Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, April 3, 2017

Dream girl

adsense here [9/14, 12:55 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/8, 8:03 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 1⃣ Tsaye nake bakin titi amma hankalina gabadaya baya jikina, tinanina kachokan ya dunguma a tunanin dream man dina, inata tsara irin rayuwar da zamu tsara a gidan aurenmu, amma abinda zai baka haushi shine kwata-kwata wanda nake tinanin bai masan abunda nakeyi ba, hasalima ko sunansa bansani ba, qarar wata babbar motace da ta doso wurin ta dawo dani hayyacina, da gudu na tsalakka titin tareda haushin kaina da nikeji, watarana sai na halakka kaina akan tinanin abunda bazan ta6a samu ba. A haka na doshi gidanmu, na tura dan qyauren gidanmu na shiga gida, na kama hanyar wucewa dan akurkin dakina naje na dasa aya a inda na tsaya na tinanin abunda bazai fishsheni ba, tsawar da mama ta dakamin ita ta katsemin hanzari, wai ke meh yake damunki zaki shigomin gida ba ko sallama, sannan maimakon ki gayamin saqon da na aikeki, kin wani wuce soqoqo zaki wuce daki, ki kwanta kina tinane tinanen iskancin da kika saba, dan narasa meh yake damun qwaqwalwarki, juyawa nayi da niyar inkoma inyi sallamar da banyi ba, mama ta katseminb hanxari hanyar tambayata saqon da ta aikeni. Nace mama wlh hajiya abu tace wai ita batada kudin da zata ranta miki, ko wanda ta baki kwanan baya sai daqyar kika........ Mama ta dagamun hannu ya isa haka, badai biyan buqata karki isheni da surutun banza wuce ki ban wuri, na wuce dan dakina ina qunquni, toh ni miye laifina daga zanfadi abunda aka gayamin, mama cikin tsawa tacemin ni kike zagi? Na wace dai ban tanka mata ba. mama kenan mutum ce mai fada da saurin fushi, amma kuma akwai saurin sauka, ni har na saba da halinta shiyasa ma idan tana masifarta bana tankamata. [11/8, 8:53 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 2⃣ daki na fada na kwanta bisa lotsatstsiyar katifata da tasha jiki, da wani kodadden bed sheet dina, da wani pillow na kamar an latse bread, ina jimami, duk da mahaifiyata masifaffiyace amma ina tausayinta, tin bayan rasuwar mahaifinmu itace taketa dawainiya damu danida qannena guda 4, nice first born khadijah amma anfi kirana da ameerah, sai qanena mai bimun Aliyu, sai suhaila, fatima da kuma autanmu umar but muna kiransa da khair. Mahaifinmu shi kadai ne a wurin mahaifiyarsa, but yanada step brothers guda biyu, mahaifiyata ma haka ita kadaice a wurin mahaifiyarta, amma tanada alots of step brothers and sisters, kuma mahaifiyarta er dangi ce sunada yawa a famly dinsu, but duk da wannan en uwa na mahaifiyata ba mai taimakamana da qwandala, idan ba wata er yayar mahaifiyarta ba da ta tashi a wurinta, itama din ba wani qarfi ne da ita ba, dan haka mama ce ke fadi tashi na ganin munsamu rayuwa mai kyau tareda ingantaccen ilimi. Inada burin na tallafawa mahaifiyata tareda qannena amma ba dama, dan yanzu nake 200level a jami'ar usmanu danfodio da ke sokoto, inda nake karanta biology, wanda ada burina baya wuce inzama likita amma kuma nayita nema bansamu ba, mahaifina ne ya qaramin qarfin guiwa na kar6i abunda na samu arzikin mutum baya wuceshi, a haka na haqura nake karanta biology. Ina 100 level ne Allah yayiwa mahaifina rasuwa, wanda mutuwar sa taso ta zautani coz my father is my best friend, da taimakon addu'oi da mama tasa akemin aka samu nadawo hayyacina. [11/8, 9:13 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 3⃣ qwallamin kiran da mama tayi ya dawo dani daga duniyar tunanin da na tafi, na tashi da sauri na fito dan inji kiran da mama kemin, nera hamsin ta miqomin kar6i wannan kije wurin isuhu ki samo kayan miya ki dora ko jolop rice ce kafin qannenki su dawo su isko ba abinci a gidan, na koma daki na zunbulo qaton hijabina na fita siyen kayan miya, Tafiya nake kaina a qasa, kamar ance dago kanki, idona karaf akan kyakkyawar fuskarsa mai cike da annuri, tsaye nayi na zama statue a wurin na saki baki da ido ina kallonsa bana ko qyaftawa, tamkar wata mayya ina ayyanawa a zuciyata wannan hadadden guy din idan yazama nawa zan shana, dan na huce takaicin da namiji a duniya, karaf najini ta ti6is a qasa, na qwalla qara, ashe wasu shanu ne sukazo wucewa nikuma na tafi dream land, banma lura ba, shine har wata ta tureni nasha qasa😢 tashi nayi na kakka6e jikina ina qwalla gashi na goge a qafa, Allah dai yasa ban karye ba😂, mai kiwon shanun ne yayo kaina yana fadar enmata shannu, inji bakaji ciwo ba, naji kamar in falla masa mari, nace cikin tsawa eh malam wuce kabani wuri kabarni naji da daya, da qasar da nasha zanji ko da asarar ganin dream man dina da kamin zanji, shidai bai fahimce mai nike nufi ba ya miqomin ledar nono wai ga wannan, har da zanqi kar6a sai naga da inyi 2-0 gwanda na kar6i kindirmon, na qwata da qarfi nace angode nayi gaba abina [11/9, 12:30 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 4⃣ agurguje na wuce ina jefa qafata, naje na siyo kayan miya, da sauri - sauri na dawo gida dukda naji ciwo a qafata, koda nashigo gida su khairi sun dawo, mama ce takemin kallon tuhuma, meh ya tsaidake, nafara inda-inda, wlh mama shanuwa ce ta tureni a hanya shiyasa na makara ina qwalla😢 jibi qafata duk na goge, su suhaila ne suka kwashe da dariya, na tashi nayi kansu, mamace ta tsaidani karki illatamin yara, ai indai baki daina wannan yawan tunanin da kike ba to wlh watarana ma sai ansaceki a hanya baki saniba, bani kayan miyar nan, ta zabce leda tabarni anan tsuru-tsuru kamar anturke 6arawo, ina wani rau-rau da idona alamar zanyi kuka, mamace tace 6acemin dagani sakarya kina girma kina chin qasa. Da gudu na wuce dakina ina fadan nidai gidannan duk antsaneni ba mai sona, sudai su suhaila sunsamu abun dariya, niko duk na qule, na shige daki na rufo qofar, mama tace ku qyaleta idan yunwa ta isheta a fito dan kanta. Haka akayi kuwa ina daki ina sana'a dan nashiga duniyar tunanin dream man dina, nama manta da abunda ya faru, yunwa ce ta tasani gaba, nafito waje ina neman abinci na, haka nasamu kitchen wayam, nafara zare ido, naje nasamu mama ina wani 6ata fuska, mama banga abinci na ba, ta kalleni ta watsar kije tunanin da kike ya baki abinci. Haushi da takaici ne ya kamani, na koma akurkina na kwanta ga azabar yunwa inaji, chan na tuna da kindirmo na, haka na tashi jikina har rawa yake na dauko leda na kafa kai, nonon ko suger babu amma haka na shanyeshi tas, sannan najini nadawo normal, na godewa Allah sannan na godewa dan fillo da yau yunwa ta illatani. [11/9, 3:29 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 5⃣Suhaila ce ta bankado qofa ta shigo, mama tace ga abincin nan idan kinga dama kici, nayi kamar banjita ba, ta gaji da tsayuwa toh bari naje na gayamata kince bazakici ba ta kama hanyar fita, miqewa nayi cikin hanzari na kar6o kwanon, marar kunya bani nan kuma ki fice kibani wuri, tafita tana dariya ashe kowa yace duhu baiji zawo ba, duk da yanzu banajin yunwa nasan kindirmon da nasha ba wani riqeni zaiyi ba, inhar nabari ta tafi da abincin na kade dan mama bazata saurareni ba. Komawa nayi na kwanta ina aikin da nasaba, Aliyu ne ya banko qofar ya shigo, miye haka zaka fadowa mutane a daki ba ko sallamah, tsaki nayi najuya mishi baya, haba sweet sis daga nazo na ganki naga kindaina zama a waje duk sanda na shigo bana ganinki wai meh ke damunki ne sweet sis, bakomai nace masa banajin dadi ne. Hmm sis kenan ai kinsan in zaki 6oyewa kowa damuwarki alinki bai dace ki 6oye masa ba, miqewa nayi zaune na nisa sannan nace my sweet bro bakomai wlh wani guy ne yake chazamin qwaqwalwa, ya hanani sakat tunanin sa nake day and night, Aliyu ne ya sake baki yana kallona, sannan ya kwashe da dariya saida yakai qasa, sis kece kike gayamin wani guy yana chazamiki brain. Cow face nayi nace kaga idan dariya zakamin gwanda tun muna mu 2 ka kama gabanka [9/14, 12:55 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/9, 3:43 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 6⃣ Aliyu yace sorry sis abunne da mamaki keda kikewa maza kallon banza bakya kula kowa yau kece da fadan haka, Aliyu baku fahimceni bane, ina mace baikamata na riqa kula kowanne namiji ba, idan har banaji ina ra'ayinsa ba shiyasa kaga bana kula kowa dan banaso na 6ata time dina a banza, kuma ma samarin yanzu majority duk en iska ne aliyu. ....... Toh sis yanzu dai ba wannan ba ma who is dis lucky guy, ya sunansa kuma a ina yake, rau nayi da ido sai hawaye Allah nima bansani ba bro, kamarya dai bakisani ba sis, joke apart plz nace wallahi bansani ba aliyu, lura da yayi yaga hawaye a idona yasa yayi shiru na dan wani time, anya sis ba gamo kikayi ba kuwa, Aliyu ba wani gamo, mutum ne kamar kai, miqewa yayi lallai sis abun naki azimun ne, toh ki dage da addu'a Allah ya za6amiki abunda yafi zama alkhairi, nima kuma zan tayaki, nace daz my lil bro daz y i love you alot, yace i love u too sweet sis nidai nafita, nace adawo lfy ina murmushi. Aliyu kenan yaro mai tunanin manya qanena ne amma munshaqu sosai rigimar nan ta mabiyi da mabiyi duk bamayinta, indai kaji ina fada a gida toh da su suhaila ne. [11/9, 4:08 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 7⃣ ranar dai ahaka na wuni a daki na kwana sallah ce kawai ke tadani, gari na wayewa bayan na tashi na taya mama ayyukan gida, na gama na kwaso kayana nafara wankewa, mamace ta kwasomin kayan su suhaila ta zubomin gashinan ki wanke, dan naga yanzu tinda kina hutu ba aikin da kike sai zama a daki, na rasa meh kike qullawa a ciki, baki na turo alamun zanyi kuka, haba mama ni gaskia bazanyiwa marar kunyar yarannan wanki ba da girmansu, ni kayan khairi kawai zan wanke, saidai idan naki zaki kwaso, mama tasan halina indai banyi niyyar abu ba ko ta tilastani yinsa bazanyi mai kyau ba. Kamar tasan meh ke raina ta kwashe kayan su suhailan ta qaromin na khairi, nayi murmushin mugunta nace wlh da tsundumasu a ruwa kawai zanyi in tsame in shanya, mama dai juyawa tayi Allah ya shiryeki nace ameen ina dariya. Koda nagama wankin duk nagaji zuwa kawai nayi na kwanta sai bacci, ban farka ba sai 3.pm da sauri na miqe nayi alwala na bada azahar sannan na shige wanka koda na qare shiryawa ankira la'asar nayi sallah naci abinci Ji nayi kawai zaman gidan ya isheni, nafita waje nacewa mama zanje gidansu saudah, batayimun gaddama ba tace adawo lfy. [11/9, 6:03 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 8⃣ saudat qawa tace da muka taso tun muna yara muna qawance, saidai ita daga secondry school muka rabu dan ita bata cigaba ba, duk da tanada ra'ayin hakan amma gidansu daga ankammala secondry sai aure, saidai idan mijinki ya amince kicigaba a gidansa. Tafe nake ina saqar zuci ai gwanda nayi keeping kaina busy ko nasamu sarari a zuciyata, nashiga gidan tareda sallamah ta, mamar saudat ce ta kar6a a'ah yau su ameerah ne a gidan ai na dauka ko ba kya gari ne, murmushi na saki na sunkuyar da kai a qasa, a'ah mama wlh inanan, mutuniyar fa tacemin tana daki, hakan yasa na wuce da saurina na fada dakin, na tarar da ita tana linke kaya, kallona tayi ta watsar, na 6ata fuska haba qawas nasan banida kirki amma amin afuwa please. Tayi murmushi ai kedince wlh sai a slow bakidamu da wanda ya damu dake ba, sai faman zuwa nike gidanku amma ke shiru ba kya leqoni, haba mutuniyar bansanki da yawan fushi ba ki yafewa qawarki mana, kinsanfa banida watche tafiki, muka tafe muna dariya. Nafara tayata linke kayan ta kalleni, amma qawas meh ke damunki u are looking so pale, kuma duk kin rame, nace kedai bari qawas wlh soyayyah ce ke dawainiya dani. Jawoni tayi muka koma gefe tana dariya kai qawas ashe kinshiga system shine baki gayamin ba, who is dis lucky guy da yake wahalarmin da qawata, amma zanso ganinsa in jinjina masa, a ina kuka hadu dan wanne garine, ya sunanshi? Tagumi nayi na zuba mata ido tana jeromin tambayoyin da nikaina banda amsarsu, girgizani tayi wai ya hakane inata tambaya kin shareni, nayi ajiyar zuciya nace how i wish inada amsar tambayoyinki qawas [11/9, 6:26 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 9⃣ kallona sauda keyi irin kallon ban gane meh kike nufi ba, na nisa nace saudah wlh dakon so nake fama dashi, saudah tace kinqara sani a duhu, ban fahimceki ba, hawaye taga na fara ita ai duk jikinta sai yayi sanyi, qawans ya haka kinfara tadamin hankali, nace saudat wanda nikeso baimasan da zamana a duniya ba, hasalima ko sunansa bansani ba, bansan a ina yake ba, nidai nasan ina ganinsa a hanya idan zani school, ko idan mama ta aikeni, amma wlh saudah Allah ya jarrabeni da sonsa day nd my night aikin tinaninsa nake, sai nafashe da kuka. Saudah kan mamaki ne ya hanata magana, tadai jawoni tayi hugging tana rarrashi, qawata take heart Allah yana tareda ke tinda har son gaskia kike masa inshaAllah zai zama naki zan tayaki da addu'a. Bansan sanda na saki wata dariya ba da saida fararen haqorana suka bayyanah, nace amin qawata daz y nikeji dake. Cikin tsokana qawas kecewa ai inaga dai alhakin misbahu ne ke bibiyarki, bawan Allah har tausayi yake bani yanda yake sonki amma ke ko oho, take fara'ar fuskata ta gushe, nace qawas ya isheki kindai san halina idan banason mutum bana iya kulashi, tin ranarda ya aikoki wurina nagayamiki kice masa yayi haquri, amma shine da nacin tsiya yaqi haqura. Toh aikema gashina kina nachin abinda baimasan kinayi ba, zumbur na miqe ni kinga tafiyata tunda abun naki ya zama wulaqanci, dariya take ta biyoni haba qawas tsokanace fa kawai kiyi haquri, kizo akwai labari ko waiwayenta banyi ba na wuce gaba abina, nace mama natafi sai anjima, a'ah amirah har anfito to kigaida mamanki, kice mata sai na shigo. [11/9, 7:29 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 🔟 fitowa nayi inajin haushin saudat da nasan wulaqancin da zatamun kenan wlh Allah da banzo ba, samun kaina nayi da biyar hanya ba tareda nasan inda zani ba, inata mita a zuciyata, daga kaina da zanyi sai naga wani wuri, . Mai tarin itace masu ban sha'awa, ga inuwa mai sanyi a wurin ko'ina yayi luf-luf, kaina nasamu da sha'awan zama a wurin, shiga nayi nazauna ina waige_waige, wurin nidai ya birgeni, tashi nayi ina dan zaga wurin, mutum na hango zaune sanye da fararen kaya, yana zaune ya dora qafa kan qafa, amma banga fuskarsa ba, sai nasamu kaina da son ganin waye wannan mutum, tashi nayi na tinkare wurinsa batare da nasan meh zanyi idan naje wurin ba, ina gaf da isa wurin ne wani dan matashin saurayi ya isa wurin wannan mutumen, khalid dama nasan indai na nemeka narasa bazai wuce nasameka nan wurin ba, hannu yabashi suka gaisa, khalid namaimaita a zuciyata take naji zuciyata ta buga, yunquri nayi na qarasawa inda suke domin inga waye aka kira da wannan sunan, cikin rashin sa'a kafin na isa sun daga sun tafi, haushi ne ya isheni batareda nasan dalilin hakan ba, zaunawa nayi na bisu da ido, mota naga sun bude zasu shiga, wannan saurayin ne naga ya waiwayo, wata kyakkyawar budurwa ce da tayi wata shiga ta daukar hankali naga ta doshi wurinsu tana wani murmushu na yaudara, dayan saurayin ne da na tarar a wurin naga ya juyo, zambur na miqe tsaye ganin dream man dina, magana naga yanayima budurwar watche banji meh yake fada ba, naga ya juya a fusace ya shige motar, dayan saurayin ne naga ya shiga da sauri shima, sunja motar da gudu sun wuce, sunbar budurwar nan a tsaye.. [9/14, 12:55 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/9, 7:56 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 1⃣1⃣ inanan tsaye a wurin kamar wacche aka dasa ina aikin murmushi kamar wata sha-sha-sha, budurwar ce ta tunkaro wurin da nike, tsawa ta dakamun wache ita tadawo dani hayyacina, malama ki jaye kin wani tarewa mutane hanya, da wani uban hijabinki kamar wata matar liman, jayewa nayi nabata hanya taja wani dogon tsaki taje ta zauna tana huci, ni abun dariya ma yabani, nace bani nakar zomonba nima..... Malama ya isheki kinji ko na wulaqantaki ana wurin, sumui-sumui naja jikina zanbar wurin, wani hankerchief na hanga daidai inda khalid ya tashi, da sauri naje wurin na dauka na qara gaba abuna, zuciyata wasai kamar wadda akayiwa bushara da aljannah, sai wane yage haqora nike, khalid kawai nike maimaitawa ina smiling, khalid khadijah, khadijat khalid, what a perfect match abunda nike ta nanatawa kenan. Sai gab da magrib na isa gida ina shiga gida ana tada sallah, makewayi kawai nashiga nafito na dora alwala na wuce daki na tada sallah, nagama nayi azkar dina tareda addu'oi tareda godewa ubangiji da ya sanar dani sunan dream man dina, tareda fatar Allah ya mallakamin shi, mama naje nagaida a dakinta itadai ta lura da chanjin yanayina dan sai wane washe haqora nike ina jan su fatima da fira, ranar dai nayi fira a dakin mama har saida na lura duk bacci sukeji sannan natashi nawuce dakina, hanky din rabin raina najawo na shaqin daddadan qamshinsa na lumshe ido, na rungumeshi a qirjina da haka bacci 6arawo yayi gaba dani. [11/10, 10:42 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 1⃣2⃣ tun daga ranar namaida gun wurin zuwana, amma kamar khalid yasani nadaina ganinsa sam a wurin, yauma kamar kowacce rana nafitoh da yammah zuwa inda namaidah wajibi, tafe nake ina faman sauri kamar wacche tamakara tana gudun bulala, fatana kawai nasamu ko glance ne na abun qaunata, kici6is naji na yi kaura da mutum, dagowa nayi da niyyar bada haquri, wa zangani wannan masifaffiyar yarinyar nan ce ta ranar, kafin na iya bude baki sai ji kawai nayi ta daukeni da mari, shashasha sakarya jaka kawai, kina tafiya amma kamar wata dabba, bloody illeterate i dunno y i just hate u tayi tsaki ta wuce ta barni riqe da kunce, wurin da nayi achan naga itama ta nufa, binta nayi cikin hanzari dan idona ya riga ya rufe, da mari zanji ko da zagin da tamin, bana ko ganin gabana ina isa wurin ta na finciko kanta, sai ga acuci mazanta a qasa😂 na kwasheta da mari har guda biyu, kukan kura tayi tayo cikina, wlh yau sai na kassaraki ko waye ubanki a garinnan tinda kika mareni yau sai kin raina kanki, wanine ya taso ya shiga tsakani yana miye haka husnah kuna abu kamar illeterates, murya naji daga bayanmu wai saeed miye haka kabarsu su kashe kansu mana, yaja dogon tsaki, ya juya gurin husnah kewai wace irin mayyace, nasha gayamiki kar ki kuskura ki qara bibiyata, amma da yake ke jakace daqiqiya kinkasa fahimta, Zuwa tayi gabansa tana rausaya, tana wani marmadi da ido, haba sweathrt kayi haquri mana wlh i can't live without you, tureta yayi den go d hell and die, ni dama na huta wlh, jarababbiya kawai nd get d hell out of here nida na aureki gwanda na mutu ba aure sakarya kawai, kuka tafara tana fadin toh wlh baka isa ba indai kudi da mulki na magani dole ka aureni, miqewa yayi kamar wani zaki yayi kanta, ko ni da ke gefe ina kallo saida na tsorata, saeed ne ya shiga tsakani da sauri tareda fadar husna just leave here pls, tashi tayi da gudu-gudunta ta kama hanyar barin wurin, waiwayowa tayi ta kalloni ke kuma wlh sai na lalata rayuwarki, tafita wurin da sauri. [11/10, 11:12 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 1⃣3⃣ sai a lokacin ma suka lurada i'm still a wurin, saeed ne ya kalloni ke kuma miye ya hadaki da wachchen mahaukaciyar, a cikin muryata mai sanyi nike masa bayani wlh kawai colliding mukayi a hanya, na tureta without my knowledge, kafin na bata haquri shine ta wankeni da mari tana zagina, shine nikuma nakasa haquri, ko mamana da tahaifeni bata ta6a marina ba zanbar wata qatuwar banza ta shani a banza. Saeed ne yayi murmushi i like dat, inason inga wanda yasan enchin kansa, mutunen nawa na kalla sai naga baya ko kallon inda muke ya murtuqe fuska, smile nayi a raina nace wannan akwai mishkili, but i still love u nayi murmushi, saeed ne yake cemun ya naga kinata faman smile en mata, murmushin naqara yin nace bakomai, kawai whether wurinnan ne so romantic, saeed ne yace wow romantic huh just kina wishing your man is by your side ko, dariya nayi da ta bayanna fararen haqorana amma dai kai akwaika da zolaya, ni bamanida saurayi, hannu naga yasa a kunnensa yana dariya i'll just pretend i din't hear dat, dariyar nayi nima ina fadar just blif me ai ni bana qarya, jinjina kai yayi yace toh shikenan naji amma bawai yarda nayi ba, en mata baki gayamin sunanki ba fa, gashi har munzama friends, sunana khadijah amma anfi kirana da ameerah, wow toh nima dai ameerar zance dan kinada sunan mummyn mu, murmushi nayi yace lets seat mana. Mutumen ne ya miqe tsaye toh uban surutu idan kagama kasameni gida ni kaga tafiyata, juyawa yayi ya tafiyarsa baiko sake waiwayenmu ba. [11/10, 12:10 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 1⃣4⃣ saeed na kallah nace meh yake damun abokinka ne he look worried, murmushi yayi don't mind my friend he is so tense, kinga qawarki, nace qawata kuma wacheche qawata, yayi dariya abokiyar fadanki mana, nache oh kajika da wani zance, what about her? Yace er deputy governor ce fa na nan garin, zare ido nayi nace ashe na debo ruwan dafa kaina, dariya yayi harda qyalqyacewa, ashe dai mummynmu matsoraciya ce, nace haba ae dole ni ba er uban kowa ba inani ina masu government, dariya yasake yi, toh itace akeso a aurawa khalid take naji gabana ya fadi, amma shikuma baya qaunarta wacce yakeso tana germany wurin karatu, sai next year zata gama sannan suyi aure, sukuma mahaifansa sunqi su amince da haka, saidai ya kawo wacce yakeso sunbashi one week time, shikuma idan ba salmah ba he promised bazai zauna da kowacce mace ba, take hawaye suka cikamun ido na juya gefe na share kar saeed ya lura, yace so kinji matsalar abokina gashi sati dayan da aka bashi gobe ne zata cika daz y kika ganshi ba annuri, na jinjina kaina lallai yana cikin matsala, toh yanzu ya zaiyi, how i wish nasan amsar tambayarki nima da na samowa abokina solution, anyway ni zantafi en mata sai wani ganin ya juya ya tafi abunshi ya barni nan zaune bana ko motsi kamar wata statue. [9/14, 12:55 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/10, 2:39 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 1⃣5⃣ zaune nake nayi jungum hawaye sai korar juna suke, har hijabina ya fara jiqewa idona har sunyi red kamar wadda uwarta ta rasu, duhu ne naga yafara sauka wurin sannan na tashi na kama hanyar gida, tafiya nake kamar wachche qwai ya fashewa a ciki, gabadaya hankalina baya jikina, ina isa qofar gida naji ana kiran sunana, ko waiwayawa banyi ba bare mai kiran sunan yasa ran zan saurareshi, haba ameerah magana fa naketsa miki tindazu nazo nan ina jiranki akacemin ba kyanan, a fusace na juyo malam na aikamaka da invitation nace kazo ne? Ko anaso dole ne wlh mustafa kafita hanyata dan nagane take_takenka dan ka kuskura ka gayawa mama cewa wai sona kake wlh sai kayi danasani a rayuwarka, baki ya saki yana kallona dan ko a mafarki baita6a tsammani na iya tsiwa haka ba, tsaki naja na shigewata a gida, Aliyu ne yazo wurinshi ashe dama yana tsaye yana kallonmu, yace danuwa kayi haquri my sis ba haka take ba inaga dai da abunda yake damunta, jst go i'll talk to her later, sannan ya tafi. Mustafa cousin dinane dan wan mahaifiyata, yaro ne mai natsuwa kuma shima din ya hadu dai_dai misali, lura nayi da en kwanakinnan yana yawan zuwa gidanmu, kuma duk yazo sai yace a kirani mu gaisa, harda en gifts yake kawomin da mama, shiyasa nagane inda ya dosa, nasan kuwa idan har ya gayawa mama zancen yana sona na kade dan nasan tsaf yadda zatayi dan yaron yanada kirki, shiyasa nikeson intaka masa birki, dan nariga nayi nisa a son maso wani banajin kira. Fusace na fada gida nayi sa'a ba kowa a tsakar gida dakina na wuce direct na kullo qofa na fada kan katifata, da yake ina hutun sallah shiyasa banma bi ta tinanin sallah ba. [11/10, 2:55 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 1⃣6⃣ Aliyu ne ya banko qofar dagani ransa a 6ace yake, haba sis haba sis ae wannan bai kamaceki ba, yanzu miye laifin mustafa da zaki wulaqantashi, ko bakomai ai dan uwanki ne, hannu na daga masa ya isa aliyu kaga kaina kemun ciwo dan Allah kafita kabarni na huta, amma dai koma miye yaha musty bai chanchanchi hakan ba, mamace ta shigo tana kallon aliyu wanne mustafan tayiwa wulaqanci, cikin sauri nace mama wani yaro ne a chan layin ya dameni bayan ni nagayamasa bana sonsa, mama tace to wai ke ubanwa ma kikeso ni nagaji da halinnan naki duk wanda yazo gidannan da sunan yana sonki zakice ba kya sonsa, ko a haka zanta zama dake a gidannan muna gwada tsayi? Aliyu ne yace yo mama dama wa zataso bayan ta dorawa kanta........ Alamar magiya nayiwa aliyu alamun kar ya fada dan Allah, sai ya fakaice yace bayan ta dorawa kanta wani ustazanci kamar wata waliyiya, mama tace yo waya gayamata su ustazan basu son maza, dariyace taso ta su6ucemin, nace mama nidai kiyi haquri zan gyara, tace karma ki gyara yarinya kisha mamaki dan duk wanda naga dama zanbashi ke inhuta, shigowar saudah ne yasa mama da aliyu suka fita suka bar dakin. [11/10, 5:44 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 1⃣7⃣ juyawa saudah baya nayi nace meh kin qara zuwa da wani sabon wulaqancin ne, dariya tayi wai ke har yanzu fushi kike? Haba qawata ki haqura mana Allah tsokanarki kawai nakeyi, ns basar toh miye labarin da kikace zaki bani, bayan kin shareni kuma wane labarin zanbaki, toh shikenan riqe abunki nayi kwanciyata na qyalete. Duka saudah ta kaimin wlh ni badan nasaba da halinki ba, da tuni mun raba hanya shegen mishkilancin tsiya kamar wata er sarkin misira, dariya nasa na kaimata duka aini namafi er sarkin misra, gimbiya ameerah kenan na dagamata gira, muka tafe muka qyalqyale da dariya, amma wannan da ake dakon son sai yayi haquri dake, nace ba wannan ne sunanshi ba sunanshi KHALEED, kwantawa saudah tayi itama, ke qawas ashe love story yaci gaba ambarni abaya, toh ya akayi kika samo sunan keda kikace bakisan sunan ba, na kwashe duk yanda akayi bayan barina gidansu har zuwa yau da nasamo wannan bad news din na gayamata. Saudah ta sauke ajiyar zuciya tace ina ke ina jayayya da er governor da er germany ai ni a ganina gwanda ki haqura kawai wannan battle yafi qarfinki, zumbur nayi natashi zaune in haqura fa kikace saudah ai kuwa wlh kiji sai inda qarfina ya qare, ni kisani wannan er deputy governor batama dameni ba dan nasan bata gabanshi, wannan salmar ce dai ta tsayamin a heart dan ita yakeso nafara hawaye, saudah tace qawas gwanda kawai ki manta da wannan khaleed din dan yafi qarfinki, hannu na dagamata qawas ya isa haka indai bazaki fadi alkhairi ba gwanda kiyi shiru kawai, in yafi qarfina baifi qarfin Allah ba, danni dakice na haqura da khaleed gwanda ki fallamin mari. Baki qawas ta riqe miyayi zafi Allah ya ba mai rabo sa'a nace ameen. Kinga kafin ki fara fushin bari na gayamiki abunda ya kawoni, gobe za'a kawo lefena, washe baki nayi dama kinada wannan good news din kiqaki gayamin da wuri saida kika 6atamin rai? Saudah tayi dariya tace ai yanzu na gyara ran ko, dariya nayi nima nace shine baki gayamin da wuri ba ina matsayin babbar qawa, tayi dariya ina naganki bare nagayamiki kina fushi dani, gashi duk sanda nazo kinfita ashe ke gun zuwa kika samu, saudah ta miqe ni zantafi kishigo da wuri gobe akwai aiki nace toh na rakata waje, sannan nadawo na kwanta ina saqa abunda zanyi dan inga na taimaki rabin raina kuma yanda za'ayi na sameshi. [9/14, 12:55 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/12, 3:22 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 1⃣8⃣ ranar dai rabin dare haka ya qaremin ina saqa da warwarar abunda zanyi, sai kusan asubah nasamu bacci ya daukeni, asubar ma makara nayi saida mama taga ban tashi ba tazo ta tadani, ina gama sallah kuwa da qyar nayi azkar dina nakoma bacci ba, bani na farka ba sai qarfe goma, da yake weekend ne su suhaila na gida inaga shiyasa mama bata tadoni ba, nayi aiki, a gurguje na fito na dibi dumame naci na fada wanka, nafito na shirya, na saka hijabina nayo waje, mama ce tace sai ina kuma, dan na lura kwanan nan qafar kare kikaci, shiyasa kullum sai kinfita wai ina ma kike zuwa, karfa kiga na sake miki kizo kiwuce gona da iri, haba mamata ai kema kinsan er da kika haifa bazatayi shashanci ba, gidansu saudah fa nike zuwa da yake bikinta ya kusa, kuma yau za'a kawo lefe shiyasa ma zanje da wuri yau, mama ta saki fuska to ai ba laifi adawo lfy, kigaida hajiya asabe sai nazo taya murna nacd toh na zura takalmina zanfita. Khairi ne yace shishta(sister) kizo mana da alala da sho6o (zo6o) dariya muka sa nace qanen shishta don't worry zakaci alala da sho6o na fice. Gidansu saudah na nufa, nashiga sunata faman aiki na cire hijabina nima na shiga akayi dani, bayan mungama ne nace bare inje gida inyi wanka, kan masu kawo lefen suzo, mamarsu saudah ce ta debomin alale da zo6o, abinci da ma wasu kayan soye-soye da akayi na tarar baqi, nayi godiya na fice gida, da shigata khairi ne ya taso da gudu ya tareni ya kar6i wasu kayan da nazo dasu, dariya nayi nace khairi baban kwadayi ga alale da sho6o nan ayita fama, mama tace har ankawo lefen, nace a'ah nadaizo in watsa ruwane kan suzo, na debi ruwa na fada makewayi. [11/12, 3:23 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 1⃣9⃣ nafito wanka na bude akwatina na za6o sababbin kayana, na sheqa kwalliya, wata atamfa nasa mai kallar ja da black, dinki atamfar ya kar6eni gashi dama red nd black color sunamin kyau, red hijab dina na dauko nasaka saidai yau ban dauko mai kaimin har qasa ba yadai rufemun hands kawai, black shoes nasaka na riqe red nd black purse dina, ina fitowa suhaila tace su sis yau ansha kyau kamar wadda zataje beuty contest, murmushi kawai nayi nacewa mama natafi, koda na isa gidan har sunzo, lefe yayi kyau ba laifi daidai gwargwado, cikin raina sai fata nike Allah ya nunamin nima khaleed ya kawomin nawa. Daki na wuce wurin saudah da yake ita bata fito ba, tambayana take qawas ya kikaga kayan, dariya nayi nace gulmammiya ai da sai kifita kigani tinda kinkasa haquri, nace sadiq din naki gaskia bai iya za6en kaya ba ba abunda yayi kyau, qirji saudah ta dafe nashiga 3, na kece da dariya kewai har kin yarda wlh komai perfect kamar ke, duka ta kaimin na goce ni har kin tsoratani tace, fira muke da saudah amma ni duk rabin hankalina yana gun dream man dina na matsu time yayi na wuce inda ya zamemin ibada kullum, da qyar naga anyi la'asar sallah kawai na sallamah na miqe tsaye, saudah na fadin ina zuwa qawas, ban waiwayota ba nace sai na dawo qawas, murmushi tayi a ranta tace Allah ya raba rai da wahala. [11/12, 3:25 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 2⃣0⃣ tafe nake ina sauri dan naga na dan makara, kar nayi missing ganin abun qaunata, shigata wurin keda wuya nafara waige-waige ta bayana naji kamar ana magana, najuya na nufi gun sa'id ne na hango yanata zuba dukda bansan meh yake fada ba, raina yamin fes dan duk na hango sa'id nasan my dream man is there too, ina isa wurin sa'id naji yana fada, dis man u ar too stubborn ita salmar taka takasa komai akai idan har tadamu dakai she suppoz to agree ko auren ne a daura den she can continue wit her studies but no, now u are left wit no other option rather dan ka aure husnah, miqewa naga yayi what are u saying man, kasan yanda na tsani yarinyar nan nida na aureta gwanda na rasa raina beside ma, i promissed salma she'll be the only one 4me, saeed yace now m sure u gone mad, sai kagayamin meh zakayi now and today is your dead line, cikin tsawa khaleed yace i don't know man, may be zanyita roqonsu ne may be zasu haqura, saeed yace karma kasa ran faruwan haka kasan halin parent naka idan sukayi niyyar abu only God can stop it. Khaleed neh yace cikin muryar tausayi now what i'm gonna do, kasan idan aka auramin dat girl angama da rayuwata, nd dat means she won over me kenan? Sallamah nayi musu wanda yasa suka juyo wurina, saeed ne ya kar6a cikin sakin fuska, ameerah gimbiyar mata kema kinfito kenan, eh nace masa cikin sakin fuska, khaleed ne ya juya zaibar wurin, nayi sauri nace masa excuse me plz ya tsaya yanamin kallon meh zanmiki, nace can i suggest something please? Khaleed yace i don't get u, nace i over heard ur conversation and akwai abunda nakeson na fada may be dat will help you............ Daga mun hannu yayi cikin fushi daz enough who do you think yo are? Waya baki damar da zaki shigo rayuwata har kiyi tunanin zaki taimakeni? I don't need any help from anybody nd definately not from someone like you, yayi tafiyarsa, jiri naji yafara daukata take nakai zaune hawaye ne naji sunfara zubomin, saeed ne yace common big girl don't cry mana don't mind my friend yana cikin tension ne, sai sannan ma na tuna da mutum a wurin tears dina nagoge nayi murmushi wanda dagani kasan na dole ne, nace bakomai he is right i should have mind my own business. [9/14, 12:55 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/25, 2:20 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 2⃣1⃣ saeed ne ya zauna kusa dani, now tell me wane suggestion ne zaki bawa abokina, miqewa nayi never mind kawai wanda zanbawa dinma he is not interested so what is the point of telling you, tasowa yayi shima, don't say dat if ur suggestion wil help my friend wit his problem ki fada kawai i'll be the one to convince him, kabarshi kawai sa'eed is ok, is not ok really i beg u in d name of God ki fadamun ko sai na duqa a qasa, dariya nayi no its ok komawa nayi na zauna shima ya biyoni, i'.m all ears rasa ta inda zansoma nayi. Nace do you know sa'eed yace no i don't, murmushi nayi nace nima halin da nikeciki daya ne da abokinka😳 yace kamar ya mumcy? Na nisa nace akwai cousin brothers dina da suke sona guda biyu , so nikuma da wanda nikeso anturashi course a england sai nan da 1 year zai dawo, so wa en nan cousins din nawa sune suka fara rigima akan ko wanne shi za'a baiwa ni, so shine mamana tace na fito da wanda nikeso kawai a raba gardama, amma da naje na sameshi shine yake gayamin inba mama haquri da zaran ya dawo daga england zai turo magabatansa ayi zancen aure, shine da nayiwa mama bayani tace batasan zancen ba dole ne na fiddo wani dan ita tagaji da maganganun da ake gaya mata a dangi, kamar ita ta hanani aure, ko dai nakawo wani ko na za6i daya daga cikinsu, ni kuma na tsane auren dangi beside ma ni da wanda nakeso banji zan iya haqura dashi ba, gashi mama tabani 1week na zo mata da zabina, ko ita tayimin na kammala zancena ina qwalla😂 nima dai deejah da nike gefe ina kallonsu mamaki ne ya turnuqeni naji yanda ameerah ta taqar qare tana zuba qarya😂😂😂 kuma ga alama saeed qaryar ta shigeshi dan naga jikinshi yayi sanyi yakasa magana, dariya ce taso taci qarfina nayi sauri na rufe bakina dan kar su lura dani su kora ni. 😂 [11/25, 2:20 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 2⃣2⃣ saeed ne yayi ajiyar zuciya yace, amma na tausaya miki mumcy na kema ashe kina cikin tension just like my friend, yanzu miye suggestion din, nace saeed abunda zanfada is strange or weired sef may b ma kaga wautata, but a tunanina daz d only solution to our problm, why not nida friend dinka muyi aure, saeed naga ya kalloni, alamun what are you saying, nace i mean muyi fake marriage kawai, muyi aure just 4 d sake of our parent and muyi avoiding auren dole, kafin wa 'yanda mukeso su dawo den kowa ya kama gabansa😳 matsowa nayi kusa ni deejah dan na tabbatar da abunda kunnuwana suka jiyomin Saeed ne ya quramin ido daga bisani ya nisa yace ameerah u are a small girl really, do you take marriage as a joke? Taya zaki iya zama da wani namijin a matsayin fake marriage? Nace sa'eed as long as mun aminche da junanmu zamuyi aure just 4 a year da zaran wanda nikeso ya dawo zai sauwaqemun na aure wanda nikeso😳 shima yaje ya aure wachche yakeso, seed yayi shiru na dan wani time sannan yace shikuma wanda kikeson kina tunanin zai aureki later on? Nace i'll tel him my plan kuma nasan shima zai aminche coz he can't afford to luz me too, saeed yace u are crazy ameerah ni ko deejah a raina nace no she think she is smart ta dauka aure game ne nd i wonder ya zatayi keeping auren idan khaleed din ya amince, saeed ne ya katsemin tunani ta hanyar cewa anyway zangayawa abokina naji meh zaice though nasan is hard ya yarda dan shi bai hada salma da kowace mace ba, nace he can keep his salma 4 d mean time now yayi tunanin matsalarsa, fake marriage din ya za6a ko auren husnah. Saeed yace clever girl toh zan gayamasa but how wil i get bak to you, kibani number ki, nace aini banda waya, yace so ya kenan nace i can wait 4u here den yace are u sure dat wil b okay nace yes sure, ya ce toh shikenan sai kin ganni nace adawo lfy ya tafi, niko na nemi wuri na zauna ina tinanin what will happened next. [11/25, 2:20 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 2⃣3⃣ nikam deejah kasa jira nayi nabi bayan saeed da gudu, motarsa naga ya shiga atake na tsaida taxi da tashigo kan layin na fada nace malam bi bayan motar chan plz, tafiya mukayi amma ba mai nisa ba naga yayi parking gaban wani tamfatsetsen gida, mai kyaun gaske duk layin ba kamarsa, hon yayi aka wangame masa gate, na la6a6a nabi ta gefen motarsa na shige kar maigadi ya hangoni ya hanani shiga, wani daki naga ya nufa yayi nocking sannan ya tura qofar, khaleed ne kwance kansa na kallon ceiling, daki kam iya haduwa ya kai tamkar na diyan sarakuna, sai zuba qamshi yake, saeed ne yaje kusa dashi ya ta6ashi sannan ya dawo daga dogon tinanin da ya tafi, my man wai meyasa kakeda saurin fushi ne, abunda kayiwa ameerah sam bai dace ba, au toh idan fada kazo kayimin katashi ka tafi, saeed yayi murmushi khaleed kenan, ko daya magana dai nike baka, atleast u should have listen to her kaji meh zatace, khaleed yace kafi kowa sanin halina saeed banason shishshigi a rayuwata, who is she da zata yi suggestion in my life? Ko dan taga kai ka sake da ita ne, you should have told her ni dakai are 2 different people, what ever d case khaleed mutum daraja ne dashi, bakasan ranar da zata maka ba a rayuwa, yanzu dai tel me dan naga alamar aikoka tayi and you wont left here without convincing me dan nasan halinka, just tel me, what is her suggestion? Saeed ne ya kwashe duk maganar da mukayi ya gaya mai, zumbur ya miqe what are you saying? Ai kaji abunda na fada nd i also think daz d only solution you have left now, gayamin meh kace naje na gayamata she is still waiting there, cikin sauri khaleed ya fito dakin kamar zai tashi sama, nida nake la6e a bakin qofa sai jina nayi a qasa an wuntsilani, saeed ne ya fito shima da sauri yabi bayansa, yana fadin where are you going man? Bai saurare shi ba, ya shige motarsa ya tada saeed shima ya shiga tashi, tashi nayi nima na kakkabe jikina nafita da gudu na fada taxi da na shigo dan dama ban sallameshi ba nace yabi bayansu, inda mukabar ameerah naga mun nufa, aguje ya tsaida motarsa naga yayi cikin wurin da sauri, saeed na biye dashi yana kiransa, amma ina baya ko waiwayensa, nikuwa da gudu-guduna nike biyarsu dan kar ayi ba dani ba. [9/14, 12:56 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/12, 8:26 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 3⃣1⃣ wucewa nayi ba tareda na tanka masa ba, a raina ina fadan anya banyiwa kaina salalin tsiya ba kuwa? Tsaye nayi ina jiran naga wuce warsu amma naga shiru. A wajen khaleed kuwa cewa yake saeed mutafi mana, amma yayi tsaye yana kallonsa yaqi tafiyar, wai kai khaleed yaushe zaka rage wannan zafin ran? Haquri mu kazo bayarwa amma duk ka lalata al'amari, so can't u hear what d girl is saying? Saeed cikin fushi yace kai kuma ka manta abunda ka gaya mata jiya ne? Kasan wanne hali ta shiga ne? Ai ko nine ita wlh kai tsaye bazan amince dakai ba, yanzu ma wai dakace zakayi keeping promise whether wit her help or not meh ka shirya yine? Kamanta halin iyayenka ne? Meh zaka cewa umma ne da take zaman jiran ka kawo mata surukarta? Wata budurwar kake da ita zata taimaka maka? I don't think any girl wil accept diz madness of yours and help you, dat girl da kake fada is your only solution dan itama tana same situation like yours ne. Qarar wayar khaleed ce ta katse masu zance, khaleed yace mum ce saeed yace ai sai ka daga wayar, bayan ya sauke wayar ne saeed ya lura jikinsa yayi sanyi, yace ya akayi ne? Mum ce tace ita tagama shiri yanzu 'yarta kawai take jira tagani, saeed yace toh ai sai kayi niyyah ka kaimata duk wacce zaka kaimatan yanzu tinda kanada yanda zakayi, juya warsa yayi zai tafi, jawosa khaleed yayi don't do this to me man, saeed yace toh meh kakeso inmaka i don't have any solution 4u now, u already spoiled everything, khaleed ne cikin muryar tausayi yace saeed karkayi fushi plz kai kadai ne ka fahimcine and banida wanda ya fika, tel me what to do now! Saeed yace hanya daya ta ragema itace ameerah ka sauke girman kai kabata haquri, ka lalla6ata ta amince, in lalla6ata fa kace? Ai naga nima taimakonta zanyi the benefit is not only 4 myself, saeed yace no kafita buqata dan ita she has d gut tayi accepting choice din mahaifiyarta, how about you do you have that gut to marry husnah? Khaleed yace no never den ka za6i meh yafiye maka zaka sauke girman kai ka lalla6ata ko kayi disappointing mum dinka ka auri husnah? The choice is now yours kasameni a mota idan ka yanke hukunci. [11/12, 9:03 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 3⃣2⃣ ni kuwa gajiya nayi da jiran wucewarsu nace may be sun chanja way ne, nayi deciding na tari acha6a kawai nayi bus-stop, haka nayi kuwa tsayawar dan acha6a keda wuya mota ta tsaya a gabanmu, dubawar da zanyi naga su khaleed ne basarwa nayi na cigaba da ciniki da dan acha6an, khaleed ne yafitoh yazo gabana ya tsaya, ameerah plz m sorry sharrin zuciyane kawai but i really need your help, nace do you think your sorry can change everything? Idan sorry tana maganin koma what iz d need for police court and law? Juyawa nayi zan hau babur din, khaleed yace malam ka tafiyarka kawai ya bashi 500, nace malam ka tsaya ai ni na tareka ba shi ba, na haye dan acha6a nace mutafi, da sauri khaleed ya shiga gaban dan acha6an yace malam wallahi idan baka saukemin mata ba sai nayi qararka, dan acha6a ya rude malama dan Allah kiyi haquri ki sauka karki jamin jidali, kiyi haquri ku daidaita da mijinki. Mamaki ne ya turnuqeni tareda wani farinciki lokaci daya, saukowa nayi dole dan acha6a ya kama gabanshi. Juyowa nayi na 6ata fuska what do you want from me mr. Man? Can't you just let me be bayan duk cin mutuncin da kamin? Haquri nake baki plz i'm really sorry just forgive me ya riqe kunnuwansa, nace shikenan ya wuce but still don't espect anything from me na juya zan wuce, ji nayi an riqe qafata na juyo a razane meh zangani wai khaleed ne a duqe a qafata, plz just help me out ke kadai zaki taimakeni i don't want to loose salma coz she is my life and i already promised her dat she'll be my first and last dan Allah ki taimakeni, tiqisah! Lallai ba qaramin so wannan guy keyiwa salma ba take hawaye suka wankemin fuska, anya zan iya kuwa? How wil i get myself a place in his heart? Amma kuma bazan iya ganin dream man dina a haka na qyaleshi ba, i will sacrifice my own happiness for his, 😢 isowar saeed a wurin ya katsemin tinani princess plz forgive my friend tinda nake dashi ban ta6a ganin ya duqawa wata mace ba beside his mum sai ke, kinsan kuwa ba qaramin so yake yiwa budurwarsa ba, so ki taimaka mana plz nace shikenan saeed na amince 4 your sake, dariya yayi thanks alot princess, sai lokacin khaleed ya miqe yace thanks alot ameerah nayi murmushin da iya fatar bakina ya tsaya nace you are most welcome, a zuciyata kuwa ina fadan na saka kaina a tarkon wahala, my DREMS will get fulfil amma kuma zuciyarsa tana wani wurin, har na tuna wani littafi wai GANGAR JIKINSA NA AURA, amma gwanda ita danni ko gangar jikin bazan samu ba, zandai auri suna i pity myself amma kuma bazan iya barin dream man dina a wani yanayin ba. [11/13, 4:03 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 3⃣3⃣ zantafi nace da su, saeed yace cikin tsokana ai kinzama responsibily namu yanzu, dan kinzama matarmu, dariya nayi kaidai baka rabo da tsokana, toh ina zuwa haka kiketa faman sauri ba'a ma so a sauraremu nace school zani, inaso na duba results dinane monday zamu fara registration, wanne school kenan gimbiya nace UDUS yace wow ashe ke big girl ce, level and course nace na siyarwa ne, mukayi dariya nace kuna tsaidani fa let me go, ko da wani abun ne? Khaleed ne ya riqa yiwa saeed inkiya da yayimun bayani, yayi kamar baisan meh yake nufi ba ya basar, muje na tayaki duba results din nace godiya nake amma ka barshi kawai, yace ko kina tsoron nazo na gano miki fatima 9 (f9) nace haba malam ae na wuce nan saidai ko Aminu guda ( A1) dariya mukasa duka yace toh idan ba tsoro ba muje din nace yayi mutafi. Zagawa sukayi suka shiga mota ni kuma na shiga baya, tafe muke muna fira da dariya da saeed a mota, amma gogan naka uffan baice mana ba har muka kai school, department dinmu na nuna masu suka saukeni, fitowa nayi na haura sama saeed ne shima ya fito zai biyoni, amma khaleed ne ya jawoshi, wai kai inata nuna maka ka gayamata request din mama amma ka wani basar dani sai zuba kake, saeed yace kai kuma meh ya same bakinka da ya kasa magana, saini suda ko? Yace haba my man kasan ni ba haquri ne dani ba and i'm not good at convincing people, yanzu zan iya lalata komai nd u are going to blame me 4 it. Saeed ne yace ya isa, u are not gud at convincing people but u are good at convincing me right? Don't worry i'll talk to her, sama ya haura ya sameni amma saboda maza sunyi yawa a gun na kasa duba result din, saeed ne yace tel me ur full name and admission number na duba miki, khadijah Abdul-rahman my number is 033 biology department, kutsawa yayi yana dubamin, course 4 ne dama suka rage kuma duk an liqa, snapping yayi daidai number ta duk inda ya duban da wayarsa sannan ya fito. [9/14, 12:56 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/25, 2:20 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 2⃣4⃣ameerah ce zaune kanta ta dora a bayan kujera, idonta a rufe tana tunanin da ita kadai tasan miye, tsawar da khaleed ya daka mata ke! Shine ya razanata ta miqe tsaye, ashe nan da nike ganinki sumui-sumui kamar ta Allah dama ke munafukace? Take idona suka ciko da hawaye, ni zaki yaudara yaci gaba, and where d hell do you get the idea of ni zan iya auren mace irinki? Kalle kanki sama da qasa kiga, kaina na duba sama da qasan kuwa, nidai ba fara bace tas amma kuma nafi chocolate color haske, bakuma za'a sakani a layin mata masu tsananin kyau ba, amma kuma na wuce a sakani a sahun munana, inada kyauna dai-dai misali, fuskata dauke take da dara-daran ido masu haske wa enda akafi kira da golden eyes, ga hancina shima pointed daidai misali, sai beutiful lips dina wa 'yanda suka qarawa fararen haqorana kyau , haqorana suna dauke da wushirya amma ta gefe, wanda duk sanda nayi dariya suke qara qawata fuskata, jikina kuwa daidai misali, baza' a sakani layin sirara ba amma kuma baza'ace inada jiki ba, Allah yayimin qira daidai misali shiyasa ma a koda yaushe nake cikin hijabina, dan akwai ranarda saudah ta matsamin na saka gyale mufita, duk inda mukaje sai anbimu da kallo, marasa haqurin ma sai sunyi magana kai Allah yayi qira anan wurin, mu basar dasu, tun daga ranar bana iya fita saida hijabina. Tsawar da khaleed ya dakawa saeed ita tadawo dani duniyar tunanin da na tafi, saeed kabarni na daidaita ta, ashe saeed tsakaninmu ya shiga, daga yau karki kuskura ki ko qara zuwa kusa da inda nake inba haka ba sai na yagamiki, cikin sauri nabi hanyar barin wurin saeed ne yake biyata yana kirana, amma ina ko jinsa banayi nidai burina inganni a dakina kawai, ina kai baki qofar gida zanshiga saeed ne ya tare gabana, dan girman Allah ki tsaya ki saurareni, sai a sannan nasan still yana bina a baya, cikin kuka nace saeed just let me be plz duk abunda ya faru ni najawa kaina, look at me look at my house, m nothing taya zanyi tinanin a guy like khaleed zai iya zama dani koda da wasa ne, shigewa nayi gida da gudu nabarshi nan a tsaye... [11/25, 2:20 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 2⃣5⃣da gudu na wuce dakina inajin suhaila na fadin sister ga yaya musty wai kizo ku gaisa inji mama, fadawa nayi dakina na fada kan katifa na, sai wani sabon kuka da yazomin.... A haka mama tazo ta sameni, waike wane sabon hauka ne ya sameki zaki riqa shigowa mutane gida da gudu ba sallamah, sannan bakiji ana fadamiki ga mustafa nan yazo kifito ku gaisa ba? Banjuyo da kaina ba dan kar mama ta lura da yanayin da nike ciki, nace mama kice masa yayi haquri kawai, banajin dadine toh meh yake damunki? Mama kainane yake ciwo sosai, shigowa mama tayi ta ta6a kan sai jikina taji ya dau zafi zau, tace ashe ma harda zazza6i ke duk hayaniyar jama'ar ne har kinfara zazza6i tun kan bikin yazo? Mama ta dauka daga gidansu saudah nake shiyasani zazza6i, batasan abun nawa na daban bane, fita tayi tagayawa mustafa yau banajin dadi ciwon kai da zazza6i, saidai ya sake dawowar ma gaisa, miqewa yayi ya fita sai gashi ya dawo da magunguna harda kayan fruits da juices, ya kawowa mama gashi a bata, riqe baki mama tayi wai kaidai mustafa ko da wata a qasa ne, naga dawainiyar da kake da ameerah ta yi yawa, ko da abunda kuke 6oyemin ne? Take mustafa ya tuna da gargadin da na masa na kar ya sake ya gayawa mama sona yake, ya basar yace a'ah mama bakomai wlh, ba qanwata bace mama ta girgiza kai dai tace idan tayi tsami maji, sai ka dauka ka kaimata da kanka. Dauko kayan mustafa yayi yazo daki ya sameni, sweet sis ya jikin naki tashi kisha magani, banyi masa gaddama ba na tashi zaune ina riqe da kaina da ke barazanar fashewa, ya bude magani ya bani tareda tsiyayomin juice a cup, na dauka nasha nace thanks 4 your care yaya musty nagode sosai, kuma ina baka haquri akan abunda ya faru ranar kawai raina ne a 6ace shiyasa. Murmushi yaya musty yayi wanda ya qara fito da kyaunsa, bakomai sweet sis ni dama ba riqeki da komai ba, i know bazaki gayamin magana ba, ba dalili, murmushi nima nayi nace thanks 4 understanding yaya musty, miqewa yayi bari intafi kar na dameki da surutu, get well soon Allah ya baki lfy nace amin shiko ya fice abunshi. [9/14, 12:56 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/14, 11:44 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 3⃣4⃣ saeed ne ya tur6une fuska ai dama na gayamiki f9 kawai zamuzo mugani, zare ido nayi, nayi kamar zanyi kuka tel me u are joking plz, miqomin wayar yayi gashi ki duba da kanki, duk jikina yayi sanyi ganin saeed still bai sake fuskarsa ba, a sanyaye na duba results din meh zangani A guda 3 da C guda, juyawa nayi da qarfi na kalli saeed, dariya ya kwashe da ita har yana buga qafa, yace din't u trust yourself ne? Dan wani yace miki kinyi failing zaki yarda, baki yarda da kanki bane? Murmushi nayi nace na yarda dakaina mana, amma kuma kasan skul life akwai mugayen lecturers wanda basa son suga students sunci gaba, kuma ana samun kuskure ayiwa mutum exchanging grades nd ko kayi complain ba lalle ne a gyara ba, yace hakane kuma, mutafi ko da abunda zakiyi ne, nace a'ah gida zani direct coz m feeling weak coz da zazza6i na kwana jiya, yace eyyah princess its my friend huh? Nace not at all abun zuwa yayi dai. Saeed yace toh shikenan amma ba gida zamu ba, da inda zamu kaiki akwai wadda ke son ganinki, zare ido nayi nace, nikuma saeed wa keson ganina? Yayi dariya wadda ke burin ta zama mahaifiya gareki, nayi dariya nace banfahimta ba, yace mum din khaleed ce tace akawo mata ke, tanaso taga 'yarta qirji na dafe ni gaskia ba zani ba, saeed ne ya ce why ameerah? Don't u worry maman khaleed is a very gentle and wonderful woman zakiji dadin zama da ita, nace ni ba wannan ba ma saeed naga ai baj dace mu sako iyayenmu a wannan qaryar da muka shirya ba. Saeed yasa dariya saida yayi mai isarsa sannan yace, ai baki gayamin cewa secret marriage zakuyi ba, ko kinta6a ganin inda akayi aure ba tareda sa hannun iyaye ba, shin ma ba don iyayen zakuyi auren ba? Da badan sun matsa muku ba ai da kunjira masoyan naku amma bakuda choice ne right? Sai yanzu na qara gano qaryar da na tafka alhali ni banida wani masoyi da ya wuce khaleed, yace ya kinyi shiru princess? Ajiyar zuciya nayi sannan nace u ar right saeed, ni duk banma yi tunanin hakan ba yanzu nima sai na gayawa mama kenan? Dariya yayi yace dama dan fari dai duk yadda akayi sai ya ta6a wauta, ai ko kiyi gaggawar sanar mata ma dan auren ba wani daukar time za'ayi ba, qwalalo ido nayi, yace yes u heard me sai kifara shiri amarya to be, yanzu dai mutafi. [11/14, 12:19 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 3⃣5⃣ saukowa mukayi qasa khaleed muka tarar jingine da mota yana latsa wayarsa, hangomu da yayi yasa ya shige mota, muma zuwa mukayi muka shiga motar saeed ya fara driving, khaleed ne yace my man kayi mata zancen, cikin tsokana saeed yace kaida matarka kuma sai nayimaka magana da ita? Khaleed yasha mur i don't like d sound of dat, kai kasan banida wata mata da tawuce salma dis iz jst a formality, take naji wani abu ya tokaremun zuciya kuka nakesonyi amma ba hali dan banso su fahimci yanayin da nike ciki, saeed naji yace maida wuqar angon salma nima tsokanace kawai, don't worry mungama magana already yanzu wurin mummy zamu wuce direct yace, a hakan? Saeed yace bangane a hakan ba, what do u mean, i mean to say dressing like that ya nunani da yatsa, cikin fushi nace what is wrong with my dressing? Ko gidan masu kudi ba'a shiga da abayane? Haushi ne ya ida turnuqeni, dama mai neman kuka ne aka jefeshi da kashin awaki, take hawayen da nike 6oyewa suka zubomin, na dubi kayana jallabiyace baqa a jikina da farin hijab, itama kuma sabuwa ce yau nafara sakata, wata maqocoyarmu ce da tadawo daga makka ta aikoma mama ita a matsayin tsaraba, mama taga bata iya sakata, ta barmin riggar ta kamamin jiki ne shiyasa bazan iya rolling mayafinta ba nafito, shiyasa nasaka hijabina fari shima fa ba wani qato ne irin wanda na saba sakawa ba, iyakacinsa guiwa amma dan tsabar wulaqanci zai kushemin dressing, muryar saeed ta dawo dani daga tunanin da nike, cewa yake don't mind my friend princess u look good, cewa nayi ae ba dole fa ni ku saukeni gida kawai tinda shigata bata shiga gidan masu kudi bace, saeed yace common amaryarmu karkiyi fushi kiyi haquri kije dan mommy dan ta shirya ganinki karkiyi disappointing dinta, beside ma ni ba inda zanbarki kije, bance masa komai ma danni na riga na qule. [9/14, 12:56 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/14, 1:14 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 3⃣6⃣ khaleed ne yace saeed ya tsaya daidai wani qaramin super market na yaro gobirawa dake gawon nama, sannan ya fita dawowa yayi ya ja saeed kazo ka rakani plz, baimasa gardama ba ya bishi, bayan sunfita khaleed ke cewa saeed plz try nd convince her to change her dressing, saeed cikin fushi yake cemasa kai wai bazaka iya rayuwa ba sai kayi wulaqanci ne? What is wrong wit her dressing? Ko dan batayi shigar tsiraici ba? Khaleed yace don't missunderstand me man, kafi kowa sanin bana sha'awar ganin mace mai shigar tsiraici daz one of d reason da na qara hating husnah, atleast she can wear something classic and expensive dat will bring her beuty out, banason mum ko dad sufara zargin wani abu coz they knows she can't be my type of woman, atleast 4 d time been if not bcoz of dat meh zai dameni da abunda ta saka a jikinta? Saeed yace shikenan i wil try and convince her but idan naga ranta ya 6aci ko bata yarda ba i will not force her dole ka haqura muje a hakan, yace its ok just try 4me plz ya shige super market din shi kuma saeed ya dawo mota. Saeed ya kira sunana nace na'am zo ki rakani plaza gatacen ya nunamin ita da hannu, murmushi nayi nace saeed karka maidani wata qaramar yarinya mana, i'm not gonna change my cloths dis is who i'm, i'm not gonna change dat, yace yes i know nd m not trying to change you kawai dai bamason iyayen khaleed suyi zargin wani abune, coz sunsan dansu duk abunda yakeso must be classic and expensive, so i don't want your plan to fail tun ba'aje ko ina ba, daz y nima na yarda da hakan bawai munason mu nunamiki ke talaka bace ko baki isa ba, but idan hakan baiyi miki ba we can still go like dis i'm not going to force you, ajiyar zuciya na sauke nace ai abonkin naka ne komai nasa sigar wulaqanci da tun farko haka yayimin bayani, saeed yace don't mind my friend he is not good at convincing people kuma indai baisaba dakai ba magana wahala take masa, nidin ma dan mun taso tare ne nasan halinsa in and out. Khaleed ne ya dawo dauke da ledodi a hannunsa ya bude bayan motar inda nike zaune ya ajiye, ya koma gaba ya zauna, saeed yaja motar kai tsaye wani mole ya tsaya dake kan titi yace your highness mutafi ko, dariya nayi nace kaidai baka rabo da tsokana, nafito nabi bayanshi wani shago naga yanufa bakomai a ciki sai abayoyi da ready made dogayen riguna naji da fadi, yace oya sai ki za6i abunda ya miki, zagayawa nafara yi duk kayan da na kalla sai inga summin kyau kamar duk na kwashe shagon nayi gaba, wata riga na hango red anyi mata aiki da black zare tasha kyau sosai dagani zatayi tsada, nasa hannu na dauka saeed yace good choice nace amma dagani zatayi kudi bari na chanja, dauko rigar yayi yace never mind ur hubby is a rich man, oya za6i wasu kuma, nace halan riga nawa ake sakawa idan za'a shiga gidan masu kudi? Dariya saeed yayi Allah ameerah baki rabo da abun dariya choose some sai nagaya miki yanda zakiyi dasu later, wata pink abaya na za6o kafin na gama saeed ya dauko wasu har 3 ya qara aka masa bill muka fitoh, shagon mayafai da shoes nd bags muka shiga, suma saida muka za6o kala 5 da suka dace da kayan da muka za6o sannan muka koma mota, saeed yace boss ga bill fa kaje ka biya danni banfito da kudi ba, atm card naga ya miqa masa shikuma yakoma ciki, inata mamaki meh zaiyi da atm card tinda nidai banga bank a ciki ba, bangama mamaki ba naga ya dawo ya miqa masa atm card dinsa gashi ancire yalla6ai, yace ai ni har naga alert kan ka dawo, nidai inata mamaki a raina nace harkar masu kudi sai su. [11/14, 1:48 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 3⃣7⃣ hanya naga saeed ya kama bamu tsaya ko'ina ba sai zuru road, daidai dan wani madaidacin gida mai kyau da baqin gate, fita yayi yace your highness gidana na kawoki dan ki shirya, amma don't you worry ni ba gobro bane kamar wane da beutiful wife dina tana aciki tana jirana, dariya nayi nafito muka bishi a baya, sallamah yayi da gudu naga wata black beuty mace ta fito tayi hugging saeed, welcome bak my angel, tamasa kiss gyaran murya khaleed yayi bafa ku kadai bane da mutane a wurin, dariya sukayi saeed yace damar abun ba haram mukayi ba, zuwa tayi ina raku6e a gefe duk kunya ta isheni, ta ja hannuna baquwa sannu da zuwa kishigo mana kintsaya a qofa, saeed yace help her get ready plz munason tafito kamar sarauniyar kyau, dariya tayi your wish is my command my darling, ta kar6i kayan da ke hannunsa, nidai rayuwarsu ta birgeni jana tayi mukaje daki tafara duba kayan, red rigar da nafara zabowa tafito min dashi, tafito min da make up kit dinta da turaruka ta ajemin ki shirya kafin nazo, toilet dinta na shiga tsaf dashi sai faman qamshi yake na watsa ruwa nafito na goge jikina, wani maine na shafa meh dadin qamshi nafesa turaruka nasaka rigar fuskata powder kawai na shafa na shafa wet lips na dauko wani mayafi red and black shima na dora akan kaina kawai, fareedah ce ta shigo matar saeed badai har kin gama ba nacemata na gama, dubina tayi batace komai ba tajani mukaje gaban mirror, zaunar dani tayi, ta dauko makeup kit tafaramin shafe-shafe a fuska, goga wannan saka wanchan da yake ni ba ma'abuciya kwalliya bace ni wasu abubuwan banma sansu ba, tagama ta dauramun dankwali, tayimin rolling gyalen tasa pins ta liqe, ta qara fesheni da tirare ta daukomin black shoes dinda muka siyo da purse dinsa tabani na riqe, na dade ina kallon kaina a madubi gani nake kamar bani bace dama haka nikeda kyau. Saeed ne yashigo baby kuyi sauri fa har mum ta sake kira mungayamata muna hanya, tsaye yayi ya saki baki yana kallona, baby amma chanjata kikayi ko duka takaimasa dama qawata mai kyau ce kuma rufe idonka ingayamaka ta turashi waje ta rufe qofa, yana dariya ya fice baby kishi ko? Toh ai kinfita kyau nidai kufito haka, hannuna taja muje ni kuma sai wani noqewa nakeyi dan kunyar fita a hakan nike. [9/14, 12:58 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/15, 10:47 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 3⃣8⃣ jawo hannuna fareedah tayi mukayo parlour, karaf idona sai a cikin na khaleed na sadda kaina qasa ina wasa da en yatsuna, shikuwa ya dan dade yana kallona a ransa yace ashe dama yarinyar na kyakkyawa ce ashe rashin gyara ne kesa ba'a saurin dago kyaunta, anyway why do i even care? A fili kuwa yace mutafi idan kungama na gaji da jira, saeed ne yace malam baka biya kudin makeup ba zaka tafi bayan angyara maka amaryarka, shiru yayi yaqi tankamasa, malam don't pretend nasan ka yaba dan kafi 10 minutes kana kallonta ba ko qyaftawa, khaleed ne yace just stop it man karka jamun raini gun yarinya, ya fice warsa a waje, a raina nace lallai ashe kallon yarinya yakemin, zannuna masa ni ba yarinya bace kuwa, saeed ne yace lets go princess baby sai mundawo, ko da muka fita gogan har ya kame a mota shiga kawai mukayi ya figi mota da gudu, hanyar sama road naga ya dosa, daidai wani katafaren gida naga yayi hon, take aka wangame mana gate mai kamar gari guda, shiga ciki yayi, yayi parking. Wata kyakkyawar budurwa ce mai kama da khaleed ta doso wurinmu da gudunta, hugging dina tayi welcome our pretty sister inlaw, murmushi na sakarmata taja hannuna, sai wani katafaren parlour, yawu na hadiye nace a raina wannan gida shi akecewa aljannar duniya, no wonder khaleed yake jijji da kanshi haka, amma dai yau ya taimakamin da nazo da jallabiyata ko er aikin gidan sai tafini kalluwa😂. Wata matace tafito daga sama tazo wurinmu tayi hugging dina tace welcome my daughter, mamaki nayi dan bazaka ce itace ta haifi su khaleed ba, coz jindadi ya 6oye tsufanta duqawa naje nayi na gaida ita ta dagoni, no my daughter don't bother consider me your mum and also your best friend, jana tayi muka zauna a kujera common my daughter now tell me all about yourself karki 6oyewa mummynki komai. Khaleed ne yace mummy we ar in hurry daga skul muka fito so zamu maida ita gida kar famlynta su damu, mom ce tace no way yanzu da zuwanta ko hutawa batayi ba zaka wani ce zaku tafi? Yau ina tare da 'yata har dare or ar u jelous son? Khaleed yayi dariya jelous of u mum no way, a raina nace wannan ashe yana dariya he' s looking so cute, a fili nace don't worry about me i know mama will understand, cewa yayi well if u say so, mum tace daz my girl son na kasaka fa she choose me over you, mukayi dariya mu duka. [11/15, 11:29 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 3⃣9⃣ khaleed ne yaja saeed yace lets go man i don't want to watch dis drama further, dariya yayi ar u jelous man? Khaleed yace no way man but i can't deny it i wish dat its salma dat mum gets along wit dis well not ameerah, coz nasan halin mum ranar da game dinmu zai qare it wil b difficult to convince her, daz y banaso su shaqu sosai, saeed yace u are right saidai ya zakayi tinda baka isa ka hana mum abunda taso ba. Mum tace my dear call your mum and tel her kina wurin mum inlawn ki kar tashiga damuwa, nace mum i don't have a phone and mama ma batada, nobody at home has one, mum tace oh how comes but don't worry about it, yanzu tel me about yourself and your famly, nace mu 5 ne a wurin mama, ni aliyu, suhaila, fatima and umar but muna kiransa khairi, mum tace what about your dad? Nace my dad is late ya rasu, ce mun tayi sorry dear tayi hugging dina, nd how about skul nace mum ina udus ne yanzu zanje 200level and m studying biology, mum tace very good swearie u and kausar are studying same thing saidai ita 300lvl zataje yanzu may b daz y bakusan juna ba. Kausar ce tazo yau mum ta samu new daughter tadaina yayinmu, but atlest mum let her freshen up a bit taci abinci, u have your whole life ahead of u to discuss, mum tace u ar right daughter ameerah kuje dakin kausar and freshen up i will bring something 4u to eat, nace toh mukaje dakin kausar. Bayan munyi sallah ne mum tasa aka kawo mana abinci muka zauna tare mu 3 mukaci, siyama ce tashigo dakin da gudunta mum i'm home ta shigo ta fado kan jikin mum, ta nunani da yatsa who is dis mum? Mum tace dis iz ur sister inlaw ameerah, she is going to be ur big brothers wife, tasowa tayi ta fadomin wow our sister inlaw is preety, zaki koyamin irin kwalliyanki, a raina nace danqari yarinya kinkawo kuka gidan mutuwa amma nima zan koya, ko dan bother dinki coz i notice how he looked at me dazun, a fili kuwa nace ofcourse sweatheart i wil teach u, sai cewa tayi sister inlaw where is my chocolates mum said u'll bring lots of chocolates to me like sister husnah did, gabanane ya fadi nace na banu, ina zanfito da chocolates yanzu? Sallamar khaleed ce ta dawo dani daga tinanina. [11/15, 1:39 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 4⃣0⃣ khaleed ya shigo ya ajiyemun ledoji a gabana, ga ledojinki da kika bari a mota, kallonsa nake irin kamarya bangane ba, ko da na duba naga ledojinsa ne da ya fito dasu daga yaro gobirawa dazun, kan inyi magana siyama ta dira ta fara bude ledojin, leda ta farko chocolates ne kawai kala-kala da biscuites, siyama tafara jumping 4 joy ta sheqo da gudu ta rungumeni sister inlawa thanks alot i love u, tamin peck a kumatu, kausar ce tace sister inlaw is not fair fa, ni ina nawa chocolates din? Siyama ta mata gwalo tace bari induba sauran ledojin, leda ta biyu ta buda taga kayan makeups ne da turaruka, ta miqawa kausar sister dis is 4u tana dubawa tafara murna tayi hugging dina wow sister inlaw dis are all my stuffs thank u, nidai yage haqora kawai nike dan nasan banda ko ficika a ciki, 3rd ledan kuma turaruka ne manya-manya designers da gani zasuyi kudi, siyama ta miqawa mom, mummy dis is 4u and dad, mummy ta duba tace wow daughter ya akayi kikasan kowa abunda ya ke so? Nace mom khaleed ne ya gayamin, mum tace you shoudn't have bother yourself but anyway mungode, amma mutum daya kika manta dashi daz salim, khaleed ne yayi sauri yace mum ni nace mata basai ta siyamasa komai ba dan yana karatu a egypt bayanan, dariya mum taya ai da baka hana ba idan yadawo he'll be happy to see her gift, nace mum don't worry next time i won't listen to khaleed, mum tayi dariya no its ok, it good to start listening to your husband ae, kallonsa nayi naga yayi kicin-kicin da rai, murmushi nayi a raina nace, now i know u ar not all dat bad, u love ur famly and kasan abunda suke so, so u know how to make dem happy, nima zantayaka son su jst hoping dat you'll love me some day. Mummy ta katsemin tunani my daughter zo ki raka kausar wani wuri zan aike ku nace toh mummy na miqe, khaleed ne ya juya zai fita mum tace son kazo kai zaka kaisu ae, ransa baiso ba amma baya iya yiwa mahaifoyarsa gardama, cewa yayi mum toh su fito su sameni a waje. [9/14, 12:59 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/17, 5:53 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 4⃣1⃣ ko da muka fito khaleed na a mota, baya na bude da niyar inshiga kausar ta riqemin hannu, gaba ta bude ta turani dis iz ur perfect place ta rufe qofa, now u look like a couple nd also u look cute together, khaleed ne ya daka mata tsawa ke suda ki shigo mota mu wuce kintsaya kina wani sanabe shiga tayi a baya tazauna ta tur6une fuska, bayan munfita get ne yake tambaya ina zamuje tayi shiru, tsawa ya qara daka mata tambayarki nike ina zamuje? tace cikin alamar kuka shagon waya zaka kaimu, kallonsa nayi naga yayi wani kicin-kicin da fuska, amma na dake nace kadaina yiwa qanwarka haka mana, hakan baidace ba, kaga har ka sakata kuka, wata harara ya watsomin da saida en hanjina suka kada, kausar tace sister inlaw karki damu aini nasaba da halinsa, shuru ne ya biyo baya a motar inba qarar motocin da ke wulgawa ba bakajin komai, a haka har muka isa shagon saida wayoyi na yaro gobirawa, mota muka bude mukafito, muryar khaleed mukaji a bayanmu karku 6atamin lokaci i have something important to do, bamu ko waiwayosa ba muka wuce, kausar take gunguni dis guy is so mean, nace mijin nawa kike gayawa haka? Dariya tayi sister inlaw kema naga kamar fada kuke har mukazo nan banga ya kulaki ba, nida na dauka zanga soyayya na yawo, dariya nayi nace kinmanta halin yayan naki ne halan? Kinsan bayason raini taya za'ayi yayi soyayya a gaban qaunwarsa? ta6e baki tayi tace too bad nikam naso nasha kallon love scene, dariya nasa nace karki damu zaki gani watarana inshaAllah . Da haka muka shiga shagon wayar tsaye tayi sis ki za6i wanda kike so, kuma ki za6awa su mama da duk wanda kikeso ki siyama, ido na fito dasu nace no way, karki damu bana buqatar waya yanzu, tace don't embrass me mana sis, gardama taga zanyimata ta daga wayarta tasa call, sai ji nayi tana fadan mum taqi ta za6a,kan in ankara ta dora mun waya a kunne, muryar mum naji tana hello, na kar6amata, tace haba daughter kin daukeni matsayin mahaifiyarki kuwa? Nace ofcourse mum tace den ki za6i wanda kike so kuma ki za6awa kowa a gida, nace mata alright mum, gefen da naga alamun masu arha na nufa na fara za6awa, kausr tace sister inlaw miye haka? Jan hannuna tayi mukayi wani gefen waya ta dauko ta miqomin ki daukin wannan , naga ansa iphone 6 ido na zare, dan nashaji a skul ana labarin wayar tanada tsada, nace kausar a'ah wayar tayi tsada bari in za6i wani, kausar ta dafe kai stop embrassing me plz sister inlaw ,yanzu kema kinshigo M khalipha's famly kudi ba damuwarmu bane. Dole tasa na dauka tace next wa zaki siyawa kuma? nace mamana da qanena, wasu samsung galaxy ta dauko guda 2, nadai kar6i daya nace mama bazata iya amfani da wannan ba, bold 5 tace akawo mata guda 3, kallon ta nayi 3? Tace yes ni daya, ke daya da mama nace bayan iphone din kuma? Tace eh zaki iya amfani da bb 4 data subscription yafi sauqi, kada mata kai kawai nayi a raina nace kudi manya, wayaga mama da balackberry 😂 mukaje aka mata bill, atm card naga ta bada sun saka a wani abu sai naga an cire anbata, nace ohh dama haka akeyi? Lallai wonders never end reciept aka bamu muka fito. [11/17, 6:19 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 4⃣2⃣ fitowa mukayi muka nufi motor, munkusa zuwa mtn office ne kausar tace big bro plz katsaya muyi register sim card, cewa yayi wane simcard bayan wanda kikeda? ke Baku's gajiya da chanja layine? tace no bro sister inlaw zatayi, ni mamaki ma nike taya za'ayi kuna soyayya kabar budurwarka ba waya? sauri nayi nace no sister, yayita insisting ni naqi saboda banason waya tasa nadaina concentrating a karatuna, ko yanzu dan mommy tayi insisting ne kuma bazan iya mata gardama ba, tace wow i wonder meh mommy takedashi ba ba'a iya yimata gardama ba, keda big bro duk daya shima baya tsallake maganarta, tsawa ya daka mata tareda taka birki da qarfi, just shutup will u? Shegen surutun tsiya kuje ku dawo karku 6atamin lokaci . Fita mukayi cikin sauri muka shiga office din, kausar jana tayi muje wurin customer na, tace masa as usuall inason kabamu special numbers guda 4, nd kayimana register da sauri coz we ar in hurry, numbers ya bamu mu za6a wasu numbers na samu guda 3 iri daya just last digit ne different na dauka, kausar ma ta za6a akayi mana register muka fito, mota muka shiga ya figa da qarfi kausar tace sister inlaw wane sim kikeso ki sama dayan wayar? Nace nima bansani ba, tace kiyi trying etisalat layin nada kyau kuma suna browsing da sauri, bro........ Dakatar da ita yayi, karma ki tambaya nagaji dan ni ba direbanki bane, tace karki damu sister inlaw zanyimiki register na kawo miki, sis yaushe zaki fara registration? ni monday zanje if u don't mind muje tare, nace am sis ni inajiran sponsorship ne sai governor ya biya, tace what? zamuyi on monday kawai ba wani jiran sponsor da zakiyi, karkidamu u ar famly now, murmushi kawai nayi mata da haka har muka isa gidansu khaleed. Sallamah mukayi a parlour muka shiga, mommy ce ta taso wow welcome bak my daughter nd hug me, kausar ta 6ata face alamun shagwa6a mommy nifa tace come here too nd hug her, mukayi dariya, wani qaton mutum naga yana saukowa daga stairs mum taja hannuna mukaje wurinshi, my dear wannan itace surukarmu kyakkyawa da ita ko? Duqawa nayi nagaidashi ba yabo ba fallasa ya kar6amin, mum tace dadyn khaleed ta kawomaka turaruka kuma duk irin wanda kake so, yana a daki kausar je ki dauko masa yana a wall drop, dakatr da ita yayi, no don't bother kausar, angode ya wuce ya zauna ya dauko jarida yana dubawa. Sallamah akayi muka juya dan ganin mai sallamar tareda da kar6awa. [9/14, 12:59 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/17, 6:31 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 4⃣3⃣ wa zangani husnah ce ta shigo tana wani yatsina fuska tana rausaya, anyi shiga duk ta tsuke jiki kannan yasha attachment da wanin siririn mayafi da ta doro a kai, hada ido mukayi nayi saurin duqarda kaina gabana na faduwa, ga mamakina sai naga ta kawar da kanta, ajiyar zuciya nayi nace i think bata ganeni ba, yau nasamu transformation ba kamar matar liman ba😂 Dady ta nufa, dady karatun jarida ake ya dago kai welcome my daughter yaushe kika shigo? Tace yanzu dad, mind dinka na kan news paper, yace so ya mutanen gida? tace all fyn dad, yace good baki gaida mummynki ba, sannan ta dago kai sorry hi mum, hi kausar, wow siyama zo kiga na kawomiki chocolate, siyama tayi tsayinta taqi zuwa, tashi tayi what is going on? Siyama tace ni yanzu bana sonki i got my new pretty sister inlaw ta kawomin chocolates da yawa nd bicuits suna dakin mummy zo muje na nunamiki, husnah tace stupid girl meh kike cewa? Taje zata kwada mata mari kausar ta shiga tsakani karki sake ki ta6amin qanwa, abunda kikaji ta fada gaskia ne, wannan da kike gani itace matar da yaya khaleed zai aura, juyawa tayi wurin dad, dady meh suke fadane ban fahimta ba? Dad yace husnah kije gida kawai zamuyi magana, jijjiga dad ta ringayi dad just tel me is not true, dad ya duqar dakai qasa tace so gaskia ne kenan? ta sakeshi, zuwa tayi gabana ta tsaya na dago kai ina kallonta, kallona take ta duqar da kai kamar mai tunani, ohhh dama kece? Tayi dariya ko a mafarki banta6a tunanin jaka irinki zata iya qwacemin masoyina ba, ta tazgo gashin kaina jst bcoz kinje saloon anyimiki transformation kindauka daidai nake dake zaki iya takara dani? Kausar ce tazo ta tureta ta shiga tsakaninmu, wanke kausar tayi da mari itama ta rama sai dambe ya turnuqe tsakaninsu, nida mum keta kokarin rabasu amma sunqi rabuwa. Khaleed ne yashigo da qarfi mum wai hayaniyar meh nikeji haka,? Lura yayi da damben da ake zuwa yayi ya wurgar da su qasa duka, sannan ya tazgi kan husnah ya jata giri-giri a qasa dad na kiransa ya daina amma yaqi ma sauraren sa, saida yakai qofar parlour ya wurgata waje ya rufe qofa, ya dawo ciki yana huci meh er iskar yarinyar nan takeyi a nan? Dady ne yazo ya wankesa da mari rufe ido nayi inajin zafin marin kamar ni akayiwa. [11/17, 6:45 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 4⃣4⃣ dady cikin fada yakewa khaleed magana idan ka jiwa er mutane ciwo fa, kace bazaka aureta ba isn't dat enough? Sai ka wulaqantata haka? Idan ta gayawa mahaifinta kasan irin asarar da zaka jamin kuwa? Bubbuga qofa husnah ta ringayi da qarfi, ku kuma munafukan Allah u'll all pay 4 dis, ke kuma zamu hadu dake i promised sai na kasheki ba wanda ya isa ya qwacemin abunda nike so, dad ne ya bude qofa yana kiranta tafita da gudu ta shiga motarta ta figa da gudu tabar gidan. Dad ya dawo ya dinga masifa baya ko tsayawa mum na bashi haquri amma yaqi saurarenta, wayarsa ta fara ringing ya dakko ya duba, deputy governor ya gani yaja tsaki ai abunda nike gudu ya faru, daga wayar yayi a handsfree yana dariya, a'ah ranka ya dade kaine da kira yau? Ya katseshi husnah ta kira ta gayamin komai harda dukan da danka ya mata, toh bari kaji ingayamaka duk abunda ya samu 'yata wlh bazan yafe ba, kuma ka manta da contracts da mukayi magana zaka samu, ya katse wayarshi. Dad ya wurgar da wayar cikin jin haushi ya nuna khaleed da yatsa, kaga asarar da kajamin ko? Toh bari kaji ingayamaka dole ka auri husnah, saidai ka fasa auren wannan matsiyaciyar ya nunani da yatsa , mum tace bazatayu ba alhaji, yace toh saidai ya hadasu su biyu kenan. Cikin hanzari na dago kaina na kalli khaleed, da hannunsa ke kan kuncensa har yanzu, yau ne rana ta farko da dady ya mareshi kuma wai duk akan husnah, take wata tsanarta ta qara ruruwa a zuciyarsa, magana yafara da qyar irin cikin fushi sosai, idon nan sun kada sunyi jawur, yace dad! Tunda nake a rayuwata baka ta6a sani abu na musa maka ba, but ni bansani ba ashe i'm just a business collateral to u, ya share hawaye, dad kayi haquri amma bazan iya auren husnah ba, gwanda na mutu ba aure da na aureta, mace daya ta isheni a rayuwata bana buqatar biyu, ya juya ya fita a fusache. [9/14, 1:05 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/17, 6:58 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 4⃣7⃣ cewa nayi toh mama ki zauna mana, tace ba zaman da zanyi ke nike jira malama, nace mama khaleed surukinki ne, mum kuma mahaifiyarsa, kausar kuma qanwar khaleed ce, saeed kuma abokin khaleed ne, wa enda sukazo dazu kuma khaleed da saeed ne, kayan da ke jikina kuma siyensu mukayi. Mama ta dakatar dani ke banason shirmeh, nace mama tambayoyin da kikamin ne na baki amsa, zama tayi tace bayani zakiyimun dalla-dalla karki 6atamin lokaci, sannan na kwashe duk yanda akayi na gaya mata tundaga fitata gidan na zuwa inda mum da nayi, amma fa bangayamata qaryar da na fesa ba, da kuma fake auren da zamuyi, ba kuma zancen husnah 😉 mama tace toh shine dan zaki gaida uwar saurayi sai kin chanja kaya? Nace mama gidan masu kudine fa so kike na shiga a rainani, kingama wasu kayan na fiddo mata sauran kayan da muka siyo? Mama ta zare ido anya ameerah ba mai yanka kanki kika dauko ba kuwa? Dariya nayi haba mama ko daya wlh barma kiga, wayoyi na fito da su, na miqawa aliyu tashi da simcard mama ma haka, niko na riqe nawa, wani ihun dadi aliyu yayi kai sister yau nine da riqe galaxy Allah ya barminke sweet sis, suhaila da fateemah suka taso mu ina namu? Dariya nayi wa zai siyamuku waya yanzu ai sai kungama secondry tukuna, mama tace aliyu miqa mata wayar nan banason shirmeh, wane dan iskan ne zai kashemiki kudi haka? Idan har ba wani mugun manufa ne dashi ba, nace wlh mama aurena zaiyi, kuma ma wannan mamarshi ce ta siya, dan nace mata banida waya kuma babu ita a gida, sanda tace na kiraki na gayamiki zan dade gunta, na dauko ledar da mum ta bani na miqawa mama, kingama abunda tace na kawo miki, mama ta duba super holland ne manya guda biyu da wani dakakken lesi da wata hadaddiyar shadda ready made da turaruka da sabulai masu kyau, watsomin kayan mama tayi harda wayar ta miqe ai sai ki maida musu kayansu mu ba makwadaita bane bare a siyemu da kudi, tsawa ta dakawa aliyu ka bata wayar nan nace, aliyu nata gunguni dan yaga samu yaga rashi lokaci daya😢suka fice suka barmin dakina. [11/17, 7:36 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 4⃣8⃣ khaleed kuwa a wurinsa fushi yake tinda yashiga daki bai fito ba, har saeed ya dawo ya sauke kausar ya shiga dakinsa, man wai haryanzu fushi kake? Kayi haquri kawai, gobe inaso ka shirya muje mugaida iyayen ameerah, miqewa yayi zaune ba inda zanje malam, yace toh taya zakuyi auren batareda ka gsbatarda kanka wurin iyayenta ba? Yace saeed ni nama fasa auren tinda dad yamun haka, dama dan su matsane har na amince da wannan auren amma tinda dad yace saidai na auri husnah ba auren da zanyi, saidai na mutu ba aure, tunda ya fara zance saeed ya sake baki da ido yana kallonsa, kasan meh kake fada kuwa? Meyasa kake wasa da feelings din mutane ne? Bayan ita ameerah ta amince daqyar kuma na ta bbatar by now ta sanarwa mahaifiyarta, sannan ga mom ta amince da ameerah kana ganin yanda take farinciki da ganinta yau, qannenka ma duk sun amince da ita, sannan kawai kace ka fasa? Indai dad ne nasan yanada zafin rai amma kuma bayason yaga dansa cikin damuwa nasan zai janye zancensa, khaleed ne ya miqe ni nace maka na fasa kawai, saeed ya miqe you are on your own kar ka qara kirana ko nemana bazan qara shiga al'amarinka ba, ya ficewarsa. Mum ce zaune tana yiwa kausar fada meyasa taqi tsayawa taba maman ameerah haquri da taga tayi fushi, da badan dare yayi ba da sunje, tace mum bari inbaki number ta sai ki kira na dauka a dazu, mum tace yauwa bani, sukayita kira amma basu samu ba, kausar tace mum kabari muje gobe kawai, tace toh shikenan dama inason inyi magana da mamanta da banason auren ya dauki lokaci atleast nan da wata daya coz nima na matsu naga jikokina. Khaleed ne yashigo da sallamah, mum ta kar6a da fara'a dan halak yanzu muke, zancen aurenka nan da wata daya muka saka yayi maka? Karka damu da abunda dadynka yace, indai ina raye ba wata husnah da za'a aura maka, khaleed cewa yayi mum ni nama fasa auren na haqura, zanyi rayuwata alone har sanda dady ya yarda da zabina, dady ne ya sauko kar kasake kace ni na hanaka aure, kaje ka auri er talakawanka ba ruwana, saidai ko ficika kar wanda ya tambiyeni ya ficewarsa. Mum tace kaji ma ya amince so don't u worry nasan ma ko abunda yace yanzu dan baigama sauka bane amma zai haqura later. Khaleed yace mum nifa na haqura da auren kiyi haquri kawai ya juya zai wucewarsa, mum tace shikenan son tinda bakaso kaga ina farinciki kaje kayi yanda kaga dama, kabari baqincikinku kaida dadynka ya kasheni, tunda ku taurin kai ne daku kamar diyan shaitan, ta zauna tana share hawaye, kausar tace wlh Allah big bro bakada kirki kasa mum kuka, kuma sai Allah ya sakawa sis ameerah nida namiji ce wlh ni zan aureta na share mata hawaye. A razane khaleed ya juyo, yazo da sauri ya duqe gun mum ya riqe qafafunta mom dan Allah ki yafemin bansan ranki zai 6aci ba wlh na amince ko gobe kikeso a daura aure, dagaoshi tayi to ya isa son na haqura kar ka sake ka qaramin zancen zaka fasa aure, bakasan yanda nake burin naga aurenka ba, kuma yarinyar nan tashiga raina Allah, ina maka sha'awanta dan nasan zakaji dadin zama da ita, yace shikenan mum bazan qara ba, ya miqe zaifita tace gobe ka shirya ka kaini gidansu ameerar, gabansa ne ya fadi amma ya daure yace shikenan mum Allah ya kaimu [9/14, 1:06 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/17, 11:54 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 4⃣9⃣ khaleed bayan ya koma daki yayi trying wayan saeed yajita a kashe, dama yasan a rina, waya ya dauka bari ya kira salmah ko zaiji sanyi a ransa, kiran wayar yake tana ringing amma ba'a dauka, ya tura mata txt just call me bak my baby i really missed u, nagaji da rashinki ina buqatarki a kusa dani, yayi ta jiran call shiru har bacci yayi gaba dashi. A wurin ameerah kuwa bayan ta kwashe kayan da mama ta watso mata ta maida a leda, sai tayi deciding bari taje ta nemo extension wire tayi chargen phones din, tasan zuwa da safe idan su khaleed sukazo suka gaida ita zata yarda tayi accepting kayan, fita tayi taje dakin mama tace mama.......... Mama tace idan haquri kikazo bani karma kifara, kibari kawai zuwa gobe ki tattara kayansu ki maidamusu, ni ba shashasha bace da zanyarda da zancenki, kuma khaleed dinma banta6a jin zancensa ba sai yau, so ni bazan dauki wannan shashanci ba, wato kinga ni banida kudin da zan siyamiki abunda kikeso ba shiyasa kika za6i wannan hanyar? Toh bazan lamunta ba inada rai ba wanda ya isa ya lalatamin tarbiyar da na dade ina ginawa. Kuka na fara haba mama ni kice komai amma dan Allah karkiyi zargina, bazanta6a zubar da tarbiyar da kukamin ba akan wani abun duniya, laifinane da naqi sanar dake zancen khaleed da wuri, amma wlh mama just blif me dagaske yake da aure yake nemana. Toh idan har dagaske yake meh yasa baizo ya gaida iyayenki ba? Nace mama zaizo gobe inshaAllah, tace toh shikenan inanan ina jiransa inji da watchche yazo. Nace mama dama kaina ne yake ciwo nikeso inje chemist din chan in siyo paracetamol, tace ba inda zaki kibari a kira aliyu a waje ya siyomiki, nace mama wato baki yarda dani ba? Toh shikenan muje tareda fatima ko suhaila, tace nace ba inda zaki, khairi je waje kace aliyu yazo ana nemansa, khairi ya fita da gudu, nace toh mama ina a daki idan aliyun yazo, tace idanma wani abu kike qullawa tun wuri ki daina, tashi nayi na wuce dakina. Aliyu ne ya shigo da sallamah, sis ance kina nemana nace, kar6i extension waya zaka siyomin a waje, yace wai sister shikenan nayi asarar galaxy din kenan? Nace no bro gobe zaka kar6i wayarka inshaAllah, cewa yayi toh sis wai waye wannan khaleed guy din? Nace your brother inlaw to be, yace bangane ba kin haqura da wanchan guy din kenan, gaskia i'm happy 4u, nace bro bafa haqura nayi dashi ba shine dai kawai, zaunawa aliyu yayi, toh ya akayi kika sameshi da sauqi haka? Nace aliyu abun sirri ne, lets just say Allah ne ya kar6i addu'armu, nidai tashi kaje kar mama ta zaci wani plan muke shiryawa, sannan ya tashi ya fita, ko da aliyu ya dawo mama tareshi tayi, tace sai taga abunda ya siyo dole ya bata, zuwa tayi a dakina, wato ke nace ki tattara kayan mutane kinqi ko? Shine harda siyo abun saka chargi wa zakiyiwa wayo? Toh kinyi asararshi kuwa a gabana ta dagashi sama ta watse ta tafiyarta, wani haushi ne ya turnuqeni nasa kuka a haka har bacci yayi gaba dani. [11/18, 7:02 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 5⃣0⃣ Nice ban farka ba saida naji ana kiran assalatu na tashi na doro alwala, nayi nafila kan a tada sallah, naje na bubbugawa su mama, da aliyu suka tashi, bayan na gama sallar asuba na dauko azkar dina nayi, bayan nagama na buda qur'ani na na rinqa rera karatu har gari ya waye, fitowa nayi na tattara kayan wanke-wanke, da yake weekend ne na lura duk sunkoma bacci, bayan nagama wanke-wanke naje, na gyara dakina tas na share na chanja bed sheet harda saka turaren wuta, na share tsakar gida, na hasa wuta na dora ruwan zafi da yake hunturu ne anfara sanyi, zuwa nayi ina tada su suhaila su tashi, na gyara daki, mama tace karna tada mata yara yau weekend nabarsu su Huta, nace mama islamiyyarfa takwas tayi fa, sannan ta miqe ta tashe su, ruwan zafin da na dora nace su diba suyi wanka, sannan na dora dumame, nakoma gyaran dakin mama, shima na gama na chanja bedsheet na kunna tirare, itadai mama ta samin ido kawai tana kallon ikon Allah. Bayan su suhaila sungama shirin islamiyya ne sukaci dumame suka wuce skul, sake share inda suka 6ata nayi, yau nice harda mopping ledar dakin mama da nawa abunda na dade banyi ba, gamawa nayi na dibi ruwa na fada wanka, ko da nafitoh goma tayi shiryawa nayi na saka kayana cikin wanda muka siyo da saeed, nayi kyauna ba laifi dukda ba wata kwalliya nayi ba, dumame naci, sannan nace mama.......... Tace indai wurin maida kayan zaki ni ban yarda kije ke kadai ba, kibari idan su suhaila sun dawo kwa tafi tare, kuma kije ki cire kayannan na jikinki dan har su zaki maida. Daki na koma ina share qwalla nidai wlh mama ta dauki abunnan da tsauri, zuwa nayi dole na ciresu, lesi na na sallah na dauko wani fari da zanen flowers purple, na saka hijabina purple na fito, kallona tayi sama da qasa, wai wa kikeyiwa wannan qyalqyalin? harda wani sabon gyaran gida toh wlh ki kiyayeni, ba inda zaki na gayamiki, nace mama gidansu saudah zani fa, tace ae saudah ta gayamin rabonki da gidansu tin sanda aka kawo lefe, toh fitar da kike da yamma ina kike zuwa? Sallamar da akayi ta katse mama da tambayoyin da take shirin zubomin, nidai na lura da mama kwata-kwata yanzu bata yarda dani ba, amma kuma banga laifinta ba zamani ne ya lallace, samarin yanzu basa kashewa budurwa kudi a banza, batareda wata buqata tasu ba, hakan yasa en mata da yawa suke lalacewa akan kwadayin abun duniya. Rungumenin da akayi yasa na dawo daga tunanin da nike, kausar na gani a gabana suprise tacemin, dan duqawa nayi na gaida mum da suke tare, ta dagoni tana murmushi muka rungume juna, mama turus tayi tana kallon ikon Allah, nace mama wannan itace mum maman khaleed, wannan kuma kausar ce kinganta jiya, mama ta saki fuska a'ah barkarku da zuwa, kuwuce ciki mana, tajasu suka wuce daki, dakin aliyu na nufa da sauri, na bashi dan sauran chanjin da suka ragemin, kayi sauri ka kar6omin exotic guda biyu a shagon Abu, da robar ruwa guda 3 karka dade, idan kadawo ka dorosu a tire, ka dauko sabbin cups dinnan na glass da mama ta siyomin suna dakina ka dora akai, ka kawomin a dakin mama, yace sis ba cups din kayan aurenki bane? nace ina ruwanka nidai kayi sauri, sannan ya tafi nikuma na koma daki. [9/14, 1:08 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/18, 7:28 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 5⃣1⃣ koda nashiga sunata gaisawa kamar dama sun san juna, sallamata ta katsesu, mum tace 'yata zo nan kusa dani, naje dab da ita na zauna, tace ' yata tun jiya nike kiran number ki bata shiga, ko baki saka layin bane? Mama na kalla ta watsomin harara, tashi nayi na dauko wayoyin da kayan da mum taba mama na ajiye gaban mum, nace mama ce bata yarda nayi amfani da waya ba tace may b sai zuwa gaba, mom tace toh naji idan wayoyin ta hanaku amfani dashi, nata wayar fa? Sannan wannan kayan fa? Shiru nayi, mum tace maman ameerah kiyi haquri nice da laifi jiya ni na riqe ameerah a wurina har yamma tayi, kuma wayar nan ba roqa tayi ba, ni naga ya dace a siyota dan faruwan irin haka, dan da tanada waya jiya ko ke kinada da ta kira nayi magana dake, da baku tashi hankalinku ba duk da ameerah bataso ba nina matsa akan sai ta za6i wayoyin, kuma wannan kayan nice na bata ta kawo miki, bada wata manufa nayi ba, naga kamar anzama dayane tinda zamu hada zuri'a. Mama ta sauke ajiyar zuciya toh dama ni ba qi nayi ba, kinsan halin yaran zamani ka haifesu ne baka haifi halinsu ba, shiyasa gwanda na tabbata inda kayan suka fito da kuma dalilin bayar dasu kan na yarda ta fara amfani da su, amma yanzu ai komai ya wuce na gamsu, ameerah ki kwashe kayan, dariya mukayi duka, a raina nace alhamdulillah, mum tace amma nayi farinciki kuma na qara natsuwa da zabin da dana yayi, na tabbatar ameerah halinki ta dakko bata watsar da tarbiyar da kika mata ba kuma na tabbatar khaleed yayi dacen mace ta gari da suruka ta gari. Aliyu ne ya shigo da sallamah dauke da lemo da ruwa kamar yanda nace yayi ya ajiye musu, gaisawa sukayi nace mum wannan shine aliyu, tace lallai aliyu anzama samari, tace a ina kake karatu ali? Yace na kammala secondry last yr amma banci gaba ba dan bansamu jamb ba, mum tace aliyu kanada ra'ayin karatu a egypt? Cikin fara'a aliyu yace idan nasamu meh zai hana? Tace toh karka damu daukar nan da za'ayi inshaAllah dakai a ciki zaka samu scholarship, akwai dana da yake karatu a chan sai ku riqa zuwa tare dama zaizo hutu ranar friday, sai ku koma tare yanzu ka hadomin takardunka na tafi dasu, godiya aliyu yayi muma muka tayashi, mama kuwa mamaki ne ya kwashe ta tana ganin kamar a mafarki. [11/18, 1:46 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 5⃣2⃣ lemo na zubawa mom da kausar a cups na basu, suka kar6a, mum tace ameerah ki dauki lemo da ruwa ki kaiwa khaleed yana a waje, cikin kunya na tashi na dauki kwalin lemo daya da ruwa, daki naje na dauko qaramin tray cikin kayana na hada da cup nayi hanyar fita, tsalle naji kamar anayi a dakin aliyu na leqa, aliyu na samu yanata rawar skelewu, dariya na saka saida nakai kwance, Aliyu yace barni nayi rawa tun bayan rasuwar baba bansake samun good news kamar na yau ba, nace toh ka hada takardun ko kuwa? Yace yanzu zanhada nace shine oya kayi da sauri, na dauki lemo na fito waje. Gabana na faduwa na daure na isa wurin motar khaleed, qwanqwasa masa nayi ya bude qofa, nace ga ruwa, har da zaiqi kar6a ya tuna yunwa yakeji mum bata barshi ko breakfast yayi ba ta sakoshi gaba lemon ya dauka da ruwa ya barni da tray da cup dina, kwalin lemon naga ya bude ya kafa kai, na juya zan shigewata a gida, kirana yayi saida naji qirjina ya buga, na juyo na dawo, so nike ki dauko wayarki ki kiramin saeed, tindazu nike kiranshi yaqi dagawa, cewa nayi ni bansaka wayar a charge ba, tsaki yayi toh wa yacemiki wayar batada charge a jikinta, anaso ne kawai ayi charge b4 use dan ayi saving battery life, anyway dauko wayar na saka battery na, na kirashi, juyawa nayi naje daki na dakko balackberry na fito na miqamishi, tsaki yayi i phone zaki dauko malama, kuma ina simcard din ko dameh zankira? Komawa na qarayi cikin gida na dauko i phone din da simcard, na fitoh again, na miqamishi, sai yanzu ya fiddota cikin kwali na lura iri dayane da tashi har color, simcard naga ya 6alle ya saka sannan ya cire battery Yasa nashi, number saeed naga ya danna yasa call, sai ya tuna ba kudi a layin tsaki ya sakeyi, ba masu saida kati a kusa ne? Nace akwai a chan layin yace toh shigo mutafi ki nunamin, nashiga motar mukaje wurin siyen katin amma kuma maj katin bai fito ba, hanya kawai naga ya miqe bai tsaya ko'ina ba sai near by bank, fita yayi yaje wurin atm, naga ya fitoda sim pack dina yana dubawa yana latsa atm machine, yagama ya dawo mota call naga yasa, tafara ringing ya miqomin wayar, muryar saeed naji yana hello, nace ranka ya dade yace da wa nike magana? Sabuwar budurwarka ce da kaba number a jiya, dariya yayi haba Gimbiya ameerah ai ko a bacci na tashi zanganen muryar nan taki mai sanyi, dariya nayi nace ya aunty fareedah yace gatanan kan jikina, murmushi nayi nace toh ka gaida ita, khaleed ne yace malama toh bafa kiransa nayi ba dan kuyi fira, kar6e wayar yayi, saeed ina gidansu ameerah kazo ka sameni zamu gaida mama, kan ya bashi amsa ya miqomin wayar, nace hello saeed yace ameerah kice masa ba inda zani, nace haba yaya saeed ai wannan ni zakayiwa wulaqanci, shiru yayi sannan yace toh shikenan gani zuwa, amma wlh dan ke kawai zanzo nace na gode yaya saeed na kashe wayar. [9/14, 1:09 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/19, 7:03 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 5⃣5⃣ nace mama zanje gidansu saudah tace adawo lfy, nace mama ba kince ba zani ba? Tace yanzu kuma nace kitafi ba, ai dama rashin fahimta ne ko kinga laifina? Nace a'ah wlh mama dama duk uwa ta gari dole tayi binceki akan duk abunda taga yaranta suna shigowa dashi a gida, a ina yafito? Wa ya basu da kuma dalilin da yasa aka basun, kar son abun duniya ya rufe mata ido ko dan tanaganin basudashi, har tayi silar lalacewar tarbiyar 'ya' yanta, kuma mama ni nasan wannan zamani samari en qarya masu amfani da kudi su lalata yaran mutane su sukafi yawa, amma ni mama Allah ki yarda dani ba wani abun duniya da zaisa na zubarmiki da mutunci, tace ai shikenan na yarda dake ameerah dama tsoro ne naji kuma duk uwa ta gari dole taji tsoron faruwar wani abu gun 'ya' yanta, kuma na lura ma yaron yanada nutsuwa ba maison hayaniya bane, Allah dai yasa shine za6i mafi alkhairi a wurinki, ya daidaita tsakaninku yasa kuma alkhairi a aurenku, yasanya aure ne za'ayi na har abada, da qarfi nace Amin mama Allah ya barmin ke na rungumeta, tureni tayi ni sakeni marar kunya karki kadani, a raina nace mama bakisan yanda wannan addu'ar taki takeda muhimmanci a wurina ba dole na kar6a da qarfi. Nace mama ki bawa suhaila kudi ta siyo extension wire da kika fasa jiya ayi chargen wayoyin chan, tayi dariya hakafa kinsan innayi fushi ba sauqi nace ai kuwa yanzu biya ya biyo gyartai mama, dariya mukayi ta qwallawa suhaila kira ta fito ta bata kudin haka yayi daidai da shigowar saudah nace er halak yanzu zanje gidanku sai gaki kinshigo, tace ba wani nan ai bakida kirki kekan nace tambayi mama kiji Allah da gaske nake, mama tace ba ruwana tsakaninku ta shigewarta daki, nima naja saudah muka wuce dakina. [11/19, 7:26 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 5⃣6⃣ saudah tayi tsaye tana qarewa dakina kallo yau kuma sabon gyara akayi ameerah? Nace eh tace wannan kwalayen fa ko biki za'ayi a gidan shine baki gayamin ba? Daga mata kai nayi alamar eh, zama tayi a katifa ta jawoni na fado qasa, na kaimata duka so kike kimin illah ayi biki amarya a nakashe? Kallona take da alamar tambaya qarara a fuskarta, ke nifa bangane meh kike nufi ba, bikinwa za'ayi ne nace na qawarki mana, wace qawar kike nufi? Nace wace qawar kikeda a gidannan? Tace ke nifa kin dagulamin lissafi, nace aurena za'ayi nan da wata daya inshaAllah, tace da waye kuma? Nace da khaleed dina mana, khaleed kuma? Wani khaleed din kika samu ne? Nace khaleed dina dai da kika sani my dream man, tace qawas kinsakani a duhu a iya sanina khaleed kince da wadda yakeso, toh taya akayi zakuyi aure yanzu? Ko kuma kina gayamasa kina sonsa ya haqura da salmar zai aureki? Dariya nayi nace relax mana qawata abunnan fa ba na tashin sense bane, aure nacemiki zamuyi ba wani mugun abu ba, toh dan Allah malama kiyimin bayani i'm curious naji yanda haka ta faru, dariya nayi mai isata, sannan na kwashe duk plan dinda na shirya na gayamata, sake baki da ido tayi tana kallona saida na girgizata, tace ashe ameerah bakida hankali? A ina kika ta6ajin anyi haka? Ni ko a films ma banta6a jin anyi haka ba, yanzu kawai sai ki aure mutum dan kawai ki cika burin shi na auren wadda yakeso, nan da shekara daya sai ya sakoki shikenan ke burinki ya cika kenan? Nace saudah ba abunda zai faru inshaAllah, ai Allah yaga zuciyata shi zai taimakeni, saudah tace ameerah dis is total madness meh kika shirya yi nan gaba? Kinga ni badani za'ayi wannan haukar ba, yanzu zan samu mama nayimata bayani ta miqe ta nufi dakin mama. [11/19, 10:23 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 5⃣7⃣ da saurina na fita na jawota wlh saudah idan har kika gayawa mama abunda ke faruwa, we are done, karki sake ki qara kirana qawarki, na koma daki, biyoni tayi jiki a sa6ule, ameerah yanzu inaji ina gani zanbarki ki lalata rayuwarki a banza a wofi sanadin soyayya? Nace indai ke qawata ce da gaske ki tayani addu'a kawai, now its too late to cry saboda munriga munsaka iyayenmu a ciki there is no going back, haka yayi daidai da shigowar suhaila ta bani extension wire din da wayoyi naje na sakasu charge, itadai saudah kallona kawai take, wannan kuma fa? Nace maman khaleed ce ta siyomin su jiya, wannan ne nawa wannan ta mama, wannan ta aliyu, kayannan ma da kike gani duk ita ta kawosu dazu da tazo, jinjina kai saudah tayi ashe abun ya girmah kuwa, Allah ya kyauta, nidai fatana kar kiyi danasanin abunda kika shirya nan gaba, nace inshaAllah bazanyi ba indai har kuna tayani addu'a, katina ta fiddo a jaka ta jefomin sai ki tashi muje rabon katinan tin shekaranjiya aka kawo, dubawa nayi nace toh tashi muje, na saka hijabina mukayi dakin mama, nace mama zamuje rabon katin saudah tace adawo lfy, nace mama ki riqa lura nasaka chargen wayoyi a daki kar khairi ya shiga ya lalata tace shikenan adawo lfy. Khaleed kuwa direct office ya wuce amma still yakasa yin komai, wayarsa ya dauko ya kira salmah, saida ya kira kusan sau uku a na hudun sannan ta dauka, hello babyna yace haba baby haba tin yaushe niketa kiranki amma kikaqi dagawa har txt messages dina ba wanda kikayi reply, i'm really sorry my baby aikine ya mini yawa kasan aski idan yazo gaban goshi yafi zafi, daz y kwata-kwata banida sukuni, amma nima kewarka tana damuna, yace to atleast baby ki riqa replying msgs dina mana, tace ok zanyi qoqari duk ma meh ya rage nadawo gabadaya na zama taka wani farinciki ya ziyarci zuciyar khaleed sai wani washe baki yake, kai ba kace khaleed din ameerah bane da baya ko smile, cemasa tayi ok i have to go baby inada lectures now talk to u later batama jira abunda zaice ba ta kashe wayar, tabar khaleed riqe da waya yana kallo yanata murmushi. Abunda khaleed bai saniba shine salmah ta qare karatu tin last year tayi zamanta tana aiki, iyayenta sunyi-sunyi ta dawo taqi, dan ita salmah kwata-kwata aure baya gabanta, rayuwar duniya ta sawa gaba kawai. Toh nidai deejah ina biye dasu inga ya wannan drama zata qare shin khaleed ke wahalar banza ko ameerah? [9/14, 1:12 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/18, 1:54 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 5⃣3⃣ juya kan motar mukayi, wata motar muka isko a qofar gida na dauka ma saeed ne ya iso har a raina nace amma saeed yayi sauri dama dai a kusa yake, kausar ce tafito love birds a ina kuka fito? Nafito waje ban tarar daku ba, soyayya ruwan zuma, wata harara khaleed ya banko mata tayi shiru ba shiri, wurin wanchan motar naga ta nufa, driver mom tace ku shigo da kayan a ciki, buhuhuwan shinkafa uku naga anshige dasu ciki da jarkar man gyada da ta manja da su semovita da wasu kwalayen da bansan miye a ciki ba, mamaki nayi nafito nabi kausar muka shiga ciki, mum da mama na isko a tsakiyar gida mama nata aikin godiya har da su kuka, mom tace wlh bakomai duk abunda na muku duk qaruwar muce dan anzama daya, hugging mom nayi nace mom Allah ya biyaki da aljannar firdausi da kowacce mace zatayi sa'an suruka ta gari kamar ke da duniya tayi dadi, mom tayi dariya don't flirter me daughter bakomai wlh, tace ina aliyun ne ya bani takardun? Tsulum yayi ya fito daki ya miqa mata, akayi dariya nace su alhaj ali ashe dama ana bakin qofa jira kawai kake ayi magana, wata dariyar aka sake, mom tace daughter ni zantafi yaushe zanqara ganinki? Nace mom sai kin ganni kawai tace toh ko kinqi zuwa ma dai na kusa daukeki na maidake kusa dani, murmushi nayi na sadda kai alamar kunya. Waje muka fito zanmusu rakiya daidai isowar saeed, duqawa yayi yagaida mum, tace a'ah saeed lfy dai ko? Yace mum zamu gaida maman ameerah ne, tace ya dace kuwa, kausar kizo mubi driver kawai ya maidamu gida sukaja mota suka tafi. Cikin gida na koma na tararda mama tsaye inda na barta, ganin take kamar a mafarki abunda ke faruwa, nace mama su khaleed zasu gaida ke, sannan ta koma daki ta saka hijabi. Waje na koma nace dasu su wuce muka shigo tare dakin mama nakaisu, suka gaisheta saeed kawai ke ta faman zuba ana dariya amma khaleed kansa na qasa baice uffan ba, daga bisani suka miqe zasu tafi bandur din en nera dubu khaleed ya ajiye suka fita tashi nayi na bisu mukayi sallamah har na juyo khaleed ya kirani malama da battery na zaki ne? Sannan na dawo na bashi waya ya cire battery ya miqomin kwalin wayata da simpack, na shige su kuma kowa yaja motarsa suka bar wurin da alama har yanzu saeed fushi yake. [11/19, 6:41 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 5⃣4⃣ Dawowa nayi cikin gida nashiga dakin mama na isko ta tayi jugum, nace mama lfy kuwa? Tace ameerah anya ba mafarki nake ba kuwa? Zuwa nayi na girgizata ta tureni wai yaushe kika rainani haka ameerah? Dariya na saka nace mama tadake nake daga mafarkin da kike, aliyu ne yashigo daki yaci karo da kudin da khaleed ya ajiye a qasa, yace iye yaushe kudi suka fara yawa a gidannan har ake zubarwa a qasa, kuma kudi har 100 thousand, mama ta zabura dubu dari aliyu? Nace mama fa khaleed ne ya ajiyesu, mama tace waisu ko wane irin mutanen da basujin wuyar kashe kudi haka, tsakanin jiya da yau nawa aka kashemiki, nifa ameerah inajin tsoro dan bamuda abunda zamu biyasu, nace mama karki damu inshaAllah ba abunda zaifaru sai alkhairi, sunada kudin ne shiyasa suke kasheshi, mama bakiji ana fadin alhaj M khalipha a garinnan ba? Tace badai shahararren meh kudin garinnan ba? Nace shifa mama, ai shine mahaifin khaleed kinga kuwa su kudi ba komai bane a wurinsu, mama ta girgiza kai shiyasa kenan uwar tace su nan da wata daya su keson ayi auren, ido na zare 1 month mama? Tace eh aikema na lura auren kikeso, nace haba mama ni wlh ba wani nan, tace toh shikenan bari ince masu kince kinfasa auren ba yanzu ba, tashi nayi na fita da gudu ina fadin nidai mama bance ba, dariya sukayi da aliyu tace ja'ira Allah ya kawomu zamani. Fitowata waje tayi daidai da shigowar su suhaila, turus sukayi suna kallon kayanda ke waje, Fatimah tace mama halan yau biki za'ayi a gidannan? Mama ta fito tace Fatimah ba biki abun alkhairi ne de aka kawomana, amma bikin ma na zuwa, suhaila tace bikin wa mama tace na yayarku mana, suka fara tsalle, muka taru muna duba kayayyakin, buhun shinkafa 3, na semo 3,buhun suger 1, na gishiri qarami 1, jarkar manja, jarkar mangyada, katin din taliya 3, na macroni 3, na coucous 3, na indomie manya 3, dayan kwalin kuma kayan magi ne aka hada kala-kala. Mama tace Allah ya sakawa wannan mata da alkhairi mukace amin, tace haka na wayi gari yau ba ko ficika har ina tunanin meh ya rannan zasuci idan suka dawo, sai gashi cikin ikon Allah abinci yanzu saidai mu baiwa wani Allah mun godemaka, a raina nace mama inshaAllah hakan zai dore kuwa, mama tace to kufara kwashe kayan ku kai dakin ali, kwalayen kuma akai na ameerah, haka muka fara kwashe kayan muna sakawa daki yanda mama tace. Mama tace aliyu ina kudinnan? Zarosu yayi daga aljihu, nace su alhaj ali meh nera ashe kudin har sunkai aljihu, dariya akayi yace sis kedai gwanda na riqe banta6a riqe kudi haka ba inadai gani a movies, mama ta kar6a ta zaro dubu 6 ta bawa aliyu kar6i wannan kaje ka siyo mana kaji, ka hado da kayan miya harda kayan salad a hada cose low, gwanda muji dadi a yau, khairi ya fara murna harda tsalle yau gidansu za'aci dadi, Fatimah tace mama yauwa kinsamu kudi a chanja mana uniform da takalmi kinga wannan duk sun tsufa, mama tace angama fatiti, har jaka ma sai an chanja kuje dai kucire uniform sukayi daki suna murna. [9/14, 1:14 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/20, 7:04 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 6⃣0⃣ mama tace ameerah ki gayawa khaleed yazo gobe alhaji na son ganinshi da yamma, dama ae ya dace sugaida mahaifin naki, nidai gabana ya fadi nace a raina mama tajamin rigima taya zan iya convincing khaleed yazo ya gaida baba shehu? Na tabbatar ma ko gaida mama da sukayi saeed ne ya tirsasashi, inaga shiyasa ma yake fushi, mama tace ba dake nake magana ba kikayi shiru? Nace ni mama ina tsoron su wulaqantashi ne kinsan halinsu, mama tace ai baiyi musu kalar wulaqanci ba bare su rainashi, ni nasan alhaji da kwadayi yana ganin dan masu haline zai aminche ayi auren, nache toh shikenan zan gwada da haka har muka isa gida. Wayoyina kawai na dauka, nace mama ina ta aliyu? Tace ai tun da rana ya dauka, dariya nayi nace aliyu sarkin rawar kai, nayi hanyar dakina mama tace toh ni baza'a tsaya a nunamin amfani da wayar bane? Dole na dawo na saka layi na kunna nafara nuna mata, dama duk da banida waya na iya harkar waya dan ina kar6ar ta khadijah nasir barau a skul, ita kadaice qawata da muke tare a skul. Daki na koma bayan na nunawa mama na kunna i phone dina, dama layin yana ciki da khaleed ya saka dazu, a raina nace waini ameerah yau nice riqe da iphone rayuwa kenan, balance na fara checking dubu goma sha tara da dari takwas nagani, nace tab wato khaleed dubu ashirin yasa a layinnan dazu lallai manya, register transfer nayi, nayiwa mama transfer 5000 aliyu ma haka, toh yanzu ni wa zan kira? Mum wata zuciya tacemin nace aikuma banida number, saeed ya fadomin a rai, na duba call record nayi saving number sannan nasa call. Muryar aunty fareedah naji, ameerah Gimbiya dariya nayi muka gaisa tana tambayar yaushe zanzo mata? Ya kamata muma mu saba da juna tinda mazajenmu aminaine, nace mata zanzo inshaAllah, sannan ta miqawa saeed wayar, nace yaya saeed dama mamace tace yakamata kuje ku gaida kawuna, yanason ganinku, yace ganinmu ko ganin khaleed? Meh yasa bazaki kirashi ba ni kinga nagaji da shiga al'amarin khaleed, nace plz yaya saeed dariya yayi yace ai gwanda ki koyi magana da mijinki, na lura ma ni tsoronsa kike, nace bahakabane fa yace to ki kirashin mana, nace toh aini banida number sa, kashe wayar yayi sai ga txt number khaleed ce har 3, saving dinsu nayi, dayar nasa MY DREAM MAN, dayar kuma PRECIOUS, dayar kuma SPECIAL, juya wayar na dingayi ina tunanin ya zan kira khaleed. Dakewa nayi nasa call sai da tayi ringing har takusa tsinkewa sannan aka daga, muryarsa ta doki kunnena take naji nakasa magana, hello hello yake yaji shiru ya gaji ya kashe wayarsa, sake bugawa nayi cikin masifa aka dauka, kowaye idan bazai iya magana ba kar ya qara kirana nonsense sai aka kashe wayar again, nace ni ameerah naga takaina dis my DREAM ya jamun lalura wannan wane irin so ne haka da kullum baya raguwa sai qaruwa yake? Saeed na qara kira ya daga ya kukayi dashi ne? Nace uhmmm nidai yaya saeed ka kirashi kawai plz yaqi dagawa, dariya yayi saida yayi mai isarsa dama ns gayamiki tsoronsa kike lemme call him nace nagode na kashe wayar. [11/20, 7:25 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 6⃣1⃣ saeed ya kira khaleed, khaleed yace aboki kayi missing dina kenan, tsaki yayi ni malam indan kai zankira saidai ka bushe, dariya khaleed yayi toh ya akayi ne? Ameerah tace ta kiraka kaqi dagawa, khaleed yace when? Saeed yace yanzu, khaleed yace ta kira dai takasa magana ashe dama itace, saeed yace ka balbaleta da masifa ya zatayi magana ae nasan halinka, yace nidai abar zancen ya akayi ne? Saeed ya kwashe yanda mukayi ya gayamasa kuma karka sake kacemin bazakaje ba coz itama tazo tagaida naka iyayen, khaleed yace toh ni bangaida mahaifiyarta bane? Saeed yace daz different dan mahaifi ke bada aure ba mahaifiya ba, ita kuma ameerah dadynta ya rasu kaga kuwa dole aje gun dangin mahaifinta neman aurenta dan haka kashirya kawai gobe muje after asr prayer, ya kashe wayarsa bai jira meh zaice ba, khaleed yayi murmushi saeed kenan, kiran ameerah yasa after yayi saving number ad FAKE WIFE😳 sorry ameerah kinban tausayi😭 Kamar a mafarki naga kiran khaleed a wayana, hannu na qyarma na daga cewa yake zamuzo gobe da yamma muje gidan uncle din naki sai ya kashe wayar, wani farinciki naji natashi na gayawa mama na dawo dakina na kwanta inata aikin murmushi, wayatace ta sake ringing na daga muryar kausar naji wato yayanmu ya riqeki ko? Tindaxu nike kira ana sakamun busy dariya nayi, nace ya akayi er qanwata tace gobe zanzo da safe mufara registration, nace mata toh sai kinzo qabwarmu, nace ki turomin number mom plz tace shikenan yanzu kuwa, tana kashewa sai ga txt nayi saving numbers din nakira mum, mundade muna fira sannan na kashe wayar, aikin downloading nafara bayan nayi sub waqoqin MAHER ZAIN DA SAMI YUSUF nayi download na kunna ina saurare har nayi bacci. [9/14, 1:18 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/19, 3:27 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 5⃣8⃣ ameerah basu dawo daga rabon i.v saudah ba sai da yamma liqis, tana shiga ana kiran sallah, dakin mama ta shiga ta zube kwance, mama tace ke ya haka bakiji anata kiraye-kirayen sallah bane kikazo nan kika kwanta? Nace wlh mama a gajiye nake yau munsha yawo, kusan duk frnds dinmu na primary da secondry da muka san gidajensu saida muka tafi, mama tace ae gwanda da kukaje, idan kintashi rabon naki katin basai kinsha wahalar nemansu ba, nace wlh Allah ni mama bazan iya wannan wahalar ba, tace ashe kuwa ko tsuntsu bazaki gani a bikinki ba, tashi nayi nidai mama ina abincina yunwa nikiji Allah tace yana dakinki a kula, tashi nayi zanfita na juyo yauwa mama ancire chargen wayoyin kuwa? Tace eh gasu nan a drawer nace yauwa bari na gama cin abinci nayi sallah nazo na koyamiki yanda ake amfani da wayarki tace toh. Daki naje na farma abinci da ci kamar ba gobe, na loda na loda naci kaji nasha zo6o, saida nayi qat naji ba space din saka wani, aikuwa sallah sai a zaune nayita ga gajiya ga qoshi, kwantawa nayi har bacci ya kwasheni kiran sallar asham ya tadani, alwala na sake nayi sallah sannan naje dakin mama. Mama ina wayoyin suke? Tace aje zancen wayoyinnan kitashi muje wurin kawunki, nace wane kawun mama? Tace ubanki shehu ko kinada wani kawun ne bayanshi? Nace mama wlh Allah kinsan na tsani zuwa gidansa, da wannan tsinanniyar matar tashi, bare ma wannan saratun mai jinkan tsiya, mama tace ae kuma ya zama dole kizo mutafi dan duk yanda nasoki bazan daura miki aure ba, dole dangin ubanki zasu auradda ke danke ba shegiya bace, gashi iyayen khaleed mu suke jira su turo magabatansu ayi tambaya, nace mama toh kitafi ke kadai mana, tace wlh ameerah kifita idona kitashi ki dauko hijabi mu tafi, haka na tashi badan raina naso ba na zunbulo qaton hijabina muka kama hanyar gidan. Alhaji shehu yayane gun mahaifina da suka hada uba, tin bayan rasuwar shi ya juya mana baya, qwandalarsa baya iya bamu, indai zamuje gidanshi zagi hantara da wulaqanci ne zai biyo baya, shiyasa muka tattara muka daina zuwa gabadaya. Sallamah mama takeyi a bakin qofar parlour, amma anqi kar6awa duk da cewar munajin alamun mutane a parlourn, qofar na fara duka iya qarfina, sai gashi anfara masifa wane mahaukacin ne yake bugamana qofa idan anqi kar6a maku basai ku tafi ba, tura qofar nayi na shige, saratu ce ta taso waike wace irin mahaukaciya ce? Nace saratu ba gunki nazo ba gun kawu mukazo, haj asabe ce tace, sara baby dawo qyalesu indai Alhaji ne qwandala bazai basu ba, dan basu ke nemomishi ba, mama tace asabe mu ba bara mukazo ba ina alhajin yake? Alhaji ne ke saukowa daga matattakala toh idan ba bara ya kawoku ba meh kukazo yi? Buhun masara da na aika muku ne har ya qare? Toh ni kusani banda abun baku yanzu, murmishin takaici mukayi buhun masarar da yake magana fa tin wanda ya aiko ne azumin bara, mama tace Alhaji mu ba wannan ya kawomu ba, saukowa yayi ya zauna toh ina saurare, tace dama kan maganar auren ameerah ne ya taso shine iyayen yaron sukeso ka saka musu rana ayi tambaya. Haj asabe tace wane matsiyacin ne zai kwashi wannan? Yarinya tana fama da hijabi kullum kamar mai cikin shege, saratu ce tace mom ai ba kama bace dama mu munsan komai bawani jami'a da ake zuwa yawon iskanci ne kawai. [11/19, 3:58 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 5⃣9⃣ Nikam dai na riga na qule, tashi nayi na wanke saratu da mari, kin dauka yanda kike hakama kowa yake? Ko kindauka bamuda labarin har ciki aka zubarmiki? Kukan kura tayi tayo cikina, muka hau dambe, take na fitar mata da jini, dama fatar ba quality duk anyi bleaching an kode, haj asabe ce ta fara ihu wayyo alhaji zasu kashemin 'ya na shiga 3 harda jini, zuwa tayi ta wankeni da mari baqinciki kikeyi dan kinga' yata fara tafiki komai, nace wannan mai siffar akuyar ce tafini komai? Inda bamusan komai ba farin ai duk na kanti ne, mama ta bugemin baki na fita ta gudu ina kuka, mama tace alhaji dan Allah kuyi haquri, hajiya tace nayi haquri bayan tanason ta illatamin yarinya ita kadai na mallaka duk abunda ya sameta sai nayi qararku, mama tace dan Allah kuyi hakuri, haj kidaina shiga fadan yara wannan tsakaninsu ne, kuma inkin lura ita saratun ita tafara, alhaji yace toh ya isa, Maryama kitafi kawai idan nasa rana zan sanar daku. Mama tace alhaji sunce nan da wata daya sukeson ayi bikin dan Allah kasa lokaci da wuri, yace yaji ki turomin yaron naganshi dan nagano idan dagaske yake, mama tace to alhaji yaushe kakeda lokaci sai yazo din? Yace ko gobe da yamma ma, mama tayi godiya ta fita. Hajiya tace alhaji ya akayi ka amince da haka, yace kawai inason inga matsiyacin da zai auri watcchan matsiyaciyar yarinyar, haj ta sheqe da dariya nimafa inason in ganshi may be ma musaki ne, suka sheqe da dariya, mama tajisu a ranta kuwa tace zaku raina kanku kuwa Allah ya kaimu goben. A waje mama ta sameni raku6e tace sai kizo mutafi aini na dauka kinkai gida, nace mama taya zan barki tareda wa 'yanchan mara mutuncin, jira kawai nake naji 6ur nashiga na watse su, mama tayi dariya waini ameerah ina kika koyo masifa ne? Nace mama gunki mana kema ai bakya daukar raini, tace um lallai kuwa amma dai yanzu nema muke a wurinsu dole mubi a sannu. [9/14, 1:19 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/20, 6:01 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 6⃣2⃣ kamar yanda kausar tacemin zatazo haka kuwa akayi qarfe goma tana gidanmu, dama na shirya shigowa tayi ta gaida mama muka kama hanyar skul a motarta bamu wani sha wahala ba da yake inkanada kudi komai yana zomaka da sauqi, kausar tayimana registration har da course registration duka angama anyi signing departments, mamaki kawai nike abunda zan dauki kusan 3 weeks inayi yau gashi angamamun within 3 hours, qarfe daya muka bar school instead of kausar ta ajiyeni a gida, sai ta shiga yawon dangi dani, ko'ina sai nunani take ga matar yaya khaleed har gidajen qawayenta saida ta kaini, shiyasa kwata-kwata na sha'afa da zuwan da zamuyi gidan kawu shehu da su khaleed, Wuraren qarfe biyar sai ga kiran mama tafaramin masifa gidan ubanwa naje tindazu su khaleed sukazo suna jirana, amma tasa aliyu ya tafi dasu yanzu duk inda nake maza da aikin sauri na wuce chan na sameshu, gabana ne ya dinga faduwa bansan irin tarbar da za'ayi musu a gidan ba, cikin sauri nace kausar ta kaini bado quaters gidan kawuna, ta juya muka nufi chan. A gidan kawu shehu kuwa, hajiya asabe na ganin mota qirar range rover sabuwa fil ta shigo gate, ta zabura ta miqe koda taga kyawawan samari sunfito a mota batama lura da aliyu da suke tare ba, ta sheqa da gudu sai dakin saratu, sara baby ki tashi mana, itako sai wani mitsitstsike ido take, tafara kukan shagwa6a ita a dole an takurata, ruwa haj asabe ta debo ta watsa mata, firgigit ta miqe zaune, hajiya tace ke gantalalliya ki tashi inajin ga saurayinnan naki dan qasar masar da kikace zaizo nan yazo, miqewa saratu tayi da gudu ta leqa waje, hajiya asabe ta jawota ke mahaukaciya badai haka zaki fita ba fuska duk yawun bacci, kije ki tsala ado nikuma zanje nakaisu dakin baqi, tace ok mom tayi ciki da gudu, ita kuma hajiya ta zuri gyale tayi waje tana wanin takon qasaita, zuwa tayi ta samesu sai a lokacin ta lura da aliyu da suke tare, cewa tayi malam lfy dai kazo ka tsare mutane? Aliyu yace dama cewa akayi na kawosu haj tace toh ai ka kawosun sai ka sani inda dare ya maka, Aliyu sumui-sumui ya kama gabansa, sukuwa khaleed da saeed sai kallon juna suke, hajiya tace ku wuce kuka tsaya anan, falon baqi takaisu, aka fara jera musu lemo da snacks kala-kala da soyayyen kaji😋, fita tayi bari na kira muku alhajin kafin baby tazo, sudai basu gane meh take nufi ba sukace toh. [11/20, 6:22 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 6⃣3⃣ Haj. Taje tacewa alhaji ya fito ga saurayin saratu nan yazo dan masar, alhj cikin washe baki ya nufi falon baqi, aka fara gaisawa alhj yace ko zansan ko kai dan gidan waye, khaleed yace sunana khaleed muhammad khalipha, dan gidan alhj M khalipha ne ni da ke sama road, haj da alhj suka kalli juna suka washe haqora, saeed yace alhj munzo neman auren 'yarka ne, muna fatar ba wata matsala? Alhj murya na qyarma yace ai ba wata matsala wlh haj tace haba wache matsala za' a samu kuwa? Aimu indan tamu ne ko gobe ku turo a daura aure, saeed yace to alhamdulillah idan munje gida zamu gaya musu sai suzo ayi magana. Saratu ce ta shigo taci wani jeans da wata ficiciyar riga, tasa belt ta tsuke kunkuru ya matse wuri daya, kamar an daurawa akuya zani😂 tasha wani uban janbaki kamar wata dodanniya, wai ita a dole ga farar mace, aranta tana nasawa ita da ta gayawa saurayinnan adress dinta bata zata zaizo ba dan yaune farkon haduwarsu, wucewa tayi tana wata karairaya ga Saratu ba shape ko'ina a shafe ba sha'awar kallo, amma ita nan ganin take cikakkiyar macece, cewa su khaleed sannunku da zuwa ta zuba masu lemo a cups ta miqa musu, ya baku ta6a komai bane haka tana wane kashe murya kamar tsohuwar karuwa saeed ne yace bakomai mungode, khaleed kuwa ko kallo bata isheshi ba. Daidai nan kausar ta ajiyeni a bakin gate nace ta wuce kawai tareda su khaleed zanwuce ta wuce abinta, koda nashiga sai naga takalmi a falon baqi, direct chan na wuce na shiga da sallamah ta. [9/14, 1:21 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/20, 6:51 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 6⃣4⃣ Saeed da alhaji ne suka kar6a saratu na ganina ta miqe tsaye, ta nunani da yatsa ke meh ya kawoki gidannan ko wani ya gayyatoki ne, kinji labarin saurayina yazo shine kika wanko qafa kikazo toh ki fice dan nan ba sa'arki, turus nayi ina kallon ikon Allah, khaleed da saeed kuwa sai kallon kallon suke, wai meh ke faruwane? Saeed ne ya miqe yace wai meh yake faruwa ne alhaji mufa zancen ameerah mukazo bamu fahimci meh ke faruwa anan ba, alhaji yace meh, amma haj tazo tacemin saurayin saratu ne yazo, khaleed sai a lokacin ya kalli saratun yace wannan abar ce zata zama budurwata? Haj cikin 6acin rai tace, meh kake nufi da wannan abar? Ita ba mace bace da meh wannan matsiyaciyar ta fita? Wlh Allah da nasan zancen wannan matsiyaciyar kukazo da ko ruwan gidannan ba zaku kur6a ba, khaleed zaiyi magana saeed ya riqeshi, amma dukda haka saida ya wurga mata bandir din dubu hamsin yace ga kudin ruwan da mukasha nan, idan sunfi haka ma sai ki fadi a qaro, mamaki ya kashe haj da saratu har alhj ma ya saki baki yana kallo. Alhaji ne yayi ta maza yace kunga ba haka za'ayi ba, misunderstanding ne kawai aka samu dan itama saratu saurayinta zaizo daga masar yau, haj ta dauka kune, amma kuyi haquri dan Allah indai ameerah ce na baku, ku turo magabatanku ko gobe ne a saka rana, kuma zanyi komai da uba zaiyi dan naga na fidda 'yata ameerah kunya, na dai na dasqare wuri daya ina sauraren kawu na zuba qarya. Saeed ne yayi godiya yace zasu tafi, saida yazo kusa dani yace mutafi ameerah sannan na motsa, nace angode kawu su haj da saratu sukabini da harara muka fice. [11/21, 7:55 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 6⃣5⃣ fitarmu keda waya alhaj da hajiya suka fara rige-rigen daukar bandir din kudin da khaleed ya jefowa hajiya, da yake alhj yafi qarfi ya ture asabe gefe ya dauke kudin😂 ture baki tayi uwa ungulu na cin kashi, alhj gaskia wannan zalunci ne, nifa aka jefowa kudin alhj yace ke asabe da a kayiwa wulaqanci aka wurgowa ai baima kamata ki kalli kudin ba, haj asabe tace Allah alhj ni kasan indai akan kudine gwanda mutuncin ya zube dama meh ya rage? Nidai ka yagomin kawai dubu goma ya ciro ya miqa mata, ta qare ture baki alhj gaskia raba daidai zamuyi, cewa yayi idan bakiso wlh ki kawo wannan dinma zanqara, dama wa yake cin kudin ba ku ba? Saratu ce tace dady nima dan yankomin mana, dubu 3 ya jefa mata shegiya da son kudi kamar uwarta, haj tace iyayenta dai ai kaima alhj gameda son kudi, ba kanwar lasa bane. Haj asabe tace waima ni alhj bangane maka ba, taya za'ayi ka wani lalla6asu harda basu haquri bayan wannan cin fuskar da sukayi mana, a gabanka sun wulaqanta mana 'ya, alhj yayi murmushin mugunta, ai haj wannan yaron da kike gani yafi qarfin wulaqanci a wurina, sai miye dan yace bayason kodaddoyar yarki? Ai amirar ma' yata ce kuma ni naga hanyar cin arziki, dan haka tsayawa zanyi na kashe kudi nayiwa ameerah duk abunda uba zeyiwa 'yarsa, ta haka zansamo kan yaron, dandama akwai wasu kwangiloli da na dade ina nema bansamu ba, amma yanzu ta hanyar yaron nan nasan komai zaizo da sauqi, kema ki saki jiki ayi komai dake kija yarinyar a jiki duk abunda ake buqata kiyi mata, ta haka zamu samu kansu, haj da alhj suka sheqe da dariya harda tafawa, dadina dakai shehu wlh akwai kwanya. Saratu ce ta fara kukan shagwa6a, hjy tace ya akayi ne sara baby, ta ture baki kamar uwarta, ni mom Allah na lura bakwa sona, wannan guy fa dani ya dace ba watchen matsiyaciyar ba, alhj yace toh ai kema ki saki jiki ki daidaita da ita ko bayan auren ne kya qwaceshi tinda dai ba uwarku daya ko ubanku daya da ita ba, zaki iya aurenshi, ai na lura er kissar nan da kwarkwasa ta mata duk kin iya, ko dazun ma na lura sai satar kallonki yake😳 dandai kawai yana gaban ameerar ne yake fadar haka, saratu ta washe watsatstsun haqoranta Allah ko dad? Yace gaskia nike fadamiki. Saratu tace nifa dama ina mamakin yanda wannan hadadden guy zai so watchen matsiyaciyar, haj tace ai ba mamaki sungaji da talaucin ne suka masa asiri, saratu kuwa tace ae asiri yazo qarshe kuwa dan yanzu khaleed sai saratu, suka sheqe da dariya. Nidai deejah nace shedanu ina jira inga yanda khaleed zai fatattaka ku. [9/14, 1:24 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/21, 8:16 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 6⃣6⃣ tafiya muke a mota amma ba wanda yayi magana kowa da abunda kemasa yawo a zuciya, saida muka isa gida saeed ke cewa niko ameerah, dagaske wannan kawunki ne? Murmushin takaici nayi ai bakuma ga komai ba, kunci sa'a haj ta dauka gun saratu kukazo, da bansan da wanne ido zan kalleku ba, ba yanda zanyi shine madaurin aurena, tinda ni banida uba yanzun amma da ba abunda zaisa mama tace kuje gunsa, kuyi hakuri da abunda ya faru, saeed yace ae ke zamu bawa haquri dan ke sukafi ciwa zarafi, anyway zamu wuce ameerah, saeed yace buddy bari inbarku kuyi magana ka sameni a mota, tsayuwa mukayi ta kusan 5minute ba wanda yayi magana sai ni da nike satar kallonshi, dago kai yayi muka hada ido nayi sauri na kawar da kaina, sai cewa yayi now what is next? Nace nima bansaniba, yace shikenan i'll tell mom ita tasan meh za'ayi, sauri nayi nace plz karka gayawa mom abunda ya faru, cewa yayi what do u take me as? Ke kika dauki abunda ya faru wani abu da har kike tinanin akwai abun fada a ciki, anyway gud night ya juya suka tafi, niko na shige gida. Sallamah nayi dakin mama, ta kar6a ta lura nayi wani suku-suku, tace meh ya faru ameerah? Na kwashe duk abunda ya faru na gayamata, tsaki tayi ni nama dauka kawun naki, yaqi amincewa ne da na ganki haka, nace mama kinyarda da abunda kawu yace na zaiyi komai? Tace ba abun mamaki bane dan ya lura yaron dan masu hali ne, toh zaiyi tunanin ya samu wani abun so ko dan haka zaiyi, tace mubar zancen su kiramin maman khaleed muyi magana, wayata na dauka nasawa mama number mummy ta kira, inaji tana gaya mata zasu iya turawa ayi magana a saka rana, suka gama plan dinsu sukayi Sallamah, mama tace wai lfy ameerah kike haka ba wani kuzari? Nace mama may b gajiyace kawai bari inje daki, tace kodai zullumin auren ne kika fara? Toh gwanda ko ki saki ranki dan aure anyi angama tinda kikace kina so, ban tankata ba nayi daki dan nima bansan meh ke damuna ba. [11/21, 8:37 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 6⃣7⃣ khaleed ma da ya isa gida gun mom ya wuce, ya gayamata sunje sungaida kawun ameerah, kuma yace ko gobe ma za'a iya turawa, mom tace ai yanzu na gama waya da maman ameerar, kuma namayi magana da dadynka, yace gobe zai tura mutane ayi magana, khaleed yace dady kuma mom? Tace ae na gayamaka dama fushi ne kawai kuma ya sauko yanzun, nd above all deputy governor yace ya fasa bada 'yarsa, yanzu ba komai tsakaninsu sai business, alhandulillah khaleed yace, mom tace khaleed bakasan farincikin da nike tare dashi ba, Allah dai ya nunamin ranar da za' a kai ameerah gidanka son, miqewa yayi yace zanshiga daki mom a gajiye nake, tace shikenan ya tafi, mom kuwa har ta fara plans din abubuwan da za'ayi a biki. Khaleed ya koma daki yayi zugum, shi da yasan ma husnah zata haqura da baiyi kaudin amincewa da ameerah ba, wata zuciyar tace masa da badan ameerar ba kuma ae da yanzu, shirye-shiryen aurenka da husnah akeyi, tsaki yaja aidai yanzu its too late to cry, ni wannan ameerah Bansan wane irin farin jini ne da ita ba, dangi kowa zancenta yake, wai nayi sa'ar mata above all ga mom, ni nasan ranar da game dinmu zaiyi over, zamuyi rigima da mom akan ameerah, amma kuma ae dole mom tayi haquri tinda itama ameerar da wanda takeso. Musqutawa yayi bari na kira salmah na gaya mata, amma kuma miye ma na gayamata tinda aure ba lasting zaiyi ba, bari na kirata dai musha fira i'm missing her alot, kiran wayarta yake amma busy ya gaji yaje ya kunna tv yana kallon news, txt yayi mata, saida ya manta da yayi txt sannan reply yazo, karanta txt din yake yafi a qirga yana aikin murmushi, daga bisani bacci yayi gaba dashi. [9/14, 1:25 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/21, 11:12 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 6⃣8⃣ lokaci nata tafiya, anyi tambaya ansaka rana nan da 3weeks, abu kamar wasa, anbiya sadaki dubu 100, daura aure kawai ya rage, sai lefe da za'a kawo gobe. Ni kuwa abubuwa summin yawa gashi muna shan bikin saudah, inajin haushin rabuwa da qawata, dan a bauchi za'a kaita gidan angonta usman, kuma mama ta hanani zuwa bauchin wai amarya tsautsayi ne da ita, ga karatu lectures muke ba kama hannun yaro, ga zullumin aure duk nayi rama, amma kuma nayi haske da yake har anfara yimin gyaran amare. Abun mamaki duk abunnan da ake tareda haj asabe da saratu akeyi, haj asabe itace, kawo wanchan jiqon bada wannan sassaqen wai duk abani nasha, nikuwa idan na fakaici idonta na zubar, abubuwanda na yarda dasu kawai nike ci, da yake akwai qawar mama da take hadamin tsimi, da wasu abubuwan a gyara kuwa harda maman saudah ba'abarta a baya ba, ni ameerah abubuwanda ake dirkamin har banason shiga gida idan na fita, na safe daban na yamma daban wai duk gyara ne, kawu kuwa duk abunda ake buqata bayarwa yake. Kamar yanda akace za'a kawo lefe hakan kuwa akayi, su mama sunyi nasu shiri daidai gwargwado na tarbon lefe, haka aka riqa jibge kaya kamar za'a buda boutique a gidanmu, mutanen sai tururuwa suke kallon kayan ameerah, ko sata akayi baza'a gane ba akan yawan kayan, dan haj da kausar dakansu sukayi visa, qasashe 3 sukaje hado kayan lefen. Hajiya da saratu ranar kasa 6oye baqincikinsu sukayi, suka rinqa masifa da mutane masu zuwa ganin kayan lefe, haj asabe tace akai kayan kawai a gidanta idan ba haka ba mutane zasu sace kayan mama bata sani ba, wata yayar mama da take nan, tasan halin haj asabe tas tache ba inda za'a tafi da kayan, tananan ita zata kula da kayan, cin mutunci sukayi tatas da ita da gorace-gorace, wai ai duk mijinta yake komai, haka dai suka bar gidan daga qarshe sukaje gida suna baqinciki, itadai saratu duk gold dinda aka zuba yafi tada mata hankali, cewa take da yanzu ita aka kawowa, amma duk da haka sai tasan yanda akayi suka zama nata. [11/21, 11:44 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 6⃣9⃣ Sannu sannu bata hana zuwa akace, yau saura kwana 3 daurin auren khaleed da ameerah, 6angarori biyu kuwa ba abunda ake sai shirye-shirye, kawu shehu ya taqarqare yana kashe kudi, kayan dakin da aka siyowa ameerah dukda da haj asabe da kanta saida tayi mamaki, tace asiri mukayiwa mijinta yake kashe mana kudi haka, shikuwa yasan abunda ya shirya, mutane ya dauko dan kawai gyaran gidan khaleed da ameerah, anjera kaya anyi komai gida sai sheqi yake kamar a dubai, kowa yaje santin gidan yake, furnitures dinda aka saka a gidan sun dace da yanayin gidan, komai yayi tsaf-tsaf, nidai DEEJAH da na leqa gidan daqyar aka fito dani, nace zanyiwa ameerah wanke-wanke, amma haka haj asabe da saratu suka taso qeyata waje, wai kar na 6ata furnitures din, tun basu mori komai ba😢, mama harda kuka tayi tanayiwa alhj godiya dan ya fitar da ita kunya, duk da cewa a qasan zuciyarta tana shakkan abunda kawu shehu keyi dan tasan ruwa basa tsami banza. Khaleed ne zaune tareda saeed, saeed yace aboki ka sanarwa da salmah halin da ake ciki kuwa? Yace inafa frnd ae ina tsoron gayamata ne takasa fahimtata, kuma naga dai auren ma na dan lokaci ne, saeed ya gyada kai amma ni abokina a ganina gwanda ka gayamata da taji a wani wurin, dan idan wani ya gayamata bazata yarda dakai ba, khaleed yace kuma haka ne fa bari na kirata yanzu, call yasa yau cikin sa'a ringing 2 tayi akayi picking, hello my baby, khaleed yace today is my lucky day, kindaga call dina without delay, tace ai kasan uzuri yasa bana picking din call dinka, bt u mean d whole world 2me, nima ina kewanka, yace can't wait to see u swthrt, khaleed yace akwai abunda zangayamiki gamma inaso ki tsaya ki fahimceni, tace don't worry sweary ai ni takace u can tel me anything, khaleed ya kwashe halin da ake ciki ya gayawa salmah, as tsaye ta miqe cikin masifa, ni zaka yaudara khaleed? Yace no salmah listen to me, cewa tayi kasan alqawarin da ka daukarmin ba wata mace da zaka zauna da ita saini huh? Yanzu kawai ka cemin aurenka saura kwana 3 kuma wai fake ne, who are u decieving? Kar ka sake ka qara nemana, i hate you ta kashe wayarta, khaleed a rude yake kiranta amma salmah tama kashe wayarta, ya tura txt har ya gaji shiru, cikin mintuna da basu wuce ashirin ba khaleed ya fita hayyacinsa, saeed kuwa sai kallon ikon Allah yake, baita6a tinanin abokinsa zaiso mace haka ba, haquri yake bashi ys bari ta sauko tayi fushine idan har tana sonshi zata fahimceshi, khaleed kuwa kuka kamar mace, waishi ya fasa auren Allah, haushi ne ya ishi saeed ya tashi ya rafi ya barshi. [9/14, 1:44 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/22, 6:53 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 7⃣0⃣ gefen mom kuwa events kusan kala 5 suka shirya kuma ko wanne da ankonsa, kuma ko wanne na kece raini, designers aka nemo dan kawai su tsara kayan da ango da amarya zasu saka a kowane event, sun kashe nera kamar su ke qerata amma mom gani take kamar batayi komai ba. Ameerah kuwa tare suke da kausar kullum da yake sunzama best frnds, kai bakace matar yayan kausar bace, yauma tare suke sunje skul sun dauko khadijah nasir barau qawar ameerah, domin su qarasa rabon invitation cards duk da ameerah tace bazatayi ba, amma kausar da khadijah saunce dole ne, dan baza'ayi biki ba qawayen amarya ba, bayan sundawo ne kausar ta tsaya da mota bakin titi, tafita ta tsallaka ta kar6o kayan dinkinta a wani shago, qishin ruwa ta dami ameerah tace khady bari na tsallaka shagon chan na kar6o ruwa wlh qishi ke damuna, khadijah tace bari na kar6o miki kar amaryarmu tasha wahala, ameerah tace bakomai jira kawai yanzu zandawo dama inason in miqa qafa ta fita ta tsallaka titin. Bayan ameerah ta kar6o ruwan tasha ta juyo da roba daya zata kauwa khadijah da ke mota, hakan yayi daidai da fitowar kausar shago, mota taga tayo kan ameerah da gudu, kiranta ta dingayi amma ina, kafin kausar ta iso, motar ta riga ta qaraso, da qarfi ta kwashe ameerah sai da tayi sama-sama ta fado, sai ga ameerah kwance a jini bata ko motsi. Wata qara kausar tayi wadda duk mutanen da ke wurin hankalinsu ya dawo gunta, iya qarfinta take gudu, ta tunkare motar da ta kade ammeerah, husnah ta hango a mota tana murmishin cin nasara, a ranta tana fadan ai dama ba wanda ya isa ya rabani da abunda nakeso duniya, kuma ya zauna lfy, yanda kika rabani da khaleed nima na rabaki da duniya. Kausar taga tayo kanta gadan-gadan taja mota da gudu tabar gun, kankace kwabo wuri ya cika da jama'a, da qyar kausar ta kutsa girgiza ameerah take ta tashi amma ina, bata ko motsi tayi facha-facha cikin jini, jama'a ne sukecewa akaita asibiti kausar tace su taimaka mata plz ga mota chan, a saka ameerah, haka akayi kuwa suka nufi mota inda khadijah ta dasqare wuri daya tama kasa motsi da taga abunda ya faru, saida aka bude qofa aka saka ameerah sannan ta motsa, kuka take gwanin tausayi tana jijjiga ameerah, its my fault duk laifina ne da naje na soyomiki ruwan, kausar kuwa kasa driving tayi coz hannunta qyarma yake, wani da ke taron ya kar6i key yaja motar, sai asibitin USMAN DANFODIO TEACHING HOSPITAL dake sokoto, emergency aka wuce da ita direct, da yake asibitin sunsan kausar da kuma waye ubanta shiyasa ba'a sha wahala ba aka kar6eta. [11/22, 8:58 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 7⃣1⃣ Kausar ta kira mom cikin tsananin tashin hankali, mom kizo asibiti husnah ta kashe ameerah, wlh mom bata motsi, mom da tashiga rudani cikin 'yan mintuna takasa ta6uka komai, sai yawo take a tsakiyar parlour, alhj ne ya sauko, Aisha lfy kike kuwa, mom sai fadin take shikenan ta kashemin ita, alhj ya rude ya kasa fahimtarta, girgizata yayi wai aisha meh yake damunki, kuka tafara mai tsuma zuciya, alhj husnah ta kade ameerah da mota suna asibiti, kuma wlh tace ameerah bata motsi, alhj yace dauko mayafinki mutafi asibitin, ki nitsu ba abunda zai sameta inshaAllah, kasa daukowan tayi alhj da kansa ya sakawa mom hijabinta yaja hannunta kamar qaramar yarinya suka fita, daidai nan khaleed ya fito waje, alhj yace son kazo muje asibiti cikin rashin fahimta khaleed yace meh zamuyi a asibiti? Dad yace muje kaga ko mene, suka shiga mota, kausar dad ya kira, ya tambiyeta suna ina? Cikin kuka tamasa bayani, khaleed dama tin fadansu da salmah ya riga ya fita hayyacinsa duk ya birkice, tsananin tashin hankalin da mom ke ciki yasa bata lura da yanayinsa ba. Ameerah kuwa likitoci biyar suka duqufa kanta, suna qoqarin ceto ranta, isowar su khaleed keda wuya, doctors na fitowa, suka nufi gunsu, wani doctor ke musu bayani, sunyi iya qoqarin su, sun tsayarda bleeding din da ameerah keyi, amma kuma tana buqatar qarin jini na gaggawa if not zata iya rasa ranta, haj ta rusa kuka da su kausar duka, khaleed kuwa tsaye yake kamar hoto dan baigama fahimtar meh ke faruwa ba, gun kausar ya nufa kausar rungumeshi tayi, yaya husnah ta kashemana ameeranmu, khaleed hannu ya dora akai, inalillahi wa inna ilaihi raji'un yaketa fada, mom its all my fault da ban amince zan auri ameerah ba da haka bata faru ba, m so sorry ameerah, mom taje ta rungumeshi son karka damu ba abunda zai faru da ita, wata nurse ce ta fito cikin masifa take magana angayamuku patient dinku tana buqatar jini cikin gaggawa, kun tsaya kuna kuka, zaku iya rasata in d next 30 minute idan kukayi wasa, alhj ne yace ku kira famlynta cikin sauri, haj tasa kiran mama ta daga amma mom takasa magana, alhj ne ya kar6a yace kuzo asibiti uduth yanzu cikin gaggawa, ameerah ta hadu da accident. [9/14, 1:46 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/22, 9:04 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 7⃣2⃣ mama tayi lu qasa jiri ya kwasheta, mutanen da suke daki tareda ita ne sukayi kanta lfy maryama? Kuka ta fara ku kiramin aliyu yazo mutafi asibiti, ameerah tayi hadari, take dakin kowa jikinsa yayi la'asar, suhaila ce tayi waje da gudu, ta kira aliyu tanata faman kuka, yaya aliyu ameerah tayi accident zumbur suka miqe da mustafa da yake taredashi, dan tinda aka saka bikin ameerah yaya mustf ya shiga tashin hankali, aliyu ne ke kwantar masa da hankali har ya fara dangana, mota mustf ya jawo suka shiga, mama ta fito ana riqe da ita kan jirin da ke dibarta, suka shiga mota sai asibiti. A asibiti kuwa khaleed ne yabi nurse din yace, jininsa blood group type O+ ne zai iya bawa kowa jini, a dibi nasa a sakamata, nurse din tajashi lab aje a gwada lafiyarsa, bayan anyi test anga lfyrsa qalau, ta wuce dashi emergency room gado aka bashi daidai na ameerah, direct connection akayi da ameerah ba'a tsaya dibar jinin ba, daga jikin khaleed direct jikin ameerah yake shiga. Su aliyu ne suka iso wurin da ka gansu kasan suna cikin tashin hankali, da isowarsu direct alhj lab yace su nufa ayi test, nurse din ce tafito tace ae already anfara sakawa patient din jini, saidai kuma zasu iya zuwa suyi test din, incase idan jinin da aka samu bai isa ba, alhj yace wai ina aka samu jinine? kausar tace yaya khaleed dad kasan O+ yakeda zai iya ba kowa jini, mom taji dadi har a ranta, sai mama take ba haquri da take darzar kuka, Aliyu da mustf kuwa suntafi ayi test din jininsu a lab. Dad ne ya sulale yaje ya samu nurse din, wai ta cire jinin yaronsa kar ta kashe masa yaro, nurse tace ae sunsan adadin jinin da zasu diba yanda bazai cutarda khaleed din ba, dad yace atafau shi sai ancire ko yayi qararsu, tinda ga en uwan patient din sunzo sa bata jinin, nurse tace toh ya bari taje ta duba results din blood test din su aliyu idan yayi match tazo ta cire na khaleed din, alhj ya dake yanzu zata je ta cire, shi sam bazai yarda ba, kafin taje ta dawo jinin dansa zai qare, dole nurse din taje ta cire tranfusion din daga jikin khaleed, khaleed yana mamaki har jinin ya isa ne bayan sunce ta rasa jini da yawa? Nurse tace masa anason patient din ta dan huta kadan kan acigaba da saka jinin, khaleed yace shikenan ya fita waje. Blood test dinda akayi jinin Aliyu daya suke da na ameerah duk A+ ne, aka fara diban nashi, na yaya musty ma O+ ne kamar na khaleed shima za'a dibi nashi gora daya a ajiye incase. Ameerah ce ta fara fisge-fisge bayan ancire mata qarin jinin, doctors sukayo kanta masifa suka dingayi meh ake jira ba'a fara saka mata jinin ba? Khaleed ya gayamusu abunda nurse ta gaya masa, take wani doctor ya kwasheta da mari tana wasa da rayuwar patient, dole su dauki mataki kanta, ita kuwa tasan za'a iya korarta, take ta fadamusu abunda ya faru itada dad, yaya mustf ne ya daka masu tsawa enof, ameerah is fighting 4 her life kuntsays kuna rigima, yace a fara zuba nashi kawai, ya basu result din test dinda akayi, doctr ya duba yaga lfyrsa qalau take yace mustf ya kwanta ya jona jinin, daga jikin yaya musty zuwa na ameerah. [11/22, 6:10 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 7⃣3⃣ khaleed da hajiya suka yiwa alhj kallon tuhuma, yace son na damu dakaine banason wani abun ya sameka, mom tace amma alhj banta6a sanin bakada tausayi ba sai a yau, da kausar ce a kwance nan zaka hana khaleed ya bata jini ne? Ko zaka hana mijinta ya bata jini? Mama tace haj kidaina 6ata ranki, ameerah ta riga tasamu jini, kuma ko na mustf bai isa ba ga na aliyu nan, ba wani abu wlh tinda ba'a daura auren ba ma haryanzu alhakin kula da ameerah yana kanmu, kuma haj bazanta6a dana sanin baki ameerah ba, dan nasan son da kike mata ko ni iya abunda zan nunamata kenan, mom ta share qwalla amma mune sanadin faruwar hakan gun ameerah, dan da alhj bai maqalawa khaleed wannan jarababbiyar yarinyar ba, da duk hakan bata faru ba, mama tace haj qaddara ce kawai ayi haquri kawai. Kausar ce ta matso amma mom bazamu qyale husnah ba dole muyi maganinta, mom tace sosai kuwa alhj ko bakayi wani abun ba ni wlh bazan qyaleta ba, doctor ne yazo yace patient dinku ta samu isashshen jini, kuma she is stable now, saidai kuma sanadiyar buguwar da kanta yayi tayi dogon suma, she is in comma right now, amma muna tunanin is temporary ko da nan da 3 days ne zata farfado, yanzu zamuyi shifting dinta zuwa ICU, u can all see her there, hamdala kowa yayi tareda ajiyar zuciya, da fatar Allah ya ba ameerah lfy. Saleem ne ya kira kausar yana airport azo a tafi dashi, shine kausar ta gayawa mom, mum tace shi saleem bai tashi dawowa ba sai yanzu, tun kwana baya muke especting dawowarsa, sai yanzu ana crises zai dawo? Alhj yace ai kuma yariga ya dawo, ina kausar tazo suje da khaleed su daukoshi airport din, amma aka nemi khaleed aka rasa. [9/14, 1:50 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/22, 8:41 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 7⃣4⃣ khaleed kuwa yana fita daga asibitin police station ya wuce, dama comissioner of police abokin dad dinsa ne, yau sai ya koyawa husnah hankali, bazata qara gigin qoqarin kashe ko waye ba a duniya, koma waye ubanta a qasarnan sai ya daureta. Kiran saeed ya shigo wayarsa, buddy where are u? Yace ina asibiti kai kana ina? Yace ina police station yanzu gidan deputy governor zai wuce, he'll teach dat stupid girl a lesson, mota saeed ya shiga da sauri, mom, dad da kausar suka bishi, ya kama hanyar gidan deputy governor yasan halin abokinsa idan yayi fushi ba sauqi, khaleed kuwa da yayiwa comissioner bayani motar en sanda 3 aka hadashi dasu direct sai gidan deputy governor. Deputy na zaune da matarsa suna shaqatawa yafara ganin police na diro masa gida kamar daga sama, cikin tashin hankali ya tashi, ya daka musu tsawa wannan wanne irin rashin hankali ne, zasu fado masa gida kamar police head quater, khaleed ya shigo yace alhj kafito da husnah batareda 6ata lokaci ba dan she must pay 4 her crime, deputy cikin rashin fahimta yake tambayar what crime, meh 'yata tayi? Inspector yace ana zarginta da qoqarin kisa, ta kade matar da khaleed zai aura da mota dazu, kuma ta gudu wanda ya tabbatar da cewa tayishi ne da gan-gan, haj ra miqe dis is rubbish, husnah bata qasar nan tin jiya taje america ta ya zata kashe mutum yau? Inspector ya bada umarni afara searching gidan lungu da saqo kar abar ko ina. Bayan sun duba ko'ina sun tabbatar bata gidan, khaleed ne yaje ya chakumi wuyan deputy governor ya shaqeshi, wlh duk inda husnah take ka fito da ita kafin kaima na qarasaka, daidai nan su saeed suka shigo, tsawa dad ya sakawa khaleed akan ya saki deputy governor, amma ina daqyar saeed da wasu police suka qwaceshi, idon nan sunyi turu-turu sunyi ja, cewa yake alhj khalipha ka fitarmin da mahaukacin yaronka a gida, nagodewa Allah da 'yata bata auri mahaukaci ba. Daidai nan wayar matar deputy governor tayi ringing, cewa tayi ga ma husnah din nan ta kira dan ta lura number america ce, Inspector yace tasa wayar a hands free, ta daga muryar husnah ce kuwa, haj tace husnah ki fadamin gaskia, ke kikayi qoqarin kashe matar da khaleed zai aura? Husnah tace common mom ai kinsan ni idan bansamu abu ba ba wanda zai samu, kawai na nunamuku na haqura ne dan kawai ku dena damuna, but d truth is haryanzu ina son khaleed, dad yace amma husnah jiya kikabar qasar nan, taya akayi hakan ta faru? Dariya tayi dad kai kamar ba dan 9ja ba? Ae visa ta yau ne da yamma i just landed, kawai na cemuku jiya ne karku 6atamin plan, mom just tel me wannan ameerah din ta mutu nafara celebration ta fashe da dariya, mom tace amma Allah ya tsinemiki albarka husnah, deputy governor yace daina tsinema 'yata, ga tsinannen yaron da zaki tsinewa nan duk laifinsa ne, now i lost my daughter, haj zubewa tayi qasa tans kuka gwanin tausayi, Allah ya isa tsakanina dakai alhj duk kai ka lalatamin ' ya ka nunamata, duk abunda takeso zata samu shiyasa batasan tayi tawakkali ba, gashi ka juyen mahaifa bare na qara haihuwa, ni wlh alhj ka cuceni, mom ce ta tasheta tafara bata haquri. Deputy governor tsawa ya saka a fice masa daga gida, Inspector yace your excellency inaso kasa a ranka ko yaushe 'yarka ta dawo qasar nan sai mun hukuntata sannan suka fice. A mota kuwa kowa shiru yana jimami, dad ke nasawa a zuciyarsa yaso ya tafka babban kuskure a rayuwarsa amma ya gode Allah da ya ganar dashi da wuri, kudi ba su ke sa yaro ya samu kyakkyawar tarbiya ba, dan ga husnah duk gatanta da kudin mahaufinta takasa samun tarbiyya, shi ya godewa Allah nashi yaran Allah ya shurya su amma dan sunyi dacen uwa ta gari ne, shima daga yau bazai qara shiga rayuwar yaransa fa zaimusu fatan samun abokan rayuwa na gari, ga alama kuwa khaleed yayi dace dan yarinyar ya lura tanada kamun kai da nutsuwa, tsanar da yayiwa talaka yasa yaqi yarda da hakan, amma not anymore da haka suka isa gida kowa yayi side dinsa. [11/23, 12:02 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 7⃣5⃣ da safe dad ya samu mom tana shirye-shiryen zuwa asibiti, yace aisha magana nazo muyi, haj ta zauna, dad yace a ganina dan yarinyar na batada lfy bai kamata a janye daurin auren nan ba, haj mamaki tayi dan batayi tsammanin wannan maganar tafito daga bakinshi ba, amma tayi matuqar farin ciki, hakane alhj a daura auren kawai idan yaso daga baya ayi bikin, tace bari na kira son namasa bayani, dada yace niko na lura yaron nan kamar ba natsuwa a tare da shi, ki kira wannan abokin nasa shi ya shirya komai, mutanen da sukaji labarin accident din ya gayamusu still akwai zancen daura aure, wanda baijiba ma shikenan. Hakan akayi kuwa mom takira saeed ta masa bayani, sannan tace shikenan idan sunje asibiti tayiwa maman ameera bayani ta sanar a gefenta. Saeed da ya tashi dakin khaleed ya nufa, ya sameshi yayi wani zugum duk ya wani kode yayi rama, saeed ya ta6ashi aboki wai meh ke faruwa ne? Khaleed yace aboki kafi kowa sanin abunda ke faruwa salmah taqi saurare na, yanzu kuma ga abunda ya faru ga ameerah, kuma duk ni naja mata, amma is not too late da Allah ya tashi kafadunta zan warware wannan auren da muka shirya, saeed yace lallai kuwa ni zantafi, zanje asibiti na duba ameerah, khaleed yace ka jirani mutafi a tare yafito suka wuche. A mota kuwa shiru sukayi kowa da bikin zuciyarsa, saeed na nasawa a ransa ba sai ya gayawa khaleed zancen daurin aure gobe ba, yaji yana qudurin janye auren, idan ya gayawa su mom gaskia, abun bazaiyi dadi ba, gwanda ya barshi kawai, beside ma salmar da yakewa fighting ya lura, ba wani damuwa tayi dashi ba, tun farko da tana sonshi bazatace yayi keeping r. Ship dinsu secret ba, duk da yake iyayenta da na khaleed aminaine, akan wani uzurin karatu, gwanda khaleed ya auri ameerah kawai, dan yana zargin ameerah son khaleed take, da bazata iya yimasa haka ba, duk da yake bai tabbatar da zarginsa ba, amma yana fatar haka ta kasance. Saeed ya katse shirun yace khaleed meyasa ba'a nemeni ba jiya da aka kawo ameerah asibiti? Duk da kasan ina asibitin, khaleed yace aboki nikaina bansani ba mom da dad kawai suka jani asibiti, daz where i found out everything, beside ma kaida kake likitan mata meh zaka iyayi? Saeed yayi dariya wa ya gayamaka gynocologists basu iya komai ba sai aikin mata? Dariya sukayi da haka suka isa asibitin. [9/14, 1:54 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/23, 3:24 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 7⃣6⃣ koda suka shiga gun da ameerah take, mamace da aliyu da su suhaila kowa yayi zugum ba mai magana, suka duqa suka gaida mama ta kar6a da dan sakin fuska, sukace ya mai jikin? Mama tace to alhamdulillah za'ace amma bawani chanji har yanzu, saeed yace doctor ya dubata? Mama tace eh yace qalau take kuma anasa ran ta farka a kowanne time. Mama tace khaleed dafatar ba wannan abun kasa ranka ba naga duk yanda ka yamutse jiya kawai? Shidai ya sadda kai a qasa a ransa kuwa cewa yake dama damuwar da ke damuna akan hatsarin ameerah ne kawai, saeed kuwa sai kallonsa yake, sai yanzu ya qara ganin yanda abokin nasa, yayi rama yayi duhu, girgiza kai kawai yayi, a ransa yace dole na fito dakai daga wannan jarababbiyar soyayya, bari ma na tashi na qarasa rabon katin aure, mama tace saeed ka riqa bawa abokinka baki kar damuwa tamasa illah, daidai nan su mom suka shigo da kayan breakfast, mom tace son ka kwantar da hankalinka ba abunda zai samu ameerah, kacigaba da addu'a kawai ka saki ranka, kada kai kawai yayi suka miqe, saeed yace mom mu zamu tafi, sai munshigo anjima, bandir din kudi khaleed ya ajiye koda ana buqatar wani abun suka fice. Mom tace salim ga ameerah how i wish kadawo kunsan juna kan haka ta faru, gashi kace jibi zaka koma, murmushi yayi mom she is preety, dukda hakan take i know zata kula da yaya khaleed sosai, kuma mom kinsan daurin auren broda kawai yasa na dawo if not sai next session, salim yace ina yaron da kikace zamu tafi tare? Mom tace kaga ni nama sha'afa wannan tashin hankali banma gayawa aliyun ya shirya, angama masa komai ba, tafiya kawai ta rage, mama ta ta6o aliyu da ya shiga wani yanayi, firgigit ya motsa, tace aliyu ga salim ku gaisa shine zaku tafi egypt din tare, hannu ya bashi suka gaisa, salim yace i'm happy nima zansamu danuwa a chan, sai kafara shiri dan jibi zamu wuce bayan andaura aure gobe. Aliyu ya kalli mama har suna hada baki daurin aure kuma, mom tace eh maman ameerah, ae dan yarinya ta samu hatsari bazaisa ace za'a fasa daura aure ba, za'a daura auren a gobe idan yaso biki a daga har ta samu sauki, mama tace haj kina ganin haka zaiyi kuwa? Mom tace ba wata matsala wlh, ko da abunda kike tunani ne? Mama tace ba komai amma dole a sanarwa da kawunta mom tace bakomai alhj zaimasa bayani da kansa, mama tace toh Allah yasa hakan shine alkhairi akace amin. Salim ne ya miqe toh ni zanwuce mom sai na dawo, hannu ya bawa aliyu danuwa kagama shiri fa kan jibin tayi, Aliyu ne yace nifa ba inda zani, salim dawowa yayi ya zauna, meyasa dan uwa? Komai fa angama karkamin haka mana, aliyu yace taya za'ayi natafi nabar er uwata a haka? Yasa kuka, mama tace cikin fada, da yake zaman da zakiyi shi zai hanata mutuwa idan Allah ya tashi kar6ar ranta, ko kuma shi zaisa ta warke, mom tace kima daina fadan haka ba abunda zai samu 'yata, kubarshi kawai idan bai amince ba, yaje next session, mama tace zuwa kam yagama zuwa saidai idan bana raye, baza' ayi kashe kudin banza ba, kuma itama er uwar tashi bazataso yafasa karatu saboda ita ba, dan haka katashi ka fice kafara shiri, Aliyu ya fita a fusace salim ya bishi ya lallasheshi hakan yayi daidai da shigowar kawu da iyalansa. [11/23, 4:33 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 7⃣7⃣ Bayan su kawu sun zauna ne, angama gaisawa budar bakin saratu mom nikuma anya wannan ba gawa muke tareda ita ba? hjy asabe tace nima fa haka nagani, mutum kwance haka baya ko numfashi ace yana raye, da ma suncire mata wanna qarafunan a binneta kawai. Kausar da ka zaune raku6e gefe tinda suka zo batace kanzil ba abun duniya ya isheta, ta miqe a fusace ke ki iya bakinki fa, ni er uwata da ranta ba abunda ya sameta, kunfi likitocin iya aikine da basusan ko tanada rai ko ta mutu ba? Mom tace kausar ya isa, amma hjy bai kamata ku furta haka ba, hjy asabe tace Allah ya baku haquri. Mom tace alhj gwanda da kukazo dan koma baka zoba alhj zai sameka a gida, zancen daurin aure ne nikeson gayamaka, hjy asabe tayi saurin katseta ai munsan dole kuce kun fasa, mutum a haka munsan ko bata mutu ba dole ta nakasa, toh meh za'ayi da nakasashshe dama? Mom cikin 6acin rai tace wai ke wace irin macece ne? Bakinki bazai fadi alkhairi ba ne kam? Toh ni ameerah ko ta nakasa ba qafa ba hannu bazaisa mu gujeta ba, bare kuma doctor ya tabbatar mana ba wani nakasa a jikinta, akai ne ta bugu shiyasa har yanzu bata farko ba, saratu tace hauka zatayi kenan? Kawu ya daka mata tsawa, saratu kifita kibar dakinnan kan ranki ya 6aci, tafita tana kukan shagwa6a, mom tace alhj zancen daurin aure gobe yana nan bai chanjaba, alhj yayi jim sannan yace toh aini har na sanarwa mutanena anfasa, mom tace lokaci bai qure ba, kasake gayamusu daurin aure yananan, hjy asabe taja tsaki idan kuma yarinyar ta mutu bayan andaura auren fa? Mom tace wannan ba matsalarki bace, ko mutuwa ameerah tayi a gobe bayan andaura aure, zamuyi farinciki ta rasu tareda auren dana khaleed, barema da izinin Allah ba abunda zai samu ameerah, haj asabe baqinciki taga zai kasheta ta fice daga dakin. Bayan tafita ne alhj yace hjy kuyi haquri, haka nike fama dasu, zantafi yanzu na sanarwa da mutane Allah dai ya tashi kafadunki ameerah ya matse qwallan munafunci ya fice. [9/14, 1:58 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/23, 4:53 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 7⃣8⃣ Bayan fitar kawu mom tace wai wannan wace irin macece, da ita da 'yarta? Mama tayi murmushin takaici, kinsan haka Allah yake halittr bayinsa, wasu mutane basason suga alkhairi gun wasu sai kansu, mom tace Allah ya sauwaqa, sallamar da akayi ta katsesu matar deputy governor ce ta shigo, sai shigowa ake da carton carton na lemuka da ruwa, tashigo ta tambiye mai jiki, akace mata da sauqi, mama tace saidai hjy kiyi haquri ban wayeki ba, hjy ta matse qwalla ta girgiza kai, ina baqincikin da ba alkhairi ne ya hadamu ba, nice uwa marar sa'a da 'yarta tayi yunqurin kashe' yarki sai ta fashe da kuka, dan Allah hjy kuyi haquri ta sauka ta riqe qafafun mama, mama ta share qwalla bakomai qaddara ce bata wuce ranarta, saidai muce Allah ya kiyaye gaba, check ta ciro ta miqawa mama na 2 million, duk da nasan wannan bazai siyowa 'yarki lfy ba, kiyi hakuri ki kar6a dan Allah ba danni ba, mama tace kibarshi wlh bakomai, bama buqatar komai, hjy tace idan baki kar6a ba zandauka baki yafemin bane kuma wannan laifi bazai ta6a barina na zauna lfy ba, idan na tuna abunda' yata tayi kuma ni banyi komai akai ba, mama ta kar6a tayi godiya sannan suka fice. Kawu kowa da suka fita masifa ya dinga yiwa haj asabe da saratu waisu bakinsu bazai iya shiru ba? Sai sun bata masa plan susa yakasa samun komai, hjy asabe kuka tasa wai ita wlh tasan asiri aka masa dan yanzu baya qaunarta da ita har 'yarta, shidai girgiza kai kawai yayi, a ransa yana danasanin auren mace mai qwaqwalwar kifi irinta, gashi ta haifa masa ' ya irinta, kansu baya ja, da haka suka isa gida. Khaleed kuwa ana wurin rabon invitation card batareda yasan nashi ake rabawa ba, dan saeed yace masa na abokin aikinsu ne, bayajin dadi shiyasa yace ya taimaka masa, duk inda sukaje saeed shikadai yake zuwa, yabar khaleed a mota, wannan kenan. [11/23, 5:39 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 7⃣9⃣ Yau takama ranar juma'a ranar da za'a daura auren khaleed da ameerah, shiga da fice a gida ana shirye-shiryen daura aure, amma khaleed baimada lbr shi ya ajiye tinda ameerah na asibiti ba wani zancen daura aure, Allah dai ya bata lfy ya warware mata wannan fake auren, shima ko zai samo natsuwarsa. Salim ne yafito yaci uban ado kamar wani dan sarki ya sauko parlour, kausar ta fara shewa wannan wankan yayi bro dole kabani poster tazo suka dauki hotona, sai ga mom da dad sun sauko suma sunci uban ado, kausar ta sheqa ta rungumosu, akayita daukar pictures, salim yace dad uban gayyarfa bai fito ba kar ya 6atamana lokaci, bari naje na fito dashi mom tace kaje ka fito dashi, ya fito ya nufi side din khaleed, qwanqwasa qofa yake, amma khaleed na kwance a daki har wata fever yakeji, masifa yafara yiwa salim ya daina qwanqwasa masa qofa, haka yayi daidai da zuwan saeed wurin, da kuma fitowar su dad, saeed yace salim kaje ku tafi da su dad kawai zanzo da khaleed din, suka shiga motocinsu suka wuce. Qofa ya fara duka buddy kazo ka bude qofar mana, khaleed haka ya taso ya bude qofar ya koma ya kwanta, saeed yaje ya ta6ashi yaji zafi gau a jikinsa, tashi yayi ya koma mota, ya bude jakaraa ta aiki allura ya dauko da wasu tabs, khaleed na kwance ba zato ba tsammani, Allura kawai yaji an soka masa, saida ya riqe gado da qarfi, 😂 yace aboki wlh ka cika dan iska, da kajimin ciwo fa? Saeed yayi dariya ai nasan kai jarumi ne, tadhi kasha tabs dinnan ka tashi mutafi, khaleed ya kar6a yasha yace, bt ni ba inda zani dan bakada tausayi bakaga yanayin da nike ciki ba ne? Saeed yace idan ma nabarka a haka ba sauqi zakaji ba, nasan ba aikin da zakayi sai tunanin salmah, dan haka ba wani dogon excuse ka tashi kawai ka watsa ruwa, mutafi ka rakani daurin aure, khaleed yace auren wa kuma, saeed yace mai katin da muka raba jiya, ae yaune daurin auren, buddy katafi kawai bazan iya zuwa ba, miqeshi saeed yayi ya tura toilet, na baka 15 minute kafito, ba barin da zammaka naje nadawo nasamu kayi mushe a daki. Khaleed yace ok u win, ya rufe toilet din ya fara wanka, kafin ya fito saeed ya fito masa da kayansa da ya dinka masa dan kawai daurin aurensa, yana fitowa ya goge jikinsa kawai saeed ya miqamasa kayan yafara sakawa, saida yasa saeed ya miqo masa babban riga da tasha aikin kamar sarkin musulmi, khaleed yace ar u mad? Ni ango ne da zansa wannan kayan? Saeed yace masa ai theme din daurin auren ne haka, nima bakaga ita nasaka ba, khaleed yace but naka is more simpler dan mine, ni ae za'a dauka nine angon, saeed yace ba wani duk salon kar kajene, ai ango ma kalar kayansa daban mune zamusa farare, kuma ma ai kowa yasan kai babban mutum ne, khaleed ya ta6e baki, ya zura rigar saeed ya dora masa hula, sanna ya fidda kwalbar turare ya fara yimasa feshi, take ko ina ya biye da qamshi, khaleed saida ya kar6e kwalbar turaren yayi wurgi da ita, wannan ae haukace wlh Allah zance nafasa, saeed yace Allah ya baka haquri nafiso ne, da munfasa taro asan munshigo, khaleed ya hararesa to takara zamuje e yaja tsaki ya fito, saeed yace Allah aboki banta6a sanin kai maikyau bane sai yau, naji dai anata fada amma sai yau na yarda, fararen takalmi ya ajemasa ya saka, khaleed sai qyalli yake komai fari, kamar wani sarki mota ya shiga ya kame, kaxo mutafi b4 i change my mind, saeed yace sorry your excellency a farar sabuwar motar chan ta dady zamu, khaleed yace frnd motar dad fa kace, makulli ya nunamasa don't u worry, dady ya bamu aro, tsaki yayi ya fito motar saeed suka nufi motar dady suka shiga, sai qyalli suke kamar taurari dan shima saeed ba bayaba wurin kyau, saeed yaja mota suka nufi wurin daurin aure. [9/14, 1:59 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/24, 8:02 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 8⃣0⃣ Wurin daurin auren kai tsaye saeed ya nufa, da yake wani qaton wuri ne da yake bayan gidan kawu sheshu, ya kama dan kawai daurin auren dan yanada yaqinin daurin auren zai tara manyan mutane dan yasan dadyn khaleed babban mutum ne a jahar, wurin saeed ya nufa kaitsaye khaleed kuwa baisan wurin ba dan haka, baiyi zargin komai aransa ba, koda suka isa wurin dubunnan mutane sun taru, ciki kuwa harda gwamna jahar, da tawagar sarkin musulmi, jan hannunsa saeed yayi suka kutsa taron, maroqa sai biyarsu suke suna musu kirari, duk wanda ya hangosu sai tasowa suke suna miqawa khaleed hannu, anamasa congratulations, khaleed yaga tarin abokanansa a wurin sai tsiya sukemasa, shidai kansa duk ya qulle, wai meh yake shirin faruwane, saeed ya nufa da yashige taro yana musu godiya anata dariya, da niyyar ya jawoshi, yamishi bayanin abunda ke faruwa, hannunsa yaji anjawo, dad ya gani, kafin yagama mamaki, dad yaja hannunsa, son ina kajeni kanaso kasa a makara, tindazu liman ku kadai yake jira, afara daurin aure, jansa yayi sai wani qayataccen daki inda taron manyan mutane yake, duqawa khaleed yayi yafara gaidasu, suna tayashi murna tareda sa masu albarka, kafin khaleed ya ankara sai ji yayi ana tambayar waliyin ango da amarya, gwamnan jaha ne ya wakilci waliyin ango, shi kuma kawu na amarya, su kawu sai. Washe haqora ake yau shine a layin manyan mutane haka lallai haqarsa takusa cimma ruwa. Khaleed dai yaje dogon tunani shifa baigane abunda ke faruwa ba, meh dad da kawu keyi a wurin daurin auren abokin saeed? Ko dama diyar kawu ce zai aura shikuma shi ya gaygato dady? Khaleed bai ankara ba sai ji yayi ana sanarwa a loud speaker, ALHAMDULILLAHI ANDAURA AUREN KHALID DA KHADIJA AKAN SADAKI NERA DUBU DARI. Khaleed ya qara maimaitawa khaleed da khadijah kuma? Wai shin meh yake shirin faruwa idan nine khaleed toh waye kuma khadijah? Na shiga 3 wace khadijar dady ya auramin? Khaleed bai ankara ba akafara bashi hannu anamasa congratulations, shidai duk ya sandare saeed yake ta wara ido ya gani dan shikadai zaimasa bayanin abunda ya faru, bai ankara ba sai hasken camera ya fara gani daga ko'ina daukar hotunansa ake, jama'a sai tsayawa suke, ana daukar photo, chan ya hango saeed a cikin taro, cikin sauri ya wuce kamar mai son ya tashi sama, jama'a kuwa sai biyarsa suke, hannun saeed ya riqo, ya riqeshi gam danma kar ya kufcemasa, abokansa suka matso ango kasha qamshi tindazu muke nemanka, sai tsayawa suke tare dasu ana daukar hotuna, murmishin yaqe kawai yake musu, jan saeed yayi da qarfi sukayi gefe, chakumarsa yayi saeed kagayamin da wacce khadijar aka dauramin aure, saeed ya janye hannunsa daga chakumar da yamasa, just calm down my man, cikin tsawa khaleed yace how can i calm down, just explain dis, saeed ya lura zai tara musu jama'a dan duk wanda yake kusa dasu saida ya waigo Jansa saeed yayi suka nufi mota ya turashi gidan baya shima ys bude dayan side ya shiga, khaleed ya sake chakumarsa banta6a tunanin za'a hada baki dakai a lalatamin rayuwa ba, kasan yanayin da nike ciki kasan alqawarin da yake kaina, taya za'ayi ka yarda da wannan auren? Kuma da wadda banmasanta ba, yafara share hawaye. Saeed haushi kamar ya kasheshi, janye hannunsa yayi daga riqon da yayimasa, khaleed meh kake tunani? Ni zansaka hannu a lalata rayuwarka? 4 goodness sake aure aka dauramaka ba, ba life imprisonment aka maka ba, ko yanzu almakashin datse igiyar auren a hannunka take, zaka iya zuwa ka kar6i speaker kayi sanarwa, kace ka saketa dan bakason auren akwai alqawarin wata a kanka, kuma 4 your own information ameerah itace khadijah asalin sunanta kenan, bude mota yayi ya fito, malam kafito kayi sanarwa kan jama'a su watse, tinda farincikin budurwarka yafi na iyayenka muhimmanci, ya rufomasa qofar da karfi ya wucewarsa cikin 6acin rai. [11/24, 3:17 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 8⃣1⃣ khaleed zugum yayi a mota, sannan ya sauke ajiyar zuciya, tinda ameerah ce aka auramasa da sauqi, tinda akwai hanyar warware abub cikin sauqi, dan dama da yarjejeniya a tsakaninsu, itama ba so take ba, qwanqwasa masa mota yaji anayi, abokanensa ne, ya washe haqora, suko suka fara masa tsiya, ango guduwa kakeson yi gun amaryarka? Ae dole ka haqura dan mu da kaika yau sai dare, shidai fitowa yayi yana musu dariya, wanne daren bayan amaryar tawa tana asibiti, wani daga cikinsu yace ohh no wonder muka ganka haka yau ba nishadi, sai gudun mutane kake, karka damu tinda andaura zata miqe ne, Allah ya bata lfy akace amin, jansa sukayi akachigaba da daukar hotuna, daga nan aka shiga motoci aka wuce giginya coral hotel domin chin abinci, dan wasu baqin ma nan aka musu masauki. Khaleed sai wara ido yake yana neman saeed, amma da ya hangoshi ya nufi inda yake, saeed sai ya kauce masa, yasan fushi yayi, amma shima baidace sumasa haka ba, ya dace a sanarmasa amma yasan duk plan din saeed ne, dan ya gayamasa zai warware auren da ameerah ta samu sauqi, shiyasa yamasa haka, da haka har aka gama liyafar, akayi addu'a aka watse, amma khaleed ko loma baisa a bakinsa ba, duk inda ya nufa jama'a tareshi suke, har yagaji. Wani abokinsu da ke tare da khaleed ne ya hango saeed ya qwalla masa kira yazo, cemasa yayi sunaso suje su duba matar khaleed a asibiti, saeed yace bakomai mutafi, khaleed ya jawo hannunsa ya riqe gam, yanata so ya sakeshi yaqi, cemasa yayi amma malam kasan kai ka janyoni anan, kuma kanaso ka gudu ka barni, saeed yace kai baka iya motar bane? Wani abokinsu yace kaima saeed kasan ango bazai ja mota ba, yacemasa toh ai sai kajashi kai, yayi yunqurin wucewa khaleed still ya riqeshi yace kuje ku shiga motocinku, ga motar da zamuje a chan, kowa ya juya zuwa motar da yazo a ciki, saeed yace khaleed ya haka? Ya kabari har kowa zaiwuce banji kafara sanarwa ba? Khaleed baicemasa komai ba yajashi sukaje mota, ya turashi driver sit shikuma ya zagaya ya shiga dayan side din saeed yaja motar. Khaleed yace saeed m sorry, amma kaima kasan abunda kukayimin baku kyauta ba, ae yakamata a sanar dani, saeed yace naga yanda mom and dad suka damu da ameerah, naga yanda mom keson ayi auren nan, sanda suka kirani sukamin bayani akan na cinye gaba da shirye-shiryen daurin auren ba dagawa za'ayi ba, amma sun lura da yanayin da kake ciki, basai na gayamaka ba dan zaka iya qin amincewa, sun dauka damuwarka da yanayin da kashiga duk akan ameerah na, niko nasan ba shi bane wannan salmar ce take wahalar dakai, har kake shirin fasa aure saboda ita, zanbarka ka ruguza farincikin iyayenka saboda wata mace da bata damu dakai bane? Shiyasa nayi maka haka dan nagane kariga kayi nisa a son wannan yarinyar, nidai shawarar da zanbaka Allah kabi a hankali da ba'a ba mace amana, ni nama rasa meh kagani a wannan salmah da ka liqe mata, idan kyaune ae akwai wa enda suka fita, kuma zasu so ka fiye da ita, hannun khaleed ya daga masa, ya isa aure dai anriga an daura kuma nace kayi haquri, amma ni bazan dauki cin zarafin salmah ba, i love her alot kuma i don't need any reason to do dat, saeed ya ta6e baki, kai kasani ayi dai mugani, idan tusa na hura wuta, da haka suka isa asibiti. [9/14, 2:02 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [11/25, 7:40 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 8⃣2⃣ Mama da mom ne zaune da kausar a dakin da ameerah take suna fira, mom kecewa yau wannan ranar ranace da yakamata ace kowa na farinciki, amma farincikin mu ragagge ne tinda ga halin da ameerah ke ciki, kausar tace mom wai nifa hankalina bai kwanta da zaman ameerah anan ba, gasgi suncemana nan da 3 days zata farfado amma har yanzu shiru, mom tace kamar kinshiga zuciyata kausar dadynku nike jira ya dawo anemi visa kawai a fitar da ita, daidai nan salim da aliyu suka shigo, mom tace angwaye har antashi daurin auren? Salim yace eh mom daga wurin liyafa ma muke duk an watse, yace mom nima na goyi bayan a fitarda sister ameerah waje kawai, amma kuma ina za'a kaita, Aliyu yayi sauri yace akaita egypt kawai, mama tayi murmushi wato Aliyu akaita egypt dan ka tare a gunta ka fasa karatun ko, akayi dariya, mom tace ae maman ameerah ba wani abu bane indai za'a samu visa egypt zuwa gobe ae sai sutafi gabadaya, shima dan ya damu da er uwarsa ne, yake fadn haka bawai wani abu ba, mama tace nidai ban goyi bayan akaita egypt ba dan nasan gunta zasu tare kawai, suda sukaje karatu, Aliyu ya so6are baki, toh ni mama angayamiki ko bamu tafi tareda ita ba zan iya karatun ne bayan nasan er uwata ba lfy? Mama tace kanka akeji kuma. Mom ta daga waya takira dad tamasa bayanin shawarar da suka yanke, yace perfect timing, ina tareda alhj salmanu kuwa zanmasa bayani yanzu, idan nazo sai na gayamuku abunda yace, dan zamu shigo tareda mai girma governor yanzu zai duba ita yarinyar mom tace toh shikenan sai kunzo, ta kashe wayar. Su saeed ne suka sallamah suka shigo, mum tace angwaye ne haka sukace eh, kusan su goma sha 12, suka duqa suka gaida mama da mom sannan suka tambiye mai jiki, aka gayamsu da sauqi, daga bisani suka miqe zasu tafi, duk wanda zai fita sai ya ajiye kudi kan gado suka fice kowa yana fadin Allah yaba ameerah lfy, saeed ne yafita rakasu shikuma khaleed na zaune wuri daya zurum, su dad ne suka shigo da sallamah khaleed ya miqe ya basu wuri dan ganin manyan mutane, suka shigo suka duba ameerah wani malami da ke taredasu yayi ta zuba addu'a ana kar6awa daga bisani suka miqe, alhj salmanu yace hjy alhj yayimin bayani saidai zaku iya samun visa zuwa india a gobe itama ta mutum 3 kawai, kuma naga suma medical facilities dinsu suna da kyau, amma idan kunfison other countries din sai nan da zuwa kwana biyar, hjy tace a'ah wlh bazamu iya bari har kwana 5 ba, ayi visar india kawai, alhj salmanu yace toh da waye da waye za'a yiwa? Mom tace mijinta da kuma mahaifiyarta, mama atafau taqi amincewa saidai ita mom taje, ita meh zataje tayi? Ae yanzu 'ya tasu ce sukeda haqqin kula da ita, kausar da ke gefe tace mom toh ni atafi dani mana, Allah zan iya kula da ita ta marairaice, mom tace kausar ni bance bazaki iya ba amma a ganina gwanda atafi da babba kawai, kausar tafara shagwa6a har da kuka ita atafi da ita kawai ba ga yaya khaleed nan ba, mom tace kausar rigima shikenan ayi mata visa din kawai idan yaso mu daga baya sai muzo. Alhj yace toh su kawomin pssport dinsu a office yanzu, mama tace saidai fa ameerah batada pssport dan ko qasar nijer bata ta6a fita ba, alhj salmanu yace ba matsala akawomin hotunanta qanana pssport sai nayi mata yanzu da na koma, mama tace sai anje gida kenan aliyu ka tashi ka tafi, ka duba bag dinta na skul ka dauko, kausar tace there is no need inada pictures dinta, ta zuge purse dinta ta dauko ta miqa musu, alhj yace toh saura pssport dinku keda khaleed, kuma karku damu governor zai dauki nauyin komai, suka miqe akayi godiya, haka sukayita jibge bandir din kudade kamar a bank sannan suka fita. [11/25, 8:10 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 8⃣3⃣ Mama ta tsurawa tulin kudin da ke gabanta ido, tace Allah mai iko a ranta, ameerah dai ita zatw zame musu sanadin arziki a duniya, Allah dai kaba wannan yarinya lfy. Mom katse mata tunani ta hanyar cewa khaleed da kausar suje su dauki psspirt din kawai su kaiwa alhj salmanu karsu bata masa lokaci, suka miqe suka fita. Mom tace maman ameerah ya dace a kai kudinnan a bank fa, baikamata a ajiyesu anan haka ba, mama tace ba toh aimu ba mai account banki a cikinmu, mom tace bakomai salim katashi kutafi first bank gurin wannan qawar tawa bjy binta, kace nace ta budawa Aliyu account yanzu katashi ku kwashi kudin kutafi, mom tace kibasu har cheque dinda matar deputy governor ta bayar, kai salim ka cika sunanka ka chire kudin, sai ku zubasu duka a account din Aliyu, yace toh suka miqe suka kwashi kudin suka fita. Khaleed kuwa bayan sunje gida sun dauko pssport din cewa kausar yayi taje takai kawai, shi bazashi ba dan bayajin dadi ya miqamata psprt din ta shiga motarta shikuma ya shige daki, tea mai kauri ya hada yasha akan yunwar da hakeji, yasha magani ya zuge babbar rigarsa ya kwanta, wannan abun da ke faruwa kamar a mafarki, wai yau shine aka daurawa aure, baqincikin shi daya bada abar qaunarshi ba, kuma ita takasa fahimtar shi, wata idea ta fado masa, tinda india zasu gobe kuma daga shi sai kausar da ameerah ba su mom, suna sauka zaije yayi visa zuwa germany kawai yaje ya sameta idan taganshi yasan dole ta saurareshi, da wannan shawarar har baccin da ya dade baiyi ba ya kwashe shi. Khaleed ba shi ya farka ba sai bayan magrib, shima salim ne ya tadashi da ya dinga bugamasa qofa, tashi yayi ya bude, salim yace mom da dady ke nemanka, yace yana zuwa, ruwa yashiga toilet ya watsa ya hado da alwala, yayi magrib, yana sallamawa aka fara kiran isha miqewa yayi kawai ya kabbara ta ya gama, yayi addu'oinsa ya shafa, ya miqe ya nufi inda ake kiransa, bayan yayi sallamah ankar6a ya duqa ya gaidasu. Dad ne ya fara magana, khaleed haquri mukeso mu baka, munsan ko wanne namiji idan aka daura masa aure burinsa ya kasance da matarsa a wannan ranar, amma kuma kai naka auren sai yazo a haka, kayi haquri haka Allah ya tsara maka, kuma ina roqonka dan Allah ka riqe yarinyar nan amana domin marainiya ce, kaima zaka samu ladar kula da ita. Mom tace kadai riga ka karanta kagani bama buqatar mu gayamaka miye aure, ko haqqin matarka a kanka, inada yaqinin wannan yarinya zata zamemaka mace ta gari, shiyasa tun farko namaka sha'awarta, Allah ya muku albarka, ya baku zama lfy da zuri'a ta gari akace amin, mom tace katashi kafara shiri jirgin qarfe goma zakubi gobe khaleed yayi godiya ya miqe ya fita, a ransa kuwa yana nazari, lallai warware wannan auren sai ya zame masa matsala ya tafka kuskure, dan iyayensa sun ba ameerah yadda da aminci 100%. [9/14, 4:21 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah Abdul 8⃣4⃣ Angama visa anyi clearance din komai, ya rage kawai suyi boarding jirgi, mom ce riqe da kausar tana jamata kunne akan ta kula da ameerah sosai, tace mom bafa sonta kika fini ba, zankula da ita fiye da yanda zankula da kaina, mama kuwa da su suhaila sai faman kuka suke, ana basu haquri, Aliyu da salim kuwa jirgin sha biyu zasubi zuwaegypt, passengers aka fara kira masu zuwa india suzo suyu boarding, ameerah aka tura ta bisa gadon marasa lfy aka wuce da ita straight sai wani special place da ake aje uncouncious patient, sukuma khaleed da kausar suka zauna a VIP side cikin sauran passengers masu kudi en uwansu jirgi ya daga sai qasar INDIA💨✈✈✈. Sukuma su mom suka juya zuwa gida kowa nata addu'a a ransa Allah ya sa qarshen wahalar kenan Allah ya bata lfy. 🍇🍇🍇INDIA🍒🍒🍒 Direct babban birnin mumbai aka saukesu, aka saka ameerah ambulance sai CITY HOSPITAL, direct ana isa suka kar6eta dama anyi process din komai kan suzo, operation room suka kaita, aka turata cikin wata na'ura ayi checking idan bata tareda ko wache matsala, luckly ba wani brain damage, sai targade da aka samu a hannunta, sauran ciwukan kuma anyi treating dinsu tin a 9ja, doctors sukayi mata abunda ya dace sukayi shifting dinta zuwa icu, khaleed da ameerah suka taso doctor ya gayamusu, there patient is ok now, there are som minor issues da ba'ayi treating ba daz y she went into comma 4 days, but yanzu zata farfado within d next 24 hours, now she is in icu za'a ajiyeta nan 4 observation, they can go nd c her now. Khaleed da kausar suka wuce dakin ameerah kausar ta zauna kusa da ita, shi ko khaleed ya juya zaifita kausar tace big bro ina zakaje, harara ya watso mata inda kika aikeni, ya juya ya ficewarsa ya barta da mamakin inda zaitafi, bayan angayamasa matarsa zata iya farkawa any moment. Direct khaleed airport ya wuce yafara neman ticket na jirgi zuwa germany, luckly ya samu coz few passengers ake nema kawai, ana gama komai khaleed ya keta hazo sai germany without any regret. Khaleed bai dade da fita ba kausar ta dora kanta a gado bacci yayi gaba da ita, chan cikin bacci taji kamar ana ta6a hannunta, cikin hanzari ta buda idonta, ameerah taga tana motsa hannunta, tashi tayi taje kusa da kanta, tafara girgiza ta sister inlaw, ameerah ta bude idonta, amma kuma sai tafara ihu tana fizge-fizge, husnah plz don't kill me, husnah plz don't kill me. [9/14, 4:27 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 8⃣5⃣ kausar tafita da gudu taje ta kira doctor, suka shigo cikin gaugawa, nurses suka riqeta tanata fizge-fizge wani doctor take ya dauko wata allura yayi mata, cikin second da baifi 20 ba ta langa6e, ta koma bacci, kausar cikin kuka take tambayar doctor what is wrong wit my sister? Doctor yace mata kar ta damu shock ne kawai da ta samu kan abun ya faru da ita, tsoron da tajine bata samu expressing dinsa ba, shiyasa ta tashi dashi amma komai zaizama normal yanzu da ta farka bacci, kausar ta musu godiya suka fice, taso ta kira khaleed ko su mum amma sim card dinta is not working, kuma bazata iya fita tabar ameerah ba kar ta sake farkawa da taje ta siyo new simcard zaunawa tayi ta qurawa ameerah ido, daga bisani ta fara tofa mata addu'oin da ta iya. 🍇🍇🍇GERMANY🍒🍒 Khaleed yana sauka qasar germany cab ya tara, yace akaishi near by hotel, aka kaishi ya sauka, ya nufi reception ya kama single room 4 2days, sauke er qaramar jakarsa kawai yayi, ya fito da wani qaramin diary yana duba adress din skul din su salmah da ta ta6a bashi, fitowa ya sakeyi ya dauki cab ya bashi adress din, ba'a saukeshi ko'ina ba sai LUDWIG MAXIMILIAN UNIVERSITY OF MUNICH. Aka saukeshi direct admin block ya wuce ya fara bincike Salmah Usman Nasir a final year student psychology department, akayi checking akace masa babu meh wannan sunan a final year students, khaleed yace a sake dubawa still akabashi same answer, but yayi request a bashi details na othr salmah da ke skul din, matar taga kamar ya shiga damuwa ta taimaka ta bashi, khaleed ya fara yawo diffrnt departments but duk salmar da ya gani ba salmarsa bace, yaci uwar wahala, ya gaji ga yunwa ga qishi, ya samu wani seat qarqashin wata bishshiya ya zauna, wata budurwa itama er nigeria da tabi wurin kusan sau 3 tana ganinshi, ta nufi wurinshi, excuse me handsome tace masa, ya dago idonnan da suka fara ja ya kalleta, robar ruwa ta miqomasa ba gardama ya kar6a ya kwankwade yace mata thanks, tace tindazu nike wucewa tanan ina ganinka, may i help you, ya gayamata salmah usman nasir yake nema, tace y don't u call her? Yace d number is not going, tace masa let me see her photo if u have one, cikin hanzari ya zaro wayarsa yanata jin haushi me yasa tindazu baiyi tinanin nuna picture ba, ya miaqawa budurwar tana gani tace masa ohh u mean (SUN)? SUN khaleed yace? Yace daz what we call her here, ae tayi graduating tin last year she is working now, tace tindazu da ka nuna picture dinta da baka sha wahala ba, coz kowa ya santa she is popular.................... Wata figigiyar yarinya ce ta katseta, ke virus who are u currupting there, tace SNACKS dis handsome is looking 4 Your SUN, kallon sama da qasa ta masa mal lfy kake neman sun? Wadda aka kira da virus tace jst help him out tindazu yake nemanta, ta6e baki tayi aike kinsan SUN bata komai da da namiji, ba namijin da ya isheta kallo, tace malm ko kaje zaka 6ata time dinka ne, yace ni brother dinta ne ki taimakeni plz, tace shikenan address din hotel dinda take zama ta bashi, cikin jin dadi yayi godiya ya wuce da sauri, a ransa ko yana gode Allah da yasa salmarsa ta riqe masa alqawari bata kula ko wanne namiji, cab kawai ya shiga ya nufi hotel dinda akabashi address. [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 8⃣6⃣ Direct THE CHARLES HOTEL MUNICH, Aka kaishi, ya sauka ya nufi reception, ya gayawa matar he is here to visit salmah usman nasir, receptionist tafara bincike, tace masa they don't have anybody wit dat name here, take ya ciro wayarsa ya nuna mata photo, tace oh you mean SUN? Is she especting ur visit now? Khaleed yace no, matar tace yayi haquri tayi masu gargadi, idan ba ta gayamusu tana especting baqo ba, kada ma su saurareshi, khaleed yace just help me plz, i came from Nigeria just to meet her, matar taga ya damu ta daga waya ta kira dakinta, tana cemata tanada baqo kafin ta qarasa zancenta, tace mata batason ganin kowa yau ta kashe wayar, khaleed yayita insisting matar tace sam she already gave her orders su hotel dinsu baya violeting order na customers dinsu, khaleed ya gaji da tsayuwa matar tace masa ya dawo gobe, ya rubuta details dinsa yace taba salmah din plz, tace zata bata, sannan ya fice jiki ba qwari, ga yunwa ga gajiya, cab ya tara yace akaishi restsurant, CHOPAN SCHWABING RESTSURANT aka kaishi, most of there food there Are italian cuisine, haka yayi order yaci ba dan dadi ba, saidai dan kar yunwa ta illatashi, ya koma hotel dinsa HOTEL METROPOL, ramuwar salloli yayi, ya watsa ruwa ya kwanta yana jiran call daga salmah, shiru-shiru har baccin wahala ya kwasheshi. 🍒🍒🍒INDIA🍇🍇🍇 Kausar na zaune kan sallaya ta idar da sallar isha'i, Abun duniya ya isheta, mamaki da takaicin yaya khaleed ya addabeta, tun da suka iso india fa ya kama gabansa, ita batasan inda yayi ba, gashi har dare yayi, tayi zugum taji alamun ameerah ta motsa, tashi tayi cikin hanzari ta isa wurinta, da kadan-kadan ta fara bude idonta, idonta qyam sai akan kausar, ta dade tana kallonta tareda tunano abunda ya faru, kausar murmushi ta sakar mata welcome bak sister inlaw kin tsoratamu ba, ameerah murmushin itama tayi mata, tace ina su mom? Kausar ta rungumeta, ameerah tafara waige-waige, tace inane nan kausar? Tafara yunqurin tashi zaune, kausar ta kwantar da ita, tace bari ta kira doctor first, doctor na zuwa cikin fara'a yace welcome bak my beutufil patient, ameerah tayimasa murmushi, zuwa yayi ya cire mata, na'urorin da ke jikinta da suke monitoring dinta, tayi yunqurin tashi doctor yace kausar taxo ta taimaka mata, wata allura doctor yayi mata, dafa hannunta tayi, tayi qara, doctor ya sangale mata hannu, a wata hand holder, da suke sakawa wa enda suka samu rauni a hannu, yace mata kar ta damu, in 2days time hannunta zai zama normal, yafita tareda cewa zasu aiko abincinta yazo, tarda magani a nurse wil help her take d medcine, ya fita ameerah tace kausar ta taimaka mata ta shiga toilet her body is weak, tazo ta kamata tace sis almost kinkusa 1week a kwance ba dole jiki yayi tsami ba? Takaita toilet tayi mata brush, ta barta tayi abunda zatayi sannan ta kamota suka fito, koda suka fito nurse na jiransu, tea mai kauri akaba ameerah tasha, da wani potatoe porridge, sannan nurse ta bata magunguna ta fita. [9/14, 4:30 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 8⃣7⃣ kausar dawowa tayi kusa dani ta zauna, ta quramin ido, na hure mata ido nace miye haka? kamar kinga wata sabuwar halitta, tace ae itace, sister inlaw munshiga tashin hankali, Allah we thought u ar going to leave us, nace kausar kenan ae mutuwa na kan kowa, da lokacina ne yayi dole zantafi, kausar tace sai gashi kindawo, mukayi dariya, tace ba inda zakije sai kin haifawa broda na kyawawan yara kamar ke, nace yo ni har wani kyau ne dani? Tace sis ae ke kyaunki sai mai hankali ke lura dashi, wanda yake lura da qyalqyali ne kawai bazai gani ba, natural beuty, beuty without makeup, nace kausar da ke namiji ce sai kinyi tsari, nace baki gayamin inane nan ba, tace mumbai india kike sis, na dan fito da ido india fa? Ta gyadamun kai nace duk ina ina akazo india? Tace kishiga comma ne sis, toh mu biyu kawai mukazo nan? . ta dan ta6e baki tareda yaya khaleed mukazo, nace mata yana ina? Oho tace tinda mukazo ya fita banqara ganinsa ba, cikin rudani nace sis shine kikazo nan kika zauna, dariya tayi tace jst relax ni naji ajikina lfyarsa qalau, shiyasa ban wani tada hankalina ba, shi bai damu ya gayamin inda zai tafi ba, meh zaisa na damu kaina? shiru nayi ina addu'a a raina Allah ka tsaremun shi a duk inda yake, nace sis kwanana nawa ne a comma? Tace aikinsan 3 days to your wedding abun ya faru, jiya aka daura aure, yau mukazo nan, daura aure nace? Dariya tayi kindauka anfasa daureki ne? Ai ke matarmu ce yanzun sai yanda mukace, ni nama rasa meh nakeji dadi ne ko damuwa, nace yau kusan 5days kenan ko? Tace eh nayi yunqurin tashi, tace ina zaki kuma? Nace ina naga zama sallar kwana biyar a kaina, tace ki bari ki qara samun sauqi mana, miqewa nayi ae na warke weakness ne kawai, ta taimakamin nayo alwala, sallaya ta shinfidamin na zauna na fara ramuwar sallah. Tun kausar na jirana har tagaji ta tashi ta fita waje neman sim card, da tambaya aka nunamata wani wurin ta siye tayi register, ta juyo, wani shop tagani na snacks da drinks ta shiga ta siyo ta dawo, har ta shigo inata rafka sallah, layi tasa ta zauna jirana, sallamawa nayi, tayi sauri tace sis bari na kira su mum, cemata nayi kinsan fa 5hours ne tsakanin india da nigeria, yanzu nan 8pm chan kuma fa? Tace kusan 1.am kenan nace toh kingani ki bari har da safe kawai karki tashesu bacci, tace ok bari na kira miki su aliyu, nace ae suma sunyi baccin, tace sis Aliyu fa na egypt da salim, baki na washe kai haba when? Tace suma yau suka wuce, nace Allah sarki danuwa, i'm so happy 4u, kausar tasa kiran salim, take ya daga yanajij muryar kausar yafara murna, bayan sungaisa yace ina sister inlaw? Tace ta farka gata ku gaisa ta miqomin waya, muka gaisa yamin ya jiki, sannan nace ina aliyu, yace bari na kaimasa yama kasa sakewa sai zancenki yake, Aliyu aka kaima waya cikin hanzari ya chafke wayar, ya fara sweet sis, nace na'am sweet bro, sai kuma ya fashe da kuka, nace danuwa miye na kuka kuma? M ok now, yace kukan farinciki ne sis, ni badan mama ba Allah da bazanzo na barki ba, nace toh meh zakamin idan ka zauna ali? Naji dadi da mama ta hanaka zama, nasihohi na masa akan ya kula da karatunsa mukayi sallamah. Sallolina na koma na cigaba, tin kausar na jirana har tayi bacci, sai around 2.am nagama nayi nafiloli nayiwa kaina da khaleed addu'a, Allah yasa aurenmu ya zama alkhairi, nasa alarm a wayar kausar na dan kwanta, around 5.30 a.m alarm ya tashemu na tada kausar mukayi sallah, bayan mungama azkar munkaranta alqur'an, muka fara fira, kausar na gayamin abunda ya faru ina comma, lura tayi ita kadai ke zuba ni namayi bacci, itama ta kwanta takoma bacci. [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 8⃣8⃣ 🍇🍇🍇GERMANY🍒🍒 Khaleed bai farka ba sai da gari ya waye, cikin hanzari ya miqe, yaje yayo alwala ya kabbara sallah, yana kammalawa ko addu'a baiyiba ya dauko wayarsa ya duba ko zaiga missed call or txt din salmah, amma ba ko daya, tsaki yaja ya jefar da wayar, ya koma yayi addu'a yana roqon Allah yasa yaga salma yau, ya koma india kan su mom suzo su samu bayanan, telphone ya kira yayi ordering breakfast aka kawo masa yaci ya qara kwantawa ko zuwa qarfe goma ya koma hotel din idan bata kirashi ba. Salmah ce tafito daga room dinta ta sauko, tazo gun receptionist ta kar6i saqo, har zata wuce ta tuna da saqon khaleed, ta miqa mata dubawa tayi, tayi tsaki shi wannan ma dan jaraba biyota yayi a germany, itafa batada time din yin wani aure a yanzu, yaga takardar tayi idan ya sake zuwa let me know plz ta wuce wanta. Around ten ya farka, miqewa kawai yayi ya watsa ruwa, ya chanja kaya ya fita, cab ya tara sai charles hotel, yana isa yayi reception, yace taganeshi? Tace eh ba shi yazo jiya ba? Yace bataba salmah saqonshi bane? Tace tabata tace idan ya qara zuwa a sanar da ita, take wani farinciki ya ziyarci zuciyarsa, ta daga waya ta kirata, bayan ta saukene tace, tace ya jirata a CHOPAN SCHWABING RESTAURANT nan da 1 hour, khaleed bai ko damu ba ya kama hanyar restsurant din, dama jiya chan yaci abinci, ko da yaje ya kama table coffee kawai yasa aka kawo masa, tin yana kallon agogo har ya daina, gashi jirgin qarfe 2 zaibi ya koma india, wayan kausar ya kira not available, yayi tsaki har ya gaji, sai wata zuciya tace masa ya tafi, wata tace karka tafi tazo ta qara fushi, dama kasan kai kamata laifi sai ya dawo ya zauna, har qarfe daya khaleed na zaune, waiters sai zuwa suke suna tambayarsa idan da abunda yakeso, khaleed sai coffee yake order yana kwankwada dan jiya yaci abincin wurin bai gane komai ba. Qarfe daya salmah ta fito hotel dinta zata fita, taje reception ta bincika idan tanada saqo, sai lokacin matar ta tunamata da wanda tace ya jirata, tsaki tayi sannan ta fito ta nufi wurin. Khaleed ya miqe haka ya tashi ya koma hotel din, ya ganta tsaye gabanshi, wani murmushi ta sakar masa tace babyna m sorry, na zana jarabawa ne, murmushi yayi ya nuna mata wuri ta zauna, aransa yace ko mehyasa batason nasan ta gama karatu sai kuma ya basar, haquri nazo na baki salmah, kinsanj rudani na kasa sukuni, na rasa nutsuwata a kanki, kinqi ki saurari uzurina, katseshi tayi wanne uzurin ai ka riga kayi auren kuma, u break our promise, so ni bazan ta6a iya sharing dinka da wata mace ba, indai abunda ya kawoka kenan u better go, ta miqe zata tafi, sai ga khaleed a qasa ya riqe qafan salmah, ni Deejah haushi kamar na mutu baisan wahalar da nasha kan na biyo shi germany ba, amma abun takaicin da zangani kenan 😢 ba'anan ya tsaya ba khaleed harda kuka salmah ta saurareshi, ni DEEJAH kamar na rufeshi da duka, ga ameerah chan zata mutu ma kansa yazo yana kuka kan wannan mai kama da aljanun, leqawa nayi na qaremata kallo gajera ce fara tas kyakkyawa ce ainun da wasu ido, idan ta budesu sai ka firgita kan girmansu🏃🏼🏃🏼. Dawowa tayi tazauna jikinta yayi sanyi a raina nace er qwal uba🙊 gwanda ma karki haqura, ta marmada qattan idonta, toh ina jinka, shiko gautan yafara fede mata biri har wutsiya yanda akayi ya auri ameerah, amma shi ko kadan baya sonta, nace zaka sota dan malfar uba🙈 waigowa sukayi na duqe qasan table basu ganni ba, sai cewa tayi toh shikenan naji na haqura i'll get bak 2u soon, ni zantafi miqewa yayi kamar jela ya bita yana mata kalaman soyayyah ni Deejah tsabar haushi kasa rubutawa nayi, motar ta taja ta tafi ya bita da ido kamar maye saida ta 6acemasa. [9/14, 4:37 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah Abdul 8⃣9⃣ Ajiyar zuciya khaleed yayi, Allah na godema da kasa ameerah ta sauraren, sai a lokacin ya duba tima 20 minutes to 2 cikin hanzari ya tari cab, ya koma hotel dinda ya sauka shiga kawai yayi ya dauki jakarsa ya wuce airport, koda ya isa jirgi kadan ya tashi, anyita qwalla kiran sunansa baya kusa, daqyar ya samu aka barshi ya shiga, suka daga sai india. 🍒🍒🍒INDIA🍇🍇🍇 ameerah da kausar sai around ten suka farka, kausar ta taimaka mata tayi brush sannan ta barta tayi wanka, ta dawo ta kwanta itama kausar ta shiga, koda ta fito nurse ta kawo breakfast dansu asibitin su kebawa patient abunda zasuci amma duk a kudinka, kausar ta taimaka mata tayi breakfast itadai ameerah taste din abincin india yayi mata, taci tasha magani, kausar kuwa snacks dinta ta diba taci da drinks. Kausar ta lura ameerah tayi wani zugum tace bari na kira su mom, tasa call dinsu take mom ta dauka, tanajin muryar kausar tace hope good news zaki bamu, kausar tace yes mom ta farka tin jiya ma now she is alright, murna suka fara, mom tace toh meh yasa baki gayamana tin jiyan ba? Kausar tace mom bansamu simcard da wuri ba sai cikin dare, nasan kunyi bacci, sis ameerah tace nabari har da safe, mom tace toh kibamu ita mana, ta miqomin wayar, waya mukayitayi dasu, mom, mama, suhaila, fatima, siyama da khairi kowa saida akaba mukayi magana, mom tace su suna airport ma yanzu zasu taso, nace mum ku duka? Tace a'ah itada mama dai su suhaila a gida zasu zauna har adawo, tace ina khaleed? Na daburce nace mata ya fita siyo magani kausar ta dago kai da sauri ta kallonj, nayi mata alama da hannu tayi shiru, daga bisani mukayi sallamah, akan sai sun iso. Bayan mungama sai ga kiran su salim da aliyu haka mukasha fira suma saida kausar ta kar6e wayan ta kashe, nace ya haka sis? Tace magana zamuyi kafin su mom su iso. Kallon tuhuma tayimin, meyasa kika hana na fadi gaskia akan yaya khaleed? Nace toh meh zakice? Tinda aka sauka india ya gudu? Kinsan meh yajeyi ne? Ta6e baki tayi, amma koma mene ae baikamata ya kwana achan ba, sister inlaw ki gayamin gaskia tsakani da Allah, wai miye tsakaninki da yaya khaleed? Qirjina ya buga nace mata kamar ya? Ni bangane ba, tace ni Allah na lura banga wani chemistry a tsakaninku ba, kwata-kwata wanda ya zauna tareda ku baxaiga alamun soyayya a tareda ku ba, duk da nasan yayana daban ne, amma ni nasan sanda yayi soyayya da wata er abokin dad ba haka yakeyi ba, take zuciyata ta buga nace mata kinsan salmah ne? Tace farin sani kuwa? Amma ke ya akayi kika santa? Take qwalla ta cikon ido na share, zuwa tayi ta dafani, dama ni nasan da wata a qasa, titsiyeni kausar tayi saida na kwashe komai na gayamata. Ajiyar zuciya tayi, gaskia kinyi wauta sister inlaw, amma kuma banga laifinki ba so ne yaja miki, kuma da kingayawa broda gaskia bazai kalleki ba, amma yanzu kinada hope kuma ni zan taimaka miki to fulfill your DREAMS, hugging dinta nayi ina kukana inamata godiya ita kuma tana bubbugamin bayana alamun rarrashi. Sakinta nayi nace mata salmah fa? Tace diyar abokin dady ce, senior ta ce a secondry skul, tin alokacin nasan tana soyayya da broda, har lokacin da ta gama aka turata germany karatu, amma daga time din banqara jin zancenta ba ko a gida broda bai fadi ba, so mundauka ma sun dade da rabuwa, i was suprised ma da kika gayamin har yanzu ita yake so, toh ko meyasa sukaqi fada a gida oho, amma ni sis inaganin Allah shi yasan abunda ya tsara shiyasa haka ta faru, ni yarinyar tuntuni batayimun, tafiye jinkai da yiwa mutane kallon banza, itama bata qaunar talaka ya ra6eta shiyasa bama jituwa tin a skul, kuma mudai yanzu kece choice dinmu, zan tayaki fighting till d end, hugging dinta nayi cikin farinciki, araina nace samu dafa, Allah ya nunamin cikar burina. Kausar tace now dat i think may b bro germany yaje, nayi rau da ido, tace jelous ko sis nayi murmushi tace karki damu, my broda iz not dat bad bazaiwuce limit ba, doctor ne yashigo yana tambayar meh nikeji now nacemasa jst a weakness yace it normal zandaina ji, allura yamin zaifita, nacemasa zanfita nagaji da zama wuri daya, dariya yayi yace lallai sauqi yazo, kausar ta taimakamin muje garden gatachan ya nuna mana, tashi tayi ta kamani muka nufi gun. [9/14, 4:41 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah Abdul 9⃣0⃣ Garden din muka shiga muka zauna ko'ina luf-luf gwanin sha'awa sai kukan tsuntsaye kakeji, shiru mukayi 4 sometime kausar tace sis amma kinsan ya kamata mom tasani ko? Da sauri na dago na kalleta, nace dan Allah sis karki fada, inajin kunyar mom da wanne idon zan kalleta, idan tasan plan dinda muka shirya, zataga kaman mun renamusu da hankali ne, kinga mom ta yarda dani sosai, kausar tace nima dalilin da yasa nace na gayamata kenan, dan nasan tana sonki sosai kuma ta yarda dake, so zata fahimce dalilin qaryarki kuma m sure mom zata taimakeki. Nidai na girgiza kai sister inlaw just promised me bazaki gayawa mom ba, dis is my battle i need to fight it alone, tinda ni nasaka kaina, a ranta tace zanyi shiru 4 now, amma duk naga abund zai baki wahala dole mom ta shigo ciki dan broda baya tsallake maganarta, a zahiri kuma tacemin shikenan sis bazan fada ba, and remember this is our fight, not yours alone, hugging dinta nayi ina qara godewa Allah ashe dama za'a samu dangin miji haka? Nidai nayi dacen dangin miji, saura mijin shima Allah ya dorani akansa. Su mom an iso birnin mumbai india, direct mota suka shiga sai FOUR SEASONS HOTEL MUMBAI, suka kama kowa daki, suka sauke kayansu sannan suka nufi adibiti. Khaleed ma yayi landing saidai traffic hold up ya tsayar dashi a hanya. Muna zaune a garden muna hutawa dan ni wurin yayimin, wata nurse tazo tace its time 4 my medcine, natashi muka koma dakin da aka maidani, dan tinda na farfado anyi shifting dina daga ICU, Mom suka iso sukayi inquiry aka basu number dakina suka nufi dakin. Ina zaune ina cin lunch sai ganin su mom nayi, da saurina na miqe har ina qoqarin faduwa, dan haryanzu jikina ba qwari na nufi wurinsu, kausar dariya tayi sister inlaw wlh kiyi a hankali kar jinya ta dawo sabuwa akayi dariya, mum ta riqoni ta rungumeni m so happy to see u my daughter nace me too mom, mundade a tsaye a haka sannan ta sakeni naje na fadawa mama, janyeni tayi kinga ni karki karyani, lura nayi tana share qwalla, na tayata mama kukan dadi kike ko? Karki damu bazan mutu da wuri na barki ba, kema sai kinga jikokinki, nayi sauri na rufe baki alamun jin kunya, dan qaramin duka ta kaimin nasa qara, tace mara kunya ashe har yanzu wannan bakin bai mutu ba, dariya akayi mom ta jawoni ta zaunar dani, nidai karki jimata ciwo daga zuwanki, mama tayi dariya ae kunfi kusa yanzu ni gwanda ma da kika daukemun ita, nace mama idan na tafi sai kinyi missing dina fa, Mom tace ina mijin naki na buda baki zanyi magana sai gashi ya fado kamar daga sama, sallamah yayi aka amsa jikinsa duk yayi sanyi ganin su mom da yayi, mom tasha mur daga ina kake, yarasa meh zaice mata, tunaninsa mun gayamata tin jiya bayanan, sosa qeya yayi mom neman wani doctor na tafi a germany, kausar ta kallan na kalleta, mama tace germany dannan wato duk likitocin da ke india basuyi maka bane? Mom tace toh ina likitan yake? Yace bayan na tafi ne kausar ta kirani ta gayamin ameerah ta farfado kuma ta samu sauqi shiyasa Ban daukoshi ba, kausar ta koma kallona nayi mata inkiya tayi shiru, harara ta watsomin ta kauda kanta, mom tace kenan ko hotel baku sauka ba? Tinda kai tin jiya bakanan kausar kuwa nasan a asibiti ta kwana, to kuzo muje hotel dinda muka sauka ku samu daki. Cewa nayi mom plz kice doctor ya sallameni nima karku barni anan, Allah na warke, doctor ne ya shigo, ya duba hannuna yamin allura, mom tace doctor za'a iya sallamarta kuwa? Yace no saidai zuwa gobe idan sun kwance hannun idan aikin yayi, zasu iya tafiya dani zan iya dinga zuwa kullum na kar6i allura 4 3days. Mom tace toh mu mungaji munso mu huta, ameerah ki haqura sai goben kawai, suka juya zasu tafi, kausar ma ta dau jakarta, mom tace ina kuma zaki? Tace mom nima inaso na huta ga mijinta nan ya tsaya da ita 4 tonight, mama tace gaskiyarki fa zo muje, haushi harda hawayena, kausar ta kalloni tayimin gwalo, suka hada ido da khaleed ta watsa mai harara ta fita. Mom ta radawa khaleed a kunne son is your chance today to spent time wit your wife, dan idan ankoma biki zamu shiga so bazaka samu chance irin wannan kusa ba, ta fice ta barshi a sandare kamar photo, niko sai share hawaye nake. [9/14, 4:43 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 9⃣1⃣ khaleed ya dade anan tsaye sannan ya shigo dakin waige-waige ya fara, ya hango ledar snacks da drinks dinda kausar ta bari yazo ya diba, ya fara turawa kamar mayunwaci, nidai kallonsa kawai nike, a raina nace ita salmar ta kasa baka abinci ne ko kuma ba abinci a germany? Yanda yake tura bread yana kora lemo ni har abun dariya ya bani, na rufe bakina kar ya lura dariya nike masa, karaf muka hada ido yace abincin germany ba dadine, murmushi nayi ae kuwa naga ka kwaso yunwa na india da dadi kuwa, ya jikin yace min nace da sauqi, sai kuma shiru ne ya biyo baya, sai chan nace masa ya salmah din? Ya wani washe haqora dariyar da baita6amin ba, lafiyanta qalau wlh, i missed dat girl da inada chance da nayi ko 2weeks a germany, bamu wani samu time sosai ba, idan kika ganta yanzu ta samu hutu ta qara kyau, kamar na daukota na taho da ita, haushi ya kamani wai dama wannan ya iya surutu? Meyasa ma na tambiyeshj ita? Cewa nayi cikin fushi a raina, toh meh yahana ka sakota jaka kazo da ita? Ashe maganata ta fito fili, dariya naga yanayi na qura masa ido, kinga ni banyi tinanin haka ba fa, amma da na sakota bag din kuwa, da yanzu sai na cire abata na riqa kallo, ya sake dariya, taisayin kaina nafara ji wato shi ko zancen salmah akayi masa nishadi yake shiga, wayyo ni ameerah, take qwalla ta cikamin ido, na juya kai na share kar ya lura. Sauri nayi nace masa yaya saeed fa? Waya ya zaro ya kirashi miqomin wayar yayi, ya daga nace hello yaya saeed, cikin farinciki yace princess, Allah mungodemaka inanan inata zullumi ashe ke kin warke? Fira mukasha dashi, yabani aunty fareedah itama, tace qawata akwai special tanadi da nayimiki fa, sai kundawo Allah ya baki lfy, nace ameen mukayi sallamah na bashi wayarshi. Shuru ne ya biyo baya a dakin, har nurse ta shigo ta bani dinner da magani nasha, fita yayi ya dade a waje saida dare ya tsala sannan ya shigo, icecream naga ya miqomin na kar6a na fara sha, shikuma ya koma gefe yana shan coffee, duk sanda zan dago kai na kalleshi sai naga yana smiling, nasan kuwa duk akan salmah ne, haushi ya isheni kamar na tsala ihu amma ba dama, a haka har bacci yayi gaba dani. [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 9⃣2⃣ da assubah alarm din khaleed ne ya tadamu, tashi mukayi sallah, azkar dina nayi na shafa addu'oi, sannan na dauko qur'an da kausar ta barmin na fara karantawa, cikin er qaramar muryata da qira'a ta mai dadin saurare. Khaleed shima ya kammala tashi sallar yayi kasake yana sauraren karatun ameerah, har wata nutsuwa ta saukar masa, saida gari yayi haske, na rufe qur' an na aje, toilet na shiga da kayan da kausar ta barmin, brush nayi nayo wanka na chanja kaya, wata 3quater riga ce da pencil trouser da mayafi, samfurin kayan india ne, kayan sunmin kyau ba laifi na fito, na kwanta a gado na, khaleed kuwa ya bini da ido aransa yace itadai komai nata a nutse takeyinsa, tsaki yayi kuma y do i even care. Karaf muka hada ido dashi murmushi na mai sanyi na masa, nace good morning, ya kawar da kansa gefe sannan yace morning ya jikin nace masa da sauqi, ear piece nasa na kunna qira'a ina saurare, kwanciya nayi na rufe ido alamun bacci, yadan jima yana kallona sannan shima ya shiga toilet ko da yafito, ya chanja kaya, baqar shirt yasa da wando ya fito fes dashi sai sheqi yake, nidai satar kallonsa kawai nike duk inda yayi ina binsa da ido kamar munafuka, wanda bai lura ba zaice bacci nake, snacks din jiya naga ya sake kwasa yaci yasha lemo, da ya gama ya miqe zaifita kuma sai ya juyo ya kalleni, doso wurina yayi niko na qara rufe ido, zuciyata sai harbawa take da sauri, duqowa yayi ya ciremin ear piece dinda ke kunnena, shi a tunanin sa nayi bacci, ya aje wayar a gefen gadona ya juya ya fita, sai lokacin na bude idona ina murmushi, my khaleed you ar not dat bad na qara murmushi, na rufe ido bacci ya daukeni. Cikin bacci naji ana ta6ani buda ido nayi, kausar ce gira ta dagamun, amarya how was your first night? Naga sai wani sheqi kike, bacci kike amma kowa ya kalleki, yasan kina tareda farinciki coz u r smiling while sleeping, duka na kaimata ke bakida kunya ko? Ina ruwanki da sirrin ma'aurata mukasa dariya, mom da mama suka shigo tareda khaleed, mom tace en matana meh kukewa dariya? Kausar tace mom abun sirri ne, tace kudai kuka sani idan tayi tsami zamuji, nurse ta shigo ta kawomin breakfast da magani, kausar ta kar6a har ta fara bani, sai kuma ta aje, brother kazo ka ciyar da matarka ni nagaji da bata, kaga hannunta na dama a sangale, yi yayi kamar baijita ba, mom tace bakaji meh qanwarka tace bane? Mama tace kibarshi may b kunyarmu yake, mom tace toh wa zai cigaba da kulamasa da ita dama? Ae gwanda ya saba, muje muga doctor yazo ya duba hannun if possibl ya bata sallamah suka fita, kausar ta miqe nima zanbiku ta wuce abunta. Tsaye yayi kamar ya wuche abunshi, ya juyo dai ya kalloni muka hada ido, ya dawo ya zauna, spoon ya dauka ya debo abincin ya zunguromin batareda ya kalla ba, jiyayi anqi kar6a ko da ya lura a hanci yake qoqarin turamin abincin, da sauri ya sauke spoon m sorry plz yace, na fashe da dariya, shima da ya kalli painting da yamin a hanci ya fara dariya, muka riqa dariya kamar zautacci, mom suka shigo, son lallai duniya tayi dadi kace dama, wuri kakeso mubaku da matarka ku kyakyata, nidai duqar da kai nayi alamun kunya, shikuma har yanzu bai rufe baki ba, duk ya kalle fuskata sai tabashi dariya, kamar wani cartoon na koma, tissue yasa ya gogemin hancin, doctor ya shigo ya kwance hannun, ya tura a wani machine ya cire, ya daga sama ya sauke, yace do u feel any pain? Na girgiza masa kai, hannun yaja da qarfi saida nayi er qara, yace very good ur hand is ok now, saidai karkiyi aiki mai wahala dashi ko ki dauki abu mai nauyi sai nan da 1week, na gyada masa kai, allura ya ciro zaimun ya lura banyi breakfast ba, ya ajiye eat your food first, idan kungama akirani namiki alluran den u can go. Mom ta kallemu wato abincin kuka aje kuna shan soyayya ko? Duqar da kai mukayi tace oya kabata abincin da sauri karku batawa doctor time, spoon ya dauka ya fara bani ina kar6a, saida na qoshi na nunamasa ya isa, ya gogemun baki ya bani magani ya fita kiran doctor. [9/14, 4:47 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah Abdul 9⃣5⃣ Da assubah ma bayan munfarka nayi 'yan karance-karancena da nasaba nagama, kuma nidai nagaji da kwanciya tashi nayi, na kama hanyar fita ya bini da ido kawai, dakin kausar naje na riqa buga mata qofa, tataso tana tsaki ta bude, koda ta bude na ingejeta na shige ciki, mitsitstsike ido tayi, au amaryar broda ya haka tin da safe? Sai kuma tafara dariya, harara na watsa mata, toh ni meh nayimiki kuma? Nace tambayata ma kike? Dariya ta saka toh miye laifi dan mata ta tafi gun mijinta? Nace nidai karki qaramin haka, cewa tayi sister do u want to get close to broda or not? Nace inaso mana tace toh kina nisanta kanki dashi taya zaki samu kusanci dashi? Nace sis nifa Allah tsoronsa nike somtimes, tace gwandama ki daina, danni yanxu ma nafara, duk wata hanya da zata sa kusamu kusanchi sai na ingizaki kinbita, cewa tayi ki tashi ki koma ni bacci zankoma, gado taga na haye na kwanta murmushi tayi ta rufe dakin ta dawo itama ta kwanta. Da safe bayan kowa ya tashi munfito, muka gaida su mom, restsurant dinda ke hotel din muka sauka, mukayi breakfast, sannan muka fito yawon buda ido. Munje amusement parks kala-kala, da ordinary parks ma irinsu, cross maiden, horniman circle gardens, joseph baptista garden da sauransu. Muna chan mom ta tuna da zuwa asibiti tace muje da khaleed, bayan anyomin allura ne, horniman garden din yace amaidamu, zuwa yayi ya samu wuri yayi zamansa, nima haka sai kallon mutane da nike, khaleed harda beach saida yasa aka kaimu, shiga ruwa yayi yanata wasa nikam ina nesa akwaini da tsoron ruwa. Bamu muka koma ba sai yamma kausar sai tsiya take mana, wai dama neman hanyar guduwa mukeyi, shine daga zuwa asibiti mukaje shaqatawa, mom tace kada ki samusu ido, mutum da matarsa, idan angama biki ma ae dole suje honeymoon, a raina nace honey wahala dai, wannan idan na yarda mukaje honeymoon guduwa germany zaiyi ya barni, ina kwance bana motsi ya tafi bare ina qalau. Mama tace ae dama ambar zancen bikinnan tinda abun yazo haka, muna komawa ta wuce gidanta kawai, tinda angama gyara komai, mom tace wai hakan yayi ameerah? Gyada kai kawai nayi, khaleed yace ae ama daina zancen wani biki. Kausar tace broda meh kake yiwa sauri ne? Ko munyi bikin ae dole akai maka matarka, harara ya watsa mata ta basar, mom nifa Allah gwanda ayi bikin komai fa munshirya, kuma kinsan kowa cemasa muke biki sai sister inlaw ta warke, mom tace nima dai haka nagani, gobema shopping zamu dan har indian night sai anyi, kausar tafara ihun murna, mama tace itadai tagaji zata shige, mom ma ta miqe, kausar ma ta tashi, jawo hannunta nayi, nace miye naki na wani dagewa sai anyi biki? Jawoni gefe tayi sis we need dis, qawayen salmah nakeso na turawa hotinan biki, nasan dole su tura mata, idan taji haushi may b tace ma ta haqura dariya mukayi muka tafe, khaleed daki shima ya wuce, niko nabi kausar saida muka kai bakin qofa ta shige da sauri ta turo qofa, ta barni waje turus, dole na miqe na wuce dakin khaleed, qwanqwasawa nayj, yace waye? Haushi naji kamar ince ubanka ne, nadai daure nace nice, ya taso ya bude cewa yayi ae na doka a dakin kausar zaki kwana dan naga dazun ma chan kikaje, murmushi nayi a raina wato saida ya biyoni yaga inda naje kenan, yau ma gado ya barmin ya kwana a sofa. [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 9⃣6⃣ cikin en kwanakinnan biyu da suka rage mana mun zagaya ko'na munbuda ido, munje cinema kala-kala munyi kallon sababbin films masu fitowa, Biggest shopping mall da ke mumbai kusan duk saida muka zagasu, irinsu , high street phoenix dake lower parel mumbai, Inorbit mall dake malad, infinity mall dake new link road mumbai, Oberoi mall dake goregan east, Artria mall dake worli, Mun jibgo kaya kamar zamu buda shop, su suhaila dake gida ma duk mun za6a musu. Yauma itace last day dinmu a india, wasu shagon jewelries mukaje da designer saries, india akwai designer jewelries both passion jewelries and gold, mom duk sarqoqin da ta zubamin a lefe, saida ta kwasarmin wasu designer gold, wai wa 'yannan na biki ne, tanaso nayi looking like a princess, mama tayita hanata mom tace itada ' yarta, mama taja bakinta tayi shiru tana mamakin irin wannan soyayya da mom keyimin, itama kausar ko kishi batayi sai za6amun take. Kausar ce ta jawo hannuna ta hade da na khaleed wani shock naji har tsakiyar kaina, ba shiri na janye, tsakiyarmu ta shiga ta jamu sai gefen saries, gasunan masu shegen kyau, wai mu za6a irin na celebrities ne, chan ta jawo wani, sis Allah wannan zaiyi masifar yimiki kyau, kinga wannan irinshi ne naga priyanka chopra tasa a wani award night da akayi last year, dariya nayi toh priyanka kikace ni miye hadina da ita, tace ae sis kinfita kyau da diri saidai ta gwadamiki hasken fata, nace Allah kausar idan mutum ya dauki zugarki sai yafara girman kai, nace ae sai ki gwadamin yanda zansaka saree din, wata mata data gani a shop din taje ta taho da ita, wai dan Allah ta nunamana yanda ake saka saree, itako da murnarta ta amince wani daki da ake chanja kaya ta shiga damu, muka cire na jikinmu, muka saka er qaramar rigar saree din, amma munbar dogon wandonmu da yake ciki, ita ko ta laulaya mana ta liqe, kausar ta walwalemin gashin da ke bayana ya zubo, harda fita ta dauko bindiya wannan da aka maqalawa a goshi ta doramin, ts jani mukaje gaban mirror, nikaina saida na kasa gane kaina, saree din ba qaramin kyau yayi mana ba, idan kaganmu kamar indiyawan barin ma kausar da take fara tas sai ta sade dasu, nima din namafi wasu indiyawan haske, dan suma da baqar fata a cikin su, jawo hannuna kausar tayi muka fito, kowa ya kallemu sai kaji yace wow u ar looking very beutiful muko muce thanks, khaleed taje ta jawo sai qaremata kallo yake, tace broda look there, sannan ya kalloni, quramin ido yayi 4 quite sometimes, kausar sai kallo take tana dariya, shi baimasan tanayi ba, saida ta kirashi broda, broda, ya kaga matar taka? Basarwa yayi, wannan wane haukane maza kuje ku chanja kayan, kausar ta ja hannuna zo muje wurinsu mom, gabanmu ya tare ba cewa nayi kuje ku cire kayan ba? Su mom suka iso wurinmu, khaleed ina su ameeran ne? Nuna mata mu yayi, dariya mom tayi wai en matanane bangane ba, wow wlh kummafi indiyawan kyau, mukayi dariya, er qaramar camera da muketa daukar pics da ita duk inda mukaje ta fiddo, ta fara daukarmu hotuna, taba khaleed taja hannun mama suka shiga cikinmu aka dauka, khaleed mom ta tura akayi mana mu 3, kausar ta jaye akafara daukarmu mu 2, kausar sai wani zuwa take tana maqalemu tana bamu style mom na dauka, mom sai cewa take muyi smile, khaleed dole tasa yakeyi har aka gama, kausar ta kar6a tana dubawa, wow mum wlh munsamu na sourveniers sunyi kyau sosai, mom tace ku wuce mutafi hakannan dare ya fara yi, kuma morning flight zamu dauka zuwa 9ja, muka wuce muka koma hotel kowa ya gaji dakinsa ya wuce direct. Nima banyi wata gardama ba na wuce dakin khaleed dan nasan kausar ma bazata bari inje nata ba, muna shiga muka jibge kaya sallah kawai muka dora, kafin intaso khaleed ya haye gado, tsaye nayi ina kallonshi nayi rau da ido alamun kuka, kalloni yayi kinga ni nagaji da kwanciya a sofa yau kije ki kwana achan, hawaye suka zubomin na ture baki alamun shagwa6a, nifa Allah bacci baya daukana akan sofa, ya dade yana kallona sannan ya matsa a gadon ya koma qarshen gado, ga space nan ki kwanta, ae ba cinyeki zanyi ba, idan kuma bakyaso kisan yarda zakiyi, danni dai yau bazan kwana a sofa ba, nagaji da tsayuwata yama juyamin baya, pillow na dauka da wanu bargo nasa a tsakiyarmu, sannan na kwanta, shidai murmushi yayi dan yaga abunda nayi, wannan quruciya ke damunta, idan har nayi niyar wani abu da ita, ta isa ta hanane? Ni ba abunda zai shiga tsakanina da ke, my body and heart na salmah ne, ya runtse ido yayi baccinsa. [9/14, 7:06 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 9⃣7⃣ Cikin dare sanyi ya addabeni bansan lokacin da na janyo bargon da ke a tsakiyarmu ba na shige, shima gogan wurinsa hakane jaye pillow yayi ya shiga bargon ba tareda munsani ba. Sai lokacin sallar assubah alarm dina ya fara ringing, na miqa hannuna na jawota na kashe, dan mun bala'in gajiya jiya da yake last day dinmu a india kenan, ji nayi kamar wani abu ya tareni, bude idon da zanyi nagannin cikin jikin khaleed shiko ya dora hannunsa a jikina, baccinsa ma yake bai damu ba, duk lokacin da nayi yunqurin tashi sai naji kamar ya qara riqeni, salmah don't leave me plz naji yana fada, iya qarfina nasa na tureshi a dan tsorace ya tashi zaune, miye haka yacemin? Nace cikin fushi idan zakayi mafarkin budurwarka kayishi kai kadai kar ka sake ka qara sakoni a ciki, nayi fuu na shige toilet, shidai sake baki yayi ya bini da ido, batareda yasan meh nake nufi ba, sai a lokacin ya lura da bargo da pillow da ke tsakiyarmu duk babu, murmushi yayi wato mafarkin da nike ina rungume da salmah wannan yarinyar na rungumo shiyasa take masifa tsaki yaja. Toilet na fito muka hada ido na watsa mai harara harda murguda baki, shidai dariya yayi ya tashi ya shiga Toilet din, koda ya fito ina sallah, shima gefe yaja ya kabbara tashi, karance-karance na nafara shiko yana saurarena dan yanajin dadin karatun ameerah. Sai da gari yayi haske na miqe na debi kayan da zan chanja na shiga wanka, ns fito shima ya shiga, ina tattara kayana ya fito yana shiri, gunguni yaji inayi, idan mutum bai iya bacci ba meh ya hana ya kwana akan sofa, haka kawai a riqeka ana kiranka wata salmah naja tsaki, qyaleni yayi, saida na kwashi kayana nakai bakin qofa naji an tazgoni na fado jikinsa, dago kaina yayi mi kike cewa yanzu? Nace ni bance komai ba, yace kindauka banjiki bane? Nayi qarfin hali nace toh kaji kuma kake tambaya? Qara matseni yayi saida nayi qara wayyo mamata, yace angayamiki son ta6a jikinki nake? Nifa dake da kausar kallo daya nike muku, so kishiga hankalinki idan inada niyan yin wani abu dake, tin ranarda muka fara kwanciya a dakinnan da nayi, kausar ce tayi gyaran murya muka waigo da sauri, sakina yayi ya koma daki, tace inaga nazo a wrong time dama mom ce tace ku fito kunsan jirgin eight zamubi, jakarsa ya dauko ya ingije kausar ya fita, hugging dina tayi, sister just gist me kice har soyayya tayi qarfi, jakata naja ta kar6e just tel me mana, nace bafa abunda kike zargi bane, na gayamata abunda ya faru tin jiya da dare har zuwa yanzu da ta samemu a haka. Kausar dariya harda faduwa tace sister inlaw wato kishi ne kika kasa controling, nace mata Allah kuwa inajin yana kiran sunan salmah wani qarfi ya zomin na tureshi, haushin abunne baigama sakina ba nafara qananan maganganu, Allah ne ya kawoki da yau inaga sai nasha duka hannunsa, dariya take tayi, jawoni tayi sister gayamin gaskia da bai ambaci sunan salmah ba zaki barshi a jikinki kenan ko? Gaba nayi nace gulmammiya kyaji da gulmarki, jawo jakata tayi ta rufo dakin muka sauko qasa. [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 9⃣8⃣ koda muka sauko qasa kowa ya fito mu kawai ake jira, aka fara zuba kaya a motor, gaidasu nayi suka kar6a, mom tace khaleed kaje da matarka asibiti ku samemu a airport, nace mom ni na yafe alluran mutafi kawai, cewa tayi daughter baxanyi wasa da lafiyarki ba, gashi india ba nan da birnin kebbi bane, bare mu dawo idan wani abu ya sameki, nace mom bafa abunda zai sameni m all fyn, allura daya ta rage fa kawai, tace we can't take d risk khaleed meh kake jira ja hannunta kuje, hannun nawa yaja mukaje muka shiga cab, da sauri na matsa gefe, kallona kawai yayi ya girgiza kai, a haka muka isa asibiti doctor yayimin allura muka kama hanyar airport, koda mukaje duk angama clearance boarding kawai ya rage, bamuyi zaman 10 minutes ba akafara kiran passengers, muka shiga jirgi muka daga sai nigeria. 🍒🍒🍒NIGERIA🍇🍇🍇 Muna saukowa jirgi na hango motoci sunzo tarbarmu, ciki kuwa harda kawu shehu da iyalansa, muka shiga motoci direct gidansu khaleed muka wuce, muna shiga su suhaila suka sheqo da gudu sukayo kaina, mom tace kungafa karku illatamin 'ya batayi qwari ba har yanzu, akayi dariya, siyama na hango ta raku6e a baya nace siyama zo mana, sai lokacin ta sheqo da gudu ta rungumeni, harda hawayenta na goge mata, nace baby siyama ya haka da kuka? Tace ba frnds dinane ke cewa kin mutu ba, wai ba mai qara kawomin chocolates, dariya kowa yayi, nace toh ae yanzu gani kinganni da raina ban mutu ba, kuma ko yanzu nazomiki da lots of chocolates, khairi yace nifa? Nace kaima haka suka fara tsalle, dady yace ku wuce ciki mana kukazo nan kuka tsaya, sannan mukayi cikin gida. Dady yace ga abincinku akan table, da sauri kausar ta miqe dad kamar kasan bamuyi breakfast ba, ta wani zuwa ta fara bude flask din abinci wow dad my favourite pepper chicken nayi missing home wlh, dad kasan tunda mukaje snacks nikeci sister inlaw kawai kecin abinci wai ita abincin india yayi mata. Mom tace hajiya kausar ba ko gayyata saikace ke kadai ke jin yunwa? Mom tace ku taso muje kan table, kowa yayi kan dining table da yake babbane, saratu da hanzari tayi kusa da khaleed ta zauna tanamasa wani kallon yaudara, shiko baimasan Allah yayi ruwanta ba, tsakiyar su mom naje na zauna, mama tace mu sa'aninki ne? Kije ki zauna kusa da mijinki, na ture baki ni wlh mama kindaina so na, mom tace kibarta kawai sai ta nemeki ta rasa, ai kuma ba kusa da ke kadai ta zauna ba, kusada mom dinta ta zauna, mama tace Allah dai yasa ba ita kadai na haifa ba, ko yanzu ga 3 nan agabana akayi dariya. Bayan angama cin food ne mom Tace tohfa biki nan da sati daya duk mai wani shiri yaje ya fara, su siyama suka dau tafi suna murna, haj asabe ta ta6e baki, kawu yace ae ni nadauka dakinta kawai zata wuce, mama tace nima dai haka nace dasu sukaqi yarda mom tace ae munriga mungama shiri baza'ayi kashe kudin banza ba, baban khaleed kai kasan wannan shine bikin aure na farko da zamu fara a gidannan, kema maman ameerah hakane wurinku, baikamata ayishi lami ba wani abu ba, Bayan an daura aure ba dadi ae baikamata akai amarya ba wani farinciki ba, dady yace hakane ayi bikin kawai, su kausar harda kida table da spoon akasa dariya. Mama ta miqe suhaila, fatima, khairi ku tashi mutafi, mom tace tin yanzu? Mama tace toh meh muke jira kuma, nima miqewa nayi nadau bags dina, mama tace waike ina zaki? Nace gida mana tareda ku, mama tace ae yanzu kinga gidanku nan, ba inda zaki bimu, kukan shagwa6a na fara harda buga qafa ni wlh a'ah gida zanje, mom tace daughter bakison zama damu ne? Duqar dakai nayi, kausar tace mom kinsan ae ba'a kaita ba tasa dariya, haj asabe tace muma dai idan ta zauna wannan abun kunya ne, kowa yasani anan aure kawai aka daura ba'a kai yarinya gidan mijinta ba sai kawai ace ta zauna? Dady yace kudai mata halinku sai ku, miye na wani abun surutu ko ta zauna ba gidan mijinta bane? Amma ke ameerah ku tafi din kawai aidai nan da sati daya za'ayi bikin sai akawo kin, yace khaleed ka amince da haka? Yace bakomai dad yace toh ka jawo mota ka kaisu gida ya fita waje jawo motar. [9/14, 7:08 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 9⃣9⃣ Khaleed na fita saratu ta bishi waje, khaleed ta kira sunansa ya waigo yana mata wani kallon raini, tana wani karairaya ta iso wurinshi tana wani kashe ido, shi dariya ma abun ya bashi ita wannan kodaddiyar nan meh take nufi ne? Ta qaraso wurinshi sai cewa yayi lfy malama, ta zuge zip din jaka ta fito da wani abu anyi wrapping ta miqamasa, ga wannan yace na menene? Tace gift ne da naso na baka na murnar aurenka da er uwata amma bansamu dama ba kuntafi india, tana wani kashe murya, ta6e baki yayi ya kar6a ya juya angode, yaje jawo mota itako ta bishi da wani kallon qurullah wannan guy ya hadu ta ko'ina dolene na mallakeshi, ni bansan meh wannan matsiyaciyar tayiwa Allah ba ya bata wannan hadadden guy din, fitowa mukayi, su kausar dauke da kayanmu, kausar ta radamin a kunne meh wannan figaggiyar take a waje? Nace oho idan ma mijina ta biyo qwalelenta nima nan fama nike da kayana, mukayi dariya. Mota ya kawo su kausar suka bude boot suka fara zuba kaya, mom tace son kafito ka tayasu mana, yafito riqe da gift din da saratu ta bashi, kausar tace broda miye a hannunka? Wurgo mata yayi kar6i idan kinaso, itako tafara yage leda wasu turaruka ne guda biyu da agogon maza, kausar tace broda ae duk kayan mazane, yace ki kaiwa saurayinki, tace ni wani saurayine dani? Sai tace ohh yes bari mu baiwa yaya saeed kawai dama yace sai munbashi tsaraba nace ai kuwa. Saratu haushi, ta cika tayi fam kamar ta fashe, sai cewa tayi mom dad kuzo mutafi mana, sukayi sallama suka juya, nace saratu bazaku bari muqarasa gida ba? Tace no munada baqi ku tafi kawai zamu shigo, taja hannun uwarta, ita kuma tace meyasa kikace haka? Kinga kuwa manyan bags dinda ake loda musu kibari muje mu yagi rabonmu, saratu tace ni mom fa na tsani ganin khaleed da ameerah a tare, kawu yayi dariya a tunanina ai kema macece sai kiyi qoqari ki qwace mata, dan ita yarinyar ma wata bagidajiya ce ba wayewa a tare da ita, haj asabe tace wlh kuwa kedai sara baby karki damu ni zan qara koyamiki kissa iri-iri suka sheqe da dariya, saratu kam ba'ayi sa'ar uwaye ba. Mota kausar ta turani gaba, su mama na baya muka dau hanya, bamaicewa qala, har muka isa gida, kowa ya fito muka fara tattara kaya zanshige gida, mama ta watsomin harara haka zaki tafi bazakiyiwa mijin naki sallamah ba? Komawa nayi na bude mota na zauna, har saida suka kwashe kaya suka shige, zaune muke zugum sai chan yace malama idan bakida abun fada ki fita ki bani wuri inada gun zuwa, fita nayi da qarfi nima din ba dan mama ta dawo dani bane toh meh zammaka dama? Na shigewata gida ido ya bini dashi saida na 6ace yayi dariya ya girgiza kai wannan yarinya akwai quruciya mutum zai zauna da ita kodan yasha dariya ya juya ya tafi. [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣0⃣0⃣ Shiga gida nayi na fada dakin mama, su suhaila agaya musu labarin india, nan muka zauna mukasha fira daga bisani na miqe nace kunga nagaji bari na kwanta na huta, tsarabarku sai na tashi, daki naje na kwanta inata mamaki yau wai nice da auren khaleed abun kamar wasa a haka har bacci ya daukeni. Sai kusan magrib na farka na shiga toilet na watsa ruwa, wata qaramar riga da wando na saka, na zunbulo hijabina nayo dakin mama, nayi sallah sannan nace mama zanje gidansu saudah na gaida mama sannan na kar6o number saudah ko ta mijinta, mama harara ta watsomin da izinin ubanwa? Ko kin manta da aure akanki ne? Kije ki tambayi mijinki ko kuma suhaila taje ta kar6omiki, haushi wai shikenan yanzu saida izinin khaleed zanfita? Dawowa nayi na zauna dan idan na kira khaleed tunanin wani abu nake nema zaiyi niko koda ina sonshi bazan bari har ya gano ba bare yayimin wulaqanci, cewa nayi suhaila jeki gidansu sauda kice ina gaida mama kuma dan Allah ta bani number ta ko ta mijinta, suhaila ta tafi, na jawo bags na fara bude kayana ina fito musu da tsaraba, kusan kowa kala biyar namasa masu kyau da tsada, harda aliyu da bayanan, su fatima da suhaila harda jewelries, saudah, khadijah nasir, da aunty fareedah ko wannensu wani tsadadden materia da jewelries na siyo musu. Sallamah mukaji maman saudah ce ta shigo tareda suhaila , tace ae nayita zuwa gidannan ba kowa tinda saudah taji hadarin qawarta kusan kullum sai ta kira naje na dubo yakike, kamar tayi tsuntsuwa tazo amma mijin ya hana, nace Allah sarki saudena nima tana raina mama bani number ta kiga na kirata, wayarta ta miqomin na kwashe number na tashi nayi daki na kira saidah. Tanajin muryata ta miqe tsaye dan Allah ameerah ce ko kunnena kemin gizo, dariya nayi nice qawas kukan farinciki ta fara, qawas wlh Allah na shiga damuwa kusan kullum sai nayi kuka, kinga usman har kishinki ya fara wai nafi damuwa dake akanshi, dariya nayi kwantar da hankalinki qawas na warke sarai, nan muka dinke da firar duniya tace qawas naji mama tace wai andaura aure, nace ba wai bane qawas yanzu nazama mrs khaleed m khaleepha, tace wato kedai saida kika dage da auren nan, nifa ina jiyemiki abunda zaifaru gaba, nace qawas aure dai anriga andaura yanzu sai ki tayani addu'a kawai, kuma wanin satin za'a fara biki, kuma dole kizo, tace ba dole sai maigida ya yarda, nace kibanishi toh ta miqamasa waya, muka dinga fira yana gayamin yanda matarsa taso ta zautu kaina, nikuma sai dariya nikemasa, nace zakabarta tazo biki nxt week ko? Yace wannan ai dole ne idan bamuzo ba ma bazata bari na zauna lfy ba, nayi dariya mukayi Sallamah akan sai sunzo ana gobe za'a fara bikin. Dakin mama nakoma na gayawa maman sauda mijin yayarda zasuzo ana gobe biki, tsarabar saudah na bata ita kuma na bata turaruka tayi godiya ta fita. [9/14, 7:13 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣0⃣1⃣ Shirin biki ake zangu-zangu, rabon kati da anko kawai muke dan wasu qawayen ankon ma kyauta aka basu, gashi muna shiga skul dan anfara lectures. Ana gobe za'a wanke amarya saudah tazo , dan abisa al'adar sokotawa sa lalle ake farawa sannan da dare a wanke amarya sannan duk wani event ya biyo baya, bayan an wanke amarya, murna wurinmu ba'a cewa komai, duk inda ka ganmu mu hudu kausar, saudah, khadijah nasir da ni, kausar ma kaya kala daya ta dinka musu su 3 na biki dan na amarya special ne. Ansaka lalle an wanke amarya, yau su kausar suka kaini wurin dilka da qunshi gun wata er sudan, an zanamin lallen da kowa ya gani sai ya yaba, anyimin gyaran jiki sai sheqe da qamshi nike zubawa idan ka ganmu basai ka tambaya wacece amarya ba ka qyalli da qamshin da nike na musamman, aunty fareedah matar yaya saeed itama ba'a barta abaya ba, dan gwana ce wurin iya tsara kwalliya da ado, duk wani kayan gyaran jiki ta samo sai ta kawomin cikin en kwanaki qalilan muka dinke da ita, nasha kayan mata band adadi dan dama mu sakkwatawa munyi suna a wannan fannin. Indian night aka fara yi, ranar ango da amarya ba'a cewa komai, duk wanda ka kalla maza da mata kowa yayi shigar indiyawa, ranar kowa kaji namaste namaste da wanda ya iya indiyancin da wanda bai iya ba kowa kwa6awa yake😂😂😂 Nidai DEEJAH DA CHUCHUN GAYE da na nemo er rakiya ba'a ganemo dama biyarsu da nayi india na kwaso mana kayan india, ranar an chashe da kidan india, chuchu ansha rawa dama gwana ce a fannin, duk da da abincin wurin na indiyawa akayi, munci su roti, gulab jamun, parathas😂 harda drink ansha su madara da kheer chuchu sai zubawa take a jaka ina hanata bafa yau za'a gama bikin ba sauran gara na zuwa. Next day kuwa Arabian night mukaje, amarya da ango kai ka rantse larabawa ne, kowa ka duba haka muka shiga taron kamar a dubai, sai zuba larabci ake ana huduba, ranar dai wa'azi muka sha chuchu an kame wuri daya kamar ba ita tasha rawa jiya ba, chuchu bata fara motsi ba saida taga anfara zuwa ana serve yourself, yau kam abincin wurin nama ne zallarsa da madara, gasassun raguna, kaji, farfesu da pepper chicken kala-kala, ni da chuchu munga banza sai ci muke muna zubawa jaka saida mukayi hmm ba wurin sakawa, nace chuchu ba banza muke qara qiba ba, yau ae munqara 10kg😂 tace ke wlh sai munchi irin wannan ba kullum take samuwa ba idan munje gida muyu burning calories da exercise, chan naji ana zubo larabci na dau biro na da takarda nayi wurin, ameerah da khaleed ne ke zabga larabci suna godewa jama'a, duk na dauko biro na rubuta abunda suke cewa maiqon da ke hannuna kesa biron ya su6uce har suka gama ban rubuta komai ba, ga qwaqwalwar bata ja bare na riqe na rubuto muku😂 chuchu kuwa na wurin nama bare ta tayani. 😂 [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣0⃣2⃣ Yau kam mothers night za'ayi, chuchu ana sallameh magrib sai sallamarta naji, nace kedai chuchu akwai son bikin tsiya wlh, kayan jiya ne a jikinta😂😂 nace wlh chuchu ba zaki bini a haka ba, dress code dinfa lace ne da filawoyi maroon da head maroon too, wani lace dina sabo na dauko na bata da yake shigen anko ne na bata ta saka, ni kuma na saka ankon da yake na samo, cewa tayi muyi gidansu khaleed, nace a'ah wlh gidan amarya zamu talakawa sunfi yawa a chan baza'ayi saurin dagomu ba, naja hannunta muka tafi. Koda mukaje aunty faredah tana tsalawa amarya kwalliya nida chuchu sakin baki mukayi muna kallo, amarya ta tsala kyau kamar a saceta a gudu, fitowa akayi akafara shiga motoci da sauri chuchu ta jawoni muka afka wata mota, ashe motar saratu ce, wani kallo ta watso mana ku kuma daga ina🙆🏻 na radawa chuchu a kunne wannan wlh batada mutunci kizo mufita kawai, chuchu tace wlh ba inda zamufita kinaga duk ancika motoci, kuma ko munje mukadai bamuda gate pass, wayancewa tayi mufa course mate din ameerah ne baki ganemu ba? Tsaki tayi sannan taja motar da wasu fitsararrun qawayenta daya gaba daya baya, pinnacle hotel muka nufa angyara wurin yasha ado kai kace new york ne chan muka samu kujeru a gaba-gaba muka kame, Chan sai ga amarya da ango sunfaso taro kamar taurari sai walqiya suke makada da mawaqa suka haukace da kida, ranar munga manyan mata, ranar anyi ruwan dollers nida chuchu kuwa duk wadda ta fado kanmu dafeta muke mu tura bag😂 Wannan biki Allah ya maimaita munchi munsha mun samu kudi har na gida ma sun shaidah. Washe gari kuma frnds evening akayi, ranar 'yan mata ce kawai, a shukrah coral hotel akayi, ranar su kausar da qawayenta, su khadijah naseer su saudah su aunty fareedah sun nuna bajintarsu, ranar harda nida bana rawa gun biki saida na taka, su nura m inuwa, umar m sharif, adam zango sun baje kolinsu nera tayi kuka, damar abun duk liqin da akayi amarya da ango ake tarawa kudinsu, su mawaqa da makida jinga ake dasu a biyasu. Yau kuma walima zamuje mu kwashe wa'azi, ameerah ansha alkyabba kamar diyar sarkin makkah ko'ina tayi binta ake da camera akan kyaun da ta zuba, malamai sunyi wa'azi mai ratsa jiki kan muhimmancin aure da hakkokin miji akan matarsa, nida chuchu ma munyi addu'a Allah ya kawo mana nagari muma mu raya sunnar ma'aiki, ranar mun kwashe sourveniers turamen atamfa tsadaddi hijabai, sallayoyi, littafan addu'oi irinsu hisnul muslim 4o rabbana, da alqur'anai aka raba, da littafai da calenders masu dauke da hoton ango da amarya sunsha kyau muka kwasa. Tohfah laifin dadi qarewa inji chuchu yau dinner kawai ta rage mana mukai ameerah gidanta, wurin dinner ma ta qayatar, mc da djs sun taka rawar gani wurin qayatar da taron, khadijah nasir tayi tarihin amarya saeed kuma na ango, angayyato comedians irinsu basket mouth sai bada dariya suke, khaleed idan kuka gansu bazaku ganeshi ba yanda yake kwasar dariya, kausar ta samu dama sai daukarmu hotuna take tana tarawa, jira take agama ta turawa abokan salmah, dama duk even sai ta bari muna maqale muna dariya take daukar hotunanta dan duk wanda ake a taron ita bazasu biya buqatarta ba, tafiso ta dauko wanda dagani za'ace dis are happy couples, yauma mun kwashi banza mun tura a jaka sourveniers har saida muka fara ba wasu, angama aka watse muka dunguma kai amarya. [9/14, 7:17 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣0⃣3⃣ Mun dauki amarya ameerah muka kaita gidan angonta dake abuja road, chuchu kallon gidan take kamar er qauye wai wannan ba paris mukazo ba kuwa? Nace a'ah italy ne, nima nayi nawa qauyancin tin a jere, amma yau sai naga gidan ma yafi kyau kamar anchanja, koda muka shiga ciki duk inda ka taka qafarka kamar ta nutse, komai na gidan black and white ne, nace lallai kawu ba qaramar dukiya ka zuba ba dole haj asabe tace anmaka asiri, na jira naga yanda zata kaya, ankai amarya dakinta anmata huduba sai kuka take kamar ta shide, abokan amarya da ango sai tsokanarta suke, suka gama siyen baki dubu dari biyar aka ba qawayen amarya, sannan suka miqe zasu tafi, ameerah ta biyosu da gudu ta riqesu, wai bazasu barta ba, kausar tace su tafi ita zata zauna, saura suka wuce ita takoma da ameerah daki, cewa tayi la kinga khadijah nasir ta tafimun da wayata bari intashi in kar6o kan suwuce, ameerah ta riqeta wlh wayau takeso tayi mata, jakarta ta cire da mayafi ta aje kinga dai ba inda zantafi ba mayafi bari na leqa na kar6o na dawo, ta gyda mata kai, ita kuma ta fita da gudu, kausar ta fada mota kuja mutafi kawai, sukace ina mayafinki da jaka? tace gobe idan munzo na dauka, wlh idan ba haka ba bazata bari na fito ba, sukasa dariya, khadijah tace nikuwa kinmin tsiya wlh kinsan medical glass dina na cikin bag dinki, kausar tace toh makauniya bari zanmiki dan jagora yau, suka fashe da dariya su duka, kausar tace bari nakira bro na gayamasa bataci komai ba tin da safe ya tilastata taci wani abun, khadijah tace mutum da amaryarsa har sai kingayamasa? ai yanzu haka yafara ciyarda abarsa, saudah da kausar dai sunsan komai murmushi kawai sukayi, kausar ta buga wayar. Nida chuchu muna raku6e wurin naga khaleed ya doso, nace chuchu jirani mana tace itafa tagaji wurin dauko rahoton JANAN zata tafi, nace ae dole kice haka tinda anqare biki gara ta qare, wlh idan akazo bikin suna, saidai na nemo su marwa da dijah sheriff su rakani, tace eh din taji dai, tayi gaba abinta, ni ko na qara gyara tsayuwa na daukomuku rahoto. Wayarsa tayi ringing ya dauka har ya kama hanyar dakinsa, kausar ce ta gayamasa ameerah bataci komai ba tin safe, ya kashe wayar ita ba jaririya ba sai an lalla6ata yaja tsaki, mota ya koma ya dakko ledojin kaji da lemo da ya manta dasu ya nufi dakin ameerah, turawa yayi ya shiga itako ta dauka kausar ce, ta taso tsaye da sauri ba tareda ta lura da wanda ya shigo ba dan kanta na a mayafi duqe, tasowa tayi ta rungume khaleed😳 shine kika wani shanyani? na dauka ko kingudu kin barni, tanata faman kuka, shi ae duk ta kashe masa body, sun dade tsaye a haka sannan yayi qarfin hali yace kukan meh kikeyi ne? A razane ta sakeshi tayi baya da sauri ta bude fuskarta, sun dade suna kallon juna da idonta da suka kade sukayi jawur, ledojin ya ajiyemata, kausar ta gayamin bakici komai ba tin safe, gashinan ki daure kici ko yunwa ta illataki, kuma ni bansan kukan meh kikeyi ba, ni nasha gayamiki ba abunda zammiki keda kausar duk daya a wurina, na zun6ure baki ae ba kai aka rabo daga gidanku da iyayenka ba, aka kawoka kazauna da wani ba, ta6e baki yayi, da kinsan baki shirya rabuwa da gidan naku ba kika wani shirya plan din aure? Shi wanchan saurayin naki, da idan ya aureki gidan naku zai barki? Nace ae dai kaima plan din nawa ya taimakeka, dan da yanzu husnah aka kawo maka, tsaki yaja kici abinci idan zakici, idan kuma kukan zakiyi sai kiyita yi, ya fita ya jawomin qofa. Fadawa nayi kan gado, na cigaba da kukana, wayyo ni ameerah , wannan wane irin aure na saka kaina? A wurina aure nayi amma a wurin mijina kuma is jst like a game, it wil b over in no tym, yunwa ta tasomin har jikina ya fara rawa kan yunwa, na jawo ledojin da ya ajiyemin, kajine da lemo naci nasha nayi qat sannan na samu nutsuwa, toilet na shiga na hado alwala nayi nafila raka'a biyu ta godiya ga Allah, da addu'an Allah ya dorani akan mijina ya samana albarka, na shafa na rufe dakina nayi addu'oin kwanciya na kwanta. [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣0⃣4⃣ khaleed ne kwance a dakinsa wai yau shi aka daurawa aure amma bada DREAM GIRL dinshi ba, waya ya dauka ya kira salmah, ta daga shine zaka cemun yarinyar da zaka aura ba sonta kake ba? Yace toh meh kika ganine? Wannan pictures da aka turomin duk wanda ya kallesu yasan happy marriage kayi, qawayena sai dariya sukemin wai an kasani, ni kuwa kasan ba macen da ta isa tayi takara dani, barema kai da nake ganin na mallaka tintini, duk cikin masifa take masa wannan maganar, yace haba sweatheart just calm down mana, ni naki ne tintini har yau har gobe, tsawa ta dakamasa , karka isheni da wannan dadin bakin naka, yace shima cikin masifa salmah ya kikemin tsawa kamar wani yaronki? Yau fa aka kawomin amarya amma yanzu gashi ina waya dake, idan amaryar tawa ta wani dameni yanda kike tinani, a daren yau har zan iya kiranki? Shiru tayi 4 sometimes toh shikenan, inanan dawowa nan bada dadewa ba, nd dat sooner dan you think, kuma idan nadawo take nakeso ka saki yarinyar nan, daz d only way da zaka tabbatar min da cewa dagaske ni kakeso kuma ba wani damuwa da ita kayi ba, yace shikenan ni ko gobe ne kidawo a shirye nike da rabuwa da ita, dama ae yarjejeniya mukayi na gayamiki. Kashe wayar tayi tana murmushin mugunta i'm sorry khaleed, ni aure baya gabana yanzu, amma dole ne na nunawa qawayena ba namijin da ya isa ya latsani, kuma ba macen da ta isa tamin qwace kamar yanda suke tinani, dama iyayena sun dameni akan na dawo, zan dawo gida just 4 d mean time, idan nayi auren na tabbatar musu da ni na kai mace later na dawo germany na cigaba da harkokina. Tohfah kunji salmah zata auri khaleed just 4 showup, dan kawai ta nunawa qawayenta ta isa, niko deejah ga khaleed ina kallo sai murna yameyi salmarsa zata dawo soon, nidai idone nawa naga yanda zasu kwashe. Waya ya daga ya kira saeed shikam har yayi bacci, wane banzan ne yake kirana yanzu? Jin muryar khaleed tasa ya miqe zaune, lfy angon ameerah? Ko wani abune yasameta yanzu? Khaleed yace relax my man good news na samu shiyasa nakasa barin har gari ya waye, saeed yace wow ashe komai ya kammala ka samu amaryarka yanda kakeso congrat my man, kasamu ruwa da dettol ka gasata kafin inzo, khaleed yace kai banson iskanci fa, ina gabas kana yamma, meh kake tunanin zai shiga tsakanina da wannan yarinyar? ko ka manta kan yarjejeniyar da mukayi aure ne? Saeed yace toh uban meh zaisa ka tadani yanzu? Khaleed yace Salmah ta wil b bak soon, saeed ya saki baki, dama shiyasa ka tadani wlh Allah ma ya isa, toh ubanme kakeso na maka? Toh meh za'ayi dan ta dawo? Khaleed yace aurenmu mana, saeed yace ameerar fa? Toh meh ya dameni dama ae yarjejeniya mukayi, saeed yace toh ae yarjejeniyarku ta shekara daya ce, khaleed yace nifa i don't care salmah na dawowa aurenta zanyi, ita kuma ta kama gabanta, saeed yace lallai kacika butulu khaleed ya Kashe wayarsa, saeed yace dole nayi wani abu kan lokaci ya quremin, amma khaleed bazan barka wannan salmar ta ruguza maka rayuwa ba. [9/14, 7:21 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣0⃣5⃣ Assubah nayi alarm ya tada ameerah, tayi sallah ta jawo qur'aninta da azkar ta shiga karantawa, tagama ta duqufa da addu'oi, sai da gari yayi haske, sai kuma ta kasa bacci, fitowa tayi tana zaga ko ina tana kallon yanda aka tsara mata gidanta, sai mamaki take dan ita ko a mafarki bata ta6a tinanin ta samu wannan daular ba, sai zagawa take tana bude ko'ina tana leqawa, har takai dakin khaleed ba tareda ta sani ba, turawa tayi qofar a bude, shiko ya fito wanka yana goge jikinsa, dagashi sai towel, ya juyo haka towel dinsa ya kwance daidai ameerah ta shigo dakin, ido hudu sukayi ta buga ihu ta fita da gudu, cikin hanzari yabj bayanta, bai tsaya ko ina ba sai dakinta, tunkararta yayi kuma still yana dagashi sai towel din, ta daka tsalle sai saman gado, ya biyota duk ta takure a bango, jikinta sai qyarma yakeyi, zuwa yayi ya matseta ya kafeta da ido, har sunajin bugun zuciyar junansu, ubanmeh kikajeyi dakina? Nidai kayi haquri wlh Allah bansn dakinka bane, ta fara hawaye ohhh toh meh kikaje nema har kika fada dakina? Ya qara matseta ita kuma sai qyarma takeyi, kayi haquri nace bazan qara ba Allah kuwa, 😭 dariya taso ta su6uce masa ya lura duk jikinta 6ari yake, kura ga tsoro ga ban tsoro, wurgata yayi a gado karki sake koda wasa kije dakina, if not zaki samu abinda kikaje nema, ya miqe ya ficewarsa itako tana kwance inda ya barta tana sauke ajiyar zuciya, wannan khaleed din akwai mugu ji yanda ya tsoratani. Ameerah bata qara fitowa daki ba har wuraren qarfe goma sha biyu ga yunwa ta addabeta amma takasa fita. Saichan taji sallamar kausar har ta miqe sai ta tunada wulaqancin da ta mata jiya ta koma ta kwanta, kausar tayi sallamah ta kar6a mata a daqile batareda ta waigota ba, tace amaryarmu fa, ameerah tayi banza da ita ta miqe toh tinda fishi kike bari inkoma ta juya zata fita, da hanzari ameerah ta riqota ta rungumeta tana kuka, shine kika gudu kika barni da mugun yayanki, kausar cikin zumudi tace meh ya miki? Ko sai munyi gashi ne? Tureta tayi dalla ba abunda ya faru, kausar tace toh meh yamiki na mugunta? Ameerah ta gayamata ta fara yimata dariya, toh ae ke kikace kinji kingani, ameerah tace wannan qatuwar jakar fa? Kausar tace kudinku ne na biki da gifts sauran ma sai mom tazo tukunna, zare ido nayi, tace kije ki kaiwa mijinki kusan yanda zakuyi, a tsorace nace kije dai ke, tace keda mijinki kuma? Cewa tayi 1st dai sai kin tsala ado tukunna, nace kausar yunwa tace ga breakfast dinku chan parlour kan dining kije ki tsala ado tukunna, ta turani toilet ta dawo ta zauna tana jiran na fito. [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣0⃣6⃣ koda nafito kausar ta fitomin da wani hadadden sari wai shi zansaka nace mata kinga mutane zasuzo gidannan bazan saka saree ba, tace shikenan wasu kayan india ta daukomin irin dogon rigannan da pencil trouser da mayafinsu masu shegen kyau, kausar ta taqarqare ta tsaramin kwalliya ta fesheni da tiraruka, ta sakamin wata sarqa indian design take na dauki sheqi, tafara daukana pics wai wannan dole nasakashi Dp, turani tayi naje dakin khaleed na kirashi na kama hanya na tafi, saida na tura qofar muka hada ido na tuna da abunda yace, duk na qara zuwa dakinsa sai nasamu abunda naje nema, ae ba shiri na saki qofar na dawo daki da gudu kamar watche aka koro, kausar har tsoro taji lfy? Meh ya faru? Wa ya koroki? Kan na bata amsa sai gashi ya fado dakin, murmushin mugunta tayi, sumui sumui ta miqe ta fita, dama shi ita yake kallo dan baisan tana gidan ba, tinkaroni yayi nafara matsawa baya, meh ya kaiki dakina? Sai ja da baya nike shiko yana matsowa, dama dama yace dama meh? Take hawaye suka zubomin nace toh ka tsaya daga chan na gayamaka mana ina share qwalla, bai tsayan ba niko banfasa ja baya ba, ban ankara ba najini a qasa jakar da kausar tazo da itace ta kadani, matsowa yayi ya miqomin hannunsa alamun na riqa ya tadani, na bashi hannun fozgoni yayi da qarfi na fado masa, matsemin hannu yayi nayi qara inajinki meh kikajeyi dakina? Duk na dabirce na rasa meh zance masa, ok kinason ganina ne? Na girgiza masa kai toh menene? Sai lokacin na kalli jakar da ke gabanmu nafara nuna masa ita da hannu, kallonta yayi miye a ciki? Sai lokacin ya sakeni naja baya da sauri, bude jakar yayi kudine fal a cikinta dollars da nera da wasu gifts anyi wrapping, yace na menene wannan? Nace mom ce tace kausar ta kawo mana, wai namune da aka tara, ta6e baki yayi toh ni meh zan dashi? Cikin mamaki na kallo shi kudi ne fa, yace and so? Ki dauka kawai ni ba abunda zanyi dashi, nace mata toh ni meh zanyi dashi yace ki watsar, har ya juya ya fita, kuma ya juyo dama shikadai na ya kaiki dakina? Kai na girgiza masa, ya fara matsowa toh menene? Da gudu na wuce nayi hanyar fita ya riqoni, ya quramin ido nafara qoqarin qwacewa, da hannu daya ya riqeni amma nakasa qwacewa, kayi hakuri dan Allah yunwa nikeji, toh a gida ba'a koyamiki girki bane? Nima nan yunwar nakeji nace abinci na kan dining mom ta aiko shine dama zangayamaka, ya sakemin hannu na fita da gudu. Dariya khaleed yayi, wai meh yasa nakeson tsorata yarinyar nan ne? Wata zuciyar tace dan kaga tana tsoronka ne, wata zuciyar tace birgeka takeyi, ya girgiza kai no dat can't be but kawai nasan its fun to watch her getting scared, dariya yayi sannan ya fito dakin. Niko ina fita na afka kan kausar dake zaune parlour wlh ko muguwa ce meh yasa kika barni nikadai? Tace toh mutum zai gana da matarsa sai na tsareku da ido? Tace toh ae naga kun dade ne ta dagamun gira? Nace kudi muka tsaya qirga ta fashe da dariya toh nawa ne? Nace bamu gama ba amma bazasufi dubu dari biyar ba, kausar tayi dariya son ranta sannan tace kefa 7million ne da en chanji na gwale ido 7million? Khaleed ne yafito ya haye dining ya fara cin abincinsa, satar kallonsa nake, shidai baya wasa da cikinsa, hada ido mukayi yace ke ba yunwa kikacemin kinaji ba? Idan kika biyewa wannar uwar sanaben sai yunwa ta illataki, kausar tace ni broda dama kazo ka bata a baki zakafi birgeni, wata harara ya banko mata, ke ki taso kici abinci kinji na miqe nayi kan table. [9/14, 7:22 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣0⃣7⃣ Har na zuba abinci zanfara ci akayi sallamah saudah ce da khadijah nasir na sheqa da gudu na rungumosu, muka zube a kujera nace kun kyauta, suka gaisa da khaleed ya kar6amusu da sakin fuska, nace ku tashi mu tafi daki, khaleed yace abincin da kika zuba fa wa zai cimiki? Saudah tace kaidai ango kace ta barka kai kadai a table, kije ki tayashi ta turani suka koma suka zauna, naje kan dining din nafara cin abincin kenan aka koma sallamah anti fareedah ce da yaya saeed, na yunqura na miqe naje na rungumota, khaleed ya takemin qafa ba shiri nakoma na zauna harda er qarata, aunty fareedah ta lura ashe, tace ango idan har bakason amaryar ta miqe ta barka shine sai ka wani take mata qafa? Sukayi dariya khaleed yace anty fareedah ae ba haka bane tindazu ta debi abincin taqi zaunawa taci kuma yunwa takeji, aunty fareedah tayi dariya wato ni nazama antinka ko? Tinda matarka na kirana anty, saeed yace idan takasa ci ba sai kai kabata da kanka ba? Wata harara ya watsomasa ya basar su khadijah suka fara sowa, ya bani abincin sugani dole tasa ya dauki spoon ya fara bani suko suka fara tafi, ni duk kunya ta kamani sai wani noqewa nike, naqoshi inata nunawa khaleed ya barni haka, dan mugunta yaqi, saida naji cikina na batun fashewa ina yunqurin amai na miqe tsaye, shima miqewa yayi yana dariyar mugunta, winking yayimin ya sauka abinshi, niko kamar nayi kuka ciki yayimin fam nishima daqyar nike, haka na jawosu nace muje daki muna zuwa na fada kan gado na kwanta kan qoshin da nayi. Aunty fareedah tace qanwata, ga alama khaleed ya wahalarmin dake, gashin da yayi baiyi ba inaga sai mun sake wani, suka sheqe da dariya, niko kamar nayi kuka wlh ba haka bane fa, aunty fareedah tace saudah gayamata munsan komai fa danmu ba baqin garin bane, haka dai muka zauna munata fira sunamin tsiya, aunty fareedah na bani tips wai yanda zan mallake mijina, niko duk kunya ta kasheni. Bayan azahar ne naji sallamar mom, da gudu na miqe naje na rungometa, tare suke da dad na duka na gaidashi ya kar6amin da fara'arsa, mom tace daughter ga lunch dinku, kinsan nace karku dafa komai dinner ma za'a kawo har nan da sati daya, nace eh mom bamu dafa komai ba dama. Tace ina mijin naki? Sai gashi sun shigo shida saeed suka duqa suka gaida su mom, mom tace toh kuzo aci lunch din mana ina qawayen naki? Naje na kirasu suka fito suka gaida su mom, aka nufi dining, nida kausar neh mukayi serving kowa, nidai dan pepper soup Kadan nasha dan har yanzu cikina fam yake, aka gama muka kwashe kayan, mom tace zasuyi magana damu nida khaleed, sauran suka miqe, aunty fareedah tace ma zasu tafi nace tun yanzu? Tace wlh bikin suna zasu yayarta ta haihu, khadijah ma tace su jirata su rage mata hanya, na miqe na dibar musu kayan gara da sourveniers da kayan cosmetics da turaruka na basu, sukayi godiya suka wuce, kausar da saudah suka koma daki. [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣0⃣8⃣ Dady ya fara magana nasiha sukeson yimana kan zaman aure da hakuri, dan duk wanda yace zo mu zauna toh yace zomu sa6a, kar muga cewa munyi auren soyayya mu dauka hakan zai dore, dolene muyi hakuri da juna, dan wasu halayen junanmu da bamu sani ba yanzu ne zasu bayyana, kuma banda zalunci a koda yaushe muyi haquri da juriya wajen ganin munfarantawa junanmu, koda kuwa mun samu sa6ani Allah ubangiji yayi muku albarka, yasa aurenku ya dore har a aljannah, nace ameen, mom tace daughter nasan ke bakida matsala zakiyiwa mijinki biyayya, kuma kiyi hakuri da son ki guji 6ata masa rai dan idan yayi fushi zuciyarsa ba kyau, amma idan kikaga ranshi ya 6aci ki nisanceshi, ki shige dakinki ki kulle mukayi dariya, dad yace kidaina kushemin dana shi ba mai yawan fushi bane, kuma baya fushi banza sai idan an ta6ashi, kuma yanada saurin sauka, kamar yanda tace dai idan kikaga yayi fushi toh ki nisanceshi na dan lokaci, nace mungode dady inshaAllah zan kiyaye. Dad yace kar6i nan, wasu mukullai ya miqomin 3 yaba khaleed 2, yace wannan makullan motocinku ne, governor da sarki suka baku daya daya, ke kuma alhj salmanu ya qara miki dayan shiyasa kikaga naki guda 3, take muka fara zuba godiya nidai harda dan kukana wai yau nice da mota har 3 lokaci daya. Dad yace nima kaina motar naso na siyamuku, amma gasu kunsamu, kai son dama kanada 2 sai ka qara, yanzu sai ku fadamun wace irin kyauta kukeso na baku, nace nidai dad bana buqatar komai Allah ya qara girma yace ameen, kaifa son? Yace nima ba komai yanzu dady amma idan ina buqatar wani abu zan gayamaka dad yace shikenan, niko nayi alqawari duk sanda kuke buqatan wani abu ku gayamin idan baifi qarfina ba zanyimuku, mukayi godiya. Mom tace nidai i won't accept no 4 an answer, ku za6i qasashe 3 da kuke so ku gayamin amuku visa ku tafi honeymoon dam gabana ya fadi, khaleed ya kalloni, nima na kalleshi harara na watsa masa, nace a raina ba wani honeymoon da zamu ka gudu germany amma kuma meh zancewa mom yanzu? [9/14, 7:22 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣0⃣9⃣ Mom tace kunyi shiru, nace mom nidai da anbar zancen honeymoon dinnan banason nayi nesa daku, kuma mom kinga skul muna lectures kuma a kowane time za'a iya yin C. A, mom tayi murmushi ni banyarda da uzurunki ba, ae dai ba cewa nayi ku tafi karku dawo ba, kuma zancen skul zaku iya diffaring semester harku dawo, ture baki nayi nafara shagwa6a, nidai mom Allah banason su khadijah nasir su rigani graduating idan gyara yamin yawa zan iya samun matsala, dady yace ke Aisha toh a haqura har suyi hutu mana, sai suje cikin hutun, dan gaskia ba dadi mate dinka su qare su barka, mom tayi jim sannan tace shikenan zan haqura har ku samu hutun, nace thanks alot mom. Miqewa sukayi toh mu zamu tafi, kira kausar tazo mu wuce, na 6ata fuska mom ki barta har anjima mana, tace baga mijinki nan ba sai kawai ta hanaku sakewa? Ke kausar kina ina? Sai gata tafito mom tace kizo mu wuce ki samemu a mota, tace toh zuwa tayi ta kwaso kayanta, ta fito na riqeta plz ki bari anjima mana, qwacewa tayi ta wuce tanamin gwalo, harda hawayena. Khaleed yazo ya tsareni da ido, na juya zan wuce wata ya fizgoni, meh yasa zakice baza'aje honeymoon ba? Kallonsa nayi cikin ido kai meyasa kakeson aje honeymoon din? Na qwace kaina nashige daki abuna na barshi, tsaki yaja toh ni miyema na damuwa tinda salmah dinma tace zata dawo very soon ya wuce warsa ya kunna t.v yana kallo. Niko na koma daki jiki a sa6ule, saudah na ciki zaune naje na kwanta mata a qafafu, tace ni tashi da son jikin tsiya kamar mage ina kausar din? Nace ta tafi, saudah tace nimafa bayan la'asar nace usman yazo ya daukeni kinsan gobe zamu tafi kuma bangama shiri ba, narai narai nayi da ido yanzu duk tafiya zakuyi ku barni? Tace ke kinji dadi ma nida aka kai bauchi aka yaddafa? Ke gaki cikin gari ko yaushe zaki iya ganin en uwa, tace keys din meh ne kika aje? Nace mata wai na motocinane, saudah tace har 3? Nace mata eh wai duk gifts ne nasamu, saudah tace duniya sabuwa, nace kedai bari amma ni nasamu soyayyar mijina duk tafiyemin wannan daular, saudah tace ae ke kikaji kika gani yanzu sai ki dage dan ganin kin samo kansa, khaleed ne yayi ma na sallamah ya shigo, ke kizo ga motocinki nan anzo dasu ki gani ya fita, saudah ta miqe tanata zumudi muje mugansu niko banji ma ina wani dauki ba nadai bita kawai tana jana. [12/2, 9:14 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣1⃣0⃣ koda mukafita wasu zuqa zuqan motoci 3 farare biyu baqaqe sidik, biyun BENTLEY ne fara da baqa, biyun MERCEDES BENZ G-WAGON fara da baqa, dayar kuma PORSCHE fara tas, take na gane iri dayan sune governor da sarki suka bamu, porsche din itace tawa, saudah tayi suman tsaye saida na girgizata, tace wannan daqwa- daqwan motoci duk nakine qawas? Sai wani zuwa take tana zagasu, nima dai mamaki ya kasheni, wannan motocin da muke gani a hanya muna hade yawu, wai yau ni ameerah na mallakesu, amma bana wani doki, khaleed ne yazo saidai ki dauki baqaqen ni farar mota is my favourite, idan kin lura motocina ma farare ne, ta6e baki nayi ka hada duka ma na baka, na wuce cikin gida, shiko ya kada kafada ya tafi abunshi mukabar saudah wurin tana zare ido. Koda ta shigo har nakai daki, zuwa tayi amma dai wasa kike da kikace ya dauka ko? Nace toh miye ni wannan motocin ba wani damuna sukayi ba, tace amma dai nakine ko gobe kuka rabu nakine dan kyautarsu aka baki ba shi ya siyaba, buge mata baki nayi bawani rabuwa da zamuyi kima daina fade, riqe bakinta tayi ni zaki kumburawa baki dan na fadi gaskia? Nace indai wannan gaskiyar ce karki koma fada banaso, tace toh Allah ya kyauta, wayarta tayi qara tace usman ne ta dauka, tana kashewa ta miqe ta dauki mayafinta nace ya haka? Tace mijina yazo yana waje zamu tafi, har hawaye sun zubomin dan Allah kiyi hakuri ki bari sai dare mana, tace nagayamiki uzurina ameerah nima bada son raina ba amma dole zantafi, bag na bude na zaro bandir din dubu dari guda 2 na miqamata, tareda kayan cosmetics dinda na dibar mata, kallon rashin fahimta takemin wannan kudin fa? Nace nakine saudah tace ita afafam bazata kar6a ba, kuka na samata nace saudah wannan ba komai bane fa, nasan mijinki ba wani qarfi ne dashi ba, idan inadashi na hanaki miye amfanin samun da nayi? Idan baki kar6a wlh bazanji dadi ba kin nunamin ban isa namiki kyauta ba kenan, rungumeni tayi tana kuka, tanamin godiya ta kar6i kudin tasa jaka, ita tinda tazo duniya bata ta6a riqe ko dubu hamsin nata na kanta ba. Koda mukafito khaleed na zaune parlour yana kallo, saudah ta masa sallamah ita gobe zata wuce bauchi, tana fatar ya riqemata qawarta amana dan qawarta mai kirki ce, yace bakomai kar ta damu, ya ciro dubu hamsin yaba saudah taqi kar6a, na kar6a na turamata jaka, ya biyomu muka rakata har gate, suka gaisa da mijinta sannan suka wuce, nadawo inata matse qwalla, cewa yayi ke ina keys din motocin? Nace ba ke sunana ba sunana khadijah, ameerah yace koma dai miye kibani, nace ae dad da yazo kowa a hannunsa ya damqamasa nasa, akan meh zanbaka nawa? Wani kallo ya wurgomin nayi ciki da gudu na rufe daki, na barshi yana dariya. Ina fadawa daki na kwanta ina murmushi, I LOVE YOU ALOT KHALEED, JUST LOVE ME KO KADAN NE PLZ, na rufe ido alamun kunya, kamar yana ganina. Waya na dauka na kira mama ringing biyu ta dauka, nace mama shine kikaqi zuwa ko? Tace nazo nayimiki meh? Karma kisa ran ganina gidanki dan kiji, nace toh mama shine ko su suhaila sukaqi zuwa, tace sai subar makarantar suzo miki? Kibari weekend zasu zo, zata kashe nace mama tsaya mana inada magana, tace miye? Nace mama kudine aka kawo mana nida khaleed na biki da aka tara, amma waishi yace bayaso na dauka, tace toh sai ki daukan ba mijinki bane? Nace mama kudin da yawa fa sama da miliyan 7 fa, tace bakwai ameerah nace eh, tace ni ina ganin kudin da aka samu asibiti da yawa kusan miliyan 4, yanzu kintara kusan miliyan 10 kenan fa, nace mama ya zanyi dasu ne? Tace oho kiyi shawara da mijinki, nace mama harda mota 3 nasamu fa tace ke kika sani ta kashe wayarta, haushi ya isheni wai ita mama bama zata jira ayi maganar arziki da ita ba, Aliyu na kira cikin murna ya daga mukayita fira, ina gayawa aliyu yafara ihun murna, nace danuwa miye shawara? Yace ki nemi qaton gida ki siyamana sauran kija jari, nace naja jari kodai mama taja jari yace hakane ke bakida buqatar kudi yanzu, sis wato kece silar arzikinmu nace danuwa Allah ne yayimana gata, haka mukasha fira mukayi sallamah. [9/14, 7:25 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah abdul 1⃣1⃣1⃣ A kwana a tashi ba wuya a wurin Allah yau na cika sati biyu a gidan khaleed, amma fa bawani abun kirkin da yake hadamu, duk wani hakkinsa ya daukemin, wai komai nake buqata basai na tambuyeshi ba, bana masa girki dan ba ci yake ba, waishi girkin yarinya bazaici ba, kuma abunda na lura dashi shine, bayacin abincin waje kullum sai kayan kwali da na gwangwani, sai danbanzan shan coffee, nidai gudunsa ma nike dan indai zamu hadu ba abunda zai hadani dashi sai mugunta, dan ya lura tsoronsa nike shiko ko meh yasa yakeson tsoratani oho, zancen kudina kuwa da na masa magana account yaje ya budamin, ya zubasu duk sati saidai inji alert kawai ya samin kudi wai komeh nikeso basai na tambiyeshi ba, Kausar kuwa ita ke zuwa tana koyamin mota danshi ogan da mom tace yafara koyamin qi yayi, waishi 6ata masa time zanyi asa driver kawai, niko nace saidai na koya gun kausar, kuma saida yayi qoqarin da ya kar6e fararen motocin, ya barmin baqaqe dan ranar yaci sa'a ban rufe daki ba, yana shogowa kan yayi magana ma na kwaso na miqamishi jikina na 6ari, zancen kudi da nayi da mom cewa tayi kudina ne nayi shawara da mama duk abunda muka yanke shikenan, ita kuma mama idan na tambiyeta sai tace nayi shawara da mijina ita ba ruwanta, hakadai na yanke shawara da Aliyu idan yazo hutu zasu hadu da yaya musty su nemi gidan da zamu siya nace hakan yayi Allah ya dawomin daku lfy, su suhaila sai weekend suke zuwamin gashi khadijah nasir da aunty fareedah sun dauke qafarsu, kausar kawai nike gani, itama dan muna koyon mota, nafara iyawa ba laifi, gashi duk abunda nike nema a duniya nasamu sai soyayyar mijina kawai ta ragemin itama addu'a nike ba dare ba rana Allah ya karkatomin da zuciyarsa. Yauma kamar kullum, nayi shirina tsaf na saka qaton hijabina nayo qasa, dan yaune nike shirin komawa skul, ko zan rage zaman kadaici, ina saukowa daga stairs naji muryar khaleed yana ihun murna, na sauko da saurina dan inji meh yakeyiwa murna da safennan haka, ina qarasowa naga yasa call, aboki ka tayani murna gobe salmah zata sauko qasar nan, bafa wasa nike ba Allah yanzu ta kira ta gayamin, my salmah is coming bak tomorrow, khaleed ya kashe wayar harda taka rawa, ni tinda nake a rayuwata ban ta6a ganin khaleed cikin tsananin farinciki irin na yau ba, daki na koma da gudu na duqunqune nafara rera kuka, kuka nike kamar raina zaifita. Saeed kuwa khaleed na kashe wayarsa, duk yashiga wani tashin hankali waitoh yanzu meh zeyi? Kausar ta fado masa a rai, yace yes bari na kirata nasan tanada kusanci da ameerah sosai, bazata rasa sanin wani abu ba, kafin nayi komai ya kamata na tabbatar da idan dagaske ameerah na son khaleed, waya ya daga ya kirata, kausar ki sameni a asibiti yanzu, kisameni a office dina its urgent, itama dama ta fito dan tare zamuje skul, a kidimeh ta shiga motarta taja, lfy yaya saeed yake nemana asibiti waye ba lfy? Yaya khaleed ne ko ameerah? Amma inhaka ne meyasa baikira mom ko dad ba, da wannan tinanin ta isa asibitin UDUTH cikin gudu-gudu sauri-sauri ta isa office dinsa, ta tura ta fadamasa a firgice, yaya saeed waye ba lfy? Yace mata relax kausar kowa qalau yake, magana nikeso muyi dake and its serious, zauna sannan ta sauke ajiyar zuciya ta zauna ta zuba masa ido. Yace kausar so nike ki gayamin tsakaninki da Allah, ameerah tanason khaleed kuwa? Tace la yaya saeed dama dan wannan ka kirani? Auren soyayya fa sukayi toh meh zai hana ta soshi? Saeed yayi murmushi kausar i know dat u are vry intellige nt girl, kuma naga yanda kuke very close da ameerah bazaki rasa noticing cewa ba wani abu dake gudana tsakaninsu na masoya ba, tacs nifa bangane ba, murmushi yayi ya gayamata yanda plan din auren khaleed da ameerah yake, yace amma ni ina zargin ameerah tanason khaleed da gaske shiyasa tayi haka, saidai banida tabbacin haka, amma ke na tabbata bazaki rasa sanin wani abu ba plz ki gayamin gaskia kausar, if not auren qawarki na gab da rugujewa, kausar ta zare ido cikin tashin hankali, tace kamar ya? Yace ae kinsan salmah ko? Er gidan alhj usman nasir abokin dad dinki? Tace eh yace ita brother ki keso, har yau har gobe, rashinta da kuma matsawar da su mom sukayi masa, yasa suka hada plan din aure da ameerah, yanzu sanadiyar wasu pictures da aka turawa salmah yasa ta harzuqa, yanzu haka zancen da nike miki, gobe salmah zata dawo qasar nan, kuma khaleed yace da tadawo aurenta zaiyi, ameerah ta kama gabanta da bazai iya hada ko wace mace da salmah ba. [9/15, 2:34 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/11, 6:12 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣3⃣8⃣ Khaleed na kwance a daki abun duniya ya isheshi, tunanin meh yasa ya fara damuwa da al'amarin ameerah yanzu yake, kuma meh yasa duk sanda ya ganta bugun zuciyarsa ke karuwa? Shidai yasan mace daya yakeso itace salmah, amma meh yasa yake jin haka gameda ameerah, kwankwasa kofarsa yaji anayi cikin mamaki wa yake masa nocking yace waye? Ameerah cikin muryarta mai sanyi tace masa itace, shidai mamaki ya kamashi tin ranarda tazo dakinsa yace idan takara zuwa sai ta samu abunda tazo nema bata kara zuwa ba, yace mata ta shigo, shigowa tayi kanta a kasa tana taku daddaya, shiko yana kwance ya mike zaune ya zuba mata ido, kallon da yake mata ne ko meh yasa kawai ameerah nagani ta zube kasa kan tiles, tayi kara wayyo mamata, tafara yarfe hannu dan taji ciwo a kafa, cikin sauri yazo ya dauketa ya dora kan gado, ya fara duba mata kafar ita kuma tana er kara, khaleed yaje ya dauko ointment ya shafa mata a kafar sai wani lailayata yake ita kuma tana kukan shagwaba, khaleed duk ya rikice sai sannu yake cemata, said yaji tadaina kukan sannan ya sauke kafar tata ya koma ya ajiye ointment inda ya daukoshi. Ita kuma hotuna ta hango a tsakiyar gadonshi ta juya taja jikinta ta jawo hotunan, shikuma ya waigo ya dawo inda take, kici6is sai akan bayan ameerah da yake bude, take numfashinsa ya dauke, yabi surar jikinta da ido, fatar ameerah sumul ba tabo sai sheki take, matsawa yayi wurinta yasa hannu ya shafi bayan nata, ya runtse idonsa wasu abubuwa namasa yawo aka, ita kuma a razane ta waigo taga khaleed a durkushe bayanta, ido ta kuramasa da mamaki, shi kuma ya bude idonsa da suka fara chanja kala, suka fara kallon junansu, ameerah taji bazata iya jure kallonsa cikin ido ba, ta sauke idonta, hannu khaleed ya daga ya fara zagaye fuskarta, tace zuciyar ameerah ta fara bugawa da karfi kamar ta ballo kirjinta ta fito, ta runtse idonta gam, bakinta ya fara zagayewa da dan yatsansa, hakan yasa ameerah ta bude idonta tana kallonsa bata ankara ba sai bakin khaleed taji a nata ya fara kissing dinta, chak nufashinta ya tsaya, shiko tsutsar lips dinta yake kamar ya samu sweet, rurar karar da wayarsa take tafara dawo dashi hayyacinsa, dakyar ya janye bakinsa daga na ameerah ya duba wayar, salmah ya gani, ya dauka hello my love, jin haka yasa ameerah ta motsa daga sandarewar da tayi, ta yunkura ta tashi jikinta duk ya mutu, haka ta daure ta mike tsaye, tana taka kafar ta saka wata uwar qara ta koma ta zauna. Arazane khaleed yayo kanta lafiya? Yama manta da waya yake, ta nuna masa kafarta tana kukan shagwa6a, yace ina zataje? Tace dakinta, chak ya dauketa kamar wata baby, yayi hanyar dakinta da ita, bai direta ko'ina ba sai kan gado, yaja bargo ya rufeta har ya juya ya tafi ya waigo kuma, yayi wani kicin-kicin da fuska meh ya kaiki dakina? Check ta nuna masa da duk ta wani dukunkuneshi a hannunta, tsaki yaja nakine mom tace sai namiki kayan fadar kishiya, kisiye abunda kikeso idan kuma bakiso ki yadda, ya juya ya ficewarsa [12/12, 7:57 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣3⃣9⃣ Ameerah tabi khaleed da kallon mamaki shi wannan wai meh yake damunsa ne? Ko har ya manta abunda ya mata ne yanzun? Juyawa tayi ta rufe idonta dan tayi bacci, amma ina baccin yaki zuwa sai abunda ya faru tsakaninta da khaleed take tariyowa tana faman murmushi abun kamar a mafarki, sai wuraren karfe 3 tasamu bacci yayi gaba da ita. A wurin khaleed ma haka ne tinda yaje daki ya kwanta, sai tinani yake ya akayi har yayi kissing ameerah yau? Harda marin kansa yayi, dole na nisanci yarinyar nan kafin ta wargazamin duk wani shiri nawa, ga alkawarin da nayiwa salmah, sai lokacin ya tinada salmah ta kirashi fa, kafin ameerah ta kwalla kara, da sauri yajawo wayarsa yasa kiranta missed call 3 taki dauka, nan wai ita fushi tayi tinda taji karar ameerah a kusa dashi dats means suna tare, namiji fa munafuki ne yana nuna mata ba abunda ke tsakaninsa da ameerah amma meh yakeyi a tareda ita? Harda ajiye call dinta yana kula matarsa, wallahi tinda khaleed yayi mata haka akan ameerah ranar da tashigo gidan gobe kenan zata sanya yayi waje da ita. Shiko baisan meyasa rashin daukar wayar da salmah batayiba, bai wani damuwarshi ba, ajiye wayar yayi, yayi kwanciyarsa, amma sai ya nemi bacci ya rasa abunda ya faru dashi da ameerah kawai yake tinani, duk iya kokarinsa na ganin ya hana kansa tinanin ya kasa, daga bisani ya tashi yafara salloli anan kan sallaya bacci yayi gaba dashi. Washe gari ta kama ranar daurin auren khaleed da salmah, karfe goma na safe za'a dauran, amma ango na kan sallaya yana kwasar bacci dakyar ma ya iya tashi yayi sallar asubah. Ameerah kuwa da ta tashi tayi wankanta ta koma ta kwanta, sai karfe goma ta farka, ta tashi taje kitchen ta hada dan breakfast, sai sallamar aunty fareedah taji tazo da gudunta ta rungomota, tace yau dai munzo tausar kirji inanan har dare, dan kar en kawo amarya suzo sumiki rashin mutunci cikin murnata nace nagode antina, dan basket ta mikomin tace ga kayan breakfast nazomiki dashi, nace ohh antina you are the best, kaman kinsan yunwa nakeji yanzu ma haka da kitchen zanje, najata muka wuce dakina. [12/12, 8:25 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣4⃣0⃣ Munje daki na zuba breakfast dina inaci, muna dan taba fira da aunty fareedah, sai ga kausar ta shigo a dan hargitse, nace ya akayi kika fado haka kamar watchche aka koro? Tazo ta wani turbune fuska, tace ina yaya khaleed? Da mamaki na kalleta kamarya ba yau ake daurin aurensa ba may be yana chan, tace kinga ina baccina mai dadi fa dad ya tasoni, wai antaru wurin daura aure amma ba ango ba alamarsa, dad da friends dinsa sai kiran wayarshi suke yaki dauka, shine akace nazo na duba ko lafiya, a razane na mike nace bari naje na duba dakinsa ko kalau yake, aunty fareedah ta jawoni ki kyaleshi kawai kar a daura auren ma, ke miye naki a ciki? Murmushi nayi anti fareedah kishi ba hauka bane fa, bazan iya yimishi haka ba bayan ya tara jama'a, after all banmasani ba ko bayada lafiya ne, kausar ta tabe baki ai sai kije ki taimaka mishi ya auromiki kishiya, nidai nafita na barsu ina dan Murmushi. Dakinsa na tura nayi sa'a a bude, chan na hangoshi akan sallaya kwance, da sauri naje wurinshi na taba jikinsa, naji ba zafi sai baccinsa yake kwasa, na rasa ya zanyi na tadashi, naje ina bubbugashi, jawoni yayi ya rungume ya cigaba da baccinsa hankali kwance, wayarsa ce ta dinga ruri, dakyar na janye hannunshi naje na jawota, dad nagani na daga dad yq fara zabgq masifa idan yasan bayason auren ubanwa yasa Ya tara jama'a wannan ai wulaqanci ne, minti goma ya bashi ya iso wurin daurin auren ya kashe wayarsa. Na rasa ya zanyi, naje na bubbuga khaleed amma sai ya bude ido ya rufe kamar dan maye, sai jawoni da ya karayi a jikinshi ya rungume, takarkarewa nayi na gantsara masa cizo a hannu, a razane ya mike zaune ke mahaukaciyar inace ne? Ar you a vampire? Are u thirsty of my blood? Yama ki bari nayi magana meh ya kawoki dakina yanzu? Mikewa nayi na dauko agogo na miko masa, koda ya duba 10.40, a razane ya mike tsaye ya dora hannu aka what have i done? Kallona yayi yafara nunani it all your fault, da mamaki na kalloshi my fault kuma? Ashe dana sani na barka ka cigaba da baccinka nazo na tadaka shine laifina? Naja tsaki na juyawata kuma dad yace 10 minutes ya baka, ka isa wurin daurin aure dan mutane sunfara gajiya da jiran ango, na kama hanyar barin dakin. [9/15, 2:34 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/13, 8:25 AM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣4⃣5⃣ Munanan zaune a daki duk ihunsu ya damemu, aunty fareedah tasa na tsala kwalliya da wani dakakken lesi orange sai zuba kamshi nike, niko sai magiya nike musu kar sutafi su barni dan Allah, aunty fareedah tace itadai mijinta na jiranta amma zata kara jira har suzo sidw dina dan a ka'idah dole akawo amarya gun uwargida indai iyayen nata datijai ne, haka kuwa akayi muna zaune mukaji alamar shigowa part dina. En kawo amarya sai santin part dina suke duk da cewa itace amarya amma ba abunda zata nunamin, muna haka mukaji anafadin ina uwargidan take ne? Aunty fareedah tace ku tashi mu samesu parlour kadda su shigo miki daki, mukatashi mukayi parlour aunty fareedah tace gafa uwar gida ran gida nan, idan bata ba gida suka tabe baki, aka zazzauna kan kujeru, wasu tsofaffi sai nasiha suke wai ga kanwata nan na riketa Amana mu zauna lafiya, duk abunda tayi ba daidai ba na luradda ita, ni sai waige-waige nake dan kwata-kwata bangane amaryar ba, tinda a al'adance za'a samu amarya rufe a mayafi tana dan kukan rabuwa da gidansu, amma nan din kam ni banga ko waccensu a lullu6e ba, aunty fareedah na dan taba ina mata rada wai wacece amaryar ne? Tace itama batasaniba, khadijah nasir tace wai ina amaryar ne mudai bamu ganta ba sai cewa kuke a riketa amana toh wa za'a rike din tinda mudai bamu ganta ba. Chan mukaji murya daga gefe gani nice amaryar ko da matsala ne? Na dubeta dakyau naga wata fara gajera mai kwala-kwalan ido ta zubo mana su, take na tunafa kaman hotunanta ne nagani a dakin khaleed ranar. Aunty fareedah tace taya za'ayi ki zama amarya? Mudai munsan amaryar hausawa da kunya suke, ko wacce a mayafi ake kawota koda kuwa batayi kuka ba dole ne ta rufe fuska ko ango sai ya biya yake gani. Tsaki mukaji tayi ai zamani ya chanja, meh zaisani kuka kamar wadda za'a kawo gidan makiyinta? Kuma na rufe fuska abun kunya nayi ne? Aure aka dauramin ba wani mugun abu ba, mudai sai kallon juna muke cikeda mamaki, sai chan wata tsohuwa ta fara yimata masifa, wato ke salamatu rashin kunya kadai kika koyo turai, ta katseta niga gwaggo ki daina yimin masifa, sai chan wata figaggiya daga cikin kawayenta tace toh wacece kishiyar tata a cikinku? Aunty fareedah tace ai batada kishiya anan wurin nan da zaman aure takeyi ba zaman kishi ba. Mikewa salmah tayi gaskiya kika fada ni banida kishiya anan wurin dan gobe saidai ku sameta a gidansu, dama duk nasan zaman da take a gidannan, yanzu mai wuri yazo sai mai tabarma ya nade, tace ku tashi mutafi kawayenta sukabi bayanta, tsofaffin wurin duk jikinsu yayi sanyi, wata tsohuwa ta fashe da kuka da nasan wannan tsinanniyar rashin mutuncin da zatayi kenan wlh da bamuzo ba, su kabamu hakuri suka fita. [12/13, 9:09 AM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣4⃣6⃣ Suna fita na fashe da kuka, aunty fareedah tace miye haka ne? Nace bakiji abunda tace bane, ya riga ya gayamata baya sona dan rashinta ne yasa ya aureni, kuma da tazo zai sallameni, niko nasan yanda yakeji da wannan salma din idan tace ya sakeni a daren nan zaiyi, kausar tace wlh saidai idan bana numfashi, gefe taja ta kira mom, bayan mom ta daga kausar cikin kuka take yimata bayani, mom tayi murmushi ki kwantar da hankalinki yanzu ya tashi a gabana ya tafi, kuma na ja masa kunne ko kuka ya saka ameerah akan yayi sabon aure ni da shi ne, ko giyar wake yasha bazai fara sakinta a daren yau ba, kuma gobe zanje dakaina nasameshi tareda amaryar naja mashi kunne a gabanta, dan tasan ameerah nada matsayi a wurinmu wanda bazata taba samu ba, kuma shi bazai taba samun mai sonsa sama da ita ba, duk wani abu da takeyi kawai dan farincikinsa ne, bata damu da nata farincikin ba, duk da cewa tana tsananin sonsa. Kausar tace mom ya akayi kikasan haka? Mom tace kausar kenan kun dauka dan kun boye gaskia zai hana gaskia ta bayyana? Nasan komai sa muku ido kawai nayi, har naki sirrin na wanda kikeso, cikin sauri kausar ta kashe waya tana murmushi, wato ranar mom taji firar da sukeyi kenan? Taje wurin su ameerah tana murmushi, aunty fareedah tace waike ina kikaje ne? Sister inlawnki na cikin tension kinje waya da saurayinki ko? A kunyace kausar tace la aunty fareedah wlh mom na kira na gayamata rashin kunyar da salmah tayi mana, kuma tace ki kwantar da hankalinki taja masa kunne, zama daram a gidan broda sukayi dariya, duka nakaimata a cinya gulmammiya toh aikinki nayi? Tace iye taimako sai yazama laifi kuma? Aunty fareedah ta mike bari na tashi nima nayi kewar mijina shima nasan haka, zantafi khadijah ma ta mike nima muje ki ragemin hanya dare nayi fa, fuska kamar zanyi kuka nace har dake kausar tafiya zakiyi ki barni? Ta girgizamin kai yau anan zan kwana, take damuwata ta gushe mukaje muka rakasu anty fareedah saida suka fita muka jiyo, inatayiwa kausar godiya tace taya zambarki kekadai a gidannan bayan naga halin amaryar taki, nan ko ita kunyar mom ce zata hanata zuwa gida yau, munkai bakin kofa mukaji shigowan angwaye, muka rakube gefe muna leke, ango naga ya fito a mota da kayansa na dinner a jiki sunmasa kyau sosai, sai kyalli yake, bakinnan har kunne, da wasu abokansa su 3 suka nufi part din salmah, koda kausar ta lura ba saeed ta fincikoni ke kizo mu wuce, nifa banga yaya saeed ba, murmushi nayi ya zaki ganshi kuwa kishi yake tayani, tayi murmushi dan halak naja hancinta bakisan har mari yasha kan ya zagi salmah ba? Ta zaro ido mari? Lallai broda bayada mutunci shine zai mareshi kan wannan fitsararriyar matarshi? Sai wani huci take tana masifa. Nace iye lallai soyayya ruwan zuma, wato saurayi yafi dan'uwa ko? Toh nidai karki dakeni bani na kar zomon ba, murmushi tayi amma dai kinsan broda bai kyauta ba ko? Nace hakane amma giyar soyayya ce ke dibarshi yanzu, duk ranar da ta sakeshi zai gano laifinsa, amma yanzu duk kushewar da zakuyi ma matarsa bazai ga illarta ba, amma zaifara gani a hankali, tace broda yayi sa'ar mace ta gari Allah ya barku tare, nace amin muka wuce daki. [9/15, 2:35 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/13, 1:40 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣4⃣7⃣ Nidai deejah nace bari naje na leko wainar da ake toyawa dakin salmah, kawayenta keta rokonta ta rufe fuskarta ko zasu samu kudin siyen baki ga angwaye nan zuwa, dakyar suka samu ta yarda ta rufe fuskar tata. Kawayen amarya wasu sai goga powder da jan baki suke. Sai ga sallamar su khaleed , suka nutsu ko wacce sai wage hakora take, suka shigo sai zuba surutu ake shidai angon hankalinsa na gun amaryarsa, daga bisani kawayen salmah suka dage akan miliyan daya za'a basu dan kawarsu mai tsada ce, khaleed ya ciro check ya rubutamusu dan shi ya matsu su daga su bashi wuri ya gana da amaryarsa, saida suka gama felekensu da zancen su irin na en bariki suka tashi abokan angon zasu wuce da wasu daga cikinsu da basuda mota, khaleed ya fita rakiyarsu saida yaga sun wuce sannan ya sauke ajiyar zuciya ya koma dakin amaryarsa. Koda ya shiga ta yaye mayafin fuskarta, murmushi yayi ya nufeta, ya zauna kusa da ita ya janyo hannunta, ya kura mata ido amaryata kenan, wannan ranar na dade inata jira for so long, alhamdulillah yau burina ya cika kin zama tawa, janye hannunta tayi banzama taka ba malam da saura, cikin mamaki ya kallota da saura meh kuma ya rage? Tace kayimin alkawari nikadaice macen da zaka zauna da ita, ba wata macen saini kadai, yace toh ai kekadaice salmah ko yanzu ba wata saike, rungumota yayi common karki bata mana first night dinmu please. Mikewa tayi ta tureshi, ai yanzu ba nikadai bace a gidan mu 2 ne, kuma idan har baka saki matarka a daren yau ba, karka sake ka kusantoni da sunan na zama taka. A razane ya kallota haba salmah meh kike cewa ne? Yanzu cikin daren nan na saki ameerah? Meh mutane zasu kirani? Daga kawomin amarya yau na saki uwargidana? Beside ma zancen mutane bai dameni ba iyayena nake ji dan bazasu taba yafemin ba idan har na saki ameerah a yau dinnan. Jawota yayi ya kankame ta baya, yana mata rada a kunne haba babyna kiyi hakuri har nan da dan lokaci koda nan da wata 3 ne, zamuje honeymoon ko wata nawa kikeso muyi a chan, kawai ki dauka ameerah zaman iyayena takeyi a gidannan ba nawa ba. Janye jikinta ta karayi stop fooling me please, kace kawai kafara son matarka, gashi har wani uwargidanka kake kiranta, yaushe tazama matarka? Ohh ranar ma naji kuna tare wuri daya da ita ranarda ka ajiyemin call kana shan zumar matarka ko? Yanzu kasan dadin matarka shiyasa bazaka iya rabuwa da ita ba ofcouurse, tsawa ya daka mata haba salmah wai ke wacce irici ranar farkon ma bazaki bari mu zauna lfy ba? Tun yaushe nagayamiki ciwo taji a kafa na taimaka mata na baki hakuri kuma kince kin hakura yanzu meh ya dawo da maganar kuma? Ya sausata murya kiyi hakuri plz kidaina zancen ameerah yanzu, kibari muyi kwanan farinciki a daren yau, wannan ranar mun dade muna jiranta, don't ruin it for us please. [12/13, 2:00 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣4⃣8⃣ har taso ta hakura kuma, wata zuciyar tace mata kinmanta kin cewa kawayen ameerah saidai su nemeta gidansu gobe? Yanzu zakiji kunya kenan gun kawayenki idan suka zo gobe suka tarar da ita kenan? Idan kika sake masa har ko yaushe uzurin da zaibaki kenan ba sakinta zaiyi ba, ko kin manta da cewa dan ki nunawa kawayenki kin isa yasa kikayi auren ne? Ja da baya tayi wallahi khaleed idan dai bazaka saki ameerah a daren yau ba, ba wani kwanan farinciki da zamuyi a yau. Baki sake yake kallonta, lallai kishin salmah ya baci, take zuciyarsa ta fara zafi kansa yana juya masa, ya zauna a gado ya dafe kai yanzu ya zanyi? Wata zuciyar tace masa harma tambaya kake? Idan kace yanda takeso zakayi zaka rasa abu biyu, na farko bazata taba baka respect ba a matsayin mijinta, na biyu zaka rasa iyayenka dan fushi zasuyi dakai sosai. Wani bangaren zuciyarsa ma ji kawai yake bazai iya sakin ameerah ba ko ba fushin iyayensa, baisan dalilin haka ba, mikewa yayi a kasalance salmah idan har bazaki iya hakuri ba mu zauna lafiya, kinzabi yau muyi kwanan bakinciki ba abunda zan iya, bazan iya sakinta a yau dinnan ba da bazan iya jure fushin iyayena ba. Da mamaki kake kallonsa, saida yakai aya ta tabe baki, tinda ka zabi haka shikenan inaso ka nisanta kanka daga gareni har zuwa ranarda kaji zaka iya sakin matarka, idan kuwa hakurina ya kare kafin lokacin, sai dai ni ka sakeni na tafi, dan bazan iya sharing mijina da kowace mace ba. Zagayeshi tayi ta wuce ta bude akwatinta, wasu fitinannun kayan bacci ta ciro ta saka, dasu da babu duk daya, taje tayi kwanciyarta tabar khaleed da hade yawu. Ya gaji da tsayuwa shima yaje ya kwanta zuciyarsa nayi masa zafi, wannan wacce irin rayuwace, ranar da yakamata ta zamemasa ranar farinciki a rayuwarsa ta zame masa ranar fitina, harda wasu zazzafan hawaye suka zubo masa ba tareda ya sani ba ya share, juyowa yayi ya kalli salmah da ta juya masa baya, sai chan yaji tafara minshari wato ita har ta iya yin bacco yau. [9/15, 2:35 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/14, 8:06 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣4⃣9⃣ Ranar dai a haka dare ya karewa khaleed, yama kasa tashi yayi ko nafilfili sai juye-juye yake, salmah kuwa baccinta take shaka son ranta da ba abunda yayi mata zafi, khaleed bai farga ba yaji anfara kiran sallar assubah, haka dai ya mike jiki ba kwari ya tashi yayi alwala, yazo ya tada salmah ta tashi tayi sallah, yaje masallaci ko da ya dawo tana a kwance sai kara Jan bargo da tayi ta rufa, ya kara tada ita sai wani mitsitstsike ido take, tana tsaki nifa banason takura ka kyaleni nayi bacci na, wannan bukukuwan da akayi duk mutum bai huta ba yanzu ma angama kuma bazan huta ba? Khaleed yace salmah sallah zakiyi sai ki dawo ki kwanta, kaga ni ka kyaleni ai har yanzu da sauran lokaci dan gari baiyi haske ba, kara jan bargo tayi ta rufa, ya fisge bargon ya ciccebeta bai sauketa ko'ina ba sai toilet, ya shafa mata ruwa a fuska ya fito ya barota sai kiyi alwalan duk sallar da zakiyi ai baza ta dauki ko minti goma ba, ita duk haushi ya isheta, shiyasa bata son bakin auren nan da rayuwar 9ja duk sai abi a takuraka ita wlh dole ta koma germany ta cigaba da rayuwarta inda ba mai takurata sai abunda taga dama takeyi. Koda tayo alwalar tafito yana zaune yana karatun alqur'an, taje tana duba kayanta batada hijabi ma ko daya, yana kalle da ita sai wata abaya ta dauko tasaka tayi rolling dankwali tazo zata kabbara sallah, yace salmah ina hijabanki? Da har bazata kar6a ba tace ko a saudi arabia dai naga ana sallah a haka, ta kabbara sallah shidai ya bita da ido. Ya lura sallameh salar kawai tayi ta dane gado, ya lura ko addu'a batayi ba bare ayi wani zancen azkar, girgiza kai yayi wannan kamar ba salmarsa ba da yasani ada tanada rikon addininta kuma batada tsiwa, amma may be gajiyar biki ce bari yayi mata uzuri, ya gama karatunshi saida gari yayi haske yaje ya raba bayanta ya kwanta harda wani rungumota, ya sauke ajiyar zuciya sannan bacci ya daukeshi. Ameerah ma haka take a wurinta, bacci gagararta yayi sam, dukda bawai saba kwanciya tayi tareda khaleed ba amma tinanin yana tareda wata macen ya hanata sukuni, tin suna fira itada kausar, har kausar ta gaji tayi baccinta ta barta, itama saida akayi kiran subh ta tashi, ta tada kausar sukayi sallah, sukayi azkar dinsu da karatun alqur'an da gari yayi haske sannan sukaje suka kwanta, sai lokacin bacci ya dauki ameerah. [12/14, 8:49 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣5⃣0⃣ Sai wuraren 9.30 kausar ta farka, ameerah kuwa bacci take kausar ta lura jiya ba bacci tayi ba dan idonta sun nuna hakan, shiyasa bata tasheta ba kitchen taje ta fara hadamusu breakfast. Kamshin girkin da ake ya tada salmah itafa yunwa takeji Allah, jiya tsabar masifa ko kazar da amare keci bataci ba, khaleed ta lura dashi da ya manne mata a jiki ta fara bubbugashi, sai bude ido yake yana rufewa akan tsabar baccin da ke idonsa, sauka tayi ta fara zagaye dakin ta lura da ledar da aka ajiye gefen gado, cikin sauri ta jawo gasassun kajine manya-manya guda biyu da yourghurt, ta jawo sai kuma taji sunyi sanyi qalau, itafa idan ba abu bai zafi taci ba bazata gamsu ba, zuwa tayi ta dinga bubbuga khaleed shikam bacci ya masa nauyi, haushi ya isheta, ta sauko ta fito parlounta tabi hanya ta shigo main parlour, sai kausar da tagani tafara jera kayan breakfast din a dining, kamshi duk ya isheta gashi ba dama tayiwa kausar magana sai hararta da kausar keyi, taja jikinta takoma dakinta, ruwa ta debo ta zubawa khaleed firgigit ya tashi zaune, kansa ya fara juya masa kamar ya tsage tsaban ciwo, dakyar ya bude ido yace ya akayi salmah zaki tadani da ruwan sanyi, duk sanyinnan da ake. Ta zumbure baki yunwa nikeji Allah kasan tin jiya bakabani komai naci ba, yace toh laifinwa kin bari anyi maganar kirki ne jiyan bare har na ciyar dake? Ga kazarki nan ki dauka kici let me sleep please jiya kinsa nakasa bacci, kibarni yanzu kaina ciwo yakeyi sosai. Cikin masifa tace toh nabarka kayi bacci ni yunwa ta illatani? Ni bazan iya cin kazar chan ba duk tayi sanyi, ni abu mai zafi nikeso, yace toh ki dauka kije ki dumama a micro wave ko a oven mana, nifa ban iya shiga kitchen ba ko ruwan zafi bana daurawa a gida, da mamaki ya kallota, kina nufin kenan komai baki iya girkawa ba, toh wa zai yimana girkin kenan? Kaga ni ba girki nazo nayi ba, kuma ai hakkinka ne ka ciyar dani, dan haka ka tashi ka nemomin abun breakfast kawai yunwa nikeji. Khaleed haka ya sauko yafito kansa kamar ya tsage, yaji kamshi main parlour ya biyo, kausar yagani tanata faman jera abinci, ya tsaya yana kallonta koda ta waigo ta ganshi duk yayi wani iri dashi, tace good morning bro ya kar6amata, yace kausar zamu iya samun breakfast dinnan kuwa? A yatsine tace masa kaida wa? Yace nida salmah mana, kausar tace ai itama macece tafito ta girka, ni abincin mutum 2 nayi, haka yayi daidai da fitowar ameerah sanye da sleeping dress dinta, tace kausar ki sammusu mana, kinsan baidace amarya ta shiga kitchen ba, khaleed ya waigota ya kura mata ido, saima ya nemi ciwon kansa ya rasa. Matsowa tayi tana masa murmushi good morning ango, ya amaryar taka? Shidai yama kasa magana baisan meh yasa yakejin wani abu gameda ameerah ba, idan yana kallonta take kwakwalwarsa ke daina aiki. Taje tana bude flask din abincin, tace haba kausar karki zama mai rowa please wannan girkin yayi mana yawa fa, kausar ta tabe baki toh uwar taimako ai sai ki dauri aniyar yiwa kishiya girki ni wlh bazan iya ba. Murmushi nayi toh ai kema sister inlawnki ce, ta waigo gurin khaleed zata iya zuwa muyi breakfast din gabadaya, ko kuma ka dibarmata girkin kai kawai ya gyada mata, ta juya nidai bari naje nayi wanka, kausar tace nima haka bari nashiga dayan dakin, yau kayanki zan saka fa dan bazan iya maida wannan ba, nace toh ki biya kudin haya, mukayi dariya muka juya, mukabar khaleed anan yana murmushi ya bi ameerah da ido. [9/15, 2:36 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/14, 7:35 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣5⃣1⃣ koda muka yo wanka kausar tazo tafito mana da wasu hadaddun kaya indian design iri dayane amma different colors, ni nawa red nata kuma lemon green, nace waike kausar meyasa kikeso koda yaushe na saka kayan India ne? Tace ai sister inlaw kayan india da English wears kyau suke maki sosai kamar danke akayi, kwalliya muka tsaya muka tsara, kamar masu zuwa beuty contest mukanmu munsan munyi kyau. Kallon kausar nayi cikin tsokana nace waini bangane ba idan ni mijina nake yiwa kwalliya ke kuma fa? Tace ina kikasani i may get lucky yaya saeed yayi spoting dina, may be he'll fall in love, dariya mukayi nace muje muyi breakfast nidai yunwa nikeji, tace itama lets go. Koda muka fito khaleed da salmah na kan dining, ita uwar kanzagin har tafara kwasar girki, kausar ta yunkura tafara masifa na tareta, na lura tinda muka fito daga ita salmah har khaleed din kallona suke, zama mukayi akan dining nace amarya kin tashi lafiya? Itadai tinda ta kalle ameerah tayi mata wani kwarjini wai dama itace matar khaleed din? Tasan tanada kyau a fuska amma ameerah tafita diri kyau dinma saidai ta nunamata hasken fata, har wannan khaleed zaice bayaso? Maganar da ameerah tayiwa khaleed ta katse mata tunani, ango kai naga baka debi abincin ba, ko sai amaryar ta koshi ne? Shidai murmushi yayi kawai ya jawo plate zai fara diba, nace amarya yakamata tayi serving dinka ai salmah ya kalla, ta takarkare tana kwasar girki ko kallonsa batayi ba. Mikewa nayi let me help you then kausar ta takemin kafa nasa kara, tsaye khaleed ya mike da hanzari yayo kaina, kafar har yanzu bata daina ciwo bane? Yazo ya duka yana dubawa, wani kamshi da ke fitowa daga jikin ameerah ya shaka wanda yasa numfashinsa ya kusa daukewa, take yaji yanayinsa ya fara sauyawa, mikewa yayi bari na kira saeed ya dubaki zanyi magana kausar ta karbe gaskiya broda ka kirashi dakyar take taka kafar, kallonta nayi da mamaki ta kannemin ido. Khaleed yace ko na kirasa ba lalle bane ya dauka dan fushi yake dani let me txt him, salmah dai mamakin duniya ya isheta, itace amarya yakamata ita yake tarairaya amma kamar yama manta da ita agun yana kula matarsa, munafuki, tsaki taja tawuce daki khaleed yabita da ido shifa shaf ya manta tana wurin Allah, lallai yau ya jawowa kansa sabuwar rigima. Juyawa yayi yabita ameerah ta riko hannunshi, ya waigo ya kallota naga bakayi breakfast dinba, kazauna kayi kafin abincin yayi sanyi, samun kansa yayi da kasa yimata gardama ya zauna tasowa tayi tayi serving dinsa yana shakar kamshita da ya fara zautashi, ya fara cin abincin bini-bini yana dagowa yana kallonta, idan sun hada ido sai suyiwa juna murmushi. Kausar sai kallonsu take tana murmushi, lallai broda yafara kamuwa, watakila baigane hakan bane amma ita ta hango son ameerah da sha'awarta a idonshi, ana cikin haka mom tayi sallamah ta shigo. [12/14, 8:26 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣5⃣2⃣ yunkura nayi intashi in tarota kausar ta rikeni idan kika fama kafar fa, wata harara na watsa mata na koma na zauna, mom da sauri ta karaso wurina meh ya sameki a kafa? Nace mom bakomai fa kawai nadan fadine naji ciwo kadan kuma ma na warke, mom tace faduwa garin ya? Toh kinje kinga doctor? Khaleed yace mom nayiwa saeed text nasan yana hanya tace toh shikenan, kirika kulawa ameerah yanzu sanyine ba wuya mutum yaji ciwo, nace relax mom mikewa nayi tsayi na dan taka naje na rungomota bafa wani ciwo naji ba, dazun ma bugewa nayi a kujera da naje tashi shine nayi kara sun dauka kafar kemin zafi, murmushi mom tayi toh shikenan Allah ya kiyaye gaba, zama tayi meh kukeci nima banyi breakfast ba, zama tayi nayi serving dinta tafara cin abincin. Kausar ta kalla tace wato jiya sai naji shiru ko kausar? Kausar ta sadda kai kasa tana murmushi alamun kunya, mom tace wato nazama sirikarki yanzu ko? Khaleed yace mom meh ya faru take jin kunyarki? Mom tace don't worry zaku sani yanzu, kausar ta dago kai haba mom please karki fada mana, mom tayi dariya naji dadi da na ganku a haka, ina amaryar taka? Yace mom yanzu ta tashi, tace toh kaje ka kirata inaso zanyi magana daku. Tashi yayi ya nufi dakin salmah gabanshi na faduwa yasan dakyar ma zata saurareshi bayan tayi fushi ta tafi kuma baibiyo bayanta ya rarrasheta ba, koda ya shiga tana kwance tana waya, toh nidai kuyi sauri kuzo nagaji da zaman kadaici ta ajiye, kwallonsa tayi ta watsar, uwargidan taka sai yanzu ta baka damar dawowa? Toh ka koma gunta danni banida bukatarka, maganarta ta kona masa zuciya amma ya dake, kifito falo mom tazo tanason magana damu, baijira meh zatace ba ya fitowarshi. Ko bayan yafito ankusa minti goma kan ta fito, zuwa tayi ta zauna a kujera mom ina kwana, mom ta karba masa da sakin fuska, aranta tace inbanda jaraba irin ta namiji meh mace irin ameerah meh zaiyi da wannan, a fili kuma tace bari karnabata lokaci nayi abunda ya kawoni. Bakomai bane jan kunne nazo nayi muku, musamman ma kai khaleed, rike mace 2 ba abune mai sauki ba, dolene ka kwatanta adalci kadda ka sake ka tauye hakkin wata akan wata, bawai dan kayi amarya zaisa ka wulakanta uwargidanka ba, duk wadda ka tauye hakkinta inaso kasani Allah zai tambiyeka, banason naji korafi daga kowane bangare, kaja girmanka matsayinka na miji, kadda kabari ko wacce ta rainaka, kazama kaine mai hukunci a gidanka, kadda ka sake kazama mijin tace, yazamana sai yanda mace tayi dakai, ku kuma ku rike mijinku hannu biyu kubashi hakkinsa, sannan ku kasance masu biyayya da zaman lafiya kadda, ku tadama mijinku hankali akodayaushe. Daga karshe khaleed inaso kasan ameerah marainiyace kariketa da kyau, kai ko matarka wani ya kuskura ya musguna mata wlh bazan yafe masa ba, duka, zagi ko wulakanci bazan lamunta ba, bare har abun yakaiga saki kadda ma kasake kayi wannan tinani, kagadai ko wata daya baku cika da aure ba amma ita da kanta ta roka maka har na amince da aurenka. Toh kuwa kadda kasake kace zaka wulakantata ko kai ko matarka, idan tamaka laifi ni kasanardani kan ka yanke hukunci, ke kuma kadda kiji na furta haka yasa kice zakiyi yanda kika ga dama, toh Allah kikayi wani abu har ya kawomin karaki zansa ya hukuntaki kwatankwacin laifin da kikayi, daga karshe Allah ya baku hakuri da zama lafiya mukace amin. Salmah kam maganar mom a ta banza ta ajiyeta, waima ita muke aure ko khaleed da zatazo ta wani yanke hukunci, shi kawai take nanatawa a ranta. Khaleed yayi gyaran murya yace mom inshaAllah zanyi iya kokarina naga cewa na kwatanta adalci, mom tace Allah ya baka iko, yakuma ya muku albarka, khaleed yace mom saidai munaso muje honeymoon idan kun amince, take naji zuciyata ta buga, nashiga 3 idan har sukaje honeymoon may b ma bazasu dawo ba. [9/15, 2:36 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/15, 6:57 AM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣5⃣3⃣ Mom tayi murmushi khaleed kamanta baka tafi honeymoon da matarka ta farko bane? Yace mom amma ita ameerah ita...... Mom ta katseshi nasani ai bacewa tayi bazataje ba an aje akan sai sunyi hutu zaku tafi kuma kaima ka amince da hakan, ta waigo wurina ke yaushe zakuyi hutun ne? Kausar ta amshe mom nan da wata dayane ai munkusa fara exams. Mom tace ni bacewa nayi bazakuje ba saidai kajira ka tafi da matarka ta farko, later katafi da ita salmar ko kuma ku tafi gabadaya, khaleed yace mom toh kibari mutafi nan da wata daya sai mu dawo kan ita tagama jarabawar, mom tace ban amince da haka ba dan yanzu mutum ake kiwo ba dabba ba, kowa yasan bakaje ko'ina da ameerah ba, yanzu sai kawai aga kafita waje da amaryarka, dama ana zargin wani mugun abun take maka shiyasa ka kirkiri kara aure bare yanzu agan kafita honeymoon da amarya ka barta a gida ai zargin mutane zai kara tabbatuwane, kaikasan idan kayi haka bakayi mata adalci ba dan ba wani abun tayimaka ba, ko tamaka wani laifin ne ka gayamin, girgiza kai yayi mom tace ke ameerah ko kinmasa wani abunne? Nace a'ah tace toh ko kinyarda su tafi din, khaleed na kallo naga ya kuromin ido, na sadda kaina dis time around i won't give in, nace mom duk hukuncin da kika yanke daidai ne shi zamubi, mom tace toh nidai ai kunji hukunci na, zabi ya rage naku, ko kutafi gabadaya nan da wata daya ko kuma katafi da ameerah first later katafi da amaryar taka, yace shikenan mom zamu jira, muka hada ido wata uwar harara ya watsomin, nace araina oho dai bandamu ba, bazan yarda wannan ta daukemin kai inaji ina gani ba. Saeed ne yayi sallamah ya shigo, yazo ya duka ya gaida mom, mom ta karba masa da fara'arta, yace bari nafita nagan kamar famly meeting ake, dama nazo duba ameerah ne, mom tace masa ai kaima famly ne ba inda zakaje, ka zauna dama inada maganar da nikeso zanyi dakai, kausar najin haka ta sunne kai kasa. Salmah dake zaune mamakin duniya ya isheta, ta dauka khaleed ya dauki wani mataki sai taji akasin haka, mikewa tayi tsaye waini dan Allah haryanzu Nigeria ba'a samu 'yancin kai bane? Kowa ya kallota bai fahimce meh take magana ba, saeed yace mata Nigeria tasamu independence tin 1960, tace ni banga alamun hakan ba saboda haryanzu ' ya'ya basuda 'yancin kansu, for goodness sake mu ba yara bane, we are all matured taya za'ayi ace na auri mijina amma bayada damar da zai yanke hukunci da matarsa saidai mahaifiyarsa ce zatayi hukunci, ita nake aure ne ko shi? Kowa baki bude yake kallonta. Khaleed ya daka mata tsawa salmah ki iya bakinki yakamata kisan da wacce kike magana, mahaifiyata ce ta isa dani, kuma ta isa ta yanke kowanne hukunci akaina, aljannata na kasan kafarta dole nayi mata biyayya. Tabe baki tayi, zan yadda da hukuncin ta idan har nasan mata biyu kake aure, mom da mamaki ya dabaibayeta tace toh mata nawa yake aure da? Salmah tace mace daya yake aure and daz me? Khaleed ya mike a fusace zaiyi kanta mom ta tareshi, salmah taci gaba idan kai matsoraci ne ka kasa fadin gaskia ni yau zan fada, mom bakomai tsakanin khaleed da ameerah, ba abunda ya taba shiga tsakaninshi da ita, asalima baya sonta ya aureta ne dan kawai kun matsa mishi, shine suka hada plan din aure da ita, da sharadin idan na dawo zai saketa tayi gidansu. Amma ni na lura yanzu, tazo ta saba da zaman daula, anfito daga gidan tsiya dama ai bazataso ta koma ba shiyasa take kokarin manne masa duk da tasan baya sonta, hawaye kawai ke sintiri a idanuna, salmah tace toh yanzu ai nadawo sai ka sallameta tayi gaba, idan kudi takeso ta fada nawane ni zanbata amma tabarmin mijina. [12/15, 7:31 AM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣5⃣4⃣ ji kake tas karar marin da khaleed ya saukarwa salmah saida falon ya amsa, ta dafe kunce da mamaki, khaleed ni ka mara dan na fadi gaskia? Yana huci yace mata yakamata kisan ni nasan darajar iyayena bazan lamunta da ayimusu rashin kunya barw har ki tsaya akanta kina gayamata magana ba, duk yanda nakesonki darajarki batayi ko rabin ta mahaifiyata ba, dan haka ki kula koda wasa kika kara gigin fadawa mahaifiyata magana wlh saina tattakaki anan wurin. Kausar tace toh aimu gwanda dangin talakawa da dangin marasa mutunci, dukda cewa ameerah talakace amma tasan girman na gaba da ita, tasan darajar dan adam dukda tasan cewa auren plan tayi hakan baisa tayiwa mom rashin kunya, mu tafiki sau dubu a wurinmu wlh, kuma inason kisan ba kwadayi yasa take zaune da broda ba biyayyace ta iyaye dan itama da wanda takeso dan ta farantawa nata iyayen take zaune da broda, ke kudinki basu tsinanana miki komai ba tinda sunkasa siyomiki tarbiyya. Mom tace ya isa kausar, wai ku kundauka bansan meh yake faruwa bane? Nasan komai zaman da suke da yanda akayi auren duk nasani, cikin mamaki muka dago kai muna kallon mom tace eh ameerah nasan komai, dukda nasan karya ba abuce mai kyau ba amma ni banyi danasanin haka ba, duk abunda kikaga Allah ya tsara akwai dalili, zuciyata ta natsu dake ameerah na yaba da tarbiyarki, nasan zaki rufawa mijinki asiri komai wuya, sannan ke macece da zaki iya sadaukar da farincikin ki domin farincikin na tare dake, shiyasa kwata-kwata ko bayan nasan gaskia banyi danasanin aurenku ba, kuma inaso ku manta da abunda ya faru ku baiwa aurenku dama ni ina hango alkhairi a ciki. Sannan ke da kike fadin rashinki yasa ya auri ameerah bakiji kunya ba ma? A lokacin da muke matsa masa da zancen aure ke kina ina? Meh ya hana ki dawo ki aureshi a lokacin idan har kina sonshi? Amma kika zabi zaman turai dukda cewa kin kammala karatunki, iyayenki ba magiyar da basu miko ba ki dawo kika ki, ko kindauka bamu sani bane? Tinda iyayenki basuda daraja a wurinki ni bazanyi mamaki dan kin gayamin magana ba. Inaso kisan wani abu ameerah tafiki daraja a wurina talauci ba abun kyama bane, dama kyawawan halaye sukesa aso mutum a zauna dashi ba kudinsa ba, kinci darajar dana yana sonki, kuma raba aure halin shaidannu ne Allah ma da kansa bayason saki, da yau na nunamiki irin darajar da nikeda a wurin mijin naki, da yau sai kinbar gidannan, salmah ta wuce da gudu tayi dakinta tana kuka, khaleed ya bita da ido duk tausayinta ya kamashi danshi duk abunda ya faru baisa yaji ya daina sonta ba. Saeed yaja tsaki dama itace macen da tasa ka nisanci ko wace mace? Dama itace salmar da kayiwa alkawarin zama da ita ita kadai a rayuwarka? Wlh tin wuri ka nemi chanji da wannan ba mace bace, khaleed ya watsa masa wata uwar harara. Mom tace wannan ai zancen banza ma yake, ama daina zancen yanzu, ameerah share hawayenki, kinfita daraja a wurina, kuma ki kwantar da hankalinki kiyi zaman aure kinji? Karki sake tinanin wai auren plan kukayi, kifara dauka aure kikayi kamar ko wace mace, na gyada mata kai kawai ina share kwalla, daga kai nayi muka hada ido da khaleed wani mugun kallo yayimin na dukadda kai kasa ina murmushi. [9/15, 2:37 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah abdul 1⃣5⃣5⃣ mom tace zauna saeed muyi magana, ya zauna duk muka tsura mata ido danjin abinda zatace, mom tace wannan zamanin yanada abun mamaki da yawa, rashin tarbiya yayi yawa, idan kaba yaranka freedom da yawa bakasan meh zasuje su kwaso maka ba, saeed wata alfarma nakeson kayimin, domin nidai tin kana yaro nasanka nasan halinka, zan iya bada shaida akanka, alfarma nakeson kayimin ko nace wata kyauta zanmaka, zuciyar kausar tafara bugawa da karfi, saeed yace mom duk abunda kike nema aguna indai inadashi ko ikonsa zanmiki, kifadi bukatarki kawai. Hayaniya mukaji ta barke a part din kausar sai shewa suke ga alama kawayenta ne sukazo, ihunsu kawai suke sunma hanamu jin komai, nace mom kutashi muje part dina may be zaifi dama, girgiza kai mom tayi Allah ya shirya tafasan duk muna zaune falonnan amma suka ishemu da ihu a gida kamar gidan kalcha, khaleed yace mom bari naje nayimusu magana, mom tace kabarshi kawai, ameerah muje part din naki, muka tashi mukatafi, saida na rurrufe ko'ina sannan muka samu dama-damar hayaniyarsu. Mom tace ai kunga irin abunda nake gudu, shiyasa nikeso nanemi wannan alfarma gunka saeed, ammafa ba dole, idan akwai abunda baimaka ba ka sanardani kawai kada kaji komai ni zanfahimceka, kausar gatanan nakeso nayi maka kyauta dan banason tayimin zabi irin na yayanta, zuciyar kausar kamar ta fito waje dan tsoron amsar da saeed zai bayar. Saeed yayi murmushi mom mace irin kausar bai kamata kice zakiyi kyautarta ba kamar wata er tsana, takai matsayin da ko wanne namiji zai iya sonta idan ya samu, amma a ganina mom yakamata muji ra'ayinta kafin mu yake hukunci. Mom tace kausar wai bakyason yayanki saeed? Kausar a kunyace ta tashi da gudu tayi dakina, mom tace ja'ira nidai nasan zabina bayada aibu, mukasa dariya, mom tace da fatar kagane amsar a yanzu? Gyada kai yayi wani farinciki yana ratsashi wa zaiki mace irin kausar, mom idan hakane bakomai na karbi tayinki Allah ya sanya alkhairi, mukace ameen, mom tace toh alhamdulillah nagode sosai duk sanda ka shirya zaka iya turo magabatanka, i'm glad ka amsa tayina, ba kamar abokinka ba muka kalli khaleed ya wani dukar dakai kamar wani mara gaskiya, mom tace na lura kamar ma ba jituwa tsakaninku dan Allah komai ya wuce ku daidaita, rashin aboki irinka agun khaleed ba karamin rashi bane, yana bukatar wanda zai rika saitashi a hanya, saeed yace bakomai mom zamu daidai ta bare yanzu zamu zama inlaws, mukasa dariya khaleed ya kaimasa duka amma kai bakada kunya fa, yanzu sai ka auri kanwata? Saeed yace ai ko yayarka ce zan aureta bare kanwa mukayi dariya mu duka. Mom tace toh mashaAllah tinda komai ya daidaita ni zantafi, sauran ku manta da abunda na gayamuku, you should give your marriage a chance kunji, kallon juna muka tsayayi har mom ta juya ta tafi, saida saeed yayi gyaran murya muka tina inda muke, mom fa ta tafi yacemin, da gudu nafita nabita har ta shige mota, nace mom har kin shige mota? Tace toh kin tsaya kallon mijinki ba dole na wuce na barku ba, a kunyace na dukar dakai mom tace ameerah just keep on trying, naga wani sirrin so a idon khaleed da yake kallonki dashi, watakila shi bai gano hakan ba, amma idan kika dage shi da kanshi zai gane har ya furta miki, ni zantafi taja motarta ta wuce, nayi wata sassanyar ajiyar zuciya na juya na koma falona. Koda na koma khaleed da saeed suna fira, khaleed nacewa friend bakasan damuwa da kadaici da na shiga ba da baka tare dani, saeed yace ai nasan baka iyayi saidani, khaleed yace oh yanzu da nayi bakai dinfa? Saeed yace ai shiyasa naga ka yamutse kamar ba ango ba, lokacin na shigo nace lallai yau kara'in abota ake, saeed yace wai ina ciwon kafar ne? Nace ni banida wani ciwon kafa inaga dai shida kanwarsa keson ganinka shiyasa suka hada plan, saeed yayi dariya oh really nace eh. [9/15, 2:37 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah abdul 1⃣5⃣6⃣ khaleed baki bude yake kallona, na daga masa gira ina dariya, wato mu zakiyiwa sharri ko? Nace ba wani sharri ba gashi kana fada masa kayi kewarsa ba? Saeed yace toh ni kiramin amaryar tawa ma mu zanta, nace iye lallai maza bakuda kunya? Wato yaya saeed haka zakayiwa antina ko? Dariya yayi toh wa zai ki kari? Kuma antin taki batada matsala zata amince, khaleed yace toh shine ni kake fushi dani din dan na nemi karin? Saeed yace ni ba karin aurenka ya dameni ba, yarinyar da kazama obsessed akantane, it turns out ma batada kunya, khaleed yace toh ya isheka dai, ai laifi akayimata, saeed yace laifin meh? Khaleed yace kishiya mana ai nasan ba macen da takeson kishiya sannan kuma honeymoon dinda mukeso muje mu sake shima cancel , saeed yace ai ita tayi wasa da damarta. Nace excuse me guy waye kishiyarta anan wurin? Ni ba kishiyarta brace yakamata ta gane, idan kuma ma haka ne ai ni akayiwa kishiyar ba ita ba, dan a bayana tazo, khaleed yace lallai yarinyar nan dama kinada baki ashe? Nace ai kai yakamata na tambaya dan nagan kana kokarin kare matarka, alhalin itace mai laifi, yace kudai kuka sani ni da badan wannan kawayen nata da suka damu mutane ba, da naje na lalla6a ta, nace malam if you are dat romantic ai kawayenta bazasu dameka ba, sai kaje ko a gabansu ka lallasheta, khaleed yace madam are you jelous, nace jealous of who? Dama ka fadi hakan ne just to make me jelous? Yace toh naga kin wani bata fuska dan nace zan lalla6a abata, dariya nayi da ta bayanna fararen hakorana, kaga malam it obvious matarka bata sona, so banga dalilin da zaisa nayi farinciki dan ka ambaci sunanta ba, ni dakai da ita kuje kuyi duk abunda kuka ga dama i really don't care amma dai a daina min zancenta a falona ehe, khaleed yace falonki ko falon gidana? Nace gidanka amma falona dan nikeda hakki a part dinnan as long as ina gidannan, khaleed ya taso yayo kaina wai yaushe kika rainani, ya bini da gudu muna zagayen falo muna dariya, saeed dai ya zama dan kallo dan anmanta dashi a falo, ya kusa chafkoni na afka dakina na datse kofa ina masa gwalo, komawa yayi baya yana dariya ya zauna, muryar saeed na jiyo nidai kifitomin da amaryata idan kungama soyayyar. Khaleed yace soyayya kuma? Saeed yace toh meh zance kiyayya kuka gama ne? Abokina ka kamu fa Allah blif it or not, you are just obsessed wit salmah but i can see a true love in your eyes for ameerah, khaleed yace kama daina zancennan ba abunda kake tinani bane, saeed yace toh gamu gani dai. Kausar na sama a daki tayi zugum, tana murmushi rungumeta nayi i'm really happy for you, mafarkinki ya kusa zama gaskia, zaki samu soyayyar wanda kikeso yaya saeed na sonki u are so lucky, how i wish nima zansamu nawa. Kausar tace may be baki lura bane amma ni na hango soyayyarki a idon broda, kibashi dan lokaci kawai shima zaigano ya kamu da sonki, nace i hope so dear, tashi muje yaya saeed nason magana dake, tace itadai kunya takeji nace kausar ai dole ne dan ku fahimci juns, naja hannunta muka fita, saeed na ganinmu ya Mike tsaye amaryata ki sameni a waje, kar su samana ido su hanamu jin dadin soyayya, ya mike yafita kausar tabi bayanshi, khaleed yace mara kunya binshi zakiyi? Abokina nane fa? Harara kausar ta watso masa ta ficewarta nasa dariya, karfa ka takurawa kanwata. Yace kanwarki? Ai ta girmeki, nace oho dai ai tinda nike auren yayanta tazama kanwata, khaleed yace dagaske ni mijinki ne? Harara na watso masa sannan nace haka naji ana cewa mukayi dariya, ashe duk abunda ake a idon salmah da kawayenta suna leke, shiru ne ya biyo baya a falon, bini - bini muna satar kallon juna, da muka hada ido na basar nace naji part din amaryar taka shiru ai sai ka tashi ka tafi ka tsaya kana kallon mutane, mikewa yayi tsaye yace hakane fa, yayi kamar zaiwuce sai ji nayi an damko ni, nafara er karar shagwaba ina kokarin zillewa, amma ya rikeni tamau jansa na rikay a haka shiko ya biyoni amma bai sakemin hannu ba. Ban ankara ba naje na buga kaina a gina, kara na saki wayyo mamata, nafara kuka shagwaba, rumfa yayimin da hannuwansa ba ta inda zanwuce? Wa kike gayawa magana tin dazu? Yaushe nafara wasa dake? Nafara hawaye kayi hakuri bazan kar ba, hannu naga ya daga kamar zai dokeni na runtse idona gam jikina ya fara bari, sai ji nayi ya fara gogemin hawayen da nike, kuramin ido yayi jin shiru yasa na bude idona, kallon juna mukeyi for quite sometimes, naji bazan iya jure hakan ba na sauke idona kasa, cemasa nayi khaleed please i'm sorry bazan ka.......... Ban kammala maganata ba naji bakinsa a nawa, tin ina kokarin kwace kaina har nagaji na kyaleshi jikina duk yayi sanyi nakasa komai, shiko baidaina abunda yakeyi ba, abun naji ya fara wuce gona da iri, na tureshi da karfi idonsa sun rikedi sunyi ja ya budesu dakyar ya kalleni, sai kuma ya juya da karfi ya nufi part dinshi, ni kuma nakoma kan seater na kwanta ina mayarda numfashi. [9/15, 2:38 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah abdul 1⃣5⃣7⃣ khaleed ya koma dakinsa ya fada kan gado yayi rub da ciki yana mayarda numfashi, wai dagaske na fara son yarinyar nan ne? A'ah inaga dai sha'awa ce kawai, idan haka ne kuwa dole na nisanceta dan idan nayi amfani da ita dan biyan bukatata kawai ban mata adalci ba, i have to be sure of my feelings first. Salmah kuwa tanan tana daukar shawarar abokai, a yanda sukaga khaleed da ameerah yau sun tabbata akwai so a tsakaninsu ita kadai dai yake fooling, wata tace a'ah ni a tunanina ma shi yake sonta dan kunga dai yadda ta tureshi daga jikinta, sukace kuma hakane fa. Salmah tace ai namiji munafuki ne wlh, shiyasa kwata-kwata i'm not into men, wannan auren ma tsautsayi ne, kuma ai duk laifinkune ku kuka rika zugani wai ankasani, wata macen ta ture sarautata, kunaga fa har marina yayi dazu a gabanta, ai tariga ta rainani dole na dauki mataki dan Allah ko zanbar gidannan sai na fitar da ita, dannifa bazama nazoyi ba bazan iya wannan rayuwar auren ba. Wata daga cikinsu tace ai salmah duk abunda zakiyi tinda mahaifiyarshi ke sonta bazaki iya sa ya saketa ba, dan gudun zuciyarta da yakeyi, hanya daya ta ragemiki ki aje duk wani jin kai ki nuna masa soyayya, ki janye hankalinshi daga kanta, idan ta lura batada wani muhimmanci a rayuwarsa dakanta zata nemi saki tayi gaba, tinda ita ba icce bace dole ta buqaci mijinta saidai kuma in duk mune, ta daga mata gira suka tafe. Salmah tace shikenan zangwada hakan naga idan zan iya, suka mike zasu tafi itako ta shiga dakinta tayi wanka, bayan tafito ta gyara kanta ta feshe jikinta, tasa wasu tsirarrun kaya ta nufi sashen khaleed. Yananan kwance rub da ciki taje ta hau kan gadon, ta dafashi sweetheart ya waigo ya bude ido dakyar ya kalleta, a yanda ya ganta yayi saurin kawar da kanshi idan banda mugunta yasan rigima kawai ta kawota mezaisa tayi wannan shigar? Kallonta ya sakeyi ta gefen ido sai yaga tayimai murmushi sabanin tunaninsa, janyo hannuwanta yayi ameerah please kiyi hakuri, ameerah ta maimaita a ranta lallai ma wannan, amma sai ta basar it ok aini yakamata na baka hakuri nice nayi laifi, kuma inaso kaba mom hakuri please on my behalf, shidai yakasa gasgata kunnuwansa sai kallonta yake, hannuwanta tasa ta tallabo fuskarsa, ya kayi shiru my baby ko bakayi hakuri bane? Girgiza mata kai kawai yayi bai ankara ba salmah ta fara kissing dinshi, ba bata lokaci ya fara maida mata da martani, cikin kankanen lokaci khaleed ya rikecewa salmah, nidai deejah nafita na basu wuri dan abun yafi karfin idona bari naje na leko ameerah yau khaleed ya angwance. Ameerah na kwance inda na barta idonta a rufe, abun duniya ya isheta shin dagaske khaleed dinta ya fara sonta ne? Wata zuciyar tace karki yaudare kanki wata kila sha'awa ce kawai kibari harki kara tabbatarwa, tana cikin haka sai ga kausar ta shigo da gudunta, ta fado mata ta Mike zaune a dan firgice, kausar tayi hugging dinta cike da farinciki i'm so happy today yaya saeed yana sona, nace congratulations dagoni tayi ya najiki haka ba kuzari, nace bakomai kausar bacci na fara kika tadani inaga shiyasa, tace ina broda ne ba nan na barshi ba? Nace mata ya tafi ai tindazu, ta tabe baki karki damu very soon kema zaki samu taki soyayyar, bari intashi intafi nace haba kausar yanzu tafiya zakiyi ki barni? Ki dawo nan gidan mana ki zauna, dariya tayi kamar dai wata karamar yarinya? Kiyi hakuri ai anan zamu rika zance da yaya saeed it possible ma kullum sai kin ganni, ta tashi tashiga daki ta hado kayanta, na mata rakiya ta fita. Khaleed kuwa yau ansamu nutsuwa ba laifi, salmah ma ta jinjina masa yakai jarumi dan ya wahalar da ita sosai toh abunka da sabon shiga, kwance suke a gado suna kallon ceiling, khaleed ya jawo salmah ta tureshi ni nagaji ka kyaleni bacci zanyi, kuma kaje ka nemo mana lunch kan natashi, bargo taja kawai tayi rufarta. Murmushi kawai yayi yatashi ya fada toilet yayi wanka, anyi kiran azahar yayo alwala yafito, salmah tayi bacci bai tasheta ba dan yasan ta gaji, yayi massalaci daga chan yayo mata takeaway a mr bigs shi kuma snacks da lemo kawai ya siyowa kansa, koda ya dawo stil tana bacci kuma gashi anyi la'asar tada ita yayi sannan ta tashi, wanka tayi a dakinsa kawai ta dauki ledar takeaway dinta tayi part dinta. [9/15, 2:40 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah abdul 1⃣5⃣8⃣ A haka dai rayuwa ta kasance a gidan khaleed, ameerah tin ranarda khaleed ya fita part dinta bai dawo ba, har ta fara zargin kanta maybe abunda ta masa ranar ne yasa yayi fushi amma ita bazata iya zuwa tabashi hakuri ba gaskiya ko main parlour da take zama yadaina shigowa duk inda ya ganta tashi yakeyi, abun duniya ya isheta. Abunda bata sani ba shima din a wahale yake, salmah sai taga dama take bashi kanta ba, kuma ko ta yarda dinma bazata bari yayi wani gamsuwa ba ta tureshi itafa ta gaji, kullum part dinta cike da kawayenta bayada sakewa da matarsa, abokanta sunfishi muhimmanci, fita take kuma son ranta duk inda taga dama, kuma sai taga dama zata dawo, shikansa ya rasa dalilin da yasa yakasa rabuwa da ita, ameerah kuwa ya kasa yadda da cewa sonta ne yake, dan duk dare sai yaje ya lekata tana bashi tausayi, amma abunda ya yarda dashi shine, rashin kulawar matarsa yasa yakejin kamar yana bukatar ameerah, da zaisamu kulawarta shi bazai ji hakan ba, kuma indai ba ya tabbatar da cewa yana sonta ba bazai amince da ya kusanceta ba. Kwanaki sai dada tafiya suke, anyi baikon kausar da saeed munyi exams na first semester har mungama, amma ba zancen zuwa honeymoon dan sarauniyarsa tace indai ba Germany za'aje ba ita ba inda zataje ya kyaleta, shiko yasan idan har ya amince da zuwa Germany ba tsira zaiyi ba dan ko chan tanada friends ba kulashi zatayi ba, da mom tamasa maganar honeymoon cewa yayi abar zancen kawai dan duk yayi magana damu munce munfasa zuwa, idan lokacin zuwa aikin hajji yayi sai abiya mana, da mom ta tambiyeni banmata gardama ba shiyasa ta kyalemu. Wasa-wasa har auren khaleed da salmah yayi wata 3, gashi har anfara shirye-shiryen auren kausar ansaka date nan da wata biyu, na zama nikadai sai rama nike, aunty fareedah kuwa banida damar zuwa wurinta dan kunyarta nike, tayita kiran wayata naki dagawa dan avoiding dinta nike, ga saudah na bauchi, khadijah nasir taje hutu minna, mama kuwa ko naje gida ba wani sakemin take ba, su suhaila ma na dan zuwa amma sai weekend, na roki mama ta bani ko khairi ko fatima su dawo wurina taki. Ranar ina zaune a falona na buga uban tagumi, sai sallamar anti fareedah naji, na karba mata amma duk na dabirce sai kame-kame nake, ta kuramin ido tana watsomin harara, tace yanzu Ameerah abunda kikayi kin kyauta kenan? Nace cikin sarkewar murya aunty fareedah dan Allah kiyi hakuri wlh ba laifina bane, wani mugun kallo ta wurgomin na dukar dakai, zuwa tayi taja hannuna muka zauna, ameerah mai kika daukeni ne? Kin dauka kawai dan saeed zai auri kausar nayi fushi dake? Shiyasa kike guduna bakya daukar call dina? Wlh ni kinban mamaki a lokacinda nike bukatar aboki kika gujeni, take kwalla ta cikomin ido kiyi hakuri wlh Allah kunyarki nikeji, gani nake duk ban kyauta miki ba, inaji ina gani zanbari ayimiki kishiya kuma kinsan yanda nike da kausar zaki doka ko ni na hadasu, murmushi tayi ni wlh banyi fushi dake ba, dan saeed zai auri kausar miye a ciki? Ni namayi farinciki da Allah yasa er gidan mutunci zai aura, kuma sanin yanda kuke da ita yasa hankalina ya kara kwanciya, dan nasan bazaki bari ta cutar dani ba. Kuka na fashe dashi na rungumeta Allah sarki antina u are d best, kiyi hakuri gudunki da nayi, tace bakomai ya wuce, har muna hada baki tare kowa yace ya naga duk kinyi rama? Mukayi dariya tacemin batada lfy ne yanzu bata cika lfy ba, amma banzo dubata ba, nace kiyi hakuri nauyinki nakeji, nakasa zuwa dubaki, tace ke kigayamin meyake damuwarki, na kwashe nagayamata, tayimin fada sosai, wai duk ni nayi sake abubuwan da duk ta koyamin na watsar, kuma ko sha'awar tawa yake miye a ciki ai mijina ne, ta haka zan janyoshi a jikina kulawar da zanbashi ita zatasa ya fara sona, nayimata godiya tare da alkawarin zan janyo mijina, na rakata ta tafi. [9/15, 2:41 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/16, 7:01 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣5⃣9⃣ bayan tafiyar aunty fareedah nida kaina, nayiwa kaina fada, wannan bazata fishsheni ba, na zauna ina jiran miracle, ko Allah ma yace tashi in taimakeka, tinda shi guduna yake ni zanbi duk wata hanya da zata sadani dashi batareda ya fahimci ra'ayinsa nike ja. Abunda na lakanta shine da safe sanda yake fita aiki, zanyi shigata cikin karamar riga da mini skirt, nashiga game field ina en tsalle-tsalle na wanda dole ne duk wanda yafito daga cikin gida zaifita dolene ya ganka, tin baya kulani har takai idan ya fito waje sai ya kir-kiri tsayawa yana wani goge-gogen mota da kakkabe kakkabe wanda baisaba haka, bini-bini ina satar kallonsa sai naga ni yake kallo, sai na cigaba da abunda nake, idan yaji alamun fitowar salma sai ya shiga mota ya wuce, dan dama ita yana fita itama zata fice. Yauma kamar kullum nasa rigana irin wannan da ake daurewa a daidai cibi, da wando 3 quarter, nafito ina buga basket ball da nagani a wurin, khaleed na fitowa yafara abunda ya saba, zuwa nayi na riko hannunsa, da mamaki yake mall on a, kannemasa ido nayi, nace the game is boring without a partner, can you play wit me please? Gyada mun kai kawai yayi, yana kallona nace kadaina kallona fa nima nan na iya games ninayi har game captain nayi a skul, yace oh really gashi kinsamu wani game captain din, nace oya let start and see the best player, mun fara buga game khaleed sai cheating yake yana saka ball da yake yafini tsayi kuma yafini karfi janyeni kawai yake ya saka ball, gefe na koma ina fushin shagwaba yazo yanamin dariya, nace Allah you are a cheater ni bazan yarda ba, janyoni yayi oya lets start a fair game yanzu bazanyi cheating ba i promised ya rike kunnensa alamun sorry. Game muka koma muka cigaba dayi munata kyalkyala dariya wannan karon nima na nunamai kwarewata dan nasa ball da yawa har yafarayimin tafi, ball din ya karbe ya daga sama na dinga tsalle inason na kamo yaki bari, zare ido na dingayi kamar naga wani abu a gabana, juyawa yayi da hanzari danganin meh nake zarewa ido, yana juyawa na karbe kwallon na sheka da gudu ina cemasa looser, biyoni yayi muka dinga gudu a compound muna dariya, hayaniyarmu tasa salmah ta fito, mune da gudu har cikin garden sai a garden din ya rikoni ta baya, muka zube akan grass carpet muna dariya, muna maida numfashi, zamewa nayi daga kan jikinsa na koma saide dinsa but still hannunmu a rike, kallon juna muka dingayi ba ko kyaftawa kamar masu son su karanto wani abu a idon junansu. Tabi mukaji anayi a bayanmu shi ya dawo damu daga duniyar da muka tafi, salmah ce taci uwar kwalliya, cewa tayi bravo romeo and juliet zance ko laila majnun? Wannan scene yayi kyau fa, oh sai ta ciro wayarta ta dinga daukarmu hotuna a yanda muke, khaleed ya taso a fusace miye haka? Kuma ina zakije kikasha kwalliya haka? Salmah tace meh ya dameka tinda kasamu mai debe maka kewa? Matatace ko kinada matsala da wannan? Har yaushe kika fara kula da al'amarina da har zaki nuna kishinki? Bakyason nasamu mai debemini kewa kike ko inkula da al'amurrana? Kuma nace ina zakije? Nidai da aka bari a zaune haushi kamar ya kasheni, ji nake kamar na shake salmah ta batamin show, tasowa nayi nace malamai ku bani hanya ni zanwuce, jayemin khaleed yayi na wuce ina takuna mai daukar hankali. Daga khaleed har matar tasa bin ameerah sukayi da ido har ta shige part dinta sannan suka waiwayo junansu, ga dukkanin alamu sunma manta abunda suke fada, khaleed hararar salmah kawai yayi yaja tsaki ya tafi yaja motarsa. [12/16, 7:35 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣6⃣0⃣ Ameerah ta koma daki ta kwanta haushi duk ya isheta, wannan salmar nidai ta isheni Allah oh God just helo me get rid of her na daga hannuna sama alamun addu'a. Ita kuma salmah dawowa tayi part dinta fitar ma ta kasa, sai safa da marwa take a tsakiyar parlour sai tayi kaman taje dakin ameerah sai kuma ta fasa ta dawo ta zauna. Chan kuma dai sai ta mike tsaye ta nufi sashen ameerah. Niko bayan nagaji da kwanciya, tashi nayi dan in watsa ruwa game dinda mukayi da gudu, duk yasa na gaji, toilet na shiga na watso ruwa nafito daure da towel, nazo ina goge jikina, na duka na goge kafafuna naji ana shafamin baya, take zuciyata tafara harbawa da sauri, a raina ina chewa yau na shiga 3 na tsokanowa kaina rigima, wato khaleed biyoni yayi, daurewa nayi na mike tsaye amma idona a rufe jikina har ya fara bari, sakaloni naji anyi ta bayana yasa na bude idona, ta madubi na hangota tana wani shu'umin murmushi, a razane na waigo da karfi dan inkara tabbatar da abunda idona ya gani a madubi, tabbas salmah ce toh meh takeyi a dakina? Meyasa kuma tazo tana shafani? Cikin tsawa nace malama meh ya kawoki dakina? Wani murmushi tayi, i never knew u ar so hot, ido na zaro nace what are you saying? Matsowa tayi ta tabani naja baya, kinga wallahi Allah karki tabani, murmushi tayi just relax deal nazo muyi dake, nasan kinason khaleed sosai amna kuma ni yakeso, ni kuma kinga kwata-kwata ba shine a gabana ba, cikin mamaki nake kallonta, idan kin amince akwai abunda nikeso kiyimin, ni kuma nayimiki alkawari zan barmiki khaleed, ni dakaina zanja ra'ayinshi a kanki, bakina na rawa nace meh kikeso? Wani shu'umin murmushi ta karayi ta lumshe idonta, it simple ta lakacemin hanci ke kawai nakeso, cikin rashin fahimta na kalleta, muryata a sarke nace mata ni kuma? Meh kike nufi da ni kikeso? Dariya tayi kinga tin zuwana a gidannan, banta6a tsayawa na karemiki kallo ba sai a yau, you are just my type sonki ya kamani kai tsaye, kuma naji ina sha'awarki ki amince dani kawai, matsalarki zata kare, idan kudi kike bukata zanbaki, kuma zaki samu mijinki. Har wani gumi ya karyomin inajin labari mace na neman mace amma ban yarda ba sai ayau, kokarin hada bakinta tayi da nawa ba shiri na tureta da karfi you animal just get d hell out of my room i'm nothing like you, dariya tayi kinga just relax duk abunda salmah keso zata samu, na shigo gidannan dan na fitar dake amma kuma I'm glad bukatata bata biya ba dan da na tafka asara, zan baki lokaci kiyi tinani akan abinda na gayamiki, amincewarki da bukatata shine zaman lafiyarki, amma idan kikaki wlh zakiyi da nasani dan bazan taba bari ki zauna lafiya ba, ta juya tw fita jikina na rawa naje na sawa kofata key nadawo na zauna jikina sai bari yake, dan a gaskiya na tsorata toh waini ya zanyi? [9/15, 2:42 PM] ‪+234 706 332 8523‬: 12/17, 8:27 AM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣6⃣1⃣ Inanan zaune wuri daya duk na takure kaina a daki da naji motsi sai na firgita, hawaye sai zuba sukemin, kiran sallah naji shiyasa na tashi naje sallah, na dauko qur'an ina karantawa, har akayi la'asar shima na tashi nayi sallah sai zabga addu'oi nake, ranar dai a daki na wuni ban ko leko waje ba, ga uwar yunwa inaji amma tsoro ya hana, bayan nayi sallar magrib naji ana bugamin kofa, muryar salmah naji da ita da kawayenta, take duk jikina ya fara rawa, wannan wacce irin masifa ce, sai cewa suke na bude kofa amma ina, sai chan naji wata tace kuzo mutafi jarababbu ku kyale er mutane, salmah tace ke nifa tinda nace muku tayimin ba hakura zanyi ba, ko yau ko gobe ne sai na biya bukatata, tinda nake a rayiwata ba macen da ta tafi da imani na kai tsaye har na rasa sukuni kamar wannan yarinyar, muryar da tayi magana dazu na karaji, atleast have some class kishiyarki ce fa, wlh dai kin bada mata kirasa watche zaki nema sai kishiya? Yanzu idan ta gayawa khaleed dinfa? Salmah dariya tayi ke aganinki zai yadda ne? Ki duba kigani koda akayi aurenmu mahaifoyarsa bataso, haka ma kanmensa da best friends dinsa, ba wanda ya halarci event ko daya na aurenmu, mahaifinsa ne kawai yaje daurin aure amma hakan baisa ya fasa aurena ba, kuma duk zaman da muke dashi for months duk garashi da nake baisa ya hakura dani ba, kuma nasan rashin kulawar da nike mishi yasa yafara kulata, amma ku yarda dani haryanzu su ba ma'aurata bane dan ba abunda ya shiga tsakaninsu, so kunga taje ma ta fada zata bata lokacin ta ne kawai, suka sheke da dariya, buga kofar ta karayi nasan kina ciki kuma kina jinmu kizo ki bude kofar nan, tinda ina sonki bazan cutar dake ba, wata shedaniyar murya naji, common baby ameerah mufa mata ne en uwanki baikamata kiji tsoron mu ba, nidai nakoma karshen gado na takure ina kuka mara sauti, wayata naji tana ringing amma tsoro ya hanani motsawa, sai chan naji shiru andaina buga kofar na sauke ajiyar zuciya. Khaleed kuwa yau a farinciki ya wuni, tunanin game dinda sukayi da ameerah kawai yake through out d day yana murmushi, aikin da ya tara office for months baiyi ba yau shi yake tayi, sallah kawai ke tadashi, idan yaji yunwa kuwa snacks ne abincinshi, bashi ya gama aiki ba sai 9.00 pm, sannan ya kamo hanyar gida. Ko da ya shigo part din ameerah ya nufa, kawai ji yayi yanason ganinta, ko da yake ya tura kofar yaji gam, har zai wuce yaji kamar sautin kuka a ciki, ya dawo ya fara buga kofa, ameerah ta daka tsalle ta mike tsaye ta koma karshen gado, magiya ta fara dan Allah kuyi hakuri ku kyaleni wallahi Allah bazan iya ba, ni zanbarmuku gidan gabadaya ma, wlh Allah zan kyale miki mijinki kiyi hakuri ki kyaleni, khaleed cikin rashin fahimta ya fara magana ameerah zo ki bude kofar nan, kunnenta ya jiyo mata kamar muryar khaleed amma gani take yaudararta suke, sai kara takurewa take a bango tana magiya. Cikin tashin hankali khaleed yayi part dinsa da gudu ya nemo spare keys, dariya yaji a falon salmah, itada kawayenta, take yayi recalling abunda yaji ameerah na fada, suyi hakuri zatabar gidan zata bar mata mijinta, does dat mean su suka tsoratata akan sai tabar gidan? Falon salmah ya nufa yana huci kamar wani zaki, tsaye kawai sukaga mutum akansu yana huci, ku da iyayenku meh kukayiwa matata? A tsorace suka waigoshi ganin yanayinshi yasa cikin su ya duri ruwa, salmah tunaninta kardai ameerah ta gayamasa kuma har ya yarda. [12/17, 9:14 AM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣6⃣2⃣ Wata tsawar ya daka musu ba magana nike muku ba? Wata figaggiyar ta fara magana haba angon salmah mu meh zamu yiwa matsiyaciyar matarka? Komai ta gaya maka karya take, take ya kifa mata wani wawan mari saida taga stars, dayar zatayi magana haba khaleed......... Bata karasa ba taji saukar nata marin, tuni salmah ta fara tsorata, a fusace ya fara magana duk er iskar da ta kara shigomin gida bare har tayi tinanin taba ameerah wlh sai ta raina kanta, nuna salmah yayi da yatsa wato dan kince na saki ameerah naki, mahaifiyata ta gayamiki bazata saku ba, shiyasa kika fito da wata hanyar dan ki tsoratata tabar gidan? Toh bari kiji ingayamiki bazan saketa ba, yanzu ma nafara zama da ita aurenki ba karani da komai ba sai bakinciki, keda baki damu dani ba, 'yan iskan kawayenki ma sufini daraja miye naki na kishi? So i' m giving you a last warning karki sake kikara zuwa inda matata take, ku kuma ku ficemin daga gida, kar er iskar da ta kara shigomin gida, cikin tsawa yace musu ku wuce nace da gudu suka fita, yaja jikinsa fuu yayi part din ameerah. Salmah ta sauke ajiyar zuciya, ohh abunda ta gayamishi kenan? Murmushin mugunta tayi, khaleed i'm so sorry fushinka bai dameni ba, nafi bukatar matarka a kanka, zuwa kusa da ita yanzu ma na fara, ta wuce dakinta. Shiko zuwa yayi yafara trying keys din yana kokarin bude kofa, jin haka ya kara firgita ameerah kukanta ya tsananta, tanajin anbude kofar ta kurma wani uban ihu ta dafe kanta, khaleed da ya firgita ya rasa meh sukayi mata ko suka gayamata da ta tsorata haka, zuwa yayi ya tabata khadijah jin ankirata da khadijah yasa ta daure ta bude idonta da sukayi jajir dan kuka da tashin hankali, da gudu ta afka jikinsa shiko ya rungumeta, tsayuwa ta gagaresu ya zauna da ita kan gado yana bubbuga bayanta, tayi shiru sai sauke ajiyar zuciya take, dagota yayi meh sukayi miki? Komawa tayi ta kwanta a kirjinsa tayi lamo, tana tuna maganar salmah ko ta gayamasa gaskiya bazai yarda ba, jin tayi yana cewa ba abunda zasu yimiki bazasu kara dawowa gidannan ba, da mamaki ta kalloshi ya gyada mata kai, tacd toh kome suka gayamasa oho, cewa yayi ameerah jikinki yayi zafi, tace yunwa nakeji banci komai ba tin safe, take ta bashi tausayi ya mike ina zuwa, da gudu ta bishi ta makaleshi karka barni anan please, tsoro nakeji cewa yayi toh dauko hijabinki da sauri ta jawo ta saka ta koma ta mannemasa a jiki shiko ya riketa tamau kamar mai gudun a kwace masa ita. Mota suka shiga suka fita, tsirai ya fara siya mata da naman kebab da youghurt tafara ci tin a mota tsabar yunwar da takeji, sukaje oasis bakery suka kwaso snacks da lemuna, aka dawo kusha shagalinku Junction suka kwashi kilishi da dambun nama kamar masu tsaraba, saida taci tayi kat sannan ta fara dawowa hayyacinta, cewa yayi toh nifa baza'a sammin ba? A baki ta dinga bashi yana karba, da haka har suka isa gida, suka kwashi kayansu suka nufi sashin ameerah duk a idon salmah. Bayan sunkoma daki ma hanashi fita tayi, saida ya jira tayi sallar isha'i, yace zaije dakinsa binshi tayi itafa bazai barta ita kadai ba yau tsoro takeji, sukaje yayi wanka ya fito, tana ganinsa ba riga ta dukunkune kanta, shidai murmushi yayi, yagama yasa sleeping dress dinsa yazo ya kwanta dan nesa da ita, a haka ameerah ta dinga jan jaki saida taji ta manna jikinta da na khaleed sannan taji ta nutsu, shiko yanajin haka ya kara jawota ya manne a kirjinsa yasa hannuwansa ya zagayeta, tare suka sauke wata ajiyar zuciya, da haka wani bacci mai dadi ya kwashesu. Jarababbiyar kuwa har cikin dare saida ta tashi taje sashen ameerah taji kofa gam, ta window taje tana lekawa tayi sa'a a bude, wayam taga dakin ba kowa, wani haushi taji wato khaleed dakinsa yaje da ameerah? Wani kishinsa taji yana shigarta ta juya taje dakinta, ranar dakyar ta samu bacci ya dauketa. TOH ALLAH UBANGIJI YA SHIRYARDA MASU HALI IRIN NA SALMAH, YAKARE EN UWANMU MATA DA AFKAWA IRIN WANNAN BALA'I AMIN. Like [9/15, 2:42 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/19, 7:06 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣6⃣9⃣ Shafa fuskarsa hawayenta na diga a wuyansa, haka yasa khaleed ya fara motsawa, ameerah ta rike hannunsa gam, sai kuwa gashi ya bude idonsa, tar sai a fuskar ameerah murmushi tayi masa shima ya maida mata yasa dago hannunsa ya goge mata hawayen yaga drip a hannunsa, cewa yayi why are you crying? Meh ya faru waige-waige ya fara ya ganshi a asibiti, dubawar da zaiyi sai ya hango salmah a kwance a dayan gadon, take ya fara tuna abunda ya faru dazu, aikuwa ba shiri ya ture ameerah mom dake kusa ta riketa, ya fizge drip dinda ke hannunsa yayi kan salmah. Kausar ta fita da gudu tayi waje takira dad da saeed da gudu suma suka shigo, khaleed kuwa har ya cakume wuyan salmah, hakan yasa ta bude ido a firgice ta fara wutsil-wutsil, saeed da dad sukayi kansa dakyar suka banbareshi ta mike cikin hanzari jikinta na bari, haka yayi daidai da shigowar iyayen salmah. Da gudu ta afka jikin mahaifinta tana kyarma khaleed kuwa sai zillewa yakeyi shi abarshi sai ya kasheta, dad ne ya wanka masa mari sannan ya dan nutsu, sai ya rungume dad yana kuka mai tsuma zuciya dad salmah ta cuceni, dad kuce ta jaye daganan banason ganinta, dad wlh na saketa saki uku take mahaifiyar salmah tasa kalima ai shikenan, dannan ba zaka ko tsaya ayi bahasi ba kayimata saki har 3? Amma yaron nan ka cucemu, yarinyar nan dakyar muka samu ta yarda zata aureka hakan yasa mukasan sosai take sonks, amma shine dan rashin mutunci zaka saketa a gabanmu? Mom tace hajiya ya kamata kafin kifara masifa kisan meh er ki tayi har aka saketan, dadyn salmah yace meh tayimishi da zafi haka? Mom a fusace tace toh mata takebi mijin nata bayada bambanci da fanko a wurinta, mom din salmah tace toh da maza kukeso ta rika bi? Ai nidai nasan salmah da yawan tara kawaye mata kuma nima inayimata fada akan haka, idan har tana biyar abokan ta bata kula mijinta ai wannan baici yamata saki 3 ba, kamata yayi ya gayamana sai muyi mata fada. Haushi ya ishi mom kamar ta kai mata duka, tace ace diyarki tana neman mata en uwanta har kice ba'a yimata adalci ba? Toh tinda sai anmiki gwari-gwari madigo takeyi, mata ke biyamata bukatarta itama auren bayada muhimmanci a gunta dan tafijin dadin mace akan mijinta. Mom din salmah ta fara girgiza kai tana kuka, sam wannan ba gaskiya bane, sam wannan kazafi kukayuwa 'yata, dama munsan bakwa kaunarta kun hada da kishiyarta kunyi mata kazafi dan ya saketa, toh ya saketa ku zuba ruwa kasa kusha, kuma wlh Allah sai ya sakamana mu kuncucemu. [12/19, 7:43 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣7⃣0⃣ Dadyn salmah ya fara masifa shima na yarda da abinda matata tace wannan kazafi ne, alhj khalipha kaban mamaki, taya za'ayi haka ta faru kana sane baka dauki mataki ba, dad ya daka masa tsawa alhj usman ya isa haka, ka dubi yanayin yarona ji yanda ya fita hayyacinsa, ji yanda yake kuka kamar mace sannan kace sharri aka yimata. Da idonsa ya ganta bawai gayamasa akayi ba, ga er takunan ta kartata idan karya akayi mata, dadyn salmah ya tambiyeta er Dady fadamin gaskia abunda suka fada gaskiya ne? Girgiza kai ta dingayi dad karya sukemin sharrin ameerah ne da kausar su suka shiryamin, khaleed ya zabura yayi kanta zai chakumota, dad da saeed na rikeshi dad kubari na kasheta kawai har tanada bakinda zata karyata da idona fa na kamata. Salmah tace dad mom kuzo mubar wurinnan tinda ya riga ya sakeni miye amfanin bada hakuri, sukace hakane kuwuce mutafi, kausar tace ku dakata, zuwa tayi gaban salmah ta tsaya kince karya muka miki ko? Toh ni inada prove din abinda kikayi. Salmah ta kara tsorata, tace mom dad kuzo mutafi karku saurareta karya takeyi, mom din salmah ta tsaya tace tanada prove ko? Inaso nagani da idona dan na tabbatarmusu da 'yata kazafi akayi mata, kausar ta zuge jakarta ta jawo wayarta video da ta dauka, ta kunna ta mika mata, take mom din salmah tayi suman tsaye, mijinta ya karbi wayar yana kallo take ya runtse idonsa wasu zazzafan hawaye na zuba, dad ya karbi wayar yakasa kallo ya runtse ido, mom ta ansa ta kalla itama tana Girgiza kai, saeed ya karba ya kalla cike da takaici, khaleed ya kwace wayar ya duba hawaye nata tsiyaya wata kara ya saka ya daga wayar sama ya watseta a kasa, saida kowa ya tsorata nan ya sake zubewa kasa, ameerah ta buga ihu tayi kansa tana Girgizashi, tana kuka mai tsuma zuciya, khaleed dan Allah ka tashi wlh idan ka mutu nima mutuwa zanyi, i can't live without you wake up please. Salmah taja iyayenta da bakinsu ya mutu, dad mutafi wani wawan mari ya sakar mata, ya tureta ta fadi salmah kin cucemu kin lalata rayuwarki, na turaki karatu ashe ke abunda kikajeyi kenan, wlh sai Allah ya saka mana, kije duk inda kikeso kiyi abunda kika ga dama, bani bake, tashi tayi dad nima bani na dorawa kaina ba Allah ne, uwarta tace karkiyiwa Allah karya wallahi ba haka Allah ya yiki ba, nima ba haka na haifoki ba chan kikaje kika koyo wannan muguwar dabi'a kuma mu ba'a gidanmu ba, cewa tayi shikenan tinda kukace haka nayimuku alkawarin bazaku kara ganina ba, zankoma chan inda akafi bukatata, dad kar ka manta sanda ka samomin admission a germany saidai naca banaso kace sai na tafi, so just don't blame me, kar Wanda ya sake yaje nemana kuma, daga yau ku dauka bakuda 'ya mai suna salmah ta ficewarta. Dadyn salmah yaja matarsa suna kuka sunkai bakin kofa ta silale kasa ta fadi, daidai shigowar doctors aka kwasheta aka dora kan gado su saeed sukayi kanta, wasu doctors sukayi kan khaleed. [9/15, 2:43 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/19, 6:36 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣7⃣1⃣ Doctors sunyi iya kokarinsu suka samo khaleed amma saida aka lika masa oxygen, doctor yayi ta fada yace a guje bata masa rai, duk wani abu da zai bata masa rai a nisanceshi. Mahaifiyar salmah kuwa jininta ne yayi mugun hawa, doctors sunyi iya kokarin su ganin sun saukar da hawan jini amma ina, take aka rasa ta ta rasu, dad din salmah yayi kuka kamar ransa zaifita, salmah kuwa tasha tsinuwa ba adadi, dad ne yaketa bashi baki aka dauki gawarta aka fita da ita aje ayimata sutura akaita makwancinta. Jikin kowa yayi sanyi, wannan tashin hankali har ina, fatar dai kawai Allah ya tsayar anan. Ameerah kuwa zaune take gadon khaleed sai mom tayi fada sannan take dagawa ko abinci sai anyi fada takeci, mama ma tazo asibitin mom tayi mata bayanin abunda ya faru, tayi mana Allah ya kyauta ta tafi. Kwanan khaleed biyu sannan aka cire masa oxygen ya dan farfado, abinci yanaci amma sai ruwa-ruwa, amma dai baya cewa kowa kala, fuskar nan a murtuke ba annuri. Satinmu daya aka sallamemu dan ya wartsake, saidai haryanzu baya fira saidai karamar magana, haka muka koma gida mom tasa anrufe part din salmah bayan sun kwashe kayan su, dan khaleed yama daina kula wurin da ta zauna bare ransa ya baci. Tinda muka dawo gida a kullum yana dakinsa zaune, baya ko fitowa saini da nike shiga ina kaimasa abinci kuma ba laifi yanaci, bayan haka ba abunda ke hadani dashi amma yau nayi kudurin nafara kokarin mantar dashi salma ya koma rayuwarsa. Sport wears na saka er body hug da mini skirt jajaye, naje kaimasa breakfast, na zauna har ya kare ci na kwashe kayan nafita yabini da kallo, koda na dawo yana kishingide yana karanta jarida, jaridar na kwace hannunsa ya kalloni da mamaki, ke miye haka nace nima zan karanta ne, cewa yayi bani kayana kinji, na mike tsaye na juya zan wuce yace ameerah kibani abuna nace, waigowa nayi ok zo karbi gashi, tsaki yaja ya taso zai kwace na dagata sama, hannun yabi zai karba na sake janyeta ina masa dariya, cewa yayi ina wasa dake ne? Daga masa gira nayi sai mu fara daga yau, matseni yayi zai kwata da karfi na wurgata waje ta window, hararata yayi ya juya zai koma ya kwanta, nace ashe ma matsoraci ne kai bansani ba, waigowa yayi ni kike cewa matsoraci? Gwalo nayi masa ya taso ya biyoni na sheka da gudu kuwa, gudu muke muna dariya muna zagaye gida najashi mukayi hanyar garden saida nakai karshe naja na tsaya ba wurin gudu kuma dan ya tare hanya sai matsowa yakeyi ina matsawa har na cimma gina, hannu yasa yayimin rumfa wa kike cewa matsoraci? Nayi shiru ina Girgiza kaina kawai, ya kuramin ido, baki yasa ya cizamin lebe nasa kara ke kin iya surutu ko, nace toh kaine kwana biyu kadaina magana kamar ina tare da kurma a gida ni kuwa kadaici ya dameni, daga kai yayi really nace eh mana, nima na cizar masa lebe, rike bakin yayi nayi sauri na tureshi, na sheka da gudu saida nayi nisa na juyo na masa gwalo, nima na rama girgiza kai kawai yayi yana dariya bai biyoni ba, ni ko na wuce dakina na fada gado ina mayarda numfashi. [12/19, 7:22 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣7⃣2⃣ inanan kwance har baci ya daukeni bani na farka ba sai karfe goma 12 agurguje naje kitchen na dora girki na gama na fito nashiga wanka na hado da alwala, kwalliya na tsaya na tsantsara, nikaina nasan nayi kyau nagama nayi sallah, sannan na fito naje dakin khaleed nakaimasa lunch, naga dakin wayam, na buda har toilet bayanan, naje falonsa da main falo duk bayanan, a dan tsorace naje waje ina dubawa motocinsa duk suna nan, garden nashiga na hango shi chan a rakube zaune, nace wato tinda nabar khaleed a wurinnan yananan kenan, zuwa nayi ina lababe, naje ta bayansa na rufe masa ido, ajiyar zuciya yayi khadijah kin rainani ko? Zagayowa nayi ina dariya, ya akayi kasan nice nadan turbune fuska, jawoni yayi na fado jikinsa, ke bakyaji ko? Ya shake kamshin jikina ya lumshe ido, na sakalo wuyansa ina murmushi, tinda nabarka anan kananan kenan? Girgiza min kai yayi tareda lakacemin hanci yanzu nazo daga masallaci na fito, nace oya tashi muje kayi lunch ya langabemin kai, bana iyaci banida karfi, dariya na kyalkyale kaganka kuwa? Kamar baby murmushi yayi kamanke dai, ke kika koyamin nace tashi mutafi, Girgiza min kai yayi bana iya tashi. Mikewa nayi tsaye, oya tashi in goyaka, mikewa yayi yace oya duka toh, na duka kuwa shiko ya dane baya aikuwa ragajab muka zube kasa, nasa kukan shagwaba shiko meh zaiyi idan ba dariya ba, dariya yake saida yakai kasa yana nunani, raguwa kawai na turbune fuska na fara bubbuga kafa ina kukan shagwaba, ni Allah sai na rama shiko dariya yaketayi, tashi nayi ina zumbure baki na kama hanyar wucewa ni namayi fushi dakai, janyoni yayi ta baya ya rungume i'm sorry, ya waigoni ya rike kunnensa yaje kasa ya taso i'm sorry nace, cewa nayi ni sai ka goyani, ba musu ya bani baya, na tattare skirt dina na dane ina dariya, jira nake naga ya fadi naga shiru, dukan bayansa nayi banga ka fadi ba, ya fashe da dariya waye kedince zaki kadani? Ni ko gudu ma sai inyi dake, shekawa yayi kuwa niko duk na tsorata na rikeshi gam na runtse ido ina ihu, ka tsaya karmu fadi muji ciwo fa. Bai direni ba sai dakinsa ya saukeni kan gado, ya juyo ya dubeni idona rufe gam, ji nayi ya cijemin lebe na bude ido ina sauke ajiyar zuciya, lakacemin hanci yayi matsoraciya, kece da tsoro kike cewa wani matsoraci, nace bawani nadauka zaka kadamu ne, hannunsa yaja ya tada muscle kinga ni mai karfi ne, hannu nasa na taba, nima na bude nawa hannun zan tada nawa amma banga komai ba, meh zaiyi inba dariya ba ke ko? Kin iya ba mutum dariya. Cewa nayi oya abincin ka, cewa yayi ok bari na watsa ruwa, ko zaki tayani? Kulalo ido nayi yayi dariya ok matsoraciya jirani inzo ya shige wanka abinsa. [9/15, 2:43 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/17, 7:22 PM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣6⃣3⃣ Kiran sallar asubah ya tadani na farka na ganni a kirjin khaleed, na tsaya ina kallon kyakkyawar fuskarsa, shima ya bude idonsa ya kalloni ya lakacemin hanci matsoraciya, ni dagani kiga kan a tada sallah, ko har masallacin zaki bini ne, narai narai nayi da ido zanyi kuka, ya janyeni gefe ya shiga toilet ya fito nima na shiga, fitowar da nayi instead of naga bayanan sai naganshi tsaye yana jirana, cewa yayi zo muyi jam'in kan ki taramin jama'a da ihu, bansan sanda na fara dariya ba shiko ya tsaya yana kallona yana murmushi, nazo nasaka hijabina mukayi sallah, bayan mungama azkar na jawo qur'an kan bed side drawer ina karantawa but a silent mode, khaleed yace read louder inaso naji nima gyadamasa kai nayi nafara rera karatuna shiko yana saurare da haka har gari yayi haske na ajiye kur'anin, yace zaki koma bacci ne? Nidai zanshiga wanka dan yau kafin 8 nikeso naje office, cemasa nima Allah bazan zauna ba, yace office din zakibini kenan? Nace eh dariya yayi shikenan bari na shiga wankan kije daki ki shirya kan nafito, gyada masa kai kawai nayi ya shige, fitowa nayi ina lababe zanje part dina kamar barauniya, da sanda na wuce wai duk dan kar aji takuna, nakai bakin kofa hannu na rawa na bude kofa na shige da sauri na rufo na mayarda key nacire key din na ajiye, na fada toilet shima nasa masa key, nayi wanka nafito daure da towel, naji ana bubbuga kofa, natsaya nayi jim aka sake bugawa cikin sarkewar murya nace waye, khaleed yace nine sarauniyar matsorata murmushi nayi na bude masa na janyoshi ciki na rufe kofa, cewa yayi wa kike especting ya shigo yanzu? Nace bakowa, kallona yafarayi sama har kasa, niko na juya ina goge jikina nafara shafa mai, zuwa yayi ya shafamin biya kamar yanda salmah tayimin jiya, na daka tsalle na kurma ihu na dane gado, a tsorace ya kalloni meh yafaru kuma? Ko tabanki da nayi ne? I'm really sorry i don't mean to scared you, bazan kara ba zo ki saka kayanki mutafi. Shi duk abun ya daure masa kai, dan na tabata ne tayi haka? Amma kuma ai a jikina ta kwana yau, meh mutanen nan suka mata ne da takasa natsuwa har yanzu? Kafin ya gama tinaninsa na saka riga doguwa ta atamfa dikin yayimin das a jiki, shidai sai bina yake da kallo, na feshe jikina da turaruka body spray na saka hijabina da takalmi kalar pattern din atamfana nace mutafi. Shidai ameerah ta birgeshi duk shigar da tayi indai fita zatayi zakaga hijabi zata saka, gashi ko batayi kwalliya ba kyau take, naturally beutiful, cewa yayi breakfast fa? Siyayyar da mukayi jiya na kwaso nace meh zakaci? Snacks naga ya kwasa nace kai baka gajiya da cin snacks ne? Yace ya na iya tinda matana basu iya girki ba, harararsa nayi ni Allah na iya girki, yace ke matatace? Wani kallo nayimai mai wuyar fassara muka hada baki tare yana kwaikwayon muryata mukace haka naji ana cewa, duka na kai masa ya goce yana dariya, muka fita na rufe kofa. Koda muka fita salmah na game field ko ta dauka zanjene oho, mota taga munwuce munshiga khaleed yaja muka fita, kwallon da ke hannunta tayi wurgi da ita cikin jin haushi, khaleed fa naso ya shiga gonarta, yana nufin bayan ya kwana da ita a dakinsa da safe ma bazai barta ba da ita zai dinga fita? I have to do something. Office dinsa mukaje kowa sai kawo gaisuwa yake, abunda ya farantamun rai duk wanda ya tambaya is she your madam? Yes yake cewa, haka mukayi ta zama a office dinsa, bini-bini ya kalloni, da nayi dogon motsi sai ya tambiyeni abunda nike bukata duk ya kasa tabuka wani abun kirki, karfe goma sha biyu nace masa zanje inda mom, tasowa yayi yace muje ya saukeni, koda ya kaini yace yaushe zanje gida? Nace ya barshi kawai kausar zata maidani idan na tashi, gyadamin kai yayi ya tafi niko na wuce ciki. [12/17, 7:54 PM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣6⃣4⃣ koda naje kausar ce zaune a falo tana ganina ta taso da gudunta oyoyo ta rungumeni, nace ba wani nan bayan kin manta dani yanzu sai yaya saeed kike yayi, ta marairaice Allah ba haka bane kiyi hakuri, natsani ganin wannan kishiyar takine, i hate naga broda yana kulata shiyasa na rage zuwa. Muka zauna tacemin ya kishiyar taki? Take taga nasha jinin jikina, nace mon fa? Tace batanan nikadai ce siyama na skul, ya naga kinyi wani zuru-zuru haka? Harda wani kodewa kikayi nace kausar ni bansan ma ta ina zanfara ba, tace fara ma ko daga ina I'm getting restless, nace mata kausar salmah is lesbian, kulalo ido tayi a tsorace, meh kikace? Taya akayi kika sani? Na kwashe duk abunda ya faru jiya na gayamata. Mikewa tayi tsaye tafara yawo a tsakiyat falo taje ta dawo, tasake dubana are you sure? Murmushin takaici nayi toh da karya zanmiki? Cewa tayi perfect daz great, nace miye wani perfect? Tazo ta jawoni tashi muje gidan, yau karshen zamanta da broda yazo, yau sai tabar gidannan, dakatar da ita nayi meh kike tinani? Kinaga idan kingayawa khaleed gaskiya zai yarda ne? Tace a'ah nasan bazai yarda ba, zai yarda ne kawai idan ya kamata red handed, just trust me kizo mutafi i have a perfect plan. Hijabinta ta dauko tasa ta jawo hannuna, muka kama hanyar waje sai naga ta jani zamu fita gate, nace ba ga motarki chan ba? Tace no bazamu tafi a motata ba, adaidaita sahu zamu shiga, binta kawai nayi batareda nasan meh take shiryawa ba, haka akayi kuwa adaidaita sahu muka shiga har kofar gida ya saukemu. Kausar ta leka gate, bakowa tajani muna lababe kamar barayi muka shiga, cemata nayi ke dalla sakeni tinda ba sata mukazo ba, cewa tayi banason salmah ta ganni ne bare tasan ina gidan, nace toh ma ai batanan ta fita duba kiga ba motarta ma, sannan ta sakeni muka taka muka shige part dina. Muna zaune a daki mukaji mota ta shigo gate, muka leka salmah ce kuwa, ta dawo ita kadai kuma, kausar tace perfect cewa tayi ina kayan da na siyomiki ranar? Nace mata suna wall drop, taje ta kwaso ta zube akan gado, wata ficiciyar riga ta zabo shara-shara da mini trouser ta mikomin, kisaka wannan yanzu, nace mata kausar have you gone mad? Ya zancemiki mace tana bibiyata kamar mayya, kice na saka wannan kuma? Ai dama wannan tsinannun kayan ne suka jamin masifa, instead of na jawo hankalin mijina sai na jawo wannan jakar. Dariya kausar tayi, just relax ai yanzu munriga munsan weak point dinta, dan haka ko yanzu zuwa zakiyi ki tsokano mana ita, nace wlh kausar bakida hankali, ni kinsan yanda nake tsoronta ma, jiya fa a dakin khaleed na kwana dan zama dakina ma gagarata yayi, dariya ta sake tace ai kin more kuwa yanzu dai karbi ki saka, nace saidai ke ki saka wolla, tace ai ke take kwadayi ba niba, indai har kinaso ta fita rayuwarku keda broda you have to trust me and wear dis, na karbi kayan naje toilet na chanja na fito, kausar tace wow kinganki kuwa so hot, harara na watsa mata, race the count down begins now. [9/15, 2:43 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/18, 7:29 AM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣6⃣5⃣ Kausar tace oya kije ki tsokanota nasan ai bazata rasa zama main parlour ba, kuma ko part dintane sai kije nace kausar you must be kidding me naja na zauna, tace sister inlaw joke apart Allah dagaske nake, nace kausar wai meh kike tinani ne? Nifa kar plan dinki ya ruftadani wlh i can't stand dat woman there, meh kikeso inyi na barta ta tabani ko meh? Kausar cikin fushi tace kefa Allah kincika tsoro nasan abunda nake, kije kawai ni bance ki bari ta tabaki ba, so kawai nake ta ganki a haka, nasan tinda ta kwallafa rai a kanki tana ganinki a haka hankalinta zai tashi, ki daure ki tafi kawai fatana kawai ta fada tarko, kina zuwa idan ta ganki ki dawo daki nasan zata biyoki idan tazo ta tarar dani ba abunda zata yimiki, nace ba kuma kince bakison ta ganki ba? Kausar tace eh banason tasan na shigo ne kawai but inaso tayimin ganin surprise just ki adana tambayoyinki kije kawai, girgiza kai nayi nace ni bansan inda kika dosa ba nafita na kama hanyar main falo fatana kawai tana ciki, dan bana fatar abinda zai kaini part dinta. Kamar da gaske na shiga main falo tana ciki kuwa, wani shedanin film take kallo irin nasu, da gudu na dawo dakina ina sheshsheka kamar watche aka biyo alhali ko ganina batayi ba, kausar ta mike da murnarta ta ganki ne? Na girgiza mata kai alamar a'ah tsaki taja ta dauki jakarta ni zantafi tinda kin gagara kiyi abunda na saki zamana anan bayada wani amfani Da sauri na sha gabanta kiyi hakuri wlh Allah zanje tace oya ki wuce toh, tsayawa tayi niko na wuce gabana na faduwa duk na waigo sai naga kausar ta tsare ni da ido, da haka har nakai kofar shiga na sake waigowa tayimin inkiya just go inside, wata ajiyar zuciya naja na sauke, sannan na dauki kasada na wuce ciki, ga dukannin alama tayi nisa da kallon abunda take kallo dan har yanayunta ya sauya kuma bataji ma shigowata ba, karfin hali nayi na wuce ta gabanta nayi gaban t.v zumbur ta mike tsaye zuwa nayi na dan duka kamar ina neman wani abu, muryarta naji daga bayana sweetie meh kike nema ne bari nazo na tayaki, da sauri na mike tsaye zuciyata kamar ta balle kirjina ta fito tsabar harbawar da take da sauri, innayi wasa fa zansamu heart attack take, amma dakewa nayi nace mata no wani movie nake nema bayanan ma inaga ba anan na ajiye ba, kallonta nayi wani fitinanne kalo takemin da wannan kattan idanun nata, sama da kasa take kallona tana hade yawu, ni ko na daskare wuri daya, cewa tayi naga fitarku da khaleed amma bansan kin dawo ba are you here for me? Wasu wahalallun yawu na hadiye, na daure na sakarmata wani murmushi, hakan ya kara mata karfin guiwa, wani murmushi tayi na cin nasara ta marairaicemin kai, Allah ina bukatarki ameerah, rashinki yasa nike kallon wannan ko zai ragemin abunda nikeji, amma abun sai dada karuwa yake, ke kadaice maganina ware hannunta tayi come to me please i will make you forget all your problems. Wani fitsari naji yana neman kuccemin, matsowa naga tanayi, sai da kama hanyar part dina ina ja da baya, just wait there please, girgiza mata kai nayi nace not here please, just follow me sai bina takeyi tana murmushi niko inaja da baya, da haka har nakai bakin kofar dakina naja na tsaya, tayi haka ta sakalo wuyana ta hango kausar a daki, sai naga taja ta tsaya, cewa nayi meyafaru? Bakya bukatana ne? Don't you want me anymore? Da ido ta dinga nunamin alamar induba bayana kamar tayi kuka, kausar nagani zaune tana ware ido, nace ohh kausar yaushe kika shigo? Tasowa tayi meh kikeyi tare da wannan? Nace oh salmah kike nufi? Mutum da abokin zamansa bazamuyi fira ba? Tabe baki tayi ku kuka sani, ni kinga zo inada magana, juyawa nayi wurin salmah i'm sorry nace mata can we chat later? Gyadamin kai kawai tayi amma fuskar nan tata tayi bakinkirin kamar ta kurma ihu, juyawa tayi kamar wadda kwai ya fashewa a ciki, kausar kuwa rufe baki kawai take dan takasa controling dariyarta. [12/18, 8:12 AM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣6⃣6⃣ tana shigewa falo kausar ta turo kofa ta fashe da dariya, kinga fuskar mutuniyarki kamar watche aka gayawa duk iyayenta sun mutu, tsalle taga na daka na sheka da gudu tace ke lfy nace ina zuwa toilet naje nayi fitsarin da ke kokarin fitomin tin dazu. Ina fitowa kausar ta taso miye? Nace fitsari kadan na saki fitsari a gaban salmah aradu, kausar ta kwashe da dariya matsoraciya kawai, ya kukayi ne? Na kwashe yanda akayi na gayamata dariya kamar cikinta zai fashe lallai za'a baki award kin iya acting, nace ai dole nayi acting kin turani gun wannan mayyar Allah da kin kwaso gawata dan da ta rikani inajin zuciyata ce zata buga, dan a tsorace nake daurewa kawai nayi, saida na kawo bakin kofar nan nadan samu nutsuwa shiyasa acting din ya kara kyau, nace ni namayi mamaki da ta kasa ganin yanayin tsoro a tare dani. Kausar tace yo ina zata gani, burinta kawai takai ga jikinki, nace ni ba wannan ba dai yanzu miye plan din kinsa na tsokanota, kausar tace kuma a yanda naga yanayinta ta zurma da yawa bazata iya hakura ba, fatana kawai tayi abunda nike bukata, and her game will be over soon, zo mutafi jan hannuna tayi muka labe a bakin kofar falo muna leke. Salmah ce sai kai da kawo take a falo, duk ta fita hayyacinta, wani abu mukaga ta kora da ruwa, taje ta zauna kan kujera ta rufe idonta chan wurin minti biyar mukaga ta mike kuma, wlh bazan iya ba, waya mukaga ta dauko jikinta har rawa yake, sury mukaji tace, sury where are you? Dan Allah come and help me ina cikin wani yanayi bazan iya jurewa ba, meh zangayamiki kinsan yanda na kwallafa rai akan yarinyar nan, yau har na samu kanta ita da kanta tazo wurina, amma wannan shegiyar kanwar khaleed ta bata komai, bansan ya akayi tazo gidan har ta shiga dakin ameerah bamu sani ba, gashi duk ta tadamin hankali just come here now please, karki damu bayanan kuma sai dare yake dawowa just come, eh zanbaki kudin ko nawane ma nidai kizo, alright ina jiranki karki dade, ta katse wayar Takoma ta zauna ta dafe kai. Kausar tace yes haka nakeso, ta koma daki da gudu ta dauko wayarta, nidai sai binta nake da ido, sai tace oh no bansan dadewan da zatayi bata iso ba bari na jira, cikin minti da baifi 20 ba saiga wata figaggiyar yarinya ta shigo gidan, kausar harda tsalle dan murna, cikin sauri naga tasa call hello broda cikin alamun tashin hankali take magana, khaleed na zaune yana aiki ya mike tsaye kausar lafiya? Broda salmah ce yace salmah ce tayi meh? Tace broda faduwa tayi yanzu batada lafiya, cikin tashin hankali khaleed yace what? Ganinan zuwa, ya kashe wayar ba ko takalmi ya fito office da gudu ya shiga mota ya tada ya fice da gudu, mutanen company sai mamaki suke kowa na tambayar dan uwansa meh ya samu oga? Amma ba wanda ya sani duk sun tsorata . Yarinyar na fadawa falo salmah ta tashi da sauri ta kankameta, suka fara shedancinsu tin a falo, kausar ta fido wayarta tayi zooming tana video recording, wai incase broda yazo late still dai ta samu evidence da zata nuna, tin a falo suka cirewa juna kayan jikinsu, sannan ita sury ta kwashi kayan taja salmah sukayi daki, dan ita salmar gabadaya ta fita hayyacinta. Kausar ta jani mukaje waje muka tsaya jiran isowar khaleed, shi kuwa tsiyace yake gudu ikon Allah kawai ne ke tafe dashi, yana kawowa gate yayi tsaya da mota dan baya ko iya jiran abude gate din, da gudu ya shigo gidan yana isowa gunmu yace ina salmah? Kausar tace munkaita a dakinta, cikin sauri ya shige yayi ciki nace kausar tsoro nikeji, wata uwar harara ta watsomin toh ya kikeso ayi? Taja tsaki matsoraciya kawai. [9/15, 2:44 PM] ‪+234 706 332 8523‬: 12/18, 3:50 PM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣6⃣7⃣ Khaleed na bude kofar salmah ya fada, da saure ya runtse idonsa yana furta ina lillahi wa ina ilaihi raji'un, fatansa kawai idan ya sake bude idonsa abunda ya gani ba dagaske bane, koda ya kara bude idonsa suna a yanda ya gansu, sun riga sun shagala da abunda sukeyi, wani karfi yazo masa ya tazgo gashin sury da take kan salmah ya makata a bango ta tsala wani uban ihu. Kararta tasa mukayi dakin da gudu, kanta ne khaleed ya buga a bango take ta suma a wurin, salmah kuwa jikinta ya hau mazari sai magiya takewa khaleed ya runtse idonsa hawaye kawai ke tsiyaya why salmah? Meyasa kika zabi wannan rayuwar? Meyasa kika aureni bayan kinsan da namiji baya birgeki, meyasa kika cuceni kika shigo rayuwata bayan kinsan bakida bukata dani a rayuwarki? Jan jikinta tayi taje wall drop ta jawo wata doguwar riga ta saka, zata wuce ya rikota, kura mata ido yayi yana zubarda hawaye, i said why? Wata tsawa ya daka mata i said why salmah? Ko mu dake gun muna kallo saida muka razana, wani wawan mari ya sakar mata nidai na tabbata taga wuta, ta dafe kunce wani marin ya sake bata answer me why? Tayi shiru takasa magana sai mazari jikinta keyi, marinta ya dingayi bako tsayawa abunka da farar mace har fuskarta tayi ja kumatu sunyi sutul-sutul, nikaina bansan sanda kuka ya fara zomin ba, zuwa nayi na fara kokarin kwatarta, wurgi dani yayi kaina ya daki gado nima take na sume, kausr ta buga ihu, amma ina khaleed yayi fushi, waje tayi da gudu ta kira wayar saeed please ko meh kakeyi kazo gidan khaleed yanzu. Cemata yayi yana ma kusa ga gun gashinan karasowa, kafin kausar ta koma daki khaleed ya shake salmah har idonta sun firfito, kausar taje iya karfinta tasa ta tureshi, amma wane ita, zuwa tayi tana yakushin shi itama tureta yayi ta bugi bango ta fadi, bakinta da kanta suka fashe amma bata suma ba, saeed ya shigo jin ihu gefen salmah yasa yayi chan da gudu. A firgice ya kalli dakin mutum uku a kwance, kausar tace just help zai kasheta Allah, yayi kan khaleed ya kwaci salmah dakyar amma saida khaleed ya makata dabango yana sakinta ta sulale tayi kasa itama a sume. Saeed cikin tsawa yace khaleed miye haka? Amma still kokarin janyo salmah yake wlh sai na kasheta tinda ta lalatamin rayuwa, saeed ya watsa masa wani gigitaccen mari sannan ya dawo hayyacinshi, amma sai kuma ya silale kasa ya some shima, saeed duk ya rikice yama rasa abinyi, ya kalli wannan ya kalli wanchan a rude, kausar tayi masa magana yaya saeed ka taimakamin na tsayarda wannan jinin, da gudu yafita mota ya dauko kayan aikinsa, yazo yayi mata dressing ta tashi tana jin jiri ta debo ruwa ta shafawa ameerah tana jijjigata amma bata motsi. Ta tsallake ta taje ta zubawa khaleed shima haka yaki motsawa, ta zubawa salmah ruwan itama haka, hannu ta dora akai yaya saeed munshiga 3 duk summutu, a firgice ya mike duk ya rikice kamar ba doctor ba ya rasa abunyi. [12/18, 7:23 PM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣6⃣8⃣ Saeed sai dawara yake a dakin ya taba wannan ya taba wanchan yana fadin kausar gayamin abunda ya faru please, itako kuka taketa rusawa yaya saeed duk laifinane Allah, ruwan hannunta ya karba ya zubawa sury dake bakin kofa, a firgice ta farka tana waige-waige, take ta tuna abunda ya faru ta debi kayanta a hannu tafita da gudu, sai a compound ta tsaya ta saka kayan. Saeed ya ciro wayarsa hannunsa na rawa, asibiti ya kira a turo masa ambulance da mutum uku za'a dauka, cikin minti da baifi ishirin ba akwa kwashesu sai asibiti, emergency aka wuce dasu likitoci suka hau kansu, kusan minti talatin ana fama kan asamo kansu, shifting dinsu akayi wani room batareda an rabasu ba. Sai a lokacin kausar ta dan samu nutsuwa ta kira mom, a firgice suka shigo asibitin kowa na tambayar meh ya faru? Kausar ta kasa bayani sai kuka take saida dad ya daka mata tsawa sannan ta fara bayanin abunda ya faru, su mom taslima suka shigayi, Allah ubangiji ya kiyaye gaba suka shige dakin, doctor ne ya shigo ya fara musu bayani, khaleed ya samu bugun zuciya ne nan take a nisanchi batamasa rai idan ba haka ba idan zuciyarsa ta kara bugawa za'a iya rasashi. Thesame goes wit ameerah, kanta ne ya bugu idan basu manta ba kwanan baya ma ta samu accident a kai, so buguwar kanta zai iya janwo matsala a kwakwalwarta, zata iya komawa comma kuma takan iya daukar lokaci mai tsawo bata farfado ba, kuma za'a iya rasata itama so akiyaye abunda zai sa buguwar kan nata. Amma wanchan patient din, ya nuna salmah wahala ce da tasha sanadiyar shake wuyanta da akayi amma da ta farka zata koma normal. Kausar tace tsinanniya itace da laifi en uwanane da samun matsala, Allah duk wanda muka rasa daga cikinsu itama sai ta mutu, mom tace calm down kausar kiyi addu'a kawai inshaAllah zasu tashi normal. Dad yace amma kausar karki sake ki sake aikata irin wannan haukar, wannan ai kuruciya ce tinda har kuka san gaskia ai ya kamata ku gayamana mu mu dauki mataki bawai kuje kuyi wannan kuruciyar ba, yanzu wa gari ya waya kun tona asirinta amma ki duba kiga abunda ya faru, zaki iya rasa dan uwanki da ita ameerar da kike ganin kin taimaka. Mom tace ya isa alhaj da tazo ta gayamaka zaka yarda ne? Ko shi dan naka zai yarda ne? Ai tunanin zakuyi dan bamu sonta ne muka lika mata sharri, wannan abun ya faru ne sanadiyar danka da baya iya controling fushinsa, kuskure daya tayi shine ta manta da yanda danuwan nata yake idan yayi fushi, kamata yayi ki nemo wasu da zasu iya taimakonku idan ya birkice tinda bayada hankali idan yayi fushi, kuma ai duk shi ya jawa kansa, yarinyar da ta zabi rayuwa da turawa kan iyayenta, dama ai dole asamu haka. Mu ka kira iyayenta su kwasheta kan ya farka ya ganta, ya kara haukace mana, tarin ameerah ya katsesu mom da kausar sukayi wurinta, dad shikuma ya fita ya kira iyayen salmah , kausar ta debo ruwa ta bata, waige-waige ta fara mom khaleed ya kasheta ko? Mom ta Girgiza mata kai tanada rai kinganta chan yanzu zata farka. Drip da ke hannunta take kokarin cirewa, mom zanga khaleed mom tace ki bari ruwan sunkusa karewa sai ki ganshi, rigima ameerah tasa kamar wata karamar yarinya itafa sai anbarta taga khaleed, dole saeed ya zo ya ciremata ruwan, kausar ta rikata sukaje wurin gadon khaleed. [9/15, 2:45 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/19, 6:36 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣7⃣1⃣ Doctors sunyi iya kokarinsu suka samo khaleed amma saida aka lika masa oxygen, doctor yayi ta fada yace a guje bata masa rai, duk wani abu da zai bata masa rai a nisanceshi. Mahaifiyar salmah kuwa jininta ne yayi mugun hawa, doctors sunyi iya kokarin su ganin sun saukar da hawan jini amma ina, take aka rasa ta ta rasu, dad din salmah yayi kuka kamar ransa zaifita, salmah kuwa tasha tsinuwa ba adadi, dad ne yaketa bashi baki aka dauki gawarta aka fita da ita aje ayimata sutura akaita makwancinta. Jikin kowa yayi sanyi, wannan tashin hankali har ina, fatar dai kawai Allah ya tsayar anan. Ameerah kuwa zaune take gadon khaleed sai mom tayi fada sannan take dagawa ko abinci sai anyi fada takeci, mama ma tazo asibitin mom tayi mata bayanin abunda ya faru, tayi mana Allah ya kyauta ta tafi. Kwanan khaleed biyu sannan aka cire masa oxygen ya dan farfado, abinci yanaci amma sai ruwa-ruwa, amma dai baya cewa kowa kala, fuskar nan a murtuke ba annuri. Satinmu daya aka sallamemu dan ya wartsake, saidai haryanzu baya fira saidai karamar magana, haka muka koma gida mom tasa anrufe part din salmah bayan sun kwashe kayan su, dan khaleed yama daina kula wurin da ta zauna bare ransa ya baci. Tinda muka dawo gida a kullum yana dakinsa zaune, baya ko fitowa saini da nike shiga ina kaimasa abinci kuma ba laifi yanaci, bayan haka ba abunda ke hadani dashi amma yau nayi kudurin nafara kokarin mantar dashi salma ya koma rayuwarsa. Sport wears na saka er body hug da mini skirt jajaye, naje kaimasa breakfast, na zauna har ya kare ci na kwashe kayan nafita yabini da kallo, koda na dawo yana kishingide yana karanta jarida, jaridar na kwace hannunsa ya kalloni da mamaki, ke miye haka nace nima zan karanta ne, cewa yayi bani kayana kinji, na mike tsaye na juya zan wuce yace ameerah kibani abuna nace, waigowa nayi ok zo karbi gashi, tsaki yaja ya taso zai kwace na dagata sama, hannun yabi zai karba na sake janyeta ina masa dariya, cewa yayi ina wasa dake ne? Daga masa gira nayi sai mu fara daga yau, matseni yayi zai kwata da karfi na wurgata waje ta window, hararata yayi ya juya zai koma ya kwanta, nace ashe ma matsoraci ne kai bansani ba, waigowa yayi ni kike cewa matsoraci? Gwalo nayi masa ya taso ya biyoni na sheka da gudu kuwa, gudu muke muna dariya muna zagaye gida najashi mukayi hanyar garden saida nakai karshe naja na tsaya ba wurin gudu kuma dan ya tare hanya sai matsowa yakeyi ina matsawa har na cimma gina, hannu yasa yayimin rumfa wa kike cewa matsoraci? Nayi shiru ina Girgiza kaina kawai, ya kuramin ido, baki yasa ya cizamin lebe nasa kara ke kin iya surutu ko, nace toh kaine kwana biyu kadaina magana kamar ina tare da kurma a gida ni kuwa kadaici ya dameni, daga kai yayi really nace eh mana, nima na cizar masa lebe, rike bakin yayi nayi sauri na tureshi, na sheka da gudu saida nayi nisa na juyo na masa gwalo, nima na rama girgiza kai kawai yayi yana dariya bai biyoni ba, ni ko na wuce dakina na fada gado ina mayarda numfashi. [12/19, 7:22 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣7⃣2⃣ inanan kwance har baci ya daukeni bani na farka ba sai karfe goma 12 agurguje naje kitchen na dora girki na gama na fito nashiga wanka na hado da alwala, kwalliya na tsaya na tsantsara, nikaina nasan nayi kyau nagama nayi sallah, sannan na fito naje dakin khaleed nakaimasa lunch, naga dakin wayam, na buda har toilet bayanan, naje falonsa da main falo duk bayanan, a dan tsorace naje waje ina dubawa motocinsa duk suna nan, garden nashiga na hango shi chan a rakube zaune, nace wato tinda nabar khaleed a wurinnan yananan kenan, zuwa nayi ina lababe, naje ta bayansa na rufe masa ido, ajiyar zuciya yayi khadijah kin rainani ko? Zagayowa nayi ina dariya, ya akayi kasan nice nadan turbune fuska, jawoni yayi na fado jikinsa, ke bakyaji ko? Ya shake kamshin jikina ya lumshe ido, na sakalo wuyansa ina murmushi, tinda nabarka anan kananan kenan? Girgiza min kai yayi tareda lakacemin hanci yanzu nazo daga masallaci na fito, nace oya tashi muje kayi lunch ya langabemin kai, bana iyaci banida karfi, dariya na kyalkyale kaganka kuwa? Kamar baby murmushi yayi kamanke dai, ke kika koyamin nace tashi mutafi, Girgiza min kai yayi bana iya tashi. Mikewa nayi tsaye, oya tashi in goyaka, mikewa yayi yace oya duka toh, na duka kuwa shiko ya dane baya aikuwa ragajab muka zube kasa, nasa kukan shagwaba shiko meh zaiyi idan ba dariya ba, dariya yake saida yakai kasa yana nunani, raguwa kawai na turbune fuska na fara bubbuga kafa ina kukan shagwaba, ni Allah sai na rama shiko dariya yaketayi, tashi nayi ina zumbure baki na kama hanyar wucewa ni namayi fushi dakai, janyoni yayi ta baya ya rungume i'm sorry, ya waigoni ya rike kunnensa yaje kasa ya taso i'm sorry nace, cewa nayi ni sai ka goyani, ba musu ya bani baya, na tattare skirt dina na dane ina dariya, jira nake naga ya fadi naga shiru, dukan bayansa nayi banga ka fadi ba, ya fashe da dariya waye kedince zaki kadani? Ni ko gudu ma sai inyi dake, shekawa yayi kuwa niko duk na tsorata na rikeshi gam na runtse ido ina ihu, ka tsaya karmu fadi muji ciwo fa. Bai direni ba sai dakinsa ya saukeni kan gado, ya juyo ya dubeni idona rufe gam, ji nayi ya cijemin lebe na bude ido ina sauke ajiyar zuciya, lakacemin hanci yayi matsoraciya, kece da tsoro kike cewa wani matsoraci, nace bawani nadauka zaka kadamu ne, hannunsa yaja ya tada muscle kinga ni mai karfi ne, hannu nasa na taba, nima na bude nawa hannun zan tada nawa amma banga komai ba, meh zaiyi inba dariya ba ke ko? Kin iya ba mutum dariya. Cewa nayi oya abincin ka, cewa yayi ok bari na watsa ruwa, ko zaki tayani? Kulalo ido nayi yayi dariya ok matsoraciya jirani inzo ya shige wanka abinsa. [9/15, 2:45 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/20, 7:21 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣7⃣5⃣ Saeed na baccinsa yaji karar waya ta dameshi ya jawo wayar yana tsaki, ganin khaleed ne yasa ya daga, khaleed a rikice yace saeed dan Allah kazo yanzu, saeed yace meh yafaru waye ba lafiya? Khaleed yace masa khadijah ce dan Allah kayi sauri, yace alright ganinan zuwa yanzu, aunty fareedah tana mitsitsiki ido my love badai aikin bane bayan kacemin bazakayi night ba yau? Cemata yayi yana kokarin sa kayansa khaleed ne ya kirani wai ameerah ce ba lafiya, aunty fareedah ta diro kan gado da sauri meh ya sameta? Saeed yace nima bansaniba itama ta zumbula riga tasaka hijab nima muje tare, Allah dai yasa ba haukar ce ta tashi ba ya dakarmin kawa ba, cikin sauri suka fice. Cikin minti ishirin suka iso gidan oga khaleed yana kofar gida yana kai da kawo sai gumi yake, saeed na isowa yagan khaleed a waje yace mutafi hope ba kan nata ka buge ba? Saeed har zaiyi part din ameerah khaleed yace masa no tana dakina, tinnan shidai jikinsa ya fara sanyi. Ameerah jin annufo dakin khaleed yasa tayi yunkuri tadan jawo bed sheet ta rufe jikinta, saeed na shiga kallo daya yayiwa ameerah ya gano bakin zaren, ya dubi khaleed da keta famar gumi da ganinshi kasan yana cikin tashin hankali kamar wanda yayi kisan kai, saeed dariya taso ta subucemasa ya gintse yace biyoni falo. Aunty fareedah kuwa ta sheka tayi kan ameerah ta tabata taji jikinta zafi gau, tace kawata meh ya faru? Ameerah ta daure ta bude idonta da sukayi jajir, cikin dasashshiyar muryarta tace aunty fareedah kincuceni sai hawaye suka zubo mata, ke kikace na amince da mijina amma bakicemin bakar wuya ake ci ba, aunty fareedah tace au dama ciwon kenan? Ta fashe da dariya toh congratulations, ai kinzama cikakkiyar mace yanzu, kuma kinzama ta khaleed aunty fareedah harda guda. Saeed kuwa suna fita da khaleed ya daure fuska yace dama abunda ka aikata kenan shine kawani kirani? Khaleed ya goge gumi kamar yayi kuka nidai kagayamin ya za'ayi daga baya kamin fadan, wlh Allah ni kaina bansan ya akayi haka ta faru ba, lokacin da na kusanci salmah banga tayi hakan ba. Saeed dariyar da yake boyewa tafito yayi dariya mai isarsa har yana buga kafa, khaleed duk ya kule wai kai wanne irin dan iskane? Ya zankiraka matana ba lfy katsaya kanamin dariya, sai yaji gudar aunty fareedah, khaleed yace ita kuma meh takeyiwa guda? Wai kunada hankali kuwa kai bakuga yanayin da take ciki bane? Saeed ya daure ya tsayarda dariyar i'm sorry my man ka iya aiki gaskiya, khaleed yace banason iskanci idan dariya zakumana ja matarka kutafi zan kaita asibiti yanzu yayi tsaki ya juya zai wuce, saeed ya rikoshi yanzu dai je ka hada ruwa masu zafi a bath tube ruwan da bazasu kona mutum ba kuma basu huce ba, tsaka-tsaki ka zuba detol kadan a ciki ka sakata sai kazo nayi maka bayani. Ya koma daki da hanzari koda yaje aunty fareedah ma ta hada ruwan, tace yauwa gwanda da kazo ni bazan juri wannan shagwabar ba daukota ka saka a ruwannan, yaje ya tallabota kamar wata baby duk ta nade a bed sheet sai dukunkune fuska take, ya shiga toilet yaje zare zanen gadon ameerah ta rike, murmushi kawai yayi ya cire zanin tayi saurin rufe fuskarta, yana sakata cikin ruwan ta buga wani ihu ta makaleshi, shiko duk ya rikice dawowa yayi da ita ya dora kan gado, bayan ya nadeta da bed sheet, ya dawo falo yacewa saeed ni bazan iya ba zafi takeji, saeed ya kalli aunty fareedah suka fashe da dariya. Aunty fareedah tace nasan har ranka kakejin kukan ta amma daurewa zakayi ka gasata idan dai kanaso ta samu releif, bakason taji zafi kayi mata abunda yafi ruwan zafi? Gumi ya share ya koma ya dauketa suka koma toilet din, tanaganin zai sakata ruwan ta makaleshi tana kuka zafi Allah zafi, khaleed harda hawaye yace khadijah i'm sorry but i must do this, sakata yayi tayi kara ya kauda kansa ya barta a ciki, sai chan yaji tayi shiru kuma, ya dubota kindaina jin zafin ta gyadamasa kai, ta kwanta a ruwan tace kafita zanyi wanka, yayi murmushi ya fita, aunty fareedah ta miko masa wasu kayan gashi ka bata ta saka, ya koma toilet din ta sa masa kukan shagwaba tareda rufe ido, nidai kafita nace, zuwa yayi ya dibi ruwan ya watsa mata, ni kuma? Miye bangani ba? Dukewa tayi a ruwan nidai kafita, ya mike ok ga kayanki nan, idan kin gama ki kirani ya fita ya nufi wurinsu saeed. [12/20, 7:53 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣7⃣6⃣ saeed yace ta gama? Khaleed yace a'ah saeed yace toh zauna, ya zauna yace khaleed nasan baka harkar mata amma banyi zaton bakasan komai ba akan abunda ke faruwa a daren farko gun wace mace cikakkiyar budurwa ba, Wannan wahalar da kaga ameerah tasha har ka rikice ko wacce mace indai cikakkiyar budurwa ce dole hakan ya faru da ita, wasu matan ma zaka samu bleeding sukeyi sosai su zubar da jini, amma ba kowace macece take zubar da wannan jinin ba, budurci wata fatace marar karfi da ake samu gun kowace mace budurwa, saidai wannan fatar takan yage ne ba ta hanyar saduwa kadai ba, wasu mata sukan rasa wannan fatar budurcin ba tareda sunsan miye da namiji ba, sukan iya rasata ta hanyar tsalle-tsalle, tsalake-tsallaken rami, hawan itace, hawan gina, hawan keke, daukar abu mai nauyi, da dai makamantansu, wasu matan kuma yawan ciwon mara ko tsananin ciwon mara kansa ayimusu wankin mara ta wannan hanyar zasu rasa budurcinsu, kuma mace ta rika yawan saka hannu ko yatsa a farjinta wannan yakan buda mace, yawan tsarki da ruwan sanyi a wurin mace shima yakan iya budasu, shiyasa ba lallai bane dan ka auri mace a daren farko bakaga ta fitarda jini ba kafara zargin er iskace ya kamata maza susan haka. Amma wasu matan wannan fatar budurcin zata zauna a jikinsu bata yageba har sai sunyi haihuwan fari, mata kala-kalane saidai duk macen da ta saba biyar maza, bazata taba zama daya da budurwa ba koda kuwa wannan fatar tata ta budurci ta yage, kadda wasu mata suyi amfani da wannan dama su rika yawon iskancinsu ba suyi tinanin mazansu bazasu gane ba. Salmah kuwa da kake cewa bakaga tayi hakan ba, dukda ba maza takebi ba mata takebi, wannan bazai hana kawar da budurcinta ba, kar mata suyi tinanin wai dan kina lesbianism ba maza kike bi ba, ki dauka kinanan cikakkiyar budurwarki, tsaf mace 'yar uwarki zata iya kawarda budurcinki ta hanyar amfank da hannu ko wasu abubuwan. Allah ya shiryarda masu aikata wannan aikin dan suna tareda fushin ubangijinsu. Abunda ya faru da ameerah is normal dan cikakkiyar budurwa ka aura saidai sanin a bukace kake bazakayi mata da sauki ba tinda tsohuwar matarka ta garaka, zaka iya jimata ciwo, dan haka kadubo idan ta fito wankan nayimata allura, ga kuma prescription na maganin da zaka siyo, sannan zan dubata idan ta yarda, khaleed yace ta yarda ko na yarda? Ai wallahi baka isa ka dubamin mata ba, zakayimata allura dai amma dubawar saidai muje asibiti doctor feenat ja'afar ta dubata badai kaiba, sukayi dariya yatashi ya shiga dakin. [9/15, 2:45 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/22, 6:04 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣8⃣0⃣ koda muka shiga hotel room dinmu sauke kayana kawai nayi na watsa ruwa, mukayi sallah nace ni yunwa nakeji, muka sauka kasa mukaje restaurant dinda ke tare da hotel din mukachi abinci, sannan muka shiga yawon gari muka fara siyayyah, bamu muka koma hotel room ba sai dare nashiga toilet na watsa ruwa na fito khaleed ma ya shiga, koda ya fito nasa night gown ya kalleni ya kauda kansa, na kwanta a gado ina jiran naga khaleed shima yazo ya kwanta sai naga ya dauki pillow da bargo ya fita, da yake dakin kamar room and parlour ne, komawa yayi falon ya kwanta a kujera, gajiya nayi da jiransa na taso na biyoshi, bargon da yake rufe dashi na yaye, na kwanta kan jikinsa na rufemu da bargon, take naji bugun zuciyarsa ya fara chanjawa, mikewa yayi zaune tare dani akan jikinsa ke miye haka? Gadon baya isarki ne? Nace ni tsoro nikeji ka barni ni kadai, tsaki yaja chan da kike bacci ke kadai fa? Dan Allah malama ki tashi ki koma ki kwanta idan na din kikeso na barmiki, ya koma ya kwanta ya barta tsaye, wasu zazzafan hawaye suka zubomin toh ni meh namasa na juya na wuce a fusace dakin, ya yaye bargon ya bita da ido, idonsa cike da kwalla, ranar dai duk bacci gagararsu yayi ido bude suka kwana, ameerah na tunanim meh ta masa shiko shikadai yasan abunda ke damunsa. Haka rayuwarmu dai ta kasance a dubai da safe idan munfita, khaleed na makale dani duk wani motsi nawa a idonsa, da dare kuma zai koma falo yayi kwanciyarsa, ganin nayi abun nashi rainin hankali ne ma, nima na daina kulashi dukda idan munfita da safe kausar kawai nakebi, da naga ya matso kusa dani na janye, idan ya riko hannuna na janye, ina ganin damuwa karara a fuskarsa amma na rasa gane meh yasa yakemin haka. Da yaga hakan saima ya daina biyarmu idan kausar tace muje sai yace shi ya gaji dama duk harkar matace muje kawai, nuna masa nake ban damu ba, nan ko kasan zuciyata kamar na kurma ihu, haka muke fita mu dawo mu sameshi a hotel room ya zama kamar wani mara lafiya. Haka muka kare kwananmu shida a dubai har ga gobe zamu dawo nigeria, bayan mundawo daga shopping nida kaisar, har mun bayarda kayan ta cargo zasu zo, wasu kananan kaya kawai zamu dauka a cikin kayan, na dawo nayi sallamah na shigo as usuall yana zaune yana kallonsa, na wuceshi na shiga daki nashiga toilet wanka, na fito daure da towel naganshi a bakin gado zaune, nayi kamar banganshi ba na cigaba da goge jikina, cewa yayi khadijah na waigo na kallesa ya kuramin ido kawai baice komai ba, nace malam lafiya dai? Ba amsa naje na juyawa ta dan towel dinda nake daure ya kwance ya fadi, na duka da sauri na dauko na daura idonsa kur a kaina, zumbur naga ya mike yayi fitarsa na bishi da kallon mamaki, zuciyata na suya, nayi sauri na saka night gown dina na nufi wurinshi dan naji meh ke damunsa. [12/22, 6:36 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣8⃣1⃣ Fita nayi na sameshi ya dafe kansa, na zauna kusa dashi, da wata murya mai kashe jiki nakemasa magana, khaleed meh ke damunka? Girgizamun kai yayi ba komai, nace ni bakamin kama da wanda ba abunda ke damunsa ba, ni namaka laifi? Ya girgizamin kai? Nace wani ya maka laifi? Shima dai ya girgizamin kan, nace ka gaji da zama dubai ne? Shima dai a'ah, nace toh menene ka gayamin dan Allah, yace ba komai nace ok salmah ka tina da ita ne? Wani mugun kallo yayimin nace yi hakuri toh kaki gayamin meh ke damunka, ok ni kagaji da zama dani ne? Wata uwar tsawa ya dakamin saida na firgita, ke dan Allah ki tashi ki bani wuri, kinzo kin isheni da tambayoyi bayan nacemiki bakomai, cikin kuka nayi hanyar daki, saida na kusa shiga na waigo naga ni yake kallo, nace indai nice inshaAllah bazan kara zuwa kusa dakai ba, kayi hakuri na shigewata na barshi nan tsaye. Daki na koma nasa kuka ni na matsu gari ya waye mu koma nigeria, dakyar bacci ya daukeni ranar, wurin khaleed ma haka take, gari na wayewa ameerah ta hada kayanta ta sauko ta wuce khaleed a daki, taje dakin kausar, kausar na ganinta tace ke sai jirgin sha biyu zamu tafi fa, nace haba na dauka na tara ne, tace har honeymoon din ya isheki? Na kalleta nayi murmushin yake, wannan ai ba honeymoon bane yawon siyayya dai mukazomiki kuma mungama, tace lafiyanki kuwa naganki wani iri, nace bakomai bacci kawai nikeji na kwanta abuna, tayi dariya broda ya hanaki bacci jiya kenan? Nace dan Allah malama kibarni nayi bacci, tace breakfast dinfa? Nace na yafe karki tadani kuma. Na juya nayi baccina. Karfe goma kausar ta sauko breakfast, khaleed sai wara ido yake yaga ameerah bai ganta ba, kausar na zuwa tayi dariya, miye kake wani ware ido tana dakina tana bacci tace kada na tada ita, yace lafiya? Tace oho ai kai za'a tambaya may be kai ka hana mata bacci jiya, tashi yayi, ya nufi dakin kausar ya tura ya shiga, gabanta yaje ya duka tanata baccinta ya shafa fuskarta, duk tausayinta ya kamashi i'm sorry khadijah i don't want to hurt you, ya tashi shima yaje bayanta ya kwanta, ya rungomota ya sauke ajiyar zuciya shima take bacci ya daukeshi. Kausar tagama breakfast ta dawo daki, koda ta duba taga sai baccinsu suke, murmushi kawai tayi soyayya ruwan zuma, wato tinda ba tayi breakfast ba shima ya fasa, gwanda susha baccin tare, nima Allah ya nunamin ina kwance a kirjin saeed dina, ta fito falo ta zauna ta barsu a dakin. Sai 11.20 taje tafara tadasu, ameerah na buda ido taganta a cikin jikin khaleed, itadai abun ya dauremata kai shi ke cewa ta kyaleshi kuma meh ya kawoshi gunta yanzu? Janye hannuwansa tayi ya bude ido, ta tashi tashiga toilet ta wanko fuskar ta, shiko ya koma dakinsu ya kwaso nashi kayan, suka kama hanyar airport. Ko a jirgi sai wani shan kamshi suke ba maiyiwa wani magana, sai ita da tafara bacci ya dora kanta a kafadarsa, itadai kausar bata dauka komai ba tinaninta duk cikin siyayyar ne. Suna saukowa jirgi direct gida aka wuce dasu dan mom bata dawo ba bare suje gaida ita, ana saukesu suka shiga gidan kowa part dinsa ya nufa. [9/15, 2:45 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/23, 7:29 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣8⃣2⃣ Haka dai zama ya kasance mana da khaleed baya zuwa part dina bana zuwa nashi, idan ma munhadu a hanya kowa zai kama gabansa na rasa dalilin haka, amma nidai na dauki alwashin bazan kara kai kaina gurinsa ba bare ya disga ni, na lura sai rama yake da baki, duk muka hadu zanga alamun yanason gayamin wani abun amma sai ya fasa, nima kuma sai na basar. Bikin kausar na matsowa dan yau sauran sati daya, shirye-shirye kawai akeyi, ni kuwa duk naje skul nadawo zanje gidan aunty fareedah bana wani tsayawa ayi shirye-shirye dani, kausar tayi masifa har tagaji, nace tayi hakuri baikamata na guji aunty fareedah yanzu ba, dukda ke kanwata ce itama kawatace kuma tanada muhimmanci sosai a gurina, dan nima lokacin da khaleed zai auro salmah ta tsayamin, da yake kausar mai hankali ce ta fahimta haka ma mom ta bani goyon baya, aunty fareedah kuwa taji dadin haka, tasan tanada muhimmanci a wurina ko kausar ta auri saeed bazan juya mata baya ba, duk da tana nunawa bakomai bane amma ni na tabbata tana juriya ne kawai dan ba macen da mijinta zaiyiwa kishiya tace bataji ciwon haka ba koma yane, shiyasa nima na boyemata tawa matsalar. Ana saura kwana 3 biki, Aliyu da salim suka zo, nida khaleed akace muje mu daukosu airport, na dade banyi farinciki irin na yau ba nayi missing danuwana rabin jiki, maimakon mutafi a mota daya kowa tasa yaja, muka nufi airport ina gaba khaleed na bina baya har muka sauka, ina hangosu na tashi da guduna na tafi inajin khaleed na kirana nayi banza dashi, naje na makalkale Aliyu cikin farinciki, yace sweet sis i missed you alot, nace nima danuwa, naje nayi hugging salim dake tsaye yana dariya khaleed ya shiga tsakani, ya jawoshi ya rungume, kannemin ido yayi, kinyi hugging dan uwanki nima kibari nayi nawa, na harareshi na basar troly aliyu naja, khaleed ya janyo aliyu yayi hugging ya hado dani, radamin yayi a kunne karki sake ki rungumemin danuwa idan hug kikeso i'm all free janye jikina nayi da sauri, a raina nace dan rainin hankali kawai, na basar nace salim ya karatun yace sis karatu ba dadi we missed home alot, nace gaskiya hakane no place like home, yanzu kwana nawa zakuyi mana yace a week, nace 1 week kawai danuwa, ya marairaicemin idan kikace na zauna ni da gudu zan tattaro kayana na dawo coz i missed you guys alot. Hannunsa naja na rike gam, tareda jawo trolynsa a dayan hannun, nace hakuri dai zakayi duk karatun kwana nawane zaku kammala very soon ku dawo, gida khaleed gyran murya yayi, ya shige tsakiyar mu, ya raba hannun cewa aliyu yayi excuse me broda inlaw this is my place, aliyu yayi dariya tareda jayewa hakanefa, bari na koma gefe nace wai miye haka mutum da danuwansa? Cewa yayi amma ai mutane zasu dauka saurayi da budurwa ne, baki bude na tsaya ina kallonsa, nace masa kanen nawa? Yace eh mana ko bakigan yafiki tsayi bane? Salim yaja aliyu danuwa muje kan sugama dramarsu mu shiga mota suka wuce suna dariya suka barmu a tsaye. Nace are you jelous? Yace yes ofcouurse i'm, dariya nayi just drop d act now, tin yaushe kafara kishina gira ya dagamin, tin ranar da kika zama tawa mana, murgudamasa baki nayi just stop pretending bayan ka daina kula dani, cewa yayi does dat hurt you? Nace ofcourse not dama indan ka batamin rai kakeyi kayi a banza na kara murgudamai baki. Jan bakin yayi wallahi idan kika kara murgudamin baki sai na baki hot kiss anan wurin, nace nan wurin with all these people you are not serious, jawoni yayi ya hada goshina da nashi, just dare me and see sai na nunamiki ni banida kunya i'll kiss yo here and right now, ganin nayi dagaske yake fa na tureshi na wuce gaba abina ina sauri, sai yanzu muka lura da su salim har sun wuce, khaleed yayi sauri ya cimmin ya rungumoni muka cigaba da tafiya, nidai na kyaleshi a raina sai mamaki nake shidai khaleed na rasa gane kansa, wani lokacin he'll make me fell like he love me wani lokacin kuma sai naji kamar banida wani muhimmanci a wurinshi [12/23, 8:13 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣8⃣3⃣ koda muka iso wurin mota duk sun shiga motata, cikin murnata na bude murfin driver na shiga, khaleed ya bude baya ya shiga, yace madam ya haka? Nace da akayi ya? Yace duk kin kwashe passengers din ni motata empty, nace toh ai dai passengers din ne suka zabi inda ya musu, nan ko sabuwar rigima ta kaure, salim yace toh wai wane kaudin ne yasa kuzo da mota biyu? Khaleed yace kasan halin mata so take tayi gasa dani, nace don't mind him salim ni bammasan daga inda yafito ba kowa hanyarsa daban, nidai mom tace nazo na daukeku, ai kuwa rigima muka dingayi har salim da aliyu suka fita motar suna dariya, salim yace danuwa idan muka biye wannan love birds din bazamuje gida da wuri ba, ni na lura basuda lokacin kowa sai kansu, yanzu dai ni bari naje motar broda kai ka zauna a ta sis mutafi, khaleed yayi kutsul yafito mota kai ka zauna anan din, Aliyu zo mu tafi a tawa, shidai yayi murmushi ya bishi, waigowa yayi yayimin gwalo akwai zancen da zamuyi tare ya sakaleshi a kafada suka tafi, naja motata muka wuce, ina gaba yana bina baya, bini-bini na kallesu ta mirror sai naga firarsu suketayi kuwa suna dariya, sabanin nida salim da bamuda abun cewa na lura ma bayason hayaniya da haka har muka isa gidansu khaleed, koda mukashiga duk anfito waje ana jiran isowarsu, sai murna akeyi bayan anzauna da minti goma mom tace su tashi su hau dining ga abincinsu chan. Mikewa nayi nace aliyu tashi muje gida su mama na jira, mom tace kibari yaci abinci mana, nace mom su mama sunriga sungama shirin zuwansa, idan yaje baici komai ba bazasuji dadi ba, mom tace hakane kuma duk da haka saida tayi packaging wasu abubuwa tace sai mun tafi dasu, naja aliyu zamu tafi khaleed ya taso muje ni zankai danuwana gida, wata harara na masa ya basar waishi dagaske kishin aliyu yake? Haka muka tafi yaja aliyu motarsa suka barni nikadai ins binsu a baya har muka isa gida. Khaleed dashi aka zauna dakin mama akayita fira da dariya, anan yaci abinci yayi komai, inason fira da danuwana ya hana, sai wuraren karfe goma mama tace mutashi mu tafi dare nayi, kuma taji dadi sosai ganinmu a haka, zargin da take ada duk ta daina yanzu ta yarda muna zaune lafiya. Mikewa nayi nace aliyu sai na shigo gobe akwai magana yace Allah ya kaimu muka fita, kowa ya shiga motarsa, kuma koda muka isa kowa part dinsa yayi kamar ba khaleed din dazu ba nace dan rainin hankali kamar nayi kuka dan haushi. Da safe kuwa ina shiryawa na kama hanyar gida, mama harda fada na dako uban sammako, anya ko breakfast nayiwa mijina? Nace mata eh kuma shi yace nazo, anan gida nayi breakfast munata fira, sai karfe goma sha daya aliyu ya fito, nace danuwa ansha bacci, sai azo abamu tsaraba ya fito dasu arabian gowns masu kyau da jewelries ya siyowa kowa mukayits murna. Nace danuwa nima inada gift kazo gida cikin motocina 3 ka zabi wadda tayimaka ya fara ihun murna, mama tayi sauri tace ba yanzu ba, sai ya kammala karatu tukunna zaidai iya zaba yanzu, aliyu yace bakomai ya amince tinda banan ma yake zaune ba yanzu. Nan nafara yimasa zancen kudina, harda 5 million dinda khaleed ya bani lokacin da zaiyi aure, Aliyu yayita mamaki aure kuma sis? Nace alkawarin da ya daukane ya cika, amma karka damu sun rabu ma yanzu, aliyu yayi hamdala, nan muka fara shawaran meh za'ayi da kudin. [9/15, 2:46 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/23, 2:23 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣8⃣5⃣ khaleed ne a zaune a office dinsa ya dafe kai hannun akan table, saeed yayi sallamah ya shigo, khaleed baimasan yayi ba, saida yazo ya tabashi firgigit ya motsa, ya bashi hannu suka gaisa da idonsa da sukayi ja, saeed ya zauna yace khaleed meh yake damunka ne wai? Yace bakomai friend bacci kawai na fara, ya shiryeshirye? Saeed yace kada kamaidani wani karamin yaro mana, ko wa ya kalleka yasan kana tattare da damuwa ji yanda kake rama, miye matsalarka ne? Mikewa yayi ya tashi na gayamaka bakomai fa, saeed yace just admit it ka kamu da soyayyar ameerah malam, kadaina tsayawa kana ba kanka wahala. Khaleed ya dawo ya zauna, ya akayi kasan haka, saeed yace gashinan rubuce a fuskarka, toh ni abunda ban fahimta ba shine ai matarkace yanzu miye matsalar? Khaleed yace ni gani nake kamar bata sona niko bazanso na chusa kaina a gunta ba batareda ta shirya ba, kuma friend duk lokacin da nayi kusa da ita take nake ganin ta fara chanja yanayi, alamun tsorona takeji tin bayan abunda ya faru, kuma ni duk lokacin da nake tare da ita i can't help it wata sha'awarta nakeji so shiyasa nake nisanta kaina da ita, dan kwata-kwata banason na cutar da ita. Saeed ya gyadakai amma ai kana cutuwa ko? Khaleed yace alot friend, i need my wife seriously saidai inaganin kamar she is not ready for me, but bazan iya boyewa ba na kamu da son ameerah, kuma kullum karuwa sonta yakeyi, saidai banason na cutar da ita ko kadan shiyasa nake nisantarta, but ina shan wahala friend ya share hawayen da suka zubo masa. Saeed dai kallonsa yake abun gwanin tausayi da dariya, dafa kafadarsa yayi friend ameerah batada matsala, kai yakamata ka nuna mata kana sonta wannan shi zaisa ta saki jiki da kai, kai zaka koya mata sonka, khaleed yace friend baka ganin har yanzu bata manta da tsohon saurayinta ba? Saeed ya hade dariyar da tazo masa, yace hmmm toh ai yariga ya rasu ko? Kai zaka mantar mata dashi ka gina soyayyarka a zuciyarta, maganar tsoro kuma wannan doleni taji tsoron tinda ita tasan wahalar da tasha a wannan daren, amma ai wahalar ba mai dorewa bace idan ta saba itada kanta zata daina jin tsoro, so kadaina tinanin cutar da ita zakayi, kai kuma ka cutar da kanka, ko kai waliyi ne? Harara khaleed yakai masa waliyi zaka sama a wannan yanayi da nake ciki? Suka fashe dariya suka tafe. Khaleed cikin zumudi yace zan dauki shawararka friend, zan mantar da ameerah koma waye a zuciyarta, saeed a ransa yace ashe ko kayi shirin yaki da kanka da ba wanda ke zuciyarta sai kai, a zahiri kuma yace hakan ya dace. Khaleed ya fito da waya bari na kirata friend, saeed yace bari nima na tafi gun amaryata asha soyayya lafiya, ya ficewarsa, khaleed ya koma gefe ya kame a kujera yana jujjuyawa yasa kiran ameerah. Ameerah na zaune wayarta tayi ringing ta dauko ganin sunan MY DREAM MAN barobaro a screen, saida ta kara goge idonta dan ta tabarta idonta ba gizo yake mata ba, a ranta kuwa addu'a take idan yaya saeed bai gayamasa komai ba, ta fita waje tayi tsohon dakinta ta daga wayar..... [12/23, 3:07 PM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣8⃣6⃣ Tana dagawa hello MY LOVE taji ya fito daga wayar, saida ta sake dubawa ta tabbatar idan khaleed dinta ne, yace SWEETHERT bakya jina ne? Har tsakiyar kanta sunan ya tsarata amma ta basar, kayi kuren number ne halan? Dariya yayi marar sauti inada wata sweetheart ce da ta wuceki, tace khadijah ce fa, tace yes khadijan khaleed ba nasani, wani dadi ya ratsata kamar tayi tsalle, yace my love where are you? Tace who is your lover? Yace ai nasan bakyasona ameerana but i love you tace na'am, yace yes kinjini ai i love you nd i love everything about you khadijah, kibani dama please zan tabbatar da cewa kinsoni kema, kuma bazaki yi danasani ba i promised, kina inane yanzun? Ameerah baki ya mutu baki, sai murmushi baki har kunne abun kamar a mafarki, saida ya kara cewa my love are you there? Tace yes ina gida gun mama, yace ok mu hadu a gida yanzu inaso mu fahimci juna, lets give our marriage a chance my shining star, gyadamasa kai tayi kamar yana ganinta, yace ok i'll be home in 15 minutes don't keep me waiting, kiss yayi mata a wayar ya kashe wayar ta sandare wuri daya, suhaila ce ta shigo ta girgizata wata kara tasa ta daka tsalle ta kankameta, su mama sukayo dakin da gudu, lafiya meh ya faru tsuru-tsuru ameerah tayi tana kyafkyafta ido tana kallonsu ta rasa abun cewa. Sai chan tace mama saudah ce ta kirani wai ta samu juna biyu, mama da kowa suka buga tsaki, shine kika cikamana gida da ihu? Allah ya shiryeki nace ameen na dukar dakai kasa ina dariya. Mama tajasu suka fita, saida nayi tsallena da ihu marar sauti sannan na fita nayi dakin mama. Ina shiga na dauki jakata da hijabina nace mama zantafi, tace bayan kince yau kina gida sai dare, nace mama mom ke nemana, tace shikenan a sauka lafiya khairi ya mike aunty ameerah zanbiki, na kwalalo ido kaga yaro yanaso ya kwafsamin, na kalli mama ina jira tace bazai bini ba, tace miye kike kallona ku tafi ni bazan hana ba, na sosa keya nace mama kinga nasan ma kasuwa zamuje, bazan iya yawo dashi ba, mama tace da yake akai zaki dorashi ba, sai kibarshi a gidan yayi wasa da siyama kan ku dawo, nace toh zo mutafi kamar na makeshi nakeji, na jawoshi na jefa bayan mota na shiga na tada. Gidansu khaleed na fara biyawa na sauke khairi, sai tsaidani ake ina zillewa hankalina na gun khaleed, saida nayi karyar ciwon kai mom tace naje na huta toh, nace khairi ya zauna nan zandawo anjima kadan na daukeshi na fita da gudu-gudu na shiga motata na nufi gida. Koda na isa na tarar da motar khaleed, nayi murmushi har zanwuce part dina, nace nariga na makara dai bari naje kar yayi fushi, ina buda part dinsa, wani sanyayyen kamshi ya daki hancina, wurin anmasa decoration da flowers ga wani slow music yana tashi and disco light ne kawai ke haska wurin, tura dakinsa nayi shima duk anyi decorating yana zaune kan gado, sallamah nayi na shiga ya dago kansa idonsa sun kada sunyi jajir, take zuciyata ta buga muryata na rawa nace i'm sorry i don't mean to be late, wani mugun kallo ya watsomin karki sake ki zo kusa dani yace cikin tsawa, mamaki yasa na sandare hawaye naga suna zuba a idonsa na matsa gunsa, khaleed what is wrong wit you? Fuskarsa na dago yasa hannunsa ya tureni nayi taga-taga na fadi kasa. [9/15, 2:46 PM] ‪+234 706 332 8523‬: 12/23, 4:15 PM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣8⃣7⃣ Ameerah na kwance a kasa duk tsoro ya kamata, toh ko bada khaleed tayi waya bane dazun? Tace no amma duk wannan decoration fa? Toh kodai gamo yayi kafin nazo? Ita kadai ke jerawa kanta tambayoyin da ba amsarsu. Khaleed ya tashi ya fara daukar frames frames dinda ya lika yana fashewa, fulawoyin ma ya dauka yana fasawa decoration din dakin duk ya wargazashi kamar wani zararre, mikewa ameerah tayi jikinta na rawa ta koma falo tasa kiran saeed, jikinta na kyarma muryarta na rawa tace yaya saeed kazo yanzu please khaleed ya haukace sai fasa kaya yake kar ya jiwa kansa, saeed na tareda kausar ya jawo mota da gudun fitar arziki, kausar duk ta tsorata yakasa gayamata komai, yana isowa gidan da gudunsa ya shiga gidan ameerah na waje tana kuka tana yarfe hannu, dan khaleed na falo yana kashe kayan falon da ya jera, saeed ya shiga da Gifu ciki ya rikeshi, kokawa suka dingayi dashi, yana saeed ka sakeni i don't want to live anymore hannunsa duk jini yake zubarwa, saeed yace kausar mikomin jakata da sauri a mota, da gudu taje ta dauko ta dawo, ya saki khaleed din ya cigaba da fashe fashensa ya fara hada wata allura, yace kuzo ku rikeminshi, muka matso sai nunani yake kadda ki sake ki tabani kasheki zanyi Allah kika tabani, saeed yace ku dakata, zuwa yayi ya dannesa iya karfinsa yace mi komin dankwalinki na cire na mika masa, yasa ya daure hannuwansa ya masa allura, sai cewa yake saeed sakeni da hankalina kabarni na mutu na kawai. Cikin minti da basufi biyar ba yayi bacci, kowa kuka saeed duk jjriyarsa saida yayi hawaye, sannan ya tambayeni meh ya faru, na kwashe na gayamasa, yace ameerah da abunda ya faru dashi, ba hauka yake ba dan komeh yake ya sani, kuma ba wanda bai ganeba daga cikinmu, komeh ya faru a kanki ne dan ke yake cewa karki tabashi, hannu na dora akai nace ni wallahi banyi komai ba, saeed yace bari mu jira ya farfado nan da awa biyu, amma ku gyara wurin nan duk wani abu da zai iya fasawa ku kwasheshi, haka muka shiga gyaran dakin da falo nida kausar har muka gama, aka daukeshi aka mayar daki, kausar na kuka tace bari na kira mom, saeed yace no karki daga musu hankali, kibari sai idan munga abin yafi karfinmu. Zuwa nayi na dora kaina a jikin khaleed ina kuka, inanan har bacci ya fara daukana, naji alamun ya fara motsawa, na tashi nayi kansa ina jijjigashi, saeed da kausar suka shigo, koda ya bude idonsa tar akaina, ya kuramin ido kamar mai tinanin wani abu, yasa hannu ya fara gogemin hawayen, na jawo hannusa na kankame ina kuka, ganin saeed yasa ya tuno abunda ya faru, qwace hannunsa yayi yasa hannu biyu iya karfinsa ya tureni nasha kasa na buge baki ya fara jini, yana kuka yace saeed kace tafita ta barmin dakina banason ganinta, saeed yace kausar ta jani mu tafi part dina zaiyi magana da shi. Kausar jiki a sanyaye ta dagani muka tashi, mukayi dakina, nida ita ba mai rarrashin wani, sai kuka muke, saeed yaje ya zauna ya dafa kafadar khaleed, meh yake faruwa? Bayan na barka a office zaka kira ameerah ku sasanta meh kuma ya faru? Karka damu ka gayamin gaskiya na maka alkawari idan har batada gaskia zan goyi bayanka , ka gayamin kawai, khaleed ya runtse idonsa wasu hawaye na zuba ya fara magana kamai zai hadiye zuciya ya mutu. Bayan nafito office na tsaya nayi siyayya nazo gida na samu bata iso ba, nazo part dina na fara decoration, bayan nagama naga har yanzu bata iso ba, nayi tinanin ko ta dawo dakinta kunya ta hanata shigowa, na tashi naje na duba, koda na shiga batanan, sai na samu kaina da yimata bincike, ko zansamu clue akan wani abu da takeso nayi suprising dinta. Akan bed side drawer na hango wani envelope ajiye na jawo dan naga meh ke ciki, ya runtse ido wasu hawayen suka zubo, saeed yace meh ka gani? Da hannu ya nuna masa gefen gadonsa saeed ya jawo ya buda envelope din, abunda ya gani saida numfashinsa ya dauke na wucin gadi ya dawo, zumbur ya mike yayi dakin ameerah. [12/23, 4:57 PM] Deejah Abdul: Dream girl na deejah abdul 1⃣8⃣8⃣ Saeed ya bankado kofa ya shigo, nida kausar muka mike har muna hada baki meh ya sameshi? Saeed yayimin wani kallo ya wurgomin envelope din, na dauka jikina na kyarma tashin hankali ya rufeni wani gumi ya tsatstsafomin, jiki na kyarma na buda hotunan, Ameerah ce kwance tana kyalkyala dariya da wasu kananan kaya, salmah tsirara a gefenta itama tana dariya, wani hoton kuma surry ce da salmah a tsirara sunsa ameerah a tsakiya kowacce hannunta daya nakan breast din ameerah, da wata gajeruwar letter don't worry sweet ameerah kinsan bazan juri rashinki 4 long ba naje germany amma zandawo soon 4u, kicigaba da zuwa sury tana debemiki kewa nasan mijinki ba wani damuwa yayi dakeba, kema kadda ki damu dashi, zamu debemiki kewarsa. Your desperate lover salmah ga wannan pictures din dafatar zasu debe miki kewa kafin na dawo. xoxo Wani jiri ya debeni take na shide a warin na fadi a sume, kausar ta dauki hotunan da letter ta duba take tayi suman tsaye, baki bude hawaye na kwararo mata, saeed a fusace yace can you guys explain dis? Tace yaya saeed wannan wallahi sharri ne, yace ta tashi tayi mana bayanin abunda ke faruwa, zuwa tayi ta tabani, a firgice ta juyo tace yaya saeed bata motsi a fusace yace je ki dobomin ruwa, ta shiga toilet ta debo ruwan tazo tana shafamin, karbe ruwan yayi ya kwaramin su a firgice na tashi, ina fitarda numfashi dakyar, saeed ya duko ya tsare ni da ido can you explain dis ya sake nunomun hotunan na karba ina hawaye, tabbas ba wanda zaice wannan editing ne ko waye yayi wannan hotunan kwararrene, yaya saeed cikin fushi yace ke nake jira fa kin tsayardani, kuka yaci karfina, kausar tace kayimata a hankali mana, ta debo ruwa tabani nasha ina sauke ajiyar zuciya. Nace yaya saeed wallahi Allah wannan sharri ne, ni bamma taba ganin hotunan ba sai yanzu da ka kawosu, da khaleed ya kalli hotunan nan very closely zai gano ko wanne photo ne wannan akayi editing, saeed ya kalloni yace kamar ya? Nace akwai ranar da na saka wannan kayan har mukayi basket ball da khaleed, ranar na tsokani khaleed ya bini, mukayita gudu a gidan har mukaje garden mun gaji muka zube a kasa muna dariya, a hakan salmah ta taraddamu ta fara tafi, ta ciro wayarta ta dinga daukar pictures wai scene yayi kyau, nidai banbi ta kanta ba na wuce abuna, yaya saeed pictures dinne tayi editing Allah. Ajiyar zuciya ya sauke kin tabbatar da haka? Na gyada masa kai, na mike bari naje na yimasa bayani, tareni yayi daz not a gud idea, ya kamata kisan baya ko son ganinki yanzu, is not easy namiji yaga matarsa a wannan yanayi har ya tsaya wani dogon nazari, bare kuma wanda aka hada hotunan da su yasan suna aikata abunda ya gani, kuma bazai yarda dake kaitsaye ba dan kinji ance wanda maciji ya ciza idan yaga tsumma ma gudu yake, salmah ta riga ta shafamiki bakin fenti mai wuyar wankewa, sukadai zasu iya wannan fentin da suka shafamiki. Yanzu ki nisanta kanki da khaleed for d mean time kadda yaje ya illataki ya illata kansa, dan abun ya tabashi sosai, zuwanki kusa dashi wil only make it worse, kiyi hakuri kinji zanyi kokarin na fahimtar dashi but ba lallai bane ya gamsu. Saeed yace kausar lets clear dis yanzu ina kike tinanin zamu samu salmah? Kausar tace no idea amma nasan wurin wadda zamu iya samun address din sury, yace ai ko ita muka kama ta isa ta warware komai, mu tafi yanzu, suka fita suka barni a daki ina kuka. [9/15, 2:46 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah abdul 1⃣8⃣9⃣ Kausar na fita da khaleed gidan wata course mate dinta sukaje, ta samo adress din sury a old airport take zama, suka nufi chan itada saee, basu wani sha wahalan nemanta ba da yake sananniya ce, saeed yabar kausar a mota ya nufi gidan yana kwankwasawa. Wata budurwace ta fito tana lekowa taga saeed taja tsaki tace zee kizo kiga meh wannan yake nema danni ba irin nawa bane, wata kodaddiyar ta taso tazo tana wani kwarkwasa irin nasu na 'yan bariki, tace handsome meh kake bukata ne? Yace sury nazo nema, aikuwa ta kwashe da wata dariya ta daga murya kunji wai sury yake nema suma na ciki suka sheke da dariya, tace handsome m sorry to say surry batayi da kalanka but ni zan iya maka komai, ta jujjuya masa dubeni kaga ba abunda na rasa, saeed ya dake sorry 'yanmata ni sury kawai nakeson gani, tsaki taja to suryn batanan taje abuja, kuma ko tanan ba abunda zatayi dakai, da rufo kofa a fuskarsa ta wucewarta. Ya koma jiki a sabule a mota, kausar tace yaya? Yace yarinyar batanan taje abuja, kuma na lura wannan matattarar shedancinsu ne, kausar tace salmah fa? Yace kinga ni banma tambiyeta ba, amma nasan kona tambaya a banza ba abunda zasu gayamin da basa harkar maza, so ke zaki iya zuwa ki binciko mana ita salmar idan batanan ko adress din inda sury taje a abuja ki samo mana, kausar tace yaya saeed kai kace fa wannan matattarar shedancinsu ce kuma zakace naje? Yace kausar banida choice nima da bance kije ba, kiyi hakuri wannan matsalar idan ta dau kwanaki bamusan iya abunda zai faru ba, kindaiga yanayin danuwanki, kuma kinga yanda mukabar ameerah, so lets solve dis problem, if not muma bazamuyi biki a dadin rai ba, kinga gobe za'a fara events a tinaninki a yanayin da suke ciki zasu iya zuwane? Idan abunnan yafita waje Allah kadai yasan abunda zaifaru, so lets clear dis i'm here wit u bazanbari komai ya sameki ba just trust me, kausar ta gyadamasa kai ta tashi ta fita ta nufi gidan. Tana zuwa tayi nocking wata ta taso ta bude, ta kurawa kausar ido, kausar tace salmah nazo nema please, ta bude mata kofa da alamun ta wuce ciki, kirjin kausar ya dinga dukan uku-uku tayi karfin hali dai ta wuce, sauran na ganinta suka mike tsaye kamar kura taga nama, wata tace nasira ina kika samo wannan hot cake din? Dariya tayi yanzunnan tazo wai salmah tazo nema, wata daga cikinsu tace oh sorry baby salmah jiya tabar kasar nan ta koma germany, kausar ta dake tace sury fa? Suka kalli junansu wata tace manta da zancen sury komeh zatayimiki zamu iya yimiki fiye dashi, kausar tayi murmushin yake ni ku gayamin inda taje kawai dan itada salmah ne kawai zasu iya yimin maganin matsalata. Wata taja tsaki toh ai batanan taje abuja, kausar tace kubani adress din inda taje please dan a gaskiya a wannan yanayin da nake ciki, ko ina take zan iya zuwa na nemota. Wadda ta budewa kausar kofa ta matso ta dafata, miye zaisa ki wahalar da kanki zuwa nemanta bayan zaki iya samun fiye da abunda zata baki anan din? Kausar tace baku fahimta bane sury tana dauke da wani sirri ne a tare da ita da zata iya kawarmin da matsalata take, wanda dukkanku nan bakudashi, and i'm loyal to her, wata daga gefe ta sheke da dariya loyal ko? Wa ya gayamiki anaba sury amana? Toh gun wata hajiya taje a abuja dan ta debe mata kewa, kausar ta dafe kirji kamar tayi kuka, ni gaskiya suryn a ba haka take ba, ta gayamin nikadaice, wannan yarinyar ta dauko wani card da wata takarda, ga wannan address din hajiyar ne a abuja, wannan kuma address din hotel dinda sury takene da room number ta, kije ki tabbatar da idonki surry batada amana, idan kika gano gaskiya inanan ina jiranki ni zan mayemiki gurbinta ta kada hannu a baki tana tsutsa. Kausar tayi murmushin cin nasara, tace ni nagayamiki surryna ba haka take ba, but idan har abunda kika fada gaskiya ne i'll com bak to you. Kausar ta juya zata fita taji Wata daga ciki tace gaskiya nusee bakiyi ba ya zakiyiwa sury haka? Nusee ta kyalkyale da dariya, ni kunmata meh tayimin ne? Wannan hajiyar fa tawace sury ta kwace so ni dan na kwace wannan hot girl din sai kuga laifina? Kausar ta kara sauri ta fice daga gidan tana fadin kwaji dashi ni bazaku kara ganina ba ma, saida ta shiga mota ta sauke ajiyar zuciya, saeed yace yanzu nike zancen shiga ciki nags kin dade, kausar tace ashe da kayi ruining plan ashe, saida na nunamusu nima irinsu ce fa, ta bashi labarin yanda akayi, ya fashe da dariya Allah ya shiryamana zuri'a yace, kausar ta mika masa adress din yana dubawa, tace yanzu ya kenan? Yace abuja zanwuce yanzu yamma tayi bazan samu fight ba, kausar tayi narai narai da ido alamun kuka, tace kabari sai gobe mana kabi flight mana, yace no kausar da zafi - zafi akan daki karfe, gwanda naje yau din na kwana achan gobe na juyo kan marece tayi afara events, kiyimin addu'a kawai muje na saukeki gida yanzu, but karki gayawa su mom komai. Yaje ya sauketa gida ya nufi gidansa, yayiwa fareedah bayanin abunda ke faruwa, ta tausayawa ameerah gaskiya kuma ta bashi goyon baya yaje, ya watsa ruwa yaci abinci, suka fito tare tayimasa addu'a Allah ya kiyaye, ya kama hanyar abuja ita kuma ta nufi gidan khaleed, sai cikin dare saeed ya sauka abuja hotel dinda sury take ya sauka shima ya kama daki. [9/15, 2:50 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah abdul 1⃣9⃣0⃣ Bayan ya shiga dakin da aka bashi ya aje jakarsa, yafito yana zagawa yana neman dakin sury, bayan yaga dakin yaje yana nocking, akwai mutane a ciki da alama dai shedancinsu sukeyi bazasu kula ba, komawa yayi dakinsa yadan kwanta ya huta, bacci ya kwasheshi, sai bayan awa daya ya farka, yayi salloli agurguje ya koma dakin sury yanata addu'a kardai ta fita, yana isa ta dawo daga rakiyar bakuwarta, tsayawa yayi a bakin kofarta, tana isowa taga mutum, taso ta ganeshi amma kuma ta manta inda tasan fuskar, cewa tayi malam lafiya ka tsayamin a kofar daki? Murmushi yayi ina zaune a hotel dinnan ne kuma ina ganin shigowa da fitarki shiyasa nikeso mu dan gaisa. Tsaki taja malam karka batawa kanka lokaci i'm not intrested ta bude kofar dakin zata shiga saeed ya rigata shiga, shigowa tayi dakin da masifa malam miye na wani shigomin daki? Na gayamaka i'm not intrested wani kallo ya wurgo mata yana karewa dakin kallo da yake a hargitse kamar inda akayi wasan kokawa. Zuwa tayi zataja hannunsa ta fita dashi ya kifa mata mari, da mamaki ta kalloshi tana rike da kuncenta, murmushi yayi, angayamiki bansan ko ke wacece ba? Batareda bata lokaci ba tuggun da kuka kulla keda shedaniyar kawarki salmah zaki warwaremin, cewa tayi wani tuggu? Yace kinfini sani ai, kinsan khaleed kuma kinsan matarsa ameerah ko? Cewa tayi malam wallahi ka fita daga dakina ko nayimaka ihu yanzu, wata karamar pistol din roba saeed ya fitar amma zaka iya cewa ta gaske ce😂 idan kikamin ihu take zanfasa kanki anan wurin, take jikin sury ya dauki bari ta rufe baki tana kuka, dan Allah karka kasheni wallahi zanfadi gaskiya, yace mata toh ina jira, tablet dinsa ya dauko ya fara video ina jiranki. Ta fara bayan salmah tabar asibiti direct gidana tazo, tayi kuka ta shiga bakinciki, sai a lokacin ta gane trap ne ameerah ta saka mata ta fada, kuma ta dau alwashin tinda ameerah tayi sanadiyar rabuwanta da iyayenta itama bazata barta taji dadi da khaleed ba, shine ta koma germany shekaranjiya tasa akamata hacking wayar khaleed duk wani conversation nashi tanaji, kuma tayi amfani da hotunan da ta daukesu da wayarta, taba wani computer expert yayi mata editing nasu, sune ta turomin ta email jiya tareda abunda takeso na rubuta a takarda, tace na tabbata na wanka pictures dinnan nasan yanda zanyi khaleed ya gansu dan taji firarsu a jiya zasu daidaita. Shine bayan na wanko hotunan naje na samu wani area boy nabashi contract din, danni gaskiya inajin tsoron khaleed ya kamani nasan ko kasheni zai iyayi, shiyasa naba wannan yaron conract, ya tsallaka gidan ya shiga. Lokacin da khaleed ya shiga gidan duk yana ciki, duk shi ya bude part din ameerah, dan na gayamasa gefen da dakin ameerah yake, yaje ya ajiyesu a ciki, kuma na tabbatar masa da kada ya fita batareda ya tabbatar khaleed ya gansu ba, bai wani sha wahala ba khaleed ya shiga dakin ameerah yana binciken wani abu, lokacin da yaga ya dauki envelope din a lokacin yafita ya bar gidan. Saeed ya kashe videon sa yace what a great plan, wato tinda ku bakuda bukatar aure a rayuwarku bakusan darajarsa ba, shiyasa kuka nemi ku wargaza auren wasu ko? Nasamu evidence saidai kuma dole a hukuntaki yanda bazaki kara tinanin aikata hakan ga kowa ba, magiya ta fara yimasa, yasa hannu a baki alamar tayimasa shiru, tasa hannu ta rufe bakinta, wata allura saeed ya fiddo yayi mata, gata ido bude saidai bata iyayin komai, ya maida bindigarsa ta roba a aljihu yajata sukabar dakin, yaje da ita dakinsa ya wurgar da ita akan carpet ya koma gado ya kwanta. Ameerah ce kwance a kafafun aunty fareedah tanata lallashinta tayi shiru tinda tazo fa take kuka kuma taki dainawa, ita damuwarta wanne irin hali khaleed yake ciki dan tin dazu rabonta dashi da ya korota, suna cikin haka saeed ya kira wayan aunty fareedah, ya gayamata abunda ya faru cikin farinciki tayi hamdala, yace ta bashi ameerah ta bata waya, yace ta kwantar da hankalinta gobe komai zai koma normal da ya dawo, tace khaleed dinfa bansan wanne hali yake ba? Yace karki damu namasa allurar bacci kafin na fita, na tabbata bazata sakeshi ba har zuwa gobe so don't worry kina ma iya zuwa ki duba kigani, ta dira kuwa da gudu tayi dakinsa, taje ta tarar sai baccinsa yake ta shafa fuskarsa, sannan ta rufeshi da bargo ta koma daki inda aunty fareedah, ranar dai a nan aunty fareedah ta kwana, tareda ita, suna addu'ar Allah ya kawo saeed lafiya komeh ya warware. [9/15, 2:51 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah abdul 1⃣9⃣1⃣ Gari na wayewa saeed ya jawo sury ya sakata mota gata ido bude amma bata iyayin komai, ya shiga shima ya tado suka kamo hanyar sokoto. Chan gida kuwa shirye-shiryen biki kawai ake, amma mom bataga ameerah ba tadaisan tace mata kanta na ciwo ko lafiya? Zuwa tayi ta tambiye kausar ta rasa meh zatace mata, sai ta kira wayan ameerah, ta daga dakyar dan duk zazzabi ya rufeta, mom tace ya jikin tace da sauki, mom tace har yanzu ciwon kan ne? Ameerah tace mom zazzabine amma nasamu sauki zanshigo anjima, mom tace shikenan Allah ya sauwaka. Har yamma tayi saeed bai isoba, khaleed ya farka yama bar gidan basu sani ba, hankalinsu duk ya tashi barinma kausar za'ayi mothers night da dare amma ba ango, shiko ashe motace ta masa tsiya a hanya ga wayoyinsa ba charge, sai bayan magrib ya shigo gari, sury kawai ya kai a gidansa ya rufe a daki, ya makala charge ya koma ya watsa ruwa ya shirya, sannan ya koma, yana buda wayarsa call na shigowa, kausar ce yace sorry kausar m fyn kuma na shiko gari yanzu ma zan iso wurin bikin sannan ta sauke ajiyar zuciya, wani abokinsa ya kira ya daukeshi suka wuce, sai a mota ya karbi wayar abokinsa ya kira aunty fareedah ya gayamata abunda ke faruwa, kuma yanzu zai wuce five star giginya hotel sai antashi bikin dole sannan zai iya yin komai. Aunty fareedah ta lallaba ameerah ta daure ta tashi suje bikinnan kar hankali ya tashi, bataso kowa ya zargi wani abu, haka ta daure tayi wanka aunty fareedah tayi mata light makeup ba laifi tayi kyau, saidai ramar da tayi, itama ta shirya ta saka kayan ameerah tajasu a mota suka nufi bikin. Mom na ganin ameerah hankalinta ya kwanta taje ta kamota, ta taba jikinta taji da zafi, tace sannu ina khaleed din Banganshi ba? Ga wurin zamansa ba babban abokin ango, nace mom khaleed ma bayajin dadi amma da sauki yanzu na samu yayi bacci sannan muka fito, mom tace kice ciwon mijinki ya sakaki kema, toh haka akeyi? Idan daya ba lafiya sai daya ya kwanta? Toh wa zai kula da wani then? Wannan ciwon bai kyauta muku ba bikin kanwar guda zai kamaku? Tajani mukaje tana nunani gun kawayenta ina gaidasu. Saeed yazo yaja aunty fareedah yaje ya zaunar da ita gun da khaleed yakamata ya zauna, suka sakashi tsakiya, sai tafi ake ga uwargidan kausar, sun birge kowa a wurin, jiri naji ya fara daukata naje na zauna, danfa gangar jikinace kawai a wurin, zuciyata na gun khaleed ganin nayi bikin kamar anja wani dogon zamani ba'a gama ba, bikin da naciwa buri yau gashi anayi bana wani jin dadi. Sai wuraren karfe goma sha daya aka kare, aunty fareedah tazo wurina, wai nazo na dauki hoto, nidai binta kawai nake kamar rakumi da akala mukaje aka dinga daukar pictures din kamar ana hoto da statue haka nake tsaye wurin, ko ruwa bansha a wurin ba saida wurin ya harmutse sannan saeed yaja kausar suka silale wurin, aunty fareedah taja hannuna mukabi bayansu, motar aunty fareedah duk muka afka, saeed yace akaishi gida ya dauko tablet din, mukaje ya dauko sannan muka wuce gida. Dakin khaleed saeed yayi direct niko na labe a baya kamar munafuka, a firgice yafito yace khaleed baya daki, rarrabuwa mukayi muna dubashi amma ba ko kurarsa a gidan, take na zube a wurin aka kwasheni aka kwantar a daki, saeed yace kausar ta zauna tare dani shida aunty fareedah su fita nemansa, dan bai kamata ta rika yawo a haka ba tana amarya ta gyadamusu kai suka fita itako ta zauna dani a gida Duk inda saeed ke tsammanin yaga khaleed ya tafi bayanan, hankalinsa duk ya tashi, chan wata zuciyar tace masa yaje garden dinnan da yake zama duk lokacin da yake cikin bacin rai, da hanzari yaja mota ya nufi gun, da gudu ya shiga yabar aunty fareedah a mota, sai zagayawa yake bai gansa ba, har ya cire hope ya dora hannu aka yana hawaye, chan wani lungu ya hango mutum a rakube da sauri ya isa wurin, khaleed ne kuwa ya hada kai da guiwa kamar wani maraya yana kuka kamar mace Saeed yaje ya dagashi, idonnan jajir jikinsa sai zafi sai rawar sanyi yake amma yaki tashi, saeed yace khaleed miye haka? So kake ka kashe kanka? Khaleed ya dago kai yayi wani murmushin bakinciki, ai ni nafiso na mutu ma, bazan iya jure wannan bakinciki ba, shikenan ni haka rayuwata zata kasance? Duk macen da nakeso banida wani amfani a wurinta, dakyar na samu na cire salmah a rayuwata, na buda wani shafin rayuwata na fara son ameerah, ni bansan itama haka take ba, saeed yace masa khaleed you are wrong ameerah ba haka take ba, sharrine kawai akayimata, khaleed yace saeed how i wish gaskiya ne bansan na kamu da tsananin sonta ba sai yanzu, abunda idona ya nunamin baiyi kama da karya ba, banason na yaudare kaina ta hanyar tinanin ba gaskia bane, ko salmah da badan ni naganta da idona ba, bazan taba yarda da hakan ba, saeed yace khaleed dan salmah ta cutar dakai ba lallai bane itama ameerah haka, ni ka kyaleni kawai i don't want to live anymore. Saeed ya tashi yaje da sauri mota ya dauko tablet dinsa, ya budo video ya dawo wurin khaleed, tabashi yayi khaleed yace nace maka ka kyalenu dan Allah, natsani rayuwata just let me die, saeed shikenan zan kyaleka, zanbarka ka kashe kanka din amma inaso ka kalli videon nan kafin ka mutu din, ya kunna masa khaleed bai kallaba, amma jin sautin abunda ke fitowa yasa ya karbi tablet din da sauri, yana kallo hawaye sai zubo masa suke, kara kunnawa yayi ya sake kallo dan ya tabbatar ba mafarki yakeyi ba, saeed ya kalla ya gyadamasa kai, idan kuma har baka yarda da videon ba, yarinyar tana a gidana yanzu haka zaka iya zuwa ka tambiyeta da kanka, khaleed yaje ya kankame saeed yana kukan farinciki, saeed ya tureshi malam jeka ka mutu kawai ni ka kyaleni, tinda dama matsala kansa kaji ka tsani rayuwarka, komeh Allah ya dorawa bawansa badan baya sonsa bane, ya kamata ka dauki tawakkali a rayuwarka, kar matsala tasa kamanta da ubangijinka har kaje ka rasa imanika, can you imagine ita ameerah ya takeji ne? Itafa akayiwa kazafi amma tafika juriya dan hakan baisa tace tagaji da rayuwarta ba, khaleed ka gyara halinka, saurin fushi, zafin rai, yanke hukunci a fushi, yakamata ka ragesu ko kasamu kaji dadi a rayuwarka, idan ba haka ba watarana zakayi danasani, khaleed yace thanks alot friend, samun aboki nagari irinka a rayuwa ba karamin sa'a bane, kausar tayi sa'ar miji a rayuwa, nima dan Allah kaini inda matata i promised zanzama mai hakuri da tawakkali, zan zame mata miji na gari, kuma inshaAllah bazan kara sata kuka ba, saeed yace alhamdulillah yanzu naji zance mutafi suka wuce. [9/15, 2:51 PM] ‪+234 706 332 8523‬: Dream girl na deejah abdul 1⃣9⃣2⃣ Saeed ya raka khaleed har cikin dakin ameerah yayiwa kausar signal ta taso su tafi, da suka fita tace ya sauketa gida suyiwa mom bayanin abunda ya faru tinda komai ya zama normal yanzu, dan takira tanata fada ina mukaje anata nemanmu. Khaleed na shiga yaje daidai kafar ameerah da ke kwance ya zauna tareda dafe kafafuwan nata, waigowa tayi da idonta da suka kada sukayi jajir ta kalloshu suka kurawa juna ido 4 quite sometimes kafin ta dauke idonta, dora kansa yayi a kafafunta tanajin saukar hawayensa a kafarta ta rintse idonta, khaleed yace ameerah bansan ta inda zanfara baki hakuri ba, nayi zarginki batareda hakkinki ba, just forgive me if you can, janye kafarta tayi ta matsa a tsakiyar gado tana hawaye, khaleed yaci gaba nasan kin tsaneni yanzu ameerah but dan girman Allah kiyi hakuri, give me another chance, nayi alkawari bazan kara sakaki kuka ba, bazan kara zarginki ba koda da idona nazo nagan wata akanki, tashi zaune nayi ya isa please, bama zaka gan wata a kaina ba, tasowa yayi ya hawo gadon shima, ya jawota ya kankame, kimun magana please ko zagina zakiyi kiyi, i just want to hear your voice, janye jikina nayi naji, but i'm not ready to forgive you yet, gydakai yayi bazan tirsasaki ki yafemin ba, i'll give you time, but don't take long time coz i can't take it, i'm madly in love wit you, dago kai nayi na kalleshi, yes i love you khadijah, farincikin da nake boyewa yaso ya bayyana a fuskata na dukar dakaina, say something please yacemin, dago kaina nayi wanda akeso ba'ayimusu haka ni ban yarda da wannan son naka ba. Girgiza kai yayi i know i hurts you alot, but zannunamiki soyayyata ba karya bace just give me a chance, nayi shiru abuna, tashi yayi yayimun peck a kumatu, take your time but ina rokonki kibani dama please ya juya ya fita, wani tumble nayi a gado saida na buge kaina a gina nadawo ina dan kuka a hankali, tashi nayi naje na leka inya wuce kardai ace ya jini, naga baya wurin nadawo daki ina rawa, sannan naje nayi alwala nayi sallah ta godiya ga Allah dafatara Allah ya dauwamar mana da farincikinmu. Haka dai mukayi bikin kausar cikin walwala da farinciki, saidai naki sakewa khaleed, shiko zaune kawai yake amma duk wani motsina akan idonsa, haka har akazo kai amarya nace nifa dani za'ayi siyen baki, khaleed baiso hakan ba, taya za'ayi ya tsaya siyen bakin kanwarsa, niko nace sai nayi, na dauka ma ya wucewarsa dan banganshi awurin siyen bakin ba. Bayan angama nafito zanshiga motar wata kawar kausar ta saukeni gida, ji kawai nayi anfinciko ni juyawar da zanyi naga khaleed, jana kawai yayi yajefa motarsa, ya zagaya ya shiga, na wani turbune fuska, miye haka zaka wani jawoni kamar diyarka? Kallona kawai yayi yayi murmushi, yacigaba da tukinsa, baice dani komai ba har muka isa gida, bude kofata nayi na fito zan wuce part dina, ina tafiyata ina rausaya ji kawai nayi andagani sama chak na kurma ihu, khaleed bai direni ba sai tsakiyar dakinsa, kallon dakin na dingayi, an qawata dakin fiyeda yanda nagani ranar, and duk anzane bangon dakin da i love you ameerah please give me a chance, ga pictures dina manya-manya da aka lika a dakin, wasuma bansan sanda akayisu ba, wasu kuwa a wurin bikin kausar ne yayita daukana su kowanne events, baki na bude ina kallo wasu hawayen farinciki na sauka a idona, dukawa yayi da guiwoyinsa yace please forgive me my love, Allah ma munayimasa laifi ya yafemu bare dan adam, just give me one more chance please, dukawa nayi nima ina hawaye, ni na yafemaka tintini, kuma kafafuna ba wurin dukawarka bane, kai mijina ne baikamata ka dukamin ba, aljannata tana kasan kafafunka ni yakamata na duka maka, dagoni yayi muka tashi tsaye shima yana hawayen farinciki, jamin hanci yayi, kinyafemin amma shine saida kikayi bani purnishment? Nace nameh fa? Kika shareni mana duk inda nazo kusa dake sai guduna kikeyi? Dariya nayi ni bammaka komai ba fa, kunnensa ya rika kiyimin rai please kada ki karamin wani purnishment din, dariya na kyalkyale da ita, ni banyarda ba nace, zuwa yayi yafara tsallen kwado kingani kiyi hakuri haka please, ya mike ya fada kan gado yana mayarda nufashi, chaf ashe dai na girma yanzu bana iya tsallen kwado, na dinga masa dariya, cewa yayi kin hakura yanzu ko? Shagwabe fuska nayi Nace a'ah ni sai ka goyani. Tasowa yayi ya duka na dane, cewa yayi ina zamuje princess? Nace dakina zaka kaini, baimun gardama ba yawuce har dakina, nace saukeni toh, yace ai na kawoki dai amma bangaji da ganinki ba, ya juya ya koma ya direni a tsakiyar gadonsa.mayafi ya dora akaina ya rufemin fuska, i want to experience dis too. Inaso najini kamar ango da aka kawomasa amarya ayau, dafa kaina yayi addu'a Allahumma inni as'aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha alaihi, wa auzu bika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaihi. Ya jawo hannuna tashi muyi sallah, haka mukaje yayi jamana sallah har muka gama, ya dinga yimana addu'a muka shafa, wata leda ya jawo kajine a ciki da leda daya ta milk, ya zubamana milk din a cup muka ciyarda junanmu, tashi yayi ya dauko wata riga ya bani, i want you to wear dis 4me. Banyi gardama ba na karba na shiga toilet na chanja, rigar itada babu duk daya, nayi kyau saidai na kasa fitowa haka, sai kallon kaina nake a madubi ya zan iya fita haka? Ban ankara ba saiji nayi anturo kofa anshigo duk na dabirce sai 'yan kame-kame na dingayi, daukoni yayi chak ya dire tsakiyar daki yana karemin kallo sai dukunkune fuska nake a jikinsa, kiss ya fara kaimin ta ko' ina take jikina ya dau bari, radamin yayi a kunne i promised i won't hurt you like before. Ranar dai khaleed ya nunamin so tsantsarsa, duk da nasha wahala saidai ba kamar daren farkonaba, daren munyi bacci da muka dade bamuyi irinsa ba. Tun daga ranar koyaushe khaleed na makale dani, kullum shi sabon ango yake komawa, yadaina zuwa office kusan 1week kenan, waishi a dole hutu yake, skul ma tare muke zuwa, zaijirani sai nagama mudawo gida tare, i love you zanshata tafi a kirga kullum, kamar a bakinsa aka kagota, korafinsa kullum ni ban tabacemasa i love you ko sau daya ba wai bana sonsa niko naki. [9/15, 2:51 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/25, 8:23 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣9⃣5⃣ Mama kebamu labari wai ashe bayan rashin mutuncin da sukayi, har dad ya basu kudi, bayan fitarsu kwana 3 da komawa gida hajiya asabe itada saratu suka sace kudin dama duk wani kudi da yakeda a gidan suka gudu, yasa nemansu a ko'ina baisamu ba, tin alokacin ya kwanta ciwo, masu kula dashi da sukaga komai ya kare suka gudu suka barshi, yanzu atakaice har gidan da yake ciki bank ta kwace sanadiyar bashin da yaci baibiya ba ko yanzu makocinsa ne ya daukoshi ya kawomanashi a haka dai ba mai kula dashi, saida mukayiwa kawu kuka. Take khaleed yace a fitar dashi waje kawai zai samu sauki inshaAllah. Nida khaleed ne muka fita da kawu india akayita masa magani cikin wata 2 ya warke tas kamar ba shiba, sai kuka yake yana yimana godiya da rokon gafara, nikam nace na yafe Allah ya kiyaye gaba. Bayan mundawo gidane nafara 'yar rashin lafiya, ranar muna zaune gidansu khaleed kowa ya hadu ana family get together, na yunkura na tashi na fadi na some, khaleed duk ya rikice dakyar aka shawo kansa akayi asibiti dani, doctor feenat ja'afar ta dubani, tafito da fara' arta tayimusu congratulations, ina dauke da juna biyu, haba take kowa ya nemi damuwarsa ya rasa sai taya juna murna ake. Khaleed ya mayar dani kamar kwai a faranti sai lelena ake, ko cup baya bari na dauka wai kar na illata masa baby, gidan saeed ma hakane aunty fareedah tana dauke da tsohon cikinta itama, wata tara, kausar kuwa nata karamine wata uku yayinda nawa yake wata bakwai, ciki kamar yayi wata tara sai danbazan nauyi zama dakyar kwanciya dakyar, nida khaleed dai tare muke renon cikin dan duk na motsa sai ya motsa ga 'yar banzar shagwaba da nake isarsa da ita ni sai anciremin cikin nagaji, shiko sai bada hakuri yake, wani lokacin idan ina kuka har tayani yakeyi, muyi tare. Ranar muna zaune a gida saeed ya kira khaleed aunty fareedah na asibiti tana labour, muka dunguma mukayi asibiti, kusan awa 4 amma shuru hankalin kowa ya tashi, sai daga baya doctors suka fito da sukayi mata aiki, ta haihu ta haifi 'ya mace, saidai muyi hakuri Allah yayi mata rasuwa tsabar kaduwa take nakuda ta tasomin akayi labour room dani. Yaya saeed kuwa anan wurin ya zube a some, kausar ma bleeding ta farayi aka dauketa itama, khaleed ya zauce ya rasa inama zaisa kanshi, wannan tashin hankali. Operation akayimin aka ciremin 'ya' yana duk 3 maza, akasakasu a incubator dan wata bakwai ne basu gama kwari ba, bani na farfado ba sai bayan kwana 3, da tashina kuma da zancen aunty fareedah na farka, kowa wurin kuka yakeyi. Barin ma khaleed da yayi uwar rama cikin kwanakinnan 3, ni ba ko ta cikina nake ba dan kwata-kwata banma lura da babu cikin ba. Sai a lokacin nasan kausar miscarriage tayi akan kaduwa, saeed kuwa haukane kawai baiyi ba, saidai fa kawai muyi hakuri aunty fareedah ta tafi saidai ayimata addu'a Allah ya gafarta mata munyi rashi. Gida na koma mama taci gaba da kula dani da yarana 3 maza, da sukaci sunan Umar faruk, Abubakar siddik, da kuma Aliyu. Akan yanda haihuwar tazo ba wani shagali da akayi saidai fatan Allah ya raya, kausar kuwa ita ta karbi jaririyar da aunty fareedah da ta haifa, ta dinga shayar da ita. Khaleed kuwa kullum yana gida makale dani da yaransa, mama kuwa gyara takemin na musamman ta matsu na cika arba'in, ta gangamani na koma gidana, dan khaleed ko kunyarta bayaji dan agabanta zai iya rungumeni ba abunda ya masa zafi. [12/25, 9:01 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣9⃣6⃣ Bayan na koma gidana kuwa sabon amarci muka bude, duk sai rama nike ga rigimar yara 3 ga ta ubansu danshi wai kullum sabuwa yake jina bana taba isarsa. Kausar kuwa saida tayi dagaske kan tasamu saeed ya dan dawo normal, ta zama uwar 'ya'ya 3 kuma duk diyan aunty fareedah, kai bakace ba ita ta haifesu ba. Bayan shekara daya, suhaila tayi candy muka shiga bikinta itada yaya musty, yarana sunyi bul bul gwanin sha' awa, kowa son daukarsu yake, bare mom da dad yanda sukeji da yarannan kamar su hadiyesu, ko yaushe suna gidan mom, nima nafison ta daukesu dan nadan sarara shegiyar barna ce da su, amma da ubansu ya dawo zai kwasosu waishifa baya jin dadin zaman gidan idan ba sojojinsa. A wurin bikin suhailat ne, mom ta gayyato matar deputy governor, ana mukejin labarin husnah, wai tana prison a america, ankamata da laifin drug trafficking, sunyi mata life imprisonment, kuka take kowa saida ta bashi tausayi, gashi deputy governor ya sake aurensa har matarsa ta haihu ita kuwa, shikenan dan ya juyar mata da mahaifa bazata kara haihuwa ba, husnah kawai ta mallaka ga abunda ya faru da ita, kowa wurin ya tausayamata, saidai fatan Allah ya kiyaye gaba. Mungama bikin suhailat muka kaita abuja da yake yaya musty ya samu aiki a chan, saidai fatar Allah ya basu zama lafiya, kausar kuwa na dauke da karamin cikinta gashi ita ke kula da little fareedah dan sunan uwarta taci shiyasa suke ji da ita sosai gashi yarinyar sak uwarta batabar komai nata ba kamar antsaga kara. 🍇🍇🍇 Bayan shekara biyar🍎🍎🍎 Ameerah ce da khaleed, da kuma yaransu 3 keta aikin buga ball, kausar da saeed sukayi sallamah suka shigo, tareda 'ya'yansu 4, uku na aunty fareedah maza biyu da kuma little fareedah, sai danda kausar ta haifa Muhammad ana kiransa ameer, gata kuma dauke da wanin cikin, yaran suka dunguma suka fada foot ball field din suka fara wasa da junansu, saeed yace ai sai kufito ku barwa yara wurin suyi wasarsu tinda ku bakwa girmah. Kausar tace mutafi ciki mubarsu anan suyi wasa, dane bayan khaleed nayi nace ni goyani nagaji bazan iya tafiya ba, cewa yayi kefa kin kara nauyi yanzu ba kamar da ba ni bazan iya goyaki ba, gefe na koma ina bubbuga kafa da kukan shagwaba, saida yaje ya duka na hau bayan sannan muka wuce falo. Saeed da kausar sai girgiza kai suke suna dariya, kukan dai ko a gaban yara ma bakwa girma, kausar tace ni kuwa sister inlawa yaushe zaki kara haihuwa ne? Ni kinga 'ya' yana 4 ga na biyar a cikina, akayi dariya sannu uwar biyar, tace i'm serious fa ko suhailat de haihuwarta biyu yanzu, cewa nayi ni 'yan 3 dina fa sun isheni. Khaleed ya mike tsaye, ai wallahi baki isaba, ashe kuwa akwai zancen karo amarya ta haifamin yara, bari ma kiga na nemo tsohuwar matats salmah may b yanzu ta shiryu tinda dama ba sona kike ba. Kwalalo ido nayi har idona sun ciko, da hawaye, khaleed kuwa ya basar yasa call, sai chan naji yana cewa toh shikenan nagode kwarai ya kashe wayar ya dawo ya zauna jiki a sabule yasha mur. Zuwa nayi na duka gabansa khaleed wasa kakeyi ko? Ya kauda kai gefe wanne irin wasa ni dagaske nake bayan bakya sona, hawaye suka kwararomin wallahi Allah ina sonka, son da nake maka bantaba yiwa ko wanne namiji a rayuwata ba, kaine namijim da na fara so a rayuwata, cikin mamaki ya kalloni, tsohon saurayinki fa da ya rasu? Juyawa nayi wurin saeed da kausar nace ku gayamasa gaskiya please. Suka fashe da dariya, wato yau zancen kishiya zaisa a tona tsohon sirri, saeed ya fara kora masa bayani ba wani saurayi fa da nayi duk karyace, shi nakeso tin asali nayi karyane kawai dan na aureshi, khaleed baki bude ido bude yake kallon saeed. [9/15, 2:51 PM] ‪+234 706 332 8523‬: [12/25, 9:31 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣9⃣7⃣ muka fashe masa da dariya, yace lallai yarinyarnan kin iya acting sosai, kuma ku nan duk daku aka shirya min wannan ko? Shine kikayita wahalardani kina nunamin bakya sona? Nace ai soyayar taka sai da nayi dagaske nasamu, nima nasha wahala kai bakayi komai ba ma. Kausar tace kaima yaya saeed fa kadaina yiwa yayana dariya dan, kaima bakasan cewa ni naganka inaso har mom ta ganeba, ta kiraka tace ta baka ni, da mamaki ya kallota, khaleed ya fashe da dariya shima yauwa kanwata kin ramamin, saeed yace lallai Matannan kun iya acting muka kyalkyale da dariya muka tafe, saeed yace khaleed nima na goyi da bayanka mu karo musu kishiya kawai, khaleed yace ni ae har nayi booking tsohuwar matata zan maida, tashi nayi da gudu na rikeshi ina kuka nidai ka dains banaso Allah yace ahaf ai sai nayi kuma, faduwa nayi kasa ina birgima da kuka ni wallahi banaso, zuwa yayi ya dagoni ya sharemin hawaye to kice kina sona inji, nace inasonka Allah, yace banji ba nace i love you, ya mike tsaye say it louder nadan bude murya nace i love you, yace ki kara fada, zuwa nayi daidai kunnensa na kwala masa ihu I LOVE YOU KHALEED ya dafe kunnensa zaki fasamin kunne, su kausar sai dariya suke. Zuwa nayi naja hannunsa, ka fasa ko? Jawoni yayi ya zaunar, kwantar da hankali kinyi belin kanki, zancen babyn fa? Nace zan haifamaka dozin ma yace really? Na gyada kai, nace anjanye zancen salmar ko? Yadan bata fuska yace Allah ya kiyaye ameerana, ko mata sunkare a duniya meh zanyi da salmah? Ki kwantar da hankalinki salmah ma bata duniyar nan, nace kamar ya? Yace yanzu wayar da nayi aka gayamin achan germany abokan iskancinta suka kasheta, wai tana musu kwacen mata shine suka hadu suka kasheta, iyayenta ko gawarta basu samu ba dan konata sukayi, wai kankamesa nayi ina kuka, Allah yayi mana kyakkyawan karshe, masu hali irin na salmah Allah ya shiryar da su, dan ita dai karshenta baiyi kyau ba. Wayata tayi kara, naga number mama, na dauka tace nazo gida wai saratu ce tazo, muka dunguma mukayi chan har yara, inkaganta abar tausayi tayi baki kirin dama farin na bleaching ne. Labari ta shiga bamu tana kuka, wai tinda suka kwashe dukiyar kawu suka gudu, london suka tafi, achan ta hadu da wani saurayi shima dan nigeria, suka kulla soyayya har ta aureshi, ashe dan giyane, duk dare in yayo shansa sai ya hada itada hajiya asabe ya kwana dasu, haka ya maidasu matanshi su 2 ya kwanta dani ya kwanta da mom, daga karshe dai duk shi ya kwashe dukiyar ta koma hannunsa, da mukayi yunkurin guduwa, shi ya kamamu anan ya harbe mom ta mutu, ni kuma dakyar nasha, saida nayi yawon karuwanci a london sannan na samu kudin dawowa gida nigeria, yanzu haka ina dauke da cutar kanjamau ta fashe da kuka, kowa dai kuka ts nemi gafararmu muka yafe mata. [12/25, 10:29 AM] Deejah Abdul💗💖: Dream girl na deejah abdul 1⃣9⃣8⃣ 🍇🍇🍇THE END🍎🍎🍎 Kawu yayi gyaran murya yace ameerah kisa baki a maganar nan, tun shekarun baya nake biyar mamanki ta amince muyi aure taki, kuma wallahi Allah na chanja halayena, gidana ma ya dawo hannuna dan yanzu business dina yadan dawo all thanks to you and your husband da yake bani contracts, na kalli khaleed ya kannemin ido. Gyaran murya nayi nace kawu karka damu ka turo magabatanka kawai ni na amince, mama ta dauko pillown kujera ta wurgomin ameerah yaushe kika zama uwata da ubana tashi tsaye nayi ina dariya toh mama ki amince mana, su umar suka fara tafi suna granny say yes please, kowa ya dinga cewa ta amince. Tashi tayi tace toh shikenan iyayena na amince, gidan ya dauki sowa da tafi. Khaleed yazo ta bayana yana radamin a kunne, nima fa m eager to b a father again kizo muje gida, anan muka silale muka gudu gida, muka lula duniyar soyayya. Aliyu da salim sunzama manyan mutane, suna aiki a sabon kamfanin da khaleed ya buda, sun shirya plan dinsu sai zuwa sukayi suka gayamana, aliyu zai auri siyama qanwar salim shi kuma salim zai auri fatima kanwar aliyu, kowa yayi farinciki da wannan plan din, sai biki muka fara shirye shirye bayan an daura auren mama da kawu shehu. INA GAYYATAR DUK ILAHIRIN MASOYA WANNAN LITTAFI BIKIN SALIM DA FATIMA, ALIYU DA SIYAMA AMMA FA BANDA 'YAN WAWASO LOLZZZ. alhamdulillahil lazi bini' imatihi ta timmussalihati, anan na dire wannan littafin nawa da na radawa dream girl, godiya ga Allah da yabani ikon farawa da kuma kammalawa, ina rokon Allah kuskuskuren da nayi a ciki Allah ya gafartamin, ladar da ke ciki kuma Allah ya bani, ina rokon duk wanda na batawa rai ta dalilin wannan littafi ya gafarceni banyi da niya ba. JINJINA DA GODIYA GA MASOYA WANNAN LITTAFIN. MY FACEBOOK GROUP DEEJAH ABDUL'S NOVELS THOUSANDS OF MEMBRS. MY WATSAPP GROUP MEMBERS DEEJAH ABDUL'S NOVELS 1&2 FEENAT JA'AFAR GROUP MEMBERS DAMARY GROUP MEMBERS BEUTY RUSH MEMBRS BE A LADY WITH CLASS MEMBRS DA DUK WANI GROUP MEMBRS MASOYA WANNAN BOOK DIN DA BANSAKA BA, DA DUK WANI MASOYIN WANNAN LITTAFIN DA BANSAKABA A DUK INDA SUKE A FADIN DUNIYAR NAN INA MIKA GAISUWATA DA GODIYA A GAREKU. GAISUWA TA MUSAMMAN A GAREKI MY ONE AND ONLY ELDER SIS NAFISA ABDULLAHI DUKAMAJE ALLAH YA RAYAMIKI YARANKI MINAL DA DADYNMU. SADAUKARWA Na sadaukar da wannan littafin ga mahaifina late Abdullahi Aliyu dukamaje, ina baran addu'a a wirinku duk wanda ya karanta wannan littafin yaji dadinsa, ya karu da kalma ko guda dayace a ciki, da ya tayani da addu'a Allah ya gafartawa mahaifina, da duk musulmin Allah da suka rigamu gidan gaskia. ALHAMDULILLAH sai mun hadu a sabon littafina idan Allah ya bani iko mai kaunarku KHADIJAH ABDULLAHI ALIYU DUKAMAJE. (AKA DEEJAH ABDUL DREAM GIRL) NAGODE adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *