Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, April 3, 2017

DR SADIQ

adsense here SADIQ novels / DR SADIQ part 1 DR SADIQ part 1 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:15 Tin daga nesa Khairat take jiyo sautin waka daga babban hotel din da ake hada Dinner. Ganin gari yayi tsit ko ina babu motsi, babu motoci ko daya haka yasa ta tako motar tata yadda taga dama. Jan motar take ranta sai faman tafasa take, bakin ciki kamar zai kasheta, zuciyarta sai faman saka mata abubuwa daban daban takeyi. Tana isa bakin gate din Hotel din ta saki wata uwar horn dake nuna alamar a matse take taganta a ciki. Cikin sauri mai gadin ya nufo bakin gate din cikin fada yake cewa. " Dan Allah maintain mana tashi zakayi?? Bata sauraresa ba ta sake danna masa wani Horn din, dan bata jin me yake fada, kasancewar glass dinta duk a rufe yake. Cikin sauri ya bude mata yana ta famar fadansa amma bata san yana yi ba. Gyefe daya tayi parking din motar, cikin sauri ta fito sanye da riga da wando duk ya matseta, kanta babu dan kwali ta kama gashinta da ribom. Kai tsaye ta nufa shiga cikin hall din. Tana kokarin shiga nan security ya tsayar da ita. " Sannu da zuwa. Gate pass naki fa??? Ta kallesa sama da kasa dan bai isheta kallo ba, taja wata tsuka bata ce masa komai ba ta cusa kai tana kokarin shiga. " Madam ji mana. Ya zaki shiga hall baki da gate pass, kuma shigar ki batayi kama da wacca zata shiga nan ba. Ya fada yayin da yasha gabanta. Cikin tsawa tace masa. " Amma tabbas na fuskaceka baka da muruwa. Kai har ka isa kana security dan wahala ka tare ni kace bazan shiga hall din nan ba. Tabdijam! Yace: " A'ah Madam ba haka bane, gani nayi sai da gate pass ake shiga, ance wanda bashi dashi karna barsa ya shiga ko waye, kuma sojojine suka ce na tsaya dan sune ke gadin wurin, yanzu suka je cin abinci. " Lallai yau naga ta kaina. Wai ace Dinner na DR SADIQ mutumin dana gama bada kaina akansa a hanani shiga. To wallahi duk hananin shiga da akayi bashi zaisa na fasa rashin mutuncin da zan masa ba daga shi har wacca zai aura din. Ta fada a zuciyarta. " Okay naji zan koma, dan bani dashi. Tayi tsuka ta hararesa tare ta juyawa ta koma bakin motarta. Wayarta dake cikin mota ta bude ta ciro ta fara danna lambar Dr din. Yana zaune kan High table daga shi sai matarsa, babu abinda kake ji a hall din sai sautin kida. Gaba daya jama'ar dake wurin kowa ya shagala yana cin abinci kafin aci gaba da sauran sha'ani. Wurin ya tsaru iya tsaruwa, ko wani table mutane biyu ne mace da namiji. Ba abinda kake gani a hall din sai hasken flash light na camera da wayoyi masu tsari ana daukan Amarya da Ango dan tsabar haduwar da sukayi. Kamar daga sama Dr sadiq yaji wayarsa na ringing. Cikin sauri ya zura hannu cikin rigarsa ya zaro wayar, cikin mamakinsa yaga DEAREST. Cikin sauri ya rufe da hannunsa dan kar Nana ta gani, ita ko tini ta gane yana rufe wani abune dan haka tace: " Ko baka da gaskiya?? Yayi murmushin dole. " No. Karki damu. Me kika gani?? " Ai ka boye dan kar na gani. " Okay.. Ba kowa bane, wani ne da ban fada masa bikina ba shine zai min korafi akai. Ya fada cikin alama na maras gaskiya. Tayi murmushi. " To ka dauka man. " . Ai ya katse sai ya sake kira. Ya fada tara da mayar da wayar cikin aljihunsa. Baiko cire hannunsa ba nan yaji sake shigowar kiran akaro ta biyu, cikin sauri ya mike daga inda yake. " Two minute, zan dawo. Ya fada yayin da yake kokarin barin wurin. Ta kofar baya ya fita inda babu hayaniya sannan ya amsa wayar. " Honey ya akayi?? " Ban sani ba. Mayaudarin banza mayaudarin hofi. Cikin sauri yaji gaban sa ya fadi. " Me nayi dearest?? Cikin tsawa tace: " Kafi kowa sanin me kayi munafukin banza kawai, ka cuce rayuwarka ba tawa ba, kuma wallahi bazan barka ba, saina hana auran nan, kamar yadda na hana na farko. Wata fadiwar gaba yaji sannan yayi saurin cewa. " waya fada miki zanyi aure Khairat?? " Kar ka yaudari kanka mana, yanzu haka ina cikin hotel din da kuke dinner a ciki, dan bani da gate pass ne da wallahi saina shiga na wulakanta maka mata. Cikin rudewa da tsoro yace: " okay... yanzu ki fadamin kina ina zanzo na ganki. " Kazo daki mai lamba 406, ka same ni yanzu, idan kuma kaki wallahi saina kashe wacca, zaka aura. Ta fada tara da kashe wayar.vels / DR SADIQ part 2 DR SADIQ part 2 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:17 Cikin sauri Dr ya mayar da wayarsa cikin aljihu kai tsaye ya nufa Reception Room. Anan aka masa kwatancan dakin ya nufa cikin sauri dan yasan halin abarsa. Yana isa layin ya dinga bin lambar dakunan daya bayan daya har ya isa dakin mai 406. Cikin sauri yasa hannu ya kwankwasa, daga ciki ya jiyo muryarta. " Ka shigo. Lokaci daya yasa hannu ya murda kofar ta bude, tara da mika mata sallama. " Wa'alaikas salaam Angon gobe. Ta fada cikin keta. Ya kalleta inda take zaune a bakin gado, cikin sauri ya karasa ya zauna kusa da ita. " My. Waya fada miki zanyi aure?? Hararan data watso masa yasa ya shiga taitayinsa. " Karya za'a maka ba auran zakayi ba makaryacin banza. Ko kana tunanin zaka iya tafiya kabarni, bayan na gama sacrificing kaina akan ka??? Ya saukar da wata ajiyar zuciya tara da kara matsawa kusa da ita. " Honey u need 2 came down. Auran nan bawai zanyi bane na tafi na barki, kema kinsan ina sonki bazan taba son wata mace ba bayanki, tinda akan ki na fara soyayya kuma akanki na fara sanin mace. Pls karki min abinda kika min akan fatima, a auran da kika ruguza shi na farko. Ta kallesa magana yake cikin lallashi da kamamman fuska. " Lokacin da muka hadu bamuyi alkawarin zamu aura juna ba, sannan bamuyi alkawarin daya zai bar daya ba, ko da sunan aure. Duniyarmu muke ci iya iyawarmu. Sai yanzu kace zakayi aure mu zama mu biyu, daya na gidanka ni kuma ina yawo a titi. To wallahi baka isa ba sai dai ka aureni ko kuma a fasa auran. Wata fadiwar gaba yaji, cikin sauri yace: " Haba Honey kema kin san bazai yiwu ba. Iyayena su suka zabamin Nana, kema kinsan da wiya auran nan ya fasu dan duk abin da zaki shirya sai sun daura min ita. " Ok.. mu zuba ni da iyayan naka, idan basu fasa aura maka Nana ba, nima bazan fasa kudirina ba akanta. Dan wallahi! Wallahi!! Wallahi!!! Sai na kasheta. Sai dai daga baya nima kasa a kasheni. Ta mike cikin sauri zata fita daga dakin. Cikin sauri Dr ya mike yasha gabanta. " Khairat nasan halinki zaki iya, amma me yasa bazaki rage kishinki akaina ba, wallahi kina cutar dani da yawa, me yarinyar nan ta miki 4 goodness sake.?? Tayi dariyar mugunta. " Idan baka son ta mutu sai ka fadawa iyayanka su fasa, idan kuwa suka ki ji, can ta matse maka. Gaba daya hankalin Dr ya tashe, ya rasa me zaiyi dan ya shawo kan mutuniyar tasa. Rage tsayinsa yayi gwiwarsa suka sauka kasa. " Khairat actually I really luv u kin sani, but pls why do u plan 2 hurt me??? " Ko kadan kada kayi tunanin haka, kawai tsabar kishinka ne da nake ji. Tasa hannu ta jawo masa babbar rigar dake jikinsa takai hancinta dan shakar kamshin turaran dake tasowa. " Harda canza turare dan zaka zama ango, ni kuma za'a yadani a kwandon shara ko. Uhmm. Duniya kenan. " Ki taimaki rayuwata ki bari nayi auran nan, idan ma kina so na daina kulata zan daina, wallahi zan iya ma sakinta saboda ke. Bana sone iyayena suji kunya bayan jama'a sun taru kowa yazo biki. Dan Allah ki rufamin asiri. Ya fada har yanzu yana duke a gabanta. Ta hararesa. " Wallahi bazan hakura ba, a fasa na Nana kamar yadda aka fasa na fatima. Idan kuwa kaki to wallahi ita Nana kasheta zanyi, dan ba'a haifi macen da zata so abin da nake so ba. Cikin sauri ta juya ta fita daga dakin, shiko nan ta barsa tsugunne idanuwan sa duk sun kada kamar zaiyi kuka. Sai daya dauki mintina a zaune, sannan yaji wayarsa ta fara ringing. Cikin sauri ya ciro daga aljihunsa. Hassan ne babban abokinsa. " Wai kana ina ne ka fita kabar Amaryarka gata nan hankalinta ya tashi, an neme ka ba'a ganka ba. Hassan ya fada bayan ya dauka wayar. " Sorry gani nan zuwa yanzu. Ya mike cikin sauri ya mayar da wayar aljihu ya fito. Yana shiga hall din ya samu kowa yayi tsuru- tsuru alamun hankali ya tashi. Cikin sauri ya amsa microphone ya bawa jama'a hakuri, sannan ya koma wurin Amaryarsa ya zauna, aka ci gaba da sha'ani. " Ina kaje ne haka, duk kasa na fara shiga damuwa?? Ta fada cikin shagwaba. Yayi wata 'yar murmushi sannan yace: " Kiyi hakuri, nadan zaga ne, cikina ne naji kamar zai baci. Dariya ta sakar masa, dan maganar da yayi. Shiko ya bita da kallo yana tunanin sharrin khairat. " Nana bazan iya jure rashin ki ba, bazan iya rabuwa dake ba saboda kece irin macen da na dade ina nema a rayuwana, samunki yafimin komai, rashin ki babban asara ne a rayuwana. Dan me zance na fasa auranki, gaskiya bazan iya ba. Cikin zuciyarsa yake magana. Karar wayarsa da yaji yasa gabansa fadiwa. A hankali ya lumsa idanunsa, dan ya san ba kowa bace illah khairat. " Bari na amsa waya 4 d last time. Ya fada. Nana ta hada rai sannan tace: " Why not ka amsa anan din, nifa bana so naga kana yin nisa dani. " Hayaniya yayi yawa ne Dear. Ya fada yana shirin fita daga hall din. Yana fita ya amsa. " Ya akayi kuma??? " Kazo ina bakin mota yanzun nan, karka batamin lokaci. Ta fada tare da kashe wayar. " Ya salam! Wai me yasa yarinyarnan take min haka ne? Ya fada yayin da yake karasawa wurin parking spaces. Tin daga nesa ya hangi motar tata, ya karasa inda take sai gani yayi ta bude masa kofar gaba. Bai mata musu ba ya zagaya ya shiga. " khairat ki dan bani break mana, kar wasu su gane abin dake faruwa fa. Ta taba baki. " Humm.. ai sa'arka daya dan kayi dabarar amfani da gate pass, da yau ka gane baka da wayo. Yace: " To ki barni na koma, ki tafi gida zanzo na sameki idan muka tashi. " Ban yarda ba. Kana tunanin zan tafi na barka kana sha'aninka da wata mace bani ba, ashe bani da kishi kenan. Yanda zan fita daga Hotel din nan yanzu kaima haka zaka biyo ni. Tayi saurin kulla kofofin daga ban garanta.SADIQ novels / DR SADIQ part 3 DR SADIQ part 3 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:18 Tana kokarin kunna motar Dr yayi sauri ya fisge mukullin motar daga hannunta. " Me kike shirin aikatawa ne wai khairat??? Ta zare masa ido. " Ka bani mukullin motata kafin na maka rashin mutunci. Idan kuma kasan ka cika namiji ka fita daga motarnan ka gani. Cikin sanyin murya Dr yace: " Honey wani irin so kike min ne da bazaki barni na saka ba na wala. Wallahi fa ina da zafi amma ina raga miki badan komai ba dan son da nake miki. " Idan kana sona da gaske ka aure ni mana, sai a fasa na Nana. Khairat ta fada. Ya kalleta sama da kasa. " No. Ni gaskiya ban shirya auran ki ba, ba yanzu ba, sai na fara auran wata tukunnan. Wata fadiwar gaba taji. " Kut!!! Lallai namiji dodone, niko idan anyi duniya dan manzon Allah S.A.W naga uban macen da zaka aura. Mun saka kafar wando daya dani dakai. Cikin sauri ta fisge mukullin motar ta kunna, yana kallonta amma ya kasa mata komai har taja motar yana ta faman babatunsa amma bata kulasa ba. Cikin wata babbar gidan ta dake boye a wata 'yar unguwa nan ta shiga dasu, tayi parking gyefe daya harda securities a gidan, sannan ta juyo ta kallesa. " Kaga wannan katafaran gidan, da kudinka na gina ta, dan mu biyu nayi badan kowa ba, ba wanda ya isa ya shigo idan bani dakai ba saboda soyayyar da nake maka. Securities ma dana saka dan ya zama dola ne, amma da baza kagansu ba. Dan haka ina sonka Dr sadiq dan bazan daina sonka ba har mutuwata. Ta bude kofa ta fita daga motar cikin sauri. Shima bai tsaya ba ya fito ya bita a baya. A falo yaga taja ta tsaya dan haka shima ya tsaya. " Khairat ina ganin mamakin kaina da kike min duk abinda kika ga dama. Wallahi babu wata mace da take takani tamin abun da take so sai ke. Idan ba ke ba wacece zata dauko ni a mota ta kawoni nan wurin ina kallonta kamar solobiyon namiji. Magana yake cikin bacin rai. Nan ta kwashe da dariya, sannan tace: " Idan ba solobiyon ba waye. Naga ma gangancin sojojin da suka yarda ka zama likitan su dan bakayi deserving ba. Duk wani bacin rai da zakayi dola kamin biyayya dan nasan kana sona, babu macen data isa ta kamo kafata ko wacece ita. Wata kallo ya mata mai tarun kunci. " Sanin kanki ne ina son zabin da iyayena sukamin, saboda suna sona sosai, kuma nima ina sonsu. Nana ce macan da zanso anan duniyar fiya da kowa amma bake ba, kuma insha Allahu saita zama matata. Cikin sauri khairat ta dauke sa da mari, lokaci daya ya firgita shima ya daga hannu zai rama amma ya dake. " Daka mara ai. Nonsense. Ta juya cikin sauri ta fita tsakar gidan. Securities dinta ta kira taja masu kunne akan kada subarsa ya fita daga cikin gidan, sannan ta dawo ciki. + Shiru-shiru Dr Sadiq zai dawo amma babu alamar ganin shigowarsa. Nana ce ta dauki wayarta ta kira amma yana ta ringing bai dauka ba, haka yasa hankalinta ya kara tashi a karo na biyu. Lokaci daya ta mike ta karasa inda abokanan nasa suke ta samu Hassan. " Hassan Dr fa ya kara fita bai dawo ba tin dazu, ya kusa 1 awa da fitarsa. Ta fada kamar zatayi kuka. " Subhanallah. Ya sake fita kenan. Ya fada tara da daukan wayarsa ya kira lambar tasa, amma sai yajita a kashe. Ya sake kiran lambar a karo ta biyo, amma ya sake jinta a kashe take. " Ya kashe wayar fa, amma ina ganin kaman ba lafiya ba. Nan da nan Hall ya kara rikicewa Ango ya bata, ba neman duniyar da ba'a masa ba amma ina shiru babu shi babu dalilinsa, ba inda basu shiga ba a Hotel dinnan amma Dr baya nan, sai dai motarsa kawai aka gani. Hankalin Nana yayi matukar tashi, kuka take yi sosai dan a ganinta an sace sa ne. Sojoji nan da nan suka bazu tako ina cikin daran nan, babu abinda kake ji illah saukar bindigogi iri iri, kota ina shiga sukeyi suna searching amma shiru babu Dr. An sanarwa iyayensa ta waya abinda ke faruwa, suma hankalinsu ya tashi sosai. Abinda Allah kenan ya mallaka musu a duniyar nan, wanda suke ji dashi har yakai ga suka shagwabasa dola sukaji tamkar cewa akayi ya mutu. Nana kam numfashinta ma har dauke wa yake yi saboda kuka, haka yasa duk wanda ya ganta cikin wannan yanayin saiya tausaya mata. Tayi kuka kamar ranta zai fita har ya kaiga ta fara suma tana farfadowa, cikin gaggawa suka kaita asibiti.IQ novels / DR SADIQ part 4 DR SADIQ part 4 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:21 Yana kwance akan gado yayi ruf da ciki inda ya kwantar da kirjinsa kan filo. Shiru yayi yana tunani dan yasan tabbas iyayansa suna cikin damuwa. Shigowar khairat dakin ne yasa ya daga ido ya kalleta, suka yi ido hudu da ita yayin da take rike da wata leda a hannunta, ta karaso inda yake kwance ta zauna akan gadon. " Sai ka tashi kayi wanka idan kaga dama, kaya ne na siyo maka. Ta fada tara da fito masa da kayayyakin dan ya gani. Ko daga kai baiyi ya kalla inda take ba, sai gyera kwanciyarsa da yayi, ya shareta baice mata komai ba. Ta sake magana. " Magana nake maka kana gyera kwanciya. " To me zance miki khairat, nagode kike so na fada??? Magana yake ba tara da ya juyo ya kalleta ba. Tace: " Bana bukatar godiyan ka, nayi ne dan neman suna a wurinka, amma badan hali ba. " Har wani hali ne dani. Na tabbata duk bad attitude nawa nasan ban kaiki ba, dan haka kisan abin da zaki dinga fadamin . Wata uwar tsuka taja masa. " Ko a jikina. Nidai burina dama ka kasance kusa dani ako da yaushe, kuma gaka nan ina ganinka ina jindadi. Cikin sauri ya mike ya zauna tara da juyowa yana fuskantarta da kyau. " Wai me kike nufi ne khairat, kina nufin zan dawo na zauna dake kenan har abada? To wasa kike yi, kima canza tunani. Just kawai ina binki ne dan saboda son da nake miki, tsakanin jiya da yanzu tunanin da nake kenan ta yaya zan cire sonki cikin zuciyata amma na rasa mafiya. But don't worry, lokaci zaizo. Ta fasa shi da wata bakar dariya, sannan tace: " Dr na riga na zama wani oart daga jikin ka, wanda idan bana nan bazaka iya functioning ba. Na tabbata soyayyar da kake min ita ta bani kwarin gwiwar taka ka yadda nake so, dan tin farko kai ka shagwabani da ita. Kaga kuwa baza ka iya auran ko wace mace ba bayan Khairat. Khairat taka ce, daga kai bata kula kowa, kaima haka baka isa ka kula wata ba bayan ita. Kaga true love kenan. Kureta da ido yayi ya kasa magana, illah tunanin zucin da yake yi. " Nasan ina son yarinyar nan matukar so, amma tana min abinda bana so, nasan Nana bata kama kafarta ba dan ta fita kyau da komai. To dan me zata dinga min haka bayan ni ba auranta zanyi ba, anya kuwa wannan so ce ko kuma hauka??? A hankali ya saukar da wata ajiyar zuciya, sannan ya lallabo ya matso kusa da ita ya zauna. " Honey, kimin rai ki daina treating dina harshly. Kinsan ina sonki kuma ina son iyaye na, dan me yasa baza ki barni ba na tafi idan aka daura auran sai na sake ta, na miki alkawarin ko hannunta bazan taba ba, amma yanzu kinsa iyayena cikin damuwa, na tabbata yanzu haka Area din mu ba lafiya, duk a dalilin ki. Dan Allah ki barni na tafi. " Idan kaga na barka ka fita daga cikin gidan nan sai nan da kwanaki biyar, burina dama a fasa auran ka da Nana, kaga nan da wannan kwanakin an manta sai na sake ka ka tafi. Na tabbata zumudi kake dan zaka zama angon Nana, to nima Amarya ce sai ka sake min soyayyar anan, amma bada wata ba. Nan da nan ya kara hada fuska dan dama can mai saurin fushi ne, amma baya tasiri akan khairat din sa, dan ko hannu bai taba gwadawa a jikinta ba da sunan duka. " Me yasa kike nema ki dinga wasa da intelligent dina ne, dan me zaki dinga min wasa da tunanina??? Ya fada cikin fushi. Ta kallesa idonta a cikin nasa. " Tafiya ne nace baza kayi ba malam. Duk wurin wadanda zaka je na tabbata baza su kareka da komai ba kamar yadda zaka zauna anan kusa dani. Dan me zaka batani bayan kasan zaka butulce min, ko kana so ka nuna min halinku na maza da ake cewa ba 'yan goyo da zani bane. To wallahi bazan yafe maka ba. Ta fara kukan shagwaba. Cikin sauri ya riko mata hannu dan ya rarrasheta, amma tayi sauri ta fisge. Cikin kuka ta sake magana. " Me zakamin bayan ka nunamin baka kaunata a fili, ka riga ka gama da rayuwata zaka wulakanta ni. Amma ba komai duniya ce. Ta watsar da kayan kasa, ta mike cikin sauri tabar dakin. Yana ta faman kiranta amma bata dawo ba. + A dai-dai bakin wata kogo mai dan girma khairat tayi parking din motarta. Jakar dake kusa da ita a dayan seat din ta rataye shi ta dauko tara da budewa ta zaro wata 'yar karamar mayafi ta daura kanta dashi, kasancewa cikin daji zata shiga. Yau kam wata 'yar 3 quarter ce a jikinta data matse ta sosai, sai 'yar top data saka shima dake nuna ilahirin jikinta a waje. A hankali ta bude motar ta fito tara da daukan jakar hannunta kawai tabar ta ratayen a ciki, ta rufe motar ta nufa cikin dajin. Wata 'yar tazara ce kadan inda bokan nata yake dan babu nisa sosai daga bakin motarta. Kai tsaye ta shiga cikin bukkansa da yake ciki, yana ganinta yayi murmushi yayin da ta samu wuri ta zauna. " Khairat 'yar baba, ba'a miki a kwana lafiya. Bokan yayi magana. Ta taba baki. " Hum.. baba kasan meke faruwa kuwa??. " Sai dai ki kara bayanin ki, amma nasan komai. Ta girgiza kai alamar taji dadi. " Baba aure suke so su masa iyayensa, kuma kasan ba wani 'da namijin da nake so anan duniyar fashe Dr Sadiq. Baba idan suka masa auran nan bansan wace irin mace zai auro ba, mayb tana da lakanin karya asiri zata iya rabani dashi, kuma wallahi zan shiga wani hali. Bokan ya tintsire da dariya sosai, sannan ya fuske ya fara magana. " Yanzu me kike so a masa??. " Baba so nake a cusa masa tsanar yarinyar da zai aura, ya koma wurin iyayensa yace baya sonta ya fasa. Sannan ina son a kara dauremin shi da sarka bakwai ya zama sha hudu, na dinga taka sa yadda nake so, duk abinda nace yayi ya daina musayar yawu dani, yaji magana ta fiye da iyayansa. Infact ma, ya zamo tamkar bawa na karshe a wurina. Bokan ya kalleta yayi murmushi. " Zan baki laya guda biyu, daya ki saka masa a karkashin gadonsa, daya kuma ki saka masa a kasan kwanon da zaici abinci kafin yaje gidansu kan maganar auran. Layan da zaki saka masa a kasan gadonsa ki tabbata cewa awannan gadon ya kusanceki ba wani wuri ba, sannan zaki iya amfani da duk abinda ya fito daga jikinsa a wannan lokacin ki masa girki yaci dashi. Kin gane ko??? " Eh na gane baba. Ta fada yayin da take zaro bandir din kudi daga cikin jakar hannun da take rike dashi. A kusa dashi ta ajiye, yayin da shima ya mika mata layar guda biyu babba da karami, tasa hannu ta amsa. " Babban ita zaki saka masa a karkashin gadonsa, karamar kuma a kasan kwanon abincin. Bokan ya fada. Tana amsa ta buda jakarta ta saka a ciki tara da mikewa ta fita ba tara data masa godiya ko sallama ba. Dama ita tasan rules na bokan ba'a masa sallama idan za'a shiga ko za'a tafi, haka ba'a masa godiya tafiya kawai ake.ovels / DR SADIQ part 5 DR SADIQ part 5 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:23 Yana fitowa daga wanka bai samu khairat ba a dakin dan haka ya bude wardrobe ya dauki towel ya fara goge jikinsa dashi. Yanzu kam yaji hankalinsa ya fara kwantawa, ya dawo yana jindadin abin da khairat din ta masa. Shigowar khairat ne yasa yayi sauri juyawa ya kalleta tara da sakar mata murmushi. Itama kallansa take yi dan tabbas tasan bokan yayi aiki. " Murmushin nan na lafiya ce kuwa??? Ta fada cikin kissa. " Zo ki zauna kiji wani abu. Dr ya fada tara da nuna mata inda zata zauna kusa dashi. Cikin sanyin jiki da jan aji ta karasa ta zauna kusa dashi tara da daura kanta akan kafadarsa. "A duk lokacin dana jiki kusa dashi, ko na samu farantarwa daga gare ki, actually, ina matukar rena kaina. A gaskiya honey kin cika mace dan kinfi min mata da dama, anan duniyar. Magana yake cikin kwanciyar hankali. Khairat ta dago ta kallesa tara da dafa, hannunta daya akan kuncinsa. " Na dade ina jin irin wadannan dadaddun kalaman daga bakin ka dear. Nasan ka daina sona yanzu, nice dai dana kamu da maitar sonka wacca take nema ta illatani akanka, dan baka son ina yi ba. Kace ka yarda da zabin da iyayanka suka maka akan wata bani ba, ni basa sona dan sunce bana impressing dinsu. Kaga kuwa iskace kawai take wahalar da mai kayan kara. Dr yayi saurin cewa: " Ba haka bane khairat. Idan su basa sonki ni kuma u really means alot 2 me. Wallahi son da nake miki yanzu zan iya converting nasa dana iyayena. Dan yanzu haka yadda nake ji, Nana ta fara fita min daga raina, dama can bana sonta anyi forcing dina ne akanta, amma yanzu a shirye nake da nace na fasa komai. Wata irin murmushin jindadi khairat ta sakar, har sai da shatin fararan hakoranta suka bayyana fili. " Allah yasa da gaske haka maganar taka take. Yanzu ka fara bani tsoro ne Dr, ban sani ba ko wasu ne suke son su shiga tsakani na da kai, dan suna rivalry akan mu. " Duk abin da zasuyi baza suci galaba akan mu ba. Dan haka I really luv u, kuma I totally mean it. Ya fada yana fara'a idonsa akan nata. Tace: " Okay sai kasa kaya ka fito muci abinci ko. " Why not, mu shirya mu fita Oasis muci, dan kinsan bana son kina wahala akaina. " Ai dole, idan banyi ba wa zanyi wa. Don't bother na riga na gama ma, yana kan dinning. Murmushi kawai yayi, sannan ya mike ya fara saka kayan nasa. + Tin da suka shiga cikin gari da mai taxi ya fara ganin poster din hotunan sa ta ko ina, duk akan cigiyarsa. Mai taxi shima tin daya dauko sa ya gane sa, dan Allah Allah yake yayi branching dashi police station dan Samun kyautarsa da akayi wa duk wanda ya gansa alkawari. Suna isa dai-dai traffic yaga driver din ya tsaya, da alama yana shirin ya shiga hannun da aka nuna musu alamar su tsaya daya hannun kuma da aka basu hannu itace hanyar inda zai kaisa amma bai bi taba. " Malam ina zaka kaini ne??? Dr ya tambayesa. Driver din bai juyo ya kallesa ba yace: " Station zan biya dakai kafin na kaika gida, dan yau kwana biyar kenan ana neman ka, dalilin batanka yaso ya jawo rikici tsakanin sojoji da jama'ar cikin gari, dan har an fara rasa rayuka da dama. Sai da General na sojojin ruwa, wanda yace shine mahaifinka yayi magana, sannan komaiya lafa. Cikin fushi Dr yayi sauri yace: " Look malam, gida nace ka kaini ba station ba, koma me ya faru ni baidame ni ba. Cikin mamaki driver din ya juyo zaiyi magana, nan yaga an basu hannu akan su tafi. Cikin sauri ya taka motar yayi hanyar station din. Dr cikin tsawa ya sake cewa. " How dear u, kanka daya kuwa, nace ka kaini gida ko. " Ka kwantar da hankalin ka, bazan iya komawa ta one way ba. Suma police's din ba komai zasu maka ba, iyayanka zasu kira su dauke ka. Ya fada yayin da yake ta taka motarsa da sauri. " Ni fa ba karamin yaro bane, zan iya taka birkin motar nan unexpected ni da kai mu mutu, dan haka ka sauke ni na fita, ko kuma na maka duka wallahi tallahi. Cikin fushi yake magana. Ganin da gaske yake yasa driver din yayi saurin parking a bakin gate din station. Cikin sauri Dr ya bude kofar ya fito yana fada. " Sai naga uban dazai biya ka stupid imbecile kawai. Cikin sauri police's din dake wurin suka karaso dan ganinsa. " Wannan bashi ake nema ba, Dr sadiq yaron General??? Cikin mintina kadan magana ya bazu ko ina, nan da nan aka cika a station din, 'yan jarida da sauran ma'aikatan gidan redio da T.V sun hadu sai faman tambayoyi ake masa amma yaki magana, dan yaki nuna musu fuska. Nan da nan jiniyar motocin mahaifinsa suka karaso wurin, ba'a dauki lokaci ba suka daukesa a mota suka nufi gida. Suna zaune a babban katafaran falon gidansu na baki, da iyayansa da sauran dangi da basu tafi ba, inda suke ta faman masa tambayoyi. " Ka bude baki kayiwa mutane magana, ko wani abune yake damun ka??? Hajiya ta fada. Ya kalleta sannan ya sun kuyar da kansa kasa. " Mum ni na gudu da kaina dan bana son ku auramin Nana. Lokaci daya jama'ar dake wurin sukayi salati, cikin mamaki kanin mahaifinsa yace: " Kana cikin hankalinka kuwa Dr, abin dakayi akan fatima zaka sake yi akan Nana??? " Uncle hankalina daya wallahi, sonta ne kawai bana yi, nace su auramin wacca nake so amma sunki, dan me zan yarda amin auran dole ina namji ba mace ba. Magana yake cikin daga murya. Yace: " Amma me yasa earlier ka amince da kaji ka gani, ko kana so kamayar damu kananan yara ne??? " Shine kuwa karamin yaro, dan ya girma ba hankali. Kodai wata ce take hure masa kunne??? Wata 'yar uwansu ta fada. Hajiya tace: " Ba ko wace 'yar iska bace na sani face khairat, 'yar gidan General, yarinyar da ko a mafarki bazan so na hada zuri'a da ita ba. Cikin sauri Dr yace: " Mum kibar bata mata suna a gaban jama'a mana. Dan me zaku tsana abinda nake so, kuma wai da sunan nima kuna sona. Lokaci daya General ya mike duk ya fusata da maganganun Dr ya daukesa da mari lafiyayyu hannu bibbiyu sau uku. Wannan shine karo na farko da ya taba lafiyar 'dansa. " Idan kwakwalwarka ta mutu zan gyera maka ita. Aure ni nayi niyya, kumat baza a fasa ba, dan haka ka shirya gobe dole ka zama Ango. Dola nasa a daure 'yar iskan yarinyar nan, dan bazata batamin zuri'a ba. Idan kai ta gagare ka, mu bata fi karfin mu ba. Ya juya ya nufa cikin dakinsa. Dr ya jigata sosai, hannunsa biyu a fuskarsa yana rarraba idanu,y dan bai san yana zubar da hawaye ba.els / DR SADIQ part 6 DR SADIQ part 6 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:25 A daki ya samu Hajiya tana zaune tana waya da kawarta kan maganar daurin auran nasa na gobe. Ganinsa ya shigo yasa sukayi sallama ta kashe wayar, ta mayar da hankalinta kansa. A bakin gado ya zauna kusa da ita, kallo daya zaka masa, kasan ya shiga cikin damuwa. "Mum yanzu da gaske kuke wai gobannan zaku auramin Nana, ko ina sonta ko bana sonta??? Hajiya ta tsare sa da ido. " Sanin kanka ne mu ba kananun tmutane bane, sannan mu ba mayaudara bane da zaka dinga yawo mana da hankali. Zabin da kake so mu baka zuri'armu tafi karfinta, batayi kama da macen da zamu baka ita ba, dan ba 'yar mutunci bace. " But Mum gani nayi fa kunsan iyayen yarinyar nan, kuma mahaifinta itama babban mutum ne a kasan nan kamar mahaifina, dan me zakuyi tunanin nafi karfinta, bata fi Nana ba sau dubu. Dr ya fada. Hajiya ta girgiza kai. " Nana ta fita komai, dan kuwa mutunci shine 'ya mace, wacca kuma bata rike mutuncinta ba bata cika 'ya mace ba. Kasancewar ta 'yar babban mutum baza ta kasance babbar yarinya ba a idanuwan mu. Dan yarinyar daka kawota cikin gidannan tsirara, baza ta zama sirikata ba. Akan yarinyar nan mutuncin gidan nan bazai zube ba a idon jama'a. Nan da nan ya kara hada rai. " Mum to ni gaskiya ko kun auramiin Nana bazan zauna da ita ba, kuma ni zan koma inda na fito ne. " Ka dade baka tafi ba idan bariki ne, kuma ka dade baka zauna ba idan aka aura maka ita. Idan kuwa kace zaka fiffita mace daya akan sauran, na tabbata zaka wahala a rayuwa, ykuma zaka jefa kanka cikin halaka. Dan haka tin farko kasan abin da kake yi, Nana jinin kace ba bare bace, kuma na tabbata baza mu zaba maka mace da bata dace dakai ba. Magana take masa cikin natsuwa. Dr dai ya fuskanci lallai maganan da Mum dinsa take masa ba wasa take ba, haka yasa yaji kansa duk ya daburce ya rasa meke masa dadi. Shi dai yasan tabbas yanzu baya son Nana ko kadan, idan suka aura masa ita bata da wani amfani a gurinsa, dan haka dole yayi da gaske dan ganin an fasa auran nan. " Mum kamar bakya sona, kamar bani kuka nuna wa so ba tin ina karami har girmana. To dan me zaku nema ku sauya min zabina akan naku??? Magana yake kaman zaiyi kuka. Hajiya tace: " Tin farko kai kayi na'am da maganar, da baka yarda ba baza mu tilassa maka ba. Dan haka mun riga munsa rana, har lokaci yazo baza kayi betraying din mu ba. Lokaci daya ya mike, cikin daga murya ya fara magana. " Mum bazan zauna ba, zan koma daga inda na fito, idan har dola sai kun min aure, to wallahi zan bar gidan nan. Ya juya cikin sauri yayi hanyar fita daga dakin. Hajiya tana ta ihun kiransa amma bai juyo ya dubeta ba. Ganin haka yasa hankalinta ya tashi, cikin sauri ta biyo bayansa amma bata gansa ba har ya shiga ban garan sa. Da sauri da sauri ta nufa bangaran General, kai tsaye ta nufa cikin falon sa nan kuwa ta samesa zaune shi kadai. " Alhaji kasan a tare ko wace kofa ta fita daga gidan nan, Sadiq ya rantse zai koma daga inda ya fito fa. Magana take cikin rudiya. Cikin sauri General yace: " Yanzu yana ina?? " Ya nufa dakinsa, kasan halinsa idan ya zuciya komai ma yana yi. Inji Hajiya. Yace: " Ok... zoki zauna bari nayi waya. Cikin sauri ya dauki daya daga wayansa, ya danna number tara dakai kunnan sa. " Duk wata kofa daka sani ta fita da shiga cikin gidannan ku rufe ta, sannan ina so a rufemin kofar falon dake bangaran Dr, bana son yayi step out din kafar sa, koda nan da tsakar gidan nan. " Alright sir. Mutumin ya fada. Daga nan ya kashe wayar, ya juyo ya kalli Hajiya wacca hankalin ta ya tashi sosai. " Ki kwantar da hankalin ki, daga yau nasa masa tarko kenan, bazai iya tsallakawa ba. Zai gane bashi da wayo. General ya fada. Tace: " Yawwa hakan ma da kayi yayi dai-dai. Dr yana shiga daki mukullin motarsa kawai ya dauka ya juyo ya fita daga dakin. Yana kai hannunsa dan bude kofar falon, sai ji yayi ana rufewa daga waje. Cikin fushi ya buga kofar, da hannunsa. " Waye wannan??? Amma yaji shiru ba'a yi magana ba. Nan ya shiga kwalla wa sojan dake gadin bangaransa kira,amma yaji yayi shiru bai amsa ba. Wata takaici yaji ta kamasa dan yasan bashi da mukulli ko daya a wurinsa, bai ma san kalar mukullin kofar ba. Cikin sauri yayi tunanin fita ta ban garan Mum dinsa, ya juya ya nufa wurin da sauri dan ya fita. Bai kai ga fitaba nan yaga Hajiya sun shigo ta wurin, yana ganinsu yaja ya tsaya. " Dad ya zasu rufemin kofa 9:30, bayan lokacin kwanciyata bata yiba?? Dr ya fada. " Of course ni nasa a rufe dan kana niyyar fita daga gidan. Daga yau ka daina fita kai kadai sai da masu tsaro, ka dai jan mota ko wata irice sai dai a jaka. Bani duka mukullayen motocin ka. Ya fada tara da mika masa hannu dan ya basa. Cikin sanyin jiki ya mika masa, dan yasan baya musayar yawu dashi. Ya sake cewa: " Ina sauran suke?? " Suna cikin bedroom dina. Ya fada kamar bashi da baki. Yace: " Jeka ka kwaso ka kawosu yanzun yanzu. Cikin sanyin jiki Dr ya juya ya shiga dakin ya dibo mukullayen guda uku ya mika masa. Daga nan basu kara ce masa komai ba suka juya suka fita daga dakin, tara dasa mukulli ta dayan kofar suka rufe. Wata ihu ya saka na takaici da bakin cikin ya fada kan kujera yana kuka kamar karamin yaro. + Khairat tana zaune akan gadonta ta matsu taga shigowar mutumin dan jin good result amma shiru. Ganin ta matsu sosai kuma dare ya fara nisa yasa ta kira wayarsa. Bai dade da fara ringing ba taji ya daga. " Dear kana ina ne??? " Honey ina gida ba hanyar fita, dad yasa an rufe min bangarena ba inda zan iya fitowa. " Kamar yaya ba inda zaka fita, kana nufin maganar auran yana nan har yanzu ne???? Ta fada cikin matsuwa. Yace: " Dearest nayi iya bakin kokari amma komai yaki fasuwa, wallahi ina cikin...... " Keep quiet! Ta daka masa tsawa. " Fine.. dama dalilin kenan daya sa ka hanani binka dan ka munafurce ni. Dama na fada baka sona,ka batamin rayuwa ce kawai dan ka biya bukatar rayuwarka. Amma Allah ya isa Dr. Magana take cikin fushi. " Wallahi ba haka bane Honey, bana son Nana ke nake so, bazan yaudare ki ba dan kin wuce tunanin da nake ciki yanzu. Pls karki fada haka. " Dola zan fada haka, dan baka da imani mutumin nan. Iyayanka sunfi nine, ko sunfi karfin ka ne. But ba damuwa, its not ur fault. Iyayanka su aura maka Nana, ka dafa ta ka cinyeta saboda tsananin son da kake mata. Ta kashe wayar. Wata bakin cikine taji ta toshe mata zuciya. Cikin sauri tayi wulli da wayar gyefe daya ta kwanta kan gadon tana kuka mai sauti. " Lallai kuwa yau za'a san an taboni. Lallai kuwa za'a san an kwace min farin cikina. Lallai Nana zata gane shayi ruwa ne. Basu san sharri na ba, suna wasa dani. Zatayi nadamar auran abin da yafi karfinta. novels / DR SADIQ part 8 - 9 - to 10 DR SADIQ part 8 - 9 - to 10 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:32 Cikin sauri ta taka motar tara da budewa ta fito da sauri ta karasa inda yake kwance. Ganin yadda jini ke fita daga jikinsa yasa tsigar jikinta tashi, bata san lokacin data kwalla wata uwar kara ba. Babu mutum ko daya da suka zo wurin, kasancewar haka hanyar take ba mutane da yawa sai daidaiku ke wuce wa. Cikin hanzari ta dago sa daga suman da yake, amma taji ya mata nauyi baza ta iya daukan sa ta saka sa cikin motar ba. Ta juya ta kalli gabas da yamma kudu da arewa amma babu alamar mota ko walkiyar mutum. " Na shiga uku, na kashe abuna da hannuna. Cikin kuka da karadi take magana. Cikin dabara ta mike ta dinga jansa jini sai fita yake a wurin da yaji rauni, da kyar ta samu ta saka sa cikin gidan baya ta rufe, sannan ta zagaya ta shiga taja motar. A hanyarta ta kaisa yasibiti taji wayayoyinsa dake aljihun wandonsa sai faman ringing suke amma bata kula suba, dan hankalin ta duk ya tafi akan ta kashe sa. Suna isa asibitin aka daukesa aka shigar dashi emergency ward. Ganin yayi rauni da yawa yasa likitocida dama suka cika kansa suka shiga treatment dinsa. Tana tsaye ta kasa natsuwa wuri daya sai zagaye takeyi dan hankalinta yayi matukar tashi ta fara nadamar abinda ta aikata. Kiran daya sake shigowa wayar tasa ce tasa takai duba ga wayar dake hannunta taga sunan MUMCY. Haka yasa tayi tunanin mahaifiyarsa ce, ta amsa wayar. " Assalamu alaikum. Cikin karamar murya ta alamar mai kuka. " wacece haka?? Ta fada dan jin muryar mace. Khairat tace: " Mum khairat ce, Dr ne ya samu hatsari wata mota ta bigesa kuma ta gudu, yanzu haka muna Turkish Hospital, dan Allah kuzo yanzu. Cikin sauri Hajiya tace: " Innalillahi wa'innailaihi raji'un... Tara da kashe wayar. Cikin mintina talatin suka iso Hospital din, bayan likitocin sun gama treatment nasa amma sun hana kowa ya shiga wurinsa. Suna shiga suka tarar da khairat zaune, da ganinta tayi kuka kamar ba gobe amma duk da haka hankalinsu baya kanta burinsu suji wani hali 'dansu yake. " Ina yake, a wani ward suka ajiyesa??? Hajiya ta tambaya cikin matsuwa. " yana Emergency ward, amma sun hana shiga. Basu saurareta ba suka yunkura gaba daya suka nufa ward din da yake. Ganin ta tare da SSS yasa likitocin suka barsa ta shiga dan sun tabbata matar babban mutum ce. A kwance suka samesa hannunsa daya dauke da jini, gashi an nada masa fararan bandages da yawa a jiki. Haka yasa hankalin Hajiya ya tashi dan ganin yayi rauni da yawa sai data zubar masa da hawaye. Basu jima a dakin ba nan su General suma suka shigo tara da khairat biye dasu a bayansu. " Ya salam. Yaushe wannan yaron ya fito daga gida har wannan incident din ya faru a kansa, me yasa yaron nan yake da kunnan kashine 4 God sake! Cikin fushi da daga murya yake magana. Umar yace: " Wallahi bamu san fitarsa ba Alhaji, muma nemansa muka yi muka rasa. Hajiya tace: " Watakil tambadaddiyar can ce ta kirasa. Ta fada tara da nuna khairat inda take tsaye. Cikin sauri kowa ya juya yana kallonta, dan wasu ma sai a wannan lokacin suka santa amma suna jin labarinta. General cikin sauri yace: " Ku kama min ita, sai nayi detention nata na wasu lokuta kafin zata barmin 'dana ya sake. " Me na masa bayan taimakon dana masa na kawosa nan, ni me zanyi da 'dan ku fashe shi da yake takura kansa akaina. Kun masa aure kuna tunanin zanci gaba da zama dashi ne, bayan bakwa sona. Ba wanda ya isa ya daure ni tinda nima da gata ta kamar yadda 'dan ku yake da gata a gurinku. Just kawai iyayena basa kasar ne da wallahi wani abun ma baza ayimin ba. Magana take cikin kuka. Uncle dinsa yace: " Kar ki nema kiyi wa mutane rashin kunya anan, dan naga alamunki baku da manya a gidanku. " Rabu da ita. Yanzu zan kira mahaifin nata daga England din da yake, zan sanar dashi. Inji General. Cikin sauri ya kira lambar mahaifin nata, tana tsaye tana jin maganganun da sukayi. Bayan sun gama gaisawa yace: " General 'yar ka khairat tana hannuna zanyi detention nata na wasu lokuta, kasancewar 'dana. Yayi aure amma tana distracting dinsa dan suna soyayya a baya. Dan haka tana zaune a gidana ba duka ba zagi, har sai 'dana ya karkatar da hankalinsa kan matar dana aura masa zan sakota. " No. Karka mata haka, kawai ka koromin ita ta dawo gida, dama ina son ganinta taki dawowa ne. " Don't bother. Zata dawo bayan na gama solving cases na gidana. Sun dauka lokaci suna waya,sannan daga baya sukayi sallama ya kashe wayar. General yace: " Ku kaita gida a bata part daya daga baya, babu fita babu shiga komai ta dinga yi a ciki, duk abin data bukata a bata, ko kadan karku tsawatar mata. I think haka ya isheta. Cikin sauri sojoji uku suka tasata a gaba, tin tana musu gardama har ta bisu suka shiga mota, suka jata suka tafi. Sai misalin bayan mangariba sannan Dr ya fara motsa jikinsa. A wannan lokacin ya farfado, abin mamaki sunan khairat ce ta fito daga bakinsa haka yasa Hajiya kanta ya daure sosai ta fara tunanin wani irin so wannan yaron yake ma yarinyar nan haka. " Mum ina khairat, ta gudu ko, tace na cuce ta kuma Mum is not my fault. Ya fada cikin karamar murya. Hajiya ta kallesa cikin tausayawa. " Dr karka damu kanka akan wannan yarinyar, yanzu aure ne da kai, ya kamata ka tsayar da hankalinka kan matarka ba akan wata ba. Yace: " Mum ni khairat nake so, ita kadai na sani ba Nana ba, bana sonta me kuke so nayi da rayuwata. " Yanzu da jikinka zaka ji ko da wani zance daban, me yasa baza ka kalla incident din daya faru dakai ba. Sai a wannan lokacin ya duba abubiwan dake jikinsa. " Meya faru dani, waya kawoni nan??? Hajiya tace: " Wasu ne suka nema su kashe ka, khairat ta kawoka. " Ina take Mum ki kirata na bata hakuri pls Mum. Ya fada cikin nuna damuwa. " Ba inda ta tafi tana nan, amma baza mu fada maka inda take ba har sai ka tsayar da hankalinka akan matarka. MU HADU A PART 9 M gwamba 08168898969 DR SADIQ PART 9 Bangaran da aka kaita babban wuri ne wanda babu abinda baza ta rasa ba a ciki, sai dai na wani daban data bukata. Abin daya kara ci mata tuwo a kwarya shine, wayoyinta da guardians din suka kwace suka barta haka shi ya kara tabbatar mata da cewa lallai mutanan nan sunyi daukan serious akan ta. Yanzu kam ma idan tayi kuka duk a banza dan tasan ita da ta kara ganin Dr Sadiq sai wani ikon Allah. Dan mayb ma zasu mayar dashi inda bata sani ba. A ganinta zai iya yuwa shima mahaifinsa ya kwace wayarsa ya canza masa sim, dan idan ba haka ba tasan komai daran dadewa zata ga abinta, dan tasan inda tushen son nata ya dosa. Bakin ciki ya cika ta kamar ta hadiyi zuciya ta mutu. " Wai yau nice aka tsare kamar wacca take cikin prison, ba dan komai ba duk akan namiji dana daura wa kaina sonsa kamar shine autan maza. To waima wani tsautsayine ya hadani da wannan mutumin har na kashe kaina da soyayyarsa. Anya ina da hankali kuwa. Ko dai haka so take, ko kuwa tawa ce ta fita daban. Kodai shima Dr asiri yamin dan na mutu akan soyayyarsa. Oh my God! Nidai naga ta kaina da wahalar duniyar, sai dai bazan daina sonka ba Dr koda kashe ni za'ayi. Maganganun data dinga yi kenan a zuciyarta, amma ko kadan ta kasa zaba wa kanta mafita cikin al'amarin, dan tabbas tasan tana cikin daka mai wiya. + Ba yanda Dr baiyi ba dan ya samu Khairat a waya amma ko kadan layin nata baya tafiya. Haushi da kuncin rai kamar ya kashe sa, dan kuwa gani yake idan babu khairat bazai iya jindadin zama da kowa ba, saboda rayuwarsa gani yake kamar tafiyar su daya. Yanzu kam ya canza ma koma baya sake masu, dan ko magana aka masa bai cika kula jama'a ba duk da cewa shi mai mutane ne, amma saboda fadin rai daya dauka na rashin sahibar tasa yasa ya daina ganin kowa da ido a fuska. Kwanakin Dr biyar, a asibiti aka sallamesu suka dawo gida, dan ganin jikin nasa yayi sauki sosai, amma shi kam bai damu da wannan ba dan abin daya saka a ransa tafi karfin wannan a ganinsa. Washe garin ranar abokansa suka rakasa dakin Amaryarsa, bayan sun masa nasiha sosai suka barosa suka dawo gida. Sai yau Nana tasa idonta akan mijin nata tin ranar daya dawo gida, dan asibitin ma bata samu taje ba kasancewar hana ta zuwa da akayi. Dr baice mata ba itama bata ce masa ba, ganin tasan hali yana da bakar zuciya kamar jaraba yasa ta kaskantar da kanta ta daga kai ta kallesa inda yake zaune bakin gadon ya juya mata baya. " Na tabbata duk wasu masoya babu ranar da yafi farin ciki a garesa face wannan daran dazasu kasance a inuwa daya, amma kai sai naga taka fuskar tasha banban data kowa. Bai san tana yiba dan kuwa ko motsi baiba balle tasan yaji abin data fada. Ganin dai yayi shiru bai amsa mata ba yasa ta sake cewa: " Dr kodai na maka lefine ka fadamin na nema gafararka, dan bana son na ganka cikin wannan halin. Pls kayi hakuri. " Banyi mamakin dan kin samu damar ki tunkareni da irin wannan maganar ba. Unfortunately ada naso ki amma yanzu bana tunanin hakan, dan kuwa an raba ni da abinda nake so kuma duk akan ki. Bana tunanin zan tausaya miki akan zaman da zamuyi da ke, dan kema sai kinji radadin da nake ji akan rabani da abin alfahari na. Cikin mamaki ta tsaresa da ido. " Nima nasan da hakan zaiyi wiya naji dadin zama dakai, dan tin da naga ka canza kafin auran nan. Nima naso a fasa kowa ya hakura amma Dad ne yaki, dan nasan nice zan wahala bakai ba. Ta fara kuka. Sai a wannan lokacin ya juyo ya kalleta. " Bakiyi komai ba tukunnan dai. Ba auran zumunci kike so ba kinyi ai sai ki jure abinda zaki tarar a cikinta. Cikin saukin kai yake mata magana. Kuka take yi na gaske. " Dan Allah Dr kayi hakuri, Wallahi ba lefina bane, iyayan mu ne suka hada abin nan bani da wata masaniyya a ciki. " Kar kiyi deceiving kanki mana, da baki ce kina sona ba zasu tilassa miki dole sai kin aure nine. Ni ban taba ganin mayyar mace mai nace wa maza bama irinki. Wata fadiwar gaba taji. " Ni ban nace maka ba, illah biyayyar da nayiwa mahaifana dan naga na faranta musu. Dr duk dabi'un ka ba wanda ban sani ba kan courtship dinka da Khairat, amma na danne zuciya dan kana 'dan uwana na aureka, amma abin da zaka zo kana fada kenan ka daura blame din a kaina. Cikin kuka take magana. Yace: " Kwarai kuwa dola zan fada dan kuma lefinki zan gani, tinda kece zaki zauna dani basu ba. Bazan miki kallon matar da nake aure ba, kuma bazan sake ki ba. Dama ni dan hutu ne dan haka dola ki fuskanci bauta da wulaknci da rashin mutunci da tozartawa daga gare ni, dan such an atom na sonki bana ji a cikin zuciya ta. Da sunan kinyi aure ne, amma ba aure kikayi ba slavery aka kawo ki. Dan haka u need 2 pity ur self tin yanzu. Ya mike ya fita daga cikin dakin. Tabbas jikin Nana yayi sanyi sosai, dan kuka takeyi kamar ba ita ba. Bata taba jin bakar magana ba irin wannan tinda take, amma gashi yau aure ya jawo mata. Lallai kam tasan ta dibo ruwan dafa kanta, dan tsautsayine tasan ya jawota gidan Dr ba komai ba. Tayi kukanta ta gaji dan taga bamai karewa bane, haka yasa ta mike ta shiga toilet ta dauro alwala ta fara nafilolin data saba. Ta dade tana addu'o'i dan samun mafita daga halin da zata shiga, dan tasan Dr ko kadan yadda take jinsa bashi da kamshin tausayi ko sassauci. Har kusan karfe daya da wasu mintina tana abu daya gashi har yanzu bata ga shigowarsa ba, dan haka yasa tayi tunanin watakil ma ya kwanta a dayan dakin bazai kwana a nata ba. Dan haka tana gama abubuwan da zatayi ta mike ta rufo kofarta ta nema wuri ta kwanta zuciyarta cike da tunani. Da sassafe tana cikin bacci bayan tayi sallar asuba, kamar a cikin mafarki taji an janye mata filon da take kwance akai. Cikin firgita ta mike nan ta gansa tsaye a kanta sanye da doguwar jallabiya. " Nan ba gidanku bane da zaki dinga farkawa bacci tara ko goma, kina da aiki a gabanki ki fito ki biyoni. Bata masa musu ba ta mike ta bisa a baya ganin yayi gaba. Suna fita daga dakin taga yayi hanyar fita daga falon suka nufa tsakar gida. Bai tsaya ako ina ba sai bakin motocin dake ajiye gyefe daya. " Kinga motocin nan su nake so ki wanke min su gaba daya kuma su fita sosai dan sababbine, dan kuwa zan fara fita da daya yau. Cikin mamaki ta juya ta kalli inda motocin suke a ajiye har guda uku. " But kasan nifa macece, gashi ban taba wanke abu kamar haka ba, dan bani da straight da zan iya wannan aikin sai maza. Why not kasa securities din gidan su wanke maka??? " U r not serious. Na sallamesu saboda na samu baiwa daga sama, dan haka ko kin iya ko baki iya ba practice make perfect. Ki wanke su. Cikin nuna isa yake magana. " Na shiga uku! Dan Allah Dr ka tausaya min, nifa macece bana irin wannan aiki, infact ka dubama fa ka gani yadda sukayi kura, it wil take me alot of time akan mota daya. Dan Allah have mercy on me, bazan iya ba. Ta tsugunna masa ta fara kuka. Ko kadan baiji tausayinta ta kamasa ba, sai haushinta da yake kara shigansa. " Idan kina son kanki da arziki kiwanke, idan kuma kina son kiyi argument da nine go ahead. Ki duba toilet dina akwai freshener ki dauko. Ya juya ya fita daga cikin gidan. MU HADU A PART 10 Zanyi amfani da wanan daman in mika dinbin gaisuwana zuwa ga 'yan uwa da abokan arziki da sunansu bazasu kirguba ma'abota bibiyan wanan shafin namu mai farin jini da fatan Allah ya karbi ibadunmu. Ameen ((((G. M. B))))) 08168898969 DR SADIQ PART 10 Haka ta kuge ta daure ta fara wanke su duk da cewa bata san yadda ake ba, kafin ta kaiga wanke na farko duk ta gaji gashi bata sa komai a cikin nata ba tin jiya. Takaici da bakin ciki taji su tamkar ta hadi zuciya, dan ko kadan bata sako irin wannan bautar a harkokin rayuwarta ba, yau gashi 'dan uwanta ne ya saka ta. Gajiyan da tayi ne yasa taji jikinta duk ya mutu dan haka bazata iya shiga kicin ba, tana ji tana gani haka ta hada tea da ruwan sanyi ta zauna tana sha a dinning. Sai a wannan lokacin ya dawo cikin gidan ya sameta anan falon. Ganinsa yasa taji gabanta ya fadi, shiko ya hada rai tamkar yaga makiyarsa. " Amma da kinyi denying akan cewa baki iya ba, yanzu wa ya wanke miki, ko uncle kika kira ya wanke??? Ya tambayeta ta fuskar rainin wayo. Zafin maganar daya mata yasa tace: " Haba Dr mai kuma ya kawo maganan mahaifina a cikin wannan maganar, koda baza kayi respecting nasa ba kasan ya kusa haifanka fa. Cikin tsawa ya duka dinning table dake gabanta sai data tsorata. " Excuse me! Har kin samu damar da zaki fara conversation dani, kodan kinga kin fara kwana a daki next to mine?? Dat should be d first nd last da zanyi magana ki amsa min. Koda mahaifin naki na zaga aure ne ya jawo miki ba komai ba. Shiru tayi kanta na kasa bata ce komai ba, dan tasan tana kara tofa abu sai dan buzunta. " Kayi hakuri bazan sake ba. Ta fada cikin sanyin murya. Ya mata kallo cike da kaskanci sannan yayi tsuka ya shiga cikin dakinsa. + A bakin wata babbar Shopping store yayi parking din motar tasa, yana daga ciki ya dauki wayarsa ya kira wata number. " Hello Fauzy ina waje. " Okay ka shigo kawai. Ta fada tara da kashe wayar. Cikin sauri ya kashe wayar tara da bude motar ya fito ya shiga ciki. Gyefe daya inda waiters ke zama suka samu wuri suka zauna, kasan cewar ba ita kadai bace shop keeper a wurin su biyu ne. " Fauzy wurinki nazo ina so muyi wata 'yar magana ce dake. Dr ya fada. Tace: " Toh fa. Ina jinka Dr. " Dan Allah tsakanin ki da Allah ki fadamin inda khairat take. Ya fada tara da tsareta da ido. Cikin mamaki tace: " Ban gane ba. Antin bata tayi ko kuma yaya??? Yace: " No ba bata tayi ba, na nemeta ne ban ganka ba, idan kinsan inda take pls karki boyemin komai, kinsan yadda take a wurina, she's my passion. " A gaskiya rabona da ganin Anty tin next week data saka akayi supplying na kaya tazo muka fitar da prices nasu ban sake jinta ba koda a waya ne, jiya ma ina ta trying number nata baya shiga dan na fada mata shagon na bukatar sababbin kaya, amma wayar switch off. " Ya salam! Ban san yadda zanyi ba fauzy ina missing khairat sosai, dama kece kadai nake tunanin zakisan inda take dan kece yarinyar shagonta. Actually nayi betrayed din kaina da kaina. Magana yake cikin rashin jin dadi. Fauzy ta kurasa da ido cikin rashin fahimta. " Dr kodai wani abune ya faru da Anty??? Yace: " Fauzy iyayena ne sukamin aure suka rabani da khairat, a gaskiya na cutu not even a little bit. " Allah sarki. To me yasa baka ce ita kake so ba?? Fauzy ta fada. " Ba yanda na iya ne. But kina ganin ba wurin iyayenta taje ba a England??? Ya tambayeta. Tace: " Ba mamaki Dr dan kayi hurting dinta da yawa, dan Allah kaje kaga halin da take ciki. Cikin sauri ya kada mata kai. " Insha Allah, I will. Daga nan sukayi sallama ya fito yaja motarsa ya tafi. + Misalin karfe tara da rabi na dare Dr yana airport, dama yana da personal visa nasa da yake zuwa England din. Karfe goma dai- dai suka dauki flight bayan kowa ya hadu. Nana kam bata ma sani ba ko gogan nata yana nan ko baya nan, dan tasan ba dakin nata yake kwana ba, ita kuma bata isa taje ta dubasa ba dan tasan hali. Washe gari da safe har ta gama hada breakfast amma bata ga fitowarsa ba, haka yasa ta zauna taci nata sannan ta mike ta koma daki ta kwanta. Sai kusan misali goma da rabi ta sake fitowa dan wanke plates din abinci, amma cikin mamakinta babu alamar anzo wurin dinning. Ta taba baki. " Dama nasan baci zaiyi ba. Ta karasa ta tattara kayan abinci ta shiga kicin. Har bakin gate din gidan Drop ya ajiye sa tara da biyansa ya fito. Yana zuwa bakin gate daya daga cikin securities din ya taresa, nan ya nuna masa identity card nasa sannan ya bude nasa kofa ya shiga. A guests room aka ajiyesa sai faman rarraba idanu yake yi ko zaiga shigowar khairat dinsa, dan yasan dola zasu san shigowarsa gidan kasancewar haka tsarin gidan yake kuma shi sananne ne. Unexpected yaga General (Mahaifinta) ya shigo cikin falon. " Ya akayi na ganka kai kadai, ina daughter din tawa??? Ya tambayesa cikin matsuwa. Cikin mamaki Dr yace: " Dad ita na biyo fa, bata zo bane??? " 4 wat excess zata zo bayan tana nan tsare a gidanku. Ya fada cikin damuwa. Dr ya tsurasa da ido. " Gidan mu kuma Dad? No khairat bata nan fa, da tana nan of course, zan sani. " Mahaifinka shi ya kirani ya fadamin zaiyi detention nata, na basa hakuri yaki dan yace yayi maka aure amma kaki zama saboda ita. I was amused dana ganka. Jikin Dr yayi sanyi. " But Dad a cikin gidan mu ya ajiyeta, family house namu??? Yace: " Don't actually know. Kaga kenan da ina son fitina yadda ka kawo kanka nan, nina sai nasa a kamamin kai, but kai nawa ne ko baka auri 'yata ba I don't bother. " Pls Dad kayi hakuri, ban san maganan nan ba sai yanzu, nima ita nazo nema. Amma I promise u duk inda take zan fito da ita, zan kawo ta gida. Magana yake cikin fahimta. Yace: " Ina son Khairat ta dawo gida, dan I wonder how I can see my daughter physically. " Karka damu Dad, zan kawo ta. Dr ya fada. Dr bai kwana a kasar ba dan yanzu hankalin sa ya dawo Nigeria inda mutuniyar tasa take. Bayan dan wasu bata lokaci da yayi dan gana da iyayan khairat din daga nan ya bar gidan ya shigo jirgi ya dawo. Cikin dare ya iso bai tsaya ko ina ba sai a Rock View Hotel, anan ya kama daki ya huta gajiya a ciki. Washe gari misalin goma na safe ya fito ya dauki taxi har family house nasu ya ajiye sa. Bai shiga ciki ba ya tsaya a bakin gate ya kira daya daga cikin securities na gidan ya jasa gyefe daya. " Na tabbata duk abin dake faruwa a cikin gidan nan dola kusani idan ta fannin tsaro ne. Ka fadamin akwai wata bakuwar da Dad yasa a tsareta??? Cikin sauri security din ya amsa masa. " No sir, babu kowa. Ya hararesa. " Kar kamin karya dan ba wasa nake ba, speak out d truth. Tana nan ko bata nan??? Shiru yayi baice masa komai ba dan an riga an masu warning akan karsu sake su fada masa komai kan yarinyar. " Gaskiya babu kowa, ban ma sani ba sir. Magana yake kamar mara gaskiya. Haka yasa Dr ya gano maganar nasa ba haka yake ba, cikin sauri ya shakosa cikin uniform din da yake. " Zaka fadamin gaskiya ko sai ka dauka vacation na tsawan lokaci. Kasan dai ina da iko daku a cikin gidan nan. Ya fada cikin buda idanu. Yace: " Okay sir. Tana nan ciki. " A wani bangare take??? Ya fada yayin daya sakar masa rigar. " Tana last building, ita daya ba kowa. Dr yaji dadi sosai amma bai nuna a fuskarsa ba. Ya dafa sojan a kafadarsa da hannu daya cikin nuna afuwa yace: " Sorry 4 my tracing, kar kayi fushi, sannan karka fadawa kowa maganar da mukayi. Ya mika masa canjin dubu goman dake aljihunsa ya amsa yana godiya, shiko ya juya ya wuce.ls / DR SADIQ part 11 DR SADIQ part 11 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:35 Inda yayi parking din motar tasa da 'yar tazara tsakaninsa da gate din gidan nasu. A hankali ya bude motar ya fito tara da duba agogon wayar tasa karfe biyu saura na dare, yanzu kam ya tabbata gaba daya securities din gidan sunyi bacci. Cikin sauri ya mayar da wayar cikin motar sannan ya tako dan karasowa bakin gate din gidan. Yana isowa cikin dabara yaja wata fito da bakinsa, nan daya daga cikin security din daya siya ya toru kofar gate din Dr ya shiga. " Sir kayi a hankali fa, dan an saki karnuka tin karfe daya. Security din ya fada. Dr yace: " No karka damu nasan inda zan shiga. Cikin hanzari ya cire takalman dake kafarsa ya mikawa security din sannan ya mike dan zuwa karshan building da mutuniyar tasa take. Yana isa second gate nan ya samu a bude take kasancewar sunyi alkawari da security din kadda ya rufe gate ko daya har sai sun fito. Cikin dabara da,sando ya shiga ciki dan yasan nan wurin anfi saka masa tsaro sosai, dan anan building din iyayensa suke. Nan kuwa ya hangi karnukan gidan gaba daya a sake suke sai faman zirga- zirgan su suke a wurin, nan tsoro ya kamasa dan kuwa yasan karnuka ba saninsa sukayi ba illah masu tsaransu. Dake zuciyarsa yayi ya labe sai daya fuskanci sun dauki hankalinsu wani gefan, yayi sauri ya shiga cikin yana rabe-rabe da sando dan kar ajiyo tafiyarsa. Haushin karnukan da yaji sun fara masa yasa ya karasa last building din da gudu, ya bude gate ya shiga. Cikin sa'arsa babu kowa a wurin sai dai security light na bangaran a kashe yake. Yana karasawa bakin falon yasa hannu ya murda kofar amma ya jita a rufe. Yana laliba hannunsa ya tabo mukulli a jikin kofar, nan yayi sauri ya bude ta ya shiga. Kamar ya sani ya karasa dakin farko dake wuri tara da tura kofar a hankali ya shiga. Dakin duhu yake dan haka ya laluba hannunsa ya kunna wutar dakin, nan ya ganta kwance ta lullube da bargo. Wani dadi yaji tara da tausayinta daya kamasa. Bai tsaya bata lokaci ba ya karasa bakin gadon ya zauna kusa da ita tara da janye bargon a hankali. Baccinta take yi tukuru dan batasan da wani a kusa da ita ba. Cikin shauki ya shafa gashin kanta, zuciyarsa cike da farin cikin yau gashi ga khairat dinsa. Wata sabuwar sako yaji zuciyarsa ta fara karanto masa, har da yayi shirin biye mata, sai yayi tunanin tabbas a cikin hatsari yake dan haka cikin sauri ya dagota daga baccin. " Dearest tashi, Dr dinki ne. Ya fada yayin daya dagata. Lokaci daya ta farka dama ita bamai nauyin bacci bace. Cikin mamaki ta kallesa inda yake zaune kusa da ita,tara da murza idanuwanta da hannu biyu. " Mafarki nake yi??? Ta tambayesa. Yace: " Ba mafarki bane ki tashi mu tafi, kafin wani ya shigo. " Ina zamuje, me kazoyi a wurina??? Khairat ta fada. " khairat bamu da lokacin wannan maganar yanzu, bari muyi escaping tukunnan, dan we r on a danger. Ya fada tara da mikewa ya dagota. Bata masa musu ba ta bisa yana rike da hannunta cikin hanzari sukafita daga falon. " Dr kar a kamamu fa, kasan ina cikin fitina, karka kara sakani cikin wata. Ta fada yayin da yake kokarin fitar dasu daga gate din wurin. Bai kulata ba sai kara janta da yake yi kamar zasu zura da gudu. Haushin karnukan da suka biyosu yasa khairat ta sake rikicewa, tsoro ya cika ta, dan haka ta dinga kokarin taga ta janye hannunta daga rikon daya mata ta zura a guje amma ta kasa taji ya rike ta gam. Har karnukan suka rakosu bakin gate suka fita amma babu wani sojan daya leko wajan. Suna isa gate din karshe ya amsa takalminsa ya masa godiya suka fito. Suna isa bakin motarsa Khairat ta fisge hannunta. " Duk gwanintar da zakamin Dr bazaka taba birgeni ba a rayuwa, yanzu nikam na tsane ka, bazan taba kara sonka ba, ka koma wurin matarka nima Allah zai bani nawa mijin daya fika. Fuskar Dr cike da mamaki yace: " ina me neman tuba gareki akan abin daya faru, wlh na sake fada miki bana sonta ke nake so, ki yarda dani dan girman Allah. " Ai yarda tsakanina dakai yanzu ta kare, sai dai tsana ta bude shafinta. Wlh Dr kai mayaudari ne na fitar hankali kuma abinda kamin kaima sai anyi maka, idan bai faru dakai ba kuwa zai faru da 'ya'yanka. Ta wuce ta barsa anan wurin tsaye. Maganar data fada masa ita ta tsaya masa a rai, yayi shiru ya kasa motsawa balle ya mata magana. Jikinsa yayi sanyi matuka. " Me yesa khairat ta fadamin wannan maganar. Na tabbata an hadani da ita ne ko kuma dai da gasken ne ta daina sona???? Cikin zuciyarsa yake magana. Ganin tayi nisa sosai kuma gashi cikin dare ne, haka yasa yayi sauri ya buda motarsa yaja dan ya shawo kanta. Cikin sauri ya tare ta da motar tara da budewa ya fito. " Haba Honey me yayi zafi haka?? " Listen Malam, na riga na gama maganar da zanyi dakai, dan haka ka kama hanyarka na kama tawa. Khairat ta fada. " Bazan iya barinki ba khairat dan na tabbata u r my life. Koda zaki dauki wuka ki sokeni da ita bazan barki ba. Ki taho muje gidana ki kwana da sassafe mubar kasar nan. Cikin tsawa tace: " Ba inda zaje Dr! Ko kai maye ne yanda na maka wulakancin nan zakayi zuciya ka barni, amma da yake kayar kare ya dauka. Ta juya zata kara barin wurin. Cikin sauri Dr ya riko hannunta ya jata zai sakata a ciki, tayi kokarin fisgewa amma taga yafi karfinta. Nan takai bakinta tara da gantsa masa cizo da karfi. Radadin da yaji yasa yayi saurin sakar hannun nata, amma ya kara dakewa ya ciccibeta sama ya jefata a gidan gaba tara da rufe kofar. Cikin sauri ya zaga ya bude ya shiga sannan ya kara rufewa. Hannu bibbiyu ta shiga dukansa tana kuka amma shiko a jikinsa ya taka motar suka bar wurin. Ita da kanta ta gaji ta kyalesa har suka isa gidan tana kuka. Yana parker motar bai mata magana ba ya bude ya fita, itama ta bude tabi bayansa. " karka kuskara tsautsayi tajaka kakaini inda zanga matarka, dan wallahi zan mata abin da bakayi tunani ba. Ta fada yayin da suke kokarin shiga cikin falon. Bai kulata ba ya shiga falon taga yana kokarin shiga daki, cikin sauri ta jawo masa rigarsa ta baya. " Magana nake kana kokarin shiga daki, kar kamayar dani mahaukaciya mana. " Honey me kike so nace miki, kin cije ni, kin rufeni da duka, kin fadamin bakaken maganganu me kike so kuma dani. Abinda zan iya ce miki shine, do as u wished. Cikin sauri ta dauke sa da mari. " Macucin banza kawai mugun namiji. Allah sai ya sakamin. Ta fashe da kuka. Ya shafe inda ta maresa, sannan ya matsa dabda ita tara da rungumota jikinsa dan ya rarrasheta. A dai-dai lokacin Nana ta fito daga dakinta dan hayaniyar da taji. " Honey ko kadan bana son ganinki cikin damuwa dan Allah ki yafemin har kwanan gobe ina sonki. Ita ko tayi kwanciyarta kan kirjinsa sai faman kukanta take yana rarrashinta. Ganin haka yasa Nana taji wata bakar kishi ta rikota, ganin basu san ta fito ba yasa ta juya da sauri ta koma dakinta tana neman makamin da zata dauka. Cikin sauri ta wawuro kwalban turaran daki daga cikin show glass dinta, ta fito a guje ta nufo falon. Ina mai bada hakuri akan jinkirin da muke samu kwanan hakan ya farune sanadiyyan watan da muke ciki me alfarma na ibada, kuma muna sanardaku daga ranan farko na goman karshe zamu dakatar da wanan labarin namu sakamakon zabarinda zamu shiga akan dare mai alfarma. Mungode.SADIQ novels / DR SADIQ part 12 DR SADIQ part 12 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:36 Cikin sauri ya zaga ya bude ya shiga sannan ya kara rufewa. Hannu bibbiyu ta shiga dukansa tana kuka amma shiko a jikinsa ya taka motar suka bar wurin. Ita da kanta ta gaji ta kyalesa har suka isa gidan tana kuka. Yana parker motar bai mata magana ba ya bude ya fita, itama ta bude tabi bayansa. " karka kuskara tsautsayi tajaka kakaini inda zanga matarka, dan wallahi zan mata abin da bakayi tunani ba. Ta fada yayin da suke kokarin shiga cikin falon. Bai kulata ba ya shiga falon taga yana kokarin shiga daki, cikin sauri ta jawo masa rigarsa ta baya. " Magana nake kana kokarin shiga daki, kar kamayar dani mahaukaciya mana. " Honey me kike so nace miki, kin cije ni, kin rufeni da duka, kin fadamin bakaken maganganu me kike so kuma dani. Abinda zan iya ce miki shine, do as u wished. Cikin sauri ta dauke sa da mari. " Macucin banza kawai mugun namiji. Allah sai ya sakamin. Ta fashe da kuka. Ya shafe inda ta maresa, sannan ya matsa dabda ita tara da rungumota jikinsa dan ya rarrasheta. A dai-dai lokacin Nana ta fito daga dakinta dan hayaniyar da taji. " Honey ko kadan bana son ganinki cikin damuwa dan Allah ki yafemin har kwanan gobe ina sonki. Ita ko tayi kwanciyarta kan kirjinsa sai faman kukanta take yana rarrashinta. Ganin haka yasa Nana taji wata bakar kishi ta rikota, ganin basu san ta fito ba yasa ta juya da sauri ta koma dakinta tana neman makamin da zata dauka. Cikin sauri ta wawuro kwalban turaran daki daga cikin show glass dinta, ta fito a guje ta nufo falon khairat na ganinta aiko tace da wa anka hadani inba dakeba yauwa daman nayi alkawarin sai na hallakaki kucakar banza ki rasa Wanda zaki aura sai mijinda zan aura, yau sai kin yabama aya zakinta don yau sainaga Wanda zai rabamu a gidanan Dr, na kokarin riketa haba Honey! mene haka? Ba nace ki daina kulataba ai wanan bama sa'arki bace. Kaga nidai Ka kyaleni in dauka ma kaina 'yanci tunda Ka kasa rabuwa da ita, ta fada yayinda take kokarin nufo Nana. Rufema mutane baki ke har wani 'yanci ne gareki da har kikebin mazan mutane? Nana ce ta fada tareda zaro kwalban da ta boye a bayanta, Dr, na ganin haka yayi wuf ya tare gabanta dominkuwa yasan Nana zata iya aikatawa don tun sanda yake da ita baitaba ganin tayi sa'insa da wani ba. Aiko ji kake taass! Sai a kan Dr, ya fadi kasa some jini ya malale ko'ina kai zakace wani katon sa aka yanka. khairat na ganin hakan ta sake yin kukan kura tayi cikin Nana wallahi sai na hallakaki kaman yadda kika hallakashi ta fada yayinda ta danne Nana a kan kushin ji kake chass! Ta cakawa Nana fasashen kwalban da ke hanun Nana. Nana ta fadi kasa tareda shure-shure tana kakarin fitan rai tareda kalman shahada khairat na ganin hakan ta kwatsa ihu tareda aza hannu bisa kai wallahi bani na kashetaba ta sheka da gudu tayi waje sanan ta dawo ta zauna sai faman numfashi takeyi sama-sama. karar kiran wayan Dr, da tajine yasa tayi firgit ta tashi tana zarar idanu kai zakace patience Jonathan ce rananrda akayi sanarwan sun fadi zabe, lolx domin Kuwa tasan ba kowa ke kiran Dr, ba illa mahaifinshi waton general, tayi kaman ta daga wayar kuma tayi tunanin tabbas idan general ya sake kamata wanan karon tau sai buzunta, wata zuciya tace ki gudu kawai. Har ta fita kuma ta dawo ta dauki makullin motan Dr, kamin kace kobo har tabar gidan kai da ganin yadda take gudu da mota kai zakace zata tashi samane. SADIQ novels / DR SADIQ part 13 DR SADIQ part 13 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:39 Yanzun kam hankalin khairat yayi matukan tashi domin ko Sai faman tuki takeyi tana sake-sake cikin zuciyanta Gashi tun da ta fito kowa bata gamu dashiba, ga titi falau! ba kowa kai zakace kufaine gabanta sai 'dar'dar kawai yakeyi ta rasa inda zata nufa. Chan sai wata zuciya tace ki gudu Kawai ki bar kasanan tau amman ina zaki samu visa a cikin darenan? Ji kake kiii! Tayi wani dogon chin burki sai makyarkyata kawwai takeyi yau kam asirina ya tonu. Ita duk a tunaninta yan sanda ne, amman saidai kash! Domin Kuwa abinda ta gani ya Kara sa saida hantan cikinta ya kada. Wasu kartine masu jajayen idanu kai zakace garwashin wutane. Suka daka mata tsawa oya! Oya! Come out and lying down on d ground, suka kwace Jakar da ke hanunta sanan suka kwantarda ita a kasa, idan kika sake yin ihu zamu kasheki, bindigarda ta gani hanunsu ya tabbatarmata cewa wayanan kasurguman yan fashine komai zasu iya aikatawa a kanta idan bata basu hadin kai Ba. bamu makullin motarki, hanunta na karkarwa ta mikamusu. babba daga cikinsu ya fizge sanan ya shureta karuwar banza ina kika fito cikin darenan? Khairat dai batace komaiba don tasan shiru yafimata abinda zata furta. da ya kwasheta mari saida taga wutan lahira ta fadi kasa war-was, Sukayi ihu sai kai Oga. khairat na ganin sun fice ta runtuma aguje sai faman gudu takeyi batamasan inda ta dosa ba har takai kusa da wata korama ta fadi. Har kusan karfe 8:OO na safe khairat batamasan inda takeba, surutun da taji anayine kaman a mafarki yasa ta Dan bude idanunta, ita duk a tunaninta kwance take akan gadonta duk abinda ya faru jiya mafarkine. Ta murza idanunta amman taga lallai ba mafarkibane domin ko ba abinda take gani zagaye da ita sai ciyayi, tayi firgit ta tashi, ta rasa inda take ta kara bude idonta amman ta hango yan matanan su biyu dauke da tulu zasuje debo Ruwa. ta matsa inda suke domin koda zata Dan samu abinda zata sakama cikinta. suna ganinta har sunyi batun runtumawa aguje amman ina har tasha gabansu, haba bayin Allah nifa yar adamce kamarku meyasa kuke guduna? Suna diban kafanta sukaga (cover shoes) aiko suka yada tulunansu sukace kafa me naci ban bakiba? Khairat na ganin haka itama ta dafamusu tunaninta mutanenanne na jiya suka sake biyota. Aiko suna shigowa gari duk Wanda ya ganeso kamin kace kobo shima ya shige yar bukkansa ya rufe garidai duk ya kicime khairat ko hankalinta sai Kara tashi yakeyi ganin yadda duk mutanen garinan sun tsorota da ita. Hakan yasa ta samu wata yar bishiya tayi zamanta ga yinwa na damunta gaya kuma batada komai, jakarta ma barayi sun kwace. Uwa uba kuma batama san inda takeba balle tayi tunanin komawa gida domin Kuwa yanzun ita duk burinta da fatan da takeyi shine ta koma gida koda kuwa za a yankemata hukuncin laifinda ta aikatane ta dauka domin Kuwa tasan mahaifinta zai iya tsayamata. Tana cikin wanan tunanin ji kawai tayi anyi sallama bayanta tayi wuf! ta tashi, Don ALLAH kuyi hakuri duk abinda ke hanuna na baku wallahi ba komai sai wanan danyen mangoron, tana juyawa don ta nunamusu sai taga wani Dan saurayi kyakyawa son kowa kin Wanda ya rasa sanye da farar jallabiya kai da ka ganshi zakace balaraben zariyane lolx. Haba malama me kikeyi a wanan gindin bishiyar tun da safe haka? Dukdadai daga ganinki alamomi sun nuna ke bakuwace, amman khairat bata cemishi uppan ba. Idan ba zaki damuba ki biyoni muje gidanmu domin Kuwa mutanen garinan zasu iya illataki, khairat tayi wuf! Ta sake mikewa illatani kuma Amman don me? Ki biyoni kawai wannan ba lokacin tambayoyi bane. A gefe daya kuma tun lokacinda general yaji Dr sadiq bai daga wayarsaba ya kira Ummi itama haka yasan lallai wani abu ya faru. Hajiya na ganishi sanye da kaki rai bace, gasun baki a murtuke tasan ba Lafiya. Guards dinshi na ganin ya fito duk suka 'kame ''morning sir'' ko karba musu baiyiba yace where is sajent Jona? Yace I am here sir, ka tabbatarda yarinyarnan bataje ko'inaba. I hope u are getting me. Ya dan donarda kai, I am sorry sir, yarinyanan fa ta gudu. What!!!! ta me? What!!! Ya sake fada a karo na biyu, She escape and u are here telling me rubbish? I gave 24 hours to make sure she is in ur custody idan kuma tayi tirjiya ku harbeta. make sure u brought her died or alive, is an order. Magana yakeyi cikin bacin rai. Oya kukuma ku biyoni haka suka kama hanya hankali tashe kai zakace dajin sanbisa zasuDR SADIQ novels / DR SADIQ part 14 DR SADIQ part 14 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:41 Hakika Halinda suka tsinci Dr da kuma Nana yayi matukar tadamusu hankali, domin Kuwa duk a tunaninsa duk sun mutu. motsawar yan yatsun da Nana tayi shi yaja hankalin kowa daga cikinsu. hakan yasa aka daukesu zuwa asibiti. Yanzun kam duk inda zuciyar general take tayi matukan baci don ji yake da ya gamu da khairat sai buzunta. Fitowan Dr Aishat yasa kowa yayi chaa! Akanta kaman za a hadiyeta, amman saidai yanayinda suka ganta yasa jikin kowa yayi sanyi. Gaskiya patient dinku na cikin mawuyacin hali domin Kuwa kwakwalwarsa ta samu tabuwa hakan zaisa ya kasance a cikin wanan halin har na Dan wani lokaci. Amma gaskiya ita dayan ta samu sauki sosai saidai tana Dan bukatan hutu Nan da zuwa awa hudu zaku iya shiga ku ganta. Mungode sosai DR Aishat, hajiya ta fada yayinda take kokarin binta a baya. Haba bakomai fatanmudai Allah ya basu lafiya. A gefe daya kuma khairat hankalinta ya fara kwantawa da usamat domin Kuwa ganinsa takeyi kaman Dr dinta. saidai kash! Kaddara ta riga fata, Dominkuwa iyayensa sun dade da nema masa matarda Zai aura wadda diyar kanin baffansane. Nan da sati biyu za'a sha biki. Dukda dai ba sonta yakeyiba ganin cewa shi Dan bokone a birni ya tashi yaya zaiyi ya auri yar kauye wadda komai bata saniba a bangaren rayuwar zamani. Kasancewar usama yarone mai ladabi yasa dole ya hakura da zabin iyayensa Amman badon yanasoba. Zaune ta cimmasa yana karatun Qur'ani bayan ta samu wuri ta zauna, ta kuresa da kallo kai zakace bakanone ya shigo birnin zazzau. Lolx. bata cemai ko uffan ba. Bayan ya gama ta daga hannu sukayi Adu'a sanan ya dago kai ya'ce kaunana kenan Yau kuma ko sallama babu. Tayi murmushi mhhm! Sanan tace yayana kenan ai nayi sallama bakadaijibane. Dukda yasan batayiba Amman ya kyaleta a hakan. Yayana wai niko in tambayeka? Hmmm! 'yan birni kenan niko wace irin tambayace wanan? Usama ya fada yayinda yake kokarin tsureta da idanu. Ta Dan donarda kai sanan ta, ce wai Niko yaya yaushe zakayi aurene naga duk yawancin sa'aninka a garinan sunyi aure banda kai? Wanan ita kadaice tambayarki? Tau kada ki damu kina garinan zanyi aure domin Kuwa bazai wuce nan da sati biyu ba, kinga zakiga yadda muke bikin aure ba irin taku ta yan birni ba. Ya fada yayinda yake kokarin tashi tsaye. Ina zaka kuma yaya ai tambayar tawa bata kareba ko Ka gaji Dani ne. Haba! Ai bako rahamane ta yaya zan gaji da bakona? Yaya injindai ba yar kauyenan zaka auraba? Ta fada yayinda take sake tsuresa da ido karo na biyu. Hmmm! Khairat kenan yanzun idan na cemiki 'yar birni zan aura zaki yarda Dani? Haba mezai hana Dan saurayi kyakyawa irinka. Hahaha! Yayi wata 'yar bazawaran dariya 'yan birni akwaiku da zolayan 'yan kauye nidai bara naje ance ummah' na nemana idan na dawo ma Ida maganan. Wanan shine karo na farko da khairat ta fitarda maitanta a fili kan usama. Kwanan khairat hudu a kauyen tugga Amman shakuwan da usamat da khairat sukayi tamkar sun shekara goma tare. Hakan yasa iyayen usamat suka fara tunanin rabasu don kada wankin hula ya kaisu dare ganin auren usamat ya gabato. Ba yadda basuyi juyin duniyaba Amman khairat ta dage akan batasan komai akan iyayentaba ganin za a iya rabata da usamat. Kabir abokin usamat ne tun suna yara Amman kasancewar iyayensa a birni suke aiki yasa a can ya tashi. Saidai sukanzo duk sallah. wanan karonma auren usamat ya kawoshi domin Kuwa sune manyan abokan ango. Ganinda kabir ya yima khairat a gidan su usamat yayi matukar bashi mamaki kasancewar ya Santa, dominkuwa makwabcin su DR sadiq ne amman saidai ita bata sanshiba hakan yasa ko a jikinta. Bayan sun bar gidan ne kabir ke cemasa Amman gaskiya Yau naga wani ikon Allah a gidanku. Usamat yayi dariya yace nasan ana haka abokina ai daga ganin yadda Ka tashi fadawa cikin randa akan kallon khairat nasan Ka kamu. Wai Na kamu rufamin asiri indai wanan yarinyan sunanta khairat tau gaskiya kun tabka babban kuskure domin Kuwa itace tayi yinkuri kashe saurayinta da matarsa yanzun haka suna asibiti. Usamat na zaune baisan lokacinda yayi buzut! Ya mike tsayeba. Kai! Abokina kodai mai kama da itace? Tabbas itace idan kuma kayi gardama mu koma Ka tambayeta ko tasan DR sadiq. Hakika wanan labarin ya katsema usamat farin cikin da yake ciki domin Kuwa kamin duk ya tabbatarda khairat ce ta aikata wancan aika- aikan duk yaji ya tsaneta./ DR SADIQ novels / DR SADIQ part 15 DR SADIQ part 15 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Dec 2016 - 21:42 Haka usamat ya wuni sakaka tamkar wanda bayada lakka a jikinsa tun iyayensa basu gane halinda yake cikiba har yakaiga mahaifiyarsa ta fahimci halinda yake ciki, saidai ba yadda batayi juyin duniyaba Amman yaki ya fada sai karyar bayada lafiya yakeyi. Yadda yaga dare haka yaga rana domin Kuwa kwana yayi yana tambayar Kansa waima idan khairat ce ta aikata wancan danyen aiki menene tasa a ciki? Tau Amman idan Ka koreta yaya zakayi da shakuwar da ke tsakaninku? Gaya kuma tace batasan kowaba anya wanan maganar nata gaskiyace? Itafa ba karamar yarinyabace, Duk wayanan tambayoyin usamat ne ke yiwa zuciyarsa, amman ya kasa samun amsoshinsu. hakan yasa kawai ya yanke shawaran gobe da safe kawai ya tunkareta da wanan maganan. Washegari usamat ya tashi bayan yaje masallaci yayi sallah kaman yadda ya saba ya dawo ya shiga dakin mahaifansa domin ya gaidasu kaman yadda ya saba. Bayan ya samu wuri ya zauna ya Dan donarda Kansa kasa cikin sanyayyar murya ya, ce amincin Allah ya tabbata a gareku ya mahaifana. Da fatan kun tashi lafiya? Suka amsa masa, har yana batun tashi Amman mahaifinsa yace yauwa mai sunan baba daman ko ina nemanka domin ko baka zoba zan aika a nemoka. Usamat na jin haka saida yaji gabansa yayi dakan uku-uku. Waa! ni abba? Halan bayan kai akwai wanda yake cema mai sunan baba gdanan? Mahaifiyarsa ce ta fada. Usamat ya Dan shafa Kansa sanan ya koma ya zauna yayi shiru. wai yaushe wanan yarinyar zata bar gidanan? Usamat ya dan donar da Kansa kasa sanan ya,ce cewa tayi tanaso taga yadda ake bikin aure a garinan inaga bayan aurena zata tafi. Sallamar da kabir yayi shi ya katse maganar da usamat keyi don yasan kabir akwai surutu kaman Suda Zai iya shiga maganar har karshe ya bijiro da maganar jiya. Bayan ya gaida mahaifan usamat sanan ya samu wuri ya zauna sanan yace usamat wai Ka fadama su dad batun maganarnan ta jiya? Wacce magana kenan? Usamat yace a'a bakomai Abba. Kai na tambaya? Kabir fadamin meke faruwane? Usamat nata kokarin kyallamar ido kar ya fada Amma ina zanzari kawai yakeyi. Abba yarinyarnan da na gani gidanan gaskiya indai itace khairat tau lallai itace tayi yinkuri kashe saurayinta da matarsa yanzun haka suna kwance a asibiti. Karar faduwar akushinda ke hanun khairat yasa kowa saida ya waiga. Khairat ce tsaye kwalla na fita daga idanunta, ta gurfana gaban su. Don Allah ku gafarceni tabbas duk abinda wanan bawan Allah ya fada gaskiyane. Ba a son raina na boyemuku halinda yasa na gujema kaddarar da take bibiyataba sai don ba yadda zanyi in iya kubutarda kaina akan wanan laifinda ake zargina. Hakika ni na aikata Amman wallahi ba a son rainabane. Ta yaya zan kashe abinda rayuwata ta ginu a Kansa? Abba ku yarda Dani wallahi kaddarace da rudin shaidan Amman wallahi yanzun na yarda, dan Adam baya iya kubucema duk wani layin kaddara da mahaliccinsa ya shatamai. Usamat Ka gafarceni. Ka yarda Dani amman ban zamo yadda kake tunaninaba ina mai rokonka gafara Ka yafeni. Mahaifiyar usamat ce ta kama hanun khaira tana lallashinta kada ki damu duk dan Adam ajizini mudai mun yafeki, saidai yafiyarmu ba zata taba yimiki amfaniba har sai kin roki wayanda kika jefa cikin halin 'ka'ka nikayi. Wanan tabbas haka yake Allah ya yafemu ga baki daya. Mahaifin usamat ne ya fada. Abba nima ina rokonku da ku yafemin son zuciyane yasa naso inki bin umurnin da kuka bani, tabbas Yau na yarda da Karin maganan da hausawa suke cewa (abinda babba ya hango Yaro ko ya hau jirgin Samane bazai hangoshiba) Kasancewar kabir shi yasan asibitin da aka kwantarda su Dr sadiq da matarsa ummi yasa shi ya yima khairat, usamat da kuma mahaifinsa jagora. Isarsu asibitin keda wuya inda suka cimma jami'an tsaro da kuma 'yan jarida sunyi dandazo kasancewar labarin yaja hankalin mutane da dama harma wajen kasanan. Sakamakon an baza hotunan khairat a ko'ina yasa 'yan jarida na ganinta sukayi chaa! A kanta. Amman tuni su sajent jonah sukayi dirar mikiya akanta. Su usamat da babansa suna magana Amman ina don ko 'kala basu ce musuba dole suka hakura suka ja baya domin sunsan wurin bindiga wane 'kyastu. Da wani kurtu ya yimata wani mazga sai gata a kasa some, general na ganinsu ya,ce well done. Idan ta farka ku kaimin ita gida ku tsare min ta don jiya munyi waya da mahaifinta gobe Zai zo ya wuce da ita turai kowa ya huta. Haka suka kwarara mata ruwan sanyi a jiki tana bude ido Dr sadiq ta fara arba dashi. Amman saidai kash!! Domin ko baya iya gane kowa sanadiyyan matsalar kwakwalwar da ya samu, tasa hatta mahaifansa sai da baya ya dan fara ganesu. Itama ummi ta fara jin sauqi domin Kuwa da ita ake faman jinyan Dr. Yanzun kam ba wadda Dr sadiq ya shaku da ita bayan ummi. Bayan sati biyu aka sallamo su ummi da Dr, dinta, iyayensu murna har kunne domin Kuwa sunji dadin halinda Dr, ya shiga don Kuwa hakan shi ya ceto rayuwan shi daga halin 'ka'ka nikayi da khairat ta jefashi. Basufi shekaraba ummi ta haifamasa diya tagwaye, kai da Ka gansu ba sai an fadamakaba kasan tabbas diyan Dr sadiq domin shi suka biyo. adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *