Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, March 22, 2017

BASAN RAINA BACE

adsense here 🏓🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓 🏓 *BASAN*🏓 *RAINA BACE* *by_________________* *_Badiat Ibrahim_* *______________1to5✍🏻* Bismillahil rahmanun raheem,✍🏻 Dukkan yabo da godia sun tabbata ga Allah subuhanahu wata ala mekowa mekomai daya bani baiwar tsara labari akoda yaushe ina mika godia da ga Allah abisa baiwar daya bani,✍🏻 Wannan labarin kirkirarrene banyishi dan wani ko wataba Sadaukarwa Na sadaukar da littafinnan ga mahaifiyata wacce da taimakonta nakawo matakinda nakekai yanzu I so much love u mom, *SHIMFIDA*✍🏻 Mama tana kichin tanata kokarin hada wutar itacannan domun takama amma ina itacan sai hayaki yakeyi kawai kasancewar yanayine Na damuna ba'a cika samun bushashshen itaceba,' Meenal ce tafito daga dakinsu itada khadija sanye suke cikin dogayan hijabansu har kasa tareda jaka arataye akafadarsu da dukkan alamu islamiyya zasutafi mama tadago tana kallonsu,'. ___"harkun gama shiryawa kunfito?,'. Khadija tace,'. ___"eh mama zamu wuce karmuyi latti, ' fitowa mama tayi daga kichin din takaraso gaban Meenal tazubama meenal idanu yayinda Meenal tasauke kanta kasa idanunta yasoma zubarda ruwan hawaye,' Mama tace,'. ____"kuyi hakuri yarana Allah yana tare damu insha Allah shizai taimakemu Meenal Allah yayi Anas ba mijinki bane shima Yusuf daya rabu dake abaya dayafasa auranki duk Allah yayi ba mazan auranki bane in lokacin yayi saikiga Allah yakawo miki mijinki kiyi hakuri kidaure zuchiyarki sannan ki manta da Anas kimanta da dukkan abunda yafaru allah yaimuku albarka,'. Meenal tadago idanunta wanda suke zubarda hawaye cikin muryar kuka tace,'. ___"mama bakomai Na yadda da kaddara mekyau komara Kyau domun Allah yana gwada imanin bayinshine tahanyar dauro musu wata kaddara danya kwada imanin bayinshi ,' Toni na yadda datawa kaddarar amma mama meyasa suke ganin laifin Fatima itada aka ketama haddi akaimata fyade mama tayi jinya sosai daga baya tasamu juna biyu wanda hakanne yai sanadiyyar barinta duniya meyasa akeganin laifinta mama dalilinda yasa kowa yatsanemu kenan cewar kanwarmu tayi cikin shege garin zubarwa tamutu mama ina kishin'Yar uwata inajin dacin kazafin da'ake jefanta dashi domun batada laifi fyade akaimata ba'asan rantaba ta rasune da juna biyu ajikinta wanda tasamu akasamakon fyadan da'akaimata sanadiyyar ciwon ciki tarasune ,'. Kukane yaci karfin Meenal tadinga kuka cikin dacin rai,' Khadija wacce itama kukan takeyi tace,'. ____"bakomai Allah shine shaida 'Yar uwarmu mutuwar Allah da annabi tayi sannan duk wanda yaimata shairin ta mutune tahanyar zubarda cikin shege shida Allah sannan auran Anty Meenal da aka fasa har sau biyu Allah yasa hakan shine alkairi agaremu,'. Meenal tashare hawayanta tareda kakaro murmushi nakarfin Hali tace,'. ___"mama karki damu dani wlh komai yawuce kuma insha Allah zancire Anas araina zanbama zuchiyata hakuri mama muntafi karmu makara,' ___"adawo lafiya Allah yatsare saikun dawo,' Sukasaka Kansu suka fita agidan suna tafe kowacce da abunda take sakawa aranta harsunkusa karasowa bakin titi Meenal tahango Anas akofar gidansu yana zaune shikadai kauda kanta tayi gefe yayinda taji wani iri azuchiyarta aikuwa yana hangota yamike dasauri tareda. Nufosu,' ___"Meenal dan Allah kitsaya inyi magana dake kinji? Kallonshi takeyi yayinda idanunta suka cicciko da ruwan hawaye tayi maza takauda kanta gefe guda tanajin wani kuka yana kokarin kwace mata,' ___"Anas ayanzu babu sauran wani magana atsakaninmu sai Abu daya nakeso kasani kafadama iyayanka cewar kanwata Fatima ba cikin shege taje zubarwaba tarasu Allah ne yadau abunshi Anas kaishaidane Fatima ba'yar iska bacce sannan alokacinda abun yafaru da'ita dakai mukaje muka daukota jina jina awajanda abun yafaru zuwa asibity Anas kasan komai tareda sanin bakar wuyarda Fatima tasha,'. Inayima fatan alkhairi Allah yahada kowa da rabonshi Na alkhari nabarka lafiya,' Tajuya tatafi tana kuka harsuka shiga Keke napep Anas yana tsaye awajan idanunshi sunkada sunyi jajir dasu dan yanasan Meenal dinshi iyayanshine sukaki sakamakon labarinda sukaji agari cewar kanwarsu tarasu tahanyar zubarda cikin shege dalilinda yasa iyayanshi sukaki amincewa kenan,' Suna tafe acikin kekennan amma kwata kwata hankalin Meenal baya jikinta tunaninta yayi zurfi harsuka karaso bakin makarantar saida keken yatsaya Meenal tadawo haiyacinta ahankali tasakko daga cikin keken yayinda khadija tabiya kudin mekeken yawuce,' Daidai motarsu tazo wucewa kenan tahangosu suna tsaye zasu tsallaka titi tayi maza tace,' ___"stop the car diraivar," Bashiri direba yataka tuwon burki danbin umarnin uwar gijiyarshi,'. Sauke glass din motar tayi tareda kurama su Meenal kallo tanutsu tana kallon Meenal har saida taga tsallakawarsu titi tareda shigansu cikin islamiyyar sannan tasauke nunfashi kasa tace,' ___"muje diraivar yimaza mukoma gida,' Yasake figar motarnan suka wuce,' yayindasu Meenal suka shiga aji sunata daukar darasi,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓 🏓 *BASAN*🏓 *RAINA BACE* *by_______________* *_Badiat Ibrahim_* *_______________6to10✍🏻* Motarsu tatsaya awani katafaran gida irinna alfarma hadadden gaske farine fentin Gidan abun sha'awa saiwasu fulawowi green dasuka zagaye wajan Gidan yayinda taciki kuma jajayan fulawars susuka zagaye dukkan illahirin tsakar Gidan abun shaawa hakanne yasake fitoda kyan gidan da tsarinshi,' hon direba yayi yayinda megadi yafito ya wangale musu get din dasauri,' Hancin motarsu takunno kanta ahankali tashigo harabar kerarren Gidan tareda tafiya kaitsaye parking place ya Parker motar dasauri yafito tareda bude mata kofar motar Jakarta tadauko tana murmushi tacema direban.' ___"nagode abakar ko,' Tawuce zuwa ciki abunta wata kofar zallan glass ne abakin kofar falon ahankali hajia tatura glass dor dinnan tareda shiga falon da sallama,' Kausar ce zaune akan duma duman kujerun fadon masu kamada Gado itada kakarta suntusa TV agaba suna kallo jin sallamar hajia yasa kausar Yar Auta tamike aguje tanufi mom dinta.'. Tana karasawa tafada jikin mom din ____"Momy saiyanzu kika dawo muntusa TV agaba sabida saura minty biyar hirarda za'ayi da *YAYA BASAM* shinefa muketa jiranki,' Momy tashafi kan Yar autarta tareda kamo hannunta zuwa falon,' ____"sannu da gida Ummu kitana dokin ganin wannan jika naki agidan TV gaskia zan fadamai kuna missing dinshi tunkamun yabar kasarma,' Murmushi tsohuwar tayi tace,'. ____"Ai basam nawane dolena inyi kewarshi musamman zamada yakeyi dani muita wasa yana tsokanata,' Dariya sukayi dukkansu daidai sanda lokacin yacika aka soma nunosu agidan TV'n nta. ___"to jama'a assalamu alaikum barkanmu dasake saduwa daku ayau batareda bata lokaciba zamu gabatar muku shahararren bakonmu wanda yayi fice kowa yasan kwarewarshi a bangaran iya buga kwAllon doki wato polo ,' batareda bata lokaciba zamusojin tabakin bakon namu medumbun masoya maza da mata wanda adaidai wannan lokacin nasan duk wani masoyin *BASAM B SALEES* yana gaban akwatin talebijin dinshi domun sauraron wannan shiri namu,'. To Malam *BASAM B SALEES GAREKA* nunoshi akayi yayinda masoyanshi dasuke Gaban TV suka soma murmushi gameda murnar ganinshi. Sanye yake cikin wasu irin tsadaddun kaya Na alfarma wandone Na jins ajikinshi fari Sol tsadadden gaske tareda farar rigarshi polo saiya daura pesincap akanshi itama farasol polo saiwani hadadden bakin takalmi kato wanda akalla in akafadama kudinshi zakasha mamaki badan kadanba idanunshi manne dawani kerarren eye glasses asalin dizaina medankaran tsada komai nashi metsadane kamar yadda yake metsada shima murmushi yakeyi ahankali yadan bude bakinshi,' ___"am assalamu alaikum masoyana maza da mata inama kowa fatan alkhairi,' __"to *BASAM B kozaka iya fadama masoyanka damamu kanmu wanne irin farin ciki katsinci kanka alokacinda kalashe gagarumar gasarda aka hada muku a Japan wanda kaikazo kalashe gasar wanne farin ciki katsinci kanka aciki?,' danna tabbata masoyanka sunasanjin farin cikin daka tsinci kanka alokacin,' Murmushi yayi tareda zare glass dinshi yace,'. ____"well alokacinda naganni waiyau nine nalashe wannan gasa takasa da'akayi agaskia nakasance cikin farin cikinda bazai iya musaltuwa ba dukka wannan gasa ba'ita bace gasarda nasomaci. Naci gasa dadama but wannan it's the best gaskia musamman irin kyaututtuka danaga anata mikamun tareda ambatan sunana da'aketayi agaskia ranarda kuma akazo kuma bikin murnar lashe gasar danaci nasarar lashewa iyayena suntafi daganan gida najeria zuwa Japan domun tayani murna sukansu 'Yan club dina sai abun yazame musu abun alfahari sosai suma agaresu,' __"to Malam *BASAM* naji masoyanka sunata fadin kayi kuka awajan taron domun yadda suka gani a mujallah. Komenene dalilin kukan naka?,' ___" amm alokacin nikaina bansan sanda kukan yazomunba domun taron jama'ar Dana gani wadanda sukazo daga kasa kasa gwamnoni da sarakai hardama sugabannin kasashe gakuma kyaututtuka danaketa karba daga wurare dadama so kukan murnane kawai nayi.' Daria sukasa dukka,' ___"to Malam, *BASAM* Naji anacewa daganan kaitsaye filin jirgin kasa zaka wuce zuwa wacce kasa nadai namanta kozaka iya fadama masoyanka wacce kasa zakatafi.,'? Murmushi yayi tareda dago idanunshi farare yace,'. __ " amm gaskia ne zanje Istanbul ahalin yanzu saura minty talatin jirginmu yatashi wani aikine da'aka turamu zamuyi nida abokan harkata wato Yan group dinmu uhm,' ___"to mungode Malam,' *BASAM* duka duka anan mukakawo karshen shirinnan saidai kamunnan zamu bude akwatin wayarmu domun karanta sakonnin masoyan *BASAM* Nan yabude akwatin wayarsu sakonni kala kala aka karanta iya wanda za'a iya yayinda akabar sauran ___"to jama'a amadadin Gidan TV ni bala yunusa shu'aibu nakecemuku sai Allah yasake hadamu awani zangon nagaba,' ko bakonmu yanada Wanda yakeso yagaisar?', ___"well ina gaisuwa ga family dina Musamman kakata. Nasan tana jina tana ganina I'm gonna miss u Ummu sai mom dina ina gaidata tareda sweet sister Na kausar love Saikuma Beb dina itama danasan tanajina kuma tana ganina I so much love u Bby,'. Saikuma dukkan fan's dina love u oll,' ___"to masu sauraranmu laifin Dadi karewa amadadin yidan tvnmu daya sadamu daku ni bala yunusa shu'aibu tareda bakonmu *BASAM B SALEES WANDA AKAFI KIRANSHI DA BB,' mukecewa muwuni lafiya bissalam,' Ummu tace,'. ___"wayyo sungama allah to yakiyaye maka hanya megidana nakaina,' Kausar tace,'. ____"nima wlh tunyanzu nasoma missing dinshi tunkamun yabar kasarma,' Daria Momy takeyi musu tace,'. ____"kukam zanga sanda zaku saba ace kullum indai babu *BASAM* agidannan kundinga missing kenan gashi shiba mazauniba daga wannan kasar zuwa wancan kasar,' Ummu tace,'. ___"uhm munsani shakuwace kawai tasamu muje kewarshi,' Wayar Momy tayi kara aikuwa kausar takwace wayar tayi magana da yaya *BASAM* sannan tamukama Ummu sukayi magana sai Momy akarshe sallama yayi musu tareda ajjiye wayar tashi.' Kaitsaye motarshi tashiga harabar airport din yafito dawata katuwar jaka arataye abayanshi yanufi Yan clup dinshi dukgasunan a zazzaune nanfa akashiga gaisawa tareda dan taba hira kowa yanajida kanshi cewar shi gwanine wajan iya tseren doki,". Wayar*BASAM* ce tashiga ruri ahankali yamike tareda .atsawa gefe,' ___"hello hot milk yaya akayine yakike kuma kinadai lafiya ko?, Cikin muryar damuwa tace,'. ___"heart beat ina lafiya sai missing dinka danasomayi tunyanzu naga hirarku tayi Dadi I love u my heart beat ina alfahari da iyawarka,' ___"come on Bby girl relax just smile bawani dadewa zamuyiba just 2 week's zamu dawo kinji banaso kina damun kanki I'm always with u kinji ko?,' __"to naji heart beat dina,' ___"olrigt hot milk love u bye take care,' uhm muah kisses 😘 Kiss ya manna mata awaya kana yadawo tareda zama nanfa akabukaci dasu taso sunsoma shiga jirgi kasancewar sukadaine acikin jirgin yam club dinsu baki daya minty goma da shigarsu jirginnan yayi sama ✈ yasoma keta hazo,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓 🏓 *BASAN*🏓 *RAINA BACE* *by______________* *_badiat Ibrahim_* *_______________11to15✍🏻* Su Meenal ne suka fito daga aji antafi break Na Rabin awa azaune take itakadai tana tunanin Anas dinta kawartace takaraso gareta tazauna akusa da'ita ___"Kawata kiyi hakuri wannan wani kaddarace sannan wannan abunda yafaru rubutaccen al, amarine daga allah koda tsautsayi bai fadama Fatima ba hakan zaifaru dake Kawata akwai daci tareda ciwo wanda kakeso yake sanka yarabu dakai alokacinda kafi kowa bukatarshi lokacinda kafi tsananin bukatar taimakonshi amma yazamuyi haka allah yaso kuma kinsan ance Matar mutum kabarinshi allah baiyi zakuyi aure da samarinki biyu dasuka fasa auranki haka Allah yaso.' Wasu siraran hawayene masu dumin gaske suka gangaro akumatunta tadago tanadan murmushi,'. ____"nagode hajjo da dukkan kulawarki agareni wlh komai yawuce inadai kokarin rarrashin zuchiyatane kawai domun kinsan taciremun soyayyar Anas araina kozan samu kwanciyar hankali Hajjo tasaka hannunta tana sharema Meenal hawayanta Khadija wacce take bakin ajinsu tayi murmushi dan ganin yayarta tayi murmushi kanta tasauke kasa kawai,' Misalin karfe shiddan yamma su Meenal suka tashi makaranta kaitsaye suka wuce gida suna shiga ana kiran magrib kaitsaye suka zari butoci suka daura alwala suka gabatarda Allah,' Mama tashigo da sallama tace,'. ___"khadija jeki Dibo muku abincinku kuci kamun akira sallar isha,' ___"to mama khadija taje kichin tadebo musu jalob din shinkafa da taliya ta mankyada sunaci yayinda kowa yashiga tunane tunanen rayuwa kowa da abunda yake sakawa Meenal dai tadan cakkakala abinci tamike tareda kuskure bakinta tashinfida sallaya tasoma gabatarda sallar esha," Mama tace___"yayadai karatun naku ankara muku akai kuwa Meenal,?' Kamun Meenal tayi magana yaro yayi sallama akofar dakinsu,' ___"dama Anas ne ya aikoni inkawoma Meenal wannan takaddar,' Meenal takauda kanta gefe khadija ce tasaka hannu ta amsa tamikama Meenal bata dubaba takawai jefa acikin jakar makarantarta,' mama tadingajansu da hira tareda basu labaran abun daria har saida lokacin baccinsu yayi suka nufi dakin kwanansu,' Meenal tana zaune atsakiyar gadanta bacci yaki zuwa mata Sam tanata tunani kanwarsu Fatima marigayiya idanu tadaga ta kalli bango hotonsune su ukune acikin hoton yayinda Fatima tadafa kafadar Meenal Suna daria,'. Meenal tatuno randa abun yafaru da Fatima,' Da yamma ne lis mama ta aiki Fatima kai kudin adashi kasancewar layinda mama ta aiketa sabuwar anguwace akwai gine gine dadama daba'a kammalasuba anan tahaduda Yan iskan suka jata sukaimata fyade kusansu uku ahaka su Meenal sukaga Yar uwarsu jina jina dakyarma suka ganta asume kuma,' Kukane yaci karfin Meenal tace,'. ___"Allah yasaka miki kanwata allah yasa kinhuta Allah yajikanki da Rahama,' Meenal tajuya takoma tareda kwanciya akan gadanta tareda runtse idanunta dakyar bacci yayi awon gaba da'ita taso karanta sakon Anas amma ina takasa koda bude takaddar sannan tayima kanta alkawarim bazata budeba domun ahalin yanzu tanata kokarin tursasama zuchiyartane domun tamanta da Anas,' Dasafe Meenal tanata shirin zuwa islamiyya domun tanada jarabawa yau karfe bakwai nasafe a gaggauce tayi Karin kumallo sannan taima mama sallama tawuce dasaurinta dan batasan tayi latti,' Tana tsaye abakin titi tarasa abun hawa duk kekenda tatawo acike take dam da Yan makaranta Meenal duktabi tadamu kanta gashi lokaci yanata tafiya,' Suna tafe abota tana bayan motar direba yana tukata aikuwa tahango Meenal atsaye abakin titi tanata tare Keke,' __"abakar kadawo baya daidai gaban waccan Yar makarantar,' .___"angama ranki yadade yadda kikeso haka zamuyi,' Meenal dataga motarnan tanufota saita sake dan matsawa gefe daidai karasowar motar gabanta Momy tazuge glass din motar cikin fara'a tace ___"'yata ina zakijene dahalama makaranta zakitafi ko? Cikin murmushi tareda girmamawa Meenal tace,'. ___"wlh mama nadade anan wajan inata tare Keke amma shiru kowacce acike gashi inada jarabawa a islamiyya,' Murmushi taima Meenal tace,'. ___"'yata inkin yadda da Allah kin yadda dani kishigo Mota mukaiki makaranta karkiji tsoro domun nibame cutarwa bace inkuma bakyaso shikenam ammadai bazanji dadiba,' Meenal tadanyi murmushi ta kalli wannan hajia tace,'. ___"to mama zanshigane sabida kince innaki bazakiji dadiba nikuma banaso inzama silar rashinjin dadin wani dan haka Na yadda dake nakuma gode,' Momy taji Meenal taburgeta azahiridai yanayinta akwai kyan nutsuwa gatada kwarjini daganinta kasan tafito Gidan tarbiya,' Mota tabude tashiga yayinda tadan takure agefe guda,' Momy tajuyo ta kalleta tana murmushi tadafa hannun Meenal tace,'. ___"menene sunanki,'? Da fara'a tace ___"sunana Meenal Al amin,' ___"sunanki me Dadi Meenal gakida nutsuwa dasanin girman manya a gaskia kin burgeni kuma kin bambamta da'irin matasan Yan matan zamaninnan namu gakida shigar kamala arayuwa inasan ganin macce tana kishin jikinta tareda suturta jikinta,' Murmushi Meenal tayi tasauke kanta kasa tace,'. ____"nagode mama,' Murmushi tayima Meenal tace,'. ___"Meenal kikirani Momy kinji domunni tamkar mahaifiya nake agareki ,' Kan Meenal adaure dukta takura inbanda murmushi babu abunda takeyi sunkaraso makarantar Meenal tace,'. ____"nagode Momy Allah yasaka da alkairi naji Dadi Allah yakaiku gida lafiya,' ___"Ameen Meenal nagode nima ga wannan kyasai wani abun,' kudi tamikama Meenal a dunkule,' __"aa wlh Momy kibarshi bazan karbaba,' tafita amotar tanadan sunne kanta kasa,' Momy taji Meenal tarafida da imaninta domun tamatukar yaba halin Meenal sosai murmushi tayi dataga Meenal tasamu shiga class ahankali motarsu tabar bakin get din makarantar *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY________________* *_Badiat Ibrahim_* *_______________16 to20✍🏻* Basam sunsauka a airport yayinda suna sakkowa motocin dazasu daukesu suka karaso kowa yashiga Mota Kai tsaye sai hotel aka diresu tareda rarrabama kowa dakinshi Na alfarma dakine da babu abunda babu aciki yahadu over kamarba hotel ba,' *BASAM* kaitsaye yafada toilet yayo wanka tareda dauro alwala daure yake da towel a kugunshi Saikuma karami wanda yakedan goge ruwan jikinshi Dana kanshi mai yadauko hadadde irinna hadaddun maza yasoma shafawa mannan ga kamshi ga laushi haka yashafe jikinshi da mannan tsab kana yadauko singlet dinshi fara yasaka tareda farin boxer wandonshi yadauko baki tsadadden gaske yasaka tareda bakar Riga hadadddiya classic nanyashiga taje sumarshi tareda shafeta damai takwanta lub lub abun shaaawa nankuma yafeshe jikinshi da tattausan turare dzaina hadadde yadan kalli mirrow *BASAM* kyakykyawane nakarshe dogone ingarman namiji me daukeda faffadan kirji domun yawan direning dayakeyi hannunshi. Amurde Amurde suke yayinda pags dinsa suke baro baro ajere abun shaawa inyasa Riga tana zamamai taimasa Kyau sosai farine Sol kamar balarabe yanada zarkadeden hanci mekamada bensir idanunshi farare kuma manya gawani Zara zaran gashi a idan nashi wandasuka Karama fuskarshi Kyau bakinshi karami kuma tsukakke lips dinshi pick abun shaawa gawani hadadden saje daya zagaye fuskarsa hakan yasake fitoda ainihin kalarshi saidan karamin gemunshi nagayu dan bantaba ganin wanda gemu ya amsa kamar *BASAM* ba inkuma yayi murmushi kumatunshi yana lotsawa dukka biyun yanada *DIMPLE'S* hakoranshi farare kamar kankara gasu shiryayyu gawani gargasar gashi wacce takwanta afatarshi tasake kyara masa skin dinshi hannunshi mekyau kasancewar yatsunshi Zara Zara dogaye abun shaawa hakama kafarshi medan karan Kyau atakaice komai nashi abun shaawane domun *BASAM YACIKA 100%* danshidin mekyaune shima yasan hakan domun kocikin turawa yashiga yafisu Kyau tareda kyan launin fata saidai inyashiga cikin larabawa saisusaje domunshi yafi kamada balarabe,' Dadduma ya shinfida tareda hawa yasoma rama sallah da'ake binshi ya'idar kenan ma'aikatan hotel din sukashigo tareda jeramai lafiyayyan abinci a daining tasowa yayi tareda hawa daining din dan yunwa yakeji yasomacin lafiyayyan abincinnan meshegen dadin gaske harsaidayaji yakoshi sosai sannan yamike tareda zaro katan takalminshi camvars baki yadaura igiyoyin takalmin yasake kyara rigarshi sannan yadauki wayoyinshi yafita,'. Yana zuwa reasapshion ya amshi key din Mota yafice dagudu ahabar hotel din zuwa cikin gari,' sim yashiyo nacan kasar tareda dan zagawa yatsaya awani pack yana zaune yasoma kiran hot milk dinshi aikuwa ringing daya zuwa biyu tayi wub tadauka,' ___"heart beat barkanka da sauka kasauka lafiya ko?,' Idanunshi ya lumshe yace,'. ___"hot milk kenan inata kewarki kinsani duknakasa sukuni damuwata indawo kawai inganki sai inajina wani single sabida baki a bangarena,' ___"heart beat hakika nafika san hakan yafaru domun kasan ninafi sanka fiyeda yadda kake sona kasani nasani inasanka fiyeda kaina ina tattalin ruhinka fiyeda yadda nake tattalin Nawa,' ___"I knew kina sona fiyeda yadda nake sanki but kinasani nima inashan wuya inbama tare dake Bby girl bagashi daga shigowata naje nasake sim domun inkirakiba kofa mom bankiraba kena soma kira amma yanzu zankirasu inji yadda suke saimuyi waya dake inna koma gida ko Bby girl?,' ___"olright heart beat kakira su mom dan hankalinsu yakwanta ba bye love u plz take care of ur self for me,' Sukayi sallama yasoma kiran wayarda zata sadashi da gida,' Ummu itakadaice agidan kausar tatafi makaranta Momy tafita motsa jiki,' taji waya tana kuka dasaurinta tatashi hardadan gudunta tana dagawa takara akunne," ___"hellow Wake magana?,' ____" 😃😃 ahhh matas naji dadin jin muryarki harkinsani daria domun inata missing dinki me gidanki ke magana Ai,' ___"ahhhh *BASAM* kunsauka lafiya ko ya hanya toh?,' ___"alhamdullah Ummu ina kausar da mom?,' ___"kausar tatafi school mom kuma tafita motsa jiki itada direba,' ___"duk filin motsa jiki nagida be ishetaba duk kayan motsa jiki dake filin bai ishetaba saitaje wani waje kuma haba ummuna why?,' ___"tanasan tadan fita wajanne kasan zaman hakan badadi bakayin aikin komai,' ___"it's okey Ummu well dama aikenakira muyi soyayyarmu abunmu bandafa fita dankinga me gidanki baya kasar kita tawo?' Daria sukasa dukkansu tace,' ___"kajimun ja'irin yaro aigaradai kayi aure kozanhuta nima,' Yace,'. ___"nidama nakeda zukekiyar budurwa sankowa kin wanda yarasa innadawo zankawo miki ita kiganta ammafa nafi sanki kamar,' Sukaita hirarsu abun shaawa haryadawo hotel din yana kwance,' sunyi sallama kowa ya ajjiye wayarshi *BASAM* bacci yayi abunshi *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN*🏓 *RAINA BACE* *BY_______________* *_Badiat Ibrahim_* *_________________21to25✍🏻* Motarsu Momy ce tashigo harabar Gidan harzuwa parking place abakar yafito yabude mata kofar tafito hartasoma takawa tajuyo tace,'. ____"abakar kayi maza kayi breakfast saikakoma makarantarsu Meenal kajira atashi kakaita gida kaga Gidan nasu,' ____"angama hajia zantafi yanzu amma waye zai dauko kausar daga makaranta?,' ____"kaje kawai har zaka kai Meenal gida kadawo dan Auta sai shidda zasu fito lecture,' ___"to to hajia aishikenan nagode zantafi yanzunnan,' Murmushi taimasa sannan tashiga palon tasamu goggo tana karanta mijallah karasowa tayi gabanta taga tabudo shafin hirarda akayi da *BASAM*tanata karantawa ' murmushi tayi. ___"sannu da karatu Ummu kina zaune kekadai badadi ko?,: Murmushi Ummu tadago tanayi tace,'. ___"eh shirun badadi danma megida yakirani munyi hira sosai dashi danaji shiru shiru baki dawoba shine nadauko mujalla ina karanta hira a akayi da megida Na wancan satin daya dawo daga tokky,' ___"Ummu ta *BASAM* gaskia kinasanshi dayawa kinfifa damuwa dashi feyeda autata mukam gaskia ana nuna mana banbanci bazamu yaddaba,' Daria Ummu tayi___"Ai *BASAM* nawane saidai kuyi hakuri kawai ni damuwatama wlh auran *BASAM* Inaso inga yasamu macce ya aura nitsatstsiya wlh domun kinga kuma duk wacce zata aureshi ba lallai ta aureshi dan Allah ba kila ta aureshi dan dukiyarki kokuma dan daukakar da Allah yaimishi,' dazu yacemun inyadawo zaikawomun matarda zai aura ingani,' amma Salma hankalina dai bai kwantaba kinsanfa Yan matan zamaninnan da abun duniya yarufe musu idanu," Ajjiyar xuchiya Momy tayi tace,'. ___"Ummu Nima kaina wlh abunda yake cimun tuwo agwarya kenan akan matarda *BASAM* zai aura mata yanzu sun lalace dasan abun duniya indai kanada kudi Kaine nasu inkuma kudin yakare sai iskanci da wulakanci yabiyo baya wata kuma tana San namijene me dukiya danta rabashi da dukiyarshi kota halin kaka matsaloli kala kala dai to balle *BASAM* daya hada abubbuwa uku matashine mekudine star ne kinga kuwa dawuya asamu macce ta aureshi dan Allah to wlh wannan abun nasani tunani,' ___"hakane Salma zancanki gaskia ne yanzu zamani ya lalace Mata sunzama abunda suka zama saikiga yan kananan Yan mata waisuna suntirin zuwa Gidan malamai da bokaye akan maza suna jefa kawunansu acikin masifa,' Salma Nima kaina inata tunanin wacce maccece zata auri *BASAM* badan tarin dukiyarshiba badan daukakarshiba?,' azamaninnan zaiyi wuya kuma daukaka tana karewa kamar yadda kudi kekarewa kinga inhaka tafaru ananne matsaloli zamu soma tashi ta bangare dadama," Momy tasauke ajjiyar xuchiya tace,'. ___"Ummu akwai wata Yarinya Dana gani sau biyu Ummu nayaba da hankalinta da nutsuwarta sosai gatada shigar mutunci ga kunya ga girmama manya Ummu mundauketa amota munkaita islamiyya wlh Ummu Dana dauko kudi nabata yarinyarnan Sam taki amsa tanatamun godia tawuce tashiga makarantarsu wlh Ummu hankalina yakwanta da Meenal sosai tashiga raina,' ___"ikon Allah amma Salma da mamaki yanda yanzu zamani yacanja harkika bata kudi taki amsa Allah sarki Yar albarka tabbas duk inda tafito tafito Gidan manyan mutane dan hakan tarbiyyace mezaman kanta,' amma Salma meyasa baki kaita gida kinga gidanba?,' Murmushi Momy tayi tace,'. ___"yanzu abakar zaikoma makarantar zaikaita gida kinga saiya gano mana Gidan,' __"to aishikenan Allah ya tabbatar da abunda zaifi zama alkhairi agaremu baki daya,'. Mairo mairo?,' Yar aikin ta amsa ___"naam Ummu ina zuwa,' dasauri mairo tafito tareda zubewa agabanta Mairo tajuyoda kallonta gun Momy tace," __"ina kwana hajia ainafito akace kinfita bamu gaisaba,' __"lafiya lau mairo kawomun breakfast tea n bread nakeso,' sannan abakar anbashi breakfast dinshi?,' __"eh ambashi nagama kamar fita zaiyi bara inkawo miki,' Tamike tatafi cikin minty biyar tadawo daukeda kakkauran tea da biredi yasha bota Momy taimata godia mairo takoma bakin aikinta yayinda itakuma tashiga karyawa,' Abakar yatafi dauko Meenal daga islamiyya yana zaune amota yana jiranta,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY__________________* *_Badiat Ibrahim_* *___________________26to30✍🏻* Sunfito daga class itada kawarta hajjo Suna tafe sunadan hirarsu Meenal tace,' ___"yaukam munfito da wuri gaskia kiduba kigafa saiyanzu Sha biyu tayi,' Hajjo tace,'. ___"eh wlh ga fitowar safen wuya wlh dakyar nasamu abun hawa,' Meenal tace,'. _____"aina manta Kawata banfada mikiba wlh dazu dasafe Ina titi narasa abun hawa kawai wata hajia tatsaya tacemun inbazan damuba sunaso sukaini makaranta dansunga inata tare Keke Kawata dabazan hauba kinsan duniya babu gaskia saitacemun bazataji dadiba inban hauba shinefa nahau muna motarnan bakiji sanyi da dadiba gashi tanata Jana da hira harmuka kawo makaranta,' Hajjo tace,' ikon allah amma da mamaki Meenal kinsan wasu masu kudin suna kyamar suga talaka akusa dasu amma ita hartamiki tayi kishiga motarsu gaskia tanada kirki sosai gaskia,' ___"wlh hajjo hartana tabani kuma babbar mata mekyau da'ita.' Suna fitowa meenal tahango motar Momy tazare idanunta tace,'. ___"Meenal kinga ga motar danake baki labari takawoni dasafe mesukeyi anan kuma?,' ___"wannan wai motar Meenal tohfa koma menene zamuji Ai Meenal,' Abakar yahangosu dasauri yafito tareda tsallako titin yakaraso gabansu,' ___"sannunku kuntashi?,' toh dama hajia ce tacemun indawo inmaidaki gida nadanma jima anan ina jiranki.' Cikin mamaki Meenal ta kalli hajjo suka hada idanu,'. ___"aa wlh nagode kabarshi zantafi gida aiyanzu akwai abubbuwan hawa nagode matuka Allah yabiyaku,' ___"kiyi hakuri wlh hajia bazataji dadiba indai tasan bankaiki gidaba malama kisa baki dan Allah,' Hajjo tace,'. ___"badamuwa Meenal inaga kishiga motar yakaiki gida kingashi umarni akabashi saimun hadu gobe kigaida mama da khadija,' hajjo tawuce abunta Adarare Meenal tashiga motarnan tanata nunamai hanya harsukazo bakin daidai inda suka dauketa dasafe ___"nanma zaka saukeni ya'isa nagode zan karasa gida kacema Momy nagode sosai,' ___"ahh kiyi hakuri incika ladana inkaiki Gidan mana indai babu damuwa hajia,' Badan tasoba tace__'to muje layinnan zaka shiga kamike,' Yasha kwanar layin tareda mikewa Meenal tanunamai kofar gidansu yana tsayawa tabude motar tashifo,' ___"nagode Malam kaimata godia inkaje naji Dadi sosai,' ___"bakomai malama Meenal kigaidasu mama inkin shiga __"zataji insha Allah Meenal tawuce kaitsaye cikin gidansu yayinda abakar shima yaja motarshi dankomawa gida,' *love u ollw* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY________________* *_Badiat Ibrahim_* *__________________31to35✍🏻* Meenal tashiga gida da sallama khadija tana zaune tana wanke tumatur zatakai Nika mama tanakan tabarma tana tsintar wake atare suka amsa Mata sallamarta,' ___"sannu dagida mama nadawo,' takarasa kan tabarnan tazauna,' ___"harkungama kindawo gida dawuri yau Meenal,' ____"wlh kuwa dawuri aka gama ne mama kinsan menene yafaru akan hanyata tazuwa makaranta?,' Waken da mama take tsincewa ta ajjiye tareda dafa diyarta,' ____"menene Meenal fadamun inji,' Meenal takwashe komai tasanarda mama har kawota gida da'akayi yanzu,' Mama ta kada kanta tace,'. ___"to mungode Allah yasaka amma kidena shiga motar mutane koda kinsansu kice kingode kinga ahalinda muke ciki yanzu saikiga wani sharrin yasake biyo baya cewar anga ansauke amota kinji ko meenal?,' ___"to mama wlh banyi niyar hawaba ita momyn ce tanace saina shiga kuma tace bazataji dadiba shiyasa nashiga sabida in girmamata kuma daya dawo daukata yadinga mun magiya akan lallai tace adawo dani gida shiyasa nashiga mama,' Murmushi mama tayi tace,'. ___"Allah yasa mudace Allah yaimuku albarka dukkanku kitashi kije kisake kayanki ga abinci a kichin kizo kici.' Tamike tareda tafiya daki murmushi mama tayi tabi diyarta da kallo khadija takaraso wajan mama,' ___"mama nawanke bani kudin nikan,' __"to khadija gashi inkika ajjiye nikan saikije karamar kasuwa tabakin titi kisiyo mana nama Na Dari biyu muma mudan taba gashi ,'. Dari biyu da hamsin Tamika mata,' Hannu tasaka ta amsa tawuce tana sanye cikin hijabi katoto har kasa,' Meenal ce tafito daga daki tasake kaya kichin tawuce tadauko abincinta tanaci sunadan taba hira data gama sunadai zaune akan tabarma subadan aikace aikacan gida,' Abakar yadawo kaitsaye yawuce falon Momy da sallama suna zaune momy tanacin apple Ummu kuwa tana saki tayi bacci,' __"barka da hutawa hajia,' __"yauwa abakar kadawo inadai fatan kakaita gida ko?,' ___"eh hajia nakaita gida dukda dakyar tayadda ma naga Gidan nasu anguwar shahararren fais ne suke,' ___"meenal kenan akwai hankali to yayi gobe zamuje darana zaka kaini saika shirya da wuri zaka iya tafiya,' Yawuce waje yayinda ma'aikatan Gidan suketa aiyukansu masu girki nayi masu shara nayi masu wanke wanke masu shara damasu bama fulawa ruwa kowa dai yakama aikinshi haka wannan hadadden Gidan yake kasancewa kullum acikin kyara zakaganshi a tsabtace yanata kamshi abun shaawa,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 Copied By HAYATU BABA ZUBAIRU (admin Novels villa Hayat hausa novels Hausa novels and fashion And Cool novel, makeup and cooking) WHATSAPP NO: 07039625239 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN*🏓 *RAINA BACE* *BY_______________* *_Badiat Ibrahim_* *________________36to40✍🏻* Washe gari tundasafe Momy tagama shiryawa tsab tana zaune tana jiran lokaci domun zuwa gidansu meenal kausarce tafito tana karasowa tazube akan cinyar Momy Sanye take cikin bakin gajeran wando tareda karamar farar Riga kanta ba dankwali ___"Momy wai ina zakijene kiketa kallon agogo?,' Murmushi taimata tareda shafa sumar kausar tace,'. ___"zanje Gidan antynkine kausar shiyasa kikaga inata kallon agogo banaso lokaci yakure mun,' Tashi tayi tana kallon Momy cikin tukuma tace,'. ___"antyna kuma Momy wacece ita a'ina take tayaya tazama antyna ma bansantaba ni?,' Tadafata ,'. ____"Auta antynkice amma baki santaba itama bata sankiba but I'm sure inkika ganta zata kwanta miki aranki sosai karki damu zakisanta insha allah.' Agogo Momy takallah tareda mikewa,' ___"I have too go know idan Ummu tatashi kisanar da'ita natafi plz Auta karkifa tasheta abacci kinji magani tasha,' Kausar tamike tareda mannama mom dinta kiss a kumatu,'. ____"saikindawo Momy bazan tashetaba nima sama zankoma indan kwanta.' Sukayi sallama Momy tawuce kausar ma takoma sama abunta,' Meenal tana tsugunne tana wankema mama kayanta yayinda khadija kuma take wanke wanken kwanuka mama tana zaune takurama meenal idanu tana nazari akanta,' Meenal kuwa tashagala wajan tunanin Anas tareda abubbuwan dasuka faru take zuchiyarta ta jagule har idanunta suka cika tab daruwan hawaye," Sallama suka tsinkayo Na macce mama ce ta amsa tareda cewa,'. ___"bismillah shigo mana,' Momy tashigo dasauri meenal tadago suka hada idanu da Momy dasauri tamike tsaye,' ___"Momy sannu dazuwa shigo momy gawaje kizauna," Mama cikin fara'a tace,'. ___"sannu dazuwa gawajan zama zauna bismillah,' Momy taji dadin tarbar da akaimata zama tayi tana murmushi,' Khadija tamike tareda debo ruwa akofin silver me murfi tatsugunna ta gaida Momy cikin fara'a ta amsa tareda tambayar sunanta,'. Meenal ta tsugunna,'. ___"Momy ina wuni kinkoma gida rannan lafiya? Nagode sosai Momy,' tajuyoda kallonta ga mama tace,'. "Mama wannan itace wacce nake baki labari sunkaini makaranta rannan,' Cikin fara'a mama tace,'. ___"ayya mungode sosai hajia da taimakonki Allah yasaka da alkhairi,' Meenal tatashi tabasu waje,' ___"a haba haba wlh bakomai meenal Ai diyatace nayabada hankalinta Dari bisa Dari musamman danazo naga irin tarbar dakukaimun kun amsheni hannu bibbiyu batareda kunsanniba naji Dadi a gaskia,'. Hakanne yasake bani karfin guiwa kan musabbabin abunda yakawoni gareku,' Mama tace,'. __"to Allah yasa muji alkhairi hajia,' ____"insha Allah aikhairine wato hajia tunranda nasaka meenal araina nayi matukar yabawa da kamalarta tareda shigarta da mutunci dakuma nadauketa amota zuwa makaranta yanayin yadda ta girmamani yamun Dadi abunda yafi burgeni da meenal nadauko kudi nabata taki amsa taburgeni sosai inbazaku damuba inkuma ba'a rigamuba ina nemama Dana auran meenal,' Mama tadago da Sauri tana kallon Momy cikin mamaki tace,'. ___"dankifa kikace kike namama auran meenal?,' ___"eh Dana ko akwai wata damuwane kokuma meenal takusa aurene?,' Ajjiyar xuchiya mama tasauke tace,' ____"aa bata kusa aureba hajia nadaiji mamakine dakikace kinzo nemama danki auran meenal,' ____"insha Allah nayi muku alkawari meenal bazatayi kukaba insha Allah dandauki amanar meenal tareda bata farin ciki kwarkwadon iyawata zanbaku lokaci kuyi tunani sannan ki tambayi meenal inta amince to zandawo jibi zanji Duk hukuncin dakuka yanke,' amma kisani harcikin zuchiyata inasan meenal nayaba da tarbiyyar dakika bata sosai,' nizan koma.' Kudi ta ajjiyema mama bandir guda ___"aa wlh hajia kibar kudinki mungode sannan insha Allah zan tattauna da meenal duk abunda tace zakiji insha Allah,' ___"babu Kyau mayarda hannun kyauta baya kinada ilmi nasan kinsan hakan to Allah yasa muji alkhairi Allah ya tabbatar mana,' __"Ameen hajia mungode sosai, meenal! Meenak!!! Kifito hajia zata tafi,' Dasauri meenal tafito tareda raka Momy har Mota tace,'. ____"Momy nagode sosai naji dadin ziyararda kika kawomana Allah yabada lada,' ___"Ameen meenal zakibani number ki yanzu saimudinga gaisawa meenal zakiji sako awajan momynki dan Allah karki bani kunya karkisani inji badadi plz ina rokonki meenal,' Dasauri meenal tadago tace,'. ___"plz Momy kidena rokona zakisa inji kunya insha Allah bazansa kiji badadiba niyimiki alkawarinnan Momy.' Murmushi tayi tareda godema meenal tabata number ta itama tabata nata meenal tana wajan har saida motarsu Momy tabarwajan sannan tasauke ajjiyar xuchiya tajuya zuwa cikin gida,' Mama tace,'. ___"meenal karaso nan muyi magana,' Atsorace meenal takaraso tareda zama kanta yana kasa,' Mama takwashe duk yadda sukayi da Momy tasanar da'ita babu abunda tarage Mata,' Hawayene yagama wanke fuskar mrenal zuchiyarta dukta jagule tarasa yazatayi nezatace,' Khadija takaraso gaban meenal tana share mata hawayanta dagowa meenal tayi suka hada idanu da khadija rungume junansu sukayi Suna kuka dukkansu Mama tayi shiru tana kallon yaranta wadanda suka bata tausayi,' Meenal tace,'. ___"aa mama kicemata tayi hakuri mama basan sake bari zuchiyata takarye akaro Na ukuba domun nasani za'a fada musu komai zasukuma gujeni mama inyi yaya da zuchiyata mikin zaimun yawa wlh bakiji yadda xuchiya takemun daciba yanzu haka bazan iyaba mama,' Khadija tace,'. ___"zaki iya Anty meenal kibashi dama domun baduka bane akazama dayaba sannan dan Yusuf ya gujeki Anas yagujeki bashi bane hujjar kindena yadda dakowaba kibama zuchiyarki hakuri insha Allah bazata sake samun mikiba awannan karon kiyi tunani kamun kiyanke hukunci,' domun nayabada kirkin Momy sosai tanada sakin fuska taredasan mutane dan Allah kizauna kiyi tunani kamun kiyanke hukunci,' Mama tasauke ajjiyar xuchiya tace,'. ___"maganarda khadija tafada gaskia ne meenal Dole zakiyi aure tunda bazaki zauna hakaba Dole kimanta da baya mufuskanci gaba meenal kiyi tunani tareda dogon nazari kamun kiyanke hukunci zanbaki lokaci kiyi kokarin tausar zuchiyarki,' Haka meenal wunin ranar tayishi basukuni dukta takura kanta tanata tunane tunane Kashe wayarta tayi dib haka meenal takwanta da tunani fal ranta,' Yayinda Momy takoma gida tanata murna tareda zaiyanama Ummu duk yanda sukayi takuma baiyana mata karamcin gidansu meenal tareda yanayin nagaartar Gidan sukaita tattaunawa suna farin ciki,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN*🏓 *RAINA BACE* *BY_______________* *_Badiat Ibrahim_* *________________41to45✍* _BASAM_ yatashi daga bacci kaitsaye yafada toilet yayo wanka tareda dauro alwala yafito yayi sallah kana yashirya tsab cikin farin wando da Riga farin takalmi farar pesincap farin agogo kamai najikinshi farine dan *BASAM* yanasan fararan kaya dan kusan dukka kayanshi farare sunfi yawa laptop dinshi yabude yasoma aiki gabaki daya yamaida hankalinshi kan laptop dinshi wayarshi tasoma kara yadago idanunshi yana ganin mekiran nashi yasaki tattausan murmushi tareda saurin daga wayar,'. ___"my hot milk yaya akayi to kinganni ina zaune inadan aiki a laptop anjima munada kwallo dazamu buga dawasu club din saikimun adda'a ko? ___"insha allah heart beat club dinkune zasuyi nasarar cinye wannan kwallo aina yadda da aikinka domun mekyaune kamarka yes heart beat,' ___"uhm kina yabona sabida ninakine ko Bby girl dama muna tare Dana sumbaci lips dinki naji dadin yabonda kikamun hakan zai sake karfafamun guiwa sosai ' "Saikuma tashagwabe mishi tanamai shagwaba tanadan kukannan nawasa ' Lumshe idanunshi yayi tareda dafe kanshi yace,'. ___"come on Bby girl relax relax menene fadamun mana aisaiki tayarmunda hankalina kinsan banasan abunda zai tabaki so tell me I'm listing to u,' ____"heart beat I missed u so much sannan yakamata muyi maganar aure sabida ina bukatarka akusa dani u have to do something plz plz Kuka tasakamai awaya,' Rarrashinta yashigayi dukyabi yarude,' listing Bby girl relax mana inbakyaso raina yabaci kiyi shiru yazaki dingamun westing mun hawayanki yana zuba abanza listing to me Bby girl I promised u ina dawowa zanfadama mom komai saita sanar dasu uncle's dina saisumu Dad dinki ayi magana ,'. So are u happy nw? 🙄 ___"yea I'm very very happy heart beat love u so much tasakamai ihu akunne yadan kashe idanunshi daya yana daria kasa kasa ___"any way Bby girl lokaci yakusa so I have to go nw,' but promise me bazaki sakemun kukaba plz Bby banaso kinsani Ai,' __"come on heart beat nashare hawayena Ai basauran kuka I promised u I will never do it again,' __"it's okey Bby girl ba bye love u muah 😘 Sukayi sallama yanata murmushi ahaka yafita sai filin polo din nankuma suka shiga shiryawa tareda daddaure hannune guiwane dadai sauransu ga dawakansu manya manya suma kafafunsu adaure da kyalle gajerun wanduna Yan club din su *BASAM* sukasa sai Riga Saikuma pesincap dukka farare sunakan dawakansu gasunan ajejjere abun shaawa kowanne yana cikin ready yayinda Yan kallo kowa yanutsu yana Allah allah asoma Yan dayan term din sungama shiryawa kowa da sandarshi ta buga kwallo nantake aka hura musu usir tareda garo karamar kwallonnan cikin filin,' Habawa nanfa dawakannan suka shiga gudu kowa yana kokarin gara kwallonnan inbanda karan gudun dawakai babu abunda kakeji,' Computer kuwa takota ina ana kallonsu sunata guje guje kwallon awa daya sukayi yayinda BASAM yaci kwallonnan harsau biyu yan dayan term din kuma sau daya nanfa akashiga ihu ana shewa ,' yan term dinsu *BASAM* sunata murna tareda RUngume BASAM ahaka akadai tashi dama abunda yakaeosu kenan kuma sungama sai Hutu dazasuyi nasati guda,' Kowa yawatse yadawo masaukinshi yayinda *BASAM* yayo wanka yadawo yanata aiki a laptop dinshi yakirasu mom yafada musu sunyi nasara kana yasanarda Bby girl dinshi anata murna ,' Saidaya gama komai yaci abinci kana yakwanta abunshi bacci medadi yakwasheshi ' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN 🏓* *RAINA BACE* *BY__________________* *_Badiat Ibrahim_* *________________51to55✍🏻* "Da misalin karfe hudun yamma jirginsu BASAM yasauka najeria Momy da kausar da Ummu suna zaune acikin filin jirgin suna jiran sakkowar su BASAM yayinda kowa yazo Tarar yaronshi a airport din,' minty goma dasaukar jirgin mutanan ciki suka soma sakkowa BASAM suka hango yana takowa cikin nutsuwa yayinda yaketa musu murmushinshi "Sanye yake cikin fararen kaya wandone Na jins farisol sai wata Riga mai dogon hannu aciki lonsleep Saikuma wata rigar Jins daya daura Asama mekaramin hannu kafarsa sanye da camvers fari tsadadden gaske yana karasa sakkowa yanufo Ummu tareda rungumeta suna daria.' ____"I missed u so much Mata's inata kewarki gashi kena soma gani Dana sakko gaskia kinaji dani,' Ummu tasaka daria tareda dago BASAM,' ____" inbaji dakaiba dawa zanji wlh bakaji dabakananba Gidan ba Dadi Sam,' Daria sukasa takarasa gaban Momy yariko hannunta ya summbata,' Tareda rungume kausar sunata murna haka suka wuce zuwa Mota,' BASAM tunda akashiga motarnan yaketa tsokanar Ummu sunata daria imbanda murmushi babu abunda Momy takeyi ahaka harsuka karasa gida,' Megadine yataho aguje tareda wangale musu get din,'. ____"ahh barka da dawowa megida,' yana dagama BASAM hannu.' Sunkarasa parking place yayinda kowa yasakko BASAM yana rikeda Ummu suka wuce kowa yaxube afalo sannanne aka gaggaisa tareda tayashi murna ___"wash nagaji inaga infaracin abinci tukunna sainaje dakina inyi wanka inhuta Mata's innafito saimuyi labari ko? Ummu tace,'. ____"to megida takobin yaki,' Sunkarasa daining table suna zaune yayinda kausar ta saving kowa awajan itama tazauna tasomacin nata,' BASAM ahankali yakecin abincinsa wajan yadauki shiru inbanda karan cokali bakajin komai,' Momy ce tayi kyaran murya tace,'. ____"BASAM inkahuta akwai wata muhimmiyar magana danakeso mu tattauna amma kasamu Hutu tukunna saimuyi maganar kaji?,' Saidayakai lomar abincin yahadiye sannan yace,'. ____"to Momy inna fito zanshigo dakinki ,' kausar karatunfa anayi kuwa?,' ____"eh yaya inayi yanzuma munyi exam muna hutune shiyasa banjeba,' ____"daz my girl kidage kita karatu indai sakamakonki yAfito mekyau zanbaki kyauta metsokan gaske,' yadan shafa kumatunta yajuyo ya kalli Ummu yakashe Mata idanu ____"Mata's zanshiga ciki ni kishirya kamun infito musha hirarmu inbaki labarin turai,' ____"ina jiranka megida saika fito,' Yajuya bayanshi yawuce yayinda kausar tatashi tabishi da jakarshi Ummu ta kalli Momy tace,' ____"Salma saiki sanarda meenal megidanta yadawo kozataji Dadi ko?,' _____"eh Ummu yanzunnan zan kirata muyi magana tashirya gobe zaije yaganta itama taganshi suyi magana ma,' ____"yauwa amma hakan yayi kuma naji Dadi sosai wlh inama BASAM murnar samun salahar mata nutsatstsiya ga girmama nagaba da ita ga iya magana,' Muushi Momy tayi najin dadin anyabi meenal wayarta tasoma lallatsawa takara akunne dankiran meenal ringing daya zuwa biyu meenal tadaga wayarnan.' ____"salamu alaikum Momy ina wuni ya gida,?' ____"Ameen wa alaikis salam meenal gida lafiya kalau,' dama nakira insanar miki BASAM yadawo yanzunnan insha Allah kiyi tsammaninmu gobe zamuxo kiganshi shima yaganki,' Gaban meenal yayanke yafadi tadafe kirjinta cikin sanyin murya tace,'. ____"to momy Allah yakaimu goben,' ___"Ameen meenal saiki sanarda ummanki zamuzo gobe,' ___"to Momy zanfada mata,' Sukayi sallama asanyaye meenal tasauke wayarta akunnenta mama tazuba mata idanu khadija take gefe tana karatu itama idanun tazuba mata,' ____"meenal lafiya lokaci daya yanayinki yasauya lafiya kuwa bada momynki kukayi waya bane?,' ____" da'itane mama dama cewa tayi infada miki gobe zasuzo itada BASAM yadawo yau shine tace insanar dake,' ____"tohh Allah yakaimu goben to meenal meyasa kika canja fuska bakyasan ganinshine kome?,' ____"aa mama bakomai wlh,' tadanyi murmushi tamike takoma dakinsu,' ___"khadija zonan,' ___"to mama,' khadija tataso tazo gaban mama tazauna,' ____"mekike gani zamu tanadar goben naci danasha aibaidace yazo haka baici komaiba ko?,' "Khadija tace,'. _____"to mama balalle bane BASAM yaci wani Abu ba domun kinga yafito Gidan arziki yasaba da cima masu Kyau to mukuma talakawane kila bazai iyacin abincinmuba,' "Mama tayi shiru tana nazari tace,'. ____"amma khadija koda bazaiciba muyidin yagani aizaiji Dadi itama mahaifiyarshi zataji Dadi kuma hakan tamkar an mutunta meenal ne,' ___"to mama shikenan inaga to muyi jalob din shinkafa saimuyi cake saikuma drinks dazamu siya sai nama yayi Ai,' ____"to khadija kije Gidan Maman Safiya kicemata dan Allah acikin kudin adashannan tarantamun dubu uku zandawo mata dashi indai tabaki kiwuce kisiyo duk abunda zakiyi amfani dashi sabida yakwana a hannunmu dasafe ssimusoma aikin ko?,' ___"to mama bari najedin saina dawo,' Khadija tafita abunta tareda nufar gidansu Maman Safiya me adashi takuwaci sa'a akabata kudin tashiga kasuwa tasiyo kayan cake tareda kayan lambu dazatayi amfani dashi a jalob din su kori ne dasu taim magi iri iri sannan tayiso nama da shinkafa Rabin loka sauran kudin daya saura tasiyo coke tareda ruwan gora swan,' Haka khadija tadawo ta nunnunama mama kayan sannan suka ajjiye,' Sukaci gaba da tattaunawa itakuma meenak tana zaune yayinda fargaba dukya cika Mata ciki,' *BASAM* yayi wanka tareda saka rigar bacci nanyakashe wayoyinshi danso yakeyi yahuta nanfa yabi lafiyar gado yayi baccinshi,' Daga bangaran Basma budurwar BASAM kuma tanata kokarin kiran wayar BASAM taji koya sauka lafiya amma duk layikanshi akashe suke,' duktabi tadamu kanta tanadai kwance abun duniya yabi ya isheta ,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY_________________* *_Badiat Ibrahim_* *________________56to60✍🏻* *SAI MISALIN KARFE SHIDDA DA RABI* *BASAM* yafarka daga baccin dayayi ahankali yake bude idanunshi yayinda yakai dubanshi kan tabkeken agogon dakinshi me daukeda dankareren hotonshi yanakan katoton farin dokinshi yasanya fararen kaya dokinnan yana gudu shikuma yana daria sosai ahaka akadauki hoton sai akayi katoton agogon bango dashi,: Dasauri BASAM yamike tareda fadawa hadadden toilet dinshi yasaki shawar akanshi yayi wankanshi tareda dauro alwala yana fitowa ya goggoge jikinshi da towel tareda shafe jikinshi damai yafeshi jikinshi da turare jarrabiya yazaro fara me wando yasaka yataje sumar kanshi tanata sheki kayan sunyi mugunyi mashi Kyau tamkar balarabe kiraye kirayan sallah yasomaji amasallacin kofar gidansu Wanda yake hade da gidansu fitowa yayi dasauri yanata kamshi yafice zuwa masallaci,' Anyi sallar magrib basam yana masallaci yanata laximi har aka kira sallar isha sannan yafito yadan gaggaisa da mutane sukuma sunata tuttudowa dan sugaisa dashi juyawa yayi yakoma gida da sallama yashigo falon,' Bakowa afalon kaitsaye yawuce shashen Momy tareda sallama,' tanakan sallaya tanajan carbi yashigo tareda zama atattausan kafet din dakin nata,' Saidata gamajan carbinta tayi adda'a suka shafa tare tajuyo tace,'. ____"katashi Ashe natura kausar tatasheka taga bakanan sainace to katafi masallaci," ____"eh Momy ainatafi masallaci yanzu shigowata shine nazo akan maganar dakikace zamuyi ina sauraranki,' BASAM yayi tsai yana kallon mom dinshi yaji mezatace,' ____"gaskia ne BASAM to dama bawani Abu bane akwai wata Yarinya wato damuka hadu kwanakin baya da'ita akofar makarantarsu sannan danasake fita nasake ganinta yarinyar ta kwantamun araina sosai nayaba da kamalarta da shigar mutuncinta hakanne yasa harna dauketa amota zuwa islamiyya wlh bakaji kalaman bakintaba cikin biyayya gasu masu Dadi,' sainatura abakar yaganomun gidansu kuma mukayi nasara yagano naje Gidan iyayanta Yan mutunci masu San mutane an karramani agidan sosai BASAM sunan yarinyar *MEENAL*", Yayima Momy murmushi yace ___"Allah sarki mekikeso to aimusu suna bukatar taimakone?,' ___"eh to kusan hakan domun natura kawunanka wajan iyayanta antsaida magana yanzuma haka da baikonka akanta kaimuke jira dama kadawo sai agama komai,' Dasauri yadago yayinda yaji wani razanannen faduwar gaba kanshi yawani saramai bakinshi yana rawa yace,'. _____"mom banganeba mekikeso kicemunne bangane hausarkiba,' ______"uhm BASAM ina nufin meenal itace matarda Na zabama kuma kawunanka sukaje nemamaka auranta kuma anbaka dan har'ankai akwatin Nagani inaso anyi baiko,' Rassss rasss yagabanshi yasake yankewa yazube yayinda yaji kanshi yanata wani Sarawa yadafe kanshi tareda sauke idanunshi kasa zuface tashiga ketomai takota ina dukda sanyin a c din dakin wani dacine yasoma keto mashi daga kirjinshi zuwa bakinshi gawani jiri dayake kwasarshi idanunshi sukayi jajir suka cicciko da kwalla yamarasa mezaice,' ___"inkaganta zaka yaba sosai sannan kasandai bazan zabarma abunda zai cutar dakaiba amatsayina na mahaifiyarka banida burin daya wuce inga kasamu macce tagari wacce zata tsarema mutuncinka da darajar iyayanka Na tabbata meenal duk zatayi abubbuwan Dana lissafo dinnan,' Idanunshi sunzama tamkar garwashin wuta yayinda fuskarshi tazama jajir yace,'. ____"to Momy bakomai nagode dskulawarki agareni tunda tayimiki shikenan Ai,' amma meyasa ba'ayi shawara daniba kuka yanke hukuncin........ ____"aa BASAM meenal itace wacce tadace tazama matarka Domun annabi (s a w) yace ana auran mace sabida Abu hudu, Nafarko zaka iya auran macce sabida dukiyarta Nabiyu zaka iya auran macce dan kyawunta Na uku ka auri macce domun danginta wato nasabarta Sannan Na hudu ka auri macce dan addininta Sannan daga karshe Annabi (s a w) yabamu shawara ka auri macce ma'abociyar addini hannunka ta yalwata ma'ana iyalanka zasu tarbiyya irinta addinin musulunci Dan haka na kwadaitama auran meenal BASAM inkanaso raina yayi fari to ka auri meenal,' Kanshi yadafe dayake kokarin tarwatsemai wai kamarshi za'a zabama macce baza'a barshi yazabi San ranshiba yace,'. ____"shikenan Momy Na amince da auran tundahar takwanta miki aranki," Murmushi tayi mai,'. ___"alhamdullah naji dadin wannan zancan Allah ya tabbatar da alkairinshi sannan gobe kashirya da yamma zanmuje gidansu meenal din ,' Aranshi yace,' ___"ninema zanje gidansu bayan ko Bby girl dina bantaba zuwa gidansuba saidai muhadu a park wainine zanje wajan wata dasunan zance tarainanima kenan hartadauka ta'isane ina bazai yuyuba gaskia,' afili yace,'. ____"gobe inada mitting dazan attending da misalin karfe uku kuma bansan yaushe zamu fitoba kibari musaka wata rana,' mikewa yayi tsaye cikin kunan xuchiya da bacin rai yace,'. ___"nizantafi mukwana lfy,' Tace ___"to tunda kanada mitting da yamma maje da rana sabida nariga nasanar dasu goben zamuzo so yakamata muje,' Baice komaiba yafice adakin bayako iya kallon gabanshi haka yakarasa dakinshi tareda fadawa Gado yana dafeda kanshi wanda yakeji kamar zai dagargaje yace,'. _____"why Momy meyasa zakisa baki acikin rayuwata meyasazaki zabamun Matar aure bayan inada wacce nakeso why why???,' Yanaushi pillow dake kusa dashi tareda mikewa yazabura tace,'. ____"ina bazai yuyuba baxan auretaba domun *BASAN RAINA BACE,'* inada wacce nabama zuchiyata I'm so sorry Momy bazan iyaba,' bude kofar yayi tareda fita yanufi dakin Ummu yasameta tana zaune tanashan maganinta Na hawan jini yasamu waje yazauna babu annuri Sam a idanunshi,' Ummu tace,'. ____"megida takobin yaki yanaga ranka abace kazomun ayanayinda bansaba ganinkaba lafiya incedai bawani Abun bane yafaruba ko?,' Yadago idanunshi dasukayi jajir dasu yace,'. ____"magana nazo muyi domunni nasan kezaki taimakamun dan bazakiso abunda zai zamemun matsalaba arayuwata ba .' Tasowa yayi tareda tsugunnawa agabanta aguiwowinshi biyu yakamo hannunta yace,'. ___"kitaimaka kisa baki kifadama Momy inada wacce nakeso wacce zuchiyata tazama mallakinta dan nariga nabata amanar zuchiyata Momy tazomun dawani batu wanda kwakwalwata takasa dauka balle zuchiyata plz kisaka baki tajanye furucinta,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY__________________* *_Badiat Ibrahim_* *________________61to65✍🏻* __"wlh banasanta,' Ummu tazame hannunta acikin Na BASAM tareda matsawa gefe .'. ____"kasani duk wacce kakeso bazatakai nagartar meenal ba nima nakwadaitama auran meenal domun meenal salahace BASAM matan yanzu basuda tabbas ta'iya yuyuwa wacce kake ikirarin kabata amanar zuchiyarka ita awajanta bahaka bane ta'iya yuyuwa tanasankane dan wani Abu daka mallaka amma meenal ta amince da auranka batareda tasankaba balle tasan kokai waye tanayima mahaifiyayyar ka biyayya tareda kyautata mata danima kaina,' zama tayi akusa dashi takamo hannunshi tace. __"inasan kayima mahaifiyarka biyayya kaso abunda takeso karkaki bin umarninta akaronta nafarko data bukaci wani abu daga gareka kuma kanada halin yimata abun sannan Kai mijin macce hudune kana iya auran waccan bayan ka auri meenal,' Hawayanshi dayaketa kokarin tarewane suka biyo kumatunshi zurrrr zurr yamike tsaye tareda juyama Ummu baya,'. ____"naji zan aureka tundakema kin amince in aureta din amma kisani *BASAN RAINA BACE* ummu I'm so much love Basma she's the love of my life yazanyi in tunkareta da zancannan ta'ina zanfara ni atsarina babu auran mata biyu kuma bazanyiba dan bazan iyaba yazanyi da Bby girl dina?,: yasauke kanshi yayinda zuchiyarshi tashiga tafasa ___"saika bata hakuri aitasan iyaye tasan mahimmancin iyaye indai da gaske tanasanka zata tayaka kayima Salma biyayya tayi hakuri tasamu wani mijin ta aura aidama ance Matar mutum kabarinshi in kaddara ta lissafota acikin matanka dole ka aureta inkuma dama ba matarka bace bazaku tabayin aureba,'. Babana kayi hakuri ka yadda zaka faranta ran Salma dani kakarka?,' Yadago kanshi ya kalli Ummu yaga duktabi tadamu kanta gashi yana bala'in San kakarshi yadaure tareda karasowa gareta yace,'. ___"Na amince shikenan bawani Abu Ummu kiyi murmushi plz karkiyi fishi da mijinki kuma karki fadama Momy munyi wannan maganar.' Murmushi taimasa tareda kamo hannayansa tace,'. ____"Allah yaima albarka kuma bazan sanar da'itaba aini takace kokaifa.' Sukayi daria dukkansu yaimata sallama yafita,' Daki yakoma yakasama yin komai yana kwance rigingine yanata tunane tunanen yadda zaiyi zuchiyarsa tanawani tafasa tunkamun yaga wacece meenal yaji duk duniya babu wanda yatsana kamarta idanunshi sunkada sunyi jajir dukyashiga firgici,'. Yashiga tunanin Basma dinshi wanda yaimata alkawari zasu hadu yau yanada tabbacin takira wayarshi yafi sau Dari zataji akashe,' yalumshe idanunshi yayinda yabude yakurama wani zabgegen hotonshi dake jikin bango idanu shi ba hoton yake kalloba amma kai inkashigo zakaga hoton yakurama idanu tunaninshi yayi zurfi,' yabude bakinshi yace,' ___"I'm so so sorry my Basma duk duniya bawacce nakeso sama dake kuma nayimiki alkawari bazanso wataba never,' Haka yaki bude wayarshi danyasan yana budewa zata kirashi shikuma baisan mezaice mataba dankuma yasan yana daga wayarta zatasamai kuka yarasa mekiyimai Dadi a duniyarshi gashi yakasa koda runtsawa ga yunwa yanaji but bazai iyasa komai abakinshi,' Meenal tana kwance itama sai tunane tunane taketayi yayinda zuchiyarta tacika dam da fargaban gobe badan komaiba saidai tana tsoron ganin waye BASAM tareda fargabar karyaganta yace tafasa auranta inkuwa hakan yafaru batasan yazayi da rarraunar zuchiyarta mecikeda miki meyawan gaske Basma tana tsaye tareda wayarta ahannu tanata Kiran layukan BASAM amma abun mamaki harzuwa lokacin akashe idanunta dasuke jike da ruwan hawaye tadago ta zubama agogo idanu karfe 2:30am nadare tafada gadanta sharab tareda sakin kuka,'. ____"why heart beat why do u do this to me baka taba sabamun alkawariba saiyau why kasan ina mutuwar sanka gashi wayoyinka duk akashe narasa yadda zanyi,' Tasake ballewa da kuka tareda jifa da wayarta,' Daga BASAM zuwa meenal zuwa Basma bawanda yaruntsa acikinsu yadda sukaga rana haka sukaga dare har garin Allah yawaye,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY__________________* *_Badiat Ibrahim*_ *_________________71to75✍🏻* Cikin sallama tashiga Gidan khadija da mama suka amsa mata yayinda aka gaggaisa Meenal tafito kanta asunkuye tagaida Momy da fara'a ta amsa sannan tamike takoma ciki gabanta yanata faduwa,' __"amm Khadija kifita kishigoda BASAM yana cikin Mota,' __"to mama,' amsarda tabayar kenan tazari hijabinta tafita atsanake takarasa wajan motar tareda kwankwasawa,' Ahankali yazage glass din suka hada idanu da khadija zare idanunta tayi tareda rufe bakinta acikin ranta tace,' ___'lahhhh wanake gani ido da ido kamar BB dama shine wanda Anty meenal zata aure?,' inkuwa shine to wlh tamore da hadadden miji kuma jaruminda duniya tasanshi ta hanyar jarumtarshi,' __"hellow lfy malama yahaka?,'. "Firgigit tadawo daga zancan zuchinta tace,'. __"dama cewa akayi inyima jagora zuwa ciki sunana Khadija ina murnar ganinka sosai bismillah kashigo,' Yadanja wani karamin tsaki Mara sauti kana yafito ahankali akyamace yaketaka kasar Layin yabiyo bayan khadija itakuma tanata mamakin ganinshi da sallamarshi yashiga Gidan dukkansu suka amsa mama tasha mayafi yatsugunna agabanta,' ___"ina wuni mama ya gida munsameku lfy,?: ___"lfy lau yahanya kadawo lfy ko?,' ___"ahh lafiya lau mama" __"to madallah sannu Allah yayi albarka Allah ya tabbatar da aikairi' khadija kaishi falo yazauna mana,' Khadija tamike yabiyo bayanta taimasa iso har falon sannan dasauri tasomakai abincin dakin shidai yana zaune tagama tsab tace,'. ___"yaya BASAM bara inkira Anty meenal din kaci abinci gashinan,' Yabita da kallo kawai ranshi yayi mummunan baci sosai,' Dagudu khadija tashiga dakinsu hartana tuntube _"ke lfy meye haka dagudu?,' ___'uhm bazaki ganeba ina wannan shahararren dan kwallon dokinnan da kwanaki akayi hira dashi a NTA dinnan BASAM B salees wanda akabi Sani da BB ?.' __"eh natuna wani abunne yasaneshi kome?," ___"aa shine mijinki shine yakawo sadakinki shine yaron Momy shine BASAM dinki gashican afalo keyake jira,'. Jadabaya meenal tasomayi tareda tariyo fuskar gayanda akayi hira dashi a Gidan TV __"BASAM shine dama yaron Momy turkashi nasanma bazai yadda ya aureniba shida yasaba Hulda da kasar turawa ina,' ___"karkice haka karkifa manta akwai sadakinshi agidannan harda baikonshi akanki aure yarage kawai kuma dama Momy tace shikawai ake jira bakiganshiba yahadu yafi Kyau afili wlh farine sosai fa,' Meenal dai gabaki daya guiwowinta sunsage khadija tabata mayafinda tace dakanta tayafa mata kana asanyaye tafito tanufi kofar falon jikinta yanata rawa ga faduwar gaba dataketayi,' da sallama tashiga,' Harsaida tashiga ta zauna sannan ya'iya amsawa a dakile baiko kalletaba yadaura kafarshi daya kan daya yana karkadawa,' ___"ina wuni kazo lafia ya hanya?,' Saidayakusan minty biyar yadaure yace ___"lfy sannu ' Kanta yana kasane yayinda shikuma baiko kalletaba dakin yadauki shiru inbanda takaici daya rurnikeshi tareda wani zugi da zuchiyarshi takeyi babu abunda yakeji dataji shirun yaimata yawa tace,' ___"bakaci komaiba koruwa baka shaba?,'. ___"hmmmm ke nalura kinajin dadin kulani ko to kisani ninafi karfinki nesa bakusaba sannan kar kanki yabuga cewarni natako kafata nazo wajanki never kinyi kadan nazone sabida Momy kuma umarninta nabi kingane ko dan haka kikama kanki bansan kauyanci,' Maganganunshi suka huda dodon kunnenta tareda ratsa duk illahirin jijiyoyin jikinta hawayene ya gangaro a kumatunta yayinda tatsuke bakinta tayi shiru kanta yana kasa yana digar hawaye Mikewa yayi tareda wani kallamata uwar harara yaja tsaki haryakai kofar fita yatsaya tareda Ciro bandirdin kudi dubu Dari yajefa mata cinyarta yafice abunshi,' Mama tana hangoshi tasoma murmushi. __"kafito kenan abincinfa kaci kuwa?,' Yadan Sosa kanshi,'. ___"am banciba akoshe nake a office ne akaikirana ana nemanmu shiyasa tafito da wuri,' yasaka hannu a ajjihu yaciro dubu Dari ya ajjiye,'. Nizan koma,' ___"to madallah Allah yasaka da alkhari sauka lafiya,' __"mom ina jiranki amota,' yasaka kanshi yafita jiyakeyi kamar yamutu yahuta da rayuwarshi,' ___"to mama saikusoma gaiyatar Yan Uwa nanda sati biyu za'a daura aure sannan ta bangaran kayan dakin amarya wannan kibarmun komai duk abunda Uwa takema diyarta nizanma meenal kudai diya muka nema awajanku ita zakubamu insha Allah bayan meenal bama bukatar komai sannan abincin daza'aci zansa akawo muku komai.' Kuka mama tasaka tanata godiya meenal tana tsaye abakin kofar falo tana jiyosu kukanta yasake tsananta tareda tsantsar tausayin kanta saidataji tashin motarsu tafito tashare hawayanta ta daddaure bataso tabatama mama rai tabata wannan kudin tahada danawajanta daki tasoma tazauna Tarasa abunda keyimata Dadi aduniya tanaso tayi kuka kozataji sanyi amma badama,' Basma v Ce amota itada kawarta manan suna tafe danzuwa gidansu BASAM suduvashi sujiko lafiya sunkaraso kofar Gidan yayinda megadi ya tambayesu sukace wajan BASAM sukazo yabude musu suka shigo taredayin parking motarsu a harabar Gidan,' Ummu tace,'. ____"leka kigani megidane suka dawo?, Dasauri kausar taleka tahansu Basma tace '. ____"basubane inaga baki Momy tayi yan matane su biyu gasunanma shigowa,' Da sallama suka shigo tareda zama akujera suka gaisheda Ummu kausar tamike takawo musu abunsha sunadai zaune sunacin dambun kifi Basma tadauki remote tacanja chanal TAKAI inda takeao ta kalla Ummu tajuyo tace,' ___"bamufa ganekuba wajan wakukazone?,' Manan tace ___"sunana manan wannan kawatace Basma munzo wajan BASAM ne Basma budurwarshice munkawomai ziyarane,' Basma tace,' ___"eh hajia nice batsman shi dama munzone muganshi yana cikine?,' Mamakine yakashe Ummu da kausar kamun suce wani Abu motar BASAM tashigo Gidan ', *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE*. *BY_________________* _*Badiat Ibrahim*_ *___________________76to80✍🏻* "Momy cetariga shigowa cikin sallama daukeda farin ciki a fuskarta ganinsu Basma yasata karaso,' ____"sannunku ahh baki mukayine kausar kawayankine?,' Manan tace,'. ___"amm sannu Momy ina wuni?,' ___"lfy lau Yan mata daga ina?,' ___"dama munzo wajan BASAM ne ,' Mamakine yacika Momy tace,'. ___"BASAM kuma?. Da sallama yashigo falon yana ambatan ,'. ____"Matas matas bazakizo kizo kimun tarbaba ko?,: carab suka hada idanu da Basma gabanshi saidaya fadi yayi kasake awajan yana kallonsu cikin tuhuma,' Ummu tamike tace,'. ___"saika karaso ga bakinka nan suna jiranka.' Tajuya tawuce kausar tabiyo bayanta suka wuce ,' Momy takuramai idanu yayinda Basma takurama BASAM idanu juyawa tayi tawuce daki falon yarage dagashi saisu,' Ahankali yakaraso tareda zama akujera yarasa mezaice mata karasowa tayi kujerar dayake tazauna tareda kamo hannansa tasaka anata dagowa yayi suka hada idanu idanta ya soma Tara ruwan hawaye girgiza mata kai yayi halamar kartayi kuka yamatse hannunta anashi taruntse idanunta hawayan yazubo akumatunta dasauri yasaka babban yatsanshi yana goge mata hawayan,' ___"why heart beat menayima zakamun irin wannan horon metsanani kaki kunna wayoyinka narasa yadda zanganka kaduba rabonmu da waya tun randa zakadawo najeria damukayi waya shikenanfa naje office dinka akace kana gida kana Hutu why?,' Gabaki daya kanshi yadauki zafi yarasa yadda zaiyi da Bby girl dinshi yasan halinta sarai. ___"come on Bby girl relax bakimun komaiba nikaina nadamu da rashin ganinki da jinki ina bukatar hutune sabida nasha wuya shiyasa nakashe duk wayoyina sabida inhuta kinsan bazakimun komaiba dazanyi fishi dake u are the best kinsani Ai plz Bby girl smile come on 😃 Murmushi taimasa tareda dan dukan kirjinshi ,'. ____"amma kabani wuya dayawa harda nasoma tunanin to menayima,' ___"ohhhh no bakiyi komaiba oya kuci abinci ina zuwa ko,'. Yamike tareda shigewa dakinshi yarasa yadda zaiyi da Basma yazataji inyasanar da'ita aure za'aimai shikanshi yana shakkar sanar da'ita Tamike tareda karasawa gaban hoton BASAM garjeje ajikin bango yanakan farin doki yana murmushi yasha fararen kaya yayi mugun Kyau tashiga shafa fuskarshi ahankali yayinda manan tagamacin dambun kifin takorada. Drink daidai BASAM yafito tace ' ___"heart beat zamutafi dama inganka ne kawai kafadama su Momy zamuwuce,' ___"wucewa yayi dakin Momy sa sallama tana ganinshi tahade rai,' ___"wadanne Mara kunyan yarane sukazo wajanka suwaye su badakai nake maganaba BASAM,?' To karnaji karna kuma ganin kafarsu agidanan kanajina?,' ___"kiyi hakuri Momy fan's dinane kawai kuma aidole inkula fan's dina Momy aduk inda suke masoyanane kiyi hakuri fan's ne kawai,' ___"to naji shikenan yawuce ,' Tare suka jero har falon sukayi sallama da Momy suka wuce yarakasu wajen motarsu sukayi sallama yadawo kaitsaye yashiga dakin Ummu tadingamai fada akan Basma,' .___"dama wannan fitsararriyar yarinyar kake kokarin kawomana cikin family dinmu kabani kunya har macce zata kwaso kafarta tazo gidansu amsaurayi nemanshi ba kunya tazauna akujera gardawani canja chanal yayima Kyau,' ____"haba Ummu nafabaki hakuri kuma in Momy tasan Basma itace budurwata wlg zata batamun rai yanzuma saida nace fan's dinane shinefa tasakko,' Ummu tace,'. ___"yawuce megida bazatajiba,' sukaita wasanninsu dasuka saba yakoma daki cikeda tunane tunane,' Haka akaita shirye shiryen biki agidan BASAM Ko'a jikinshi bai gaiyaci kowaba kuma baida niyar gaiyatan kowa sai abokinshi amininshi wato Khalid shima Momy ce tasanar dashi BASAM yaki fadamai yanzuma suna dakine shida Khalid,' ___"waibakasan abun takaiciba Momy wai harwani honeymoon tashirya washe garin kawo amarya wai zamu wuce kaikaji bakaga yarinyarba bagidajiya abun kunyane wlh aganni da'ita wlh jinakeyi kamar zanmutu wlh inna tuno wai yarinyarnan za'abani ,' Khalid yace,'. ___"ni wlh daria abun takebani inbanda iyayanmu da karambani inasu ina zabamana matan aure alaji abarka kaxabi choice dinka barinma kaidakake star kowa zaiso ganin wacce mesa'arce tasameka kawai Saikuma aga Beb din gashi kace Yar kauyece badadin ji wlh,' ___"kaidai bari shiyasa banfadama kowaba secret marriage zanyi duniya bazatasan me'ake cikiba sai lokacinda zan auri Basma haba Ai itace text dina,' Sukaita aibanta meenal baiwar Allah,' Gidansu meenal acike yake dam da Mata anata dafa lafiyayyan abinci harda kaji amarya kuma tana zaune ana kyaramata kai anamata Jan lalli tayi Kyau fatarta tamurje tasake haske,' Hajjo kuwa tanata hada hada da kawayansu Na islamiyya dasuka gaiyato sunata surutai irinna kawayan amarya Baraka tace,' .___"Allah yayi BASAM shizai dauka shiyasa kaddara tarabaki da Yusuf da Anas gashi kinyi dace da masoyi jarumi wanda jarumtarshi tafito duniya tasani gaskia Kawata inatayaki murna bansan wanne irin Kyau yaranku zasuyiba ke mekyau mijinki me Kyau,' Hajjo tace gashi abun Dadi da'ankaita Gidan mijinta washe gari zasu wuce honeymoon abunsu har kasashe uku naturawa suje suhuce gajiyar biki gaskia abun kwanin Kyau.' Meenal tanajinsu sunata surutansu batace musu uhumba itadai,' Yan guima sunata shigowa dansuyi gulma anata Yan kutsiri tsoma cewar duk yadda akayi mijinda zai auri meenal baisan kanwarta garin zubarda ciki tamutuba,' Kujifa halin dan Adam afili yanunama farin ciki yaxoma amma acikin ranshi bahakaba yana nuna adawarshi agareka Allah yashiryemu,' Da daddare akasa amarya a lalli tanata kuka akabama kawayan amarya dubu saba'in NASA lalli kawai haka suka kwana da amarya dan dasafe bayan andaura aure za'atafi walima Tamara zallah wacce aka gaiyaci malaman addini mata irinsu malama barira wacce tayo tattaki daga garin Kaduna irinsu malama Aisha wacce tazo daga garin Kano,' Haka gidansu BASAM yakacame da yanzuwa da abokan arziki acike Gidan yake dam shikuma gogan yana park shida abokinshi Khalid suna jiran isowar Basma domun susanar da'ita meke faruwa BASAM jikinshi dukya mutu baisama ta'ina zaifaraba motar Basma tashigo cikin park din yayinda tayi parking tafito tanufosu,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY________________* *_Badiat Ibrahim_* *________________86to90✍🏻* Jerin gwanon motocin masu kawo amaryane suka shigo harabar Gidan anfitoda amarya tanata kuka kaitsaye akashige da'ita falo Gidan acike yake malik basu tsayaba sai cikin dakin Momy anan aka ajjiye amarya tana mayafi tanata kuka idanunta sun bunbura ankawo musu abincin kawayan amarya soyayyar shinkaface da pepper chicken sai drinks sukaci sukasha Yan uwan meenal manyan suka tafi yarage sai kawayan meenal kawai hajjo tana kusa da meenal tamatso kusada kunnenta tace,' ___"Kawata kekinga tangama tangaman hotunan BASAM kuwa acikin falonsu manya manya wasu yanakan dokinshi yana gudu wasu yahau dokin yana daria aka dauka bakiganiba abun shaawa,' Meenal batace komaiba tadan zame mayafinta tanadan shan iska dataji motsi saitarufe dan anata zuwa ganinta haka akawuni ana bikinnan Saida magrib ummu tashigo dakin tace', ___"to kishiyata Nazo siyan bakinki tunda abokan ango basu karasoba gadare yanayi kawayan amarya kufadi kudinku a sallameku motoci suna jiranku awaje,' "Hajjo tace,'. ___"to Ummu duk abunda aka bamu allah ya amfana,' Taciro dubu Dari biyu tabasu sunata godia sukaima meenal sallama suka wuce,' Itadai tana zaune tanata kukanta ciki ciki abun tausayi kausar tazo tazauna da'ita ita ta taimaka mata tayi alwala tayi sallah,' Tana takure adda tashigo kanwar Momy tace,' ___"ayya am amarya tatakura kausar kaita dakin BASAM tasamu taci abinci ta kwanta itada sukeda tafiyar asuba,' Kausar tariko hannun meenal harzuwa shashen BASAM tabude dakin suka shiga afalo meenal tazauna akujera kausar tadan dafata,' __"Anty bara inkawo miki abinci kici saikidan huta kamun yaya yazo,' ___"to kausar nagode" Tawuce taje tahado mata abinci takawo Mata sannan tabata waje,' Haka meenal tadan caccakali abincin tasha ruwa dan yunwa takeji sosai shiyasama harta iya cin abincin tanadai zaune kwalam ita kadai saitana tuno zamanda sukeyi atsakar gida sudasu mama suita hirarsu cikin annashuwa dajin Dadi tashare hawayanta kausar taxo tafitada kayan abincin,' Meenal tanata kallon hotunan BASAM kala kala da hotunanshi ba award's daya karkarba gasunan tareda turawa dadai sauransu,' Sai shadayan dare yashigo Gidan rannan nashi abace yake sosai babu ko fara'_a a fuskarshi yana shigowa yasamu su Ummu dasu Momy hardasu adda afalo yace,' __"sheet nasan wadannan nisuke jira,' Aikuwa anaganinshi suka kirashi yakaraso sukaitamai nasiha sunajan kunnenshi Momy tace,' ___"saika hada akwatinka jirgin karfe bakwai zakubi meenal kausar tahada mata duk abunda zata bukata kaje kasameta tana dakinka nasanma tagaji da jiranka tayi bacci,' Aranshi yace ___"wat dakina kuma meyasa xa'akai kazamar yarinyarnan dakina kalan tasani amai?, afili kuma yace ___"to nagode muku saida safenku yamike yanufi dakinshi afusace yana shiga yaganta atakure akan kujera tayi bacci sanyin a c yatakurata ta dukunkune,' __"whaaaaaat kujerarda nafi laba'in so arayuwata ashi wannan kazamar yarinyar takwanta Tabb yacije lips dinshi tareda tunanin mezaiyi mata yayi tsai yana tunani 🤔 murmushin mugunta yayi yanufi Frisch yadauko ruwa sassanya cikin gora yana zuwa yabude gorar yawatsa mata ruwannan a fuskarta da jikinta gadan karan sanyi,' "Agigice tamike tsaye tana digar ruwa suna hada idanu tasauke kanta kasa jikinta yanata rawa tatsorata sosai,' ___"bakida hankaline zaki kwantamun akujera da wannan kazamin kijin naki kina tunanin anan dakin zaki kwanta dani ni ina bedroom kina falo karya kikeyi kichin zakije kikwanta inrufeki kazama,' wuce muje,' Tabi bayanshi sum sum harzuwa kicin yace,' ____"nanne daidai dake kazama kawai,' yatureta tafadi yafice tareda garkame kichin din,' Kuka takeyi ranta daya tatakure ga sanyi gashi akasane sanyin tail's yanata ratsata tarasa yadda zatayi haka ta shimfida dankwalin kanta amma ina shima ajike yake ga jikinta duk ruwa haka tazauna tanata kuka can tahango table awajan tahaukan table din takwanta tanata rawar sanyi abun tausayi,' BASAM kuwa yana tattausan gadanshi yayi wanka yasaka kayan bacci yana cikin bargo suna waya da Basma ahaka dai bacci yadebeshi cikeda tsanar meenal da kyamarta Meenal tanata tuno nasihohinda mama taimata taimata tatuno dakinsu dakuma kan katifarta da bargonta tasake fashewa da kuka yaugashi itace a kichin zata kwana abun tausayi,' 😭😭😭😭😭😭😭 *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY________________* *_Badiat Ibrahim_* *_________________96to100* Tadade tana kuka a durkushe awajan sannan tajawo akwatinta zuwa cikin dakin tanata karema dakin kallo aljannar duniya bazakayi tunanin hotel bane komai akwai namore rayuwa zama tayi tareda zuba tagumi tanata kallon dakin da girmanshi ace itakadai zata zauna kwana da kwanaki,' Murmushi tayi tareda mikewa tanufi toilet nanma tadinga kalle kalle tazama Yar kauye sosai dakyar taga yadda zata kunna shawa tayi wanka wanka tayi tareda dauro alwala tafito tazage zip din akwatinta tazaro dadduma tareda katan hijabi tatada kabbarar sallah ta gabatarda sallolinda akebinta hannu tadaga tanata kuka tana rokon Allah yakawo mata agaji da dauki tana hawaye tashafa adda'ar tamike tareda zama jigum da'ita kwankwasa kofar taji anyi atsorace tatashi tareda nufar kofar taleka taramin kofar saitaga ma'aikatan hotel dinne tabude maccece daukeda trai Na abinci cikin ladabi tagaisheda meenal cikin harshen turanci da fara'a ta amsa tareda wucewa ta ajjiye mata abincin tawuce,' Dawowa meenal tayi tareda dafe kanta dakyar ta'iyacin abincin shima dantanajin yunwane sosai TV takunna amma hankalinta bayagun tvn kwata kwata tanata tunanin gida mamanta da khadija yanzu tasan sunacan suna kewarta gashi babu wayarda zata kirasu wayarta bazata iya kiransuba da'ita gashi tanasanjin muryar mama da Khadija amma ina,' Haka meenal tadinga tubka da warwara,' BASAM yana kwancene bayan yayi sallah yaci abinci yana hutawane domun yagaji gawani tukukin bakin ciki dake turnikeshi inyatuno waida wannan bakauyiyar yarinyar akasa yataho wannan haddaddiyar kasar,' Tsaki yaja tareda mikewa dama ashirye yake tsab takalmi yadaura akafarshi tareda ficewa yashiga cikin gari tareda siyan sabon sim dazaiyi waye wayanshi kana yazauna awani joint yanadan nishadinshi amma daya tuno fuskar meenal take sairanshi yabaci sosai ahaka yadawo hotel din yana zaune a farfajiyar hotel din akan daya daga cikin fararen kujeru da aka tanada dan shakatawa tareda wasu rumfuna kyawawa dagacan gefe kuma yanmatane da samari suketa rawa yaran turawa," Wayarshi yakara akunne yasoma kiransu mom ,' ___"hello mom munsauka lafiya shine nace bara inkiraku insanar daku dan hankalinku ya kwanta,' Momy tace ____"alhamdullah mungode Allah ina meenal bani ita muyi magana tana kusa dakaiko,"? Shiru yayi nawucin gadi tareda rashin sanin amsarda zaibama Momy domun tasan lalle yanzu yakamata suna tare to mezaice mata?,' ____"kayi shiru lafiya cewanayi kabani meenal muyi. Magana yanzunnan,' Cikin kunar rai da takaici tareda sake tsanar meenal musamman yadda yaga Momy tadamu da'ita sosai,' ___"amm mom tana bayine bara tafito saikuyi magana ko mom?,' ___"to zankira dakainama domun inaso in tambayetane wani Abu me mahimmanci,' Yazazzare idanunshi waje taredajin tsoro tome Momy zata tambayi yarinyarnan to?'. Bashida mebashi amsa haka akabashi Ummu awaya sukaita surutai kausar ma data karba tace tanasan waya da Anty meenal bayan yakashe wayar dasauri yamike tareda haurawa sama," Abakin kofarta yatsaya yakasa kwankwasawa dan yatsani ganin fuskarta arawarshi yarasa yadda zaiyi gashi yana tunanin inya kwankwasa kofar tabudemai kamar ajinshi yazube dan zatayi tunanin yabiyotane,' Yadafe kanshi tareda runtse idanunshi yace,'. ____"ohhh my gosh yanzu meye abunyi in mom takirani incemata me?,' bata taba yadda daniba to menene mafita?,' Yanadai tsaye abakin kofar dakin,' nan wayarshi tasoma ruri yana dubawa yaga mom kekiran wayar tashi kamewa yayi awajan tareda rashin sanin mafita!' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY_______________* *_Badiat Ibrahim_* *_______________101to105* Juyawa yayi dasauri tareda karasawa reasepshion ya tambayi abashi key din dakin nata akabashi yasake komawa ga Momy tanata kiran wayarshi yana karasawa yasaka key din yana murdawa dakarfi itakuma tayi tsuru tsuru tsoro dukyabi yakamata ana turo kofar tarufe idanta tareda sake wata Yar kara,' Kallon tsana yaimata tareda karasowa cikin dakin Itakam har lokacin idanta arufe dan batasanma wanda yashigoba saidata tsinkayi amon muryarshi,' ___" ke zonan yanzunnan kizomun bansan hauka,' "Jikinta yana rawa takarasa tareda tsugunnawa a gabanshi yawani kalleta kafarshi yadaga ya take hannunta data ajjiye akasa dakarfi harsaida sukaji ciwo,' Ihu tasaka tareda saurin dauke hannunta tana yarfewa idanunta suka cicciko da ruwan hawaye tayi kasa dakanta suka soma zubowa sharsharshar,' ____"to bara kiji karkiyi tunanin konazo wajankine aa kodaya nazone inbaki phone kuyi magana da Momy idan koda wasa ta tambayeki akanwani abu kika fada mata kasheki zanyi inkashe banza insa aburneki babu meji,' ga wayar kuyi magana kuma kiyi daria dole,: oya,: Tasaka hannu ta amshi wayar tareda karawa a kunne.' ___"salamu alaikum sannu Momy ina wuni?,' ___"ohh Ameen wa'alaikis salam my dear meenal yakike kun Isa lfy ko?,' nakira tuntuni yace kinshiga toilet hop everything is fine?,' Tadago suka hada idanu da BASAM yazare mata idanu Tareda kada mata kai tace eh,' ___"lfy lau Momy yasu Ummu da kausar?,' ___'lafiya lau meenal yaushe zaisoma kaiki yawon bude idanu kusoma zazzagawa ?,: Cikin in'ina tace,'. ____"amm amm dama am saizuwa gobe tukunna munhuta eh Momy,' ___"to yarinyata shikenan anjima zamuyi waya ko?,'.. Tasake kallon BASAM yawani harareta tareda tokararta tafadi bakinta tatoshe kar momy tajiyo wahalallen ihun data saki haka tana hawaye sukaita waya dasu mom,' Haka BASAM yacigaba da gana Mata azaba kullum saiya cusguna Mata amma tadauki hakuri dan tana tuno nasiharda mama taimata taredajan kunnen dataimata,' Sunacan sunata murna meenal tana kasar waje itada mijinta khadija tace,' ____"allah sarki Anty meenal tanacan tanata yawon bude idanu sainakeji dama nice mama inganni awaje mekyau inga turawa inyi kalle kalle inyi hotuna,' Mama tayi murmushi tace,'. ___"kema Allah yabaki khadijana fatana kema kisamu miji kiyi auranki sai hankalina yafi kwanciya inamiki adda'a Allah yabaki miji nagari mesanki dasan danginki kamar BASAM din meenal,' Khadija tarufe idanunta tanata daria mama taimata daria itama,' Wasa wasa satinsu BASAM uku a London yaki yadda suke wani kasar kamar yadda Momy tatsara zasuje kasashe uku yaki Sam,' Meenal tana zaune tayi tagumi tana goge gefen fuskarta dayake zubda jini BASAM ne yakwada mata glass cup awajan yafashe gogewa taketayi taredasa ink awajan sanye take cikin abaya pink tadaura dankwalin abayar hawayanta tashare tareda danyin murmushi BASAM ne yasake bankado kofar yashigo dasauri tatdugunna tanabashi hakuri ___"shishshs rufemun baki ki tattara kayanki zamutafi gida shashasha bakauyiya kimun sauri ina waje,' . Dasauri tadaga mishi kanta tareda mikewa tasoma tattara komai nata tahada a akwati kana tasaka hijabinta har kasa tafito dasauri tahau lifta tasauka kasa,' Taga bakowa awajan tashiga juye juye bataga halamarshiba takoma tanata kwankwasa kofarshi bakowa aciki atsorace tasake sakkowa tatare Mota tace takaita airport,' Tashiga motarnan tanatajin tsoro kartazo tabace yatafi yabarta suna karasawa tahangoshi yasauka kenan shima yabiya kudin motar kana yabarmata akwatinshi tanataja dakyar harsuka shiga harabar filin jirgin anakan layi anata kiran sunaye harsuma akakira nasu suka shiga tazauna awaje daya itakadai kanta bala'in ciwo yakeyi mata gakuma ciwo agefen fuskarta Wata matace tashigo itama dagani Yar najeria ce kuma musulma dan tayi lullubi abunta tayi Kyau gata Yar gayu takalminta yanata kwaskwas tazauna kusada meenal cikin sallama,' Meenal kuma cikin ladabi ta amsa tareda gaisheta cikin fara'a cikin ladabi,' Babbar matace sosai dagani tanada kudi sosai dan yanayin kayanta dayanayin shigarta sunbaiyana hakan,' Meenal dai tayi shiru abunta can wannan Matar tace,' ___"Baiwar allah menene sunanki kuma wanne gari kike kekadai kikazo London naganki Yarinya dake,'? Meenal tayi murmushi tace,'. ____"sunana meenal a Katsina nake sannan bani kadai nazoba nida mijinane honeymoon mukazo,' ___"mijinkifa kikace shine bakuzauna kujera daya dashiba kikazauna agefe ga fuskarki cikeda damuwa ina mijin naki yake?,'.. Meenal tanuno mata BASAM daidai yajuyo kuwa yana magana da ma'aikatan jirgin,' ___"kina nufin BASAM b salees yayi aurene dama yaushe koba wannan shahararren dan kwallon dokin nanba wato polo?,' ___"shinedai hajia satinmu uku dayin auran amma duniya batasan yayi auranba,' idanun meenal ya cicciko da ruwan hawaye,' Matarnan tayi shiru taima meenal kallon sharia guda daya saitaga fuskarta akwai damuwa,'. ___"meenal zan taimaka miki da'ikon Allah sunana hajia kaltume madawaki ina zaune agarin Kano tazuge Jakarta tareda Ciro katinta Tamika mata,'. __"wannan katinane kinemeni aduk sanda kike Neman taimako kinji?,' Hawayan da meenal take tarewa ya gangaro kumatunta tareda saka hannu ta amshi katinnan tasaka a Jakarta taima wannan hajia godia haka sukaita dan hira jifa jifa,' Awansu ashirin da hudu,' Jirginsu yasauka a airport,' Momy da Ummu da kausar suna zaune suna jiran jama'ar cikin jirgin susoma sakkowa,' Momy tace," ___"Allah Allah nakeyi inga diyata meenal nasan tasakeyin Kyau tayi fari,' Ummu tace,'. ___"Ai megidana ya'iya tattalin macce sosai,' Sakkowa akafarayi sukuma suka mimmike tareda zuba idanunsu,' BASAM yarike hannun meenal yana zare. Mata idanu,' ___"inbakiyi murmushiba harkikasa su Momy suka gane wani Abu ko,' wlh saina ballaki oya muje kifara murmushi,' Kakaro murmushi tasomayi tayaba a fuskarta sannan suka saka soma sakkowa,' Hangosu su Momy sukayi hannunsu rikeda juna sunata murmushi suna sakkowa harsuka karasa sakkowa,' Momy tarungume meenal yayinda Ummu ta rungume BASAM sunata farin cikin ganin junansu,' Momy tadago fuskar meenal takuramata idanu taga fuskarta tadan rame gakuma ciwo agefen fuskarta yasake tallafo fuskar tagani tace,' ___"meenal meyasameki agefen fuskarki haka?,' Ba meenal kadaiba hatta BASAM saida gabanshi yafadi hada idanu sukayi itada BASAM,' Ummu takatse shirun dacewa,'. ___"yanzudai mukarasa gida kinga agajiye suke insuka huta koma meye atattauna ayyau zamusha hira sosai,' BASAM yace,'. __"sosai kuwa harsaikun kuremu meenal tanata dokin dawowa gida taga Momy tabata labarin abubbuwan datagani,' Daria sukasa dukkansu kana momy tarike hannun meenal suka wuce su Ummu ma suka wuce,' Meenal tashiga motar momy yayinda BASAM yashiga motarsu Ummu yanata fargaban kar meenal tafadama momy shiya buga mata glass cup agefen fuskarta yafashe,' Hakadai sukaja motocinsu suka nufi gida,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY_______________* *_Badiat Ibrahim_* *______________106to1010*✍🏻 Motorsu tayo hon abakin get megadi yataho dagudu ya wangale musu get suka shigo ma'aikatan gidanne suka fiffito tareda zuwa yima amarya da ango murnar dawowa sai .murmushin yake sukeyi ahaka suka shiga gidan kaitsaye sai daining table suka zazzauna kausar ta zuzzuba musu abincin shinkaface jalob taji kayan lambu sai soyayyan kaji da tuwon shinkafa miyar agusi,' kowa yamaida hankalinshi wajancin abinci momy tace,' ___"fadamun BASAM meyasamu meenal naga tarame kuma ga ciwo katoto agefen fuskarta hw come's?,' Yadago idanshi yana kallon momy yayinda meenal itama taketa kallon BASAM taji amsarda zai bayar,' ____"amm dama tadanyi ciwo ne harta kwanta a asibity gudun karmu tayarmuku Da hankali musamman ke momy meenal tace karna sanar daku,' Ciwannan kuma jiyane zatashiga bayan gida jiri yadebeta tafadi shine taji ciwon,' ___"garin yaya meyasameta kaje asibity me Dr yace maka?,' Yasake Sosa kanshi yace,'. ___"zazzabine saikuma canjin ruwa shine kuma tasha magani harda allura," ___"amma BASAM shine kabarta tashiga bayi itakadai kasan batada lfy?,' Yarasa mezaice kuma yayi tsuru tsuru meenal tace,' ___"momy ninace yazauna danyagaji shine yazauna jikawai nayi jiri yadebeni banyi auneba nafadi baida laifi,' Murmushi yayi yace,'. ___"momy diyarki taurin kai gareta bataji kina ganinta,' yadan taki kanta kadan sukasa daria sungamacin abincinsu BASAM yatashi yace,' ___"zanje inyi wanka inada miting a office me mahimmanci Matar innadawo zakisha labarin kishiyarki harsaikin Gaji,' ___"to megida saikadawo adawo lafiya,' Momy takalli meenal tace diyata kishiga dakin kausar kiyi wanka mekikeso yanzu?,' Tace,'. ____"dama inaso inje ingasu mama da khadija ne,' Murmushi momy tayi tace kije kiyi wankan saikisamu kidanyi bacci da yamma sai direba yakaiki kigansu ki?,' __"to momy nagode," Sukawuce itada kausar tayi wanka tsab tasake kaya aikuwa tanayin sallah tahau Gado batasan sanda bacci yayi awon gaba da'itaba,' BASAM yagama shiryawa tsab cikin wata sut fara Sol da'ita yayi Kyau yasaka takalminshi sauciki fari yayi mugun Kyau yanata tashin kamshi yataje kanshi tareda shafe sumarshi damai,' Kana yafito a gaggauce yaimusu sallama yafice afarar motarshi yana karasawa yaga Yan jarida tab gun yanakuwa fitowa sukayo kanshi tareda tbayoyi kowa yanata tambayarsa masu daukar hoto sunayi masu rubutu sunayi haka yakasa magana yawucesu yana shiga akafaramai murna domun matsayi da'aka karamai wanda shibaima saniba sai yanzu nanfa yashiga murna akashiga mitting da manyan manyan Yan polo wadanda sukazo daga kasa kasa nanfa akashiga tattaunawa tareda ciccike wasu takaddu BASAM yasassaka hannu nanfa akaci akasha nanfa akashiga daukar hoto yayinda Yan jarida suketa rubutu anfito mitting BASAM yashiga motarshi yafice Meenal tagama shiryawa tsab cikin shigar kamala tafito tanadan murmushi,' ___"momy nagama. Shiryawa,' Momy tajuyo tana kallon meenal taredamika mata wata katuwar farar Leda me kayau kayau cikeda kaya fal tace,'. ___"kikaimasu mama tsarabar tasu in BASAM yadawo zaizo yadaukeki kudawo diga kigaida kowa dakowa,' Meenal tashigayima momy godia sannan tafita direba yana canta harsuka fice agidan,' Sunata tafiya har sukazo kofar gidansu dagacan gefe kuma mazane cike sunata hirarraki suna hangota akashiga gulma abakar yafito yabude mata Mota tafito sannan yarike mata ledarta tace,' __"dakabarshima zanrike wlh karka damu bani tasaka hannu ta amsa tareda wucewa ,'. Shikuma yakoma yaja morarshi yatafi yayinda itakuma tashiga cikib gidansu da sallama,' Mama tana kwance atsakar gida batajin dadin jikinta yayinda Khadija take damama mama kokko,' ___"ahh Anty meenal sannu dazuwa,' aguje khadija takaraso ta rungume yayarta tana murnar ganinta,' ___"aa sannu mama lfy Khadija meke damunta haka duktarame tana kwance?,' ___"amm dama ciwo tadanyi shekaranjiya damukaje asibity shine likita yace wai takamuda wajan jini da ciwon sugar,' ____"innalillahi'wa'inna ilaiyin rajiun hawan jini da ciwon sugar Maman?,'. Sannu mama amma yakarfin jikin naki,' meyasa basubaki gadoba kuka dawo gida kuka kwanta?,' "Adaddafe mama tamike zaune tanadanyima meenal murmushi tace', ___"meenal naji sauki ma sosai kuma ninace sudawo dani gida domun kwanciyar babu amfani Sam,'. Jikinnawa saidai adda'a amma inaganin nesace tazo kusa,' Cikin kuka meenal tace,'. ___"aa mama baxaki mutuba kimutu kibarmu dawa bamuda kowa saike sai Allah Allah zaibaki lafiya insha Allah aicuta ba mutuwa bace,' Suka daddafa mama suna kuka cikin nunfashi sama sama tace,' ___"kayya nikadai nasan abunda nakeji ajikina koda ta Allah zata kasance dani nasan dangina dasukenan bazasu yadda surikemun khadijaba balle kuma dangin mahaifinku dasuke ganin bakina akan rasuwar Fatima meenal akwai Yar uwata a Kano hajia kaltume babbar matace tana nasarawa G R A akano kikaimun khadija can tazauna kekuma kirike surukarki tazama tamkar mahaifiyarki mijinki kuma kirikeshi hannu bibbiyu yazame miki uba agareki Allah yaimuku albarka yarana,' Inbanda kuka babu abunda su meenal sukeyi sunata mama bazaki mutuba,' ___"la'ilaha'illallahu muhammadun rasulillah,' Kan mama yakarye yayinda idanunta suka soma kallon sama,' ___"mama karkitafi kibarmu dawa zamuzauna wazamu gani muji Dadi mama kitashi kitashi mama,' Meenal tashiga jijjiga mama amma ina khadija tarasa mezatace ihu tasaka mekarfin gaske take makwabta sukajiyota nandanan akasoma shigowa su meenal da khadija sunajikin mama suna kuka abun tausayi,' Kulli nafsin za'ikatul maut Duk daukacin merai mamacine,' Meenal wani shidewa tayi tasake fashewa da kuka kankace me dangin mama dangin abbansu suncika gidan maza da mata,' Khadija ce tadaga wayarrta takira momyn meenal tasanar da'ita tana kuka kamar ranta zaifita,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY__________________* *_Badiat Ibrahim_* *______________111 to115✍🏻* 'Agaggauce momy tafito duktabi tarude Ummu tana ganinta tamike,' ____"Salma lfy meke faruwane?,' Cikin murya kasa kasa tace,'. ___"Ummu mahaifiyar meenal Allah yaimata rasuwa yanzunnan kutaso mutafi yanzunnan,' ___"ALLAHU AKBAR Allah yajikanta Allah yabasu hakuri Allah yayafe mata kausar kisamemu amota kidauko mayafi,' Wucewa sukayi da gaggawa momy tadaga wayarta takira BASAM,' ___"kasamemu agidansu meenal rasuwa akaimusu yanzunnan kataho dawuri kasamu sallar gawan,' Kausar tafito dagudu suka wuce fuuuu fuuu gudu sukeyi sosai nandanan suka karaso kofar Gidan ancika makil maza haka suka kutsa tareda shiga cikin gidan nanma matane dam Gidan anata koke koke anyima mama wanka annadeta a lukkafaninta masu kawo makara kawai akejira,' Meenal tana hangosu momy tataso tana kuka kamar ranta zaifita tafada jikin momy'. ___"tatafi tabarmu munzama marayu babu Uwa babu uba bamuda kowa shikenan mutuwa metonan asiri kenan,' Sulululu meenal tafadi sumammiya nankuma akayo kanta aguje Khadija tanata jijjigata tanacewa,' __"karkitafi kibarni dan Allah nidawa zan zauna kitashi Anty meenal kitashi karkitafi kibarni kamar yadda Fatima da mama sukatafi suka barmu kitashi,' Kowa nawajan saidaya tausayama meenal da Khadija momy tace,' ____"kausar kamata mutafi asibity Khadija kuzauna da Ummu munazuwa,' Sunfita da'ita tana sankare kowa yanata kallonsu sunshiga Mota dasauri sai asibity,' Mazane akofar Gidan acike Anas shima yazo Yusuf shima yazo suna wajan,' BASAM ne yakaraso wajan dasauri yafito amotarshi yayinda jama'ar wajan suketa kallonsu ana nunashi shine wannan dan kwallon dokin,' Yakaraso yanata gaggaisawa da mutane kana yashiga Gidan yaimusu ta'aziyya nanyaga Ummu tasaka Khadija ajikinta tana rarrashinta,' ____"BASAM kaga ikon Allah ko mutuwa kenan medauke wanda wa'adinshi yacika kowa dan hakane,'. Momy da kausar suna asibity wajan meenal tayanke jiki tafadine,' ___"to ummu Allah yajikan mama khadija sai hakuri kiyi hakuri nizankoma waje wajan maza,' Yafita yasamu gefen wasu matasa yatsaya yayi shiru shikanshi baisan meyake tunaniba wadannan matasa kuwa saisuka soma magana,' ___"ohhh mutuwa kenan yanzu gashi mamansu meenal tarasu zataje ta taradda diyarta wanda suka jagoranceta tamutu wajan subarda cikin shege ,' BASAM yayi tsai tareda mamakin abunda samarinnan suke fada amadu yace,' ____"duniya ba gaskia saikuga yarannan acikin hijabi da kamala a fuska amma abun ba hakaba shege ayarsu sukeyi awajan layi inace ahakanne Fatima kanwar tasu takwaso cikin shege Yan uwanta kuma sukakaita azubar garin zubarwan kuma tarasu ohh jama'a Bello yace,' ____"kuhangacan zakuga Anas inace shine da zai auri meenal din har anmusu baiko iyayan sukaji labarin yaisu meenal Yan iskane rikakkun Yan iska kanwarsuma garin zubarda ciki tarasu akafasa to kamun Anas dinma kunga wancan farin saurayin?,' dukkansu sukajuya sukaga Yusuf ciki harda BASAM dayakeji kanshi yana saramai ,'. ___"toda shiza yakawo sadaki akafasa Saikuma kwatsab naji labarin ta auri wani hamshakin me kudi,'. Ai inaji nace nasan baisan suwaye meenal ba shiyasa ya aureta amma dukranda allura zata tono garma zaijine,' Sunata gulmarsu BASAM kuwa harwani jiri yakeji yayinda ranshi yayi mummunan baci yanata maimaita kalamansu akanshi aranshi yace,'. ____"lallai yarinyarnan asirinsu yatonu dan ko momy datakesanta intaji wannan labarin bazata sake kaunartaba Allah nagodema daka baiyanamun gaskia acikin sauki,' Anfitoda gawar mama Khadija tanata kuka aka ajjiyeta agaban Gidan akasomayi mata sallah gashi tayi mutane sosai daganan aka dauki mama zuwa gidanta Na gaskia,' ALLAHU AKBAR Meenal kuwa anshiga da'ita wani daki anata kokarin ceto rayuwarta cikin gaggawa dakyar suka samu nunfashinta yadawo tasamu bacci dan anmata allurar bacci Dr yafito yanadan share zufarshi,' Momy tataso dasauri itada kausar ___"Dr yaya tafarfado kuwa ko haryanzu?,' ___"relax hajia tafarfado amma munyimata allurar bacci sabida tasamu ishashshen bacci dan tana bukatar hutu kuma a kallah sai gobe da rana zata samu farkawa babu wata damuwa a tattare,' da'ita tasamu dimuwane da razana,'. Allah yabata lafiya zaku iya shiga,' Momy da kausar suka shiga dakinnan meenal tana kwance ga Karin ruwa a hannunta fuskarta hartayi wata Yar rama kadan momy tace,' ___"Allah sarki mutuwa yanzu sunzama marayu basuda Uwa basuda uba kenanfa abun tausayine gaskia mudama bamuda uba mukeda Uwa ake tausaya mana balle megabadaya,' Kausar tace,'. ___"nima banida uba sai Uwa yarasu banma sanshiba nikam,' Momy tariketa gabaki dayansu sunacikin wani mawuyacin Hali,' Meenal dai batasanma ina kanta yakeba,' BASAM yanadai zaune acikin Yan zaman makoki yanajin labarurruka dadama akan rasuwar kanwarsu meenal wacce tamutu wajan zubarda cikin shege acewarsu fa kenan labarin aketayi BASAM yakurama Yusuf da Anas idanu yanata kallonsu,' Aranshi yace,'. ___"suma kenan iyayansu sukaki yadda su auri meenal saini momy ta jajirce saina aureta nidanake sananne sunana bawuya zai baci ina bazan cigaba da zamada Yar iskaba sunana saiyabaci dole murabu kosunaso kobasaso domun lokacin rabuwar yazo,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY_______________* *_Badiat Ibrahim_* *______________116to120✍🏻* "Anata zaman makoki yayinda khadija taketa amsar gaisuwa duk wanda yazo saiya tambayi meenal sai'asanar dasu tana asibity batada lfy,' Dangin mama sunata Dora abincin daza'a fitarma da maza yayinda aketa kawo abinci daga waje waje nan fiffitarma da maza abinci sunataci yayinda BASAM yayi shiru yanata tunane tunane kala kala aranshi,' ansoma kiran sallah Na magrib awajan kowa yayi alwala akatada sallah awajan bayan an idarne akaitama mama adda'a kana aka shafa,' Ahankali BASAM yamike tareda Shiga cikin Gidan yasake gaida matan Gidan anata ambayar yajikin meenal sai cewa yakeyi dasauki yadauki Ummu suka wuce,' ____"megida asibityn zamuje muga yaya jikin matar taka,' Baicemata komaiba yajuya kan motar zuwa kwanar asibityn badan ranshi yasoba danyatsani yaga fuskar meenal Sam haka sukakarasa tareda kiran wayar kausar tafito taimusu jagora zuwa dakin,' Tana kuwa fitowa tagansu suna biye da'ita harzuwa dakinda meenal take da sallama suka shigo dukkansu momy ta amsa sallamar tasu suka shigo,' Ummu tace,'. ___"Salma yayadai jikin nata naga tasamu baccima ko?,' ___"eh Ummu allurar bacci Dr yaimata domun yace tanada bukatar Hutu dan tana cikin dimuwa saizuwa gobe da rana zata farka insha Allah,' BASAM yakura mata idanu cikin tsana take kallonta aranshi yace,'. ___"munafuka zakiyi bayanine zamana dake yakare zan yarda kwallon mangwaro inhuta da kuda,' Ummu tace,'. ___"ayya am Yar uwar tanacan abun tausayi tanata tunanin Yar uwarta domun yanzu meenal itace Uwa itace uba agareta mutuwa kenan Allah yasa mutafi asa'a tata tayi Kyau dantasamu mutane sosai,' Sunata jimamin abunda yake gabansu yayinda BASAM yaji dukyatsagu yabar asibityn danji yakeyi tamkar yakashe meenal kowa yahuta tsabar tsanarta dayayi Ummu ce takatsemai maganarda yakeyi azuchi,' ___"to yanzu kausar tazauna da'ita sukwana kenan kokuma za'aje adauko daya daga cikin Yan uwanta sukwana da'ita?,' ___"aa Ummu kukutafi gida nizankwana da meenal anan basaima antaso wasuba Ai tamuce meenal wlh rasuwarnan da'akaimusu yasa nasake Kaunar yarinyar tareda tausayinta,' __"to Allah yabaki lada Salma muzamu wuce asaukemu agida abakar zaikawo miki abinci da kayan tea saiki ajjiye saimumzo da safen,' BASAM yace', ___"saidasafe momy saimunzo,' Sukaimata sallama suka wuce dukkansu idanun BASAM yakada yayi jajir yayinda yakeji zuchiyarshi tanawani tafasa yarasa yadda zaitsoma rayuwarshi yaji Dadi Sam,' Ahaka suka karaso gida Ummu tana shiga tabama abakar komai da komai tace yakai asibity BASAM baikula kowaba yawuce kaitsaye dakinshi Yana tsaye yarasa mekemai Dadi aduniya maganganun su amadu da bello sune suketa yawo akanshi yayinda kwakwalwarshi taketa haskomai hotunansu Anas da Yusuf yanata sintiri adakinshi yayinda idanunshi suka Tara ruwan hawaye ___"an cuceni da'aka hadani aure da Yar iska fasika mazinaciya me kisan kai domun su meenal rai biyu suka kashe sunkashe kanwarsu yayinda suka kashe abunda yake cikinta Allah ya'isa tsakanina da meenal tacutar dani data amsa sunan matata,' Yafada kan gadanshi yana kallon sillin hawayene me dankaran zafi yazubomai a ido daya yayinda wutar tsanar meenal taketa ruruwa acikin zuchiyarshi ahaka daran yakasancema BASAM cikin tunane tunane har akakira sallar asuba yamike Yaje yadauro alwala kana yasaka jallabiyya yawuce masallaci Da asubannan Ummu tasaka akayi girki meraida motsi cikeda katuwar kula hardasu kaji tasaka abakar yadauka yatafi yakai sukuma suka karya suna zaune suna jiran fitowar BASAM Fitowa yayi jikinshi duk asanyaye yagaida Ummu ta amsa tareda sakemai ta'aziyya kausar ta gaisheshi kana suka wuce kaitsaye Ummu tace awuce dasu asibity suga ko meenal ta farfado dan shadaya tawuce,' Kafafunta suka soma motsawa ahankali yayinda taketa kokarin bude idanunta momy tamike tana tofa mata adda'a ahankali tabude idanunta tana salati hawayene yaketa kwararowa a idanun meenal,' ___"mama tatafi tabarmu ko momy tatafi kamar yadda Fatima da abbanmu suka tafi innalillahi wa'innah'ilaiyin rajiun mutuwa zanyi nima momy,' ga amanar Yar uwata khadija nabaki kikakaita Kano wajan hajia kaltume yayar mamanmu zanmutune Nima bazan yaruba,' Sallama su Ummu sukayi tareda shigowa sukazo suka samesu ahalinda suke ciki,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY________________* *_Badiat Ibrahim_* *_______________121to125✍🏻* Momy tana rikeda meenal tanaimata adda'a tana hawaye tace,'. ____"bazaki mutuba meenal bayanzuba saikinga 'ya'yanki da jikokinki insha Allah,'. Kausar kirawo Dr yazo yadubata,' Dasauri kausar tatafi tanatajin tausayin antynta domun ahalinda take Dole a tausaya mata,' Meenal tabude idanunta wanda suketa zubarda ruwa tace,'. ___"momy mama tatafi tabarmu wazamu dinga kallo muji Dadi yanzu?,' ___"meenal mutuwa tanakan kowa Allah baya barin wani danwani kisani iya wa'adinda Allah yadibar mata kenan kisani kuma bazata wuce hakanba kidaure kiyi tawakkali ki karfafama Yar uwarki guiwa dan Allah babu abunda mahaifiyarki tafi bukata ayanzu daya wuce adda'a domun itace iyakar soyayyar dazaki nuna mata,' "Ummu tace ____"sannan kidaure ansani da daci amma hakuri zakuyi ki rungumi kanwarki kidinga rarrashinta dan yanzu kece Uwa kece uba agareta ayi hakuri adanne xuchiya,' "BASAM jiyakeyi tamkar yaje yashaketa tamutu domun yatsaneta fiyeda komai arayuwarshi yatsaneta over idanunshi suka kada sukayi jajir yatsagu yabar asibityn kozaidena ganinta yaji sanyi,' Meenal tashare hawayanta tadan samu sassauci kausarce suka shigo da Dr,' Ya gaishesu kana yasoma Yan gwaje gwahansa yace,'. ___"amm. Jikin dasauki gaskia yanzudai abata abinci taci saitasha magani tukunna,'. Kaikuma BASAM biyoni muje office zanrubuta muku sallama kaje kabiya shikenan saikutafi gida Allah yakara sauki ko?,' Ummu tace ___"Ameen Dr mungode BASAM jeka mana katsaya abunka kabishi kuje,' Wani kululun bakin cikine ya turnikeshi ahaka yabi bayan Dr suka wuce,' Meenal momy tanata bata abinci abaki kadan taci tace takoshi akabata magani tasha sukuma suka fiffita dakomai sukasa amota BASAM kawai suke jira yazo suwuce.' Bawanda zaiyi haka yabiya kudin yadawo suka wuce meenal tana zaune tanata tunane tunanen rayuwa haka harsuka karaso kofar gidansu datasake ganin mutane zuchiyarta tasake tsinkewa tashiga hawaye,' Ahaka aka rirrike meenal akashiga da'ita dasauri Khadija tamike tareda karasowa ta rungume meenal sukasaka kuka dasauri BASAM yajuya yafice,' ___"ayi hakuri ayi hakuri dan Allah," Anshigada meenal daki anata zuwa gaisheta tareda mata ta'aziyya itadai tanata daga kai dan kuka takeyi sosai dangin abbansu sunata zage zage suna surutai,' Haka akaita zaman makoki har akayi bakwai ranar Gidan kowa yawatse yarage daga Khadija sai meenal sunadan tattaunawa,' ___"Ashe mama tayi gaskia datace cikin danginta nanan da dangin abbanmu babu me rikeki kiduba yadda suketa zaginmu suna aibanta mamanmu baiwar Allah mehalin kirki mudai babu abunda zamucema mama saidai Allah yajikanta yaimata rahma,' zuwa jibi zankaiki Kano Khadija domun hankalina yau bazai taba kwanciyaba innatafi gida nabarki kekadai anan,' Cikin muryar kuka Khadija tace,'. ___"banaso inrabu dake Anty meenal nafiso inkasance da'Yar uwata akoyaushe amma babu yadda zamuyi dole mubi umarnin mama muyi abunda takeso.' ___"Khadija namiki alkawarin zandinga zuwa akai akai ina dubaki insha Allah karki damu kinji?.' __"to Anty meenal inasanki sabida kimdamu dani sosai I so much love u.' Murmushi sukaima junansu kawai meenal tatashi tasaka hijabinta har kasa tareda rataya Jakarta takamo hannun Khadija suka fito tazauna amota taciro dubu goma tace,' ___"kidinga siyan abinci kamun jibin da sassafe zanzo mutafi Khadija yanzu danatafi kisaka sakata agidan kiyi zamanki abunki banda fitowa.' ___"nagode Anty meenal Allah yabarmunke,' Murmushi tayi tashiga motar yayinda habu direba yaja motar suka wuce meenal tafashe dakuka abakar yanata bata hakuri harsuka karaso Gidan,' Sunshigo Gidan yayinda akayi parking meenal tafito tana share hawayanta tayi sallama zuwa cikin falon BASAM yana tsaye yanata zurga zurga yanajiyo sallamarta yajuyo,' Dakata daganan wajan karki kuskura Kitako gidannan kazama fasika mazinaciya,' Tsayawa tayi cikin tsoro da fargaba yayinda Ummu tajiyo muryarsa tafito momy ma tafito tasamesu meenal nadaga kofar falon yayinda BASAM yake tsakiyar falon,' ___"meke faruwa BASAM nakejiyo hayaniyarka abunda bantabajin kanayiba?, gakuma meenal abakin kofa kishigo mana meenal,' Kafarta tana rawa tadaga zata shigo yace,' ___"karki shigo nafada miki" *Love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN*🏓 *RAINA BACE* *BY________________* *_Badiat Ibrahim_* *_____________141to145✍🏻* Sunshiga cikin tasha tareda nufar motar Kano suka biya kudin kana akasa musu akwatunansu abayan both sunadai zaune amota kowa yayi jigum jigum kowanne da abunda yake sakawa aranshi Nandanan motarnan tacika tab akatashi yayinda meenal da Khadija sukayi adda'a motarsu tashiga titi sai tafiya,' Wanka yafito jikinshi dukbabu karfi Sam yarasa meke damunshi arayuwa wayarshice tayi kara basma ce kekiranshi,' ___"Bby girl ya"akayi yakike yagida?,' ___'heart beat ina lafiya sai rashinka dake damuna inafa missing dinka over nigaskia yakamata kasan yadda zakayi dani yakamata muyi aure mana,' ___"come on yanzu fadamun inda kike inaso insameki mu tattauna,' ___"ina kalamu waheed nazo shopping ne,' ___'okey jirani a mall din zanzo insameki Bby girl ba bye sainazo,' Yana ajjiye wayarta sai wayarshi tasoma ruri daga office dinsune ake kiranshi yana dagawa akasanar dashi zasuyi tafiya ta gaggawa yaudinnan da yamma jirginsu zaitashi zuwa Paris akwai kwallon doki dazasuyi nakasane baki daya comfatishion za'ayi danhaka yataho yanzu zasuwuce Abuja asoma shiryawa,' Dasauri yasoma shiryawa yahada kayanshi tsab yasakko da gaggawa dukkansu suna falo sunyi jigum jigum dasu yana sakkowa momy tace,' ___"zonan BASAM inada. Magana dakai zokazauna,' Waje yasamu yazauna yanadan duba agogo yace,'. ___"mom dasauri domun yanzu haka Abuja zamutafi zuwa yamma jirginmu zaitashi zuwa Paris akwai kwallon daya tasomana nakasa dazamuyi so kutayamu adda'a mom,' ___"hmmm BASAM kenan kai abunda yadameka kenan kana ganin kayima kanka adalci kayima kuma meenal adalci kenan haba BASAM Ai in hankali yagushe hankali ake turawa yanemoshi yaduba yarinyarnan acikin irin halinda take cikifa amma ahakan kakoreta to mekake nufi da'ita kasaketane koyaya inaso inji,' Yadafe kanshi yarasa mekemai Dadi danbayaso yaji koda sunan meenal an ambata saiyaji tamkar anwatsamai garwashin wuta,' ___"ni bansaketaba momy nacedai takoma inda tafito kigafarceni bazan iyazamada mazinaciyaba gaskia sannan wannan maganar dakuke gani inda duniya zatasan menake ciki saikuga tajamun bacin suna karfa kumanta ni jarumine kowa yasanni wadanda basusaniba sunsan sunana,' to yanzu saikuga labarinnan a jaridu da gidajan TV plz mom banaso asakemun maganar meenal dan Allah arabu dani,' Ummu tace,'. ___"Salma rabu dashi tunda yazabi hakan shikenan BASAM Allah yakiyaye kuma Allah yabaku nasara tashi katafi kaji,' Yamike ranshi dukyabi tahagule yafita yanayi musu sallama momy tace,'.. ___"meyasa kikace haka Ummu kingoyi bayanshine kome?,' ___"bana goyi bayanshi bane Salma domun yanzu koda mun tursashi yadawoda meenal wlh Salma wuya zatasha domun yadinga cusguna mata kenan yanzu meenal tanacikin wani haline shima haka yakamata abasu lokaci suhuta inyadawo daga tafiya saimusakemai maganarta tunda Ai matarshice baikuma saketaba,'. ___"hmmm to shikenan Ummu Allah yazaba mana abunda yafi alkairi shikuma Allah yasaukesu lfy,' ___"Ameen kokefa,' Su BASAM andebesu Mota Mota har Mota hudu zuwa garin Abuja,' Motarsu meenal tasauka agarin Kano tadabo tumbin giwa,' pasinjojin motar suka soma sakkowa.' Ciki hardasu meenal suma sunsauko sunsamu Yan dako suka daukarmusu akwatinsu zuwa titi,' Sunbiyasu kudinsu sunsamu adaidaita sahu meenal tace,' ___"Malam nasarawa G R A zaka kaimu saidai mubakine bamusan garinba,' ___"to kushigo zakubani Dari biyar kubiyun,' Suka shiga duksungaji sun galabaita yajasu sunata tafiya khadija tace,' ___"to Anty inma munjedin da'ina zamu soma tambayar Gidan mamanmu din zamusha wuya gaskia gashi dukna Gaji,' Meenal wacce tayi tagumi ta tsunduma tunanin mijinta tadago tace,'. ___"to nima tunaninda naketayi kenan gashi mubawanda mukasani agarinnan,'. Cansai meenal taruno wannan hajia dasuka hadu ajirgi tacemata akano take kuma aitabata katinta,' Jakarta tashiga budewa tana laluben cart din amma bataganiba haka tahakura Me adaidaita sahun yace ____"kuna Neman gidan watane menene sunanta konasanta?,' Khadija tace,'. ____"hajia kaltume sunanta kokasanta dan Allah,' ___"kwarai da gaske aiduk fadin garin Kano bawanda baisan baristar hajia kaltume ba babbar lauyace dake babban kotun garinnan nasanta har gidanta nasani ,' Meenal tace,'. ___"to Malam gidanta zakakaimu dan Allah ita mukazo nema,' ___"ahhh badamuwa aimunzoma Gidan gashinan,' Tabkeken gidane asalin babba medaukeda garjejen get baki fentin Gidan kuman mint green gawasu fulaloyi green dasuka zagaye Gidan Gidan yaginu yatsaru over,' Sunsauko sunata kallon Gidan suka biyashi kudinshi sunatamai godia," Sunkarasa kofar gidan tareda kwankwasawa megadine yafito yana surutai ___"anga shigowar hajia har mabarata sunsoma zuwa wayene?,' Yaleko yagasu meenal ___"lfy malamai suwaye Ku daga ina wakuma kukazo nema?,' __"munzo wajan hajia ne daga Katsina muke yaran kanwartane asanar da'ita munzo,' Baice komaiba yawuce yashige yasanar da hajia waiga Yan kanwarta sunzo daga Katsina abarsu sushigo?,' ___"kashigo dasu sannan kaimusu jagora zuwa ciki,' Yawuce aguje yaje yashigo dasu sunata kalle kalle harsuka karasa sunshiga Gidan cikin sallama suka shiga falon,' Juyowa tayi tareda amsamusu sallamarsu tana juyowa suka hada idanu da meenal cikin fara'a tace,' ___"hajia meenal ko wacce muka hadu a jirgi daya London zuwa Katsina right?,' Mamakine Yakama meenal dataga matarda suka hadu a jirgi hartabata cart dinta,' Khadija takurama hoton hajia kaltume idanu wanda suka dauka da mama anyi katanshi takafa abango sunkumayi kama,' Meenal da khadija suka fashe da kuka dasukaga hotonnan khadija tatashi takarasa gaban hoton tana hawaye,' ___"Allah yajikanki mamanmu Allah ya rahamsheki yasa aljannace makomarki,' Hajia kaltume tamike tareda karasowa gaban khadija tadafata saitaga sunyimata kamada kanwarta ta Katsina Aisha wacce take jikin hoton,' ___"baiwar Allah wacece ke kinsan tajikin hotannance dakike magana akanta kanwatace Uwa daya uba daya kefa mecece taki?,' Meenal tataso tana kuka takaraso wajan tace,'. ___"wannan kanwatace sunanta khadija wannan kuma tajikin hoton dakikace kanwarkice mukuma mahaifiyarmuce ,' kukane yaci karfinta,' Shiru tayi tana kallonsu lokaci guda ta gasgata abunda suka fada danga kamanni tagani sosai,' Rungumesu tayi ajikinta sukuma suka sake fashewa da kuka itama hawayene yasoma kwarara a'idanta ta kankame yaran Yar uwarta tanajin wani masifar sansu yana ratsata suma kankameta sukayi sunajin dumin mahaifiyarsu ajikinta,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY_____________* *______________151TO155✍🏻* ___"aa Salma kwado nakegani agidan kamar arufe yake tohfa,' __"Ummu nima abunda nagani kenan amma tako mudanshiga makwabta muyi tambaya,' "Ummu tatako ahankali sukayi sallama agidansu mama Ladi,' Tana tsakar gida tana wanke gero suka shigo ta amsa sallamarsu cikin fara'a tareda saurin dauko tabarma ta shinfida musu,' ___"bismillah mana kuzauna hajia gawaje bara akawo ruwa,' ___"aa kibar ruwan wlh mungode,' zama sukayi aka gaggaisa tareda karama juna ta'aziyya,' ___"munzo kuma munga gida akulle basananne ina sukaje?,' ___"aa meenal bata sanar dakuba suntafi wajan yayar mahaifiyarsu kuma banjin zasudawo dan Khadija tacemun ita meenal tasamu sabani da mijinta,' ___"yayar mahaifiyarsu sunfada miki awane garine?,' ___"Kano sukacemun uhm lafiya daiko hajia?,' "Ummu tace,'. ____"munzo kifada mana gaskia danganeda abunda ake fada akan kanwarsu meenal wacce tarasu menene gaskiar al'amarin?,: ___"to agaskia Fatima hakane tarasune daciki ajikinta kamar yadda kukaje saidaifa ba Yar iska bace aa fyade aksimata awani kango dan alokacin ayashe akaganta acikin kangon tasume kssanta yayi kaca kaca ranga ranga akakaita asibity saida skaimata dinki tasha jinya tareda bakar wuya aka sallamota bayan wata uku ciki ya baiyana ajikin Fatima tayi kuka kamar ranta zaifita Saikuma cikin yazomata da laulayi harkumafa hakan yayi sanadin mutuwarta amma mutane sunacewa su meenal Yan iskane garin zubarda ciki kanwarsu tarasu wlh tallahi karyane kazafi akeyi musu tareda bata suna,' "Dan ankawo sadakin Meenal har saubiyu akafasa auran duk akan wannan zancan danake fada miki wlh yaran arzikine masu mutunci Allah shine shaida,' "Momy tasauke ajjiyar zuchiya tace,'. ___"yanzu ina zamuga meenal Ladi?,' ___'to Kano sukace suntafi kuma sukansu basusan takamaimai inda suka dosaba saidai ayi hakuri Allah yasada fuskokinmu da alkairinsa innaji labarinsu insha Allah zan sanar daku eh,' Ummu tace,'. ___"mungode sosai Ladi Saikuma munjiki din muzamu koma ,' ___"to insha Allah zakujini kugaida gida mungode,' Sukaimata ihsani suka wuce jikinsu duk amace,' Suns falo sunata jimami saiga Kiran BASAM awaya,' ___"hello megida yakake kun'isa lafiya ko?,' ___"lafiya lau Matar ina mom take?,' ___"gatanan akusa dani yanzu muka dawo gidansu meenal basananma bawanda yasan inda suke Gidan akulle yake,' ."shiru yayi aranshi yace,' ___"basananfa ba'asan ina sukeba lallaima wannan yarinyar da aure akanta take yawo ko zanyi maganinta,' __"to bani momy muyi magana,' Tamikama momy wayar,'. ___"BASAM kaga irin abunda kajamana ko to meenal suntafi ba'asanma takamaimai inda sukeba kuma har makwabtansu muka shiga basusan ina sukayiba sannan maganar da'aka fadama akansu meenal karyane sharrine inkana musu bara inturama recording dindanayi alokacinda akebamu labarin kashe wayarka yanzu inturama,' Yakashe wayarshi tareda dauko laptop dinshi aikuwa cikin kankanin lokaci yashigo shiru yayi yana sauraron maganar ma Ladi gabaki daya saiyashiga rikici da damuwa mikewa yayi yashiga tunane tunane barkatai yarasa mekemai Dadi ma ga momy tanatamai fada,' Adaddafe BASAM yayi wata biyu a Paris din suna gama aikinsu yadawo anata tayashi murnarcin nasara dayayi amma shibayako farin ciki dankoda Gidan TV suka gaiyaceshi cemusu yayi bazaiyiba akace za'ayi walima yace bayaso dukyafita haiyacinsa yarasa mekemai Dadi aduniyarshi,' Yana kwance momy tashigo tace,' ___"BASAM meke damunka kaduba yadda dukkarame kayi duhu anya lafiyanka kalau kuwa kuma kullum kana daki bakayin walwala dasakewa kamar yadda kakeyi ada kaduba shirye shiryen bikin Yar uwarka kausar akeyi amma kai ko'ajikinka kana daki kakulle kanka,' ___"momy nafada miki babu abunda yake damuna nikam ina lafiya kawai inatunanin wani kaikine dazai taso mana nangaba shiyasa momy amma bakomai,' ___"to naji yamaganar kuma auran naka da'ita wannan Yarinya basmah?,' ___"momy zamuyi magana yanzu bara nafita kamun Yan biki sucika Gidan inkasa fita.' Mikewa yayi dama ashirye yake tsab yazari car key yafice takofar baya motarshi yashige kirar range rover fara Sol da'ita "Kaitsaye yanufi layinsu meenal wanda shikanshi baisan kwana biyunnan abunda yasa yakezuwa yakurama kofar Gidan idanuba kusan kullum yanzu haka BASAM yakeyi,' Anyi bikin kausar Nagani nafada ankaita Abuja itada mijinta suna zamansu Na lafiya abunsu,' *BAYAN SHEKARA DAYA* Motarsu meenal ce tashawo kwanar layinnasu motocine guda uku susuna tatsakiya yayinda sauran Yan uwansu suke sauran dansundawo gidane za'ayi bikin khadija ta kammala karatunta hartasamu aikinta awani company ananne me company din yaganta yace yanaso dayake Allah yayi rabomshice shine gashi yanzu za'ayi bikin,' Gidansu meenal din abude yake ragowar Yan uwan mamanta da dangin abbansu suna ciki anata girke girken biki danyaune za'asa Salle,' Daga gefe BASAM ne zaune amota shida abokinshi Khalid sunata kallon kofar gidansu meenal din wanda sukaga anata Shiga ana fita da dukkan alamu biki akeyi,' ___"waini BASAM yaushe kakamu da soyayyar meenal ne metsanani haka dakullum saikazo kofar gidannan yanzufa rabonka da meenal shekara guda kenan kaduba yadda karame kayi duhu sabida soyayya dakasa agaba yakamata kaima kanka fada kilama tayi auranta kananan kanata haukarka yarinyarda ada katsani koda a ambaci sunanta amma wai yanzu itace takebaka wuya harkina wulakanta basmah akanta,' ___"✋🏻😠 dan Allah dakata Malam kabarni naji da radadin da zuchiyata takemun akan tsantsar kaunar meenal sannan tayaya meenal zatayi aure da'akwai aurena akanta aibazai yuyuba zancan basmah kuma dakake magana kaikaje ka aureta aikaima namijine meenal dinna tafimun komai arayuwata inasanta inasanta da dukkan rayuwata,' Motarsu takaraso kofar Gidan ahankali akabude murfin motar tasako kafafunta wanda sukasha Jan lalli fulawarnam tafito tazauna afatarta sosai takalmine baki metsinin gaske akafarta ahankali tazaro jikinta sanye take dawani danyan lace baki me fulawowi pink tayi hadadden daurinta me hawa hawa yazauna akanta sosai idanunta. Manne da bakin glass metsadar gaske saidan mayafinta madaidaici pink tayi mugun Kyau takalminta dajakarta bakake sukuma sannu ahankali tasoma takawa zuwa kofar Gidan nasu ranawani shan kamshi tana daga kanta,' BASAM yazare idanunshi tareda shagala wajan kallon meenal cikin rawar murya yace,'. ___"Khalid wannan ba meenal dinabace kuwa itace tazama haka?,' Khalid da mamakin ganin haduwar meenal yasashi dimaucewa yace,'. ___"itace abokina amma tahadu sosai wlh,' Khadijace itama tafito cikin ado yayinda sauran Yan uwansu tareda kawayan Khadija da kawayan meenal suma suka fito,' Batareda bata lokaciba suka shige Gidan,' "BASAM yaballe murfin motarshi dasauri zaifita Khalid yarike hannunshi,' ___"mekake kokarinyi BASAM karkacemun zakabi matarkane cikin danginta?,' kasani duk irin wulakancin dasukaima kaikajawo kamanta wulakantata dakayi kakoreta alokacinda take tsananin bukatar taimakonka,' "Idanimshi suka cicciko da ruwan hawaye yace,'. ___"menene mafita yanzu khalid banaso tasake kubcemunne yanzu kaje kakira mun momy da Ummu saisuzo susushiga adawomunda matata plz bazan iya barin kofar gidannanba,' ___"to naji relax zanje inkirasu yanzu kaikatsaya ammafa karka sake kashiga ina fadama kenan,: ___"bazan shigaba kayi Sauri khalid,' Haka khalid yaje yasanardasu momy abunda ake ciki aikuwa bashiri sukataho,' *love u oll* 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN🏓* *RAINA BACE* *BY_______________* *_Badiat Ibrahim_* *_______________156to160✍🏻* "Suna karasowa suka samu BASAM acikin Mota inbanda kallon kofar gidansu meenal babu abunda yakeyi,' ___"BASAM gamu munzo zamuje mubada hakuri akan abunda yafaru abaya insha Allah kwantar da hankalinka,' Yasauke kanshi yana zubarda hawaye baice komaiba Ummu da momy suka shiga Gidan da sallama,' Kawai da meenal sukaci karo momy taganta tayi Kyau tayi kiba ga kirjinta yacika dam komanta yazauna,'. ___"meenal dina kece?,' Gabaki daya kallo yadawo garesu meenal tataho aguje ta rungume momy saisuka kuka dukkansu suna kankame da juna hajia kaltume takada kanta kawai tanajin tausayinsu domum talura meenal takamu da matsanancin san mijinta sosai.' ____"nice momy inata missing dinki momy ina kausar?,' Murmushi tayi ___"kausar tayi aure tana Abuja da mijinta meenal ina kikaje kikabarmu mijinki yashiga wani Hali akanki,?' Hajia kaltume takaraso ___"sannunku meenal suwaye kuma wadannam?,' Kanta yana kasa tace,'. ___"mahaifiyar BASAM ce da kakarshi,' ___"ayya bismillah kushigo. Mana kwatsaya anan meenal kaisu falo suzauna tunda bakowa,' Taimusu jagora zuwa falo suka zauna anata gaggaisawa sukayi ammaba meke faruwa akasanar dasu bikin khadija akeyi sukayi murna taredasa alkhairi,' Hajia kaltume tazo tace,'. ___"to dama kobakuzoba dama zanzoni dakaina akan maganar takaddar meenal tasaki domun yakamata danku yasaketa domun tasamu tayi auranta manema sunmata cakowa soyake ya aureta.' "Ummu tace,'. ___"aa hajia abunda yafaru abaya aiyawuce domum mubamuda laifi yaro shine yayi kuskure kuma wlh yanzu yagane kuranshi aimasa afuwa awanke matarshi takoma suyi zamansu kuyi hakuri kuduba,' ____"babu zancan afuwa domun shima lokacin aibaimata afuwaba danhaka takaddarta kawai nakeso abamu itama tasamu freedom tayi auranta nadadi,' ___"momy tace kuyi hakuri dan albarkacin annabi da alqur'ani karku kashema meenal auranta inasan meenal asalima Nina zabamai meenal amatsayin mata azamanda nayi da:ita kitbayeta soyayya nakenuna mata dan banyarda wani Abu yatabataba sannan aranarda abun yafaru nabartane tatafi badan komaiba sabida ranta yabaci shima nashi yabaci akan in dukkansu suka sakko sai aimusu sulhu washe gari danazo natarar gida akulle mama Ladi tanada ranta ainashiga nasameta munyi magana tacemun sunce Kano zasuje amma suma basusan takamaimai akanon ina zasuba sannan acikin mutanena nasaka aimun bincike koza'agansu amma shiru dan Allah dan girman Allah dan soyayyar dake tsakaninku da annabi (S A W) kubar meenal da BASAM,' Hajia kaltume tace kunhadamu da babban bango to badamuwa kuturomun BASAM din inji daga bakinshi tukunna,' ___"aiyana waje ina meenal taje takirashi to,' ____"meenal meenal,' ___"naam momy ina zuwa dasauri takaraso "gani momy,' ___"kifita waje kikarawo BASAM kutaho tare harda abokin nashima suzo,' Asanyaye meenal tafita tatsaya azaure tasake kyarawa gabanta yanata faduwa tafito tanufi motarsu cikin tsoro,' Kalid yace,'. ___"yimaza kashare hawayanka ga meenal nan tanufomun maza,'.. Yasaka tissue yagoge hawayansa daidai karasowarta Sallamar datayi tasauya tunaninshi sautin muryarta daya sauka akunnanshi sautinda ya firgita tsigar jikinshi dasauri yadago suka zubama junansu idanu kofiyoyin soyayyace ta harbi zuchiyoyinsu dukkansu biyun tausayin BASAM yakamata taga yarame yayi duhu dashi,' Tasauke kanta kasa,'. ____"sannunku dama cewa akayi kushigo ciki anasan ganinku,' tajuya dantaji tanasan tayi kuka dasauri suka fito sukabiyo bayanta sun tsugunna sungaida matan tsakar gida kana sukashiga falon Yan uwantane kab acikin falon saisu momy waje sukasamu suka tsugunna suka kwashi gaisuwa kana suna zauna kannan nasu akasa harda meenal ma tanaso tadago takalli farin cikinta amma abun ya faskara takasa kyaran muryar hajia kaltume ne yakatseta __"amm BASAM gashi tamikamai bairo da takadda yadawo ya amsa hannunshi yana rawa.' ____"takaddace danakeso karubutama meenal saki uku taje tayi auranta tahuta itama,' Jiyayi kamar ankwadamai guduma akanshi bashiri yasaki takaddar da bairon yana hawaye Meenal itama wata faduwar gaba tayi dataji abunda momy tace tasauke kanta tana kuka dan tanasan mijinta sosai,' Yace ___"kugafarceni wlh koda amafarki bazan iya sakin meenal ba domun meenal matatace kuma inasanta yanzu fiyeda kaina karku tursasamun insaketa domun zan iya rasa raina baki daya dan Allah kugafarramun laifinda Na aikatama meenal domun nasan natabka babban kuskure,' __"meenal kiyafemun dan Allah nasan nacutar dake nazalunceki to ina Neman gafararki kiyafemun badanniba plzz inasanki,' Kuka yakeyi sosai meenal tadago itama kukan takeyi tace ,'. __"nayafema dukdadai dama niban rikekaba Allah yayafemu nima kayafemun abunda naima,' Hajia kaltume tace ____"algamdullah komai yadaidaita tunda sun daidaita Kansu aishikenan saikuma mukiyaye gaba zuwa gobe zamusamu wakilin ita meenal din shima yaturo wakilinshi sai akyara auran takoma Gidan mijinta shikenan saidai akiyeye gaba in angama biki jibi zatadawo dakinta,' Godia BASAM yashigayi shida khalid sunata farin ciki su momy ma sunata godia sunzauna za'_ayi biki dasu yayinda Meenal tafita rakasu BASAM,' Suna hada idanu azaure sukaima junansu murmushi jawota yayi jikinshi yakankameta suna daria rada yaimata ' ___"I love u my heart I so much missed u ,' Tawaniji Dadi yana shigarta waiyau itace ajikin BASAM kuma yakefada mata kalaman soyayya,'. ___"I love u too,' Sukasaki juna hannunsu yana rikedana juna haryashiga Mota sannan yajuyo yana kallonta yace ,'. ____"sai gobe inmunhadu kenan ko amma zamuyi waya Ai sakamun nber ki,' Yamika mata wayar tasakamai tanamai murmushi,'. ____"to sai kazo goben,' ____"wlh kamar karna barki haka nakeji tsoro nakehi karki gudu kabani akarona biyu,' Daria sukasa dukkansu yashiga Mota yanatafe yanadaga mata hannu harta bace musu Ihu yasaka tareda tafawa da khalid yanawani murna Mara musaltuwa,' *love u oll 🏓🏓🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓🏓 🏓🏓🏓 🏓 *BASAN* *RAINA BACE* *BY_______________* *BADIAT IBRAHIM*_ *____________161to165✍🏻* *THE END* "Misalin karfe takwas nadaran ranar BASAM yana Gidan TV ana tattaunawa dashi kamar yadda akasaba,' ___"assalamu alaikum masu sauraranmu barka da warhaka barkanmu dasake saduwa acikin wannan shiri namu shirine Wanda yakebamu dama tattaunawa da manyan mutane wadanda sukayi suna duniya tasanmu to yauma Muna tareda bakonmu wato BASAM B SALEES ,' bakonmu bismillah,' ___"assalamu alaikum masoyana dawanda suke gaban akwatin tvnsu da wadandaba basanan inamuku fatan alkairi,' Sanye yake cikin wasu kananan kaya hadaddu wandone fari Sol ajikinshi tareda wani takalmi green hadadde yasanya rigarshi medogon hannu shima green yatoshe idanunshi da bakin glass yayi mugun Kyau yanata murmushi Meenal datake gaban TV tana kallon hadadden mijinta tayi murmushi wani Sanshi da kaunarshi yana shigarta ___"amm Malam BASAM kwanakin baya akwai kwallo da'akayi takasa baki daya Wanda ake gabatarwa duk shekara sannan awannan karonma ance kaikasakecin nasarar lashe gasar menene cikakken gaskiar?,' ____"ammm hakane Nina nashe wannan gasa awannan karonma sannan hakanne yasa nasake samun matsayi Na musamman gaskia ne dannayi hira da Yan jaridu dadama akan gasar danaci uhm,' ____"to Malam BASAM jita jita yayi yawa Agari wasu sunacewa kayi aure wasukuma sunacewa bakayiba shin kayi auran kobakayiba inkayi wacece wannan mesa'ar data sameka?,' Murmushi yayi hadadde yace,'. ____"tabbas nayi aure shekara daya da Rabi dasuka wuce nayi auranne aboye cikin sirri kamar yadda naima kaina alkawari dakuma matarda zan aura cewar zamuyi auranmu aboye batareda duniya tasaniba hakane inada aure,' ___"ammm malam BASAM kozamu iya ganin matarka koda awayane domun masoyanka suma suganta susamata albarka sannan zamu iyasanin sunan Matar tamu?,' ___"dukda nakasance metsananin kishin matata amma lokaci yayi da duniya zatasan wacece Na aura sunanta MEENAL wannan shine hotonta,' Wani katon hotontane yacika gaban TV tana sanye da doguwar Riga pink tayane kanta da bakin gyale tayi mugun Kyau tana murmushinta Na burgewa,' Kankace Me akashiga surutai kowa da albarkacin bakinshi momy da Ummu farin ciki Mara musaltuwa a fuskokinsu meenal da Yan uwanta kuwa ba'a magana,' ___"gaskia matarka tayi sanar samunka kamar yadda kaima kayi sa'ar samunta domun tahadu da dukkan alamu kanasanta matuka,' ___"hhhhh sosai kuwa dan koda ina cikin damuwa innatuno cewar itace matata sainaji da sanyi zuchiyata tadenayin kuna nasan tana jina tana ganina u love u meenal my beautiful wife,' Anan suka dakatar da tattaunawarsu yadawo gida angama bikin Khadija ankaita Gidan mijinta yayinda aka rako meenal gidanta tanata musu nasihohi masu ratsa xuchiya dagabaya sukayimata sallama suka wuce,' Tana falo tana kallo tajiyo sallamarsa daukeda ledoji ahannunshi tataso dasauri tareda karasawa gareshi ___"sannu da dawowa,' tasaka hannu zata amshi ledar hannunshi yajawota jikinshi tareda sauke sassanyar ajjiyar xuchiya sunkutarta yayi suna daria sukayi uwar daka akan Gado suka zuba suna daria abaki yadinga ciyarda ita namannan yana koramata da fresh milk har saida takoshi sannan itama tabashi yakoshi tare sukayo wanka sukadauro alwala sun gabatarda sallar lafila raka'a biyu yadinga ragargazo musu adda'ar zaman lafiya,' Daganan zancan saiyasha bambam yashiga rudata da maiyar soyayyarshi dukkansu basa haiyacinsu ahaka yasanta macce yasha shagwaba da kuka haka yadinda jinyar matarshi danbayako fita yatsaya sosai yana lallaba matarshi tareda tattalinta sunata ragargazar amarci,' Satinta biyu da tarewa sukawuce honeymoon nagani nafada ananne taga soyayya sosai taji dadi BASAM yamantar da'ita komai narayuwarta rayuwa tadawo neet neet sunata soyayyarsu a america Watansu daya acan meenal tasamu cikimurna awajan BASAM ba'acewa komai haka yadinga waya najeria yana sanarda mutananshi koda labarin ya'iss kunnansu momy murna awajansu ba'acewa kamai yan Uwa duksunsani yayinda yasanarda duniya halin farin cikin dayake ciki Motsi daya meenal tayi sai BASAM yaimata tambayoyi goma mekikeso mezanmiki wani abun kikiso kici kokuma kingajine ingoyaku?,' Kullum haka har meenal tazo tanajin tausayin BASAM matuka haka yashiga siyayyan kayan bebies acan hadaddu sunata siyayya dan yace duk wani Abu da bebie zai bukata a america zasu siya sannan yace sai cikinta yagirma zasudawo najeria intana dabda haihuwa,' Tana zaune afalo cikinta yafito yayi kato tayi Kyau tasake fari tanadancin kayan fruth tanadan kallo tajiyo shigowarshi harzata yunkura tamike yace,' ____"ahhh bansakiba banaso kiwahalarda kanki dakuma bebin dake cikinki,' Karasowa yayi yatsugunna agabanta tareda sumbatar cikinta ___"Maman bebie yaya akayi kunata missing dinako?, sorry nima inata tunaninku gani nazo kinshirya ko?,' Murmushi tayi tareda shafa sumar kan BASAM tace,'. ___"ina alfahari dasamunka amatsayin abokin rayuwata inasanka matuka,' Murmushi yayi,'. ___"naji nagode ainikuma aikina nakeyi domun banasan kisha wuya oya come on tashi ahankali musamu mutafi,' Dagata yayi ahankali sunata sakkowa harzuwa cikin Mota saidata zauna tukunna yakoma yadauko musu akwatunansu kana sukawuce sai airport sunshiga anata kiraye kirayan Suna suma ankira sunansu sunshiga sunadai zaune meenal tanatajin ciwon Mara kadan kadan tanadan daurewa dankarta dagama BASAM hankali dan yasamu bacci tausayi yakebata tasaka hannunta tana shafar cikin ahankali ahankali idanunta arufe itakadai tasan metakeji dan mararta tatasanma ciwo kafafunta da bayanta duksun rike har BASAM yafarka yanata tambayarta menene tanadan murmushin bakomai,' Antaru a airport din ana jiran isowarsu meenal harda hajia kaltume da Khadija da mijinta tareda khalid da matarshi Basma su Ummu hard a kausar da mijin mutane dadama aikuwa saiga jirgin yasauka Saukarsa da minty biyar akasoma fitowa BASAM yayi yayi meenal tamike takasa kafafunta sunrike tana hawaye tace,' __"dear nakuda nakeyi bazan iya tashiba,' Duksaiyabi yarude yakuwa sureta suna sakkowa ahankali tana hawaye yayinda tarike mararta kam yana sakkowa akayo Kansu dasauri.' ___"mom nakuda takeyi abude Mota maza mutafi asibity ankuma suka dunguma zuwa asibity ankarbeta da gaggawa tanata nakuda zanga zanga duktahada zufa,' ___"Dr plz kabarni inshiga dan Allah mijintanefa ni inasan in taimaka mata,' Dr yabar basam yashiga yasaka hannunshi acikin Na meenal tarike kam tanata zufa yace,' ___"Bby come on kiyi nishi mekarfi bebien yafito kihuta kinji?,' Nose tace,'. ___"gayaron yasoma fitowa karfinta yakare plz kiyi nishi,' Yace,'. ___"come on Bby kiyi inatare dake takuwa kankame hannunshi ta dakarkara tayi wani nishi aikuwa bebie yafito tashiga sauke nunfashi,' Kankame junansu sukayi suna murna yanata mata sannu dasauri yafito yasanar dasu ta haifi namiji suna lfy nanfa asibity yarude da murna nan akashiga nasarda Yan Uwa mejego angama kintsasu itada hahadden kyakykyawan bebien ta ankawosu dakin Hutu bebien yana cikin wani hadadden seti fari Sol yanata kamshi meenal tazubamai idanu kamarshi daya da BASAM sak yarannan kato kamar dan turawa taji wani soyayyar yaron da soyayyar BASAM nashigarta,' Ahaka akashigo anata mata sannu sukaita daukar yarannam anamai hotuna anamai adda'a meenal da BASAM kuwa sai kalon junansu sukeyi cikin soyayya,' Kankace me gari yadauka Matar BASAM ta haihu BASAM yaima yaron huduba da sunan abbanshi wato salees Ransuna kuwa anci ansha abubbuwa daban daban shanu da raguna BASAM yayanka mejego kuwa tafito sharshar da'ita tayi Kyau tadau makeup tanata kamshi tasamu akwatuba goma awajan BASAM nata biyar Na bebie salees biyar momy taimusu akwati biyar Ummu uku hajia kaltume uku sunsamu kaya Mara musaltuwa,' Sadab sadab BASAM yashigo dakin bakowa kuwa sai meenal tanaba bebie nono yatashi bacci yana shigowa yadagasu sama dukkansu yana juyasu tashiga daria,' ___"ina alfahari daku Bby I love u more,' ___"kana ranmu dadynmu love u too,' Yashiga kissing dinta itada bebie din tanata babbaka daria rayuwa tayima kowa fari kowa baidawata damuwa khadija tahaihu ta haifi macce yarinyar taci sunan mama khalid matarshi ta haifi namiji yaro yaci sunan BASAM kausar tahaifi macce Yarinya taci sunan Meenal abundai kwanin Kyau sunhada family babba,' *ALHAMDULLAH* Ina mika godia ta ga dukkan groups Na Hausa novels musamman,' Manshat group Hausa novels Home of hausa novels Jiddah novels Aisha gana novels Faxy novels Muradina novels Da dukkan wani group Na novels Ina mika godiyata agareku baki daya Sai Allah yasake sadamu awani sabon book din nagode, adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *