwaro coffee colour aka sa musu da takalmi da yar jaka duk kalarsu coffee colour, sarkarsu itama golden ce da abin hannu da warwaro, motoci aka kawo aka daukesu cikin wata jibgegiyar jeep kirar Toyota, suna zuwa wurin ga kujeru nan an tsarasu kowannesu an tanadar musu wurin zama ita da angonta wato jama'a kyan da hanfa tayi a wannan rana abin ba acewa komai tayi kyau nagaske, suna nan zaune an kunna wakar "lokacinkine amarya yar amana........ Aure ibada ne" ga kawayensu yan makarantarsu sai zuwa suke kasancewar zarah tayi inviting dinsu, shiru hanfa tayi tanata kallon jama'a sai hada hada suke yayinda kawayensu suke zuwa suna ta daukar hoto da ita wasu kuma suna daukarta ita daya, anan nan anata gudanar da bikin sai ga tawagar angwaye akan dawakai nanfa wuri ya rude da guda daidai lokacin aka sauya waka aka kunna wakar "Ran rabuwa ake yin kuka inna da baba sai watarana ku yafen dukkanin laifina zan tafi dakin aurena" hanfa ji tayi kamar ta fashe da kuka amma ta daure sai dai duk da haka kwalla taciko idonta, kallon wurin tayi yakayatu mutuka harta decoration din wurin coffee & golden ne kalar shigarsu itada zarah, daidai lokacin ta hango tafida yana saukowa daga kan dokinsa yana sanye da shadda light brown yasha rawani da alkyabba, hannunsa rikeda sandar sarauta yanufo mazauninsa, dauke kanta tayi daga kallonsa har ya karaso yazauna shima faisal yaje ya zauna, yana zama yaji kamshin turarenta da humrar data shafa sun taru sun cika masa hanci ga wani kyau datayi kamar aljanna lallai sai yau ya yarda da maganar bature da yace black is beauty & unique, idan kana son ganin kyau na hakika to ka kalli bakar mace,kallonta yayi amma sai yaga ta dan rame, hannunta ya kama yafara murza yan yatsunta su kuwa masu video camera da masu hoto sai daukarsu sukeyi tunda suka zauna, ahankali yace maman baby ya naga kin rame? Bakya cin abinci ko? Murmushi tayi babu komai,to meyasa kika rame? Ni ban rameba tafada cikin shagwaba to ki kwantar da hankalinki kinji, nasan abinda kika saka aranki har kika rame, murmushi tayi batace komai ba tana jinsa yanata wasa da yan yatsunta sai shafa kunshin hannunta yake amma koda ta kalli su faisal sai taga su abin ba haka yakeba ko kusa da zarah bai jeba balle ya tabata, kallon tafida tayi tace kaga fa mutane sai kallonmu sukeyi. [5:06PM, 12/1/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 1⃣0⃣0⃣ Na UMMI A'ISHA Murmushi tafida yayi ya matsa yatsun hannunta dakarfi yace to meye? Su kallemu mana and so what? Cigaba da murza yatsun hannunta yayi har aka gama program din aka tashi, tundaga lokacin duk inda ka leka a social ntwk babu abinda zaka gani sai hoton tafida da hanfa an rubuta Tafida & his beautiful wife hanfa@ hawan angonci day, kar kuso kuga comments da likes da suka rinka samu,nikaina ummi A'isha sai da abin ya burgeni har nayi comment, can nahango yan uwana marubuta suma sunyi comments babu adadi. Bayan an tashi daga taron ne aka fara shirye shiryen kai amare gidan mijinsu bayan sunsha tsume tsume, da misalin karfe 9 aka daukesu aka nufi gidajensu dasu wanda ke girke a unguwar new G. R. A, manyan gidaje ne guda biyu ajere komai iri daya kuma tacikin gidan anyi kofa wadda zata sadaka da daya gidan batare da kafito kabi ta gate din waje ba,kowacce gidanta aka kaita, tunda yan kaiwa amarya suka tafi hanfa take sharbar kuka har tafida yashigo ya sameta yana sanye cikin farin yadi da hula, gefen gadon yaje ya zauna yadago kanta wai kukan nan da kike tayi na menene? Shiru tayi ta tsagaita da kukan da take, hadata da jikinsa yayi yafara rarrashinta ni sai nake ganin kamar dan zaki zauna danine kike kuka ko bakyaso mu zauna mu 2? Bayan da a takure muke daga ni har ke, yau kuma tunda gani gake ai sai mu godewa Allah saboda wannan ranar ta yau is d most important day to you, me and all our fans, more than all days that past in our life, hanfa you are d love of my life, my life without you is just like a tea without sugar, i love you with all my heart, hannunta yakama domin kunshin hannunta yayi masa kyau, kitashi muyi salla batayi musu ba ta tashi tashiga toilet tayi alwala tafito, alwalar shima yayi yafito sukayi salla raka'a biyu bayan sun idar ya dauko musu kayan da yashigo dashi wadda ya hada da kaza da kayan motsa baki da fruit da drinks masu sanyi, dakyar hanfa ta yarda taci kazar tasha fresh milk, kallon tafida kawai take duk sai wani zumudi yake mata, wai zumudin me kake yitayi haka? Ko ka manta kai bawani ango bane na kuzo ku gani, murmushi tafida yayi wlh dokinki nake kuma zumudinki nake saboda tunda na dandani zumarki nakasa samun nutsuwa banida buri illa na kasance dake, tashi tayi tahau kan gado ta kwanta aranta tana cewa dokin me zakayi bayan ni ba budurwa bace, sai da tafida yagama cin kazarsa sannan ya shiga wanka,yana fitowa yafesa turarruka masu dadi ajikinsa sannan ya hau kan gadon. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [7:28PM, 12/4/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 101 Na UMMI A'ISHA Inda hanfa take ya karasa yashiga jikinta ya rungumeta tsam tsam ajikinsa kamar wadda za akwace masa ita, ahankali hanfa tace dan Allah kabarmu yau muyi bacci tunda ka riga da kasan komai kagama abinda zakayi,acikin kunnenta yasa bakinsa yace kece kike ganin haka hanfa amma to me wlhi wannan ranar tanada mutukar muhimmanci agareni kuma kece kike ganin kamar nagama komai dan haka yau basai na kulaki ba the thing is not like the way you think it, i will show you how much i luv you this night, kafin tayi magana yahada bakinsa da nata yafara kissing din bakinta tareda fara kokarin cire rigarta ta hanyar laluben zip din rigarta, nan yashiga rudu kasancewar jin laushin da fatarta ta sakeyi ga kirjinta ya cika dam fiyeda da, nan yafara shafarsu yana wasa dasu duk yagama rikicewa ita kam hanfa dama tasan dole ayi haka saboda yadda aka tsumata, tafida dai zautuwa ne kawai baiyi ba dan jin hanfa yayi babu maraba da ranar daya fara saninta a matsayin mace take yashiga yi mata surutai marassa kan gado, tajigata tasha wahala sai wurin 4 nadare ya barta nan tashiga tunani oh wannan wahala ta isa, ni dai tunda ake abinnan wahala nakesha, wannan wahala dayawa take ko sai yaushe zanji dadi? Kankameta tafida yayi ajikinsa nan bacci ya dauketa saboda tagama gajiya shikam tafida baiyi bacci ba tashi yayi yashiga toilet yayi wanka yazo ya kwanta nan shima baccin ya daukeshi sai da asuba tayi sannan ya tashi yayi salla amma bai tashi hanfa ba sai karfe 7:sannan tasamu ta tashi duk jikinta a mace kanta tadauke bata kalli tafida ba tashiga toilet tayi wanka tafito tazo tayi salla tana idarwa tatashi takoma gadon tana cewa munib ina kwana, lfy my sugar baby murmushi hanfa tayi kajika ko? Kallon fuskarta yayi kwanta kiyi bacci sugar baby rungumeta yayi tsam tsam ajikinsa yana kissing din goshinta. [7:31PM, 12/4/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 102 Na UMMI A'ISHA Baccine ya daukesu wanda yake cikeda nishadi da annashuwa sai wurin 11 sannan hanfa ta tashi tajanye jikinta ahankali tayi kissing din kumatunsa tatashi ta shiga toilet tayi wanka tafito ta shirya ta tsara kwalliyarta cikin wata yar doguwar riga mai hannun shimi ja bata da nauyi tafitar da shape din jikinta, ta fesa turare masu kamshi, sai alokacin ta kalli dakin nata sosai wanda yasha Italian bed light blue komai na dakin light blue ne har fentin, falo tafita ta lalleka yanda fasalin gidan yake daga nan tadawo dakin inda tafida yake lokacin ya bude idonsa, hannu ya mika mata cikeda kunya ta karaso tashiga jikinsa kiss yafara bata tako ina yana shakar kamshin jikinta wanda yayi mutukar ruadashi, gashin kanta yafara shafawa,ahankali tace kaje kayi wanka kaji, um um nidai kece zaki yimin yafada cikeda shagwaba dariya hanfa tayi tasake kamkame shi nanfa yafara yi mata salo wadda babu yadda ta iya dole sai da ta biye masa suka lula, wurin 12 suka shiga wanka suka cudi junansu sannan suka fito suka shirya, sabuwar kwalliya hanfa tayi cikin material kore mai kyau wanda yayi mata kyau tayi kwalliya sosai tasha turare shi kuma tafida kananan kaya yasa thee quarter da bakar riga, hannunta yakama suka fito falo nan taga breakfast jere akan dining table, har kan table din yajata ya zaunar da ita asaman cinyarshi, abinci ya zuba musu soyayyiyar doya da kwai da farfesun kaji da kunun shinkafa ga wainar shinkafa da miyar agushi da kayan tea, abaki yafara bata har ta koshi hannunta ya kama sugar baby nima bani abincin kinji, diba tafara yi tana bashi a baki wani lokacin idan ta bashi sai yaki sakin hannun nata ko ya dan cijeta da haka tagama bashi, daukarta yayi yakaita cikin falo ya ajiye ta akan carpet ya kwantar da ita ajikinsa hannunsa yasa acikin rigarta yafara laluben na shanunta ganin rigar jikinta zata rage masa jin dadi yasashi janye zip din rigar hannunsa hanfa ta rike, munib kabari mana dan Allah ka kyaleni haka nahuta, ni wankan nan ya isheni haka, rigar yacire ya dora bakinsa akan dukiyar fulaninta yafara wasa dasu da harshensa haka ta kyaleshi har yagama sha'aninsa sannan ya rabuda ita, wunin ranar nan tafida bai iya koda leka kofar gida ba. [7:34PM, 12/4/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE! 103 Na UMMI A'ISHA Sai bayan sallar la'asar sannan tafida yabarta tayi wanka ta shirya cikin blue din shadda dinkin doguwar riga tasha daurin dankwali mai kamada gwaggwaro tafesa turaren night feelings da unforgettable me ta nufi dakin tafida, agefen gadonsa ta sameshi yana zaune ya nutsu yana waya dagaji da mai martaba yake wayar, hannu ya mika mata alamun ta isa gareshi, ahankali ta shiga jikinshi tazauna shafarta yafara har yagama wayar, hannunta yakama zo muje na nuna miki yanayin gidan naki, tashi tayi yajata jikinsa yasakalo kunkuminta ya riketa suka fita babban falo ne guda daya da manyan dakuna guda biyar kowanne yasha Italian bed wani royal bed wani Europe bed wani kuma Dubai bed, kowanne daki fasalinsa daban, tsakar gida suka fita wanda yake wawakeken gaske ga wurin packing din motoci nan tamkar kamfanin saida motoci ne, ta bayan dakunan kuma swimming pool ne da dan karamin lambu domin shakatawa, lambun yajata suka shiga anan tatsaya kallon yadda wurin ya tsaru, kan wata farar kujera yajata suka zauna ya kwantota jikinsa yafara sinsinarta kallonsa tayi dan Allah kayi hakuri abban baby, dariya tafida yayi yanzu kin yarda ke maman baby ce? Um nayarda tunda daga jiya zuwa yau nasan nazama maman baby, hannunta ya kama yafara wasa da yan yatsunta nan hanfa tafara tunanin kawarta zarah ko yanzu awanne hali take, Allah sarki zarah yanzu kema nasan kinji yadda naji ranar farko,tsotsar da tafida yake yiwa bakinta ne ya katse mata tuninta, maman baby za akawo miki kuyangu wadanda zasu rinka tayaki aiki yafada yana kissing din wuyanta, ni bani son masu aiki dakaina zan rinka yin aikina in yaso kai sai kana tayani dana waje, da girman kujerarki yafada yana murmushi. [7:38PM, 12/4/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 104 Na UMMI A'ISHA Hannunsa hanfa ta rike tashi muje ciki na huta wlhi nagaji, tashi tafida yayi,murmushi tadan saki kaga kafata gyara min takalmi na babu musu yaduka ya rissina yafara gyara mata dalaf ta haye bayansa kaini daki, riketa yayi yamike dama wayo ashe kike son yimin ko? To bari muje dakin sai na rama, kwantar da kanta tayi abayansa haba mijina nakaina yau dai kayi hakuri kabarni nayi bacci kaji, gaskiya bazan iyaba saboda ni da zarar naji kamshin nan da kikeyi mai dadi sai nakasa jurewa, daidai lokacin suka shiga falo nan ya direta akan kujera thee sitter ya haye jikinta, mutsu mutsu tafara amma babu yadda zata iya, akunnenta ya rada mata yau zan fada miki ma'anar sunanki hanfa, sunanki yadace dake manan baby domin sunane mai daraja kuma kema kinada daraja,murmushi tayi tashafo sumar kansa kadaina fasa min kai kawai kafadi abinda kasani gameda sunana, hannunta ya rike yagyara kwanciyarsa ajikinta lokacin dana ganki hanfa na rude na nemi nutsuwata narasa gaba daya kin sauya min tunani saboda tunda nake ban taba jin so ba sai a kanki ban taba tsintar kaina cikin shauki da zazzafar soyayyaba sai akanki alokacin da naga kyakkyawar fuskarki saura kadan zuciyata ta buga saboda tsaruwar halittarki babu shakka hanfa you are very beautiful among d beautifully, you are so cute and pretty, akanki nagane bakar mace itace mace nidai ke kadai kin isheni rayuwa saboda kece mahadin rayuwata, wani unexpected kiss yaji hanfa ta bashi a goshinsa kamar wadda yake jira ya rukunkumeta yafara bata zafafan kiss a kowanne sashe na fuskarta, dakyar ta dakatar dashi tace to ai baka fada min ba har yanzu, kansa ya kwantar akan kirjinta yaci gaba da cewa alokacin danaji ke kurma ce kuma bebiya nayi tsananin tausaya miki ganinki kyakkyawar yarinya amma babu ji babu magana, kuma alokacin dakika ce naje na nemo ma'anar sunanki wlh aranar naje na nemoshi. [7:40PM, 12/4/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 105 Na UMMI A'ISHA Ranar banyi kwanan farin cikiba saboda lokacin dana zo domin sanar dake sunan aranar natarar da bakya nan ashe cikin hikima ta ubangiji ke matata ce halal malak, i love you hanfa, i really love you, ma'anar sunanki kuma yasamo asaline daga sunan matar sayyidina isma'il (AS) hakane? Kai ta daga hakane domin haka babana ma ya fada min, to kinga ashe sunanki yanada mutukar daraja kamar yadda kike da daraja kafin tayi magana taji ya hade bakinta da nasa. Daren ranar ma haka hanfa ta kasance cikin ciwon jiki domin ko kadan tafida bai iya saurara mata ba nan tsoro yashigeta saboda tunanin dawainiyar tafida akanta, washe gari tunda wuri ta tashi tafita tafara gyara gidanta, da falo tafara tagyarashi fes ta shiga kitchen tafara ciro kayan da zatayi amfani dashi, dama daga ita sai yar karamar rigarta mai kamada shimi milk colour shara shara da dan karamin gajeren wandonta iya cinya, flaks da dishes tafara cirowa saboda dasu zatayi amfani, caraf taji hannun mutum akan kirjinta tana jiyowa atsorace taga tafida tsaye yana yi mata dariya daga shi sai gajeren wando fari da farar best ta maza, duka takai masa ya goje, shine zakazo ka tsorata ni ina aikina? Am sorry my sugar wife aikin nima nafito na tayaki to kuma sai naga bamu gaisaba da abubuwana ba, juyawa tayi taci gaba da aikinta Allah yashirye ka dai sam bakajin kunyata, murmushi tafida yayi ina jin kunyarki mana shiru tayi ta kyaleshi saboda tasan idan ta biye masa bazai barta tayi aikin ba, fita tafida yayi zuwa harabar gidan da kansa ya sasshare mata tsakar gidan yazo kitchen din ya sameta lokacin tana soya kwai har takusa kammala hada breakfast din duk gidan ya gauraye da kamshi abayanta tafida ya tsaya ji yake kamar ya rungumeta amma kuma tana aiki, ci gaba da tayata aikin yayi har tagama bayan tagama ta debo kayan ta jera akan dining taja hannunsa zo muje muyi wanka amma idan naga zaka wuce gona da iri fitowa zanyi na barka. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [12:51PM, 12/8/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 106 Na UMMI A'ISHA Jan hannun tafida hanfa tayi zuwa dakinta inda ta shiga toilet ta hada musu ruwan wanka suka shiga sukayi suna fitowa ta shiryashi cikin blue din trouser da bakar t shirt ta fesa masa turaren active man ita kuma ta shirya cikin wani leshi pink colour tagyara fuskarta tasha kwalliya tasa jan janbaki tayi jagira tafesa jikinta da turare takafa daurin dan kwali sannan taja hannun tafida wanda ke zaune yana aikin kallonta kamar wadda ya samu tv, falo takaisu suka hau kan dining table ta zuzzuba musu abincin tahaye kan cinyarsa tafara cin abincin tana fadin muci, kafada ya make um um nidai kece zaki bani abaki, murmushi hanfa tayi tadiba tafara bashi shima yana bata, katuwar lauma tadebo ta saka masa abaki, hadawa da hannunta yayi yacijeta ahankali tasaki yar kara, haka suka gama ciyar da junansu har suka koshi, makalkaleshi hanfa tayi karage cin abinci kaga nauyinka yayi yawa gashi sai kiba kakeyi, waya fada miki abincine yake sani kiba? To meye yake saka? Daukarta yayi cancak ya nufi dakinsa da ita yana fadin muje na nuna miki abinda ke sani kibar, akan gadonsa ya direta ya shige jikinta kece kike sani yin kiba sugar baby, murmushi tayi oh ashe ni kake tsotsewa kai kana kiba ni ina ramewa ko, bakinta ya tsotsa yafara kokarin cire rigarta, nan ya shiga romancing dinta karar wayarsa ce ta katse masa hanzari ahankali yasaketa ya nufi inda wayoyinsa suke yana dubawa yaga mai martaba ne yake kiransa shida faisal suje su sameshi agida, jiki asanyaye yaje inda hanfa take kinga mai martaba ne ke kiranmu murmushi hanfa tayi to meye abin damuwa kaje ka dawo zan yi maka babban tanadi murmushi tafida yayi yaja hancinta dagaske? Daga masa kai tayi dagaske mana, kajita kamar gaske sai nazo kuma zata fara cewa kayi hakuri dan Allah wlh da zafi, murmushi hanfa tayi to dai ka shirya kaje ko faisal ya rigaka zuwa, kinga kuwa kwana 2 banga abokina ba, wasu kayan hanfa ta dauko masa shadda fara kar da farin takalmi da hula tabashi yasa yafesa turare yayi kissing din bakinta yafita, bayan sa tabi tana fada masa zata shiga wurin zarah anjima, har bakin gate ta rakashi sannan ta koma gida. [1:18PM, 12/8/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 107 Na UMMI A'ISHA Bayan tafiyarsu ne hanfa tashiga wurin zarah, tana shiga ta tarar da ita zaune afalo acikin kujera tana ganin hanfa ta tashi ta rungumeta tana murna, zama hanfa tayi tana cewa kaga amarya murmushi zarah tayi ai wlh kibari kawai abin babu sauki mrs tafida, dariya hanfa tayi jikinki ya fada miki kenan? Wlh hanfa da wahala abun yadda kika san na daure kayana nagudu gida haka nakeji, dariya hanfa tayi ai wlh zarah sai dai hakuri kawai nidai har yau kullum sai nayi kuka in yazo nakasa sabawa har yanzu kuma nakasa daina jin zafi yabani maganin har ya hakura yadaina bani, to Allah yabamu da sauki zarah tafada, nan suka jima sunata hirarsu har azahar tayi sannan hanfa tayi mata sallama ta tafi gidanta. Tana komawa tafada kitchen tadora girki ta shirya jallop rice with salad tayi farfesun danyen kifi ta zuzzuba acikin flasks tajera akan dining sannan ta zubawa zarah taje ta kai mata tana dawowa ta shiga wanka tafito tayi salla ta shirya cikin wata riga da skirt na english wears,rigar kalarta coffee mai hannun shimi da babban botir guda daya agaban rigar daga kirji sannan ta matse ta sosai ta bayyana surar jikinta skirt din kuma iya gwiwa ce baka itama takamata hips dinta sun fito ainun, bakin dan kwali ta daura akanta tafesa turarruka da humra kala kala tayi kwalliya a fuskarta sannan ta fito falo tana fitowa tafida yana shigowa dagudu taje tafada jikinsa ta rungume shi tafara kissing din bakinsa, fuskarsa, goshinsa da kumatunsa, hannunsa takama zo muje karage kayan nan kazo kaci abinci, kayan jikinsa ta cire masa ta barshi daga shi sai best fara da dogon wando, dogon wandon yafara kokarin cirewa tarike hannunsa dan Allah kayi zamanka haka ni idan naganka daga Kai sai gajeren wandon nan tsorata nake murmushi tafida yayi yajata suka koma falo akasa kan carpet ta sauko musu da abincin nan tafida yafara yi mata santi yana bata labarin mai martaba dasu inno har suka gama cin abincin suna gamawa yajata jikinsa yadauketa zuwa dakinsa agadonsa ya direta yakai hannu yacire botir din dake gaban rigar tata nan yafara wasa da albarkatun kirjinta. Sai da komai ya lafa sanan tafida yashiga wanka yafito lokacin bacci ya dauke hanfa kamar yadda tasaba duk lokacin da aka gama, zama yayi agefenta ya jawo remote ya kunna tv yakamo tashar kwallo yafara kallo, yana kallo yana duban kyakkyawar fuskar hanfa, ahankali ta bude idonta ta kalleshi, jikinsa tashige ta rungume shi sai kuma tafara hawaye dasauri yafara tambayarta menene? Kankameshi tayi dan Allah kar ka rabu dani tafida, kar kayi min irin halinku na maza ka juya min baya, kar kamin kishiya dan Allah, harshensa yasa akan kumatunta ya fara lashe hawayen dake gudu akan kumatunta kar ki damu sugar baby ke kadai kin isheni rayuwa kuma i promised you bazan yi miki kishiya ba zan zauna dake ke kadai har karshen rayuwata. [1:41PM, 12/8/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 108 Na UMMI A'ISHA Hanfa najin haka ta kalleshi kayi alqawari? Nayi miki alqawari yafada yana shafar dukiyar fulaninta rungume shi tayi tafara kissing dinsa, tasa harshe tafara lasar kowanne sashe na jikinsa shidai tafida duk tagama ruda shi, kunya ta ajiye agefe tashiga nuna masa soyayya sosai sai da la'asar tayi sannan ta iya kyale shi, wanka suka shiga sukayi suna fitowa tafida ya fita masallaci ita kuma tayi sallarta agida. Haka zaman tafida da hanfa ya kasance cikin nunawa juna soyayya da kauna,bayan bikinsu da sati 2 tafida yakoma office amma kullum shine yake share mata tsakar gida ya gyara mata dakunan barcinsu sannan ya tayata shirya breakfast sai sun gama komai sai ya shirya ya tafi office ita kanta hanfa tana mamakin irin wannan saukin kai na tafida, satinsu uku da bikin takoma makaranta, motoci guda biyu iri daya mai martaba ya basu ita da zarah saboda zuwa makaranta, yanzu kullum dakanta take driving zuwa sch taje ta dawo. Yau tunda akayi sallar asuba tafida bai kyaleta ba sai da yagama tara mata gajiya sannan ya barta, dakyar ta tashi tafita kitchen tashiga ta dora girki tafara shirya musu breakfast tafida ne yashigo kitchen din ya rungumo ta tabaya maman baby sannu da aiki, murmushi hanfa tayi ni ba yanzu zan haihu ba sai nagama school, dariya tafida yayi yadora kansa akan kafadarta zancen yaushe kuma yarinya, ai kin riga da kin makaro dariya hanfa tayi ban makaro ba wlh tunda har yanzu..... Cikin sauri yasa hannunsa ya rufe bakinta wlh kar ki kara magana saboda gaba daya alamun shigar ciki sun bayyana ajikinki kiga yadda hips dinki ya bude, kirjinki yakara cika kamar me shayarwa, wannan kuma ai kaine ka mayar dani haka, kaine ka budani nazama haka,dariya tafida yayi to ayi aiki lafiya, fita yayi yaje compound din gidan yafara gyarawa yana gamawa yakoma bedrooms dinsu duk ya gyaggyra lokacin hanfa tagama shirya breakfast tajera akan dining, ruwan wanka tahada musu suka shiga sukayi suka fito, shi tafida ya hade cikin bakaken suit ita kuma tasa arabian gown yellow,breakfast sukayi sannan tafida yafita office ita kuma tashiga wurin zarah daga can suka wuce school. [5:18PM, 12/8/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 109 Na A'ISHA (UMMI) Hakan zaman tafida da hanfa yayita gudana cikin son juna da tattalin juna har watanni suka shude kwanaki suka tafi, yau tunda wuri hanfa ta tashi bayan tagama koduwa a hannun tafida, kitchen ta shiga tafara kiciniyar hada musu breakfast yayinda shi kuma tafida yana can yana gyara musu bedrooms dinsu sai da yagama sannan ya fita tsakar gidan yafara shasshare shi, ita kam hanfa tunda tafara fasa kwai taji zuciyarta tafara tashi haka tadaure tafasa tahada ta kada tafara soyawa nan da nan taji zuciyarta tana tashi cikinta yahau juyawa dasauri tadauke kaskon ta nufi dakinta da gudu ta shiga toilet tafara sheka amai kamar zata amayar da kayan cikinta lokacin da tafida yashiga kitchen din ya tarar bata nan ga gas yanata ci, sai da ya kashe gas din sannan yabita dakinta a toilet yajiyota tanata aikin sheka amai dasauri yabita cikin toilet din ya riketa har ta gama aman ta kuskure bakinta, a kafadarsa ya daukota ya kaita kan gado ya kwantar da ita, bargo taja ta lulluba saboda sanyi taji tana ji kamar me,nan tafida ya rude ya fara yi mata sannu dasauri ya fita yaje ya dauko first aid box dinsa yazo inda take ya zuko allura asirinji ya yaye bargon data rufa tana ganin allurar tafara kuka nan suka shiga kokawa, dariya tafida yafara kinjiki matsoraciya to ranar da zaki haihu yaya zamuyi? Hawaye tafara taki yarda lallashin duniyar nan yayi taki yarda matseta yayi ajikinsa wata kara ta callara da sauri ya hada bakinsa da nata ya kankameta yajanye rigar jikinta ya soka mata allurar nan tafara fusge fusge amma bai barta ba sai da yayi mata allurar, kwanciya tayi tafara nishi daga nan kuma bacci yayi awon gaba da ita, rigarta tafida yadaga yafara shafa cikinta da rabon dai hanfa zaki haifa min yara ysfada yana kissing din cibiyarta. Ta jima tana bacci kafin ta tashi tana tashi tafida ya matso me zakici maman baby? Fuska ta yamutsa ni babu abinda nake son ci zobo kawai zaka samo min nasha, to bari naje nadawo yafada tareda fita ya nufi dakinsa kayansa yasa yafita cikin gari yaje ya siyo mata zobo mai sanyi jarka hudu yadawo gidan lokacin da yadawo har tayi wanka tana daure da towel, kusa da ita yaje to ga zobon na kawo miki, hannu ta mika masa alamar yabata tasha, bari ni zan baki da kaina janta jikinsa yayi yafara zuba zobon abakinsa yana hada bakinsa da nata yana zuba mata da haka suka shanye jarka daya shida ita, tun daga lokacin lafiya ta yiwa hanfa wuya ga uban amai da takeyi komai taci sai ta amayar amma har yau takasa fadawa zarah tana da ciki saboda kunyarta take ji. [5:52PM, 12/8/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 110 Na UMMI A'ISHA Hanfa ce kwance acikin kujera a falo shi kuma tafida yana kitchen yana soya mata plantain, falon ya kawo mata ta tashi tafara ci sai data cinye tafara sheka amai shi kanshi tafida sai data wankeshi da amai, rigar jikinta ya cire mata yafara gogge mata jikinta nan ya tsurawa na shanunta ido ganin yadda suka cika suka kara girma take yaji ranshi ya biya, daukarta yayi yakaita toilet yayi mata wanka shima yayi yadaukota yakawota daki nan kuma yafara nuna mata bukatarshi tureshi tafara yi tunda kayi min cikin basai ka kyaleni ba tafada cikin shagwaba sorry sugar baby kinga ai nayi hakuri fa dawayo da komai yashiga jikinta. *********************** Cikin hanfa ya girma haihuwa ko yau ko gobe gashi tunda aka kawota bata taba zuwa disina ba har yau, komai nata tafida ke yimata hatta wanka da wanki shine yake yi mata, cikin dare ta tashi da ciwo cikin kankanin lokaci ta haifi jariranta tagwaye guda biyu duk maza nanfa tafida yafara murna, gari yana wayewa yan uwa da abokan arziki suka yita xuwa ganin jariran hatta mai martaba yazo ya gansu shida su inno anan inno take cewa hanfa gida zata tafi ayau sai tayi 40 zata dawo, nan kuma tafida yace bai san zancen ba babu inda hanfa zataje, fada inno ta rufe shi dashi ta shiga hadawa hanfa kayanta ita kanta hanfa bata son tafiya tabarshi amma bazata iya cewa inno a'a ba, haka aka debi hanfa da jariranta sai disina nan itama nata iyayen suka shiga murnar ganinta, tunda ta tafi bai kirata ba dan fushi yake wai meyasa zata tafi bada izininsa ba, ko disinan ma yaki zuwa sai faisal ne yake zuwa amma shi fur yaki yaje sai dai duk abinda ya taso faisal yaje hatta sunan jariran ma faisal ya fadawa yace yayi musu huduba da umar da Aliyu wato hydar da faruq. Ranar suna anyi shagali sosai inda yara suka ci suna hydar da faruq, shi dai tafida yana can kadaici yana damunsa tunda su hanfa suka yi arba'in yake zuba idon ganinsu amma shiru har sukayi watanni 3 dole ya ajiye fushinsa ya nufi disina yana zuwa iyayen hanfa suka karbeshi cikin karramawa,bayan sun gaggaisa ne aka nuna masa dakin da hanfa take, tashi yayi yashiga dakin tana kwance tana bacci ta dora hydar akan cikinta shi kuma faruq yana kan kafafunta dukkaninsu bacci suke da alama kuma sun dade suna baccin, akusa da ita ya zauna ya tsura mata ido tana sanye da jar atamfa mai ratsin baki ajiki tayi dan kwalliya a fuskarta kuma ba laifi ta zama katuwa saboda tayi kiba kirjinta ya cika sosai, hydar ya dauke daga kan cikinta ya kwantar dashi agefe ya dauke faruq din shima ya kwantar dashi agefe, ahankali yadaga rigarta ya kwantar da kansa acikinta, bude ido tayi kamar a mafarki taga tafida yasha shadda ash colour da hula sai zuba kamshi yake, hannunsa takama yaushe kazo? Nazo kinata bacci murmushi tayi yaranka ne suke hanani bacci da daddare yaran ya kalla tamkar yayi kaki ya ajiye saboda tsananin kamarsa dasu, ayya sorry baby yafada tareda hayewa jikinta duk kamshin jikinta yagama rudashi kamar ba mai jego ba sai kamshi mai dadi take itada yaran hatta dakin kamshi yake (Sabanin wasu matan da idan suna jego hatta gidansu karni yake dan Allah mata mu kula) kallonsa ya maida kan yaransa an saka musu kaya iri daya pink din riga da blue din jeans, kansa ya tura cikin rigar hanfa saboda duk kamshinta ya rikitashi, batayi niyyar hanashi ba saboda itama tayi missing dinshi. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:19PM, 12/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 111 Na UMMI A'ISHA Yan yatsun hannun tafida hanfa ta murza yadai? Tafada tana kallonsa bai bata amsa ba ya tura kanshi cikin rigarta ya fara lasar cibiyarta, murmushi hanfa tayi tashafo sumar gashin kansa tace ya hanya? Shiru bai bata amsa ba domin duk ta gama tafiya da hankalinsa, ita kanta yatafi da imaninta saboda kamshin turarensa kadai yakashe mata jiki, hydar ne ya motsa ya callara kara cikin sauri tafida yatashi ya daukeshi ya mika mata shi, tashi kiyi feeding dinsa nagani, tashi zaune tayi ta zuge zip din rigarta takarbeshi ta fara kiciniyar shayar dashi, cikeda sha'awa tafida ya zuba ma kirjinta ido tareda kai hannunsa yafara lallatsa su, sugar baby haka kika dawo? Murmushi tayi eh haka kuka dawo dani kai da yaranka, a'a baby kinyi kyau ne dayawa fa, kiga kirjinki kamar ba shayarwa kike yi ba, uhm kadaina zugani dai, Allah dagaske, yaushe zaki dawo ne? Kinga har yarana sun girma dan Allah kudawo haka, hannunsa takama tasaka cikin nata abba yace next week zan dawo, kiss yabata akan lips dinta yawwa baby gara ki dawo kinji kinga gidan yayi min girma ni daya, hydar ta mika mishi ta dauki faruq shima tafara feeding dinsa, rungume hydar yayi ajikinsa yana kallonsa komai na yaron irin nashi ne babu ta inda ya barshi, wani son yaran yaji yana ratsashi shi dai hanfa ta gama yi masa komai, Allah ya raya min ku yarana yafada yana kissing din goshin yaran, tana gama feeding din faruq ta ajiyeshi tafara kokarin zuge zip din rigar, rike hannunta tafida yayi haba maman baby ni kuma fa? Da sauri ta kalleshi abincin yaran? Sorry baby dan kadan zaki sammin kinji, pls & pls baby, nidai ka bari sai nadawo,yanzu haka zan tafi? Sorry nawan tafada tana kissing din hannunshi nan yaji tasake rudashi, hydar ya mika mata ya dauki faruq shima ya saka masa albarka ya ajiyeshi ya kalleta ni zanje na tafi saboda naga idan na zauna za ayi abin kunya agidan nan dan kin gama rudani, ranar friday zan turo su sarkin mota su daukeku, rungumeta yayi itada yaran dan ji yake kamar kar ya tafi ya barsu, haka yayi mata sallama ya tafi yana cikeda kewarsu itada twins dinsa. [9:19PM, 12/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❕ 112 Na UMMI A'ISHA Tunda tafida ya tafi ya fara shirin karbar hanfa gaba daya gidan ya sake mata komai sabo tun daga kan furnitures har fentin gidan komai yadawo sabo kamar gidan amarya, itama hanfa acan gyara kanta tayi tafito ral da ita tayi kunshi tagyara gashinta, ranar juma'a kamar yadda yace ya tura aka debosu, lokacin da tazo gidan baya nan yana asibiti dan haka wurin zarah ta shiga ta ajiye yaran tafada kitchen ta dora delicious, fried rice tayi da farfesun hanta wanda nidai ummi A'isha sai da naji yawun bakina ya tsinke, bayan ta gama hafa komai ta dauka takaiwa zarah daga nan ta debo yaranta, tana zuwa tayi musu wanka ta shirya su itama tayi tashirya cikin body hug ja da bakin wando kirar fela, takama gashin kanta da jan ribom, sai da ta turare gidan da kanta da daddadan kamshi tukunna tazauna a falo tana jiran zuwan tafida domin yaranta tuni sunyi bacci. Karfe 3 daidai tafida yashigo gidan shida faisal, kallon faisal tafida yayi malam bafa ciki zaka shiga ba muyi sallama tun daga nan kashiga gidanka dan yau ni angone, dariya faisal yayi to agaida amarya nagode, zataji tafida yafada tareda shigewa gida, yana shiga ya hangota zaune cikin kujera das da ita tamkar budurwa yar 19 tsayawa yayi yana kallonta tana juyowa suka hada ido ya tsuke cikin bakin suit, tasowa tayi tazo ta shiga jikinsa tana magana a hankali sannu da zuwa abban dady, kasa magana yayi ya cafki bakinta yafara tsotsa tuni itama tafara mayar masa da martani, ganin tsaiwar zata gagaresu yasata kama hannunsa zuwa bedroom dinsa suna shiga yajata kan bed, ya kwantar da ita ya fara sinsinar ta rike shi tayi ka zo kaci abinci, bazan iya ba yafada acikin kunnenta kece kika yi min alqawari so karki hanani pls, wannan ai salon rowa ne zaki saka wannan kayan, cire kayanta yafara dasauri dasauri nan yashiga nuna mata zallar so, sai dai ita hanfa ji tayi kamar ranar farkonsu dan dakyar ya iya shiga ga wani radadi da takeji, shi kam tafida washar dashi dan ji yayi hanfar Sa tadawo sabuwa fil. Bayan komai ya gama wanzuwa ne tafida yatashi yashiga wanka yana cikeda annashuwa yana fitowa yanufi dakinta acan yaga twins dinsa sunata mutsil mutsil alamar sun tashi daga bacci. [9:19PM, 12/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❕ 113 Na UMMI A'ISHA Faruq ya fara daukowa yakai shi wurinta inda take kwance tana bacci sai gumi take duk kuwa cewa dakin akwai ac, ahankali yahau kan gadon yakwantar da faruq kusa da ita yadauki breast din yasa masa abaki sannan yakoma dakin ta yadauko hydar sai da faruq yakoshi sannan ya daukeshi ya sawa hydar shima,yaran suna koshi suka koma bacci daidai lokacin ita kuma ta farka daga baccin, kallon tafida yayi idonta jajur duk jikinta ciwo yake yi mata gashi ji take ko tafiya bazata iya yi ba, zanyi wanka tafada ahankali daukar ta yayi yakaita toilet yahada ruwan zafi yayi mata wanka dakyar ta iya taka kafarta tadawo daki, tana dawowa tawuce dakinta ta kintsa tasa riga da skirt na atanfa fitet batayi wata doguwar kwalliya ba tadawo dakinsa zo muje kaci abinci danni yunwa nakeji sosai,tashi yayi daga shi sai gajeren wando sukaje falo dakyar take tafiya suna zuwa ya kwaso musu abincin ya kawo kan carpet ya ajiye yafara zuzzuba musu nan tafara ci kamar zata hadiye har kwanon, kallonta tafida yayi sannu baby,batayi masa magana ba har sai data koshi gaskiya abban baby baka bina ahankali koda yaushe da karfi kake yi min, kiyi hakuri ba laifaina bane, kan kujera tahau tamike Shi kuma yafara cin abincin yana gamawa yadauko magani ya bata. Tsakanin tafida da hanfa zamane suke yinsa na kaunar juna da soyayya, yaransu sun girma sunyi wayo yanzu watansu 9 amma idan ka gansu zaka zaci sun shekara daya dan suna gudunsu ko ina itama hanfa yanzu tafara shirye shiryen gama school, lokacin da zata yi final exam hostel tafida yabarta takoma dan tasamu damar fuskantar karatunta, tana gamawa tafara laulayi lokacin watansu hydar 10 anan tafida yace ta yaye su, kuka hanfa tafara wai ko hutawa batayi ba zata fara wani laulayin? Ita dai ya cire cikin nan bataso tana haihuwa kusa da kusa, cikeda mamaki tafida ya kalleta baby kin san kuwa abinda kike fada? Cikin nawa ne bakya so? Kodai kin daina sonane? Haba hanfa wannan fa itace kadai hanyar da zaki nuna min soyayya, kuka taci gaba dayi nidai gaskiya acire, rungumeta tafida yayi yafara tsotsar bakinta kiyi hakuri hanfa ina son yara sosai musamman ma wanda suka fito daga cikinki, duk wadannan kalaman basu yi tasiri agun hanfa ba gaba daya ta birkice masa ita dole sai yacire cikin, tun yana lallashinta har yayi fushi ya fara balbaleta da fada bazan cire cikin ba kema ai malamar lafiya ce dan haka kina iya cirewa da kanki, yana gama fadin haka ya fice daga dakin yaje ya harhadawa su faruq kayansu ya daukesu yakaisu gidan mai martaba wurin inno. [9:19PM, 12/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❕ 114 Na UMMI A'ISHA Tun daga wannan lokacin zamansu ya canja kowa ba ruwanshi da dan uwansa, ko girki yanzu hanfa batayi saboda cikin nata mai laulayi ne danma inno takawo mata masu aiki guda biyu wanda suke yi mata aiki, cikin nata yanzu yashiga wata na 4,tsakaninta da tafida sai dai ido. Yau takama juma'a tana zaune a falo tafida yashigo yana sanye da farar shadda da hula, yana rikeda faruq da hydar wanda kana ganinsu kaganshi sak shine, yaran sunyi bulbul suna sanye da kaya iri daya bakar riga da bakin wando, da gudu sukaje suka dale jikinta shi kuma tafida ya wuce dakinsa, surutu suka fara yi mata wai mai martaba yabasu doki, dariya tafara to ku kun iya dokine? Mun iya mana momy, haka suka yita mata surutu babu laifi ganinsu ya sanyaya mata zuciyarta, daren ranar ajikinta ta rungumesu suka yi bacci saboda yanzu dakinta take kwana tafida ya dauke mata kafa ita kuma bata bishi ba. Washe gari da kanta tayi musu wanka ta shirya musu breakfast sukaci shi kam tafida sarkin zuciya ko abincin gidan baya ci, tana zaune a falon daga ita sai wata yar shimi ja tadaura zani kanta babu dan kwali cikinta yadan fito su hydar suna zagaye da ita, sallama akayi aka shigo kallon mai sallamar tayi itace taje duba tafida lokacin da yayi accident, dagudu su faruq sukaje suka rungumeta suna cewa oyoyo anty, ciki ta shigo ta zauna tana dariya yakuke yarana? Daurewa hanfa tayi tai mata sannu da zuwa tareda kwallawa mai aiki kira tace ta kawo mata abin motsa baki, ina abbanku? Bakuwar ta tambayi yaran, daddy yana daki dagudu faruq ya nufi dakin tafida ba ajima ba sai gasu sun fito tare yana sanye da thee quarter iya gwiwarsa da body hug maroon, daga gani bacci yake kuruciya karara a fuskarsa kamar saurayi dan 27,baby bacci kakeyi ne? Bakuwar tafada tana murmushi shi kuma dan yabawa hanfa haushi yace ah yau sweety nace tazo bakya yi min waya ni nazo? Kusa da ita yaje ya zauna kamar wadda zai shiga jikinta,yakike? Lfy baby yau hutawa kake kenan, eh wlh ina gida yau, murmushi tayi baby ina ne dakin nawa kasan ni bana son kananan dakuna dan nafi so nasake nida yarana, yaran naki har nawa zaki haifa? Babu adadi har sai kaji sun isheka sannan zan daina haihuwa, anya kuwa zaki iya a wannan dan karamin cikin naki? Yafada yana satar kallon hanfa wadda tacika tayi fam, kai ai kasan ba anan takeba tafada tana dariya, tashi hanfa tayi tashiga dakinta saboda tagaji da wannan cin fuskar. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:19PM, 12/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❕ 115 Na UMMI A'ISHA Tana shiga daki tafada akan gado tafara kuka marar sauti, sai da tayi mai isarta sannan ta tashi ta leka falon lokacin nana ta tafi, window ta bude ta leka, tafida ta hango tsaye shida bakuwarsa ta dafa motarta su kuma su hydar sun kwasa da gudu sun nufi gidan faisal wurin zarah, tana nan tsaye har tafida yazo ya wuceta ya shige dakinsa, bayansa tabi zuwa dakin ta sameshi kwance rigingine kansa ta fada ta shiga jikinsa sai kuma tafara kuka, jiyo da ita yayi takoma kasa shi kuma yana samanta, baby menene? Cikin kuka tace bakai bane, ok to naji nine kiyi shiru stop crying my dear! Shiru tayi takalli fuskarsa yasaita fuskarsa kan tata numfashinsa yana sauka akan tata, hanfa! Yakira sunanta, na'am tafada ahankali, akwai abinda na rageki dashi a zamantakewarmu? Kai ta girgiza, to tunda na sauke nauyin ki kiyi hakuri zan kara aure, shiru tayi bata amsa ba jin haka yasashi dagowa ya kalleta, asume yaganta bata motsi dagudu yaje yasamo ruwa ya kwara mata amma bata farfadoba, agurguje yazira mata doguwar riga ya dauketa yakaita mota daga nan ya nufi asibitinsu da ita, yana zuwa yakaita anternatal, take yaga tafara zubar da jini da alama cikin jikinta zai samu matsala, anti miscarriage yayi mata guda biyu (allura) take bacci ya dauketa shi dai duk ya gama rudewa yana ganin tayi bacci yafara kaiwa da komawa, sai da tayi awa daya tana bacci sannan ta bude idonta tana budewa tafara surutai marassa kan gado, dama nasan dole yayi aure tunda ni yanzu yadaina sona bayan kuma shine ya tsofar dani da ba haka nake ba, tun ranar da yafara kusantata yafara nuna min mugunta dakarfi ya rinka shigata babu irin ciwon da bai Jimin ba ranar ashe so yake ya gama dani ya auro wata, ko ba ranar ba ni duk lokacin da zai zo min dakarfi yake zuwa min haka lokacin da yaje ya daukeni a makaranta wuyar da ya bani ko tafiya kasawa nayi, wlh idan cikina ya zube sai ka biyani, kallonta kawai tafida yake cikeda tausayawa dama yawancin mata idan akayi musu wannan allurar to daga sun farka surutai zasuyi tayi duk abinda ke cikin zuciyarsu sai sun fada ranar,wata allurar yasake yi mata take bacci yayi gaba da ita, oh yanzu da badan mu kadai bane adakin nan ai da hanfa tagama bude mana sirrinmu yafada acikin zuciyarsa. Ta dan jima tana bacci sannan ta tashi, cikinta tashafa cikina ya zube? Jikinta ya matsa yakai bakinsa jikin kunnenta cikinki ko cikina? Cikinki bai zubeba amma da kin kusa yi mana asara, ki kwantar da hankalinki hanfa bazanyi auren ba kiyi hakuri kinji, kuma wlh bada mugunta nake zuwa miki ba halittarki ce haka duk lokacin da nayi fiyeda kwana 5 ban kusanceki ba sai ki hade ki sake komawa kamar budurwa shiyasa idan nazo kike shan wahala ni kaina sai nayi dagaske kafin na iya budewa hanyar, kanta ta dauke duk kunya takamata ita me ya kawo wannan maganganun saboda bata san tayi surutan nanba dazu. [9:19PM, 12/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❕ 116 Na UMMI A'ISHA Kansa ya dora akan kirjinta, hanfa kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki, jiyowa tayi wai ni meya faru? Badai kace aure zakayi ba to ai ban hanaka ba amma sai dai kar ka manta kayi min alqawari alokacin da kake tsaka da cin amarci alokacin da kake ta tawa, alokacin da nake budurwa lokacin ban haihu ba wani abu bai ragu ajikina ba, lokacin ban zama haka ba, bakinsa yakai kan nata wannan dalilin yasa tayi shiru, hannunsa yazira cikin rigarta ya dora hannunsa akan brest dinta guda daya, duk kushena bazance wannan ya zube ba kamar na budurwa yake kuma kema kina komawa budurwar, dakyar ta samu ta zame hannunsa amma bai yarda ba saida ya gama jagwalgwalata sannan ya barta ko ya manta agadon asibiti suke oho. Wurin karfe 4 ya dauketa suka tafi gida tun daga lokacin suka shirya komansu yadawo normal, yanzu zamansu har yafi nada armashi soyayya suke nunawa junansu bil hakki da gaskiya da haka har ranar haihuwarta tazo ta haifi yan tagwayenta mata masu kamada tafida, ranar Suna tafida ya kashe kudi kamar bai san zafinsu ba,an radawa yara sunan inno da momcy ana kiransu mama da mami, wannan karon tafida cewa yayi babu wankan da zataje gida, bata yi 40 ba zarah itama ta haifi yaronta namiji aka sa sunan mai martaba. BAYAN SHEKARA 15 Sanye take cikin wani tamfatsatsen leshi mai kyau baki tasha gwalagwalai a wuyanta da kunnenta sai kamshi take zubawa, falo ta fito babu kowa, a filin wasa tajiyo hayaniyarsu bakin window taje ta tsaya ta daga labulen ta leka tafida ta hango shida faruq da hydar da dan autanta faisal (little) sunata buga kwallo murmushi tayi ta zubawa tafida ido har yanzu yaki tsufa kullum yana nan tamkar saurayi, little ta hango yana yiwa faruq magana kallo tabishi dashi lallai kyan da ya gaji ubansa domin komai nasa irin tafida ne yanda tafida yake magana dakyar shima haka yake duk da shekarunsa 13 aduniya, tana nan tsaye ta hango faisal shima yafito jan tafida yayi abokina nifa unguwa zanje kallonsa tafida yayi har yau baka daina iskanci ba? Dariya faisal yayi yanda kadaina shan ganye haka nadaina neman mata, dariya tafida yayi ya wuce gida [9:19PM, 12/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 117 Na UMMI A'ISHA Cikin gida ya shige daga shi sai farin short nicker da farar riga ta yan ball suma yaran nasa duk wannan shigar sukayi,yana shigowa ya hangota tsaye tana kallon yaransu ta window, bayanta yaje ya rungumeta akoda yaushe son hanfa yake ji yana shigarsa sosai gata dai haihuwarta uku yaranta biyar amma har yau bata gundurarsa, cak ya dauketa a kafadarsa yayi cikin dakinsa da ita dariya tafara yi wai kai baka girmane? Kan gado suka fada yafara yi mata wasanni masu rikitarwa yana fadin ta yaya zan girma bayan har yanzu ni yarone, dole ta biye masa suka lula sai da suka gurji junanau sannan sukayi wanka suka fito, kwalliya suka sake tasaka yellowar atamfa shi kuma yasa orange colour da blue din wando yace kizo muje ki rakani, fitowa sukayi yabude mata gaban mota tashiga shima ya shiga suka fita daga gidan, can karshen gari yakaisu inda ya gina wani katon asibitin yara da mata, ya tsaru mutuka an gama komai an zuzzuba duk abinda za a bukata ajikin symbol din asibitin an rubuta, Dr Tafida & his Lovely wife female, children hospital, wani dadine ya kama hanfa ta rike yan yatsunsa nagode abban baby to amma waye likitan? Hannunta yakama ni dake mune consultant din fata dai Allah ya bamu nasara, amin tafada tana kissing din bakinsa haka suka dawo gida cikeda farin ciki, suna dawowa gida tasake ganin abin mamaki domin tafida ya shirya musu bikin cika shekaru 15 da aure haka suka sha bidiri aka watse bayan taro ya tashine da daddare hanfa tafito daga wanka tana daure da towel tafida yashigo dakin, kugunta ya rike yace shekaru goma sha biyar da suka wuce zaki iya tuna abinda ya faru? Idonta ta rufe yes natuna abinda kayi min adakinku agidan su inno, bakinsa ya hada da nata yana cewa kin kasa mantawa da ranar nan kamar yadda nima nakasa mantata hakika na yarda ALHERI DANKO NE. ALHAMDULILLAH! Anan nakawo karshen labarin Alheri dankone duk wanda yayi min editing ban yafe ba. Na sadaukar da wannan littafi ga mai girma TAFIDAN GUMEL, HAKIMIN YALAWA ALH IBRAHIM AHMAD M SANI, Allah yaja zamaninka amin. Lots of luv babbar yaya ADDA BENAXIR OMAR Gaisuwar ban girma ga uwar dakina HAWWA M JABO Gaisuwa ga baby faty & sady kawata Ban manta dakuba Falmi, halamcy & momy adama hakika nasan kuna sona Babbar kawa kuma aminiya KAUSAR LUV still u r d 1 & only ina sonki kawata Allah yabarmu tare amaryar umar faruq Nagaisheki Anty bebeelo kinfi kowa son alheri dankone Fatan alkhairi ga takwarorina, da yan uwana marubuta musamman ma yan taskar marubuta Hakika masoyana babu abinda zance daku sai dai godiya, duk mai son novel din ummi A'isha ko mai kaunarta to ummi A'isha loves you too, ina gaisheku daukacin masoyana aduk inda kuke, anty meenah dan musa ummi ta gaisheki! Nagode sai mun hadu a littafina nagaba nice taku ahar kullum UMMI A'ISHA!. www.gidannovels.blogspot adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *