Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Thursday, February 9, 2017

Amal complete

adsense here [12/29, 10:34 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI. GODIYA TA MUSAMMAN GA ALLAH SUBAHANAHU WATA ALAH,DAYA BANI DAMA DA BASIRA TA RUBUTA NOVEL,TARE DA GODIYA GA HAMAGEE NOVELS GROUP,ALLAH UBANJIGI YA BARMU TARE AMEEN. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 1-5 Amal! Amal!! Hjy ladi take faman kwala mata kira kamar Wanda makoshinta zai fito waje.hakanne hakan ne yasanya Amal rawar jiki,da murya mai rawa tace,ganinan hajiya.tsoki tana sannan ta koma saman kujera ta zauna,tana faman mita.yarinya sai shegen nawa,saikace wacce zata gasan sarauniyar kyau,karasa ubanme take,acikin daki,wani tsaka taja,sannan takuma bude murya ta a fusace.wai ubanme kikiye cikin dakinnan,wlh kika batamin lokaci jikinkine zai gaya miki,sai shegiyar nawa kika iya,cikin hanxari tafito daga dakin tana daura dankwali.cikin zuciyarta tana fadin,ko minti goma mutun beyiba amma ake faman yimasa fada kamar za'a cinyeshi. Zuwa tayi ta durkusa agaban ta,kanta akasa,cinkin rawar murya tace hjy gani Dan girman Alla.....,Bata karasaba ta kwasheta da wani wawan mari,daya sata kifawa ba shiri ta dafe kuncinta tana hawaye. Ubanme zaki gayamin shegiya mekama da aljannu,wallahi saina hanaki yin wankan gaba dayama,kin mai danima sa'ar wasanki,kin barni tun daxu anan ina faman jiranki,kuma kinsan sarai fita zanyi. Cikin muryar kuka tace kiyi hakuri wallahi bansan fit......,Rufemun baki munafuka,inma kinsani fadamin zakiyi,wallahi kika cikani saina fasa miki baki,cewar hjy tana zaro Ido waje. Ki bude kunnuwanki dakyau kijini,zanyi bako Dan gidan hajiya bilki zaizo daga London, kuma anan gidan zai zauna,Dan tayi tafiya zuwa Dubai. Girki zakiyi mai,kuma ki hadami drinks, sannan ki huce ki gyaramai wannan dakin nawajan garden. Kina jina ko kuwa.cikin rawar murya tace eh.yauwa saura kuma kimin hauka wallahi saina karyaki. Cikin muryar kuka tace hjy ammafa yau kusan satina biyu banje islamiyaba kum.....,kuma me,kina nufi bazakiyi abunda nasakiba kenan.lallai Amal huyanki ya isa yanka,wallahi saina hadaki da ubanki,inni ban isa dakeba,shi ya isa dake.cikin kuka ta rike kafafunta tana kuka,wallahi zanyi hjy Dan Allh karki sanar masa,zanyi.mikewa tayi tare da hankade ta tafada sanman kafet,en dakin tana kuka.karma kiyi,gyalenta ta yafa,tareda rataye jakarta,tadau key din matarta ta fice daga falon. Wani irin kukane mai karfi ya kwace mata,wannan wani irin ukubane ni Amal nake ciki,yaushene zansamu gata irinna kowane da,Allah na rukeka kasamamin mafita ya ubangiji,hawayene me zafi taci gaba da bin kuncinta. Abun bakin cikinta shine ace itada gidan ubanta amma yn aeki sunfita samun hutu.kukan tacigaba dayi bame lallashinta harna wani Dan lokaci. Hanne me aikici ta shigo Wanda shekarunta baxe dare na Amal enba.haba Amal kuka kuma,Dan Allh kiyi hakuri,nasan koda baki fadaba hjy ce,amma inda sabo kin saba,so kike kijama kanki wani ciwon ko Amal? Dan Allh kibar kuka kinji,badamin yanxu me zakiyi. Hanne kinsan yau kusan satina biyu rabuna da islamiyah,kuma hadda zanyi amma shine hjy saboda tsabar mugunta tabani wani uban aeki,Wanda bawani nataba za aemawa,kawai dan gidan kawarta.hmmmm to shikenan naji yanxu de babu abundant zanyi taso muje muyi tare,dn Allh kibar kuka,baranaje na shanya kayan nan,saina dawo kinji tashi.Ahnkali ta taimaka mata ramike tabar falon. Komai tare sukayi da hanne Har gyaran dakin,sai wajajan 4:00pm sannan suka kammala. Saman dinning suka jere abincan da drinks en.sanna ko wance tayi dakinta da tsaftace jikinta. Misalin karfe 5:00pm daidai jirgin so Annur ya sauka a airport en jigawa.bayan en mintina da saukarsa fasinjoji suka fara saukowa. Ahankali yake takowa daga steps en jigin zuwa kasa,iska mai ddi tana kadawa,fuskarshi dauke da murmushi,fone inshine yayi kara,cikin nutsuwa ya sanya hannun shi cikin aljihunsa,da amsa kiran.murmushi yayi lokacin dayaga sunan me kirannashi. Hello ummina abunda ya fada tare da kara wayartashi a kunne.daga dayan bangaran ta amsa, Son kun sauka lfy.lfy qlau Ummi.yauwa ga kawatana hjy ladi tun daxu take jiranka,a gidan ta zaka sauka nasan zata kulamun dakai sosai kaji son,cikin sanyi jiki yace ohk.be jira cewartaba ya katse wayar,Dan harga Allah ya tsani wadannan frnds en na umminshi Dan de bayanca zaiyi. Hajiya ladi dake zaune akujerun gurin,lkc lkc tana kallon agogon hannunta,da tun around 4:30pm take agurin,waya dake rike a hannunta tana kallon pic en Annur da hjy Bilki ta turo mata. Daga kan da zatayi ta hangoshi yana tahowa fuskarshi ba annurin dariya.baki bude take kallon sa,da ganinshi a zahiri. Kyakyawan namiji dogo,me bakin suma da tsayi,yr madedeciyar fuska mai dauke da manyan idanu,a lumshe kamar namejin bacci,dagon hanci,da karamin baki,duk enda ake Neman namiji cikakke da yahada komai,kwarjini,ilmi,kudi,hankali,kasaita,Annur ya hada. Gabanshi tasha tare da washemai baki,umm ..ammm Annur ko?kai kawai ya gyadamata tare da yimata Kallan mamaki,gaba yayi tareda jan trolley ensa,batare da yakuma magana ba,idonta ta kulle hadeda hade hanna yanta a kirji,son Annur na da da,shiga zuciyar ta,ta furta dulema alhaji kabar duniya Dan na samu cikar burina. Dis page goes to my best grp ❤BEST FRIENDS❤tnkuuu for d Lov nd care. Written by zeenaseer😘 [12/29, 10:34 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 5&10 Misalin karfe 5:19mp, Suka isa kobar gidan Alhaji Aliyu Dutse,horn biyu me gadi yabude gate en gidan,hancin motar ta tura zuwa cikin gidan,a parking space tayi park en motar.a hankali tabude side enta na driver,tafito,A hankali ta nufi side en da yake axaune,kafin ta budemai ya futa a hankali,sannan ya nufi Boot da fito da kayan sa.sanna ya tsaya yana jiran ta nuna masa masaukin sa,cikin kararraya takaraso tana kissa,yauwa muje mana ko,nabarka kanata faman wahala,ko kallanta beyiba yaci gaba da danna wayarsa,saida ta kuma maimaitawa sannan ya nuna mata hanya.tana tafiya tana rangwada,shikuwa kota kantama bayayi,har dakin ta rakashi,sanna ta bude masa,kanshin turaran hutan da sanyin AC ne ya daki hancinsa,ahankali ya lumshe idanunsa Dan turaran yayi masa ddi.da sallama ya shiga dakin bakin gado ya anje trolley ensa,sannan ya juwa ya fuskanceta cikin sanyin murya yace nagodeee!.lumshe Ido tayi sabo da ddin muryarsa tare da rufe idanu.juyawa tayi tana rangwada harta fice,murmushi yayi danshi mamakima take bashi,babba da ita amma take abun yara.hadawa yayi kan gadon tareda rufe idanun sa,ya bude ahankali ya saukeshi akan silin dakin.mikewa yayi ahankali yanufi toilet dan watsa ruwa.ya dade a toilet en Dan ruwan yayi masa ddi,sosai ya jima kafin ya fito ya sanya jallabiyan shi. Masallaci yanufa danyin sallah magrib. Bayan hjy ladi tagama tabaro dakin Annur, daki tanufa danyin wanka,bayan ta fito daga toilet zama tayi ta tsara kwalliyan ta,kamar wata budurwa,English wears ta sanya sannan matsatsato,tafbas tayi kyau.hjy dadi farace tas amma akwai Karin mai,tanada jiki,amma ko kadan bata da kyau,farinne kawai ya ceceta. Bayan ta gama shirinta tamike cikin takunta na kasaita.dakin Annur tanufa tana rangwada.knocking tayi sau biyu sanna yabada iznin shiga,cikin sallama tashiga tana,ta huce bakin gado,tazauna kusa da kansa,a fusace ya miki yana kallan ta,meye hakane baki da hankaline,ko ke ba matar aure bacene,zakina shigewa mutumin daba muharraminkiba,pls kibar dakinnan karki batamin rai pls.cikin sanyin jiki tamike tanufi kofa,sannan ta juyo cike da kissa,dama cewa zanyi dakai abincinka na jiranaka.tana gama fadin haka ta turo masa kofar.tsaki yaja yana jin haushi irinna wannan ballagaxar mata.mikewa yayi badan yana soba,saboda yinwar dayake ji. A dinning en ya sameta a zaune kujera yaja can nesa da ita ya zauna,yana danna wayarsa.kallonsa taci gaba dayi kamar mayya. Amal! Amal!! Amal dake zaune kan abun sallah tamike da hanzari tanufi kofar fita,a dinning ta sameta tare da bakwanta,cike da harara ta kalleta,kin tsayawa mutane,baki iya gaisuwaba,batare da ta kalleshi ta gaidashi,gabanshine ya buga lokacin dayaji murya mai ddi da sanyi,yana san dagowa ya kalli me wannan muryar amma yana ganin kamar ya zubda girmansa. Dalllacan kizo kiyi serving en mutane suna jin yinwa,batace mata komai ba tafara zuba musu abincin.white rice ce,da stew tasha kaji,ta zuba masa fruit salad,da mango juice, sannan ta turamai gaban sa.tunda aka bude abincin kanshi ya cikamai hancinsa,burinshi kawai yafara ci yaji tests en abakinsa. Jellof en taliya da tasha vegetable da kifi,ta zubama hajiya.sannan ta juya tanufi dakin ta. Tafdi Jan!,abunda ya fito kenan daga bakin Amal,wato matarnan neman maxa kuma ta koma kenan,kina da auranki kizauna kina cin abinci da wani katan gardi,cikin irin wannan shiga,Allh ya kyauta. Saida ya dauki kusan mintina goma kafin ya jawo abincin yafara ci,cikin nutsuwa,hajiya ladi data anje spoon enta,tana kallan Annur cike da so da kauna,komai nashi burgeta yakeyi,Allh ya bani wannan yaro,abunda take ta faman nanantawa cikin zuciyarta.shikuwa da besan tana yibama abincinsa kawai yakeci,cikeda jin ddin shi,yayi mai ddi sosai kamar Karya kare.sosai yadau lokaci kafin ya gama cin abincin,sannan ya shanye fruit salad en nasa,mikewa yyi,sannan ya nufi hanyar dakin sa. Binshi kawai take da kallo kafin ta cemai saida safe.ko takanta be buba ya hucewar sa.naunauyar ajiyar zuciya ta sauke,sannan itama ta mike ta nufi part enta. Sunday mrng 4:56am ****** Lokacinne Annur ya farka daga bacci Dan fita masallaci,Sauri yaketa faman yi Dan yamakara sosai.sannan ya fito. Adaidai lokacinne Amal ta farka Dan gabatar da sallanta.Dan itama ta makara sosai.bayan ta idar da sallah ne,tadauko Alqurni Dan gabatar da tulawanta.Dama taruga da tasaba a kowace safiya.saida gari yafara aske sannna ta mike dan gabatar da breakfast. A kitchen ta tarda hanne,wadda ta taho ragema Amal en aeki Dan tasan sarai itace meyin girki kowace rana.bayan sun gaisane,hanne tace wlh Dama yanxu nake shirin zuwa na tambayeki abunda xa'a Dora,murmushi tayi,hmmmm hanne kenan ae koma meye kawai ki dafa.toh sikenan bara muyi kunun gyada da fankaso kawai.shikenan ba,Amal tace barana kwaba fanken,ke saiki hada kunun,yauwa,suna hira suna aekin Dan dannan suka gama,kai dinning suka jera sannna suka huce Dan hutawa. Sanye take cikin duguwan rigan atamfa,ammata kwalliyan White nd green tayi mata kyau sosai.kai tsaye dakin Annur ta nufa. Daidai lokacin yake fitowa daga wanka daure da towel a kugunsa,da wani a hannun sa yana goge kansa.karar bude kofar dakinne ya sashi dago da kansa wanda sukayi ido hudu da hajiya ladi. Wani dogon tsaki yaje,wake wata irin matace wlh dolena nabar gidannan nibansan me yasa ummina ta hadani dakeba,taya zakina behaviour enki kamar na marasa ilimine,gaskiya banasan irin wannan,pls leave cikin muryar tsawa yake mgnar saboda ta fusatashi. Murmushi tayi na en duniya,Annur kenan!,dama xuwanayi nagayama abi.......enough pls,kullum abinci to naji na gode,kuma bana bukatar kikuma shigo part ena pls.ya juya ya koma tailor cikin haushi. MUJE ZUWA😜😜 Dis page goes to u nemcy Allh baki lfy ameen. Written by zeenaseer😘 08105857631 [12/29, 10:34 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 10-15 Hmmm! Murmushin takaici tayi sannan ta jamai kofar dakin.falo tadawo ta zauna tana mamaki irinna wannan yaro,rayuwa kenan ita datake juya maza a hannun ta,yau ita karamin yaro yake yima hulakanci,hmmm! Yaro besan wutaba saiya taka.mikewa tayi tadau key en motar ta,ta fice daga gidan. Bayan ya fito daga toilet en,ya shirya cikin kanan kaya,sunyi masa kyau sosai,key dinsa da wayarsa ya dauka.dinning ya nufa kai tsaye,yaxauna ya kwashi girkinsa ya koshi, sannan ya dauki wayarsa Dan kiran abokinsa.ringing biyu ya dauka,yeh! ASA yane karde kace kana kasar tamu,murmushi yayi sannan ya bashi amsa,wlh kuwa tunjiya na sauka ina garinku kuwa.habade dagaske wlh ummi ce tahadi da wata frnds enta kafin ta dawo,pls kaxo ka daukeni,xan turoma address inasan zaga gari.ohk! Maza gani nan zuwa.sannan ya katse wayar. Mikewa yayi yafito harabar gidan,kai tsaye wajan me guard ya nufa.sallama yayimai,cikin fara ya amsa mashi,sannan ya bashi gurin zama.Annur yace baba,barka da hutawa,yace lafiya qalau dannan.hira suka dan taba kadan kafin Uthman frnd enshi yaxo. Bayan mintina dabasu haura ashirinba ya danna hrn.cikin hanzari me gadi ya mike dan bude masa.Annur ne ya dakatar dashi,A'a baba ka barshi fita zanyi insameshi.to shikenan saikun dawo Allh ya kiyaye,ameen Annur ya amsa tare da sa hannu a aljihu dan yimasa alkhari,sannan ya mikamai,cike dajin ddi yana godiya ya amsa,yana masa addu'a.sannan ya fice. A cikin mota yasameshi,sannan ya shiga da sallama.Uthman ne ya kalleshi cike da zulaya,Aa kaga Dan gidan hajiya Har wani kyau ka kara.harara ya yimasa ta gefan Ido,malam banasan irin wannan kawai kaja mu huce.dariya yayi sannan yaja motar suka bar unguwar. Zaune suke suna hira sama sama,Amal ta dubi hanne cikin silar tausayi,tace hanne kekuwa meyasa bakya San zuwa gida,saide koda yaushe ki zauna in wata yayi,abaki kudinki,kiyi zaman ki,ko baki da iyaye ne. Murmushi hanne tayi,Aa Amal iyayene sun rasu tun ina karama,saide ina tareda kakata,ta wajan uba,shine wata makociyarmu tayimin hanyar aiki,anan gidan,bayan zuwana nan gidan da shekara biyu,shine Allah yayi mata rasuwa,shiyasa nama dena zuwa,yanxu so nake Allh ya bani miji nayi aurena. Allh Sarki Allh ya jikansu cewar Amal. Sun jima suna hira kafin a kira sallar azzahr,sannan suka mike Dan sauke farali. Annur da Uthman yawo sukayi sosai,dan Har gidan su Uthman suka huta sosai,sai bayan magariba ya dawo.lokacin daya shigo Baba baya wajansa so shigewa kawai ciki yayi Dan watsa ruwa. Hjy ladi kuwa tunda ta fice bata kara daho waba Har lokacin. Shigarshi cikin falon yayi daidai da fitowar Amal daga kicin,sallama yayi cikin muryarsa mai sanyi,haka itama ta amsa mishi tareda dagowa taga me sallamar,kallan juna suka tsayayi nadan lokaci ko wannan su da abunda yake sakawa a ranshi.lokaci daya ta koma kicin shikuma yayi hanyar dakinsa. Saman gadanshi ya fada yana tunanin wannan yarinyar,shin yar gidan hajiya ladi ce ko me aiki ci,Aa ai in yartace baxatana bari tana wahala haka ba,kuma bata kama da yn aiki,komade wacece ita yana san yakuma ganin ta.mikewa yayi ya shiga toilet. Amal kuwa tana komawa kitchen zaman dirshan tayi a kasa,gakiya wannan ba Dan gidan hajiya bilki yar duniya Dana sani bane,ko kadan basa kama,wata kilama kawai Dan isakane hajiya ta daukoshi shine ta rufemun Dan karna gane,nan danna taji ta tsaneshi danko kallonshi vata fata takara yi. Kiran sallah insha dakayi yasashi fitowa daga dakin Dan tafiya masallaci. Yayi daidai da shigowar hjy ladi,da alamu a gayiye take.suna hada Ido ta sakarmai murmushi, shikuwa kotakanta beyiba ya bude kofar ya fita,itama din bata damu da hakanba Dan tasan halinsa,daki tanufa Dan yin wanka. Yana shigo dinning ya nufa Dan yin dinner.an an yatarda hajiya ladi,takuma cin uwar kwalliya,ko kallan ta beyiba ya zauna tare dayin sallama,cike da yanga da kissa ta amsa mishi.murmushi tayi tare da cemasa nasan ban kyautaba na barka kai kadai a gida,kayi hakuri wallahi biki naje kuma gashi da Dan nisa,kuma daxan dawo Montana tasamu matsala,kashi kamarna kira woka,natuna ba muta a hannun ka,shide kota kantama bayayi ita kadai take haukanta. Amal takirawo Dan tayi masu serving shikuwa cewa yake a ransa Allh yasa ya rinyar dazuce Amal. Cikin takunta na nutsuwa ta karaso wajan,ahankali ta russuna hajiya sannu da dawowa.bashina tambayekiba kinsan abunda zakiyi min,basaina fada miki.a hankali ya dago da kansa ya sauke su,akan Amal, cigaba yayi da kallan ta,shide komai nata burgeshi yake,hannunta yake kallo yanda take zuba abincin cikin nutsuwa. Hajiya ladice,ta lura da hakan wani kululun bakin cikine ya tsaya mata arai,cikin tsawa ta yimata maga.wai bazakiyi da jiki bane kinsan irin yinwar da mutane suka jine.idanunta ta rumtse tare da cije lips enta,zuciyarta na mata zafi,duk duniya bbu abunda ta tsana irin tsawa.maza tayi tagama,xubawa ta tura musu.dandanan tabar wajan,shi kanshi Annur beji dadin hakanba,toh ita wacece da hjy keyimata irin wannan,yanda take da kyannan,aeko yr aikice guduwa zatayi,Allh ne masani,dole yasan wace ita dan tana bukatar temako.kasacin abincin yayi,yabar wajan. Daran ranar kasa bacci yayi yana faman tunani Amal. Ita kuwa hjy Neman baccin tayi tarasa,lallai Annur karde ace son Amal yake,inkuwa tagane hakan wallahi zai Amal tayi nadamar kasancewarta a gidan duniya, Dan akan Annur babu Wanda zata kyale kowaye yayi jijin shiga tsakaninsu. Written by zeenaseer😘 [12/29, 10:34 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 15-20 Monday mrng 7:30am Annur ne yafito cikin shirinsa na kananan kaya sunyi mutukar yimasa kyau.zama yay adaya daga cikin kujerun falon da baya jin zai iya cin wani Abu batare da yasa Amal a idansaba. Batare datasan dashi afalon ba,tafito da kayan baccinta riga da wando ne blue colour a jikinta,kanta babu Dan kwali,gashinta me tsayi da santsi baki ne huluk,ya sakko Har gadan bayanta,ta kamashi da bakin ribbon.sosai tayi kyau,ahankali ta nufi kitchen tunda tafito yake binta da kallo,harga Allh kamar ya saceta ya gudu.bata huce minti biyar ba tafito daga kitchen din hannun ta rike cup da alama coffee ne aciki.tana gab da shiga dakinta.Amaaal! Cikin sanyi murya da besan lokacin da bakinsa ya subuce masaba.cup in hannanta ne ya subuce Dan harga Allh ta tsorata.a firgice ta waigo.ganin mutun zaune akan kujera cikin shiga ta kasaita,tabbas ya burgeta amma bata kaunar ganin shi,dan duk axatunta Dan iskan hjy ne.tsayawa tayi da mamaki tana kallansa,shima itan yake kallo. Ahankali ya mike daga inda yake yatako har gabanta,batare daya San lokacin da yayi hakan ba.har saida ya rage baifi taku biyu tsakaninsuba.cikin sassanyar muryarsa,yakuma kiran sunan ta,kasa amsawa tayi kanta a kasa,yace da ita ba gaisu!.cikin sanyin jiki ta rissina kadan tace,ban ganka bane "ina kwana! ,murmushi yayi lfy qlau kintashi qlau.bata bashi amsaba ta huce ta gefansa,dan gyara wajan da coffee n ya xube.mop ta dauko,sannan ta durkusa dan ta kwashe pieces en cup en.har lokacin yana tsaye yana kallan ta.jikinta har rawa yake dan Iran kallon daya tsareta dashi.garin sauri,tayanke da abun cup en.dan kara kadan ta saki,Wanda ya sanya yay maxa ya durkusa kusa da ita yana kokarin kama hannun ya duba,janye hannun tayi tana kallan shi,yana kikarin yimata magana ta mike tashige daki da gudu,kokarin binta yashiga yi,amma tasama kofar key.tsayawa yayi yana kallan kofar takasa furta koda kalma daya. Tsayawa tayi daga kan step cike da mamaki tana karemai kallo.takowa tayi har gabansa cike da kallan tuhuma.Annur lfy?me kakeyi a nan?nanma shuru be bata amsaba,cikin bacin sai takuma kallon sa,Annur tamba.......,bata garasaba ya fice daga falon.cikin wani irin hali ta kurma wata uwar ashariya tafdijan!,lallai km inde abunda nake tunani hakan ne,cikin fusata tashiga buga dakin Amal din. Ita kuwa Amal tana shiga dakin ta danna key,gabanta na faduwa,lallai ma wannan mutumin ko ya dauka nima yr iskace it in hjy,dazai wani kamamin hannu,harda wani rike sunan saboda bashida hankali.toilet ta shiga dan tsaida jinin hannunta.tana fitowa taji karan buga kofar. Tasan koba a fada ba hjy ce,ahankali ta karaso ta bude kofar,atsaye ta ganta tana uban huci kamar wadda,tayi tseran gudu. Wani uban kallo ta watsa mata.kanta a sunkuye murya na rawa tace hjy iiina kwana.daban kwanaba zaki ganni munafuka,uban me yaha daki da Annur ta watsamata wannan tmbyr.kanta ta dago tana kallonta da mamaki dan ita harga Allh inba yanxu da hjy ta fadi sunan sabama bata sani ba,koba tambayar ki nake ba.wlh hjy niban sanshi...yimin shi shegiya munafuka naxakiyima bariki bafa mutun a kofar dakin ki kice baki sanshiba. Wlh da gaske nake,coffee na xubo shine ina zuwa nan ya zufe,kawai naganshi anan,kuma yana zuwa na shiga ciki.saida hajiya taji haka hankalinta ya kwanta amma bata nuna mata hakanba.toh naji shikuma gurin wa kika anje ya gyara miki.Aa dama yankewa nayi shine na shiga na goge jinin kiyi hakuri dan Allh. Bata kulataba ta yi hanyar steps harta kusa ta jiyo.Amal ta kira sunan ta.naam!.abunda nakeso dake shine wlh duk ranar dana sake naganki da Annur wlh wlh na lahira saiya fiki jin ddi,ke saima kinyi nadamar kasan cewarki a cikin duniyar nan.sannan ta juya tahaye sama. Nannauyar ajiyar zuciya ta anje.ta bita da kallo tana fadi a ranta,inbanda abinki hjy meze hadani da dan iska,ai sai irinku,nide fatana Allh ya raba Abbana dake,da kokadan baki dace da zaman gidan saba.sannan taci gaba da abunda zatayi. Shikuwa lokacin daya fita ,xagayawa yayi yakuma cikin garden ya hau kan kujera,yana tunanin abunda ya faru.karde abunda zuciyar shi takeyi rayamai yaxamo gaskiya,tamfas yana da tabbacin zuciyar shi Amal take so,amma ya hakan zai faru,yazai kamu da soyayyar yarinyar da batasan wacece itaba,tabbas zuciyar sa batamai adalciba.idanshi ya rumtse tabbas yaci gaba da zama a gidan nan komai zai iya baruwa,amma gaskiya kafin yabar gidan yanasan yasan wacece Amal,amma yaga kamar tsoransa takeji,batada kwanciyar hankali a cikin gidan.da wannan tunanin axuciyar shi bacci yafara daukarsa.wayar shice tadau kara,mikewa yayi yana kokarin daga wayar.umminshi ce take kiransa. Sallama yayi mata sannan gaisuwa tabiyo baya,bayan sun gama gaisawa ne.take tmbyrsa ko da matsala.Aa ummina bbu matsala amma inasan naje kano cikin satinna,dan yana San yin wani Abu mai mahimmaci.bata hanashiba saide fatan Allh bada sa'a,ameen kawai yace sukayi sallama. Tun bayan hawan hjy sama,Amal tayi dukkan aiyukanta dan batajin dadin jikinta,bayan tafito daga wankane taga hanne zaune gefan gado.aa hanne yaushe kika shigo,naji ae kina wankane ya jikin da sauki wlh.amma Amal bazaki gayawa hajiya a kaiki asibiti kuwa,dan wanna matsalan naki.hanne nima inasan ganin likita,amma sai Abbana ya dawo,inga ganin cikin satinnan zai dawo insha allh. Toh Allh ya yarda yakuma kara sauki,bara naje nakarasa aikina.toh hanne nagode.ba komai ,tafada tareda kullo mata kofar. Bayan tagama shafe shafanta,ta sanya doguwar riganta,me kwalliyan stone agabanta color green,tayi mata kyau sosai.dankwalin rigan ta daura ta tsaya tana karema kanta kallo a mudubi.tabbas tasan ita kyakyawace. Amal yarinya yar kimanin shekaru 17.farace tas ga fuskarta daidai,me dauke da dara daran idanu,da dogon hanki,dan karamin bakinta me color pink.tanada shape me kyau,sannan tanada doguwan suma mekyu da sheki.tana da tsayi kadan dakuma kauri amma bacanba.tana da fara'a dasan mutane,ga ilimin addini,dan tun tana 12 yrs tayi saukan kur'ani mai girma.kuma tayi graduate tun last yr,lkcn tana 16.amma hjy ladi fir tahana taci gaba. ****** 8:00pm Lokacin ne Annur yashigo gidan kai tsaye dakinsa ya nufa dan yay wanka ya kwanta.yana murda dakin.zaune yaganta a saman gadun sa,taci uban ado,da alama fita zatayi.be matsa daga inda akeba saboda mamaki,ita kuwa ko a jikinta saima wani kallonsa take yi. PLS READERS KUYI HAKURI WANNAN SHINE NVL ENA NA FARKO,DUK INDA MAYI MISTAKE KUNA GYARAMUN,NO BODY IS PERFECT.LOV U ALL😘😘😍 Written by zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) Bece mata kalaba illa shige warsa dayayi,mikewa tayi tsaye dede inda yake har suna iya jin numfushin juna.murya kasa kasa ta kira sunan sa,Annur nasan bakaso ina shigo maka dakin ka,amma dolena yasa saboda bani da num.enka pls kabani mana.shide yana tsaye bece mata kala ba.am dama ba wani abune yasa kaganni anan ba illa inasan ka shirya zaka rakani dinner pls karka ce Aa. Shirune ya ratsa na wani dan lokaci,sannan yayi gyaran murya.Banajin zan iya fita at dis time,pls kibarni na huta.Amma yazaka min haka bacin nagama shiri na tsaf.ohk! Dama mun anje appointment dake ne akan zanmu fita? Kokuma inada Chance ne nagita da matar auren daba tawa ba? Kinga nagaya miki kidena shigo min daki but u refused to do so,zan bar miki gidan ki,maybe dan kin ganni aciki kike disturbing ena. Kayi hakuri ba haka bane naga baka zuwa ko ina,shiyasa nakesan muna outing dakai amma tunda bakaso am srry pls,I don't mean to upset u pls.naji pls have a way out frm ma rum.cikin sanda kamar kaxar da kwai yafashe ma aciki ta kama hanyar fita.hyy yakuma dakatar da ita.duk lokacin da kikesan mgna dani,kina kirana falon inde da gaske ne.kuma bake nake da bukatar ganiba,kina turo wani.yana kaiwa nan ya fada toilet. Ta dade a tsaye anan wajan.tafdi jan ! Dan kari lallai akwai aiki agabana ni ladi.wai ni dan cikina yake gayawa wannan maganar. Bayan ya gama shirin kwanciyar sa,harya kwanta bacci,sai kuma ya kasa tamfas yana bukatar cin wani abu dan yinwa yake ji,yanxu kenan ya zaiyi. Juye juye yake famanyi gaskiya inbesa wani Abu acikinsaba baxaiji ddiba.mikewa yayi a hankali yanufi kofa,dan yi samu abinda zaisa a cikin sa. Dakin Amal yanufa dan yana ganin kamar itace kawai xata taimaka masa.ahankali yashiga bubbuga mata kofar. Amal dake a kwance tun bayan magrib zazzabi na damunta,taji ana buga mata,kofar naki.jitake kamar baxata iya tashiba,amma tasan hjy ce,zata iya mata rashin mutunci.a hankali jikinta na rawa,ta fito daga dakin. Kallan sa take da mamaki,totlly speechless. Murmushi yadanyi sabo da ganin yadda hankalinta ya tashi.ba komai dama dan Allh wani Abu nakeso kidan samamin saboda yinwar danakiji ya karashe maganar yana dafa cikin sa.dan tausayi kam ya bata,amma gani take kamar baxata iyaba.cewa tayi dashi ina zuwa. Daki tashi,dan sako hijab inata,sosai tana jin jiki,amma dan bayanda zatayi,tunda Har ya tako da kanshi ya roka.da ta fito bata sameshi a nan ba,dan haka bata damuba kai tsaye kitchen ta nufa,zaune ta ganshi a daya daga cikin kujerun dinning en,yana duba fone ensa.hucewa tayi batareda ta kalleshi.sauran sandwich da coffee ta hado masa.agabanshi ta anje sannan tajuya dan barin wajan.Amal yakirayi sunan ta,bata jiyoba saide ta tsaya tana sauraran abunda zai fada.nagode sosai kuma ina neman wata alfarma a wajanki,batare data jiyoba ta amsa da inajinka,pls kozaki iya gayamin damuwar ki,naga kamar baki da lfy dan Allh karki tafi baki bani amsataba. Babu komai nagode da kulawanka.bata jira cewar saba tayi tafiyar zuwa dakinta. Saida ya cinye gaba daya sannan ya koma dakin shi. 10:02am Cikin takunta na kasaita take sakkowa daga steps in.har takarasa.dining ta nufa Dan tsabar yinwar datake ji,ga mamakinta taga dinning din wayam babu alamun abinci.tabbas Amal bata da mutunci to yanxu ubanme zanci kenan.kiranta ta somayi cikin daga murya kamar wanda zata fasa gidan da kara. Amal dake kwance ta kudundune da blanket saboda wani irin sanyi da takeji.duk tsoran datake ji baxata iya mikewa ba.hakanne yakara fusata hjy dakin tanufa gadan gadn dan wlh yau ko ita ko Amal. Da karfi ta banka dakin ta shige dan baxata sauraramata ba,ga mamakin ta,ganinta tayi kwance saman gadanta,tana faman rawar jiki.janyota tayi tundaga kan gado Har tsajiya falon.daidai lokacin ne Annur yake fitowa daga daki xowa falon.saboda tsananin wahala ko magana bata iyawa. Xaki tashine kosaina laka damiki tsinannan duka.lokacinne Annur ya shigo cikin falon,ganin Amal kwance a kasa da alamu ko numfashi cikin hanzari ya karaso wajan jikinshi na rawa,lafiya meya sameta Amal! Amal!! Amal!!! Har sau uku amma ko motsi batayi.baisan lokacin da daya dauke ta cak yayi hanyar fita daga falon da itaba. Hajiya ladi datayi mutuwar tsaye saboda mamaki ba tasan lokacin data fada kan kujera ba.dan kafafuwantama sun kasa daukarta.lallai tana cikin tashin hankali mundun Annur son Amal yakeyi,wani irin zazzafan hawayene yake zubo mata. Written by zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) 25-30 Me gadi dake zaune saman benci,ya hango Annur dauke da mutun a hannunsa.cikin hanzari shima ya taso,yallabai lafiya kuwa?Baba wlh ba lfy ba.toh abude muku gate mana ka dauko motar,Aa Baba budemun kofa na fita,konan kusa zan samu asibiti?gaskiya bazaka samuba,amma de kawai chemists nan gabanmu kadan. Hannun shi ya zura cikin aljihunsa dan dauko wayarsa ya kira Uthman, ringing biyu ya dauka.yauwa Uthman pls kayi Sauri kaxo ka daukeni mana,saiyace OK,dama ina kusa daku. Sunanan tsaye shida Baba me gadi,cikin mintina da basu haura goma ba,ya iso wajan.har lokacin Amal najikin Annur ko motsi batayi.shine abunda yake kara tayarme da hankali, tababas hajiya ta kashe Amal ba makawo da hannayansa zai kasheta. A sit in baya suka kwantar da ita,sannan suka shiga suma.Uthman ne ya dubi Annur cin mamaki yake kallon sa.wannan kuma wacece?kuma ina zamu kaita.kaga malam asibiti nakeso ka kaini na nan kusa pls.bai kuma cewa dashi komai ba yaja motar suka nufi asibitin. Tunada Annur ya dauki Amal yayi waje da ita komai na hjy ladi ya tsaya,dan tabbas tana kaunar Annur kamar yadda take kaunar rayuwarta.rashin kasancewa dashi,kamar baraxana na ga rayuwarta. Mikewa tayi tanufi kofar fita,dan cinma su Annur dan tasan bashi da mota. Kai tsaye dakin me gadi ta nufa,tasan baxai huce yasan inda suke ba.Bala! Bal.... Bata karasa ba,yafito jikina rawa.dan tsoranta takeji,tabbas yasan a haife ya haifi hjy ladi amma kai tsaya take fadin sunan sa saboda batasan darajar na gaba da itaba. Inamakama magana katsaya kana kallona,ina mutumin da yafito da yarinya yayi?. Eh toh gaskiya hajiya naga lokacin daya fito da ita,har yama tmbayeni koda asibiti nan kusa,dana gayamasa babu kuma, sainaga yakirayi waya,anxo harnan an dauke su.amma bansan wani asibiti suka nufaba.uban tsaki taja sannan tayi hanyar komawa cikin gidan. Tabbas yau duk inda Annur ya tafi da Amal saina nemosu kuma ko zatamutu ba likitn dazaiyi aiki a kanta. Cikin yn mintina suka isa wani saban asibiti, da alama baijima da fara aikiba.saban shi anyi rubutun da paint blue colour da many an baki ALKHAIR CLINIC. kai tsaye cikin asibitin suka nufa.dan ko kadan Annur baya haiya cinsa,burinsa Amal insa ta kasance araye tare dashi. Nurse ne suka amseta suka nufi emergency da ita.zama sukayi akan kujerun reception din.cikin mugun tausayin abokin nasa yace,Annur nifa gaskiya kasani acikin rudani,wai wace wannan yarinyar ne. Dagowa yayi da idanunsa sukayi jajir,cikin murya kamar ta masu kuka yace,nima bansani bro,bansaniba,abunda nasani anan kawai shine ina kaunar ta,inasanta kamar rayuwata,hawayene suka shiga biyo wa saman kuncinsa.sosai Uthman ya tausaya masa,hugging insa yayi yana bubbuga bayansa.tabbas abokinsa yana cikin bala'i,dan ba karamin Abu bane zai sashi kuka hakaba. Wata nurse ce ta karaso wajan cikin sallama, da Allh suwaye suka kawo mace yanxu.cikin hanxari Annur ya amsa da mune,tace Dr.nasan ganinku.su duka biyun bayanta sukabi xuwa dakin likitan.su biyu suka. Wata kyakyar matace da baxata haura shekaru 32 ba.tayi musu nuni da mazauni.bayan sun zaunane.tayi gyaran murya.tace waye mijinta acikinku.kallan juna sukayi sannan,Annur yayi karfin hali yace duk brothers inta ne mu.ohk,to magana ta gaskiya sis inku tana cikin wani hali,bakwa bata kulawan daya kamata.taya kuna raye zaku bari ciwo yayi mata irin wannan kamu.ko bakwa Santa ne. Ammm Dr.pls kiyi hakuri ba'a tare damu take zaune ba.bama wannan ba meke damunta? Tabbas tanasan kamuwa da ciwon zuciya,ta sanadiyar damuwar datake ciki.ka ciwon kai da zazzafi me zafi.yanxu cikin ikwan Allh, munsamu ta farfado,kuma munyi mata allurai.yanxu haka tana bccine.zakuje Ku biya kudi gaba daya harna magunguna duk.OK Dr.mungode sosai, mikewa sukayi tare da zuwa biyan kudin.Annur ne ha kalli Uthman guy nifa bn fito da ATM inaba.ae ba damuwa duk taimako ne.ayi amfani da nawa mana. Sunje duk sunyi abunda yakamata suyi,sannan aka nuna musu dakin da take.da sallamar su suka shiga dakin har lokacin bacci take hannunta dauke da drip.Annur ne ya zauna kan kujerar kusa da ita,yana kallonta.toh frnd kasande dare yayi kuma I guest mum nacan tana jirana so nixan huce,inyaso gobe zamuxo tareda mum,ryt Allah bata lfy.kai kawai ya gyada masa,ya fice tare da rufe musu kofar.wata iriyan ajiyan zuciya ya sauke,ya kama hannunta guda daya,yana kuma karema fuskanta kallo.ta rame sosai takuma fari.afili ya furta ina tare dake,Amal Har karshan rayuwata Allh ubangiji yavaki lfy. Tana shiga cikin gida,kai tsaye dakinta tanufa,tare da dauko key din motar ta,danyau ko karshan duniya suka shiga saita nemosu.fitowa tayi da Sauri tayima motar key.tafice daga cikin gidan. Babban asibitin garin jigawa tanufa dan tasan baxasu huce nan ba.tana faman sake sake a ranta. Tana isa tayi pakin ina motar ta.reception ta nufa,bayan sungaisa da me duty agarun take tmbayar ko ankawo wata budurwa me suna Amal. Nan tayi yn dube dubanta tace gaskiya hjy ba'akawo ba.nan tayi sallama da ita tafita. Wasa wasa saida hajiya takai taje asbitoci akalla guda biyar amma ba amal ba dalilinta,amma saboda naci da jaraba irin nata ko gajiya batayiba.kuma duk inda taje amsar dayace,gashi bata da num.Annur kuma bata da alamun komawa gida. 2:17am Shine daidai lokacin da Amal ta farka daga nannauyan baccin datakeyi,idonta arufe take furta kalamar ruwa zatasha.Annur da duk tsayin lokacinnan idanuwansa suna gaza bacci yamike dan taika mata da ruwan.bayan yafito ne daga cikin asibiti ya hangu wanidn shago da amala abubu suke saidawa acikin harabr asibitin. Shine yayi daidai da tsayiwar motar hjy ladi.cikin asibitin ta nufa dan agajiye take.tana shiga nan ma,reception ta nufa,yan sun gaisa da matr wajan take tambayarta ko ankawo wata mai sunan amal. Lokacinne Annur yashigo cikin asibiti hannun sa dauke da Leda da alama ruwanne aciki.huce hjy ladi yayi dake tsaye tajuwa baya,ya isa dakin. Eh! Hajiya ankwo mai suna Amal,amma meye sunan babata.ita wance aka kawo Amal Uthman ne(dayake Uthman ya sign din kawai yasa sunan sa)kuma da alama matar aurece..hjy ta danyi naxari nadan wasu lokutan tace nagode tajuya zata fita.matar tace hjy koxakixo muje kigani ko itance.Aa barshi nagode ina saurine. Lokacin da Annur yashiga dakin Har lokacin idanunta arufe suke.ahankali yakarasa wajan ta,Amal ga ruwan,taimaka mata yayi tasha ruwan sannan ya maida ya anje. Ahankali ta bude idanunta hada idon datayi da Annur shine take faman kokarin tashi,karasowa yayi cikin fuskar tausayi yace mata,kinaga pls niba abunda zanyi miki ki kwantar da hankalin ki.komawa tayi ta kwanta tare da lumshe idanunta dan ta gamsu da maganganunsa. Har kusan asuba hjy ladi na neman Amal da Annur amma Allh be muna mata suba.hakan ba karamin daga mata hankali yayiba.haka nan ta hakura takoma gida badan taso ba. Bayan Annur ya fita masallaci danyin sallah,haka itama ta daure tashiga toilet tayi alwala tayi sallah. Lokacin da Annur ya dawo daga masallaci gari yafara haske.abakin gado yataddata azaune zama yayi kujeran dake facing inta.rissinawa tayi kanta a kasa ta gaida shi,cike dakin ddi ya amsa mata,ya jikinta?da sauki. Nagode allh yasaka da alheri.murmushi yayi tare da cewa ameen. Ki kwanta kikara hutawa kafin akawo miki abinci kici,kisha maganinki ko! Ba musu ta juya ta kwanta dan tana bukatar hakan. Bata jimaba bancin ya dauketa,shima baccin yayi dan darn jiya be runtsaba. 8:30am Shine tym in da Uthman da mum inshi suka shigo cikin asibitin. Kai tsaye dakin suka shiga tare dayin sallama.Amal dince dake zaune a bakin gado ta amsa musu,danshi bccinshi kawai yake. Tsugunnawa tayi ta gaidasu,mumce ta zauna kusa da ita dan tana tausayinta.shikuwa Uthman tashin Annur yashiga yi yana dariya.idanunsa yabude.Au! Mum harkun Ido dariya tayi tana zolayarsa yo Annur aikai take jinya bakai ke jiyar taba.dariyar shima yayi sannan suka gaisa.yame jiki tace mai,da sauki wlh.Allh kara sauk,ameen duk suka amsa. Abinci suka dauko musa.saida suka wanke baki sannan suka shiga ci.mum da kanta take bawa Amal abaki,ita kuwa sai faman kunya takeji. Hajiya ladi tunda farar safiya tashiga kiran kawarta hjy bilki.bayan sun gaisa take shedamata.tun daran jiya Annur ya dauki wannan shegiyar yarinya Amal (dayake tana zuwa gidan kuma ta tsaneta)gashi Har safiyar yau danake miki zancannan basu dawo ba. Wata uwar asha riya ta dura,ita tama isa ta siyema yarona zuciya lallai kawai tashin hankali ba karamiba ba kuwa,cikin satinnan zan dawo wlh saina koya maka hankali. Shikuma bara na kirashi,inji ina isa dashi.. Written by zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) Bayan sun gama cin abincinne suta raha cikin farin ciki dan mum mata me sanyi hali da barkwanci.amma duk abunda suke Amal kawai jinsu take wani lokacin kuma ta saki murmushi. Shikuwa Annur hankalin sa na kanta,duk mayan mintina yana lura da ita. Suna nan zaune wannan Dr. Din tajiya ta shigo tare da nurse guda daya na biye da ita.bayan ta gaisa dasu mum,ta dubi Amal ya jikin naki,da sauki ta furta.babu inda kiyimiki ciwo eh takuma cewa.toh alhmdullh.ki ringa cin abinci kinji,kuma kinashan magani insha allh zakiji ddi sosai.magani ta anso wajan nurse in nan ta mikawa Amal in gashi ki shanye yanxu,za'a na kawo miki magani in tym in sha yayi Allh akara sauki.duk suka ce ameen.sannan suka fice. Annur ne ya mike ya dauko mata ruwa,dan san magani.bayan ta shanye ne. Mum ta kalli Annur tace yakamta ka dauko mata kaya kota samu tayi wanka ta canja kaya ko zataji dadin jikin ta. Toh mum bara muje da Uthman saiya kaini mu dauko mu dawo.shi kenan sai kun dawo. Sannan ya kalli Amal, toh yaza ayi kenan yasan ko hauka yake baze fara tunkarar hjy ladi da wannan batu ba. Ahankali ta furta idan kaje ka neme hanne acikin gidan take saika gaya mata Tavaka kayana da duk abinda yakamata ta kawo min. Ita kuwa hanne tanajin lokacin da hajiya ke bali'i.amma taki fito dan tana fitowa,zata kama xaxxaga mata nata raban shi yasa take yin shiru a daki,dan tana mutu kar tausayin Amal in. Bayan da taji komai ya lafa ne,sannan ta lallaba tashiga dakin Amal in,ga mamakin ta ta duba ko ina a cikin gidan amma ba Amal ba da lilinta.nanfa ta yi xaman dirshan tana kwasar kuka,shikenan hjy ladi ta kori Amal, ta raba yarinya da gidan ubanta.kusan kana tayi tana kuka tana rokon Allh ya dawo da Amal. Gashi babu Wanda zata tambaya taji in Amal ina ta bar gidan. Haka safiyar yauma,tananan inda tayi sallar asuba,sabo da tunanin halin da Amal in zata shiga. A kofar gidan Uthman yayi parking in motar shi,dan zuwa xaiyi ya fito.lokacin daya shiga cikin gidan gaba daya kayansa ya hada,ya fito da su zowa mota,da baxai iya cigaba da zama gidan hjy ladi Saide umminsa tayi mai koma me nene.bayan yagama hada kayansa.ya dawo tsakiyar falon yana kwala ma hanne kira. Hajiya ladi dake zaune saman kujera kusada mirror tana kwalliyan, dan tunda hjy bilki race zata kira Annur han kalinta ya kwanta.jin kamar karar muryar Annur yasata yin maxa ta sauko kasa,kanta ko dan kwali babu tasha uban kitsan gashin roba,kanana. Ga mamaiinta taga Annur tsaye a tsakiyar falon. Hanne na zaune taji ana faman kwala mata kira.jin muryar namijine ta dan tsorata,aina wani yasan sunan ta.hakan yasa ta kasa fita,saida taji kiran ya karo sannan ta fito da Sauri.turus tayi tana kallan shi dan ita batama taba ganin saba.kode aljannune suka sha feta. Yauwa kece hanne? Kai ta gyada masa alamun itace.Amal ce bata da lfy shine aka kwantar da ita a asibiti. Tace ki kwaso mata kayan sawanta kamar kala uku haka,Dade sauran kayan amfani,ina waje inkin gama ina jirani. Hanne sabo da dadin jin Amal inta nanan yasa ta juya jiki na rawa,zata kwaso kayan. Hjy ladi dake tsaye a steps tana kallon su,ta dakawa hanne wata mahaukaciyar tsawa.dakata idan kika sake kika kara motsi naya anan wajan abakin aikin ki dan uwarki. Hanne da jiki yahau rawa,hawaye ta soma. Annur ne ya kare mata kallo,sannan ya dubi hanne yace canne dakin Amal din ko? Yau nuni da yatsa zuwa dakin. Sannan yay hanyar.Annur wlh zan cimaka mutunci mundu kashiga dakinnan.iska yabawa anjiyar ta,ya shige warsa kai tsaye. Yanayin akin nata yy masa kyau komai a gyare tsaf sai kanshi yake.wardrobe din daya hango ya nufa,budewa yayi kayan komai neat.daga kasa ya hanko wani dan karamin trolley, kaya daya dauko yashiga zubawa aciki.saida ya hada komai tsaf sannnan ya rufe ya fito. Tsaye yasameta a bakin kofa tana faman huci.sai muga ta wace hanya zaki fita da kayan.harni zaka ciwa mutunci karamin ka dakai,wlh bara kaji na gayama kai karamin dan iska ne,kuma babu inda zaka fita da wadannan ayan. Waya sanima ko baki kuka hada kuka tafi yawan iskancinku zaku fake da rashin lafiya.in gaskiyane wani asibitine acikin garinnan banjeba. Cikin fusata ya kalleta,tir! Allh ya kiyaye angaya miki kowa irinkine jahili,ni bansanma wani tsautsayinne ya hadaki da ummina,bakisan darajar mutane ba balle ki wani ya kalleki da daraja.varakiji babu wanda ya isa ya rabani da Amal ko duniyace zata taru.Amal matatace kuma saina aure ta insha Allh. Tasss tasss! Ta dauke shi da mari.ni kake gayawa haka.hanne dake tsaye tana kallan su ta dafe baki da mamaki. Kaje ka tambayi yr duniyar uwarka,wacece hajiya ladi.kuma sai hali yaxo daya ake bota.niba jahila bace uwar........ Tasssssss tasssss! Shima ya wanke mata fuskarta da mari,ya hankadeta ta fadi kasa.yayi fice warsa. Cikin mota ya isa.ranshi a bace.Aa guy lfy nakanka haka? No! Muje kawai.motar yayimaki sannan suka kama hanyar asibitin. Kuka sosai tashiga yi agurin,hannunta akan kuncinta.sosai zuciyarta ke tafasa ,ko kadan bataji zafin marinba zafin,son da Annur kema Amal takeji.wani kukan takuma fashewa dashi tayi. Hanne na ganin ammari hjy ta Ruga daki,zuciyarta na mata dadi.dama hausawa sunce gaba da gabanta.hannu ta daga sama tana hamdala ga ubangiji Allh sa da gaske auran Amal in zaiyi. Basu dau wani likaciba suka isa asibitin. Bayan ya dauko mata kayanta yace frnd bara,na kaimusu kayan ina ganin gidanku zan koma,naga waccan matar na kokarin yimin hauka.Uthman dariya yayi,yace ina jiranka. Da sallama ya shiga dakin dan Har Amal ta shiga wanka.yauwa mum ga kayan nata.ko yanxu zaki koma?. Aa nikam ina nan har dare kuje kawai kwadawo Ku daukeni.kucema mama Ido ayi abincin da yawa harda na asibiti. Toh kawai yace da ita suka huce. Saida tasha kukanta ta gode Allh,sannan ta mike,da hau sama dakinta.tana shiga,kira na shigowa wayarta.Abban Amal ne ke kiranta.jiki a San yaye ya dauki wayar.sallama yayi mata kafin yace da ita yana hanya yau ze dawo.toh Allh ya sauke Ku lfy,ameen. Ina Amal take ne? Tana nan kalau.ywwa a gaidata. Sannan sukayi sallama,sosai hankalinta ya tashi tasan sarai akan Amal komai zai iya faruwa.mikewa tayi dn zuwa ta shirya masa abincin. Bayan yayi wanka a gidan su Uthman sallah sukayi sannan sukaci abinci. Maln kataso mu koma asibitin mana,kasan bawani sabawa tayi ba da mum.hhhhhh !kenan kai ta saba dakai ko? Cewar Uthman. Eh mana shima dariyar yake. Wayar shi ya dauko dan tun jiya ya kasheta,saboda zafin da kansan ya dauka.ko minti biyu beyi da bude taba kiran umminshi ya shigo.yana murmushi ya daga. Kabani kunya wallahi Annur!. Ummina me kuma nayi.yimin shiru nixaka cima muntunci,kanuna ban isa dakaiba kenan, tunkafin nayi maka rashin mutunci ka maida yarinyar nan gidan ubanta.amma Ummi naga taimakonta fa nayi bata da lfy.sannu Sarki tainmako ga masu bukatar taimako nan a gari saime karfi zaka karawa karfi.toh bakai ba ita inde nina haifeka,ayau dinnan inasan kabar jigawa ka koma kano Na gaya maka.Ummi dan All......be karasaba ta kashe wayar. Kuka ya saki mai karfi.shikadai yasan yadda zuciyar shi ke masa,jiyake kamar tafita daga jikinsa. Baki bude Uthman yake kallon sa,shi yazatama Ummin tashi ce ta mutu. Annur lafy?Uthman ummina ta zata rabani da Amal, bazan taba iya rayuwa ba tare da itaba,wlh daukarta zanyi mu gudu. Haba Annur sai kace ba jarumin dana saniba,taya kamari mace tashiga zuciyarka haka,pls ka dena irin wannan. Cikin wani irin ya nayi ya dubi Uthman, wlh akan Amal babu abinda bazan iyaba.mukullin mota ya dauka tareda,ficewa daga dakin.Uthman ne yabishi yana kiransa,abakin motar yayi sa'ar cimmasa.haba Annur kar zuciya ta kaika ta baroka mana.kabi komai a sannu mana,kasan ba lfy garetaba tana bukatar abubuwa da yawa.kuma kaji de abunda Dr.tace,inkuma so kake ka karasata shikenan. Jikinshine yayi sanyi.yace shikenan. Yauwa kokai fa,yanxu muje muga jikin nata.. Written by zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) I dedicated dis page to my cwt frnd shaheeda,u passed a frnd to me ur ma blood sis,I rwwly Miss u dia,Allh bar zumuci ameen😘😘 35-40 Kai tsaye asibitin suka nufa.bayan sun sauka cikin dakin suka shiga da sallama. Mum ce ta amsa musu.Amal na kwance akan gado saboda drip in dake jikinta da alama bacci take. Annur ne yadubi mum.cikin wani irin hali,mum bade jikinne ya dawo ba?.wlh kuwa,zazzabinne yadawo shine suka yi mata allura kuma suka saka mata drip. Kujera yasamu ya zauna danji yake tsayuwar na kokarin gagararsa.tabbas Allh ya jarabceshi da San Amal Har yana jin in babu ita adoran kasa baze taba rayuwa ba.hani hawayene yakuma sakko masa.amma bai Bari kowa ya ganeba. Wayar shice ta kama kara.jiki a sanyaye yamiki,dan amsa kiran,ina xuwa kawai ya ce da Uthman ya fice.shi kanshi Uthman din tausayi sa yake ji. Can harabar asibitin ya nufa,sannan ya amsa wayar. Shiru yayi yana sauraran abunda zata fada. Annur! Dafatan ka kama hanyar ka ta komawa gida.saboda gobe gobannan zan shigo garin kano nima.nafasa kaiwa Friday din. Amma Ummi dan Allh kibari sai goban nataho mana,yanxu yamma tayi kuma kinsan banasan tafiyar dare pls kiyi hakuri,yakarasa maganar kamar zaiyi kuka. Shiru tadanyi na wani lokaci kafin tace,Allh ya kaimu,banasan kuma na rigaka shiga gida.bata jira me zaiceba ta kashe wayarta. Kanshi ya rike saboda wani axa babban ciwan da yake masa,tabbas umminshi bata kaunarsa,kasheshi take da shirinyi.kawai kashe wayarsa zaiyi koma me zai faru ya faru. Hajiya ladi kam ,dan gajiya ta gaji,ga faduwar gaba datake faman damunta,mundun Abban Amal ya dawo be tandata acikin gidan ba.sai kusan magriba tagama duk abunda zatayi. Wanka taje tayi,sannan ta ca6a uban ado.tana zaune tana faman gyaran dauri taji karan motoci.ko ba'a fadaba tasan Abban Amal ne.dakewa tayi zuciyarta na gayamata saikace ba hjy ladi ba ina kika baro, makircinki da kissar ki.murmushi tayi,sannan ta mike dan zuwa tarar me gidan nata. Da sallamar sa yashigo cikin falon.cikin kissa da kisisina take tafiya. Zama yayi saman kujera tareda cire hular kansa.zama tayi a kujerar da ke facing dinsa,sannu da zuwa andawo lfy,ya hanya. Murmushi yayi tareda amsawa lafiya kalau ina mamana.gabanta ne ya fadi,amma saita dake,ta kakalo murmushi karya,kabari mana ka huta saita zo taga Abbanta. Mikewa yayi tareda fadin bara na watsa ruwa Jamila,toh Alh.tafada tare da bin bayansa. Yadau tsawan lokaci kafin ya koma dakin.lokacin daya shiga amfara kiraye kirayen sallar magrib.Uthman yayiwa magana,dan Har lokacin Amal bacci take.mum ma mikewa tayi tanufi toilet. Annur de tunda suka fito kasa magana yayi dan gaba daya kanshi a daure yake.shima Uthman beyi masa maganar ba dan tausayinsa yake. Sallah sukayi sannan suka koma cikin asibitin. Alh.na zaune suna cin abinci shida hjy ladi.ya kuma kallan ta wai ina Amal ne kobatasan Abban ta ya dawo bane.shiru tayi bata bashi amsaba taci gaba da cin abincin ta. Cokalin ya anje tareda xuba mata idanu.mikewa yayi yanufi dakin Amal in. Da sallamar sa yashiga dakin amma shiru,saiyayi tunanin ko tana toilet amma shiru bata fitoba. Jamila! Jamila!! Ya kwala mata kira.gani tafada tana tsaye abakin kofa,tunda nashigo gidan nan nake tambayr inda Amal take amma kinki bani gamsarshiyar amsa. Alh.dama banasan tayarma da hankali ne amma yau kwanan Amal biyu ba acikin gidan nan ba. Mikewa yayi daga Zaunan da yake.me kike nufi ina tatafi? Wata sani acikin garinnan? . Oho wannan kuma amsar sai inka ganta kayi mata.ta shige warta.cikin tsawa ya kuma kiran Sunanta,kamrya zaki na gayamin irin wannan maganar. Lallai kai dinnan dama zaman aure naxo ko kuma gardin yrka daxakaxo kanamin tambayoyi kamar wani lawyer. Gaskiya ni banasan irin wannan can ka nemeta. Dakata jamila duk wani rashin mutunci da zakiyi zan jureshi amma banda akan Amal wallahi na gaya miki. Toh meye aciki iya kaci kace kasakeni saime kaikadaine namiji,zance kasan kowace ladi! ,dan haka wlh baxaka takuraniba. Upstairs ta haye warta,batare da takara kallon inda yake ba. Gaba daya kansa ya daure,tabbas yasan Amal baxata taba yin abunda aka fadaba.yanxu ina ma zai fara Neman ta,yasan duk inda take tana cikin tashin hankali. Dakin hanne ya nufa dan yasan zata san inda Amal in take. Hanne da tun tafiyar Amal bata cikin jin dadi.kofar dakinta taji ana bugawa.mikewa tayi ,ta bude dakin.ganin Alh. Tsaye bakin kofa yasanyata saurin risisnawa tana gaidashi.bayan ya amsa mata. Yace dan Allh hanne kinsan inda Amal dita take? Har saida kwallah ta zubo mata ,tagayamai duk abunda ya faru.mamaki yashiga yi,waye wannan da zai shigo har cikin gidanshi ya marar mai iyalinsa. Cikin fishi shima ya nufi hanyar upstairs in. Kwance ya sameta saman gado.Jamila yani dan iskane yashigomai gida hada dukan mai iyali. Gabanta ne ya fadi.ba magana nake mikiba. Dama dan gidan hajiya bilkine,yauwa kice biri yayi kama da mutun ban rabaki da wannan yr iskar matarba harxaki jahomin danta cikin gidana,kice kawai kun hadashi da yata yatafi da ita ko? Wallahi aa dama bata da lfyne shine ya kaita asibiti kuma aka kwantar da ita. Wani asibiti ne? Ji tayi kamar tayi fitsari a Wanda. Wallahi nima ban saniba.hmmm! Jamila ni zaki maida karamin yaro,wlh duk abunda ya sami yata court ce zata rabani daku. Be kuma cewa komai ba yabar dakin. Hankalinta atashe tashiga Neman layin hjy.bilki harta gama ringing ba'a dagaba,sake kiranta tayi,wannan karanne ta dauka. Wlh hjy Annur zai jawo mana bala'i,kinga Abban amal ya dawo,gashi sai fada yake harda court ce zata rabamu dashi. Dallahcan rufemun baki kina babbar mace amma baki iyada gidan kiba,Har namiji ya zauna yana gaya miki magan,gobe zan shigo kasar.zansan yadda zamuyi.shikuma Annur wlh ko zai mutu wallahi bazai aure Amal ba.kashe wayar tayi.hjy ladi taji dadin hakan dan tasan kawar ba wasa.. Bayan su hajiya suntafine aka kawo musu abinci.shikuwa Annur ko kadan bayajin zai iya saka wani Abu acikin sa. Har Amal ta farka amma be saniba yana can yana faman tunani. Kallan shi ta tsaya yi cike da tausayinsa.sai yanxu ta gane ba halinsa daya da Babar saba. WANE NE ANNUR?....... Written by zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) 45-50 I dedicated dis page to ma sistoo Maryam Naseer nd sis fareederh.Lov u to d Moon nd bck.Allah ja daranku ameen👄🌹😘 WANE NE ANNUR? Asalin sunan sa shine Annur Shu'aeb Abubakar. Mahaifinsa dan garin jigawa ne,mahaifiyar sa kuma yr kano ce.sunan mahaifiyar sa hjy.Bilki.sunyi auran soyayya ita da me gidanta Shu'aeb. Shide bawani me kudi bane amma yana da rufin asiri. Shekarar su uku da aure amma ko batan wata bata taba yiba.shikuwa Alh. Shu'aeb yana da mutukar San yara.hakanne yasanyashi karin aure.ya auri wata mata mai suna Hauwa.hayan Hauwa taxo ba dadewa,hjy.Bilki ta samu ciki,murna wajan Alh. Ba'a cewa komai. Amma ita hjy.bilki ta dauki kishin duniya ta Dora kan Hauwa.duk da hauwan batajin ddin abunda take yimata,kasancewa mace ce me hakuri bata nunawa. Har Allah ya sauki hjy.bilki lafiya,ranar suna data yaci suna Annur. Sosai yasamu kulawa wajan iyayen sa,da Hauwa na kaunarsa kuma tana San tarinka daukarsa,amma fir hjy.bilki bata bari ko kofar dakinta yaje.inde ba babansa bane yaje dashi. Har Annur yafara tafiya amma Hauwa ko bantan wata bata taba yiba.hakan na mutakar tayar mata da hankali.amma ta fauwalawa Allah lamuranta. Bayan shekara 10 da haihuwar Annur tun daga lokacin haihuwa ta tsaya a gidan Alh.Shu'aeb. Saiya ci gaba da godewa Allah daya bashi tillon dansa,tamkar dubu.dan yaran ataso cikin gata da kulawa,gashi da kokari makarta.haka kuma duk lokacin dabai gane wani abunba yakanje gurin antynsa Hauwa ta koyamai. Saboda ita hjy.bilki bata yawan zaman gidan kullum tana yawan kasuwancinta.na kayayyakin sawa Dana amfanin gida. Shiyasa Annur yafi sabawa da Hauwa. Haka rayuwa taci gaba cikin gidan Alh.Shu'aeb. Wata ranar laraba da misalin karfe 6:15pm,Alh.sunje kano ziyara shida matansa da dansa,suna kan hanyar dawo warsu zuwa kafuna.sukayi hatsari.nan take Alh.Shu'aeb Allah ya mai rasuwa.ita kuwa Hauwa abun sai Wanda yagani,dan ko numfashi da kr take iyawa.Annur kuwa karaya biyu yayi a kafar sa.amma hjy.bilki da ikon Allah ko ciwo batajiba. Haka aka dauke gawar Alh.Shu'aeb akayi masa jana'iza. Nan aka dauki Annur da Hauwa akayi asibiti dasu. Bayan kwana uku da rasuwar Alh.Shu'aeb. Allah yayima Hauwa rasuwa.sosai Annur yaji mutuwar iyayensa guda biyu.ita kuwa hjy.bilki ko a jikinta dan gani take dabarar tace tasa bata ji ko kwarxane ba a accident in da sukayi. Haka akaci gaba da zaman makwaki Har aka gama. Bayan anyi sadakar 40 ,lokacin Annur ya samu sauke sosai dan haryama koma makaranta. Dama anriga da abbata gadansu.nan ta xubasu cikin business inta.hankali kwance takuma bunkasa. Lokacin da Annur yakai zai shiga jss1,sai hjy.bilki ta kaisa boarding sch.dan aganinta zatafi samun kwanciyar hankali.tunda so take tafara fita kasashan waje tana gama takaba. Akwana atashi ba huya gurin Allah yau ne Annur yayi graduate a makarantar su.yanxu kuwa hajiya bilki tazama babbar antajira.dan tabar garin jigawa gaba daya ta koma,kano ta gina tanka memen gidan ta. Business take sosai kasashe ba inda bata zuwa.takuma gogewa tayi kyau tana samun kudi sosai. Bayan Annur yagama secondary sch.dinsa sai hjy.bilki ta turasa London dan cigavan karatunsa. Tun bayan tafiyarsa London hankali ta,takuma kwanciya,sosai tana kula dashi dan komai yakeso tana yimasa shi.kuma lokaci lokaci tana kaimai ziyara.dan tana mutukar kaunar sa kuma shima yana mata biyayya sosai. Annur yasataso cikin gata da kuma kulawa gurin mahaifiyar sa,amma duk da hakan besa ya lalaceba,shi ko mata basa birgeshi bare shaye shaye.Yakama karatunsa sosai na Art and design. Gashi yana da kokari shiyasa yake da farin jini a makarntar.kowa kaji suna kiransa young ASA. Bashi da buri arayuwar sa da yahuce ya gama karatunsa ya zama babban Artist. Shiyasa ya maida hankali akan abunda yasa gaba. Hajiya bilki kuwa an kama kasa.kullum cikin shiga ta alfarma ta zama kamar wata budurwa sai cin duniyarta take da tsinke. A yawanta na fita abroad, tagamu da hjy ladi a Dubai. Hjy ladi cikakkeyar yr duniyace,ita sana arta shine Neman maxa,da kuma business din kaya.tunda take bata taba aureba.kullum suna yawan gantali,shiyasa ta tara abun duniya.sosai.gidan ta yananan a garin jigawa amma iyayenta yn yobe state ne. Nan suka kulla alaka da hajiya bilki, taxama aminiyarta sosai harta dorata akan harkar banxan da takeyi.sosai hajiya Bilki taji dadin hakan dan arxiki yaci uban Nada. Wata rana taje Dubai ta hadu da wani mai kudi Alh.muktar ta aureshi.amma tamai karyar ita baxawara ce,mijinta ya mutu.haka ya yarda ,akasha biki sosai danshi Allah ya sakamai San hajiya ladi wato Jamila. Amma da sharadin zataci gaba da business inta,haka ya yarda,nanfa tasamu damar cigaba da iskancinta a boye. Bayan shekara 4 . Yaune Annur yagama kara tunsa gabaki daya.dan haka yana cike da tsananin murna.sunyi shagali sosai a sch dnsu. Haka umminsa ta shiryamai party hadadde anan London din dan tayashi murna.naira tayi kuka ranar.tun daga ranar yagane umminshi ta canxa,tana tareda Mayan mata da maxa wanda basu dace da itaba.ya yi bakin ciki sosai amma ba yanda ya iya.haka kuma yasamu kaututtuka sosai daga mutane.dan Har wani company sunce suna San aiki dashi duk lokacin daya shirya. Bayan wasu yn kwanaki da gama karatunsa.yaune ranar da,sukayi da umminshi zai dawo gida,saide ta gaya masa,bata kasar.ya zauna gidan hajiya ladi kawar ta.... Muje zuwa!😜 Written by zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 50-55 AN DAWO LABARI! Ajikinshine yaji tabbas ana kallonsa,a hankali ya dago suka hada ido dashi,kasa dauke kanta tayi,taci gaba da kallan sa batasan lokaci da ta sakar masa murmushi ba,shima tsintar kansa yayi cikin yi mata murmushi. Zamansa ya gyara ya kirayi sunan ta! Bata amsa masaba illa cigaba da kallan sa da tayi. Amal yanxu babu inda yake miki ciwo,daga kanta tayi a hankali tace babu.toh Allah ya baki lfy,ameen tace tare da juya kanta dayan bangaran. Tabbas Annur yana da tausayi kuma mutumin kirkine. Abbntane yafado mata aranta,ko mezaice idan yadawo bata gida,kallace ta zubo mata,lallai tasan hjy.ladi zata iya bata mata suna a wajansa.Allah ka taimakeni,abunda ta furta kenan. Amal kuka keki,juyo da kanta tayi side din da yake.kallon fuskarta da yayi hawaye na bin kuncinta.hakanne yasa shi rashin jin dadi. Haba Amal kinsan baki da ki kakkiyar lfy amma kike sa damuwa a ranki,kinsan ko wani mutum yana da kandararsa.kuma mumine anasan a yanda da kandarar data sameshi mekyau ko marar kyau. Kiyi hakuri kidena damun kanki.kinji insha Allah bayan huya sai dadi. Taji dadi sosai da kalamansa.kuma tana dada godiya ga Allah daya barta da ranta. Yanxu kitashi kici abinci sannan kisha magani. Mikewa tayi ahankali, toilet ta shiga bata jimaba ta dawo ta zauna. Kallan ta yayi,kafin yace na hada miki tea kisha.kai ta gyada mai,da kanshe ya hada tea en,ya mika mata,sannan ya xubo mata ruwan semo miyna danyar kubewa Tasha kifi daman shanu.shima din mika mata yayi. Tea in tafara shanyewa gaba daya.sannan ta shiga cin tuwon ahankali Har ta cikinye gaba daya. Ita kanta tayi mamaki dan rabanta da cin abinci ta koshi harta manta. Shima mamakin yadda ta cinye yake.kawo a kara miki.Aa nakoshi,mikewa tayi taje toilet ta wanke hannuwanta.sannan ta dawo. Magani ya mika mata,anshi ki shanye sai kikuma jin dadin jikin naki.ba musu ta hadiye maganin tare da korawa da ruwa.mikamai ruwan tayi.ta juya zata kwanta. Aa kibari abincin ya gama bin jikinki,ni zantafi sai gobe da safe zan dawo.kina bukatar wani abunne.aa bana San komai nagode. Shikenan banasan godiynki Allah zaki godewa tunda shiya hadamu dake.tattara kayan yayi,sannan ya zaro waya daga cikin aljihunsa, gashi inkina bukatar wani abun ki kara num.in ciki ita kadaice aciki kinji. Toh kawai tace.saida safe yace tareda jamata kofar. Juyawa tayi tana mamakin irin kulawa ta wannan bawan Allah. Tabbas ya cancanci ko wata irin sakayya ta alkhari daga agereta.amma magana ta gaskiya baxata taba iya hada jini da hajiya bilki ba.koda kuwa Annur zai mutu itama zata mutu akan San juna.da wannan tunani aranta bacci ya dauke ta. Hajiya bilki da zuciyar ta kifaman tafasa burinta shine taganta a gida Nigeria. Abun bakin ciki shine tun daxo take kiran num.Annur amma gaba daya yaki dagawa.lallai tana da aiki a gabanta. Dandanan tayi Bucking din jirgin safe,gobe insha Allah 10:00am nasafe tana gida.da kr ta samu bcci ya dauke ta. Shima Abban Amal kasa baccin yayi burinshi Allah ya hadashi da wannan tsinannan yaran daya daukar masa yrsa. Wani hawayen bakin cikine suka zubomai.mudun aka lalata rayuwar yrsa saiya dau munmunan bataki.Abbunda yake ta gudu yau gashi ya faru.wannan wani irin bakin cikine,Allah ya tsinema hajiya ladi.gashi yarasa meyasa baya iya musu da ita,baze iya sakin taba. Shima haka ta kasance ga Annur din,dan kokadan wani Abu me suna bacci ya kaurace a idonsa.wallahi koda za'a kashe shi baze iya rayuwa babu Amal ba.lokaci daya Allah ya jarabceshi da Santa. Bandaki yatshi ya shiga,alwala ya dauro,ya shiga yin nafilla yana kaima Allah kukansa. 10:00am🕙 Shine lokacinda mum,Uthman da Annur suka iso asibiti dauke da kayan breakfast.room din da aka kwantar da Amal suka nufa.zaune take akan gado tayi wankanta tayi kyau kamar ba itaba harta danyi kumari.turo dakin sukayi da sallama. Cike da jin dadin ganinsu ta amsa musu.mumce ta zauna kusa da ita tana kallonta, kaga patient ae ta warware Allah kara sauki. Sunkuwar dakai tayi cikeda kunya,tana gaidada mum din. Lfylau jikin Amal? Da sauke,Allah kara sauke.sannan ta gaida Annur da Uthman suma duk cikin fara'a suka amsa. Abincin suka shiga zuba mata.sannan mum ta mika mata. Wainar masa ce,da miyan ganye tasha kayan cikin ragu sai kamshi take.ga kuma kunun gyada me kauri. Ahankali tashiga cin abincin, tana San kunun harta ci ta koshi. Kofar akayi knocking, sannan aka shigo,wannan likitanci mai kirki.bayan sun gaisa dasu mum.sannan taima Amal ya jiki. Duba Amal din tashiga yi,Alhmdullh jiki yayi kyau ta fada,zaku iya tafiyama yau,Allah kara sauki.ameen suka amsa.harxata fita tajuyo tace yawwa sunana Dr.Fatima Ibrahim labaran.amma anfi saninada Dr.shaheeda.hannu ta zira ta dauko musu card dinta a aljihunsa rigarta.gashinan full address in gidanane da kuma num.koda zaku nemeni nagode.tajuya ta fita. Sunji dadi sosai da karamcin da tayi musu.sosai matar tashiga ran Amal. Har tanajin dama su kasance tare.mum ce ta yimata mgn ta dawo daga tunanin da take.kitashi ki muje mu saukeki a gida.ba musu ta mike ta sanya hijab inta.kwaso kwanikan da duk abubuwanta akayi suka fito dan tafiya gida. Gaba daya tunda garin Allah ya waye Annur baya jin ddin jikinsa,dan yaune ranar da zai rabu da mafi soyuwa agareshi.tabbas koda yabi umarni umminshi, saiya dawo ga Amal insa. Zaune yake a daya daga cikin kujerun falon.dan yana tunani irin na sakacin da yayi nakin tafiya da Amal dinsa.maganganun hjy ladi yake tunuwa lokacin da ya nuna,zai tafi da Amal en China. (Haba Alh. Danni ban haifaba,kabarta mana agurina,tudda nima kamar uwa take agurina,zan kula da ita,kuma zatana debemin kewa) Wani bakin cikine yakuma ziyartar zuciyarsa.tabbas baxai kara barintaba.dama gata ba cikakkiyar lfy ba. A daidai kofar gidan sukayi parking da motar,da mum tace baxata shigaba tayi Latin zuwa wajan aiki amma insha Allah zatana zagayowa tana dubata. Ita da Annur aka sauke dan shima daga nan kano zai huce.sannan sukayi sallama da Uthman suka huce. Ahankali suka turo kofar dakin,Amal na gaba Annur na binta abaya dauke da kayanta,danshi nashima awajan me gadi ya anje dan ba dadewa zaiyi ba. Yana zaune a inda yake yaji sallamar Amal kamar a mafarki. Da hanxarinshi ya mike,tare da tahowa gunta.Annur ya gani tsaye abayanta,nan danan annurin fuskarsa ya kau.ya bata rai.Amal dake tsa dan murnar ganin Abban ta.tama kasa cewa komai. Cikin fishi ya cakuma wuyan rigarsa,wanda sanadin hakan kayan dake hannunsa suka zube a kasa. Kaine marar mutuncin daka daukarmin yata ko,wlh saika gayamin gidan ubanda ka kaita. Cikin murya me ban tausayi Annur yace,Abba dan Allah kayi hakuri wlh ban cutar maka da yrkaba gata nan ka tambayeta,ni bana nufinku da sharri da alkhari nake nuf... Tasss tasss! Nizaka maida mahaukaci,yayi maganar yana nuna kansa da hannun sa.wani alherine kake nufi da ita zaka rabata da gida harna tsawan kwana uku. Kuka sosai take,tareda durkusawa agaban Abban nata,Abba wlh da gaske yake ka tsaya ka saurareni. Nan danan ta kwashe duk abunda ya faro,tun daga lokacin data fara rashin lafiyar harkawo I yanxu.jikin Abbane yayi sanyi,amma saiyaki nunawa. Yakalli Annur dake tsaye kansa a kasa,zuciyar sa na masa kona.yaji Abba yace nawane kudin da kakashe.?. Dago da jajayan idanunsa yayi,da kyar ya yiya bude bekinsa yace Abba nidan Allah nayi.kuma ina Neman wata alfarma a gurin ka, ahankali ya karaso har gabansa ya durkusa kusa da Amal... Ita kuwa hajiya ladi tun lokacin shigwar su Amal tana labe tana jin meke faruwa.dan ita a tsorace take. Hajiya Bilki kuwa,tana sauka a garin kano.bucking takumayi,ta hau jirgin dazai kaita jigawa.cikin lokaci kadan ta Iso kai tsaye gidan hjy.ladi ta nufa.tana isowa taba wa mai taxi din kudinsa.ta banko gate din ta shige.dama hjy ladi ta sanar da ita Annur na gidan. Abba dan girman Allah ka taimaka min kabani auran Amal, nayi maka alkawarin rike ta tsakani da Allah har karshen rayuwata... Banko kofar dakin da akayine ya sanya su mikewa tsaye gaba day an su.ga mamakin Annur umminshi ya gani tsaye ba alamun wasa ko wani Abu fara'a atare da ita. Cikin karfin hali ya ambaci Sunan ta can kasan makoshinsa. Um....um.mi.! Kware rai kuwa nice,tunda ni ban isa da kaiba,to naxo da kaina na tafi dakai.banxa marar hankali. Abban Amal ne yakalleta,cikin fusata kekuma waya baki iznin shigo min gidana. Sannu me gida kaihar kana tunanin nan gidane.inbanda kandara me Dana zaiyi da wannna jakar yr taka. Kece jaka bilki! Kificemin a gida tunkafin nasa ayimin waje dake. Annur inde nonona kasha ka girma kaxo ka huce mu tafi.kuma da yahuna wlh baxaka auri Amal ba.saide in bana Raye. Haka zalika koda Amal zata mutu batayi aureba,baxata aure dankaba. Hjy.ladi dake tsaye najin bala'i.kasa cewa komai tayi.dan itama Neman hanyar rabuwa da Alh take. Ummina dan Allah kiyi hakuri wallahi bazan iya rayuwa in babu itaba. Wallahi zan tsine maka inde kabari narigaka fita. Zuciyar shi dake mai zafi da,kanshi dake bara zanar tsagewa. Dakyar ya iya daka kafarsa ya fice daga falon. Amal kuwa da ta dade da shigewa daki saboda kukan dayaci karfinta. Kaikuma Alh.Muktar,tanunashi da yatsa,wallahi nidakai gaba Har a lahira.kuma zakasan Wanda ka hulakanta. Dama in banda ke jahilace,yaushema zaki ganni a lahira.yrtace nace baxan badaba koma danki koda zai mutu akan Amal baxan aura masa itaba wallahi nagaya miki.kuma duk sanda na kuma ganinku a gidan nan saina illataku...... I dedicated dis page to u my lovly Aunty sa'a,ur d bested Aunty ever.I rwwly appreciate ur Lov nd care to me.Lov u to d moon nd bck.Allah raya miki yarnki ameen🙏🏻😘😍 Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) I dedicated dis page to my Aunty's Angeles, maryam,hameederh nd cwt Asy.may gud bless u,rwwly lovs u dearest😘🌸😘. 55-60 Ko kallan sa batayi ba.ta fice daga gidan tare da banko musu kofar. Lokacin data fito waje ko kadan bata ga Annur ba,bakin gate in tanufa. Can nesa ta hango sa,cikin Sauri gudu gudu ta isa gareshi. Annur kanka kalau.kana da hankali kuwa,kana gani nan fa,hanyar motoci na hucewa yanxu inda tsautsayi mota abige kafa Cikin murya kuka ya ja da baya tareda yarfe hannunsa. Na mutu mana,ni yanxu mutawata tafiyemun komai tunda kika rabani da Amal. Wlh Ummi gwara na mutu. Durkushe yayi awajan.tare da dafe kansa yana kuka. Tabbas tana kaunar danta.amma koda zata rabashi baxata taba barinshi ya auri Amal ba.ko wace mata yakeso adoran kasa zata aura mai ita amma banda Amal. Tashi mutafi kana batama kanka lokaci,koda mutuwa nayi Annur ban yarda ka auti Amal ba.in kaga dama ka mutu awajan,kuma wlh kabari Babar gurin nan batare da kaiba.toh kaje bani bakai. Cikin kuka,idanunsa sunyi jajir kamar huta. Ahankali ya kamo hannunta. Ummina nayi miki alkawari aduniyarnan bazan taba ketare umarnin kiba.amma dan Allah kidena fadin Kalmar rabuwa tsaka Nina dake. Taimaka masa tayi ya mike tsaya.tabbas Annur kacika dan halak.muje Allah yayi maka albarka.ameen ya furta tare dabin bayan ta. Shikuwa Alh. Saboda bakin ciki rasama abunyi yayi.kai tsaye dakinsa ya nufa.amma Sam ya kasa samun sukuni a zuciyar sa. Dakin amna ya shiga,kwance ya tanda ta saman gado,tana faman koka. Magana gaskiya yana kaunar yarsa aenun,amma yakasa share mata hawayenta. Amal! Yakira Sunanan ta,dagowa tayi da idanunta da suka rune sukayi jajir saboda tsabar kuka,dan furkar ta harta kumbura. Kema kinasan yaronne Amal shine kika zauna kina min kuka Amal. Ahankali kali ta karaso gabansa,jikinsa ta fada tareda fashewa da wani saban kukan. Abbana meyasa banida sa'a a rayuwata,tunda na taso bana samun kwanciyar hankali daidai da kwana daya.kullum cikin fargava da tsoro nake. Abbana shin ko wace yarinya haka take fuskanta a rayuwa, kokuwa danni bani da uwane.Abbana me yasa baka kaunata kaima. Sake matseta yayi ajikin sa,shima hawayen yake saboda tausashin tilon yar tasa. Abbana banasan Annur, nima bana kaunarsa kamar yadda baka sansa.Abbana banasan kara wata rayuwa me tsayi acikin gidan nan,kawai kamin aure koma da waye,kona samu kwanciyar hankali. Amal kiyi hakuri nayi miki alkawarin kasancewa dake Har abada.zan tafi dake,kije kisamu ilimi mai kyau da gata irin na kowace ya.kidena sa damuwa a ranki Abban ki na tare dake. Insha Allah karshan watannan zamu bar kasarnan dake kinji.kai kawai ta daka mai. Yauwa yr babanta.yanxu ki kwanta ki huta kinji,in anjima kiyi wanka ki shirya zamu fita kinji.toh tace mai.sannan suka bar dakin. Kai tsaye airport suka nufa danyi bucking din jirgin da zai kasu kano. Amma basu samuba dan sai 5:30pm zai tashi. Restaurant suka nufa dan yinwar da takeji.bayan sun zauna aka tambayesu abunda suke bukata. Shide Annur ruwa kawai yake bukata, ana kawo musu yadauki ruwan tunda ya kafa kanshi saida ya shanye tas.sannan ya anje. Itama kanta mamaki take.gaskiya Allah ya isa tsakaninta da Amal, ta mayar mata da jarimin danta zuwa karamin yaro. Annur bakajin yinwa ne.banaji kawai yace. Mikewa yayi tare da cewa ina zuwa.wani dan guri ya samu,yanayin gurin yayi masa kyau,ga iska mai ddi.dan kishiggidawa yayi tare da lumshe idanunsa. Tabbas yana axaftuwa da San Amal.dole yabi umminsa ahankali, inta yarda da shi.ya saiya dawo ya roki Abban Amal dan yaga mutunne mai sanyi.ya auramai Amal din yabar kasar da ita.murmushi yayi dan harya hangoshi tare da Amal dinsa da yaransu, Da wannan tunanin bacci ya dauke shi. Lokacin da hajiya bilki ta gama cin abincin ta, Neman Annur tashiga yi,can ta hangoshi yana faman baccinshi hankali kwance.taji mutukar ddi ganin yanda ya kwantar da hankalin sa Har yake bacci.Neman guri tayi kusa dashi.ta zauna.tana kallon sa,ta lura da yanda lokaci kadan ya fada.tausayinsa ne ya kuma rufe ta. Hjy ladi, hankalinta yayi mutukar tashi,dan gani take kamar hajiya bilki tayi fishi da ita,kartaje ta rasa Annur rabun ranta. Ahankali ta janyo wayar ta,gabanta na faduwa ta kira num.din hjy bilki, ringing daya biyu ta daga. Hmmmm! Jamila kenan wallahi kina bani mamaki,wai yanxu muktarne zai rabani dake,saboda ba amana.toh bara kiji,mundin kina San mukasance tare dolene ka dauki dukkan shawarar Dana baki.yanxu kare 5,zamu tashi, inasan kafin mutafi kano mu hadu dan inasan magana dake,duk yanda zakiyi ki fito,inkinxu airport ki kirani. Insha Allah yanxu zanxo bara na shirya. Katse wayar tayi. Kiran sallah aka farayi na azzahar da 12:30pm tayi.Annur ne yafara motsawa.mikewa yayi tareda hamdalah ga ubangiji, gaskiya bccinnan da yayi yaji zuciyar sa tayi sanyi.murmushi ya sakarma ummin nasa. Itama mayarme tayi da murmushin.sannan ya mike batare da yace mata komai ba ya mike da alama alwala zayi. Saida aka tada sallah sannan ya dawo dan zuwa yin sallah. Tana nan zaune kiran hjy ladi ya shigo wayarta.nan tayi mata kwatancan inda take. Bata dau wani lokaciba,ta risketa nan zaune. Karasowa tayi ta zauna tare da gaisawa.amsawa tayi ba yabo ba fallasa. Jamila! Nasan kin ddi kinasan nasan badan kinsan muktar kika aureshiba,kuma kina Neman hanyar da zaku rabu,ki samu dukiyarsa.tabbas yanxu dama ta samu. Wlh kika hi duk abunda zan gaya miki,nasan Annur kike so tona bakishi duniya da lahira mundin kika kawar min da muktar daga doran kasa shine bukatata kawai. Mikewa tsaye tayi,tare d kallon hjy bilki da mamaki.haba bilki kinsan duk,abuna da barikina ban taba kisan kaiba.kuma bamakya tuananin police su kamani. Hmmmm jamila kenan karki manta koni wacece.inkika kasheshe yrsa zamu kalawa,kinga shiya mutu,Amal na gidan yari,ga tarin dukiya,ga kuma angonki Annur. Wata irin dariya ta saki gaskiya bakida dama.tafawa sukayi suna dariya.... Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) I dedicated dis page to oll ma fans nd y lovs once. Especially my Preety queen nd my Bestie Ummie Jafar. Allah Ubangiji ya saka mukuda alkhair,takuma bar xumunci da lobayya.much Lov for u dearest🌸🌸😘😍. 60-65 Annur tunda yaje yayi sallah a masallaci,zama yayi be fitoba.Har saida akayi la'asar.sannan ya fito. Lokacin da ya fito wajan umminshi ya nufa,daya karaso be tarda hjy ladi awajan ba.dan haka zama yayi batare da yace mata komai ba. Annur yakamata muje muci abinci,dan inmun koma gida inada abinyi,inkuma zakaje restaurant kaci acandin to!. Shide be tanka mataba, Annur dakai nake magna fa! Ummi naji,nifa ba karamin yaro bane,in inajin yinwa zanje naci mana. Baki ta tabe batare da takuma kallon inda yakeba. Basu jima a gurin ba.ya mike tsaye tare da kallon agogon hannun sa. Yakamata mu huce da 5 din takusa.bai jira cewar taba yabar gurin. Itama kallon shi tayi,tare da yin Murmushi yaro kenan,abunda ta furta kenan tareda mikewa dabinshi. Kamar yanda aka sanar da sudin 5:30pm daidai jirginsu ya tashi zuwa garin kano. Doguwar abaya tasaka baka mai adon Golding din Stone a gaban huyan rigar da kasan hannuwan.light make up tayi,tare da rolling din dankwalin abayar.tayi kyau sosai, kamar ka saceta ka gudu.sak kama da larabawa tayi.jikinta ta feshe da turaruka masu kanshi,Wanda baxakiji kanshinba inba a kusa da ita kake ba. Fitowan ta daga dakin yayi daidai da sakkowan Abban ta daga stairs. Murmushi ya sakar mata. Tama shi tamayar masa.yaji dadin yadda ta saki ranta tayi kyau sosai.masha Allah ya fada tare da karaso wa wajan ta. Abba barka da hutawa.barka yar Abba. Taho mu huce ko. Ba musu tabi bayansa, Har zuwa bakin motar sa. Lokacinne me gadi ya budema hjy ladi gate,ko kallon inda take Alh. Beyiba,budema Amal gaban motar yayi.cikin jin dadin yanda Abban nata yake kula da ita,ta shiga ya kullo mata. Zagayawa yayi shima ya shiga side din driver. Suna tafiya suna hira,Har suka isa wani babban communication center. Ciki suka shiga cike dajin dadi.ya dubeta tana ta faman kallan wajan. Amal ina,ki zabi laptop, fone me kyau da kuma camera kinji yar Baba. Bakinta kin rufuwa yayi tsananin farin ciki.komai ta zabi mekyau,cike da farin cikin.tana ta faman yima Abban nata godiya,suka fito daga shagon.daga nan boutique suka nufa nan ma kaya masu kyau da tsada ya siyo mata,ta dauki takalma da cosmetic, komai intace tanaso baya hanata dauka.siyayya sosai yayi mata.harda kayan ciye ciye. Lokacin da suka shigo cikin harbar gidan ana kiran sallar magrib.yana yin parking kai tsaye masallaci ya nufa.ita kuma kayan tashiga dauka tana kaiwa daki Har tagama ga baki daya. Tun da motar su Amal tsaya,hjy ladi take lekensu ta window dakin ta,tana murmushin mugunta. Sannan ta koma ciki. Tana shiga daki toilet ta nufa ta dauro alwala,ta saka hijab dinta danyin sallah. Bayan ta idar tayi addu'o'in ta,kayan gaba daya ta dauka dan ta nunawa hanne. Dakin ta tura da sallama.sallah itama take amma bata idar ba,bakin gadan tasamu ta zauna dan jiranta. Batadau lokaciba tayi sallama. Kallonta tayi fuskarta da murmushi. Amal ya kayin sauki,da sauki dama kinga kayan da Abbana ya siyomin.Aa tubara kalla kaya sunyi kyau.sosai ta tayata murna,sannan ta bata abunda ta siya mata. Godiya tayi sosai dan taji dadi.sannan ta rakata suka kai kayan dakinta.fone enta da laptop danan ta Adana sauran kayan. Kaya ta canja zuwa marasa nauyi.kitchen ta nufa dan yima musu abincin dare. Lokacin da suka sauka anyi sallar magriba.dan haka kai tsaye suka mufi gidan su dake sharada. Suna sauka,Annur masallaci ya nufa danyin sallah. Ita kuwa hajiya gida tashiga.dakinta tanufa dan wanka kawai take bukatar yi,mutukar gajiya ta yi mata lilis. Kayanta ta anje,tashiga toilet ta sakanma kanta ruwa. Saida yayi sallar insha sannan ya shigo gidan. A falo yasameta azaune tana kallon TV,amma hankalinta ba akan kallon yakeba. Sallamar shike tamaidata daga tunanin da takeyi.dakinsa ya nufa dan yana mukatar yay wanka ya huta. Annur! ,tsayawa yay cak tareda rufe idanunsa. Dawo ka zauna nan inasan magana dakai. Badan yaso ba ya dawo ya zauna tareda kallan TV. Inasan kabani hankalinka nan,banasan kasaka damuwa akanka,saboda kwanannan zaka fara aiki.dan haka nemo nutsuwa agareka yaxama dole. Batare daya kalletaba ya amsa.insha Allah Ummi. Saida safe kawai yace sannan ya mike ya shige dakinsa. Toilet shima ya shiga saida yay wankan sannan yayi shirin bacci. Wayar shi ya dauko dan kiran Uthman, saida yayi trying din num.sau uku sannan aka daga. Ya ASA,har kakoma kanan kenan yanxu nake shirin kiranka ansauka lfy. Lfy qlau. Amma kasan akwai babbar matsala kuwa. Subhanallah! Mekuma ya faru? Nan ya kwashe duk abunda yafaru ya gaya mai.sosai ya tausayama abokin nasa.kuma zaitayi masa addu'ar Neman sa'a. Amma kasan menake so dakai kuwa.dan Allah gobe kaje gidan su Amal, kasamu wannan me gadin nasu,ka gayameshi kace Nina turoka,kanasan ganin Amal cikin sirri,inkasamu damar ganin ta saika kira ni pls bruh... Ba komai insha Allah, Allah kaimu goban.ka gaida Ummi.ohk nyt. Sanan ya kashe.idanunsa ya rufe tareda hurar da iska mai zafi.lallai akwai aiki agabansa. Jallof in taliya ta dafa musu tasha kifi da kayan lanbo.kan dinning ta anje tareda komawa kitchen din tayi dan gyara gurin data bata.bayan ta gama duk abunda zatayi.Abban ta ne yashigo falon tareda sallama. Amsawa tayi. Abba barka da dawowa.barka de yar Abba. Sannuda kokarin Allah yayimiki albarka . Ameen Abbana. Ga abin cinan nagama kazo kaci nasan kana jin yinwa.yauwa mamana.kamarko kinsan nayi missing din girkinki.dariya tayi tareda gyaramai kujerar da yake zama,zama tayi tareda jin dadin yanda take nunamai kulawa sosai. Zubamai tashiga yi suna dn taba hira. Yawwa haka ya isheni zauna kema ki zuba kici kinji.toh abbana zama tayi kusa da kujerar sa,tazuba.haba mamana saikace wata yar tsana. Maxa ki kara karnayi fishi dake.wlh Abba na koshi,kamanta kaika cikamin cikina da kayan ciye ciye. Dariya yayi toh naji,amma ki dunga cin abinci ko kyayi kumari.in sha Allah. Hajiya ladi kuwa tunda taga Alh.sunfita da Amal ranta yayi mugun baci.dan tasan kudi zai je ya kaso mata.haka nan de,ta huce cikin gida,tana babbamin bala'i.hanne takira dan ta gyara mata dakinta.sannan ta huce garden ko taji dadi a ranta. Tunanin plan din dazata hada dan cimma burinta,tabbas zata samu farin ciki na Har abada inde ta mallaki Annur... Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 65-70 Bayan Amal tagama cin abincin tare da Abban ta cike da farin ciki da nishadi sallama yayi mata yanufi dakinsa. Ita kuwa abincin hanne ta diba ta nufi dakin ta dan ta kaima ta. Kwance tasameta saman gado.tana ganin Amal ta shigo dauki da plate din abinci,mikewa tayi daga kishingidan da tayi,dama muguwar yinwa takeji. Hanne ga abinci kici. Ywwa Amal wlh kamar kinsan yinwar nakeji dan najima banci abinciba. Murmushi tayi,ai gashi saikici ki koshi ki kwanta.mika mata tayi,nantasa spoon ta hau ci,tanaci suna dan taba hira,Har ta kammala. Tare suka fito,Amal taimata saida safe ta nufi dakinta,ita kuma kitchen ta nufa dan maida kwano ta kuma sha ruwa. 8:00am Amal tagama hada musu breakfast ta gera komai a dinning. Daki tanufa dan yin wanka. Zaune yake saman gadansa dan har yayi wanka yana binciki cikin laptop dinsa.amma hankali sa,yana can kan tunanin Amal. Dan gaba daya,so yake yaji muryar ta. Wayar shi ya jawo dan kiran Uthman. Har tagama ringing ba'a dagaba.yasan shima kansa yanxu bacci Uthman yake be tashiba. Maida wayar yay ya ange,dan tabbas inya tashi yaga kiransa zai biyo kiran nasa. Tunda safe hajiya Bilki ta tashi ta hadamusu breakfast.ta gaji sosai dan rabanta da girki ta jima. Tana gamawa wanka tayi sannan ta dauki wayarta dan kiran wata mata ko zata samu yar aiki. Kira daya biyu,ta dauka. Sallama alaikoum hajiya antayi lafiya. Lafiya lau talatu,dama yarinya nakeso kinsan ina gari,zata rinka yimin girki da sauran aikin gida inzan samu. Eh! Zaki samu amma saide zuwa anjima insha Allah. OK! Tam ba damuwa Allah kaimu anjiman. Katsa wayar tayi,tanufi dakin Annur. Da sallama ta tura dakin.zaune ta gansa saman gado ga laptop agabansa ya dora waya saman cikinsa da earpiece a kunnan sa ya jingina a jikin pilo.da alama waka yakeji,idanunsa a rufe ko shigowarta bejiba. Karasowa tayi Har gabansa,sannan ta dafashi. Ahankali ya bude idanunsa yana kallon ummin tasa.zare earpiece din yake tare da mikewa zaune. INA kwana ummina. Katashi lfy son. Lfylau. Ywwa tashi muje kayi breakfast. Ba musu ya mike tareda tartare kayansa zuwa wani side in. Sannan ta mike yabi bayanta. Dinning din tanufa yana biye da ita.zama yayi yana jiranta.nan danan ta shiga zuba masa.chips ne da kwai ,sai farfesun ragon ruwa,da tea. Bayan ta gama zuba mai itama zubawa tayi.sannan ta zauna kujerar da take facing dinsa. Sosai ya shiga cin abincin saida yaci ya koshi duk tana faman kallonsa.sannan ya mike dan barin gurin. Bata tanka masaba,dakinsa ya nufa,be jimaba ya fito dauke da waya a hannunsa. Key din mota ya dauka,tare da hanyar fita daga falon. Sai kuma ina? Tafada batare da ta dubeshiba taci gaba dacin abincin ta. Juyowa yayi sannan yace zan shiga garine,be jira cewar taba ya fita daga dakin. Tanan zaune taji karan fitarshi da mota. Tana fitowa daga wanka,kayanta tasanya,atamfa tasaka Riga da skirt, me red da yellow, sunyi mata kyau sosai kamar ba Mara lfyba.gashinta ta gyara,sannan ta daura dan kwalinta.tayi kyau sosai ta feshe jikinta da turare. Tana fitowa daga falon.Abban ta tagani zaune yana amsa kira. Zama tayi akusa da kafafunsa,tana jiran yagama wayar.bata jima da zamaba yayi sallama da Wanda suke kiran. Mamana! Yakirata. Naam Abba ina kwana. Lafiya qlau kintashi lfy,ya krn saukin jikin. Hmmm! Abba aina warke sosai. Toh dama haka ake bukata. Abbana nagama hada breakfast kataso muje kayi.ywwa yr albarka sannuda kokari. Je ki kira mamanki,sai muyi breakfast din tare ko? Toh Abba tanike ta nufi upstair. Dakin hjy.ladi tanufa.knocking kintayi sau biyu,sannan aka bata iznin shigowa. Da sallama ta shiga tareda turkusa Har kasa tana gaidata.da mamakin ta tiji ta amsa cike da fara'arta.dago da kanta tayi dan tabbatarwa idanta,abunda kunnanta yajiye mata. Murmushi ta sakar mata.sunkuyar dakan takumayi tana mamaki. Amma!hjy dama angama hada breakfast shine nazo nagaya miki. Toh Amal gani nan zuwa. Ficewa tayi tareda janyo mata kofar. Aa to meyasami hjy.kode tamanta nice Amal din da bata kiran Sunanta,saide shegiya,mayya,munafuka etc.amma yau harda yimin murmushi. Da wannan tunanin ta karasa dining din. Zamatayi dan jiranta.Abba da ya lurada ita tun saukowarta,shine yay kokarin cewa mamana lfy ko cewa tayi baxata zoba. Murmushi dole ta nemo ,Aa gatanan abunda takuma cewa kenan. Yana kokarin sake mgn,hjy.ta karaso cikeda tfyrta ta yanga tana faman rangwada. Saida ta zauna sannan cikin kissa ta gaida Alh.ba yabo ba fallasa ya amsa.dan Har lokacin fishi yake da ita. Amal ce mike dan yin serving insu. Aa Amal banshi bara na yi,kede sanninki da kokari.daga Abban Har Amal in kawai kallon ta sukeyi.haka tayi served din kowa sannan itama ta zuba nata.sukahauci.kowa da abinda ke sakawa cikin ransa.hakade Har suka gama cin abinci.Abba ne yafara tashi dan yana da gurin zuwa.sai ka dawo sukace dashi.sannan hjy.dan itama tana da gurin zuwa. Amal de duk ta tsargu da abinda hjyn takeyi.kwanukan ta kwashe tayi kitchen dasu.tana kokarin fitowa suka gamu da hanne.bayan sun gaisane,take gaya mata inda abincin ta yake. Sannan tayi dakinta.fone dinta ta dauko tareda saka sim en da Abba ya bata. Bayan ta kunna ne,tana ta faman dubata,dan tayi mata kyau sosai. Yana gama shirinsa zai fita,ya dauko wayarsa ya kunna dan kiran Annur, missed call insa yagani,murmushi yayi tareda bin kiran nasa. Daga can bangarenne Annur yace,ina kashige inata faman ke ranka shiru. Wlh km kaima kasan ban mantaba Angon Amal yafada cike da xolaya.dariyar jin ddin sunanda Uthman ya kirayeshi dashi yake. Yauwa guy Ade taimaka. Ba damuwa yanxu mum ce ta aikeni amma ina dawowa zan je .ohk sai munyi waya.OK ba damuwa ya katse kiran. Shikuwa Annur can cikin gari ya nufa dan baya jin dadin zaman gidan. 4:45pm Uthman yayi parking din motarsa can nesa da gidan su Amal kadan.sannan ya fito ya nufi gidan kai tsaye. Tura kofar yayi tareda sallama. Gurin zama Baba me gadi ya basa.tareda amsa sallamar.bayan sun gaisane. Yake sheda masa sakon Annur, yakuma fito da kudi ya bashi dan duk ya ji ddin kira masa ita.dadi yaji sosai dan yana San Annur shima. Mikewa yayi yanufi cikin gidan. Sallama ya shiga yi,yayi sa'a kuwa Amal dince ta amsa,tareda fitowa,sanye take da hijab dinta. Aa Baba ne ina yini ya aiki.lfy lau. Sannan ya sanar mata da sakon Uthman. Cike da mamaki tace nikuma.tabbas fa.toh Baba kace gani nan zuwa. Cikin gidan ta koma tana sake sake aranta Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) 70-75 Lokacin data fito bata hanyar gate din ta nufa,ga mamakinta ba kowa sai baba me gadi. Aa Baba ina bakwan nawa tafa tana dube dube. Yawwa gashi can waje cikin mota,yace kisameshi can gudun kr Abban ki,ya gnku tsaye nan. Ba musu ta bude kofar gate din,tahau dube dube ta hanyar dazata hangoshi.can nesa da gidan su. Hanyar tabi hata cimma motar inda ta motar take.yana cike,ya bude kofar ya zuro kafarsa guda.yana jin waka. Cikin sallama ta isa wajan,da fara'arsa ya amsa mata.sannan ya mata ya jikin. Itama amsamai tayi.tare da tabayr mum. Mum na lafiya tace tana gaida ke kuma yaushe zaki kawo mata ziyara? Inde Abba ya barni insha Allah zanxo.toh Allah kawoki Amal yn mata.dariya ta danyi tari da boye furkarta cikin hijab. Ywwa inba damuwa ki shigo ki zauna dan inasan magana dake kuma be kamata ki tsaya hakaba ko. Ba musu ta zagaya ta shiga dayan side din.bayan ta shigone ta zauna.yake gaya mata cewan Annur ne ya aikoshi koma yace inkin samu damar fitowa a hadaku a waya,ba damuwa na kirashi. Itama kanta sai taji tanasan jin muryar Annur din.kai ta daga mishi. Nan take yakira shi,yana dauka yace,toh gani ga Amal de,cike da murna Annur yace ywwa bro bata mana mika mata wayar yayi tareda cewa bara nabaku waje.sannan ya fita. Tsawan lokaci bawanda yace da kowa komai.sainda shirun yayi yawa,sannan tayi karfin halin yin sallama. Lumshe idanun sa yayi sakamakon jin muryar ta da yayi,sai yaji kamar an wankemai duk wata damuwa dake cikin zuciyar shi. Shima amsa sallamar yayi. Amaaal! Yakira sunan sa da wata irin murya meban tausayi.nasan bakya sona ko Amal? Shiru tayi idanunta a rufe.nasani Amal ni kadai nake wahala akanki,amma dan Allah ki tausayamin kinji! Wallahi kin kasance wani bangare a jikin tun lokacin Dana fara jin muryarki. Har lokacin kasa bude idanunta tayi kamar akusa da ita yake maganar. Na kasance ina me fegenki dare da rana Amal! Inaji ajiki komin daran dadewa bazan iya dena tunaninkiba. Amal pls ki tausayamin zan iya rasa komai arayuwata in bana tare dake. Amal kice wani Abu dan Allah, kice kina sona ko zanji sanyi a raina. Tunda ya fara maganar ya katse mata komai,jikinta yayi mugun sanyi,gaba daya tausayinsa da kaunarsa ya tsarga mata zuciyarta. Amma tabbas tasan koda zata mutu Abba baze taba aura mata shiba,tasan halin Abban ta sarai.kanme zata yaudari zuciyarta ta amince da soyayyarsa karshe ta kamu da ciwon zuciya ta mutu. Amal dan Allah kiyi magana ko zanji sanyi a taina.wani irin kukane ya kwace mata.yarda wayar tayi tareda fita daga motar da gudu tayi hanyar gida. Uthman dake zaune saman wani dakali,ya mike yana kwalla mata kira,amma ina harta shige gida. Cikin sauri ya shiga motar,wayar ya gani yashe saman kujera.dauka yayi tareda karawa a kunan sa. Annur lfy? Annur da hawaye kibin kuncinsa ya kasa magana.haba Annur wallahi kana bani mamaki,sai kace ba namiji ka rinka dauriya mana. Uthman inasan Amal wallahi inji ajikina San Amal zai iya kasheni. Ya isa haka naji pls.sai munyi waya.kashe wayarsa yayi tareda shigewa motar sa yayi gida. Jingina yayi da kujerar motarsa,tabbas so wani babban al'amarine mu samma ga Wanda be taba yiba. Yanasan Amal amma besan yanda zaiyi ya shawo kan matsalr iyayensu.wata iska ya hurar me zafi,tabbas inde beyi da gaske ba,ba makawo zai kamu da ciwon zuciya. Wayar shice tayi kara,da kamar baze dauka ba,sai kuma ya dauka.umminshi ce.karawa yayi a kunne tare dayin sallama. Annur kana inane,? Ina cikin gari ummina lafy. Kadawo gida inasan ganinka.ohk gani nan kan hanya. Motar yyma key yanufi hanyar gida. Da gudu ta shige gidan,dakinta tanufa ta fada kan gado tareda fashewa da wani saban kukan.tabbas baxata yima zuciyarta karya ba tana son Annur. Amma ya hakan ya faru,taya tabari San Annur ya shiga zuciyarta.taya haka ya faru,wani saban kukan tashiga rerawa,saida tayi mai isarta sannan ta mike dan gabatar da sallah magrib. Yana shiga gate din gidan yayi park en motar.alwala yayi a nan,ya huce masallaci. Bayan ya dawo ne,ya shigo gidan da sallama baiga umminshi a falon ba,kai tsaye dakin ya nufa.da yashiga karar tuwa yaji a toilet, saiya jawo dakin ya dawo falo. Kan kujera ya zauna yana kallon film din da akeyi.amma azahiri ba kallon yakeba tunanin mafita yake yanda zai shawo kan matsalar iyayensu. Ya jima nan kafin ummin ta fito.nan kan kujera itama ta zauna tana kallo sa. Yanxu Annur tun safe kabar gidanan amma sainace kadwo sanan zaka dawo? Haba ummina kinsan ai bazan kwana a titiba,na Dade banyi yawa a garinnan ba shiya sanya na fita ganin gare kuma nadnje wajan frnds ina. Toh yayi! Dama company da nake nemama aeki sun dauke ka on Monday zaka fara aiki,saika zauna cikin kari.ya nuna murna sosai kuma yakuma kara godema Allah da Ummin tashi. Yanxu katashi kaje kaci abincin ka mana. Aa ummina a koshe nake.toh ai shikenan. Kallon suka cigaba dayi kuma suna dan taba hira jefi jefi.Har aka kira insha,ya mike dan tafiya masallaci. Bayan ta idar da salln magrib din kitchen ta nufa dan hada musu dinner. Amma kana ganin ta kamar maras lafiya.haka tayi musu girkin ta gama jikinta duk baya mata ddi. Ana kiran insha lokacin ta gama hada musu komai,bayan ta gama jerawa saman dining. Daki tanufa dan yin sallah.sannan tadan shingida kafin Abban ta yadawo...... Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) Bata jima da kwan ciyaba Abban ya dawo. Kai tsaye dakinsa ya huce dan watsa ruwa ajikinsa yaji sanyi.bayan ya gama duk abun da zaiye. Falon ya sauko amma ba kowa,wayar shi ya Ciro dan kiran ta. Tana nan kwance kan abun sallar da Har bancinta ya bara nauyi, Karan da wayar tata ke famanyi ne ya tasheta.ga mamaki ta dauko dantasn batasa num.din kowa cikin wayarsa.Abbana taga ansa.murmushi tayi tasan shine yasa num.din tasa yayi mata saving. Da sallama ta daga,tareda gaisheshi da yimai sannu da zuwa.Amal abbanki na falor yinwa zata zautashi a taimaka mai da abinci. Dariya tayi tare da cewa toh gani nan. Cikin murmushi ta fito daga dakin.zaune ta sameshi a daya daga cikin kujerun dinning din.Aa lallai Abba yinwa kk ji harka karaso nan din.shima dariyan yayi. Yinwa nakeji Amal a taimaka. Zuwa tayidanta zuba masa abinci sai bayan sunci sun koshi. Sannan ta mike ta tattara kwanikan. Ywwa Abbana tunda yanxu kaci ka koshi naje na dauko laptop dina kanan koyamin kayimin settings in wasu abubuwan. Toh jeki dauko yr Abba. Mikewa tayi tadauko laptop din kasa suka zauna yana ta faman gyara mata tana gani. Ga games kala kala.sosai taji dadi koba komai zasuna abe mata kewa. Nan suka zauna sunata hira da raha.yanata bata labarai kala kala.tana ta faman dariya. Hjy ladi ce ta iskesu zaune sunata faman dariya.nan ta nemi guri ta zauna tana kalansu,barkanku da hutawa.ywwa Abba yace da ita. Hjy ga abincinki can kan dinning.aww! Ku harkunci kenan Wlh nima bccine ya daukeni.bara naje naci,bade wanda yace da ita komai ta mike ta nufi dinning in. Nan suka cigaba da abunda sukeyi,sosai Amal ta gane duk abunda Abban ke koya mata cike da farinci... Annur ne kwance saman gadan sa,yana kokarin kiran Uthman din. Uthman dinne ya kirasa. Ya yanxu nima nake kokarin kiranka,ywwa ya kaje gida.lafiya qlau. Ywwa pls Uthman ya za'ai maganar Amal so nake ka kuma komawa wajanta.ka kaimata waya kaga kaima ba sai kana shan wahalar zuwaba kagane. Kaga Annur gaskiya ba inda zani,haka ake yarinya kawai ta tafi ta barni ko sallama babu koma ina kiranta ta yimin banza. Pls frnd karka min haka mana,kasan yanda nakesan yarinyar be kamata kana min irin wannan ba.pls ka taimaka.ni ummice matsalata amma da goben zan shig jigawan. Kaga nasan dama ta zautaka! Zani basai kaxoba kasan halin Ummi karka jama kanka wata matsalar.goban zan shiga insha Allah. Ywwa frnd na gode,ohk nyt ka gaida ummin.sannan sukayi sallama. Monday mrng 7:00am. Annur ne yafito cikin shirin dinsa na office yayi mutukar kyau.sanye yake cikin black suet, ta amsheshi sosai.rataye da briefcase dan hucewa gurin aiki. Dining ya nufa danyin breakfast.Har gama amma umminshi bata fitoba.yasan bacci take dan haka dakinta yanufa kai tsaye saida yayi knocking sai uku amma shiru ana hudunne aka bashi iznin shiga dakin. Zaune ya ganta saman gado ta shigida da pilo a bayanta,ta rufe rabin jikinta da blanket. Kusa da ita ya zauna,cikin sakin fuska ya gaidata.amsa mai tayi tareda fadin harka gama shiryawa sai tafiya,eh Ummi . Ywwa dan albarka kadeyi breakfast dinka ko, dan bansan kana tafiya da yinwa,shiyasa na samo mana kuku. Ohk! Nide zan huce saina dawo. Adawo lfy Allah badan sa'a. Ameen yace da ita tare da kullo mata kofar. Parking side ya nufa tare da shiga car din dazai fita da ita,key yayi mata nan me gadi ya bude masa gate.hancin motar ya tura waje bayan sun gaisa da me gadi. Office ya nufa cikin kwanciyar hankali.ahankali yake driving din yar ya isa enterprises din su.nan yay parking din motar sa inda aka tanada dan hakan.bayan ya fito tareda rufe motan ciki ya nufa inde naga an rubuta da manyan baki a saman building fin.AREWA ENTERPRISE NG.LTD. Nan yashiga da yake kansan da zuwansa nan mutane suka fara tarbarsa cikin kulawa da yake shine saban manager en su.shima cike da farin ciki da sakin fuska yake amsawa Har office dinsa suka rakashe sannan kowa ya watse. Bayan kamar minti biyar da faruwar hakan,sakatariyarsa ta shigo dan bashi duk wasu documents daya kamata ta bashi ta kuma sauran bayanan da zatayi masa. Da sallama tashigo office din bayan ta dauki permission din shugowar.zaune yake kan kujera yana duba wasu files daya tarar agurin.batare da ya kalletaba ya amsa mata sallamar da tayi. Gud mrng sir! Tafada cikin muryar yanga da yayi bala'in burgeta. Mrng yafada tareda nuna mata gurin zama. Zama tayi tareda cewa tnkuuu sir.my name is Fareeda Mahammad nice sakatariyar ka.nakawoma duk wasu documents da sauran files da yakamata na baka. OK tnkuuu fareeda nagode.sannan ta hau yimasa bayanan komai dalla dallah,harta gama sannan yayi mata godiya. Bayan ta fitane,ya janyo files din yahau dubawa. Aiki sosai yashiga yi yanda ya kamata. Har lokacin sallah yayi sannan ya fita dan yin sallah da cin abinci. Yau Abban Amal bai fitaba dan haka tun safiyar yau suna tare,saida lokacin sallah yayi sannan ya fita masallaci.itama dakin ta tafi danyin sallah. A masallacinne dayaje sallah suka hadu da wani saurayi shima anan yake aiki Har sukayi musayar num.da Annur din bayan kowa ya sanar da kowa sunan sa. Abokin nasa mai suna kabeer ne,yajashi Har zuwa wani restaurant nan kusa dasu sukaci suka koshi sunata faman hira Har suka gama.kabeer din ne yabiya kudin baki daya sannan suka fito. Lokacin da Abba ya dawo daga masallaci be tarda Amal a falon ba,dan haka key dinsa ya dauka dan yanasan fita cikin gari. Bayan ya fitane,bada jimawaba Amal din ta fito rike da fone dinta tanufi dakin hanne dan Sudan taba hira dan taji karan fitar Abbana. Hjy ladi ce ke saukowa daga kan steps cikin yanga harta gama saikowa,dakin Amal in ta shiga amma batanan kwala mata kira tashiga yi. Amal dake kwance kan gadon hanne tana nunawa hanne pics din da sukayi itada Abban ta sunyi kyau sosai ko wanne sunyi murmushi. Hanne ce ta dubi Amal. Anya kuwa ba kiranka akeba naji kamar ana kiranki ko bakijiba. Saurarawa itama tayi sannan sukaji muryar hjyn. Da Sauri ta fito Har tana kokarin faduwa dan Sauri.a tsakiyar bafo ta taradda da ita. Tsugunnawa tayi Har kasa ta gaidata kanta a kasa. Ywwa dan Allah yau mezaki dafama Abban naki.dago da kanta tayi tareda gyara hannun rigarta. Tuwan alkama da miyan danyan kubewa. OK! Pls macaroni Nikum nakeso ko hanne sai kisa ta tayaki dan Ku gama da huri banajin dadin jikina kinji. Ba komai Allah ya sauwake.nagode zaki zaki iya tafiya. Mikewa tayi tana taba baki ta nufi dakin hanne. Hmmmm! Yarinya ke nan Har wani wasa da dariya kuke yima mutane kida wannan banxan uban naki.toh yau zanga karahen iskanci.dariya takumayi tare da juyawa ta bi hanyar upstairs..... Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) 80-85 Dakin hanne ta tura ta shiga,bakin gadan ta koma ta zauna. Hanne nikuwa kin san wani abu,wlh gani nayi hjy duk ta canza anya ba wani abun bane kuwa. Lallai Amal kema saukace yau kuka fara rayuwa da hjyr.wata kila dan taga Abban ki gida shiya sanya take sassauta maki wani abun. Toh koma menene Allah ya kyauta.amma cewa tayimin wai batajin ddi,na girka mata abincin ta daban ba batare Dana gidaba. Toh! Sai kiyi matan saiki muyi tare na tayaki,nan suka cigaba da hira..... 5:50pm Shine lokacin da Uthman yay parking kofar gidan su Amal. Gaisawa sukayi da Me gadi sannan yakuma rokonsa daya kira masa Amal din. Babu matsala dan Alh. Ya kusan dawo wa. Babu matsala insha Allah, dan ba jimawa zanba sako kawai zan bata, Toh shikenan bara inkira maka ita. Be wani dau lokaci ba yadawo tareda ce masa gata nan zuwa. Komawa ciki yayi ya zauna. Ba dau lokaci ba tafito daga cikin gidan dan itama tabbas tana missing din Annur ba karya. Sallam tayi mai tareda gaida shi. Beyi mata maganar jiyaba dan sauri yake be dadi da tasowa daga office ba. Ywwa Annur ne yace akawo miki waya dan kuna gaisawa. Shiru tayi nadan lokaci ,sanan tace Abba ya saimin waya daya dawo,saide kabani number din shi danni ban rike tawaba. Ohk! Ba damuwa.pen ya dauko da memo karami ,nan ya saka mata numb.Annur din sannan ya mika mata. Nan tayi masa godiya tareda cewa ya gaida mata mum.bata gama gaya masa ba.motar Abba ta riske su. Rasa abin bafa tayi dan gaba daya ta tsorata.dan batayi tsammanin ganin sa a wannan Lokacin ba. Uthman ne ya gaidashi cike da fara'a ya amsa masa sannan ya ja motarsa yabar kofar gidan. Nan Amal itama ta shige gidan jikinta a sanyaye duk da taga yanayin furkar Abban nata ba ta nuna damuwar hakanba. Abanne ya shigo da motarsa cikin gidan sannan ya huce masallaci. 6:00pm. Shine time en da Annur ke tashi daga office. Kai tsaye gida ya nufa dan yayi mutukar gajiya. Badau lokaci ba ya iso gidan parking yayi dan Har anfara sallah. Haka ya daure ya nufi masallaci dan bayasan jam'i ya huce shi. Sai bayan idar da sallah ya cikin gida be tarda ummin sa a falon ba.dakin sa ya nufa da watsa ruwa. Yana shiga ya tube kayansa ya daura towel sannan ya shiga wankan. Be jimaba ya fito bayan ya gama shafe shafan da zaiyi. Ya sanya brown din wando 3quarter da White T.shirt.sannan ya fito falo dan cin abinci. Zaune yaganta tana jiransa dan suci abincin tare. Zama yayi kusa da ita tareda fadin Wash Allah! Ummina sannu da gida. Ywwa Annur ya office din. Alhmdullh amma na gaji sosai wlh. Sai hakuri ahankali zaka saba insha Allah karka samu damuwa kaji. Insha Allah Ummi. Mikomai abinci tayi yahau ci suna dan hira jefi jefi. Tana shiga dakinta ta zauna dan gabaki daya bataji dadin hakan daya faro ba.yanxu me Abba zai ce idan ya shigo.da wannan tunanin tashiga toilet danyin alwala. Sai bayan tayi sallah sannan ta tuna da numb.Annur. Mikewa tayi tashiga sakawa bayan tagamane tayi save da sunan sa dan batasan me zata rubutaba.tana kokarin kiransa taji Abba na kiranta. Cikin rawar jiki ta wurga fone din karshan gado.fitowa tayi sanye da hijab a jikinta. Abba sannu da zuwa. Ywwa yaki inasan magana dake. Zama yayi akan kujera yana facing dinsa. Itama zama tayi kusa da shi. Amal wanene wannan yaran da naganku tsaye dashi a waje. Am! Abba dama lokacin da na kwanta a asibiti shida mamansu suke kula dani Har abinci suke bani shine yaxo yakuma dubani. Shiru yayi nadan lokaci sannan yace da ita. Amma baki gayamin ba nayi musu godiya ba.itama shiru tayi kanta a kasa. Toh Allah saka musu da alkhari kinji. Ameen tace dashi. Lokacin ne hajiya ta sauko ta samesu a falon zaune. Barkanku da hutawa uba da yrshi.Alh. ne yayi murmushi tareda ce barknki de. Amal abincin yayi. Eh tace da ita. Ywwa bara naje nayi serving dinku. Aa Abba kadai za'a zuvama tun dazu mukaci namu. OK ba damuwa. Mikewa tayi da Sauri tayi hanyar danin din.ta bude macaroni dinta sai kamshi ke tashi. Miyar tuwon Alh.ta bude batare da kowa na ganiba ta barbada wata kawa guda daya sanan tasa hannun ta ta juwa.rufewa tayi sannan ta shiga kitchen din hannunta ta wanke tas ,sannan ta fito. Kallon inda suke zaune tayi sannan tace Alh.kataso mana kaci abincin. Saina dawo daga sallah insha yace da ita batare daya kalle taba yana duba mail a wayarsa. Komawa tayi tana murmushi ta zauna tareda cin abincin ta San ranta sannan ta mike.tayi dakinta cike da farin ciki. Amal data koma daki key tasan ya a kofar tata sanan ta koma saman gadonta takwanta tareda janyo wayarta,dan kiran Annur din. Shikuma lokacin da Uthman yabar gidan su Amal. Annur ya kira ya shaida masa da abunda ya faru tsakaninsa da Amal din dakuma Abban ta. Nan yaji dadi sosai kuma yayi masa godiya. Tunda Uthman ya sanar dashi cewa Amal zata kirasa. Yashiga daki dan jiran kiranta amma shiru.Har yaje yayi sallar insha ya dawo amma bata kira ba.hakan yasa shi cikin da muwa dan yana bukatar jin muryar ta. Tana kiran shi badau lokaciba ya daga. Yasan da Amal dinsace zata kirasa da sabuwar numb. Cikin muryar ta me sanyi tayi masa sallama kamar batasan yin magana. Nan yaji wata kasala ta saukar masa.lumshe idanun sa yayi tareda yima Allah godiya daya kayatar yakuma halicci abubuwa kyawawa masu sanya niwadi. Shima amsa mata sallamar yayi. Sanan shiru ya ratsa na waso yn lokuta. Amaaal! Yakira sunan ta da wata iriyar murya. Bata amsaba illar shirun da tayi masa. Amal naga alama so kike ki kasheni ko?. Aa tace dashi tareda jirjiza kanta kamar tana gabansa. Toh kashe wayar na kira ki kinji Amal ina. Kashe wayar tayi sanan ya kiranta. Amal kina jina? Eh tace dashi. Toh meyasa bakya sona,ko wani abun nayi wanda bashi dakyau?.wlh ki gayamin duk wani Abu maras kyau da kikasan inayinsa na miki alkawarin a darannan zan gyara dan Allah Amal. Ji tayi kamar tayi kuka dan tana mutukar tausayin Annur. Wallahi bakamin komai ba,kuma a iya zaman da nayi dakai ban taba ganin kayi wani Abu maras kyauba.kuma nayarda dakai💯. Yaji ddi sosai da irin kalamun da Amal din tayi. Naji ddi da kika yimin irin wannan shedar. Amma Amal meyasa baki sona dan Allah ki gayamin. Idanunta ta rumtse da shima besan irin San datake mai bane shiyasa yake gaya mata irin wannan maganar. Bance bana sanka bafani.kawai de baka tunanin halin da zamu shiga nan gaba.kasan su Abba baxasu yard...... Haba Amal ya katseta cikin Sauri.kinga inde kina sona shikenan ba abunda zasuyi mutukar Allah ne ya hadamu shikadaine zai iya rabamu.nide burina Amal ki furta Kalmar kina sona ko naji sanyi a raina. Kunya taji kamar tana gabansa.murmushi ta saki sannan tace wlh kunya nakeji. Shima murmushi yayi,nasan zakiji nauyin hakan tunda Kalmar ta kasance me tsada agareki musamman danasan yaune karo na farko dazaki fara furta ta gada namiji. Pls Amal ki gayamin mana pls kinji. Rufe idanunta tayi tare da furta: 💞💞 You are the one who I can open up to. I feel so comfortable in your presence. I love you my sweetheart. 💞💞 Tana gama fadar haka tayi maza ta kashe wayar gaba daya. Shikuwa Annur totally speechless. Dn beyi tsamanin haka daga gurin Amal dinba,besan lokacin da yayi wani ihun dadi ba.mutukar farinci ya bayyana aransa.dan duk wata gajiya da damuwa ya nemeta ya rasa. Numb.tata yakuma kira.amma yajita switch up.murmushi yayi dan yasan kunyace tasanya ta yin hakan. Mikewa yayi dan yin alwala yayi sallah rakh biyu dan nuna godiya da farin ciki wa Allah daya bashi Amal.. Ita kuwa tana gama fadar haka ta kashe wayar gaba daya tareda dorata a kirjinta.idanunta ta rufe San Annur na dda shiga cikin rainta. Mikewa tayi dan zuwa kitchen ta dan zubo abinci.dan bataci komai ba. Fitowa tayi cikin tsananin farin ciki.tana yo hanyar dinning. Ganin mutum kwance a kasa ya sanyata kurma ihu. Ihun da tayine ya jawo hankalin yn gidan gabaki daya sukayo waje. Ganin datayi kamar Abban tane ya sanyata kara sawa wajansa da gudu ta fada kansa tana kuka. WACECE AMAL ??. I dedicated dis Page to my lovely,cwt mum.Allah ubngiji ya karamiki lafiya da kwari yasa kigama da duniya lfy.ya cika miki burinki. Mama ur my angle un earth.ur my life first person,I may fail to express my self about her but she is my life forever.rwwly Lov u ma mum❣❣😍😍🌷. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) 85-90 WACECE AMAL.?? ASALI. Alh.muktar Sunusi dutse.shine ainahin sunan mahaifin Amal. Su uku iyayensu suka Haifa anan garin dutse. Hajiya Khadija itace babba,tana aure a sokoto amma tunda take Allah bai bata haihuwa.Har mujinta ya kuma south African da ita dan acan yake aiki. Sai mace ta biyu mai suna Sadiya ita kuma Allah yayi mata rasuwa tun tana karama.bayan ta rasune aka haifi muktar shine na uku tun daga nan ba'a kara haihuwa agidanba.Har Allah yayma iyayensu rasuwa. Sai hajiya Khadija ta dauki kaninta tun lokacin yana sokoto.ba laifi sun rike shi tsakani da Allah Har ya gama karatunsa na secondary. Bayan nan ne suka nema masa admission anan university of sokoto.nan ya karanci business administration. Sosai yana da kokari.Har Allah yasa ya kammala kara tunsa. Bayan nan ne yashiga yin business dinsa Allah ya buda masa. Wannan kenan dan gane da mahaifin Amal. Mahaifiyar Amal sunan ta Zainab. Ita kadai iyayanta suka haifa.mahaifin ta da mahaifiyar ta yn asalin fulanin sokoto ne.suna nan zaune a madaidaicin gidansu dan basu da wani arziki.sana arsu shine kiwo.iyayensu ko mata sayarda nono da manshanu ne sana'arsu.Zainab ta taso cikin gata da kulawa agurin iyayenta da kuma yan rugarsu. Dan tataso da kyau kuma tana da farin jini gurin mutane. Lokacin da Zainabu sunan da ake kiranta kenan ta dan tasa dan bazata huce shekara 15.suna fita daga cikin rugarsu,au fito cikin gari dan saida nono ita da kawayenta. Wata rana mahaifin ta sunfita birni dan saida shanunsu,da lokacin babbar sallah ta matso,.nan aka kawo gawarsa sunyi hatsari Allah yayi masa rasuwa.sosai mutanan kauyen sunji mutuwar sa,dan yana da mutukar kyauta da San mutane.bayan anyi arba'in itama mahaifiyar ta Allah ya amshi ranta.sosai Zainabu tayi kukan bakin ciki da rasuwar iyayenta amma haka ta rungume akdara. Nan rukwanta ya koma hannun baffanta wan babanta.tun daga nan rayuwa ta canxa.kullum cikin tsangwama da kyara,kuma sun rike mata gadanta da iyayenta suka bari.kullum cikin kuka take.batada lokacin kanta saina tallah.Har mutane tausayin ta suke yi. Wata rana tayi wankanta taci ado da kayansu na filani,ta dauki tallan nono ta,tare da kawayenta dan ranarce za'aci kasuwa agarin nasu. Nanne suka hadu da muktar shima yaje siyayya. Tunda ga wannan Lokacin suka saba dashi har soyayya ta shiga tsakaninsu.dan Har suna maganar aure. Hakanne yasa wata rana muktar binta rigarsu dan sanarwa baffanta. Bayan sunje yasami baffan nata harya yanda da bayanan sa.yana zuwa ya sanarda matarsa tace fir batasan zanceba wannan aure bazai taba yiwaba.hakan kuwa akayi.dan baffa ya Sanar da muktar ya hakura da Zainabu dan anyi mata miji. Lokacin da muktar ya sanar da yayarsa batin auransa da Zainabu itama ta yarda amma taso ace yasamu yar birni kuma me ilimi ya aura,Amma tunda itama yarinyar kirki ce Allah sanya alheri tace dashi. Nan itama ta sanarwa me gidanta. Shima cewa yayi ae be yarda ba.yariga yagama tsara komai nanda wata guda zai aurama muktar kanwarsa maryam. Nanfa zance ya rikice dan kuwa bazai taba yiwaba. Sosai muktar yaji ba ddi dan baxai taba auran wata maryam ba Zainabu yake so kuma itace matarsa. Nan Alh. Auwalu mijin yayarsa yace inde kuwa muktar bazai auri kanwarsa to dole yabarmai gidansa kuma ya maidomai aduk abunda yasan mallakinsane. Nanfa kan muktar yakuma daurewa,hankalinsa ya tashi. Nan yasamu Alh.auwalu ya shaida masa cewa zai auri maryam din da Zainabun shikenan. Alh.yace besan wannan ba dan baza a hada yr uwarsa da yr talakawaba. Nan muktar ya tattara duk abunda yasan na shine ya maidama Alh auwalu kayan sa.ya dauki sauran kudinsa Wanda zasu iya isarsa jari. Kai tsaye rigarsu Zainabu ya nufa.nan yasamu baffan Zainabun ya bashi dukiya me tarin yawa dan yace inya kawo zai aura mai ita,amma insun tafi karsu sake su dawo. Nankuwa aka daura musu aure muktar ya tafi da Amaryarsa Zainabu. Nan baffanta ya sanar da mutane ai Zainabu tabi dan birni sun gudu.nan aka rinka tsine mata ana Allah wadai.tun daga lokacin basu kara jin duriyar Zainabu ba.koda dangin mahaifiyar ta sukazo suma hakan aka sanar dasu.sunyi kuka sosai na rashin ta amma haka suka hakura. Kai tsaye jigawa ya nufa da ita.gida suka kama haya.sannan a hankali ya fara sana'arsa.Har Allah ya buda masa.ya sai gidan kasa. Sunanan cikin farin ciki da kaunar junan su. Har sukayi tsawan shekara 2 da aure.amma Allah bai basu haihuwa ba. Haknna ya fara daga mata hankali amma shike kwantar mata yacemata haihuwa ta Allah ce. Tunda suka basu danginsu basu kara waiwayarsuba.sunan cikin farin ciki dajin dadi. Saida sukayi shekara 3 da aure sannan Allah ya bama Zainabu juna biyu.murna gurin muktar basai anfadaba.yayi farin ciki sosai.Har macca yaje dan kara godiya ga Allah. Zainabu tana nan cikin kulawa dajin ddi.nan Alh ya sami wata bazawara take kula da ita tana kuma tayata aiki. Sunan wannan mata laraba. Laraba tanada mutunci da kuma amana nan ta rike Zainabu kamar yar uwa a gareta. Ranar wata alhamis ranar da muktar bazai taba mantawa da ita aduniyaba. Ranar ne Zainabu ta tashi da ciwon nakuda.tasha wahala sosai dan saida ta kwana biyu tana nakudu sanan Allah ya sauketa ranar alhamis din da daddare ta santalo yarta mace kyakkyauwa tana haifota tace ga garinku nan.dan muktar daya sami labari kusan binta yayi. Sai ranar juma'at da safe akayi jana izarta.mutuwar ta girgiza laraba sosai dan sun shaku sosai. Yarinya kuwa madara ake bata danma bata da rigima.koda yaushe tana bayan laraba. Ranar sadakar ukune yarinya taci sunan mahaifiyar muktar Fatimatus Zahra. Haka rayuwa taci gaba Har aka yi 40. Muktar ya roki laraba data zauna da Amal a gidansa Har Allah ya kawo mata miji tayi aure. Haka kuwa akayi Har Amal tayi shekara 2 .tataso cikin jin dadi da kulawa agurin laraba da Abban ta.komai idan ya gani na Amal dinsa komai ya samo Amal. Itace dan ginsa.itace komai nasa shiyasa ya dauki San duniya ya dora akanta. Haka muktar zaiyi tafiya zuwa abroad dan saro kaya yabar su Amal agida. Bayan shekara 5. Lokacin Amal nada shekara 7.tana primary 3.ta taso cikin wayo da kokari dakuma kyau ga surutu.kuma tanada shiga rai komai nata cikin nutsuwa take yinsa. Lokacin ne laraba tazo masa da batun aure zatayi tasamu miji. Sosai ya tayata murna amma yana tunanin yanda Amal zata dau al'amarin. Haka ya shirya mata kayanta lokacin yana gaf da komawa Dubai dan haka ya sallami laraba ya kuma yimata alheri me yawa.ya mata alkawarin inya samu lokaci zai dinga kawo mata Amal. Amal taso atafi da Auntynta amma yace mata zata biyosu daga baya murna taketa famanyi zata shiga jirgi.ta dawo tana bama frnds dinta labari. Bayan sunje can ya nema mata makarnta anan taci gaba da zuwa.lokacin da zai dawone ya barta gidan wani amininsa da matarsa dn basu da da ko daya.sunji ddi sosai barntana Amal da take da shiga rai haka kowa ya barta Har lokacin da zata gama primary. Sosai Amal taji ddin zama dasu,dan sun dauke ta tamkar iyayenta. Har lokacin da Abban ta yaxo tafiya da ita.nan suka rokeshi akan ya barta tayi secondary inta.hakan kuwa akayi amma da sharadin inya samu mata yayi aure zai dawo ya dauke ta.nan sukace sun yarda. Bayan shekara 3.lokacinne Amal tayi junior graduate dinsa.na aji uku har party aka hada mata. Lokacinne muktar ya hado da hjy ladi kuma Har sunyi aure.dan haka yaxo daukar Amal dinsa.danshi kansa ya bukatar ganin Amal dinsa. Uncle Hakeem da Aunty Humairah basu ji dadin rabuwa da Amal ba sunsha kuka haka suka hada mata sha Tara na azziki. Saida jirgin su ya tashi sanan suka dawo cike da kewar baby Amal. 🔸🔹🔸🔹 Lokacin da su Amal suka dawo daga Dubai. Lokacinne Amal ta shiga sabuwar rayuwa. Abban tane ya nema mata makarnta dan cigaba da karatunta. Farkon lokacin da Amal ta fara karatunta cikin jin dadi,kuma bata samun rashin kulawa a wajan hjy.ladi. Saide Abu daya ne yake kona mata rai wannan ba komai bane irin San da muktar yakema Amal.mai tace tanaso burinsa yayi mata shi.bashida lokacin kowa inba na Amal ba inde yana gida. Hakan yasa ta nemi kawarta hjy Bilki dan sanar da ita halin da take ciki.nan ta gaya mata tanan kan hanyar zuwa gidanta. Bata dau lokaciba ta iso.nan ta tarda Alh da Amal suna kokarin fita. Bayan sun gaisa cikin fara'a nanta dubi Amal tana dariya Amal yan mata unguwa za'a eh tace da ita tareda gaida ta amsawa tayi sanan ta shige cikin gidan. Dakin ladi ta nufa zaune ta ganta bakin gado.zama tayi kusada ita tareda dafata. Lfy kuwa jamila kinga yanda kika rame kuwa. Wlh Bilki kede bari. Gaba daya wannan yarinyar ta gama tusamin bakin ciki. Kwata -kwata Alh.baya kulani inde suna tareda ita.komai Amal wannan wani irin bala'i ne. Haba kawata ki kwantar da hankalin ki,sai kace ba ladin dana saniba.kar ki bani kunya mana.Har wannan yarinyar ce zaki tsaya kina damun kanki. Hanzu ki kwantar da hankalin ki,zan San abinyi insha Allah kibani kwana biyu.nandai suka taba hira sannan tabar gidan. Bayan ynkwanaki data dawo.a falon ta tarda hjy ladin.zama tayi suka gaisa sannan ta kalleta da murmushi. Andace mutuniyar.yanxu nanda kwana uku zanbar kasar ,saboda haka zan tafi da Amal a boye.kinga saina sata cikin harkar da nakeyi dama akwai mutanan dake sansa buwar dauka.kinga daman gata kamar su koma yarinya. Muktar dake tsaye yana jin duk abunda ke faruwa cikin bacin rai da fushi a fuskarsa. Nan yahausu da bala'i da fada.Har saida sukayi kaca kaca da hjy Bilki nan ya korata da kashe din yakuma ganin jamila da Bilki wlh zasu rabu Har abada. Tunda ga wannan rana hjy.Bilki da Alh.muktar suka bar shiri.hakan ya sanya hjy.ladi ta tsani Amal take taku ramata. Mundin Alh.muktar baya gida toh Amal bata da kwanciyar hankali.musamman idan baya kasar. Tana shan wahala ba karamaba. Hakan ya sanya ta fara tambayar Abban ta inda mamanta take,abunda bata taba tambayaba tunda take arayuwata.hakan yayi mugun daga masa hankali. Amma tambayar duniyarnan da yayi mata saitace kawai tana San ganin ta ne. Haka de yayita kwantar mata da hankali.dan bayanda zaiyi ya tafi da ita,saboda exams zasu fara,shiyasa ya dinga lallashin ta. Sannan ya kuma gargadin jamila kan ta kula masa da Amal. Haka ta nuna masa ba damuwa zata kula da ita. Tunda ga wannan lokaci Amal ke fuskantar wahala iri daban danan har suka gama exam dinsu. Amma kullum tana fuskantar bakin ciki. Ta dalilin hakanne ciwo ya kamata me kama da hawan jini.shine take ta fama dashi Har yayi mata babbar illah. WANAN SHINE LABARIN AMAL!💝 Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 90-95 AN DAWO LABARI. Kuka sosai Amal keyi yayin da Abban ta ke kwance a kasa daba asan wani hali yake cikiba. Wayyo Allah Ku taimaka Abba na ya mutu. Hjy ladi dake tsaye dan murna itama kukan take,amma na karya. Hanyar waje Amal ta nufa tana faman kuka.gurin Baba me gadi ta nufa ko dan kwali babu a kanta.gashin kanta ya zubu Har kafadar ta. Baba dan Allah ka taimaka. Lafiya me yake faru. Abbana ya mutu. Batasan lokacin data janyo hannun hannun me gadi ba zuwa cikin gidan.Har gaban Abban ta kaishi tana kuka. Dan Allah Baba ka taimaka min mu kaishi asibiti. Gaba daya ta rikice kamar mahaukaciya tayi nan tayi can. Me gadi da hanne sune suka kamawa Amal Abban ta har suka sakashi a mota. Da gudu ta dawo cikin gidan tana kuka ta nufi wajan hjy ladi dake zaune tana faman kuka. Dan Allah ki taso mutafi ki taimaka karya mutu. Cikin muryar kuka tace Amal wata mutuwa kuma bayan kina gani ko motsi bayayi. Me kuma kikesan muyi wani saban kukan ta kuma fashewa dashi. Toh kitaso mana muje asibitin mu duba kodai be mutu ba dan Allah ki tashi. Kuka take sosai ranta kamar zai fita saboda kuka.lokaci daya duk ta fita hayyacinta kamar ba itaba. Mikewa hajiyar tayi tana rufe fuska da hannu.alamun kuka.key ta dauko suka fita.da ker hanne ta sama Amal hijab dan gaba daya tana mutukar tausayin ta. Amal baya tashiga kusa da Abban ta ,tana gaman kukan. Hanne da hajiya sune a gaba. Kai tsaye asibitin suka nufa,Amma yanda kasan ma driving take ba. Amal ji take kamar ta kwace motar ta tuka dan bakin cikin irin tukin da takeyi. Cikin zafin nama tayo kukan kura ta shako huyan hajiya dake driving tana kukan munafurci. Cikin daga murya tace wlh Abbana ya mutu saina kasheni. Hajiya da taji shaka kasa tokin tayi neman gurin da zatayi parking tayi. Parking ta samu tayi tare da kwankwale hannun Amal da ker daga huyanta. Tari ta kamayi bayan ta kwaci kanta da ker. Bude motar tayi tareda fitowa waje.kana ganin ta kaga za rar riya. Kan titi ta nufa kanta tsaye batare da tunanin kar wata motar ta kade taba. Hannu ta rinka dagawa tana ihu ko wata motar zata tsaya.amma kusan minti goma ba wanda ya biyo hanyar da mota. Hakan ya sanya Amal da da rudewa. Da gudu tabi wata hanya tana tunanin ko zata ga mota amma shiru. Tsungun nawa tayi agurin ta kuma fashewa da wani saban kuka.sosai take koka kamar ranta zai fita.hakan ya sa kirjinta ya kama yimata wani irin mugun ciwo dan ji take kamar zata mutu. Hakan yasata fara ganin dishi dishi. Hanne ce tabiyo bayanta tana faman kiranta.can ta hangota rike da kirjinta tana tsaida wata mota data taho. Nan takuma yin gaba tana daga hannunta alamun motar ta tsaya. Ahankali motar tayi parking mutumin ciki ne ya fito.wani dattijo suka gani ya nufosu yana tambayar lfy. Gaba daya kasa magana tayi.kanshi tayi kamar zata fadi hanne ce ta rukota. Ta fadi kasa. Subhanallah mutumin ya fada tare da kara sowa kanasu.bayin Allah lafiya meya sameta.da ker ta iya cewa. Ruh...wa ruuu..wa zansha. Da sauri ya nufi motarsa ya bude ya dauko mata ruwan. Sannan ya bude ya mikawa Amal. Amal da idanunta suka fara lumshe suna budewa ahankali tana kallon su gasu nan de. Hanne ce tana hawaye tace Amal bude bakin ga ruwan kisha kinji. Ahankali ta bude mata bakin ta sa mata robar ruwan,saida ta shanye gaba daya.sannan ta sauke wata irin ajiyar zuciya. Idanunta na hawaye tace hanne Abbana Ku taimaka min kar Abbana ya tafi ya barni. Kiyi hakuri Amal Abban ki bazai mutuba kinji.kiyi hakuri tashi muje. Mutumin ta kalla tare da fashewa da kuka ta durkushe a gabansa tana rokwansa.dan Allah baba ka taimaka min Abbana ne zai mutu ka taimaka Baba. Aini banga kowaba anan yana ina Abban naki yake. Mikewa tayi tana mai nuni da hannunta gashi can muje. Toh kuyi gaba gani nan zan biyo bayanku bara na dauko motata. Da sauri yayi gurin motar tada.key yay mata dan shima yaran sun mutukar basa tausayi. Ga mamakinsu basu hango alamun motar awajan ba.da gudu Amal ta kuma falfalawa ixiwa gurin. Ihu ta kurma rashin ganin motar a wajan. Hanne ma data karaso hankali tashe itama ganin ba motar awajan. Rungume Amal din tayi suna kuka.hanne hjy ta kashe min Abbana, dan Allah me mukayi mata me muka tsare mata ta kareshe maganar tana kukan. Nima kaina kukan nake saboda tsananin tausayin su Amal din. Mutumin ne ya karaso da motarsa tare da fitowa yana tambayar su ina mahaifin nasu. Cikin kuka tajuyo dan bayyana mai abunda ya faru. Abban ta hango kwance tsallaken titi.da gudu ta karasa tana gashinan kuzo mu sakashi a motar mu kaishi asibitin. Da Sauri suma suka karasa wajan daukar shi sukayi suka sakashi acikin motar.suka nufi asibitin dashi. Basu wani dau lokaci ba suka isa wani babban asibiti. Nan suka fito dashi kai tsaye emergency suka nufa dashi.nan sukuma suka tsaya anan waje suna safa da marwa. Bayan kamar 30mins likitan ya fito daga dakin sanan yace da wannan dattijo ya biyoshi office. Sannan yayi gaba. Kallon Amal yake itama kallon shi take. Rugawa tayi tabi likitan sai hawaye take. Tare suka shiga office din,zama yayi kan kujera sannan itama ta zauna. Cike da mamaki ya kalleta dan ta bashi tausayi.yn mata bake nakiraba Baban ki nakira. Muryar ta na rawa ta ce ba babana bane maras lafiyan ne babana.bamu da alaka da wancan mutumin kawai taimakwanmu yayi ya rage mana hanya. Toh kina nufin duk wasu baya nai da yakamta ke za'ae wama. Girgixa kanta tashiga yi tareda furta eh. Menene sunan ki, Fatima muktar. Shikuma maras lfy fa, Muktar sunusi. Bayan yai rubutu sannan ya kalleta da kulawa. Yace Fatima mahaifinki yaci poison acikin abinci. Wani kukanne ya taho mata tayi saurin toshe bakinta. Tabbas yaci guba ,kuma tayi sana diyar lalatamai kaso 40 cikin hanjinshi.yanxu munyi masa allura nanda karfe 5:00am zamuyi masa theater. Sabo da haka zaku biya kudi 500,000k. Ya mika mata wata takarda gashi zaki sa hannu anan. Jikinta na rawa ta sanya hannu. Ki kwantar da hankalin ki insha Allah Abbnki zai samu sauki.ba kuka yake bukata daga garekiba yana bukatar addu'ar ki daneman sa'a abisa aikin daza ai masa. Cikin kuka ta furta insha Allah. Sannan yace zaki iya tafiya ki biya kudin. A jikinta gaba daya yayi sanya,ahankali ta fito daga dakin.hanne na ganin ta tayo gurinta da sauri.ita ta taimaka mata ta zauna. Bashewa tayi da kuka tare da rungume hanne. Amal kiyi hakuri me likitan yace. Cikin kuka tafara fadin hajiya ladice wlh.taya haka zata faru Nina dafawa Abbana abinci da hannuna ya akayi yaci goba taya hanne taya,tare da kara fashewa da kuka. Ita kuwa hajiya ladi tana ganin su Amal sunbar gurin ta fito da Alh.ta yadda shi anan wajan.tayi tafiyarta.gida ta koma ta koshe duk wani abunta.sanan ta dauki abunda take so.tahau mota tanufi kano kai tsaye.dan duk a tunanin ta Alh ya mutu.. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 95-100 Har kusan 1:15am Su Amal na nan zaune dan ko alamun bacci babu a idanunsu. Amal ce ta dago da kanta ta kalli hanne da idanuwanta sukayi jajir duk suka kumbura saboda kuka. Hanne ina mutumin nan daya taimakemu?. Cewa yayi dare yayi kuma iyalansa na jiransa fone din shi na gida bare ya kirasu.Amma yace insha Allah gobe zanzo da iyalansa. Hawaye ne yakuma zubo mata.Allah sarki.Allah ya biya shi ya saka masa da gidan aljanna. Ameen hanne tace. Wata nurse ce ta karaso wajan su.da Sauri Amal ta mike tsaye. Nurse din murmushi tayi tare da cewa ki kwantar da hankalinki insha Allahu mahaifin ki zai rayu kinje kidena yawan kuka bakya tunanin zai iya zamar miki matsala. Goge hawayen tayi tareda cewa insha Allah. Ywwa kokefa gashi fone din mahaifin kici a aljihunsa muka gani. Amsa tayi tareda yimata godiya. Allah kara sauki tace da ita sannan ta juya ta tafi. Wayar ta amsa ta kunna pic dinta ne tayi murmushi akan screen din wayar. Wani saban kukanne ya daga kwace mata.tabbas inde abbanta ya rasu bata da wani sauran jin dadi arayuwata. Haba Amal saikace ba musulmaba ki rinka irin wannan maganar kidau kandara mana.kidena irin wannan furuci dan Allah. Shiru tayi tareda nazarin Wanda zata kira ta sanarwa da abunda ya samu Abban nata. Dasauri ta shiga contact din wayar da neman numb.uncle Hakeem dake Dubai. Cikin sa'a kuwa ta samu. Kiranshi tashiga yi ba sassautawa.saida tayi mai kusan missed call 5 amma ba'a dagaba. Duk da haka bata hakura taci gaba da kiran nasa. Cikin sa'a kuwa aka dauka. Assalamu Alaikoum! Aka fada cikin muryar bacci. Kuka ta fashe dashi Wanda hakanne yayi sanadiyar sa Hakeem mikewa zaune daga kuncan da yake. Lfy Amal ce,menene ya faru meya samu Abban naki. Dakyar yasamu tayi shiru.cikin murya mai rawa tashiga yimasa bayanin abunda yafaru. Humairah ce tashiga tamfayar lafiya ganin mijin nata ya tashi cikin dare yana waya kuma hankalin sa atashe. Kinga Amal kiyi shiru kidena kuka.jeki hadani dashi Dr.din muyi magan pls tashi yi Sauri. Mikewa tayi tashiga neman Dr.din.amma wata nurse ta gaya mata yariga ya tafi gida saide abata numb.ninshi. Nandanan ta amsa jikinta na rawa ta turawa Hakeem din. Kiranta yayi ta shaida masa saide ya kira Dr.ga numb.dinshi nan yatafi gida. Nan yace mata bara ya kira Dr.din yaji yanda ta bakinsa.sannan ya kashe wayar. Dr.na shirin kwanciya ya gama duk abunda zaiyi yaji wayar shi na ringing. Da kamar bazai dagaba ganin sabuwar numb.ne yasa shi dagawa. Bayan sun gaisa dashi Dr. Din yayi masa bayanin shine uncle din yarinyar da takawo babanta yasha poison. Nan ya gane kuma yakuma yimasa duk bayani yanda zai gane. Hakeem ne yace da Dr.dole sai nan da 5 din za aeyi masa aikin.ko zai iya huce hakan. Dr.ne yace eh zai iya kaiwa 10:00am. Hakeem yace toh Dr.munasan hada mana takardu dan Allah munasan ayi masa aikin anan Dubai. Yanxu saina turo wani aje ayi musu bucking da wuri inde ba matsala. Yauwa gaskiya ka bada shawara mekyau yanxu ba matsala zan hada komai inyaje asibitin saiya nemu Dr.James zai bashi komai sai ya sameni a airport ayi musu bucking din. Ywwa Dr nagode sosai Allah saka da alheri. Cikin Lokacin dabe huce 30mins ba aka gama komai. Nan Hakeem ya umarci Amal da tafi wani dazai aiko ya kaita gida ta dauki duk abun zata dauka kuma ta kwaso duk wani Abu me amfani na Abban nata.nanda 2:30am jirgin su zai tashi. Nanta nufi bakin gate din itada hanne dan jiran Wanda zai dauke sun. Amma hanne hankalinta duk ya tashi dan zasu rabu da amal din. Suna nan tsaye saiga wani mutum ya karaso wajansu amota ya tambayesu ko sune su Amal eh suka cemasa tareda shiga motar. Kwantancan areas sukayimasa kai tsaye ya kaisu ya gaya mata da tayi Sauri nanda wasu yn lokaci zasu tafi airport zai huce da ita. Cikin gidan suka nufa.ta bawa hanne umarnin ta hado bata duk wani abunda tasan tana amfani dashi.ta kaisu cikin mota. Upstairs ta haura da gudu ta nufi dakin Abba. Karamin trolley ta jaho,duk inda tasan yana anje wasu mahimman takardunsa da ATM dinsa.laptop da duk mukullayen sa.sanna ta kulle dakin ta sauko.nan sukaci karo da hanne ta shigo daga kai kayan Amal motar. Yauwa hanne kinkai bara mutafi. Haba Amal ko kaya mana kibari ki canza da Allah kawo nakai kayan ki gyara jikinki. Mikamata mata kayan tayi tanufi dakinta da gudu,dan toilet ta nufa dan dauraye fuskarta. Sannan ta fito Riga da wando ta sanya.tayi rolling din Vail din kayan.fitowa tayi tareda janyo dakin. A can bakin gate ta tarda hanne.rungume juna sukayi suna kuka. Hanne yanxu ke kadai zaki zauna ko bakyjin tsoro. Aa amal zan tafi gidan wata yr uwarmu Dana sani.inyaso inkundawo sai nadawo.Amal Allah ya bada sa'a a wannan aiki da za'ae.ameen tace da ita tareda yin hanyar waje.Amal ga wayar taki.da Sauri ta dawo aa hanne ki rike zamuna waya dake.kuma dan Allah duk wanda ya tambayeki kice masa Abbana ya rasu kinji.ki kulle gidan inzaki tafi.hannu ta zura cikin jakar hannunta,gashi kibawa me gadi wannan shima ki gaya masa yace Abba yarasu duk Wanda ya tambayeshi.dan Allah hanne ga amanar komai nan ahanun Ku.zan dinga turo muku kudi kinji. Suna kuka suka rabu abun tausayi. Tanaji tana gani motar su Amal ta tashi zuwa airport. Ita kuwa hajiya ladi sai misalin 1:00am sannan ta isa kano.kai tsaye gidan su Annur ta nufa.dama sunyi waya da hajiya tana kan hanya. Tana karasowa Me gadi ya bude mata gate.hajiya dama da tasan da shigowa gidan nasu.ita ta tarbeta suka huce dakinta. Nan tafara gaya mata duk abunda ya faru. Haba jamila gaskiya kinyi wawta yanxu me kike tunanin mutane zasuce.mijinki ya mutu kina wani garin gaskiya zaki bata mana plan namu. Amma inde ya mutu ae shikenan kin cikamin burini.dani muktar yake zancan wlh.yanxu ki kwanta ki huta karkisa komai a ranki. Lokacin dasu Amal suka iso airport din 2:25am saura mintina kalilan jirgin su ya tashi.da Sauri aka fito da kayan nasu.dama anriga ankawo Abban tun dazu.nan sukayi sallama da likitocin da mutumin kowa yana mishi bata alheri. Daidai lokacin da aka sanya jirgi yatashi zuwa Dubai. Saida Amal taji jirgin ya tashi hankalinta ya kwanta,sassanyar anjiyar zuciya ta sauke tareda jingina kanta jikin kujerar.lumshe idanunta tayi tana tunawa da irin rayuwarta da sukayi da Abban ta.tabbas ambanta ya mutu zatayi babban rashi.tana wannan tunanin bacci barawo ya sace ta.. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) 100-105 Ba ita ta farkaba sai suka kusa sauka. Tana tashi ido suka hada da wata budurwa.murmushi tayi mata.itama mayar mata tayi.idanun Amal har yanxu a kumbure suke saboda kukan data sha. Gyara zamanta tayi. Wancan budurwar tace da ita kinsha bacci. Wlh kuwa,aiko danayi baccin harna ji ddin jikinna. Allah Sarki ko baki da lafiya ne? Aa wallahi lafiya ta qlau Abbana nede bashida lfyn. Ayyah Allah ya sauwake amma da alama kuka kikayi dan ga idanunki nan duk sun kumbura. Wallahi hankali nane ya tashi sosai.ameen na gode. Hannu ta mika mata suka gaisa. Ni sunana Sakina Abdulsalam.kuma ina zaune anan garin jigawa.ina karatune a Dubai amma nakusan gamawa.naxo bikin yayana ne. Allah Sarki. Nikuma sunana Fatima muktar. Amma ana kirana da Amal.nimade a jigawan nake.yanxu de abunda zai kaini Dubai Abba ne bashida lafiya shine za'a yimasa aiki. Allah ubngiji ya sauwake Amal. Insha Allah inde zan kawo miki ziyara. Toh na gode. Nande sukaci gaba da hira. Har lokacin saukarsu yayi. 6:00am Lokacinne jirgin nasu ya sauka anan Dubai.kai tsaye asibitin suka nufa dashi.anan suka tarda uncle Hakeem da Aunty Humairah. Da gudu tayi gurin su tana kuka.lallashinta suka shiga yi. Hakeem asibitin ya bisu. Itakuma Aunty Humairah kayan duk suka sanya a mota sannan suka nufi gida. Ana isa dashi asibitin dama Hakeem ya Riga yayi duk abunda yakamata yayi.nan da nan likitocin suka amshe shi,kai tsaye theatre sukayi dashi dan ceto ransa. Nan suka umarci Hakeem daya tafi tunda ya saka numb.dinsa in suka gama zasu neme shi.danshi ko jinya ba'ayi ko kwana saide kuxo kuga patient Ku tafi.komai daya kamata anayi yiwa mutun. Haka Hakeem ya nufo gida.badan yaso ba saide dan yabi dokar asibiti. Suna isa gidan.komai suka fito dashi. Dakin aka nuna mata.dan baxata taba mancewa da dakin da tayi rayuwa acikisaba.komai yananan.saide yn gyare gyaran daya sha. Trolley dinta ta anje tare dana Abba. Kayanta ta tube ta nufi toilet danyi wanka ko taji ddin jikinta.koda ta shiga zama tayi cikin ruwan dumi tana jin dadin hakan. Shikuwa Annur bayan ya idar da sallah daranshi.gadansa ya haye dan yana cikin farin ciki.bacci yasha harda munshari. Saida asbah tayi sanna ya tashi danyin sallah. Yana tashi wayar shi ya dauka dan tashin Amal tayi sallah. kiranta ya shigayi amma shiru ba'a dagaba. Saiya yi tunanin ko sallah take yi. Sai kawai yayi alwala ya nufi masallaci. Bayan ya dawo daga masallaci nanma yashiga kiran layin nata amma har lokacin bata dagaba. Damuwa ya fara shiga dan ji yake kamar ya tashi yayi tsuntsuwa yaje gurinnata ya ganta.yana nan zaune har 6am tayi. Mikewa yayi dan yin wanka yatafi office.. Ita kuwa hanne tunda ta koma cikin gidan kuka tayi sosai dan bakin cikin rabuwa dasu Amal,har saida tayi mai isarta.sannan ta mike tayo alwala tayi sallah dan taya Amal addu'ar Neman waraka wa Abban ta. Bayan ta idar tana nan zaune tana jan casbahha,bacci ya dauke ta. Dama ga hanne da nauyin bacci. Nan ta anje wayar kan gado tareda kudin. Har Lokacin da Annur yaketa kira amma hanne batajiba saboda baccin da takeyi. Haka bangaran su hjy ladi.tunda suka kwanta bacci basu farka ba,dama sallah ba damunsu tayi ba.bare ta asvah. Daki guda hajiya bilki ta bama ladi ta yi zaman ta aciki. Bayan Amal ta fito daga toilet din wanka tayi tare da dauro alwala dan gabatar da sallah ta ta asbah. Tana fitowa.zani ta daura tareda sanya hijab dinta. Saida ta idar da sallah sannan ta zauna tana ta mikawa Allah kukanta akan ya baima Abban ta lafiya. Tadau tsawan lokaci tana faman addu'a. Sannan ta mike.mai ta shafa.sannan ta gyara gashinta.doguwar Riga ta sanya me gyau ta English wears daga sama tadan kamata kadan milk color. Tayi mata kyau sosai duk da batayi wani Makeup ba harta dan fada kwana daya gal.murmushi tayi tana kallon kanta a mu dubi. Kayanta ta yi musu ma'ajya sannan tadan shigida kadan nan danan wani saban bancin yakuma dauke ta. Bata dau lokaci dayin bacci ba Aunty Humairah ta shigo dakin da sallama. Ganin ta kwance kan gado tana bacci ya bata tausayi. Karasowa tayi cikin dakin Har bakin gadon da take kwance. Gyara mata kwanciyar tayi, tare da ja mata blanket din Har wajan kirjinta. Tsayawa tayi tana karema fuskarta kallo. Tana mutukar kaunar Amal da kuma tausayinta.daga karshe fitowa tayi ta barta dan tana bukatar Hutu sosai. Fitowa tayi tare da jawo mata kofar dakin. Ganin Hakeem zaune kan kujera yayi tagumi yasanya ta kara sowa wajansa. Lafiya ya jikin nasa.tafada tare da zama kusa da shi. Yanxu de aiki za'ae masa,bamu da tacewa saide mu tayashi da addu'a dan ko motsi bayayi wallahi yanda kikasan gawa.nicewama nayi anya be mutuba. Haba kaima yazakace haka ae inya mutu baza su baka wahala da tun a can Nigeria za'a ce dasu ya mutun. Toh komade yayane Allah ne masani.Allah ubangiji ya tashi kafadunsa. Ameen tace. Yawwa ina Amal din take? Wallahi tayi bacci.bakaga yanda hankalin ta yayi mugun tashiba. Wallahi nima naga hakan,gwara da tasamu tayi baccin ko ta samu saukin jikin nata. Dan kwanaki ya fadamun itama ba cikakkiyar lafiya gareta ba. Allah de ya sauwake.. 7:00am Annur yabar gida zuwa office dan duk hankali sa yagama tashi kasan cewar Amal taki daukar wayarsa.hakan ya sanya ko abinci be Ciba ya fita.dan bayasan yayi latti. Yana tafiya yana kuma kiran nata amma Har yanxu shiru. Ahaka Har ya isa.kai tsaye office ya nufa,koda ya shiga kasa zama yayi yanata trying din numb.tata. Rigarsa ta sama ya cire tareda gayara tie dinsa. Yana cikin wannan Abu na tsawan lokaci sannan Fareeda ta shigo bayan sun gaisane ta bashi wasu files.sannan ta sanar masa yana da meeting 1 to 3:00pm.da wasu mutanan kasar Uganda. OK ba matsala yace da ita.sannan ya hakura da kiran nata ya tambata inde taga missed call dinsa zata kira shi.nan ya shiga aikin abansa. Karfe 10am,akayi sa'ar gamawa Alh muktar operation. Yanxu haka yana dakin da aka bashi. Yana nan kwance kan gado.ga na'urori nan kala kala acikin dakin. An sanya masa robar oxygen a hancinsa. Amma ko motsi bayayi kawai gashinan de kwance amma yana numfashi . Ita kuwa hanne sai bakwai saura ta barka. Sallati ta fara,mikewa tayi tanufi toilet tayi alwala ta dawo ta tada sallah. Bayan ta idar mikewa tayi tanufi kitchen da hada abunda zataci. Kayan wanke wanke tafa hadawa nan taga abincin da Abba yace yazama yellow shar.nan ta saka plate din da auran abinci takai shara.sanna ta wanke kwanikan tas ta gyrara kitchen din. Sannan ta hada abunda zata karya. Nan tashiga gyara gidan dan batasan ta barshi bata gyaraba. Tasha aiki sosai sai wajan 11 sannan ta gama. Toilet ta nufa danyin wanka saida ta gama shirinta tsaf.sannan tahau hada kayanta. Suma ta dibi daidai wa daida sannan ta dauki abunda zata bukata. Bayan ta gamane.tanufi kitchen ta kwashe duk wani abunda zai lalace kamar su nama,lemo etc. Tahadasu guri guda sanan ta kullo kitchen din.tabi ta kashe duk wani socket gudun gobara. Saida tayi sallar karfe daya sannan ta hado kayanta dan tafiya. Harta kai bakin kofa zata fita.saita hango wayar da Amal ta bata da Sauri ta karasa bakin gadon ta dauka tare da dannawa. Agogon wayar ne ya nuna 1:34. Lokacinne taga missed call din Annur guda 41. Ido ta zaro wannan yaushe ya kira,toh karde ace tana bacci.nan dannan tabi numb.amma shi ba'a dauka ba.saida ta kira kusan sau biyar amma no answer. Sanya wayar tayi cikin jakar hannunta sannan ta fice daga gidan. Bakin gate tagamu da mai gadi. Bayan sun gaisa nan tamai bayanin komai.kuma tace yacigaba da gardin sa zatana kawo mai kudi akan lokaci. Kudi ta mikamai tace ga wannan yana cin abinci dasu.nan ma godiya yay tayi sannan yayima Alh.addu'a. Itade hanne ameen kawai take cewa. Sannan tayi mai sallama ta tafi. 11:10am Shine daidai lokacin da Amal ta farka daga bacci.da sallati ta farka.sannan ta mike tare da gyara Vail din kanta. Falo ta fito ta nufi kan kujera ta zauna ganin ba kowa a ciki. Humairah ce tafito daga kicin.ganin Amal zaune kan kujera yasa ta karaso wajan tana murmushi,Amal kin tashi?. Eh Anty ina yini barka da gida. Lfylau Amal ya jikin Abban. Insha Allah Anty da sauki. Toh Allah yasa Amal. Yanxu kije ki wanke bakinki a breakfast nan kan dinning kije kici. Yanxu uncle dinki yamin waya,Har anjima Abban naki aikin kuma anyi sa'a yanxu inya dawo zamuje.yafita ba dadewa zaiyi ba kintashi kinji. Cike da farin ciki Amal tanufi daki dan yin brush taci abinci. Suma su hajiya ladin sai kusan 11 din suka tashi.ko wacce fitowa tayi cikin ado da takunta na kasaita. Bayan sun gaisa dining suka nufa danyin breakfast. Wato Annur yau kokaryawa baiba yafita office, zai dawo ya same ni. Auu! Har Annur ya fara aiki. Wlh ya fara aiki.kinga ko yaro ya girma sai kuma aure. Murmushi hjy ladi tayi danjin an ambaci aure. Tasan inta auri Annur ba karamin dacewa tayiba. Ita kuwa hajiya bilki murmushi mugunta tayi tana kallon ladi amatsayin jaka.danko karan haukane ya cijeta bazata aurama Annur hjy.ladi ba saide ya mutu ba aure. MUJE ZUWA😜😜 Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 110-115 Sunan zaune suna hira suna ta faman dariya kamar mahaukata. Ita kuwa Amal,bayan ta idar da sallah falon ta fito. Bata tarda kowa ba dan haka dinning din ta nufa dan cin abinci. Zama tayi tareda zuba dan kadan,kawai zataci abincinne badan tanajin yinwaba. Nan ta zauna tanaci tana tunane tunanan data saba. Har Humairah ta fito ta zauna kusa da ita amma bata saniba. Amal! Takirayi Sunanta tareda kamo hannunta. Kici abincin ki koshi dukda nasan ba wani cin abinci kikeba. Amma ya kamata ki dinga ci. Inkin gama uncle dinki na kiranki. Toh Anty bara nagama zanxo. Mikewa Humairah tayi takoma falon. Ita kuwa Amal dan danan tagama cin abincin dan gani take za'a yima ta wata magana ne Dan gane da Abban ta. Falon ta shiga tareda sallama sannan ta zauna kusa da kafafun Humairah akan carpet din dakin. Amal kinci abinci? Gyada mai kai tayi tareda cewa eh! Kanta a kasa tana wasa da yatsun hannunta. Yauwa magana nakesan yi dake. Kinga yanda jikin Abban ki yake. Kuma nasan ya Samar dake cewar,zai taho dake nan dan cigaban karatunki.munyi maganar nan dashi kafin koma warsa. Kuma anyi duk abunda yakamata. Kuma a Lokacin da aka dauka 15th of dis month zaki fara zuwa. Kuma yau kinga firsts. Dan haka komai zai tafi daidai yanda Abban ki yake so insha Allah. Gobe in Allah ya kaimu zamu kaiki ki siya duk kan abunda kk bukata na karatunki. Tunda ga kan kayan sawa,takalma,jaka,dade sauran su. Ki kwantar da hankalin ki. Ki nutsu kiyi karatunki kamar kina gaban Abban ki. Na tambata shima zaiyi alfari da hakan. Kina jina ?. Kai tagyada masa tareda fadin, Insha Allah uncle zan kasance me kula da duk abunda kafada kuma zanyi karatu kamar yanda Abbana yake bukata insha Allah nadau wannan alkawarin. Yauwa Amal,ko kefa Allah yayi miki albarka cewar Anty Humairah tare da shafa kan Amal din. Sun jima nan zaune suna hira.Har Amal ta fara jin bacci sannan tayi musu sallama ta nufi dakin ta. Nan suma suka ci gaba da yanda zasu kula da ita Har zuwa warkewar Abban nata. 10:00am Shine tymdin da Amal ta tashi daga bcci bayan ta koma daga sallar asbh da tayi. Tana farkawa dakinta ta gyara tsaf.sannan ta shiga toilet tayi wanka. Bayan tagama shirinta cikin bakin jeans da top White me photo babie doll pink a gaban rigar. Gashinta takama ta daure da bakin ribbon. Karamin bakin Vail ta daure kanta dashi gashinta ya zubo Har bayanta. Tana fitowa daga dakin.kai tsaye wani dan corridor ta nufa da zai sadata da dakin Anty Humairah dan bata ganta a falo ba,kuma bataji duriyarta a kitchen ba. Tana karasawa tayi knocking amma ba'a bata iznin shigaba. Hakan ya sanya tayi zatan ko tana toilet. Da sallama ta shiga. Jin karan ruwa a toilet ya tabbata mata da wanka take. Hakanne ya bata daman,gyaramata dakin duk da ba wani dirty yayiba dan Anty Humairah akwai tsafta. Har tagama amma bata fitoba. Fita tayi tanufi dining dan yinwa takeji. Zama tayi ta shiga cin abinci. Tunda bataga uncle ba tasan ya fita aiki. Cikin konciyar hankalin take cin abincin ta. Tanan zaune Anty Humairah ta fito.cikin shirinta na fita unguwa. Zama tayi kan kujera tareda sakamma Amal din murmushi. Itama murmushi tayi mata tareda fadin Anty ina kwana. Lfylau Amal. Dama tunda na fito naga angyaramin dakin nasan kin tashi. Kai Anty dakin daba wani dirty gareshiba. Eh! Kinga kuwa ai kin sa yakuma yimin kyau. Lallai Anty kema de,dan nadan gyara miki daki. Eh! Wallahi kam na gode. Dariya tayi sosai, ta kuma tuna irin uban aikin da take sha agidan. Kiyi maxa kigama zamuje asibitin daga nan kuma zamu huce masu. Tun dazu uncle dinki ya tafi shima office Toh Anty!tace da ita. Nan danan ta karasa cin abincin ta kwashe kwanikan. Daki tanufa ta dora black Cort ajikinta.tareda rolling black Vail.ta dauki jakarta karama baka. Sannan tasa takalminta mekyau plat me igiyoyi.tayi kyau sosai. Fitowa tayi tare da janyo kofar, Sannan suka fita. Yauma Annur banyi breakfast ba ya fita office. Dan gaba daya hankalin sa na kan Amal. Shi tunanin yanda zai tafi Dubai din yake.ga office ga kuma umminshi sune suka tukareshi. Yana zaune kan kujera a cikin office dinsa kanshi duk yadau caji. Kabeer ne yayi sallama tare da shigowa office din. Kara sowa yayi da murmushi a fuskarsa yana kallon abokin nasa. Zama yayi kan kujerar yana mamakin abokin nasa da ko amsamai sallmarsa beyiba saboda duniyar tunanin daya tafi. Table din gabansa ya buga yana kiran sunan sa. A firgice ya dawo daidai. Kabeer dake masa kallon tuhuma.yace Annur lafiyarka kuwa.kace baka da aure Amma meke damaunka Har kake irin wannan tunani haka. Dama kwana biyun nan ina lura dakai kana cikin damuwa sosai. Ammm! Kabeer kenan tabbas ina cikin damuwa Amma insha Allah zanci gaba dayin addu'a kamar yanda na saba. Ya ake ciki nifa yinwa nakeji danyau late na fito ko breakfast ban samu nayiba. Ohk! To Allah ya kauta. Mikewa yayi tareda fadin sauka taso muje kaci abincin. Shima mikewan yayi tareda daukar fone dinshi.sannan suka fito. Fareeda ya sama ya sanar da ita duk Wanda yaxo yajira shi. Sanan suka huce,zuwa cin abinci. Tana zuwa dinning din dancin abinci, Yauma still Annur baiyi breakfast ba ya fita.toh me yake nufi lallai yarannan ya rainani. Zai dawo ya sameni. Gurin hajiya ladi ta koma falo ta zauna.tana kallonta. Hajiya ladi ce ta gyara zama tare da kallan hjy.Bilki. Nifa Har yanxu naga shiru baki sanar dani matsayina agurinkiba. Kallan ta tayi da mamaki.haba jamila bakya ganin raina abace yake. Kuma duka duka kwana nawa da mutuwar mijin naki. Mikewa tayi tabar gurin dan ta bata mata rai. Murmushi tayi ta kuma gyara zamanta saman kujera. Ai gwara ki gayamin dan bansan Abun yadau lokaci. Tabbas saina auri Annur inkuma anki asiri ya tonu kowa ya huta.ta fada tareda mikewa tabar falon ita. Hajiya bilki data labe dan taji abbunta zata fada.ta tsaya tareda rike baki. Lallai ma yarinyar nan,ni zaki tunama asiri kice barin duniyar kike sha'awar yi. Suna fita daga gida asibitin suka nufa.parking din motar ta tayi sannan suka shiga. Already sunsan dakin.elevator suka hau dan suyi saurin shiga.dan dakin a third floor yake. Nan danan suka karasa. Dakin suka bude tareda shiga.yauma kwance yake yanda suka tardashi jiya. Saide an rage wasu na'urorin ba kamar jiyaba. Amal ce takuma matsawa kusada Glass din dayake ciki. Hawaye ne ya shiga bin kumatunta. Muryar ta na rawa tashiga fadin Allah ya baka lafiya Abbana. Addu'a tashiga yimasa. Sosai ta jima agurin.kafin ta juyo ga Anty Humairah. Mutafi Anty. Mikewa tayi tareda fadin yauma kukan kikayi ko. Da Sauri ta guge wata sabuwar kallon data fito mata. Insha Allah bazan karaba pls karki gayama uncle. Murmushi ta kuma sakar mata.tareda rungume ta.bazan gayamaiba kinji Amal. Hannunta taruko sannan suka fito daga asibitin... I dedicated did page to u all my fans.wallahi nima ina kaunar Ku kamar yanda kuke kaunata.Allah ubngiji ya barmu tare. I rwwly lovs u to d moon nd bck.😘😘🌹 Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 105-110 Suna cin abincin suna taba hira Har suka gama. Lokacin da Annur ya fito daga meeting.kai tsaye office dinshi ya nufa dan gaba daya hankalin sa yana gurin Amal dinsa.Allah Allah yake kar ta ga missed call dinshi kuma ta kira shi suna meeting. Yana shiga fone din tashi ya nufa dake anje kan sofa din office din. Salati ya saki ganin 5 missed call na Amal. Jikinshi Har rawa yakedan burinshi ya kirata.. Ita kuwa hanne tana isa can gidan da zata je. Bata sha wahalan gane gidan ba.amma ta dade bata jeba. Da sallamarta tashiga cikin gidan ba'a amsa mataba.hakan yasa ta zauna kan wani dan turmi a tsakar gidan. Batafi minti biyuba da zama wata dattijuwa ta fito daga bandaki hannunta rike da buta. Tsayawa tayi tana karema hanne kallo. Wanake gani haka kamar hanne. Hanne da murmushi a fuskarta ta durkasa kasa tareda fadin nice Gwaggo. Anya hanne ba batan hanya kikayi,shikenan haka zumunci yace daga Inno ta rasu sai kibar zumunci.wlh baki da kirki. Wallahi ina nan,nasameku lafiya. Lafiya muke ya kowada kuwa hanne lafiya wallahi. Toh bismillh shigo mana. Tayata daukar kayan tayi tareda shiga cikin dakin. Abakin gado suka zauna.kuma gaisawa sukayi sannan ta dauko mata abinci da ruwa. Bayan taci ta koshi.nan tashiga bawa Gwaggo labarin komai dan bazata boye mataba.kawar kakartace sosai. Dantane yasamu kudi shine ya maidota cikin gari. Sosai Gwaggo ta tausayama Amal da Abban ta.kuma ta cewa hanne ba komai ta zauna Har Lokacin da wowarsu.nan hanne ta dauko duk abunda ta taho da shi tabama Gwaggo, sosai tayi mata godiya. Tana zaune a dakin,ita kuma Gwaggo ta fita tsakar gida. Wayar ce tahau ringing da Sauri ta dauka ganin an rubuta Annur ta yi saurin daga.tare da sallama. Anjiyar zuciya ya anje jin an daga wayar. Haba Amal me kuma yayi zafi tun dazu ina faman kiranki baki daga ba. Kayi hakuri ba Amal din bace hanne ce. Ohk! Hanne ce.ina Amal din bata waya pls. Kayi hakuri Amal batanan sun tafi Dubai. Wani saban gumine ya keto masa.besan Lokacin daya zauna ba. Dubai kuma lafiya de ko. Abban tane ya rasu shine,yn uwansu suka tafi da ita. Innalillahi wa inna ilaihir raji'un. Yaushe hakan ya faru. Jiya da safe. Allah ubngiji ya jikansa.Amma insha Allah gobe da safe zan shigo jigawan. Aa bama saika zoba,dan basu yi zaman makokiba.gidanma an rufeshi.nima bana gidan nakoma gidan mu. Toh yanzu hanne dan Allah ya zansamu numb.din Amal ki taimaka min.gaskiya nima bata kirani ba tunda taje Amma inta kira saina baka. Toh nagode hanne sai anjima.bai jira me zataceba ya kashe wayar dan gaba daya kansa ya kwance.taya haka amma bara ya kira Uthman naji. Yana karinsa ya dauka. Bayan sun gaisa yake gaya masa Abban Amal ya rasu. Shima kansa yaji mutuwar. Yaushe ya tambaya. Wallahi yanxunnan yar aikin nan tasu take gayamin. Pls kaje gidan nasu kadubamin dan Allah. Ohk ba dumuwa insha Allah. Sannan sukayi sallama. Tana gama breakfast dinta suka dawo falon suka zauna itada Anty Humairah. Dan ita burinta uncle Hakeem ya dawo taje taga Abbanta. Sunanan zaune sukaji karan bell en kofa. Da Sauri Amal ta mike dan bude kofar. Tana budewa ya Sakar mata murmushi. Kunya tadanji sannan ta gaida shi. Yar gidan Abba har an tashi daga bacci. Eh.to ai yanzu zamuje adubo shi.maxa kije ki shirya. Uncle aina shirya kai muke jira. Toh ina Humairah. Itama fitowa tayi tareda cewa gani nan nima sai mu huce. Yanda tayi maganar da barkwanci. Hakan yasa dukansu sauka sanya dariya. Duk suna yin hakanne dan Amal ta samu kwanciyar hankali. Dukansu suka dunguma cikin motar uncle din suka tafi asibitin. Basu lokaci ba suka iso asibitin sunata barkwanci a motar. Parking uncle yayi da motar sannan suka fito dukkansu. Cikin asibitin suka shiga,kai tsaye bangaran marassa lafiya suka nufa. Fone dinshi ya dauko dan duba numb room din da yake. Basu dau lokaci ba suka samu dakin. Ciki suka shiga.Amma ba'a bari a karasa inda yake saide su hangoshi ta cikin wani glass da aka sakashi,likitocin ne kawai ke shiga. Amal na ganin Abban a cikin wannan hali ta fada jikin Humairah tana kuka.itama hawayen take saboda tsabar tausayin ta. Dakar suka lallasheta. Suma suna hawayen. Dan duk Wanda ya gansa sai yayi tunanin bazai kara tashiba dan ko zai tashi za'a dau lokaci. Sunanan zaune har 4pm tayi.lokacinne suka lokacin tafiyar visitors. Dama 1 to 4:pm ake rufe ziyara. Amal ji take kamar abanta tareda Abban ta ko bataje wajan shi ta dunga hangoshi. Haka suka tafi jikin kowa a sanyaye suka koma gida. Lokacin da Uthman ya karaso gidan su Amal. Me gadi ya samu zaune yana alwala yin sallah la'asr. Bayan sun gaisa yake tambayar sa Ashe me gidan Allah yayimai rasu. Shide me gadi eh yace dashi dan haka aka umarceshi yace. Amma saiyace da Uthman ba'anan suke zaman makokinba. Nande shima Uthman yayi sallah sannan ya tafi. Ahanyar komawarshi office ya kira Annur ya sanar masa hakanne Amma ba'a nan ake zaman makokin ba.sannan sukayi sallama. Annur dake zaune kan kujera cike da tunani kala kala.to Amma ya akayi haka. Koda yake ba zaman makoki tunda hanne tace Amal din na Dubai. Gashin kansa ya hargitsa tareda shingidawa jikin kujerar yana nazarin abinyi. Tunda suka dawo gida Amal ta shiga daki tana faman kuka,dan gani take kamar Abban ta baxai kuma tashiba.sosai hankalinta ya tashi. Humairah ce ta turo kofar dakin da sallmarta.zama tayi kusa da Amal din tana kallon ta. Rungumota tayi jikinta tana lallashinta. Haba Amal sai kace bakya kaunar Abban naki.ko kukankine zai saya warke.Amal addu'a yake bukata.kina mishi addu'a koda yaushe zai warke.zai tashi kamar da.zai cigaba da rayuwa dake kamar yanda kke bukata. Ko gaya masa akayi bakya sakin jikinki kina walwala Wallahi bazaiji dadi ba. Yanxu kitashi kiyi sallah la'asr na tambata bakyiba.dan tunda muka dawo kike Kuka. Oya maza kije kiyi ki fito kici abincinki. Ana tashi daga aiki.Annur gida ya nufo dan yana bukatar hutu.yana shigowa parking din motarshi yayi.sallah ya farayi kamar yanda ya saba kamin yashiga gida. Da sallama ya tura kofar dakin. Mutuwar tsaye yayi ganin hjy.ladi xaune suna hira da umminshi. Annur sannu da zuwa harka dawo.Ummi ta fada dauke da murmushi a fuskarta. Bai kula taba.ya huce dakinsa. Yana shiga yayima door din key.dan baya San damuwa. Tabbas kenan Abban Amal ya rasu.toh Amma ita da aka yima mutuwa akanme zata dawo gidan mutane ta zauna. Shifa harga Allah baya kaunar Matan nan Har cikin xuciyarsa. Saman gadanshi ya haye yana tunanin barkatai. Da ker yamike ya shiga toilet dan watsa ruwa ajikinsa ko yaji sanyi. Bai jimaba ya fito tareda alwalansa. Jallabiya yasaka sannan ya fito dan tafiya masallaci. Inda ya barsu da zai shigo anan yakuma taddasu. Bai kula suba yanufi hanyar fita daga falon. Annur umminshi ta kirashi. Bai jiyoba yace da ita an kusa tada sallah. Be jira mezataceba ya fice daga falon. Hajiya ladi dake zaune ta kalli Bilki tareda kama baki. Kina nufin kema Annur haka yake miki. Uhhhm! Kede bari haka yake wlh.wannan shegen halin nasa yana kona min rai bansan ranar dazai denaba. Allah ya kyauta de. Abunda yakuma bata masa rai shine,yanxunma suna nan.kenan basuyi sallah ba. Dakinsa ya nufa dan baya San ganin fuskar hjy.ladi. Cikin fusata hjy.ladi ta mike tareda dakama Annur tsawa. Annur dakata,banasan iskanci,ya za ae kamaidani kamar kanwarka.ina ma magana kana wani tafiya. Dama kasan da tamu dakai kafice a gidan nan bakayi breakfast ba kuma yanxu kadawo shima na daran me kake nufi. Ummi nif..... Anan zaka yimin magan.kadawo nan ka zauna mana. Hajiya ladi itade kallon Annur kawai take.ji take kamar ta hadiye shi. Ba asan ranshi ya dawo ya zauna kan kujera yana kallon TV. Ina jinka tace tareda zama. Na koshi,banacin abincin a koshe nake. Kaji mahaifin Amal ya rasu. Toh Allah ya jikansa! Kawai ya mike ya nufi dakinsa. Kallon juna sukayi tareda kwashewa da dariya. Kinga yaro ya ganu gaskiya ya rabu da ita.wallahi ko ajikinsa. Shikuwa Annur saboda hajiya ladi yayi haka.dan kardu kuma ta kuma Amal dinsa. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 115-120 Suna fita daga asibitin, kasuwa suka nufa. Nan suka hau yawa daga wannan shago zuwa sannan. Siyayya sosai sukayima Amal din. Harda waya suka saimata sabuwa,kaya kuwa ba'a magana. Dan ita kanta tayi mamakin irin wannan siyayya da sukayi mata. Sai kace bada kudi sukeyintaba. Haka aka jigo musu kaya cikin mota. Sai kusan 2pm.sukabar lasuwa. Gidan wata kawar Anty Humairah suka nufa. Ta tarfesu da fara'a gata ga barkwanci. Sunan ta Asma'u.sosai itama taji Amal ta shiga ranta.saida sukayi sallah suka ci abinci. Sannan sukayi mata sallama dan salon suke san zuwa.Har waje ta rakosu.tabama Amal turarurruka masu tsada da kamshi.sannan suka tafi. Salon suka nufa,nan aka wanke musu Kansu aka gyara musu. Danma basu jima anan ba,sannan suka nufi gida.dan 5pm ta kusa. Tunda Annur ya dawo daga sallah azhr.yake kiran numb.Amal ko ince hanne, Amma bata dagaba.dan harya fara jin haushinta. Sai yanxu daya dawo daga sallar la'asr sannan ta daga. Bayan sun gaisa yace da ita ke menene amfanin rike wayarki. Tun dazo ana kira Amma baki dagaba lafiya de ko. Lafiya kalau tace dashi. Tareda fadin Wallahi ita ba wanda yake kiranta shiyasa take anjeta kawai.sai yanxu taga kiran nasa. Dama ba wani Abu bane tambayar ki zanyi ko Amal ta kiraki. Wallahi nima Har yanxu shiru. Toh pls karfa ki manta tana kiranki ki turomin kinji. Toh tace dashi insha Allah zan turo maka. Sannan sukayi sallama. Ana tashi daga office gida ya nufo.bayan yayi sallar magrib. Ya shigo da sallama. Yanxu ba kowa cikin falon hakan yai masa ddi sosai. Dakin shi ya nufa yayi wanka. Laptop dinsa ya dauko dan tura mail. Umminshi ce tashigo dakinsa da sallama. Amsa mata sallamar yayi.tareda nuna mata gurin zama.zama tayi tana kallon sa. Yauma daka anjemin breakfast ni kakesan in ciye kenan. Ummi pls ba haka nake nufiba wlh. Yau na fita late ne shiya.ku ma yanxu inna dawo daga sallah zan zo naci nawa. Toh naji yanxu, Dama magana nakeso muyi dakai. Laptop din tashi ya ture gefe daya,tareda maida hankalinsa kanta.ina jinkii Ummi. Yawwa! Kaga yanda nadau dawainiyarka tunda kana karamin kawo eyanzu.kayi karatu kuma yanxu gashi kana aikinka,yanxu aurene kawai ya zagema. Da Sauri ya dago kansa yana kallonta. Kai ta daga mai alamun hakan take nufi. Tabbas aure nakesan kayi Annur. Kasamo mata ayi maka aure. Nabaka nan da wata daya. Inkuma baka kawo ba nixan nema maka da kaina. Cikin wata iriyar murya daya shiga cikin tashin hankali ya dubeta. Haba ummina kinsan de yanxu neman mata azamanin na da kakeso akwai huya.kumani inasan auran macemai nutsuwa da hankali. Kowa ni da fatansa kenan, kuma ai ba duka aka zama dayaba.sabo da haka Nide na gayama,kuma ba sha wararka nake nemaba umarni nake baka inhar na isa dakai. Bata jira mai zaiceba ta fice daga dakin tareda kullo masa kofar. Kanshi ya dafe da yake bara zanar tsagewa. Wannan wani irin bala'i ne. Ya zai iya solving din matsalar dake tsakanin umminshi da dangin Amal.acikin wata daya. Ga aikinsa yauashema yake da lokacin yin hakan.koda yaushe yana busy. Inna lillahi waa inna ihaihir raji unn.! Yaketa furtawa. Ahankali ya farajin sauki acikin zuciyar shi. Yanji anata faman kiran sallah Amma bazai iya zuwaba. Tabbas so babbar cutace,yanxu menene mafita. Da ker yamike yashiga toilet. Alwala ya dauro.abun sallah ya shinfida,dan bayajin zai iya fita masallaci. A daddafe yayi sallah, dan wani irin Ciwan kai dayake ji.yan idarwa ko sallayr bai dauke ba ya haye gadon ya kwanta tareda lumshe ida nunsa. Suna shiga gidan suka hau shiga da kayan har suka gama. Wanka duk sukayi. Tare suka shiga kitchen danyin girki, Sunayi suna hira kamar ya da kanwa. Har suka gama. Ana kiran magriba, uncle ya shigo gidan. Dakin shi ya huce shima. Saida sukayi sallah sannan suka fito falon. Amal ce ta fara fito. Sai Anty Humairah. Can kuma saiga uncle din yafito. Nan suka yimai sannu da zuwa.sannan shima ya musu ya gajiyan kasuwa. Hira sukahau na kasuwan suna dariya. Sunan Har akai insha'i. Shine yajasu sukayi sallah. Sai Bayan sun idar,suka nufi dinning. Sosai sunji ddin abincin. Anaci ana hira suna dariya. Har suka kammala. Amal ce duk ta tattara kayan ta kai kitchen din. Sannan suka dauko masa kayan. Nan yayita yaba kayan. Nan Anty Humairah ta dauko fone din da tasiyama Amal. Nima ga abunda na siyama yar tawa.nan ya amsa tareda yimata godiya. Bude wayar yayi.harda kyautar layi aciki. Nan ya hada mata komai.ya sanya mata numb.dinshi dana Humairah. Sannan ya kira.ankuwa yi sa'a da kudi aciki. Saina yayi mata setting din komai sannan ya mika mata tareda fadin aje asanya caji. Daki ta nufa cike da murna.ta saka cajin. Sannan ta dawo falon kayan ta dinga dauka tana kaiwa dakinta. Nan Anty Humairah ta nemi tayata tace Aa ta barshi. Tana gamawa ta koma falon tayi musu sallama dan baxata kuma fitowa ba saboda gyaran kayanta zatayi. Auuu! Yau ba hira kenan Amal din Abba. Dariya tayi uncle kayana zan gyara saida safe.sannan suma suka yi mata saida safan ta koma daki. Nan tashiga gyara kayan nata tana shirya su cikin wardrobe. Tanayi tana murna tana karasu ajikinta. Har tagama gaba daya. Saida tayi shirin baccinta duka sannan ta koma kan gadanta. Wayar Abban ta ,tadauko tareda kofar wasu numbs.cikin wayarta sannan ta mai da ta sanya wayarta a caji. Tayi addu'o'in data saba inzata kwanta bacci.sannan ta kashe wutar dakin ta kwanta. TWO WEEKS LATER 💝 Monday morning🌝 7:00am🕖 Lokacin Amal ta gama hada musu breakfast, dama already tayi wanka. Nan dannan ta shirya ta fito. A dining ta samu su uncle nan tagaida su dan ranarne zata fara zuwa makarnta. Itama breakfast din tayi sannan suka fito tareda uncle sanshi zai dinga anjeta a makarnta in tanada lecture. Anty Humairah Har motar ta rakosu tana cema Amal yau ita kadai zata bari cikin gida. Uncle yayi dariya tareda fadin kozaki bitane.suna dariya,hakde Har suka fice da gidan sannan ta koma cikin gida. Shikuwa Annur tunda umminshi tayi masa wannan magana Har yanxu bai dawo lafiya ba.duk yabi ya rame kamar bashiba. Gashi kullum sukayi waya da hanne sai tace Amal bata kira taba. Abu goma da ashrin ya hade masa. Dan ko a office bashi da nutsuwa duk wanda ya tambayeshi saiyace bashi da lfy. Hakanne ogansu ya umarceshi da in cutar nashi yayi tsanani ya dauki break mana yaga likita. Saiya cemasa zai dauka amma ba yanxu ba. Kuma Har yanxu wata magana bata taba hadusu da hjy ladi ba. Itama kanta Ummi tashi shiga wani hali ganindan nata kwana biyu duk ya wani fita daga haiyacinsa. Gashi ita baxata janye maganar aurensaba. Dan sotake ayi auran sannan ta kuma taci gaba da sana'ar ta hankali kwance. Ita kuwa hajiya ladi jin shirin yayi yawa,yasa zata yima hajiya maganar taji ina zancan yake. Itama hanne ta shiga damuwa ganin Har yanxu Amal din bata kiraba,ga Annur nata faman damaunta. Nan tashiga tunanin ko Abban ne ya mutu hankalin ta ya tashi sosai. Dande Gwaggo na dan tausasa mata zuciya. Amal yau anshiga makarnta kuma tabbas taji ddin makarnta balaifi. Musamman yanda taga kowa yana abunda ke gabansa ba tareda wani ya sanya masa idoba. Zaune take kan wata kujera tana kallon yanda mutanan gurin ke rayuwarsu.hakan yana mutukar birgeta. Dan basu dadi da fitowa daga lecture ba. Lokaci lokaci takan duba wayarta. Hanne ce ta fado mata arai.nan danan ta shiga neman numb.dinta cikin contact dinta.amma bata ganiba,hakan yasa tadau alkawarin tana komawa gida zata kiranta. Wata ta hango kamar wanda suka hadu cikin jirgi.da sauri ta dauki Jakarta tabi bayanta tana dan Sauri. Harta cimmata. Ammm! Excuse me ta fada. Juyawa tayi ta kalli Amal. Laaah! Amal ko,kace anan? Hannunta taja suka zauna.Ashe zamu kara haduwa inata tunanin indazan ganki. Amal daketa faman murmushi tace Allah Sarki. Ya kk ya karutu. Lafiya qlau wallahi ya jikin Abban naki. Da sauki tace. Toh yanxu kinga lecture zan shiga kibani numb.dinki inna fito saina nemeki. Nan ta amshi fone din sakina ta sanya mata numb.din sannan ta mika mata. Ywwa Amal na gode saimun sake haduwa. Sannan tabar wajan. Ta jima anan zaune kafin su shiga lecture suma. Jikin Abba da sauki. Amma Har yanxu be farkaba.Amma sun cireshi daga glass din. Kusan kullum sukaje in Amal batayi Kuka ba to zatayi hawaye. Yauma kamar kullum suna zaune shida kabeer bayan sun fito daga sallar la'asr yake shaida masa ai ankusa bikinsa. Sosai Annur ya tayashi murna. Kabeer ne ya kalli Annur yace dashi nikuwa Annur kaje kaga likitan kuwa. Naga kamar kana wasa da rayuwarka kamarma baka damu da cutarkanba. Hmm! Kabeer kenan ba haka bane,kawai de nasan cutar bata likita bace. Ohh! Kenan kaima auran kke bukata. Kabeer bazaka gane bane.wato akwai wata yarinya danakeso.kuma andan samu matsala ne.kuma inasan nayi solving matsala. Kaini bama hakaba,Dubai nakesan zuwa. Dubai kuma Annur, kai kuwa me zakai a Dubai. Inasan ganin yarinyar ne,kuma bansan ta inda zan faraba. Tafdi! Kace kai cutar taka ta so ce. Toh Allah ya taimaka ya bada sa'a. Ameen yace tareda mikewa tsaye.toh saika tashi ka koma dan ankusa tashima. Sannan suka rabu. 4:30pm. Amal ta fito daga lecture. Wayar ta taduba taga missed call din sakina. Itama kiranta tayi. Bata jimaba ta dauka. Hello Amal na fito inata kiarnki baki dagaba. Pls kiyi hakuri na shiga lecture ne. Ohk Nina tafi gida sai gobe ma hadu kinji. Tamm nagode sai anjima ta katse. Da kanta tadawo gida.da mamakinta Humairah taga,Amal. Aa! En makarnta Har an dawo?. Zama tayi kan kujera dan agajiye ta ke.ruwa ta dauko cikin fridge tasha sannan tace. Anty sannu da gida,karatu akwai wuya Anty yanda ka kasan anmin duka. Aidama sai hakuri. Bayan wuya sai ddi. Sai kije ki watsa ruwa ki huta. Toh tafada tareda mikewa.ta nufi dakin,da ker ta cire kayan ta shiga toilet din . Saidata gasa jikinta sannan ta fito. Gado ta fada tareda, lumshe Ido. Nandanan bacci ya dauke ta. Ba ita ta farkaba,saida magrib. Mikewa tayi tanufi toilet tayi alwala danyin sallah. Saida ta sanya kayanta sannan tayi sallah tana idarwa ta dauko wayar Abban ta dan kiran hanne. Annur na zaune a office yana aiki. Fareeda ta shigo. Sir kana da baki. Nan yabata iznin su shigo. Tana fita suka shigo su biyu ne. Hanne na zaune itada Gwaggo suna hira.taji wayar na kara.dan tunda Annur ya mata magana akan tadena barin waya nesa da ita. Tsoro taji Lokacin dataga wata irin numb.da bazata dagaba harta kusa tsinkewa Gwaggo tace da ita ta daga mana kar ta katse. Da sallama ta daga. Amal cikin farin ciki ko amsa sallamar batayiba. Tace hanne Amal cee! . Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 120-125 Cikin murna hanne ta mike tsaye sabo da tsananin farin cikin jin muryar Amal din. Cikeda zumudi hanne tace.ya Dubai din ya kowa da kowa ya kuma jikin Abban. Wallahi kowa lafiya qlau,Abba kuma jiki da sauki za'a,amma Har yanxu be farfadoba,saide kullum muna cikin addu'a. Toh Allah ya bashi lafiya. Yakuma tashi kafadunsa. Ameen Amal tace,tareda cewa ya en gidan da kike zaune suma qlau ko? Lafiya lau muke wallahi suma suna gaida ke kuma suna yima Abba ya jiki. Yana amsawa.hanne harna fara karatu anan fa. Da gaske Amal. Kice hankalin ki ya kwanta to Allah ya taimaka. Tashi tayi daga gaban Gwaggo ta shige daki. Sannan ta Amal. Hmmm in gaya miki har nayi saban saurayi dan gidan Gwaggo ne,kuma tsakani da Allah yake sona aurena ma zaiyi. DA gaske hanne. Allah ya sanya alkhari na tayaki murna, Amma de yana da aikin yi ko. Nagode, eh yana Sana'a ba laifi yana da rufin airinshi sosai dan Har mota gareshi.matar shice ta rasu shekara 3 da suka huce. Shine zai kara aure.dan harya sanar da Gwaggo. Itama taji ddi sosai. Shine ta ce masa yabari iyayen gidana su dawo. Gaskiya naji ddi.Amma yanxu hanne Har kyajira Abba ya warke. To menene Amal. Nimafa kamar uba yake a gurina kede kawai kiyi fatan Allah bashi lafiya. Ameen thumma ameen, babude wata matsala ko. Babu komai.Yawwa Amal wannan mutumin yanata kiranki,yanxu yacema inkin kirani na tura masa numb.dinki. Ywwa Annur. Allah Sarki dan Allah ashe yana kiranki.toh ki tura masa. Toh. Yanxu kinga na dawo daga makaranta.zanci abinci na kwanta na huta sai kuma na kuma kiranki. Ywwa baki gayan sunan yayan nawaba.kuma ki gaida shi. Hmmm! Sunansa Ahmad. Saida safe ki gaida su dan Allah kuma ki duba jikin Abba nabarki lafiya. Sannan ta kashe wayar. Nan ta nemi gajiya ta rasa.dan taji ddin waya da hanne sosai. Tanasan hanne itama tana kaunar ta.shiyasa take kewarta. Wardrobe dinta tabude ta dauko kayan bacci ta sanya. Sannan ta saka hijab dinta tare da fita falo dan yinwa takeji. A falo ta tarda su uncle suna hira. Amal idanki biyu dama.aena dauka gajiyan makarntar ne yasaki bcci. Cewar uncle yana kallonta. Wallahi na danyi baccinma,Amma wayama mukayi da hanne me aikin gidnmu. Wallahi tana da kirki so sai kuma tana kaunarmu. Tacema tana gaida Ku. Masha Allah, muma muna amsawa.Anty Humairah ta fada. Maza ga abinci kije kici nasan kina jin yinwa. Abincin ta dauko ta dawo falo ta zauna. Tanaci suna hirar makarnta, tana basu lavarin abubuwa daban daban. Wani suyi mata dariya wani kuma su gyara mata. Amma fa uncle sun iya lecture, kamarba larabawa ba.dan wallahi ana gane turancinsu sosai. Eh hakane kinsan akwai turawa acikin su.kede ki Dage.dan karatun medicine ba karamin Abu bane. Allah de yabada sa'a. ameen suka fada itada Anty Humairah. Tanci suna hira harta kammala ta maida plate din kitchen tasha ruwa sannan ta dawo falon.Sunanan Har akayi insha'i sannan ta shiga daki ta sako alwala ta dawo falon sukayi jam'i. 5:55pm Ya baro office din. Yana cikin driving a mota yaji message ya shigo fone dinshi. Be damu da koma wayeba.dan baya da bukatar sanin akanme aka turo shiba. Burinshi be huce hanne ta kirasa ta shaida masa sunyi waya da Amal. Ita kuwa hanne. Bayan sun gama waya da Amal. Wayrta ta duba ko akwai kudin dazata kira Annur. Saura #4. Dan haka ta yanke shawaran tura masa da numb. Nan danan ya karaso gida.saida yyi sallah magriba ka'ida kenan yake shiga gida. Danko yadwo ba'ayiba saiya jira Har yayi sannan. Da sallam ya shigo cikin gidan.yauma ba kowa cikin falon.da Sauri ya nufi dakinsa dan yau bayasan haduwa da kowa. Yana shiga yayima kofar key. Wanka ya fara shiga kamar ynda ya saba danyau ko sallah insha'i a gida zaiyi. Bayan ya gama duk abunda zaiyi. Har sallah, sannan yayi shirin kwanciya dan bacci yakeji.wayarshi ya janyo da duba sakonni. Sakon hanne ya fara gani dan ya canza sunan tun tuni. Jikinshi Har rawa yake ya buda. Kamar haka yaga an rubuta. ASSALAMU ALAIKOUM. ANNUR GA NUMB.DIN AMAL NAN.BA KUDI A WAYAR DANA KIRA KA. HANNE. Nan daran ya danna kira a numb.kuma ya shiga harta fara ring. Ita kuwa Amal dan gajiyar makaranta da tayi,ya sanya bata tsaya kallo ba ta musu sallama ta nufi daki danyin bacci. Tana shiga daki hijab din ta cire ta haye gado tareda kashe wutr dakin. Tana nan kwance Har baccnta yayi nisa dan ta gaji. Dayake bata da nauyin bacci taji kamar karan wayar ta. Mikewa tayi ta dauka tareda karawa a kunne. Cikin muryar bacci tayi sallama,ba tare da ta duba numb.me kiraba. Amsa sallamar yayi tareda fadin. Amal! Annur nefa. Da Sauri ta gama watsakewa. Da farkode ya hakuri. Da mamaki tace hakuri kuma. Shima mamakinne ya rufe shi. Tabbas kuwa haka nace dan an shaidamun cewa Abban ki ya rasu. Abbana bai rasuba illade yana kwance dan haryanxu bamusan amatsayin da yakeba,nasa afadi hakanne saboda wata manufata daban.Amma kaima inasan ka dauka a hakan. OK insha Allah. Amm! Amma kinsan Allah zai sakamin saboda irin huran da soyayyarki take yimin. Kullum fa cikin tunaninki nake. Wallahi da Dubai din zan taho. Murmushi tayi mai sauti,wanda shima kansa yaji. Dubai din zaka taho? Eh mana ko kina mamaki ne.kuma Har yanxun ban janye ra'a yinaba. Zanzo na duba Abba kuma naga masoyiyata. Murmushin takuma yi.Amma kasan Ummi bazata taba yar daba. Na sani,amma kuma sai naxoba. Ko korata kikesabyine. Nina isa nidaba kasa taba.Allah ya kawoka lafiya. Ameen. Yanzu de bacci nakeji saide da safe. Auuu! Koratama kikeyi my heart princess 👑. Nina isa na koreka. Toh najide bansan ina takura miki,sai goban kinji my one nd only👌🏻. Hmmm! Toh Allah ya kaimu tace dashi. Too I Lov u❣ Kema ki fada pls. En dariya tayi tareda rufe idanu sabo da kunya. Zata fada kenan yace Dakata! Saura inkin fada ki kashe wayr kisa zuciya ta tabuga.tunda wancanma haka kikayi Saiyau Allah ya kara bani ikon jin muryarki. Insha Allah. I Lov u too💕 Mutukar ddi Annur ya jishi. Kamar karsu rabu da juna da kr sukayi sallama. Kowannan su kasa anje wayr yyi tana ruke da su. Suna tunanin ynda rayiwar dayansu zata kasance batareda dan uwan taba. Sosai Amal tana jin Annur cikin zuciyar ta.dan Har tana da burin kara ganin kyakkyawar fuskarsa. Lallai in Abban ta ya warke zata gaya masa tana San Annur Har cikin ranta. Shikuwa gogan ba'a magana.dn a fadin duniyar nan aka cire umminshi, bbu wanca yakeso sama da Amal. Kowannan su da tunanin dan uwansa yayi bacci. 🔺🔺🔺🔺🔺🔺🔺 🔻🔻🔻🔻🔻🔻🔻 Pls dearest kuyi hakuri bnyi page din nan da yawaba,yankewa nayi a hannu. Did page also goes to u my fans lovs u ba'a dadi💝💝 😘😘 Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) 125-130 Yau Amal 10am take da lecture dan haka bata tashi dahuriba. Tana kwance saman gado tanata sharar baccinta hankali kwance.taji wayarta na faman ringing. Mikewa tayi ta dauko wayar. Assalamu Alaikoum Habibtee! Tana jin haka tasan Annur ne ya kiranta. Kara shigewa cikin blanket din tayi.tareda amsa sallamar tasa. Yanaji muryar taki haka ko baki tashiba. Wallahi bantashiba sai zuwa anjima tukun. Kina hutawa ba haka nakesun ki kasance koda yaushe cikin jin ddi da kwanciyar hankali. Hmmm! Kaima ae kana hutawan. Amal ina wani Hutu,kinsan na fara aiki yanxuma ina office kinga kuwa banida wani sauran Hutu. Nima ai hutun nawa na wani dan lokaci ne,zuwa anjima zan shiga lecture kasan na fara karatu. Alhmdullh dama nima burina kenan kayi karatu Amal kizama wani Abu.me kike karantane. Medicine nakeyi inasan nazama likita arayuwata. Toh Allah ubngiji ya bada sa'a yasa agama lafiya. Amen ta fada. Yauwa saiki samin rana yaushe zan shigo Dubai din. Aa kayi zamanka mana,kanasan janyowa kanka matsane,kasan Ummi bata sona taya zakace zaka taho gurina. Amal kenan ya kikesan nayi,bani da burin daya huce nazo na ganki Amal ina kaunar ki da yawa. Nasani Annur Amma kasan halin mahaifiyar ka,banasan abunda zai sakata kara tsanata. Ba komai insha Allah komai yazo kareshe insha Allah babu abunda zai kuma faruwa sai alkhari. Toh nagode sai anjima. Toh my bby San mun kuma waya. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Zaune hajiya ladi take a falo tana faman shan kanshi dan tagaji da giran gawan shanu. Hajiya bilki ke ta sauko daga upstairs tana faman yauki. Karasowa cikin falon tayi tareda zama kan kujera. Dukkan su babu wanda ya kula wani tsawan lokaci. Bilki! Hajiya ladi ta kira sunan ta,A gaskiya na gaji da irin wannan abun da kikemin. Kin maidani kamar wanda tazo cin abincin a gidan nan,saide ki bani abinci ki barni kara zube. Jamila me kikesan nayi miki.ina baki ci da sha da gurin kwana.toh kuma bayan wannan wani Abu kekisan da namiki. Dakata aiba haka mukayi dakeba,ina maganar aurena da Annur? Haka zakice dani kenan, jamila nayima Annur magana yace baya kaunar ki,baya sanki kuma inna takura masa yace zai bar gidan.kinga yanzu saiki hakur.... Cikin fishi ta mike tsaye,dakata Bilki, ba haka mukayi dakeba munriga munyi magana dake yanxu kuma da bukatarki ta biya zaki watsa min kasa a Ido. Kince inde Annur dankine toh zaki sashi ya aureni.kenan yanxu ba danki bane.Wallahi kin bani mamaki Bilki ban taba tsammanin haka agareki ba. Nagode sosai kuma kinsan koni wacece. Waboda haka Wallahi ko kina so ko bakya so saina auri Annur Wallahi kinji na rantse. Feeeee tanufi hanyar shiga dakinta dan barin gidan zatayi. Jamila itama takirata tareda mikewa. Hjy ladi tsayawa tayi ba tareda tajuyo ba. Kiyi hakuri dan Allah. Insha Allah zan San yanda zanyi,ki kwantar da hankalinki,inde ni na haifi Annur zai auri jamila. Murmushi hjy ladi tayi tareda shigewa cikin dakin. Ajjiyar zuciya tayi tareda zama kan kujera.tabbas tasan halin jamila bata da mutunci,dan haka dole tadau mataki akanta. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Tana gama waya da Annur, mikewa tayi tareda gyara dakinta tas.sannan ta shiga wanka. Saida ta gama wanka ta shirya tsaf,sannan ta fito cikin shirinta na makarnta. Dogowar riga ta sanya light blue, ta sanya bby hijab white. Sannan ta sanya takalminta ta dau hand bag dinta da fone dinta ta fito. Bata ga Anty Humairah a faloba,dining ta huce ta ci abinci,sannan ta mufi dakin Anty Humairah. Da sallama ta shiga cikin dakin. Kwance ta ganta saman gado tana waya. Zama tayi kusa da gadon tana kallon ta harta gama wayr. Matsowa tayi kusa da ita. Antyna inakwna ina fitowa naga banganki faloba. Lafiya lau my Amal, ina gama aikina na shigo daki ina waya da gida,kanwar Maman muce zasu zo siyan kayan auran kan wata. Wow! Kice Anty zamu sha biki,Allah yasa lokaci ba skul. Insha Allah babu. Wayar Humairah ce tayi kara. Hannu tasa ta dauka dan ganin uncle ne ke kiranta. Tana dagawa yace. Ina Amal ta shigane ina ta faman kiran wayarta no ans. Ka gantanan maybe tabar wayar daki.bata mana. Ansa tayi tareda gaida shi.yauwa Amal barka,yanxu aka kirani daga asibiti Abba ya farka Har an bashi abinci. Wani uban tsalle ta yi,tareda saukuwa daga saman gado. Tana murna. Zagayowa tayi tareda rungume Anty Humairah, Anty Abbana ya farka wayyo dadi Wallahi Har yaci abinci. Ahhh! Barka Allah ya kara sauki. Toh sarkin murna sai kici gaba da addu'a, mikawa Antynki wayr. Da Sauri ta mikawa Anty Humairah wayar. Yanxu suka kirani Wallahi kinga jiki ya fara samun sauki sai acigaba da addu'a Allah ya kara sauki. Ameen ya Allah ga shinan anata faman murna. Dariya yayi,sannan yace,ki tashi ki kaita skul in antashi saiki biya ki dauke ta Ku taho asibitin nima yanxu zanje. Toh adubashi kafin muzo. Amal dake tsaye tsananin farin ciki tama rasa inda rata sanya kanta dan ddi. Anty Humairah ce ta mike tareda fadin,saiki huce na kaiki makarnta in an tashi zamu huce asibitin. Haba cwt Anty mu fara zuwa asibitin mana. Uncle dinki cewa yayi saikin taso,saurin me kike yine ,maza ki huce mu tafi kinga bai kamata da fara zuwa makarnta ki fara missin lectures ba. Ba haka tasoba amma bata nunaba,toh Anty na muje. Jakarta ta dauka da fone dinta.suka fita tareda kulle gidan. Suna shiga motar. Amal ta shiga kiran hanne. Ba tadau lokaci ba ta daga kiran nata. Hello! Amal ina kwana. Lafiya qlau hanne,dama kiraki nayi na shaida miki Abba ya tashi. Alhmdullh barka Allah ya kara lafiya. Ameen hanne yanzu makarnta zan tafi innaje asibitin zan kiraki. Nan sukayi sallama. Suna karasawa makarnta ta sauketa, Sauri taketa famanyi dan ta yi latti. Kai tsaye class dinsu ta nufa dan tasan anshiga. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 1:00pm 🕐 Suka fito daga lecture sai kuma zasu shiga ta.( 1:45 to 3:00pm). Gauri ta samu kasan wata bishiya ta zauna tana duba wani littafi. Wayr tace tayi kara. Tana dauka taga Sakina ce ke kiranta.tana dauka. Amal kina inane yanzu na fito daga lecture. Wallahi nima yanzu na fito,ina bayan library a zaune wajan flowers din nan. Ohk to gani nan zuwa. Toh saikin karaso sukayi sallama. Cigaba da abunda take tayi. Bayan 10mins. Sakina ta karaso wajan hannunta rake da Leda. Itama zama tayi kusa da Amal din sunama juna murmushi. Amal sannu da hutawa ya kikaji makarantar tamu. Hmm! Ba magana karatu akwai huya sai an daure wlh. Sosaima kuwa me kike karntane Amal? Sakina ta yima Amal wannan tambayar tana kokarin fito da abunda yake cikin Leda. Meat pie ne da lemo guda biyu ta shiya musu. Sannan ta mikawa Amal di daya ta dau nata. Tnkuuuuu! Ta fada, Ina karantar medicine ne. Yayi Allah ya bada sa'a. Sannan ta kurbi meman hannunta. Nikuma ina karantar mass comm.ne. Itama Amal din ci tafarayi tana kallon sakinan.wow! Kinsan nima abunda nakesan yi kenan Amma Abba ya fisan science wlh. Gaskiya science yayi,gwara kiyi science din muzo muce Dr.Amal amana allura tafada cikeda zolaya. Dariya itama Amal din tayi. Sunaci suna hira Har suka kammala. Sannan suka nufi skul mosque dan gabatar da sallah. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Yana zaune a office dinsa yana faman aiki wayar shi tayi kara da alama kiran sa ake. Daukowa yayi tareda duba kowaye sanna ya kara a kunan sa dayan hannunsa rukeda paper. Uthman ne yake kirasa. Hello Angon Amal ya office din,Uthman ya fada yana dariya. Shima dariyar yayi, tareda fadin lafiya qlau Wallahi. Kai mutumin nan daga ji muryar ka kana cikin farin ciki.bani nasha mana. Kaide bari mlm ai munyi maja da mutuniyar dan muna waya sosai. Hhhhahha! Kace na fara shirye shiryan biki. Shima dariyar yayi. Amma kasan Abban ta nanan da ransa.akwai de abunda yake faruwa shiyasa sukayi hakan. Amma de Har yanxu be farfado ba. Ayyah Allah sarki Allah kara lafiya. Ameen yace dashi,ya ake cikine mutumin kwana biyu. Wallahi kaide bari abubuwa sunyi yawa.yanzuma on Thurs su mum zasu huce Dubai kasan yr gidan yayrsu za'a yima aure shine zasuyi siyayya. Toh kuma naji mum na fadin na shirya dani za'a. Ahabade kaga nima Dana biku inasan ganin Amal ita,saide problem daya Wallahi inada meeting da wasu yn kasar Spain saide next week. Amma mutumin kana ganin Ummi zata barka. Kai in bata barni naga maso yiyataba ni zata aura.commot Dallah. Ahhhhhhh Allah my guy kace Lov ba wasa.nimade zan samo wata cika najide yanda kukeji. Dayafi de. Dariya sukasa gaba dayansu.sannan sukayi sallama. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) 130-135 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Suna fitowa daga masallaci, suka rabo. Ita Sakina gida ta tafi. Ita kuma Amal class ta koma dan tana da wata lecture. [3:00pm] Daidai lokacin suka fito daga lecture. Tunkafin su fito Anty Humairah ta fito cikin shirinta dan tafiya asibitin. Tana fitowa daga lecture ta kira ta,nan ta gaya mata inda zasu hadu. Cikin mota ta sameta zaune tana jiranta. Side din da zata shiga, Ta fude tareda sallama ta shiga. Harkin fito? Anty Humairah ta tambaya tana kokarin yima motarki. Eh! Wallahi amma da alama kin dan jima anan. Eh to bawani sosai bade. Ya skul din. Alhmdullh, gobema 10 nake da lecture. Hutana frdy,sat nd sun. Amma kullum ina zarya. Amal kenan aishi haka karatun ya gada,saide hakuri. Ta karashe maganar tare da shan wata corner. Amma Anty uncle ya kiraki sunyi magana da Abba. Eh gaskiya yade ce mini yaje jiki alhmdullh. Allah mun godema,dan Wallahi duk atunanina Abba baxai tash..... Fone dinta dake cikin jaka ce tayi kara. Hannu ta zura ta dauka. Annur ne ke kiranta,duk sai taji tanajin kunyar Anty Humairah. Kuma bazata iya katsema hrtcontrol dinta wayaba. Dagawa tayi tareda sallama. Ya kk ya skul din ko Har kin dawo. Um! Yanzu na fito daga lecture muna kan hanyar zuwa asibiti duba Abba ance ya samu sauki dan Har ya farfado. Toh alhmdullh pls ki duba shi,in kinje,nima insha Allah nextwk zan shigo. Bazade ka hakura da zuwanba kenan ko? Kamar zai mata kuka yace. Haba Amal ko bakya San gani nane, Aa ba haka bane aikin naka fa? Amal break zan dauka danna zo na ganki. Kinga Uthman ma yana nan shigowa. Insha Allah zaizoma gurin ki. Ki gayamin me kikesan ya kawo miki. Shiru tayi tana San tace wani Abu Amma tanajin nauyin Anty Humairah. Zan fadama yanxu mun karaso asibitin sai anjima. Ohk saikun dawo kinji. Bye. Daidai lokacin sukayi parking motarsu. Gitowa sukayi Anty Humairah tana kallon Amal da murmushi. My Amal ko mun samu siriki ne? Kai Anty ba wani siriki abokine. Hahahah ja'ira abokinne ake kashe mai murya haka. Itama dariyar ta bata. Sanan ta zagaya suka nufi cikin asibitin suna hira abun aha'awa. Elevator suka hau nan da nan suka isa. Dakin suka nufa, Amal ji take dan dadi kamar tayi tson tsuwa ta shiga cikin dakin. Da sallama suka tura dakin. Ganin Abbanta zaune wata nurse gabanshi da alama magani ta bashi. Da sauri ta fada kansa tana kukan dadi. Shima murmushi yayi tareda shafa kan nata. Ita kanta nurse din sun burgeta Har murmushi tayi sannan ta fice daga dakin. Anty Humairah ce ta karaso tadan rissina tareda gaida Abban. Ahankali ya amsa,tareda tambayar ta ya gidan. Lafiya qlau ya Karin sauki. Alhmdullh yace. Amal din Abba kukan me Nene koma kikeyi tashi ki goge hawayanki. Dagowa tayi abunka da farin fata Har fuskn ta danyi ja. Abbana sannu Allah ya kara sauki. Ameen Amal dina. Dazu na tambayi Hakeem kina ina! Yace ai kina makarnta. Naji ddi sosai. Allah ya miki albarka ya baki miji na gari kinji. Ameen Abbana, hanne tace tana gaida kai. Ina amsawa Amal. Bani rau insha. Da Sauri ta juya ta dauko ruwan kan wata yr wardrobe ta dauko ruwan tareda zubawa a cup. Matsawa tayi gaf dashi,ta bashi a baki. Yan sha yadan kware. Maza tayi ta anje cup din agefe ta rungumoshi kamar karamin yaro tana ahafamai baya a hankali tare da yimai sunnu. Humairah dake gefe ita kanta sun bata tausayi koma sun burgeta Har kwalla saida ta zubar. Tana manne jikinshi tace Abbana. Naam Amal! Annur yace yana gaida kai. Amal waye kuma Annur? Hmm zaka sanshi yacema shima zaizo ya dubaka insha Allah. Toh Allah kawoshi. Ameen ta fada tareda janye jikinta daga nasa tana kallon sa. Abbana duk ka rame . Hmmm ke kuma kinyi kibarki ba,su Humairah sun sa yarinyar ta koma yar lukuta. Dariya sukayi gaba daya. Humairah ce tace aikode gatanan ba wani abincin kirki take Ciba. Abban ne yadan bata rai ya kalleta. Kunnan ta takama tareda make kanta jikin kafadunta. Am sowie Abbana dama saboda tuna ninkane banaci Amma tuna gashi ka warke zan dungaci sosai Wallahi. Karar wani Abu sukaji kamar ana magana. Mikewa Humairah tayi,tareda fadin Amal kuma saita taso mu huce Lokacin visitors ya kare. Kamar zatayi koka ta kuma makewa jikin Abban nata, Shima bayasan Amal din tashi tayi nesa dashi,Amma ba ynda ya'iya haka dokar asibitin yake. Sallama sukayi masa tareda yi masa alkawarin zata dawo gobe harda yr kwallanta. Kiranta yayi tareda goge mata hawayan. In kika kara kuka, Ya dubi Humairah karki kara kawota. Murmushi tayi tareda kara rungume shi. Insha Allah Abbana na dena. Hannu suka rinka dagawa juna Har suka bar dakin. Itade Humairah kallan su take famanyi da mamakin irin soyayyar da sukema juna. Sannan suka fita tareda shiga mota saikuma gida. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Suna gama waya da Amal. Nan ya shiga tunanin ko inyaje ya zata kaya musu da Abban Amal dukda yana tunanin bazaisha wahala wajan shawo kansaba. Umminshi ce zata kawo matsala amma insha Allah yau zaije mata da maganar. 🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺 Dakin hajiya Bilki ta nufa.ko sallama babu ta tura dakin tareda shigewa taci uwar kwalliya kamar wacca zataje gasar sarauniyar kyau. Bilki ni zan fita saikuma na dawo. Ba tareda ta kalli inda takeba tace saikin dawo. Murmushi tayi tareda janyo mata kofar ta fice. Harabar gidan ta fito tahau motarta. Sannan ta fita. Hajiya bilki dake tsaye bakin window tana kallonta. Murmushi itama tayi hmm! Ki gama haukanki nan da wata biyu zuwa uku zanma Annur din aure sai naga abunda zakiyi. In banda haukama irin naki me Annur zaiyi da mata irinki. Tsoki taja sannan tabar wajan window. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Suna komawa gida. Wanka amal tayi sannan tayi sallar la'asr. Fitowa tayi dan neman abunda zata sama cikinta. Kitchen ta nufa. Ta dauko abinci. Rashin ganin Humairah a falo ya sanyata binta dakin dan batasan zama ita kadai. Da sallama ta tura dakin. Humairah dake tsaye jikin wardrobe tana gyara wasu kaya ta jiyo ta amsa. Zama Amal din tayi tareda bara cin abincin ta. Anty ni kuwa yaushene in uwankun nan zasu zo. Amal kenan kin matsu suxone? Eh! Wallahi Anty, amma de harda amaryar zasu zo ko?. Eh da amaryar da kanwar mamanmu sai kuma danta. Allah ya kawo su lafiya. Allah Anty banaso suzo ranar da ina da skul. Aikuwa inaga ranar Thurs zasuzo,kuma exactly kina skul. Amma ai zaki dawo ki tanda su. Amma nide gaskiya Anty banso hakanba. Dariya tayi mata tareda fadin Amal sarkin San mutane.. Wallahi kuwa kinga ya kama jibi ke nan.Allah de ya kaimu lafiya. Ameen. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Annur yau da huri ya dawo daga office yana zaune a daki yana signed din wasu files. Umminshi tayi sallama tashigo dakin. Zama tayi bisa gadon tana fuskantarsa. Shima ita yake saurare dan duk ya anje komai gefe daya. Sannu da aiki tace dashi. Shima amsa mata yayi tareda fadin yauwa ummina ya gidan. Lafiya qlau Annur. Dama akan maganar da mukayi da kaine nayi maka magana Amma kayi shiru saboda haka Nina sama maka mata nanda 2months za ayi mikin. Sara yr gidan hajiya murja da suke a Lagos sabo haka nariga na yanke hukunci kuma aure ba fashi. Nanda 3wks zatazo gidan nan ta zauna Har Lokacin bikin naku.dan anan nakesan ayi komai. Wallahi yarinya abar tausayi kasan babanta ya rasu tunda jimawa. Kallonta yake da mamaki. Sannan yace Amma Ummi ita yarinyar cewa tayi tana sona? Eh na tura musu pic ka,sunce kayi musu. Amma ni kinsan ina santa ko bana Santa. Nasan Annur ko kare na kawo maka acikin gidan nan zaka soshi balle mutun sukutum,kaima dan baka ganta bane Amma nasan zaka sota. Mikewa yayi tsaye tareda fadin toni bana Santa bana kuma kaunarta, Wallahi ummina bazan taba San wata ya mace acikin zuciya taba inba Amal ba. Tasssss yaji ta kasheshi da mari. Wallahi Annur sunan tama nakuma ji acikin gidan nan saina tsine maka. Kai wani irin mahaukacine,kanada hankali kuwa. Ko kunya bakaji a hulakanta uwarka agabanka Amma kace still kan San hada jini da wadnnan hula kantaccin mutanan. NA gayama kuma nakara maimaitama banasan Amal kuma bazaka taba auran taba koda hakan zaiyi silar barinka duniya. Kuma ka shirya ba abunda zai hana auran ka da Sara,sakaran banza wanda besan mutuncin kansaba. Sannan ta juya tabar dakin. Murmushi yayi ko ajikinsa yasan babu abunda ya isa ya hana ikon Allah, kuma yanaji ajikinsa Amal matrsa ce. Toilet ya shiga danyin alwala sallah insha.. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) 135-140 Yana fitowa, masallaci ya fita dan yin sallah. Umminshi na zaune a falo tana kallon sa Har ya fice ba tareda ta cemai komaiba. Shima kuwa ko kallon inda take baiyiba. Bayan an idar da sallah ya shigo gida. Lokacin yayi daidai da fitowar hajiya ladi daga mota.da Sauri ta kulle ta karaso gaban Annur din. Annur ta kirayi Sunansa. Kallonta yayi samada kasa sannan yace ya akai.? Naji sakon ka gurin mahaifiyar ka,Amma inasan ka gayamin dalilin da yasa baka sona. Wata iriyar dariyace ta subuce masa,harda rike ciki sosai yake dariyar bashida alamun tsayawa. Sabida bakin ciki kasa koda motsawa tayi tana ta faman kallonsa. Cigaba da dariyar sa yayi tareda shigewa gida.dan bama zai iya sauraran haukan matar ba. Da sallama ya shiga falon fuskar sa dauke da alamun murmushi. Ya huce zuwa dakinsa. Umminsa data zubamai Ido da mamakin murmushin me Annur yake.bata gama yankewa kanta hukuncin hakanba. Hajiya ladi ta shigo fuskarnan ba alamun dariya kamar karamar yarinya. Hakanne ya baima hajiya bilki dariya itama. Tsayawa tayi cak! Tareda juyowa a fusace tana kallon ta. Wato kun maidani mahaukaciya keda danki ko,kun ajjeni agida ga joker kuna kallo.yayi muku kyau. Ta juya fuuu! Tashige dakinta tareda banko kofar. Hakanne ya sanya hajiya kara tuntsirewa da dariyar da tafi ta farko. Wato shima Annur din kin bashi dariyar kenan. Mikewa itama tayi tareda shigewa dakinta tana fadin Allah ya kyauta.. Thursday morning [9:00am] daidai ya nuna agogan Dubai. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Amal ce ta fito sanye cikin shirinta na tafiya skul. Riga da wandone ajikinta green color na Pakistan sunyi mata kyau sosai sai jacket baka data sanya saboda yanayin garin na sanyi. Tayi rolling mayafin kayan a kanta. Sannan ta rata jikarta. A dining ta tarda Anty Humairah. Zama tayi tareda gaidata. Cikeda fara'a ta amsa mata. Harkin fito kenan yau ba ai baccinba kenan. Wallahi Anty Sauri nakeyi yau test ne dani Har gudu biyu,shiyasa nake Sauri danxan duba wani littafi cikin library. Toh Allah ya bada sa'a ya kuma sa acinye gaba daya. Ameen tace. Tanata faman Sauri ta cinye abincin dan 10am zasu shiga lecture.nan danan ta tuttura. Sannan ta mike dan tacema Anty Humairah zata tafi da kanta dan itama tasan gari kuma aikina take yi danyaune bakin su zasu zo. Mikewa tayi tareda rataya jikarta sannan ta zagayo wajan Anty Humairah ta manna mata peck a kumatu. Tareda fadin bye my Anty,in baki sun karaso asanar dasu ina gaidasu kafin na karaso. Dariya tayi tareda fadin insha Allah my cwt hrt bye. Sannan ta fita daga gidan tareda janyo mata kofar. Bakin titi ta nufa sannan ta tari taxi sai makarnta. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 [6:00am] Daidai ya nuna a agogon Nigeria. Kai tsaye airport na nufa. Da alama passengers suna cikin jirgi.dan naka jirgin bai tashiba. Maza nayi na fada cikin jirgin ina nishi saboda uban gudun danasha. Neme neme yashiga yi. Can nahango. Uthman zaune shida wani saurayi da alama yanxu suka hadu dan gaisawa sukeyima.murmushi nayi nakuma matsawa. Mum na hango zaune kusa da ita wata kyakyawar budurwace da gani shekarunta bazasu huce 19 zuwa 20 ba.ta kwanto da kanta jikin mum. Ita kuwa mum tana ta faman mita. Ace mutun sai shegen San jiki Allah Nana (Halimatu sunan ta shine suke kiranta da Nana). Zanga ranar da zaki dena sai kace mage. Nana dake faman dariya tana kara shigewa jikin mum. Kai dan Allah Mum Uthman dayake haka suke kiranta. Auremafa zanyi basai nazoba zn dinga zama jikinki. Naji uwar rashin kunya daga. Dariya tayi tareda dagata.innayi aure nasa Aliyu bai hanani kwanciya jikinshi. Jeki kita kwanciyar maras kunyar banza.Allah yaran zamani baku da kunya. Mum Uthman meye kum.... Kene rufemun baki sai shegen surutu kamar parrot. Dariya taci gaba dayi tana kallon mum din. Suna cikin hakanne jirgi ya tashi dama already sun daura belt dinsu. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 Shima Annur yau da huri ya tashi saboda yanada meeting har guda biyu. Yanxu zai shiga 7am ya fito 11am. Bayan nan zai shiga wani da 2pm zuwa 4pm.shiyasa baibi su Uthman din ba. Amma yana da burin yin hakan Amma tunda 2wks zasuyi shima zai bisu yayi ko 1wk dayane inyaso saisu dawo tare. Nan danan ya gama shirinsa. Falo ya fito ya nufi dinning ba komai sai ruwan tea.shiya zuba yasha sannan ya fice daga gidan. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Koda Amal ta karasa makarnta kai tsaye library ta nufa. Tana shiga ta shiga neman littafi da zata duba. Ba tadau wani lokaciba ta dauko shi tashiga dubawa dan remains 15 mins su shiga test din. Wayar tace tayi kara da Sauri ta zira hannu ta dauka tareda karawa a kunne sakina ce ke kiranta. Amal yau bazan samu damar zuwa skul ba Amma ki gayamin lokacin da zaki fito a lecture nasan raki dubo Abba sai na zo najiraki mu huce asibitin. 2pm zan fito inyaso saiki jirani mu tafin. OK saikin fito bye. Ta kashe wayar. Nan taci gaba da abunda takeyi dan Sauri take batasan lokacin yayi bata gama ba. Bayan wasu yn mintina ta mike ta nufi class dinsu da gabatar da test din dake gabanta. 🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺 Anty Humairah kuwa.sai faman aikin tarbar baki akeyi ta dora wannan ta sauke wancan. Ta gyara gidan babu abunda yake sai kanshin girki😋😋😋 Dan Anty Humairah gwanace wajan girki ta iya abinci kala daban daban. Shiyasa take koyawa Amal. Gata da tsafta da kwalliya.komai nata tsaf yake. Shiyasa uncle Hakeem kejida ita suke zaman su lafiya koda basa haihuwa hakan baya daga musu hankali saide koda yaushe su kaga yaro yana burgesu. Shiyasa suke kaunar Amal kamar yar cikin su. Ita kanta Amal din tausayinsa takeji harta daukama kanta alkawarin inde tayi aure ta haihu zata basu first born dinta kyauta wa su dan saka musu da alkharin da sukayi mata.😪. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 (2:00pm) Harsun sauka sun iso gidan Anty Humairah, da yake ita taje ta dauko su. Sai yaba kyan gidan da tsarinsa suke. Boys quoters ta kai Uthman daki mai kyau da toilet nan ya haye gado yana kallan ta.wlh nagaji Anty Humy. Saika tashi kayi wanka kazo kaci abincinka. Sannan ta fice daga dakin. Dakinta takai mum Uthman da Nana. Suma zama sukayi tareda fadin gaskiya mun gaji. Mumce ta kalli Nana dake kwance tana wani latsa fone. Yimin shiru bayan duk akaina kikaxo yarinya sai shegen San jiki. Allah inzamu koma baki zama kusa dani. Dariya Humairah tayi tareda fadin Allah ko mum. Wallahi yn nan bata da kunya karama da YAYA zata aurar da ita. Dariya Nana ta kamayi. Mum Uthman me nayi kuma. Zaki min shiru ko saina kode miki baki. Dariya Humairah ta kama sannan ta kalli Nana toh zaki zauna nan dakin ko kuwa dakin Amal zaki zauna. Yauwa Anty ina Amal din Allah na matsu na ganta. Ayyah zaki ganta tana makarnta sai zuwa anjima zata dawo.itama yanata faman jin ddin zuwanku Wallahi bakiga yanda take sankuba tunkan Ku zo. Mumu ce tace Allah Sarki harkun tuna naming da wata yarinya abar tausayi itamako Amal Sunanta. Anty nide kaini dakin Amal din na watsa ruwa can zan zauna Allah sa tana da surutu musha shagalin mu. Mum ce ta kalleta Allah shiryaki Nana. Dariya sukasa sannan ta dau trolley dinta Anty Humairah ta dakata dakin Amal din. Sai kiyi maza ki shirya ki fitu kici abinci. Toh tace da ita. Kallan dakin ta tsaya yi komai gwanin ban sha'awa sai kanshi dakin yakeyi. Matsawa tayi jikin wani dan karamin pic na wata yarinya kamar balarabiyya tayi kyau sosai tun tana karama ne. Amma tabbas in wannan ce Amal din tana da kyau.toh Amma Anty tace dani su a Nigeria suke kika kawar tace balarabiya anan garin. Da wannan tunani ta shiga toilet danyin wanka. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 2pm tafito daga lecture. Ta gaji sosai amma dole sai taje asibiti dan taga Abban ta. Wayar sakina ta kira nan ta gaya mata inda take. Nan ta karasa.kuma dauko wayar tayi ta kira Anty Humairah. Anty Humairah nata faman hadama bakinta launch. Taji karan wayarta. Dauka tayi tareda murmushi tasan Amal ce. Cwt mum cwt Anty. Murmushi tayi tareda fadin my Amal ya test din. Alhmdullh. Nasan de baki sun iso Ade mikamin gaisawa kafin na karaso pls. Toh bbyna. Kin tafi asibitin ne? Eh yanxu zamu tafi nida Sakina sanna frnd din tawa danake baki lbr.itama zata je ta duba Abban. Toh bbyna ki gaida Abban kinji saikun dawo we Miss u bye. Bye itama tace tareda kashe wayar. Kara sowa tayi tareda fadin Sakina mu huce ko. Yawwa Amal kinsan harna kosa Wallahi.. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) 140-145 Taxi suka Tara kai tsaye asibitin ta nufa da ita. Suna zuwa suka sauka tareda bashi kudin sa. Suna tafe suna hira Har suka karaso dakin. Da sallama suka tura suka shiga. Da gudu Amal ta kara tareda shigewa jikin Abbanta. Sakina dake tsaye tana dariya,ta karasa tareda durkusawa a gaban abban. Inayini Abba Lafiya qlau ya amsa cikin fara'a. Ya Karin saukin jikin. Jiki alhmdullh mun gode Allah. Abba itace frnd dina tun a jirgi muka hadu da ita sch.din.mu daya da ita.amma zata Riga ni fita. Allah Sarki Abba ya fada tareda kallan kalan Amal. Ya karatu kuma duk komai lafiya de ko. Lafiya lau Abba. Toh! Allah ya muka albarka. Ameen suka fada tareda koma wa kan kujera ta zauna. Amal dake jikin Abbanta tace Abba yau fa baki zamu yn uwansu Anty Humairah za suzo daga Nigeria. Toh! Inkinje duk ki gaida munsu.zasuji sosai insha Allah. Nan fa ta zauna ta dinga bashi lbrn skul sunata faman mata dariya shida Sakina. Sakina tace Abba gaskiya zata sa cikinka yayi ciwo inde ta nan.Wallahi ka korata. Abba ka ganta ko? Ta fada cikin sigar shagwaba. Aeee! Gaskiyane Amal, yanxu kinzo kin hayemin gadan kamar mu biyune bamuda lafiya. Gashi kinata sani dariya. Tashi ta takoma kusa Sakina tana murguda mata baki. Dariya suka kama gaba daya. Abba yanzu ba'abunda kake iyaci ne. Aa Amal alhmdullh ina iya cin abo ,amma liquid ban fara cin abincin bade. Toh kaga jiki ya fara kyau Allah ya kara lafiya. Ameen suka amsa tare.nan suka hau hira gaba dayansu. Dan sakina wayayyiyace ba ruwanta tanada sakin jiki duk inda take.hakan yasa take da shiga rai. Sun jima sosai wajan abban sannan suka yimai sallama dan tafiya gida. Sosai Abba yaji dadin ziwansu yayi musu addu'a sosai.tareda fatan alkhari. Sun fito daga asibitin Sakina tace gida zata huce. Haba sakina kibari mana muje gidnmu kici abinci tunnda in kinjema gidan ba abunda zakiyi. Kinga kuwa munyi baki kema kyaga in gida kiji ddi. Dariya Sakinar tayi tareda fadan kede kawai so kk mu tafi muje de yau in gaida Anty Humairah taki. Ywwa kokefa kinga nima saina rakoki gidan naki kinga shikenan da na tashi zuwa basai kinmin kwatanceba. Wata taxi din suka kuma Tara tareda shigewa ciki suna hirar su. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 Kowa ya shirya ya fito zuwa dinning din. Nan Anty Humairah ta gabatar musu da abincin data girka musu kala kala. Nan fa aka hau cin abincin ana ta faman hira da dariya. Yan uwa masu ddi. Burin Anty Humairah ta faran tawa yn uwanta. Sunaci suna hira kowa cikin nishadi Har kowa yaci iya cinsa. Uthman ne fara tashi ya koma falon ya zauna. Sai mum din sa. Humairah aka bari tareda Nana, suka kwashe kayan suka maida dinning. Nana ce tace Anty ki barni na wanke miki kwanikan na gyara miki kitchen din. Aa gaskiya ki bari kawai.zan gyara kuje kuyi hira. Kece ya kamata kuje kuyi hira tunda kin jima baki ga kowaba. Gaskiya ne,toh sannun ki godiya ba adadi. Sannan tabar kitchen din ta koma gurin su mum suna hira. Nan Nana tashiga gyara mata ko ina.tas ta wanke mata kwanikan ta, ta gyara mata kitchen din gwanin ban sha'awa. Sannan ta dawo falon ta zauna. Washh! Gaskiya nadan gaji. Mum ce ta kalleta tareda fadan uwar San jiki,saima kin yi aure tukun zaki gajin. Hhhhh! Kai mum, Wallahi bani da San jiki ki tambayi YAYA. Uthman ne yayi dariya tareda fadin da kenan amma yanxu ai baki da aikin daya huce waya da Aliyu. Kaiii ya Uthman harda ka.....bata gama rufe bakintaba wayarta tayi kara. Da Sauri ta dau wayarta tareda shigewa daki da gudu tana dariya. Ja'ira marar kunya inji mum. Sallama su Amal sukayi tareda shugowa falon. Cak Amal ta tsaya Sakina na bayanta. Uthman ta fada tareda kallon mum. Mum! Sai kuma ta karasa shigowa falon tana musu kallan mamaki. Suma shi suke mata.itade Sakina zama tayi kan kujera tana kallon ikon Allah. Saikuma ta karasa ta rungume mum tana dariya. Itama rungume tan tayi. Mum ce ta kalli Humairah dake zaune tana kallan ikon Allah. Humairah itace Amal din Dana ke gaya miki. Nan mum ta bayyanama Humairah komai data sani game da Amal din. Taji ddi sosai sannan kuma aka fara gaisawa. Sakina ce tasan zamo daga kan kujerar tana murmushi tareda gaidasu. Sannan suka gaisa da Uthman dayake ta faman kallan sakina tun shigo warau. Nan akahau hira da dariya kuma Uthman da mum sukayi mata dubiya. Sosai kowa yaji dadin haduwa da kowa. Can de amal dake jikin mum tace Anty nida banga Nana amaryana. Nana ce ta fito daga dakin tareda fadin ga Nana Amarya. Saikuma aka kuma kwashe da dariya. Sakina tace Amal fa ga Amarya nan. Wallahi kam ta fadi tareda karasowa ta zauna kusa Sakina. Sannan suka shiga gaisawa. Itama Amal din gaisawa sukayi. Sannan ta tambayi Amal din jikin Abba. Da sauki ta amsa mata. Toh mum kina cewa inada San jiki ga wadda ta fini nan. Ta wani make a jikinki kamar yr bby. Hhhhhh Amal tayi dariya tareda fadin aini yr bbyce ke kuma kin girma tunda gashinan zaki zama Amarya. Toh abarni mana na Dana jikin tunda tafiya zanyi. Ke Amal malama dagamin uwa Har wani fada kuke akanta kamar kun samu katifa. Duka dariya sukayi. Amal ta mike tareda komawa kusa da Humairah.ta shige jikinta itama ta rungomata. Nana aka kuma dariya. Nana da Sakina ma suka rungume juna suna dariya.😂😂. Duk wanda yabar gida,gida ya barshi Wallahi. Toh Amal maza atashi aje aci abinci keda sakinan fadin mum. Toh mum! Dining suka nufa Har Nana. Nana ce tayi serving dinsu Amal. Su naci suna hira kamar sunyi shekara da sabawa. Suna gamawa,Amal ta kalli Sakina tareda fadin zandan watsa ruwa pls kumu koma daki dan na dinga jiyo muryarku. Dariya sukayi tareda fadin kumu je to. Sannan suka koma ita kuma ta shiga wankan. Dama itama Sakina yr Shaftace nan aka hau hira.. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 1pm NG. Lokacin bai jima da fitowa daga meeting ba.zama yayi kan kujera. Numb.Amal ya kira yaji wayar akashe yasan tanada lecture shiyasa ya jita a kashe. Kuma yasan su Annur basu saukaba da ya kirasa yanzu. Wayar shi ya dauko tareda kiran numb. Kabeer dasu je suci abinci. Bugu biyu ya dauka. Ya kana inane yanxu na fito daga meeting ka fito muje muci abinci. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 Jamila! Jamila!! Fitowa tayi daga dakinta tana murza Ido da alama bacci takeyi. Ganin hajiya bilki tsaye tayi kwalliya da alama unguwa zata. Lafiya hajiya bilki kike faman kirana. Kamar wadda tayi wani lefi. Dama fita zanyi,saboda haka maybe bazan Dawo yauba dan karki ga shiru. Murmushi tayi tareda fadin saina kin dawo. Sannan ta juya ta koma cikin dakin. Itakuma fita tayi tareda janyo dakin. Murna hajiya ladi ta shigayi yau zata burge Annur zata nuna masa soyayya karma ki dawo din. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 Suna dawowa da cin abincin suka kuma shiga meeting. Shikuwa Kabeer office dinsu ya nufa. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Tana fitowa daga wanka suna nan suna ta faman hira suna dariya. Murmushi tayi tareda kallan Nana, Nana ba wasa ansa Sakina a gaba ana ta faman zuba mata lecture. Kede bari Amal cewa nayi da sakina tun shigowar ta na lura da irin kallan da Uthman ke yima sakina. Amal dake daure da towel ta karasa jikin mudubi tareda matsa lotion a hannunta tana dariya tace Wallahi nima na lura da hakan. Wallahi baku da mutunci yarannan haka ya gaya muku. Nana ta gyara zama aiba sai ya gaya mana ba,mu mungani. Gaskiya sakina kawai ki aminci musha biki.kinga dama kin kusa gama karatunki kina gamawa sai biki kawai ko kuwa Nana. Allah kuwa, Nede kiyi hakuri Ku bari shiya fada mana. Nana tace nasan halin ya Uthman Wallahi bashida boye boye tsaf zai gaya miki kede ki zuba Ido kisha kallo. Hmmmm! Nide Amal maza ki shirya muje. Aww! Kenan fitama ma zakuyi ni bani. Cewar Nana tareda mikewa tsaye. Amal da tagama shirinta cikin doguwar riga multi color tareda rolling farin mayafi,ba komai fuskarta sai farar powder. Laaah! Nana gidanta zanje in gano ,kinkuma zaki taso. So saima nima ai sai in gano.tafada tare da dauko mayafinta da fone dinta. Sannan suka fito. Anty Humairah da Uthman ne kawai a falon . Suna futowa ya sauke idanunsa kan Sakina. Murmushi su Amal sukayi. Antyna dama zamu yima Sakina rakiyane kuma muga gidan datake zaune. Ahhh gaskiya kam kin kyauta. Mikewa tayi tareda fadin ina zuwa. Dakinta ta nufa taje ta hado mata yan kayayyaki a wata jaka mai kyau tabata. Sosai taji ddi tayita godiya. Bakomai Sakina ai duk me kaunar amal tou me kaunar mune ki gyaida gida. Toh insha Allah saina sake zuwa. Allah kawoki kema ainan kamar gidan yake a gurinki. Ta juya ta kalli Uthman dake satar kallan sakina,Uthman ga key din motata ka kaisu mana sai tana nuna maka. Ohk ya fada ranshi tas. Amma beji dadi da yaran nan za'a tafi ba,su Nana kenan.. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) 150-155 Tunda suka fara tafiya babu wanda yama wani magana. Nana kwa na baya tana faman game a wayarta. Amal kuwa data manto wayarta a gida kalle kalle take ta faman yi. Wayar Uthman ce tahau ringing dauka yayi tareda karawa a kunun sa. Ya inajin ka? Daga dayan bangaran kuwa Annur ne ke tambayar Uthman ya kira wayar Amal bata dagaba ko lafiya. Wallahi kaganta nan kusa dani sun takura mun ita da Nana saina kaisu shan ice cream. Murmushi yayi tareda fadin toh ka kaisu mana haba mutumina na...amma yama sunan ta. Naji Dallah karkuma kasande bani kadai bane. Ohk toh dan bata mana mu gaisa kafin Ku koma gida kansan banji muryar ta gaba daya. Dariya yayi kafin ya mika mata,sannan ya mikawa Amal tareda fadin gashi Annur nasan magana dake. Amsa tayi tareda danyin murmushi. Sallama tayi masa sannan shima ya amsa. Habibtee tun dazu nake ta faman kiran wayarki Amma u refused to ansa. Wallahi mun fitone kuma nabar wayr a gida. Ohk! Ykk ya gdn ya jikin Abban. Da sauki Wallahi kuma ina lafiya. Masha Allah. Sai kuma kikaga Uthman ko? Wallahi nima nayi mamakin ganin sa,Ashe Anty Humairah cousin dinshi ce. Wallahi kuwa ai naji ddi sosai. Kinga mum ko? Wallahi nima naji ddi sosai saide muyita musu addu'a. Murmushi yayi wanda saida taji sautinsa. Ina Nana Amarya. Aww! Dama ka Santa ne. Sosai ma Nana sarkin surutu, ai Aliyu abokin mu zata aura kinga ita surutu shima surutu. Gaskiya kam Allah ya kaimu lokacin. Yanzu bata mu gaisa nasan tana kusa dashi. Nana kuwa tunda taji ance Amal ta anshi waya inji Annur kanta ya daure,kar de Annur din data sani. Mika mata wayar tayi tareda fadin gashi Nana zakuyi magana da Annur. Amsa tayi tana murmushi. Hello! Malan Annur kuma shikenan tunda aka rabu a London sai a dena ganin Ku. Hmm! Wallahi ba haka bane Nana kinsan abubuwa sai ahankali kuma ai normal ne tunda muna tareda guy dinki. Allah ko,Ashe Amal ce tayi dace,gaskiya ka iya zabe Allah ya sanya alkhari ya sa ayi damu. Ahhh! Insha Allah,nima zan shigo Dubai din next week, kinsan ina missing din bbyn tawa. Gaskiya ne,Wallahi Allah ya taimaka muna nan muna jiranka.sai anjima. Mikawa Amal wayar tayi tareda karawa a kunnan ta. Mine! Yanzu saikun koma gidan mayi wayar ko? Toh insha Allah ka kulamin da kanka. Kema haka I Lov u. Murmushi tayi tareda fadin I Lov u more😍. Sannan sukayi sallama ta mikawa Uthman wayar shi. Murmushi yayi ya amsa batareda yake mata komai ba,dan shima kansa yana mamakin yanda Amal ta fada San Annur lokaci daya. Nana dake baya tace.hmmm! Amal kenan ana cewa bani da kunya. Dama nasan kowa be tashi nasa ba. Itade Amal dariya take ciki ciki,dan ita kanta tana mamakin yanda in suna tareda Annur bata jin kunyar kowa burinta ta faran tamasa rai. Daidai wata ha daddiyar plaza sukayi parking sannan suka fito. Kai tsaye ciki suka nufa sun sashi atsakiya.sunata faman hira da murmushi abun sha'awa. Nan ya zauna kan wata yar kujera sukuma ya umarcesu su shiga suyi abinda zasuyi koma saura su manta dasu Anty Humairah. Haba yaya ya za'ai mu manta. Nana an bata gari dama akwai ta da shegen kwadayi. Nan ta dinga zabe kala kala. Har mamaki Nana keba Amal. Yanxu nan duk wadan nan abubuwan da kika dauka ina zaki kaisu. Cikina mana kin sanni akwai san dadi. Allah bada sa'a. Ita kuwa Amal ice cream dauka da en cookies sai chocolate. Sannan ta dauko wani dan rose me kanshi cikin wani dan curve me design heart. Shi kenan abunda ta dauka. Nana kuwa ba'a magana. Nan suka fito Nana da tilin kayan ciye ciye Uthman kawai kalanta yake da mamaki. Nan akayi total suka biya kudin suka fito. Duka Uthman ne ya biya kudin dan kudin da Abba yaba Amal ma dawo dasu yayi. Sannan suka zuba kayan a motar suka shiga ya mata key. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Sosai hajiya ladi ta hadama Annur girki hadadde kala kala😋. Ko ina kanshi yake acikin gidan kamar gidan amare. Gab da kiran magriba tagama komai tanufi toilet dan yin wanka. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 Annur yana tashi daga office suka nufi wajan wani event fin bikin wani dn office dinsu. Saida sukayi sallah magrib sannan suka nufi gurin. Duk manyan mutane ne,suka ci suka sha saida akayi sallah issha sannan suka nufi gida. Yana tashi akan hanya ya kira Amal dan yasan zuwa anjima tayi bacci. Hira sujasha sosai sanna ya mata sallama tareda yi musu fatan alkhairi. Sannan ya shigo cikin gidan. Dama yariga yayi sallah shi,yana shiga mail zai duba koma ya tura wanda zai tura sannan ya kwanta. 🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺 Ta gama tsara kwalliyar ta tayi kyau iya kyau,sanye take cikin wani ha daddan less milk color da adon flowers green tayi kyau sosai. Ta kame saman kujera tana jiran Annur din. Da sallama ya turo kofar dakin tare da shogowa.batare da yasan da zaman mutun a hurin ba kai tsaye daki ya nufa. Tana jin sallamarsa taji wani dadi cikin ranta. Annur! Cak ya tsaya dan tama bashi tsoro. Amma!dama inasan magana dakai dan Allah ka saurareni. Batareda yace mata komai ba ya dawo da baya tareda zama saman sofa din dake falon. Dama ummin kace tabani sako,tace batanan in baka gantaba,kuma kwana zatayi. Batareda ya tambayi inda ya tambyi inda ta nufaba yace saita dawo. Yana kokarin mikewa ta ruko hannunsa tareda mikewa tsaye itama. Malama lafiya zaki rikemin hannu? Dan Allah karka tafi nayima abinci ka tsaya kaci mana kafin ka tafi. A koshe nake naci abinci sakeni. Amma Annur kasan irin tym din Dana kashe wajan hada ma dinner kuwa. Aibani nasaka kiba,ko kin nemi shawarata kafin ki girma saboda haka inma baki saniba yau kishani Har abada bazan taba cin wani Abu daya fito daga garekiba.kuma nace ki sakeni. Dur kusawa tayi agabansa tareda fadin. Haba Annur waikai wani irin tsana kamin hakane dahar kake tunanin haram tama kanka abunda ya fito daga gareni. Fisge hannunsa yayi tare da juyawa ya nufi dakinsa. Da gudu ta karaso gabansa tareda bude hannayanta tana fadin Mundin baka ce kana kaunataba zan kashe kaina. Tsayawa yayi yana kallonta tareda harde hannayansa. Ki mutu mana kinga kinyi asara dan duk wanda ya kashe kansa ya mutu kafiri. Kibani hanya na huce ko ranmu ya bace duka. Nasan abunda yasa baka kaunarka kana tunanin na girme ba kuma bazawara. Tana magana tana matsowa garesa Har suka kai jikin bango. NA yarda da baka kaunata,toh dan Allah ka bani hadin kai insha Allah zan zama me rufama asiri. Wani wawan mari ya kwada mata dan saida taga taurarin wahala.Har kasa ta fada. Nonsense! Ya huce tareda bude dakinsa ya shige ya turo kofar ya mata key. Kuka ta kamayi sannan ta mike saboda bakin ciki Lallai Annur ni zaima haka Wallahi saina cika burina akanka mu zuba nida kai. Daki ta nufa itama ta dauko key din motarta. Me aiki ta kira tareda umarta ta kan tasan yanda zatayi da wannan abincin sannan ta fice daga gidan. Zama yayi kan gado yana tunanin yanda zaiyi da matsala dake damun sa. Umminsa taxo da nata,itama wannna mahaukaciyar tazo da nata. Tsaki yayi tareda mikewa ya nufi toilet.. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 145-150 Nan ya amshi key din yayi gaba. Har bakin mota ta rako Sakina.sannan ta musu Allah kiyaye. Cikin motar suka shiga gaba dayansu.duk a baya suka zauna. Aa wai driver kuka maida ni,wata ta dawo agaba Wallahi ko Ku tafi a taxi. Nana tai carab ta dauka,Sakina koma gaba dan Allah,bansan zaman gabannan. Bayanda zatayi haka ta fito ta koma gaban,dan kunyar Uthman din takeji. Key yayima motar tareda barin gidan.nan ya rinka tambayarta inda zasuyi tana nunamai har suka isa. Bama nisa sosai gidan nata. Gurin kamar estates haka yake. Gaba tace suyi nan suka yi dn gaba kadan sanna suka tsaya. Mafi akasarin yn estate din duk yn makarnta ne ake kama musu gidajan wajan. Fitowa sukayi tareda gadin Ku shigo mana. Nan su Nana suka shiga shikuwa Uthman cewa yayi suyi Sauri su fito. Tana budewa cikin falo suka shiga. Falone dan madaidaici,komai na cikinsa White nd black ne.yayi kyau sosai sai kitchen da dinning karami a gefe sai kuma bedroom. Gwanin sha'awa ko su dakin ya burgesu,gashi komai angyarashi tsaf. Sai kanshin freshener yake. Nana ce ta zauna kan kujera tareda fadin wow! Gaskiya dakin nan ya burgeni kamar kar intafi. Sakina data cire jacket din jikinta da Vail din kanta. Ta zauna kusa da Nana tare da fadin aikuwa kafin Ku tafi saikinzo kin min ko kwana biyune pls. Amal tace karki samu damuwa zamuzo insha Allah. Me kukeso yanzu na hada muku. Tafdi ya uthman fa na waje,kuma tashi mu huce karya fara mana bala'i kinsan besan jira. Mikewa sukayi tareda fadin ai zamu dawo bayan muna tare. Masayar numb.sukayi sannan suka fito daga gidan. Yana cikin mota a zaune yana jiransu. Harnan ta rakosu sannan sukayi mata sallama suka tafi. Suna tafiya suna hira,wannan karan Nana ce taxauna agaba. Ya Uthman kamata yayi kadan kaimu gurin shan ice cream. Baza a kaikiba uwar kwadayi. Kai yaya dan Allah, Allah zan gayawa Aliyuna. Inye lallai yarinyar nan bata da kunya. Kana jintafa. Rabu da ita Amal ta kirashin daidai nake dashi ta kirashin. Sorry yyna dan Allah muje. Allah ban zuwa saikin kirashin Wallahi. Toh inna kirashi saiki sa ya kaiki. Toh.wayrta ta dauka ta fara kiran Aliyun. Yana dauka ya ta fara yimai kukan shagwaba. Amal dake kallan ta tarufe baki tana dariya,tafdijan ita Yawwa zata iya yima Annur wannan Abu. Nana dake rike da waya ta fara kukan shagwaba. Bbyna kaga ya Uthman wai baze kaini nasha ice cream ba.kayi mai magana. Shima kanshi Uthman din dariya ta bashi. Mika masa wayar tayi. Amsa yyi yana murmushi,wannan yrnyr Allah inaga kafin mubar kasar nan saina karyata. Kaikuma tana maka shagwaba Har wani rikicewa kake kana biye mata. Aliyu daketa faman dariya yace yimin shiru malan ko kai kasamu mai yimaka dadi zakaji. Yanxu de dan Allah badan itaba kuma badan niba akaita tasha. Dariya Uthman yayi tareda fadi kace Allah Wallahi da saide kazo ka kaita. Kaima kasan da ina nan da ni xan kaita amma dan Allah a taimaka. Ba damuwa zan kaita amma ka mata magana karta kuma. Insha Allah bazata karaba babanyaya,kwana nawane Har za'ana jamana rai. Ohk ja muku rai ake kenan. Aa ya kuri. Mika mata wayar yayi. Hello bbyna yace zai kaini ? Ze kaiki ki kwantar da hankalin ki sai munyi waya anjima. Amal dake baya tana game awayarta tana faman dariya kasa kasa. Nan ce ta juyo tareda fadin dariya kike mana ko Amal. Ba dole nayi dariya ba Nana irin wannan rashin kunya haka. Dallacan ya kajitafa,kina wannna maganar ahankali Allah ne kadai yasan yanda kike ruda boo dinki zakina min dariya. Hhhhhh! Kai Nana Nide ba haka nakeba. An gaya miki kowa irin kine Uthman yana magana yana kallan titi. Amma de Yaya kasan Amal nada saurayi. Tabbas ma kuwa,amma ita tanada kunya ai ba irinki bace. Hmmm! Ya Uthman kenan gwara nayi a fili kowa ya sani da in zauna ina boye boye. Ai saikiyita himma kina rashin kunyar.ya fada tareda yin parking kofar gidan. Amal ce ta bude motar tareda fita tana dariya. Amma de Yaya kaima kanka kas.... Malam Dallah fita kiba mutane gurin keko ciwo bakinki bayayi sai shegen surutu. Haba ya Uthman toh mutun Allah yayi masa baki saiyaki magana,ni Wallahi kuna bani mamaki. Naji jeki de Harta shige gidan tana faman mita. Tafdi yaga kokarin Aliyu da zai auri Nana koda yake shima ai haka yake murmushi yayi.tareda kulle motar ya nufi part dinshi dan Lokacin sallah magrib ya kusa. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 (4pm) daidai yafito daga meeting. Office dinsa ya nufa tareda zama,wayr shice tayi kara murmushi yayi tareda dagawa. Ahhh! Mutan Dubai ya candin. Kaide bari ai kayi missing. Allah ko mutumin kace kana jin ddinka. Ai barama kaji tun dazu nake kiranka amma nasan kana meeting. Wallahi kaide bari yanxu nan na fito.ya ake cikine. Ai wato gidan da muka sauka kaji na gayama anan Amal dinka take. 😳haba de!! Wallahi kuwa yanxun nan muka rabu dasu,munkai wata frnd dinta gida nida Nana. Na huce nayi sallah. Ai malam nima nayi mamaki sosai. Kaga yanda ta kara kyau ta yi kiba Wallahi tanajin ddi. Allah abokina. Wallahi da gaske baka ganta ba.ka kirata mana zata cema muna tare. Amma fa guy kawar nan tata tayi Wallahi. 😃Allh malam? Wallahi kuwa nima nan zan shiga kaga nima nan gaba kadan nazama magidanci. Gaskiya kuwa kaga ka huce gori.Amma nayi mamaki ko dama yr uwarku ce baka saniba. Allah kadai ya sani.zata iya yihowa hakan,dan ba kaga yanda suke ji da itaba. Gaskiya naji ddin hakan,ya su mum da Amarya. Wallahi duk suna lafiya qlau. Toh masha Allah sau anjima mayi waya bara na kira gimbiya. Ohk toh sai anjima din. Sannan sukayi sallama. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Suna shiga dakin alwala sukayi dan yin sallah. Bayan sun idar,Amal tace da Nana.ina zuwa Amarya. Murmushi Nana tayi tareda fadin saikin dawo. Falo ta fito,bataga kowaba tasan suna daki suna hira. Kitchen ta nufa ta Dora musu abinci marar wahala. Nan danan tayi ta gama,tana jerawa a dinning. Anty Humairah ta fito daga dakin. Ganin Amal harta gama abincin tace my Amal harkin gama kike nufi, Wallahi Anty, ai maras wahalane taliyane kuma dama akwai ruwan zafi a heater. Toh sannu da kokari Allah miki albarka ya kawo mata tagari. Kai Antyna.ameen ta fada tareda jin kunya. Sannan ta koma cikin daki.tana shiga ta tarda Nana na faman waya. Toh sarkin wa 8:30pm Har tayi saiki tashi kiyi sallah issha ko?. Dariya tayi tareda dagoma Amal hannu alama bayanxuba. Yayi kyau shi ba sallah zaiyiba kya sani. Ta fada tareda shigewa toilet. Tana fitowa ta sanya hijab dinta tareda tada sallah. Saida ta kusan idarwa sannan Nana ta yi masa sallama tareda mikewa ta sanya hijab dinta itama ta tada sallah. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Suna gama waya da Uthman ya fita masallaci dan yin sallah la'asr. Bayan sun idarne sun fito kabeer yake sanar masa cewa saura 3wks bikinsa. Ahhhh Ango kenan kace bikin ya matso Allah ya kaimu lokacin. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 Hajiya ladi kuwa yau da kanta tace zata shiga kitchen me aikin yauta huta.ita zatama Annur abinci. Nan yahau tunanin abunda zata girka masa. Harde ta gama yanke hukunci.kitchen din ta shiga dan duba abunda zata hada masa. Can kuma wata zuciyar tace da ita taje ta gyara masa dakinsa inyaso saita dawo tayi masa girkin. Dakinsa ta nufa ga mamakinta ta murda ta jishi a kulle.ta kuma murdawa amma still a kulle.tsaki taja tareda barin kofar dakin. Falo tadawo ta zauna tana tunanin abunyi. Danyau so take ta faran tawa Annur din rai. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Suna idar da salln. Amal tace da Nana taso muje muci abinci. Ba tareda tayi mata musu ba afalo suka tarda mum,Hakeem da Uthman da alama Anty tana kitchen. Zuwa tayi tama uncle sannu da zuwa sannan ta koma kitchen din itama. Aa Amarya ce uncle ya fada yana kallan Nana. Wallahi nice uncle Hakeem inayini Lafiya qlau kunzu lafiya ya kowa da kowa ya Ango da shirye shiryen biki. Tana murmushi kanta akasa tace kowa lafiya lau wallahi. Toh masha Allah. Mum ce ta kalleta tareda fadin ja'ira Ashe kinada sauran kunya ba dika ta guduba. Dariya duk sukayi. Hakeem ne yace aa kode kune Baku fashimce taba. Wata fahimta kuma Hakeem Allah bata da kunya. Humairah ce ta fito tana dariya tareda fadin dinner is ready. Mikewa duk sukayi kowa ya nufu dinning din dancin abincin. Amal da Nana ne sukayi serving kowa sannan suka zauna. Nan akahau cin abinci ana hira kowa na yaba dadin girkin Amal din.😋😋. Saida suka kusan karewa sannan Nana taceda Uthman. Ya yamaganar shan ice cream din. Harararta yayi tareda fadin baza'aba uwar kwadayi. Ammafa kayi alkawarin zaka kaimu ko Amal. Itade Amal murmushi take batace komai ba. Hakeem ne yace aa Ku barshi ya huta ni saina kaiku. Mum ce tace da Hakeem aa kayi zaman ka shi zai kaisu. Wallahi da kin rashi ya huta niba saina kaisu ba. Allah Hakeem ba inda za kaje ba kannan shi bane ya kaisu mana. Anty Humairah ce tace itama Nana da shegen San yawo ta hakura mana sai gone zatace sai taje wani shan ice cream saikace me ciki. Shide Uthman be kuma cewa komai ba. Illar sai kiyi Sauri Ku gama mu huce. Mikewa yayi daga gurin. Itama mikewa tayi tana dariya.ta kalli Amal, tareda fadin taso mana Amal. Mikawa tayi tareda bin bayanta.daki suka shiga tareda dauko Vail insu sannan suka fito. Hakeem ne yace ga kudin shan ice cream din. Nanace tace aa ka banshi ya Hakeem mungode. Tunda ke bazaki amshi kudina ba my Amal zoki amsa. Murmushi Amal tayi tareda fadin mun gode uncle sannan suka fita. A mota suka sameshi sannan suka karasa. Nan ce ta roki Amal da tashiga gaba dan haushin ta yakeji karya daketa. Dariya Amal din tayi sannan suka shiga. Ba wanda ya kula cikin su yama motar key tareda fita daga gidan. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki ( Zeenaseer😘) Dis page goes to you Ummie Jafar ( Autar mama😍). Allah kara basira ya barmu tare👩‍❤️‍💋‍👩 155-160 Waka yayi tareda fitowa towel daure a kugunsa. Zama yayi gefen gado yana tunanin ina kuma umminshi ta nufa.tabbas har yanzu akwai sauran aiki a gabansa zaita yimata addu'a dan tana bukatar hakan. Har kwalla yayi sabo da tausayin mahaifiyar tasa da irin wannan rayuwar da ta daukama kansa. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Washe gari Amal bata da lecture. Koda tagama abunda zatayi. Breakfast sukayi gaba dayansu suka nufi asibitin dubo Abba. Sosai yaji ddin ganin su nan Amal ta gabatar mai da rose flower data siya masa. Sunsha hira sun debemai kewa har suka dan jima sannan suka fito daga asibitin. Uncle da Uthman gari suka shiga su kuma suka nufi kasuwa dan fara siyayya. Sosai sukayi yawa dan gaba dayan su sun jigata. Koda yaushe kuwa Annur cikin kiran Amal dinsa yake susha hirar su ta masoya.duk Lokacin da Annur ya kira Amal Anty Humairah na lura da hakan. Sai kusan magrib suka dawo gidan dan ko girki baza su samu damar yiba nan Humairah ta kira Hakeem tunda su basu karaso gidan ba.dan su taho musu da abinda zasuci. Ko wance toilet ta nufa danyin wanka. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Sai bayan la'asr hajiya bilki ta dawo gidan koda ta shigo ba kowa falo,kara tajiyo a kitchen kai tsaye kitchen din ta nufa me aiki tagani tana aiki. Cikin girmamawa tayi mata sannu da zuwa. Bayan ta amsa take tmbyrta ko hajiya ladi na nan. Aa hajiya tun jiya da daddare ta fita kuma Har yanxu bata dawowa. Ohk! Annur ya fita office ke nan. Eh tunda safe ya fitan. Juyawa tayi dan taji mugun ddi da hajiya ladi batanan dan tasan zata iya yaudarar Annur din.dakinta tanufa dan sauke gajiyar da takoso a unguwa. 🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺 Tunda Annur ya fito daga gida office ya nufa dan yauma yana da meeting Har zuwa lokacin shiga masallacin juma'a. Shiyasa ya fita da huri. Yanxunma be ddi da fitowa ba. 🔱🔱🔱🔱🔱🔱🔱 Wednesday (3:00pmNG)% (6:00pm Dubai) 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Annur ya Riga ya dauki break na 2wks a office dan haka sai faman shirye shirye yake mafanyi. Da har ya matsu goban tazo dan ji yake kamar ya janyo ta. Koda yaushe yana tareda Amal dinsa a fone ba dare ba rana gashi sunyi wani irin sabo da juna. Ya riga ya gayama umminsa kan cewar yana da meeting a Dubai kuma sati gida zaije yayi. Da ker ta yanda ya tafi dan sun riga sun canza magana da Maman Sara. Ranar Sunday zasu shigo garin kanon.shiyasa bataji dadin tafiyar tasaba dan so take su saba da Sara sosai. Shikuwa dadi yaji dan tunkafin ya hadu da ita yaji ya tsaneta ainun ko ganin ta baya sanyi ballantana asa maganar aure. Hakanan ta yarda ba dan tana soba,saidan tana San aikin nasa kuma batasan ya samu matsala da aikinsa. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 Ita kuwa hajiya ladi data tafi gidan wata kawarta ta koma dan ta dauki shirinta Mundin ta dawo Wallahi sai ta aure Annur ko ita ko hajiya bilki. Hakan yasa hajiya bilki jin ddin tafiyar hajiya ladi dan itama kanta saitafi jin ddi kuma tafi sakewa dama ga baki zatayi. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Lokacinne Amal ta shigo gida dan daga makarnta ta dawo. Dan gaba daya kwanakin batanan tana makarnta, dan haka suke fita siyayya babu ita hakan baya mata ddi dande babu yanda zatayi ne. Haka itama Nana batajin ddi in Amal din tatafi makaranta dan gidan baya mata dadi ko kadan.dan sunyi wani irin sabo kullum suna tare cikin raha. Dan haka itama yau Amal na cikin farin ciki dan murnar gobe habibeen nata zai shigo duk da goban tana da test a skul Amma tana cikin farin ciki. Jikin Abba kuwa yayi kyau sosai dan yanxu Har tafiya yanayi kuma abinci ko wanne yana iya ci. Sosai su Amal na kai masa ziyara kuma hakan nayi masa dadi. Dana Amma kusa sallamarsa dan jiki alhmdullh yayi kyau sosai. Sakina ma na yawan zuwa gidan dan itama sun zama kamar yan uwa. Hakanne ya bama Uthman damar bayyana mata abunda ke cikin ransa kuma tayi accepting nasa sosai suma suke zuba soyayyarsu. Hakan yayima mum dadi data samu labari wajansu Nana. Dan ta yaba da hankali da nutsuwa na ya rinyar.dan tana komawa zata sanarma Abban sa dama shima ya matsu dan nasa yayi aure. Sai suje gidan su sakina su tambaya dan basa San abun yadau lokaci. Uthman ya samu uncle Hakeem ya sanar masa bukatar Annur nasan auran Amal din kuma ya sanar masa yanda Abban Amal din ya dauki abun da kuma tsakanin Abba da ita ummin Annur din.kuma ya nuna masa yanda Annur din da kuma halayyarsa take. Yakuma nunamai yanda suke neman taimakon sa,wajan neman auranta gun ddi. Sosai Hakeem yaji ddi dan yanda Uthman yayi masa bayanin komai batareda ya buya masa wani abuba.kuma shima kansa yasan hajiya bilki da ladi gaba daya. Kuma yayi masa alkawarin insha Allah zasu samu narasa. Zaijema da Abban Amal maganar inya fito daga asibitin. Uthman yaji ddi sosai kuma yayima uncle din godiya. Annur ya kira duk ya shaida masa yanda sukayi da uncle Hakeem. Shima yaji ddi sosai yayi ma Allah godiya Yakuma yima Uthman din godiya daya ciki aboki na gari. 🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺 Tana shigowa gidan danjin shiru tasan ba kowa daki ta nufa tayi wanka. Kitchen ta nufa kafin ayi sallah. Girki ta dura musu sannan ta koma daki. Bayan ta idar da sallah ne taji karar shigowar su. Batareda ta cire hijab din jikin nata tafito falon.sannu da zuwa tayi musu sannan suka shiga da kayan dakin dasuke ajjewa. Amal ta kalli Nana data baje akujera.sannu Amars ya hanya. Harara ta watsa mata ta wasa tareda fadin zan kamaki shine kika boyemin wayata ko. Ba kowa a falon sai su biyu dansu su mum sun shige daki. Haba tawan banasan kina tafiya kina waya danna rage miki wahalama. Pilon dake kusa da ita ta cilla mata tana dariya. Itama dariyar takeyi ta shige cikin tana fadin sowie Aliyu's wife to be. Hahhha Wallahi zaki shigo dakin ki sameni kuma kema yau babu waya da Annur.. Sannan ta shige dakin. Amal dake cikin tana karasa girkinta tace lallai ma aida kin kasheni dama kina gani yau skul ta hanamu waya.. Bata jimaba ta gama girkin ta jera kan dinning sannan ta koma dakin dayin sallah issha. Lokacin data shiga sallah Nana takeyi dan haka itama sallah ta tada. Kusan atare suka idar. Saida suka shafa addu'a sannan Nana ta kalli Amal da hararar wasa. Allah Amal baki da mutunci yanzu ko wani hali kikesan Aliyu ya shiga.kuma gashi bama tareda ya Uthman balle ya kira shi. Dariya tayi ciki ciki.tareda mikewa tana fadin haba uwargida sarautar mata gashide ki kirashi ki cinyeshi.ta dauko mata wayar daga cikin Jakarta ta mika mata tana dariya. Nana dake zaune tana jira ta miko mata wayar. Tana mika mata ta janyo ta tana dariya tana mata dukan wasa. Mum ce ta turo dakin da sallama. Daga bakin kofa ta tsaya tana kallansu. Allah ya shiryeku kullum saikace kananun yara Ku dosa dukan juna. Amal data janye jikinta daga na Nana tana dariya gashin kanta duk ya hargitse ta kalli mum tace Wallahi Nana ce mum.ta karashe maganar tana kallon Nanar dake zaune itama kanta ba ribbon. Mumce tace aidama nasan sai ita. Nana ta kalli mum kamar zatayi kuka. Wallahi Amal cefe ta tafarmin da wayata makaranta kuma bamuyi waya da Aliyu ba. Baki ta rike da hannunta Oo ni yrnan! kunga Ku taso kuci abincinku. Toh mum Amal ta fada tareda gyara gashin kanta. Ni sai nayi waya da Aliyu tukun. Mum ce ta shigo dakin ta nufi Nana tana fadin zaki tashi ki huce kosaina ci kwal baki keda wayar.. Da gudu suka fito falon suna dariya😆😆 Sai bayan sungama cin abincin sannan suka dawo falo danyin hira banda Nana data shige daki danyin waya. Uncle Hakeem ne ya kalli Amal sannan yace da ita naji duk abunda Uthman yace dani game da yaran dayace yana sanki. Yanzu ga Uthman, Antynki harda Maman Uthman. Zansamu Abban ki da wannan magana Amma kafin nan inasan naji da bakinki in kina kaunarsa. Amal da kanta ke sunkuye a kasa cikin kunya kanta na can kasa. Tace eh! Uncle! Yauwa toh alhmdullh kinga yanxu inada confidence din magana da abban ki. Anty Humairah da mum ma duk sunji ddi musamman ma Uthman. Mum ce tace tabbas Amal tayi dacan miji dan Wallahi Annur yarone mai hankali da kuma kirki.dan Hausa na fadin albasa batayi halin ruwa ba. Saide fatan Allah ya sanya alkhari aciki. Kowa de ameen yace. Anty Humairah ce tace,aimu zama be kamaniba zan aurar da yr guda nike zaune haka. Dariya de suke ita kuwa Amal diki ta shige dan kunya.. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 160-165 Daki ta shige da sauri tana dariya itama. Tabbas taji ddi kuma Allah yasa Abban ta ya amince. Nida fans mukace ameen ya Allah. Saida sukayi waya sannan suka kwanta. 🔱🔱🔱🔱🔱🔱🔱 Thursday morning (7:00amNG) (10:am Dubai) 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Annur ne yafito cikin shirinsa tsaf na tafiya afalo ya tarda umminsa zaune kan daya daga cikin kujerun dinning din.da alama shi take jira da batasan ya tafi beyi breakfast ba. Har kasa ya durkusa tareda fadin Ummi ina kwana. Lafiya qlau Annur harka fito ne? Eh Wallahi Ummi. Toh Allah ya kiyaye hanya ya saukeka lafiya,naso tare zamuyi tafiyar nan Amma nayi alkawarin bazan komaba sai bayan bikinka. Yanxu de kafin katafi kazo kayi breakfast tukun sai muje na anjeka a airport din. Bai musa mataba ya mike tareda zama kan kujerar,nan ta mika masa abincin Shide kawai yana cin abincinne badan yana soba. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Tana tashi da safe tayi dukkan abunda zatayi sannan ta shirya cikin shirin makarantar ta. Dan tasan ba wanda ya tashi acikin gidan sai uncle Hakeem shima dan fita zaiyi. Dinning ta nufa tayi breakfast dinta dan tasan uncle ya dade da fita tun 7am. Bata dau lokaci ta gama sannan ta fice zuwa makarnta dan yau tana da test. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Yana gamawa ta dauko mayafinta da key din mota suka tafi. Suna tafiya suna hira sama sama,dan duk hirar tata akan bikin shine da Sara. Shikuwa hankalinsa ma baya gurinta kawai tunanin yanda Amal zatayi inya ganta. Har suka isa airport din tana ta faman zuba ita kadai danshi bama jinta yake ba. Basu jima ba aka fara kiran masu tafiya nan danan suka gama komai,saida suka kara sallama da Ummi sannan ya huce. Saida jirgin su ya tashi sannan tabar airport din. Cike da so da kauna dakuma kewarshi dazatayi. 🔱🔱🔱🔱🔱🔱🔱 (3:19pm Dubai). Jirgin su Annur ya sauka. Kai tsaye daga airport din hotel ya nufa nan yayi bucking din komai aka bashi dakin dazai zauna. Nan ya haura da kayansa ya shiga dakin. Iya haduwa dakin ya hadu komai a gyare an kayatashi sosai gwanin ban sha'awa. Kayan shi ya anje nan ya nufi toilet dan watsa ruwa ajikinsa. Bayan ya fito daga toilet din daure da towel a kugunsa,wayar shice da take ringing ya nufeta dan duba me kiran. Uthman ke kiranshi murmushi yayi ya dauka. Ya mutumin harfa na sauka,yanzuma na kama hotel yanzuma nayi wanka zan shirya na taho. Yawwa pls kayi Sauri kaganta can tana faman jiranka. Ohk insha Allah gani nan. Maza yayi ya shirya cikin ka nanun kayan da suka amsheshi yayi kyau sosai ya feshe jikinsa da turare sannan ya fita.yana fitowa wani dan gurin saida gold ya tsallaka ya siyoma Amal wani zobe me kyau sosai dan karami daidai hannunta sannan ya sanya a aljihunsa. Wayar shi ya Ciro ya turama Uthman address din hotel din sannan ya kira shi. Pls kazo ka daukeni kaji. Baka da damuwa gani nan zuwa. Bai wani dau lokaci ba ya karaso wajan da Sauri ya fito sukayi hugging din juna suna murnar ganin juna. Sannan suka shiga cikin motar. 🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺 Amal kuwa tunda aka taso daga makaranta, gida ta nufo cike da murna. Tana zuwa suka hau yimata tsiya dan kowa yasan da zuwan Annur din. Toilet ta nufi tayi wanka ta fito. Data dawo anan ta tarda Sakina ita da Nana suna mata tsiya Har daki suka bita. Kwalliya ta shiga tsan tsarawa tayi kyau kamar ka saceta ka gudu. Wani hadaddan blue green din material Anty Humairah ta dauko mata yana da adon flowers silver. Jewelry silver tasa tayi kyau ainun sannan ta sanya silver plat shoe da mayafi silver OMG! I can't explained how pretty she look. Su Nana dake zaune kan gado kallon ta kawai suke dan tayi mugun haduwa. Sakina ce tace anya kuwa yau Annur bazai zauceba irin wannan haduwa haka.gaskiya Amal kinyi kyau ba karya. Masha Allah Nana ta fada tana daukar ta photo. Sannan suka fito falon. Anty Humairah ce ta taso da Sauri ta rungume Amal din tana fadin tubarakallah Masha Allah. Mum ce tace dole Ku zautamin yarona irin wannan ado haka. Dariya suka sa gaba daya. Lokacin ne Uthman yayi dakin a daidai kofar gidan. Amal ce ta dafe kirjinta tare da rufe idanunta. Nana ce ta rike hanci tareda ran gada buda. Megida ya karaso Angon Amal ya iso. Mum ce tace kede Nana Allah ya shiryeki. Dariya sukayi gaba dayan su. Annur da Uthman ne suka shigo da sallamar su. Batare da Annur yaga Amal din ba ta shige daki da Sauri tare da rufu kofar. Jingina tayi da kofar ta rike kirjinta tana numfashi sama sama. Fuskar ta dauke da murmushi dan wani irin farin ciki takeji wanda bazata iya fasalta irin shiba. Hawaye taji suna sauko mata. Ita kanta ta rasa hawayen menene. Zama sukayi saman kujera. Fuskar shi dauke da murmushi ya russuna ya gaida kowa na cikin falon. Sosai Anty Humairah taji ya burgeta.kuma taga kamala da nutsuwa a tare dashi tabbas Amal dinta tayi dace.itama kanta saida tayi kwallar farin ciki. Bayan sundan jima ana hira sannan sukace bara su basu guri.akira masa Amal din tazo ta zuba mai abinci. Uthman kuwa inkiya yayima sakina dasu hadu a waje. Su mum daki suka koma.ita kuma tabishi suka fice. Nana ce tashige dakin dan kiran Amal din. A gaban mudubi ta ganta tana gyara fuskarta. Oo! Ni Amal ko fuskar za'a canza.sai faman kwan kwalarta ake. Itade murmushi tayi batare da tace komai ba. Toh kije inji habibeen naki ba kowa a folan sai shi kadai. Batareda tace komai ba ta gyara mayafinta Nana na mata dariya ta fice daga falon. Zaune ta ganshi kan kujera yana duba fone dinshi. Da sallama ta karaso wajan cikin murya mai kayatarwa sannan ta zauna kujerar dake facing dinsa. Shima amsa sallamar yayi tareda dago kansa ya sauke ida nunsa kan fuskarta. Idanunta arufe da suka sha kwalliya da eye-shadow, eyelashes dinta Zara Zara da suka karama fuskars kyau.tareda karema fuskar kallo data sha make-up. Gaba dayan ta tayi kyau komai nata mai kyaune. Barazai iya dena kallontaba. Jin shirun datayine ya sanyata bude idanunta. Aikuwa suka hada Ido. Da Sauri ta sufe su tana murmushi. Shima murmushin yake.ahankali ya furta sunan ta. Amaaalh kunyata kikeji ko. Ahankali ta jirjiza kanta. Toh inde ba kunya ta kike jiba ki bude idanunki pls. Bude su tayi suka kuma hada idon. Wannan karan kasa sauke idon tayi daga kallonsa.sun jima ahaka. Kafin tace katashi muje kaci abinci kaji? Ki bari mugama hirar tukun kinga inna gama cin abincin tafiya zanyi. Batace mishi komai ba taci gaba da wasa da yatsun hannunta kanta akasa. Tasowa yayi ya karaso gabanta ya tsugunna. Dago da kanta tayi tana kallan fuskarsa. Hannunta ya kamu tareda fadin kyauta zan miki Amal dan na nuna miki irin San da kaunar da nake miki Amal. Zuciyarta tayi alkawarin fada miki halin datake ciki tsawan lokaci Amal. Kallan shi kawai takeyi gaba daya burgeta yakeyi kamarta hadiyeshi haka takeji. ❣❣❣ 💘 I can't explained hw i feel about u Amal. I feel like a lost child when ur not around me Amal. Nothing feels right when u r nt around me. Pls Amal don't Ever leave me.ya fada tareda kara matse hannunta cikin nashi. Gaba daya taji tausayin sa ya kamata kamarta rungume shi ta lallashe shi. Kwallar data taru cikin idonsa itace ta dugo kan hannunta. I Lov u Amal ya fada. Hannunsa yasa cikin aljihunsa ya ciro zoben nan ya kama dan yatsan dazai sa mata. Ya dago da kansa shima yana kallonta zoben da hannunta na rike a hannunsa. Amal I don't know wat is life wit out u,I'm mighty glad dat god gave you to me.my Amal I feel suffocated when u r far away frm me.pls don't ever leave me cwt hrt. Hawaye sosai yakeyi sannan ya sanya mata zoben. Itama hawayen ne yake zobo mata.hannu tasa ahankali tana kogemai hawayen fuskar tashi. Muryar na rawa itama tace . I promised to b wit u till end of my breath Annur no matter wat it takes,I will never give up d relationship we share fr anything in dis world. I Lov u nd I will always Lov u bby💕 Mikewa yayi ahankali tare da manna mata peck a goshinta. Rufe idanunta tayi sauran kwallan da be zubo ba ya karasa zobowa. ❣❤❣❤❣❤❣ Duk wanda chapter en nan tamai dadi pls show me shoki💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼😂😂 Lovs u oll Muah......💋 Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) ⚜⚜⚜⚜ I dedicated dis page to u pple u show me Lov nd care I rwwly appreciate ur kindness, hospitality. I will always remmbr u any I go ur d bst ever😍 My special tnks to u ummiekhaleel,dimples, leemcy nd maman Na'aiym.nd ma my 😍muah...Autar mama💐. 165-170 Hannunsa takama har izuwa dinning ta zaunar dashi kan kujera tana kallansa tana murmushi. Abincin ta shiga zuba masa sannan ta tura gaban tareda fadin Bismillah! Dago kansa yayi ya kalleta. Ta tsaya tana mai murmushi sannan ta dan bata fuska alamun yaci. Murmushi shima yayi sannan ya sanya spoon daya na abincin a bakinsa tare da rufe Ido da alama yayi masa ddi. Zama itama tayi kujerar dake facing dinsa.tana kallansa. Komai nasa birgeta yake yanda yake cin abincinma acikin nutsuwa. Ajikinsa yaji kamar ana kallansa. Dago da kansa yayi suka hada Ido. Murmushi ya kuma yimata tareda daga spoon din hannunsa alamun ko zataci. Girgizamai kanta tayi alamun aa ta koshi Shide yaci. Cigaba dacin abincin sa yayi,Har saida yaji ya koshi sannan yace mata ya koshi. Zaro Ido tayi sannan ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka tace dan kadan fa kaci. Dariya yayi tare da kwaikwayar maganarta Wallahi nima na koshi. Rufe fuskarta tayi da tafin hannunta alamun jin kunya. Toh kinga dare yanayi zan huce ki kiramin su mum da Antyn muyi sallama. Tsayawa tayi tana kallansa alamun bazataba. Dariya yayi tareda tsayawa kusa da ita ya kamo hannunta. Haba mine! Bayan koda yaushe muna tare.hannunta ya dora kan kirjinta dede zuciyarsa ur always here bby.kinji cwt. Taimaka ki kirasu kinji. Kamar zatayi kuka ta nufi corridor dakin Anty Humairah. Dakin ta tura da sallama tareda fadin Anty yace zai huce. Toh bara muje muyi sallama gashi har yanxu uncle bai dawo ba.sannan suka biyota suka fito falon. Anan suka tsaya suna sallama da su mum. Daki Amal ta shiga Nana nakan gado tana waya kanta ta haye tana dariya. Dagowa itama tayi tana dariyar Aliyu ta cema ai matar Annur ce ke damunta ta zuwa ta kashe wayar Ya akai Juliet Har Romeo din ya tafi. Hahhha banasan iskanci ke kuma laila ko za'a ce miki.pls tashi kisa hijab zamu kai sakina gida. Ohk! So Amal ansha Lov sai rawar jiki ake ta mike tana dariya. Kede kika sani kinga nama tafi saikin fito. Tana fitowa falon su mum harsun koma daki. Wajan ta nufa zaune ta gansu su uku Har Sakina Uthman nama Annur din tsiya. Da sallama ta karasa wajan nasu. Uthman ne ya kalli Annur tareda fadin ga Queen din kanan ta iso kuyi sallama kafin parrot ta fito nasan itama zatace saita bimu. Tashi yayi ya karasa wajanta.toya bbyna zan huce saikuma gobe zamuje asibitin insha Allah Uthman zai dauke Ku inyaso saimu huce ko?.ya karasa maganar yana leka fuskar ta. Allah ya kaimu toh amma ai zakana zuwa ko? Me zai hana dama aidanke nazo kuma ina tare dake. Nana ce ta fito tare da fadin toh masoya saiku tashi kunsan de dare yayi ko?. Gaskiya kam Annur ya fada yana dariya. Uthman ya fito da mota suka shiga dukkan su auka nufi hotel din da Annur ya sauka baya sun sauke shi suka nufi gidan sakina. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Tunda Annur ya tafi gidan ya dena yima hajiya bilki dadi gashi hajiya ladi bata nan. Wayarta ta dauko tare da kiran Maman Sara. Bayan sun gaisa ne take tambayarta ina sirikar tata. Wallahi gatanan akwance kinsan ta akwai San jiki. Dariya tayi tareda cewa ai haka akeso yanzu yaushe zaku taho kenan. Dama munyi dake ai sat.zamu shigo. Toh Allah ya kaimu kinsan Annur din bayanan yaje Dubai meeting gidan duk baya min ddi Wallahi. Allah Sarki karki samu damuwa ai muna kan hanya nan da sat.zamu shigo. Sannan sukayi sallama. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Washegari dukkan su suka nufi asibitin dan dubo Abba. Annur shiga manyan kaya yayi. Harda su mum aka tafi uncle Hakeem ne kawai yace zaizo ya tarda su. Abba yaji dadin zuwansu gaba daya yayi murna sosai. Kuma be nunawa Annur din komai ba duk da yaganeshi Amma saiya basar. Hakan yayima kowa ddi duk da sunsan tsakanin su Annur da Abban ba shiri. Sun jima azaune Nana natafaman labari ana shan dariya dan harsun saba da Abban. Uncle Hakeem ne ya turo kofar da sallama sannan ya nemi guri ya zauna kan kujera suka gaisa da kowa sannan yayima Abba ya karfin jiki Har yake gaya masa on Mon zasu bashi sallama kowa yaji ddin hakan. Dakinne yadanyi shiru nadan wani lokaci. Hakeem yayi gyaran murya tareda fadin muktar da fatan ka gane yarancan ya nuna Annur da hannu. Tabbas na ganeshi ba dan gidan hajiya bilki bane. Alhmdullh nagode Allah daya yadamu anan gaba dayan mu. Sannan yace muktar,Uthman yamin bayanin komai kuma ko kadan bai boyan wani abuba. Kowa da yake gurin nan ya shaida da hankali,nutsuwa, ilimi,tarbiya na Annur. Daidai da wannan yarinyar ya nuna sakina da take Baku wace ana gurin tasan wanne Annur. Kowa kai yake dagawa alamar tabbas. Duk inda uba yakesan nemawa yarsa miji na gari ya samu kamar Annur toh fa ya godema Allah. Sabo da haka ni ina ganin kamar ubane agurin Amal. Kuma bana fatan yimata auran dole dukkan su nan shaidane sunsan yarinyar nan tana kaunarsa. Shiya nayanke shawarar acikin asibitin nan zanyi maganar da sai ka fito amma tunda Allah yasa daranmu da lafiyar mu ayi maganar. Ni Abdul Hakeem amatsayin uba agurin Amal kuma waliyinta nabama Annur ita halak malak. Sannan ya juyo gurin Abban Amal da yake murmushi. Yace ko kana da ja.dariya yayi tareda fadin nina isa.insha Allah ni zan zamar masa waliyi ma. Duka dakin dariya sukasa Annur kuwa harda kwallar farin ciki. Kai hausawa na cewa abari ya huce shike kawo raban wani inji uncle sannan ya dora da fadin bani sadakin Amal ahannuna tun ina dare inyau nine gobe bani bane. Jikin Annur Har rawa yake yama rasa me zaice dan ddi.haka zalika Uthman ma kai gaba daya illahirin yan dakin kowa yaji ddin wannan Abu. Hannunsa yasa cikin aljihunsa tare da Ciro duk kudin jikinsa Uthman ma ya hada da nasa suka mikawa uncle kudin duka. Alhmdullh kowa ya fada sannan uncle yace Amal yar gata ce nasanya bakinta nan da wata biyu insha Allah muna mana. Gaba daya dakin suka ce ameen. Sannan suka mike dan tafiya masallacin juma'a. Da gudu Amal ta mike ta nufi Antyn ta rungume ta tanajin ddi itama da din takeji. Nana ce tace ya Humairah in an idar da sallah inasan mukuma shiga kasuwar inasan kara wasu abubuwa. Harararta tayi a wasa tare da fadin ai yanxu muma saide a rakamu siyayyar ba muyi rakiyarba. Dariya suka sanya duka dakin. 🔱🔱🔱🔱🔱🔱Saturday (2:30pmNG) (3:30pmDubai) 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Motace tayi parking kofar gidan hajiya bilki. Sara da mamantane suka shigo cikin gidan Masu aiki na biye da iyayen kayansu. Sara tayi maza rungume hajiya bilki tana dariya. Sannan Ku da zuwa barka da isowa tun daxu naketa zuba ido. Wallahi kuwa halin tafiya gamu de mun iso. Sara farace doguwa siririya bata da shape ko kadan kanta kullum cikin kitsan gashin doki,gashi bata da kunya ko kadan. Zama sukayi kan kujera tana wani kallan dakin daidai tana yatsina fuska. Kallan hajiya bilki tayi fuskarta ko murmushi babu. Hajiya ina room en dazamu zauna dan Wallahi na matsu inasan hutawa. Sallama hajiya ladi tayi tana taunar chew gam.tsayawa tayi tsakiyar falon tana kallan su ahulakance. Sannan ta kalli hajiya bilki tace ni zaki hula kanta bilki zaman amanar da mukayi dake Ashe na muna furcine. Kinban mamaki kuma Wallahi inde ban auri Annur banga yr iskar da zata aure shiba. Maman Sara ce tace ke dakata karki kuma kiran yata shegiya da ubanta. Juyowa hajiya ladi tayi tareda kallan mamansara tana harararta. Ke kuma suwa ina maga zaki sakomin baki. Ni a uwar matar Annur. Hannu tasa ta dauketa da mari. Sara dake zaune tana danna waya ko kallan hajiya ladi batayiba tunda tashigo itama ta kwadama hajiya ladi mari. Ki kin isa ki dake uwata narabu dake. Cike da mamaki hajiya ladi ke kallan Sara hannunta kan kuncinta. Ni kika mara ? Lallai yarinya baki sanniba ta fada tana cire dankwali,mayafi da alama dukan Sara zatayi. Nan ta shiga dukan Sara kamar Allah ya aikota dama ba wani karfi Sara ke garetaba. Maman Sara da hajiya bilki su suka shiga kwatr Sara. Da su kaga Abu yaki karewa sai suka taramma hajiya ladi gaba dayansu... Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 170-175 Dukan tsiya suka mata sannan ko wacce taja baya tana nishi. Da ker tamike tare da hada kayanta ta kalle so daya bayan daya ta nuna kanta da hannunta. Ni kukama haka ko zaku gani sannan ta juya ta fice. Sude ba wacce tace uffan kawai binta da kallo sukayi harta fice. Sara ce tajuyo tareda galla musu harara sannan ta shige cikin daki. Mamantama bin bayanta tayi sukabar hajiya afalon. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Sukuwa su Amal rayuwa tayi musu ddi kullum suna kasu wajan shakatawa kullum basa gida koda tana makaranta tana dawowa zasu fita. Ga wata soyayya da sukeyi ita da Annur da kuma sakina da Uthman.haka zalika tare zasu dawo gida da sakina.shiyasa Amal din batajin ddi dan zasuyi gaba bayan 1mnth ta gama exam dinta zasu tafi bikin Nana kuma mum tace maybe inta sanar da Baban Uthman ahada dana Amal din. Abu kamar wasa yauda gobe ba huya. Yauta kama Thurs su Annur zasu dawo gida gaba daya Amal harta fada dan kewarsu da zatayi musamman Nana da suke kwana tare su tashi tare. Tasha kuka haka da zasu rakosu airport sunsha kuka suma dan kowa saida yayi kwalla. Har Abban Amal aka rako su airport din.saida jirgin su ya tashi sannan suka dawo gida shima Abba ya huce gidansa. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Sai dare suka sauka,kowa ya kama gabansa. Nana,mum da Uthman gida suka nufa dama sun Riga sun turo da kayansu tun ranar Tues. Haka Annur shima ya nufi gida itama sakina haka. Kowa yana kewar kowa.cikin daran Annur ya nufi kano dan wani jirgin yayi bucking 11pm zai isa kano. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 Lokacin da Annur ya shigo gidan Har sun riga sun kwanta dan haka dakinsa ya nufa ya kwanta da ji yake kamar an yimasa duka. Suma su Uthman din haka. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Time din dasu Amal suka dawo gida Lokacin ne ta kuma kewar su gaba daya gidan yabar mata ddi. Haka data shiga dakin sai tana ganin kamar Nana haka ta dinga kwalla Har saida Anty Humairah ta dinga lallashinta tana bata baki akan suma sun kusa tafiya kowama ya huta. Toh in kina kuka Amal kemafa aure zakiyi kuma ki tafi ki barmu mukuma ya kike tunanin zamuyi saboda haka ki share hawayen ki dama Hausa wa na fadin sabo tarkwan wawa. Hakade tayita nuna mata da kuma lallashinta har ta kwantar mata da hankali sannan ta barta tayi bbci. Washe gari bata da lecture dan haka bata tashi da huriba. Har kusan 11am.sannan ta tashi tayi breakfast sannan tayima Anty duk abunda zatayi sannan ta dauko littattafanta dan on Mon.zasu fara exam. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Shikuwa Annur koda ya dawo daga sallah asbah baccinshi ya koma dan bazai je sallah ba. Koda umminshi ta tashi da safe batasan ya dawo ba.breakfast sukayi ita da bakinta sannan Sara ta haye kan kujera. Sukuma shiryasa sukayi dan zasu fara shiga kasuwa. Sai kusan 1pm sannan ya tashi yayi wanka ya nufi masallaci dan sallah zuhr.koda ya fito falo ba kowa hakan yasa yafice warshi. Saida ya dawo daga sallah yana shigowa falon da sallamar sa. Tana zaune kan kujera taci uban Riga da wando Jean ta dame duk da bata da jiki. Kanta ba dan kwali.tazubo da kitsan nan kanana. Sai kallo take abunta bata wani damu da sallamar da akaiyiba. Ko kallan inda yake bata yiba,shima kuwa haka yayi hucewarsa kan dinning. Ganin babu abincine yasa yakoma dakinsa key din motar shi da fone dinshi yayi sannan ya fita daga gidan. Tabe bakinta tayi tare da fadin lallai yaro kana da aiki inde saina kulaka zaka yimin magana waikai dan jijji dakai toh Wallahi na fika.mu zuba nidakai shege ka fasa in banda mama ta nace ubanme zanyi dakai😆😆(kinji fa). Cikin gari ya nufa dan bama yasan dawo wa gidan sai dare. Dan gama daya yama matso yayi auran ko yabar gidan gaba daya duk abi an takura masa wai kamar shi bashi da right na zabar macan da zaiyi harsai anzabamai wannan. Kuma umminshi ta rasa wanda zata zaba mai sai wannan me kama da maxana ko hankali ma bata dashi wama ya sani ko arniyace.😆😆... 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 Koda su hajiya bilki suka dawo Sara bata gaya musu Annur yana nan ba kawai shiru sukayi. Sai bayan issha sannan ya shigo gidan dakin umminshi ya nufa da sallama ya shiga dakin dukkan su suna zaune kan kago suna hira. Bayan ya gaida su. Take tambayar yaushe ya dawo sai kawai ya cemata daxu yq shigo garin dan yaga alamun bata saniba. Sannan ta gabatar masa da Sara da mamanta ,shide ba abinda yace ya mike yabar dakin. Sara tashi mana ki bishi ko gaisawa ce kuyi. Gaskiya ni mama ki rabu dani shi baimun magana saini zan masa. Shiru tayi ta rabu da ita dan taga alama batasan Annur din itade lallabata zatayi dan so take ta aure Annur din koba komai tasa ta sato mata dukiya. Ita kuwa hajiya bilki batasa bakiba cikin zuciyarta tace lallai kuwa yarinya zaki dade bai kula kiba kuwa. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 AMAL kuwa rayuwa taci gaba kullum tana cikin samun kulawa kuma Anty ta suta faman shirin dawo wa gida Nigeria dan bazasu komaba sai bayan bikin Amal din sai faman siyayya suke mata ana aikowa gida. Kullum basa zama suna yawa sayan kaya Har Abban ta duk abunda ya samo na Amal ne. Yanzu kuwa jarabawa ta mika alhmdullh Amal tana kokari sosai kuma kullum suna waya da su Nana dan Har ta shaida mata tareda sakina za'ayi bikinsu Har an tabayo kuma ba'asa bikin da nisaba komai rana daya Dana Nana. Sosai Amal taji dadi. Kullum suna waya da Annur in basuyi sau 10 a rana ba sayi sau 7 .Amma bai taba gaya mata umminshi na shirin yimasa aure da wataba soyayya suke hankali kwance. Dan yanxu saura 1wk su gama exam kuma ranar da suka gama washe gari zasu taho 9ja. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 Su nan da sakina sunan sunata faman shiri dan sunzama kawayen juna Har sun matsu amal din ta dawo itama. Haka ban garan su hajiya bilki komai na tafiya daidai matsala dayace Har yanxu Ango sunki ganawa da amaryarsa Sara. Shikuwa hakan ko ajikinsa illa ddima da yakeji. Kuma bikin yanda suka sakashi ya kama rana daya danasu Nana. Ban garan hajiya ladi itama tana nan tana shirya tsiyarta tace inde da ranta Annur bazai auri wata ya mace inba itaba. 🔷🔷🔷🔷🔷🔷🔷 Tun kafin su iso 9ja Amal ta fara shan gyaran amare. Yaune ranar da tagama exam dinta kuma yayi daidai da zaga yowar shekarar haihuwa tar 21 kenan. Uncle Hakeem ne ya hada mata yr liyafa agida iya yasu yasu Anty Humairah ta hada mata cake sukasha shagalinsu kowa cike da murna da farin ciki gobe sai gida. Karfe 10am jirgin su Amal zai tashi daga Dubai zuwa Nigeria dan haka duk an sanar da juna da abokin arziki. ✈✈✈ Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 175-180 Washe gari tunda safe su Amal suka gama duk wasu shirye shiryensu gaba daya komai sun tsara. Sai bayan sun gama duk abunda za suyi suka yi wanka ko wacce ta fito cikin shirinta.kai tsaye daga gida airport suka nufa.dan lokaci ya fara kure mudu.nan sukayi abunda za suyi a airport din sanna suka shiga jirgin su. Amal kusa da Anty Humairah ta zauna. Sukuma Abba shida uncle Hakeem suka zauna nan jirgin su ya daga zuwa 9ja🛫. 🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶 Gidan su Amarya Nana cike yake da yn uwa da abokan arziki kowa kagani yana kai kawo. Duk en uwansu yn sokoto sun hallara kowa kagani cikin farin ciki yau babbar yayarsa zata aurar da yr autarta. Nana kuwa gaba daya cikin busy take gashi ranar weds.za'a fara biki kuma yau sun.gaba daya ta shiga rubibi koda yaushe cikin waya take musamman da sakina. Tunda duk wani event nata ya tare za'a yi dana sakina. Itama haka gidan sakinar yake.dan haka mum ma gidanta cike yake ba masaka tsinke. 🔻🔺🔻🔺🔻🔺🔻 Yauma gidan su Annur cike yake da in uwan su Sara da kawayan hajiya bilki da yn uwa ko ina hayaniya. Sai faman gyaran Amarya ake suma ranar Wed zasu fara bikin.kowa kagani cikin hidima yake. Shikuwa Annur ko ta kan suma baya ni danshi aganin sa haukama sukeyi danshi bazai taba iya auran wannan mahaukaciya yarinyar ba saide komai za'ae ayi. Satin da ya huce akayi bikin Kabeer abokinsa sunsha hidima sosai dan su suka raka Ango ma. Annur ya rasa karyar da zai yima umminshi dan zuwa bikin su Uthman dan haka ya ynke shawarar shara mata karya. Kiranta yayi awaya dan tazo dakinsa,dan bazai iya shiga cikin mutanan nan ba. Bayan tazo cikin fara'a da walwala ta shigo dakin shima murmushi yake alamun bashi da wata damuwa. Amm dama Ummi tafiya zanyi. Tafiya kuma Annur kana da hankali kuwa,za ai bikin naka kace za kai tafiya inma tukun zaka. Ummi meeting muka anje appointment zamuyi da wasu turawa a Abuja kuma kikazo kika rage bikin nan yayi daidai da tym din. Yanzu kenan ya kakesan ayi kasande bazan taba daga bikin nan ba ko? Gobe zan tafi koma ranar sat 2pm zata min ajigawa.zance dama wajan dinner da daurin aure ake bukata ta. Anjiyar zuciya ta sauke tare da fadin Allah ya kiyaye bata jira me zaice ba ta fice tare da kullo mai kofar. Wani mugun tsalle ya buga yana dariya. Dama already ya gama hada kayansa dan yama sakasu cikin motar shi dan amota yake San tafiya. Hahhah lallai Ummi ai kawai natafi kaikuma nextwk insha Allah. Sannan ya dau key dinsa ya fice daga gidan. Cikin motar sa ya nufa tare da yimata key dan yasan yanzu Amal dinsa nacan tana jiran shi. Gate aka bude masa sannan ya fice daga cikin gidan. 🔺🔻🔻🔺🔻🔺🔻 Anty Humairah ce tayi waya kan azo atafi dasu. Basufi minti 10 da saukaba mota ta iso airport da driver dan daukar su. Abban Amal aka fara kaiwa gidan sa.dama yariga ya yawa wani yaransa waya akan a anshi key gurin me gadi abude agyara masa gidan. Dan kullum suka kira wayar hanne akashe dan sun rasa ko lafiya. Har kofar gida suka kawo su,mai gadi ya rinka murnar ganin uban gidan nasa nan ya shigar mai da kayansa gida. Saida sukayi sallama da su Amal sannan ya huce. Kai tsaye gidan Hakeem na nan aka huce dasu.suma sunsa an gyara ko ina dama kusa da gidan su Nana ne. Cikin gidan suka shiga tare da kayansu. Dakin da Amal zata zauna Humairah ta nuna mata sannan ta dau trolley dinta ta shige. Wanka ta shiga tayi sannan ta fito tayi sallah la'asr. Kayanta ta dauko atamfa Riga da skit ta sanya dinkin yayi mata kyau sosai sannan ta danyi light make-up. Tayi kyau sosai ta kara fari da kiba. Tana fitowa falon rataye da mayafi a kafadar fone dinta na hannunta dan Anty Humairah ta kira ta akan ita gama ta fito su shiga gida. Nana ce ta turo kofar dakin da gudu ta shigo ta rungume Amal din tana dariya itama rungume tan tayi tana dariya. I misssss u my Amal. Dariya tayi tareda fadin nima haka my Nana. Kunzo lafiya ya hanya, Alhmdullh Nana ya garan biki. Wallahi taro gashinan saima kun shiga gida. Allah ko,ina sakina? Wallahi yanxu muka gama waya kinsan gobe zamuje kunshi gidan da ake mana gyaran jiki. Tafawa sukayi,Nana tace ke vakiga na canzaba. Wallahi kuwa naga Har wani kumatu kikayi. Hhhhhh bana San sharri kema can zamu kaiki a gyarama Annur ke. Dariya suka kumayi.sannan tace banga ya Humairah ba ina ta shige. Fitowa tayi itama ta gama shiryawa tayi kyau sosai tana fadin gani nan Amarya. Gaisawa sukayi,sannan Nana ta musu ya ban gajiya. Lafiya qlau Nana ya taru Wallahi taro nan saima kin shiga gida. Aiko ynzu kinsan na matsu naga yn uwa da dangi. Aikuwa sunacan suna jiranki. Toh maza Ku huce muje bazan kulle gidan ba Hakeem na ciki. Sannan suka bi bayanta suka fita. Gidan nasu suka nufa tun daga bakin gate suka fara gaisawa da mutane dan Humairah mace ce ta mutane. Har suka shigo cikin gidan. Kuzo kaga dangi da yan uwa sai rungumar juna ake ita kanta Amal sun burgeta sai taji inama ace dangin tane. Itama Amal din sai gaida mutane take ana amsa mata cike da fara'a. Nana na rike da hannun amal duk inda Humairah tayi suna biye da ita. Wani falo suka shiga duk yawan cinsu matane manya da tsofaffi acikinsa. Nan suka durkusa anata faman gaidasu wasu su rungume Humairah suna fada mata irin kewarta da sukayi. Wata yar dattijuwa ce me fara'a ta kalli Amal sannan ta kalli Humairah tace Aisha ina kika samo diya kamar yr gidn jikar gidan mandibbo? Kai inna bafa yr can bace. Allah sarki gani nayi tana min kama da Zainabu yar gidan dije Allah jikar rai. Amal najin haka ta dago kai gabanta na faduwa ta mike tsaye. Kowa sai kallanta yake. Anty Humairah ce ta juyo tareda fadin lafiya Amal. Anty ji nayi an ambaci sunan babata.nide a yanda Abbana ya bani labari. Ya auri mamana a sokoto kuma kuma su nanta Zainabu kuma yatafi da ita tundaga ranar basu kuma komawa. Tabbas wannan jinin sarkin fulanice.cewar dattijuwar.sannan ta kalli wato yr tsohuwa tace da ita Inno duba diyarnan dakyau bata maki kama da Dije. Nima tunda na shigo nike kallanta.kamar Dije Allah jikan rai. Yaki yarnan jinin gidan sarki basa buya inde tana da taban ruwa a bayanta ba makawa ko tawaddar Allah cikin ido Allah yayi masu wannan baiwa. Nan Amal tana hawaye ta matsa gaf da matar,duba jikinta tashiga yi amma bataga taban ba. Har ta hakura sai kuma tace muga bayanki juyawa tayi ta dage dan kwalin kanta. Ga taban nan manne a saman huyanta kadan kafin keyarta. Nan fa aka hau murna.Amal kuwa farin ciki kamar ya kasheta. Sai kukan ddi take haka Nana d Humairah da wasu yan tsirari a falon. Kinga diyata bar kuka kinji nan kamar gidan Ku yake duk nan yan uwanki ne. Sannan tace kinga wannan ta nuna Inno yr tsuhuwa uwassu daya uban su daya da ka karki Dije Allah jikan rai. Mukuma nan da kike gani duk kannan kakarkine Har Babar su halima(Nana). Da uwar Uthman kinsan ta ko? Eh Amal ta fada toh duk iyayanki ne da kakanninki dan haka kibar kuka.abunda ya faruwa wa mahai fiyarki Allah zai saka mata. Dan Lokacin da aka tura a dauko Zainabu sai cewa ake tabi saurayi ta gudu.sai daga baya gaskiya ta fito. Sabo da haka kinga dangin mahaifiyar ki saiki godema Allah. Kowa ya taya Amal murna sosai nan ta shaida musu sunanta . Sunji ddi suma abinci aka zubo mata ita da Nana suka zauna sunaci sai faman hira ake da farin ciki. Nan Humairah take shaida musu maganar bikin Amal din. Nan fa akahau buda da wani saban farin ciki.kacede muna da biki nan kusa bayan na Nana. Nan aka yayima Humairah godiya abisa rukun da tayima Amal. Wallahi ba komai shiyasa koba kasan mutun ba ka taimaka mishi koda bai zama dn uwankaba wata rana zai jiknka. Nan de akayi ta hira ana maida zance Har aka kira magrib.. Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 180-185 Bayan sun idar da sallah magrib Amal ta kira Abban ta tagaya masa abinda ya faru. Shima kansa ba karamin ddi yajiba dan bashi da buri daya huce na farin cikin Amal din. Wayr tace tayi kara dan tana jin ringing tasan me kiranta. Da murmushi a fuskarta ta daga tareda sallama. Bbyna nima fa ina jigawa. Dagaske da Har kasa na bar jin ddi dake min bazaka samu damar zuwaba. So don't wrry beauty yanxuma kin gani dakin Uthman Ango gashi kani. Kace masa nagode koya kira yamin ban gajiya. Yan daga gafe yace ayi hakuri hakuri pls. Murmushi tayi tare da fadin kasa loudspeaker zan gaya muku wani abun farin ciki. Cikin zumudin ji Uthman ya mike daga kwancan da yake. Muna jinki . Yau nasamu dangin mamata.kuma Uthman pls ka gayama mum dinka. Wow! Gaskiya mun tayiki farin ciki amma aina kuka hadu dasu cewar Annur. Hmmm dangin su Uthman am also part of them. Cike da mamaki suka hada baki tare da fadin da gaske? Sosaima kuwa.toh wannan wani irin farin ciki zamu tayaki kawai Allah zamuyita gode mawa.tunda shine kadai yasan irin farin cikin da muke ciki cewar Uthman. Dan shi Annur yama kasa magana gaba daya. Sun tayata farin ciki sosai kuma tabbas taji ddi.sannan take kuma gode musu tukun sukayi sallama. 🔻🔺🔻🔺🔺🔻🔺 Washe gari tun 11am suka bar gida ita da Amal suka tafi gidan kunshi. Can suka tanda sakina duk da suna waya da Amal din taji ddin ganin ta. Nan aka fara gyrama amare jiki ana tsantsara musu lalle me kyau.ga gyara gashi da suka sha. Basu suka dawo ba sai GAF da magrib suka shigo gida. Wanka sukayi sannan sallah. Itama sakina gida ta huce dan kawaynta duk sunzo. Haka gidan su Nana ma ba'a magana dan ankuma cika sosai. Kowa yaba kunshin su yake dan yayi kyau ainun. Saida sukaci abinci sukayi sallah insha sannan Nana taja wasu kawaynta su biyu Hassana da fadila suka nufi gidan Anty Humairah dan a can suke kwana dakin Amal din. Shima uncle Hakeem ya taya Amal murna sosai.dn yan tausayin yarinyar. 🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺 Yaune kamun amare kowa kagani yasha anko sunyi kyau sosai ansha bidiri anci ansha amare ansha kyau. Itama gidan hajiya bilki sunyi kamu ansha shagali sosai sunsha kida da rawa kuma tayi taro sosai. Haka biki yay ta tafiya Har ya zo ranar assabr dinner ranar da Annur yayima umminsa alkawarin dawo wo gida.tun da yayi sallah zuhr ya kashe gaba daya wayoyinsa danma kar afara ne mansa. Har yamma tayi lokacinne amare suka gama shirin su ko wacce da kalar kayan data sanya sunyi mutukar kyau gabaki dayansu. Haka aka aiko da motoci kala kala suka dauki amare da kawayansu zuwa hall din da zasuyi dinner din su cikin farin ciki da kwanciyar hankali. Komai suna yinsa acikin natsuwa. Amal ce ta fara bude taro da addu'a cikin harshan larabci da kuma turanci,kowa na gurin saida ta burgesa. Musamman habibeen zuciyarta dan ji yayi kamar ya saceta ya gudu kowa sai kallanta yake Har yaji kishi ya kama shi😆😆. Haka suka cigaba da gudanar da abubuwansu kala kala. 🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺 Can kuwa tunda akayi sallah la'asr Annur bai isoba hankalin hajiya bilki ya tashi dan tabbas tasan Annur karya yayi mata dan baya San Sara. Dan haka ta kudiri niyar babu abunda zai hanasu party dole suyi. Kuma washe gari dole a daura aure. Haka suka ci gaba da shirinsu Har Lokacin tafiya yayi haka zalika itama Amarya ba damuwar ta bace itade burinta ta aureshi ta kuntata masa tunda ya hulakantata ya kuma nuna baya kaunar ta. Itama cikin ado ita da kawayenta yn duniya da kuma kawayan hajiya bilki da na mamata. Tabbas ciki ya cika manyan mata sun halacci bikin nan. Motoci suka dinga hawa suka isa hall din basu jima da fara abunda ya kawo suba. Masu video da pic anata famanyi. Can sai aka dinga ganin kartin maza suna shigowa cikin hall ko wanne da makamai a hannunsu sun kai kimanin su 30 ko wanne ba imani atare dashi. Ko wacce acikin gurin hankalinta atashe yake. Cikin takun kasaita ta shigo Hall din tana tafi. Tabbas yau ni NA cika yr halak kuma zan nuna muku bani da hankali bani kuka dokaba zakuga duka. Ta kalli wannan kartin tace kada Ku ragama ko da yaroni cikin su so nake duk wanda ta zo dinner en nan karta manta da ita a rayuwa sa.jikin ko wace shegiya ya gaya mata. Nan aka hau duka babu tausayi gaba daya guri ya kaure da hayaniya ko wa takanta take. Hajiya bilki kuwa da Sara da Mamanta masu dukansu daban kuma da gora. Duka yake ba tausayi duk inda ya samu saida ya musu lilis saida ko wacce a gurin ko motsin kirki batayi. Amarya kuwa suma tayi su hajiya bilki jikinta duk yayi tsami tayi nadamar sanin hajiya ladi arayuwata. Kuka sosai ta zauna tana yi,wannna kadan ta fara gani kenan tun aduniya ta fara ganin irin wannan ina ga ta mutu. Da alama hannun ta yama karye. Sara kuwa karaya 2 aleg 1 acinya. Gatanan kwance kamar matacciya. Mamanta sai faman kuka take. Cikin en party kuwa wanda yaga zai iya mikewa ya mike wanda bai iyawa ya kira atafi dashi. Ita kuwa hajiya ladi dama ta riga ta sallama yn iskan data hayo. Suna fitowa babban cikisu yace hajiya baki cika mana kudin bada. Duka nawane za'a cika muku kudin banza ni kar Ku batamin rai wlh. Bafa haka mukai da keba gaskiya muna ganin mutuncin ki Wallahi. Banzaye en iska Ku harwani mutunci kuka sani,to na cinye kuma bazan biya ba. Wani daya dake tsaye abayan ta ya buga mata sanda akai nan yayi mata dukan tsiya.sannan ogansu yayi mata fyade. Suka dauke motarta da jakarta daga ita sai kayan jikinta.kanta ko dan kwali babu ga tsinannan dukkan da tasha ko motsi bata iyawa. Karan motar yansanda najiyo da alama kan titin suka biyo. Ganin mutun kan hanya ya sanyasu dakata wa tareda duba ko lafiya. Suna fito wani mutun medan hake ya kuma haska fuskarta tareda kallan photo hannusa. Da Sauri yace yallabai ai itace wanda muke nema duba dakyau kagani Hajiya kece jamila ahankali ta daga kanta tace nice dan Allah Ku taimaka min karna mutu. Yauwa isa Ku sakota cikin mota mu tafi.ba musu suka sanya hajiya ladi cikin mota suka kuma hucewa suna jiniya.. Biki yayi ddi sosai cikinfarin ciki suka tashi aka maida kowa gida lafiya. Sannan washe gari da safe aka daura auran.HALIMA ABUBAKAR DA ALIYU ISA RINGIN. AND SAKINA ABDUL'S SALAM DA UTHMAN ABBA DUTSE Taro yayi albarka manyan mutane an uwa da abokan arziki duk sun halacci wannan biki mai albarka. Yamma nayi ko wace Amarya aka mikata gidan mijinta. Alhmdullh biki ya kare. 🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺 Biki ya kare kowa ya kuma gidansa lafiya saikuma na Amal kowa haka yake fadi. Rayuwa ta dawowa Amal sabuwa ta kuma saman wani saban gatan wajan dangin mahaifiyar ta. Ga kuma Abba ta da yake kula da ita shima sosai. Yaune ranar da Annur zai koma gida sunyi sallama da juna shida ita da fatan kuma sai sun sake haduwa dan zasuje south African ita da Abba sai kuma sun dawo.haka suka rabu badan suna so ba. (9:00pm) Annur ya isa gida gabansa na faman faduwa yanxu shikenan an aura masa wannan mahaukaciya Wallahi sakinta zaiyi dan bazai yima Amal kishiya ba. Da sallama ya shiga cikin falo zaune kan kujera ya tanda umminshi. Gabansa na faduwa ya karasa wajanta tareda fadin. Dan Allah dan annabi kiyi hakuri ummina nasan ban m..... Ya isa Annur, ni ba kamin komai ba nagode kwarai da Allah yabani yaro kamarka. Kuka sosai takeyi.Annur nice zan roki yafiyarka ka yafemin kaji Dana. Cikin mamaki yace Ummi wai meke faruwa ne dan Allah. Nan ta kwashe duk abunda ya faru ta gaya masa. Nan yace Wallahi sai yadau mataki akan hajiya ladi. Rabuda ita Annur kaji inde duniyace taje zata gani. Yanzu ya hannun naki.kinga likita. Eh dasauki harma nasha magani kuma an Dora. Toh Allah ya kiyaye gaba. Ameen tace dashi. Sannan ya mike ya nufi dakinsa. Gaskiya yayi mamakin yanda ummin ta canza Lokaci daya. Allah ya kiyaye de... Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 190-195 ONE WEEK LATER🌸 Annur da Amal suna cikin jin ddi dakuma tsantsar soyayya da sukema junansu. Burin kowanne acikinsu ya sanya dan uwansa farin ciki. Yauma sun shirya da yamma da zuwa kaima hajiya bilki ziyara. Taji dadi mutuka kuma tayi farincikin ganunsu.rasa inda zata sanya amal tayi dan murna. A gurinta suka samu lbrn ankama hajiya ladi da hodar iblis koma ta yima wani mutun sa'a kuma harda kisan kai. Yanxude an yanke mata hukuncin daurin rai da rai. Suntausaya mata sosai kuma suka yi mata fatan Allah ya yafe mata. Basu jimaba sukayi mata sallama. Rayuwar su Annur abin sha'awa abin burgewa sunyi kyau abun su sun kara fari. Yau tunda suka waye gari suka nufi jigawa dan yima su Anty bangajiya da kuma sallama dan zasu koma. Da huri soka isa Anty taji ddin ganin yr tata yanda tayi kyau hankalin ta kwance. Sannan ta shiga gida gurin yaya( Maman Nana). Itama tayi murnar ganin amal din kuma takuma yimata nasiya sosai. Ranar de sunsha yawo Har gidan sakina da Nana sukaje sunsha hira. Kwana su biyu a jigawa saida uncle suka tafi sannan suma suka dawo gida. Lokacin aikin hajji na zuwa bayan wata biyu da auran su Annur ya biya musu su tafi da suka gama aikin su suka biya ta dubi nan ma sunji ddin ziyarar tasu kwanan su biyar a Dubai suka nufi sokoto nan ma sunyi yawo gidan dangin Amal da sosai sannan suka dawo lokacinne Amal ta fara laulayin ciki. Murna wajan yan uwa ba magana musamman Abban Amal da su uncle nan Annur yaci gaba da tattalin matarsa da dansu Har zuwa Lokacin da Allah zai sauketa. Gaba daya Anty Humairah ta taso daga Dubai ta taho tayima Amal zaman jego. Kwana Humairah uku da zuwa Amal ta santalo jaririnta kyakyawa me kama da Annur. Kowa yayi murna sosai lokacin su sakina duk sun haihu suma. Annur ma yayi murna sosai yaran yaci sunan baban Annur Shu'aeb suke kiransa da ARIF. Anty Humairah tana kula da Amal da Arif Har lokacin da sukayi 40 sannan ta koma gidan ta da murnar alkawarin da Annur da Amal sukayi mata ana yayi Arif zasu kawo musu sun basu halak malak. AFTER 3 YEARS🌸🌸 Amal da Annur sun Dada girma sunzama mum nd dad. Dan yanxu haka ma Amal ta kuma haihuwa Amma wannan karan mace ta Haifa. Suka Samara Zainab amma suke kiranta da AMNA.duka yrnyr batafi wata biyu ba. Kyakyawa sak Amal Har suman kan nata. Ko wanne gida suna cikin jin ddi da annashuwa kuma suna zumunci sosai. Sun hade kansu gadaya. Shikuma Arif yana Dubai gurin Anty Humairah yayi kiba yayi kyau kamar dan larabawa komai yake so shi suke yimasa. Yana jin ddi sosai yana San Anty Humairah da uncle Hakeem sosai dan yama zata sune iyayansa. END✅ Written by Zeenaseer😘 [12/29, 10:35 PM] Zeenaseer: 🌹🌹🌹🌸🌹🌹🌹 🌷🌷🌷 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 AMAL NA Zainab Naseer Sarki (Zeenaseer😘) 185-190 BAYAN KWANA BIYU Annur na zaune dayake wkend ne yana duba wasu files. Da sallama ta shigo dakin nashi tare da zama bisa gado. Ummina harkin tashi? Ina kwana. Lafiya qlau Annur katashi lafiya ya aiki. Alhmdullh Ummi ya saukin hannun. Hannuda sauki sosai Wallahi. Amm Annur dama abunda ke tafe dani shine.tunda naga kana kaunar Amal kuma kaga yarinyar kirki ce mezai hana muje abama iyayenta hakuri su baka ka aura. Hmm Ummi kenan dama anriga ambani Amal, kice ban gaya waba dan naga bakya santa.yanxu nan da sati uku za ayi bikinmu insha Allah. Baki tarike da mamaki tana kallan Annur din.kace daban zo ma da maganar ba da yanzu shikenan saide naga Amarya. Murmushi yake tare da dan Sosa kai. Toh Alhmdullh tunda Allah yasa mun gane gaskiya yanxu ka shirya.zamuje na bama dangin mahaifin ka hakuri akan abunda nayi musu kuma na nuna maka au insha Allah. Cikin tsananin dadi ya mike yana murna dan danan ya shirya suka fita. Cikin ikon Allah duk ta gane gida Jan. Nan ta dinga bi daya bayan daya tana neman yafiyarta koma Masha Allah kodan darajar Annur sun amshe su hannu bibiyu kuma sunji ddi sosai. Nan ta shaida musu da auran Annur din kuma ajigawa zama ayi bikin sun nuna farin cikin su kuma insha Allah duk zasuje biki. 🔺🔻🔺🔻🔺🔻🔺 Alhmdullh itama Amarya sunje south African ita da Abban ta sun sulhunta shida yayarsa kuma ya dawo gida ya daidaita da dukkan in uwa harda wadanda be saniba. Kuma duk sun tarbesu musamman amal yrsu.kuma ya shaida musu bikin Amal din suma. Alhmdullh komai ya daidai ta kuma kowa ya samu nutsuwa acikin zukatansu. Amare su sakina da Nana koda yaushe suna waya da Amal kuma dukkan nunsu suna jin ddi agidan mazajan nasu. Har yanxu Amal taba gurin Anty Humairah dan tariketa ta hana kowa ita dan tadau alkawarin ita zata aurar da ita. Biki ya kan kama saura sati daya. Gaba daya sun tattaro sun dawo gidan Abban Amal din.duk wanda zaizo nan yake sauka. Sannan ummin Annur tazo Har gida ta nemi yafiyar Amal da Abban ta kuma sunyafe mata Har Abba ke shaida mata sakin hajiya ladi da yayi. Gida kuwa yacika ba masaka tsinke yn uwa da abokan arziki Amarya tasha gyara ta koma tamkar sarauniyar sai faman kayalli take tana zuba kamshi. Dangin Annur sun kawo lefe har akwati dozon biyu,da mukullin mota.anyi musu tarba ta mutunci an karramasu kuma suma sunji dadin hakan. Yaune yakama aka fara bikin Amal, baaaina tsaya ina gaya muku irin haduwar da bikin yayi ba'a magana. Kudi kuwa sunyi kuka an kashe kudi sosai. Hanne ma tazo itama tayi aurenta dan lokacinma cikine da ita karami. Biki yaci sunan sa biki duk inda ake neman hadaddan biki toh wannan biki yakai. Kamar yanda aka tsara ranar lahadi mutane suka tazu kofar gidan Alhaji muktar dan daurin auran yarsa Amal. Manyan mutane sun halacci wannan biki,bayan an gama daurin aure uncle Hakeem ya shirya musu hadaddiyar walima anci ansha kuma angode Allah. Saide fatan Allah ubngiji ya sanya alkhari ya kawo yaya nagari masu albarka. Yamma na farayi aka dauko Amarya daga garin Kaduna acikin jirgi tareda yan uwa da kawayanta suka nufo kano da ita. Suna isowa airport. Aka aiko da hadaddun motoci suka kwashe inkai amarya sai gidanta dake Bamfai. Nan ne hadaddan gidan da Annur ya siya ya hadu iya hadu kamar ba'a Nigeria ba. Shima cikin gidan yayi kyau komai an tsara shi gashi yasha kaya masu kyau da tsada sai kace yar shugaban kasa. Kowa sanyin gidan nan yake. Haka aka kai Amarya gidan miji tasha kuka ita da Antyn ta mai Santa da kaunarta dazsu rabu. Haka suka bazo ta cikin wannan gida sannan suka koma dan Abba yace komin dare bame kwana gidan Amarya kowa ya dawo gida. Shiru ba kowa sai ita kadai.karan kofar da tajine ya tamfatar mata da Annur ne. Da sallama ya shigo dakin hannunsa dauke da Leda. Anjeqa yayi ya karasa kusa da ita ya zauna. Ahankali ya sanya hannunsa ya bude mata fuskar da aka sanya cikin lafiyayyiyar lifayarta me mugun kyau. Kanta a kasa ta rufe idanunta. Ahankali ya masa dedai kunnanta ya furta Welcom to my world bby😘 Kara rufe idanun nata tayi murmushi yayi ya sanya hannunsa ya kamo habarta ya dago da kanta tare da karema fuskarta kallo. Tayi kyau sosai sai yaga ta kara yimasa kyau kamar ba itaba ga wani kanshi da take famanyi kamar zai Shide. My wife ya furta I can always d presence of ur Lov in my life.everything you do make me even Lov u more wify. I feel overwhelmed in ur nevereding Lov. I Lov u so much Amal. Da sauri ta rungume shi tare da fadin I Lov u too my world. Toh yanxu kitashi muje muyi sallah kamar yanda annabi ya kowar.kuma mu godewa Allah ta kyautar junan mu daya bamu. Mikewa itama tayi,shiya fara dauro alwala sannan ita. Shiya jasu sukayi sallah raka'a biyu sannan sukazauna sunata faman addu'a wa junan su. Sundau tsawan lokaci sannan ya umarceta data dauko masa ledar daya shigo da ita. Kajine aciki ice cream da lemo kala biyu. Dama yinwa takeji dan raban data zauna taci abinci da yawa tun da aka fara bikin nan ko tunkan bikin. Saida taci ta koshi shiya ringa bata abaki sannan tasha Ice cream din. Sannan ta nufi toilet wanka tayi sannan tayo brush.koda ta fito baya dakin. Rigar bacci maikyau da ado orange ta sanya ta hade gashinta da orange ribbon ta feshe jikinta da turare sannan ta haye gadanta tayi kwanciyarta. Koda Annur ya tafi dakinsa shima wankan yayi sannan ya sanyo black singlet da ash 3qtr ya fashe jikinsa da turare sannan ya shigo. Ganin ta cikin bargo ta kudundune yayi murmushi shima yahau tareda janyota jikinsa ya kashe fitalar dakin . Asbah ta gari amarya da Ango😊. 5am na tura kofar dakin na shiga Annur baya kan gadon dan haka nayi tsammanin ko yana toilet dan naji karan ruwa. Kusa da Amal na matsa tana kwance gashin kanta kamar an bazashi kan pilon idanunta sun kumbura dukda arufe suke fuskar tayi bayau duk hawaye ya bushe daga gani bccin huya take😓 Bayan ya fito daga toilet din kugunsa daure da toilet ya shiga gashinta ahankali. Idanta arufe ta amsa masa. Hmmm bazaki bude idanba. Kamar zatayi kuka toh ina ruwan ka. 🙊naji ba ruwana muje kiyi wanka kinga za'a tada sallah. Ni baran yiba ka rabu dani. Naji Allah baki hakuri toh kije ki kinji dan Allah. Duk idanta akulle take magana toh zan tashi amma saika fitarmin a daki. Hakuri naji zan fita tashi to. Kayan shi ya sanya ya bar dakin yana jin tausayinta. Saida ta tabbatar batajin motsin kowa ta bude idanunta da sukayi jajir saboda kuka. Ahankali ta mike ta zuro da kafafunta kasa tareda dukar rigarta ta sanya kanta kamar na wanda tahau bori.haka ta nufi toilet ahankali tana kuka. Ruwan dumi ta hadama kanta sannan ta shiga tayi wanka da alwala sannan ta fito. Zaune ta ganshi kan gadan ya gyara dakin tas. Daga ita sai towel ta fito ko kallan shi batayiba,ta shafa lotion dinta ta gyara kanta. Sannan ta dauko wata doguwar Riga medan kauri ,toilet din ta koma ta sako rigar sannan ta dawo ta haye gadan ta lullube. Shide yanata faman kallan ta duk inda tayi.kamar jira yake ta hawo gadan ya bita ya rungume ta. Pls bby am sowie pls. Ahankali tace it's OK. Toh kiyi bccinki ko? Gyada masa kai tayi. Peck ya manna mata a goshi tareda fadin I Lov u cwt hrt. I Lov u too😘 Ahaka Har bcci ya dauke su.... Written by Zeenaseer😘 adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *