Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Thursday, February 9, 2017

Aliyu haydar complete

adsense here  .ALIYU_HAYDAR Page ((1)) ©Kausar M Hassan Bismillahi Rahmani Raheem! "Alhaji dan darajar Allah kayi hak'uri ni bansan laifin da nai maka ba, mai ya kawo maganari saki"??? Cewar yar matashiyar matan dake tsaye a gaban wannan dattijon, wadda ta kasance ita ba fara ba ita kuma ba baq'a ba, shekarunta bazasu wuce 30 ba. "Hajiya na fad'amaki cewan na' sakeki saki daya saboda hka idan Allah y baki miji kiyi aure" Yana gama fad'in yaja rigarsa fuuu y wuce. Kai kawea ta girgizah saboda tasan tabbas mutum baya tab'a wuce kaddararsa, hakan yasa ta koma d'akinta ta tattara kayanta a cikin jaka ta had'a ta dau mayafinta ta fito, zuciyanta cike da k'una da bakin ciki, tana kawowa tsakiyan gidan d'anta na dawowa dga makaranta, jakar makarantar shi ya yarda akasa, da gudu ya isa gareta. "Mame tafiya zamuyi ne naganki da jaka a hannu"? Rage tsayenta tai dea2 nashi tasa hannunta ta dafa kanshi "Aliyu ba tafiya zamuyi ba, nidea zan tafie, kuma a nan zan barka, ina mai maka nasiha da kazama namiji, kazama mai hakuri da juirya akan duk abunda zai biyo bayanka" "Mame dan Allah kada ki tafie ki barni, wallahi zan rik'a jin magana, bazan k'ara fasa kwano ko d'aya a gidan nan ba, zan rik'a share ko ina, mame dan Allah". Rungumeshi tai tana zubar da hawayen rabuwa da d'anta, wanda yake shine sanyin idaniyanta. "Aliyu ni wnnn duk baya damuna, ko wanne yaro haka yake, hasali ma ni kullum addu'ah nake maka akan Allah ya shiryaka, nasan kuwa Allah zai amshe addu'ahta" Gyaran muryan da tajine ya katsie mata zancen da takeyi "Kai zubairu amso min yaron chan" ya fad'a murya a fusace. Zubairu dake kusa dasu, yasa hannu yana raba uwa da d'anta. Zubairu ya amsheshi, hajiya ta juya ta nupie kopan dake fita gidan. "Mame dan Allah ki dawo kada ki tafie, mame!!!". Haka ta fice ta barshi a gidan zuciyoyinsu cike da tarin bakin ciki mara misaltuwa... Like · 3 · Reply · Report · Jul 29 Kausar M Hassan ALIYU_HAYDAR Page ((2)) ©Kausar M Hassan Ganin baida mafita sea ta Allah, yasa ya cigaba da huci kaman wani sabo zakin daya fito neman abunci, hannun zubairu ya garzawa cizo, wnda hakn yay sanadiyar sakinshi da zubairu da yay, da gudu y haura gidan saman, ya bud'e wani d'aki wnda da alama wannan shine d'akinshi, banka kopar yay ya maida y kulle da padlock ya hau kan d'an karamin gadonshi ya kwanta ya cigaba da kuka. Alhj baiji dad'in kasantuwar hakan ba, shi kanshi baisan maisa yay hkn ba. Cike da tak'aicin abunda ya aikata y kama hanyar shiga d'akinshi. Wata mata na hango fara tas da itah, iya inda akeso mace takai to ta kai, sanye cikin dogowan riga bak'a tasa dan k'aramin hijab, da baqaqen takalmi, chewing gum ne a bakinta tana tauna DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009Karas_karas. Ganin Alhj da tai yasa taja ta tsaya chack kaman gunkin da aka ajiye. "Alhj ina hajiya salma"? Shiru yay jim kad'an tukkuna ya nisa "Na saketa hajjah rabi, kuma nace idan ta samu miji to tayi aure. Kirji ta daka cike da nuna rashin jin dad'i fal a fuskanta "Haba Alhj dan Allah, kayi hkuri ka dawo da ita mana mai yay zafi haka shi ba wuta ba"? A fusace ya bata amsa "Kinga na gama magana, kuma bana so a k'ara dawomin da ita farko" Zatayi wata magana ya ra6ata ya wuce, kai ta girgizah tukunna ta qaraso tsakar gidan, ganin jakar Aliyu da tai yasa ta tabbatar da cewan ya dawo dga makaranta. "Zubairu!!!" Hajjah ta hau kiran sunanshi Jiki na rawa ya amsa kiran da take masa "Na'am hajiya gani" ya karaso kusa da ita cikin ladabi. "Aliyu y dawo dga makaranta ne"? "Eh hajjjah ya dawo" "Yana inane"? "Yana d'akinshi hajiya" Alama tai masa da hannu wadda ke nuna cewan ya wuce, da sauri y kama hanya y bar falon. Hajjah rai a 6ace ta hau gidan saman, dai_dai d'akin aliyu taja ta tsaya, a hnkli ta fara kwan_kwasa kopar. Aliyu daya riga ya hasala ya fara magana "Wanene"? "Aliyu nice mamanka ka bud'e kopan nan" "Nifa ummi bazan bud'e ba sea abbi ya dawo min da mame" Shiru tai tukkuna ta qara cewan "Ka bud'e d'ana zan maka komai kake so kana so kasa mamanka kuka ne, kasan idan bana ganinka bana jin dad'i' Cikin muryar shagwa6a ya bud'e baki "Ummi zaki hana anty nana ta daken" "Na maka alkawari bazata kara dukanka a gabana ba kaji aliyuna jan gwarzo zakin fama, ka bud'e dakin". Tasowa yay ya bud'e dakin, da gudu ya fad'a jikin ummi, ummi ta rungumeshi sosai, a jikinta ya matuqar bata tausayi har a cikin zuciyanta" "Yi shiru d'ana ka deana kuka, ga umminka nan tare dakai, zan baka dukkan gatan da mame dinka ke baka kaji ko"? Kai ya d'aga tare da cewan "To ummina" Murmushi tai masa taja hannunshi zuwa d'akinta. Tana isa ta tarar da nana zaune a d'akin, cike da hasala ta taso akanshi "Ummi ya zaki shigo mana da yaron nan a d'aki sarai kinsan bayajin magana ynxn nan zai fara fasa mana kaya" "Ke"! Ummi ta daka mata tsawa "Bana son iskanci da d'iban albarka, ke kinsan da ya nai renonki ne, kowanne yaro haka yake, kurciya ce idan yay ta kuma zata wuce, komai lokacine" Nana ta dubie aliyu ta dubie ummi "Naji ummi amma gskya nifa... "Kefa mi? Bazaki zauna da d'an uwanki lpy bane? Tsaya kiji wallahi nai maki iyaka da yaron nan, fice ki bani guri' Baki ta tunzure ta kama hanyar fitah dga d'akin, yayinda ummi ta juya ta dubie Aliyu "Kada ka damu kaji d'ana mamanka na nan tare dakai" Mujie in baka chocolate" Murmushi yay ya saki ranshi, suka wuce chan kuryar dakinta Yayinda Nana tai d'akinta ta maida ta kulle, zuciyanta nai mata k'una sbd ita a duniya ta tsani aliyu, bata sonshi ko kad'an a cikin rayuwanta... Meye dalilil"?... DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ALIYU_HAYDAR* Page ((3)) ©Kausar M Hassan A chan bangaren hajiya salma kuwa tana fitah dga gidan kai tsaye taxi ta tsayar tasa jakarta a ciki. "Malam mai taxi unguwar shanu zaka kaini" "To hajiya" Suka kama hanya sea unguwar shanu, suna isa dea2 kopan gidan da zata shiga ta tsayar da mai taxi di'n ta ciro kudi'nshi naira d'ari ta bashi, ta dauki jakarta, dea2 kopan ta tsaya tana kallonshi, rabonta da gidan tun ranar da aka sata lallen aurenta sea kuma yau datazo, kuma zuwan bana wuni ba na zama gabad'aya, hawayenta ta share tasa kafanta a gidan daya kasance matsakaici tare dayin sallamanta. Yar dattijowan dake zaune akan kujera ta d'ago idanunta, ganin "yarta da tai yasa ta d'ago ta dubeta "Salma ina Aliyu"? Wannan shine tambyan da tafara yimatah Kuka ta fashe dashi tai zaune dirshan akasa "Mama alhj ya sakeni, kuma yace "idan nasamu miji inyi aure". Dattijowan ta girgizah kai "Bkomai salma Allah yasa haka shine mafi alkhairi, dauki jakarki ki shiga da ita dga ciki" Hakan ko akayi ta dauki jakarta ta shiga dakin da rabonta dashi shekara goma shaa biyu. Rayuwa kenan. Karfe takwas na daren wannan rana ta alhamis. Aliyu ne kwance akan kafafun ummi, yana wasa da d'an super man d'in roba, anty nana ce ta shigo a d'akin ta zauna kusa da ummi. "Ummi abbi na kira" Ummi ta tashi zaune ta dubie aliyu duba na soyayya "Aliyu ka jirani ynxn nan zan dawo, bance kai fad'a da kowa ba, kaji ko? Kai y girgizah ya cigaba da magana dashi da super man dinshi kaman ynda yake daukan yanayi. Ummi ta kama hanyar fita d'akin yayinda ya rage dga anty nana sea aliyu. Kallonshi tai tun daga sama har k'asa ta watsar tasa hannu ta rik'e masa kunne "Kai dan ubanka waye yace ka shigo d'akin nan"? Shiru yay, yaja jinin jikinshi sbd tsabar tsoron nana dayakeyi. "kana jina kayi shiru kasan cewa bana son ina magana ana kyaleni ko"? Cikin rawar murya ya fara magana "Anty nana mai nai maiki dan Allah? ynxn fa zaune nake banyi komai ba" "Taras"! Kaji saukan mari a fuskan aliyu , wnda hakan yay sanadiyyan sakin mutum butumin super man din dake hannunshi ya kwallah k'ara saboda zafin marin dayaji. Tashi tai ta kalleshi "Dan ubanka ka sake ka fad'awa ummi sea na maka wnda yafi wannan" Sheisheikar kuka ya hauyi sbda anty nana ta hanashi kukan, da gudu yay kuryan d'akin ummi kan gadonta ya cigaba da kukanshi "Mame kina inane, dan Allah kizo plsss" Haka ya dinga fad'a har bacci yay awon gaba dashi... Wanene Aliyu? Wanene Abbi (alhj)? Wacece Nana? Wacece mame? Wacece ummi? Ya ya alaqar su take a cikin gidan"? Ku biyoni ni kausar M Hassan dmn jin wannan labari ®Kausar Luv💞 DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ALIYU_HAYDAR* Page ((4)) ©Kausar M Hassan Aliyu haydar, d'ana ga Alh shuraihu isah shine dea d'anshi namiji a duniya d'aya tamkar da dubu, wnda ya dauki son duniya y d'ora masa, kasancewar, shi d'ayane d'anshi namiji a duniya, aliyu dea farine mai matsakaicin baki, dogon hancinshi ya k'ara masa kyau gashi da d'an jikinshi kadan dea2 misali, shekarunsa bazasu zarce tara zuwa goma ba ynxn haka yana primary 5 ne a matakin karatun zamani, a b'angaren addini kuwa yana karatunshi dea2 gwargwado kaman ynda ya kamata. Wacece mame? Ainahin sunanta salma, itace matar alhj, cewa da baban aliyu ta 2, yana sonta sosai, kasancewar itace ya aura bayan ya auri maman nana, aliyu ne kad'ai d'anta a duniyah, hajiya salma mace ce mai addini da son ibada, batada matsala a rayuwanta ko kad'an. Wacece ummi? Ainahin sunanta rabi'atu usman, wadda aka fisani da hajjah, itace matar alh shuraihu ta farko, tanada yara 2 tare dashi "Nana asma'u da kuma nafisa, nafisa tana gurin kanwar mamanta mai suna zaliha, a chan take karatu kimanin shekarunta 8 a duniya.. Ummi ta kasance mace mai kamar maza, kasancewar ta uwar gida ga Alhj shuraihu, ta tsaya tsayen daka gurin ganin tai hakuri da komai ke biyowa bayah. Duk da ba ita ta haipie aliyu ba tana matuqar sonshi da gskya, ko kusa bata daukanshi d'an kishiyarta, ta daukeshi tamkar d'anta data haifah... Wacece Nana? Nana asma'ah shuraihu isah wannan shine sunanta, kimanin shekarunta 18 a duniyah, idan akuy wanda ta tsana a gidan to bai wuce aliyu ba, sanadiyyar wannan kiyaya kuwa itace tana ganin mahaipinsu Alhj shuraihu y nuna masu banbanci tsakaninsu da d'anshi namiji wato aliyu a ynda take gani, nana fara ce, mai d'an matsakaicin jiki, da manya_manyan idanunta masu kama dana mage, ma shaa Allah nana Allah ya bata kyauwun fuska amma bbu kyauwun hali, tana s.s.3 a matakin karatun zamani.. wannan kenan. Wanene Alhj shuraihu?? Alhj shuraihu mutum ne mai arziki, yana d'an shekara 25 yay aure, ya auri hajjah, shekarunsu 7 a tare amma Allah bai bata haihuwa ba, bayan wad'an nan shekarun ta haipie yarta ta farko mai suna jamila, bata jima ba Allah yay mata rasuwah, haka ta dinga haihuwa har sau hud'u tana jiro "ya "ya mata suna rasuwa tukkuna Allah y bata nana, bayan ta haipie nana sea da tai shekara 5 bata kara haihuwa ba, byn alhj ya auro hajiya salma ta haipie aliyu, bayan shekara 2 itakuma ta haipie nafisah. Wannan kenan.... DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ALIYU_HAYDAR* Page ((5)) ©Kausar M Hassan Washe garin ranar ta kama juma'ah, bayan ummi ta shiryawa aliyu ta had'a masa kayanshi da lunch box d'inshi gaba da'yah. "To aliyu sai ka dawo ko"? Kiss ya manna mata a kumatu "Bye ummi sea na dawo" Murmushi unmi tai tukkuna tai masa hannu. Da gudu ya ruga ya shiga cikin motan, nana ce a gidan baya, shikuma ya bud'e gidan gaba ya shigah, cike da murmushi ya gaidah driver d'in dke kaisu makaranta mai suna musa "Ina kwana kawu musa"? Murmushi yay ya amsa da "Lpy qlw aliyu zakin fama, aliyu ikon Allah" Harara nana ta aika masa mai rai da lpy "Kai dallah malam kajamu ka kaimu makaranta ka tsaya kana yima mutane wani surutun banza" Humm! Y fad'a kawea yaja motan aka bud'e masa gate suka bar gidan zuwa makarantarsu dake nesa da gidan sosai. Suna isa yay parking suka fita, suka karasa kowanne yay 6angarenshi, kasancewar makarantar su primary and secondary school ne. School d'insu d'aya. ****** Hajiya salma ce zaune a d'aki bayan ta had'a karin komallo taci ta zauna gata ga mama, hajiya salma tayi shiru tana tunanin duniya. Mama ta kalleta ta dubieta "Salma dan Allah ki deana tunanin nan, kada ki sawa kanki hawan jini". Juyawa tai ta dubie mama "Mama bana tunanin komai a raina face d'ana aliyu, aliyu yana bani tausayi sosai sbd shi kad'ai na haifah, duk da nasan hajjah na kulamin dashi, amma ina tsoron nana, sbd nana batada kirki bata son yaron nan kuma bansan dalili ba" Mama ta dafa kafad'anta "Salma kiyi hkuri, kicigaba dayi masa addu'ah, Allah yana amsa addu'ar iyaye musamman ma ta uwa zuwa ga "ya "yanta". "To mama" ta fad'a jiki a sanyaye.. Karfe 1pm aka tashi su aliyu dga mkrntah, jakarsa ya dauka tare da abokinshi mai suna shafi'u suka kama hanyar fita dga mkrntar, kasancewar ko sun tashi dga makaranta sea ya jira an tashi su nana sea azo a d'aukesu su dawo tare. Shafi'u shine babban abokin aliyu a makaranta, koda yaushe tare kake ganinsu, abunda ya k'arwa abotarsu amarshi shine shima shafi'u yayarshi ajinsu d'aya da nana kuma k'awartace sosai.. Like · 1 · Reply · Report · Jul 30 at 6:48pm Kausar M Hassan *ALIYU_HAYDAR* Page ((6)) ©Kausar M Hassan Dea2 bus stop din skul din suka tsaya shida sauran wad'anda ke jira azo a daukesu. Wasa sukeyi Yar boya, shida shafi'u, su nana suka fitoh, yana ganinta ya natsu abunshi ya daukie jakarshi ya daura a bayanshi. "Tashi ka wuce" Sim2 ya tashi y wuce, shida shafi'u, yayinda nana ta zauna itada kawarta siyama yayar shafi'u abokin aliyu. Bayan sun zauna siyama ta kallie nana "Haba nana wea mai yasa kika tsani yaron nan dan Allah"? Nana ta d'ago idanunta ta dubie siyama "Siyama kisani cewa mahaipina shi yaja komai" Ta tashi tsaye ta kallie siyama "Bara in baki labarin abunda yasa na tsani aliyu siyama a rayuwata" " Abbi d'inmu mutum mai son jama'ah da mutane, gidanmu ya kasance babban gidah, gidan sama ne, d'aku nan dake gidanmu sunyi 10 saboda yawan bakin da ziyartarmu da kuma yan uwah, lokacin da mahaipiyata ta haifeni mahipina ya nuna min soyayya dea2 gwargwado, yana kula dani, hka ummi da kuma mame, bayan wasu shekaru Allah y baiwa mame ciki ta haipie Aliyu. A lokacin mahaipina ya daukie son duniya ya daura mashi, komai yay baya laipie, sea in nema abu a gurinshi ya hanani ya dauka ya bashi, bazan manta ba tun yanada shekara 8 yake d'aukanshi suna yawo duniyah, yama manta da wata y"a wea ita Nana asma'u, kinji siyama wannan shine abunda yasa na tsaneshi, saboda da ba dan an haipieshi ba da banda damuwa" Nana ta juya ta dubie siyama "Kuma wallahi zan iya halaka aliyu akan hakan" Siyama dake zaune da sauri ta tashi tsye tasa hannu ta dafa kafad'anta "Nana kiyi hkuri ni banga wni abu gameda hakan ba tunda mahaipinku komai yanayi maki kuma shi ai namiji ne fa, dole ne ya rik'a daukanshi yana fita dashi" Nana tai ajiyan zuciya "Hmm siyama kenan kada ki manta a cikin Al_qur'ani mai girma Allah yana cewa "y'aku wad'anda kukayi imani kuji tsoron Allah kuma kuyi adalci a tsakanin "ya "yanku". Allah bai ban_bamta "ya "ya maza da "ya "ya mataba, dukkan mu "ya "yanshi ne da siyama... Siyama ta nisa ta bude baki "Buh amma... Dea2 lokacin mai zuwa daukansu yazo hkn yasa siyama tai shiru, aliyu na hangoshi da gudu ya karaso inda suke "Anty nana gashi mota tazo mu tafie gidah" "Jeka gani nan zuwa" ta fad'a tare da watsa masa harara. Jiki a sanyaye ya k'arasa cikin mortar ya bude gidan gaba ya shigah. "Aliyuna har an tashi"? "Eh an tashi kuma kasan next week zamu fara last exam dinmu a primary kaga sea in shiga secondary ko"? Murmushi yay "Allah ya bada sa'ah aliyu" "Amin uncle" ya fad'a yana daria. Nana tai d'an murmushin mugunta "Yau aliyu ina fadamaki bazea kwana a duniya ba, ba dea ice cream yake shaa ba? Yui kuwa zaisha na ajalinshi, kada ki kashe wayanki dan zan kiraki in fadamaki cewan aliyu ya mutu" Ta kyalkyale da daria ta kama hanya zuwa mota, yayinda siyama ta girgizah kai cike da tsoro take kiran sunanta, dan daukan take ta haukace. Nana najin kiran da take mata tai banza da itah, hka ta shiga mota ta maida marfin motan ta rufe, kawu musa yaja motan suka karasa gidah.... DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ALIYU_HAYDAR* Page ((7)) ©Kausar M Hassan "Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un" Siyama ta furta a fili, yayinda ta kira shafi'u ganin mai zuwa d'aukansu yazo. Da gudu ya karaso suka shiga motan duk a gidan bayah, tunani ta hauyi na anya kuwa za'a samu irin wad'an nan mutanen a duniyah lallai kuwa nana ta tabbata batada hankali kuwa, amma ya zatayi tai saving din Aliyu gameda nana "?? Wannan shine tunanin data shigayi a hka har suka karasa gidah dukansu. Suna isa aliyu da gudu yay kan abbi, abbi yaja hancinshi kad'an "Ma boi an dawo skul ko"? "Yes daddy and kasan kuma cewan ranar monday din nan zamu fara jarabawa, I need to read hard sannan kuma ynxn babu shan ice cream babu wasa, babu game" Murmushi abbi yay "Ma boi kenan, kaga kuwa abunda ya kamata ayi shine kana kammala primary dinka tunda akuy yaron abokina dake karatunshi a london shima secondary yake sea in had'aka dashi kaje chan ka kammala har degree dinka ka dawo ko"? Aliyu daria yay "Abbi ni bana son zuwa chann, America nakeso" ya fad'a cikin muryan shagwa6a. Duk wannan abun dake faruwa a gaban idon nana akeyinshi, wani d'an guntun tsaki taja tukkuna ta haura sama tai d'akinta cike da takaici. Abbi ya d'go kai ya dubie ummi dake tahowa "Kinga d'anki nan wea nace na kaishi U.K yace U.S yakeso idan ya gama primary dinshi. Ummi ta dafa kanshi tare da cire masa jakar makarantar dake goye a bayanshi. "To alhj inda yakeso ba sea akaishi a chan ba, tunda dea d'ana ne, maza kaje kai wanka kazo kaci abunci sea driver ya kaika gurin mame ko". Alhj shuraihu y d'ago kanshi "Babu inda zashi yana nan tare damu" Zatayi wata magana kawea ya haura sama yay d'akinshi, yayinda aliyu ya tafi ya aikata kaman yanda umme tace ya dawo da kanta take bashi abunci yana ci, har ya koshe ya tashi yay d'akinshi ya fara karatu kaman ynda ya fad'ah... Like · 1 · Reply · Report · Jul 30 at 10:06pm Kausar M Hassan *ALIYU_HAYDAR* Page ((8)) ©Kausar M Hassan A chan bangaren siyama kuwa tun bayan komawarta gida tunani kawea takeyi, saboda tasan nana zata iya aikata abunda ya zarce wnda ta fad'a gameda duniyah. Da wannan tunanin ta wuni har dare Misalin karfe 8pm na dare, bayan sun kammala dinner d'insu, ummi taja hannun aliyu sukai d'akinta, tana zaune tana kallo, sea ga kira wayanta ya hau ruri. Dauka tai ta kara a kunne tare dayin sallama "Assalamu alaikum" "Amin alaikum salam ummi, nice siyama kawar nana dan Allah aliyu nakeson yin magana dashi idan yana kusa" Ummi ta kira aliyu, da sauri ya taso yazo "Kar6a waya wea siyama kawar nana keson magana dakai, kayi magana ni zan tafie kasa in dauko maka lemo in dawo ko"? Kai ya d'aga mata alamar to tare da amsan wayan ya kara a kunne. Cikin muryanshi mai dadin sauraro ya fara magana "Hello" "Hy" "Aliyu kana jina ko? Daga ynxn duk abunda nana zata baka kada kacishi" "Saboda mi"? Ya fad'a a takaice. "Saboda tace tana so ka rabaka da mame kaji ko"? Kai ya girgizah tukkuna ya kara da cewa "To anty siyama bazan ciba" Ya maida wayan ya kashe. Idonshi da zai d'ago sukayi ido 2 shida nana, ido ya ware, yayinda nana ta shigo a d'akin tana yimasa murmushi rike da ice cream a hannunta. Da gudu ya hau kan kujera ya dauki remote ya chnza channel zuwa MBC 3 ya hade hannayenshi guri d'ayah. Nana murmushi tai ta matsa kusa dashi ta zauna "Aliyu na" Ido ya d'ago "Na'am anty nana" "Ga ice cream na kawo maka, nasan kana son ice cream" Kai ya girgizah "Ni bazan sha ba anty nana, ummi tajie ta daukomin lemo" Nana ta turnukie fuska "Haba aliyu mai yasa bazaka shaa ba, kaga bazan kara dukan ka ba kaji ko"? "Na fadamaki bana shaa ki kyaleni anty" "Dan ubanka sea ka shashi ina maka magana kana kyaleni ko"? A zuciye ta bud'e roban ice cream d'in ta d'ebo a cikin chokali ta fara mika mashi tare da murd'e masa baki, kokawa ta 6arke tsakaninsu. "Hakan yayi dea2 da shigowan ummi "Ke! Mai kike yine haka"? Cikin rawar murya ta fara magana "Ummie a'a... wea.. dama ice cream ne na bashi shine yace baya shaa" "To ana dolene nana, tunda baya sha ki kyaleshi mana dan Allah, ki daukie kayanki ki shaa mana" Ta karasa maganar da karasawa cikin d'aki taja hannu aliyu suka wuce ciki A cikin zuciyanshi yake cewa "Kin shiga 3 kuwa nana" yay mata gwallo😜 Like · 2 · Reply · Report · Jul 30 at 10:06pm Kausar M Hassan *ALIYU_HAYDAR* DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009Page ((9)) ©Kausar M Hassan Washe garin ranar ta kama assabar tunda safe aliyu ya tashi ya tattaka zuwa kopar dakin nana, kasancewar masu aikin gidan da an kammala sallan asuba suke tsafatace ko ina da ko ina na gidan. A hnkli ya daukie ruwa a cup, dea2 kopar d'akinta ya zubar dasu ya ruga a guje y koma d'aki ya kwanta. Ba'a jima ba nana ta fitoh dga d'akin, taku 2 tai kajita kasa tim😂 kamar an zube kayan wanki, kugu ta rike ta fara waiyyo! Dkyar ta iya tashi tukkuna ta karasa d'akin aliyu ta kwankwas, tasowa yay ya bud'e tare da cewa "Ina kwana anty nana" "Lpy qlw aliyu, zo muje kitchen yau ni zan dafa maka abuncin daka fiso kaji ko"? Murmushi yay suka kama hanya sukai down stairs, a kasan ta samu dogon towel ta d'aura ta cire kayan baccin ta shanya a igiyah suka shiga kitchen din, ta fara har_hada masa indomie, shidea yana zaune yana kallonta Har ta kusan kammalawa ta dubie aliyu "Jeka d'akina ka dauko min kaya na nan kan karamin drawer dina yi sauri" Babu gardama ya haura saman, koda ya isa an goge ruwan, daria yay kad'an ya bud'e dakin ya shiga y dauko kayan kaman ynda tace ya dawo kasa. Koda ya sauko ya tarar da ta had'a abuncin akan dinning. "Yauwa aliyu kawo kayan nan zauna ga abuncinka nan na had'a maka" Murmushi yay ya dubieta yaga tana yin yar daria "Anty nana ina ruwa, kinsan bana cin abunci sea da ruwa fa". Har ta bud'e baki zatayi masa fad'a sea ta fasa ta tashi ta koma kitchen, kapin ta dawo yay maza y chnza kwanon abuncin ya fara cin na gabanshi. Tana dawowa ta tarar dashi yana cin abuncin, haka yasa tai murmushi ta ajiye masa ruwan kusa dashi, ta zauna ta fara cin nata, tana ci tana murmushin muguntah, shi kuwa aliyu sea cin nashi yakeyi. Har taci abunda yafi rabin abunci sea taji cikinta ya fara murd'awah, da sauri ta rike cikinta, ta fara hawaye, aliyu ta kalla tagan lapiyanshi kalau, take ta kai k'asa, aliyu dake zaune da gudu ya haura sama ya kira ummi, tare suka dawo shida ummi a rud'e, da sauri tace "zubairu kiramana Dr bilal, haka kuwa akayi , kasancewar shi makocinsu da hanzari yazo gidan, yana ganin hakan yace "a bashi madara peak, da sauri aka shiga kitchen aka kawo masa, fasata yay yace "ummi ta rikata", haka ummi ta d'aga kanta ta bata madaran tasha, take sea amai, nan aka dauketa akai da ita d'aki, Dr bilal ya dubata bayan d'an lokaci kad'an ya dubie hajjah "Hajja guoba ce taci a cikin abunci, Allah ma yayi mata arziki dan da ta kasheta"! 🙆🏾Nana u wan kill d lion😏? Cike da mamaki hajjah ta amsa da "Guoba kuma dr, kai aliyu waye y baku abuncin da kuke ci"? Cikin sanyin murya y kalleta "Ummi ita ta dafa fa kuma ita ta bani nawa da nata" Ummi ta jinjina al'amarin "Allah ya sauwaka, nan Dr ya basu tabbacin cewan zata farka zuwa wasu awowi, in shaa Allah kuma zata buqaci hutu sosai, ya kuma yi masu sallama. Fitarsa keda wuya, ummi ta fitah ta bar aliyu a d'akin Daria yay a fili ya furta "Am back bakin samu na rika jin magana ba har ina jin tsoronki ba, to na dawo da asalin sunana na aliyu" Dama chaan bana jin magana, haka nake wollah😂 sbd hka ki kuka da kanki... Nanuwa😏 ®Kausar Luv💞 DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 *ALIYU_HAYDAR* Page ((10)) ©Kausar M Hassan Nana bata farfado ba sea kusan la'asar tana nan tana bacci, yayinda Aliyu ya tafie makarantarsu ta islamiyya dake nan kusa da gidah. Bayan nana ta farka dga bacci, a hnkli ta bu'de idonta chaan ta tuna abunda ya faru sea ta girgizah kai "Yaro kaman aljani, nikam yau ai danayi mutuwan mazuru" Tashi tai ta shiga toilet ta watsu ruwa, tare da d'aura alwala tai sallah. Aliyu bai dawo ba sea karfe 6 dea2, yana shigowa sukayi arangama shida nana, jaa da baya yay kad'an tukkuna ya kalleta "Anty nana ina kwana, ina wuni"? Hannu tasa ta rike masa kunne "Kai uban wa yace maka ka chnza kwanon abunci nan d'azu"? Baki ya torou "Nifa anty nana kinga ba ni naiba, kefa kika bani abuncin nan" A kunne take fad'amasa "To yayi aliyuna yi maza kaje d'akin ummi" Murmushi yay "Ok anty nana" Kai tasa ta fita wajen gidan yayinda aliyu cikin sand'a yay dakin nana ya maida ya kulle. Kasancewar akuy wata kujera a d'akin da nana ke zama mai kamar ta karfe, kuma d'aurata akeyi mutum take zea iya kwance ta y kuma had'ata. Aliyu daria yay, ya daukie kujeran ya kwance d'an abunda akasa aka d'aureta ya maida ya ajiye, ya lalla6a ya fitoh dga d'akin zuwa nashi d'akin ya cire kayanshi yay wanka ya chnza kayan jikinshi abunshi yasa takalminshi sandals ya fitoh. Aliyu haydar kenan ba dea tsafta ba, ga son gayu kwata2 baya son k'azanta a rayuwnshi, gashi dea yaro amma kuma abokin manya sbd Kanshi na jaa... Yana fitowa kai tsaye dakin ummi ya nufah, chaan ya tarar da abbi zaune kan carpet yana kallon CNN, yayinda ummi ke had'a lemun ginger. "Assalamu alaikum" aliyu yay sallama "Amin alaikum salam" abbi da ummi suka amsa Da gudu yaje kusa da abbi ya zauna shima ya kurawa TV d'in idanu yana kallon news, duk da primary school yake amma yana jin turanci, irin wnda ba big2 grammars d'in nan ba. Chaan kaman an ta6ashi ya dubie ummi "Ummi ni gskya ki fad'awa abbi bana son america kuma, makkah nakeso" Abbi dake zaune yay daria kad'an ya dafa kanshi "Aliyu mai yasa kake son zuwa chaan Makkah"? "Abbi saboda kaga chaan duk muslimi ne" "Shekenan Alhj kaga d'ana yayi zabi mai kyau sea akai shi a chaan" "Allah y kaimu lokacin" Ummi ta amsa da "Amin" Yayinda Aliyu yay murmushi abunshi wnda ya k'ara masa kyau.. Like · 1 · Reply · Report · Jul 31 at 6:47pm Kausar M Hassan *ALIYU_HAYDAR* Page ((11) ©Kausar M Hassan Karfe shida da rabi nana ta dawo dga inda ta'je, kai tsaye dakinta ta nupa, taja kujera ta zauna, zaunawan da zatayi kajita kasa rum, "Waiyh Allah" A daddafe ta tashi ta koma kan gado ta zauna, tana mamakin abunda ke faruwa, sea kuma ta tuna da cewan Aliyu fane, chaab! Hka sukai spending ranakun karshen makon, tskanin aliyu da nana kuwah, duk tarkon data had'a masa sea ya ketareshi abun y koma kanta. Yau ranar ta kama monday, sbd hka Aliyu da nana suka shirya zuwa makaranta, kasancewar yau itace ranar dasu zasu fara jarabawa yasa shi natuswa, hka suka shiga class din, da uniform din makarantar dark blue din wando da farar riga, da abun wuya shima dark blue, na matan kuwa duk hkne dfrnce din shine bbu abun wuya, sea farin hijab.. Hka sukai exams d'insu har ta tsawon sati 2 suka kammala. Ranar da suka kammala akai hotona na bankwana, tare da malamai da kuma d'aliban makarantar. Akuy wata yarinya a ajinsu aliyu mai suna Nadiya, ita dea aliyu yana matuqar burgeta, hakan yasa tai duk ynda tai sukai hoto su 2, sannan sukai tare da shafi'u.. Bayan kammala exams d'inshi, ya rage dagashi sea ummi ke zama a gidan, kasancewar nana tana zuwa makaranta yin waec, rayuwarsu sukeyi cikin jin dadi yayinda abbi yasa aka fara nemawa aliyu admission dinshi a wata makaranta dake nan gaein madina birinin manzo, brinin karamchi.... Like · 1 · Reply · Report · Jul 31 at 6:47pmDOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Kausar M Hassan *ALIYU_HAYDAR* Page ((12)) ©Kausar M Hassan Bayan wata 3! Yau ranar ta kama ranar juma'ah, yayinda ummi keta faman had'awa aliyu kayanshi na wucewa makarantar da aka sama mashi admission din a kasar madina. Bayan ta kammala hada masa kayanshi tsaf, ta dubie abbi dake zaune yana kallonta yana murmushi, Cike da tsoro da kuma fargabar abunda zai biyo baya ta fara magana. "Alhj dama cewa nai mai zai hana akai yaron nan yaga mame dinshi kapin ya wuce makaranta, tunda yanzu idan ya tafie kuma sea ya jima bai dawo ba"? Abbi dake gincire y tashi tsaye ya dubie ummi "Ina wasa dake irin wannan ne? Kada ki koma yimin wannan maganar idan ba haka ba ranki zai bace a gidan nan" Yana kammala fadar haka ya tashi ya zarce d'akinshi Ummi binshi tai da kallon mamaki, a zuciyanta ta furta "Ikon Allah ikon gskya, ynxn ni daga magana sea abu y dawo kaina? Ni ina laipiena dan kawea inaso kayi abunda yakamata, wannan ai baso bane kana kokarin raba uwa da d'anta, Allah ya sauwaqa" Washe garin ranar ta kama assabar, ummi ta shirya ta fitah bikin wata yar kawarta da akeyi, aka bar nana da aliyu a gidan Nana ce zaune a babban falo, tai zaune kan kujera, aliyu ne ya fara saukowa dga d'akinshi, idanunta da zata d'aga tagan shi yana kokarin yayou downstairs. Cikin kakkausar murya ta kira sunanshi "Aliyu kai" D'agowa yay ya dubeta dan bashida idea akan abunda zata iya yi masa yasa ya sakko k'asan, kusa da ita yaje ya rage tsayenshi ya kafeta da idanunshi, hannu tasa ta zungureshi akai, ya dago idanunshi da sukai narai2 ya dubeta "Kai zaka tafie saudi karatu ko"? Ta d'aga hannu kenan zata mareshi sea ga sallama Wadda wannan ba sallaman kuwa bane face na Anty zaliha, kanwar mamansu, tare da nafisa kanwar nana. Hakan yasa ta fasa niyyan abunda zatai, da gudu nafisa ta rugu, duk daukan nana gurinta zatai sea taga tayi gurin aliyu. "Yaa aliyu i miss u" Murmushi yay kad'an "Kanwata inace kin dawo gidah dea sbd nima a rika cemin yaya" Nafisa ta d'aga masa kai Aliyu yaja hannunta suka haura saman d'akinshi yayinda anty zaliha ta zauna kan kujera, suka fara tadie da nana, nan ta dauko mata ruwa da lemo ta kawo mata tare da kiran zubairu daya sanarwa ladidi mai aiki ta dora girki anyi bakuwa. Zubairu! Shine babban yaron gidan Alhj, shine ya zaama tamkar d'an uwansu na jini da tsoka jiki da jijiya. Yazama kamar sarkin gidan, duk abunda ake a gidan yana sane, haka ya daukie aliyu tamkr d'an daya haifah.. Haka kuwa ya fice ya aikata kaman ynda ta fad'ah. Ba ummi ta dawo ba sea bayan la'asar lis tukunna, nan suka gaggaisa da kanwarta ta kuma shaidamata cewan nafisa ce tace tana son dawowa gidah shine tace bara ta kawotah. Bayan d'an lokaci kadan tai mata sallama tare da kama hanya zuwa garinsu wato Kadunah.. Aliyu da Nafisa kuwa wata shaquwa ke kara shiga tskaninsu, suna son junansu a matasyin yan uwan junah.. A wannan rana dea a d'akin ummi suka kwana dukansu. Washe gari! Da asuba aliyu yay d'akinshi yay sallah, ya zauna yana tunanin mamanshi, shi ko yama zayyi ya ganta bai sani ba. Nana ce ta bud'e d'akin sad'af2 kaman wadda zatayi satan wani abu ta shiga, tana shiga ta maida kopan ta rufe...😳🙆🏾 Waiyyo dear little aliyu lion😰 ®Kausar Luv💞DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ALIYU_HAYDAR* Page ((13)) ©Kausar M Hassan Tana shiga ta dubie aliyu, kan kujera ta zauna ta bashi umarni "Oya fara tsallen kwad'o ka gama kuma kayi kamun kunne mazzah, kai ya d'aga mata jiki a sanyaye ya fara yi. Nafisa dake kwance ta lalaba taji babu aliyu inda suka kwanta hakan yasa ta tashi ta mum_murza idanunta ta yaye abun data rufa dashi tabi hanyan d'akin aliyu, direct ta murd'ah kopan koda ta bud'e ta tarar da aliyu sea kuka yakeyi, da gudu ta isa gareshi ta d'ago kanshi "Yaya aliyu mai yasa kake kuka"? A hnkli ya d'aga dayan hannunshi na hago y nuna mata nana, da sauri nafisa ta fara magana cike da rud'u "Anty nana mai yaa aliyu yayi maki da zaki dakeshi haka"? "Nafisa tashi nan kada in hada dake wollah" Nafisa tasa hannayenta ta rungumou aliyu cikin muryan kuka ta fara magana "Ni wallahi anty nana sea dea ki hada dani amma gskya bazan yarda ki daki yaa aliyu ba" Huci nana tai tare da yin tsaki a fusace ta wuce ta bar d'akin.. Aliyu a hnkli yaja da baya kad'an kan carpet ya fadie kasah, kanshi har juwa yake gani, saboda tsaban wuyan dayasha, hawayene keta faman zuba a idonshi.. 🤔Rayuwa kenan wata rana sai labari. "Yaa aliyu bara in tafie in fadawa ummi" Har ta tashi ya riko hannunta "A'a nafisa kada ki fadama ummi ki kyaleta kinji ko"? Nafisa kuka ta hauyi itama saboda tausayin aliyu.. Hka aliyu ya wuni a wannan ranar jiki a sanyaye, kowa a gidan mamaki yakeyi, ita kuwa ummi ta d'auka cewan sbda zai bar gidane. Shi kuwa aliyu abu 2 ke damunshi da azabar da nana ta bashi da kuma rashin ganin mame gashi har ranar tafiyanshi ta kama gobe... Kasancewar akuy d'an abokin abbi da zasu tafie tare mai suna zayyanu shima a chaan zai fara karatun, duk kusan sa'an shi daya da aliyu lion. Shafi'u ma yzo sunyi bankwana da junah...DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Like · 1 · Reply · Report · Aug 1 at 8:52am Kausar M Hassan *ALIYU_HAYDAR* Page ((14)) ©Kausar M Hassan Washe garin ranar ta kama ranar tafiyan aliyu, saboda hka ummi ta hada masa abunci, saboda bataso yaci abuncin jirgi, karfe 12pm jirginsu zea d'aga dga babban filin sauka da tashin jirage na margayi sarkin musulmi abubakar na 3 dake sokoto. Tun wayewar gari, nafisa da aliyu suke tare, nana kuwa ta rasa abunda ke mata dad'i sea faman safa da marwa takeyi a d'aki. Dad'ina da agogo aiki, haka lokaci ya buga karfe 11:50am, saboda go slow din kan hanya abbi yace "aliyu ya fito su tafie, tashi yay sukai sallama da dukan ma'aikatan gidan, nana ce kawea bata gurin, sun jima suna bankwana shida nafisa tukkuna abbi ya rika hannunshi suka kama hanya. Sautin muryan da sukajie nayin sallama ne yasa abbi dakatawa y saki hannun aliyu tare da d'aga idanunshi, arba yay da hajiya salma. "Ke mai ya kawoki gidana" Cikin muryan tausayi ta hau yin magana "Alhj nasamu labarin yau aliyu zai tafie makaranta shine nazo in ganshi muyi sallama" Da gudu aliyu yay inda mame, ma'aikatan gidan kuwa har zuwa ummi sunji dad'in wannan gamuwa tasu. Rungumeshi tai sosai tana hawaye "Aliyu Allah yay maka albarka, kayi karatu banda wasa kaji ko"? Murmushi yay ya k'ara laqamie mame, mame kada ki barni dan Allah" "Ina tare dakai d'ana a koda yaushe, bazan tab'a barinka ba" Zubairu!!! Alhj ya hau kiranshi "Na'am alhj" Yi maza ka karbomin aliyu saboda zamuyi late idan muka tsaya nan Da hanzari zubairu ya matsa kusa dasu "Aliyu alhj na kiranka" Kara shigewa jikin mame yay. Yayinda zubairu ya kasance baida zabie illah yayi kaman yanda alhj yace Hannu yasa ya fara jan aliyu dga jikin mame Kuka aliyu ya hau yi tare da kiran sunanta "Mame! Mame dan Allah kice ya kyaleni, bana son tafiya ni gurinki nakeson zama" Kuka aliyu ya hauyi har idanunshi sun kada sunyi jajir "Mame! Dan Allah" Ga aliyu a hannun zubairu ya rikeshi, yana kucce2 a hannunshi, iya karfinshi ya dage yana kiran sunan mame "Mame kuka takeyi sosai sboda tausayin d'anta "Aliyu!!!"" Ta kira sunanshi ta fashe da kuka. Da karfi ya su6uce ga rikon da zubairu yay masa ya qara rugawa da gudu yay gurin mame ya rungumeta "Mame! Pls ki daukeni mu tafie, mame pls"😭 Kanshi ta shafa itama din kukan takeyi.. Ganin hakan yasa alhj ya tako da kanshi ya rika hannun aliyu tare da janshi, ga kasa . Aliyu y fara bubbuga kafafunshi a k'asa yana kiran mame "Mame!!!😭 kuka aliyu keyi sosai, har sun kai kopar fita falon ya kara ruguwa da gudu ya k'ara kankamie mame yana kuka yana kiran sunanta.. A falon bbu wnda bai zubar da hawaye ba saboda tsabar tausayin aliyu, illah nana data kasance tsaye ta dora hannayenta akan matar takalar stage din. Abbi hasala yay da zuciya ya dirkako kan aliyu yaja hannunshi, ya dga hannu ya wanka masa mari mai kyau, wanda yasa aliyu natuswa lokacin da bai zta ba. Hannu mutanen falon suka saa suka rike baki, ganin abbi bai tab'a daukar hannu ya dorawa aliyu ba sea yau. B'acin rana kenan😕 Nikam ido na zaro ina mamakin wannan al'amari wea meye dalilin yin hakan na raba uwa da danta da kuma wannan tsanar data shiga tskanin alhj shuraihu da kuma hajiya salma... Uwar d'ansa tilo namiji wadda kuma a cikin so ya aureta, tabbas akuy wata a qasa😱... Like · 1 · Reply · Report · Aug 1 at 8:52am Kausar M Hassan *ALIYU_HAYDAR* Page ((15)) ©Kausar M Hassan Idanu Aliyu ya d'ago sukai ido 2 da abbi, abbi yaja hannunshi suka kama hanyar fitah dga gidan, suna tafiya aliyu na waigen baya yana kallon mame tana hawaye tanai masa bye2, yyinda nana keta faman yin dariar jin dad'i, haka har suka bar gidan suka shiga motah. Kawu musa ganin yanda fuskokinsu sukai yasa bayyi magana ba, kawea yaja motan sea airport. Suna isa kuwah, yaron abokin abbi na zuwah, aliyu shiru yay baice da kowa komai ba, abbi na kallonshi ya bashi tausayi yama rasa da wanne baki zayyi rarrashin shi, hakan yasa ya barshi yayta huci Abbi ka taba mana lion fa Haka aka kirasu suka tashi kowa yaja jakarshi, da kuma jakar goyanshi suka shigah jirgi suka zazzaunah, aliyu da zayyanu guri d'aya suka zaunah. Zaiyyanu yay ta magana, aliyu yay banza dashi haka har jirginsu ya tashi dga Nigeria zuwa saudi Arabia... Wani irin abu aliyu ke ji a cikin ranshi, baqin cikin dake ranshi yay masa yawa fiye da tsammani, har ynxn fuskan abbi yake kallo ynda ya rabashi da mame, mahaifiyanshi, sanyin idaniyarshi, gatanshi, nisful hayat dinshi... Allah sarki Aliyu haydar😭😭 ®Kausar Luv💞 DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ALIYU_HAYDAR* Page ((16)) ©Kausar M Hassan Rayuwa tafiya takeyi, lokaci gudu yakeyi a gogo, shekara ta koma kmn wata, wata ya koma kamn sati, sati ya koma kaman kwana d'ayah, a kwana a tashi kuma babu wuya ga Allah mai dukkan komai.. Haka aliyu ya wuce makaranta a kasar madinah, iyakarshi da gidah bayan duk shekara d'ayah, idan ya dawo kuma abbi baya barinshi fitah koda wajen gidan, kudurin nana yana nan a cikin rantah, yayinda mame ta kuma chaan wani kauye kusa da garin sokoto wnda ba zea daukeka awa d'aya ba kapin ka isa.. 19years later! A kan matattakarlar shiga da saukowa daga jirgi na hangeshi, kafafunshi sanye da cover shoes brown in colour, sanye da wando shima hka irin mai laushi din nan, da riga fara mai ratsin brown kadan a tsakiyanta, ya rataya jaka a hannunshi tre da riko irinta jaa din nan a kasa (trolley) idanunshi a lumshe kaman wnda ya rufesu ruf, sajen dake fuskanshi ya k'ara masa kyau, dan madaidaicin bakinshi ya kara tsukewa a cikin kyakyawar fuskarshi, d'an jikinshi bul2 dashi, gwanin ban sha'awa. Murmushi yay shaqar iskar da yayi, ya cigaba da sako kafafunshi zuwa kasa a hka har ya sauko dga kan abun hawa jirgin. Lion kenan👍🏼👌🏽 "Aliyu" A hnkli ya bud'e idonshi yagan wake kiranshi. "Shafi'u" y furta cikin siriryan muryanshi. Da sauri shafi'u ya isa gareshi suka rungume juna Shafi'u ya dubie aliyu "Kai kaganka kuwa, kayi wani extraordinary fresh sea wani kyau kake karawa alhj" Kai aliyu y d'aga masa tare da furta "Ya batun aikin nan anyi kuwa" Murmushi shafi'u yay "Aiki an gama lion, ynxn dea muje gidah ummi na chan na jiranka tun d'azun" Juyawa yay sukyai sallama da zayyanu dake kusa dashi, shafi'u ya daukar masa jakar shi, suka kama hanya zuwa gidah... Like · 1 · Reply · Report · Aug 1 at 10:21pm Kausar M Hassan *ALIYU_HAYDAR* Page ((17))DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ©Kausar M Hassan A cikin mota shafi'u keta faman zuba masa surutu, iyakacin aliyu dea "eh, a'a em......." A haka har suka k'arasa gida, koda suka isa ummi ce zaune kan kujeran main falo na gidan, ma'aikatan gidan na kai da kawowa. A hnkli ya cire takalminshi ya nunawa ma'ikatan gidan suyi shiru kada suyi maganar da zata gane cewan ya shigo gidan. Ta baya ya lalla6a ya rufe mata ido, ummi hannu tasa ta saukar da hannunshi ta rike tare da cewan "D'ana aliyu kenan kana zaton bazan ganeka ba, kamshin turarenka ma yasa naganeka da wad'an nan tafukan naka" Narai2 da ido yay "Kai ummi, nikam wata rana sea nasa kin kasa ganeni" Ummi daria tai "Mu zuba mu gani to" Daria sukai dukansu dea2 lokacin abbi ke fitowa dga d'akinshi, aliyu y k'arasa kusa dashi suka karaso tare. Masu aikin gidan suka fara zuwa ban gajiyah. Suna zaunawa shafi'u ya dubie aliyu "D'an balarabe ni zan koma sea munyi waya ko"? Ummi dake zaune ta juya ta dubieshi "Haba shaf'u kai kaman wani bako kumah, ka hana aje a daukoshi gashi ya dawo kuma sea ka tafie ka barshi ana hka"? Murmushi yay "Ummi inada d'an uzuri ne amma zan dawo in shaa Allah" Aliyu tashi yay ya taka masa har kopan gidan sukai sallama ya dawo, kusa da ummi ya zaunah, ga kugunshi ga nata, sea faman murmushi sukeyi ita da d'anta aliyu haydar (the lion🦁). Chaan aliyu ya dudduba, baiga nafisah ba, ummi ta d'aga masa kai "Wa kake nema ne eyye"? Dan murmushi yay kad'an "Ummi ina nafisa kuwa"??? Rufe bakin da zayyi ya hangota tana zuwa, cikin shadda mai kyau taji aiki, rike da yaro a hannunta, daka ganshi ka ganta, a falon ta zauna ko kallon inda aliyu yake batai ba. Kai y girgiza shima yasan laipienshi ai, a hnkli ya tashi ya matsa kusa da ita kan kujerar ya zauna "Kanwata fushe kike da yayanki ko"? Juya masa fuska tai ta bashi bayah, aliyu ya rike hannun yaronta wanda baisan sunanshi ba. "Ya sunanka little kid"? Cikin yar muryar su ta yara y amsa da "Muhammad amin" Aliyu y rike hannun Muhammad "Kaga mamanka na fushi da yayanta, idan bata min magana ba ni zan koma inda na fitoh, tashi yay zai wuce, har yayi taku 3 ta tashi tasha gabanshi ta fara bubbuga kafanta a kasa "Ni Allah yaya aliyu ka dawo" Daria duk mutanen falon suka saah, ganin yanda tai, ita d'in kanta ta baiwa kanta daria. Takun sawo sukajie a falon wnda yasasu duba dga ina yake. Wnda wannan ba kowa bace face nana, murmushi aliyu yay y cigaba da abunda yakeyi. Kan kujera taja ta zaunah, tana yiwa aliyu wani kallo na rashin so, abunci ummi ta dauko ta bashi "A'a ummi ina buqatar inyi wnka b4 inci abunci ko b hka abbina"? Abbi murmushi yay "Haka take d'ana tashi maza" Aliyu tashi yay ya dauki bags dinshi yay daki dasu, wanka yay ya fito ya chnza kayan jikinshi zuwa na shan iska, farare tas dasu da fararen takalmi, ya feso turare ya fitoh d'akin zuwa kasah. Ummi da kanta ta bashi abunci yana ci suna fira wasa da dariah, nana batace dashi komai ba hka shima baice da itah komai ba duk da yaganta kuma itama tasan yagantah. Like · 1 · Reply · Report · Aug 1 at 10:24pm Kausar M HassanDOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 *ALIYU_HAYDAR* Page ((18)) ©Kausar M Hassan A wannan rana dea haka suka wuni har dare a gidan, cikin farin ciki mara misaltuwa. Sai karfe 9pm mijin nafisa yazo ya dauketa mai suna jafar, haka sukai sallama da nafisa ta tafi gidan mijinta dake wurno road. Nikam cewa nai ita nana bazata tafie gidan mijinta bane ko yaya🤔 ko ita batayi auren bane. Ganinta da nai ta shiga d'aki yasa na tabbatar da har ynxn batayi aure ba, ko mai take jirane oho? Kodayake aure kuma lokacine dashi. Muma Allah ya kaimu lokacin namu, amin.. Duk wadda/wanda batace amin ba to banda ita. lol😜 Aliyu d'akinshi ya nufa wanda aka chnzawa tsari da komai, ga babban photonshi yana yaro da kuma wanda yake yanxn duk da pic din ya shekara 3, dan lokacin daya kammala degree dinshi in computer ya dawo gida yin service yayi shi, to bayan y gama service din ya koma yay masters dinshi duk dai a 6angaren na'ura mai kwakwalwa. Kwance yay kan gado chan kuma ya tashi ya shiga toilet y watsa ruwa tare dayin alwala, ya chnza kayan jikinshi zuwa wando 3 quarter, ya maida gabanshi gabas yay sallolin dare, har kusan 11pm tukkuna ya kammala yay addu'ah sosai, ya tashi ya hau gado tare dayin addu'an bacci ya kwanta ruf abunshi. Nima d'in 😲hamma nai na fita dga dkin na koma tsohon d'akin nafisa na kwanta abina saboda tsaro😉... Washe garin ranar, aliyu bayan ya tashi shida abbi suka tafie masallaci sukai sallah, suka koma kai tsaye d'akin ummi y nufah ya gaisheta, ya d'an zauna suka tab'a firan yaushe gamo tukkuna yay nashi d'akin, yana shiga ya dauki wayanshi ya kira waya wnda wannan ba kowa bane y kira face shafi'u "Ka shirya kazo muje xuwa 10am" Shine kawea abunda ya fadamsa yayinda shafi'uh ya amsa da to "zakin duniyah" Aliyu ya maida wayan ya kashe, ya juya kenan xai kwanta sea ga nana ta shigo a d'akin, kallonta yay tukkuna ya basar ya juya, cike da izzah da gadara ta fara masa magana "Kai kana ganina bazaka gaisheni ba, kasan bana wasa dakai dea ko". Aliyu tashi yay ya sakko dga kan gadon ya tsaya dea2 inda take tsaye "Nana" Aliyu y kira sunanta, cikin kakkausar murya ya fara yimata magana, irinta mazan da basa tsoro "Daa ba ynxn bace, idan kinmin chaan daa na d'auka to kisani ynxn bazan d'auka ba, kada ki kuskura kice zaki shiga gabana, get out of my sight". Ido nana ta zaro ta kalleshi "Aliyu ne ke fadamata irin wad'an nan maganganun, lallai tana buqatar tashi tsaye gamedashi" Fuu ta wuce ta bar d'akin yayinda aliyu ya koma ya kwanta, kusan karfe 9am ya tashi, a gurgujie yay wanka y chnza kayah zuwa kana nan kaya, ya daukie wayanshi yay kasah tare da saka brown din glass, breakfast ummi ta hada mashi da kanta, kad'an yaci tukkuna yasha ruwah... Like · 1 · Reply · Report · Aug 1 at 10:24pm Kausar M Hassan *ALIYU_HAYDAR* Page ((19)) ©Kausar M Hassan Ba'a dau wani lokaci mai tsawo ba sea ga shafi'u yay sallama, amsawa sukai a gurgujie suka fitah gidan, tare dayiwa abbi da ummi sallama. Suna fita kai tsaye wata hanya suka mik'a, sun jima akan titi tukkuna suka yanka ta wata hanyar suka isa a wani d'an kauye, gidajen kauyen duk aksarinsu ginin bulun kasa ne, gidan cement bai wuce 5 zuwa 6 ba. Kopan wani gidah shafi'u yay parking, gidan matsakaicine mai kyau da haske a wajenshi. Bayan shaf'u yayi parking duk suka bud'e motan suka fitah, dea2 kopan gidan suka same yaro, aliyu yace "Kajie kace wea ana kiran mame" Yaron dayake bazai wuce shekara 10 ba, ya kuwa dushie kopan gidan ya shiga tare da sallamanshi. Mame dake zaune kan tabarma ta amsa masa sallaman. "Wea ance ana kiran mame" Jin sunan da aka ambata yasa mame hawaye take, ciki da zumud'ie ta amsa masa da "Kace nace ya shigo" Yaron fita yay ya koma inda su aliyu, ya fadamasu sakon mame tukkuna ya wuce abinshi. Glass din dake fuskanshi ya cire ya maida aljihu, tukkuna ya d'ago idanunshi ya dubie shafi'u "Shafi'u ka bari in shiga in fito" Shafi'u kai y d'aga masa alamar "to". Taku y fara kaman wnda babu laka a jikinshi tare da goge hawayen da keta faman yimai zarya dga ido zuwa fuska... A hka ya shiga gidan dauke da sallama, mame ta amsa, dukansu suka kasa magana, sea chaan ya rage tsayenshi "Mame I miss you su much" Mame rungumo d'anta tai da duk idanunsu sun cika da kwallah. Kusan minti 3 suka d'auka a hka tukkuna aliyu ya zaunah kan tabarmar da mame take zaune akai, ya kama hannunta ya rike gam. Cikin muryan kuka aliyu y fara magana "Mame shekara nawa rabona dake, har ynxn idanuna na kallon rabani dake da abbi yay, wannan abun yana cikin zuciyata mame, shine mummunan abu da bazan ta6a mantawa dashi ba a rayuwana, ina ganin hawayenki akaina mame". Hawayenta ta share tukkuna ta fara magana "Allah yayi dare aliyu gari ya waye, komai lokacine d'ana! Nayi bakin cikin rabuwa dakai da nai aliyu, tun bayan rabuwana dakai rayuwata take cikin kunci da tashin hankli, bansan yaya kake ba a wanne hali kake ba, ni har na yanke kauna da ganinka aliyu" Aliyu yay murmushin takaici "Mame kinsan kuwa ko bayan na kammala degree dina lokacin ina service nata nemanki ban sameki ba, haka har na kare na koma nayou masters dinah, na dawo gidah na koma, sea a wannan karon abokina Shafi'u ya gano inda kike mame, mame mai yasa baki neman ba". Mame tai shiru na d'an lokaci tukunna ta kalleshi "Aliyu y zanyi da rayuwar dana tsinci kaina a ciki kuwa, abbinka yace kada in koma shigar masa gida shiyasa" Aliyu y nisa ya dubieta "Mame kinyi aure ne"? Kai ta girgizah mashi alaman a'a, hannunta y qara rikewa "Mame mai yasa"? Kallonshi tai duba na tausayi "Aliyu bbu komai , kaga bani labarin ka, kukan nan ya isa hka kaji ko"? Tasa hannu ta share masa hawayen. Murmushi yay tukkuna ya kara duban mame😊😄... Humm Life is some how *KABHI KUSH KABHI GHAM*😉... sun dea jima tana jin labarin rayuwanshi da yanda yay karatu, wani lokacin tai daria wani lokacin ta girgiza kai, haka sukai sallama tare da bata tabbacin zea rika zuwa akai2, kaman kada su rabu da juna.. 😭soyayyan uwa da "ya "ya kenan... Ya Allah ka sakawa iyayenmu da alkhairi, wad'anda suka rigamu gidan gskya a cikinsu ya Allah kai masu gafara, ka yafemasu, ka sasu a aljanna firdaus... Aminnnnnnnnnnnnnnn👏🏽 Fitowa yay ya tarar da shafi'u zaune a cikin mota har y fara gyangyadie. Hannu yasa y fara bubbuga kafanshi, firgigit yay ya tashi, basu tsaya dogon zance ba suka karasa gidah, kai tsaye aliyu ya nupie d'akinshi, a kopar d'akin yaci karo da nana😚 Kallonshi tai, zatai wata magana, aliyu ya dga mata hannu tare da cewa "Shhhh! Y isa hka nana, bana tsoronki dama chaan bana tsoronki kada ki kuskura ki shiga harkata, kingane ko? Matsa ki bani hanya in wuce". Ido ta bishi dashi yyinda yake shirin bankad'arta ya fice, a cikin zuciyanta take cewa "Ina buqatar in chnza taku" Ta kama hanya tai d'akinta. "Oh su nana anki aure dai🤔 Washe garin ranar aliyu ya tashi da safe ya shirya yay wnka kai tsaye ya fitoh, yana fitowa kasa ya tarar da ummi, ummi da murna ta tarbieshi "D'ana sauko ga abunci na dafa maka" Da sauri y karasa ya zauna kan dinning d'in ta zuba masa soyayyen kwai da farfesun naman rago, sunan Allah y ambata tukkuna ya fara cin abuncin, kad'an y tsakura, ya yunkura zai tashi sea ga abbi. Aliyu y koma ya zauna, suka kara gaisawa da abbi, abbi y ciro key a aljihunshi ya mikawa aliyu, aliyu y kar6a ya jujjya key din "Abbi wannan ai key din motane ko"? "Eh shine aliyu, motan na nan waje farace, anyi mata duk abunda take buqata, sbd hka na baka wannan mota d'ana". Gdya Aliyu yay wa abbi tukkuna ya maida dubanshi ga ummi "Ummi kimin gdya ni zan tafie gidansu shafi'u sea na dawo" Fita yay dga gidan dea2 lokacin misalin karfe 9am. Kai tsaye gidan mame ya nupah. Like · 1 · Reply · Report · Aug 1 at 10:24pmDOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Kausar M Hassan *ALIYU_HAYDAR* Page ((20)) ©Kausar M Hassan Dea2 kopan gidan yay parking motanshi ya fito ya shiga, koda y shiga ya tarar da ita tana sharah, tsintsiyar hannunta y kar6a ya karasa sharan tukkuna suka koma d'aki, kan kafafun mame y d'ora kanshi sunata fira abunsu bayan d'an lokaci aliyu yay mata sallama dga nan ya zarce gidansu shafi'uh. Bayan kwana 2! Aliyu ne ya fito dga motanshi dauke da ledojie guda hudu, ya shiga dasu, ya baiwa mame. Amsa tai tare dayimasa addu'ah, shikuma yay mata sallama y kama hanyar fitah. Akan hanyarshi ta fitah, ya hangi wata kyakyawar halittan Allah, tana tafiya sanye cikin hijab iya guiwantah, yarinyr black beauty ce, gata da tsayi dea2 misali, ga tsinin hanci, son kowa kin wanda ya rasah, shekarunta bazasu zarce 14 ba. Aliyu bai san sanda y taka birki ba, ya kura mata idanu har ta kusa giftawa ta gabanshi, a hnkli yace "Malama sannu"! Fararen idanunta ta d'ago "Malam zaka siya goro ne"? Cikin rawar murya ya amsa da "E... Eh... Zan siya nawa nawa ne" Kasancewar goron kashie2 ne, yasa ta zaro siraran yatsunta ta fara nuna masa. "Wannan goma, wannan manyan kuma ashirin, kullin kuma naira hamsin ne" "Juyemin shi duka, gaba d'aya zan siyah" Ido ta zaro "Malam na dari biyar nefa" Kapin ta kara wata maganar ya ciro naira dubu a aljihunshi y mika matah. Ido ta zaro, sea hawaye shar a fuskanta "Ni gaskya ka dau kudinka bazan siyar maka ba" Kapin aliyu bud'e baki yay wata magana yaji ana kiran *DIJE*. da hanzari ta amsa da "Na'am! Ina zuwa", da gudu2 ta bar gurin zuwa inda ake kiranta. "Dije" aliyu ya jinjina sunan, kawea y gyad'ah kai tare da juya starin motan. Dad'ina da mota aiki, maza irinsu Aliyu kuwa akuy yawu amma fa akuy jan aji, hka y wuni yana zaga gari shida shafi'uh. Misalin 10pm! Aliyu ne kwance akan gado, ya kasa bacci kalma d'aya rak kemasa yawou a cikin zuciyanshi watou Dije, shin mai yake faruwane ya tambayi kanshi Humm *KUCH KUCH HOTA HAI* Aliyu.😉 Tunani ya hau yi chaan kuma ya yanke shawaran komawa gobe dmn ganin dije... Wa yaga dije 14 years da aliyu😂 wea rigima da aiki... WACECE DIJE?? ®Kausar Luv💞 DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((21)) ©Kausar M Hassan Khadeejah Muhammad, wannan shine ainahin sunanta wadda aka fisani da dije a kauyen su dake chaan yamma da garin sokoto, a kauyen da suke zaune, suna rayuwa ne kmn sauran al'umma shekarunta 14 a duniya, tayi karatun islamiyya dan har ta sauke al_qur'ani mai girma, a 6angaren karatun zamani kuwa ta kammala primary school dinta a nan wata makaranta dake cikin kauyen. Washe garin ranar aliyu y shirya cikin manyan kaya, bowel ne a jikinshi fari tas ya saka takalminshi farare da farin agogo, da sauri2 ya fara sakkowa dga d'akin nashi, a falo y tarar da kafatarin ilahirin iyalin gidan Alhj shuraihu isah zaune kan dinning table, kusa da ummi yaje ya tsaya ya gaisheta ya gaida abbi tukkuna yaja kujera ya zauna. Addu'ah sukayi tukkuna suka fara breakfast din, bayan sun kammala, abbi ya dubie aliyu y kira sunanshi "Aliyu" "Na'am abbi" Abbi yay shiru kapin ya d'ago idanunshi ya dubie aliyu "Aliyu kaga dea Allah ya horemin a matsayina na mahaipinka na baka suna mai kyau da ma'ana, nasaka a makaranta kayi karatu, na maka tarbiyya, ynxn abu 2 ya rage mani, kuma kaima ya rage maka, wannan abun kuwa ba komai bane face ka fara aiki, idan kana buqatar aiki a tare dani sea a baka manager na company dinmu idan kuma baka so to sea ka nema wani, ynxn kai nake jira mai kace"? "Am gskya ni abbi inasone in fara business, dama munyi magana nida shafi'u akan hakan" Abbi ya nisa kad'an "To aliyu Allah y tabbatar da alkhairi sea kuma magana ta 2 wato maganar aure, ykamata kayi aure dmn aure shine cikar addninka kuma shine zai nuna cewa gashi yau aliyu y zama babba" Kai ya sosa tukkuna ya amsa da to abbi a bani lokaci zan fito da matar da nakeso in shaa Allah. Ummi tai daria kad'an "Oh wea su aliyu sea zama ango, Allah ya nuna mana" Duk suka amsa da "amin" Nana itama ba abarta a baya ba, nan take ta fara samun daman had'a wani sabon makircinta.. Aliyu tashi yay, yayinda abbi ya dubieshi cike da mamaki, ya fara tambyrshi "Aliyu kwana 2 d'in nan fa na rasa ina kake zuwa fa" Cikin rawar murya ya amsa da "Abbi ina d'an zaga garine" Abbi yace "A dawo lpy aliyu haydar" Sallama yay masu dea2 lokacin misalin karfe 10am y kama hanya bai tsaya ko inaba sea kauyensu dije, dea2 kopan gidan mame yayi parking tukkuna ya shiga gidan, bayan y shiga sun gaisa, ya zaunah kan kujera kanshi akan kafafun mame. "Mame" Aliyu y kira sunanta "Aliyu ya akai ne"? "Mame wea dan Allah mai kikaiwa abbi ne a rayuwa daya tsaneki haka"? Ajiyan zuciya mame tai tukkuna ta amsa da "Aliyu wannan Allah ne kad'ai yasani, nidea nasan lpy nake zaune dashi, har kawo ranar daya sakeni, bazan iya cewa komai akai ba sea dea ince Allah yay mana maganin abunda ke damun mu" Aliyu ya tashi xaune "Mame to mai yasa kika dawo kauyen nan da zama"? "Wato aliyu wannan kauyen da kake gani, akuy zaman lpy a cikinshi, bayan rasuwar mahaipiyata yan uwan Babana suka matsamin akan sea nayi aure, nikuma banaso, shine fa inada yan kudina nazo nan na siya wannan gidan, aikin ma daa na d'an fara kuma sea na watsar, ynxn hka dea business akemin na acahaba da kuma keke napep" Aliyu y nisa tukkuna yace "Allah y sheigiemana gaba mame" Duk suka amsa da "amin" Har karfe 11am tai suna zaune suna firah kapin aliyu yay wa mame sallama ya kama hanya y fitoh waje yana duddubawa ko zaiga dije...DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Like · 2 · Reply · Report · Wednesday at 9:45pm Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((22)) ```©Kausar M Hassan``` Kaman dga sama y hangota tana tafiya rike da faranti a hannunta, da alama inda yake zata biyou ta wuce, wani d'an dakali ya samu y zaunah kapin ta karaso. Hka take takunta kaamar d'awisu har ta karaso inda yake zata wuce ya kira sunanta "Dije" chack taja ta tsaya tare da waigowa ta dubieshi, ta gane fuskanshi sarai Fuska ta had'e ta dubieshi "Gani" "Kizo zan siya goro" A cikin ranta ta furta "Wannan d'an gayun mai zai da goro ne nikam" Matsawa tai kusa dashi, cikin shagwa6a ta fara magana "Gani" Murmushi aliyu yay "Am dije sunana Aliyu, kefa"? "Sunana Khadeejah amma ana kirana da dije, dijen inna" Aliyu ya jinjina tukkuna ya cigaba da cewa "Dije ina ne gidanku" Kallonshi tai da idanunta "Mai sa zan fadamaka gidanmu? Kuma da alama kai d'an birni ne, nasan ko mai zakamana a gidan" Aliyu baisan sanda yay daria ba "Dije ni bazan cutar dake ba hasalima ni wlh sonki nake, kina sona"? "Kai! Chabb ai mu bama soyayya a gidanmu kawea dea aure ake mana, ynxn haka duk kawayena sunyi aure ni d'ayace banba, shima sbd wanda zamuyi aure dashi watanshi d'aya da rasuwa ynxn". Aliyu baisan sanda y furta "Kina sonshi to kapin ya mutu"? Kallonshi tai sea hawaye sharr a fuskanta Da sauri aliyu y furta "No!!! Kada kiyi kuka pls dije bana son kina kuka kinji" Cikin muryan shagwa6a ta maida "To ba kaine kake min wata tmbya ba" Kai aliyu y girgiza tukkuna ya furta "Kinga dije zaki zama kawata"? Kallonshi tai ta yatsine baki "To amma fa, banda min abinda banaso, na amince" Aliyu yy murmushi ya dubieta "An gama dije, to amma inane gidanku"? Wani gidah ta nuna masa, gidan na bulu da cement ne. Aliyu y nisa "Zan iya binki muje naga kaman gidah zakijie ko"? Kai ta d'aga masa alamar eh. Tashi sukai suka jera suna tafiya, mutanen kauyen sea kallonsu sukeyi har suka karasa kopan gidan. Tsaye sukayi dea2 kopan gidan. Aliyu ya kalleta "To zan iya zuwa muna gaisawa da kawata ko"? Hannu tasa a baki tare da d'aga masa kai. Aliyu yay mata sallama har zai juyo sea y juyah yaga tana nan kuma shi take kallo, kusa da ita yje y tsaya "Dije kinada wayan hannu"? Kai ta girgizah masa. "Idan na kawomaki xaki kar6a"? "A"a" ta bashi amsa a takaice.. Murmushi aliyu yay "To ni zan komah dije sea na dawo gobe ko"? "To" shine kawea amsar data bashi, ya juya ya kama hnya y shiga motanshi ita kuma ta shigah gidah.DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Like · 1 · Reply · Report · Wednesday at 9:47pm 1 reply Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((23)) ```©Kausar M Hassan``` Tana shiga tai sallama tare da ajiye farantin da take tallan goron dashi, yar matashiyar matar dake tsaye ta dubeta da alama mamanta ce dan suna kama "Dije har kin dawo"? "Eh inna na dawo wlh nagajie bbu abunci a gidan"? Inna ta dauko wani kwanon ta'sa dake kusa da ita ta mika mata "Ga shinkafa nan dazun nan na siyeta gurin idi" Kwanon ta kar6a ta tashi ta wanke hannunta ta dawo ta zauna, ta lankwashe kafafunta tasa kwanon a gabanta ta fara cin abuncin. Tana cin abuncin tana tunano kyakyawar fuskan aliyu, da murmushin shi da lokacin da take kuka yake bata hkuri, kawea sea ta tsincin kanta a cikin nishad'i mara misaltuwah, wnda hkan bata iya boyeshi a cikin zuciyanta ba yakai ga har fuskanta ta nuna. Inna dake kusa da ita kan tabarma tasa hannu ta d'an bubbuga cinyarta, a firgice ta dawo dga duniyar tunanin data lula. "dije lpynki kuwa irin wannan murmushin haka"? Dije ta nisa ta dubie inna "Inna kindea san bana boye maki komai ko, to wlh wani d'an birni ne na had'u dashi yace yana sona, to nikuma nasan bama za'a bashi ni ba shiyasa kawea nace masa bama soyayya". Inna ta nisa ta kallie yarta "Kada ki damu kedea kiyata addu'ah kinji ko"? Gyaran muryan da sukajie anayine ya katsie musu zancen "Dije har kin dawo"? "Eh baba na dawo" Dattijon daya zauna kan kujera ya dubiesu "Wace wainar kuma ake toyawa bada niba maman dije"? Inna ta nisa ta dubieshi "Yarka ce ta had'u da wani d'an birni shine fa take fad'amin" Da sauri baba ya kalleta, cikin kakkausar murya ya fara magana "Ko alama dije "yan birni mafi aksarinsu yan iskane, haka suke zuwa kauye su same yara k'anana irinku su lalata masu tarbiyya dga karshe su gudu sukie aurensu, ko kusa kada a fara wannan maganar kinji mai na fad'a ko"? Yana karasa fadar hka ya tashi kai tsaye ya wuce dakinshi. Dije tsintar kanta tai cikin rashin jin dadin da batasan dalilinshi ba, ita dea aliyu y burgeta matuqa. Fashewa da kuka tai na hawaye, wnda yasa inna tashi "To malam gata nan kasata kuka sea kazo ka rarrashieta daman kasan halin kayanka ai da an ta6ata sea kuka" Ta wuce daki, yayinda dije ta tashi ta ture kwanon abuncin, ta wuce dakinta, ta fada kan katifar dakin ta cigaba da hawayenta..DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((24)) ©Kausar M Hassan Aliyu kuwa daga nan kai tsaye gidansu shafi'u ya nupa, a kopar gidan suka hadu suka d'unguma suka karasa gidan, a d'akin shafi'u aliyu y kwanta kan gado, yayinda shafi'u ke zaune akan gadon shima. Shiru sukai kaman wasu strangers, chaan shafi'u y fara magana "Abokina wea lpy ne dan Allah, naganka so silent, kmn ba lion ba" "Humm! Kadea ka bari kawea abokina wlh na kamu, wata yarinya ce chaan d'an kauyen nan nasu mame, na rikice a kanta wlh, kuma kasan me"? Shafi'u ya girgizah kai "Sea ka fad'a lion"🦁 Aliyu ya tashi zaune "Shekaranta 14 fa" Daria Shafi'u yay sosai tukkuna yace "Hba aliyu ina kai ina "yar 14yrs, nafa san halin kayana yo ai sea ka 6allata" Hararanshi aliyu yay "Tunda ka maidani har...ji ko? Murmushi Shafi'u yay "Aliyu kafa san gskya, kada ka aure yarinyr mutane wlh ka halakata nidea na fadamaka, inama laipien ka samu yr shaa takwas hka"? Aliyu ya dubieshi "Man! Ni ita nakeso, zan iya hakura har ta kai girmanta indea za'a yarda a auramin ita" "Hhhh! Kai wlh aliyu kana bani daria nidea, kasan ynda Allah yay maka desire dayawa fa, ynxn dea tashi muje yunwa nakejie wlh, dan ko breakfast banyi ba". Tashi sukai suka runtuma cikin gidan, kai tsaye gurin ammi (Maman shafi'u) suka nupa dama ta had'a mashi breakfast, suka dauko suka dawo dakin, Shafi'u nacin abuncin yana faman ketawa aliyu daria... ```Bayan sati 2.``` Aliyu ne kwance a d'akinshi, tunanin dije kawea ykeyi, yanda take murmushi, tafiyanta, kurciyanta, yar siririyar muryanta, kai komai na dije burgeshi yakeyi, amma mi? Shi kanshi yasan dije bazata iya daukan lalurarshi ba, amma hak'uri zayyi koda ya aureta har ta girma. "yes hka za'ayi" Nan y tashi y shirya ya kamo hanya lokacin misalin dea2 karfie 12pm. Yana isa gidan mame ya zarce ya ajiye motanshi ya shiga suka gaisah. Hannunta ya kama "Mame inasone in fad'amaki wata magana" Mame ta gyara zamanta "Ina jinka d'ana menene" Aliyu ya nisa "Mame naga wata yarinya a garin nan sunanta dije yar gidan malam mamman, kuma nidea ina sonta da aure wlh". Mame tai ajiyan zuciya "Aliyu kai ynxn ya zakayi ka aure dije? Naga kaman tai karama ai" Aliyu yace "mame nidea ina sonta pls, ya kikaga halayenta"? Mame tai murmushi "Ai dije yarinya ce mai kirki wlh, batada matsala, gata da son addini, halayetna kam sea dea muce Allah sam barka". Aliyu yace "To mame ngd, ni zan tafie gidansu dga chaan zan wuce, ko akuy wani abunda kike buqata"? Mame ta amsa da "A'a, komai da nake buqata ka bani shi, Allah dea yay maka albarka" aliyu ya amsa da "amin" Hka ya kama hanya ya fitah bai tsaya ko inaba sea kopar gidansu dije, ya samu yaro ya aika yace ya kira masa itah, haka kuwa akayi yaron ya shiga y kirata, ta bashi amsa daDOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ga tana zuwa.... Like · 1 · Reply · Report · Wednesday at 9:47pm Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((25)) ©```Kausar M Hassan``` Hijab d`inta ta saka kaman ynda ta saba tasa takalminta ta fitoh, a natse ta gaisheshi ya amsa tare da kallon kyakyawan fuskanta. A hnkli ya fara furta "Dije nifa ina tunanin ykamata in sanar a gida saboda azo ayi maganar aurenmu ko"? Kallonshi tai take idanunta suka cika da kwallah "Yaa aliyu babana yace "bazai aura min d'an birini ba saboda yan birini bakuda amana" Kallonta yay ido cike da mamaki "Dije mai yasah? Ni ba haka nake ba dije, ga gidan mahaipiyata chaan za'a iya tmbyawa aji yaya halayena suke idanma ba'a yarda ba zan iya bada address din unguwarmu sea a tafe chaan a duba, amma mai yasa kike kuka"? Hawayenta ta share ta kalleshi "Yaa aliyu haka nake da saurin kuka, bansan daliliba" Kallonta ya k'ara yi, cikin muryan rad'a yace da ita "Sona ne yasa kike kuka, idan ba haka ba mai zaisa ki kuka dan ance bazaki auri d'an birni ba" Idanunta ta d'ago ta kalleshi ta k'ara saukar da kanta kasa. "Nifa.... Kapin ta karasa sea ga baba ya karaso gurin, take jikinta ya hau rawah. Hawaye suka dinga zarya akan kumatunta. Baba a zuciye ya karaso inda suke, gadan2 yay kanta "Ke dan kina mutuniyar bnza ban hanaki tsayuwa da wad'an nan yaran yan birni ba, bakisan cewa basuda kirki ba" Aliyu ido yabi baba dashi sbd ynda yaga ya dage yanata faman zuba fada. Hannu y d'aga zai mareta, aliyu da karfe y rik'e baba "Baba dan Allah kai hkuri kada ka mareta, laipiena ne kuma bazan kara zuwa gurinta ba" Jin haka da dije tai yasa ta ruga da gudu ta shiga d'akin inna, kan kafafunta tai ta kuka. Sun jima tsakanin aliyu da baba suna tattaunawa tukkuna, aliyu ya wuce baba ya shigo cikin gidan. Har y shigo kukan takeyi, kusa da ita yaje ya zauna, cikin muryan lallashi "Dije basonki da yaron nan ne banayi ba, amma ki duba arziki da nasu da namu ba d'ayah ba dije, muna rayuwar mu cikin rufin asiri yazo yace zai aureki ya lalata maki rayuwa dije shine abunda banaso, sarai ya fad'amin gidansu yxn kuma nasan babanshi yanada kud'i, ai ga mamanshi nan a kauyen babanshi ya saketa, wannan shine halin "yan birni" Tashi tai ta dubieshi, ido cike da kwallah, idanunta sunyi jajir. "Baba aliyu yanada halaye masu kyau, baya d'aya dga cikin wad'an nan mutanen da kake tsammani, d'an saninshi da nai na sati 2 yasa na k'ara sanin wasu abubuwa na addini baba, baba ka bashi dama dan Allah, ba'a sanin nagari sea an gwada, na tabbata watarana kai da kanka zakace gwanda da akayi haka, in shaa Allah". Inna ta kara da cewan "Haka ne gskya malam, dan kaga kullum nan yake iskota a kopar gidan, idan ta fita ina lek'awa wlh ko kusa da ita baya zuwa balantana wata mummunar hali ta biyo bayah". Baba yay shiru na d'an lokaci tukkuna yace "To Allah ya za6amana abunda yafi zama alkhiari, na bashi dama Khadeejah" Hawayenta ta share tai murmushi tare da chusa kanta a jikin inna tana daria. Aliyu ne akan hanya zuciyanshi sea kuna take yimasa, driving yakeyi, bai sanma ta ina yake bi ba, kaman dga sama wata babbar mota ta gibto ta gabanshi, Allah ya tsare da sunyi karo da juna, ya taka birki ya buge wata motah, take sea ga jini a jikinshi, kasancewar akuy mutane a gurin aka samu na Allah suka kaishi asibiti tare da taimakawar wani d'an sanda.. Suna isa kuwa aka fara dubashi, bayan an kammala treating dinshi, mutumin daya kawoshi, yaji wayan aliyu dake hannunshi na ruri, wnda wannan ba kowa bane face shafi'u. D'an snda bayyi k'asa a guiwa ba ya sanar dashi abunda ke faruwa, take shafi'u y kira ummi ya sanar da ita halin da ake ciki. Babu 6ata lokaci suka angaya zuwa asibitin, in banda nana... Hka suka tarar da d'an sandan ya mika masu key din motan aliyu da waynshi ya kuma k'ara shaidamasu ynda abun y faru, gdya sukai masa tukkuna suka wuce d'akin dayake kwance... ```Bayan sati 3``` ```Dije``` ce zaune akan tabarma ta kifa kanta akan guiwuwinta, hawayene keta faman zuba a idonta, inna ce gefenta ta dafata "Dije kiyi hkuri dama malam y fadamaki halin yan birnin, sea kiyi hkuri ai" Idonta ta d'ago ta kallie inna "Hba inna ni na tabbata yaa aliyu bazeayyi haka ba, ko gidan mamanshi fa ya deana zuwa fa, tabbas akuy wani abu a qasa, nidea dan Allah inna a bani dama injie birni indibo ko lpy" Ido inna ta zaro ta dubieta "Ke dije kin kuwa san mai kike cewa"? Kapin tai wata magana baba ya shigo gidan "Dije baki ba zuwa birni kuma dan kisani, Illu d'an gidan malam saminu to shi zaki aura nan da sati 2 kima manta da batun wannan aliyun" Bugun zuciyanta taji ya k'aro, hnklinta ya matuqar tashi, cikin rawar murya ta fara magana "Haba baba dan Allah kayi hkuri, ka bani lokaci" "Babu wani lokacin da zan baki, idan zakiyi hakuri to kawea kiyi hakuri". Wucewa yay d'aki, yayinda dije ta fadie qasa kan kafafun inna ta hauyin matsanancin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro.. Oh poor dije, wannan soyayya, son gaskiya kenan.. To y lbrn Aliyu???DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ®Kausar Luv💞 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((26)) ```©Kausar M Hassan``` Chaan cikin wani d'aki na hangoshi, rufe da abun rufa iya kirjinshi, da alama ya fara samun sauki, shafi'u ne kusa dashi. A hnkli2 aliyu y fara bud'e idanunshi, ya kallie d'akin dayake ciki, sea y fara tunano abunda y faru, da sauri y mieqie zaune, shafi'u dke kusa dashi yay maza ya rike hannunshi "Aliyu ka tashi ne, y jikin naka" Dkyar y iya bud'e baki ya amsa da "Alhmdlh" "Shafi'u dije fa"? Ajiyan zuciya shafi'u yay tukkuna ya kallieshi "Haba aliyu ko ta kanka bakayi dga farkawanka yau sea kuma batun wata dije" Kallonshi aliyu yay "Shafi'u ina buqatar ganinta yau kuma, dan Allah ka daukeni mu tafie" Cike da mamaki shafi'u yke kallonshi "Kaga aliyu nifa bazan maka alkawari ba, ka tsaya ka samu sauki mana" Dea2 lokacin ummi ta shigo d'akin, murmushi tai tace "Duk naji abunda kuke fad'a, amma aliyu ka bari ka samu sauki mana, ko kuma shi shaf'u yajie ya dauko ta ta ganka, ko ba anan gari take ba"? Juna suka kalla tsakanin aliyu da shafi'u. Shafi'u ya gyara zamanshi ya kara duban aliyu "In fadamata"? Kai Aliyu y dga masah, yayinda shafi'u ya labartawa ummi komai tundaga biri har wutsiya y fydie mata. Ummi ta jinjina al'amarin tukkuna tace "Kai aliyu ina kai ina yar 14yrs, mamadin ka dauko yar 18 dama2 ko 20" Ajiyan zuciya ya sauke "Ummi nifa ita nake son in aura, dan Allah ki fad'awa abbi". Murmushi tai tare da cewan "Ya isa hka zan fadamasa kuma zasu tafie tare da shafi'u dmn a tambya maka aurenta". Murmushi yay kad'an "Ummi ngd" Bkomai d'ana wannan wajibinane, ka samu ka huta kaga jikinka yay sauki nan da kwana 2 Dr yace za'ayi discharging dinka kaji ko"? Kai y daga mata yayinda ya tuna da maganar da sukayi da baban dije. ********* ```Bayan sati 1!``` Ummi ce zaune akan kujera ta mike kafanta, yayinda aliyu ke dakinshi, sanye cikin kana nan kayah, rigan mai d'an guntun hannu da wandon hka iya guiwa, babu abunda yake tunawa in banda dije, ko awanne hali take ynxn Allah ne kawea masani". Ummi ta kallie abbi "Alhj dama aliyu ne y aikoni" Abbi y gyara zama ya maida hanklinshi gaba d'aya y tattara y mika mata 'Ina jinka mai y fad'a halan"? "Nan take ummi ta fad'amasa komai ke faruwa akan yarinyar da aliyu y gni kuma yakeso". Abbi jim yay kad'an tukkuna ya maida "Ya zayyi da yar shekara 14 kuma, kuma yar kauye"? Ummi murmushi tai "Au ka manta chaan daa hka akeyin auren kuma a zaunah, kai dea kawea ynxn kaji sakonshi". Abbi yay murmushi "Yo ko ban aminta ba ai nasan ke zaki shigiemasa gaba tunda ni kun maida ni barie, ynxn dea idan Allah ykaimu nan zuwa next week zan shirya in tafie in shaa Allah". Murmushi ummi tai "Hba ko kaifa, ai hka yafi nasan d'ana aliyu sarai zabin kirki zayyi" Daria sukai dukansu yayinda ummi ta tashi "Ina zuwa kuma"? Da mamaki ta kalleshi "Zan shaidawa d'ana cewan ka amince mana" Daria sukai dukansu kapin nan ta haura sama ta shaidawa aliyu ynda sukai da abbi, murna yay sosai da kuma fatan Allah yasa a dace... Like · 1 · Reply · Report · Thursday at 2:46pm Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((27)) ©Kausar M Hassan Aliyu tsintar kanshi yay a cikin shauki da jin dadi, yau shine za'a tafie tambyowa auren dije, dije masoyiyarshi abun k'aunarshi da alfaharinshi, gaskiya yanaji da wannan rana ta yau. ****** A chaan kauye kuwa, mame hankalinta a tashe ganin har yau wata d'aya y cika cib bata saa d'anta a ido ba. Zaune take kan kujera tana sauraren wa'azin Dr mansur sokoto, hanklinta rabuwa yyi gidah 2, tunanin d'anta duk y tafie da ita. Sallama tajieh, ta amsa sallaman tare da bada izinin shigowa. Shiga tai d'akin ta cire nikab din datasa ta zauna kasa, duk ta ramie dama abu chaan ba kiba ba, kai da ganinta kasan tana cikin tashin hnkli, gaisawa sukai da mame tukkuna tace "Mame kwana daywa banga Yaa aliyu ba, ko lpy"? Mame ta kalleta "Khadeejah ni kaina nan da kike gani rabona dashi kimanin wata 1 kenan, fatana dea Allah ubangiji yasa lpy". Kuka dije ta fashe dashi wnda ita kanta tasan na rashin ganin aliyu ne. "Mame ynxn shikenan ko bankwana bazanyi da yaa aliyu ba, gashi yau saura kwana 5 baba yamin aure" Tashi mame tai tsaye cike da tashin hnkli "Khadeejah mai kike cewa ne, aure kuma"? Kai ta d'aga mata alaman eh "Mame dan Allah koda sau d'ayane ki d'an gwada kira minshi a wayar hannu". Mame ta sauke ajiyan zuciya "Wayanshi baya shiga dije, ynxn dea abunda nakeso dake tashi mujie gidanku inyi magana da babanki ko Allah zaisa yay hkuri ya kyale maganar auren nan" Hannu dije tasa ta rike hannun mame tare da girgizah mta kai "Mame dan Allah kada kijie, banason nabana ya wulqantaki, bazanjie dadi ba, inajinki kaman ynda nake jin mahaipiyata, dan Allah mame" Hannu mame tasa ta share mata hawayen fuskanta "Ki deana kuka to kiyita addu'ah in shaa Allah indea aliyu mijinki ne to zaki aureshi". Murmushi tai ta maida nikab dinta tasa taiwa mame sallama, ta koma gidah. A chaan bangaren aliyu kuwah, tun bayan da yay accident shafi'u ya kashe wayanshi sbd yawan kiran da ake masa, to har fa yau bai kunna ba, yama manta shafff... A kwana a tashi babu wuya ga Allah, Allah ya kaimu yau ranar illu da nana Khadeejah Muhammad AkA dije za'a d'aura masu aure. Kuma ranar ne da Abbi ya shirya shida shafi'u da kuma zubairu dmn nemawa aliyu auren dije. Shafi'u tunda safe ya isa gidan ya mikawa aliyun wayanshi, da aliyun keta faman murmushi, duk wannan shagalin da akeyi Nafisa na sane kuma tana yiwa yayanta addu'ah, itama nana tana sane tare da cigaba da shirya makircintah... Hka suka kama hanya zuwa wannan kauyen ***** Karfe 10am, dije ce sanye cikin wata shadda wadda kudinta ba zea wuce 2000 ba, tayi d'an kwalliyanta dea irin nasu na kauye, kai da ganin idanunta kasan tana cikin bakin ciki da tashin hnkli. Kawayenta duk suka zagayeta da yan uwa, dea2 lokacin kuma aka fara shirye_shiryen d'auren aurenta da ilu saminu. Su abbi na kan hanya, a nan kauye kuma ana rabon goron d'auren aure...DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Like · 1 · Reply · Report · Thursday at 2:46pm 1 reply Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((28)) ```©Kausar M Hassan``` Parking sukai dea2 da kusa da gidan mame, da hanzari suka kama hanya kasancewar mota tai kai 3 wadda suka shigo dan harda baban shafi'u suke da mijin nafisa, hka suka karasa kopar gidan dea2 lokacin za'a fara dauren aure. Ganin su abbi da akai yasa aka d'an dakata aka maida kallo garesu, abbi yay wa shafi'u magana a kunne "Ina baban yarinyar"? Chaan Shafi'u ya hangoshi ya shaa shadda miyan goro, sea kyallie takeyi, "Gashi chaan abbi" Abbi da kanshi ya tattaka tare da rakiyan shafi'u da zubairu suka karasa inda yake. Sallama abbi ya masa tare da sanar dashi akuy magana mai muhimmanci data kawoshi. Baba ya dubie jama'an da suka tarou yace "Yayi baki dga birni sbd hka dan Allah a jirashi zea d'an gana dasu cikin gida yadawo" Hanya suka kama suka shiga gidan, suka ratsa matan dke zaune gurin bukin, suka shiga dkin abbi. Bayn sun shiga suka zazzaunah kan tabarma, abbi yay gyaran murya "Am sunana shuraihu isah, inada yaro mai suna aliyu, ya sanar dani cewan yagan yarka mai suna dije kuma yana sonta da aure shine na taso da kaina dmn in nema masa aurenta". Shiru abbi yay tukkuna yace "Alhj kayi hkuri dakai da jama'arka da kuma d'anka sabdoa ynxn hka wannan taroun dka gani, tarou ne da akayi na d'auren auren Khadeejah, saboda na fad'amata cewan yan burni basuda amana, ta bani hkuri akan in bashi damah, to ranar da mukayi magana fa shine bai kara dawowa ba to sea yau dayajie za'ayi mata aure shine zai torou da wakilanshi". Abbi cikin muryna rashin jin dadi yace "Malam kai hkuri, amma ni nasan d'ana mutum ne na dban, yanada kyawawan halaye da hkuri, bazea taba cutar da makiyanshi ba balantana masoyanshi ba, abunda yasa kaga bai zoba to hadarin mota yay" Dije dake la6e tana saurare sea hawaye sharr a fuskanta. Abbi ya cigaba da cewa "To sea ma kwana 2 din nan da suka wuce aka sallamoushi dga asibitin, amma babu komai zan shaida masa sakonka nasan in shaa Allah zayyi hkuri ya kuma mika komai ga Allah, ita kuma Khadeejah Allah ya basu zamn lpy ita da wnda zata aura". Abbi cikin sanyi jikin ya amsa da "amin" Suka kama hanya suka fitoh, yayinda dije ta koma dakin inna da gudu ta hau gadonta ta fara kuka, shi kuma malam Muhammadu ya fitoh waje tare da baiwa Al'umma hakuri, aka cigaba da shirye_shiryen dauren auren dije.. Fatiha 🙆🏾🙆🏾🙆🏾 Dijen zaki tai aure😭DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ®Kausar Luv💞 ``ALIYU_HAYDAR``` Page ((29)) ```©Kausar M Hassan``` Hka su abbi suka kama hanyar zuwa gidah, zuciyoyinsu cike da 6acin rai, musamman ma shafi'u wnda shi yasan irin son da aliyu keyiwa khadeejah, hka suka isa gidan jiki a sanyaye, suka dire a falo. Ummi ce rike da kwano a hannunta na abunci, tana ganinsu da far'anta ta tarbesu ta fara maida magana "To ya akai ne, nasan dea an dace dan babu budurwan da babanta zaikie baiwa d'ana matah, an biya kud'in auren"? Abbi ya dubieta cikin irin tsantsar farin cikin da take ciki, sea ranshi ya qara 6aci, cikin sanyin murya ya fara furta "Hajjah Allah yayi Khadeejah ba matar aliyu bace, ni har banma san mai zan fadamasa ba, kwanon dake hannunta ta saki a qasa, ta zaro idanu cike da 6acin rai tace "Mai yasah"? Nan take abbi ya zayyana mata yanda sukai. Dea2 lokacin aliyu ke fitowa dga d'akinshi, kuma duk yaji abunda suka fad'ah, dga kan step ya fara saukowa, kai tsaye y nupie hanyar fita, da sauri shafi'u ya tarie shi, da hnklinshi yay matuqar tashi "Ina zakaje hka aliyu"? Tmbyr da shafi'u yay masane yasa duk mutanen falon suka maida kallonsu garesu "Shafi'u pls kyaleni gidansu dije zan tafie" Cikin muryan tausayi y fara magana "haba aliyu mai yasa bazakayi hakuri ba, ka daukie kaddara mana". Abbi ya girgizah kai "Aliyu bance kajie gurin nan ba, addininmu y hana neman aure cikin aure kuma ynxn ma kilan har an d'aura mata aure" Idanunshi ya d'ago y dubie abbi "Abbbi dan Allah ka barni in tafie, ni ba wea maganar aure zanba kawea zanmata murna ne". Abbi ya dga masa kai alamar ya yarda, hnya y kama zai fice shafi'u y rike hannunshi "Ina tare dakai through out ur bad times and gud, so lets go" Da gudu2 suka fitah dga gidan, cikin motan shafi'u suka shiga, yayinda shafi'u ke driving din motan, aliyu na gefe yana duba agogo, haka har suka isa kauyen, kopan gidan mame sukai parking. Da sauri suka karasa kopan gidan, koda suka isa babu mutum ko d'aya a kopan gidan, aliyu baisan sanda hawaye suka kwararo a fusaknshi masu zafi ba. "Yanzun dije tayi aure"? Shafi'u dafa kafad'anshi yay "Be strong! Kazo mu samu yaro mu aika muji" Hka akai suka samie yaro suka aika, yaron ya jima bai fitoh ba, koda y fitoh kuma baibi ta kansu ba, da gudu ya fice, aliyu y dubie shafi'u "Anya kuwa lpy? Nidea shiga zanyi wallah" shafi'u yace "Muje to, idanma dukanne sea musha abinmu tare" Murmushi aliyu yay, suka kama hnyan shiga gidan. Tare sukai sallama suka shigah, kowa ya watsie a gidan kaman ba bikin aure ake ba, tsakanin aliyu da shafi'u kuwa kowanne a cikinsu mamaki yakeyi. A cikin gidan kuwa bakajin motsin komai in banda sautin kuka, wanda wannan ba sautin kukan kowa bane face dije..... Da hanzari sukai sallama. Jin sautin muryanshi da tai kamar a mafarki yasa ta share hawayenta ta d'ago idanunta, dea2 lokacin aliyu ya yaye labulen d'akin, sukai ido 2 wani irin murmushi ta sakar mashi. Kafafunshi yasa a d'akin ya shiga kan tabarman da take zauneh shima ya zaunah, shafi'u kuwa tsayenshi yay waje nikam nace sea naga kwam ehe..DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Like · 2 · Reply · Report · Thursday at 9:47pm Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((30)) ```©Kausar M Hassan``` Shiru sukai kapin aliyu y fara magana, cikin zafin zuciya yce "Dije ki deana kuka ki daukie qaddara haka Allah y nupa, Allah y baku zaman lpy keda mijinki" Hawayenta ta share, cikin rawar murya tace "Yaa aliyu amma kasan cewan ka barni da ciwo a cikin zuciyata ko"? Murmushin takaici yay "Kiyi hkuri kinji Dije"., Itama din murmushin tai, zasuyi wata magana sukajie muryan baba. Shiru sukai, lokcin baba ya shigo yaja kujerar roban dake d'akin ya zauna ya dubieshu "Aliyu" Baba y kira sunanshi "Na'am baba" Aliyu ban iya bada auren Khadeejah ga kowa ba, na tabbata kai mai sonta da gsky ne, saboda hka na baka auren khadeejah, Allah yasa abokiyar arzikin ka ce" Murmushi sukai dukansu saboda tsabar jin dad'i, baba tashi yay bar d'akin, yayinda aliyu ya kurawa dije idanu itama d'in shi take kallo. Cikin siririyan muryanshi ya furta "Kukan y isa hka ki deana kuka to" "Uhm2 to kaima ka deana kuka yaa aliyu"? Murmushi yay "Ni yaushe kikaga ina kuka"? "Hararanshi tai kad'an "Hba yaa aliyu, naga kana hawaye fa, kuma ynxn zakace wea bakayi kuka ba"? Gira y d'aga mata "Dijen Aliyu kenan" Ynxn kin kusa zama amarya ta ko"? Hannu tasa ta rufe fuskanta sun dea jima a hka tukkuna aliyu yay mata sallama, fitowa tai ta rakoshi, har lokacin shafi'u na nan tsaye, bayan baba y shaida masa cewan ya baiwa aliyu auren dije. Shafi'u ya dubie aliyu da fuskanshi tai wasai kamn yaune ranar auren. "To kai sabon ango tunda ka samu amarya sea ka manta dani ko"? Murmushi dea sukai, shafi'u yay masu addu'ah da fatan alkhairi tukkuna suka fitah kai tsaye gidan mame suka nupa, mame na ganin aliyu ta tashi ta rungumeshi "D'ana mai ya sameka ne"? Baija lokaci mai tsaye ba y labartamata komai gameda abunda y faru dashi har kawowa yau, mame ta jinjina al'amarin ta maida kallonta ga dije "Dama na fad'amaki cewa idan Aliyu mijinki ne to zaki aureshi ai, Allah y baku zaman lpy, abunda zance daku shine ku rike gskyar ku, ku zama masu rike sirrin junah, Allah y nuna mana auren lpy" Duk suka amsa da "Amin" Sallama sukai wa mame suka kama hnyn fita, har sun kusa fitah mame ta kira aliyu, Aliyu y koma d'akin "Aliyu inason kada ka fad'awa mahaipinka ko wani naka ina garin nan, sbd muddin yasani to tabbas ba zai barka ka auri dije ba" Kai ya d'aga mata "In shaa Allah mame bazanyi ba" "Allah yay maka albarka" Aliyu y amsa da "Amin".. Fita yay yayinda ya tarar da dije da shafi'u jingine a jikin motanshi, shima d'in kusa da ita yaje ya tsaya ya dubeita tare da sakar mata wani irin murmushi, maida mashi da murmushin tai. "To dije ni zan koma bazaki sake ganina ba sea ranar da akace za'a kowamin ke a matsayin mata". Ido ta rufe, cikin muryan shagwa6a ta furta "Kanama farawa"? Murmushi yay "Ni inama zan iya kauda idona akan kyakyawan fuskan matata, Allah dea y kaimana rai da lpy". Amsawa sukai da "amin" Yay mata sallama ya bud'e mota ya shigah. Kaman kada su rabu da junah amma ya zasuyi? Dole suyi hkuri, hka suka kama hnya suka bar kauyen, dije ta kama hanya tai gidah. Suna isa a gidan suka Tarar da abbi da ummi xaune jugum a falon, misalin dea2 karfe 1pm. Zaunawa sukai kan kujera, aliyu y dubie ummi Ummi ta dubieshi "An d'aura mata auren"? Ta fad'a jiki a sanyaye Kapin aliyu yay magana shafi'u ya zayyanawa ummi ynda akai. Murna a gurin ummi da abbi abun ba'a cewa komai... Nana dake tsaye a saman bene take sauraren duk abunda suke fad'a ta jinjina a cikin ranta "🤔 Dije kuma yar shekara 14, wannan zatayi dad'n halakawa da ita da mijin nata, Allah y kaimu lokacin auren, gaba tsakanina da Aliyu ba yau tke ba kuma bazata kare ba, da aliyu da duk wani jininshi, da duk wani masoyinshi sea naga bayansu!!!...DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ®Kausar Luv💞 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((31)) ```©Kausar M Hassan``` ```Bayan sati 2``` A kwana a tashi babu wuya a gurin Allah, Allah ya kaimu lokaci an biya kudin sadakin dije, an kuma had'a kayan lefe naji da gani, aka kai a gidansu dije, abbi da kanshi yay magana da baba akan kada ya damu da kayan daki ko wani kayan amfanin gidah duk shi zai siyawa dije, saboda ya dauketa kaman yarshi daya haifa a cikinshi.. Aliyu y siyawa dije dank'areriyar waya taji da gani, ya kuma koya mata ynda zatai amfani dashi. Aliyu ne zaune a kan tabarmar d'akin inna, yayinda dije ke zaune gefenshi, wani irin murmushin k'auna suke aikawa junansu. "Amaryata ynxn saura sati nawa auren"? Murmushi tai kad'an "Sati 10 ko"? "Chaabb kina wasa kenan" Wayanshi ta hau ruri, koda y duba number d'in wani abokinshi ne mai suna Maher da sukai makaranta tare a KSA, d'auka yay ya fara zuba larabci, dije kafeshi da ido tai, sea bayan dya kammala wayan ya maida kallonshi gareta "Ya akai ina waya naga sea wani kallona kikeyi"? Idanunta ta saukar kasa saboda ta d'an ji kunya "Ashe kana jin larabci hka, amma ya naji larabcin ba irin namu bane"? Kallonta yay "Wannan gargaliya kenan, kinsan a KSA nai karatuna tundaga matakin sakandirie har na kammala masters d'ina" "Lallai kajie d'an balaraben saudiyaa kenan" Daria sukai dukansu tukkuna ya tashi yay mata sallama y biya gidan mame itama d'in sallama yay mata kapin y kama hnya zuwa gidah.. Yana isa gidan kai tsaye d'akinshi ya zarce ya kwanta kan gado kanshi na kallon sama, waya y dauka ya danna kira, wayan dake hannun dije ta hau ruri, murmushi tai ganin sunan daya bayyana akai tare da daukan wayan ta kara a kunne "My lion ina fatan ka isa gida lpy? Dan dea ynxn ka isa zuwa gidah" "Kamar kinsani matata ynxn hka ina kwance kan gado" Dije murmushi tai "To yyi my lion sea ka huta ko"? "Hka za'ayi my queen, amma kinsan me"? Kai ta girgizah masa kamar wnda ke ganinta, Aliyu ya cigaba da cewa "Dije "ya "ya nawa zaki haifamin kinsan ina son yara dayawa fa" Ido ta zaro "My lion to ba sea naci towu dayawa ba zan haifo maka yaran ba". Daria aliyu yay sosai harda rike ciki "Dije mai kike fad'ah haka"? Gyara zamanta tai "Hkne mana yaa aliyu, akace idan mace taci towu mai yawa sea ta haifa yara dayawa idan kuma taci kad'an sea ta haifa yan kad'an" Aliyu murmushi yay "Dan Allah kideana bani daria hka dije" "Shikenan ai zaka gani" Hka sukai sallama da junah, yayinda dije ta bar aliyu da tarin tunani a cikin ranshi, musamman dagewan da tai na cewa idan akaci towu dayawa ake haifan yara dayawa, to badea dije batasan menene aure ba, chaab ashe ko akuy aiki jaa a gabana".DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((32)) ```©Kausar M Hassan``` Misalin karfe 9pm na dare, aliyu ne kwance akan kujeran main falo yana hutawah, ummi da abbi ne suka fito dga kuryan gidan, suma kan kujera suka zaunah yayinda aliyu y tashi zaune. Abbi ne ya fara magana "To aliyu dama cewa nai tunda kunfara business d'in, kuma naga Allah ya sawa abun albarka, to y kamata ace ynxn ka samu gurin da zaka zauna kai da matarka, saboda ba'a nan tare damu zaka zauna ba, saboda hka ga gida nan bayan layin nan na baka shi wannan mai farin paint". Gdya Aliyu yay wa abbi tukkuna yace "Abbi ngd sosai amma ai na siya gidah kusa da nan, na kuma gyarashi, gida 3 ne tskaninmu" Abbi murmushi yay "To duk da haka dea wannan gida na baka shi Allah ubangiji ya baku zaman lpy kaida matarka, tunda ka fara boyemin sirrinka dga kai sea umminka" Daria suka saa dukansu A kwana a tashi babu wuya ga Allah, Allah ya kaimu ranar wannan buki, bukin da aka jima ana tsumayen yinshi, dama ance komai lokacine da lokacin abu yazo sea kaga anyishi. Events 2 akai a wannan bukin, dga walima wadda akayi a masallacin juma'an dake kauyen sea kuma dinner wadda yau juma'ah ta kama ranar yinta. CITY HALL aka kama dmn yin wannan shagalin, manyan mutane sun halarta a wannan buki, nafisa itace ke gyara amarya gurin kwalliya taimata irin kwalliyan yan birni, su shafi'u sune b'angaren ango, hka karfe 8pm ta buga aka fara wannan ciye2 da lashe da d'an kid'a mai taushi. Haka akai dinner din, manya_manyan mutane sun halarta, hkama abokanan aliyu na saudiyaa suma sunzo, gasu farare tas, ko ina suka gibta anga larabawa sea kallonsu akeyi, akan higher table suka zauna aliyu da khadeejah, sea a ranar aliyu yake k'arewa dije kallo, irin yanda Allah yay mata maxaunah masu d'aukar hankali, kasa kauda idonshi yay a kanta. Chaan na hango cwt ummi aysha, maman shakur, fido sodangi, maman khdja (Matar dr), pherty, serdeeyer, zarah b_b, asea b aliyu, basmar er lele, Khdy candy, munay, kdeey, miemie, kai da dea sauran su, wai sunzo cin kaza😂, oh ni wad'an nan dea akuy kwad'ayi. Haka suka kwashe abunci a leda tsakanin sardeeya da pherty har fad'a aka so ayi, fido ce ta shiga tsakaninsu tai wannan rabo dan nikam kausar ina gurin daukar rahoto, hka aka kammala dinner din aka maida amarya da kawayenta gidah. Bayan sun dawo gidah mame ta same dije ta bata humra da wasu kaya na gyaran jiki ta kuma fad'amata ynda zatai amfani dasu, tare dayi masu addu'ah da fatan alkhairi akan wannan auren. Washe garin ranar ya kama ranar d'auren aure, a chaan kauyen aka d'aura, aliyu yasha manya kaya harda babbar riga fara tas, komai dea yay fari, kamshin turarenshi kawea ke tashi, na white diamond, kasancewar aliyu baida turaren daya wuceshi, ga su maher, sudais, shuraim, da sauransu duk sunzo, abokananshi yan saudiyaa sunyi 20 wad'an da suka zo, hka aka kammala dauren auren a bisa kudi'n sadaki naira dubu hamsin, aka kammala aka watsie, misalin karfe 8pm aka daukie amarya daga kauyen zuwa cikin garin sokoto, dije kuka kawea takeyi na rabuwa da inna da baba. Hka hausawa suka ce aure yakin mata, dije sea hkuri... Hka aka sata a mota aka lula da ita a gidan mijinta, aka direta a tsantsarerin gidanta, aka barta akan gado "yan kai amarya kuma suka juyo suka barta ita kad'ai kapin shigowar ango... ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((33)) ```©Kausar M Hassan``` Bayan fitarsu banda hawaye babu abinda take zubarwa, aliyu ne da shafi'u a cikin motan shafi'u dea2 lokacin misalin 9pm, shafi'u ya dubie Aliyu "To ango dan bazance dea kasha mai ba, tashi muje in rakaka tunda an watsie". Murmushi aliyu yay ya daukie ledan dake hannunshi suka kama hanya shida shafi'u suka shiga gidan da mai gadi y bud'e masu kopah. Kai tsaye d'akin da aka dire dije suka nufa, suna isa aliyu y rangad'a sallama tare da shiga ciki shida shafi'u, kan gadon aliyu ya zauna, yayinda shafi'u yay tsaye Addu'ah shafi'u yay masu da nasihohi kapin nan yay masu sallama ya fitah, aliyu tashi yay ya rufo kopa ya dawo, ya cire babbar rigan dayasah, ya zaunah kusa da dije a hnkli yasa hannu ya yaye mayafin data rufa dashi, ya kalleta "Masha Allah! Matata ta kaina kinyi kyau, tashi muje mui alwala muzo muyi sallah dmn mu godewa Allah" Babu gardama dije ta tashi ta bishi suka shiga d'an wani guri da aka ke6e a d'akin dn yin alwala, kmn dea gurin nan dake cikin ban d'akin haramin madina, alwalan sukai tukkuna suka dawo, aliyu lion yay masu jagoranci sukai sallah, raka'a 2 bayan sun kammala sallan, ya daukie ledan kazar dayazo dashi ya bude ya ciro, da kanshi ya fara bata, dkyar yasamu ta tsakura kad'an shima din kad'an yaci tukkuna ya maida dubanshi gareta "Khadeejah! Ya kira sunanta A tsorace ta amsa da "Na'am yaa aliyu" Murmushi yay kad'an kin gaji kina buqatar ki huta kwanta ki hutah, tashi tai kmn ynda yace ta kwanta ta kudundune da gyalenta. saboda a ranar ana yanayi na sanyi sosai, bata jima ba bacci mai nauyi ya sureta yayinda aliyu ya tashi ya bud'e loca ya ciro abin rufa da kayan bacci ya ajiye akan gadon, hannu yasa ya tallabota a hnkli ya zare gyalen data kudundune dashi, ya fra kokarin cire mata riga, kamn zatai motsi sea ta juya fuskanta gefe, ajiyan zuciya ya saukie ya cigaba da cire mata rigan, abunda yagani yasashi shiga cikin wani yanayi, daurewa yay hka ya balle bra dinta, ya cire ya maida mata da rigan, wadda take iya guiwa ya cire mata zanen, yasa abun rufan ya rufeta, ya kashe wutar d'akin ya fita zuwa falo y kwanta dan bazai iya jure rashinta a tare dashi ba, saboda wani irin matsanancin desire din dake damunshi.... ®Kausar Luv💞 `ALIYU_HAYDAR``` Page ((34)) ```©Kausar M Hassan``` Ba ita ta tashi ba sea asuba, a hnkli ta fara bud'e idonta, ta tashi ta sauka daga kan gadon ta daukie wayanta ta kunna light, ta nupie hnyr toilet, ganinta da tai da yar karamar riga yasata tsorata tare da rike kwalan rigan dake jikinta "Na shiga 3 waye y chnza min kayan jikina? Waiyyyo shikenan an ganni🙆🏾😪" Ta fara kuka tna hawaye, hka ta shiga toilet din tayou alwala ta dawo ta saka zanenta ta daura, ta daukie gyalenta kasancewar babba ne ta yafa ta maida gabanta gabas tai sallah, ta kammala ta tsaya tai addu'ah sosai tukunna ta d'an kishingid'ah. Shi kuwa aliyu dama a gidah yay sallanshi, bayan y kammala ya koma kan kujera ya kwantah, bayan d'an lokaci ya shigo d'akin a hnkli, dije dake zauneh ta gaisheshi, amsawa yay cikinn far'ah. Cikin shagwa6a ta tmbyshi "Yaa aliyu waye y chnza min kayah jikina bayan nai bacci"? Murmushi yay "Ni" y bta amsa a takaice Ido ta rufe sosai kunya ta kamata "Yaa aliyu mai yasa babu kyau fa" Ajiyan zuciya ya saukie "Na deana to tunda matata tace bbu kyau, ynxn dea ki tashi kizo muje kiga gidanki ko"? Babu gardama ta tashi ta bishi suka zaga gidan, gidan ya had'u sosai, a cikin gidan harda lambun shaqatawa ke akuy wanda aka kawatashi da flowers iri2 da shuke2, a tsakinyashi da gefe2 aka dora kujeru irin dogayen nan sannan a chaan b'angare d'aya akasa grass carpet wnda ya karawa gurin kyau, dakuna 4 ne a cikin d'akin dije, idan aka had'a da falo sun zama biyar, da kitchen dinta da store duk a guri d'aya suke sea gurin da aka d'ora teburin cin abunci, a falo na farko kujerune milk, to a wannan falon komai nashi milk ne, akuy dakin da komai pink ne wani kuma brown, daki 2 aka samata gado, kai gidan dea y had'u masha Allah.... Karfe 8am na bugawa sea ga masu aikin gidan ummi ta aikosu da kyn breakfast, hka sukai breakfast din byn sun kammala aliyu yay wnka yay mta sallama y fitah, bai jima da fita ba yan uwa da abokan arziki suka fara tururuwah a gidan, hka dea ta wuni a ranar tana kar6an baki. Nafisat kuwa a gidan za'a ce ta wuni, dan ta zaunah ta koyawa dije d'an abubuwa hka kaman aiki da gas cooker, electric yanda zata kunna heater, yanda zatai wnka da shawar duk dea ta nuna mata komai, ta dauko littafin mu koma kitchen ta mika mata 1 to 3, tace ta rika dubawa a ciki zata koyi girki. Haka dea har dare yay mijinta yazo daukanta taiwa dije sallama, ta fita dea2 lokacin shi kuma aliyu ya dawo gidan... Like · 1 · Reply · Report · Yesterday at 10:15pm Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((35)) ```©Kausar M Hassan``` Sallama yay wa nafisa tukkuna ya karasa cikin gidan, koda ya isa kan kujeran falo ya tarar da ita, sanye da hijab tana karatun al_qur'ani suratul maryam. Kusa da ita yaje ya zauna, ganinshi da tai yasa daa ta takai aya sea ta maida kur'anin ta rufe ta ajiyeshi akan abun dora al_qur'ani ta maida dubanta gareshi "Yaa ka dawo"? Kai y d'aga mata, tare da binta da wani irin mayattaccen kalo, murmushi tai masa ta shagwa6e fuskanta dama duk wasu gabobin jikinta "Yaa haydar tun safe daka fita sea ynxn ka dawo ba dan nafisa ta tsaya ba to sea ka barni ni d'aya" Hannu yasa y dafa kafad'anta, da sauri ta d'an jaa da baya kad'an, mamaki y kama aliyu amma sea y danneshi a zuciya "To ke maatar ali ai ni nace ta tsaya mana, inachan gurin business dinmu, yau za'a kawomana kaya dga Dubai shiyasa na jima hka amma aliyu yana baiwa masoyiyayrshi hkuri, dftn tayi"? Kai ta d'aga masa ta tashi tace "Bara in dauko maka abunci ko"? Tashi tai ta miqe hanya Hannunta aliyu ya janyou ta fad'a jikinshi, gashin kanta ya rufe mata fuska, a hnkli yasa hannu ya fara yaye gashin, jikinshi na wani irin tsam, da azama tai maza ta miqe, cikin rawar murya ta hau yin magana "Em yaa aliyu abunci ne zan dauko maka" Kai y dga mata alamar to, da sauri2 tabi ta gabanshi ta wuce duk da tana da hijab, mazaunanta sea juyawa sukeyi, wani irin nishin wahala ya saki kapin ya zaunah. Ku'la ta dauko da faranti da cokalin zuba abunci ta dawo ta zuba masa a farantin, a kasa ya sauka dan a gajiye yake ko kan dinning table din bazea iya hawa ba, jallop din shinkafa ce da kayan lambu a cikinta da naman rago, ummi ce ta aiko masu da wannan, kad'an ya tsakuri abuncin ya tashi yay toilet ya watsa ruwah, ya chnza kaya zuwa singlet da wando brown iya guiwanshi ya fesa turaren white diamond, gaba d'aya dakin ko ina ya dau kamshi, fitowa yay ya tarar da ita zaune a falon tana kallie2, kusa da ita yaje ya zaunah. "Khadeejah bacci zakiyi ne"? Kai ta girgizah masa, tashi itama tai ta shiga toilet din ta watsa ruwa ta fitoh, ta daura d'an towel wnda yake iya cinyarta, ta fitoh, gashin kanta duk y barbazu a bayanta kasancewar batai kitso ba, had'in humran da mame ta bata ta dauko ta fara murzawa a jikin fatarta, ta baya taji an rungumeta tsam, hkn yasa taja ta tsaya, kanshi y d'ora a bayanta ya fara shakar daddad'ar kamshin jikinta, idanunta ta lumshe kapin ta fara magana cikin shagwa6a "Yaa aliyu meye hka dan Allah"? Kallonta yay da idanunshi da suka kankance "Matata ni bkomai zan maki ba" "Uhm to nidea ka deana ta6ani bana so" Juyuwa da ita yay, suka fuskanci juna ita dashi, kyakyawar sumba ya kaimata a kumatunta, yasa hannunshi y murxa mataunar abuncinta, wani iri taji daban wanda yasa taja da baya tai kan gado ta k'ara kankamie towel din jikintah, binta yay kan gadon shima, yana kallonta ido a rufe. Bakinta ya kama ya fara tsotsawa, duk kokarinta na ganin ta kufce ta kasah, kukan hawaye ta farayi wnda hkn yay sanadiyar dakatarwarshi ya tsaya yna maida numfashi, gaba d'aya ga6o6in jikinshi sun mutu, babu abinda yake buqata a tare dashi inba dije ba, binta da yay da wani irin mayattaccen kallo.. ®Kausar Luv💞 ``ALIYU_HAYDAR``` Page ((36)) ```©Kausar M Hassan``` Chaan kuma mai y tuna sea kawea y bar d'akin zuwa d'ayan d'akin dake da gado y kwanta, kanshi na kallon sama, wasu hawayen wahala keta faman ketowa a idanunshi. Dije kuwa yna fitah tai maza tai sauri ta maida d'akin ta rufe ta jingina jikinta da kopan, tana mai tunano abunda y faru ynxn tsakaninta da lion, wani irin murmushi tai ta wuce ta cigaba da abunda takeyi, byn ta kammala ta samu kayan baccinta ta'sa ta kwanta ruf abunta.. 😲Asuba ta gari... Washe garin ranar dije bata farka ba sea karfe 7am, saboda tsaban bacci da sauri2 ta tashi ta shiga toilet tai alwala ta fitoh tai sallah, tana kammalawa ta tashi ta bud'e kopa sad'af2 ta fitoh falon. Dea2 lokacin ta hango lion kan dining table, sanye cikin kana nan kayah rigan fara da black d'in wando iya guiwa, gashin kanshi y matuqar kwantawa luff a kanshi, ga zara_zaran gashin idonshi dana gira ya fitoh, ko ina d'akin ya daukie kamshin white diamond. Tattakawa tai kusa dashi taja kujera ta zaunah, yana ganinta ya sakar mata wani lallausan murmushi "Ina kwaana yaa aliyu"? Kallonta ya karayi tundaga sama har kasa "Lpy qlw yan mata, kin tashi lpy"? "Lpy qlw yaa" Idonshi ya maida kan dinning din tukkuna y d'agosu "Am kinga fa har ummi ta aikomana da breakfast kina bacci, bismillah" Ajiyan zuciya ta sauke, a hnkli ta kara kallonshi tai murmushi, aliyu ya zuba mata komai da komai da ummi ta had'u. Ganin ya cika plate da abunci yasa dije zare ido "Yaaa nikam ina zan tafie da wannan abuncin hka, Allah ko rabinsa bazan iya cinyewa ba" Murmushi yay mata, tukunna ya kalleta ya d'aga hannunshi ya nunata "Inasone ki rika cin abuncin mai yawa saboda ki haifaman yara masu yawa" Daria tai kad'an tukkuna taja plate d'in a gabanta ta d'an tsakuri abuncin ta maida ta rufe. "Yaa aliyu yau bazakjie ko ina bane"? Kai y d'aga mata alamar eh tare da cewa "Ai ni ba kullum nake fitah ba, amma zamu bud'e wani guri inda zamu rika saka manyan kayanmu kamn su gado, da dea sauransu, to zamuyi office chaan idan mukai kullum zan rika fita in shaa Allah, amma 4 now dea ina gidah". Murmushi tai tukkuna ta tashi ta wuce ciki ta shiga toilet, tai wanka ta fitoh, tai yar simple make up dinta, riga da siket atamfar super wax, mai light blue and wyt, tasa ta daukie turaren humra ta bade jikinta da wasu turarunka masu dadin kamshi, hatta gashin knta bata barshi haka ba ta saka masa nasa turaren, tana kammalawa ta dawo falon, kamshin turarenta ne ya bashi tabbacin cewan dijenshi ta shigo falon, idanunshi ya d'ago sukai ido 2, tai maza ta saukar da nata kasa, cikin tafiyarta mai fizgar hnklinshi ta karaso kusa dashi, hannu y mika mata alaman tazo gareshi, kafad'a ta maqe. Tashi yay zaune ya kafeta da idanu, wani irin abu yakjie yanayi masa yawou a jiki, hannu yaasa ya janyuta a jikinshi, ya had'e kirjinshi da nata. "Uhm2 yaa ka deana mana" D'agota yay ido cikin ido ya kalleta, ya lumshe idanunshi, wuyanta ya kaiwa sumba, kapin ya dawo kan na fulaninta, ta ko ina y shiga shafata, hklinshi gabad'aya ya fita a jikinshi, dije jikinta gaba d'aya ya hau rawa. Iya karfinta ta d'age ta kwallah yar kara, da sauri y cikata, ta tashi da gudu tai d'aki ta maida kopan ta rufe. Hannu ya yarfar kapin ya fara baiwa kanshi magana "Duk ni na jawo wlh, bazan iya hakuri ba, bazan iya jure ganinta hka ba, ina buqatanta, oh my God!" Wasu hawayen wahala suka sauka a fuskanshi, yasa hannu y share a daddafe yatashi yay kopan d'akin a hnkli ya fara knocking, dije dake kwance kan gado tana hawaye jikinta duk yayi la'asar, ta matuqar razana dashi, dan bazata iya bud'e masa kopa ba. Hka aliyu y gaji da knocking ya bar kopar d'akin ya dawo y kwanta kan kujera... Like · 1 · Reply · Report · Aug 6 Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((37)) ```©Kausar M Hassan``` Haka suka wuni a gidan a wannan ranar, suna wasan boya da junah, karfe 8pm tai bayan aliyu ya dawo daga masallaci, ya tarar da kopan d'akin dije a bud'e, kai tsaye y chusa kanshi a ciki, zaune ya tarar da ita kan gado, kusa da ita yaje ya zauna "Khadeejah saa hijab dinki zamujie gida ki gaida su abbi" Tashi tai tasa hijab d'inta kaman ynda yce ta kalleshi suka had'a ido, murmushi sukaiwa junah, suka pitah zuwa gidan, suna isa a falo suka tarar da ummi, abbi da kuma nana, da sallamansu suka shigah. "Maraba da d'ana" Kan kujera d'aya doguwa suka zauna, har qasa dije ta rage tsayenta ta gaida ummi da kuma abbi, ta juya ga nana ta gaisheta, amsawa tai babu yabo babu fallasa, nan dea suka tayin fira, idanun dije na akan aliyu, ynda taga sunayi da ummi sea abun y burgeta wea kuma kishiyan mamanshi ce, amma gskya ummi tanada kirki, kuma tana son aliyu sosai. Mai gadi ya shigo yace anaiwa abbi sallama, abbi tashi yay ya fitah, yayinda ummi tacewa aliyu ya daukie khadeejah ya nuna mata gidansu, tashi tai suka dinga shiga lungu2 yana nuna mata gidan har suka isa d'akinshi, yasa key y bud'e, babu abunda ya chnza a cikinshi, kamshin turarene kawea ke tashi kaman da akuy mutum a ciki. Kan gado ta zaunah tana kallon d'akin, irin ynda taha dakin sea ya burgeta, hotonshi ta hango wanda yake yaro d'an shekara 10, yayi murmushi ya d'aga yatsunshi 2 a sama, da wando dark milk da riga mai jaa da fari, da zanen keke a ciki, tashi tai ta k'arasa inda photon tasa hannunta ta shafa fuskanshi, ji tai a cikin tattausan murya yana cewa "Matata"! Tsayawa tai tare da juyo bayanta, karaf ta fad'a a kirjinshi, kallon ta ya tsaya yanayi wnda hkn yasa ta janye daga inda yake, light din dkin ya rage zuwa dim one, ya juyo gareta ya rage tsayenshi dea2 kan kafafunta da take zaune a kan gado, hannunshi yasa y rike nata, cikin sanyayyar murya yace "Dije ki taimakawa bawan Allah, nasan bazaki iya dani ba amma ki d'an barni in rika jin dumin jikinka mana, zata tashi y rike hannunta, bata ankara ba ya zare hijab din dake wuyanta y wurgar, ya sakala hannunshi a cikin rigarta. "Yaa aliyu ka deana bkyau, dan Allah ko in kira ummi" Kara janyuta yay suka lula kan gadon, ya shiga yin wasa da itah sosai.. Dije banda yaa ali babu abunda take iya furtawa, jin yaki tsayawa yasa tai dif kamn nunfashinta ya fitah, dkyar aliyu y iya saita kanshi y dawo yana lalla6ata, tashi tai ko kallonshi batai ba ta daukie hijab dinta tasa ta kaman hnyn fitah, tana fitah taci karo da nana... ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((38)) ```©Kausar M Hassan``` Wani irin mugun kallo nana tai mata kapin ta wuce ta gabanta, da sauri2 ta sauko falon ta tarar da ummi, shima aliyu ajiyan zuciya ya sauke ya fitoh y maida d'kin ya rufe, ya karaso falon, basu wani jimawa ba sukai wa ummi sallama suka karasa zuwa gidah, suna isa dije tai daki ta kulle, aliyu murmushi yay kad'an ko kokarin binta baiba. Haka sukai sati 2 a gidan, babu abunda ya shiga tsakanin aliyu da dije. Yau ranar ta kama monday aliyu ne zaune akan kujera, sallaman dayaji anayine yasashi d'agowa ya amsa. "Oh yh ango kasha mai". Suka tafa shida shaf'iu, aliyu ya girgizah kai "Abokina muje dea kaji" Duk dije na jinsu da take zaune a d'akinta, wani dakin suka shiga suka maida kopan suka rufe, kan kujera suka zaunah, aliyu ya dubie shaf'iu, cike da damuwa "Abokina zan fadamaka sirrina kuma dan nasan zaka iya rike minshi, shafi'u dije batasan meye aure ba, baata yarda ko ta6ata inyi, ni zan iya hakura indea har zata barni inajin d'umin jikinta amma bata yrda sam" Daria shaf'iu yay tre da cewa "Yaro kenan man kaza, bakai ne auren yarinya ba ga irinta nan, wlh mukam idan desire ta kasheka muna gefe muna kallo ehe" Aliyu y dake kirjinshi "Haba be serious mana dan Allah" Shafi'u y gyara zamanshi "Look! inaganin abunda ya kamata shine kasata a makaranta, tunda kaga ma zamuyi tafiya nan da karshen watan nan kuma zamui kaman 1yr so kawea ka maidata gidah gurin ummi asata a makaranta, koda zamu dawo kaga ta qara girma kuma zata san meye aure in shaa Allah" Aliyu yay shiru tukkuna yace "Kafa kawo shawara nawa, hakan yayi dea2, hkama za'ayi, amma anya zan iya rabuwa da dije har na tswon wannan ranakun kuwa"? Shafi'u tashi yay "Zan biya THE ROYAL INT. SCHOOL in siya mata form idan mun had'u gobe ka kar6a" Hannunshi aliyu y rike, cike da mamaki "Kai maza da matane fa a mkrntar, bnason wasu mazan su kalle min mata" "Eh nasani ai b damuwa akuy wadda zan hadata da ita itama JSS 1 take" "Ok, kasan ai nyrda dakai" Sallama sukai, yayinda aliyu y tashi ya zarce d'akinta, kan gadon ya zaunah ya bata bayah "Am dije dama zanyi tafiya ne na manta ban fadamaki ba" Da sauri ta juya ta matsa kusa dashi ta fashe da kuka ta fara tuttura kafafunta "Haba yaa gskya ni ban yrda ba ya zakayi ka tafie ka barni kuma"? Murmushi yay "To kideana shagwa6ar nan bana sonta a ynxn" K'ara shagwa6ewa tai ta narke masa gabad'aya, a cikin zuciyanshi yake furta "U wan kill me ryt"? Bata san sanda ta fad'a jikinshi ba ta cigaba da zuba masa shagwa6a tana yarfie da hannayenta, wani irin nishi ya saukie ya kama bakinta ya fara tsotsa, kafafunta ta cigaba da bubbugawa a kasa tana dukan bayanshi kad'an2 da hannunta, amma ina aliyu sam baijieba, ganin hka yasa ta dage iya karfinta ta kufce, k'ara janyouta yay ya fara shafa ko ina na jikinta musamman inda yafi d'aukan hnklinshi, kara kufcemasa tai a hannu ta tashi tsaye cike da rud'ani... Aliyu ya tashi tsaye kenan jiri, ya d'ibeshi ya fadie kasah, dije na ganin hka tayou kanshi, kaman mahaukaciya ta fara jijjigashi "Yaa Aliyu dan Allah k a tashi, zan bari ka ta6ani, ina kake so, nan? Ta nuna kirjinta, ta cire riganta ta yarfar gefe, kuka ta hauyi sosai "Yaa aliyu amma dan Allah ka tashi, ta qara kankamieshi sosai a jikinta tana kuka, ganin bai bata amsa ba, kuma gashi yanata rike kanshi yasah ta daukie wayanshi tai searching number din ummi, a rud'e jikinta har rawa yakeyi, cikin kuka ta sanar da ita abunda ke faruwa ta maida wayan ta kashe, sauri2 tai ta maida riganta, ta dauko kanshi ta d'ora akan cinyarta ta cigaba da kuka, da hanzari su ummi suka isa a gidan babu 6ata lokaci driver yajasu zuwa asibiti a emergency aka direshi saboda irin yanayin dayake ciki, likata 3 ne a kanshi suna dubashi da gaggawa bayan sun kammala suka fito. Ummi da sauri tabi bayan dyn likitan dtaga alaman shine babbansu, yayinda dije tai tsaye ta glass take hangenshi kwance an saka mashi oxygen, glass din ta dafa tare da share hawayen dake zarya a kumatunta. Ummi na shiga ta zaunah cike da rud'ani ta hau tmbyn dr, ya mai yake faruwa?" Dr din mai suna Moses, yay gyaran murya "Wato yaron nan yana da ciwo a brain dinshi, amma wannan ciwon da sauki, sannan yana buqatar mace a tare dashi, halan baida mata ne"? Ummi tai jim kad'an "Yanada mata mana, amma basu jima dayin auren ba" Dr din yace "Well, so far dea gskya yaron nan bai taba sanin wata mace ba, so akuy abunda yake buqata yay releasing" Ummi a cikin zuciyanta take cewa "To aikam dole ka kara aure aliyu ko kuma ka saki wannan yarinyar tunda dai tayi karama ka auri wadda ta girma... Tabbas dole cikin 2 d'in nan ayi d'aya.....DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ®Kausar Luv💞 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((39)) ```©Kausar M Hassan``` Dr din yacigaba da cewa "Ynxn dea zamu diba kwakwalwanshi ne tukun, kapin ayi maganar mata, amma yna buqatar kulawa sosai dga gurinmu da ma Ku yan uwanshi. Ummi ta jinjina "Bkomai likita mungode" Fitowa tai jiki a sanyaye, ta matsa kusa da dije dake ta faman hawaye, hannu ummi tasa ta dafa kafad'anta, waigowa dije tai da idanunta da suka rikid'a zuwa jaa Ummi ta narkewa da wani irin kuka mai ban tausayi, rungumeta ummi ta karayi, tare da shafa bayanta "Deana kuka hka khadeejah addu'ah zaki yimasa kinji"? Kai ta d'aga mata tare da kara duban inda aka kwantar dashi. Karfe ukku na rana, ummi ce zaune a harabar hamdala hospital, tare da dije. Kan dije yana akan cinyar ummi, tana sharar hawaye, yayinda har lokacin aliyu bai farka ba. Haka suka wuni a asibitin hankalinsu gaba d'aya a tashe, musamman ma dije saboda duk kanta take daurawa laipie, haka har dare yay, yayinda ake jigilar kawomasu abunci, nafisa da shafi'u ma duk suna gurin. Bayan sallar isha, ummi ta dubie dije "Dije y kamata ki tafie gidah ki d'an huta ki kwanta saboda ni a nan zan kwana" Idanunta ta d'ago da suka cika da kwallah cikin siririyan muryanta "Ummi ni gskya nan zan kwana, bazan bar yaa aliyu a nan shikadea ba" Ummi zatai magana abbi yace "Ya isa hka ki barta ta zaunah, mu zamu koma sea da safenku" Shafi'u yace "To abbi sea da safe ni ina nan" Sallama sukai masu, tukunna suka koma babban d'akin da aka maida aliyu a ciki, ummi kan tabarma ta kwanta, yayinda shafi'u ya kwanta kan dogowan kujeran dake dkin, ita kuma dije ta janyou kujeran roba ta zaunah kusa da aliyu ta kafeshi da idanunta sea hawaye sharr a fuskanta.... Like · 2 · Reply · Report · Aug 8 Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((40)) ```©Kausar M Hassan``` Kusan a wannan daren batai bacci ba, addu'ah ta kwana yi, a hka har safiya ta waye, aliyu dake kwance hannayenshi suka fara motsi da sauri dije ta rike hannunshi tare da shafa gashin kanshi. "Yaa aliyuu" Jin muryan yay har a cikin kwakwalwanshi, "A hnkli y bud'e idanunshi, murmushi tai masa, cikin karfin hali ya mayar matah, ummi da shafi'u duk sukayi kanshi suna yi masa sannu a hnkli yake amsawa. Rayuwa kenan! Haka dea aka cigaba da jinyar aliyu har na tsawon sati 2,dije ce ke bashi duk wata kulawa duk da karancin shekarunta amma tayi matuqar kokari, itake yi masa fira, karanta masa jaridar hausa, ta bashi labari yay ta daria. Yau ranar ta kama monday, aliyu ne zaune akan gado kasancewar ya samu sauki sosai, dije na kan kujerah tana yi masa sosan kafah tana matsa masa itah, shi kuwa ita kadea yake kallo babu abunda ke ranshi inba lokacin da take cire rigan jikinta da lokacin data rrungumeshi tana yarfie da hannayenta, matsowa yay da hannunshi charaf y kama hannunta, ido 2 sukai wanda yasa dije saukar da nata idanun a kasa, cikin muryan rad'a yake rad'amata "Dije zaki barni in...?? Kapin ya karasa tai maza ta janye hannuntah, dea2 lokacin likita yazo ya basu takardan sallama. D'unguma sukai zuwa gidah, a falo suka zazzaunah dea2 lokacin misalin karfe 8pm, shafi'u sallama yay masu y zarce gidah, ita kuma ummi ta tashi tai d'aki tana tunanin ynda zata furta wannan magana, aliyu tashi yay ya kallie dije "Muje ko"? Babu gardama ta tashi ta bi bayanshi tana shiga y maida d'akin ya kulle ya shiga toilet ya watsa ruwan d'umi ya fitoh d'aure da towel iya kugunshi, da ruwan duk dake jikinshi ya rungumeta ta bayah. Idanunta ta lumshe tana jin lokacin dayake bin duk wata kusurwa ta jikinta yana latsawa, wuyanta ya rika kaiwa sumba. "Ah yaa.. Bata karasa ba taji y dauketa ya dora akan gado yana kokarin rabata da kayan jikinta, hannunshi ta rike tare da girgizah masa kai alaman a'ah, chaan kuma mai ta tuna sea tai shiru, wani irin kallon buqata y rik'a aikamata, idanunta ta d'ago ta kalleshi shima d'in ita yake kallo. A cikin zuciyanta take furta "Nikam yau komai yaa aliyu xaimin hakuri zanyi sbd kada y kara yin irin wannan rashin lpyr, znyi hkuri da koma meye... ®Kausar Luv💞 ```ALIYU_HAYDAR``` Paga ((41)) ```©Kausar M Hassan``` Kara shigar da ita yay a cikin kirjinshi yana mai shakar kamshin jikinta, riganta y cire ya wurgar a gefen gado, ya shiga duniyar dayafi buqata da kuma kauna a jikinta. Hawayenta da yaji suna zuba masa a jiki ne yasa y dan dakata ya dubieta, cikin dakusasshiyar murya mai d'auke da desire ya furta "Deejah ya kai ne"? Da hawayen dake zuba a fuskanta ta kalleshi tasa hannunta ta d'an share hawayen "Yaa aliyu wannan abun babu kyau fa amma bkomai tunda hka kakeso ni koma meye kayi bzan fadawa kowa ba" Ta karasa maganar da kauda kanta gefenta tana mai ajiyan zuciya, ga yan madaidaitan na shanunta a tsaye suna kallonshi... Gabad'aya tausayinta ya kamashi, a zuciyanshi yake furta "Ba zan iya yin komai ba a ynxn saboda dije daukana d'an air zatayi, so I have to control my desire, and my feelings" Tashi yay ko kallon inda take baiba, ya koma kan kujera ya zaunah tare da dafe kanshi, dije riganta ta janyou da sauri2 ta maida ta daukie hijab d'inta ta saka, ta tashi a hnkli ta lalla6a ta bud'e d'akin a guje tai d'akin ummi, tana shiga ajiyan zuciya ta sauke ta kwanta kan kujerah tasa hijab dinta ta kudundune akai, take bacci ya karbie amanarta. Kasancewar ummi tana zaune ne akan gado, kaman wadda aka tsakura ta tashi tayou falo, mutum ta gani a kudundune cikin hijab, hannu tasa ta bubbugata, firgigit dije tai ta mike zauneh, tasa hannu ta shafa fuskanta ta d'aga idanunta sukai ido 2 dana ummi... Ummi ta dubeita "Ke dije mai kikeyi a nan? A ina kika barou aliyu kuma"? Kai ta sauke kasa "Ummi dama.... "Dama mi? Tashi ki koma gurin mijinki" Sim2 tai ta tashi ta bar d'akin Ummi ke cewa "Na shiga 3 yarinya zata kashemana yaro ai gskya kam dole ayi wannan maganar gobe idan Allah y kaimana rai". Dije kuwa tsaye tai a kopan d'akin, chaan dea tasa hannu a hankli ta bud'e dakin, koda ta bud'e kwance ta tarar da aliyu akan gado, yasa d'an 3 quarter din wando da singlet, d'akin sea kamshin white diamond yakeyi, ita kuwa tana shiga tai kwancenta kan kujera tai add'uah ta k'ara kudundunewa a cikin hijab d'inta ta kwanta abunta.... Asuba ta gari Mrs Aliyu Haydar... Like · 2 · Reply · Report · Aug 9 Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((42)) ```©Kausar M Hassan``` Washe garin ranar ba ita ta farka dga bacci ba sea 7am, da sauri ta miqe tsaye, dubawan da zatai sukayi ido 2 da aliyu, murmushi ya sakar mata tare da cewa "Heyy hr kin tashi"? Kai ta d'aga mashi alamar eh "To tashi kiyi sallah ko?" "To" shine amsar data bashi cikin takunta ta kama hanyar fitah dga dkin. Da sauri ya tari numfashinta "Ga toilet mana ki shiga kiyi alwalan ko so kike ace kinyi latin sallah"? Murmushi kawea tai masa ta wuce toilet din tai duk abunda zatayi ta fitoh. Koda ta fitoh ta tarar da darduma a kasah, hawa kawea tai tayi sallanta ta kammala tai addu'ah. Bayan ta kammala ta dudduba babu aliyu a d'kin, hakan yasa ta fitoh, akan dinning duk ta hangesu dga saman d'akinshi, ummi, abbi, nana, da kuma shi gwarzon nata wato ```aliyu haydar```. Jiki a sanyaye ta sauko ta gaisheshu, duk suka amsa cikin far'ah, idan aka cire nana, kujera taja ta zaunah yayinda ummi ta had'a mata breakfast dinta, kad'an ta tsakurie abuncin ta shaa drinks da kuma ruwa kad'an. Bayan sun kammala nana tashi tai tayi d'akinta yayinda ya rage aka bar dije, aliyu, ummi da kuma abbi zaune a tangamemien falon. Aliyu yay d'an gyaran murya kad'an yace "Abbi dama tafiya ta kama mu nida shafi'u zuwa dubai, kuma a kalla zamuyi shekera d'aya" Kallonshi abbi yay cike da mamaki "Wace irin shekara kuma? wannan wace irin tafiya ce"? Aliyu y gyara zamanshi "Abbi akan business dinmu ne, saboda muna so mu samu sabuwar hanyan kawo kaya sannan kuma mu kara fahimtar business d'in, dan wnda muke harkar dashi ya sanar damu akuy workshop din da za'ayi kuma yanada matuqar muhimmanci" Ummi tai jim kad'an "To a ina zaka bar ita khadeejah"? Kallonta yay koda ya duba ta saukar da kanta kasa kallo d'aya yay mata ya gane ranta a 6ace yake. "Ummi nan zan barta a gidah" Da sauri ta d'ago idanunta ta dubieshi, a cikin ranta take furta "Ynzn haka zakamin"? 😏To meye amfaninki uwar tsoro😚.. Ummi cike da zuciya ta kalleshi "Tayi maka me a nan d'in to kaji shashancin banza da wofi to halan wa ka aurowa matan"? Aliyu ya d'an murmusa kad'an "Haba ummi ki d'an jira kiji mana, dama makaranta za'a sata tunda bana nan, kinga ta rage zama kuma zata samu ilimi, gashi ynxn nxt week tafiyanmu" Abbi ya nisa ya dubiesu dukansu "To yayi aliyu ba damuwa Allah ubangiji ya tsare ku, ya bud'a maka harkan kasauwancinka" "Amin" suka amsa dashi dukansu Ummi tai ajiyan zuciya tare da maida dubanta ga dije "To dije tashi ki shirya kizo ya kaiki gidah kiga su mamanki dan idan ya tafie ba zuwa chaan zakiyiba" Tashi tai jiki a sanyaye ta fara takawa zuwa saman har ta shiga dakin ummin Tana shiga ummi ta maida kallonta ga abbi, cike da 6acin rai ta hau yin magana "Alhj yaron nan yana da buqatar matarsa a tare dashi, hka Dr ya fadamin, Dr ya shaidamin babu wata alaka ta aure data shiga tsakaninshi da matarshi, dama an fadamashi cewan tayi karama ya dage ya aurota to ynzn dea gashi ga ka kuma a cikin 2 dole ayi d'aya". Ummi ta maida dubanta ga Aliyu "Aliyu wajibine gareka ka k'ara aure ko kuma ka rabu da wannan yarinyar ka auro wata daban wadda ta girma, dole cikin 2 din ayi d'aya wallahi, ina jinka aure zaka kara ko kuwa sakin dijen zakayi"??? Tashin hankali.... Aliyu haydar ya zakayi??? ®Kausar Luv💞 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((43)) ```©Kausar M Hassan ``` Kallonta yay ido cike da kwallah, cikin tausassar murya ya furta "Ummi dan Allah kiyi hakuri amma gskya bazan iya yin ko d'ayah ba, saboda nidea ina son matata kuma banda ra'ayin zama da mata 2, abbi pls kasa baki mana". Ummi kallonshi tai dkyau dan aliyu bai ta6a musa mata magana ba "Ynxn ya kakeso? kaji na rantse ai" Abbi ya girgizah kai tare da gyara zamanshi "Ya isa hka, duk ku dakata, ynxn kai aliyu kace kana son matarka, kuma baka son rabuwa da ita, to abunda ya kamata shine ka samawa kanka lpy ina fatan ka gane"? Kai y d'agawa abbi, ummi ta juya bayanta "To wlh idan wani abu ya sameka babu ruwana" Kusa da ita ya matsa y dora hannunshi akan kafad'anta "Ummi relax zanyi maganin komai in shaa Allah, ynxn dea bara a kira zubairu a fitar maki da kono, murmushi tai masa tare da cewa "D'ana na kaina kenan, dga nan idan kun dawo sea ku zarce gidah, ranar da zaka tafie sea dijen ta dawo nan" Murmushi sukai dukansu "Chabb d'i! Anya kuwa za'a samu kishiyar uwa mai irin wannan halin a ynxn? Anya kuwa ummi batada sa hannu a cikin abunda y faru tskanin mame da abbi kuwa"? Muje zuwa dea... Bayan yan mintina kad'an sea ga dije ta fitoh da dogowar riganta jaa da kuma farin hijab, tayi d'an simple make up d'inta tai kyau, sallama sukai wa su abbi suka kama hanya sea kauyen su dije... A dea2 kopan gidan mame sukai parking suka fitah, gidan suka shiga tare, da murna da d'okin ganin d'anta aliyu ta tarbesu, kan kujera duk suka zazzaunah, bayn d'an lokaci kad'an ta fahimci cewa akuy abunda ke damunsu, take ta hau tmbynsu. Aliyu ya sanar da ita batun tafiyarshi ne, bayan d'an lokaci mame tai ta bashi baki har ya sauko ta juya ga dije "To "yata ke kuma fa mai ke damunki"? Idanunta ta d'ago ta dubie aliyu ta sadda kanta kasa "Am dama.... Zatai magana aka kira aliyu a waya ya tashi ya fice dga gidan ma gaba d"ayah. Hakan ya baiwa dije kwarin guiwa akan ta furta duk abunda take so. "Mame dama yaa aliyu ne... Ta kwashe duk labarin ta baiwa mame gameda abunda aliyu ke mata😂 Kujini da wannan yarinya😏 Mame shiru tai tana kallon dije dan zancen tajieshi wani iri, amma y zatayi? Matsayinta na uwa ga mijinta hka ya baiwa dije lasisin zama 'yrta. Mame ta gyara zama ta matsa kusa da ita ta dubie dije. "Dije wato shi aure da kike gani ibadane, ginshikin aure kuwa shine kauna da hakuri, kauna kaman zuciya take, hakuri kuwa kaman rayuwa ne, aure baya cika sea da shigar da wani abu a cikin wani abu, ma'ana tarawa tsakanin namiji da mace, wannan shi yake tabbatar da aure, ko wacce mace da kikagani haka akai matah, domin ba iskanci bane, iskanci shine kije ki samu namiji wanda ba mijinki ba, kiyi mu'amala dashi to haka ya zama 6arna, anyi zina kenan, kuma saboda zina batada kyau Allah mai girma da kanshi ya fad'a a cikin al_qurninshi mai girma cewan "Kada ku kusance zinah".... Hka dea mame tai ta fahimtar da dije menene aure da kuma ma'anonishi. Jikinta duk yay sanyi ta fahimta sosai matuqa. Dea2 tym d'in da suka kammala aliyu ya dawo gidan, kallon kauna dije take masa sosai sbd ya matuqar bata tausayi, ta kuma duban kanta a cikin ranta tke furta "To ni ynxn ai komai ma zan iya, zan jure da yardar Allah". Hka sukai wa mame sallama suka nupie gidansu dije. Like · 1 · Reply · Report · Aug 10 Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((44)) ```©Kausar M Hassan``` Suna isa kuwa kan tabarma suka tarar da inna tana tsintar shinkafah, a kai suka zauna, inna ta ajiye farantin shinkafan ta rungume 'yarta sosai tana mai jin dadin ganintah, sun jima suna fira a gidan tukunna baba ya dawo dga gonah, shima d'in nan ya tarar dasu, dije ta shaidamasu tafiyan aliyu, da kuma makarantar da za'a sakata. Sunyi murna da farin ciki sosai, aliyu ya dauki abin arziki ya basu y fitah zuwa waje zaman jiran dije. Yana fita inna ta dubie dije "Hakika mijinki mutum ne mai kirki ki bishi sau da kafah, ki kula masa da hakkinki dake kanshi, da yana nan da kuma baya nan, kinji ko"? Kai ta d'aga mata alamar to, basu wani jimawa ba ta fitoh saboda inna ce ta koruta. Hka suka koma motah, suna fitah dea2 lokacin misalin karfe 1pm. Kai tsaye dga nan gidansu shafi'u suka zarce, nan fa maman shafi'u taja hannunta zuwa d'akinta ta kara koyar da ita rayuwan zaman aure. Lallai a wannan rana ta fahimci menene aure. Hka suka wuni a gidan har yamma tukkuna suka karasa gidah gurin ummi kayanshi ya tattara tare da nata dea2 lokacin ana sallar maghrib, bayan sunyi sallan maghirb sukai dinner, akai isha sukaitah tukkuna suka zarce zuwa nasu gidan. Bayan sun isa kowanne a cikinsu b'an d'aki ya nupah ya watsah ruwah, dije na fitowah ta bad'e jikinta da turareh, ta kwance towel d'in jikinta ta dudduba "Yo ai ni nacika mace" murmushi tai ta cigaba da gyaran kanta a gabn madubi ta kammala ta bud'e kayan lefenta wasu matsattsun kayah riga da wando ta dauko red in colour, wandon iya cinyoyinta da rigan iya cibiyantah ta k'ara shafa turare mai dad'in kamshi, ta bazo gashin kanta a bayah ta saka d'an karamin d'an kunne white. Ta dubie kanta a cikin zuciyanta take furta "Wow nayi kyau sosai".... Juyuwan da zatai suksi ido 2 da aliyu haydar, sanye cikin dan 3 quarter milk, da riga mai d'an karamin hannu black, ashe duk wannan juye_juyen da take yana nan yana kallonta yana murmushi, kanta ta sauke kasa kad'an. Matsawa yay kusa da ita yasa hannayenshi 2 ya dafa kafad'antah, kamshin turarenshi da nata y had'e ya gauraye ya bada wani daddad'an kamshi...DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Like · 1 · Reply · Report · Aug 10 Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((45)) ```©Kausar M Hassan``` Kanshi y dora akan nata, numfashinta ya rika had'uwa da nashi, shiru sukai basu ce komai ba, a hnkli ya rad'amata a kunne "Khadeejah ina buqatanki" Jikinta taji ya hau rawah, bata ankara ba taji y dauketa chack ya dorata akan gado, a hnkli yasa hannunshi ya fara shafa gashin kantah, kanta ta juyar gefe guda, ya hade bakinshi da natah ya fara tsotsa, cikin salo na buqata ya cigaba da aikamata sumba, hannunshi ya sakala a cikin riganta yana mai had'uwa da abunda yafi so, yar rigar ya cire ya yarda ya cigaba da shigar da ita a cikin jikinshi. Da azama ya hau kokarin rabarta da d'an wandon dake jikinta, gadan2 ya hau nuna mata irin buqatar daya jima yana matah, ta ko ina lalabarta yakeyi, tun dije na kuka harta deana. Aliyu ba sararamata ba sea da ya tabbatar daya samu natsuwa tukkuna, shi kanshi mamakin dije yakeyi, ynda ta iya d'aukanshi. Da sauri y maida dubanshi gareta, idanu kwea ta kafeshi dasu saboda tsabar wahala Hannu yasa ya dafa kanta da duk y barbajeshi, hawaye shima yakeyi, cikin sanyin murya ya fara mata magana "Oh yh Dije ngd"! Ina sonki sosai ngd! Allah yay maki albarka, tnk u!!!!.... Bla.. Blaaaaaa.... Hawaye ke biyowa akan kumatunta sirrr sbd zafin da takeji kaman zata mutu. Ganin hka yasa aliyu y d'an dakata da surutun da yake mata ya shafa fuskanta cike da tausayi "Mine mai zan maki? Dan Allah ki fad'amin"? Bata iya ce dashi komai ba, sea ta nuna mashi kasantah. Cikin tausayi yace "Sorry mine pls kiyi hkuri nine ko"? Kai ta girgizah mashi alaman a'ah, da sauri ya d'auketa ya kaita toilet yasa mata ruwan zafi kad'an zai fara sakamata ta buge masa hannu tare da nuna masa alaman y fitah, kai y girgizah kawea ya wuce d'ayan toilet din yay wnka, itama din ruwan zafin ta d'auka ta fara zubawah. "Waiyyo ni Allah" Ta furta a fili, haka ta daure ta gasa kanta tukkuna ta dauro towel ta tattako a hnkli ta fitoh, tana fitowa taji an suretah sea d'ayan d'akinsu dake da gado, akan gadon ya ajiyeta ya bud'e loca ya dauko rigan sanyi ya saka matah, tukunna ya kalleta "Mine zakisa wani abune"? Kai kawea ta d'aga masa, hannu yasa ya dauketa zuwa inda kayanta suke, bakinta ta turo "To ni ka fita" Kalma d'aya bai furta ba ya juya bayanshi, a hnkli ta bud'e loca ta daukie pant dinta ta saka, tukkuna ta juya taga gadon, ido ta zaro ynda taga anyiwa gadon. Aliyu juyuwa yay "Kin gama"? "Eh" ta furta jiki a sanyaye Daukanta ya karayi zuwa d'ayan d'akin kan gadon ya direta, shima y kwanta akn gadon ya rungumeta a cikin fadadden kirjinshi, ita kuwa ajiyan zuciya ta sauke ta kara shigiewa a kirjinshi tare da shakar kamshin jikinshi... "Oh yh finally dea su dije an zama cikakkiyar mace, dama ai duk wayoun amarya sea ansha manta...DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ®Kausar Luv💞 ``ALIYU_HAYDAR``` Page ((46)) ```©Kausar M Hassan``` Hka sukai bacci kanta na akan kirjinshi, shi kuwa farin ciki yakejie wnda bai ta6a jin irinshi a rayuwarsa ba, sarauniya dije ta kammala mashi komai a yau. Washe garin ranar ba dije ta farka ba sea karfe bakwai da rabi na safe, a hnkli ta fara bud'e idonta har ta kammala tare da furta addu'an tashi dga bacci "Alhmdlh lazy ahyana ba'ada ma amatana wa ilahin nushur" Kafafunta ta fara saukarwa dga gadon, wani irin zafi taji wnda yasa ta ajiyesu kasa ta tada kanta sama tana kallon d'akin. "Hey, mine har kin tashi"? Taji muryan aliyu yana fad'a Kai ta d'aga masa, y matsa kusa da ita ya rage tsayenshi dea2 nata, ya dora hancinshi akan natah "My deeja kin tashi lpy"? "Kai ta d'aga masa again, murmushi yay "Baza'min magana ba"? Cikin siriryan muryanta data shaa kuka ta furta "Ni sallah zanyi" "Ba damuwa matana, ya kama hannunta ya tashi tsaye "Muje kiyi sallan ko, kamar mai koyoun tafiya haka ta bishi, suka isa gurin yin alwala tai alwala a falo tai sallah ta kammala ta jingina bayanta akan dogowan kujeran d'akin, tare da cije le6en bakinta na kasa. Dea2 lokacin aliyu y fitoh dga kitchen d'auke da katon faranti a hannunshi, a gabanta ya direshi ya kalleta, cikin sexy voice ya furta "Mine kideana cizon le6en nan pls ina son abina fa". Kallonshi tai kawea tai murmushi "Yauwa ga tea nan, ga kwai ga bread, sea kici ko" ya yago bread d'in ya hadeshi ya mika matah a baki, a hnkli ta bud'e bakinta yasa mata a ciki, murmushi tai masa ta had'eyi, hka y dinga bata abunci kaman wata er baby har ta koshi tukkuna ya janye plate din gefe, ya janyouta y dorata akan kirjinshi ya rungumeta sosai.. Dije tasa hannunta akan kirjinshi "My lion wanka nakeso inyi" "Tohm mine, muje in maki" Ido ta zaro cikin shagwa6a ta furta "A'a my lion gaskiya bazan yarda ba ka kalleni" Daria aliyu yy kad'an a kunne ya rad'amata "Nafa ga komai mine kawea ki bari in maki, bazan maki komai ba" Bai jira amsar da zata bashi ya dauketa zuwa toilet. Lokacin ni kuma na jaaa wayana🏃🏿 muka kara giyah dan muma ni da ita jiya bamu samu munyi barci ba...DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Like · 1 · Reply · Report · Aug 11 Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((47)) ```©Kausar M Hassan``` A kwana 4 d'in nan da suka rage a cikin wannan satin wanda zai kama daga shi saura kwana 2 tafiyan aliyu zuwa dubai, dije taga kauna da soyayya rarrashi, kai komai ma tagani. Tun first nyt har yau ba'a sake second nyt ba. Lol.. Yau ranar ta kama friday, misalin karfe 9pm, dije ce zaune a falo sea faman rubuce2 takeyi a takardu, idan ta rubuta sea tasa day 1 haka har takai kusan 100, tanayi tana murmushi abuntah. Kasancewar aliyu yana sallan nafila ne, bayan ya kammala ya dawo falon kusa da ita ya zaunah ya dora hannushi a bayanta "Mine wea tun d'azun rubutun mai kikeyi hka"? Murmushi tai ta kalleshi "My lion wannan naka ne amma bana so kagani ynxn sea ka tafie" Janyouta yay ta fad'a jikinshi "Khadeejah zakiyi missing d'ina kuwah"? "Sosai kuwa yaa aliyu" Hannunshi yasa ya fara lalubar bakintah, da sauri ta miqe zaune dga kwanciyar datayi '"Uhm2 yaa aliyu nifa Allah zafi" Murmushi yay kad'an ya had'e kafafunshi akan kujera "Look Allah yau bazakiji zafi ba, kinga tunfa ranar banyi ba kuma ina buqatanki, kawea dea nayi hkurine sbd banaso ki wahala". Ido ta d'ago kad'an ta dubieshi "My lion plsss kada kayi" Kai ya d'aga mata alaman to, hakan yasa ta dawo kan cinyarshi ta d'ora kusan rabin jikinta gaba d'aya... Washe garin ranar ya kama assabar, kuma ya kama tafiyan aliyu monday, misalin karfe 8pm, aliyu ya kammala had'a kayanshi da duk wani abu da zai buqata a cikin jaka tare da taimakawar dije, bayan ya had'a dije ta tashi jiki a sanyaye tai toilet ta sheiku wanka ta fitoh, akan dressing mirror ta tsaya tana shafe2 bayan ta kammala ta fesa turare, ta saa wasu irin arnakun kayan bacci, red n black, dogowan rigane amma iyakarta cinyarta, duk ilahirin jikinta a waje yake, ta daukie katon hijab ta saka ta kama hanyar zuwa gurin aliyu dake falo. Tana isa kusa dashi taje ta zaunah "Wow gskya kinyi kyau" "Ngd" ta furta tare dayin fari da ido. Kallonta yay ya matsa kusa da ita sosai "Wannan hijab din ni gskya a cire minshi inasone inga kwalliyan da akamin" Dije kasa attaka komai tai, aliyu tashi yay zaune dkyau ya fuskanceta, a hnkli ya fara d'ago tundaga kasan hijab d'in har ya kawo sama ya cireshi. Kallonta ya tsaya yanayi sosai, hannu tasa ta k'are fuskanta, a hankli shima ya dora nashi akai tare da janye nata y manna mata kiss a kumatu. Kiss ya shiga aika mata ta ko ina "Yaa Aliyu pls wlh da zafi fah kada kamin" Romancing dinta ya shigayi sosai, bakinta yake tsosta tare da mutustsuka yan madaidatan na shanuntah... DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 . ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((48)) ```©Kausar M Hassan``` "Yaa aliyu dan Allah ka bari, saboda yanda yake handling dinta yasa tai kwance kan kujeran, shima d'in baya y rufa matah, gabad'aya ya fitah hayyacinshi aliyu kaman ba shi ba, duk yabi ya rud'e ya firgice, wani irin karfie yakeji kaman na doki, haka ya saukar da duk karfinshi akanta Dije kuka ta hauyi wiwi kaman motan kashe gobara😂... Sea daya kammala tukkuna ya dawo lallashi da kuma tausayintah "Yar 14yrs fa naiwa wannan kmn wata babba" yake furtawa a cikin ranshi... D'aukanta yay ya shiga da ita d'aki, ya kulle nima nai hamma na wuce na kwanta abina😲 asuba ta gari. Washe garin ranar ya kama lahadi, y rage ranar monday ne tafiyan aliyu, hka suka fitah zuwa bankwana wa da "yan uwa da abokan arziki shida shafi'uh har gidan nafisat sea da suka tafie sun jima suna fira a chaan, kapin suka zarce gidan yayan Shafi'u kawar nana, itakam yaranta 3 mah, hka hr gidan mame da gidansu dije suke. Hka suka wuni a chaan kapin kowanne yay sallama da d'an uwanshi, aliyu yayou gidah shima hka shafi'uh. Yana isowa ya rangad'a sallama, jin bata masa ba yasa ya nupie d'ayan d'akinsu, ganin nan ma babuta yasa ya shiga toilet ya watsa ruwa ya fitoh ya chnza kayan jikinshi zuwa "yan kanti ya fesa d one and only perfume dinshi wnda ynxn ya zama jikinshi ko kayanshi kamshin shi sukeyi koda kuwa bai shafa ba. Kai tsaye ya nupie d'ayn d'akin, chaan ma babuta, haka ya dudduba nan ma duk bata nan, har kitchen yake duk bata nan, hnklinshi ya matuqar tashi ya koma ya tmbyi mai gadi ko yaga ta fitah, mai gadin ya bashi tabbacin cewan lallai bata fitah ba. Chaan kuma sea yay lambunsu, yana zuwa ya tarar da ita tana tsalle ala dole sea ta ciro d'anyen mangwaro. Tsallen da take yasa ko ina na jikinta ke motsawa, ga wata daddad'ar iska tana kad'awa, tana tsalle tana yarfie da hannayeta, murmushi ya tsaya, ganin ta kasa cirowa yasa y matsa kusa da itah ysa hannu zurawa d'aya ya tsunko mango d'in y mika matah. Kar6a tai tayi murmushi "Tank u" Murmushi yay mata shima "Ashe nan kika zo kika sa inata nemanki ```mine```" Murmushi tai kad'an "My lion xuciyatah na baiwa zakinta hkuri, nazo shaan iskane sea naga wannan mango din shine fa na tsaya tsinkowa". "X ok my dear" Hannunta yaja "Boyoni kigah, babu gardama tabi bayanshi suka lula cikin lambun sosai, wata kopa tagani, aliyu yasa hannu ya murd'a ta budeh, ciki suka shiga, d'an wuri ne mai kyau sosai, an kawatashi da titimai da carpet2 gurin dea ya had'u. Ciki suka shiga ya maida kopan ya kulle, ya zaunar da ita kan carpet ya kura mata idanu "dije kinsan gobene tafiyana ko"? "Kai ta d'aga masa" Aliyu yace "Komai da kike buqata na tanadar maki shi, zan baki jaka akuy kud'i a ciki sea kina d'iba kina yin lalura dashi ko"? Murmushi tai masah, wnda yasa aliyu kara shiga yanayi, babu ko kunya yasa hannu ta gabanta yana kokarin rabata da rigarta, saurin nokewa tai kan carpet shima din y bitah...DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ®Kausar Luv💞 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((49)) ```©Kausar M Hassan``` "Pls! Ya aliyu a'ah" Cikin muryan tausayi ya furta "Khadeejah kiyi hakuri dani, haka nake ina tsananin buqatarki a rayuwana, kinji"? Ganin yanda yay yasa tai shiru, hka ya rabata da komai natah, ya lula cikin wata duniyar ta daban, sea da ya gamsu tukkuna ya barta, hka suka lula zuwa cikin gidan suka tsaftace jikinsu sukai wanka, bayan sun kammala suka dawo suka manne da juna kaman chewing gum. Soyayya kenan ruwan zumah, Allah y bar kauna hajji aliyu n dije. Ko a daren ranar bai barta ba, kaman zan cinyeta d'anya, da soyayya fa bada eh aha ba😉 Washe garin ranar kasancewar jirginsu zai tashi karfe 10am, dije tsintar kanta tai cikin bakin ciki mara misaltuwah, saboda aliyu ya zama ```Ruwa da kuma jinin jikintah, a duk lokacin da take tare da aliyu ta kan manta da duk wani bakin cikin rantah, takan tsinci kanta cikin farin ciki, aliyu ya zama wani 6angare na jikinta wanda rasashi zai iya zama barazana a rayuwantah``` Hka ya kammala shirinshi, ya fitoh ya tarar da ita zaune a falo, jiki a sanyaye, zaune kan kujera ta d'ora kafafunta akai, tana sharar kwallah. Rage tsayenshi yay dea2 nata "Khadeejah ki deana kuka shekara fa kamar kwana take, kuma kulllum zan kiraki, ni kaina banda tafiyan nan ta zama dole wallah dana fasa yintah" Hawayenta ta share ta dubieshi tare da dauko wani envelope "Yaa Aliyu ga wannan, naka ne idan ka tafie ka rika daukan d'aya kana karantawa a kullum" Hannu yasa y amsa tare dayin murmushi "Ngd sosai deeja tah ina sonki sosai" "Nima ina sonka my lion" Hancinta yaja kad'an ko in d'an... Ya kyafta mata ido, kirjinshi ta daka kad'an tare da cewa "A'a kada kayi late amma alkawarine ranar daka dawo zan baka kainah dama ni taka ce" Murmushi yay "mujeh ko"? Tashi tai ta daukie hijab d'inta ta saka ta daukie wayanta suka komah d'aki duk wani kayan wuta ta kasheshi, dama ta had'a kayanta suna gidah gurin ummi, kai tsaye chaan suka nupah bayan tayi sallama da mai gadin gidan, dan ya bar kudinshi a hannun ummi na shekara dayah. Suna isa duk a falo suka tarar da jama'ar gidan...DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Like · 3 · Reply · Report · Aug 12 Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((50)) ```©Kausar M Hassan``` Harda nafisat tana a gidan itama, kan kujera suka zazzaunah, suka fara bankwana, kaman kada su rabu da juna, aliyu ya cewa abbi form din dije na hannun nafisa, abbi yace "Ai tama bani, dan gobe zan kaita". Hka dea suka cigaba da tattaunawa suna yin bankwana. Lokaci baya jiran kowa, yau da gobe kake dashi, jiya kuma ta wuce bazata sake dawowa ba. hka aliyu ya kama hanya ya fitah gidan zuciyanshi cike da kewan matanshi sanyin zuciyanshi, hka duk suka rakashi har kopan gidan, kasa jurewa dije tai wanda hakan yasa ta ruga da gudu tai falon, ji yay kamn ya janyou ta ya hadeta da kirjinshi amma ina lokaci ya riga ya barsu, dea2 lokacin shaf'iu ya karaso, driver d'in gidan abbi ne ya suresu zuwa airport, hka suka isa akai komai aka kammala suka shiga jirgi, Aliyu kaman ba shi ba. A cikin jirgin shafi'u ke cewa "Namjin duniyah, zakin fama, kenan ya akaine"? D'ago idanunshi yay sukai ido 2 da shafi'u "Ina jini kaman na rasa matata, zuciyata bugawa takeyi, ji nakeyi kaman na bar wani sashe na jikina" Daria shaf'iu yay, ganin aliyu baice dashi komai ba yasa ya kara yin wata. "Hba kaipah gwauro ne baka san dad'in aure ba shiyasa kake ta wannan darian, ai alhj ina fad'amaka aure ni'ima ne aure rahama ne wlh, aure natsuwa ne". Shaf'iu yce "Hkne hkuri zakayi shekara yau ai ta koma kaman kwana 1, saboda hka kaita add'ah kaji". Kai kawea ya d'aga masah. ```Bayan awa 2``` A nan gida nigeria kuwah, dije ce kwance a d'akin aliyu, tana matuqar kewarshi, duk da basufi awa 2 da rabuwa ba, kamshin turarenshi kawea ke tashi a d'akin. Hawayene ke zarya a kumatuntah, duk ta yamutsie gashin kanta kaman wata mahaukaciya, kan gado tajie tai zauneh ta d'ora hannunta akan goshinta "Ina kewarka mijina, ina kewarka" Ta furta a fili tare da kefie kanta a gadon, ta kudundune a cikin zanen gadon, hka tai bacci a ranar cikin bakin ciki, dan ynxn ta riga ta saba da kwanciya a jikinshi, da shakar kamnshin jikinshi, duk da baya nan amma dkin na nan da kamshin mai d'akin..... ``` DUBAI``` Babban filin sauka da tashin jirage dke kasar dubai suka saukah, bayan isarsu, abokin cinikinsu yazo ya daukesu ya kaisu masauki, wanka suka shiga sukayi tukkuna suka fitoh. Dije ta fara yi masa gizo akan mirror d'in d'akin tana murmushi, murmushi yay shima "Oh ni aliyu ina cikin yanayi".. Washe garin ranar tunda safe misalin karfe 8am, abbi da kanshi ya shiga mota shida zubairu suka zarce the king int school, kai kodaga ganin gate d'in makarantar kasan ta tsaru, ta had'u iya had'uwah, story building ne dukantah har gudah 6. A office d'in principal suka shigah, bayan sun shiga abbi ya gabatar da dije ga principal ya kuma shaida masa cewan ga 'yar shi nan ya kawo. PC din ya baiwa abbi amsa da "Ranka ya dad'e za'ayi mata interview idan taci to sea mu duba da class d'in data dace" Hka kuwa akai PC ya kira wata mata tazo ta tafie da dije, nan aka fara yi mata tambayoyi tana ta bada amsa, har aka kammala, tanayi tna rubuta result din dije. fitowa sukai suka koma office d'in PC ta mik'a masa result din. "Wow amma gskya tayi kokari, 70 point ta samu sbaoda hka zamu sata a Js3 tunda ma tayi girma kuma tana da kai sosai. Nan dai akai komai aka kammala, abbi ya maida kallonshi gareta "To Khadeejah an gama komai sea gobe sea ki fara zuwa ko" PC din yace "Ai ko ynxn ma za'a iya barintah, ke malama kaita Js3 A. Tashi tai tabi bayan matar suka shiga aka kaita class din, kasancewar akuy wani kujera da babu kowa akai malaman tace ta zaunah akai, ga ajin duk mata da maxa sea magana akeyi. Zaunawa tai tana k'arewa yan ajin kallo, haka ta wuni a ranar batai magana da kowa ba a ajin, sea dea da anyi tmbya tana kokorin bada amsar data sani, driver ne yazo ya d'auketa lokacin da suka tashi suka k'arasa gidah bayan an tashe su... Suna isa a falo ta tarar da nana, nana na ganinta ta taso da far'arta da komai ta tarbeta. Nikam ido na saki ina kallon ikon Allah, anya kuwa wannan nana ce? To tabbas akuy wani abu da zata kulla kuwah. Murmushi dije tai matah, nana taja hannunta suka zauna kan kujerah, ta kira mai aikinsu ta kawo mata abunci, dije tasa cokali ta fara yakutar abuncin, kad'an taci tukkuna ta tashi ta haura sama. Murmushin mugunta nana tai A cikin zuciyanta take furta "Baka sanin halin mutum sea ka zaunah tare dashi, zanyi amfani da wannan damar in haddasa tsana tsakanin dije da aliyu, yanda zea tsaneta fiye da mutuwarshi, in kuma yi sanadiyar rabuwarsu sannan kuma in aika aliyu lahira..... ®Kausar Luv💞 DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((51)) ```©Kausar M Hassan``` Washe garin ranar dije ta shirya cikin kayanta riga dogowa da hijab dinta fari, ta fitoh tawa abbi sallama da ummi. Nana na tsaye "To my in law sea kin dawo ayi karatu dkyau" inji nana Murmushi tai mata "Sea na dawo" Fita tai driver d'in ya d'auketa ya kaita makarantar dea2 lokacin misalin karfe takwas saura kwata. Kasancewar ba'a share2 a mkrntar akuy masuyi, ajinsu ta wuce direct kan kujera ta zaunah, bayan ta zaunah na d'an lokaci kad'an sea ga wata yarinya tazo wucewa, fara mai tsaye dea2 misali. Kusa da dije ta zaunah ta d'ora kapanta d'aya akan d'aya Cikin muryan shed'ana tace 'Sunana _Nazee_" Kallonta dije tai tundaga sama har kasa ta watsar tukkuna ta daukie wayanta, data hau ruri da sauri ta kara a kunne tare da furta "Har ka mnta dani ko"? Aliyu da sauri ya furta "No! capital NO kuwa ya zan manta da rainah, farin cikina kuma mahad'ar rayuwata"? Murmushi tai sosai "Tohm yayi zan kiraka zuwa anjima ynxn ina makaranta" Sallama sukai tukkuna ta kashe wayar tare da mannata a kirjinta. Hannu nazee tasa ta bugeta "Hey! Ta furta da karpin tsiya. "Akan mie ina maki magana zaki wani kyaleni, kin kuwa san wacece nazee a makarantar nan? Ko PC yana shakkuna wlh" Kallonta dije ta karayi again batace da ita komai ba, Nazee ta zukole sosai, Ta d'aga hannu kenan ta mareta sea ga wani saurayi kimanin shekarunsa zasu kai 16, yasa hannunshi ya rike nata cikin masifa ya hau yin magana Ke! Lpy dan ubnki zaki daki yarinyar mutane haka? Huci tai ta janye hannunta "Kai Muslim wallahi ka kyaleni deana ganin ina sonka ina kyaleka, sea kana kokarin shiga harkata"? "Wuce muje nidea" ya furta a takaice. Hannunta yaja zuwa kujeranta. Yayinda dije ke mamakin hali irin na nazee yo kuma meye sunanta ne oho?DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Like · 1 · Reply · Report · Aug 14 at 10:07pm Kausar M Hassan ```ALIYU/HAYDAR``` Page ((52)) ```©Kausar M Hassan``` Hka suka wuni a makarantar, bayan an tashi PC ya aiko mata da uniform d'inta a cikin ledah, kar6a tai ta fitah zuwa gate, a chaan ta tarar da driver d'insu yazo d'aukanta, kai tsaye gida ta nupa, nana ce a falo tsaye, tana ganin dije ta rungumetah sosai, murmushi dije tai mata wanda hkn yasa nana farin ciki. Washe gari dije tasa uniform dinta, tayi kyau sosai, da jakarta mai dogon hannu iya cinyarta, d'akin ummi ta shiga tai mata sallama hka abbi, nana har mota ta rakatah, tare suka shiga hr kopar makarantar aka ajiyeta tukkuna nana da driver suka kama hanyar juyawa, yayinda dije ta shiga class d'insu. Tana isa ta tarar da nazee zaune akan kujeranta, murmushi tai tare dayi mata sallama ta gyara zamanta ta zaunah. *BAYAN SATI 2!* Dije ce zaune akan kujeran makarantar su misalin karfe 10am, lokacin an tashi break, tana zaune akan kujera, nazee dake nesa da ita, ta matsu kusa da ita "Hey sunana nazeefa, amma ana kirana da nazee, ina sone in zama kawarki saboda naga halayenki masu kyau ne duk irin abubuwan da nake maki baki rikeni a rai ba" Dije tai murmushi "Ngd nazee, buh ni gskya bana son abota dake saboda bakida tsoro" Daria nazee tai ta dubie dije "Na maki alkawarin kasancewa tare dake a kowanne lokacin da zaki buqaceni, kawea ki amshe hannun abota na". Dea2 lokacin muslim ya karaso gurin "Nima hka, zan zama abokin kamilalla" Murmushi tai masu tare da cewan "To amma fa ni inada au... Kapin ta karasa taji wayanta na vibration, wanda wannan ba kowa bane face haydar... Hka dea rayuwan ta cigaba da tafiyah, tsakanin aliyu da dije kuwa a kullum suna nan manne da juna a wayah, tana bashi labarin yanda take rayuwa a makarantah, da ynda nana take kula da itah, yayi matuqar mamakin jin hakan, amma sea yace kilan lokacin shiryuwanta ne yayi. Haydar kuwa a koda yaushe yana fad'amata yanda yay missing d'intah, shagwa6anta, murmushin ta, kukanta, kai komai dea nata yayi missing d'inshi, takardun data bashi sune ke d'ebie masa d'an kewanta... Tsakanin nazee, muslim da dije kuwa sun zama abokai, dan akan kujera d'aya suke zama, muslim a farko sea nazee a tsakiyansu ita kuma dije a karshe. Duk da dije bata wani sakin jiki da muslim ba saboda zamanta matar aure... Like · 1 · Reply · Report · Aug 14 at 10:07pmDOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((53)) ```©Kausar M Hassan``` *BAYAN WATANNI 10* Tsaye take sanye da riga da skit d'unkin na atamfah, ya matuqar yi mata kyau, kamshi take ta ko inah, jikinta ko ina ya k'ara developing, musamman sama da bayanta. Sea nishad'inta takeyi abuntah. Dea2 lokacin nana ta karaso ta kalleta dkyau tai murmushi "Yarinya mai kyau dake ga diri ga komai son kowa kin wanda ya rasa, gskya k'ani na yayi sa'ar mata" Daria dije tai sosai "Kai anty nana wannan irin fad'a hka"? Murmushi nana tai "Wea nikam ina abokinki nan musulm"? Kallonta dije tai "Kai anty nana yo ai tun friday rabona dashi, kawea nazee ce mukai waya da itah, sea kuma in an koma mkrntar monday" Daria nana tai sosai "Tohm yayi yaushe haydar zai dawo ne"? "Yace wea next month zai dawo" "Yayi kyau yan matah" Dije ta kallie nana "Amma fa anty nana kinsan yaa aliyu yace wea zai bani mamaki to mamakin mi zai bani kuma"? Murmushi tai "Ah to gamu gani dea" Haka monday ta kama dije ta tafie makarantah, bayan an tashi aka bar dije, nazee, da kuma muslim, fira suke sosai tsakanin nazee da muslim, iyakacin dije murmushi, kallonta kawea muslim keyi sosai yana mai raya wani abu a zuciyanshi, a hka har aka zo d'aukan dije, tare da nana suka zo, kai tsaye gidah suka zarce. *BAYAN SATI 3* Motace baqa anyi parking d'intah mai tinted, da wani a gidan gaba na motar, da nana a gidan baya. "Nasan kana son dije ina sone kayi duk yanda kai ka d'auki hoto da ita wanda zaka had'a jiki da itah. Muryan namiji ya amsa da "To amma mai yasa kike son hakan ta faru"? "Babu ruwanka kaedai, zaka samu dije ni kuma zan samu biyan buqata" "OK" ya furta an gama aiki" "Ba haka nakeso ba, kar6a wannan" ta mika masa wani leda fari. "Ka zuba mata a abunsha zata zama bata tuna komai so hka zakayi pics d'in har ga gama kuma inason pics d'in dayawa" "Tohm yayi amma nawa zaki biyani"? "Dubu d'ari zan baka ina buqatar pics d'in zuwa jibie" "An gama" ya fad'a tare da bud'e ganbon motar ya fitah, dubawan da zanyi ni kausar naga muslim. Ido na zaro ina tunanin rashin mutunci irin na nana, da yanda take kokarin raba tsakanin aliyu da dije, to ko mai zatayi da pics d'in oho?? Shi kuwa muslim ai rayuwa batace hka ba, saboda dije ta gama yarda dashi sosai, ta d'aukeshi kamar yayanta uwa d'aya uba d'ayah. Washe garin ranar ta kama monday, dije ce zaune ita da nazee suna fira bayan sun fitoh dga office d'in PC. Nazee ce ta dubie dije "Wea dije yaushe zakiyi aure"? Ido dije ta zaro zatai magana sea ga muslim rike da maltina guda 3 na roba, ya mik'awa kowacce a cikinsu d'aya2, shima ya bud'e tashi. A cikin zuciyanshi yake furta "An kusa gama aiki, yi maza khadeejah kisha malt d'in nan" Dije ta fara kokarin bud'e roban haka har ta bud'e ta kafa a baki.....DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ®Kausar Luv💞 . ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((54)) ```©Kausar M Hassan``` Kad'an ta kurb'a ta furzar ta dubie muslim "Na manta azumi nake, kaga dana karya wallahi" Ranshi idan yayi dubu ya 6ace. Daria nazee tai ta kwace malt d'in a hannunta "ai sea in had'a 2 duka in shanye dma kinsan inason malt" Cike da raud'ani da matsanancin tashin hnkli muslim ya fige goran "Ke wallahi kin fiye shigien kwad'ayi yar iskare kawea" Kai ta girgizah masu kawea ta kama hanyr shiga ajinsu, nazee ta d'aga gira ta rike kugu, cike da zargie ta dubie muslim "Kai! Tabbas akuy abunda ke faruwa, fadamin mai ke faruwa? Cikin alamaun rashin gaskiya ya dubieta "Em.. Am.. Bangane ba nazee mai kike cewa hka? Oya wuce muje". Hnya suka kama suka wuce aji, a hka har aka tashesu, kowanne a cikinsu yay gidah, in banda muslim. Zagaye2 yakeyi kaman wnda yasha kwaya, hka har nana ta iskoshi da motah, bud'e motan yay ya shiga "Ranki ya dade wlh aiki bai samu ba wea yau azumi takeyi kiyi hkuri sea dea zuwa gobe" Cikin munafukar muryarta tai wani irin kallo na mugunta "Kafa sani cewan kaji sirrina saboda hka dole kai man abunda nasaka" "Kada ki samu damuwa gobe in shaa Allah zan gama maki aiki" ya bude motan ya fitah zuciyanshi na bashi kwarin guiwa akan abunda ya dosah. Dije na isa gida a falo ta tarar da ummi, kan kujera ta zaunah kusa da ummin. "Ummi ta dubietah "Ke dije aliyu ya kusa dawowa ko ya fad'amaki ranar da zai dawo"? Kai dije ta girgizah mata alaman a'a "Amma dea ummi yace cikin satin nan" Ummi ta tashi tai d'aki ta dawo da wasu kayah na fruit rike a hannunta, da madara peak irin manyan gwango d'in nan ta mik'a matah "Ungo wannan ki rik'a cinyewa kullum, akuy kula na nan fara idn kika shiga parlour na, ki dauka abunda ke ciki ke cinye, ki had'a kan kana da madarar nan ki shanye kinji ko"? Amsa tai "Amma ummi fa ina azumi" "Ba damuwa idan kika shaa ruwa sea kisha ai, ynxn tashi kije" Tashi tai ta haura saman zuwa d'akin ummi... "Assalamu alaikum" Nafisa tai sallama a gidan, cikin farin ciki ummi ta amsa mata sallaman, nafisa ko zama batai ba, ta tambyi ummi ina dije, ummi ta bata amsa da tana d'akinta, a chaan d'in ta bitah ta bata wasu abubuwan gyara. Dije karb'a kawea take ita kam ta rasa na menene haka.. "Mata kenan akace sea da gyarah, idan babu gyra babu mace, duk wadda batada tsafta ku kirata da ballagaza, ki gyra kanki dan samun ni'ima wannan ba tsafi bane ko sihiri.. In b hka ai maki kishiya☺..... DOCUMENTS CREATED BY KING BOY √ HAUSA NOVELS 08096831009 ``ALIYU_HAYDAR``` Page ```((55))``` ```©Kausar M Hassan``` Washe garin ranar kamar kullum kuma kamar ko yaushe, ta shirya ta tafie mkrnta, koda ta isa ta tarar da muslim, gaisuwa tai masa ta samu guri ta zaunah as usual. Kyararta yay da ido kapin ya bud'e jakarshi ya fitoh da roban lemo na cock ya miq'a mata "Barka dea tunda jiya bkisha baa kin kuwa ga yau nazo maki da cock, tun dga gidah kuwa" Dije da murmushi ta karb'a "Ngd muslim" Taja cock d'in ta ajiye a gaban tebur. Kusan minti 10 batace dashi komai ba, zuciyan muslim na kanta, ya k'agara tasha ganin hr lokacin bata bi ta kanta ba. Yasa yace "Am khdy nace bazaki shaa lemun bane"? "Hmm kaga ni har na manta wlh, zansha amma sea ya rage sanyi, ngd ko" Murmushi yay mata, dea2 lokacin nazee ta karaso "Sea gani nazo yan matasa" Hannu ta kai kan lemun "Yauwa na kuwa gode maku ni daman nasan kuna sona ai" hannu takai kan roban, muslim ya kwace "Ke kam wlh anyi kwad'ayayya, to wannan na khdy ne" "To shekanan" Hka suka zaunah har tym d'in tashinsu ya rage saura 10mnt dije batasha lemun ba. Ana buga karaurawa muslim yace "Khdy b dea zakisha lemun nan bako"? D'aukan lemun tai tare dayin murmushi ta bud'e ta kafa kai ta shanye shi tass tukkuna ta ajiye roban "To nasha ko"? Murmushi yay matah, hannu dije taji an doramata a kafad'a tare da fad'in "Muje gidah ko"? Hanya suka kama suka mika, akan hanyar jiri ya fada d'iban dije, bata koma sanin abunda ya faru ba kuma. A hnkli ta fara motsa hannayenta tare da bud'e idonta ta d'aga kai ta dubie saman dan taga inda take, ganinta tai babu hijab, gashin kanta a barbajie a bayanta, babu takalminta a kafah, wani irin k'ara ta saki ta kankamie jikinta, tare da rirrikie suman kantah "Na shiga 3! Waiyyo ni Allah! Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un" Kok'arin mik'ewa ta soma, dushe2 ta fara hango mutum a tafieh, hakan yasa ta kara murza idonta. "Nazee" Dije ta furtah Da sauri nazee ta isa gareta "Khdy mai yake faruwa dake ne hka? Ya akai baki tafie gidah ba gashi ynxn har kusan karfe 5pm, nima nan gurin malama rabi nazo kinsan nan take kusa shine tace inzo in rakota tayi mantuwah, ni kuma nayou nan" Kuka ta k'ara fashewa dashi, ta miqe tsaye ta daukie hijab d'inta ta saka, tana waiwaye tana kallon nazee "Nazee ba wanda ya shigo a ajin nan ko? Bansan mai ya faru dani ba, bana iya tuna komai wlh" Ta rage tsayenta tayou kasa Rungumeta nazee tai "Deana kuka hka khdy, babu abunda ya faru, sannu kinji tashi muje in rikaki muje gidah" K'ara kankamieta dije tai "A'a nazee ki barni kawea zan tafie dkaina" Nazee ta shafa bayanta tana mamakin abunda ya faru da ita. "Is ok am here so stop crying" Tashi nazee tai ta hadamata sauran kayanta da takalminta suka fitah, keke napep suka tara. Har kopan gida aka sauke dije, nazee tace "Dama nan ne gidanku? Kai ta d'aga mata tai saurin juyawa ta shiga gidah, koda ta shiga a falo ta tarar da jama'ar gidan, hanklinsu a tashe. Sallama tai wnda yasa gabad'aynsu waigowa zuwa gareta. ®Kausar Luv💞 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((56)) to ((58)) ```©Kausar M Hassan``` Ummi tai saurin karasowa kusa da ita ta rike mata hannu, cike da tashin hankali mara misaltuwa ta hau jira mata tambayoyi "Dije ina kika tsaya hnklinmu gaba d'aya ya tashi" Idanunta ta d'ago da sukai jajir "Ciwan kaine ummi shine fa kawata nazee tajani mukajie gidansu tunda ita bata san gidanmu ba, ummi tace "Alhmdlh! Wlh har naji dad'i. Abbi yay ajiyan zuciya "Irin hka ki rika kira saboda a san inda kike" "Zan kiyaye abbi ngd" Wucewa tai saman d'akin aliyu ta shiga ta maida kopan ta kulle "Na shiga 3 mai ya faru dani, bana jin anmin wani abu a jikina amma hakika akuy abunda ke shirin faruwa dani, mai yasa bana tuna komai ne"? Ta fashe da wani irin matsanancin kuka mai ban tausayi, toilet ta shiga ta had'a ruwan zafi tai wanka ta fitoh, tai sallolinta tukkuna ta d'auki wayantah dubawan da zatai ta ganshi a kashe, a hnkli tasa hannunta ta danna power dinshi ya zama on. Ta d'ora kanta a gefen gado, hawaye suka dinga zarya a kuncintah. D'aga idonta tai sukai ido 2 da pic d'in haydar wanda yay a Saudi Arabia, kusa da masjid ya d'aga yatsunshi 2 sama yana murmushi, murmushi ta saakar mashi itama kaman wanda ke kallonta.. Nana kuwa farin ciki fal a rantah, muslim ya cika mata aiki, yau kam nasara tana bayantah. Washe garin ranar kamar koda yaushe hka ta kasance, bayan ta gyara d'akin duk da ba wani datti yay ba, ta sakamashi turaren kamshi, komai dea2 yayi zar_ sha'awah, ta shirya ta nupie skul bayan tayi sallama da jama'ar gidan. Nazee taci k'aro da ita zauneh kan kujera "Zaunawa tai "Ina kwana nazee" Nazee ta d'ora hannunta akan kafad'an dije "Hey yan matah ya jikinki? Hope bakisa damuwa a ranki ba"? Kai ta d'aga mata alamar eh. Dea2 lokacin muslim ya karaso kusa da nazee ya zaunah ya gaishesu kaman ynda suka sabaa. Muslim kallo d'aya zakai masa kagane akuy abunda ke damunshi, jikinshi sukuku, baida wani karfie. Haka suka kammala karatun a wannan ranar suka karasa gidah, misalin 2pm. Suna isa wanka dije ta shiga tai ta koma dkinta ta baiwa gado amana, ba ita ta farka ba sea kusan 4pm. Ta tashi tai alwala tai sallah ta zarce d'akin anty nana, akan kujera ta tarar da ita, gaisawa sukai sosai tukkuna suka shiga firah, dije na baiwa nana labarin irin zamansu a mkrnta komai na tafiya dea2, tana fad'amata ita kuma sea daria takeyi, yau kam nana na cikin farin ciki sosai, ko meye sila?🤔 A hka dea har akai maghrib ta tashi tai d'kin aliyu tai sallah ta kama karatun al_qur'ani har akai isha ta maidata tai nafilfili tai addu'ah sosai. Dea2 tym din karfe 9pm, ta shiga toilet dmn tai wnka... Like · 1 · Reply · Report · Wednesday at 8:41pm Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((59)) to ((60)) ```©Kausar M Hassan``` Kasancewar ummi na a falo ne, tare da abbi yasa sukajie sallaman da haydar ke rangad'awah, nana dake d'akinta tai maza ta fitoh cikin sand'a ta shiga d'akin aliyu kasancewar hanklin jama'ar gidan ya d'auku gurin magana dashi, kusa da abun gado ta d'ora envelope akai a jiki an rubuta ```"Wlcm back swthrt"``` Tai maza ta fitah ta koma d'akintah Aliyu yayi kibar shi, yayi kyau sosai gidan ya dauki kamshin turarenshi, jama'ar gidan kowa kawo gaisuwa ake, gaggaisawa sukai kapin ummi tace "Wuce d'aki d'ana kai wanka dije ma na ciki" Kanshi ya sosa tukunna ya haura sama da yar jakar hannunshi, dan jakunkunanshi suna motan shafi'u da akajie daukosu da ita dga airport. Kamshin d'akin yasa ya fitar da wani deep numfashi, aliyu yay zauneh kan kujerah, yana kallon d'akin yana murmushi. Kopa ta bud'e a hnkli ta sakko kafarta, ta fitoh ko gabanta bata duba sea ta fara yarfar gashintah, ta kwance towel d'in ta kara d'aurawa, ga mazaunanta suna juyawa, ta kara d'an girma. "Ma shaa Allah" Jin wannan kalman yasa tai maza ta daure towel d'in a kirjintah, kallonshi take kmn yau ta saba ganinshi, mamaki take anya kuwa shine ko ba shi bne, matsawa yay daf da itah ya kashe mata ido. "Deejah kice kika girma hka"? Idonta ta rufe da tafukan hannayentah "Waiyyo yaa ni kasa naji kunya wlh" D'aukarta yay duk da ruwan dake jikinta y zaunah akan kujera ya dorata akan cinyarshi "Na baki mamaki"? "A lots yaa aliyu ka bani shi kuwah" Murmushi yay ya fara shinshinar tah kamar mai kokarin gano wani abu. "Ehum2 yaa aliyu ka gaji wlh ka bari kai wnka ko"? "Oh ni yarinyr nan ta kara girma sea wayou takeyi" Murmushi tai masa sosai wanda yasa shi, afkawa bakintah ya manna mata kiss, kokarin fita take amma ya qara zaunar da itah, sea da ya tsotsie bakin nan tass tukkuna ya d'ago idanunshi ya dubieta "Kyan alkawari cikawa matata, kince ranar dana dawo zaki bani kanki, so ynxn lokaci yayi" "Waiyyo yaa aliyu ka tsaya kaji dan Allah" Ta fashe da kuka "Ya isa hka my dear kukan mie kikeyi kuma"? "Wallahi bana jin karpin jikina ka bari ko zuwa anjima ne" Murmushi yay mata "Ba damuwa ai gani gaki, shekara 1 ba wasa bace dear" Juyawan da zayyi idanunshi suka tsinakyou mashi envelope d'in nan Dea2 tym d'in dije ta tashi zuwa drawer dmn daukan kayan da zata saka. Tashi aliyu yay ya matsa kusa da gun, ganin abunda aka rubuta akai yasa ya dauka, tare dayin murmushi ya jujjuya a hannunshi ya fara kokarin bud'ewah, haka ya bud'e ya zura hannunshi ya ciro d'ayan photon dake ciki.. ®Kausar Luv💞 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((61)) ```©Kausar M Hassan``` "My lion" Dije ta kira sunanshi, hakan ya tsayar dashi dga duban photon ya mayar a cikin envelope d'in. Waigawa yay a hnkli, ganin dije a gabanshi taci wasu arnakun kayan bacci, jikinta kusan ko ina a waje, ta tufke gashin kanta da d'an karamin ribom, yasa shi sakin envelope d'in hannunshi ya maida kallonshi gabad'aya zuwa garetah "Wow!! Deejah kece hka"? Murmushi tai masa ta matsa kusa dashi "Am yaa aliyu ina zuwa ko"??? Hannunta ya janyou ya rike gam tare da k'arewa jikinta kallo. Gira ya d'aga mata tare da furta "Hey! haka ake? kawea dan kin ganni sea ki wani cewa fita zakiyi"? "Uhm2 nifa yaa ba fitah zanba" Kiss ya manna mata a kumatu "Ina zuwa ynxn nan zan fitoh, kada ki sake ki tafie ko ina kinji? Kai ta d'aga masa tare dayin murmushi. Toilet ya shiga ya watsou ruwa ya fitoh, jakarsa ya bud'e ya fesa turarenshi tukunna ya dawo y maida kallonshi ga dije Ganin da tai yanayi mata wani irin kallo yasa tai maza ta miqe tsaye cikin rawar murya ta furta "Am yaa na manta ummi tace inzo bayan isha" D'an guntun murmushi yay wnda ya kara masa original, qualitative and quantitative beauty... Lol. Da sauri ta nupie kopa kapin ta bud'e ya chapko hannunta suka had'a ido, kallon kallo suka rika yiwa junah, numfashinsu ya rika had'uwa, take jikinta ya hau rawa. "Em yaa plz kaga.... Bai jira abunda zata fad'a ba ya had'e bakinshi da natah tare da zura hannunshi cikin yar rigantah... Let's go honey🚶🏽 naja wayana muka karasa gaba🙊... Washe garin ranar misalin karfe 7am, ta farka, a hnkli ta bud'e idanunta "Oh my God"! Ta furta saboda ynda tagan kantah, gabad'aya a hargietie, bargon dake gefen gadon tai maza ta janyou ta rufe jikintah. Dea2 lokacin Lion ya fitoh dga toilet, kusa da ita yaje ya zaunah... Like · 1 · Reply · Report · Yesterday at 5:18pm Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((62)) to ((63)) ```©Kausar M Hassan``` "Khadeejah" Ido ta k'ura masa, tana k'are masa kallo. Hak'ika ita kanta tasan aliyu y had'u, samunshi da tai kuwa a rayuwanta to kawea baiwar Allah ceh, a ynxn kam tasan meye so saboda hka tana matuqar son aliyu sosai. "Na'am" ta amsa Shgiewa jikinsa tai sosai, tana mai jin laushin fatan jikinshi" Aliyu ya janyouta "Tashi kiyi wnka, da sallah, sea muje kasa ko" "OK" ta fara tattara xanen tana kokarin tashi, ya riko hannuntah. "Injin dea baki manta ynda ake wnkan ba"🙊 Murmushi tai masa "Ina zuwa dea" Da sauri2 ta shiga toilet d'in tai wankan da alwala ta fitoh ta saka atamfarta ta maida gabanta gabas tai sallan asuba, bayan ta sallamie tai addu'ah. Ta miqe tsaye kusa dashi taje ta zaunah ta fara wasa da yatsun hannunta "Yaa aliyu yau bazan tafie mkrnta bane"? Kallonta yay, cike da so da kaunah "Chaab ai kuma kin gama mkrnta dije, dan nafison dga safe, rana har dare ina tare dake" Murmushi tai masa kad'an "To ba damuwa tunda haka kake so ai my lion" Tashi sukai zuwa falo, koda suka isa sun tarar da su ummi. Cike da mamaki nana ke kallonsu saboda batagan alaman hargitsi a tare dasu ba, sea ma soyayya da nishad'i da d'umbin tarin farin ciki, kuma inda ta aje envelope d'in tasan dole sea ya ganshi. Gaisuwa sukai da abbi da ummi suka fara breakfast, bayan sun kammala, abbi ya dubie aliyu "Da fatar dea ynxn ciwon dake brain dinka baya tashi ko"? Murya ya gyara "Abbi ai na tafie asibiti an min duk abunda ya kamata" "Allah ya k'ara sauki" Ummi ta furta. Abbi ya dubie dije "Hadizatu yau bazaki mkrntar bane"? Shiru tai batce dashi komai ba "Abbi cewa nai tunda na dawo ai... Murmushi abbi yay "Toh ai matarka ce ynda kake so hka za'ayi maka da ita, zuwa anjima dea sea ku tattara ku koma gidanku, gobe sea ka kaita gidansu taga iyayenta ko"? "To abbi" Tashi nana tai rai a 6ace ta wuce d'akintah, ta kasa zama tai tsaye zagayen d'akin kawea takeyi kaman wata mahaukaciyah. "A cikin ranta take furta dole in k'ara ajiye wasu, ta dauko wata katuwar jaka a hannuntah, pictures ne gasu nan da yawah kala2, kai abun dae babu kyaun gani😓. Tai murmushin mugunta kad'an tare da kyallara ido "Idan baiga wanchan ba zaiga wannan, alkawari ne sea na haddasa tsana tsakanin aliyu da dijeh, na tsanesu kaman ynda na tsani mutuwana, da aliyu yaga wadan nan photonan na tabbata tsakaninshi da dije sea dea a memory... "Hohohooooo shiyasa nake burge kaina wallahi ni nana asma'u😉" Like · 1 · Reply · Report · Yesterday at 5:18pm Kausar M Hassan ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((64)) to ((65)) ```©Kausar M Hassan``` A makaranta. Nazee ce zaune duk batajin dad'in zaman ajin, muslim ne kusa da itah "Heeeeeyy! nazee anya lpy kike"? D'an karamin tsaki taja "Wlh muslim just kawea ina missing d'in Khdy ne, jikina na bani kaman wani abu zai faru da itah wnda ba mai kyau ba" Idanu muslim yabi nazee dasu "Hba nazee ya zaki ce hka? Ki rika kyautata zato mana da kyakyawan niyya kinji ko"? Murmushi tai masa tare da rike hannunshi "Muslim kasan na daukie Khdy kaman yar uwata, zan iya fighting akantah, a cikin kowanne hali, duk wnda ke kokarin cutar da ita kuwah wallahi makiyi nane kuma sea inda karfie na ya kare gurin bimata hakkintah" Muslim ya dafa kanta "Hba deana dan Allah, babu wani abu da zai faru da ita sea alkhairi, ynzn dea tashi mu shiga class" Tashi tai suka jera da junah suka karasa ajin, a hka har aka tashi a mkrntar. Misalin karfe 2pm. Dije ce kwance saman jikin aliyu tayi luff a kirjinshi tana shakar kamshin jikinshi. Goshinta y sumbatah "Khdy yaushe zaki haifamin yara"? Ido ta zaro! "My lion ni yar karama dani ya zanyi in haihu, kana ji ance fa da zafi gurin haihuwa, kuma ni wallahi bana son haihuwa ynxn" Murmushi yay ya sakala hannunshi a cikin riganta ya fara shafa jikinta "Ynzn Deeja bkya so inga bayanki"? Murmushi tai kad'an "My lion shekenan Allah ya kawo yaran" "Yauwa my dear ko kefah"? Murmushi tai masa ta manna masa d'an sumba a gefen kumatunshi. Misalin karfe 8pm na dare, bayan sun kammala had'a kayansu gaba d'ayah, aliyu ne zaune kan kujera yayinda dije ke tsaye tana sauraren waqan Hasbi_rabi wadda sami yusuf yayi. Kallonta kawea aliyu yakeyi, shi kam yayi dacen matah babu fad'a babu masifah, Idan yace tayi abu bata musa masa, a gskya ya godewa Allah daya bashi dije a matsayin mata a rayuwarshi.. Kiran da akai mata ne a wayah yasa waqan ta dakatah, wayanta ta hau rurin ringtone d'intah "Hum sath sath hain, A.B.C.D" D'auka tai ta kara a kunne "Hey nazee ykk"? "Well am gud and u"? "Same" "Ya skul? Ya muslim"? Nazee ta amsa da "Yana nan lpy qlw yau munyi missing d'inki Khdy maisa baki zo skul ba"? Dije d'an guntun murmushi tai "Kedea ba komai, ki gaida gidah zan kiraki gobe" "Alryt 'yan mata" Wayan ta kashe tare da offing d'in waqan, d'agawan da zatai suka had'a ido da aliyu, murmushi ta sakar mashi "Am zan tafie in dauko wani kaya da ummi ta bani yana d'akintah" A kunne ya rad'amatah "To kisa hijab d'inki mana" Murmushi tai masa taja hijab d'in ta saka, ta daukie wayanta, da tashiga recording ta fice zuwa d'akin ummi. Abunda kunnenta yajine yasa ta dakata a kopar dkin "Kamar yanda nai sanadiyar fitar uwarshi a gidan nan, haka nakeso inyi sanadiyar rabashi da babanshi, saboda yafi son uwarshi da shi kanshi dani, zan rabashi da duk wani abu dayakeso a duniyah, asiri ne ba yau na fara ba' Hannu dije ta d'ora aka tare da zaro idanu, murya na rawa ta furta "Ummi" Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!! Nikam kausar cewa nai kai ummi amma bakida imani ko kad'an🤔 ©Kausar Luv💞 ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((66) to ((68)) ```©Kausar M Hassan``` Jin hakan yasa dije tai maza takai kasa gefen d'akin, jikinta a sanyaye anya kuwa wannan maganar mai yinta nada imani kuwah? Hakika rayuwa ta zama yanda ta zama, tana matuqar tausayawa aliyu da mame. Haka ta daure ta miqe tsaye bayan d'an lokaci ta rangad'a sallama a d'akin, amsawa ummi tai dauke da far'anta "Maza zaunah khdja" Ta rike hannunta, ta dubieta "Ki rike mijinki sau da kafah, banda jayayya akan abunda yace kiyi masa idan har bai sa6awa shari'ah ba, kinji ko"? Kai ta d'aga mata jiki a sanyaye "Ummi zamu tafie sea da safe" Addu'ah tai mata tukunnah ta fitoh d'kin rike da wayantah ta karasa dkin aliyu, suka fitoh tare zuwa gidansu. A wannan daren kasa bacci dije tai jikinta duk a sanyaye. Wayanta ta dauko ta shiga audio dmn kunna karatun Al_kurani mai girmah, murya taji a cikinta wadda batasan ta dauka ba. A natsie ta tattara duk hanklinta ta fara saurara. Muryan nana taji, wnda yasa gabanta faduwa "Daman ba ummi ce ke magana ba, inna lillahi wa inna ilahi raji'un, wannan wace irin rayuwane haka? Yaushe ma har mutum zai kokarin raba mata da miji ita ba kishiyarta ba" Hawayen da suke kwararo mata a fuska tasa hannu ta share, a fili ta furta "Zanyi kokari dmn ganin mame ta dawo gidan abbi in shaa Allah" Haka ta tashi ta koma ta kwanta kusa da aliyu daketa baccinshi hankli kwance zuciya zaune, tasa hannunta ta rike nashi tana mai jin tausayinshi. Washe garin ranar da safe shafi'u ya kawo masa bags d'inshi har guda 5, sea tsiya yake yiwa dije. "Wea duk ta rikita lion ya koma kaman bashi ba" Bayan sunyi breakfast ya bud'e bags d'in ya ciro tsarabanta jaka har guda 2 duk English wears da Arab wears masu shigein kyau ya mika mata da wata sarkar azurfa mai kyau da itah har da duwatsu ne da itah, kar6a tai, tai ta masa gdyah. Bayan sunyi wnka suka fitoh, dama ya had'a kayan da zasu kaiwa mame da kuma su innah, shiryawa sukai tsaf tukkuna suka fitah, dama motanshi an wanketa suka kama hanya sea kauyensu dije. Kai tsaye gidansu mame suka nupah, sun jima suna fira a chaan ya mika mata kayantah, ta kar6a tai gdya da saka albarka. Nan suka wuce gida gurin innah. Inna gurin murnar ganin dije harda kukah, ta kar6a kayan da aliyu ya kaimata ita da baba tai gdyah. Sun jima a gidan dan har towuou sukaci kapin sukai masu sallama. Dea2 kopan gidan mame suka bi, dije ta dubie aliyu "My lion ina zuwa bazan jima ba zan fitoh" Ido ya kyafta mata "Ina jiranki MUHIBBATY" Da gudu2 ta shiga gidan a d'aki ta tarar da mame zaune akan kujera, kusa da ita taje ta zauna ta dubieta tare da rike hannunta ta kira sunanta "Mame, inaso muyi wata magana plzz" Mame ta gyara zamanta "Ina jinki dije" Tashi tai tsaye ta fara yimata bayanin komai da taji, ta kunna mata recording d'in.. Sun jima suna magana kapin nan mame ta tashi ta saka hijab d'intah ta fitoh zuwa kopan gidan tare da kulle kopah ita da dije... ```ALIYU_HAYDAR``` Page ((69)) to ((70)) ```©Kausar M Hassan``` Ido aliyu ya zaro yana kallon mame, cike da mamaki ya karasa kusa da itah "Mame ina zuwa kuma"? Kallonshi tai da idanunta da suka cika da kwallah "Aliyu jaa mota muje zuwa gida" Bai k'ara cewa komai ba, ya shiga motan suka lula sea kopar gidan Alh shuraihu. fitowa sukai mame na gaba dije na bayanta, hannun dije aliyu y janyou cike da tashin hnkli ya hau tmbynta "Ke! Mai ke faruwa ne"? Kallonshi tai ido cikin ido "Ka yarda dani my lion babu abunda xai faru sea alkhairi kaji"? Murmushi yay, shima ya rufa masu baya suka shiga gidan. A falo suka tarar da abbi, ummi da kuma nana bom. Abbi na ganinta cikin tsatsauran murya ya hau yin magana "Hajiya wea ban hanaki zuwa gidan nan ba"? Batace dashi komai ba taja tai tsayenta. Dije ta karasa kusa da nana ta dubieta tace "Nana dan Allah ki fadie gskya mai kika aikatawa mame? Da har kikasa abbi ya tsaneta hka"? Cikin rawan murya ta hau yin magana "Dije mai kike nupie ne"? Dije ta tashi tsaye ta dubie su ummi "Ummi ke macece mai wuyar samu a irin wannan Al'umman, hakika tunda nake ban ta6a ganin mace irinki ba, ka haifie d'ane ne baka haipie halinshi ba, nasan tabbas ke ba haka kike ba, amma kisani cewa nana ta zama albasa batai halin ruwa ba" Nana cikin rashin fahimta ta dubie dije "Ke dije wai mai kike nupie"? Waya dije ta d'auko ta kunnah recording d'in da tai, kowa ya saurara. Abbi dagewa yay ya d'aga hannu ya wanka mata mari mai kyau. "Ke wace irin macece, haka tarbiyyan da muka koya maki itace wannan"? Kuka nana ta fashe dashi ta yarfie hannayenta cike da zuciya ta fara magana "Ni wallahi abbi baka sona, baka k'aunata, baka ta6a farin ciki dani ba, tun ranar da aka haipie aliyu a gidan nan aka nuna min bam_banci tsakanina dashi, to ba dole kiyayya ta shiga tsakanina dashi ba" Ta k'ara fashewa da kuka "Shiyasa naje gurin wani malami yay asirin dayasa ka saketah abbi" "Yes! Nayi na amsa da nayi amma ke kuma" Ta maida kallonta ga dije "Mai zaki iya cewa a matsayinki na matar aure kina tarayya da wasu mazan"? Dum!!! Dga aliyu har su abbi suka ji fad'uwan gaba. Nana ta karasa kusa da dije ta rike kafad'anta ta dama "Kice karya nake dijeh" Ummi data riga ta hasala cike da baqin ciki da tarnakin abunda nana ta aikata ta karasa kusa da itah ta sharara mata mari, har 3 mai rai da lafiyah.. Cikin kuka ta hau yin magana "Nana bansan haka halinki yake ba, ashe dama bakida hankali, shiyasa kikai zaune a gidan kika kie aure duk wanda yazo yana sonki bkya sonshi"? Kunci nana ta rike tana hawaye "Hba ummi kema bkya sona? Kinfi son kishiya da d'an kishiya dani "yar ki wadda kika haifah"? Ummi cikinta tai zata daketa mame ta riketa "Deana dan Allah babu duka, duka baya shiryarwa add'uah kawea zamuyi matah" Huci nana take kaman wata sabuwar kuturwa, cike da bakin ciki ta furta "Tunda babu wnda ya yarda dani nasan idan anga shaidu dole za'a yarda" Da gudu ta haura zuwa saman d'akinta direct zuwa loca ta nupa ta dauko wata jakah, da gudu ta sauko zuwa kasan, a gaban aliyu ta watsa jakar "Ka duba ka gani, ga abunda nake fad'amaka" Ummi tace "Waike wace irin mahaukaciya ce mai kike kokarin proving"?? "Ummi ki kyaleni dan Allah ya duba yagani, tunda baku yarda dani ba". Aliyu idanunshi ya d'ago ya dubie dije, itama dijen shi take kallo, alamaa yay mata daya bud'e"? Kai ta d'aga masa da eh. Aliyu yasa hannunshi ya dauki jakar ya bud'e, tare da zazzagata kasa, wayam babu komai a ciki😳... To ina photo nan sukajie ne? ®kausar Luv💞 adsense 2 here
Share:

8 comments:

  1. Ok mungode sosai amma acigaba don gaskiya yadauko dadi novel din sosai wallahi

    ReplyDelete
  2. Gsky novel dinnan ya dau dadi a cigaba please

    ReplyDelete
    Replies
    1. The story is too sweet please we need the continuitio

      Delete
    2. The story is too sweet please we need the continuitio

      Delete
  3. Please complete 😢

    ReplyDelete
  4. Cigaba Dan allah

    ReplyDelete

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *