Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Thursday, May 25, 2017

Idan zuciya ta gyaru

adsense here

Idan zuciya ta gyaru 1-01 Posted by ANaM Dorayi on 07:28 AM, 27-Jan-16 Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU ______________Na ______Fauziyya D Sulaima 19/81992. "Chalo! Chalo! Chalo!" Zazzakar muryar hatsabibiyar yarinyar ta fadi, ko ba'ayi bayani ba kasan abinda kalmar chalo take nufi, wato tsokanar fada ne da 'yan wani layi ke yiwa wani layin, ko 'yan wata unguwa zuwa wata unguwar. Jama'ar dake gefen hanya masu saida rake zuwa goba, da yalo da doya suka fara hada kayansu, daya daga cikin su ke fadin, "Kowa ya hada kayansa don shegiyar yarinyar nan tun da ta ambaci wannan kalmar ta chalo, to kuwa wanda yayi sakaci zai yi a..." maganarsa ta tsaya tsak dai-dai lokacin da ya hango zugarsu sun nufo su da gudu, sun biyo wasu, ya suri farantinsa wanda aci bal-bal ke tsakiya na kifi, suma 'yan uwansa suka rufa masa baya kowa na neman inda zai adana kayansa. "Chalo! Chalo! Chalo!!!" Muryar zugar yaran dake biye da Abu suka cigaba da fadi suna biye da 'yan uwansu wadanda suka biyo, sukuwa yaran da aka biyo sai kuma kara gudu suke yi, domin kada a badesu da barkonon tsohuwar da su Abu ke wulwulawa. Toka ce ake hadata da citta da barkono a dake sai a kulle ta a leda a sanya dutse a tsakiya a sanya zare a dinga wulwula ta, idan aka cillata daga nesa sai ta fashe kamar an cillah tiyagas (barkonon tsohuwa), duk mutumin da ke harabar gurin sai yayi tari ko ya shide, idan kuwa akaci karo da mai cutar (ASMA) kuwa sai ta tashi. "A cilla- A cilla." Muryar Abu ta kuma futowa tana baiwa abokan ta umurni kenan, dan ganin yaran da suka biyo sunyi musu nisa, ai kuwa babu bata lokaci suka hau cillah kullinan tokar dake hannun nasu ji kake tush! tush! tush! Tana fashewa a tsakiyar yaran dake neman tsira daga farmakin su Abu, wadanda Allah ya taimaka sun tsere wadanda kuma keda rabon shan wuya tokar ta fashe a tsakiyar su don haka suka fara tari da atishawa, hatta mutanen dake makota dasu suma sun hau atishawa, balle maza dake zaune a kofar gidaje ana hira duk suma sun hau atishawa. Su kuwa su Abu dariya suka sanya gami da ihu suna fadin "Eye! Eye! Eye! Munci gari ba namu ba, munci gari ba namu ba- munci gari ba namu ba, munzo gidansu mun cisu" Wani mai kanti dake kokarin zuba kananzir dai-dai lokacin da abun ya fashe, ya shide kalanzir din ya zube a kasa ya hasala don haka ya shiga shagonshi da sauri yana atishawa ya dauko dorina yayi kansu yana fadin "Shegun yara masu kama da iblisai ba a sati guda baku bada mana wannan jarabar ba, wallahi yau duk wanda na kama sai na fasa masa jikinsa da dorinar nan" Yayi kansu da gudu, Abu ta fara hangoshi don haka ta kuma fasa ihu tana fadin "Kowa yayi ta kansa! Nima nayi ta kaina, kowa ya guje dai, nima na guje dai, kowa yayi ta kansa." Ko batayi bayani ba sun san abunda take nufi, wato wani ya taho zai doke su don haka kowa ya gudu, wai ai kuwa sai suka kama gudu mai kantin nan ya bisu da wasu samari biyu, da suma ke cin abinci aka bude su su da abincin da kura, basuyi nasarar kama ko daya ba domin yaran sun fisu gudu tamkar barewu don daman sun san za'a biyo su. Don sun saba duk randa aka yi biki ko suna a gidan wasu aka kai musu cingam din fati akube-kube sai anyi fada, don haka iyaye da yawa ke hana 'ya'yansu zuwa akube-kube (fati), yauma haka dince ta faru domin 'yan layinsu Abu (Hatsabibiya ce) ta gayyaci akube-kube (fati) tofa shine wani dan bayan layin nasu ya warcewa 'yar layin.. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 yauma haka dince ta faru domin 'yar layinsu Abu (hatsabibiya ce) ta gayyaci akube-kube (fati) tofa shine wani dan bayan layin nasu ya warcewa 'yar layin su kwanonta na akube-kube lokacin da suke tsaka da rera wakar akube-kube sai walo, munje mun dawo sai walo, sannunku da zuwa sai walo, ga kwanan fati sai walo. Tofa shine Abu tace a futo da kwanon suka kiya shine fa fada ya harke ana ta karawa sannan aka bada oda a dauko bom, shine fa aka biyo 'yan bayan layi. A bakin wata makarantar boko suka dinga zubewa suna haki don sun san sun tserewa wadanda suka biyo su. Sai tillikar dariya sukeyi suna mai da yanda akayi. Abu ta fito da kifi a hannunta soyayye tace, banzaye nifa mai kifin nan da yake gudu sai dana suri kifi daya wanda ya fado, nan fa kowa yayi karaf yace raba dai-dai (wato wata sarace ake kullawa idan kuka kulla raba dai-dai to da kaga mutum yana cin abu idan ka riga shi fadin raba dai-dai to sai ya raba biyu ya baka idan shima yaga kana ci yace maka haka to sai ka bashi kaima, idan kuma mai cin abin ne ya riga fadin bazai bada ba). Abu ta sha kunu tace "Dallacan wa zan baiwa wa zan hana" Ta bare ta cire kayar ta lunkuma a bakinta tana muzurai, kowa ya tsaya yana kallonta don dai ita masifaffiyace tsoronta ake ji, wani yaro ne a cikinsu yayi karfin hali yace "Gaskiya mu kwance ke Abun nan." Ya mika mata hannu "Idan kece kika ga mutum yana ci kika ce raba dai-dai idan bai baki ba warta kike yi, amma idan kece sai kiki badawa." Ta cire dankwalinta taci dammara dashi tace "Anyi din, duk wanda ya isa ya kwata wallahi" Habu yace "Banza ai ba tsoronki ake ji ba, daga yau mun kwance nima." "La-la-la, ni kake zagi wallahi ba zan yadda ba." Ta danki kasa a hannu biyu ta matsa gabansa tace "Gata tsiya gata arziki." Ya tankwabe ta tsiyar ai kuwa sai ta rarumeshi, nan fa dambe ya kaure sauran yaran suka rude da ihu eyeh-eyeh-eyeh, sannu suna musu wata waka, "Ku chasu arna ku chasu, ku chasu ba mai raba ku, wanda ya raba su shi yayi barna, kai ku chasu arna ku chasu, ku chasu ba mai rabaku." Su kuma tamkar ana kara zugasu sai dambe suke yi, da yake Abu 'yar dama-dama ce mai kiba gata da karfi da karfin zuciya ta daga Habu ta naka shi da kasa, aka kuma rudewa da ihu da kyar aka janye ta daga kanshi tana fadin "Wallahi da kun barni yau da sai na chas-chas karashi." Shi kuwa ihun da ake masa ya sanya ya fashe da kuka yayi hanyar gida, suma saura suka bishi ana masa ihu, ita kuma Abu sai kuma masifa takeyi tana tafa hannuwa tana fadin "wallahi mutum yaje ya fada a gidansu wanshi yazo ya tabani gobe nima na zane shi." Sauran 'yan fadan ta suna ta zugata tana dariya, a haka suka isa kowa ya nufi gidansu, Abu tace "Bari naje na dauko gyada ta na kasa wallahi kuma naji yaro ya zageni ya sani." Ta shiga gidansu har lokacin da damararta, Babarta dake zaune wacce asalin sunanta Salamatu ne suke ce mata Sala tace "Yauwa 'yar albarka yanzu nake tunaninki tun da kuka tafi akube-kube baku dawo ba." Ta fashe da dariya tace yau na gaya miki Sala wallahi na chas kara yaron nan Habu, daman ya raina ni har kuka na saka shi wallahi ya tafi gidansu yana ta kuka. Sala ta fashe da dariya tace "Yata giwar mata, wanda ya tabaki ya tabo ramin zuma, bana son sanya ki cigaba da chasa duk wanda ya kawo miki wargi ni na saka ki." Tayi dariya tana gyara kashin gyadar tata tace "Ta nawa ce Sala?" Tayi dariya tace "Haba maitsada (Sunan da take kiranta dashi kenan) ai ke ba sai an kirga miki ba, ke ai me kan arziki ce yanzu zaki dawo nasan kudina ba zasu bata ba sai dai ma su karu, dauki kawai kije da dai Karimatu ce mai kan kwantai (kanwar Abu ce)" Abu tayi dariya gami da daukar farantin wanda aci bal-bal ke tsakiyarsa tayi waje da kujerar zamanta. Can hanyar 'yar kasuwa ta nufa inda masu lemo da agwaluma da rake ke saidawa, tun da ta fito aka karbi kujerar wata kawarta Laraba, suka tafi suna tafe suna hirarsu akan fadan da suka yi da Habu, da kuma chalon su. Sanda ta isa bakin 'yar kasuwa ta ajiye farantin ta, samari suka fara zagayeta kowa ya dauki gwangwani guda yana ci ana hira, rabin hirar duk batsa ce, amma da yake Abu ta saba jin irin wannan hirar sam bata damu ba, sai dai ta sheke da dariya tace shege wane, can wani Rosi yace "Ke ai wallahi Abu har yanzu baki waye ba, ki duba ko kwana bakiyi a waje kullum kina gida." Ta mike tsaye tace "Kan Uban can, har zaka ce ban waye ba, don Allah dubeka Rosi din nan kaifa wallahi tsami ne, don dai yayana jarababbe ne wallahi da nima kwana zan dinga yi kamar Laraba ko yaya kikace kawas?" Ta bawa Laraba hannu suka tafa Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 . Mudi Niga yace "A'a ba wani Laraba taso muje muyi zancen mu bayan makaranta kada 'yan sa ido su ganmu." Abu ta tabe baki tace "Wallahi nima don jarababben yayana ya saka min ido ne, yanzu da an ganni za'a gaya masa yaci ubana, wallahi da nima acan zan dinga zancen, amma zan yi maganinsa." Su Laraba dai suka mike suka tafi ita kuma suka cigaba da hira da su Rosi. Karfe goma da rabi sannan ta dauko kayan tallarta tana ta mita a fili "Banza su Rosi din nan shiyasa bana sakar musu fuska, da Kwage ne ko Damisa ai da tuni sunyi mini juye mtss!" Taja tsaki, yanzu da kwantai zan koma gida? bari dai na biya gurin dan Oga dan nasan shi dole ne kila ya siye yanzu. Ta nufi chemist din nasa da fitilar kwai a bisa tebur, yana zaune a bisa kujera mai kama da tsohon soja, babu ko sallama ta bankade dan yalolon farin yadin dake kofar da sunan labule ta shiga tana fadin dan oga kana nan baka tashi ba? Ya mike cike da murna yace Wow! Habu yanzu kana rena wallahi ina son ka da gani (cikin gurbatacciyar muryarsa yake mata magana) ita kuwa ta ajiye gyadar bisa wannan tsohon tebur din ta hure aci bal- bal din tace "Daman zan biyo yanzu ga gyadar zaka siya duka ko?" Ya matsa jikinta yana cewa "Habu Habu, wallahi kana da cho, ina ta sonka da yawa, amman zaka kwana anan ko?" Ta zaro ido waje tace "Kaifa baka da hankali wani lokacin, idan na kwana a gurin ka nace me a gida....." Ya jawo ta jikinsa yana mata abinda ya saba duk da ba gamsuwa yake yi ba, domin dai lalubeta yakeyi, don taki amince masa dari bisa dari sai dai yayi abinda ya samu (Allah ya shirya, jama'a ku duba diya mace ta futa har zuwa wannan lokacin uwarta bata neme ta ba, tur da irin wannan Uwa). . …Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Can tace "Malam na gaji zan tafi kada jarababban can ya biyo sahuna don ma nasan Sala zata kareni sallameni na tafi." Ya mike yana gyara riga yace "Habu-Habu, wallahi yarinyar nan baka da cho kina yawo da akalina, amman zan rama ne." Tayi dariya tana fadin "Dan oga kenan." Ya miko mata Nairori har na Naira ashirin tace "La-la nagode." Ta sunkuci farantin gyadar ta fuce da sauri tana fadin "Duka gyadar ma ta naira ashirin ce amman ya bani Naira ashirin" Shi kuwa sai kiran sunanta yake yana dariya har ta kulewa ganinsa.(Wallahi sai mun zamo masu taka tsantsan da irin kabilun nan da suke mu;amala da yaranmu)….Sanda ta isa gida an turo kofar da tirmi ba'a kulle ba, don haka ta tura a hankali ta shiga da kullin namanta na naira daya da ta siyo don kudin dake hannunta naira ashirin da shida ne ga kuma sauran gyada. Ta shiga dakin Sala ta taddata abisa leda tana ta sharara bacci kamar matacciya (Ku duba irin wannan Rashin tunani, ki tura diyarki talla tayi dare amma ko damuwa bakiyi ba, bacci ma kikeyi hankalinki kwance!!) A hankali ta dinga taba ta tana fadin "Sala! Sala! Sala! Na dawo." Sala ta mike tana magagin har ta wartsake tace "Diyar arziki kin saida ko?" Abu tayi hamma babu ko rufe baki balle salati, sai wani nishi da tayi hmmmammman har bakin ya rufe da kanshi, sannan tace na dawo ga kudin nan da sauran gyadar dai, Sala ta sha kunu tace "Haba Abu, kince fa a kunga-kunga har ta kare...." Tayi shiru da zancen da taga ruwan Nairori a gabanta, ta debo su da sauri tana kirgawa sai ga naira ashirin har da Uku. Ta washe baki tana fadin "Diyar albarka lallai kice samuwa kika yi daga sama, wannan fa shine riba biyu ga kudi ga sauran gyada, na baiwa Shehu da safe ya karasata idan kin tafi makaranta, kin siyo naman? Domin mai nema idan baya ci wata rana shi za'a tafi nemowa." Abu ta nuna mata ledar naman ba tare da tace komai ba ta mike, Sala tace "Gwara dai aje a huta don ai kin gaji na sani, sai da safe mai tsada." Tace to Allah ya kaimu. Ta fuce a tsakar gida taci karo da Sadiku yayanta ya shigo yana huci, ke don Ubanki ina kika biya naje bakin 'yar kasuwa ban ganki ba kuma ban dade da barin gidan nan ba? Ta murguda baki gami da harararsa tace "To ina ruwanka dani eyeh malam...." "Ke don ubanki rashin kunya zakiyi mini? To yau idan baki gaya mini inda kikaje ba wallahi sai na faffasa miki jikinki." Yayi kanta ai kuwa suka kwasa da gudu tayi dakin Sala wacce sukayi karo a bakin kofa. Cikin hargowa da bala'i Sala tace "Malam meye haka zaka biyo mini diya da gudu salon taje ta karye ka cuceni? Wallahi yaron nan ka futa daga idona na rufe kaji ko? Kai waye ne da zaka matsa mata eye? Ko kai ne uwarta daka haifar mani ko kuma kai ne Ubanta eye?" Cikin hargowa take bala'in, ita kuma Abu tana gefe ta rike kugu tana murguda baki da gatsina fuska. Ransa ya kuma baci yace "Haba Sala, yaushe zaki rufe idonki kina ji kuma kina gani Zainabu ta dinga kaiwa dare a waje kuma idan ance za'ayi mata fada kice baki yarda ba, yanzu ki duba agogo karfe sha biyu har da rabi na dare ace sai yanzu yarinya mace zata dawo gida." "To Ubana ai sai kazo ka rufeni da duka, nace kazo ka rufeni da duka!" Ta fadi da hargowa, kana ta cigaba da cewa "Ina ruwana da wani lokaci ko karfe dubu na dare zata dawo bai shafeka ba, ai ba kai ne ka haifar mini ita ba, kuma da kake cewar neman kudi hauka ne inace kaima nan kake shigowa kana rara gefe a sammaka abinci, kato dakai ba don tana nemowa ba zakaci ne? shi solobiyon Uban naku idan muka daka ta tashi zamu rayune? tun yaushe ya bar gidan nan tun asuba ya tsallakemu ya gudu har yanzu bai shigo ba sai mun kuma wani bacci, to zamu zauna ne mu mutu idan bamu nema ba? Wallahi ka fita daga idona ka samawa yarinyar nan lafiya idan ba haka ba ranka zai baci." Ta kuma cigaba da masifa. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 A gidan nan dame zata ji, da tsanar ta da 'yan unguwa sukayi ko ko da jarabarka, yanzu daga safiya suwa yanzu kasan nawa ta samu tun safe kake,zan bata maka rai wallahi." Ya kwantar da murya duk da ransa a bace yake yace "Sala ki fahimce ni, ba wai ina yiwa Zainab fada don bana sonta ba, sai dai a matsayina na dan'uwanta ba zanso ace ta lalace ba, ki dubi yanda kowa ya budi baki a unguwar nan maganarta zaiyi, idan tsokanace itace gaba, Sala yaushe... Kai rufe mini baki sai kwarara zance kake babu kwama babu fulsu tof, ratatata kamar zubar ruwan sama. To tayi din uban wani ya hana, wato kafi so a dinga koro mini ita da duka ko? To ban haifi sallamammiya ba, kai tunda sallamamme ne sai kaje kayi tayi, ta dubi Abu mai tsada shige daki kici namanki kiyi kwanciyarki kamar tsumma a randa, naga shegen da zai kuma takura miki." Abu ta kuma murguda baki gami da yin gatsine ta shiga cikin dakin su ita da kannenta duka uku duk matane ta haye bisa katifarta ta bude namanta tana ci gami da kunna rediyonta da wani saurayinta ya bata, wakar lagireto ta fara futowa a hankali. Itama Sala daki ta shige tabar Sadiku a can tsaye kamar ya hadiyi zuciya ya mutu yake ji don takaici, me ake da irin wannan rayuwa ace kiri-kiri an san gaskiya ake takewa saboda son duniya? Yaja tsaki yana fadin "Allah ya ganar daku gaskiya." Ya nufi dakin sa dake soro yayi fakare cike da tunani, jin kidan dake tasowa a rediyon Abu yake yi har cikin ransa, don dai yana shakkar bala'in Sala ne da wallahi sai ya maka rediyon da kasa uban kowa ma ya huta, yana nan kwance ya jiyo ta kashe da alamu bacci zatayi kenan. Ba'afi minti talatin da hakan ba yaji alamun shigowa, ko ba'a fada masa ba ya san Babansu ne, ya dubi agogo karfe daya da minti goma sha tara, yaja tsaki cike da takaici, yana jinsa ya rufe kofar gidan ya leko ta tsakanin labule yana kallonsa takalminsa a hannunsa suke sai sanda yake sadaf-sadaf! Da haka ya nufi daki, daga inda yake yana jiyo munsharin Sala da alama bacci yayi awon gaba da ita, ya saki labulen ya koma ya kwanta yana tunanin wannan mummunar rayuwa da suke yi da iyayensu, a haka har bacci barawo yazo ya sace shi. Da sassafe ta tashi ta shiga bandaki tayo alwala tayi sallah, sannan aka jawo kayan kwalliya aka maka mai, hoda da jan baki wato dai tayi tsaka tsami kenan. Jagirar nan da aka ja har ta kusa taba kunne ga jambaki an saka shi an kawo baki an zagaye saman leben dashi, anyi wani digo a tsakiyar goshin akayi wani bisa hanci, ga gefen haba,sannan aka bude adaka aka dauko wata atamfa 'yar kaduna Nichem, aka sanya aka yafa gyale a kafada bayan ta daura dan kwali disko, ta kalli madubi tayi kyau matuka, tayi murmushi ta futo tsakar gida. Sala dake can kicin tana suyar funkaso da miya tace "A'a kin shiryo, to maza a dauka mai kan albarka kada lokacin makaranta ya kure gashi nan na zuba miki naki," tace To, kana ta nufi gurin da aka ajiye mata nata din cikin watan fanteka, da miya a cikin bokitin fenti, ta dora a kanta su kuma kannenta suna ta mikawa na kofar gida dake zaune suna siya. To maza mai kan albarka kada a dawo da ko guda daya kinji ko? Bata ce komai ba ta fice da digirgire don gwana ce gurin daukar kaya a kanta. A hanya suka hadu da Laraba, itama tana dauke da waina bandashe mai kuli da mai da albasa) suka tafa kana suka rankaya bakin tashar 'yan kifi, suna tafe suna shan hirarsu suna dariya. Karfe takwas da minti arba'in ta dawo, Sala ta tareta tana cewa "Yauwa diyar arziki maza sauke ki shirya kada ki makara, na zuba miki kici ne?" Tace "A'a naci acan bakin tasha." ta mikawa Sala kudin ta shige cikin dakin ta sanyo kayan makarantar ta bulu din uniform da farin hijab, amman bata sanya hijab din ba sai cin damara dashi tayi ta rumgume littafai a hannu ta fice. Sala tace "Ga kudin mota." Tace, "Ina da kudi ki barshi kawai." "To a dawo lafiya a dawo dai da wuri." Tace to. Ta fuce da sauri, tana fita ta sami hayis ta haye aka sauketa a kofar makarantar 'yan mata ta G.G.S.S Dala. Sanda ta isa ana taron 'yan latti ko ma nace an gama, don wadanda aka tare din an tura su cikin makaranta tsintar bola, sai Discipline master da prefect ne a bakin kofa. Babu ko shayi ta nufi kofar tana taunar cingam din ta kas-kas, malam Kabiru discipling master ya dubeta da takaici sanda take shirin shigewa ko kallonsa ma bata yi ba yace "Ke zo nan." Babu ko shayi ta nufeshi tana taunar cingam. Ya dubeta a kufule yace "Ni sa'an Ubanki ne da zaki tsaya mini?" Ta murguda baki tana kunkuni taki durkusawa, ya zanbada mata bulala yace "Kade doron sha-sha-sha." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ta murguda baki gami da cigaba da yin kunkuninta ta durkusa "Me kike cewa?" "Uwarka nace" Ta fada a hankali, da motsin bakin ta yaso ya fahimci abinda tace yace "me kika ce?," Tace "Ni fa bance komai ba malam." Yayi ajiyar zuciya kana yace "Mai yasa ke kullum sai kinyi latti ne eye? Idan baki son makarantar ki daina zuwa mana sai kace an miki dole, shegiya tun baki tafasa ba zaki kone, kina aji daya tal amma kin gallabi kowa, to wallahi idan bakiyi hankali ba sai an kore ki daga makarantar nan,tunda ta uwarkace ba?" Ta fadi a hankali, yaso ya juyo amman bai fahimci abunda tace din ba, don haka yace "me kike cewa?" Ta dubeshi da shagwaba "Haba malam ni fa ban ce komai ba." Yace shikenan tashi kibi 'yan uwanki kuyi tsintar shara. Ta ce "To shege." Ta fada a hankali,Ta mike ta nufi inda ta hango dalibai sunbi, sai a sannan ya hango hijabinta daure a kugunta "Ke! ke!! ke!!! Zo nan." Ya kuma kwala mata kira amman tayi banza "Ke! Zainab ba kiranki nake yi ba?" Ta juya tace "Au ai naji kana cewa ke ne bansan dani kake ba, gani malam." "Ki cire hijabin nan ki saka a jikinki." Ta yamutsa fuska tace "Gaskiya malam zafi nake ji, bazan iya yafawa ba" Da haushi yace "Idan baki yafa ba ko zan zaneki a gurin nan." Lallai Malam Kabirun nan bai san Abu bane, ta murguda baki gami da dafe kugu da hannu daya tace "Allah ko kasheni zakayi ba zan yafa ba don zafi nake ji, haka kawai ba za'a sanya kurajen gumi su futo mini ba, dan babu mai sai mini magani." Ya hasala sosai ya nufeta da fushi ya daga bulalar dake hannunsa zai maka mata, amman ta rike ta gam tace "Allah malam ba zan yafa ba." Can wata firifet ta hasala tace "Malam ka barmu da shegiyar yarinyar nan taurin kai ne da ita bata da mutunci, kusan kullum haka muke da ita taki ta daina yin latti," Bata gama mai maganar ba, ya fisge bulalar daga hannun Abu ya tsula mata, Ai kuwa sai ta fasa wata uwar kara kana tayi kansa ta cakumu wuyar babbar rigarsa ta shige ciki, ya rasa yanda zai yi da ita sai hargowa yake yi yana fadin "futo don ubanki, kina ina ne?" Tana ihu ya rasa yanda zaiyi da ita dole ya cire babbar rigar data makale a jiki ya kalleta da takaici yace "To tashi kije ki wanke bandakin can na seniors." Ta wurgar da malum-malun din "ni gaskiya ba zan wanke kashin wasu garada ba, haka kawai?" Ya rasa yanda zaiyi da ita, yau Allah ya hadashi da shegiyar yarinya mara tsoro, duk yanda ake jin tsoronsa a makarantar banda ita,ya mike ya nufi Ofis din principal yana fadin "Yau zaki ci Ubanki wallahi," babu ko shakka ta bishi wata firifet tace, Zaki ci ubanki yau, za'ayi maganinki. Ta dalla mata harara tace "banza kiji da wadannan hakoran naki masu kama da kaca, "Ke ni kike gayawa haka?" Tayi kanta da bulala, ita ko ta tsaya kyam tana jiran ta karaso ta huce a kanta, wata ce ta rike ta tace ke me yayi miki, Malam Kabiru ya kwala mata kira da yayi nisa, ta debi littafanta dake hannu ta bishi kamar ba zata taka kasa ba. Ya shiga Ofis din principal dake zaune a wata katuwar kujera taci kwalliyarta ta sha glass dinta, daga ganinta kaga tsohuwar 'yar boko. "Yaya dai Malam Kabiru lafiya ne na ganka rai a bace?" Ya sami kujera ya zauna yana huci yace "Hajiya yau wata fitinanniyar yarinya ce ta bata mini rai bari ki ganta." Abu ta shigo Ofis din babu ko sallama ta dubi principal din tace "Sannu Ma." Bata amsa ba illa kara gyara glass dinta da tayi tana duban Abu dake tsaye kerere tace "Kika tsaya mana a kanmu kamar wasu sa'anninki." A hankali Abu tace "Da fa?" Sannan ta tsugunna. Malam Kabiru yace "Kinji ko da kunnenki?, tun dazu wannan kun-kunin take mini bana jin abunda take cewa, sai dai ina zaton zagina take yi." Hajiya Kubra tace "Malam Kabiru sanar dani me ya faru kwantar da hankalinka." Babu bata lokaci ya zayyane mata komai tun daga farko har karshe. Hajiya Kubra ta dubi Abu da harshen nasara tace mata "Haka ne abinda yace?" Da yake Abu jaka ce bata iya turanci ba, domin ba zuwa makarantar takeyi ba sai taga dama, idan tazo kuma din bata yin komai sai hatsabibanci, don haka bata iya komai ba, hakan ce ya sanya ta yiwa shugabar makarantar shiru tana guna-guni. Shugabar makarantar ta hasala ta doka mata tsawa gami da kara maimaita mata abinda ta tambayeta da fari. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Abu tace "Maa nifa bana jin abinda kike fada gwara kiyi mini da yarena, don ni bana jin abinda kike fada." Tana wani fisge-fisge take wannan maganar. Ran Hajiya Kubra ya kuma baci, don haka ta dinga zagin Abu da turanci, tana fada mata "Banza jaka, baki san komai ba sai shegen iskanci da rashin mutunci, a haka za'a gama karatu ba'a san komai ba sai a kare a auren dan dako ko dan acaba."Kalma daya Abu ta fahimta a duk cikin maganar Hajiya Kubra wacce tace mata "donkey" wato jaka, hakan ne ya sanya ta fahimci irin cin mutuncin da ake mata dan haka ta kama guna-guninta tana fadin "gaki nan babbar jaka, ki dubeki fa tamkar kayan wanki." "Me kike cewa?" Shugabar ta tambaya da dacin rai jin Abu na magana kasa- kasa. Ta murguda baki tace, "Ni fa bance komai ba." Hajiya Kubra ta dubi Malam Kabiru tace, "Malan zane mani ita kafin na bata horon da zan bata tukunna." Duk da gabansa ya fadi dan yana gudun makalewar da Abu take masa, amman sai ya daure yayi ta maza ya nufeta da zabgegiyar dorina. Ai kuwa yanda tayi masa dazu haka tayi masa yanzu, ta cukwikwiye shi tana ta zabga ihu, amman babu ko alamar digon hawaye a idonta, da kyar ya samu yayi mata guda Uku yana mai da numfashi.Hajiya Kubra tace "To maza dauki tsintsiya ki share harabar malamai duka yanzun nan." Ta mike tana guna-gunin nata tace "Oho dai! Ko yanzu na wahalar daku,"Me kike cewa?" Ta tambayi Abun wacce tuni tayi fucewarta, ta kuma duban Malam Kabiru tana fadin "Lallai yarinyar nan bata da mutunci, shegiya irinsu ne idan suka hadu da maza jahilai irinsu suke lakada musu duka." Shi dai baice komai ba, yayi godiya ya fuce domin dai Abu ta wuce iyakacin tunaninsa. Abu tayi zaton abun na wasa ne, sai gashi wankin hula yana neman ya kaita dare, dan bata kammala ba har aka fita tara (break), sannan ta nufi Ofis din shugabar makarantar (principal) tace "Maa na gama." Ta dubeta a wulakance tace "Ki yafa hijab dinki, sannan kada ki kuma yadda a kawo mini kararki Ofis dina, idan ba haka ba sai na koreki ko kuma kizo da Baban ki." Abu ta cire hijab din nata ta sanya wanda daman dan mitsitsine tace "To!" Sannan ta fice daga Ofis din. Hajiya Kubra tayi kwafa gami da yin tsaki tana fadin "Dakikiyar banza, bata san komai ba sai iskanci." Ita kuwa Abu tana yin nisa daga Ofis din ta cire hijab din daga kanta ta kuma yin damara dashi sannan ta nufi ajinsu. Kawayenta ne suka tarota ana ta ihu suka rungumeta suna mata kirarinta, domin wadanda abun ya faru a gabansu sun basu labari, da haka suka karasa aji suna shewa har aka koma break. Sai dai da zamanta da rashinsa kusan duk daya ne a ajin, domin dai bata tambayi abinda akayi ba da bata nan ba, sannan yanzu ma da malami ya shigo bata tsaya ta saurareshi ba hirarsu kawai sukeyi da wata kawarta, kusan sau uku malamin yana gargadinta akan tayi shiriu amman batayi shurun ba, har ya gaji dai ya tambayeta kamar haka "Abu, tell me how many are types of letter?" Yana nufin ta gaya masa kashe-kashen wasika. Tayi tsuru-tsuru don bata fahimci tambayar bama balle tasan amsar da zata bashi, sai wani murguda baki kawai takeyi tana guna-guninta. ganin bata da niyyar bada amsar ne ya sanya ya kuma gargadin ta akan tayi shiru ta saurareshi, dan darasin turanci yana da amfani ga dalibai don ta haka ne zasu koyi yanda zasuyi magana dashi, amman har ya fita daga ajin nan Abu bata daina surutunta ba sai dai ta rage murya ba kamar da farko ba. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Da aka tashi ma sai da sukayi fada da kwandasta domin dai idan da sabo ta saba, domin dai maimakon ta bashi naira biyar sai ta bashi naira uku ba kuma don bata dasu ba, a'a dan dai neman jidali kawai irin nata. Kwandastan ya dubeta ransa a bace yace "Ke! Malama cika mana kudin mu saura naira biyu." Tayi tafi gami da doka cinya tana fadin ba zata cika ko kwandala ba don haka kudin motar yake. Nan fa rikici ya rincabe amman Abu ta kekashe akan ba zata cika ko kwabo ba. Daga karshe yace wallahi idan bata cika masa ba zai warci dankwalinta, maimakon ta saduda ina sai ma ta cigaba da tsiwarta tana tafa hannu, kawayenta na ta zugata. Abin ya hasala direban yace masa ya cire dankwalinta tunda bata da mutunci, dan haka ya cire dan kwalin nata. Sai dai abu da kwandastan bai sani ba shine tuni Abu ta gama dana masa tarko, don haka da ta sauka kafin ya hau motar tace masa "Malam ka bani dan kwalina." Yace "Na karfi ne, idan kina son dankwalinki ki cika mini naira biyu.......Warce gudar Naira ashirin da fellewarta da gudu ne ya katse masa zancensa, ya saki baki galala yana kallonta tamkar zata tashi sama dan gudu, don Allah ya yi mata baiwar gudu. Direban ya hau masifa sanda ya ankara da abinda ya faru yana fadin "Banza sakarai, kana me wannan 'yar mitsitsiyar yarinyar ta warce kudi a hannunka? ai sai ka shigo mu tafi." 'Yan cikin motar banda dariya babu abinda suke yi, shi kuwa cike da jin haushi yake fadin "Haba Oga baka ga shammata ta tayi ba? An bani murtala ina shirin bada canji ta fisga ba?" "Kawai kazo mu tafi, shegiyar ta bamu a can" Direban ya katse masa magana. Ya dubi inda Abu tabi ko alamunta baya gani dan akwaita da gudu tamkar filfilwa, hayaniyar fasinjoji ce ta sanya shi shiga motar yana fadin "Ai na gane wallahi duk ranar da Allah ya kuma hadamu sai taci ubanta." Ya shiga mota har lokacin wasu fasinjoji suna dariya abinda ya kara kular dashi. Ita kam Abu tunda ta falla da gudu bata tsaya a ko'ina ba sai a tsakar gidan su, ta zube a kasa tana mai da numfashi. Sala dake kwashe wake da shinkafa ta dago tana dubanta a rude tace "Yaya dai Maitsada, lafiya kike wannan hakin kamar wacce tayi tseren gudu?" Sai data numfasa sannan ta kwashe da dariya harda rike ciki, duk da Sala bata san ko dariyar me take yi ba sai ta hau tayata tana fadin "Hatsabibiya, yanzu haka tsiyar taki kika shuka tunda naga kina wannan dariyar." Tayi kokarin tsagaita dariyar sannan ta fara magana "Bari ke dai Sala, yau wani shege na hadu dashi zai nuna mini zara bai san na fishi ba....." Ta kwashe duk abinda ya faru ta sanarwa da Sala din, gami da karasa zancen da cewar "Shegen kinga ashirin din dana warto, gobe ma ya kuma." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Sala ta kuma fashewa da dariya tana fadin "Lallai kinyi maganin dan iska shege, banda iskanci akan naira biyu sai ya warce miki dankwali? Da ba'a cin arziki ai da bai sami kwandastan ba tunda nasan ba motarsa bace, amman maganinsa kenan kinga ai gobe ya kuma. Maza tashi ki shiga wanka kada lokaci ya kure Abulata mai kan alheri, ba irinsu O'o ba mai kan kwantai Wato tana nufin Karima kanwar Abun, domin dai ita bata da hali irin na Abun dan tana jin irin nasihar da Yayansu yake mata, dan haka ma basa shiri da Sala sam. Ta mike har lokacin tana haki da dariya ta shiga bandakin, kwandan wankanta daban ne, dan ita sabulunta dankwali ne kamar yanda take cewa giv da dai sauransu, ba irin nasu Karimaba dan yanka. Bayan ta fito daga wanka aka kuma zauna zaman kwalliya, Jagira kam da aka jata har saida ta tabo kunne, ga kuma dige-dige da aka yi a fuskar ko ina, leben nan kuwa yasha baki sama da kasa, sannan aka cokala daurin dan kwali ture kaga tsiya aka fito. Sala nayi mata kirari ta nada gammo ta dora a kai, akayi digir-gire da fanteka wacce ke dauke da wake da shinkafa da robobi a gefe da mai da yaji duk a kai, sai hannunta data dauki wani bokiti wanda dashi take wanke kwanukan da sukayi datti, aka fice babu addu'a sai da kirarinta data bita dashi, sai da ta fice daga soron sannan Sala ta bita da sauri ta leka duk rabin jikinta a waje ta kwala mata kira ta juyo tana guna-guni. Sala tace "Yi hakuri Abule na dawo dake, na manta ban tina miki maganar makarantar allo ba kada jarababben yayanki yaga ba kije ba ya hadani da malam, wanda yake jin kamar ya jefani a wuta dan dai nafi karfinsa ne kawai. Don ba dan jarabar su ba daga bokon har allon daina zuwa zaki yi tunda dai kin sami na sallah." Ita dai Abu batace komai ba ta juya ta tafi tana kun-kuni tana fadin "Kawai daman akan wannan maganar kika dawo dani, wallahi da na san a kanta ne da ba zan dawo ba." Sala din kuwa tace "Mai kan arziki a kukkunga kada a dawo da ko kwalli daya, na san ki, ai ba kya kwantai." To kawai tace sannan ta wuce. Kai tsaye tasha ta wuce tashar kofar Wambai, tana isa kwastomominta suka yi mata caaa, domin akwaita da araha ga sakin fuska da tsafta, idan kana so takai maka har shagonka zata kai maka Tun karfe hudu saura minti goma abincin nata ya kare amman sai ta tsaya hira da samari da wasan jakai da kawayenta 'yan talla. Can ta hango Rodimasta, wani da take bi kudi tuntini, ai sai ta cire gyalanta tace dammara dashi tana fadin "Yau Allah ya kama tsinannan can, wallahi idan bai bani kudina ba sai nayi masa rashin mutunci wallahi, dan yau sai anyi bala'i a cikin tashar nan wallahi." Laraba kawarta ta riketa tana fadin "Haba Abu yawa ne, ki kyale shi kawai kin san halinsa dan akuya ne..." Ta fincike tana fadin "Dalla malama sakeni ai ya san wadanda yake yiwa akuyancin nasa, ni idan ya kawo raini ai sai inci (ta kunduma zagi)." Ta isa gabansa yana shan tabar wiwi sai wani lumshe ido yake yana rere wakoki kala-kala na gambara zuwa wakokin 'yan dambe da na barayi, kai gasu nan dai barkatai. Abu ta rike kugu tana wani karkada kafa tace "Kai barawo bani kudina, rannan na zuba maka abinci ka gudu baka bani kudina ba, to yau Allah ya kama ka, ko ka bani kudina ko nayi maka rashin mutunci wallahi. Ya dubeta yana murmushin mugunta yace "Banza ke wallahi karamar arniya ce, har kin isa kiyi mini wata barazana, to na cinye na karfi ne ki kwata." Ta tafa hannu tana fadin "Kan Ubancan, lallai yau ka tabo ma kanka, yau zan nuna maka kai karamin dan iska ne, dan ko sama da kasa zata hade sai ka bani kudina." Ta kama kwalar rigarsa ta cukwikwiye tana cigaba da bala'i. Shi kuwa sai dariya yake yana fadin "Yarinya kece mai aikin yi, in dai nine wallahi mu kwana a haka." Ya cigaba da zukar wiwinsa yana lumshe idanu. Jama'a sukayo gurin suna bada hakuri, Abu tace wallahi ba zata cikashi ba sai ya bata kudinta idan kuwa ba haka ba zata dauko masa folis ita kam Laraba da yake matsoraciya ce sai hakuri take baiwa Abun. Maimakon ta hakura sai ta doka mata tsawa tana fadin "Dalla can malama gafara daga nan, Uwarsa ta kauye ce take bani jari ko ubansa na karkar....." "Ke Abu don kazanki ni kike zagi?" Rodimasta ya katseta a hasale dan ya fara kufula da rashin mutuncin da take masa. Babu tsoro balle fargaba tace "An zageka din, kai wanene da ba za'a zageka ba eye?" Ya kuma hasala da zafin rai yake fadin "Ke wallahi idan baki sakeni ba zan tattakaki a gurin nan na farfasa miki jiki." Tayi shewa "Ahayye! wallahi Bismillah dan halak ka fasa, don ka sani duk mari daya a folissitashan naira dari yake, don wata kila sai an hada da gonar kauye sannan za'a biya kudin marin....." "Ke Abu dan Allah kiyi hakuri ki sake shi, wannan ai ba mutuncin ki bane kina mace kina fada da maza." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ta kalli mai maganar tana fadin "Kaga Baba mai taba ina ginin mutuncinka dan kana biyana kudina ba irin wannan dan bashin ba, dan haka kawai ka bar gurin nan sai ya biyani kudina zan sakeshi." "Kinga ya isa sakeshi nawa ne kudin naki na biya, tunda shima ya rantse ba zai biya ba dan idan rigimar tayi zafi har mu zaku jawo wa tunda dai haka 'yan sandan can ke so a fara fada suzo kame." Ta murguda baki tana fadin "Ai wallahi nima ba zan sakeshi ba sai dai idan ka biyani, naira biyar ne dan haka sai ka biya." Ya dauko naira biyar a aljihun gaba rigarsa yace "Gata shike nan rigimar ta kare ko?" Ta saki rigar Rodimasta tana fadin "Banza matsolo matsiyaci, yau Allah ya rufa maka asiri da yau kaga karshen rashin mutunci." "Ke! Ya isheki tunda dai an biyaki kudinki 'yar matsiyata, dan wallahi kika zageni sai na tattakaki." Ya fadi yana nunata da yatsansa. Ta tsaya ta rike kugu tana wani girgiza tana fadin "Wanda bai fasa ba baya kaunar uwale da ubale..." Laraba ta janyeta tana fisfisgewa da kyar aka samu ta kama hada kayanta tana cigaba da bala'i ta bar tashar. Tana isa gida ta dire fantekat kayan ta mikawa Sala kudin wacce ke washe baki, ta fada daki ta kwanta. Sala taji shiru ta leka dakin ta ganta a kwance ta bude baki da mamaki tace "Au Abula kwantawa kika yi? Ke da zaki je makarantar allo? kada jarababban yayanki yazo ya ishemu da mita." Ta mike gami da daukar allo ta fice tana kun-kuni. Miskili kafi mahaukaci ban haushi, Sala ta fada tana dariya. ta dora da cewar "Abula diyar Salamatu wani lokaci idan kina shan kunu ko miskilancin naki ya motsa sai na ganki kamar wata diyar wani sarki, sai da lallashi Abula ta." Bata dai ce komai ba ta ficewarta. Makarantar dake kusa da gidansu, dan tsakaninsu gida uku ne, koda taje dinma hira ta kamayi da kawayenta sai da malam din ya doka musu tsawa sannan suka rude da hayaniya wai su nan dole karatu sukeyi. Da ya kirawo ta ta biya allonta kuwa inda-inda ta kama yi, nan fa ya hauta da fada, tayi kum da baki kamar ba Abula diyar Sala ba, dan idan akwai wanda take tsoro da shayi a duniya bai wuce malam da yayanta ba, dan malam din bai mata ta dadiba tun tana 'yar mitsitsiyarta kuwa, gashi babu yanda zasuyi dashi dan shine kamar matsayin kakanta na gurin Uba, ya kuma maimaita mata ta karanta kuwa tsaf. Domin dai duk iskancin da takeyi tana sane don da ace tana maida hankali akan karatu da mai kokarice ita dan kwakwalwarta akwaita da saurin rike abu, sai dai shiririta da wasa da ta sanya a ranta, dan yanzu data koma gida zata fita yawo da wasa dan da kyar gobe zata iya biya yanda ya biya mata, rudewar da akayi da karatun tashi ne ya kwace ta. Ana cewa fatiha kowa ya mike yara suna ta waka suna fadin "Tashiiii." Su Abu da zugar kawayenta kuwa tsayawa akayi ana maida yanda aka yi, dan wai wata Lantana tayi gulmarta, wai yau zasu dirji bakin Lantana da rubabben kwai. Ai kuwa suka saka ihu aka sanya Lantana tsakiya tana kuka, sai waccan tace nima kince mini kaza kince mini kaza, sai ta tabe baki tana fadin, "Laaa! Ni din?" Sai kuma ta sanya kuka, Laraba ce ta kuma tunzura fadan da tace "Eh, nima rannan kince mini wai Abu tana zuwa gurin Dan Oga mai kyamis, Kutumar uban can, lallai yarinya a gulmar taki har da ni? dan ubanki?" Abu ta shiga masifa tamkar zata ci babu, taci dammara da gyalanta tana cigaba da girgiza gami da ambaton sunan iyayanta tana kunduma musu zagi gami da dungure mata kai da lakuce mata hanci, yara sai ihu suke yiwa Lantana wacce banda kuka babu abinda take yi. Malamin sune ya farga da abinda ke faruwa yayi kansu da dorina, ya samu daya ya caula mata ta gantsare gami da fasa ihu, abinda ya ankarar dasu kowa ya bazama da gudu dan gujewa bulalar malam, wannan ne ya ceci Lantana daga fasa mata baki da akayi niyya da rubabben kwai. Ana idar da sallah Abu ta fito daga gida tana rera wakar kiran wasa don tunda ta taso itace ke kiran 'yan wasa don ita ce boss din, don haka ko yara ne ba'a gani ba gidansu ake zuwa nemansu Sala tayi ta bala'i. Ta fara rera wakar wasa kamar haka: "'Yan wasa ku futo wasa, idan baku zo ba ubanku yazo, bani na fada ba bature ne, baturen ma na kasar borno. 'Yan wasa ku fito wasa." Ai kuwa sai sai ga yara suna fitowa daga gidajensu da gudunsu maza da mata.Yayanta Sadiku dake shagonsa yana jinta, ji yake tamkar yaje ya shaketa, sai dai yana gudun jarabar Sala ne, don shi a zatonshi tun da ya samar mata makarantar gaba da firamare zata daina wannan wasan haukan, amman sai yaga babu abinda ta daina, dan haka yayi niyyar hanata da tsiya amman Sala tayi tsalle ta dire tace Wallahi bai isa ba ya kyale mata yarinya ta wataya. "Aljana a kwaba ba tsari, aljana a kwaba ba tsari....." Wannan wakar ce ta katse masa tunanin da yakeyi, ya mike ya leko da sauri don yasan wa suke tsokana. Ai kuwa yana hango su sunyi zuga suna biye da wata karuwa da taci kwalliya da wani matsats-tsan siket kanta babu dankwali balle mayafi, tana tafe da kyar da sauri tamkar siket din zai yage, kanta tamkar tozon rakumi ga takalmi sakadale tumeme da kafarta, amman sunki saurara mata sai binta suke suna mata wakar da ihu gami da bula mata kasa. Can wasu dattawa wadanda ke zaune suma suna zabga uban musu, dan sunan majalisar tasu ma majalisar 'yan musu, suka yo kansu sanda suka ankara da duka. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Nan fa suka runtuma da gudu suna dariya, sai da sukayi nisa sannan suka zube a kofar wani gida sunata dariya. Can Abu tace "Laaa! Ku tsaya kuji wallahi yau mu kai sumame gidan shegun can Karuwai mun dade wallahi bamu je ba ko?" Yaran suka amsa da "Eh! Wallahi mu badawa shegu tiyagas din toka." Abu tace "To kowa ya tsaya bari naje gida na samo toka da citta a gurin Sala." Ai kuwa cikin kankanin lokaci suka hada citta da barkono dakakku da kuma toka cikin ledoji suka kulle da dutse a tsakiya suka nufi gidan karuwai ta bayan layi don kada a gansu. Sun yi sa'a kuwa da yawan karuwan suna daki suna hira da lalatattun maza 'yan uwansu, wasu kuma ma suna caca da masu aikata babbar alfasha. Suka shiga cikin gidan da sanda kamar wasu barayi, har tsakar gidan suka isa, cikin daga murya Abu ta bada umurni, "A fasa! A fasa!!.Ai kuwa ji kake tush-tush-tush, nan da nan karuwai suka kama ihu da atishawa, na daki suka yo waje da gudunsu wasu daga su sai siket, wasu kuma sai zani, harda masu dan kamfai. Su Abu suka fasa ihu suna dariya gami da ficewa da gudu daga gidan dan kada a kamasu, sai da suka isa wani kofar gidan can nesa da gidan karuwan suka zube suna dariya, suna hango yanda suke ta atishawa. Hantsi ya dubi ludayi sanda Abu ta dawo daga tallar waina. gashi anyi sa'a ranar babu makarantar boko, dan haka ta zauna a tsakar gida tana baiwa Sala labarin yanda sukayi da karuwan jiya suna ta kwasar dariya, Sala kam harda durkusawa tana rike ciki. Can suka jiyo sallama, tun kafin sukai ga amsawa aka shigo, mutane guda biyu da kayan 'yan sanda a jikinsu riga da siket, sun daure kugunsu da bel. Sala ta mike cike da mamaki tana tambayarsu "Yaya dai bayin Allah lafiya ko? Don ganinki babu alheri." Daya daga cikinsu ta fara magana "Hajiya munzo mu tafi da 'yarki mara mutuncin can Abu, domin dai ta addabi uban kowa a unguwar nan, idan yaso idan munje folis sitashon kya ji abinda ta yi." Abu ta mike da sauri tana tillika dariya dan tasan kwanan zancen tana fadin "To muje din mana, Sala kiyi zamanki yanzu zan dawo." Sala tace "A'a ba zan iya bari ki tafi ke daya ba muje." Ta dauko gyale akan igiya suka fice tana fadawa Karimatu ta lura da abincin da ta dora kafin ta dawo. 'Yan sandan suka fara kuluwa da dariyar da Abu take musu, dan haka suka ce wallahi idan bata daina ba zasu yi mata shegen duka, ta gumtse baki tana yi a ciki don bawai tsoronsu takeji ba, a haka suka isa har folis sitashon din. Ganin karuwai sun jeru ne har da 'yan daudu ya sanya ta kuma tabbatar da zargin da takeyi, kamar ta fashe da dariya amman dan tana gudun sharrin 'yan sanda ya sanya ta gumtse bakinta. Ta isa gindin kanta inda wani dan sanda yake zaune da gashi buya- buya a bakinsa wai shi nan sajan ne. Yana wani muzurai ya dubi Abu yace "Ke mai ya sanya kika je gidan wadancan masu zaman kansu kuka barbada musu toka hade da yaji?" Abu tayi shiru taki cewa komai, ya kuma maimaita mata maganar amman taki tankawa. Wani kurtun dan sanda dake tsaye ya daga kulki ya maka mata a gadon baya, ta gantsare gami da fasa ihu tana sosa gurin tana fadi "Wayyo Allah na na shiga uku, wallahi idan ka karya mini kashin gadon baya na bazan yadda ba." Ya kuma dagawa zai maka mata amman mai mukamin sajan din ya hanashi domin idan da sabo sun saba da halin Abu, sannan ya maida dubansa gurin Abu ya daka mata tsawa ya kuma maimaita tambayar da yayi mata da gargadin idan ta kuma yin shirun zasu saba mata. Ta murguda baki gami da kallon sa kyar da idonta babu alaman shakka ko tsoro tace "Wallahi ko zaku kasheni ba zan yi magana ba sai dai muje gaban (D.P.O)." Sala tace "Abu kiyi magana kada su tsamama miki jikinki." Ta kuma hasala tace "Sala kiyi shiru, haka kawai sai su kama dukana bayan basu kama ni da laifin komai ba? Ai nasan 'yancina dan haka ba zanyi magana ba sai dai muje gaba." Ran 'yan sandan ya kuma baci suka yi mata caa tamkar zasu cinyeta amman ko gezau batayi ba, ana cikin haka sai ga (D.P.O) din ya shigo, Da mamaki ya dubi Abu yace "A'a, Abu lafiya na ganki a nan?" Ai kamar jira take ya shigo sai ta fasa kuka kamar wacce aka yiwa dan banzan duka, amman fa idon nan nata babu alamar hawaye ko digo sai dai burarin kawai da takeyi tana rike bayanta . (D.P.O) din yace su shigo daga cikin Ofishinsa su duka, Dan daudun dake tare da Karuwan ya rike haba yana fadin "Oh! Ni Hajiya Ladi yau na gamu da shegiyar yarinya mai sharri, wallahi ko kwallaba nan ta ganki ta kyale, ai wallahi ko mutuwa zakiyi ba kuka ba sai kinci ubanki." Ya karasa maganar yana tafa hannu da cinya. "Kai! keep quit kayi mana shiru." Wani kofur ya doka masa tsawa. Yayi fari da ido gami da fadin "Lalala! Ka manta wallah Hajiya Ladi nake ba kai ba." Da haka suka shiga ofishin D.P.O din. Mai tuhumar Abu Sajen Barewa ya karantawa D.P.O tuhumar da ake yiwa Abu, da kuma abinda ya faru. Ya dubi Abu yace "Kina jin zargin da ake miki? haka ne ko ba haka na ne?" Ta lankwashe murya cikin ladabi tamkar mutuniyar arziki tace, "Yallabai karya suke mini, ni jiya da daddare ma ina gurin tallan gyada ta, har kazo wucewa kace na kai maka gwangwani goma a majalisarku ko?" Ya dubi karuwan yace "To ku kunji abinda wacce ake tuhuma tace, ko kuna da wata hujjar da zata nuna mana itace din ta bada muku toka?" Hajiya Ladi ya tafa hannu yana fadin "La'ilaha illallahu, Allah na yarda yarinyar nan shegiya ce kwalba." "La-la-la ka zage ni?" Abu ta fadi ta dora da cewar "Yallabai kana ji yana zagina a gabanka hakama acan waje yayi ta zagina." D.P.O ya doka masa tsawa yana fadin "Kada ka kuma zaginta." Ya rike haba yana fadin "O! Ni Hajiya Ladi na shiga uku, tuba nake Yallabai ayi hakuri na daina zagin, amman kwaran-kwatsa dubu jiya ina suyar doya na shiga bandaki dan na rage marata, na jiyo hayaniyar su Abu, kafin na farga har na fara tari da atishawa a cikin bandaki da kokarin shidewa har zani na yana faduwa, da kyar 'yar fisuwa ta kamoni ina kokarin bankawa cikin masai. Ko ba haka ba 'yar fisuwa?" Ya kalli wata karuwa da taci uban bilicin, kan nan tamkar tozon rakumi daga ita sai gajeren wanda iyakacin gwiwa da riga tishet. Tana tsaye rike da kugu tace "Haka ne yallabai, tabbas yarinyar nan ce ta gayyato mana yara suka watsa mana toka mai yaji, dan da muryar ta ma muka gane ita ce" "Karya kike yi bani bace, daga jin murya sai kice ni ce? Idan kuma kin yarda ki rantse da Allah ko a kawo Qur'ani ki dafa." Abu ta katse ta. D.P.O ya ce "Kunga tunda dai abun nan baku da shaida zargi ne kawai kuke yi, dan haka ki basu hakuri ke Abu, idan yaso a gaba sai kuyi kokarin kama koma su waye ke muku haka." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ya dubi Sala ya cigaba da magana "Ke kuma kije ki baiwa sajan din da ya karbi laifin kudin shan ruwa, na kashe case din kowa ya fita." Sam ba haka karuwan nan suka so ba, amman tunda dai basu da cikakkiyar shaida dole suka hakura suka fice, ita kuma Sala ta baiwa Sajan Barewa Naira hamsin tace ya sha ruwa. A harabar caji ofis din suka kuma cin karo da karuwan da Hajiya Ladi suna mai da yanda aka yi.Abu ta dubi Hajiya Ladi tana dariyar keta har da gwalo, Hajiya Ladi ya dalla mata harara yana nuna ta da yatsa alamun kashedi, ta kuma sanya dariya gami da sanya hannu a wuyanta ta ja shi alamar yanka, sannan ta nuna Hajiya Ladi. Hajiya Ladi ya saka Salati "La'ilaha illallahu, ni zaki yanka? Lallai yarinyar nan baki da mutunci, to gwara na koma na fada su zama shaida tun bamu bar gurin ba." Yana magana da karfi yana tafa hannu da buga cinya, gaba daya hankalin jama'ar dake gurin yayi kansu. Abu ta marairaice tana fadin "Dan Allah jama'a wa yaji sanda na yiwa mutumin nan magana balle har nace zan yanka shi? to muje din mana a kwatar mini hakkina tunda abin naka sharri ne, tunda dai kowa yana ji anan bance da kai komai ba." Sannan tabi bayan Hajiya Ladi da sauri dan su koma ciki tare. Hajiya Ladi ya tsaya da sauri sororo yana kallon Abu, domin dai lallai ya hadu da wacce tafi shi sharri da iya iskanci. Da zolaya Abu tace "Yaya ka tsaya mu tafi mana." Ya dallawa Abu harara yana fadin "Kwalba uwar sharri, kada ki kuma kirana da kai sunana Hajiya Ladi, idan kuma jurinki iskanci zamu kuma gauraya sai na nuna miki ke din baki isa komai ba wallahi." Ya tafa hannu gami da bugawa a cinya yana wani murguda baki da karkafa ido, ya dora da cewar "Kun ga kuzo mu bar harabar police station tun shegiyar yarinyar nan bata haddasa mana ciwon zuciya ba, kunga tafiya ta." Ya gyara daurin zanin dake bisa wandonsa gami da dane hannu yana tafiya yana wani yanga, suka rufa masa baya suna mai da yanda aka yi. Abu ta kyal-kyale da dariya gami da nufar gida. Sala tana biye da ita itama tana dariya da yi mata kirari, "Abula tawa, kowa ya ja dake yaji kunya. Mahassada kun sha kashi. Yarinya mai tsada kalar manyan maza." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 KANO 11 GA WATAN 6, 1993. Rayuwa mai sauyawa, sai dai ga Abu sauyi da aka samu kalilan ne, domin dai cigaban nata bai wuce na daina daukar abinci akanta,sai dai a dorawa dan dako tana biye dashi ba, sai kuma chalo da ta daina zuwa da dibar 'ya'yan jama'a a tafi tsokanar fada duk ta daina. Sannan kyawun ta da kirar da Allah yayi mata mai daukar hankali sun fara bayyana. Sai kuma Abu mafi girma da za'a idar bai wuce daina tallar safe ba, saboda shugabar makarantarsu ta budewa Abu wuta saboda jarabawa da aka yi ta shiga aji biyu na sakandire amman sai ya zamana Abu ce ta dauki na karshe a ajinsu, sannan ko a jikinta (wai an mintsini kakkausa). Abun ya konawa Hajiya Kubra rai, don haka ta sanya aka tara mata duk wadanda suka zo na karshe na kowanne aji, ta sanya su a gaba tayi musu kaca-kaca, sannan tace lallai sai kowacce tazo da mahaifinta domin tana son jin dalilin da ya sanya basu mai da hankali akan karatun ba har suka zo na karshe, dukkansu yaran jikinsu sai kyarma yake yi kowacce a tsorace take amman banda Abu dake ta murguda baki tana magana kasa-kasa, sarai Hajiya Kubra ta ganta amman sai ta rabu da ita da zummar idan mahaifinta yazo za tayi mata hukunci a gabanshi, haka nan suka tashi kowacce ta nufi gidansu tun lokacin tashi baiyi ba. Abu tana shiga gida babu ko Sallama bagazan-bagazan- bagazan ta yadda jaka da hijabin tana fadin, "Wallahi Sala ba zan kuma zuwa makarantar nan ba, don na gaji da masifar shegiyar principal dinmu, sai kace wata uwata haka kawai ta tsane ni." Sala ta dubeta da kulawa tana tambayarta "Mai tsada yaya akayi ne? Mai ya faru naga ko lokacin tashi daga makarantar bai yi ba." Ta tabe baki kana tace "Wai kawai dan munzo na karshe shine ta sanyamu a gaba tanata zaginmu, baki ga sauran ba jikinsu har rawa yake yi, ni kuwa duk abinda tace sai na bata amsa amman dai a hankali, kuma tama yi sa'a dan 'yan arzikin a kaina da saina rama," "Kinyi mini dai-dai, sai kuma aka yi yaya?" Sala ta katse ta. "Wai kuma duk cin mutuncin da tayi mana bai isheta ba wai lallai sai mun zo da Babanmu, ni kuwa wallahi bata isa ba ai dai ba karatun shiga Aljanna bane." Sala ta amshe "Wannan tsabar rainin hankali ne, haka kawai dan kunzo na karshe sai ace wani sai kunzo da Babanku? To ai ba laifinku bane sune basu iya koyarwa ba, ai zuwa makarantar ba dole bane kiyi zamanki kin huta da tashin safe ma." Wannan ne ya sanya Abu ta share gindi tayi zamanta a gida har kusan sati biyu bata je makaranta ba, sai rannan da Sadiku ya shigo da hantsi wajen karfe goma, shima ya dawo makaranta sai kuwa suka yi kicibis, yayi kanta da masifa yana fadin mai ya hanata zuwa makaranta. Ta zura dakin Sala da gudu dan duk iskancin Abu tana tsoron Sadiku dan bai mata ta dadi, dan babu wuya ya lakada ta. Sala ce ta fito tana hargagi gami da sanar dashi yanda aka yi. Ya kuma kulewa yace maza ta shirya ya maida ta idan kuwa ba haka ba sai dai idan ta daina fita ne wallahi sai ya karya mata kafar talla. Sarai Sala ta san halinsa dan haka ta lallaba Abu dake ta kunci ta fita suka nufi makarantar. Sanda suka isa ofishin (principal) shugabar makarantar ya dinga bata hakuri yace Babansu ne baya gari shi ya sanya ba'a kawo ta ba, shi kuma bai sani ba yana makaranta sai yau da ya dawo ya taddata a gida. Da farko Hajiya Kubra tace ba zata saurareshi ba sai dai idan ya nuna mata katin shaidar cewar shi dalibi ne I.D card, tayi mamaki sosai da taga abinda yake karantawa (Law) amman kanwarsa muguwar dakikiya. Ta bashi guri ya zauna sannan ta sanar dashi irin mugayen dabi'un Abu da kuma dakikancin ta. Yayi kwafa cike da takaici yace "Babanmu yace a baki hakuri sannan yace kafin na bar Ofis din na kiyi mata bulala guda hamsin, kuma yace daga yau kowane irin laifi tayi a daina korata gida tunda ba fada takeyi ba dan bata son karatun, a dinga bata horo mai tsanani kowanne iri ne." "Karya kake yi wallahi, yaushe har kaga Baban mu daya fada maka haka?" Ta katse masa magana da rashin kunya da hargowa. Mamaki da takaici ya kama Hajiya Kubra, wato bata bar na gida ba balle na waje ma. Shi kuwa Sadiku saboda tsabar takaici kasa magana ma yayi, sai dai yaga wata bulala a kan teburin Hajiya Kubra dan haka ya dauko ya hau zabga mata, tun tana ihu da makaleshi har ta gaza bakin nan nata sai da ya mutu, gashi babu Sala mai kwatarta ita kuwa Hajiya Kubra dama a cike take da ita dan haka ko uffan bata ce ba, daman duniya idan akwai abinda take tsoro bai wuce dukan Sadiku da na Malam ba, domin basa mata na wasa, gashi sune kadai zasu daketa a duniya su daki banza dan babu abinda Sala zata iyayi, sai dai tayi hargaginta ta gama dan ba zata iya rama mata ba, su kuma bata isa ta dauko musu 'yan sanda ba kamar yanda ta saba. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Yawan dukan da yayi mata ne ya sanya ran Hajiya Kubra yayi haske, ta tabbatar lallai akwai mai kwabar Abu jine kawai da bata yi. Bayan ya jibgeta ya gaji ya dubi Hajiya Kubra yace "Hajiya ki bata fartanya tayi noma da kuma wankin bandaki." Abu dake kwance tana kuka ta kuma kurma ihi tana fadin "Wayyo Sala na shiga uku kizo da kanki,A zuciye ya kuma kai mata duka a bakinta wanda ya sanya ta yin shirun dole dan sai da bakinta ya fashe, amman bata daina harararsa da murguda baki ba. Haka ya tafi ya barta saida tayi noman nan da wankin bandakin dalibai wanda yayi kaca-kaca da kashi babu kyan gani, dan saida ta daure hancinta da dankwalinta sannan ta iya wankewa, shi dai Sadiku yayi tafiyarsa, amman yasan yau bala'i sai yasha ya more gurin Sala. Ai kuwa haka din akayi domin dai data dawo gida taga idonta da bakinta sun kumbura ta zabura da sauri tana tambayar abinda ya faru. Abu ta zube a tsakar gida ta dora hannu a kai tana zunduma ihu kamar wacce akayi wa mutuwa ko kuma a sannan ake dukan nata tana fadin "Wayyo Sala na shiga uku, wallahi bazan taba yafewa Sadiku ba ko kabarinsa zai dinga balbala da wuta..." "Wai me ya faru? na san za'a rina daman, me yayi miki?" Sala ta tambaya a rude. Ta kwashe duk yanda akayi ta sanarwa da Sala tana ajiyar zuciya dan babu alamar hawaye ko kwalli a idonta. Habawa ran Sala idan yayi dubu ya baci, ta dinga sirfa masifa tana fadin "Ai makarantar ba dole bace da har za'a kama ki da wannan dukan a fasa miki baki da hanci, tunda kin iya daurin dankwali ai magana ta kare, ladan ya isa haka. Shi kuwa dan Baba zaizo ya sameni wallahi sai nayi mummunan saba masa, sai ya yabawa aya zakinta." Haka nan ta wuni tana mita kamar zata ci babu. Shi kuwa Sadiku yana sane yaki dawowa gidan da wuri sai da ya bari dare yayi ya lallaba kicin dan ya dauki abincinsa, ai kuwa tayo waje daman lambo tayi tace dawa Allah ya hadamu, donma dai ya wuce duka ne da ranar sai yasha duka a gurin Sala, shi kam ko kala baice ba da yaga ba'a ajiye masa abincin ba ya juya ya fice. Ta bishi har zaure tana fadin "Babu zuciyar nema sai ta ci, ita dai wacce ka tsana din ce ke nemo abinda kake ci kuma wallahi ko ruwa ba zaka sha a gidan nan ba, idan kayi zuciya ka siya, wanda na san ko sisi baka da shi baya ga tarin takardu da bakar zuciya." Shi dai dakinsa ya shige ya kwanta ranar haka ya kwana da yunwa, ita kuwa saida ta kusa kwana tana mita. Wannan shine sanadiyyar daya sanya dole aka daina tallar safe, domin dai Sadiku yace duk sanda tayi laifi a daina turata gida tayi noma da wankin bandaki, abinda ta tsana a rayuwarta, ya kuma rantse idan ta daina zuwa makarantar sai ya ballata yaga da kan da kafar da zata yi tallan, dole kanwar naki aka hakura da tallan safe dan ta dinga zuwa da wuri. Da farko Sala tace bata yadda ba amman ganin da rana ma ana samun ciniki mai yawa kuma ita Abu tana tsoron bala'in Sadiku ya sanya dole suka hakura, sai dai su Karima suyi tallan safen kafin su tafi makarantar, amman ita da yake ba irin halinsu daya da Abu ba takanyi hanzari ta saida ta tafi makaranta, domin ita halinsu kusan irin na Sadiku ne shiya sanya basa shiri da Sala sosai kullum tana mata fada da cewar mai kan kwantai. Misalin karfe biyu na rana ta fito daga gidansu dan dakonta yana dauke da fantekar abinci da kwanuka da miya a kansa, ita kuma tana rike da farin bokitin roba mai haske an yanka salak da tumatir da albasa, daya hannun kuma kaji ne soyayyu cikin irin farin bokitin, anyi wanka an ci kwalliya, zanin nan an daurashi kwauri a waje anja jagira lebe yasha jambaki da baki, sai dai anyi kilin an daina dige-dige da kwalli, hatta takalmi dan madina dake kafarta yasha wanki sai sheki yake yi, ana tafe dagwas-dagwas kamar mai jin tausayin kasa, domin tun can daman Abu akwai tsafta da kwalliya balle yanzu da aka fara zama 'yan mata, gwalli da feleke ya karu, duk cikin kawayenta tafi kowa iya tsara kwalliya, daman gata ba baya ba gurin kyau. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 zandakata a nan,insha Allahu Zuwa yamma zamu dora,domindai aikin Littafin yayi bisa,Wata tangarda ce ta hanani farayimuku a ana,nagode.. Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 Idan Zuciya Tagyaru 1-02 Posted by ANaM Dorayi on 05:26 AM, 28-Jan-16 Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU _________________ Na ________Fauziyya D Sulaiman____ Mustafa dake zaune kofar gidansu bisa farar kujera karkashin bishiyar Umbrella, yana karatun jarida kamshin Abu ya bugi hancinsa ya daga kansa da sauri yana dubanta, kusan sati guda kenan yake ganinta tana wucewa irin wannan lokacin, kwarai yarinyar ta kwanta masa a ransa, da kuma dai alamun ba za'a sha wahalar samun kanta ba, kullum yana son yi mata magana amman ya rasa ta yanda zai fara, yau dai dabara ta fado masa dan haka ya fara kwala mata kira. "Ke! Ke mai abinci! Kawo." Ta tsaya turus gami da waigowa tana dubansa, domin bata saba saida abincinta cikin unguwa ba sai ta dangana ga tashar kofar wambai, amman sai taga yayi mata kwarjini ba zata iya kin saida masa ba, domin dai abincinta sai wanda taga dama take saidawa, don haka ta hau kwalawa almajirin dake dauke da abincin kira "Kai Mudi! Kawo abincin za'a siya. Babu musu yayo ribas ya juyo, ya isa gaban Mustafa wanda ke zaune akan farar kujera mai tambarin kamfanin coca-cola ya tsaya kerere. Ta galla masa harara tana fadin "Kai fa tamkar jaki kake komai sai ance kayi zaka yi ko? To sauke kayan." Sannan ta dubi Mustafa tace "Malam na nawa za'a zuba maka?." Yayi wani mayaudarin murmushi yana mata wani duba na yaudara da kwarewa a harkar iya soyayyar 'yan zamani yace "Haba 'yan mata babu ko gaisuwa?" Tabbas yayi masifar yi mata kwarjini, hasalima tunda suka hada ido taji wani abu ya bugi zuciyarta wanda ya sanya ba zata iya yi masa musu ba ko rashin kunya, shi kansa ya gano hakan a kwayar idonta ya kuma san haka nan Allah yayi masa kwarjini da farin jini ga kowa, domin dai da wani ne cewa zatayi, ban iya ba ko kuma tace baka kai matsayin da za'a gaidaka ba din ne, amman shi sai ta tsinci kanta da ce masa "To ina wuni?" Yayi dariya yace "Ko ke fa, lafiya kalau, yaya sunanki ne, dan kallon farko naga kin mini dari bisa dari." Ta kosa da zancan nasa ta daure dai tace "Ka ga sauri nake kada rana tayi mini, na nawa za'a baka? Dan kada kaja nayi kwantai." Ya kuma murmushinsa dake kashe mata jiki yace "Haba dai, ai kyawawa basa kwantai, ko domin kyanki ai a sayi abincinki." "Ka ga nifa zan wuce kana bata mini lokaci, wallahi dan kaine kawai na tsaya." Ta fada tana yamutsa fuska. Ya kanne mata ido daya yace "Haba dai ke kya soma tafiya ban san sunanki ba? domin dai zaman nan naki ne, dan tun randa na fara ganinki Allah ya dasa mini tsiron sonki a raina wanda kullum yake kuma girma, dan haka nake zama kawai naga wucewarki naji dadi. Ta dubeshi cikin ido, yanayin kallon da yake mata ya kashe mata jiki ta gaza masa komai, amman sai ta dubi Mudi da ya baza kunnuwa kamar na zomo yana sauraran abinda suke fada tace "Mudi dauki mu tafi yana bata mana lokaci." Mudi ya yunkura zai dauka amman sai Mustafa ya dakatar dashi yana fadin "Kai ajiye, maza nemo 'yan uwanka almajirai ka raba musu, kyaky-kyawa kamarki ai kin wuce tallan shinkafa, ke fa gimbiya ce." Yana maganar yana dubanta da wani kallo daya bambanta da wanda samarinta kucaku ke mata. Mamaki ya cikata amman sai ta gaza cewa komai tayi shiru kawai tana dubansa. "Kaje mana ka kira 'yan uwanka ka raba musu ka baza kunnuwa ka saki baki sai kuda ke fadawa." Yace da Mudi wanda ya saki kunne da hangame baki yana dubansu. Mudi dai gani yake kamar da wasa yakeyi, amman da yaji ya doka masa tsawa ya kuma nanata masa ya sanya ya fara kwalawa 'yan uwansa kira. "Alalan Alalan almajiri, Alalan Alalan kazoo kaci, Alalan Alalan Alalan kai ba tumatiri." Ai kuwa nan da nan gurin ya cika da almajirai, yace "To maza abi layi." Ya kalli Mustafa dake kallon su. Mustafa yace "Ka rarraba musu mana." Ai kuwa nan da nan ya fara zubawa almajirai kafin kace kwabo sai fanteka da bokitin salad. Abu na tsaye rike da kugu cike da mamaki tana kallonsa, lallai wannan mutumin dan rikice ne, ko tambayarta kudin abincin baiyi ba yasa aka raba, zata yi maganinsa kuwa yau, don wallahi sai ta tsuga masa kudi masu yawa. Ya dubi Mudi yace "To maza a hada kayan a koma gida uwar dakin naka zata taho yanzu." Sai da yaga Mudi yayi nisa sannan ya dubeta na dan wani lokaci tana tsaye rike da kugu da alamun mamaki da shakka a fuskarta. "Adon gari tunanin me kike yi? Har yanzu baki fadi mini sunanki ba." Ta yamutsa fuska tace "Sunana Abu......" "A'a babban suna Zainabu Abu mai tagwayen suna kenan, gaskiya Zainab baki dace da kalar tallah ba, dubeki fine baby ace kina daukar tallah? to gaskiya ni dai daga yau na soke tallar nan." Ta dubeshi a tsiwace tace "Ka ji mu da mutum sai kace wani Ubana? ko kai ne zaka dinga biyana kudin da nake samu eye?" Yace "Eh mana zan dinga biya ko nawa ne, don gaskiya bana son rana tana taba mini kyaky-kyawar fuskarki, kyanki hutu Zainabu." Ta tabe baki don zancen bai gamsar da ita ba, don tasan bai san yawan kudin bane shiyasa yake wani cika baki amman yanzu zata yi maganin firiritarsa. Don haka tace "Ka ga ka cika ni da surutu bayan baka biyani kudin abincina ba." Yayi dariya yace "Haba Zainab, baki yarda dani ba naga alama, ko don kin ganni da dan wando jeans da shet? kin san mu 'yan boko bamu san kaya masu nauyi, amman nawa ne kudin? Kila idan na baki hankalinki yafi kwanciya." Ta murguda baki wanda ya zame mata kamar al'ada sannan tace "Dari uku da ashirin da biyar ne, sai nama na naira talatin da biyu...." "A'a Zainab, duka zaki hade mini?" Tayi dan duru-duru don tasan zulake tayi duka kayan nata basu wuce na dari biyu da tamanin ba, don haka ta kasa hadewa ta fadi don bata iya lissafi ba (bata da Maths tab akin yara), da ya fahimci halin da ta shiga sai ya zura hannu a aljihunsa ya debo 'yan murtala (Naira Ishirin) har na dari hudu yace, "Ga dari hudu ma ni na kara miki." Mamaki ya cikata matuka, hannunta har rawa yake yi gurin karba don tana ganin kamar zai maida yace ya fasa ne. Sai da taji dumin kudin a hannunta sannan hankalinta ya kwanta ta dube shi da mamaki tace "To nagode! Zan tafi gida." Yace "A'a ai dole na yiwa gimbiya rakiya ko don naga gidansu." A wannan karon bata yi masa musu ba don yayi mata ba zata, don haka suka nufi hanyar gidansu, a kofar gida yayi mata sallama yace sai gobe tace Allah ya kaimu. Ta shiga gida da gudunta Sala na zaune tayi tsuru cike da shakkun labarin da Mudi ya bata, gaskiya tafi zargin bari kawai suka yi yace wani wai juye wani saurayi dan gaye yayi mata. Abu na shigowa ta mike da zakuwa tace, "Ke maza sanar dani menene ya faru?" Abu tayi dariya gami da nuna mata kudin da saurayin ya bata, ta fizge daga hannun Abu da azama ta hau kirgawa, Abu kuwa sai dariya takeyi. Sala ta kammala lissafawa ne ta dubi Abu cike da farin ciki tace "Diyar arziki yau kuma wane mai arziki kika hadu dashi? Kai wannan diya da kan arziki kike, shi ya sanya aka tsangwameki a unguwar nan, ki dubi yadda su Sarai da Sakina kawayenki suke kwantai kullum sai sun dawo da ragowar abinci, sai dai a cinye ko kuma akai dakalin 'yan kwantai da daddare abincin naira biyu a karyar dashi naira daya koma sis daya. Abu tace "Bari ke dai Sala, ni tunda nake ma ban taba haduwa da mutum mai ban mamaki irin wannan ba." Sala tace, "Yaya ne sunansa?" Ta tabe baki tace "Oho!!! Ni ko tambaya ma banyi ba." "Kiji sokuwa, arziki yana kiranki kina masa kutufo, to gobe ki tambayi sunansa kuma ki saki jikinki dashi, kin san su irin wadannan basu son ki dinga dari-dari da su, idan abin ma gaba daya....." Abu tayi dariya gami da shigewa dakinta. … Allah ya shirya. Washegari ma haka ce ta faru, Mustafa yayi mata juye ya rako ta gida, sai dai wannan karan ya tsaya sun dan taba hira duk da ya lura sokuwa ce sam bata waye ba, da kuma alama girman jiki ne kawai da ita babu shekaru, sai dai ko menene shi dai yaji ya gani yana kuma so a haka. Yau da gobe sabo da shakuwa ya shiga tsakaninsu har ya zama an daina fita da abincin ko ina sai dai a bawa almajirai a gida. Abu an daina fitowa kamar yadda Mustafa yace bai son kyaky-kyawar fuskarta ta baci da zafin rana don haka tana gida kullum. Wani abu kuma da Mustafa ya koya mata shine cin dadi, yanzu abincin kala-kala take ci ba irin wanda take ci ada can ba, ga kaya da yake kawo mata na kwalliya da na sanyawa, sai ga Abu ta kuma futowa fes da ita kuma yanzu da motar Babansa ma yake zuwa zance gurinta ko ta Mamanshi don haka cikin motar suke zancensu. Ta futo daga wanka tana tsakar gida bisa tabarma da kayan kwalliya a gabanta ana ta kwalliya da hasken wutar nefa, dan Mustafa na gab da zuwa, Sala ta zauna daga bayan ta tana kallonta cike da murmushi tace, "Kai diyar nan wallahi akwai ki da kwalliyar daukar ido, dubeki kamar wata sarauniya. Ai ba don bamu gama cin kudin ba da kin auri yaron nan don ya dace dake, ga kyau ga kudi, sai dai na lura kamar dai iyayensa ne masu kudin ba shi kansa ba ko?" Abu ta tabe baki tace, "Oho! Ni ban sani ba, ke idan banda abinki ma Sala yaushe na isa aure? Ni yanzu ma sai nayi digiri, don Mustafa yace mace idan tayi ilimi wai tafi kyau da tsada. Ni fa yanzu Sala dan-na-sanin talla ma nake yi, ki dube ni ki gani yanzu kamar wata diyar wani basarake." Sala tayi shewa gami da rangada guda tace, "Kai Allah nagode maka, ai abinda nake ta nusar dake kenan tun da can, ki sami samarin da zasu dinga kashe miki kudi mu huta da tallan, yanzu ba gashi munyi kyau ba? Ga kudi suna shigowa, wannan shegen yayan naki yana saka mana ido." Ta ja tsaki, "Mtsw! Wallahi idan ya sake sai nayi masa baki, wai har ni zai kalli idona yace mini sai Allah ya tambaye ni duk abinda muke aikatawa, wai don kina zance a mota, wai 'yan unguwa sai zarginki sukeyi gashi kin daina talla ma a ina kike samun kudi yanzu? Nace a gidan ubansa. Sai fa da nayi masa wuta-wuta sannan na samu ya fice daga gidan nan, kuma nayi masa barazanar duk randa ya kuma shiga shirginki sai na tsine masa, idan muka biye ta tashi zamu rayu ne? Da yanzu mun mutu, Mtsw!" Ta kuma jan tsaki. Abu ta hasala ta murguda baki gami da tsiro shi gaba tace, "Ki fita harkarsa kawai Sala, na lura talauci ne ke damunsa, kuma wallahi yayi sa'a shi yayana ne da wallahi 'yan sanda zan dauko masa." Sala tace, "Ai bake ba ni kaina ba don gudun abin kunya ba da saka ido irin na tsinannun mutanen unguwar nan, da wallahi sai na hadashi da 'yan sandan sun lallasa mini shi." Sallamar da wani yaro yayi ce ta katse musu hirar tasu tamkar wasu kawaye, su kuwa sauran kannan nata duk sun bazama tallar gyada a can kofar gida. "Kai!! Meye ka ishemu da sallama?" Sala ta katse shi cike da haushin katse musu hirarsu da yayi ba tare da ta kai aya ba don ko amsa sallamar ma bata yi ba. "A'a daman wani ne a mota ke sallama da Abu..." "Au! Yi hakuri na hauka da fada, kace tana zuwa dan albarka, ka ji?" (HMMM) Yaron ya fice yana fadin to. Ta dubi Abu da ta mike ta nufi daki don sanya kaya tana dariya tace, "Yau dai naga kwalliyar nan ta daban ce, kiyi sauri kada ki bata masa lokaci." Ita dai bata ce komai ba ta shirya ta fito sai kamshi take yi, kai tsaye ta fice ta nufi gurin da Mustafa yake, yana hango ta ya bude mata gaban motarsa wato kusa dashi sai wani malalacin murmushi yake mata na tsananin yaudara irin na gogaggun samari, ita kuwa sokuwar sai wani kara zobara baki takeyi tana wani yauki har ta shiga ciki ta zauna tana wani fari kamar 'yar tsana. Ya shaki kamshinta gami da lumshe ido, cikin mayaudariyar muryarsa yace, "Kai Zainabu, kin yi kyau kamar wata sarauniya." Tayi dariya cike da jin dadi tace, "Haka ma Sala tace wai nayi kyau sosai." Yayi murmushin jin wautarta, Ya riga ya gama karantar halin Abu da Sala, don haka ya san ba zai sha wahala gurin samun hadin kan Abu ba, don haka ya mika hannuwansa ya kamo hannun Abu yana wasa dashi yace, "Kai yatsunki akwai ban sha'awa, dube su zara-zara. Dadi ya kuma cika ta na yabon da yake mata tace, "Haka kowa ke cewa, wai yatsuna da na hannu da na kafa suna da kyau kamar ba nawa ba." Yayi dariya yace, "Gaskiya haka ne, amman kyanki ai yaci suma suyi kyau." Cikin dabara ya jata jikinsa yana fadin, "Ya dace dai yau na shaki kamshin nan naki da kullum ke ruda ni." Ga mamakinsa sai yaga Abu ta saki jikinta har ma tana kokarin taya shi, abin ya bashi mamaki don yayi zaton sai yasha wuya zai sami kanta, sai gashi ya same ta a ruwan sanyi, amman sai ya danne ya dinga aiwatar da mugun nufinsa da zuciyarsa ke ingiza shi. (Allah ya kiyashe mu da aikin assha. amin). Da ya tabbatar ba zai sami wata matsala da Abu ba, sai ya lankwashe murya yace, "Abu ko zaki rakani wata 'yar unguwa?, daga can kin ga sai mu wuce nayo miki siyayya ko?" Tace "Babu damuwa muje kawai." Ya dubeta ta dan hasken dake cikin motar na farin wata da ya shigo yace, "Kina ganin babu matsala idan Sala ta aiko bata ganki ba? dan kada tayi fada." Ta tabe baki tace, "Kada ka damu ba zata ce komai ba tunda dai ta san siyayya zaka yi mini, kuma ta san ai muna tare." Yaji dadin abinda tace dan haka ya tada motar gami da karo sautin wakar dake fita a cikin rediyonsa, muryar Bob Marley ce a wakarsa ta One Love, duk da Abu bata jin turanci wakar tana mata dadi musamman da yake koda yaushe za kaji kaset din Bob Marley Mustafa ke sanyawa, har ma ta iya bin wakar tana girgiza kai duk da ba daidai take fadin wasu kalmomi ba. Suna tafe a hanya suna hira har suka isa wani hotel, kasancewar kaurin sunan da hotel din yayi baka ganin jama'ar kirki a cikinsa domin kada sunansu ya baci, wannan ya kara baiwa 'yan iska damar cin karensu babu babbaka, gurin shiru babu alamun jama'a, sai ka shiga daga ciki zaka ga kamar tsakiyar rana ce dan haske da tashin kida. Ya dubi Abu yana murmushi yace, "Zainabu ya dace mu dan tsaya a nan musha lemo mu huta, kafin na wuce yi miki siyayyar domin har dan kunne da sarka na gwal zan sai miki, kema ki shiga sahun manyan mata ko?" Yana mayaudarin kallonsa yake maganar. Tayi dariya cike da jin dadi tace "Babu damuwa." Ya sami guri ya faka motar tasa, ya bude ya fito sannan ya bude mata ta fito suka jera, Abu jin kanta take yi da girma saboda ta fito daga mota, a ganinta ta gama cinyewa. Sanda suka isa cikin reception din hotel din sai ta kama zare idanu cike da kauyanci, domin tunda take bata taba ganin guri mai kyawun wannan ba, ta saki baki galala tana kallo ga hasken wuta ga fankoki suna juyawa ga A.C da Tibi, ga 'yan mata nan kala-kala kowacce da shiga ta rashin mutunci, sai taji ta raina kanta, lallai ta yadda da Mustafa da yace zai nuna mata rayuwar 'yanci da wayewa, gashi kuwa ta fara gani. Sai ta kama muzurai kamar ta koma gida ta sanyo atamfarta Wagambari da tafi kowacce kyau da tsada, amman sai taga ai ko ta sako ba zata yi kyawun wadannan ba, ta shagala da kallonsu tana fadin dama itace wannan, can kuma idan taga wata sai taji tafi waccan tace, kai waccan zan zama, shi kuwa yana can yana biyan kudin dakin da zai kama musu. Ya kammala ya amshi makulli ya nufe ta, sai yaga sam hankalinta baya tare da ita har hannu take sanyawa tana taba duk abinda ya burgeta, ya kama hannunta suka nufi dakin da ya kama musu. Sanda suka shiga dakin kuwa sai labari ya sha bamban, sai taga ai can wajen ma ba'a sanya komai na more rayuwa kamar nan ba, ta fada kan tumemiyar kujerar dake falo da karfi tana fadin, "Kai bari muga za ta loma kuwa?" Ta saka wata dariya ganin ko motsi sosan baiyi ba, can idon ta ya hango mata wani gilas dake dauke da ruwa da kifaye da wasu 'yan kananan bishiyoyi, ta mike da sauri ta isa gurin, ta saki baki tana kallo da shafawa, can ta kuma fashewa da dariya tana fadin "Wallahi kifin da ransu kuma yawo suke kamar a teku." Shi kam Mustafa yayi tsaye yana dubanta, hannuwansa cikin aljihu yana dariya saboda ganin irin kauyancin da take yi, lallai ya kuma tabbatarwa Abu sokuwa ce mara wayo, sai dai rashin kunyar, domin da ace tana da wayo ba zata yi wannan kauyancin ba, ko kuma dan bata da wasu shekaru da yawa ne? Can ya hango ta tana kiciniyar bude wata kofa sai turawa take iyakacin karfinta. Ya karasa yana dariya yace "Dakin bacci ne, bari kiga yanda ake budewa." Ya kama marikin kofar ya murda a hankali sai gashi ta bude. Ta kuma bude baki cike da mamakin ganin wani irin katon gado kuma dan karami ba irin na Sala mai rumfa ba, ta nufi gadon da gudu tayi tsalle ta fada tana kyalkyala dariya har da rike ciki tana kuma birgima. Can kamar wacce aka kuma tsikara sai ta kuma mikewa da sauri saboda hango wata kofa da tayi ta san lallai wani abin kallon zata kuma gani, wannan karon bata sha wahala ba ta bude domin taga yanda ya bude waccan, ta rufe bakinta cike da tsananin mamaki taca cewa "Na shiga Uku ni Abula, menene wannan kuma?" A cikin kunnenta taji yana mata rada, "Wannan bandaki ne gurin wanka irin na 'yan gayu, idan kina son irinsa zan gina mana." Ta juya tana dubansa da mamaki dan bata yarda da abinda yace ba, yaya ma za'a yi aga bandaki a cikin daki kuma ga wasu irin abubuwa a ciki kamar daki ma? Ya daga mata kai alamar haka ne da gaske, ta nufi gurin kwamin wanka ta shiga sai ya sakar mata shawa, ta firgita ta fito da gudu tana ihu,ta kankame shi domin ta firgita, ya fashe da dariya. Lallai Unguwarsu da manyan gidaje amman bata taba shiga ciki taga yanda suke ba, domin ita kam bata iya jure wulakanci ko kaka yake, su kuwa 'ya'yan masu kudin unguwarsu wulakanci ne dasu, sam basu kula su ko fita zasu yi ma sai dai a mota, shi kansa Mustafa sanda ya fara cewa yana sonta tayi mamaki sosai, sai daya dinga yi mata kalamai masu dadi da yaudara sannan ta yarda, har yana cewa shifa so babu ruwansa da mai kudi da talaka duk yana shigarsa, da haka ya samu kanta dan wani lokacin har mamakin kanta take yi data afka son wanda ta tsana a da can. Tasha yiwa motocin jama'a faci domin ta tsani gudun da sukeyi a layin suna kade kaji da akuyoyi wani lokaci harda mutane, idan anyi magana sai su biya dan suna da kudi, sai da takai duk kofar gidan da aka ganta sai an koreta domin idan ta kullawa mutum duk sanda taga mota a kofar gidansa koda ta baki ce sai ta koma gida ta dauka kibiya ta kitso ta sossoka a tayoyin, dan masu gadin da sun ganta zasu bita da bulala. Ya janye ta yana dariya saboda yanda ya ga ta tsorata yace "Bari naje na samo mana abinci da dan ruwan lemo." Bata ce masa komai ba illa tafiya da tayi gurin wani abin tana tabawa. Ya dawo dauke da wani katon faranti mai dauke da abinci da manyan kwalabe na giya (wa iyazu biLlahi) ya ajiye bisa tebur din dake falon kana ya shiga ya kirawo ta, da kyar ya samu ta baro bandakin tana cewa ya tsaya tana kallo, yace In dai kina son kallon kullum zan dinga kawo ki." Dadi ya cikata, da wannan dabarar ya samu ta futo. Abinci ya mika mata mai dauke da naman kaza zuku-zuku, ta amshe kuwa da azama ta fara ci, shima yaja nasa farantin yana ci yana kallon ta yana dariya ,Can ya dauko kwalbar Shandy dinsa ya bulbula a kofi ya kafa kai ya kyankyama ya dire kofin. Ta dubeshi da mamaki a tsorace tace, "Kai Musty (haka take ce masa) Giya ce fa? ba zata bugar da kai ba? Naga dan tasha idan ya sha yayi ta maye har kwata yake fadawa." Yayi murmushi gami da lumshe idanuwansa kana ya bude a hankali, "Ai shi karamar giya yake sha wato burkutu shi ya sanya yake maye, amman wannan original ce wato mai kyau din ce, bata sanya maye bari na zuba miki ki sha kiji." Ta manne kafada da sauri tana fadin "Kai bana sha tsoro nake ji ni dai." Yace, "Haba dai tawan don Allah kisha wallahi ba zaki bugu ba sai dai kiji karfi." Da kyar ya samu ta sha kofi guda, can kuma sai ta wawuro kwalbar ta kafa kai ta dinga kyankyama, ta dire kwalbar bisa tebur din. Ya fashe da dariya gami da tafa mata yana fadin Wonderful, wato mamaki ta burge shi, ya zira hannu cikin aljihunsa ya zaro tabar shedan wato wiwi) ya kunna ta ya zuka kana ya mika mata, wannan karon batayi gardama ba ta amshe da azama ta zuka domin bata cikin hayyacinta, sai dai zuka daya ta kware ta kama tari, ya tashi da sauri ya nufe ta yana rike ta har tarin ya lafa. Amman don ta saba maimakon ta hakura sai ta kara zuka don abin ita sha'awa ma ya bata, don ta dade tana sha'awar yanda ake shan taba musamman idan taga wanda ya kware mai fesar da hayaki ta baki ta hanci. Dadi ya kama Musty sai ya kuma zaro wata cikin aljihunsa ya kunna ta ya hau zuka. Ta fashe da dariya karan tabar na tsakiyar yatsunta guda biyu shima ya taya ta suka dinga dariyarsu da zukar tabar shedan din har suka gama, sannan ne kuma Abu ta soma tangadi tana zage-zage da yarfe hannuwa. "Wallahi karya ne! Babu wani sauran shege da zai raina mana hankali wallahi! Ha-ha- ha." Ta fashe da dariya. Ya isa inda take da azama yana fadin "Kwantar da hankalinki yarinya." Ta fada jikinsa shabar tamkar kayan wanki, ai kuwa ya sami yanda yake so don haka ya shiga aiwatar da mugun nufin da zuciyarsa ke kintsa masa, da fari bai samu matsala ba sai da abu yayi nisa data fara jin zafi sannan ta nemi kwace kanta, amman da yake a buge take hakan bai samu ba har sai da ya cimma burinsa a kanta (Wa'iyazu billahi). Duk irin iskancin Abu da gantalinta namiji bai taba aike mata kai tsaye ba don tana tsoro da gudun kar aji mata ciwo, ko su Dan Oga da dan tasha da suke siyan abincinta, basu taba samun hadin kanta haka kai tsaye ba sai Musty, yau ya samu daga sama don haka shine mutum na farko da ya fara sanin Abu diya mace, abunda ba zata taba mantawa ba a kundin tarihin rayuwarta. A nan bacci ya dauke su don duk cikin su babu wanda ke cikin hayyacinsa. Basu ankara ba sai da gari ya waye tangararau, sannan suka farka a firgice Abu ta saki kuka da ta tuno abinda ya faru a daren jiya, shi kuwa Musty kwantar da kansa yayi ya dinga bata hakuri harda guntun hawayensa, karshe dai yayi mata alkawarin kaya da zai sai mata kala-kala har ya samu ya shawo kanta don ya lura muguwar kwadayayyiya ce, ya samu ya lallaba ta ya hada mata ruwan dumi cikin bahon da tayi kauyanci daran jiya ta shige ciki. Shigar ta bandaki da kuma tuno irin alkawarin kayan da yace zai siyo mata ne ya faranta ranta har ma ta daina ganin aibun abinda suka yi din, don haka da kwarin gwiwarta ta fito shima ya shiga don ya shirya. Sanda ta kammala shiryawa ne gabanta kuma ya soma dafuwa tana tunanin me zata ce da Sala yanzu don ta Babanta sam bata jinsa, domin sam ba zai lura bata gidan ba, domin bai shigowa gidan sai dare ya raba, haka nan daga gurin Sallar Asuba yake wucewa majalisarsu, idan ka ganshi a gida da rana to lallai Alhazan da suke wa a dawo lafiya sun kawo musu zakka zai zo yaci abincin rana a kudinsa, yakan ce sai ya ci guminsa wai, sai kuma jarababban yayanta da take tsoro kada ya gane bata kwana a gida ba. Ya fito shima ya gama shiryawa, ya dubeta sanda suke karya kumallo sai ya ga ranta har lokacin a bace yake, gabansa ya shiga faduwa domin shi yanzu ma yaji ya fara sonta, don haka ya kwantar da murya ya kamo hannunta yana fadi, "Wayyo masoyiya ta, mene ne? Har yanzu fushin ne? Ko baki huce bane?" Yanda yake maganar ya kashe mata jiki, ta dinga jin soyayyarsa da kaunarsa suna ratsa jikinta, ga wani shaukinsa, ta kwantar da kai tace, "Wallahi na huce, ina dai tunanin yanda zan sanar da Sala ne, don ka san ban taba kwana a waje ba." Ras! Ras! Shima gaban sa ya fadi don sai yanzu ya tuna ya fito da motar Mominsa gashi ya kwana, me zai ce mata yanzu? Lallai yasan zai sha fada a gida, amman sai ya dake domin dai yanzu matsalar Abu ce a gabansa. Ya kuma kwantar da murya yana wasa da hannunta yace, "Kada ki damu za muje nayi miki siyayya ta ban mamaki wacce zata faranta ran Sala din, na san ba zata yi fada ba muddin taga kayan, ga kuma kudi da zan baki, kada ki damu kinji ko?" Tayi ajiyar zuciya gami da cewa, "Shi kenan." Wani katon kantin sayar da kaya suka je. Bayan sun shiga yace ta zabi duk abinda take so. Lallai kam yaga hauka domin dai haka ta dinga jidar kaya kala-kala tana sanyawa cikin dan keken da suke turawa har sai da taga babu gurin da zata sa ta hakura, dan wani abun ma sam bata san amfaninsa ba take dauka, in dai taga kwalin yayi mata kyau to an gama, domin har abin aski na maza sai da ta dauka, shi dai binta kawai yake yi da kallo cike da mamaki, amman bai ce komai ba domin dai lallaba ta yake yi kada yayi magana yayi laifi. Da suka isa gurin biyan kudin aka lissafa aka gaya musu, kudin tsababa ne amman shi ko a jikinshi domin dai yasan ta cancanci ya sai mata abinda yafi haka ma. Ita kuwa 'yar jidalin wani kallo tayi wa mai karbar kudin tana fadin, "Kai malam dan wannan kayan ne zaka tsugawa wannan kudin wanda yafi na buhun shinkafa 'yar gwamnati? Kawai kayi mana ragi idan ba haka ba mu fasa saya wallahi." Ta karasa maganar tana tafa hannu da doka cinya. Kunya ta kama Mustafa dan dai ta nuna cikakkiyar 'yar kauye ce ita wacce bata taba zuwa irin wannan wajen ba. Ya dubi mai karbar kudin sanda yake ajiye masa kudin yace, "Ka yi hakuri daga kauye aka kawo ta." Cikin harshen turanci yayi maganar dan haka sam bata ji abinda yace ba. Mai karbar kudin yace "Babu damuwa." Tana kallo ya biya kudin don ma kada tayi magana ya kama hannunta suka fice yana fadin ma'aikatan su biyo shi da kayan, kamar jira ake su fita sai wadanda ke gurin suka kama dariya. Tana daga can ta hango suna mata dariya dan haka ta kutuntuma wani zagi tana fadin, "Lallai ma wadancan mutanen 'yan rainin wayo ne, ni sukewa dariya? Wallahi bari naje nayi maganinsu." Ta nufi gurin nasu da sauri. Ya riko hannunta yana fadin, "Haba Zainabu na kada ki mai da kanki 'yar kauye mana, ki zama wayayyiya." Tayi kwafa tana dubansa tana huci tace, "Wallahi sunyi sa'a da yau sun gane kurensu, ni kawai ka fasa siyan kayan ma ka bani kudin kawai na rike abuna." Yayi murmushi yace, "Don Allah kiyi hakuri in dai kudi ne zan baki." Da haka ya lallaba ta suka saka kayan a mota suka wuce gida. Bayan sun shiga motar ta turo baki gaba tana fadin, "Gaskiya wadannan mugaye ne, dan wannan kayan zasu ce kudinsu kenan, wallahi zai sayi buhun shinkafa har da na wake ma, kai zai iya kai mutun Makka da Madina ma." Dariya ta kwace masa har yana dukan sitiyari yace, "Kai Zainabu akwai ki da wauta wallahi, koma dai nawa ne yawan kudin ai kinfi karfinsu a gurina, fatana dai kawai ki dinga bani hadin kai, zaki zama tauraruwar mata gagara-gasa a cikin unguwarku, zaki zama abin kwatance." Ranta yayi fari kal! Amma bata ce komai ba har suka isa kofar gidansu ya tsaida motar. Ta dubeshi bata ce komai ba amman ya lura da fargaba take yi dan haka yace, "Kin ga kada ki damu tsaya kiga dabarar da zamu yi." Ya bude motar ya fito ya kirawo wani yaro yace maza ya shiga da kayan cikin gida zai bashi lada, nan da nan yaron ya fara jidar kayan yana shiga dasu cikin gida, su kuwa suka cigaba da hirarsu, har saida yaron ya gama shiga da kayan ya sallame shi. Ya dube ta da salon da yake kashe mata jiki yace, "Yaya dai Zainabu ina fatan babu matsala." Bai jira ya ji abinda zata ce ba ya zura hannu cikin aljihunsa ya zaro wata sabuwar ambulan mai dauke da sabbin murtala (N20) ya mika wa Abu yana fadin, "Ga wannan kyautar faranta mini rai ce, sai da daddare idan na dawo." Ta fizgi kudin da sauri kamar wani ne zai kwace, ta bude murfin motar babu ko sallama ta fada gidansu da sauri. Ya girgiza kai cike da dariya sannan ya tuka motarsa ya nufi gidansu amman gabansa na faduwa dan bai ma san irin karyar da zai shirya ba. Abu ta fada gidan babu ko sallama kamar wacce aka hankada, a tsakar gida ta tadda su Sala da kannanta suna kallon kayan da aka shigo dasu, fuskar Sala cike da annuri. Tana shigowa Sala ta mike da azama ta rungume ta tana fadin "'Yar albarka, jiya sam banyi bacci ba na dinga darura da sake-sake ko 'yan yankan kai ne suka yi gaba da ku, sai yanzu da naga ana shigowa da kayan nan hankalina ya kwanta nace na san dare ne yayi muku a inda kuka je kuka ki dawowa saboda 'yan sa ido, ai gwara da kika kwana a can din ma dan baki ga yadda jarababban yayanki ya dinga sintiri ba, sai da nace masa kina daki kina bacci sannan ya hakura ya kwanta, shi ya sanya na dinga fargaba kada ki dawo ki buga kofar yaji ya hau surutu da wa'azin nashi tamkar dan sarkin Limamin Makka." (Kuji fa irin wannan Uwa, wacce ya dace a ce hankalinta ya tashi saboda kwanan da diyarta tayi a waje amman ko a jikinta saboda tsabar kwadayi da son duniya, Allah dai ya shirya). Abu kam da taji abinda Sala ta fadi sai taji hankalinta ya kwanta, don haka ta share karya da ta shirya da zata fada, cewar wai mota ce ta lalace musu a hanya da suka dawo daga siyo wadannan kayan, sai da gari ya waye sannan suka sami masu gyara. Sai kawai ta dauko kudin da ya bata na ambulan tana fadin "Sala har da kudi fa ya bani." Sala ta amshe da sauri ta kama kiciniyar farke ambulan din ta hau kirgawa, Naira dubu biyu cif! Nan fa suka kama tsalle da murna Sala tana fadin, "Kai wannan yaro dan arziki ne, dan haka Abu ki rike shi da kyau, Ubangiji ya sanya ya gama da duniya lafiya." Haka nan suka dinga murna, ranar nan dai ko abincin sayarwa Sala bata dora ba. ga Abu kuwa wannan daurin gindi da ta samu daga gurin Sala shine ya kaita ga fandarewar da duk wanda yake da hannu gurin lalacewar tata sai yayi da-na-sani wata rana, rana mara alkhairi a kansu gaba daya, da-na- sani mara amfani. (ALLAH YA KIYASHE MU DA SHARRIN SON ZUCIYA, WANDA BAHAUSHE YACE “BACIN ZUCIYA” Ameen) KANO: 22|12|1993 Rayuwar Abu gaba daya ta sauya daga fari zuwa baki, idonta ya kuma budewa da harkar banza, domin wannan dan lokacin ta iya shan tabar shaidan ta hanci ta baki, sannan kowane dare kai wata rana ma har da rana Mustafa sai ya zo ya dauketa sun tafi hotel sun sheke ayarsu. Amman fa a wannan dan tsakanin sun sami kudi mai dama a jikinsa, wanda duk iyakacin shekarun da Abu tayi tana talla basu samu ba, karatunta na boko kam sai dai muce sam barka, domin Mustafa mai son ilmi ne dan shi ma dan boko ne, dan ya kan sanar da ita irin yanda mutum kan zama idan yayi karatu, yana zama wani a duniya. Karatun allo kuwa tuni ta watsar, Malam yayi hargagin a banza dan ba sai ya ganta ba ma sannan zai doka ba. Sai dai kullum tayi wanka taci kwalliya tana taku daidai a unguwa, su Larai duk ta raina su yanzu idan tayi kwalliya takan zagaya su tana musu yanga idan sun dawo daga tallah. Baba Abubakar ma sanda ya isa da fuffukarsa da Malam ya sanar dashi halin da Abu ke ciki, ya shiga gidan da fuffukarsa yana yiwa Sala korafi. "Yanzu Sala ba zaki dinga tsawatarwa da yarinyar nan ba tana neman ta jawo mana magana a unguwar nan, kina kallonta....." "Kai Malam rufe min baki!" Sala ta katse shi, ta dora da cewar "Kai har wani namijin arziki ne da zaka zo kana mini wata maganar banza, to tsaya kaji na gaya maka, wallahi babu shegen da zai takura wa Abula a garin nan, tun da dai ba Uban wani ya haifar mini ita ba, kuma Uban wa muka je muka ce ya taimaka mana da abinda zamu ci? Ko uban waye ke ciyar damu? don haka babu wanda ya isa yace mata 'yar iska na kyale shi. Shi kansa Malam din da yake wannan fuffukar 'ya'yan nasa ba karatun boko suke suna sheke ayarsu a can ba? Har makarantar kwana sukayi fa, don ni Allah ya bani yarinya mai kashin arziki za'a saka mu a gaba? To wallahi ba'a isa ba, kuma daga yau idan ka kuma zuwar mini da irin wannan maganar sai ranka yayi mummunan baci, soko sobarodo da baka yin maganin sisi, sai yau zaka hau ni da fada." Duk da tsananin hakuri irin na Baba Abbakar sai da ransa ya baci da tijarar Sala yau, ya dubeta a hasale sanda ta diga aya yana fadin "Au dan na gaya miki gaskiya shine kike mini wannan tijarar? Wato dan kinga bani da shi ko? Don da ina da shi baki isa kiyi mini irin wannan rainin hankalin ba, dan haka ki shiga taitayinki, idan ba haka ba ranki zai yi mummunan baci wallahi Salamatu." "Ahayye ayyururuuuiii!" Ta rangada guda da tafa hannu sannan tace, "Lallai yau mazantakar za'a nuna mini kenan ko? To tsaya kaji Abbakar, wallahi baka isa ba, ka yi kadan, idan kuma kayi wasa a cikin daren nan sai mu baiwa hammata iska." Ta kama cin damara da wani zani dake yashe a gefenta tana wani girgije-girgije da buga kafa. (Tambaya: wai shin akan samu masu irin halin Sala a wannan Zamanin kuwa????) Ya fi kowa sanin halin Sala, don a shekarun baya gidansu kamar silima yake gurin kallon dambensu, sai dai shi da jarabar ta ishe shi ya sallama mata, don haka yanzu ma ba zai iya biye mata ba, don haka yabi lafiyar gadonsa na karfe yana fadin, "Kanki ake ji, wai mahaukaci ya fada rijiya, da girmana da 'ya'yana aga muna raba hali a titi, ki yi da wani ba dai dani ba." Ya runtse idonsa duk da ba bacci yake ba. Ta ja dogon tsaki gami da fadin, "Oho dai! Kai dai kawai kace ka ji tsoro, wallahi da ka tsaya da ka gane kurenka yau, munafuki kawai wanda ake gulmar 'ya'yansa da shi maimakon ya hana sai maya kara tunzira abin." Ta haye gadonta na katako tana cigaba da mita, "Ba ku da aiki sai zaman gindin bishiya kuna gulma, sam ba a iya juya kwandala ta koma Naira, ba don Allah ya bani mata masu daukar min tallah ba ai da nasha haushi, ka dubi wannan yaron da ya kwaso matacciyar zuciya irin taka, idan don taku ne sai dai yunwa ta kashe mu." Haka nan take ta bala'in ita kadai, shi dai bai kula ta ba har bacci yayi awon gaba dashi don dare ya tsala, domin bai shigowa gidan da wuri sai dare yayi sosai. Duk yaran nasu suna jiyo abinda suke yi amman basa fahimtar maganar da suke yi sai dai hayaniya kawai da suke ji, Sadiku yafi kowa tashin hankali don tun yana yaro yake takaicin abinda iyayan nasa keyi don ma abokinsa Zaid na bashi baki. Sai dai addu'a al'amarin nasu, lallai ba a sakewa tuwo suna, haka nan ba'a sauya iyaye, shi kam da tuni ya sauya da ace suyo su ake yi, domin kowanne da tabonsa. Sala masifaffiya mai shegen son kudi da abun duniya da son 'ya'ya, yayin da Baba Abbakar ya kasance mai matacciyar zuciya da gulma da munafurci, don sana'arsa kenan kullum yana gindin dirimi shi da abokanan sana'ar ta shi (magulmata) suna ta sana'ar tasu, bai saida komai balle ya sanya ran zai samu ya kaiwa iyalansa, 'yar sana'ar tasa ta saida shayi ya watsar tuni zuciya ta mutu, sai dai gulma a gindin dirimi. Don haka a cikinsu akan rasa na zaba, shi dai yana godewa Allah da ya sanya bai dauko halin ko daya ba a cikinsu, amman dai yana takaicin irin rayuwar da 'yan uwansa da iyayensa ke yi, don haka ranar da bakin ciki da takaici ya kwana, amman yayi alkawarin zai yi maganin abun da kansa, koda kuwa Sala zata tsine masa ne Allah dai yaga niyyarsa. ******************* Karfe takwas na dare Mustafa ya tsaida motarsa a kofar gidansu Abu, ya tura yaro ya kira masa ita, kusan tare suka futo da yaron taci uwar kwalliya da atamfa mai barewa, tayi daurin Hindu Rufa'i, ana wani tauna cingam wai ita dole ga 'yar gayu, leben nan ya sha jambaki a sama baki da kasa, an ja jagira mai cin birki a gefen kunne. Ta hasken wutar lantarki ya hango ta kamar ya yi dariya, don kwalliyar tata kamar 'yar kauye tayi mata, sai ya dake don kada ya tsokanowa kansa don yasa halin tsiwar Abu. Ta isa ta bude gaban motar aka zauna irin a karkacen nan ana wani fari da ido wai ita a dole ga 'yar gayu. Ya kamo hannunta yana dariya kasa-kasa yace, "Kai gimbiya, kin ga yanda kika yi wani kyau kuwa? Irin wannan kwalliya ai sai....." Finciko ta da aka yi ne ya sanya shi yin shiru cike da mamaki da razana. Sadiku ne ya finciko ta ya watsar a tsakiyar titi, sannan ya kalli Mustafa dake kallon sa sororo cike da mamaki yace, "Kai dan iska mara mutunci wallahi daga yau na kuma ganinka a kofar gidan nan sai nayi maka rashin mutunci, don haka ka ja tsummar rayuwarka ka bar kofar gidan nan tun ba sanya yara sun maka atile ba." Ya juya kan Abu wacce ta mike tana goge jikinta wai ita nan ya bata mata kwalliya, sai murguda baki take yi tana kun-kuni wanda ya san zaginsa kawai take yi, ai kuwa yayi kanta ya zabga mata mari sannan ya sanya kafa ya haure ta. Ta zube a kasa gami da rike cikinta ta fasa ihu gami da fadin, "Wayyo Sala na shiga uku!" Ya kuma kai mata duka amman ta yunkura ta mike ta kwasa da gudu ya rufa mata baya da bel din wandonsa da ya zare. A soro suka ci karo da Sala wacce ta futo a gigice saboda jiyo ihun 'yar lelenta da tayi. Ai kuwa Abu na ganin Sala din ta zube a soron tana fadin, "Wayyo Sala na shiga uku zai kashe ni cikina Sala, zan mutu na shiga uku (Kuji Makirci). Sala tace "Na shiga uku, wane shegen ne ya taba mini ke Abula?...." Shigowar Sadiku yana huci ne ya sanya ta gano abinda ya faru. Sala ta zaro ido waje cike da bacin rai tana fadin, "Lallai ka cika mara mutunci, yarinyar tana zancen ta kawai za ka kama dukanta, to me tayi maka, mugu?" "Haba Sala wane irin zance? Iskanci dai kawai. Waye a unguwar nan bai san abinda yarinyar nan takeyi ba? Haka kawai ta sanya ana zaginmu da raina mana hankali, wallahi na kuma ganinta da shegen mutumin nan sai na karya ta." Sala ta kuma yi masa kallon banza tana fadin, "Sannu Abbakar Ubanta da yayi cikinta, to tsaya kaji na gaya maka, kayi kadan kai uban da ya haife ka ma yayi kadan balle kai karan kada miya, haka kawai ka takurawa yarinya ka hana ta rawar gaban hantsi? Kai ne ka haifar mini ita ko kaine ka halicceta, eye? Bala'in naka ya wuce na baki har ka fara kai hannu kana dukan ta? Za ka zo kana gaya min ana gulmarku a unguwa, ina ruwana da wasu 'yan unguwa 'yan saka ido sana'ar banza ana ruwa suna kirgawa, su bari su koma sata yafi. To bari inyi maka mai gaba daya ta mahaukata tunda naga abun naka yana neman ya wuce gona da iri,Wallahi daga yau idan ka kuma taba mini yarinyar nan ko ka kuma shiga rayuwarta da sunan fada ban yafe maka nonona da ka sha ba!" Sadiku ya dafe kai cike da tashin hankali yana fadin, "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Sala mai yasa haka? Yanzu dan ina gaya muku gaskiya dan gudun kada ku fada cikin halaka ya sanya zaki tsine mini....."gaskiya ko kuma munafurci da sanya ido? Kai waye ya shiga rayuwarka? Kullum kana yawo da kodadden wando jins da rigar gwanjo kamar tsohon matsiyacin bature." Ya girgiza kai cike da takaici yace, "Shike nan Sala Insha Allahu kome Abu zata yi a unguwar nan da gidan nan na daina yi mata magana, taje in dai duniya ce ta ishe ta riga da wando, za ta koya mata hankali." "Ka ga malam kada kayi mata baki, koda yake ai ba kai ka haife taba balle bakin ka ya bita ba, wadanda ma suka fika sunyi sun gama babu abunda ya same ta sai ma cigaba balle kai, don kurwar Abu kur! Maye yaci kansa." Sadiku bai kuma cewa komai ba ya juya ya fice daga gidan, don sai yaji gaba daya gidan ma ya ishe shi. Sala ta kama Abu dake zaune dirshan tana kallonsu don taji yanda Sala ke afke masa ta wanke mata zuciya, Sala din tana fadin "Tashi muje gida ki kwanta kinji? Koda yake Alhaji Mustafan yana can yana jiranki. Goge idonki kije ku cigaba da zancenku, ki gaya masa ya kwantar da hankalinsa kamar tsumma a randa, nayi masa maganin dan saka idon can, ba ku da sauran mai matsa muku yanzu, muje na raka ki ko yana kofar gida a labe bai tafi ba." Ta daga ta tana goge mata idon ta wanda babu ko alamun kwalla ko guda daya, daman kukan nata na sharri ne bawai na zafin duka ba. Suka nufi kofar gidan tare, sai dai babu motar Mustafa babu alamarta sai dai filin wajen kawai, dan yana ganin sun yi cikin gida ya ja motarsa yayi gaba don kada Sadiku yazo yayi masa tijara a cikin jama'a har asirinsa ya tonu, don haka ya ja motarsa ya gudu. Ai kuwa suna ganin baya nan ran Sala ya kuma baci suka koma cikin gida tana ta masifa da bala'i, wanda har makota suna jiyota, ita kanta Abun ma taji takaicin tafiyar Mustafa dan ta saka ran ya bata wasu kudi yau na ankon bikin Larai, dan haka dai sun dauki laifi gaba daya sun dora akan Sadiku wanda ya bar musu unguwar ma gaba daya. A daran nan Sala batayi baccin kirki ba sai bala'i da masifa kawai take yi har Baba Abbakar ya dawo tana yi, shi dai yayi mata banza bai kulata ba dan dai yasan 'yan bala'in ne suka motsa, idan kuma suka motsa babu wanda take saurarawa dan haka shi dai ya lallaba ya haye gadonsa na karfe yayi lamo kamar mai yin bacci amman a zuciyarsa Allah wadarai yake yi da halin Sala, har ya tuno wata mata data wuce ta gabansi dazu suna majalisa wani yayi subutar baki a cikinsu yace "Ka ga wannan matar idan ta fara bala'i sai ta kwana tana yi." Ashe matar nan ta jiyo shi don haka ta dawo ta tsaya a kansu gami da rike kugu tana kallonsu shekeke tace, "Mai kuka ce, eye?" Wanda ya fadi maganar ya yi murmushi irin na matsorata yace, "A'a Hajiya ai yabonki muka yi nace duk unguwar nan babu irinki a mutunci, ba irin babata ba 'yar bala'i, idan ta kama masifa sai ta kwana tana yi." Jin abunda yace ne ya sanya tace, "Allah ya so ka wallahi, da yau na lakada maka duka a unguwar nan na ga mai kwatarka, da sai kaga karshen masifa ta." Sai da tayi nisa sannan suka fashe da dariya suna zolayarsa sai yace, "Ku ai gwara da na yi haka, dan wallahi yanda na ga tana wata girgiza bata ki mu casu a tsakiyar titin nan ba, ni kuwa ina zan iya da ita kana ganin mace kamar bishiyar kuka? Ai irin wadannan sai da lallashi." Lallai kam haka ne sai yanzu ya gano gaskiyar Malam Sabo, masifaffu ba'a iya musu sai dai a bisu da lallashi ko kuma ayi musu banza kawai. Shi dai har bacci ya dauke shi bai san sanda Sala ta gama masifarta ba. Da safe ma da bala'in Sala ta karya dan Sadiku ko koko da kosan da ake bashi ranar ba'a bashi ba sam, shima bai nema ba ya tafi makarantar sa da yake yana karatun Low ne a B.U.K, karatun da yake matukar shan wahala a kansa dan babu wanda ke taimaka masa a iyayansa sai Malam ne ma yake taimaka masa wani lokaci da kuma rufin asirin Allah, dan ya iya zane idan ya samu ya kan yi, ko kuma idan bashi da lakca ya tsaya shagon wani abokinsa ya taya shi aski a bashi wani abu, da kuma tallafi na karatu da suke samu (Scholarship), haka nan yayi ficewarsa da yunwarsa gashi banda kudin mota bashi da ko kwandala. Ita kuwa Abu 'yar mulkin ko shirin makaranta bata yi ba, don kwanciyar ta ma tayi tace kanta ciwo yake yi, yinin ranar a daddafe tayi shi dan takaici, ita kuwa Sala sai kawo mata kayan dadi takeyi kala-kala wai dan ta kwantar mata da hankali. Yamma na karatowa aka yi wanka aka ci uwar kwalliya ta jiran Mustafa aka kame akan kujera, duk yaron da ya shigo gidan sai taji kamar ita zai ce ana kira, gashi ita yanzu ta daina kula samari dan a ganinta ita kalar manya ce kamar yanda Mustafa ke gaya mata. Sai dai me? Har kusan karfe goma na dare babu Mustafa babu alamar sa, har gajiya tayi da lekawa amman babu shi babu alamunsa. Daga karshe dai ta sanyawa Sala kuka tana fadin "Sala ina ga fa Mustafa fushi yayi da wulakancin da Sadiku ya yi masa jiya, dan baki ji maganganun da ya dinga gaya masa ba, shi ya sanya ya yi fushi ya ki zuwa." Sala tace, "Bari ke dai Abula ai wannan yaron ya goga mana bala'i, yanzu idan yaron nan ya daina zuwa ina zamu sanya kanmu? Ki duba ki ga irin kudin da yake bamu a sama ba tare da mun sha wahala ba, yanzu idan ya daina zuwa sai dai mu koma abincinmu kenan." "Abinci Sala? Cabdijam!! Wallahi Sala na fi karfin tallar abinci yanzu, dube ni fa ki gani? Ni samari ma tsami na daina harka da su balle wani tallah, idan mutum bashi da kudi ko kallo ma bai ishe ni ba." Sala tayi dariya tana fadin, "Ho Abulata, kinyi gaskiya wallahi kin fi karfin talla yanzu, tunda Allah ya baki abun neman kudi ai shike nan. Ki sha kuruminki na ma sani zai dawo, watakila wani abin ne ya tsre shi, dan na san ba kowa ne zai sami kamarki ya yasar ba... Ke kamar na ji karar mota ma." Sukayi shiru, can Sala tace, "Allah karar mota ce." Suka bazama suka yi kofar gida har suna karo da juna, sai dai me? Kurar mota kawai suka gani ta wuce tuni, haka nan suka dawo suna zaman tsammanin warabbuka, Malam ya ki noma yana jiran sadaka. Sai dai har suka fara gyangyadi babu Mustafa babu alamarsa, haka nan suka hakura kowacce ta kama makwancinta cike da takaici. Abu kamar wasa karamar magana ta zama babba inji Garba Sufa, dan yau kwanaki shida kenan amman babu Mustafa babu alamarsa, uwa da 'ya sun shiga tashin hankali, tun suna tunanin zai zo har sun hakura sun fidda ransu da zuwan nasa, shi kuwa Sadiku da har yau bai daina shan bala'in Sala ba murna yake yi don ko babu komai ya kori Mustafa, lallai barazanar da ya yi masa tayi tasiri a kansa. Daran daya cika kwana bakwai suka yanke shawarar zuwa gidansu dan su bashi hakuri, domin dai kudi sun fara musu karanci don ma su Karimatu suna daukar abinci da funkaso, don ita macece mai jarababban neman kudi dan tun tana budurwa bata iya zama babu sana'a ba. Washegari da yamma Abu taci kwalliyar ta duk da kanta da yake mata ciwo, ana taku dai-dai kamar ba zata taka kasa ba, aka nufi gidan su Mustafa wanda yake can gangaren layinsu. Sanda ta isa ta tsaya tana kallon gurin da yake zama bisa farar kujera karkashin bishiyar Umbrella, lokuta da dama da jarida a hannunsa, sai dai yanzu babu ko alamarsa ko kujerar tasa ma babu a gurin. Katuwar koface wacce ke garkame, bata mantawa da can suna zuwa tsokanar kare, idan ya biyosu su zunduma da gudu ko kuma suyi ta jifansa, wata rana sun taba fasa masa kai mai gadin ya bi su da gudu ya kama daya a cikinsu ya zane, shine fa suka kulla masa, ai kuwa rannan maigidan ya futo da motar zai tafi sai kuma yayi mantuwa ya koma cikin gidan, su kuwa daman suna fakonsa dan haka suka dauko wani abu mai tsini suka soka a tayar gaba ta sace, ai kuwa sanda mai gidan ya futo ya gani ya dinga yiwa maigadin fada daga karshe dai sai wata ya hau ya bar wannan a nan, bayan maigidan ya tafi suka dinga yiwa maigadin ihu da tsokanarsa, ai kuwa ya bisu da gudu sai dai kasa kama kowa yayi dan 'yar zilliya suka dinga yi masa, haka nan ya gaji ya koma yana nishi, don haka yanzu take fargaba kada ya gane ta. Ta daure dai ta kwankwasa kofar, ya bude ta 'yar karamar taga ya leko dan yaga wanda ke magana, yana ganin ita ce ya zaro ido waje yace, "Me kike nema a anan, eye?" Yana maganar fuskar nan tasa a murtike. Ta rike kugu da murguda baki a hankali tace, "Banza dan gadi, kai ba don ta kama ba ka isa a wani tsaya ana magana da kai, dalla ka bude da wani bakinka duk gansa-kuka." Ya kuma hasala dan dai bai ji abinda tace ba amman da alama zaginsa take yi, dan haka ya bude ya futo da wata zungureriyar bulalarsa yana muzurai. Ko a jikinta bata ji ko dar ba don ba dabi'ar ta bace tsoro, ta kuma ayyana a ranta wannan tsohon ya tabata zai gane kurensa dan wallahi sai ta yi masa sharri, ta kuma gyara tsayuwa. Ya hasala matuka dan haka da zafin rai ya fara magana, "Ke yarinya bana son rashin mutunci, don a haife kin san na haife ki ko? Don haka ki bar gurin nan tun ban zane ki ba." Ta yi masa kallon baka isa ba sannan tace, "Ka ga Malam ni ba wani abu ya kawo ni ba Mustafa nazo nema, idan yana ciki kace masa Abu tana magana da shi, ka daina mini surutu kana feshe ni da yawu." Mamaki ya bayyana a kan fuskarsa, mai ya hada Mustafa nutsatstsen yaro da wannan hatsabibiyar yarinyar? Amman bai san alakarsu ba, dan haka ya dan saki fuska ya ce, "Mustafa fa kika ce?" Ta motsa fuska tace, "Ko kana mamaki ne?" A ransa yace, "Kai wannan yarinyar 'yar bala'i ce, gwara ya lallaba ta su rabu lafiya. Don haka ya kuma gyara tsayuwa ya fara kora mata bayani, "Ai Alhaji Mustafa ya koma don daman hutu yazo da kuma ciwon Babansa da ya tashi na hanta, dan a can kasar waje yake karatunsa, yau kwanansa shida da komawa, kuma ba shi da ranar dawowa dan tun da ya tafi shekara uku sai wannan karon ya dawo." Ta dafe kirji cike da tashin hankali ta ce, "Yanzu ya tafi wata kasar babu daman na ganshi dan Allah?" "Af! Ai kuma sai kiyi, mutumin da aka ce miki bai kasar gaba daya ma, kinga komawa ta ma." Ya koma ya garkame kofar tasa. Kafarta ta yi mata nauyi ta kasa dagawa, yanzu yaya zata yi da rayuwarta? Don Mustafa ya koyar da ita darussa masu wuyar mantawa, yanzu waye zai dinga bata shandy tana sha? Waye zai dinga bata tabar shaidan tana sha? Waye zai dinga kai ta hotel taci kayan dadi ta hau gado mai laushi?, waye zai dinga bata kudi mai yawa irin na Mustafa? amsar ita ce babu, babu wanda zai maye mata gurbin Mustafa ko ta ina. Da kyar take iya gane hanyar da take sanya kafarta duk hankalinta a tashe yake, don ma Allah ya taimake ta ba wata tafiya bace mai nisa, da kyar ta samu ta lallaba ta isa gidan dan zazzabi da ciwon kai sun hadu sunyi mata taron dangi. Bisa wata tabarma da ta tadda a tsakar gidan ta zube, wacce Sala ta shimfida ta shiga kicin dora sanwar dare, ta zauna idonta na zubar da hawaye, azaba biyu take ji a jikinta gata rabuwa da Mustafa ga kuma ta ciwon da ke addabarta, ta zame ta kwanta ta kama juyi da malailaikuwa a tsakar gidan tana kuka mai ciwo da taba rai. Sala ta futo daga kicin dan ta dan huta, sai dai mai zata gani? Abu ce 'yar lelenta tana birgima a tsakar gida tana kuka dafe da kanta. Ta isa gurin da sauri tana tambayar ta, "Abula diyar kirki yaya aka yi? Bai hakura ba ne Mustafan? Idan bai hakura ba ni sai naje da kaina na bashi hakuri. Kwantar da hankalinki, banda abun dan yau ma ai saurin fushi ba nasa bane ba, idan yayi mana haka ai yayi mana tsiya, bari naje da kaina na bashi hakuri ina ne gidan nasu?" Ta mike tana neman gyalen da za ta yafa. Abu da taga da gaske take yi ta ruko hannunta, ta juya tana kallon ta amman ta gaza cewa komai, cikin kuka Abun tace, "Kada ma kije Sala, ko kinje ba zaki same shi ba don baya nan wai daman a kasar waje yake karatu hutu ya zo, yanzu ya koma yau kwanansa shida da komawa. Wayyo Sala cikina zan mutu." Ta karasa maganar da kuka tana rike ciki. Sala ta rude sosai ta ruko hannun diyar tata tana mata sannu gami da lallashinta tana fadin, "Kiyi hakuri Abula na san zai dawo ya nemeki komai dadewa, domin ke din mace ce da duk namijin da ya ganki sai ya rude balle shi Mustafa da yake sonki, share hawayenki ki daina kuka kinji Abula ta? Na san zai dawo komai dadewa." "Ni fa cikina ne yake mini ciwo. Wayyo Sala ciki....." Sai ga amai kyah! kyah! kyah! Tana kwararawa. Sala ta kuma rudewa ta mike da azama tana neman fo don taimakawa diyar tata, tun tana yin amai na abinci da ruwa har ta koma na majina take yi, da kyar suka samu aman ya fada. Sala ta taimaka mata ta raka ta bandaki dan ta wanke jikinta, ita kuma ta dawo dan ta gyara gurin zuciyar ta na cike da tsananin tausayin diyar tata, dan ta gano ta fada kangin soyayyar Mustafa. Haka nan ta karasa yammacin a kwance ga juwa da tashin zuciya dake damunta, daga karshe dai Sala tace bari ta je gurin dan Oga ta karbo mata magani ko aman ya tsaya. Tana isa dan oga ya kama wage baki yana fadin, "A'a mana ne? Sannu ka da zuwa. Ina Habu ne dan bana ganin shi yanzu?." Sala tace, "Abu tana nan, yanzu ma ita na zo na karbawa magani bata da lafiya." Ya kuma wage baki yana fadin, "Habu babu lafiya? Bari a bata magani mama, ka bari kudinka ma." Ya kama hada magunguna bayan ya kammala yayi mata bayanin yanda za'a sha kowanne, ta amsa da azama ta nufi gida. Sanda ta sha maganin kamar gaske dan aman ya tsaya har ta sami bacci, sai dai wajen karfe goma sha daya aman ya kuma dawowa dan shi ma ya tashe ta daga bacci, sai da ta amayar da duk maganin da ta sha samman ta sami sa'ida, sannan ta sami wani bacci ya dauke ta. Da safe kuwa sai ta tashi jikin babu laifi dan aman ya tsaya, sai dai jikin nata babu kwari daga kwanciya sai kwanciya, har ta samu ta tsakuri abinci kadan ta ci, Sala sai ta kama murna jiki yayi kyau. Sai dai yamma tana yi amai ya dawo sabo, har dare yayi ana abu daya, sai da aka kuma samo wani maganin. Sala kam bala'i ta hau yi tana fadin, "A'a na gamo lagon abin ma, wato marasa mutuncin nan ne ke neman kama mini diya (mayu), lallai kam zan yi maganinsu, don ga alama nan ciwo baya tashi sai almuru yayi, wallahi duk shegiyar matar da na san mayyace a unguwar nan sai naci ubanta, za su san wannan karon sun ciwo mai zafi, dan ba zan yadda da rainin hankali ba, dan sun ga diyata ta taso bul- bul da ita gwanin sha'awa ga farin jini shine zasu lashe mini ita? To wallahi kurwarta kur! Kai bari ku gani ma ba'a bori da sanyin jiki, ai mune maganin mayu." Ta debo garwashi ta gumbuda garin tazargade da wani maganin mayu, nan fa gida ya tirnike da hayaki sai tari suke yi. Sannan ta kuma jika tazargadan a cikin ruwa ta mikawa Abun tana fadin, "Amshi nan shanye, mayu za su ci kan ubansu yanzu a gidan nan." Cikin ikon Allah har ta gama shanyewa ba tayi amai ba don da duk abinda ya shiga cikinta sai ta amayar da shi, amman wannan ya zauna. Sala tayi dariya tana fadin, "Ahaf ai na sani, mu za'a gayawa zancen banza? mu maita ma bamu so yi bane, abinda ake saidawa a kasuwa." Haka nan ta dinga mita da balokoko a tsakar gidan kamar wadan da take zargin suna nan a tsakar gidan. Cikin kwana biyu sai jikin yayi kyau, domin in dai ta sha ruwa da tazargade a ciki bata yin aman, hankalin Sala ya fara kwanciya da ita kanta Abun, sai abu daya da ya dawo musu da hannun agogo baya bai wuce dawowar aman ba. Tana tsaka da bacci aman ya taso mata, tayi kokari ta fita amman ina ya riga ya yunkuro dan haka ta zauna a nan ta dinga kelayawa. Kanwarta Karimatu ce ta mike ta yi dakin Sala da gudu tana gaya mata, ai kuwa a rude Sala din ta taho, ta rike Abun kam-kam tana mata sannu har dai suka samu aman ya lafa ta dan sami bacci. Sala ta koma daki ta kwanta, sai dai ba'a yi awa guda ba Karimatu ta kuma komawa da gudu taba buga kofar dakin Sala gami da fadin aman ya dawo. Sala ta tashi a rude, sai ta kalli Baba Abbakar dake ta shararar bacci ta kuma hasala, ta daddage iyakacin karfinta ta maka masa duka, ya tashi a gigice yana ta soshe-soshe, ta galla masa harara tana fadin, "Ka saki baki kana ta sharara bacci bayan ka san Abula bata da lafiya, ko sisi baka taba bayarwa kace a sai mata magani ba sannan sannu ma ta gagara? To ka zo muje ka ga jikin nata kada ta mutu." Ta shiga gaba yana binta a baya zugui-zugui kamar makaho da dan jagora, ai kuwa yanda suka ga Abu hankalinsu ya tashi dan ta galabaita sosai. Sala ta rude matuka ta saki kuka tana fadin, "Wayyo Abula! Dan Allah kada ki mutu ki barni, na shiga uku ni Salamatu." Baba Abbakar ne ya dinga lallabata da kwantar mata da hankali, zuwa gurin asuba kuma sai Abu ta fara suma, dan haka gari yana dan kara haske aka samo mota suka kwashe ta sai asibitin murtala (Murtala general hospital). Sun yi sa'a suna zuwa aka karbe ta, nan da nan aka rubuta musu abinda zasu siyo, Baba Abbakar babu ko sisi a jikinsa don haka ya zame ya gudu, Sala ce ta kwance jakarta ta dauko kudin ta bada, nan da nan aka daura mata karin ruwa, sai da babbar leda ta shiga jikinta sannan ta fara dawowa hayyacinta. Cikin ikon Allah kafin azahar ta dawo hayyacinta, da taimakon Allah da taimakon karin ruwan da aka yi mata. Sai washegari da likita ya dawo yaga jikin ya dan fara kyau ya rubuta mata gwaje-gwaje bayan 'yan tambayoyi da yayi mata, gwaji kala uku aka rubuta mata, akwai na taifot da na maleriya sai kuma wanda yake tantama a kansa dan ance masa budurwa ce, amman dai ya zama dole a yi din don ya tabbatar da binciken sa gwajin masu ciki. Sala ce ta taimaka mata suka nufi dakin gwaje-gwajen aka auna komai aka basu sakamako cikin ambulan, suka ce ta kaiwa likitan da ya turo su, suka koma dakin da aka kwantar dasu suna jiran zuwan likitan. Sai da ya gama ganin marasa lafiya sannan ya dawo dakin nasu, ya fara bin gadaje yana dubawa har ya zo kan na Abu. Ya gyara gilashin din idonsa gami da kara tambayarta jikin nata, Sala ce ta amsa sannan ta bashi sakamakon dake cikin ambulan. Ya amsa ya farke yana dubawa, ya kuma gyara gilashin din dake idonsa yana kallon Abu, sannan yace da Sala, "Baba kika ce budurwa ce ko?" "Fil ma kuwa a ledar ta. Don ko kudin toshi ba'a kawo ba balle a sanya rana balle kuma ta kai ga biki ba." Sala ta bashi amsa da sauri. Ya girgiza ka ya ce, "Haka ne." Yace, "Baba ku same ni a ofis dina yanzu zan baku sallama dan ta warware." Bai jira jin amsar su ba ya wuce gado na gaba. Sun dade tsugunne a kofar ofis din nasa da kayansu a zube suna jiransa, har ya zo ya bude ya shiga suka rufa masa baya, ya nuna musu gurin zama sannan ya dauki wata takarda ya fara rubuce-rubuce a cikinta Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 Idan zuciya ta gyaru 1-03 Posted by ANaM Dorayi on 07:50 PM, 28-Jan-16 Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU _________________ Na ________Fauziyya D Sulaiman_____ Bayan ya gama ya daga kansa yana kara kallon Abu wacce tayi wuki-wuki, ya ma rasa ta inda zai fara, can dai ya daure yace, "Baba wannan diyarki ce?" Batayi mamakin tambayar ba don jama'a da dama kanyi mamaki idan aka ga 'ya'yanta wanda sam basa kama da ita, dan kamar mahaifinsu suke yowa wanda idan ka gansu tamkar Larabawa suke, ita kuma gata nan bakikkirin, don haka baki a hangame tace, "Ka ga bamuyi kama ba ko? Ai mutane da dama na mamakin ace 'ya'yana ne don idan suna yara suna kuka a gidan biki har cewa ake na maidawa uwarsu sai anga na ciro mama ina basu tukunna ake yarda nawa ne, ai diyata ce ta biyu. Ha ha ha" Ta saki dariya daga karshe. Ya girgiza kai cike da takaici ya ce, "A yanda na gani a jikin kati yanzu shekararta goma sha hudu ko?" Ta kuma yin dariya tana fadin, "Haka ne likita ka ganta gaba-gaba haka nan take da girman jiki babu shekaru, ka ganta kamar 'yar shekara ashirin ko? Girman jikin ne kawai musamman yanzu da take cin kayan dadi sai tayi wani fari da kiba kamar diyar wani basarake, bul-bul da ita gwanin sha'awa." Likitan yayi murmushi don ya gano inda Abu ta samu matsala, wato rashin uwa tagari ne, dan haka babu wani boye-boye ya ce, "Hajiya ke da yarinyarki ta sauya kin tambayeta dalilin da ya sanya ta sauya?." "Haba dai likita wace irin tambaya ai jin dadi shi ke sanya mutum ya sauya, ka ga dai yarinyar nan kullum da sai ta dauki talla safe da dare, yanzu kuwa ta samu mai ba ta kudin sai dai taci ta kwanta sai dai makaranta." Ya girgiza kai cike da takaici ya ce, "Haka ne, to tsaya na gaya miki diyarki tana dauke da juna biyu, ma'ana ciki, dan haka wannan sauyawar da tayi ba wai ta jin dadi bace illah ta ciki....." Sala ta mike da tashin hankali ta dafe kirji cikin karaji tana fadin, "Me? Likita cika fa kace? Lallai baka san aikin ka ba, dubi Abulan duka nawa take da zata yi ciki? Kai dai ka kara dubawa ka gani ko katin wata ka dauko." Ita ma Abu dake zaune tana jin caftar da Likita da Sala ta dafe kirkji da sauri tana fadin, "Na shiga uku ciki ne dani." Sai ta saki kuka. Sala ma ta sanya kuka tana fadin, "An ya likita ba karya ka fadi ba? Ko kuma aljanu ne suka hura mata ciki ka ga kamar ciki ne da ita, dan yaushe ma ta fara al'ada duka, ka dai sake dubawa." Shi dai rubutunsa kawai yake yi akan wata takarda, sai da ya gama sannan ya daga kansa ya mika mata kayin yana fadin, "Ko ki yarda ko kada ki yarda 'yarki tana da ciki, dan haka idan baki yarda ba sai kije wani asibitin a duba miki ita, na gama daku sai ku tafi, a gaba a dinga kula da tarbiyyar yara." Ta kuma fashewa da kuka tana fadin, "Don Allah likita ka taimake mu, yanzu yaya zamu yi da wannan abin kunyar? Na shiga uku ni Salame....." "Kinga Hajiya ku fita can kuyi kukanku don na tashi zan kulle ofis dina." Ya mike yana hada kayansa. Ta tsagaita kukan tana fadin, "Likita yanzu babu wani taimako da zaka yi mana?" "Kinga Baba babu wani abu da zanyi bayan addu'a Allah ya rabata da shi lafiya, kuje waje zan kulle ofis dina nace." Yana magana yana kallon agogonsa. Haka nan suka fice daga Ofis din Abu tana kuka Sala kuma duk ta gigice, suka yi zaune turus a gaban kayansu kowacce tana kuka, har yazo ya wuce su bayan ya kulle Ofis din nasa. Can dai Sala ta daure ta ce, "Wai ni Abula garin yaya kika yarda har yayi miki ciki ne ma? Ai da kince yayi wasu 'yan dabarun da bazaki samu ciki ba" (Fauza tace, kuji fa jama'a bata bakin ciki da lalata mata diyar da aka yi sai ra samun cikin, shima don tana jin kunyar idon jama'a ne, kai tir da irin wadannan iyayen). Abu ta cuno baki gaba tana wani kumbure-kumbure tace, "To nima na san zan sami cikin ne Sala? gashi yanzu ya gudu ya barni da ciki. Kuma na san 'yan gidansu ba zasu yadda shi yayi ba, na shiga uku yaya zanyi da gorin 'yan unguwarmu? Ga shi dama sun tsane ni, yanzu idan suka ji ina da ciki zasu dinga tsokana ta." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Sala ta fyace hanci wanda ke kwaranyo da majina ga hawaye sun hadu sun cakude sannan tace, "Au!! Gaya musu zamu yi? ai kama bakinmu za muyi muyi shiru, ko Abbakar ba za'a gayawa ba, dan kada dadin hira ya kwashe shi a majalisarsu ya kwaza, kin san shi da shegen surutu, kija bakinki ki yi shiru har mu zubar da shi....." "Zubarwa Sala?" Abu ta fadi a kidime. "Eh mana zubarwa zam yi, dan da kunyar duniya gwara ta lahira, kuma ma ai ma tuba kafin mu mutu. Goge hawayenki ni na san ta inda zan bullowa al'amarin, ki sha kuruminki, bari na samo mana mota mu tafi gida." Ta fita ta samo musu mota suka loda kayanzu suka nufi gida da sunan Abu ta warke. Tana isa gida ta sanya aka samo mata madaci ta hada da darbejiya da omo da kanwa ungurnu ta dafa su suka dahu sannan ta kawo wa Abu daki. Tana kwance lamo ta ce, "Abula na tashi ki kafa kai maza ki shanye wannan." Ta mika mata kwanon dake dauke da hadin. Babu musu Abu ta karba ta kafa kai ta kama kyankyama tana rintse ido saboda rashin dadinsa da daci kamar zai yanka mata harshe, ko kofi guda bata sha ba amai ya ciyo ta, ta yadda kwanon ta kama amai, gaba daya hadin ya zube, wanda ta sha kuma ta dinga dawo dashi tamkar zata amayar da 'ya'yan hanjinta. Sala tana tsaye ta yi tagumi, sai dai tana ganin aman ya lafa ta kuma dauko wani kwanon cike da maganin tace, "Maza Abula na daure ki shanye wannan....." Ta girgiza kai cike da fargaba tana fadin, "A'a Sala gaskiya babu dadi, hanjina kamar zasu tsinke ji nake kamar zan mutu." Sala ta waro ido waje tana fadin, "To dama waye yace miki dadi ne da shi, eye? Daman ai za ki sha ne dan ki rabu da wannan jarabar dake tare dake, da don dadi ne yaushe zan baki? Da dadi nake so kiji sai na sayo miki kaza da madara, amshi ni ki sha tun raina bai baci ba ko asirinmu ya tonu ba." Abu ta amsa idonta na fidda hawaye ta amsa ta kafa kai tana sha, ai wannan karon ko rabin kofi bata sha ba aman ya kuma dawo wa, ta dinga yunkuri kamar za ta amayar da 'ya'yan hanjinta, hankalin Sala ya kuma tashi, haka nan suka hakura dan babu yanda zasu yi suka yi zugui-zugui da su cike da tashin hankali. Sadiku ya shigo gidan da Sallama, Sala tace da Abu, "Maza kwanta ki rufe idonki zan ce bacci kike yi, Waye......? Tsaya ina zuwa." Bakinta yana kyarma take fadin, ta fita da sauri tana kokarin gyara daurin zani dake shirin faduwa. Ya dubeta da mamaki dan ganin yanda ta fito a firgice, idanuwan nata duk sun yo waje. Ya kalle ta da damuwa a ransa ya ce, "Lafiya Sala ko ba ki jin dadi ne?" Da sauri Sala tace, "Lafiya ta kalau me ka gani? Jiya ne dai 'yar uwarka ta tashi da ciwon kai har muka kai ta asibiti kana makaranta, amman yanzu jikin da sauki dan har an sallamo mu." Yace, "Allah ya sawake." Ya dauki bokiti ya zuba ruwa ya shiga bandaki, ta yi tsaye tana muzurai wai dan kada ya shiga dakin, har ya gama ya futo daga bandaki. Sanda ya futo har tsoro ya ji dan ganin yanda ya bar ta haka ya tadda ta tana tsaye, ya dube ta da mamaki ya ce, "Sala yaya dai, lafiya?" Ta gatsina fuska ta ce, "Lafiya kalau, ina shan iska ne kawai." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ya dubeta sosai ya ji gabansa ya fadi dan ganin yanayin ta, amman sai ya dake kawai ya wuce, har ya isa soro sai wani tunani ya darsu a ransa, sai ya juyo har lokacin tana tsaye tana dubansa. Ya kalle ta da kyau yace, "Sala kunje asibiti kika ce? Me suka ce yana damunta?" Munje mana da Baba Abbakar muka je ma jiyan ta sami sauki yanzu haka bacci take yi. Bai yadda da abun da tace ba, dan haka ya ce, "Ki bani katin na duba ko da wani abu da suka ce." Kululululuuu! Cikinta ya duri ruwa, amman sai tayi saurin yanko karya tace, "Laaa! Ka ga sai yanzu ma na tuna da katin, ai mun baro shi a can asibitin wallahi, ai tama warke idan ka ganta kamar bata yi ciwon ba ma." Kamar ya kuma yin magana, amman sai ya ga rashin dacewar yi din dan haka kawai ya juya ya fita ya nufi dakinsa, sai dai ransa cike yake da zargi kala-kala amman yana ta addu'ar Allah ya sanya abin da yake zargin ya zama ba gaskiya ba ne. Sai da Sala taga ya shige dakinsa sannan tayi ajiyar zuciya gami da shiga dakinta da sauri tana fadin, "Oh! ni Salame yaro sai shegiyar tambayar tsiya kamar dan jarida? Koda yake an ce ai karatun Lauya yake yi sun iya sharri, ai da na gaya masa abinda ya faru na shiga uku da surutunsa kamar wani ubana." Kusan daran nan a zaune suka kwana suna sake-saken abinda zai fish-she su, daga karshe dai sun yanke shawarar komawa asibitin watakila su sami wanda zai zubar musu da cikin tunda an ce ana zubarwa. Amman sun yanke shawarar ba zasu je asibitin Murtala ba za suje Kuroda ne dan kada Likitan jiya ya tona musu asiri. Sanda suka isa asibitin suka bi layi har ya kawo kansu suka shiga, bayan sun zauna likita ya dubesu yana tambayar abinda ya faru. Sala ce ta fara kwantar da murya tana fadin, "Wallahi likita tsautsayi ne ya faru da yarinyar nan, yarinya ce 'yar albar....." Ya dubi katin yana magana, "Hajiya kece Zainabun ne?" "A'a ba ni bace gata nan." Ta nuna Abu. Ya maida dubansa ga Abu ya ce, "Zainabu me ke damunku?" Idonta ya kawo kwalla ta dubi Sala tana matse idanu, Sala ta daga mata kai alamar ta yi magana, ta kwantar da murya ba kamar da ba da take magana a tsiwace tace, "Daman kaina ne yake ciwo da ciki na da kuma amai....." Ya dubeta da kyau sannan ya maida kansa ga katin yana rubuce-rubuce, ya daga kansa bayan ya gama ya ce, "Hajiya zaki kai ta ayi mata gwajin fitsari da jini." Ya dubi wata ma'aikaciyar jinya (nurse) yace, "Sister nuna musu dakin gwajin jini." Ma'aikaciyar jinyar ta mike tana fadin, "Hajiya taso muje mana." Abu ta kalli Sala wacce ko motsawa bata yi ba, Sala kam wani busashshen yawu ta hadiya da kyar sannan tace, "To likita ai daman a babban asibiti anyi mata gwajin, an gano tana da ciki ne.... Daman zuwa muka yi ka taimaka mana kamar yanda Allah ya taimake ka ka zubar...." "Me?" Likitan ya tambaya da mamaki, ya dora da cewar, "Hajiya an gaya miki muna zubar da ciki ne mu?" Bai bari ta bada amsa ba ya cigaba da maganarsa, "To ki sani mu bamu zubar da ciki a nan, idan kika kuma kasadar zuwa wani asibitin na gwamnati da sunan a zubar miki da ciki za'a iya kama ki a daure, wato kina jin kunyar duniya ba kya tsoron Allah ko? Wato kinfi jin kunyar duniya ba kya tsoron Allah ko? Me yasa kika yi sakaci da tarbiyyar 'yarki har tayi ciki? A ce kamar wannan karamar yarinyar da bata gama sanin kanta ba balle ma ta san mecece rayuwa ta yi ciki....." "Ai dai kaddara ce ba ta wuce kanka ba kai ma." Abu ta katse shi tana murguda baki da wani kyafta idanuwa. Sala ta kai mata duka tana fadin, "Kin ci Ubanki nace, ana neman ya raba ki da wannan kajagar kina masa rashin kunya?" "Kin ga Hajiya ku tashi ku fita na gama da ku, don ina da marasa lafiya dake jirana." Likitan ya katse mata maganar. Sala ta gurfana bisa gwiwowinta za ta fara roko, amma ya katse mata hanzari ya daga mata hannu yana fadin, "Hajiya I said get out of my Office, (Na ce ki fita daga Ofis dina)." Jikin Sala ya yi sanya ta mike duk da bata ji abinda yace ba ta gane korarsu yake yi, Abun ce ma ta dan gane wani abu tunda ta san (get out) dan haka suka fice babu shiri. A bakin titi suka yi tsaye cike da tashin hankali, dan duk iyakacin dabararsu ta kare. Abu ta fashe da kuka tana fadin, "Yanzu Sala shi kenan gorin da nake yiwa Ladi mai danwake ta haifi shege nima haka za'a dinga mini? Kin gani har hana ta fitowa muke muna bula mata kasa idan ta fito, gaskiya Mustafa ya cuce ni, Gashi ya gudu ya barni da abin kunya." Sala ta matse ido cike da takaici tace, "Bari ke dai diyar nan, na rasa inda zan tsoma kaina da wannan abun kunyar, wallahi yaron nan ya shammace mu, da ina ganin sa yaron arziki ashe dan tsiya ne." Tayi kwafa gami da fyace majina da hawayen dake zubo mata da gefen gyalenta. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Abu ta dube ta tace, "Sala yanzu gida zamu koma?" Sala tace, "Eh, to! Ko dai zamu je gurin bokan can na kan tudu mu gani ko za'a sami maganin zubar da ci....." "Sannu Hajiya." Wata murya ta katse mata magana daga bayanta, gaba dayansu suka juya da sauri dan ganin mai musu magana. Ma'aikaciyar jinyar nan ce da suka gani a dakin likita, wadda ya ce ta raka su dakin gwajin jini. Ma'aikaciyar jinyar ta fara magana, "Ina ta addu'ar Allah ya sanya daman baku tafi ba, na dan tsaye bata lokaci ne dan kada likitan ya gane ku na biyo. Ai shi na gaya muku dan ka'ida ne ba ya zubar da ciki, yana wani fama da gemu kamar gaske. Don ma bai kama yi muku wa'azi ba, shi ya sanya sam bama shiri da shi, amman daman ka'ida ce duk asibitocin gwamnati ba'a zubar da ciki idan na da matsala ba, sai dai zan taimake ku yanzu dan kun bani tausayi, bai dace yarinya karama kamar wannan rayuwarta ta lalace tun yanzu ba." Fuskarsu ta fadada da fara'a Sala ta ce, "Kai amman likita mun gode miki kuwa, Allah ya sanya ki gama da duniya lafiya." Ma'aikaciyar jinyar tace, "Amin." Sannan ta fara yi musu kwatancen wani asibiti mai zaman kansa inda za'a cire musu cikin. Sala ta dinga godiya kamar ta kwanta don durkuso tana godiya. Ma'aikaciyar jinyar ta ce, "Babu komai idan baku gane ba dai ku fada mini, sai dai yanzu rana ta yi gobe da sassafe za kuyi sammako kuje." Sala tace, "Mun gane ma." Haka nan sukayi Sallama suka tafi suna ta godiya. Daren ranar dai cikin farin ciki suka kwana, sai zumudi suke yi gari ya waye su tafi, dan abun da ya so tauye musu farin cikin su ma da farko bai wuce rashin kudi ba, sai dai da yake ance mai kadara ba matsiyace bane, sai suka daga wasu kayansu na sawa har da wani saitin dankunnen gwal wanda Mustafa ya saiwa Abu suka kai kasuwar Rimi da kasuwar 'yan tsaye suka saida, Cas suka amso kudinsu, dan haka suka daina fargaba suka kwana da farin ciki wanda rabon su dashi tun ranar da suka ji Abu tana da cikin. Sai dai idan za suyi magana kasa-kasa sukeyi dan sun lura da Sadiku ya sanya musu ido, ko ma su kulle kofar. Da sassafe suka yi sammakon shiryawa suka nufi kwatancen asibibin da Ma'aikaciyar jinyar nan ta musu, basu wani sha wahala ba suka gano a nan cikin Sabon gari yake. Sanda suka isa suka cika da mamaki dan ganin wannan Ma'aikaciyar ta jiya, ta tare su tana dariya tace, "Kun gan ni anan ko? ai ina aiki anan ma sanda bani da aiki a can. Dan haka ne ma ya sanya nayi muku kwatancan nan din, kuzo muje gurin likitan." Wani katon Inyamuri ne kansa da sanko ya sha kot, idanuwansa jajir suke da alamun shan taba a lebensa, ta cikin gilashinsa ya dinga leken Abu yana wani lasar lebe. Cikin harshen turanci Ma'aikaciyar jinyar ta yi masa bayani duk abinda ke damun Abu. Ya yi dariya cikin gurbatacciyar hausarsa ya ce, "O.k na gane, Yarinya ka zauna mana." Yana magana yana dubanta kamar maye. Duk rashin tsoro irin na Abu sai da ta tsorata da ganin mutumin, dan haka ta tsaya ta kasa zama. Sala ta dubeta da kulawa tace, "Abula zauna mana, shine zai raba ki da wannan kajagar da ke tare da ke." Ta zauna tana cigaba da kallon sa har lokacin hankalinta bai kwanta dashi ba. "Hajiya ciki wata nawa take?" Ya tambayi Sala. Tace, "Ban sani ba likita, sai dai ka duba ka gani." Ya Umurci Abu da ta kwanta a wani gado da aka zagaye da labule sannan ya shiga yayi mata awo. Sai da ya kammala sannan ya fito ya dubi Sala ya ce, "Hajiya yarinyarka tana da shiki na wata uku ne, amman kada ka damu idan da akwai kudi za'a cire shi yanzu." "Nawa ne kudin? Mun zo da shi." Sala ta fada da saurinta. "Ka je can waje ka biya za su gaya maka kudin." Sannan ya dubi Abu yana fadin, "Ka sauko za muje da ke dakin aikin yanzu." Sala ta je ta biya duk kudin da aka caje ta suka bata takardar shaidar ta biya, duk yawan kudin bata ji kyashin biya ba. Bayan ta karba ta kai masa ya amsa ya karanta ya umurci Abu da ta shiga wani daki ita kuma Sala ta jira a can wajen shakatawa. Sai da ya sanya ta tube kayanta sannan yace dole sai ya fara kusantarta sannan zai mata aikin. Hankalin Abu ya tashi matuka ta mike ta daura zaninta tana masa wani duba na tsana da tsiwa ta ce, "Sannu tsohon dan iska Bunsuru, bayan an biya ka kudinka, to na fasa ai ba kai kadai bane mai aikin ba, ka biya mu kudinmu mu tafi wani gurin." Hankalin likitan ya tashi don ya kwadaita da Abu dan ya jima bai yiwa yarinya karama mai kyau da kyan sura irin tata aiki ba, dan haka ya kwantar da kai da gurbatacciyar hausarsa ya dinga lallashinta, amman fir Abu taki yadda. Da dai ya ga ba zai shawo kanta ta haka ba sai ya ce, shikenan ya fasa ta hau gadon yayi mata aikin, bata yi musu ba ta kwanta, tana ji ya zurkuda mata wata allura wacce ko minti uku bata yi ba taji duk jikinta ya mutu ko hannu ba zata iya dagawa ba, bakinta ma ya kasa buduwa balle tayi magana, za mu iya cewa tayi karamar suma ne, Amman tana jin duk abinda yake faruwa sai dai ba zata iya yin ko motsi ba dan allurar bacci yayi mata da yake tana da karfin jini ya sanya ba tayi baccin ba. Tana ji tana gani katon Iyamirin likitan nan ya biya bukatarsa amman bata da halin hanawa, sai da ya kammala dan kansa sannan ya dauko kayan aiki ya fara yi mata. Sanda ya tura karafunan da zai dagargaza abinda ke cikin nata ji tayi kamar ana zare mata rai dan azaba, amman ko motsi ba zata iya yi ba, sai dai hawaye dake zubowa ta gefen idonta. Shi kuwa katon kedarin ko a jikinsa, ya sanya karfan ya burge abun da ke cikin kamar yanda ake markada kayan miya, bayan ya gama watso abinda ke cikin ya kuma sanya wani ruwa mai magani ya fara wanke cikin, sai da ya wanke shi tas sannan ya maida mata kafafunta yanda suke. Azaba dai ta sha ta, hawaye sai da ya jika gefen da take kwance, ajiyar zuciya kawai take yi amman ba zata taba mantawa da wannan azabar a rayuwarta ba har abada. Yayi mata wasu allurai na rage radadi sannan ya tura ta can dakin hutu, cikin dan kankanin lokaci duk kamanninta sun sauya saboda tsabar azaba. Sala ta isa kanta da sauri tana mata sannu sanda aka sanar da ita an gama, sai a lokacin ta sami bakin magana ta fashe da kuka mai ciwo. Wannan Ma'aikaciyar jinyar ce ta shigo dakin hannunta rike da magani ta yiwa Abu sannu sannan ta ce, "Likita ya gama da ita babu komai a cikinta dan haka nan da awa uku idan ta huta zaku iya tafiyarku, sai dai Hajiya daga yau sai ku daina sakaci ciki yana shigar 'ya'yanku, don ke Zainabu yanzu kin ji azabar da kika sha, dan haka gwara ku dinga rigakafi kafin ciki ya shiga." Sala ta dube ta da mamaki tana fadin, "Dakta yanzu akwai wani abu dake hana daukar ciki dama?" Ma'aikaciyar jinyar ta ce, "Eh akwai mana, allura ce da magani har da kulle mahaifa ana yi, in mace tayi daya daga cikinsu ba zata sami ciki ba." Sala ta amshe cike da mamaki a fuskarta, "Oh! Ni Salamatu ki ji wata fasaha, rashin sani yafi dare duhu, da mun sani da yaushe za mu sha wannan wahalar? Kin ji fa Abula." (Sala ba ta ji tsoron Allah ko yin nadama da abin da ya sami Abu ba, ba ta hankalta da isharar da Allah ya nuna musu ba har take neman hanyar da diyar ta ba za ta kuma yin ciki ba, hakan ke nuna daman tashin hankalin da suka shiga na samun ciki ne ba na gyaruwar zuciya ba. Menene amfanin irin wadannan iyaye? Kai, tir! Da su, domin su ne tushen gurbacewar al'umma a ganina). Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ma'aikaciyar jinyar ta yi ta musu bayani, Sala tana ta girgiza kai cike da mamaki, ita kam Abu ita kadai ta san abunda take ji, sai dai tana jin dadin bayanin likitar, ta kuma yi alkawarin ba zata kuma samun ciki ba, yanzu ma rashin sani ne. "To, yanzu likita a ina ake samun maganin tsarin iyalin?" Sala ta tambaya. Sister din tace, "Ai ana samu a duk asibitocin da kika je, sai dai su asibitin gwamnati suna da ka'ida, basu bayarwa sai matan aure, ko kuma idan kinje da mijinki, har wasu masu zaman kan nasu ma akwai wadanda ba sa zubar da ciki saboda rakiyar asara, amman kin ga mu nan babu ruwanmu za ki iya zuwa ki siya ko a chemist dina." Sala ta ce, "Kai likita mun gode da wannan kirkin naki." Ta yi murmushu ta ce, "Suna na Sister Asibi, ko da wata rana kunzo neman wani taimako,ta yi musu kwatancen gidanta ta tafi ta barsu cike da murna, dan itama tana da nata kason, don ka'idar asibitin nasu idan mara lafiya ya zo ta sanadiyyar ka kana da kaso mai tsoka musamman ma zubar da ciki. Karfe biyar suka koma gida, shatar mota ma suka dauka, da kyar Abu take iya taka kafarta, san da suka isa jama'a na ta kallonsu, masu zargi na yi masu addu'a kuma na yi, da haka suka shige gida. Da suka isa daki suka baje Sala ta dauko naman da suka yo tsaraba da shi suna ci suna mayar da yanda aka yi suna ta dariya ta abunda suka dinga yi jiya har da kukansu. Ita kuma Abu sai baiwa Sala labarin irin azabar da tasha take yi. Sala ta ce, "Ai an gama, da kin samu kwarin jikinki zamu koma su yi miki allurar da suka ce din, tunda dai duniyar ta sauya gwara mu fizgi rabonmu muma, dan na san idan kika murje kika goge, Alhazan birni ne zasu yo miki caaa, tun da dai kina da kyau da sura mai daukar hankali." Suka kwashe da dariya har da shewa. Sadiku da duk maganar da suke yi a cikin kunnansa ya daga labulan ransa a bace hankalinsa a tsananin tashe, nan fa suka yi tsamo-tsamo kamar wadanda aka watsawa ruwa, cikinsu aka rasa ko mai tari balle su yi magana, dan daga ganin fuskarsa sun san ya ji duk abin da suka ce. Shaf! sun manta basu rufe kofa ba, ko su yi a hankali ba. Da kyar ya iya bude bakinsa cike da takaici ya ce, "Sala yanzu tsakaninki da Mahaliccinki Ubangijin da ya halicce ki kun kyauta abinda kuka yi? ko tsoron Abu ta rasa ranta a gurin zubar da cikin nan baki yi ba, daman tun ranar da na ga kin gigice na yi zargin wani abu na shirin faruwa koma ya faru, na yi iyakacin iyawata a kan tarbiyyar yarinyar nan har kina jin haushina. Sannan wannan abu da ya faru bai zame muku ishara ba sai ma kara kangarewa da Abu ta yi? Shin Sala kun san sanda zaku mutu? Ba kwa tsoron Allah? Ba kwa tunanin Ubangiji ya dauki rayuwarku kuna cikin wannan mummunan sabon? Da nayi niyyar fita daga harkarku sai dai ya zama dole na tunatar da ku gaskiya koda kuwa zaku tsireni ne nauyi ne a kaina, tunda shi Babanmu ya gaza. Sannan ke Abu azabar da kika sha ba zata zame miki ishara ba? dan bata kai kashi daya cikin dubu ta azabar lahira ba, dan haka ki hankalta ki san..." "Kai! Ya isa haka malam." Sala ta katse shi. Ta dora da cewar, "Ka wani saka mu a gaba kana mana surutu mara ma'ana sai kace wasu 'ya'yanka, idan aljannar ta ubanka ce ka hana mu shiga, sannan idan kace za'a yiwa Abu azaba dan tayi ciki shi kuma mai saka ido sana'ar da babu uwa babu riba yaya za'a yi dashi? Ka saka mana ido kamar wani Ubanmu, wallahi ba dan a tsakar dakin nan na haife ka ba da asibiti ne sai nace musanya miki kai aka yi, dan baka kaunarmu ka tsane mu, to ta Allah ba taka ba dan saka ido." Yayi wani murmushi mai cike da takaici yace, "Sala ina kaunarku a matsayin wadanda bani da kamarsu a duniya, wannan ya sanya ni nake gaya muku gaskiya, dan wanda baya kaunarka bai gaya maka gaskiya.......Malam ka ishe mu haka, ba'a san gaskiyar taka soko shashasha, har ni zaka ce zaka gayawa gaskiya? Tun kafin a haife ka na san gaskiya. Bace min da gani tun ban daga maka nono kabi duniya ba." Ya saki labulen jikinsa sanyi kalau zuciyarsa tana suya. Abu tace, "Sala kiyi masa kashedi kada yaje yayi ta fadi a duniya yace nayi cikin shege mun zubar." "Hakane fa." Sala ta fadi da sauri ta daga labulan tana fadin, "To, saura naji wannan maganar a bakin wani, ranka zaiyi mummunan baci Sa'idini, sarkin sa-ido." Shi dai baice komai ba don ko juyawa ma baiyi ba ya cigaba da tafiyarsa ransa yana cigaba da suya. Sala kuwa cigaba tayi da balbalin bala'inta tana fadin, "Haka kawai an saka wa yarinya ido dan anga Allah ya bata kirar da zataji dadin rayuwarta, dan haka babu ruwan uban kowa koda sadaka take bada kanta balle ma da makudan kudi ne." (Ubangiji ya shirya mu har wadanda suka bata, mu gane gaskiya kuma ya bamu ikon binta, Amin).Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 KANO: 15/5/2003 Kyakykyawar budurwa fara tas, sai dai bata cika tsawo ba dan haka koda yaushe zaka ganta da dogon takalmi,ba ta da gashi mai tsaho amman akwai yawan gyara shi, tana da dogon hanci wanda ya fito da ainihin kyawunta, bakinta kuwa irin dan karamin nan ne kamar na yara, sai idanuwanta wadanda ke ruda 'yan maza duk sanda ta kalle su da shi saboda girmansu da kuma kyansu, har wata digon zaiba ce a ciki, ga ta da dan karan yanga da iya kwalliya, wadannan abubuwan suka hadu suka maida ta irin matan da zamani ke yayi. Tana sanye da riga da siket na atamfa wanda ya matse ta tsam-tsam daga kugunta, 'yar kibarta ta yi cas- cas cikin kayan, fatar jikinta na da laushi tamkar 'yar jaririya, tana sanye da katon takalmi mai kama da tsani don tsaho, fuskar nan tasha ado irin na wayayyu, sai ta shafa jambaki kalar kayan jikinta, bata sanya kwalli ba, sai dai ta zizara jagira cikin idon nata, gashin girarta ya kwanta luf-luf gwanin sha'awa, daga yanayin shigarta da tafiyarta kadai ya isa ya yaudaro 'yan maza dan duk inda Zainabu ta bi sai an kalle ta. Kayanta kalar katuwar jakarta ce, ga wani kamshi da ke tashi a jikinta kamar kana kantin sai da turare, tana da matukar fizgar hankalin duk wanda ya dora idonsa a kanta, sannan hatsabibiya ce ta fannin mu'amala, domin ta kware ainun a iyar tafiyar da namiji don haka duk mutumin da ya kusance ta ko sau guda ne sai ya kidima a kanta. Ta fito daga dakin nata bakinta sanye da wata alawa mai tsananin kamshi tana tsotsa, Sala dake shan kayan marmari wanda Zainabun ta kawo musu tsaraba jiya da ta dawo daga Abuja, zaune ta bararraje a tsakar gida tana kallon Zainabu, duk da ranta a bace yake sai da ta yi murmushi dan ganin yanda Zainabu taci uwar kwalliya, tana dubanta da fara'a tana fadin, "A'a 'yar albarka kin fito? Sannu da fitowa." Zainabu ta yamutsa fuska gami da amsawa. Salan tace, "Jiya na so muyi maganar yarinyar nan sai naga kin dawo a gajiye, ga shi kun yo dare....." "Wani Abu ne kuma ya faruwa?" Zainabu ta katse Sala din (don yanzu ta tashi daga Abu ta koma Zainabunta). "A'a a kan dai maganar nan ce ta kwanaki ta matsiyacin yaron nan da ta nacewa, shi kuma wannan yaron dan saka ido yana ziga ta kamar shine uwarta, to yanzu wai iyayansu za su aiko, ni kam sam ba na son tayi auren nan, me take da shi? Ita ko sha'awarki bata yi, koda yake ko ba tayi auran ba ma bata da wani amfani tunda ta ki yarda ta ciwo arziki, dan haka sai kiga shegiyar tayi sati biyu bata da ko kwandala, sai dai idan an yi musu albashi ya sanmata, wanda duka albashin nasa bai wuce kudin takalmi da jakarki ba."Zainabu ta yamutsa fuska tana fadin, "Sala ki barta ta yi auran nan taji, in dai Maza ne ai zata gane kurenta, banza ana neman a samo mata mai maiko tun da ta nace sai tayi auren tana ki tana wani rawar kai, ki rabu da ita kawai, dan rannan baki ga wani abokin Alhaji T.J ba yanda ya mato a kanta, har na nuna masa ya rabu da ita kanwata ce, sai ya rantse mini da cewar shi da aure yake sonta, amman babu yanda banyi ba yarinyar nan ba taki ko kula shi, haka ya hakura ya kyale ta don ya yi-ya yi ya gaji, shi da mata ke sonsa kamar me? Shine fa kwanaki ya bani kujerar Makka guda ukun nan da na kai ku ke da Baba." "La'ilaha Illallahu, kai amman yarinyar nan bata da rabo, arziki yana kiranta tsiya tana janye ta, ina ga fa matsa mata zamuyi ta aure shi kawai ko ta tsiya ko ta dadi." "A'a Sala ina ruwanmu? Ita ce fa zata zauna da mijinta, sannan yanzu idan muka hada su haushinmu zata dinga ji, gwara mu kyale ta ta yi hankali, ni bari na wuce kada na yi latti, kin san nace miki muna da bikin cikar Asma shekara ashirin da biyar, zan je mu fara shiri saboda shi na dawo jiya." "To-to, Allah ya kiyaye, zaki dauki shatar mota ne?" Zainabu tace, "A'a Alhaji Danlami sabon kudi yana waje yana jirana." "To Allah ya tsare, ya bada sa'a." Tace, "Amin." Gami da ficewa. Yana cikin mota zaune ya sha manyan kaya kamar wani mutumin arziki, tunda ta fito ya zuba mata ido tamkar maye, ita kuma tana tafiya tana rangaji tamkar ganyen bishiyar da iska ke kadawa, tafiyar dake dauke hankalin 'yan maza. Tana isowa ya bude mata kofa yana murmushi gami da fadin, "Barka da warhaka Hajiya, irin wannan shanyar haka har na bushe?" Tayi wata mayaudariyar dariya ta jan hankali, tace, "Lallai kam, to waye ya gayyace ka? Ina ga kaine fa ka sakani fitar nan, da ka gaji ba sai ka tafi abinka ba na huta." Ya kanne ido yana mata wani kallo yace, "Ni na isa? ai kina da tsayawa mutum a rai Zainabu, kusan duk aikin da nake fa idan kika fado mini bani samun sauran sukuni muddin ban iso gareki na ji duminki ba, ko matana na kasa zama da su kamar ke, anya Zainabu kina tausaya mini kuwa? Dan Allah ki daure ki aure ni mana ko na sami nutsuwa." Tayi masa wani malalacin kallo ba tare da tace komai ba ta kauda kai gefe, ya kuma rudewa ya matsa kusa da ita jikinsa har rawa yake yi. Ta kuma matsawa gefe tana harararsa gami da fadin, "Haba Malam, ko dai dan bunsuru ne ka saurara mu bar kofar gidan ubana da kuma tsakiyar ranar nan, duk iskancina ban taba yi a kofar gidan ubana dan ina mutunta gidan." Ya ja baya yana shafa haba yace, "Kai Zainabu kina juya ni wallahi kamar waina, amman babu komai zan matsa lamba har ki zama mallakina." Ya tada motar yana ta sumbatunsa, ita kuma murmushi kawai take yi, ta gama kashe shi da kissarta da kallonta gami da tsananin kamshinta. Sai da ya kaita wani babban gidansa na shakatawa suka gama watsewarsu sannan ya cika mata jaka da kudi dan ya san Zainabu mai tsada ce, sannan suka dauki hanyar gidan Asma, har lokacin yana ta sumbatu a kanta da yaba kyanta da iya mu'amalarta. Sanda suka isa gidan Asma ya kwantar da murya kamar wani abun tausayi ya ce, "Yaya dai Hajiya, karfe nawa zan dawo na dauke ki?" Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ta galla masa harara tana fadin, "Kai fa tsiyata da kai kenan ba ka iya cin kwan makauniya ba, to ai ni din ba matarka bace da zaka hana ni sakewa." Ta kammala maganar tana murguda baki. Ya lankwasar da kai yana fadin, "Tuba nake Hajiya, kece din sai a hankali, amman na hakura sai gobe zan bullo." Ta daga kafadarta gami da fadin, "Kai dai ka sani, sautun mahaukaciya." Ta fice daga motar. Har tayi nisa yana kallonta kamar ya kuma binta yake ji. Zainabu macece hatsabibiya mai tsayawa mutum a ransa, ta san yadda take iya tafiyar da shi kamar wacce ta karanci abun, ya rasa abinda ya sanya matansa ba sa masa irin yanda Zainabu ke masa, da zai sami mai masa kamar Zainabu cikin matansa ai da babu abinda zai sanya shi yawo ana wulakanta shi, dan yana ga idan ya sami Zainabu ta aure shi yana jin ko kofar gida sai anyi da gaske zai fita, da kyar ya samu ya iya jan motarsa ya bar kofar gidan. Ta shiga gidan da ihu babu ko sallama, Asma dake zaune daga ita sai gajeren wando da 'yar rigar mama tana busa tabar wiwi tana wani lumshe ido, ta mike tana ihu suka rungume juna. Asma ta ce, "Shegiyar, wallahi na yi zaton ba zaki zo ba, da kin kwafsa mini." Suka zauna suna mai da numfashi, sannan tace, "Haba Hajiyata ai kin san dole na zo, yaushe zan yarda chasun nan ya wuce ni?" Asma ta fashe da dariya tana fadin, "Dan akuyan naki ne na san shi da jaraba ko bunsuru ya rufa masa asiri, na san da kyar zai barki ki dawo, ko da yake Zainabun akwai iya iskanci, har tsoro nake ji idan na ga saurayina yana kallonki, don har ta kafa sigina kike yiwa namiji,suka fashe da dariya gami da tafawa. Zainabu tace, "Wai ni yaya shirye-shiryen fatin ne? Ina fata kin tanadar mana komai?" Asma ta tabe baki tace, "Kin san akwai maza 'ya'yan wahala wadanda iyayensu da matansu suka sallama mana, sun gama komai. Senator Tanko ya kama mana hotel dama komai da za'a ci a gurin, sai dai shegen wai ba zai zo ba dan kada 'yan adawa su sami abin da zasu soke shi a kafafan watsa labarai. Oho, ni ko a jikina dan daman bana son ganin wannan mummunar fuskar tasa wacce zata hana samari 'yan bana bakwai isowa jikina mu sha minti, dan kin san sun kwana biyu sai a hankali, dan wallahi duk sanda na kalli fuskarsa sai ta tuno mini da wani tsohon goggon biri." Suka kuma fashewa da dariya gami da tafawa. Zainabu ta zira hannu cikin jakarta da dauko kwalbar Shandy ta kama tsotsa, ta jingina da kujera tana lumshe idanuwa Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Asma ta kalle ta gami da fadin, "Ke 'yar duniya babu ko dandano? Kin kafa kai kina tsotsar abun ki?" Zainabu ta dube ta da ido daya dayan kuma ta kanne shi, "Malama kada ki matsa mini ki bar ni na yi dif! Ina ce tadda ke na yi kina busa tabar mulki kin mini tayi ne?" Ta kuma matsawa gabanta tana kwantar da kai tace, "Haba tawan ki yiwa Allah ki ba ni na kurba ko sau daya ne, na kwana biyu ban tsotsa shandy ba" "Amshi 'yar jaraba ba zaki bar ni na sha ta ishe ni ba." Ta mika mata kwalbar giyar, sannan ta dauko nadaddiyar tabar shaidan a jakarta ta bata wuta, hayaki ya fara gauraye dakin, Asma ta sakar musu kidan Bob Marley nan fa suka tashi suna cashewa suna wani gantsare- gantsare, daman Zainabu gwana ce gurin rawa. Misalin karfe goma na dare motoci suka fara sauke mata a kofar hotel din da zasu yi fatin, sun ci uwar kwalliya sai dai babu wacce zaka kalla kace diyar Hausawa ce balle Musulmai, don duk irin shigar turawa suka yi, daga masu gajerun wanduna sai masu damammnun kaya da 'yan kananan wanduna. Dakin taron kuwa kida ne kawai ke tashi kamar zai tsaga daki, kowacce da saurayinta take shigowa. Shigowar Zainabu da Asma ne ya sanya kallo ya koma kansu, dan komai iri daya suka sanya, wani gajeren siket suka sanya wanda ya tsaya iyakacin gwiwarsu ya matse su sosai yana ta kyalli, sai wata 'yar yalolowar riga mai rawa ta zauna das a jikinsu, takalmansu har gwiwarsu, sai gyaran gashi da suka yi, duk da Zainabu bata fiye sanya gashi ba yau ta sanya, fuskar nan ta dauki kwalliya sai wani kamshi ke tashi daga jikinsu. Mai jawabi sai kwarara musu kirari yake, "'Yan mata adon gari, 'yan matan da duniya ke yayi, Asma ta Zainabu manyan Bebis da duniya ke yayi, kun girmi kwailayen Kano, kuna ruda mazan kano." Aka fashe da ihu. Zainabu sarkin rawa sai ta hau taka rawa dan daman yanda ka san mazari haka take, gaba daya sai ta dauke hankalin mazan dake gurin dan Zainabu daban ce, irin matan nan ne masu kamar fitila duk inda suka je sai sun haske shi, nan fa maza suka yi caa a kanta, ana ta mata liki amman miskilar ko a jikinta dan babu wanda ta baiwa fuska.Zainabu daban ce ko a duniyar barikin tasu, dan idan namiji bai yi mata ba duk kudinsa bai isa ko kallo a gurinta ba, tana jan zaranta yanda take so, dan ta san Allah yayi mata kirar daukar hankalin maza, an sha dambe da yanke-yanke a kanta, ko waye kai idan zaka kwana dubu kana mata magana ba za ta tanka maka ba, musamman idan tayi dif da Shandy dinta. Sai karfe hudu na dare aka tashi daga fatin nasu, an rakashe an cashe an sha kayan maye kala-kala, Zainabu kam tangadi take yi dan ta cake da yawa, ganin haka ya sanya Asma ta sanya ta a motarta suka nufi gidanta don ta san 'yan gidansu basu san tana shan giya da wiwi ba sai dai tana fita yawon gantalinta. Sai da gari ya waye sannan ta dawo hayyacinta, bayan ta farka ta shiga ta yi wanka ta yi ramuwar Sallar dake kanta sannan ta yi shirin tafiya gida. Tana sanye da doguwar riga ta atamfa super da aka ciwa mutunci, dinkin ya kama ta tsam daga kirjinta yayin da yayi baza daga kasa, hannun rigar tamkar shimi yake, ta yafa karamin gyale, sai tsireren takalminta mai kama da tsani, ta sanya zobba na gwal kirar dubai, da wani dogon dan kunne a kunnenta, kamshin dake daga jikinta tamkar kamfanin turare dan Zainabu ma'abociyar son kamshi ce. A adaidaita Sahu ta sauka dan bata nemi dan rakiya ba, duk yawan mazan da ta dauki hankalinsu daran jiya dake neman shiga, ta shiga gidan nasu da sallama muryarta tamkar sarewa. Sala da ke zaune ta mike tana hangame baki gami da fadin, "A'a diyar albarka har kun dawo? Har an gama fatin kenan." (Kuji wannan Uwa fa, diya budurwa ta kwana ta hantse a titi amman wai mahaifiyarta tace har ta dawo? Hmmm, su Sala ko sai yaushe za’a dawo kan hanya). Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ta zauna jabar bisa tabarmar da Sala din ke kai tana fadin, "Mun dawo Sala, wallahi fatin yayi kyau.Yaya na ji gidan shiru ne ko duk ba sa nan?" Sala ta tabe baki gami da fadin, "Yaran dai basa nan amman Karimatu na nan, dan jiya nayi wa yaron nan tas mai hure mata kunne, nace kada ya kuma zuwar mini gida shine take ta kumbure-kumbure, motarsa fa daya ce tal Abula, mai na sama ya ci balle ya baiwa na kasa, mtsw!" Ta yi tsaki cike da takaici. Zainabu ta yi kwafa kana tace, "Ke ma Sala da son bata ranki kike a banza, ina ce tun jiya mun gama maganar, tunda ta dage sai shi ai sai ki rabu da ita ta aure shi, kowa rai yayi ma dadi baya ga mai shi ne." Sala tace, "Ai shike nan, kina ji ke Karimatu sai ki gaya masa ya turo iyayen nasa ko ma huta da naci kamar maye." Sala dai kamar tsoron Zainabu take ko dan tana kawo mata kudi? Duk hukuncin da ta yanke a gidan babu wanda ya isa ya ja da shi koda yayanta kuwa. Karimatu dake daki tana karatun Kur'ani dan ta sami sassauci a zuciyarta saboda kwana tayi tana kuka saboda yanda Sala ta bada ita ga saurayin, wanda ko da ya aure ta ba zai kuma ganin darajar Mahaifiyarta ba, tayi hamdala ga Allah gami da yin Sujjada tana kara gode masa, don Allah ya sani tana son Abbas kamar ranta, shima yana masifar son ta, soyayya suke mai tsafta, sai dai tun da ta kawo shi gidan da sunan wanda zata aura Sala take aibata shi, daman yaya lafiyar kura balle ta yi hauka? Don daman basa shiri sam da Sala, dan tun tana yarinya taso ta yi hali irin na Abu amman ita Allah ya tsare ta shine fa Sala ta tsangwame ta kamar ba diyarta ba, ko da harkar karatunta Sadiku ne ke tallafa mata da komai,Don zamu iya cewa kusan su kadai ne shiryayyu a gida, dan kannanta dake bin ta maza duk sun fara shaye-shaye, Sadiku ya yi dasu har ya gaji don yana tufka Sala na warwarewa ne, su kuma 'yan kannansu mata kanana guda biyu suma tallan suke yi, kusan hanyar da Zainabu tayi rayuwa suke kai, sai dai karamarsu ce ta dauko halin Karimatu da alama sai kuma autansu. Bayan Karimatu ta gama godiya ga Allah ta dauko wayarta da sauri duk da tana jin nauyin Abbas din amman haka ta yi kiransa, bugu daya ya dauka don tun jiya yake neman wayarta har ya gaji ya hakura, ita kuma ta rufe ne saboda nauyinsa da take ji don ma kada ya kira ta bata san mai zata ce masa ba kuma. Gaba dayansu suka yi shiru kowanne yana jin nauyin dan uwansa ita kam har da kunya ma. Shine ya daure ya ce, "Yaya dai Karimatu, tun jiya nake neman wayarki a kulle, har hankalina ya tashi na yi zaton ko kin daina daga waya ta ma." Tayi wata doguwar ajiyar zuciya kana tace, "Abbas kunyarka nake ji ban san da idon da zan kalle ka ba, don na sani Sala jiya tayi maka cin mutuncin da ina jin ba'a taba yi maka ba, sai dai ba kai tayi wa ba illa ni, don Allah ka yi....." Kuka ya kwace mata ya hana ta karasa maganar tata. Ya kwantar da murya yana fadin, "Kin ga Karimatu ki kwantar da hankalinki, na riga na san halin Sala tuntuni na kuma ji na gani don babu gudu babu ja da baya a son ki, na san tayi haka ne dan na yi fushi na rabu da ke, ni kuwa sai na ji ma yanzu na fara son ki, dan haka ki kwantar da hankalinki mu yi batu a kan abinda zai fishshe mu." Ta dan ji sanyi a ranta dan haka ta sami kwarin gwiwar gaya masa abunda ake ciki, na yanda Sala ta amince ya turo da iyayensa, abin ya bashi mamaki sai ya ga kamar mafarki yake yi don shekara nawa suna fama da Sala, amman ace lokaci daya ta amince? Sai Karimatu ta nuna masa kawai karfin addu'ar da suke yi ne ya sanya hakan ta faru, ya amince da lallai hakan ne dan haka ya dinga hamdala ga Allah, daga karshe suka yi sallama cike da farin ciki. Abbas kam jin sa yake kamar yafi kowa farin cikin zai mallaki Karimatu, duk da sanda ya fara nuna wa abokansa yana son Karimatu sun kwabe shi dan suna cewar waye bai san iskancin da yayarta Zainabu ke yi a unguwar ba ‘karuwar gida’ haka suke kiranta a bayan idonta, yace shi kam ya ji ya gani dan ko Allah bai kama wani da laifin wani, Tunda kowa ya san halin Zainabu da na Karima ba daya ne ba, don babu wanda zai ce gida daya suka taso ma, sai dai kamar su da tayi daya baya ga Zainabu gajera ce amman ba can ba, sannan tana da dan jiki yayin da Karimatun ta kasance doguwa siririya, Allah ya kuma sanya iyayensa masu ilmi ne kuma wayayyu dan haka suka goya masa baya gami da yi masa addu'a ta gari, wacce ita ce ke dawainiya da shi a duk inda ya sanya gabansa. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 ************* Ba da wani dadewa aka sanya rana ba wata uku ne kacal, sai dai tun da aka sanya ranar Sala ke mitar bata da shi, dan bata ga abinda Karimatu ta yi da zata mata kayan daki ba, dan ko sanda suka yi talla banda kwantai babu abun da take yi, balle yanzu da bata da ko na sayen kwalli. Shi kuwa Baba Abbakar ba'a ta tasa, don kudin da aka kawo na zance ma so ya yi ya cinye sai da Sadiku ya yi masa jan ido, shine ya ji haushi shima yake fadin, "Ya ga mai yin gadon." Shi dai Sadiku kallon su kawai yake yi yana ta kokarin ya rufawa 'yar uwarsa asiri. Biki ya rage saura kwana uku Sadiku ya shigo da kayansa na katako irin wanda ake yayi, da kujerunsa masa kyau da tsada. Maimakon Sala ta yi murna da sanya albarka sai ta hau tabe baki tana fadin, "Eh! Da yake Karimatu ce kayi mata kaya masu tsada, da Abula ce da ka tsana da ko tsinke ba zaka yi mata ba." Sadiku yayi murmushi ya ce, "Sala kenan, da Zainabu da Karimatu duk 'yan uwana ne, ita ma ta daina iskancin ta fito da miji kin ga idan ban mata wanda ya fi wannan ba." Zainabu da ke zaune tana yankan kumba tana zaune bisa darduma ta doka tsalle tana tafa hannu ta ce, "Wallahi karya ne, na fi karfin na tsaya ka yi mini kayan daki, dan yanda kake aiki nima ina yi, da kake ce mini 'yar iska ai na gode Allah tunda ba na neman mata, ka duba ka ga yanda yanzu mata ke neman....." "Dalla can, rufe mana baki marar kunya, ki yi abinda duk kika ga dama ai rayuwarki ce, na san komai dadewa zaki gane kurenki, Karima dai Allah ya rufa mata asiri, ba ta yi irin halinki ba, dan haka kuka tsane ta gidan nan....." "Ahaf! Ahaf!, Wato dai ni kake gayawa magana ko?" Sala ta amshe da saurinta, "To ka ga fita daga gidan nan tun ban bata maka rai ba, duka yaushe ka fara samun kudin? Kafin ka fara rike dubu daya Abula ta rike dubu goma, kuma duka albashin naka nawa ne? Abin da ko kudin takalmi da jakarta ba su kai ba? Ka da ka kuma furta mini ko kala, fice ka bani guri tun ranka bai kai ga baci ba." Ya gallawa Zainabu harara wacce ta rama sannan ya fice, yana yiwa Karimatu magana, "Ki lura da yanda za'a shiga da kayan kada fentin su ya goge." Tana daga can zaune gefen kicin tana yanka Salad da zasu ci abincin rana da shi tace masa "To." kawai. Ai sai bala'in Sala ya koma kanta, ina wuta ta jefa ta, zagi ta uwa ta uba da gori tana fadin, "Dadin abin dai da abincin da Abula ke ciyar da ke kika rayu ke da shi din." Ita kam ko kala bata ce ba, dan idan da sabo ta saba, ita kam aikin ta ma ta cigaba da yi ko a jikinta. Zainabu ta ce, "Haba Sala, ki yi shiru haka mana ka da muyi bakin kunya." Ai kuwa tamkar ta ji wahayi daga mala'ika ta yi shiru. Ita dai Karimatu dariya ma abin ya bata ta ce, "Idan ka ki sharar masallaci kayi ta rumfar kasuwa ai." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 CALIFONIA: 30/9/2003 Yana tsaye jikin window hannuwansa nannade a kirjinsa, dogo ne ba sosai ba yana da dan jiki irin na maza majiya karfi, jikin nasa a murde yake, yana da kyau irin na gogaggun maza da suka san duniya, bai cika fari ba amman ba zaka sanya shi a layin bakake ba, yana da irin gashin nan da samari ke ajiyewa a fuskarsu, ya iya daukar kwalliya irin ta namijin duniya. Bai fiye hayaniya ba, miskili ne ga wanda bai san shaidancinsa ba, ma'abocin farin jini ga shan yabo ga jama'a saboda faran-faran din sa da sakin hannu (kyauta), amman a badini mutum ne mai tsananin son holewa, sai dai yana da matukar taka tsantsan don yana gudun bacin ran iyayensa. Ransa a cunkushe yake, lokuta da dama idan abin ya motsa masa sai ya ji kamar ya zama tsuntsu ya bar garin, ya dade yana tausar zuciyarsa a kan abinda yake gani ba komai ba ne, sai dai yanzu abin yana neman fin karfinsa da shallake iyakacin dauriyarsa. Abin da ya faru dashi tsahon wasu shekaru da yake ganin a can baya mara amfani da muhimmanci, har idan ya tuno abin yakan kira shi da tsuntsu daga sama gasashshe, sai dai tunda ya yi nisa abin ya fara damunsa, da farko yakan ga kamar abin nan ne da Hausawa kan kira 'Sabo tirken wawa' sai dai da yaga duk kwanan duniya abin yana kuma tsiro a zuciyarsa har ya kai matsayin da ya cika zuciyar tasa babu sauran wani gurbi na tirjiya da dauriya. Ya yi kwafa a karo da dama ya juyo yana kallon kayataccen falonsa wanda ya sha kayan alatu kamar ba za'a mutu ba, ya isa dan gurbin shan lemo, ya zuba lemo a kofi ya hada da shandy ya cilla kankara ya daga ya shanye wai ko zai ji sanyi a zuciyarsa, sai dai har lokacin abin yana nan, sai yaga kamar ma karuwa ya yi saboda mutuwa da jikinsa ya yi sabon tunani ya shige shi. "Me ya sa haka ne?" Yayi wa kansa tambaya, wadda tsawon lokaci yake yiwa kansa, ya dauko taba ya kunna ta ya bata wuta a hankali yana lumshe idanuwansa amman har lokacin bai ji sanyi a ransa ba. Ya jawo takardar da ya bayar da irinta a Ofis dinsu jiya ta barin aiki yana kuma dubawa, wayarsa ta fara kara ya dauka da kyar yake magana, abinda aka gaya masa kamar kara hasala shi aka yi don haka da zafin rai yake magana cikin harshen nasara. "Eh! Ni ne na rubuta dan na yanke shawarar barin aikin nan don jama'ar kasata na bukatar gudummawa ta, sannan iyaye na sun damu da su ganni,haba Mustafa kada ka yi mana haka, idan albashinka ne ya maka kadan zamu iya kara maka mu." A ransa yace, "A wannan karon babu wanda zai hana ni tafiya dan zan biyawa raina bukatarsa ne, dan idan na cigaba da zama a haka zan iya asarar farin ciki da kwanciyar hankalina." Amman a fili sai yace, "Oga kuyi hakuri ba zan iya janye kudirina ba a wannan karon na tafiya ko da nawa zaku kara mini, nayi muku alkawarin dai duk sanda na sami dama zan dawo muku gaba daya, amman yanzu hankalina ya yi kasata." Dan Baturen da suke maganar ya sare, dan 'dan zaman da suka yi sun san Mustafa mutum ne kaifi daya, idan ya sanya abu a gabansa babu wanda ya isa ya hana shi aiwatarwa, dan haka ma ya rike aikinsa da gaskiya da amana, dan haka suke masifar ji dashi, shine zai bare inji ba tare da ya tsaya ya kalli 'yar takardar bayani ba ya maida ya hada shi kuma ya tashi tsaf, ba kamar sauran Turawan da sai sun duba ba a rubuce, ya dai daure yace, "Shike nan Mustafa muna maka fatan alkhairi, sai mun hadu a Ofis din. Ya yi ajiyar zuciya ya ce, "Shike nan Oga sai mun hadun." Ya kashe wayar tasa gami da lumshe idanuwansa, wata rayuwa ta dinga bijiro masa wacce ta wuce shekarun baya wacce a da can yake daukarta shirme, sai dai yanzu ya tabbatar ita ce rayuwarsa mai cike da ainihin farin ciki da sanya shi nishadi da dariya, sai dai duk sanda yake tunanin wani abin mai fadar da gaba kan fado masa, sai dai yana addu'ar Allah kada ya tabbatar da wancan abinda ke fadar masa da gaban. Washegari jikinsa babu kwari ya fito daga Ofis din nasu dan alhinin rabuwa da abokan aiki, sai dai daman haka rayuwa ta gada dole wata rana za'a rabu, walau ta gurin zama ko aiki ko kuma ta har abada ma (mutuwa). Daga nan kai tsaye gurin neman Visa ya nufa ta komawa kasarsa ta haihuwa wacce rabonsa da ita tsahon shekaru. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 KANO-NIGERIA: 15/10/2003. Bayan ya sauka ya dauki shatar mota tun daga filin jirgi har gidan Mahaifinsa. Maigadi ne ya fara ganinsa don haka ya zuro da gudu cike da murna da doki yana fadin, "A'a Alhaji Mustafa yau kake tafe? Marhabun lale, sannu da zuwa." Mustafa yana murmushi yake amsawa ya sallami mai tasin, sannan ya dubi maigadin ya ce, "Malam Bala a shigar da kayan ko?" Daga nan ya shige cikin gidan kai tsaye, ya yi sa'a kuwa jama'ar gidan duk suna nan domin la'asar ce. Da Mominsa ya fara cin karo tana zaune a falo tana karatun jaridar Leadership Hausa, tana sanye da (Medicated glass), ya shiga da sallama bakinsa a washe. Ta daga kai cike da tsananin mamaki, suna hada ido dai ta tabbatar da lallai shine, ta mike cike da murna tana fadin, "Babana! Da gaske kai ne ka iso garin ba tare da ka sanar da mu ba?" Ya isa gaban Mahaifiyar tasa cike da farin cikin ganin Mahaifiyar tasa don ya kwana da dama bai ganta ba, dan ma wani lokacin ta kan bi Mahaifinsa suje ganinsa, don shi tunda ya tafi bai kuma waigo wa Nigeria ba, wanda shi wai nan dabara ya yi dan ya manta da abinda ke damunsa a ransa, a cewarsa idan ya yi nisa da abin zai samu sassauci koma ya manta gaba daya, sai dai yanzu ya gano dabararsa ba za ta kai shi ko'ina ba. Ya ce, "Momi barka da gida, na same ku lafiya?" "Lafiya kalau muke sai dai mamakin dawowarka yanzu babu sanarwa, Allah dai ya sanya lafiya." "Momi Lafiya kalau wallahi, na so kwarai na ba ku mamaki ne dan na sha sanya rana zan zo amman bana zuwa, dan haka nace wannan karon sai dai ku gan ni kwatsam." "Lallai kam ka ba mu mamakin, bari na je na samo maka dan abin tabawa." Ta mike ta nufi kicin din gidan. Tana isa kicin ta tadda 'yan matanta suna ta faman kacaniyar girkin dare, ta ce, "Albishirin ku?" Gaba daya suka ce, "Goro Momi." "To yayanku ya dawo yanzun nan, yana falo dan haka sai a hado masa abin motsa baki kafin a kammala girki." Gaba daya suka yi falon da gudu suna murna suna ihu, sun ma manta da abinda aka ce su dauka, ta yi murmushi sannan ta dauka ta tafi da shi. Yana ganinsu ya ce, "Lallai 'yan matan Momi an girma, kalle ku don Allah." Suka kalli juna suna dariya. Ya so tun daran ya fita ya fara aiwatar da abinda ya kawo shi garin, sai dai gajiya ta hana shi dan haka dole ya hakura har gari ya waye. Washegari ya shirya cikin manyan kaya wadanda suka kara fito da kimarsa da martabarsa, duk da zaman da yayi kasar waje bai daina sanya manyan kaya ba, musamman yakan aiko a yi masa, idan ya sanya turawan suyi ta sha'awarsa musamman idan zai je gidan biki ko wani fati, yawaita sanya manyan kayansa tun yana nan gida ya kara masa martaba a idanun jama'a har suke ganinsa wani mai hankali da tsantseni. Motar Babansa ya hau dan na shi yayo Odarsu ba su karaso ba, yana tafe yana jin wakar Bob Marley don mutuminsa ne, sai kada kai yake cike da nishadi, yau ce ranar da zai cikawa ransa burinsa, yau ne zai je ga Zainabu Abunsa karo na biyu da sunan soyayya, idan ya tuno abinda ya faru a baya sai ya dinga jin wani farin ciki da nishadi. Sai dai abinda ke fadar masa fa gaba idan ya tuna anya Zainabun tasa ba tayi aure ba? Idan aka ce Zainabunsa ta yi aure kuwa lallai yana cikin tashin hankali da rashin nutsuwa, dan ya gano yanzu itace rayuwarsa, sai yake ganin nisan gidan nasu da yake su sun tashi sun koma cikin G.R.A. Ya isa kofar gidan yayi fakin yana kallon gidan, kusan yanda ya san shi haka yake yanzu, sai dai wasu sauye-sauye da aka samu, mutane ne a kofar gidan can da can suna cikin kwalliya. Gabansa ya tsananta da faduwa da ya ga Sadiku sanye da manyan kaya da gani sababbi ne sai daukar ido suke ya zama babban mutum mai kamala, sai fito da abinci yake shi da wasu cikin farantai. Ya zubawa Sadiku ido har lokacin gabansa na faduwa, ya zuge gilas din motar a hankali yana kara kallon jama'ar dake kai kawo kofar gidan. Can ya hango wani maroki yabi Sadiku yana masa kirari ya sanya hannu a cikin aljihu ya dauko kudi ya ba shi, da alama yana cikin farin ciki, daga ganin alamun babu ko tambaya aure aka daura sai dai bai san ko na waye ba, ya yafito wani yaro da yazo wucewa ta kusa da shi yana kallon motar. Yaron ya karasa yana kallonsa a alamun rashin sani a fuskar yaron, "Dan Allah yaro daurin auren wa aka yi a kofar gidan ne?" Ya nuna kofar gidan da hannunsa. Yaron yace, "Daurin auren wannan din nan aka yi 'yar gayun nan mai kwalliya ni na manta sunan ta ma." Ya rasa gane wacce yaron ke nufi sai dai hankalinsa yayi kololuwar tashi don yana ganin kawai Zainabun sa ce ma, ammai sai yayi ta maza ya ce da yaron, "Na gode ka ji abokina, un go wannan." Ya mika masa Naira dari biyu, yaron ya amsa cike da murna ya tafi. Yana cikin mota yana ta sake-saken yanda zai yi, shin kundumbala zai yi ya futo ya tambayi wacce aka daurawa aure ko kuma hakura zai yi ya koma.Tunaninsa ya tsaya cak sanda ya hango wasu hadaddun mata sun nufo shi, dayar doguwa ce sosai fara amman da alama ta dan kara da na kanti, sai dayar gajera ce amman ba can ba, tana da wani irin kyau na daukar hankali, daga shigar ta har tafiyarta sun yi matukar burge shi, yana hango su suna doso shi, sai yaga mara tsahon da yawa fuskarta tana masa gizo kamar ya santa. Suka zo suka gota shi suna taku sannu a hankali, gaba daya sun tafi da hankalinsa, wani irin kamshi ya ji ya bigi hancinsa san da suka wuce, ya lumshe idonsa saboda kamshin da ya ji Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 "Anti Abu ga wayarki in ji Sala ta ce kin manta ta." Wata 'yar yarinya da ta fallo da gudu ce ke fadin haka. Mustafa ya bude idonsa da sauri. Wacce tafi tafiya da hankalinsa yaga an mikawa wayar, ta amsa ta sanya a jaka, yayi wata sanyayyar ajiyar zuciya mai cike da rudani yana fadi a ransa, "Yanzu wannan Abu ce da ya sani a can baya 'yar mitsitsiya da ko kwalliya bata iya ba, 'yar tallan abinci da ya wayar da ita, ita ce ta zama wata irin tauraruwar mata ta wuce yanda duk yake tunanin zai gan ta?" "Ya Salam" Ya fadi a fili. Ko da wasa ko a mafarki bai taba zaton Abunsa zata yi irin wannan wayewar ba, ya daukarwa kansa zai dawo Kano na Nigeria ya auri Zainabu, ba don tsananin kyau, ilmi ko dukiya ba sai dai dan tsananin sonta kawai da Allah ya jarabce shi, sai dai abun mamaki da tsoro sai ya ga Zainabu ta sauya ta wuce iyakacin tunaninsa gaba daya. Tashin motar da yaga sun dosa ne ya farkar da shi daga dogon tunanin da ya fada, ya tada ta shi ya bi bayan ta sun sai dai ina sun riga sun yi masa nisa, dan haka ko hangosu baya iya yi, dan hala dole ya dauki hanyar komawa gidan su dan ya ji kiran wayar Dadin su. Karfe takwas na dare ya kuma dawowa kofar gidan su Zainabu, don yinin ranar haka ya yi shi sukuku, ya dinga tuno yanda ya ga Zainabu na tafiya da kamshinta na yanzu, musamman yau Babansa bayan sun gaisa sai yayi masa maganar aure dan sun jima suna masa maganar yana cewa suyi hakuri har yanzu baiga wacce ta yi masa ba ne. Cikin wata shigar ya iso ya yi kyau matuka, shaddar har wani kara take yi saboda tsabar bugu da ta sha, sai dai ya tarar da cincirindon mata a kofar gidan, sai motoci ne ke diban su, sai dai addu'arsa Allah ya sanya ba Zainabunsa aka daurawa aure za'a kai dakin miji ba. Yayi fakin ya fito ya jingina da motar yana kallon matan dake kaiwa da komowa cikin hasken fitilar da ya haske kofar gidan. Har ya gama kalle-kallen sa bai hango Zainabu ba, wata budurwa mai shegen yangar tsiya da take ta wucewa ta gaban sa ko zai taya ya daure ya yafito, babu musu ta nufe shi kanta ya kuma fasuwa don ga dan gayu mai hadaddiyar mota yayi kiran ta zata buda gurin 'yan matan gurin, ta nufe shi tana kara salon tafiya tana wani girgiza, duk da ba wani kyau ta cika ba amman daga gani tana ji da kanta. "Barka da yamma adon gari." Ya fadi da wata mayaudariyar muryarsa, yayi mata kuri da idanuwansa wadanda ke ruda 'yan mata. Tayi wani far da idon ta da kyar kamar bata son magana ta ce, "Yauwa ya kake?" Yayi dan murmushi yace, "Kalau nake. Na ce banga amarya Abu ba ko har sun wuce ne?" Ya shirya hakan ne don ya tabbatar da gaskiyar abin. Ta yi masa wani kallo mai cike da mamaki sannan ta ce, "Hala dai mantuwa ka yi naji kana cewa Abu, dan dai na san Karimatu ce amarya ba Abu ba, yaushe Abu zata yi aure ita da ta daurewa bariki gindi?" Ta karasa maganar tata tana yatsina fuska da alamun kishi a muryarta jin ya ambaci Zainabu don ta zaci cewa zai yi yana son ta. Ransa yayi wani wasai cike da farin ciki da yaji ba Zainabunsa ce aka yiwa aure ba, duk da bai ji dadin abinda ta ce din ba amman sai ya dake ya ce, "Kai na shafa'a ne, yi hakuri Karimatu nake so na ce miki na manta." Ta dan saki ranta tace, "Babu damuwa idan gurin fatin za ka mu zo ka rage mana hanya mana ni da kawayena?" "Me zai hana, ki shigo na kai ki mana." Ya yi haka ne dan yayi amfani da wannan damar ya ga Abun a can. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Zaharaddeen Shomar whatsapp 08168575100 Idan zuciya tagyaru 1-04 Posted by ANaM Dorayi on 01:13 PM, 30-Jan-16 Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU _______IDAN ZUCIYA TA GYARU_____ _____________ Na _______Fauziyya D Sulaiman______ Dadi ya cika ta ta yafito kawayenta da ke can tsaye suna kallon su da mamaki da sha'awar ina ma ace su yace yana so. Ta shiga motar tana fadin, "Ga kawaye na nan zaka rage musu hanya." Yace, "Su shigo mana." Dadi ya kuma cika ta tace musu, "Ku shiga baya mana." Ta umurce su sanda suka iso jikin motar. Ta so ya dan ja ta da hira sanda suka hau kan kwalta don ta kara budawa a gurin kawayen nata, sai dai shi kaset kawai ya kunnan na mutumin na sa, yana gyada kai zuciyarsa na can ga Zainabu Abu yana kwadayin yanda zai ganta ko da sau daya ne. A haka suka isa har inda za'a gabatar da fatin, hotel ne hadadde, tun daga waje za ka san fatin na manya ne dan manyan motoci ne a gurin. Sisters night aka rubuta da kyalli baro-baro wanda ke haske a gurin. Fatin Abu ce ta shirya shin don taya kanwarta murnar biki, Malam ne ya daura auren sannan 'ya'yansa suka shige gaba gurin bikin dan duk yawancinsu suna auran masu hali ne suna tukinsu, don haka a motocinsu aka dinga dauko mata ma. Bayan yayi fakin sauran 'yan matan suka fice da saurin su, ita kuwa 'yar gwallin ta tsaya tana wani yauki da fari, har zai ce ta fita mana sai ya tuna yanda take masa wani yauki da yanga. Dan haka yayi murmushi ya ce, "Ga shi har zamu rabu ban san sunan Hajiyar ba." Tayi dariya mai cike da nishadi ta ce, "Sunan ai ba wani na ku zo mu gani ba ne, sunana Salimat." Yace, "Lallai nice name, suna mai dadi." Ya zaro kudi a aljihunsa ya mika mata ya ce, "Ga wannan kya yi liki kafin na shigo zan ga wani abokin da bai karaso ba, idan na shigo zan gan ki." Yayi mata haka ne dan ta rabu da shi. Ta yi wani fari da idonta don ta yi zaton da gaske yake musamman da taga ya bata kudi masu yawa, dan haka ta ce, "Babu damuwa, amman fa ban ji sunanka ba." Da sauri yace, "Sunana Mustafa." Don ya gaji da ganin ta ya matsu ta bashi guri ya shiga ya ga rabin ransa. Ta ce, "Shi kenan na gode Mustafa sai ka shigo." Ta fita tana wata yanga. Ya bita da kallo har ta kule sannan ya yi tsaki yana fadin, "Ki ga mace kamar an zana one amman sai wani firirita da iyayi take, ita wannan ko a kafa aka daura mini ita ai zan yage ta na zura da gudu ne." Ya kuma gyara fakin ya kwantar da kujera gami da kara sautin wakar da yake ji, ya kunna taba yana sha yana kada kai kamar kadangare, ta cikin hasken gurin yake karewa matan da ke shige da fice kallo. Ya dan jima a haka sannan ya bude motar ya fice ya kukkullo ko ina, sannan ya nufi inda ya ji kida yana tashi na Mahmud Nagudu don shine yake taya su shakatawa. Gurin ya tsaru matuka, mawakin ya dage yana ta rera wakarsa cikin tattausan lafazi, amarya da ango suna tsakiyar makeken filin suna takawa a hankali, yana daga inda yake tsaye ya gane Karimatu dan ya santa tun tana karama, sai dai daman can ita tafi Zainabu hankali da nutsuwa. Ya sakale hannuwa a kirji yana ta waige-waige, bai kula da matan dake ta kallon sa wasu ma har sukan yi masa sigina. Can ya hangota ta shiga filin rawar tana sanye da wani irin material golden anyi masa wani matsiyacin dinki da ya kama jikin ta tsaf kamar a jikin ta aka kera shi, ta daura wani nadi mai kyalli shima, wani dan ziririn gyale a kafadar ta, sai wani katon takalmi da ta sanya mai kama da tsani dan tsaho, ta yi kyau matuka, ta zaro kudi daga jakar dake hannunta ta fara watsa musu. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Tana yi itama tana taka rawa a hankali, da yake gwana ce gurin rawa sai abun ya kayatar da jama'a da dama. Sai mawakin ya koma kanta da waka, "An gaishe ki yayar amarya karkada tsiwar ango, magajiyar uwa, manyan matan da duniya ke yayinsu, Zainabu tauraruwar zamani mai haske duniya, kin dade kina tashe har gobe ke ce tauraruwa farin wata sha kallo." Kanta ya kuma fasuwa ta dinga zaro kudi tana zuba masa, Asma ta shigo filin da irin kayan Zainabun komai da komai, ita ma tana shiga ta hau yiwa Zainabu likin kudin. Ango ya kama hannun amaryar suka fice yana dariya yana fadin, "Kada ta gaji ta isa haka rawar." Suna fita ya kuma mai da kidan kansu yana wakesu su kuwa sai rawa suke yi ta burgewa. Mustafa dake gefe a tsaye bai san sanda ya kutsa filin rawar ba don Zainabu ta tsumo shi da yawa, yana shiga ya zura hannu a aljihu ya dinga debo daloli yana manna mata, ta dinga dubansa da mamaki sai dai tana ganin kamar gizo idonta ke mata ko kuma mai kama da shi ne, amman da yake miskilar kanta ce sai ta dake kawai ta yi kamar bata gane shi ba, sai da ta gaji don kanta da rawar sannan ta fice daga filin, yana ganin ta fita shima ya bi bayanta, duk wanda ke shirin yiwa Zainabu liki sai jikinsu ya yi sanyi dan sun ga mai liki da daloli, gurin ya kacame da ihi da tafi na burgewa. Ita kam can wani tebur ta nufa dake can baya da jama'a, Asma ta bita da gudu har suka zauna. Asma ta dube ta tana fadin, "Shegiyar ina kika sami wannan hadadden gayen ga kyau kuma ga 'ya'yan banki? Ya yarfawa 'yan mazan gurin nan wallahi." Zainabu tayi mata wani kallon banza sannan ta sanya hannu cikin jakarta ta dauko tabar shaidan ta kunna ta, ta jingina da kujera tana fesar da hayakin ranta ya dauki zafi. Lallai ko a duhu taga Mustafa ba zata manta shi ba, shine mutumin da ya fara lalata mata rayuwarta kuma ya gudu ya barta a lokacin da take matukar bukatarsa, ba ta taba son wani mutum kamar Mustafa ba sanda ya nuna mata kulawa da soyayyar da sai daga baya ta gane tsananin yaudara ce, sannan a yanzu bata da wanda ta tsana a mutane sama da shi din. Asma kam sai maganar Mustafa take mata ita kuma zafi take ji a ranta dan haka ta kulle idonta kam har Asma din ta gaji ta yi shiru, a tunaninta ko ta bar gurin ne don haka ta bude idon ta. Tsaye ta gan shi a kansu ya nannade hannuwansa a kirji yana kallonsu, babu wani abu da ya sauya na daga kamanninsa sai kiba da haske da ya kara, yana nan har yanzu a dan gayunsa, yanda ya kura mata ido itama haka ta kura masa har lokacin tana cigaba da shan tabarta ta shaidan, Asma ta dinga kallonta tana kallon sa ta gaza gane abun da suke nufi, ta dai tabbatar da lallai yau kawarta ta hadu da daidai ita. Ya jawo kujera dake kusa da su ya zauna sannan ya jawo jakarta dake ajiya, ba ta ko motsa ba balle ta yi masa wani abu, ya dauko tabar shaidan shima ya kunnata, a hankali ya dinga fesar da hayakin sannan ya kai dubansa ga Zainabu wacce ke wurga masa wata uwar harara kamar idon ta zai fadi kasa. Yayi wani murmushi wanda ya kuma futo da haibarsa ya ce, "Zainabu Abun Musty!" Ta ja tsaki kana ta mike a fusace ta rike kugu bayan ta kashe tabar ta ce, "Malam lafiya dai ko? Don ni ban sanka ba ko don ka ga na kyale ka kayi mini liki kake neman zakewa da yawa?" Ya yi murmushi ya ce, "Zainabu kenan, kina tsammani ko a buge kike zan yadda baki gane ni ba? Na san na yi laifi amman na san zaki yafe mini dan Mustafa naki ne." "Ka ga Malam ni fa ban sanka ba, ban san daga inda ka futo ba, ka je can ka nemi wacce kaka nema, idan kuma buguwa ka yi kwakwalwarka ke gaya maka karyane to ka bari ka nutsu ka dawo hayyacin ka sai ka nemi wacce kake nema." Yayi dariya sosai wacce ta kara kular da Zainabu sannan ya dora da cewar, "Haba Zainabu, ai kinfi kowa sanin giya ko taba basa bugar dani, sai dai ke farin shiga balle yanzu ma na daina shan giya dan haka ya dace kema ki daina." Ta doki tebur gami da fadin, "Karya kake yi wallahi karamin kwaro, ka dube ni da kyau ban yi maka kama da wacce ka sani ba a da, dan kuma baka bar gurin nan ba zan sanya yanzu a yi maka rashin mutunci wallahi." Asma dake kallon su ta zunguri Zainabu wai tayi shiru, amman kamar ta kuma zigata sai cewa ta yi, "Dalla Malama ki kyale ni, ba irin wadannan ake saurarawa ba, wannan da kike gani cikakken dan iska ne da bai dace a dagawa kafa ba." Maganar tayi masa zafi a ransa amman da ya tabbatar dai ta gane shi din tsiya ce kawai sai yayi murmushi ya ce, "Ni dai na sani Zainabu ko giyar wake kika sha ba zaki manta dani ba, dan haka na dawo rayuwar ki bada wasa ba, ina fatan zaki manta da duk abinda ya faru a baya." "Wallahi karyarka ta sha karya, ka dube ni da kyau, sama da kasa zaka ga ba Abun da ka sani da can bace, wannan Zainabu ce, dan haka ka ja tsummar rayuwarka ka bar nan gurin idan ba haka ba zan rotsa maka kanka da kwabar nan." Ta nuna masa wata kwalba da ke kan tebur din da suke zaune ta lemo. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ya yi murmushi gami da gyara zama har lokacin yana zukar tabar sa yana kallonta babu ko kyaftawa. Ta san halinsa mutum ne mara tsoro sannan duk abin da ya sanya kansa babu mai hana shi, dan haka tasan babu wata barazanar ta da zata bashi tsoro, idan har ta yadda suka cigaba da zama guri daya komai zai iya faruwa, dan haka ta ga barin gurin kawai shine mafita a gare ta, dan haka ta dauki Jakarta ta bar gurin tana huci. Ya bita da kallo har ta bace wa ganinsa, yayi murmushi sannan ya dawo da dubansa ga Asma wacce ta zuba masa ido kawai tana kallonsa, ta san lallai kawarta ta debo mai zafi dan barazanar da takewa maza suna tsorata shi tayi masa amman ko gezau bai yi ba. Ya yi dariya ya ce, "Kawarmu yaya gida?" Ta yi wata wawiyar ajiyar zuciya dan maganar ta zo mata a bazata, sannan ta ce, "Lafiya kalau." "Kinga yanda muka yi da kawarki ko? Na san halin Zainabu muguwar 'yar buyagi ce zata iya yin abinda ya fi haka ma, sai dai ban damu ba ko dar ma banji ba, don na gano tsagwaron sona a cikin idon Abu" Ya nuna kirjinsa da yatsansa yana cigaba da fadin, "Ni ne mutum na farko da ya san wacece Zainabu, duk wani iskanci da Zainabu ke takama da shi nine na koyar da ita, ba wai ina alfahari da haka bane, a'a zuwa yanzu ma duk sanda na tina ni ne silar lalacewarta na kan ji takaici kuma na ji haushin kaina, don haka nayi alkawari yanda na zama sanadiyyar lalacewar rayuwar Zainabu zan kuma zama jagora gurin ganin na shiryar da ita." Ya manta Allah shi ne ke shiryar da wanda ya so, ga shi ya yi hasashe ba tare da ya nemi yardar Allah ba. "Amman ki bar ni da Zainabu ni da ita kar ta san kar ne, na san na yi mata laifi amman zata yafe mini komai dadewa tunda nine mutum na farko da ta fara so a rayuwarta." Gaba daya ya gama burge Asma har ma take ganin inama ace itace ke da wannan hadaddan gayen, amman ta san tunda Zainabu ce a gabansa ba zai kalli kowa da daraja ba musamman da yace shine masoyin ta na farko, dan haka da wuya ya kalli wata mace da daraja. Don haka ta share wannan tunanin ma a ranta dan ta san ba mai yuwuwa bane, yanda kuma suke da Zainabu ma ba zata iya yi mata zagon kasa ba, dan haka ta fara jan sa da hira ta Zainabu kawai, ya ma manta da Zainabu 'yar buyagi ya zauna suna ta hirarsu har aka tashi daga fatin, sannan ya nufi gurin Zainabu wacce ke ta hada kayan su na fatin da ta san nasu ne, ya isa gabanta yana dariya ya ce, "Yaya dai uwar dakina ko za'a taya ni kwana ne yau dan ina tare da gajiya wallahi na yo doguwar tafiya mai nisa." Ba ta kalli inda yake bama balle ya sanya ran zata kula shi, ya cigaba da surutunsa don a ganinsa dole zata bi shi don yanda dare yayi kuma kowa ya watse a gurin har amarya da ango dole ta bishi dan babu wanda zai dauke ta, don haka nema ya share guri ya zauna yana ta cigaba da surutunsa. Can wata dankareriyar mota ta kutso kai harabar da suke zaune, Zainabu ta mike tsaye gami da kallonsa sama da kasa ta ja tsaki sannan ta ce, "Malam ina gargadinka karo na biyu da ka fita daga rayuwar Zainabu, ka kuma gane yanzu Zainabu nake ba Abu ba." Tana gama fadin haka ta nufi motar da salon tafiyarta na yanga da jan hankalin maza. Ransa ya yi masifar baci har yana ganin ba zai dauki wannan raini wayon ba, don yana da masifar kishin tsiya. Don haka ya nufi motar da sauri cike da bacin rai, amman ina tuni ta riga ta shiga, bayan ta zauna ta kalle shi yana wani huci kamar tsohon zaki, ta yi wata mayaudariyar dariya mai kularwa sannan ta rufe murfin motar, yana kallo suka fice a guje, ya ji kamar ya rufa musu baya a guje amman ina sun yi masa nisa. Ya doki iska yana huci gami da fadin, "Ba zan taba daukar wannan rainin hankalin ba wallahi, zamu gauraya ne." Ku ji fa karfin hali namiji da suna Hajara Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 . Suna daukar hanya DPM ya kalle ta yana wani lasar lebe yace, "Yaya dai gimbiya za'a taya ni kwanan ne mu wuce gidan shakatawa ta?" Ta galla masa harara ta ce, "Au abinda kake yiwa kenan shiya sanya ka nace daman zaka dawo ka dauke ni? Tsaya ka saukeni dan ka san kuna da yawa 'yan iskan garin zan sami mai kai ni gida, dan ni na gaji babu wani abinda zan iya yi." Ya ce, "Kai Zainabu ke fa 'yar buyagi ce wallahi, daga dan tayi sai jidali, shi kenan na hakura muje kawai." Bata kuma cewa komai ba ta jingina da kujera ta lumshe idonta tana tuno abinda ya faru, wani ciwo mai zafi da ya dade yana damun zuciyarta ya fara taso mata, tsigar jikinta ta fara tashi yar-yar kamar mai jin sanyi "Mustafa! Mustafa!" Ta fadi a cikin ranta gami da girgiza kai. Lallai ta sani abu ne gingimeme a gabanta, dan Mustafa da ban ne a cikin maza a gurinta, kuma tayi wa kanta alkawarin a can baya duk sanda Allah ya hada su ko a hanya ne sai tayi masa rashin mutunci, amman sai ga shi a gabanta amman ta kasa aiwatar da komai a kansa, sai ma wani abu da yake neman ya dawo mata da shi. Har suka isa kofar gidan su bata san sun iso ba don tayi nisa a tunani, sai da ya kai hannunsa yana shafarta tamkar wani maye sannan ta farga, ta yunkura da masifa ta hambare hannunsa gami da dalla masa harara. Ya kama sosa keya yana dariya ya ce, "Tuba nake yi, ai na zaci ko kinyi bacci ne, Allah Zainabu sam ba na gajiya da ke, ke din ta daban ce, kamshin ki kawai kan tayar mini da hanlaki, yanzu ji yanda kamshin ki ya cika motar nan tamkar ni ban sanya turare ba, wai ni da wane turare ki ke amfani ne ma?" Ta yamutsa fuska ta ce, "Su kuma wadanda ka ajiye a gidan fa meye amfanin su? Dan haka wallahi nake tsoron aure, sai ku baro matan ku a gida kuzo kuna hurewa kadangarun bariki kunne da naira, yanzu haka matan ka suna can suna jiranka kana nan kana gantali da wannan daran." "Ke rabu da wadannan matan, babu wani abu da suka iya sai jarababban kishi da shegen bin Malaman Banza, burin su kawai su tara kudi, da kun hau gado su yi maka wani sumbukaka kamar jakai, babu wani salo da suka iya wai su kunya, sau da dama idan nayi niyyar daina bin matan titi na zauna da su idan suka gaza gamsar da ni sai kiga na dawo ruwa, balle ke Zainbau daban ce wallahi kin san kan da namiji matuka, ko makarantar kika yi ne na kawo matan nawa ki koyar da su?" Ta yi dariya sannan ta ce, "Matsalarka ce wannan, wata kila kai ma da laifinka, kana shigar musu gida ne tamkar mala'ikan tsaron wuta babu fara'a shi ya sanya suke kasa sakin jikinsu, ni dai yau duk jarabar ka nan gani nan bari, ka ga fitata ma. Ta bude kofar ta fice tana fadin, "Asuba ta gari." Ya bita da kallo har ta shige cikin gidan na su, yayi tsaki da damuwa gamida kifa kansa bisa sitiyarin motar tasa, Zainabu ta zame masa masifa a rayuwarsa, muguwar hatsabibiya ce, muddin ka yarda ta lasa maka zumar ta a baki to lallai ka shiga uku, idan ba kana da kwararriyar mace mai iya salo-salo ba sai ka ji ka rainawa matan ka.Ya figi motar tasa ya bar kofar gidan tamkar mai tsere da iska, ita kuwa tana isa gida ta tadda gidan shiru kowa ya gaji da kacaniya ya yi bacci, ta shiga ban daki ta dauro alwala ta sanya kayan ta na sallah, ta shimfida sallayar ta wacce ke ta kamshin turare ta haye ta fara gabatar da Sallah. Idan ka ga yanda take nutsuwa idan tana Sallah zaka rantse idan aka sanya mata hannu a baki ba zata iya cizawa ba, dan duk iskancin ta bata wasa da Sallah, tunda ta taba jin wa'azi akan Sallah da irin azabar da mara yinta ke sha ta nutsu da yin sallah, wannan shine kadai abinda zaka daga a rayuwar Zainabu ta yi tutiya da shi. Mu dai bi ta a sannu don duniya ai takaitacciya ce. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Mustafa kam da kyar ya iya komawa gida, ya dade a dakin sa yana sintiri hannuwansa sakale a bayansa, wani masifaffan kishi da zafin Zainabu ke addabarsa, lallai yau da yana da hali da sai yayi wa Zainabu da wanda ya dauketa dan banzan duka, gaskiya ba zai iya lamuntar wannan halin nata ba na kula kowa, lallai dole ta daina harka da kowa indai tana son kanta da zaman lafiya, ya dade yana sintiri da kyar ya iya daurewa ya dan kishingida har bacci ya dauke shi. Da safe ya so yaje amman ya san da kyar zai sami ganin ta don hidimar bikin da sukeyi dan ya ji suna cewa yau din ne yinin biki, dan haka ya yanke shawarar sai dare sannan zai shiga. Karfe tara na dare ya isa gidan nasu ya rasa ta yanda zai yi ya ganta, sai can ya sami wata budurwa yace ta kira masa ita. Ta dube shi ta ce, "Ai Anti Abu tun da aka yi Sallar Magariba suka fice da kawarta Asma." Ya yi mata godiya ya koma motar sa ya zauna, Allah ya sanya jiya ya amshi lambar wayar Asma din, dan haka bayan ya shiga motar ya zauna ya fara neman layin Asma din. Da yanga ta dauka a yauki take maganar sanda taji kira, "Hello wa ke magana?" Ya yi ajiyar zuciya sannan ya ce, "Mustafa ne, don Allah ina son ki bani kwatancen inda kuke, amman kada ki sanar da kawarki yanzu zan zo." Ta dubi Zainabu da ke zaune tana zukar tabar shaidan ta dora kafa daya kan daya, tunda suka iso gidan abun da take yi kenan dan cewa ta yi ba zata je kai amarya ba don ranta a bace yake su wuce gidan ta ta sami hutu, amman tun da suka karaso din ta gaza tabuka komai baya ga busa taba, dan haka ta riga ta gano kawar tata tunanin Mustafa ne kawai don bata taba dora hankalin ta ga namiji kamar haka ba. Sai ta ce, "Shike nan zan yo maka text." Daga haka suka yi sallama. Minti talatin da biyar kacal ya kwashe ya iso gidan ya danna kararrawar kofa, Asma ta mike da sauri don ta san Mustafa ne. Zainabu ta bita da kallo ta ja tsaki tana fadin, "Banza, kin gayyato mana wani kwarton ko? Ni da nazo dan na huta zaku dame ni, daman tunda naji kina magana kasa- kasa a waya na san jarabarki ta motsa." Bata ce mata komai ba sai dariya kawai da tayi ta nufi kofar, yana tsaye sanye da kananan kaya, wando ne na jeans bulu da shet fara tas mai taswirar birnin London, da silifas na fata a kafarsa dan gasken, sai agogo na azurfa da wani kwalelen zobe shima na azurfar, ya yi kyau matuka. Suna hada ido da Asma ta yi ajiyar zuciya sai taga yau yafi kyau ma fiye da jiya, dan ta kuma yadda irin gogaggun mazan nan ne ma, ta kwantar da murya tana fadin, "Yallabai barka da isowa." Ya yi murmushi gami da fadin, "Yauwa kawarmu ya gida?" Tana amsawa ta bashi hanya ya wuce ciki, sannan ta kulle. 'Yar buyagin tashi tana zaune tana ta busa hayakinta bata ko kalli inda suke ba balle ma ta gane waye ba. Ita ma Asma tana shigowa kiran wayar Alhaji Buba ya shigo wayar ta, yace ga direba nan ya turo su taho, dan shi baya zuwa da kansa dan kada masu ganin sa da daraja su ganshi girma ya fadi, dan haka sai dai duk sanda ya bukace ta ya turo direbansa a kaita can gidan sa ta kwana, dan haka dakin ta ta wuce ta hado 'yan kayanta. Har ya isa kusa da ita ya zauna bata san ya zo ba, dan tabar shaidan din ta fara gaya mata karya, ta jingina da kujera ta lumshe idanuwanta tabar tana tsakanin hannunta.A hankali ya zare tabar dake tsakanin hannunta, kamar wacce ya tsikarawa allura ta bude idonta firgigit ta ware manyan idanuwanta a kansa suka yi ido hudu, sai ta yi zaton ko gizo yake mata kamar yanda yake mata tun dazu. dan haka ta mai da idanuwanta ta lumshe wai ta daina ganin gizon sa, sannan ta kai tabar ta bakin ta da zummar ta kuma zuka, amman sai taji wayam babu komai, ta bude idonta da sauri a kansa, shine din dai da gaske yana taya ta shan tabar tata. Haushi da takaici ya cika ta tama rasa yaya za tayi masa, amman ta san ba kowa ne yayi mata wannan iskancin ba illah Asma, dan haka ta mike da bala'inta ta nufi dakin kwanan Asma din, sai gata sun ci karo a hanya, ta ci uwar kwalliya sai kamshi take zubawa rataye da jaka a jikin ta. Ta rike kugu tana harararta, ita dai Asma dariya ta sanya sannan ta nufi Mustafa ta cilla masa makullin tana fadi cikin harshen turanci "Take care, good night." "Wai Asma wannan wane irin iskanci ne?" Zainabu ta tambaya a kule. Asma ta daga kafada alamar Oho sannan ta fice da saurinta tana dariya. Ta kulu matuka, ta mai da kallonta ga Mustafa dake kallonta yana murmushi ta ce, "Wai kai kana gani kayi mini dabara ne, to ka sani a yanzu na girmi wayo da dabararka, sanda ka yi kaci nasara dai ka yi amman ban da yanzu, don haka sai ka zauna ka jire mata gida." Ta dauki dan yalolon gyalenta da jakarta ta nufi kofa. Sai dai ina ya rigata dan mikewa yayi da azamarsa ya sanyawa kofar makulli ya cilla makullin cikin aljihun wandonsa. Ta yi tsaye tana kallonsa cike da takaici da masifa, ya isa gaban ta ya tsaya cak ya zira hannuwa cikin aljuhunsa ya ce, "Ga ni gabanki kiyi mini hukunci daidai da laifina zan iya dauka, amman ki yi mini alfarma ki daina gudu na sannan ki dai na mini kallon kiyayyar nan dan yana bakanta mini raina, domin Allah ya jarabceni da son ki Zainabu, na gaza kallon kowace mace da daraja a rayuwata, ki taimaka ki yafe mini laifin da nayi miki nasan mai girma ne, amman na yi ne ba da son raina ba." Ta rike kugu tana kallonsa idanuwanta sun sauya launi zuwa jawur, duk wannan farin da kyallin babu saboda tsabar dacin ran da take ciki, tayi wani yake wanda yafi kuka ciwo sannan tace, "Mustafa na sanka tuntuni gwani ne kai gurin iya yaudara, da irin wadannan kalaman ka sami nasara a kaina a wancan lokacin hadi da kuruciya da talauci da son kudi irin na Mahaifiya ta, sai dai ka sani a yanzu Zainabu Abu ta wuce duk iyakacin tunanun ka, baka da sauran kalmar da zaka iya yaudararta da ita, baka da kudin da zaka iya yaudararta dasu, domin ina mu'amala da wadanda suka fika kama daga Gwabnoni sai Sanatoci da Ministoci zuwa manyan 'yan kasuwa dake rike da akalar Nigeria, dan haka yanzu ina da kudi da farin jikin da nafi karfinka, a yanzu idan na buga waya kadai duk abinda nake nema zan samu, dan haka kaga baka da makamin da zaka yaudari zuciyata a yanzu, duk da kana takamar kaine silar fadawa ta a wannan muguwar harkar da kullum nake tsinewa mara albarka." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ya kuma kwantar da murya ya ce, "Zainabu tunda na diro garin nan na ganki nasan lallai ba Abun da na sani da can bace, kuma ban dawo rayuwarki dan na nuna miki kudi ko kyau ko mukami ba, na zo ne da sunana Mustafa masoyin ki nida zuciya ta kadai ina fata zaki yafe mini abinda nayi miki can baya, sannan na mai da matsayina da martaba ta a zuciyarki kamar da, koma yafi haka don a yanzu Mustafa bai zo da zummar fasikanci ba sai dai da zummar auran Zainabu, domin a yanzu Ubangiji ya jarabi zuciyar Mustafa da tsananin son Zainabu." Ta kalleshi a lalace tamkar ta ga mahaukaci sabon kamu tace, "So! So! Lallai ka hadu da mugun ciwo idan har da gaske kake, balle na san karya kake yi, domin kai mutum ne mai yaudara da karya, don haka ka bude mini kofa na fice kawai, dan bana son ko kallon fuskar ka domin kai ne mutumin da ya sanya rayuwata a cikin fargaba da tashin hankali, nasha azabar da har abada ba zan manta da ita ba dan haka bude mini kofa na fita ko na daina ganin azzalumar fuskarka!" Ta karasa maganar tana hargowa. Ya hadiyi wani miyau mai daci, maganganunta suna yi masa zafi da suya a cikin zuciyarsa, dan haka da kyar ya iya buda baki yace, "Zainabu ba zan bude miki kofar nan ba har sai kin amince dani kin yarda yanzu ni ba mayaudari ba ne..." "Ba zan taba yadda da kai ba, ka bude mini kofa kawai na fita tun ban maka rashin mutunci ba wallahi." Yana tsaye kyam babu alamun zai ko motsa, ranta ya kuma baci matuka, ta ga lallai da gaske yake dan haka ta nufe shi da azama ta kama kokarin kwatar makullin, nan fa suka fara kokawa amman ina namijin duniya ne maji karfi dan haka ta gaza kai hannunta balle ta iya dauka har karfinta ya kare, tayi kokarin janye jikinta amman ya hana ta hakan dan ta tuno masa da wani lokaci da wasu al'amura da ke masa dadi da sanya shi nishadi a duk sanda ya tuno. Tayi kokarin ta kwace amman ta gaza sai ma wani abu da yake shirin jawo mata dan shin din daban ne a zuciyarta ya san kanta da yanda yake samun ta a sama, daman haka yake so ta shiga jikinsa dole sai ta sakko don dai shine ya santa ya san wacece ita, tayi luf a faffadan kirjinsa mai kirar zaki ta gaza kasa aiwatar da komai. Ya sami yanda yake so dan haka yake da salon yaudarar da sace zuciya, yanzu kam ya soma nasara a kanta dan tana jin zafinsa a ranta amman tana matukar son sa, dan haka komai ya kwance mata, Mustafa ne namiji daya tal da idan tana tare da shi take manta kowa, amman duk sanda take tare da wani sai ta tuno shi da soyayyarsa, don haka bata da karfin halin da zata kwaci kanta duk da haushinsa da take ji, dan haka sai ta fashe da kuka kawai. Jikinsa ya dauki rawa don yasan ba karamin abu ke san ya Zainabu kuka ba, don tana da taurin zuciya, dan haka cikin tausasa murya da rada ya ce, "Zainabu don Allah ki yi hakuri ki yafe mini na tuba....."."Me ya sanya ka tafi ka bar ni sanda nake tsananin bukatar ka a rayuwa ta eye?" Ta tambaye shi tana kuka. "Ki yi hakuri na san nayi miki lafi, sai dai na yi miki alkawarin ba zan kuma barinki ba har abada, ni din naki ne ke kadai, ba zan iya kuma barinki ba Zainbau, ni kaina na sha wuya, na yi miki alkawari." Ta yi luf ta gaza cewa komai dan yayi mata yanda ba zata iya kuma musa masa ba, anan suka baje suna shashancin su. Sai karfe goma na safe suka sami sukunin tashi suka fada wanka sannan suka yi sallah, sannan Zainabu ta fada kicin da sauri don ta samar musu abin da zasu karya dan yunwa suke ji matuka. Ya bita kicin din tana sanye da wani dan guntun siket, tare suka yi aikin suna ta dariyarsu. San da suke karyawa yayi mata kuri da ido yana kallo don Zainabu ta bashi mamaki, ta wuce duk yanda ya santa, gaba daya ta gama haukata shi a daran jiya, yanzu abu daya ya rage masa ya auri Zainabunsa ya huta, kullum yana manne a jikin ta shi kadai, sai ya ji wani kishi ya kama shi mai tsanani dan bai san iyakacin adadin mazan da ta yi mu'amala ba, sai yake da na sanin tafiya da yayi ya bar ta, da shi kadai ya san abarsa. Ita ma wani irin farin ciki take ji a cikin zuciyarta, dan ta sha karo da maza kala-kala a yawon iskancinta, amma bata ji wanda ya taba yi mata dai-dai da Mustafa ba, don haka tana yin bariki ne bawai dan dadi ba sai don neman abun duniya(Allah ya kyauta), Zainabu hatsabibiya ce ta kin karawa, dan haka maza da dama ke shan wahala a kanta, yanzu ma mikewa tayi tsam ta isa inda yake ta zauna cinyarsa, ta sakala hannuwanta a wuyansa ta mika masa bakinta wai ya sammata abin da yake taunawa (wainar kwai), bai yi mata gardama ba dan shima gwani ne, dan haka ya hada bakinsa da nata yana ciyar da ita abinda ke bakinsa, da haka ta dinga kara susuta shi tamkar wani karamin yaro ta mai da shi. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Bayan sun kammala cin abincin suka yi masauki a doguwar kujera mai cin mutum uku. Ta kwanta lamo a kirjin sa tana shafar sa tamkar mage, cikin kunnensa ta ce, "Musty wai me ya sanya ka tafi ka bar ni sanda nake tsaka da bukatarka?" Yace, "Sai kin sanar da ni irin wahalar da kika ce kin sha sannan zan sanar dake nima." Ta yi kwafa tana fadin, "Labarina mai cike da abun tausayi ne da takaici, domin daga ranar da na nemeka na rasa na shiga tashin hankali, naje har gidanku aka ce mini daman hutu kazo wai a kasar waje kake karatu, na shiga tashin hankali da ciwo mara misali, abu fa kamar wasa sai ciwo ya dinga yin gaba, da farko na zaci ciwon soyayya ne, sai da abu yaci tura aka gano ashe ciki ne dani....." "Ciki da gaske Zainabu ko na wasa?" Ya tambaya da sauri. Ta yi dariya tana fadin, "Da gaske Musty wallahi ciki ne na gaske, kai ai munga tashin hankali ni da Sala a wannan lokacin." "To yanzu ina abun da kika haifa din?" Ya kuma tambaya. Ta tabe baki tana fadin, "Cabdijam, ai tuni muka zubar da shi." Ya dafe kai yana fadin, "Ya salam, ai sam ban san kina da ciki ba, har na ji ina son abuna wallahi Zainabu." Ta warware masa duk abin da ya faru sannan ta dora da cewar, "Bayan mun gama da wannan muna murna mun dawo gida da kwanaki kuma sai ciwon ciki ya balle mini ga zubar jini kamar jinina zai kare, amman da muka je gurin shegen likitan da ya zubar mini da cikin ya caje mu kudi masu yawa gashi a lokacin bamu da komai duk mun saida 'yan kadarorinmu, don haka yace ba zai taba ni ba, sai nurse din da tayi mana hanya ce tace muje asibitin kuroda tun da dai yanzu ba zubar da ciki bane zasu karbeni, gahi an kwana biyu da zubar da cikin sai nace ina da aure bari na yi, sai ta shige mana gaba da sunan ni 'yar uwarta ce daga kauye aka kawo ni. Amman duk da na Gwabnatin ne ma sai da aka rubuta mana magunguna masu tsada ga karin jini, sai yaya na ne ya bada jininsa aka diba, sannan Sala ta je ta ciwo bashi aka sayi magunguna, lokacin adadin kudin kusan dari shida ne. Bayan na warke muka fara tunanin inda zamu samu kudin da zamu biya dan daman irin kayan nan na bashin watan nan ta amsa ta karyar da su ta saida sannan aka sami kudin, don ma matar tana shakkar Sala ba tayi magana ba, da na samu sauki sosai Sister din nan ta bani shawarar na dinga fita good evening (karuwanci), cikin kankanin lokaci komai ya sauya domin dai kasan ni ta daban ce." Suka yi dariya gaba dayansu sannan ta cigaba da maganar, "Yaya Sadiku kamar zai shake ni ya kashe ni don tsabar tsana da yayi mini, don har cewa yayi da ya san ci gaba zanyi da iskanci da bai yadda an kara mini jininsa ba, gwara na mutu kowa ma ya huta, sai da Sala ta tsawatar masa harda barazanar zata tsine masa idan bai fita harka ta ba sannan ya saurara mini. Sister ce tace na koma karatu domin rayuwa babu ilmi tana tawaya don haka Sadiku na komawa ya maidani makaranta wacce na yi kusan wata shida banje ba, da farko yace ba zai maida ni ba sai da nayi masa alkawarin ba zan kuma yawo ba sannan ya yadda ya kwashi katina da zai tabbatar da bani da lafiya ne sannan muka wuce makarantar. Sanda muka isa Principal dinmu ta ce ba za ta amshe ni ba domin dai nayi wajen wata shida ban zo ba 'yan ajinmu har sun zana jarabawar sake aji . Sadiku ya marairaice yana bata hakuri, ji nake kamar na harbe shi don haushi, daga karshe ya dauko kati ya bata don ta tabbatar bani da lafiya ne. Ta ware idanuwa domin dai duk da bata fahimci abinda likitan ya rubuta ba ta fahimci kalmar (bleeding after abortion), wato zubar jini bayan bari, ta daga katin cike da tsana da takaici take kallona sannan ta fara magana. "Lallai yarinyar nan kin cika tantiriyar 'yar iska, bayan iskancin da rashin kunya har karuwanci kike tabawa, kamar ki ace an zubar miki da ciki? Kai tir da halinki, Allah ya wadaran halinki." Sai ta jefeni da katin akan fuska ta. Sadiku ya mike jikinsa yana rawa domin bai san likitocin da suka yi mini karin jini sun rubuta bari nayi ba don bai san karyar da muka shirya ba, sannan bai tsaya ya duba katin ba duk da ba komai zai gane ba ma, ya fara magana da rawar jiki, "Don Allah Hajiya kiyi hakuri kaddara ce da tsautsayi....." "Da kuma sakaci da rashin tarbiyya." Ta karbe daga bakinsa, sannan ta dora da cewa, "Wallahi ka ji na rantse yarinyar nan ta gama zama a makarantar nan, alfarma daya zan iya yi maka na rubuta maka takardar (transfer) canji zuwa wata makarantar, don ban ga amfanin zama da daliba irin ta ba, ita ba kokari ba sannan ga shegen iskanci ta addabi dalibai da malamai tun yanzu tana matsayin kwaila, ina ga ta zama babbar mace? (No i can't) ina ba zan iya ba." ta karasa maganar a hasale. Ni kuwa ina gefe na cika nayi fam, domin Sadiku ya gaza rama mini cin mutuncin da matar nan take mini, don haka na mike daga tsugun nan da nake yi na dole, domin tun a gida ya gargade ni na durkusa da munje kuma na gaida ta don ta san na yi hankali. Ke! Ma ya ishe ki haka, haka kawai zaki sanya ni a gaba kina zagina kamar wata uwata? Ko abun da yafi ciki nayi ina ruwanki, idan ba zaki karbe ni a makarantar ki ba kawai kice ba zaki karbeni ba amman kin saka ni a gaba kina zagina, ke wayasan iskancin da 'ya'yanki suke..... Marin da Sadiku ya dauke ni dashi ne ya sanya ni yin shirun dole, na dinga dubansa da jin haushi kamar nayi masa Allah ya isa, amman tunda lallabashi nake yi ya sanya na hakura ina ta kunkune dai. Kana ji a gabanka tana zagina ma ko? To maza ku bar mini Ofis dina tun ban hada ku da (security) ba, ta fadi a hasale. Ya dauki katin da yake a kasa yace, Malama nagode, kiyi hakuri hali ne kowa da irin nasa, sannan ya dubeni yace idan kin ga dama sai ki taho mu tafi. Bai jira abinda zan ce ba ya fice daga Ofis din. Na dalla mata harara ina fadin, "Allah ya sanya ba kece kika kawo ilimin boko duniya ba, sannan Mangwafak ba dan gidanku ba ne, don haka zanyi karatu a wata makarantar ko kina so ko baki so....." "Ki fitar mini daga Ofis dan ubanki ko na sanya a zane mini ke ko na hada ki da 'yan sanda su kulle mini ke wallahi shegiyar yarinya mara kunya kawai karuwa..... Na ce, "Kin ga karuwa dai a gidanki ba niba." Ina gama fadin haka na ficewata ina hangota sanda ta zauna a kujera cike da bacin rai da bakin ciki mara misaltuwa, na dai ji dadi don na rama wulakacin da tayi mini. Bayan mun dawo gida Sadiku ya yi kamar ya cinye ni don bala'i, yace kuma babu ruwansa da ni, don haka na rasa yanda zan yi na koma karatun, don na gane idan mutum yana zuwa makaranta yakan rage 'yan sa ido. Daga karshe dai Sister Asibi ce ta yi mini hanya na koma Sheka da karatuna, acan dai na kammala Secondary dina, bayan sakamako ya fito babu lafi na samu admission a FCE, domin a wancan lokacin ba'a tsaurarawa gurin makin jarabawa, don haka da 2 credits 2 passes na sami admission. A wannan lokacin ne na kuma wayewa na san lallai da kai na a duhu yake, duk da dai ba wani karatun ne a gabana ba, na hadu da malamai 'yan ban gishiri na baka manda da taimakonsu na kammala. Dai- dai lokacin da na kammala karatuna na hadu da wani dattijo ma'abocin son holewa DPM ne a wata karamar hukuma. don haka tunda ya kyalla idon sa a kaina ya makale mini, shine dai ya kawo min takardar fara aiki (upper) har gida tun sakamako na bai fito ba, don haka na fara aiki na, amman fa a kanyi wata banje Ofis ba domin dai ina da manya a sama, sun ajiye ni a cikin Sakateriya bangaren (Accountant), mai raba kudi, don haka Salary bana wasa nake samu ba, duk da ba abinda na karanta kenan ba kasan Nigeria jaga-jaga inji wani mawaki, don wallahi wadanda muka yi karatu dasu da dama basu sami aiki ba har yau, kuma yawancinsu sune masu kokarin sun fito da first class amman da yake basu da wani a sama suna zaune, kai Nigeria sai a slow wallahi." Ya yi dariya yana fadin, "Wallahi ke din nan 'yar buyagi ce, ni kaina wani lokacin tsoro kike bani, barin ma yanzu, don haka ne ma na dinga jin tsoron dawowa don kada kiyi mini buyagin naki." Ta yi dariya gami da kai masa bugu na wasa, suka kama dariya gaba dayan su, sannan ya gyara zama yana kuma shinshinarta kamar wata diyar mage sannan ya fara bata labari kamar haka.Kamar yanda kika sani daran da yayanki Sadiku ya yi mini wannan wulakancin na tafine raina a tsananin bace, domin tun da nake ba'a taba mini wulakanci kwatankwacin wannan ba, don haka na kudirta a raina na hakura dake tunda daman yace duk randa ya kuma ganina a kofar gidan ku sai ya sanya an jefe ni, ni kuwa bana son iyayena su san halin da nake ciki sam. Sai da na koma gida ne ma sannan na tuna da abinda ya kaini gurin ki, don muyi sallama ne ni zan koma makaranta duk da na san ban taba gaya miki hutu nazo ba. Sai da tafiyar ta kama gadan-gadan sannan na ji wani irin masifaffan son ki yana bijiro mini da kewar ki, amman na dake don ina ganin da zarar na bar garin duk zan daina ji, don haka na bar Kano da zummar na bar Zainabu Abu na nufi birnin Califonia. Sai dai tunda na isa garin na jini kamar wani mara lafiya, surarki da kamar ki ta dinga bijiro mini don haka na yi zaton ko kewar ki ce, don haka na fara mu'amala da mata kala-kala masu kyau masu ilimi har ma da masu dukiya, amman sun gaza gamsar dani kamar 'yar kwaila Zainabu, amman na dinga yaudarar kai na da lallai sai na manta Zainabu, duk macen da na kalla sai naji na raina ta burin yana ga Zainabu, na ki na dawo hutu don ina ganin idan na dage zan manta dake din, sai dai iyayena suzo mini hutun can, har na kammala karatuna kina nan a raina na kuma baiwa kai na wani lokacin na mantawa da ke, don haka na fara aiki a can duk da ba haka iyayena suka so ba, sai dai shi Mahaifina mutum ne mai saukin kai da baiwa mutum damar sa inda yaga babu cutarwa a kanta. Dare daya na ji duk iyakacin dauriyata ta kare, musamman da nake ta fama da yawan ciwon kai da aka auna ni akace na rage sanya damuwa a raina, na yadda muddin na cigaba da zama a can ciwon zuciya yana gan da kamani saboda yawan tunani, na yanke shawarar zan dawo Nigeria na neme ki amman a wannan karon auranki zan yi, don na gane kece kadai nake so a rayuwa ta, na kuma yi kokarin jifan tsuntsu biyu da dutse daya don daman iyaye na sun damu da lallai na dawo nayi aure.Sai dai idan na tuno ki sai naga kamar na rasa ki ko kin yi aure, da zarar na tuno hakan sai naji duk hankalina ya tashi, na yawaita sallah da rokon Allah ya sanya baki yi aure ba, da wannan shawarar na dawo gidan Nigeria, da zummar ko a yaya na sameki zan aure ki, don ban yi zaton Abun da na sani zata koma mace mai girma da daraja da aji kamar haka ba, don dai a yanzu so ne tsagwaransa a raina ba wata sha'awa ba. Sai dai na sha mamaki a yanda na ganki a yanzu, nasan tun a can baya kina da kyau don yana daya daga cikin abunda ya sanya nayi mu'amala dake, ga tsabta koda yaushe zaki wuce ta gaba na sai na ganki tsaf dake, takalminki kamar ba kya sakawa.Don haka Zainabu ba da wasa na dawo ba da zummar na aure ki na dawo, don haka bana son a dauki wani lokaci mai tsaho, sannan dole ki daina kula 'yan iskan samarin nan naki don ina da kishi mai tsanani, shi ya sanya a wancan lokacin ma nayi kokarin ganin baki kula kowa ba, don haka Zainabu gani gabanki da kokon barata ina fata zaki amince da bukata ta." Tayi dariya cike da jin dadi ta ce, "Lallai Mustafa ka debo ruwan dafa kanka, ta yaya zaka ce kai kadai zan dinga kulawa bayan ba mijina kake ba? Ai hakan ba mai yiwuwa bane ba." Ya mike zaune yana mata wani duba idonsa fal da masifa ya ce, "Wallahi kina so ne na fara rotse a kofar gidanku, don duk dan iskan da yayi mini rainin wayo a kanki zan yi maganinsa, da can sun yi yanda suke so, yanzu kuwa mai guri ya zo kowa sai ya matsa ya bashi gurin sa, duk mai neman kansa da arziki. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ta makalkale shi tana dariya ganin yanda yake masifa kamar zai rufe ta da duka, suka kama dariya don tana masa irin salon ta da take siye masa zuciyarsa. Bugun kofar da akeyi ne ya fargar da su, Zainabu ta mike da sauri tana fadin, "Ina zaton shegiyar nan ce ta dawo." Ta dubi agogo sha daya da minti uku, sannan ta nufi kofar da sauri tana kokarin budewa. Asma ta shigo da gudu tana ihu da dariya tana fadin, "Shegiyar ashe akwai mai maganin iskancinki, gaskiya Mustafa ka ci a baka na daya, ya ci a sara maka wallahi, don kayi mana maganin mai shegen taurin kan nan." Mustafa ya mike tsaye yana dariya sannan ya ce, "Daman ke muke jira mu wuce." Ya mika mata makullin sannan ya dubi Zainabu ya ce, "Ke madam sai ki shirya na sauke ki a gida ko, don na san idan na tafi wannan dan iskan ne zai zo ya dauke ki." Suka fashe da dariya ita da Asma har da tafawa, yayi murmushi yana fadin, "Lallai kwa yi mini dariya don kun san kun kama wuya na, ni kam na wuce mota kya tadda ni a can." Har ya kusa kaiwa kofa sannan ya tsaya yana fadin, "Ahaf! Hajiya Asma na gode kuwa zan gan ki." Tayi dariya tana fadin, "A'a don ni kada ka damu babu damuwa ai duk yiwa kai ne, don bani da kamar Zainabu duk Kano." Yayi murmushi ya ce, "Na dai gode din sai mun sake haduwa." Sannan ya fice. Asma ta kalle ta gami da fashewa da dariya su dukan sannan suka tafa Asma ta ce, "Wallahi kawata kin iya iskanci, ki dubi yanda kika juyar da zuciyar dan talikin nan a lokaci kankani don Allah, don Allah yaushe ne zaki sanar da ni sirrin nan ne?" Zainabu ta tafi tana fadin, "Sirri ne abin." Asma ta bita da gudu tana fadin, "Haba kawar, ki taimaka mini don Allah." Zainabun tayi dariya sannan ta ce, "Ki bari sai mun hadu kinga yanzu lokaci ya kure, don zumana yana jirana a mota." Suka kuma fashewa da dariya, sannan Asma tace, "Lallai Mustafa ya ciri tuta don ban taba jin kin ambaci wani namiji da ko sunan da iyayansa suke gaya masa ba, daga shashasha sai dan wahala ko dan akuyan can, amman Mustafa yaci Zuma gaba daya ma." Zainabu ta zame da sauri ta falla da gudu tana fadin, "Malama ki kyale ni haka nan, kina bata mini lokaci." Sanda suka isa gida duk 'yan biki sun gama watsewa sai dai sauran kwadayayyu, sun jima a mota suna sallama sannan ta fita tana takawa da tafiyarta ta daukar hankalin 'yan maza, sai da yaga shigarta gida sannan ya ja motar tasa cike da tsananin sonta, da wani nishadi da farin ciki. Tana shiga Sala ta kama yi mata sannu da zuwa, ta sami kujera 'yar tsugunne ta zauna don cike take da nishadi. Sala din ta kama murmushu don ganin diyar tata a cikin farin ciki sannan ta ce, "Hala yau diyar tawa ta hadu da mai barin dala ne naga bakin naki ya ki rufuwa." Ta yi 'yar dariya sannan ta ce, "Sala kin san abun mamakin da ya faru kuwa tun daran jiya?" Bata bari ta bata amsa ba ta dora da cewar "Mustafa ya dawo." Da mamaki Sala din tace, "Mustafa kuma? Waye me wannan sunan, ba dan dan banzan yaron nan da ya cuce mu shekarun baya ba can?." Zainabu ta bata rai matuka kamar zata yi kuka, ganin haka ya sanya Sala din ta tsuke bakin ta, don ta yi zaton zata yiwa Zainabun gwaninta ne, don ta san irin alwashin da taci akan Mustafa. Ita kam mikewa tayi tana fadin "Ashe daukar hakkinsa muka yi daman, don ba laifin sa ba ne." Ta sha ruwa a randa sannan ta dawo ta gaya mata duk yanda suka yi da Mustafan. Sala din tayi dan murmushi tana fadin, "A'a lallai bashi da laifi to mun yafe masa." Zainabu ta ji dadin abunda Sala din ta fadi, don haka ta mike tana dariya sannan ta ajiye mata damin 'yan dari dari na dubu ashirin tace, "Sala gashi nan kya kashe." Sala din ta dauka tana dariya sannan ta ce, "Ke Zainabu ba kya gajiya? Na ga fa kin sha kacaniyar biki kwanan nan." Zainabu tayi dariya tace, "Ai Mustafan ne ya bada ya ce a baki kya sha ruwa kafin yazo bada hakuri da kansa." Sala ta fashe da wata wawiyar dariya sannan ta ce, "Kayya ki gaya masa ya kwantar da hankalin sa komai ai ya wuce gashi kin ce daman ba laifinsa ba ne." Ita dai Zainabu daki ta shige domin tayi baccin gajiyar kwanakin da bata yi ba can baya, kafin yamma tayi su hadu da zuman nata ************ Cikin kwanaki kalilan soyayya da shakuwa ta kuma shiga tsakanin su, duk da suna rikici duk lokacin da Mustafa ya ga Zainabu da wasu Musamman Alhaji.... Dan haka duk inda tasan zata gamu da samarin ta kan guje masa don bata son ace kullum suna samun sabani da Mustafa dan yana da matukar kishi, su kuma sun gaza hakuri dan duk kusan namijin da ya fara mu'amala da Zainabu bai iya daina wa dan ta fiye fitina da yawa, sai dai idan Allah ne ya kwato shi daga hannunta. Shi kam Mustafa kullum hankalin sa a tashe yake dan bai kaunar ya ga Zainabu da wani, dan haka nema suka yanke shawarar yin aure a wannan lokacin. Shi kam yana shakkar tinkarar Momin sa da maganar auren nasa don ya san ta bata san wargi sam ita, ga shi daman kullum tana masa maganar ya zabo mace cikin 'yan matan gidan ko kuma ya duba cikin 'yan uwa masu tarbiyya dan bata son yayi zaben tumin dare, sai dai shi a iyakacin ganinsa daga 'yan matan dake cikin danginsu har na waje bai ga wacce tayi masa kamar Zainabunsa ba. Yau ya tadda Momin nasa a karamin falo, 'yan matan ta suna karamin falo suna kallo sai musu a keyi tsakanin 'yan matan, don gidan nasu bai rabo da 'yan mata na 'yan uwa dan su basu da yawa su biyu ne kacal, gashi Momin su tana da son jama'a dan haka koda yaushe gidan a cike yake banda masu zama dindindin, banda kuma wadanda aka aurar, dan haka tunda ya ga take-taken Momin na su na son ta hadashi da wata a cikinsu shi ya sanya ba ko da yaushe yake sakar musu fuska ba. Ya shiga falon da sallama, ita kadai ce don ya baro Alhajinsu a falo da baki, ya isa gaban ta ya gaishe ta, sannan ya koma babbar kujera ya zauna, ya dubi tibin inda yaga hankalinta ya karkata. Yakin Falastinawa ne dai da Isra'ilawa wadanda kanwa uwar gami America ke daurewa gindi, ana nunowa a tashar C.N.N. "Kai wadannan mutanen wallahi azzalumai ne, ka dubi yanda suke kashe farar hula da basu ji ba basu gani ba, sannan su yi farofagandar basa taba farar hula, Allah dai ya bi musu hakkinsu kuma ya nuna musu karshen su, Amin." Hajiya Kubra ke fada da bacin rai. Mustafa ya ce, "Haka ne Momi, sai dai idan kika duba daman can zaki ga abun nasu bawai suna yi bane don wani abu sai don su yaki addinin musulunci kawai, yanzu fa idan kika shiga kasashen turawa da gemu sai kaga an mai da kai wani abin tsoro saboda sunyi farofagandar batawa musulmi suna a idon duniya, dan ma yanzu Allah yana nuna musu ishara mutanan su turawa sai musulunta suke, musamman matansu kamar su Kristian Barkeu da 'yar uwar tsohon shugaban kasar Birtaniya Tony Blair, Laurent Bothh wacce ma'aikaciyar jarida ce, da sauransu, shine fa muke dan samun sassauci a gurinsu, abun nasu dai sai addu'a." Ta amsa da "Amin, ina wai ka shiga ne?, tun da safe nake saka rai da shigowarka amman shiru." Gabansa ya fadi, don yanzu sam bai zama a gida kullum suna makale da Zainabunsa, amman sai ya dake ya ce, "Momi kin san ina fafutukar fara aikin tun da sun bani (offer), takardar daukar aiki, shi ya sanya yanzu bana zama." Ta ce, "Lallai kam haka ne, Allah dai ya taimaka ya sanya a fara a sa'a." Ya ce, "Amin." Sannan ya kama inda-inda don ya rasa ta yanda zai gaya mata. Hajiya Kubra ta dube shi tana dariya tace, "Babana duk yanda aka yi da magana a bakin nan naka." Da yake sunan Baban ta ne da shi. Ya yi murmushi yana sosa keya ya ce, "Momi sirika na yi miki shine nake kunyar sanar da ke."tayi dan murmushi dan ba hakan taso ba taso ace anyi 'yar gida, amman sai ta danne dan tana son yayi auren, dan haka tace, "Lallai kam kace yau zanyi kwanan farin ciki, a ina ka samo matar taka ko a can American ne?" Yayi dariya ya ce, "A'a Momi a can dai unguwar da muka taso take, can kasan layinmu na da, sunan ta Zainabu." Ta ce, "Lallai kam, Allah ya tabbatar mana. Waye kuma Babanta, a wane gida take ne ma?" Da sauri ya ce, "Sunansa Malam Abubakar." Tace, ai shike nan bari Alhaji ya shigo sai a sanar da shi, amman dani na so ace cikin 'yan uwanka da suke gidan nan ka zaba, amman tunda Allah ya kaddara matar taka a waje take ba zamu ja da ikon Allah ba, sai dai muyi addu'a Allah ya tabbatar mana da alkhairi kawai. Ya ji dadin abunda ta ce, yayi mamakin kuma saurin shawo kanta da ya yi, duk da saurin daukar zafin ta. Daga nan suka cigaba da hirar su a cikin hirar nema take cewa tana fatan zainabun tasa mai hankali ce da nutsuwa. Ya ce, "Momi ko ke kika ga Zainabu sai kinyi sha'awarta, ta kammala diplomarta yanzu haka tana aiki ne." Tace, "To ai shike nan, na san dai sai Baban ku ya sanya anyi masa bincike don kada ayi zaban tumun dare." Kirjinsa ya bada ras-ras, amman dai ya dake yace, "Na san ma babu wani aibu da zai tadda ga Zainabu in dai ya sanya mutanan kirki a binciken ba munafukai ba." Tun daga sannan ya ji hirar ta fita daga ransa gaba daya, don bai san irin abinda za'a ce akan Zainabunsa ba, shi kam yaji ya gani dan haka koma me zai faru sai dai ya faru amman shi dai da ikon Allah sai ya aure ta. Da haka yabar dakin mahaifiyar tasa ya nufi na shi, amman yana cike da tunanin abunda zai biyo baya idan suka san wacece Zainabu. Kwanaki biyu shiru babu wanda yace masa ko kala akan maganar, shi kam ya damu kwarai ya ji anyi masa zancan, dan Baban sa ma da suka yi maganar da Hajiya Kubran abinda ta fadi ya maimaita, cewar zai sanya ayi masa bincike sosai. Ya sami wani tsohon abokinsa acan unguwar da suka taso ya ce don Allah ya bashi amana ya binciko masa labarin wata yarinya Zainabu diyar Malam Abubakar kamar yanda aka ce masa, sai dai abokin nasa ya dan sami matsala da farko dan duk wanda yace wa sun san Zainabu diyar Malam Abubakar sai suce gaskiya basu san taba, mutum hudu ya tambaya amman duk ba'a dace ba. Sai da ya isa majalisar da yake zama ya fara kawo maganar neman Zainabu da yake yi, sai wani cikin abokan hirar tashi yace, "Ko dai Zainabu diyar Baba Abbakar mutumin Sudan din nan ake nufi, in dai itace kuwa bai yi mata ba, domin dai kowa yasan karuwar gida ce, duk da babu kyau suka akan maganar aure amman tunda dai amana ya baka sai ka sanar da shi gaskiya in dai ita ce din, da dai kanwarta da aka yiwa aure kwanaki ce ma da sauki dan ba halinsu daya ba." Nan suka hau sanar dashi irin halinta dan gaskiya shi ma'aikacine bai fiye zama ba sai karshen sati kuma yawanci hirar siyasa suke yi da matsalar da kasar ke ciki. Ba shi da wani ja Zainabu diyar Baba Abbakar ce dai dan abokinsa yake nema, dan haka ya je ya sanar dashi yanda suka yi, daga karshe har kofar gidan su Zainabun suka zo tare ya nuna masa. Haka nan Alhaji Abdullahi ya koma gida jikin sa sanyi kalau, domin dai ya tabbatar da lallai itace wacce dansa ke so, shi kuwa duniya sam bai san ya takurawa dan sa, yaso ace Zainabu da dan sa yake so ta kasance kamila ce ba lalatacciya ba, kafin ya shiga sallar Magariba ya kirawo wayar Mustafa yace lallai idan an idar da sallah yana son ganinsa,babu bata lokaci Mustafa ya iso gidan dan kusan tare ma suka yi sallar Isha'i da Baban nasa, ya dade a raka'ar karshe yana addu'ar Allah ya sanya Zainabu ta zama rabonsa, don yaji muryar Mahaifinsa kamar da zafi shi ya sanya duk ya kidime. Ya riga Baban nasa shiga gida, Momin nasa ta zuba masa abinci amman ya gaza ci duk da uwar yunwar dake addabarsa, dan kada ma Momi ta zargi wani abu ya sanya ya dinga tsakurar kadan yana ci har ma taso ta gane. Ta dubeshi da kulawa ta ce, "Baba anya wani abu baya damun ka? Na ga kwana biyu duk ka wani shiririce, balle yanzu ka gaza cin abinci sai tunani." Ya kakalo murmushi yana fadin, "Laaa! Momi me kika gani? Babu komai gajiya ce dai kawai." Ganin tana son ta gano shine ya sanya ya saki jikinsa yaci abincin sosai, har Baban nasa ya shigo, ya shige sashinsa ya kira Hajiya Kubra ta wayar gida (land line) ya ce, "Baba ya shigo ne? Idan ya shigo kuzo tare ke da shi." Ta amsa da "Ya shigo, ga munan zuwa." Bayan ta ajiye wayar ta dube shi duk ya sha jinin jikinsa ta ce, "Alhaji yana kiranka." Sannan ta mike ta nufi sashin Maigidan nata yana biye da ita a baya har suka isa. Mustafa bai zauna akan kujera ba a kasa ya zauna ya sunkuyar da kansa yana gaida Baban nasa, fuskar sa babu annuri yake amsawa, ba kamar yanda ya saba amsa masa da sakin fuska ba, hakan ne ma ya sanya gaban Mustafa ya cigaba da faduwa dan yana ganin lallai wani abu yana shirin faruwa. Sun jima a haka yana cigaba da duba jaridar leadership da suka taddashi yana dubawa, labarin ya dauke masa hankali wanda aka ce wai waye ya haifi Obasanjo, sai da ya karasa shafin da yake sannan ya daga kai yana duban Mustafa kur da idonsa, abinda ya kuma fadar da gaban Mustafa. Can ya daure ya ce, "Baba ka ce yarinyar da kake nema acan kasan layin da muka taso take har ma ta kammala karatunra a F.C.E ko?" Bakinsa yana rawa yace, "Haka ne Baba." Alhaji Abdullahi ya kuma gyara zama ya ce, "To nayi bincike kamar yadda addini ya umurci muyi a duk sanda aka tashi neman aure, sai dai abun takaici duk mutanen da aka tambaya wadanda ba zasu yi karya ba sun sanar dani ko wacece Zainabu, dan haka sam ban yarda da tarbiyyar ta ba da ta gidansu ba ma gaba daya, don haka kaje ka nemo wata, ba zan maka auren dole ba amman ya dace ace ka samo mace mai mutunci da daraja a idon duniya." Hankalin Mustafa ya yi mugun tashi ransa ya baci, makwallaton sa sai kaiwa da komowa yake yi, duk da sanyin A.C da fankar dake dakin basu hana shi yin gumi ba, da kyar ya iya bude bakin sa yace, "Baba kayi hakuri bawai zan maka musu bane, ni na san Zainabu diyar kirki ce, ka san halin mutanan yanzu ba duka ne ke fadar gaskiya ba, dan haka ma yanzu idan za'a yi aure ba'a cika zuwa a tambayi mutanen unguwa ba, dan basu kaunar wani ya cigaba, dan haka nasan zasu iya yiwa Zainabu sharri dan haka ina neman yardarka akan na auri Zainabu, watakilama ba wacce nake so aka gaya maka ba." Alhaji Abdullahi yayi dariya dan shi yana da hakuri da bin komai a sannu ba kamar Hajiya Kubra ba mai saurin daukar zafi ba da saurin fushi, sannan ya ce, "Baba bana shakkar ba Zainabun da kake nema aka sanar dani ba, amman bari nayi maka wasu tambayoyi idan har ba ita bace shike nan." Ya goge zufar dake tsats-tsafo masa ba tare da ya iya cewa komai ba Baban nasa ya fara jeho masa tambaya"Asali Abu ake ce mata sanda tana yarinya, yanzu ne ake ce mata Zainabu ko?" Ya ce, "Haka ne." "Kuma da can tana tallar abinci da gyada da dai sauransu ko?" Ya hadiyi wani yawu dan dai ya san lallai Baban nasa ita ya gano, da kyar ya iya cewa, "Haka ne." "Tana da wani Yaya mai suna Sadiku wanda shi ba irin halinta gare shi ba, da kuma wata kanwarta da aka yi mata aure kwanaki ba ko?" Yayi shiru bai bada wannan amsar ba dan dai ya san Babansa yayi bincike matuka akan Zainabu. Alhaji Abdullahi ya cigaba da bayanin sa duk da bai bashi amsa ba, "Babanta mutumin Sudan ne, sunan shi Baba Abbakar, kuma ana kiran Babarta da Sala....." "La'ilaha Illallahu! Yanzu wannan karuwar yarinyar kake so Baba?" Hajiya Kubra ta amshe zancen tun bai kai ga bada amsa ba. Jikin sa ya kama rawa da rawar murya ya ce, "Momi ba karuwa bace, don dai tana aikine a (Local Govt.) ne shi ya sanya ake mata kallon 'yar iska, wallahi ina sonta Baba kayi hakuri don Allah, sharri kawai aka yi mata." Hajiya Kubra ta amshe, "Sharrin gidan Uwar wa? Ai ni sai yanzu ma na gane da ka fadi sunan Mahaifinta Abbakar da sunan Babarta, yarinyar da tun tana 'yar labubuwarta take iskanci, har ciki aka zubar mata tana da shekara sha hudu a duniya." Mustafa ya ce, "Kin ji ba Momi, sharri ne aka yi mata dan ana....." "Sharrin Uwarka? to tsaya ka ji na sanar da kai, na san Zainabu shekarun da suka wuce, yarinya ce mara mutunci kuma mara kunya dakikiya, ta addabi kowa, duk wannan lami ne ma akan iskancin da take yi." Ta dubi mijin nata tana magana, "Alhaji idan baka manta ba na taba baka labarin wata 'yar iskar yarinya shekarun baya da tayi mini rashin kunya har cikin Ofis dina, lokacin ina makarantar 'yan mata ta Dala (G.G.C DALA), dan ranar da tayi mini rashin mutuncin nan kasa bacci nayi, don har sai da jinina ya hau, har yau ina addu'ar Allah ya hadani da yarinyar nan nayi mata rashin mutunci amman har yau Allah bai hada mu ba, sai daga baya ma na ji 'yar unguwar da muka baro ce a bakin wata 'yar ajinsu, sai yanzu zaka ce kana son ta wai kuma da aure ma? Ai ko da ku biyu kuka rage a duniyar nan ba zaka aure ta ba muddin ina raye." Ya dafe kansa idonsa ya kada yayi jajir yana fadin, "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un." Dan ya riga ya gano Momi ta san komai, ta san Zainabu farin sani, ashe ita ce wacce take bashi labari din nan, sai dai ya rasa ta yaya zai sanar da su wannan cikin da take tsanar Zainabu saboda shi dan ta ne yayi shi, ta yaya zai ganar da su shine ya fara lalata Zainabu tun a wancan lokacin da take zarginta, duk da ya tadda Zainabu da wasu muggan halaye amman shine ya koyar da ita kashi saba'in cikin dari. Ya yi tsamo-tsamo da shi kamar wanda kaza ta fashewa a cikin sa, bashi da damar da zai kuma musa musu abinda suka fadi, don idan yace na Babansa sharri ne to na Momin sa fa wanda Zainabu da bakin ta ma ta bashi labari, a sanda take bashi labarin bai yi zaton Mahaifiyarsa bace dan shi ko tambayar ta makarantar da take bai taba yi ba balle har ya gano hakan ba. Alhaji Abdllahi ya katse masa tunaninsa ta hanyar fadin, "Baba ka sani ba wai muna kin Zainabi akan kanta bane, A'a muna kin Zainabu saboda halinta, don babu wanda zai so ace yau ya hada zuri'a da lalatacce, da ace irin halin kanwarta gareta babu abinda zai hana mu kyaleka ka aure ta, dan haka ina baka shawara da lallai ka koma ka sake nemo matar aure dan wannan bata yi ba." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 Idan Zuciya Tagyaru1-05 Posted by ANaM Dorayi on 08:00 PM, 03-Feb-16 Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU _____________ Na ________Fauziyya D Sulaiman_____ "Yo to banda abunsa ma a gidan nan wacce irin mace ce babu kuma masu tarbiyya da kyau idan ma shine ya rufe masa ido, don haka ka kwantar da hankalinka ka zabi wacce ta dace da kai duk 'yan uwanka ne." Alhaji Abdullahi ya amshe, "Ki na ji Kubra, ba wai dole sai anan gidan zai zabi mata ba don zai iya yiwuwa bai ga wacce ta dace da ra'ayinsa ba, ya je ko ina ya samo mata in dai diyar musulunci ce kuma mai tarbiyya." Shi kam duk bai fahimtar duk abinda suke fada don sam hankalinsa baya jikin sa, ji yake kamar ya dora hannu a kansa yayi ta zunduma ihu kawai ko ya ji sanyi a ransa. Alhajin na sa ya ce, "Ka tashi ka tafi Allah ya zaba maka abinda yafi zama alkhairi." Ya mike da kyar yake iya daga kafarsa yana hada hanya tamkar wanda ya sha giya ko kwayar sanya maye, idanuwansa sun kada sun yi jajir da su kamar gauta, har ya fice basu ce komai ba illa binsa kawai da suka yi da kallo. Hajiya Kubra ta ja tsaki tana fadin, "'Ya'yan yau ba'a iya musu, banda haka daga ganin yarinya baka san halin ta ba ka dage sai ka aure ta, ni abun ma mamaki yake ba ni, yaushe har ya dawo garin nan suka kulla soyayya da hatsabibiyar yarinyar nan har ta dauke masa hankali haka? Duka baiyi ko cikakkaken wata guda a garin nan ba, ni ko bayan raina ba zan so ya auri diyar nan ba, Wallahi Alhaji dan baka san ta bane sam bata da kunya da ladabi ko miskala zarratin, tuntuni na tsaneta wallahi." Alhaji Abdullahi ya kuma gyara zama cike da tashin hankali dan dai yana tausayin dan sa, don ya gane ba karamin so yake yiwa Zainabu ba ya ce, "Ai haka Allah yake ikonsa, shi kadai yasan a inda suka hadu, sai dai muyi masa addu'ar samun mace ta gari, da addu'ar ita kuma Allah ya shirya ta." Hajiya Kubra ta ce, "Amin dai." Shi kam Mustafa da kyar ya iya kai kansa sashinsa saboda tsananin tashin hankalin da yake ciki, dan Allah ya sani duk duniya baya ga iyayansa babu abinda yake so sama da Zainabu, ya sani Zainabu wata tsoka ce a cikin jikinsa mai yawo da jininsa, a da can baya yana daukar son Zainabu shirme kuma shiririta a zuciyarsa, sai dai a yanzu ya sani muddin bai auri Zainabu ba lallai kam rayuwarsa tana tare da hatsari. Ya kwanta rigingine a gadonsa ya rintse idonsa, ina ma zai iya kuka da lallai yayi ko ya sami sassauci a cikin zuciyarsa. "Zainabu! Zainabu!" Ya fadi a hankali ko ya ji sanyi a zuciyarsa, ya sani hakkin Zainabu da sauran matan da ya cuta ne Allah ya saka musu ya jarabce shi da son macen da ya raina a da can, lallai da iyayansa sun san irin yanda yake son Zainabu da sun barshi ya aure ta ko yaya take. Haka nan ya dinga juyi a gadonsa bai san sanda bacci barawo ya silalo ya dauke shi ba, don yana cikin tsananin tashin hankali. Da asuba da kyar ya iya tashi dan jikinsa duk ya masa nauyi, a masallaci ya jima yana addu'ar Allah ya karyo da zuciyar iyayansa su amince ya auri Zainabu, har gari ya waye yana ta lazimi, sam ya manta da zuwa Ofis dan haka sai da ya makara. Ko da ya isa dinma kasa tsinana komai ya yi, banda kallon hoton Zainabu dake bisa tebur dinsa babu abinda yake yi, ya sani muddin iyayansa suka hana shi ya auri Zainabu to kuwa lallai zai jima bai yi aure ba, kai babu ma rana. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ya nufi kujerar da ke Ofis din doguwa ya kwanta yana neman layin wayarta, bugu daya ta dauka. Ita ce ta fara magana, "Hello My honey, Zuma ta."Ta fadi da wata irin murya mai tsananin fisgar hankalinsa, wacce ta ke siye zuciyar 'yan maza da ita. Ya yi ajiyar zuciya sannan ya ce, "Zainabu ina tare da matsala mai girma, na rasa yanda zanyi da rayuwata ba ni cikin hayyacina da walwala ta." Ta ji gabanta ya fadi amman sai ta dake ta ce, "Ayya Zumana ka kwantar da hankalinka komai zai zamo da sauki Insha Allah, ka na ina ne yanzu?" Ya lumshe idon sa kana ya bude ya ce, "Ina Ofis yanzu amman na gaza komai, ji nake kamar bani da lafiya ma." Ta kuma kwantar da murya ta ce, "Kana jina ko zumana, ka kwantar da hankalinka gani nan zan zo yanzu Ofis din naka don bani son bacin ranka....." "A me zaki zo ne?" Ya tambaye ta da sauri. Ta yi murmushi don ta san Mustafan ta da shegen kishii ta ce, "Ka kwantar da hankalinka zan zo a shatar tasi ne, don nima ina Ofis yau." Ya ce, "Yayi kyau, ina jiranki kada ki jima." Ta dubi abokin aikin nata da yake kallonta tamkar maye sai dai duk iyakacin jarabarsa da gulmarsa ya gaza jin abinda take cewa, ta galla masa harara kana tace, "Wallahi Oga kai mugun dan saka ido ne, wannan kallon da kake mini fa kamar maye?" Yayi dariya yana sosa keya ya ce, "Ke din Zainabu da tsokano mutum kike, banda ni waye zai daure zama da zukekiyar mace irinki yana kallonta..... yanzu dai ina zaki naga kina shirin fita bayan yanzu D.P.M yayo waya zai zo." Ta yamutsa fuksa tana fadin, "Idan yazo kace masa na fita idan da dama zan dawo." "Zainabu ki yiwa Allah ki tsaya idan ba....." Ko kuma bi ta kansa bata yi ba ta fice abunta ya bita da kallo yana girgiza kai sannan ya ce, "'Yar jidali, yarinyar nan kina gara zama wallahi, ko da yake kin isa ne." Ta isa Ofis din nasu cikin wani ubansu leshi, zanin ya zauna dam a kugunta rafa ne,rigar bata fiye girma ba don da kadan ta iya wuce cibiyarta, sai dai hannunta dogo ne, yanayin kirarta ta kalangu ya fito sosai duk wanda ya kalleta sai ya kara sai dai mai karfin zuciya, kamshinta ka dai zai iya sanya ka kalle ta balle kyau da tsarin tafiyarta. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ta murda kofar Ofis din ta yi sa'a kuwa a bude take don yasan zata zo, ta san Ofis din dan kusan tare suka tare ma, ta shiga da sallama, yana bisa kujera yayi tagumi, har ta isa inda yake bai motsa ba sai dai idonsa yana kanta har lokacin. Matuka kwalliyar ta burge shi, ta isa ta zauna bisa cinyarsa ta janye hannunsa daga tagumin da ya yi, ta shafi gurin tana magana kasa-kasa, "Zumana waye ya taba mini kai?, hankalina a tashe na iso Ofis din nan." Ya daga idonsa yana dubanta, abinda ya kuma bata tsoro don ganin idon yayi jajir da alamar tashin hankali, ta kuma shafar fuskar sa abinda ke sanya shi jin sanyi a ran nasa ta ce, "Zumana ka sanar da ni abinda ke faruwa wallahi hankalina a tashe yake." Ya lumshe idonsa sannan ya fara magana har lokacin tana shafar fuskarsa yace, "Hajiya Kubra tsohuwar Shugabar makarantar ku ta G.G.C Dala wacce kika yiwa rashin kunya itace Mahaifiya ta....." Ta mike a zabure gami da dafe kirji tana fadin, "Innalillahi wa inna ilahihi raji'un, na shiga uku, Mustafa yanzu Hajiya Kubra Mominka ce? Wayyo Allah na yanzu ya ya zan yi? Ina fatan baka sanar da ita ko ni wacece ba?"Ya ware idanuwansa wadanda suke jawur yana fadin, "Zainabu babu hanyar fita, Momi ta sanki farin sani kuma tasan kece Zainabun da nake so yanzu a raina, Baba na ya sanya anyi masa bincike a kanki matuka, ina sonki Zainabu amman iyayena sun hanani auranki, abunda basu sani na yanda Zainabu take haka ma dan su yake, amman na rasa ta yanda zan sanar dasu abinda suke gudun Zainabu saboda shi na dansu ne." Jikinta ya dauki rawa dan ta shiga tsahin hankali matuka, ya kamo ta ya tallafe ta a jikinsa yana shafar ta, ta yi lamo a jikinsa tana ajiyar zuciya tamkar diyar mage, ta ayyana a ranta wannan wace irin masifa ce ta doso su, yanda suke son juna ace an haramta musu auran juna, don dai duniya bata da abin so kamar Mustafa, ta gama sallamawa kanta a yanzu shine bango majinginarta, don ta gaji da walagigin yawon iskanci da shan bakar azaba ta saida mutunci a gurin maza, domin dai ta lura yanzu ta sani babu abinda ke tattare da bin maza sai bata da sai da mutuncin kai, amman gashi wani katon abu na neman ruguza mata wannan burin nata. Ta san halin Hajiya Kubra mace ce mai kafiya da dagewa bisa duk abinda ta sanya a gaba, wuya da dadi basa sanyawa ta sauya daga kan ra'ayinta, bata manta kirarin da malamansu ke mata lokacin tana makaranta, "Mace mai kamar maza kwari ne da babu." Sun yi shiru na tsahon lokaci kowa da abinda yake sakawa a zuciyarsa, sun gaza sanya kansu farin ciki kamar yanda suka saba a duk lokacin da suka hadu don basu gundurar junansu. Ita ce tayi karfin hali tace, "Musty zumana yanzu yaya zamu yi, ko shike nan mun rabu babu mafita?" Ya kuma rungumar ta tamkar zai maida ta cikin sa kada wani ya kuma ganinta sannan ya ce, "Zainabu abinda nake tunani kenan tun daga daran jiya har zuwa yanzu amman na gaza samun mafita, sai dai na sani ruwa ko iska da duk wata azaba basu raba ni da sonki, ko da an rabani dake a fili ba za'a iya cire sonki a raina ba, son ki shine so na gaskiya mai wahalar da ruhin Mustafa da zuciyarsa." Tayi sanyayyar ajiyar zuciya mai cike da jin dadin kalamansa, sannan tace, "Shike nan zumana kada ka damu ka kwantar da hankalinka mu cigaba da addu'a, sannan mu tsaya kan ra'ayinmu na son juna duk wuya da dadi ina ganin zamu yi nasara komai dadewa." Yace, "Hakane Zainabu kin kawo shawara mai kyau, har naji raina yayi fari." Ta kuma kwantar da murya tana fadin, "Kada ka damu ka kwantar da hankalinka ni din taka ce har abada." Ta fara masa salon nata na jan hankali a cikin kunnensa take fadin, "Musty zumana (I love you so much) Ina sonka da yawa." Bai iya hakuri da Zainabunsa musamman idan tana masa salonta na kauna dan haka sai ya shiga maida mata martaninta, ya ma manta inda suke. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 ************** Abubuwa sun hadu sun jagulewa Mustafa har ma da Zainabun kanta, don dai yanzu ba ta iya kallon kowanne da namiji da gashin arziki idan ba Mustafa ba, wadanda take watsewarta dasu a da can ma ta kisu yanzu, kawarta Asma tayi mata lallashin duniya akan ta cigaba da harkarta ko da a boye ne amman ta gaza, dan sai dai tayi mata wani kallon ta ce, "Asma baki san Mustafa ba ne, shine namijin da idan ya baki zumarsa baki iya jin dadin ta kowa, shine namijin da ya iya soyayya mai kwantar da zuciya, shine mai kula da duk wasu bukatu na macen da yake matukar so, shine ya sadaukar da kansa ga Zainabu, shin kina tunanin yana gabana da ransa zan iya kula wani da namiji? Ki barni kawai baki san Mustafa ba kina kallonsa ne kawai." Don haka Asma sai dai ta zuba mata ido kawai don ita da kanta ta san Mustafa daban ne a cikin maza kamar yanda kawarta ke fadi. Samarin ta da dama sun damu da wannan sabon halin da ta bullo musu da shi musamman Alhaji Jamilu da kuma D.P.M, don haka ma ta kashe duk wayoyinta, idan kaga ta kunnasu lallai Mustafa zata kirawo. Hankalin Sala idan yayi dubu ya tashi, domin dai tana ganin kamar ana son kashe mata jin dadin diyar tane da walwalarta, dan da farko ma fada ta kama yi mata tana fadin, "Haba maitsada yaushe zaki zauna namiji kwaya daya yayi ta gare-gare da rayuwarki a banza, ki dubi irin wahalar da kika sha a baya, amman yanzu duk kin daga hankalinki don uwarsa tace ba zai aure ki ba, ga maza nan kala-kala suna binki wadanda suka fishi komai kamar su cinye ki amman kin makale masa, dan haka ki rabu dashi kawai tunda dai yanzu ba da bace." Ita dai shiru kawai tayi tana ayyanawa a ranta, "Sala baki san so bane shiya sanya kike fadin haka, da kin san irin abunda nake ji akan son Mustafa da kin tausaya mini, zan iya jure rashin komai amman banda Mustafa, wannan wata jarabta ce da Allah ya doro mini." Da dai Sala taga fada da mita ba zasu yi magani ba sai ta koma lallashi, amman duk a banza wai talaka ya girmi Sarki, su kuwa abokan watsewar ta sai kyauta ta bajinta suke mata wai ko zasu shawo kanta, amman idan an aiko ma sai dai Sala ta karbe tana godiya tace bata jin dadi ne shiya sanya bata fito ba. Idan mutum ya fiye matsa mata da aike kuwa fita take yi tayi masa rashin mutunci, don dai muguwar 'yar buyagi ce.Haka zaka tadda ta tayi dif da tabar shaidan ko shandy din ta a gidan Asma dan can Mustafa ke tadda ta suyi watsewarsu acan da lallashin juna, don ma dai shi yanzu Mustafa bai son shaye-shayen da take yi don shi kam baya ga taba yanzu bai shan komai sai dai idan wani yana shan tabar shaidan a kusa dashi ya amsa yayi ja uku ko hudu, amman giya kam tuntini ya daina sha, don haka take rage shan su don su kan yi fada idan ya tadda ta tana sha. Al'amura sun kuma tsauri a gare su, don Momi ta kama shi da hoton Zainabu wacce tayi tunanin ya rabu da ita tuntuni ya fara neman wata ma, ta yi matukar girgiza musamman da taji kalaman da yake furtawa akan Zainabu din. Ta yi neman wayar sa ne ta sanar dashi sallahun da Babansa ya bari ya kaiwa kanin sa Kawu Sale, amman duk wayoyin nasa a kulle suke, gashi kuma ta ga motar sa a kofar gida abun da ya tabbatar mata yana ciki kuma dai lokacin babu yara a gidan don haka ta nufi sashin nasa da kanta don ta sanar dashi sakon Baban nasa. Ta tadda shi zaune bisa kujera ya dora (laptop) akan cinyar sa ya kura mata idanu wadanda suke rine saboda tsabar tashin hankali, a fili yake fadin, "Zainabu yaya zanyi da son ki a zuciyata, ni kadai na san irin azabar da nake sha saboda raba mu da ake shirin yi, na gaza ganin ko wace mace da kima da daraja don kece kadai kika san Mustafa, ba zan iya auran wata mace ba muddin kina raye a duniyar nan ba, san yani a kafadarki ko naji sanyi a raina, na zama mutum-mutumi sai yanda kika yi dani Zainabu." Hankalin Hajiya Kubra yayi mugun tashi da jin kalaman da Mustafa ke furtawa, ta kuma jin tsanar Zainabu ta lunku a ranta don sai taga kamar yanzu yafi son Zainabu sama da ita ma daga yanda take jin kalamansa, kai ita tana ganin wannan son da yake wa Zainabu ma bana Allah bane asiri kawai tayi masa, banda haka meye hadin shi da ita, don ya fita komai a ganinta, ta nufe shi da sauri dan ta bayansa take baiga shigowarta ba, sai ta tsaya turus tana kallon abinda ya dauke masa hankali har bai ji shigowar ta ba. Wani katon hoton Zainabu ne ta dauka da wani yadin material (light purple), mai yarfin fulawowi jajaye da ruwan zaiba, tana sanye da wani dankunne na fashion mai kyau, ta tallafe habarta da tafin hannunta tana dariya, (dimple) dinta ya fito sosai, fuskar ta yi fayau, gashin idonta ya tashi gazar-gazar, girarta ta kwanta luf-luf, labbanta sun sha jambaki kalar kayanta sai walkiya suke yi tamkar ba a hoto ba, hoton ya dauko matuka don an futo da ainihin kyan Zainabu. Lallai ba Zainabun da ta sani da ba ci, don ta goge matuka tana kuma da kyan da lallai zata iya yaudarar Mustafa ya sota, sai dai ita kyanta baya gabanta tunda bata da kyan hali. Zuciya ta dauke ta don ganin wai har lokacin bai san ta shigo ba hankalinsa yana ga Zainabu ne kawai, ta fisge laptop din ta kwadata da kasa, ai kuwa sai gashi ta bare gida biyu, da alama da kyar zata kuma moruwa gashi mai kyau ce dan daga kasar waje ya taho da ita.ya daga kansa a gigice dan yaga wanda yayi masa wannan yankan kaunar sai yaga Momin sa a tsaye tana ta huci ta cika fam, nan da nan gumi ya fara karyo masa don yasan Momi babu wargi ba iri Babansa bane mai sanyi ba. "Mustafa! (ta kirawo sunan sa yau babu sayawa saboda bacin rai), wato dama baka rabu da wannan karuwar ba ko? to tsaya kaji na gaya maka ko mutuwa zaka yi akan sonta ba zaka auro mana jaraba ka kawo mana gida ba, da mun sakankance ka rabu da ita, ashe 'yar jarabar tana tare da kai. Shin wai ni me ka gani a jikinta da har tafi sauran mata da ka kasa kalla da daraja ne eye? Kai yanzu ba zaka ji kunya ba ace matarka tsohuwar 'yar tallan goro bace mara tarbiyya ba? Bata gaji tarbiyya daga uwa ko uba ba sam?, to tsaya kaji na gaya maka ta mahaukaci, ko bayan raina ka auri Zainabu ban yafe maka ba, sannan daga yau idan ka kuma zuwa gidansu ko inda zaku hadu ban yafe maka ba." Ya runtse idonsa gami da dafe kai hankalinsa yayi mugun tashi, babu abinda yake fadi sai, "Innalillahi....." Ta kuma kufula tana fadin, "Kai ko mutuwa zaka yi babu kai babu Zainabu na gaya maka in dai nice na haifeka dan halak." Tana gama fadin haka ta juya ta fice sam ta manta da abinda ya kawo tama sashin nasa. Ya zauna jabar a kujera har lokacin bai cikin hayyacinsa, ya kuma fadin, "Ya Salam! Ya Salam!" Har lokacin zufa tana karyo masa duk da sanyin A.C da fankar dake dakin. Maganar Momin ta dunga masa amsa kuwwa a kunnensa sai yake ji kamar har lokacin tana tsaye a kansa tana ta maimaitawa ne, don haka ya sanya hannuwansa ya toshe kunnuwansa wai ko ya daina ji, amman da yake abin daga zuciyarsa yake fita sai ya cigaba da ji kamar ma karuwa ya yi. Lallai ko yaki ko ya so yasan rabuwar sa da Zainabu ta zo kenan, idan har ya kasance da mai albarka, don dai ya san duniya bai hada Mahaifiyar shi da kowa ba, ko da kuwa zai mutu din kamar yanda Momin nasa ta fada din ya rabu da Zainabu har abada. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 WAI WACECE ZAINABU-ABU MAI TAGWAYEN SUNA NE? Asalin Salamatu mahaifiyar Zainabu 'yar cikin birnin Kano ce, ta tashi babu arabi balle boko, bata da aiki sai dai ta dauki tallan soye (dan tayi da ake cirowa daga dabbar da aka yanka na kasa mata a kokuna sannan a jera a cikin faranti). Don haka kullum da sassafe zata yi sammako ta tafi Mayanka ta siyo dan tayin wanda zama suke kusa da dabbar da ake yankawa da zarar an hango da dantayi sai a kwasa da gudu, wacce ta fara kamawa nata ne sai ta saka a kwanonta ayi ciniki sannan su kuma matsawa gaba da haka har ka tara na iyakacin kudinka, sannan sai ta tafi gida a yayyanka shi a soya, a zuzzuba a kokuna sannan a tafi tallanshi kasuwanni. Idan ta dauki tallan tun safe sai yamma likis take komawa gida, don haka bata da lokacin karatu, sai dai ran da taso sai ta tafi makarantar dare ita ma bata fahimtar komai dan banda gyan-gydi babu abinda take yi, don an sha yawo an gaji, idan kuma ranar alhamis da Juma'a ce a tafi gidan amare a yita wasan 'yar carafke ko lido da sauransu. Mahaifinta yana so tayi karatu sai dai bai isa ba dan matar sa tafi karfinsa, don haka yana ji yana gani 'yarsa ke wannan rayuwar babu kwaba balle harara, sannan idan dare yayi wani lokacin zaka ga samari sun cika kofar gidan anata zance da shewa da kawayenta kuma bana aure bane illah ayi shashanci da zancen batsa a watse, amman babu na aure a cikinsu. A gurin da take sai da soye wani mutumin Sudan sunansa Abbakar, shayi yake saidawa irin na babbar butar nan wanda ake dauka a hannu da biredi da kofuna a faranti, Abbakar mutum ne mai kirki da hakuri dan kullum Salamatu sai ta tsokane shi dan hausar sa bata fita sosai, gashi kuma da shegen surutu da son tsegumi. Duk danginsa suna can Sudan, yaki ne ya sanya suka watsu suka yo Nigeria da 'yan uwansa, sai dai tun da suka zo kowa ya nemi masauki, shi kam yayi sa'a ya fada hannun wani Malami Malam Nadabo mutumin kirkine ya bashi gida inda yake saukar baki ya zauna cikin almajiransa, yana fita neman abincinsa don shine ma ya bashi jarin da ya fara sana'a tun yana zagaye cikin unguwar har ya koma yana shiga kasuwanni.Da yake ya iya shayin sai ya samu kwastomomi dan irin na larabawan nan yake yi, a haka suka hadu da Salamatu ma, don Allah yayi shi mutum ne mai shegen surutu da son gulma dan haka duk abinda ya gani sai ya nuna mata ko ya tambaye ta da haka har soyayya ta shiga tsakaninsu. Abu kamar wasa sai gashi sun saba matuka, sai dai tun a wancan lokacin tayi mugun raina shi tayi ta masa masifa bai damuwa, domin yana da matukar hakuri sai dai zancan gulama amman sam baida abokin fada, sai dai mutane da dama suna ganin abun nasu kamar ba zai yiuw ba don shi fari ne tasa kamar balarabe gashinsa ma a nannade yake sai dai wahala ta sanya shi ya dan dafe, yayin da Salamatu take baka, amman bata da muni, sai dai bata da tsawo gajera ce sosai mai jiki. Malam Nadabo dai shine kamar matsayin mahaifinsa don haka shine ya tsaya masa har aka yi wannan auren, suka tare a nan gidan Malam din da yake zaune da almajirai, wasu suka koma shagon gidan wasu kuma suka koma daya gidan. Ta addabi kowa a gidan don gidan kusan a hade yake da na Malam kasancewarta masifaffiya ce, su dai matan malam bata yi da su don sun ja girman su haka malam, sai dai duk 'ya'yan gidan 'yan dakinta ne musamman matan, amman duk kusan almajiran malam tayi fada da su don ma malam yakan yi mata fada, don haka babu wanda take shakka kamar malam don babu wargi, a nan gidan ta haifi dan ta na fari Sadiku wanda aka haifa rana daya da dan Malam Zaidu, don haka rana daya aka yi suna Malam ne ma ya rada musu sunansu duka. Sun tashe tare da Zaidu da yake Sala bata wani damu dashi ba don ita ta fi son ta haifi mace wai itace abokiyar neman kudi, don haka kullum a cikin watangariri yake a cikin gidan musamman da ta yaye shi sai ta bar musu a can, don haka kusan a gidan nasu ya taso.Tare Malam ya sanya su a makaranta Ma, sannan ta kuma samun wani cikin tayi ta tanadin kayan mata har su dankunne da awarwaro amman sai gashi ta kuma haifar namijin, shima din haka ya taso a gidan malam din, sai dai daga kansa bata kuma samun haihuwa ba har ya shekara biyar, sai wata annoba ta zo ta kyanda shima yana ciki, ai kuwa dai wannan kyanda itace ta yi ajalin Sabitu. Rashin samun cikin nata ya sanyata fara tunanin wai matan Malam ne sukayi mata asiri don ta fara haihuwar da namiji, su a kan Zaidu suka fara haihuwar namiji duk mata suke haifa, ita fadi take banzaye ni da ana musanye da munyi don nafi son matan, sai dai bai ya wata goma ba da rasuwa Sala ta kuma samun wani cikin. Ai kuwa dai wannan karon tayi sa'a a wannan karon ta samu abinda take so din, don haka murna ba'a magana, sai da dauki son duniya ta dora akan Zainabu sunan Mahaifiyar malam din ya sanya mata kenan, da farko tace bata yarda ba sunan Sima take son a sanyawa diyarta, shi kuwa malan sunan matarsa ta fari ne da ta rasu yana son sunan, sai da Abbakar yayi ta lallaba ta sannan ta amince, akan Zainabu sai tayi fada da uban kowa a kuma sannan ne Abbakar ya kammala ginin gidansa da taimakon malam, don haka suka tattara ya nasu-ya nasa suka koma, amman banda Sadiku wanda sai dai yaje gidan nasu ya koma gidan malam don kamar ba Sala dince ta haife shi ba musamman idan Zainabu tana kin ji yana mata fada, dan haka shima bai fiye zuwa gidan ba sai da ya shiga sakandire ne ma yake zuwa sosai.Sala kam sana'a ta kafa sosai a gidan ta, don daman tun tana gidan malam jarabar neman kudi ne da ita, don haka ba ta zama kullum cikin neman kudi take. Tun daga wannan lokacin shike nan haihuwa ta bude a gidan nasu, sai dai yaran suna tashi babu tarbiyya, da farko malam ya fara kiran Baba Abbakar akan halin da yaransa suka tashi da shi, don haka yayi masa nasiha mai shiga jiki, sai dai idan aka ce namiji bashi da katabus a gidansa babu tarbiyya, don haka san da Baba Abbakar yaje mata da abinda Malam din ya ce, tsalle tayi ta dire tana fadin, "Wallahi baka isa ba, wacce tsiyar kake tsinana mana da har zaka yi mini wannan tsarin (don a lokacin babu ciniki a sana'ar ta shi sai dai yayi ta yawo bai samun ciniki sosai, daga karseh sai ya koma kame-kame)." Malam Nadabo yana ji yana gani gidan Baba Abbakar ya koma yanda yake don dai yayi har ya gaji, sai dai shifa duk wani abu na tsawatarwa yana musu dan haka shi kadai suke shakka a rayuwarsu, don duk wanda ya doki Zainabu sai inda karfin Sala ya kare, amman idan Malam ne sai ta ce, "Sai kiyi hakuri na gaya miki ki daina zuwa gidansa mana." Shi kam Sadiku ya sami karatu mai kyau don ya sami makarantar firamare mai kyau da sakandire, daga nan ya wuce kwalegin share fagen shiga jami'a, shi kuma Zaidu da yake bangaren Arabic ya dauka yana Jami'atu Ummul Qura dake birnin Makkah yana karantar harshen larabci, wannan shine mafarin komawar Sadiku gidansu don dai babu abokinsa. Da kyar da sidin goshi Sala ta bar 'ya'yanta suke makarantar boko da ta allo don Malam yana fada ne da kuma Sadiku, sai dai duk da haka Zainabu ba kullum take zuwa ba sai jefi-jefi. Sai dai da yake ba karatun ne a gabanta ba sam bata yi, Zainabu ta taso da hali irin na Babarta don haka bata da wargi duk wanda ya taba ta sai ta rama, don dai Sala ta bata ta tun tana yarinyarta, ga fadan ta baya mutuwa kamar fadan kurma, don sai tayi wata tana fada sai dai idan iyayen yaran sun gaji su zo gidan a baiwa Sala hakuri sannan za ta hakura, idan mutum yafi karfinta ba ta raga masa don da cizo da yakushi zata kwaci kanta, ko kuma idan ka doke ta tayi ta jifanku ko duk inda kuka hadu sai fadan ya tashi. Wannan halin nata ya sanya duk unguwar kowa yake shakkarta, abinda ke farantawa Sala rai kenan don takan ce, Abulata da na kai kararki gwara a kawo mini wallahi, don haka duk wanda ya taba ki koda gemunsa yana jan kasa kada ki kyale shi ki rama, daga nan har ofishin kwamishinan 'yan sanda zan iya zuwa a kanki Abulata. Don haka har siyan fada take yi, duk wanda bashi da karfi Zainabu kan sayi fadan ta casa wanda ake fadan da shi don akwai ta da karfi, idan kayi gulmarta za ta sanya a kama ka a tura ka lungun ka-ci-uwaka a tura maka kashi a baki ko bara-gurbin kwai, don haka ta addabi kowa a unguwar tasu. Ko fakin din mota aka yi bai gamshe ta ba sai tayiwa mutum faci a motar tasa, don haka duk kofar gidan masu hali na unguwar da an gan ta masu gadi zasu bita da gudu tana dariya. Idan aka tura ta makarantar firamare kuwa masu kosai da 'yar tsala na sadaka take bi da waina wadanda ke yawo da almajirai mutane na siya suce su raba wa almajirai sai an fita tara take tafiya makarantar. Yawo kuwa ko kare ya gan ta ya kyale, don kullum za ta hada zugar yara suna shiga karkashin manyan motoci da ke fakin a nan kan tudu, dan haka duk wanda baiga dan sa ba yana tare da Zainabu, yawo bola-bola sun iya shi, gashi babu dama kayi magana sai Sala ta hau bala'i tana fadin, "Kun ga kada ku sanya mini diya a gaba, waye Abula ta daurawa igiya a wuya kowa na ga da kafarsa ya bi ta, don haka duk matar da ta kara cewa Abula ta ja mata 'ya'ya yawo wallahi sai na dirji bakinta, duk wacce ba ta son 'ya'yanta su je yawo ta daure a kofar gida, kurwar Abula kur! Na gaya muku." Wannan shine kadan daga cikin labarin Zainabu Abu mai tagwayen suna. **********Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ubangiji babu ruwansa yakan bar bawa ya sakata ya wala ya yi sabo son ransa ba tare da ya matsa maka ba a duniya, amman abu kalilan zai jarabce ka dashi duk sai ka gigice ka ga ashe kai din ba komai bane, ka koma abin tausayi. To, Lallai kam hakan ce ta faru ga Mustafa, don bai taba zaton zai shiga ko da kwatankwacin wannan matsalar a rayuwarsa ba, Allah ya jarabce shi da son Zainabu wacce ita kuma mahaifiyarsa ta tsana kamar mutuwarta, Zainabun da ya raina a baya, sai ga shi son ta yana neman raba shi da duk jin dadin rayuwarsa, don wacce ta kawo shi duniya ta yi musu katangar karfe a tsakaninsu. A da can da suka hana shi auran ta bai damu kamar yanzu ba, don yaka je gurinta ya kwanta a kafadarta ta lallashe shi, amman yanzu babu dama don haka abubuwa suka masa yawa, yanza haka yana ofis ya hada tagumi da hannuwa biyu- biyu kamar wani karamin yaro, wani inji aka ce ya je ya duba amman ya gaza tashi, gashi yafi kowa iya gyara a sashen nasu, yanda kasan maye haka yake idan ya sanya gyara a gabansa sai ya ga ya gyaru, don haka suke ji da shi.Yana nan zaune ya ji kiran wayarta ya shigo, ya zabura da sauri ya dauka ya kara a kunnensa. Da kashe murya da shagwaba ta ce, "Zumana shiru kwana biyu babu kai babu wayarka, ko Zainabu ta yi laifi ne bata sani ba?" Ya lumshe idonsa gami da kwanciya jikin kujera, ransa ya yi fari tas saboda jin muryar Zainabu kawai da yayi, sai dai ya gaza bude bakinsa ma balle yace wani abu. Hankalin ta ya kuma tashi da jin shirun da ya yi mata, ta kuma duban wayar ta ga lallai a kunne take, da tashin hankali ta ce, "Mustafa ka ce wani abu mana, ko dai ka manta da Zainabunka ne?" Hankalinsa ya kara tashi don jin muryarta kamar za ta yi kuka, ya daure ya bude bakinsa da kyar ya ce, "Zainabu baki yi mini komai ba, illah dai Mahaifiya ta ta kafa mini mummunan sharadi a kan idan na kuma zuwa inda kike ko duk inda na san zamu hadu, to lallai ba ta yafe mini ba....." "Me ka ce Mustafa? Yanzu kana nufin shi kenan mun rabu har abada? Yanzu yaya zan yi da sonka a raina Mustafa na? Anya zan iya rayuwa babu kai, Zumana?" Yayi kokarin jawo dauriya ya sanyawa ransa ya kwantar da murya da lallashi ya ce, "Kin ga Zainabu kwantar da hankalinki, ni din naki ne har abada ba zan iya rabuwa da son ki ba, sai dai dole zanyi biyayya ga maganar Mahaifiyata don ina son na rabauta duniya da lahira, na yi miki alkawari ni naki ne har abada, sai mu cigaba da addu'a komai ya zo da sauki, don ina ji a jikina ke matata ce da zan rayu da ita cikin ni'ima da soyayya." Hankalinta ya dan kwanta ta yi ajiyar zuciya tana fadin, "Zumana yanzu yaya za muyi kenan? Don na san zan sha walahar rashin ganinka matuka." Ya lumshe idanuwansa wadanda yake jin suna masa nauyi ya ce, "Ki bari zan ga Babana idan ya dawo zan sanya shi ya lallasar mana Momi din, ina ganin shi zai tausaya mini idan ya ga halin da nake ciki, don yafi Momi saukin kai." Ta ce, "Shike nan zumana, amman zan dinga jinka a waya ko?" Ya ce, "Dole ne ai Zainabu na kiraki a waya, idan ba haka ba zuciyata ai bugawa zata yi." Ta yi murmushi gami da fadin, "Ina sonka matuka zumana." Ya yi dariya ya ce, "Nima haka Zainabu, sai dai ina son don Allah ki yi mini alkawarin kin bar hulda da maza kamar kina ganina, don na danka miki amanar kanki, ina jin kamar zuciya ta zata babbake idan na ganki da wani, shin zaki iya rike mini kanki da alkawari har komai ya lafa?." Ta yi murmushi gami da fadin, "Mustafa ko da ba kace ka ba ni amanar kaina ba ba zan iya hulda da kowanne namiji ba, don kai din kayi mini yanda ba zan iya kallon kowa da gashi ba, ka kwantar da hankalinka a yanzu Zainabu taka ce kai kadai." Da kyar suka iya rabuwa a wayar don suna ta sanar da kawunansu irin son da suke yiwa junansu ne kawai. Sai a sannan ya sami karfin gwiwar da zai iya tunkarar aikin da ke gabansa, don haka ya shiga dan wani daki ya sauya kayansa daga na gida zuwa na aiki ya nufi inda injin da zai gyara yake. Ita kuwa Sala ce a kanta a tsaye tana rike da kugu jira kawai take ta kammala amsa wayar, ai kuwa tana ganin ta gama wayar din ta dirar mata da jaraba. "Yanzu Abula shi kenan zaki zauna namiji daya tal yana miki yawo da hankali? Ga wadanda ke son ki kuma sai wahalar da su kike yi? Yanzu jiya Alhaji Hayatu Tumbin kudi sai da ya kashe kunyarsa ya zo ya sameni ya ce don Allah ki fito ko gaisawa ne ku yi, shi da gaske yake auranki zai yi ma, ya cake mini dubu hamsin a hannuna ke kuma ya ce idan kin fita zai baki duk abinda kike so, amman yarinyar nan kika bada mini kasa a idona, har mutumin ya gaji da jiranki ya yi zuciya ya tafi, kin kwallafa ranki a kan shegen mayaudarin yaron nan, kin ki ki saki zuciyarki ki ci arziki ki bar arziki a mazauninsa? Wallahi kin bani mamaki Abula ban taba zaton zaki koma sokuwa a hannun namiji ba, su da kike juya su kamar waina?." Zainabu ta dinga duban Sala da mamaki da takaici da kyar ta iya buda bakinta ta ce, "Sala kin san So kuwa?" "Ban san shi ba sai ke diyar zamani, ba kuma na fatan na san shi tunda shi din masifa ne da jaraba, ki dubi yanda ya maida mini ke, wallahi da zan gan shi shi So din dana rade masa kai don Ubansa, tunda ya hana ki ki zauna lafiya." Ta dafe kirji gami da jingina da kujera tana fadin, "Sala ki kyale ni kawai tunda dai kin ce baki san So ba, yanzu haka kirjina ciwo yake mini, lallai idan na rasa Mustafa na san mutuwa zan yi don Allah ya jarabce ni da tsananin son sa, zan iya yin komai don na same shi Sala, yanzu kam na gane so yana gaba da kudi da komai, ki rabu dani kawai don na yiwa Mustafa alkawarin ba zan kuma kula kowa ba zan yi ta jiransa har ranar da Allah ya sanya iyayansa suka amince ya aure ni din." Sala tayi Salati tana tafa hannu tana fadin, "Shike nan an sammace mini ke Zainabu, don in dai ba asiri ba babu abinda zai sanya ki gaza hulda da kowa sai shi kadai, kuma yanzu ba ya nan baya ganinki ba kya ganinsa ma, amman kin ce ba zaki iya kula kowa ba, to wallahi ya yi a banza, don ni ma ai ba'a zaune nake ba, duk neman sa'ar da nake miki a ce ya tashi a banza, bari na tafi gurin boka na kan tudu zan sanya ya raba min ku, idan ya so sai na ga karshen shegen So din, tunda dai shi ciwon masifa ne." Zainabu ta riko hannun Sala da ke shirin fita daga dakin nata tana fadin, "Sala kada ki rabani da Mustafa idan dai ba so kike na mutu ba, shin wai kin san abinda ya sanya iyayan Mustafa ma suka hana ni aurensa? To ba wani abu bane illa yawon da nake yi na bin maza tamkar karya, kowa ya zo ya dauke ni a mota ya je yayi abinda ya ga dama da ni kan kudi, sun ce ni karuwar gida ce, yanzu me ye amfanin irin rayuwar iskancin da na yi? Ni kam zuciyata ta gyaru don haka na bar abinda kike so na yi." Sala ta kuma shiga rudu ta ce, "Ahaf! Kinji ba? Ai na sani asiri yayi miki, banda asiri ke da bakinki ki dinga kiran kanki 'yar iska, yanzu kin yarda ke din 'yar iska ce? Kalmar da da idan aka gaya miki sai inda karfinki ya kare amman yanzu kike gaya wa kanki, to ba karuwa ba ko ke mecece kinfi karfin danta wallahi, idan tace kuma ke karuwa ce shi dan nata ai karuwi ne tunda dai shine ya watsa miki rayuwa, sai nayi maganinsu shi da uwar tasa in dai sunana Sala." Ta warce hannunta daga rikon da Zainabun tayi mata ta nufi waje tana cigaba da bala'inta.... To, masu karatu, mu hadu a littafi na biyu don jin yadda Sala zata aiwatar da wannan mataki. Take cewa kar ku damu na dayan tare suka fito da na biyun,Mai kaunarku da yi muku fatan alkhairi a kullum: FAUZANKU CE! Mrs Q for Q, Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Idan Zuciya Tagyaru2-01 Posted by ANaM Dorayi on 12:38 PM, 08-Feb-16 Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU _________________ Na ________Fauziyya D Sulaiman_____ Zainabu ta zame ta kwanta ta lumshe idanuwa tana hango hoton Mustafa a zuciyarta, yanzu idan Sala ta raba su yaya za ta yi da sonsa? Hawaye ya shiga malalowa ta gefen fuskarta, ji take kamar ta koma baya da rayuwarta ta goge duk abinda ta aikata, amman ina lokaci ya gama kure mata da ba za ta iya gyarawa ba. A da can baya takan ga wautar masu cewa idan basu samu wane ba ba zasu iya rayuwa ba, sai ga shi yanzu ya zo kanta ita ma. Asma ta fado mata a ranta, wai ina ta shiga ne a duniyar ne don ta nemi wayarta ta rasa? Yau sati biyu kenan da tayi tafiya da wani saurayinta, sai dai ta gaza samun wayarta, gashi ita kadai ce ke bata shawara idan ta shiga tashin hankali. Ta kuma dafe kirjinta da take jin kamar zai tsage don ciwo, wai yau ita Zainabu Abu dake gara maza kamar gare-gare, ita ce ita ma yau zuciyarta ke tamaula da son wani, ta lumshe idonta tana fatan ta yi bacci ko ta huta da azaba.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 ******************* Kwanaki suna tafiya amman dokarsa tana nan ta hana shi kula Zainabu, abin yana damunsa matuka, don haka tafiya kawai yake yi amman shi kansa ya san bashi da koshin lafiya, gurin aiki ma sai hakuri suke yi da shi don yayi rahotan bashi da lafiya, ya gaza cin abinci ya koshi sai dai ya sha fresh milk kawai da safe da da dare. Abin ma biyu ya hade masa, na farko raba shi da Zainabu da aka yi sai kuma kin kula shi da Mominsa ke yi, ko da gaishe ta ya yi bata amsawa. Shi kam ya yi alkawarin ko me zata yi masa ba zai daina gaishe ta ba. Yau ma ya shirya cikin shadda koriya ta amshe shi matuka, sai dai daga gani yana cikin tsananin damuwa matuka, ya nufi dakin Momin tasa da zummar ya gaishe ta duk da ba amsawa take yi ba. Tana ta hada kayanta don makaranta zata tafi, kanwarsa Sumayya tana gefe tana tambayarta a kan wani aiki (assignment) da take yi tana gaya mata tana rubutawa, ya shiga dakin da sallama. Ya sami kujera ya zauna jabar yana fadin, "Washi." Kamar wanda ya yi wani aikin. Sumayya ta dube shi da kulawa tana fadin, "Ya Mustafa ina kwana?" Ya ce, "Lafiya lau. Ina 'yan uwan naki suke musamman aminiyar Zainab." Ta yi murmushi ta ce, "Sauran sun tafi lakca dan duk ta safe suke da ita, mu kuma muna da jarabawar gwaji ne ga shi motarmu ta samu matsala, don haka Momi za ta rage mana hanya, Zainab nake jira tana shiri." Ya kalli Momin da ta zauna tana shan shayi ya ce, "Momi ina kwana?" Ko kallon inda yake ba tayi ba ma balle ya sanya ran zata amsa masa, Sumayya da ke kallon Momi din ta yi narai-narai da idanuwanta kamar za ta yi kuka tana fadin, "Momi don Allah kiyi hakuri haka, ki dubi yadda Ya Mustafa ya koma, na san share shi din da kike yi ne kuma ya sanya shi komawa haka, don Allah ki sassauta masa kin ji Momi?" Ta gallawa Sumayyan harara wacce take ji da ita duk gidan, don ita ce 'yar gaba goshi sannan ta ce, "Ina ruwa na da wani hali da ya shiga? Ai shine ya dorawa kansa, wannan halin kuma da ya shiga ne ya tabbatar mini da lallai ban isa da shi ba, don da na isa da shi da ya saki ransa ya hakura da auren shegiyar karuwar yarinyar nan ya cire ta ma daga ransa gaba daya." Kirjinsa ya shiga bugawa da sauri kansa ya hau sarawa kamar zai tsage gida biyu, lallai Mominsa uwa ce ta fi gaban komai, don ban da ita babu wanda zai zagi Zainabu a gabansa da sunan karuwa ya kyale shi, amman Mominsa tafi Zainabu daraja da girma a gurinsa da zuciyarsa gaba daya. Ya mike da zummar ya tafi jikinsa sai rawa yake yi, ta kuma galla masa harara sannan ta ce, "Baba in dai nice na haife ka na baka kwana biyu ka fito da matar aure, idan ka bari har kwana biyu ta wuce ba ka fito da mata ba to lallai zan aura maka wacce na ga dama, kana ji na ko?" Ya gyada kai da sauri yana fadin, "To Momi na amince da duk abinda kika yi a kaina, fatana dai ki yi hakuri ki dinga kula ni ko zan ji sassauci a zuciya ta." Tausayi da soyayyar danta ta shige ta, musamman yanda ta ga ya amsa babu wata jayayya ba kamar yanda ta zata da farko ba, sannan bai damu da hukuncin da ta yanke masa ba sai ma rashin kula shi da bata yi bane ya fi damunsa, ta ce, "Shi kenan ya wuce, sai dai ka yi kokari ka cika umurni na cikin kwana biyun da na ce, don idan kai idonka bai gano ma mace ta gari ba, to ni nawa garau yake ina gani tar, zan zaba maka mace mai daraja ta kwarai." Shi kam bai kuma cewa komai ba ya nufi kofa zai fita, sai dai gaba daya idanuwansa sun disashe ba ya fahimtar komai, bugun kirjinsa ya kuma tsananta fiye da yadda yake a ka'ida, amman hakan bai hana shi dauriyar cigaba da tafiya ba duk da kwakwalwarsa na neman gaza aiki yanda ya dace,Ya kuma daga kafarsa amman ya kasa sai ma kafafuwan nasa da suka gaza cigaba da daukar nauyin jikinsa, don haka a nan ya yanke jiki ya fadi gaba daya ya daina fahimtar komai don mai alhakin sanar da shi din ita ma ta sami matsala, wato kwakwalwarsa. Sumayya ce ta fara ankara ta mike da azama gami da kwala ihu ta yi kansa, Momi ta ankara da abinda ke shirin faruwa itama ta yi kansa da saurinta ba ta san sanda ta yar da kofin shayin da ke hannunta ba. Suka kama jijjiga shi suna fadin sunansa amman ina, ko motsawa ba ya iya yi. Momi ce ta bazama da gudu can harabar gidan tana kwalawa direba kira, Allah ya sanya ya dawo daga kai 'yan makaranta don haka shi da maigadi suka iso da sauri suna tambayar abinda ya faru ganin yanda take a kidime, kasa magana ta yi illa dakinta da take nuna musu, suka shiga da saurinsu tana biye da su a baya. Suna shiga ta fara magana da azama, "Maza ku dauke shi mu wuce asibiti kada ya mutu." Sumayya ma sai kukan take yi, haka Zainab da hargowar Momi din ta fito da ita ita ma kukan take yi, haka nan suka kwasa suka yi waje da shi, shi kam Mustafa ya yi nisa, sam bai san wanda yake kansa ba. Suna isa asibitin dakin 'yan hatsari aka yi da shi (A&E), na asibitin Malam Aminu Kano, nan da nan likitoci suka rufa a kansa domin matsalar babba ce. Su Momi suna waje suna ta sintiri, gaba daya hankalinsu a tashe yake, sai da kyar ta samu ta rarrashi su Sumayya, da suka ga karfe daya ta yi suka wuce masallaci suka yi Sallah suka zauna suna ta addu'a, masu karatu kuma suna ta yi. Ranar kam sun manta da wani abu wai shi abinci, balle makaranta. Bayan sun kammala sallar suka dawo, amman har lokacin likitoci suna ciki, abinda ya fara firgita Hajiya Kubra har take ganin kamar mutuwa ma ya yi aka ki sanar da su. Sai karfe daya da minti hamsin da shidda sannan likitocin suka fara fitowa, Hajiya Kubra ta bi babban likitan da sauri tana tambayarsa ya ya mai jikin?. Ya dube ta ya ce, "Ke ce mahaifiyarsa ne?" Da sauri ta ce masa, "Eh! Ni ce." "Ina mahaifin sa yake yanzu?" Ya kuma tambayar ta. Ta kuma cewa, "Ba ya gari wallahi, yana can kasar Spain ne." Ya yi dan jim sannan ya kuma cewa, "O.K, shike nan, idan dai da hali ayi masa waya a ce muna son ganinsa da gaggawa, idan kuma yana da dan uwa sai a turo shi sai a yi masa bayani." Ta kuma shiga damuwa da jin abinda likitan ya fadi, ta dinga fadin, "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un." Sannan ta kama neman layin wayar Alhaji Abdullahi na can garin. Bugu biyu ya dauka ya ce, "Ya ya dai Kubra kowa lafiya ko?" Ta goge hawayen da ke zubo mata ta ce, "Eh, to! Da sauki. Amman idan da hali ka zo cikin satin nan, ko gobe ma don wata matsala ce ta taso mai karfi." Hankalinsa shima ya tashi ya ce, "Ko dai wani ne ya rasu kike boye mini, eye?" Ta ce, "A'a wallahi babu wanda ya rasu, ka dai daure ka zo din." Da haka suka yi sallama.Haka nan suka dinga sintiri a asibitin har dare, sai daga baya ne ma da suka ji babu wanda za'a bari ya kwana a gurinsa don yana bukatar kulawa daga ma'aikatan jinya, ya sanya suka hakura suka wuce gida. Washegari da safe suka kuma rankayowa suka yo asibitin, amman basu sami damar ganinsa ba har lokacin ba'a shiga inda ya ke, sam! Abinda ya ba su mamaki bai wuce ganin Alhaji Abdullahi ya iso wajen karfe uku na yamman ba, amman sun san babu mamaki don duniya ta kuma cigaba matuka ba kamar da ba. Kai tsaye Ofishin likita ya wuce bayan sun gama gaggaisawa da su Hajiya Kubra da yara, don ta yi masa bayanin abinda likitan ya ce mata. Bayan sun kammala gaisawa da likitan ya ce, "Kai ne Mahaifin Mustafa kenan?" Alhaji Abdullahi ya ce, "Eh! Ni ne." Likitan ya gyara zama yana tambayarsa, "Daman yana da wani ciwo ne da ya shafi ciwon zuciya tun yana yaro?" Alhaji Abdullahi ya yi dan jim sannan ya ce, "Ba na jin ya taba yin wani ciwo da ya danganci wannan duk tsahon rayuwarsa, kuma ina fatan yanzu ma ba shi bane ba." Likitan ya yi shiru kamar ba zai ce komai ba sannan ya dauko wasu takarsu na hoton kirji da aka yi yana dubawa, sannan ya kalli Alhaji Abdullahi ya ce, "Alhaji (I am sorry to say) ka yi hakuri da abinda zan gaya maka, yaronka ya kamu da ciwon zuciya, don yanzu haka zuciyarsa ce ta kumbura saboda yawan bacin rai da damuwa da yake ciki, don haka ne ma muka hana kowa ganinsa don yana bukatar hutu da rashin hayaniya, amman ya farfado tun jya da yamma." Alhaji Abdullahi ya fara fadin, "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, La haula wala quwwata illah billah. Yanzu likita ya ya za'a yi kenan?" Dokta Bukar ya ce, "Kar ka damu, tun da yanzu mun samu ya farfado, sannan a gwajin da muka yi masa yau da sauki a kan jiya, sai dai kawai wani suna da yake yawan ambata idan yana bacci....." "Likita za mu iya ganinsa ni da Mahaifiyarsa?, don tana cikin damuwa matuka kada a yi biyu." Ya katse likitan. Likitan ya ce, "Babu damuwa, tashi mu je ka gan shi." Yana kwance a gado yana bacci, amman a fuskarsa ta fada matuka, ramar da ya yi ta bayyana, Hajiya Kubra ma ta shigo, don an ce ta shigo, ta isa inda yake tana shafa kansa a hankali hawaye yana zubowa daga idonta, shi ma Alhaji kallonsa yake cike da tausayinsa, ya kama hannunsa ya rike. Ya yi wata ajiyar zuciya kamar wanda yake ido biyu sannan a hankali ya fara fadin, "Zainabu! Zainabu!! Zainabu!!!" Kunnuwansu sun jiye musu abinda yake fadi, Hajiya Kubra ta janye hannunta da sauri gami da kallon Alhajin, Ya matsa kusa da ita sai ta fada jikinsa tana kuka tana fadin, "Alhaji kana jin abinda yaron nan yake fada? Ba ya ta lafiyarsa sai ta wannan 'yar iskar yarinyar, ni kam na shiga uku da wannan jaraba." Ya dafa kanta yana shafawa a hankali yana fadin, "Ki yi hakuri Khadija, na san ba yin kansa bane sharrin so ne, wanda ke ma kin san shi, koda yake ke baki san wahalarsa ba sai dadinsa kika sani, ki duba ki ga bacci yake amman yana ambaton wacce ba ta kusa da shi ma, so yana shiga zuciyar mutum ne ba tare da neman shawara ko neman yarda ba. Ki dubi halin da yake ciki, kin san me likita ya ce yana damunsa?"Ta girgiza kanta alamar A'a. Ya ce, "To ki sani danki Mustafa yana fama da ciwon zuciya ne, yanzu haka kumbura ta fara yi shi ya sanya......." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 "Me ka ce? La'ilaha illallahu, na gamu da masifa ni Kubura." Sai ta kuma fashewa da kuka. Ya fara lallashin ta yana fadin, "Ya isa kiyi shiru kada ki tayar da shi daga bacci kin ga ance ba'a son ana damunsa da hayaniya, don haka ma aka hana kowa ma shiga inda yake, fatana ki kwantar da hankalinki ki yi hakuri da duk abinda zaki ji yana fada, kin ji ko?" Ta daga kai alamar, To.Ina Zainabu? Tana can itama cikin tsananin tashin hankali, domin dai tun jiya da safe take kiran wayarsa amman ba'a daga ba, ga shi tana ringing, ta tura sakonni su ma babu amsa, don haka ranta ya baci hankalinta idan ya yi dubu duk ya tashi. Daga karshe sai ta yi zaton ko ya amince da maganar Mahaifiyarsa ne ta rabuwa da ita, don haka ta ga ya dace ita ma ta rabu dashi tun da dai ga wayarsa tana shiga ga sakonni ta aika masa bashi da sauran bukatarta. Ranar nan haka ta kwan cike da bakin ciki da tashin hankali, domin dai ta san ba karamar masifa za ta shiga ba saboda rabuwa da Mustafa ba. Tana dakin ta a kwance lamo tamkar mara lafiya tun da gari ya waye ta kasa tsinana komai, Asma ta shigo dakin da ihunta kamar yanda ta saba. Zainabu ta mike da sauri tamkar ta ga maganin ciwon ta tana fadin, "Kawas ina kika shiga ina nan ciwon so zai kashe ni?." Asma ta zaro ido waje tana fadin, "Haba dai Babbar harka Musty fa yana hannunki sai yanda kika yi da shi meye zai dame ki, ko kuma kin masa buyagin naki ne?" Ta rausayar da kai idanuwanta suka ciko da kwalla ta ce, "Sanin da kika yi, don Mustafa ya kuma yaudara ta karo na biyu, a wancan lokacin ya yaudare ni da kudi ne, amman a wannan karon da abu mafi ciwo da wuyar mantawa ya yaudare ni wato soyayya, kin gan ni kamar wacce aka yiwa mutuwa duk na gaza tsinana komai a rayuwa ta." Asma ta sha kunu tana fadin, "Don Allah ki bar gayan wannan bacin ran ma, yanda kike din nan, Mustafan me? Maza nawa ke neman ko da rabin sa'ar da ya samu a kanki? Lallai ya yi wa kansa, wai ni yaya aka yi ne ma? Ba ni labari don Allah." Ta kwantar da bayanta jikin kushin din da take kai a zaune, sannan ta zayyane mata duk abinda ya faru. Asma ta dafe kai cike da takaici sannan ta kunduma zagi tana fadin, "Ke kin ji ni da shegiyar tsohuwa, ba ta tambayar kanta me ya sanya dan nata ya makale miki? Ai sai ta nemi dalili, wallahi mutanen mu suna bani mamaki matuka, namiji zai tsula tsiyarsa son ransa a cikin unguwa kowa ya sani watakila har ta kai shi ga yiwa wata ciki, amman ba za'a gaza ba shi mata a cikin unguwar ba, amman idan mace ta aikata sai ki ji an yi mata caa kamar wacce ta yi ita kadai, ana ce mata karuwa, shi wai ba za'a ce masa karuwi ba, amman dai dadin abin duk laifinsu daya ne a gurin Allah, babu ruwanSa da cewar wai iskancu ado ne ga namiji, mts!" Ta ja tsaki daga karshen maganar tata, sannan ta dubi kawar tata ta ce. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 "Wai yanzu yaya kike ganin za'a yi ne, eye? Ni fa ba na zargin Mustafa ba zai iya gudun kiba, don ni shaida ce da irin son da yake miki, akwai dai abin da zai hana shi daukar wayarki, ya kamata dai mu kuma bincika mu gani." Zainabu ta galla mata harara tana fadin, "Allah ya sawake, ai wallahi na fi karfin nan, ki bar shi kawai, idan aure bai kawo shi ba ai saki zai kawo shi." Asma ta ce, "Shike nan, bari mu ba shi lokaci mu gani, amman yanzu ki tashi ki shirya mu zagaya club don Allah, wallahi tun da na dawo garin nan nake samun wayar wahalallunki." Babu musu ta mike don ita kanta tana son ta dan sami shakatawa, domin daman ta gaza sakewa ta tsotsi tabar shaidan din tata balle shandy, don tana shakkar yayanta don ya saka mata idanuwa tamkar ubanta, don ma yana shakkar Sala ma. A bakin kofa suka ci karo da Sala ta dawo daga yawonta, ba ta yiwa Sala din magana ba ta shige bandakin, Sala din ta tsaya tana kallonta cike da murna har tana ganin aikin malamin da ta je gurinsa ne har ya fara aiki, can sai ga Asma ta fito daga dakin don su gaisa don ta ji muryarta. Sala ta ce, "Ahaf! Ki ce ke ce kika zo 'yar albarka, tuntuni nake neman ki ban samu ba, domin na rasa yanda zan yi da kawarki, wani dan banzan yaro ya zo ya janye mini hankalinta, ko kofar gida fa Abula ba ta zuwa balle ta yi wata kwalliya, ta zama kamar mai takabar kauye, Abula na sarkin kwalliya ki gan ta cas-cas tamkar diyar gwabna." Asma ta yi dariya tana fadin, "Sala kenan, yanzu ma fadan da na yi mata kenan, ki kwantar da hankalinki komai zai daidaita yanzu ma unguwa za mu." Sala ta ce, "Yauwa, amman na ji dadin zuwanki wallahi, kin gan shi nan na (ta rage murya) kin ga wannan sunansa mantau, a gurin boka na amso shi, ki san yanda za kiyi ki zuba mata a cikin abinda za ta ci, domin yanzu sai ta ga dama take cin abun hannuna, so nake ta manta da shegen yaron nan sam, ga manyan mutane nan suna ta sintiri a kanta me za ta yi da shi?" Asma ta amsa tana fadin, "Shi kenan Sala ki kwantar da hankalinki tamkar na zuba mata na gama."Ta ji dadin abunda Asma din ta fada don haka ta kuma rage murya tana mata gulmar Mustafa wai kada Zainabu ta ji su, ita kam bata ma san suna yi ba har ta fito daga wankanta ta shigo don ta shirya. Ta shiryo kanta cikin wani material bulu, da yarfin ruwan dorawa mai haske da kalar zaiba a jikinsa, dinkin riga da siket ne, rigar 'yarr figil da ita don da kadan ta dara cibiyarta sai siket din dogo ne sosai ya kama ta daga kugunta yayin da ya bada fadi daga kasa, an tattare gaban da wata zuga, ta yi daurin da ya zauna a kanta tsam, sai ta yafa wani dan yalolon gyale kalar kayanta, sannan ta dauki jaka mai kyalli da takalmi ta sanya wanda yake kamar tsani, sai kamshi ke fita daga jikinta wanda ba za ka iya tantance daga ina yake fitowa ba, kwalliyar ta yi mata kyau don ta iya tsara kwalliya balle dama ga kyan ta hada abubuwan da suke jan hankalin maza kanta. Tana fitowa Sala ta dinga dubanta, can sai ta fashe da dariya tana fadin, "Ko ke fa mai tsada, ki dubi yanda kika yi kyau don Allah, amman da kin wani kama zaman daki tamkar wata matar liman. Ita dai ba tace komai ba don ba ta son haka din da take mata yau, har suka nufi hanyar fita daga gidan. Sala ta bisu tana ta rafka musu addu'a, har soro ta raka su sannan ta ce, "To idan dare dai ya yi ki yi kwanciyarki kawai a can, don kada ki dawo dan saka idon nan ya kama yiwa mutane jarabar ta sa." Haka nan suka isa bakin titi Asma tana ta mita, domin dai tunda suka fito motoci ke tsayawa amman Zainabu ta dage ba za ta hau motar uban kowa ba yau, don haka sai da suka isa har bakin titi Asma sai mita take yi tana fadin da ta sani ta zo da motarta, don wani saurayinta ne ya kawo ta a mota, duk inda suka gifta sai an bi su da kallo domin dai Zainabu akwai ta da daukar idon duk wanda ya kalle ta, sai ka ji kamar ace matarka ce, sai tasi suka tara ta kai su gidan Asma din, sai da dare ya yi sannan suka fita suka tari tasi ta nufi club din. Sanda suka isa club din sun tadda shi dinke sai cashewa ake yi, nan fa kawayensu suka yi musu caa a kansu ana ta cafkewa don sun kwana biyu ba su gansu a club din ba. Idan ka ga yanda gurin yake da irin yanayin shigar su zaka rantse babu wacce ta san Zo na kashe ka da hausa, balle a je ga addini, domin gurin yana can cikin sabon gari cike yake da tantiran 'yan iska kamar ba a garin Kano ba ne garin musulunci ba . Wani saurayin Asma ya isa ya kama kugunta suka shiga filin rawa suna takawa, Zainabu ta yamutsa fuska sannan ta nufi gurin shan barasa (wine station) tana wani taku tamkar tarwada, ta jawo kujera ta zauna ta amshi kwalbar mutuniyar tata ta balle bakinta ta kafa kai ta kama sha babu ko kofi, sai da ta sha ta ishe ta sannan ta dauko tabar shaidan ta kunna ta dora kafa daya kan daya tana kallon kowa daidai, can ta fara caji ga shi an sanya wakar da take masifar so ta love is wicked, ai kuwa ba ta san sanda ta yi tsalle ta fada filin rawar ba, daman ga ta gwanar rawa musamman an sanya wakar da take masifar so, sannan ta dace da lokacin da take ciki, habawa nan fa 'yan maza suka mai da hankalinsu gare ta, wani mai karambani ya shiga da zummar taya ta har yana kokarin ruko ta, sai kawai ta zabga masa wani uban mari gami da yin taga-taga kamar zata fadi. Gabadaya gurin aka sanya ihu da shewa har da masu fito, ya dube ta cike da tsananin takaici sai ya daga hannunsa da zummar ya rama, amman sai ya ji an rike hannunsa gam. Ya waiga domin ya ga wanda ya rike masa hannu sai ya ga wani hadaddan saurayi ne, ya kalle shi yana dariya sannan ya ce, "Haba yaya zaka taba mana golding baby? Kai ne fa ka zo har inda take bayan ba ta gayyace ka ba, ka ga matsa ka bamu guri dalla." Ya yi kwafa ya bar gurin cike da tsanani kunya. Ita ma sai ta fice daga filin rawar don ranta ya baci da iskancin da ya yi mata, don ba ta shirya kula kowa ba, zuwa ta yi kawai ta sha abunda za ta sami sanyi a ranta, amman wani dan iska yana neman bata mata rai. Gayen da ya rike hannun wawan ya biyo ta sanda take janyo kujera tana kokarin zama, ya kura mata ido tamkar maye, ita kam da ta kalle shi sau daya sai ta kauda kanta gefe. Ya rausayar da murya cike da yaudara ya ce, "Barkan ki da hutawa golding baby. Ta rausayar da kanta tana dubansa kawai tana zukar tabar shaidan din ta, sai ma ta lumshe idonta ta ki cewa komai. Bai damu da hakan da ta yi ba ya cigaba da magana, "Sunana Amir, tunda na shigo club din nan kika kashe mini idona, domin dai ke ce tauraruwa mai haske a gurin." Ta kuma kallon sa shekeke, sai dai ko babu komai yana da kyau da iya gayu, sai ya fara tsokano mata kamannin Mustafa ma, amman sai ta dake ta ce, "To kai yanzu yaya za'a yi? Ni ka ga abinda ya kawo ni na sha na ji sanyi a raina." Ta nuna masa tabar dake hannunta. Ya kuma kwantar da murya irin ta 'yan mazan da suka iya sace zuciyar mata ya ce, "To ban da abinki ai duk jirgi daya ya kwaso mu, ki kwantar da hankalinki za ki samu duk abinda kike so a gare ni kin ji ko? Mata da dama suna so na amman ke daya tal kika mini, na san zan iya burge ki." Ta yi murmushi kawai tana dubansa a ranta tana fadin, "Malam baka san Mustafa ba ne ya fi ka komai, ai za'a dade kafin a sami kamar sa a cikin maza, amman tunda ya yadda ni bari na gwada ka, ai da babu gwara babu dadi."Da wannan shawara ta mike yana biye da ita suka nufi dakin da ya kama don irin haka. Ta fuskanci Amir shi ma hatsabibi ne irin ta, sai dai sam bata ji ya burge ta ba, hasalima ji ta yi ba zata iya mu'amala da shi ba, sai kamannin Mustafa suka fara yi mata gizo duk da kwayar da take kanta daram shi ta dinga gani a can bakin kofa yana mata murmushin da yake kashe ta da shi, don haka ta hankade Amir ta kwashi takalminta da jakarta da gyalanta a hannu ta nufi kofa. Ya bita da sauri yana fadin, "Oh! Baby kada mu yi haka dake mana, zo ko nawa kike so zan baki, please kada ki bar ni ki taimaka mini mana." Ta yakice hannunsa daga jikinta da ya kamata ta galla masa harara tana fadin, "Kai gaye ka rabu da ni." Da tsawa take maganar don haka ya tsorata ya sake ta da saurinsa. Ta fice fuu kamar mahaukaciya, tana tafe tana hada hanya kamar zata kifa saboda tasha ta fi karfinta. Shi kuwa zaman dabaro ya yi bisa kafet din ya dafe kansa cike da tashin hankali, shi a tarihin rayuwarsa bai taba neman yarinya ta ki shi ba saboda yana da kyansa da kudinsa ga ilmi, sannan shi din gwani ne gurin iya soyayya, amman ya sami wacce ta kwafsa masa, lallai Bebin nan ta shammace shi matuka, ga shi ta tsaya masa a ransa, don ya dade a bariki bai ga macen da ta hada komai dari bisa dari kamar ta ba, amman babu komai in dai kare yana yawo zabo ma yana yawo wata rana za'a hadu, don haka ya fice neman wacce za ta rage masa daren nasa. Ita kam haka ta nufi hanyar fita tamkar zata kifa, takalmi da jaka da gyale duk a hannunta, Allah dai ya taimaka Asma ta hangota bayan ta futo daga watsewarta, don haka ta nufe ta da sauri tana mata magana amman ko kallonta bata yi ba, da dai ta lura kawar tata tayi duf ta koma gurin saurayin nata ta nemi alfarmar ya kaisu gidanta, babu musu ya amince don yana ganin wata karin dama ce a gare shi ma. Da kyar ta samu ta turata a motar tana ta tirjewa suka nufi gidan Asma din, a falo ta zube Asma ta fara tambayar ta abinda ya faru, amman ko kala ba tace ba daga karshe ma sai ta mike da kayanta a hannu ta nufi dakin kwanan Asma din.Asma ta kalli saurayin nata wanda yake tsaye yana kallonsu da alamun rashin damuwa a idonsa, ya daga kafada yana fadin, "Wannan kawar taki muguwar 'yar buyagi ce wallahi, ki dubi yanda ta yi duf ta kuma ki sauraron kowa, sai gasawa 'yan maza gyada a hannu take yi, ki rabu da ita kawai ki zo mu kwanta." Bata yi masa musu ba suka nufi daya dakin baccin nata. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ita kam tana isa dakin baccin ta yi watsi da kayan dake hannunta ta kwanta jabar a gado, duk da bata cikin hayyacinta hakan bai sanya ta manta da kamannin Mustafa zuman ta ba, harma sai take ganin kamar sanda take cikin hayyacinta tafi dauriyar rashinsa akan yanzu ma. Wani irin ciwo mai zafi ya taso mata a kirjinta, ta ji zuciyarta kamar tana tafasa, ta dafe kirjin da taji yana mata zafi hawaye suka shiga wanke mata fuskarta a hankali ta dinga fadin, "Mustafa mai nayi maka ka guje ni, ka san yanda nake jin zafin rabuwa da kai a zuciyata kuwa? Zo ka taba zuciya ta kaji kai kadai ne ka mamaye ta, muddin ka barni zan mutu ne kawai, bani son kowa sai kai, kai ne rayuwar Zainabu." Tamkar yana gabanta haka take magana, saboda kwayar ta dake gaya mata karya wai gashi nan a gabanta zaune a kan kujera, ta lumshe idanuwanta ta mika hannunta tana fadin, "Ka daure ka taba zuciya ta ka ji, domin na kusa mutuwa da sonka." Ta jawo fulo ta rungume sai ta saki kuka mai ciwo, wai wacce irin masifa ce ke barazanar daukar rayuwarta ne? Ta yunkura ta wurgar da fulon ta nufi jakarta domin wata shawara da zuciyarta take kitsa mata. Ta kama binciken kayan jakar tana watsarwa, har ta ci karo da abinda take nema wato wayarta ta tafi da gidanka, ta kama laluban lambarsa har ta yi sa'a ta samo ta da kyar tana ganin dusu-dusu ta kama kokarin nemanta. Daga can gidan Momi ce a kwance ta sanya wayar Mustafa a caji wacce ta ci karo da ita a dakinta, don anan ya yadda ta sanda ya suma, ta ji ta tana kara ta mike da sauri don taga mai kiran, don tana zaton ko abokansa ke nemansa ta sanar da su bashi da lafiya. "Zainabu Zuma." ta gani baro-baro a jikin gilashin wayar, haushi da takaici sai ta ji kamar kada ta daga, amman sai taga wannan ce damar da ya dace ta gargadi yarinyar ta rabar mata danta kawai. "Musty zumana! Yaya kake?" Daga jin muryar ta kasan tana cikin maye ne. Hankalin Hajiya Kubra ya kuma tashi matuka, don haka da bacin rai ta fara magana, "Ke! 'Yar iska ba Mustafan ba ne, shegiya karuwa kin dafe mini yaro kamar kaska, yanzu haka yana can a gadon asibiti rai a hannun Allah saboda mallake shi da kika yi tsafi da tsafi, to bari na gaya miki ko da kinfi kuturu naci, kuma koda kuna tsafi da kare ne baki isa ki auri Mustafa ba wallahi, domin shi yaro ne dan mutunci da ya futo daga gidan mutunci, kurwarsa kur!" Zainabu sai taji ta wartsake gaba daya domin dai ko daga bacci ta tashi ba zata taba manta muryar Hajiya Kubra ba, ga shi kuma tace Mustafa ba shi da lafiya yana can rai a hannun Allah, sai taji ko kusa maganganun ta basu bata mata rai ba sama da ciwon Mustafa, ta daure da kyar tace, "Hajiya ki yi hakuri don Allah ki bani Mustafa mu yi magana ban san bashi da lafiya ba, yana ina yanzu? ki bani shi kada na mutu." "Ki mutu din mana, ai da mun huta da bala'in da kika ja mana, shegiya macuciya kiji yanda kike magana da alama giya kika sha, Allah ya tsaremu da hada zuri'a da ku, dangin na ayya gayyar tsiya." Ran Zainabu ya yi matukar baci da jin kalaman Hajiya Kubra, lallai ta yadda wani yana cin arzikin wani ko a lahira, don haka Hajiya Kubra ta ci albarkacin danta, amman duk da haka ya dace ta sanar da ita ko da kalma daya ne, ta bude baki da zummar tayi magana amman sai ta ji layin ya dauke, alamar ta katse kenan. Ta kuma kiran layin amman sai aka sanar da ita yana kashe ne ma, ta fada gado cike da tashin hankali ga maganar da Momin ta gaya mata ga kuma rashin lafiyar da aka ce mata Mustafa yana yi, haba ta san haka kawai Mustafa ba zai iya rabuwa da ita ba ashe bashi da lafiya ne. Hajiya Kubra tana tsaka da wayar ta ji ta mutu tana dubawa sai ta ga caji ne ya kare don bata dade da jona wa ba, kuma sanda take wayar ta goce daga cajin, ta yi kwafa gami da wurgar da wayar cike da bacin rai, don yau ta so ta gayawa yarinyar nan maganar da zata rabar mata da danta dole, ta fada gado ta kwanta amman sai taji bacci ya kauracewa idonta gaba daya, ta mike zaune ta hada tagumi da hannuwa bibbiyu. Wai yanzu wannan 'yar iskar yarinyar Mustafa ke so? Lallai bata raba dayan biyu daga ji a cikin maye take magana ma, tabbas komai zai faru sai dai ya faru amman ba zata yadda danta ya auri karuwa ba, ga shi ta lura kamar Alhajin ya fara amincewa, don yanda taji kalamansa ta fuskanci ya sauko daga kan kudurinsa, don dai bai san wacece Zainabu ba ne, ita kam ta yi mata farin sani. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Da safe ma ta kuma kiran layin nasa amman a rufe yake, tunda ta idar da Sallah da asuba take kiran layin nasa amman a rufe yake, yau kam ta jima tana yiwa Mustafa addu'ar samun lafiya a sallar ta, a bandaki ma gurin wanka ta jima tana tunanin yaya za ta yi, har ta gaji da dukan shawar amman bata sami wata ma futa ba, daga karshe dai ta yanke shawarar ta ta tadda Asma ta ji irin shawarar da za ta ba ta. Ta shirya cikin koriyar atamfar Asma super wax, dinki ya kamata sosai don tafi Asma din jiki, ta dora dankwalin ta yayi das a kan nata, duk da bata da wadataccen gashi ta kanyi kitso koda yaushe ko ka tadda ya sha gyara, da yake kuma tana da saje na gefen kunnen kuma gashin nata mai taushi ne sai kayi zaton tana da gashi mai dama kasancewarta fara tas. Fuskarta ta yi fayau domin babu kwalli balle jan baki, sai ta futo a ainihin (natural) din ta, hakan ma ta yi kyau matuka, don idanuwanta daman masu kama da kalar zuma ne bata sanya kwalli sai dai taja jagira kadan a cikinsa, don har wani kore-kore yake yi tamkar na mage saboda kyau da kyalli, masu irin idon nata kadan ne a duniya ma, musamman idan ta so iskancinta sai ta dinga wani lumshe su tana wani budewa sai ka ga mutum ya sukurkuce mata. A falo ta tadda Asma daga ita sai wando (three quarter) iyakacin gwiwa tana karyawa gami da kallo, ta sami kujera ta zube can kuma sai ta mike tana fadin, "Ina fatan dai ba shegen dan daudun nan ne ya yi miki girki ba don kin sanni ni ko a gidan mu da kaina nake girki na don bana son jagwalgwalo." Asma ta yi dariya tana fadin, "Ai kuwa sai dai ki dafa wani don nasan halinki ni kam ina da mai aiki babu abinda zai sanya ni shiga kicin." Ta ja tsaki tana fadin, "Ai kya ci mara dadi da kazanta ,tashige ciki ta kama kacaniyar samarwa kanta abinda za ta ci. Bayan ta kammala girka abinda zata ci ta futo falon ta zauna ta kammala ci sannan ta ce da Asma din, "Wai ina sha-sha-shan naki ban ji motsin sa ba ko har kin gama da shi ne?" Asma ta yi dariya tana fadin, "Shegen Ofi ya wuce don da kunya dai yace zai koma gida shiri sai dai yayi musu shigar dare." Ta ja tsaki tana fadin, "Allah dai ya shirya shi." Sannan ta sauya maganar da fadin, "Ke nifa jiya na kira wayar Mustafa....." "Kai amman kin bada gayu wallahi, ke da nace ki share shi har sai ya kawo kansa mu gasa shi tamkar gyada?" Ta tabe baki sannan ta ce, "Na so yin hakan amman na gaza, jiya ban cikin hayyacina sosai nayi kiransa, don ban zaci zan wayi gari ba, saboda wani irin zugi da zuciyata ta dinga mini, kai Asma so masifa ne wallahi, sai dai me, kin san Babarsa ce ta daga wayar?" "Bar gayan don Allah. Ya ya aka yi wayarsa ta je hannunta? Lallai ki ce kunyi babu dadi." Zainabu ta dan tsuke fuska ta ce, "Allah sarki zumana ashe bashi da lafiya, duk da dai bata gaya mini ainihin abinda ke damunsa ba sai cin mutunci da ta yi mini na san ciwon so na ne, don haka maganganunta kadan suka yi mini ciwo domin ta saba gaya mini irinsu, amman nayi alkawarin da izinin Allah sai na auri Mustafa don na nuna mata don ta haife shi ai ba ita ce ta halicce shi ba, sai na nuna mata iyakacin takamarta wallahi a kansa, maganganun da take gaya mini yanzu ne zan nuna mata karuwancin da nake yi ai da danta nake yi, ta ce daman waye zai auri 'yar iska to dan ta ne zai aura da iznin Allah, ni yanzu yanda zan yi na ganshi ne ma ya fi damuna domin nasan ba karamin ciwo ne zai sanya Mustafa ya gaza kirana ba." Asma ta ce, "Lallai ki ce da walakin goro a miya, ni kaina na yi mamaki da kika ce wai Mustafa ya bar ki, amman dole ne mu binciki asibitin da yake mu je mu duba shi, gama karyawa muje gurin maigadinsu mu ba shi na cin goro muji asibitin da yake." Karfe tara na safe likita ya shiga duba shi, sai ya jiyo shi yana magana a hankali, ya matsa daf da shi ya kara kunnensa daidai bakinsa sai ya jiyo yana fadin abinda yake fada tun da ya farka, "Zainabu! Zainabu!" Ya yi niyyar yi masa wata allura amman sai ya fasa ya kara matsawa kusa da shi ya fara shafar kansa a hankali yana kiran sunan sa a hankali. Ya fara far-far da idanuwansa alamar yana son ya bude amman ya gaza, ya kuma matsawa dai dai kunnensa yana fadin, "Mustafa kana son ka ga Zainabun ka? kana son a kawo maka ita ka ganta? to maza bude idanuwanka na gani." A hankali ya bude idanuwansa yana kalle-kalle, likitan ya yi murmushi sannan ya ce, "Msutafa Zainabu kawai kake son gani yanzu? ka tabbatar idan ka ganta ka warke kenan?." Bai iya yin magana ba saboda bakinsa da yaji ya yi masa nauyi sai dai kawai daga kai da yayi alamar eh!.Likitan ya ce, "To shi kenan ka kwantar da hankalinka za'a kawo maka Zainabu har nan gurin ka ganta kaji ko?" Da haka ya fice waje ya tadda Alhaji Abdullahi da Hajiya Kubra dake zaune suna jiran jin abinda zai ce musu, ya dube su ya ce, "(Cogratulations), ina taya ku murna, domin dai danku ya farka, Hajiya Kubra ta daga hannu tana fadin, "Alhamdulillah, mun gode likita." Ya kuma cewa amman akwai wasu sharudda da zan gindaya muku, kai Alhaji ka biyo ni Ofis ku kuma kuna iya shiga ku gan shi. Dadi da farin ciki ya cika su saboda ganinsa idonsa a bude yana ta kalle-kalle, suna shiga ya bisu da kallo sai kuma ya yi murmushi don ya shaida Mominsa ce da kannansa. Suka isa suka zauna kusa da shi suna dariyar murna, Momin ta hau shafar kansa tana fadin, "Babana sannu ka ji, yaya jikin naka?" Ya bude bakinsa ya ce, "Alhamdulillah, Momi yaushe aka kawo ni nan ne?" Da lallashi ta ce, "Kada ka damu ka kusa komawa gida tun da kai ka sami sauki, za ka ci abinci ne?..... Ko da yake bari likita ya dawo mu tambaye shi." Haka nan ta dinga jan sa da hira cike da jin dadi da farin cikin farfadowar tasa. Karfe goma suka isa dakin da yake, domin dai sun ga Maigadin ya sanar da su asibitin da yake har ma da dakin da yake don ya je ya duba shi, sai dai ya roki alfarmar kada su ce shine ya sanar da su. Sanda suka isa Momi ce ta fara ganinsu, Zainabu ta ci kwalliya matuka da wani Swiss lace haka ma Asma din, ko da daga bacci ta tashi ba zata manta da kamannin Zainabu ba, don haka ta mike a gigice da masifa. Shi kuwa Mustafa tun da yaji muryarta ta yi sallama ya kura mata ido da wani mayataccen so, ji yake kamar ya zama tsuntsu ya isa inda take. "Ke! Me ya kawo ki nan? 'Yar iska karuwa, ina ce jiya na yi miki gargadin ki rabar mini da da na, ko shi ne don masifa kika kuma biyo shi." Mustafa ya runtse idonsa cike da jin zafin kalaman Momi, ita kuma Zainabu kyam ta tsaya kamar an dasa ta ta dukar da kanta kasa. A tarihin rayuwarta yau ce rana ta farko da wata ta zage ta tayi kurum ba tare da ta rama ba, zuciyarta ta yi bakikkirin sai tafasa take yi, lallai Momin Mustafa ta ci darajar masu daraja. "Ba magana nake miki ba? Ki fice mana daga daki in ba haka ba na yi miki rashin mutunci, ki dubi irin zuri'ar mu kin san ko dagamu yaron nan bai dace da ke ba, don haka ki rabu da shi tun da girma da arziki, ba zamu yadda ya auri karuwa 'yar shaye-shaye ba muddin muna raye." "Momi don Allah ki yi hakuri kin ga fa yanda Yaya Mustafa ya rintse idonsa kada ciwon nasa ya dawo." Ran Momi ya baci don haka da zafin rai ta ce, "Ke rabu da ni idan wannan 'yar....." Shigowar Alhaji Abdullahi ne ya sanya ta yin shiru. Ya dubesu ran sa a bace ya ce, "Kubra kin manta kuna tare da mara lafiya ne, eye? Ko so kike yi zuciyar yaron nan ta buga ne, wannan wane irin so ne kike yiwa danki? To ki yi hattara in ka kashe shi sai naga wanda zaki kuma matsawa haka."Ta kwantar da murya ta ce, "Ka yi hakuri Alhaji ba da shi nake ba yarinyar nan ce ta zo Zainabu ga ta nan." Ta nuna Zainabu, "Shine na ce ta fita." Ya bi Zainabu da kallo wacce kanta ke a kasa gefe da kawarta wacce ta rikewa hannu, don Asma din ta so rama mata cin mutuncin da aka mata amman ta rike hannunta gam alamar kada ta ce komai, don haka suka yi shiru gaba dayansu. Ya dube ta da kyau ya ce, "Wannan ce Zainabun?" Ta ce masa "Eh." da sauri. Ya ce, "To wuce mu je waje, ke Sumayya taso mu je waje. Zainabu je ki ki ga jikin nasa." Hajiya Kubra ta yi sororo cike da tashin hankali, amman ganin babu wasa a maganar Alhaji Abdullahi ya sanya ta bi bayansa shi da Sumayya domin dai har sun nufi kofa su, bayan ta zabgawa Zainabu harara gami da yin kwafa. Zainabu ta yi murmushin cin nasara ta rufe kofa da sauri ta nufi gurin Mustafa wanda har lokacin idonsa yana runtse. Ta durkusa a gabansa ta kwantar da kanta daidai kirjinsa ta kamo hannunsa ta sakale cikin nata, ta matsar da bakinta dai dai kunnensa, cikin wani salo da kashe murya ta ce, "Musty Zuma please wake up, ka tashi." Ya bude ido a hankali yana duban ta, bugun zuciyarsa ya fara sauyawa zuwa daidai, jinsa yake yi tamkar a wata duniyar daban, ya dago hannunsa wanda ke rike a cikin nata, wanda ba'a sanyawa karin ruwa ba ya rungumeta sosai a jikinsa, cikin kunnuwanta yake fadin, "Zainabu ke ce da gaske? Ina kika boye ba ki zo ba na kusa mutuwa?" Hawayen dadi suka dinga disowa daga idanuwanta suna sauka a kirjinsa, wanda yake jinsu kamar ana yayyafa mai dadi ne a kirjin nasa don yana wanke masa zuciya ne. "Ba zan kuma barin ka ba, ina sonka ban san ba ka da lafiya ba, nima ina can cike da zullumi da fargaba, na yi zaton ka bar ni, ina matukar kaunarka Musty, ina sonka da yawa Mustafa."Wani farin ciki ya dinga shigarsa, ya saki dariya a hankali sai ya ji kamar wani karfi yana shigarsa, sun jima a haka kamar ba zasu rabu ba, Asma na tsaye harde da hannuwa a kirji tana dubansu cike da tausayi da sha'awa. Shi kuwa Alhaji Abdullahi da ya fita kai tsaye Ofis din likita ya nufa, ko bai yi magana ba ta san abinda yake nufi wata ta bishi Ofis din, don haka ta bishi har ofis din. Sumayya kuma ta sami guri ta zauna bisa wasu kujeru ita da Zainab. Likitan yana shirin fita ya shiga ofis din nasa da sallama, ya daga da sauri ya dube shi yana tambayarsa , "Alhaji akwai wata matsala ne?" Alhaji Abdullahi ya ce, "A'a babu wata matsala, ina dai so kayi mata bayani ne kamar yanda kayi mini." Ya nuna Hajiya Kubra da ta shigo Ofis din. Likitan ya ce, "Ok sit Hajiya, na gane ki zauna Hajiya." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Babu musu ta jawo kujera ta zauna, shima Alhajin ya jawo kujerar ya zauna. Likitan ya dauko file din Mustafa ya dan dudduba kana ya kalle ta ta cikin gilashin kara gani, (medicated glass) ya ce, "Hajiya gaskiya kamar yanda na gaya miki tun da farko yaron ku ya kamu da ciwon zuciyar har zuciyar sa ta fara kumbura. kuma a binciken da aka yi muna zaton wata damuwa ya sanya a ransa, mun yi iyakacin kokarin mu ya fara samun sauki, sai dai mun lura ba zai koma dai dai ba har sai da wata Zainabu, wacce albarkacin sunanta muka samu yau ya bude idonsa....." "Na shiga uku na lalace, gaskiya likita ka sake magana, ka san kuwa ko wacece Zainabun da yake fada? ka san halin....." "Ba lallai sai mun san wacece Zainabu ba, fatan mu dai tazo kusa da shi idan har zata amince, domin ganinta ne zai sanya ya dawo cikin walwalarsa, sannan ciwon yayi gaggawar barinsa, idan ya so idan ya warke kome ya dace a yi sai a yi." Likitan ya katse ta da dogon sharhinsa. Ta yi tagumi ranta a tsananin bace, ta kuma daurewa ta ce, "Yanzu likita bayan haka babu wata shawarar da kake ganin zata inganta lafiyarsa? Dole sai dai wannan din?" "Eh, shi ya sanya ma kikaji na ce haka din, sai kuma kashedi na biyu dole ne a guji bata masa rai, duk wani abu da zai zamana akwai damuwa a cikinsa dole ne ya nisance shi, idan kuwa ba haka ba akwai barazanar zuciyarsa ta buga lokaci guda (heart failure), ya fadi ya mutu, don haka ne a kiyaye ka'idojin da na gindaya muku." Ya mika mata file din ya ce, "Ki duba nan wata kila zaki fahimci wani abu tunda kina da ilimi ai." "A'a bar shi kawai ba zan gane jawabinku ba don rubutun likitoci ba kowa ne ke ganewa ba....." "Ta shi mu tafi." Maganar Alhaji Abdullahi ta katse ta, ta mike salo-salo ta bi bayansa jikinta a sanyaye babu kuzari har lokacin ranta a bace yake. Kai tsaye gurin motarsa ya nufa ya kirawo Sumayya a waya ya ce ta taddashi a gurin da yayi fakin din motar ta sa, kusan tare suka iso da Sumayyan, Hajiya Kubra ta shiga gaba ta kame zuciyarta na suya. Sumayya ta leko ta windon gilas ta ce, "Ga ni Dady." Ya dubeta gami da fadin, "Yau ki kula da Dan uwanki zan turo direba ya kawo muku abinci ke da bakin naku, sai da yamma zamu dawo da mamanku, kin ji ko?" Ta ce, "To Dady a dawo lafiya." Ya ce "Amin." Kana ya ja motar suka bar harabar gurin. Sumayya da Zainab suka koma dakin da Mustafan yake ta kwankwasa lokacin Zainabu na gefensa rike da hannunsa suna hira jefi-jefi, gabansu gaba daya sai da ya buga domin sun yi zaton ko Momi ce ta dawo. Zainabu ta dubi Asma ta ce, "Ki bude kofar mana." Asma tayi jim kamar ba zata bude ba can kuma sai ta mike ta bude.Sumayya da Zainab suka shigo fuskarsu cike da fara'a suka gaida su Zainabu. Zainabun ce ta fara magana, "Hala ke ce kanwar tamu da Mustafa ke yawan bani labarinki?" Ta dafa Sumayya tana fadin, "Don kamarsu da Mustfa ta baci." Sumayya ta ce, "Eh nice." Zainabu ta ce, "Allah sarki, yanzu kina wace school ne?" "Ina BUK (Dep. Of Nigerian Languages) bangaren harsunan Nigeriya, ina karanta Hausa Ingilishi." "Allah ya taimaka, bari mu tashi mu wuce gida don mun bar su Dady a waje." "Laa ku yi zamanku yanzu ma sakon dadi din ne ya shigo da ni yace ku zauna su sun wuce gida sai da yamma zasu dawo, zai turo direba ya kawo mana abinci, mu yanzu gurin wata kawarmu zamu da muka yi secondarary school zamu don tana (Catering Dept.) bangaren abinci, za mu gaisa don kullum muna zuwa gwara na bar Yayar tamu ta duba jikin (Big brother) sosai, don daga ganinki har ya wartsake, amman da tamkar gawa yake sai numfashi kawai." Suka yi dariya gaba dayansu har da Mustafa yayi murmushi, suka mike suka fice suna fadin sai mun dawo. Asma ta ce, "Lallai kawata kin kasance mai sa'a, ki dubi yanda komai ya zo da sauki, wallahi ban yi zaton zamu sami ganin Mustafa a yau ba yanda kika sanar da ni yanda kuka yi da Mominsa jiya a waya." Zainabu ta dubi Mustafa tana murmushi ta ce, "Abin a jinin mu yake, haduwar jini ce Allah kadai ya san abinda ya boye a tsakaninmu ko zumana?" Tana magana da wani salo na sace zuciya. Ya yi murmushi kawai sannan ya ce, "Zainabu dan dagani mana ki jingina ni da fulo bayana ciwo yake yi." Ta kamashi sosai a jikinta ta taimaka masa ya tashi ta sanya masa filo a bayansa. "Yaya ko a hada maka shayi ne?" Ya dan girgiza kai ya ce, "Sai dai ki je ki tambayo likita idan yace na sha sai ki hada mini." Ta ce, "Shi kenan bari na je na jiyo, kawar zo muje." Suka fice gurin likita. Su kuwa su Alhaji da suka isa gida kowa sashinsa ya shige, Hajiya Kubra tamkar zata mutu don bakin ciki, ita gani take yi kawai wata makarkashiya aka hada domin ta hada danta aure da karuwa kamar yanda take kiran Zainabu. Da wayarshi Alhaji Abdullahi ya kirawo mai aiki yace maza ta shirya abinci ta baiwa direba ya kai asibiti.Ta ce "To Alhaji an gama." Nan da nan ta hada kayan abinci ta hau girki, shi kuma babbar rigarsa ya cire ya haye gado ya kwanta don ya sami hutu. Sai karfe daya da kwata ya tashi ya watsa ruwa kana ya nufi masallaci ya bi jam'in Sallar azahar kana ya shigo gida, kai tsaye sashin Hajiya Kubra ya nufa. Tana zaune bisa darduma da alama Sallah ta idar itama, sai dai ta hada uban tagumi, daga ganin yanayin fuskarta tana cikin tsananin damuwa ne. Ya zauna a gefen gadonta ya kirawo sunanta, ta juyo da sauri cike da mamaki tana dubansa, domin ba tayi zaton zai shigo sasashin ta a wannan lokacin ba. "Ina so mu yi wata magana da ke, ina fata zaki nutsu ki yiwa magana ta duba na tsanaki, kada ki sanya wata fassara a cikin zuciyarki." Ta daga kai alamar to kawai. Ya ce, "Yauwa, daman akan maganar yaran nan ne, naga kamar kin kufula ko nace kinyi fushi da abinda likitan ya yi miki jawabi. Na sani duk iyaye ba zasu so ace dansu ya auri macen da ba ta gari ba, sai dai mu yau Allah ya jarabce mu da dan mu yana son irin wannan matan, abu daya nake so ki kawo a ranki ko kiyi alkalanci shi ne a ina Mustafa ya gano Zainabu? Wacce alaka ce ta hada su har suka shaku haka har ya kamu da ciwon zuciya don za'a raba su? Amsa daya ce, abokin barawo dai inji 'yan magana barawo ne, ba na raba dayan biyu can gurin shashancinsa ya hadu da ita, ban taba zargin Mustafa yana wannan harkar ba sai da ya furta da bakinsa zai auri Zainabu, sannan na san lallai yana wannan mu'amalar. Duka hukuncin Zainabu da Mustafa daya ne a gurin Allah, don shi babu ruwansa da jinsin mace ko namiji kamar yanda mu hausawa muke cewa, wai iskanci ado ne ga da namiji to shi Allah babu ruwansa, kuma ina zaton wata jarabawa ce Allah ya dorawa Mustafa ta son 'yar iska ko karuwa kamar yanda kike kiranta, domin ya nuna mana shi babu ruwansa da wancan magana ta bahaushe. Don haka ina son ki kwantar da hankalinki muzubawa sarautar Allah idanu,idan ya kaddara aure dan Allah zai iya dora miki wata lalurar da kina ji kina gani dole za'a yi wannan aure. Ki kyale shi ya auri Zainabu don idan Allah ya kaddara matarsa ce duk irin kin da muke mata sai ki ga Allah ya kaddara anyi abin, idan kuma Allah ya kaddara ba matarsa bace sai kiga sun gama soyayyar ya auri wata can daban, ki yi masa addu'a da neman shiriya garesu baki daya, domin shi da na kowa ne, ina fatan kin gamsu da jawabi na? Amman fa kina da damar da zaki aura masa wacce kike so daga baya don kina da iko a kanshi ba wai ina son na nuna miki karfin iko ba ne, a'a nayi haka ne domin samun ingancin lafiyarsa da kwanciyar hankalinmu." Ta yi doguwar ajiyar zuciya gami da goge hawayen da ke sakkowa bisa fuskarta ta ce, "Shi kenan Alhaji Allah ya zaba mana abinda yafi alhairi, ni daman ba yarinyar naki ba illa halayenta don babu wanda zai so ace yau a zuri'arsa an samu batacce, amman shike nan Allah ya shirya zamu ce, sai dai Allah ya sani bana kaunar yarinyar nan har abada don tayi mini abinda har abada ba zan manta da ita ba, sannan idan Allah ya nufa ta auri yaron to babu ruwana da harkarta, sannan zan aura masa nitsatstsiyar mace kamar yanda nake da buri a rayuwa ta." Ya yi murmushi ya ce, "Hadizatul Kubra kenan, na ji ra'ayinki kuma ra'ayi ba gaba bane sai dai ina son ki sassauta kiyayyar da kike mata darajar danki don Allah." Ta tabe baki kamar ba zata ce komai ba kana ta daure ta ce, "Shike nan ya wuce, amman duk sanda za ta zo asibiti ba zan je ba hasalima na daina zuwa da rana sai da daddare don haka sai ta dinga zuwa a lokacin kada mu hadu ban sani ba na gaya mata mummunar kalma." Ya ce, "Shike nan, yanzu dai a daure a bani abinci don cikina ya fara kiran ciroma, don naga yau fishi aka yi dani ko abinci ba'a yi mini tayi ba." Ta ji kunya ta kamata ta mike da sauri tana fadin "Tuba nake, kaje sashin naka yanzu zan kawo maka." Ya ce, "A'a anan zan ci tunda dai sarautar ta motsa yau." Ta yi dariya gami da ficewa dauko masa. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Cikin ikon Allah jikin Mustafa ya yi sauki, kullum Zainabu na zuwa tana wuni a gurinsa, takan dan zo masa da abin motsa baki, duk da kullum ana kawo masa daga gidansu, wata rana su zo da Asma wata rana kuma ita kadi take zuwa. Gaba daya yanzu Hajiya Kubra ta daina zuwa da rana sai dai da yamma ko da safe, don haka suka sami damar baje kolin soyayyarsu. Sala ma tayi mitar har ta gaji domin dai samarin Zainabu ko nace abokan watsewarta tun suna sintiri har sun gaji sun fara janye jikinsu, dan kudin da suke kawo mata yanzu duk sun daina, ita ma Zainabu yanzu babu kudi kamar da sai wata ya kare take samun albashi, don ma Sadiku yana kawo mata kayan abinci da kuma kanwarta Karima da ita ma take dan kawo mata wani abun wani lokaci, amman duk ta raina tafi son a dinga kawo mata na banza(wai a banza,masu karatu kuyi alkalanci abanza take samu?) shi kuwa Baba Abbakar yana nan jiya iyau, tsufa yana kama shi amman ya gaza tsinana wa kansa wani abin kirki. Kullum yana gindin bishiya duk wanda zai wuce ko zata wuce sai sunyi gulmarsa, idan mai kudi ne su bishi da sai kayi ko a dawo lafiya ya hajjaji, a bisu da naira dari biyar ko dari biyu-biyu suna wawaso. Su kuwa sauran yaran sunan nan wasu suna karatun wasu kuma suna nan suna ta yawon talla, don babu wanda ya isa ya cirewa Sala ra'ayin talla a jikinta. An sallame shi cike da samun cigaba a lafiyarsa, sai dai an kafa masa dokoki na shaye-shaye, dole likita ya hanashi shan ko da taba ne balle kwaya ko giya, amman tsakaninshi da shi yayi masa kashedin don dai iyayan nasa basu san yana sha ba da bamu san yanda Hajiya Kubra zata kuma ji ba. Ya dawo gida cike da dardar domin dai bai san yanda ake cikin akan maganarsa da Zainabu ba, shin sun amince ne ya aureta ko kuma suna nan akan bakansu ta dole sai dai ya nemo wata ya aura? Shi dai bai cigaba da zuwa gidansu Zainabu ba, sai dai sun cigaba da yin waya, a wannan lokacin sai suka ji tamkar an daure su a kurkuku ne, ga shi har yanzu iyayensa ba su ce masa komai ba, har ya koma bakin aikinsa yana zaman dar-dar. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 **************** Ranar wata juma'a wacce tayi dai-dai da sati biyu da fitowarsa daga asibiti Alhaji Abdullahi ya yi kiransa falonsa da yamma. Gabansa ya kama faduwa don bai san kiran da yake masa ba, ya isa falon idan zaka tsaga jikinsa tamkar babu jini, ya zauna a kasa ya kuma durkusawa ya gaida Baban nasa. Alhaji Abdullahi ya amsa fuskarsa babu yabo babu fallasa, kana ya fara magana, "To Mustafa ka ga dai abubuwan da suka faru tun daga ranar da wannan al'amarin ya faru. Da farko ni da Mahaifiyarka mun nuna bama son auran nan har mun kafa maka wasu sharudda to kuma sai gashi wannan ciwo ya bullo sanadin dokar da muka kafa maka. Ba wai muna kin Zainabu akan mu bane a'a sai dai muna kinta ne saboda halayenta, amman a iyakacin tunanina da kuma yanda ka dage kana son yarinyar nan duk da illar da muke hange maka nasan akwai wani abu da Allah ya boye a kasa kuma dai 'yan magana suna cewa, abokin barawo dai shima barawon ne. Don haka muka amince ka auri Zainabu domin samun wanzuwar lafiyarka, amman da sharadi, da farko dole ne ta zama mace ta gari, abun nufi ta tsarkake daga halayen ta miyagu, sannan ta sami tsarki, sharadi na biyu kuma dole ne ka rintse idonka daga jin duk wata magana daga mahaifiyarka don ta fadi bata kaunar yarinyar nan, abu na karshe kuma tace dole zata zaba maka wacce take so ka aura daga baya, ina fatan ka amince da wadannan sharudda? Tunda ya ji Babansa ya amince da auransa da Zainabu ya ji wani irin dadi ya rufe shi, tamkar ya shide don dadi, bakinsa ya kasa rufewa don murna, ya bude baki cikin farin ciki ya ce, "Baba nagode Allah ya saka, kuma Insha Allahu zanyi aiki da abinda ka ce." Sam yama manta da sharadin Hajiya Kubra da haka ya bar falon cike da farin ciki. A hanya saka ci karo da Hajiya Kubra, ta kalle shi kawai babu yabo babu fallasa, ya dukar da kansa kasa yana fadin, "Momi na gode." Bata ce masa komai ba ta shigewarta cikin dakin, bai ji dadin abinda tayi masa din ba, amman dai tunda ta amince shi kenan, ya fice daga gidan cike da murna ya nufi sashinsa. Sanda ya zauna bisa kujera ya kirawo layin Zainabu ta daga wayar da sauri tana fadin, "Zuma yaya dai kwana biyu?" Yayi murmushi gami da kwanciya bisa kujerar da yake kai ya ce, "Albishirinki?" Ta yi dariya cike da jin dadi gami da kashe murya cikin kissa ta ce, "Goro fari kal, na kuma baka kyautar Zainabu har abada." Ya yi dariya ya ce, "Zainabu zuma kin gama da ruhina, lallai da su Momi sun hanani ke da ban san yanda rayuwata zata kasance ba, yanzu dai ina miki albishir da cewa, Momi da Alhaji sun amince na aureki, don haka ki shirya yau kina da babban bako." Dadi ya cikata ta doka tsalle gami da fadin, "Don Allah da gaske kake Musty, kai amman naji dadi, har naji kamar na zo yanzu ma na ganka, don baka san yanda raina ke kuna ba akan rashin ka ba, ina sonka Mustafa zumana." Tana magana cikin salon sace zuciya da jan hankali. Duk ya wani sukurkuce tamkar ya tashi ya tafi, da kyar dai ya samu yayi hakuri har zuwa dare don bai san ya nuna zalamarsa a fili har Mominsa ta ji haushi, gwara ya zauna ya ci abincin dare kamar ko da yaushe yanda ko ya dawo ba zata gane ba. Suna gama waya ta mike ta fara shiri, ta dauko magunguna na mata ta fara sha tamkar wacce mijinta ne yayi tafiya zai dawo (Fauza ta ce, "wata masifa ce yanzu ta same su ta 'yan matanmu ko nace karuwan gida na shan maganin mata, zaka ga mace bata da aure amman saboda an daurewa iskanci gindi sai ka ganta da magani kala-kala, daga na mata zuwa na tsarin iyali wai don kada su dauki ciki, ya Allah ka shirya mana al'ummarmu ta wannan zamani masu irin wannan muguwar dabi'u, idan kuma ba zasu shiryu ba Allah kafi kowa sani, kayi mana maganinsu don albarkacin Masoyinka Rasulullahi Sallallahu Alaihi Wa Sallam", Amin). Sala ta fara murna ganin diyar ta ta fara giringidishin shiryawa a zatonta ko ta hakura ne da Mustafa zata cigaba da harkarta kamar da can, don haka ta fara mata kirarin nata, ita kam Zainabu murmushi kawai take yi, tana fadin a ranta, "Sala kenan, ita dai kudi kawai sune burinta idan babu su babu sauran zaman lafiya, idan zaki hakura ki hakura Mustafa ya gama da ruhina ba zan iya cigaba da abin da kike nufi ba." Karfe takwas da kwata na dare wayarta ta fara kira, ta mike da azama tana kuma gyara kanta, tana sanye cikin wani leshi ne wanda aka hada shi da yadin Swiss gurin dinkin, kalarsa purple ne dark da fari, dinkin ya kamata tsam a jikinta riga da siket ne matsatstsu tamkar zasu yage, kugun nan ya fito cas-cas, ta yi kyau matuka kamshi kam ba zaka iya tantance wanda take yi ba takamai-mai. Ta nufi kofar gida tana wani yauki da yanga, ya dinga kallonta cikin hasken fitilar nefa da ta haska kofar gidan na su, tamkar ya zama tsuntsu ya je ya tarota, ya lankwasar da kai yana lumshe idanuwansa. Ta isa ta bude motar ta shiga ta maida kofar ta rufe, ya maida dubansa gurinta yana wani lumshe ido, duk ta gama kacalcala masa lissafi, shi da yazo da wata niyya daban. Ta rangwadar da kai gefe cikin kissa da kisisina ta ce, "Musty zuma ka ganka kuwa yanda ka hadu tamkar wani prince? Dan sarki, shigar nan tayi mini wallahi." Ya ji dadin maganarta har ransa, Zainabu daban ce tana da salo na sace zuciyar mutane, ji yake tamkar ya aiwatar da abinda zuciyarsa ke ingiza shi, amman ya dake ya ce, "Zainabu dole ki daina wannan shigar har zuwa lokacin da zaki zama mallakina, idan ba haka ba zaki wargaza mana lissafi." Ta dubeshi da rashin fahimta ta ce, "Ban gane abinda kake nufi ba, na zaci kace komai ya wuce ne." Ya kwanta jikin kujera ya lumshe idanuwansa ya ce, "Zainabu mu din nan musulmi ne diyoyin musulmi, dan haka ya dace duk abinda za muyi mu yi shi bisa tsarin addininmu, na sani muna sane muke take gaskiya saboda son zuciyarmu, amman mu godewa Allah da ya fargar da mu muna raye, Masha Allah, abin da nake son na sanar da ke shine, Mustafa zai auri Zainabu da kyakykyawar niyya da nufin samun tsarkakakkiyar zuri'a."Ya dago gami da bude idanuwansa yana dubanta wacce duka jikinta yayi sanyi kalau, "Zainabu ba zan kuma kusantar ki ba har sai kin zama mallakata, kin zama matata da izinin Ubangiji, za ki yi Istibira'i, ma'ana zaki tsarkaka muyi Istighfari mu fita daga fushi Allah sannan muyi aure cikin kyakykyawar niyya, ina fatan kin fahimci abinda nake nufi yanzu?" Ta yi ajiyar zuciya, jikinta duk ya mutu wani Imani da tsoron Allah ya shigeta, ta dukar da kanta kasa ta ce, "Shi kenan Mustafa, duk abinda ka tsara ina maraba da shi, na kuma ji dadi da ka tuno mana da wannan hanya ta neman gafarar Mahaliccinmu, sai dai ban gane yanda ake yi ba ka fahimtar da ni." Ya ce, "Yauwa abinda ake nufi da Istibra'i shine, idan mace tana sabon Allah (Zina) ta kuma amince za ta yi aure sai ta tuba ga Allah ta kuma samu tsarkin mahaifa, ma'ana ta zauna ba tare da ta kuma hulda da wani namiji ba har sai tayi jini uku, ba wata uku ba, a wata mazhabar kuma ance jini daya ne, domin dai yin jini shine hukuncin, don kin san wata matar sai ta yi wata biyu sannan take al'ada wata kuma wata hudu, don haka sai sunyi jinin nan dai sau uku, kin tabbatar kin sami tsarki sannan ki yi aure, muddin kina son yin tsarkakakken aure, duk wacce tayi aure tana sabon Allah (zina) ba tare da ta yi Istibra'i ba to tamkar tana cigaba da aikata sabo ne in dai ta sani, sai dai idan bata sani ba, amman shi Allah babu ruwansa baya amsar uzuri da jahilci, amman dai ilimina kalilan ne ban sani ba ko da gyara, dan haka zan sami wani malami yayi mini cikakken bayani, sai dai zamu fara lissafi daga gobe ne. Za ki daina zuwa ko ina sai dai gurin aikinki, shima ba zaki dinga mu'amala da kowa ba, ni kaina ba zan dinga zuwa kullum ba saboda gudun tunzirawar shaidan, sannan zan yanko miki hijab gobe wadda dole lallai da su zaki dinga fita duk inda zaki....Zandakata a nan,inshaAllahu zancigaba nan ba dadewaba,amma a gaskiya quick response dinku shi ke karamin kwarin gwiya,kenan inna bukatar comment dimin cigaba,Nagode.Naku ANaM Dorayi Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 Idan Zuciya Tagyaru2-02 Posted by ANaM Dorayi on 06:34 PM, 09-Feb-16 Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU ______________ Na ________Fauziyya D Sulaiman_____ Sannan zaki sanar da iyayenki halin da ake ciki domin su zama shaida ga alkawarinmu."Ta ji dadin abinda ya ce har cikin ranta, don haka babu musu ko jayayya ta ce, "Na amince Mustafa Allah ya shige mana gaba." Ya dubeta fuskarsa ta sauya kala zuwa bacin rai, bakin kishinsa ya fito balo-balo a kan fuskarsa, har ya bata tsoro kamar ba zai yi magana ba can dai ya daure ya ce, "Zainabu ni mutum ne mai kishi kin sani, balle ke da nake jin tamkar ruhin jikina, na baki amanar kanki don girman Allah ki rike mini amana kada ki ci amana don Allah, kada ki bata mana aure ki amince mu yi tsarkakakken aure don Allah." "Kada ka damu Mustafa, nayi maka alkawari zan kare kai na, ba zan ci amanar ka ba Insha Allahu." "Shi kenan ki shiga gida, amman kada kije ko ina gobe har sai nazo." Ya zira hannu cikin aljihunsa ya zaro kudi masu yawa ya mika mata, "Ki rike wannan don bani son ki nemi wani abu ki rasa." A karo na farko da Zainabu ta ji kunyar amsar wani abu daga hannun namiji kenan, ta ce, "Ka barsu kawai ina da kudi cikin akawun (account)." "Ki amsa don bani son ki cigaba da mu'amala da wadannan kazaman kudin." Ta amsa babu gaddama ta bude murfin motar ta fice tana fadin, "Zuma sai da safe." Ya ce, "Allah ya tashe mu lafiya, ki kula da kanki sai goben." Ya dukar da kansa bisa sitiyarin mota don baya son shaidan yayi galaba a kansa, sai fadin Innalillahi wa inna Ilaihi raji'un kawai yake yi, don wata irin sh'awa yake ji tana bijiro masa ta Zainabu wacce bai taba jin irinta ba, ya kuma sani sarai shaidan ne ke tunzirashi don ya lalata masa kyakykyawar niyyarsa, haka nan ya ja motar ya bar kofar gidan jikinsa babu kwari tamkar wanda aka yiwa duka. Itama da ta shiga gado ta fada cike da kewar Mustafa, sai take ganin watanni uku suna da tsaho, amman yaya zasu yi muddin suna son yin tsarkakakken aure dole ne su bi dokar Allah. Sai dai tana tunanin za suyi rigima da Sala muddin ta ji zancen zata yi aure, domin dai ta lura Sala sam bata son tayi aure tafi son tayi ta watsewa, bayan babu abinda ke tattare da karuwanci sai bakar wahala da tozarci da wulakanci daga gurin maza, sannan jama'a su dinga kallonka a watse. Za ta fara yiwa yayanta Sadiku magana duk da ba jituwa suke yi ba, ta san idan ta kawo maganar aure zai amince. Tana zaune a dakinta tana yin game a wayarta ta ji shigowarsa zai dauki abinci, ta yanda ta gane ta mitar Sala ne tana fadin, "Kai na gaji wallahi da wannan doguwar Sallamar taka kana firgitani, don sai na yi zaton kirana ake zan amshi kudi, don jaraba kullum ba zaka tashi shigowa daukar abinci ba sai kusan goma na dare?" Ya yi murmushi ya ce, "Sala kenan, kin san dai daga makarantar dare nake, tun da da rana bana samun zuwa saboda aiki, kuma ba'a tasowa da wuri." "Oho! Kai ka sani can kaje ka karata ni ba zaka gaya mini karatu ba, Allah dai ya kusa raba yari da barawo, don ma iyayen matar taka kananan mutane ne suka sanya rana har wata biyar, da ba haka ba ai da tuni anyi mun huta da saka ido."Shi dai ya dauki abincin sa ya fice yana murmushi, idan da sabo ya saba da mitar Babarsa, kuma wai duk don yace a yi aikin kirki abi dokar Allah ne ya sanya take gaba da shi. Sai da Zainabu ta kintaci ya gama cin abincin nasa sannan ta yafa gyalan da take Sallah da shi, don duk kayanta shine babba ta nufi shagon na sa. Yana zaune bisa kujera yana duba wani katon littafi na addini wanda ita kanta bata san ko wanne ne ba, ta shiga dakin da Sallama. Mamaki ya kamashi, don dai rabon da ta shiga shagonsa har ya manta, balle yaji tayi sallama, yarinyar ma da bata yi masa magana sai taga dama, amman ya daure ya amsa sallamar dan bai san meke tafe da ita ba. Ta zauna a daya kujerar dake cikin shagon ta ce, "Sadiku gurin ka na zo, ina son muyi wata muhimmiyar magana." Yan dubanta da mamaki tamkar ya ce ta bar masa shagonsa, amman tun da bai san da maganar da ta zo ba ya hakura ya ji idan da shirme ta zo masa ya fatattake ta, ya ce, "Ke nake saurare, ina fatan dai lafiya?" Ta gyara zama tana fadin, "Lafiyar kenan, domin dai na yanke shawarar zan yi aure ne....." "Aure?" Ya tambaya da mamaki. Ta ce "Aure zan yi Insha Alla, zan auri Mustafa dan gidan Alhaji Abdullahi tsohon saurayi na, mun yanke shawarar za muyi aure duk da tirjiya da muka samu daga gurin iyayensa, amman yanzu sun amince yau ya zo ya sanar da ni, yanzu mun yanke shawarar zan yi Istibra'i na tsarkaka sannan ayi auren, shine ya ce na sanarwa da iyayena, to ni ina shakkar sanar da Sala ne domin ban san yanda zata dauki maganar ba." "Masha Allah, Alhamdulillahi." Ya fadi da jin dadi, domin dai abinda ya dade yana son ji kenan, ya kuma dade yana addu'ar gani, A ce Zainabu ta shiryu ta yi aure kamar 'yar uwarta wacce ke zaune lafiya gidan mijinta yanzu. Ya gyara zamansa ya ce, "Ya ya za kiyi dole ne ki sanar da ita, don tasan dole za kiyi aure komai dadewa, duk da nasan tafi son kiyi ta watsewa, amman tunda Allah ya shirye ki ya juyo da hankalinki shi kenan, sai muyi wa Allah godiya, ki sanar da ita yanzu idan kin shiga cikin gida ni kuma gobe zan sanar da Baba idan mun fito daga sallar Asuba, sai dai kiji tsoron Allah ki tsarkake kanki, kada ki ci amanar wanda zaki aura da mahaliccinki, domin ko ana ya gobe zaki kammala Istibira'in kika yadda da wani namijin to kuwa duk kwanakin da kika yi sun zube a banza, kuma ba aure za kiyi ba illa zaman zina, duk kuma 'ya'yan da kika haifa zasu kasance shegu ne." Ta ce, "Shike nan nagode." Ta mike ta nufi cikin gida, daman da alwalarsa don haka ya dora goshinsa a kasa yana tasbihi da kabbara gami da godiya ga Allah da ya nuna masa wannan rana ta shiryuwar Zainabu, duk da ya lura kwana biyu ta dan daina fita yawon banzar nata, domin duk wani takunta yana hankalta da shi. Da ta shiga kai tsaye dakin Sala ta nufa, ta taddata zaune a tsakar daki tana lissafin kudin gyadar da Umar kaninta ya siyar, tana kirgawa tana gyangyadi saboda bacci ne a kanta, amman dan jarabar neman kudi ba zata kwanta ba, sai ta tafi luu tamkar zata fadi sai kuma ta farka a firgice ta cigaba da lissafin, da ta fara baccin zai kuma daukarta a haka ta tadda ta, ta zauna a kusa da ita ta tabata tana fadin, "Sala-sala."Ta farka a firgice tana fadin, "Ba fa bacci nake ba ina jinki mai tsada yaya aka yi ne? Yau ai kin faranta mini rai, zuciyata kal da naga kin shirya kin ficewarki, ina fatan kin samo kudi da dama don kinga kwana biyu ina fama da rashin kudi wallahi." Zainabu ta yamutsa fuska kana ta ce, "Kinga ni fa babu inda naje ina kofar gida Mustafa ne ma ya zo, kuma mun yanke shawarar za muyi aure, don haka daga gobe ma zan fara Istibira'i Insha Allahu." Ta yi watsi da kudin hannunta tana fadin, "Kan Ubancan! Lallai yarinyar nan kin bari Mustafan nan ya raina miki hankali da yawa, yanzu don zai aure ki sai kinyi wani Istibra'i? Wato bai yadda dake ba kenan? Yana zargin ke karuwa ce kenan. To tsaya na gaya miki sam ban amince ba, shegen yaro ya zo duk ya hargitsa miki lissafi kamar aljani, yanzu kamar ke namiji zai dinga juyawa tamkar waina? Duk kin sake hali kin susuce, wannan idan aka yi auren ma ai sai yanda yayi dake, don haka ban amince kiyi auran nan ba." Zainabu ta ji haushin abinda Sala ke fadi, ta yamutsa fuska gami da fadin, "Sala na lura baki kaunar nayi aure kin fi son nayi ta yawon gantali da karuwanci a titi, da zaki wani hakikance ba zan yi Istibira'i ba kuma ai kin san dai abinda nake aikatawa sarai, na yo zina na kawo miki kudi babu ruwanki da irin wahalar da nake sha, kije ki tambayi duk wacce ke sana'ar karuwanci dole take yi, dan kullum kana cikin fargaba ne na daukar mugayen cuwuka, ga hatsarin da muke shiga na mu'amala da kowa kada ka hadu da dan yankan kai, domin kawarmu Saliba har yau ba'a san inda take ba tun da wani Alhaji ya dauketa kwanan gida, ni kam na gaji wallahi aure na zanyi kome za kiyi sai dai kiyi amman aure babu fashi." Sala ta mike a hasale tana huci tana fadin, "Kan Ubancan, Abula ni kike gayawa wannan maganar akan wani dan iska can? To wallahi Abu zan yi maganinki a gidan nan, naga uban da zai daura miki auran in dai ina raye." Masifa take yi babu ji babu gani. Ita dai Zainabu bata kuma cewa komai ba ta shige dakinta ta kullo kofa, sai dai jarabar Sala ta cika mata kunnen tamkar zata koma gidan banda karadin maganarta cikin dare babu abinda ka ke ji. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 A haka Baba Abbakar ya iso gidan, tun daga zaure ya fara jiyo hargowarta da ihunta, a fili ya ce, "Yau kuma waye ya tabo 'yar bala'in nan? Amman ko waye ya jawo mana masifa domin dai da kyar yau zata kyalemu mu runtsa." (Tabdijan Allah kabamu mata nagari)Ya dade tsaye a soro yana fargabar shiga, domin da yana da inda zai kwana tabbas da komawa zai yi can ya kwana, haka nan ya daure yana addu'a ya shiga dakin. Kamar daman jiransa take yi ta ce, "Yauwa Abbakar daman kai nake jira, ka zo naji idan kaine ka daurewa Zainabu gindi a gidan nan har take shirin auran wanda nace mata bana kauna saboda asiri yayi mata ba son Allah yake mata ba." Maganar ta zo masa a ba zata don bai san abinda take nufi ba don haka ya ce, "Ni fa Salamatu ban fahimci abinda kike nufi ba sam." Ta kara gyara zama ta ce, "To ka sani ko baka sani ba bari na sanar da kai, Abula ce ta taso da zancan zata yi aure yanzu, ni kuwa sam wanda zata aura din bai kwanta mini a raina ba, dan haka gwara ma idan da hannunka a ciki ka zare dan banga dan kan uban da ya isa ya daura mata aure da shegen yaron nan mayaudari ba."Baba Abbakar yayi murmushi gami da fadin, "Salamatu kenan, ai kunfi kusa da Zainabu, amman dai ina ganin tunda Allah ya karkato da hankalinta tana son yin auren ni gwara ki rabu da ita ta yi, kinga ai mun huta da zagin da jama'a suke ma....." Ta mike a fusace tana buga hannu da dukan cinya tana fadin, "To sannu munafuki algungumi, bashi da aikin da ya wuce gulma, ina ruwana da wani zagun mutane? Su yi tayi, ai da zagi yana kari da yanzu jikina da na Abula babu ko masakar tsinke, to munsha tabara mun sha yasin, mun sha fate-faten alatsine, kurwarmu kur na gaya maka, . Maganar aure kuma babu ita wallahi baku isa ba.... Kai nama lura bakinku daya, ni kuma na isheku riga da wando....." Masifa take yi tamkar zata rufe shi da duka, Zainabu dake can dakinta bala'ain da masifar Sala ya ishe ta, kai duk wanda ke gidan ma bala'in ya ishe shi, shi dai Sadiku sai ya kunnan rediyo kawai dan haka daina jin hargowar, ita kuwa zainabu sai kaiwa da komowa take cikin dakin zuciyarta na kuna. Kamar wacce aka tunawa sai ta nufi jakarta da sauri ta dauko kwayarta ta sanya a bakinta kana ta nufi kofarta ta kulle gam ta kulle wunduna sannan ta dauko tabar shaidan ta kunnata da ashanar bature (lighter) ta zauna gefen gadonta tana zuka tama lumshe ido, dakin ya gume da hayaki tamkar tasowar hadari, dan duk mutumin da ya shiga dakin muddin bai taba shan kwaya ko tabar shaidan din ba sai yaji kansa ya juye, amman ita babu ruwanta tin da dai 'yar caburos ce, sai da ta cake sosai kanta ya dauki caji sannan ta yarda tabar a gefe bayan ta kashe ta kwanta rigingine a gado, kwakwalwarta na shirya mata abubuwa na karya, yawanci kuma da Mustafa ne. Da safe ma da bala'in suka karya kumallo, shi dai Abbakar daga gurin sallar asuba bai dawo gidan ba ya wuce gurin buga-bugarsa, shima Sadiku shiryawa yayi ya fice sai dai ya turawa Zainabu sako a wayarta. Zainabu kam da kyar ta iya tashi saboda nauyi da jikinta yayi mata, kai tsaye wanka ta shiga dan ta danji dadi, yau ko abin karin da aka saba kawo mata ba'a kawo ba, dan haka ta kirawo wani kaninta ya amso mata shayi da wainar kwai gurin mai shayi, don yunwa take ji tamkar zata ci babu, domin dai duk mutumin da ke shaye-shaye yana da saurin jin yunwa saboda fafare masa cike da take yi gaba daya. Tana kunna wayarta ta ci karo da sakon yayanta Sadiku dan haka ta shirya ta fita, dan yace su hadu a gidan Malam. Tana kokarin kulle kofarta ne Sala ta iso tana tambayar ina za ta, ta yi murmushi da rashin damuwa ta ce, "Sala tun da kike kin taba tambaya ta inda zani? Bayan kin san yawon iskanci nake tafiya amman yanzu dan nace zanyi aure duk kin gigice har kina tambaya ta ina zani." "Au zagina za kiyi kenan ko Zainabu?." Ita dai bata kuma cewa komai ba ta nufi kofar fita. Sala ta yi kwafa gami da fadin, "Zan yi maganinku a gidan nan zanga wanda ya daure miki gindi." A zaune ta tadda Malam din da Sadiku, har ta manta rabon da ta shiga gidan, domin dai a cewar Sala ba kaunar su suke ba balle Malam da take ce masa dan saka ido, dan haka ko ta kofar gidan bata wucewa dan idan ta wuce dole ta gaida shi saboda ta san shi babu wargi, abinda ta tsana a rayuwarta ta gaida wani dan haka bata bin kofar gidan da kafarta sai dai a mota.Ta sami gefen tabarma ta zauna kanta yana kasa kamar mutuniyar arziki ta gaida Malam din. Ya amsa fuskarsa cike da farin ciki sannan ya cigaba da magana, "Zainabu na yi farin ciki da na ji zaki yi aure daga bakin yayan ki, wannan ba karamin abin alhairi ba ne, amman na ji yanda kuka yi da Mahaifiyarki, sai dai ku yi hakuri da halinta, domin shi hannunka ba ya rubewa ka yanke ka yadda, tuntuni ina bakin ciki da halin da kike ciki, Allah ya sani na yi duk iyakacin iyawata ta ganin na tsamoki daga halaka amman abin ya faskara, na hakura daga karshe don na san Mutum bai isa ya shirya dan uwansa mutum ba in dai Allah bai nufa ba, na dai cigaba da yi muku addu'a dan na dauke ku tamkar jinina, sai dai babbar matsala tana ga Mahaifinku Abbakar duk lalacewa daga gurinsa ne, duk wa'azi da nasiha na yi masa amman a banza, dan haka yanzu ina farin ciki da wannan aure da za ki yi, ina addu'ar Allah ya sanya ya zama hanyar shiryuwarki." "Yanzu Malam yaya za'a yi? Kana ganin mu daina sanar da ita komai a yi a nan gidan ka ko yaya?" Sadiku ya tambaya Malam din. Malam ya gyara zama kana ya ce, "A'a babu wata fa'ida a boye mata din dole za'a dinga sanar da ita tayi mitarta ta gama, tun da idan ta ji ma daga baya ma fadan za tayi ko tace an rufe ta, amman kada ku sake ku sanya Abbakar cikin wannan sha'ani don na san babu wani abu da zai iya tabukawa." Ya maida dubansa ga Zainabu wacce har lokacin kanta yana kasa ya cigaba da magana, "Ke kuma ki sani yanzu ba irin da ba ne dole ne ki kame kanki idan har kina son ki yi tsarkakakken aure, ki kyautata zuciyarki domin sai ta gyaru sannan dukkanin ayyukanki zasu zama gyararru da jikinki kamar yanda Ma'aikin Allah ya fada." Muryarta da sanyi ta ce, "To Malam na gode." Ta mike kamar mutuniyar arziki ta bar Malam da Sadiku suna hirarsu domin dai mutuminsa ne. Sanda ta isa gidan ta tadda Sala ta cika tayi fam kamar zata fashe, amman don wai taci asirin da ta amso na mantawa da Mustafa gurin Malami ya sanya ta dan saki ranta ta ce, "Ga abincinki nan na rana, ina shirin miko miki na safe kika fita." Bata ce komai ba ta amsa ta shige dakinta. Ta bude abincin, shinkafa da miya ce har da Salak da nama, sai dai ga maganin nan kore-kore cikin miyar, Zainabu ta yi dariya tana fadin, "Sala tawa uwa ta ta kaina, bata san son Mustafa a jinina yake ba ko da naci magani ba zai rabu da ni ba." Kawai sai ta dauko cokali ta kama cin abincinta bayan ta yi Bismillah, don tayi imanin babu abinda asirin Sala zai yi mata in dai akan Mustafanta ne. (Daman dai 'Yan magana sun ce tsafi gaskiyar mai shi, kuma sai ka yadda da canfi yake maka ka). Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 ******************* Da yamma tana daki a kwance tana karanta littafin Fauziyya na kaddara ko son zuciya, duk jikinta yayi sanyi da halin da taga yarinyar ta shiga sai take tunanin kada itama Mustafa yayi mata haka, kan ubancan lallai da ta koya masa hankali, domin dai idan ita 'yar iska ce shima shi ne, littafin ne ya dauke mata hankali daga mitar Sala har tayi ta gama, kiran da wayar ta ke mata ne ya sanya ta mike zaune da sauri dan ta shaida kiran Mustafa ne. Ta dubi kanta jikin madubi, ta yi kyau matuka amman kuma idan ya ganta a haka tasan ba zai ji dadi ba, tunda dai yace ta daina fita da irin wannan shigar, don haka ta dauko wani gyale mai dan girma da take yin sallah da shi ta yafa ta fice, ta yi sa'a kuwa babu kowa a tsakar gida, Sala tana daki tana ta faman gyangyadi saboda rashin bacci da take fama da shi, don asubanci take yi gurin tashi, haka nan sai takai karfe goma sha biyu ba ta kwanta ba saboda shegen neman kudi, sai dai tayi ta gyangyadi har da dingurawa wani lokaci. A kofar gida suka ci karo da Mustafa, abin ya girmameta ya bata mamaki, domin dai basu taba yin zance a waje ba sai a cikin mota ko da yaushe, ko ma su bar kofar gidan idan suka ga da 'yan saka ido su yi tafiyarsu inda zasu wataya, har kwana suke yi wani lokaci, wani lokacin kuma sai dare zai dawo da ita, nan din ma da kyar suke rabuwa. Idonsa kyar a kanta har ta iso inda yake, zuciyarsa ta hau azal-zalarsa, amman sai ya dake ya kauda kanshi gefe. Ta iso cikin yanayin tafiyarta ta jan hankali ta tankwashe muryarta mai dukan kunnansa har zuciyarsa ta ce, "Musty Zuma barka da zuwa." Ya dago kansa yana dubanta yayi murmushi ya ce, "Zainabu yaya kike? Kin ganni yau da yamma ko? Gani na yi gwara na kawo miki da wuri alkawarin namu ga shi." Ya mika mata. Ta sanya hannu ta amsa yana mata bayanin hijaban ne da yace zai kawo mata. Ya dubi agogonsa ya ce, "Zainabu bari na wuce ko?" Ta dubeshi da wani yanayi kamar za tayi kuka domin ganinsa ya sanya ta ji wani dadi da nishadi a rayuwarta, amman ya ce mata zai tafi, amman sai ta dake kawai ta ce, "Shi kenan ka gaida gida." Ya dubeta kamar zai yi magana amman ya fasa kawai ya juya ya nufi motarsa. Ta yi tsaye sororo tana dubansa har ya shige motarsa, sai da ya dubeta sannan ya figi motar ya bar unguwar da gudun shi, jikinta babu kwari ta koma gida, ji take yi kamar ta bishi ta makale shi, tana son Mustafa tamkar zata lashe shi take ji. Washegari da safe tayi shirin zuwa aiki ta kammala kwalliyarta tsaf kamar yanda ta saba, sai kuma ta dauko hijab dinta guda daya ta sanya, ya kawo mata har gurin gwiwarta sai tayi kyau tsaf da ita, ta kalli kanta a madubi tayi murmushi, lallai ta yadda shigar mutunci ke fito da darajar mace, don sai take jinta daban. A tsakar gida taci karo da Sala tana gyaran wake da zata dafa, tayi sororo tana kallonta kamar wacce taga sabuwar halitta, can kuma sai ta hau salati tana tafa hannu, "La'ilaha illallahu, Abula me zan gani haka kuma? Haka ya maida ke? Lallai na yadda yaron nan shaidani ne, wato baiwar da Allah yayi miki ta kyau ma ya hanaki nunawa duniya su gani bayan ba ubansa ne ya kera ki ba, lallai Abula abin naki yayi nisa sai dai addu'a." Ita dai bata ce komai ba ta nufi hanyar fita, sai da ta kai kofa sannan ta tsaya ta juyo ta dubeta wacce har lokacin bakin ta bude ta ce, "Na tafi Sala sai na dawo."Ta yi kwafa gami da mai da kanta ta cigaba da gyaran wakenta, yau ba a yi mata kirarin da ake mata ba, Zainabu Abu mai tagwayen suna, kowa ya ja dake ya sha kunya, mahassada ku rufe idonku yarinya mai tsada ta danno, yarinya wacce bata da kirar Allah ya isa. Zainabu ta fice tana murmushi a ranta tana fadin, "Wato yanzu an daina yi mini kirarin ma balle a dawo lafiya, Sala kenan." Ta tare mai adaidaita sahu ta hau, Mustafa da ke can gefen layin cikin motarsa ya daga bakin glass cikin motarsa yana hangota, ransa ya yi sanyi don ganin ta bi umurninsa, a hankali ya dinga bin bayan mai adaidaita sahun har ta isa (local government) karamar hukumar da take aiki. Tun daga bakin kofa aka fara kallonta, maigadi ne ya saki baki cike da tsegumi yana fadin, "Allah buwayi, yau kuma Zainabu Hijab aka sanya, lallai duniya ta fara biyar da ita dubi kamar ba ita ba." Da ta shiga cikin sakatariyar kuwa kallonta aka yi ta yi, ita kam ko a jikinta wai an mintsini kakkausa, kanta tsaye ta isa ofis dinta, gashi daman ita ba kowa take kulawa ba a cikin sakateriyar, a cewarta wai duk kazamai ne basa wanka, dan haka nema da yawa ke shan kashi gurin ganin sun sami ko da dariyarta ne. Oganta yana bisa kujera yana ta rubuta bococi na kudi ta shiga da sallama, ya daga kai yana dubanta baki bude ya ce, "A'a Malama Zainabu sai yau ake ganinki a ofis....." Ya so ya cigaba da magana akan hijab din da ta sanya amman ganin ta hade rai ya sanya ya tsuke bakin sa don ya san hali, yanzu sai tayi masa wankin babban bargo. Ta jawo kujera ta zanua tana fadin, "Wash, yallabai kenan, yaya aiki kasan sakateriyar ce shigowarta sai a hankali wallahi, idan da wani aiki kawo a tayaka." Ya yi dariya ya ce, "Wane ni, ai ban isa ba na saka manya aiki, sai dai wallahi rashin zuwanki kwana biyu ya yiwa yallabai DPM karan tsaye gashi yana ta neman lambar ki bai samu ba, haka ma HOD na works suke ta sintiri, ke harda mai gayya mai jama'a Chairam yana ta aike, har sallahu ya bar mini na lambar wayar da zaki neme shi, yace kuma yana daula hotel dan gidanshi na shakatawa an dameshi baya sakewa sosai.....""Haba Oga tunda na shigo ka tsinke da surutu sai kace baure." Ta katse masa magana, ta dora da cewar, "Kowanne shege ya kuma zuwa nemana wallahi sai nayi masa rashin mutunci, sai kace wata karuwa, idan iskanci za suyi ai ga gidajen karuwai can a sabon gari, banzaye masu shegen son matan tsiya, kai! Aiki a sakateriya ko bala'i, kowanne banza kucaki dame warin baki da me warin hammata ya ce wai zai nemeka, mts!" Ta ja tsaki, "Wallahi zan yi maganin kowanne shege." Oga Bala yayi dariya yana rubutunsa ya ce, "Ho! Zainabu ai ke din wallahi duk wanda ya ganki sai miyansa ya tsinke, ni kaina dan dai anki kulani ne amman ba karamin sonki nake yi ba tuntuni, to sai dai nasan ban isa ba, amman duk randa kika shigo aiki ji nake yi kamar ki zama tawa ni kadai, don daga shigarki har kamshin turaranki mannewa suke a zuciyata, idan naje gida sai na raina matana, kin san matsalar matanmu na hausawa kadan ne ke gyara kansu irin yanda kike yi, shi ya sanya kowa ya lashi zumarki sai ya dawo, wallahi DPM tamkar zai zautu dan rashinki, shi ko damuwa da zuwanki aiki bai yi, shi dai burinsa ki zo ki cire masa gibin da kika bar masa a zuciyarsa, amman da kina irin wannan shigar ai kinga babu wanda hankalinsa zai tashi, ki dubeki kamar wata matar liman yau, nasan kalilan din maza ne zasu yi sha'awar ki sai jarababbu irinmu." Ta galla masa harara tamkar zata rufe shi da duka, Oga Bala takadirin dan iska ne, shine akawu na (local government) karamar hukumar, tunda ta zo aka turota ofis dinsa ba wai dan cancanta ba sai don tana da hanya, don kyan karatunta koyarwa, amman da yake Nijeriya ce idan kana da kafa sai a kai ka inda baka dace ba ko da zaka kashe jama'a kuwa, kamar a asibiti da ake daukar wadanda basu yi karatun ba sam-sam ga kuma wadanda suka yi karatun saboda basu da hanya. Tun da tazo ofis din oga Bala ya kyalla idonsa ya ganta ya fara mika kokon bararsa, domin dai idonsa idon mata ne, gashi su babu ruwansu ko da matar aure ce in dai zata yadda da su (Wa iyazu billah) musamman masu neman aiki ko a yi musu (promotion) karin girma sai kaga suna amfani da wannan damar suna lalata watsatstsun mata, sai masu tsoron Allah daga cikinsu kiyi komai yanda ya dace da dokar aiki. Ita kuwa Zainabu idan namiji bai yi mata ba duk kudinsa bai isa ya kusance ta ba, balle oga Bala da ta raina masa ajawali, bakinsa kullum da tikar goro ko taba yana sha, hakoransa duk sun dafe gashi kullum kamar an kwatoshi daga bakin kura, irin katon kauyen nan ne mara fasali, don ma su Baba sun taimakeni an sakani a makaranta da yanzu muna gona, haka yake cewa da kanshi idan suka hadu da abokansa shakiyyai, don haka ya buga ya buga amman babu fuska ga Zainabu, gashi ya lura bata da tsoro ko shakka ko daya, ko DPM bata tsoro, dan haka ya gama barazabar shi da girman kujerarsa ya dawo ta lallashi da kashe mata kudi amman a banza, ko kallon tsiya bai isheta ba balle na arziki. Duk da hararar da take wurga masa baiyi shiru ba dan haka ta doka masa tsawa "Kai! Oga Bala wallahi ka yi asara kazo gurin aiki kana tonawa matanka asiri, ina ma ace ina daya daga cikin matanka wallahi da sai ka gane kurenka." Yayi wata shashashar dariya har da dukan tebur yana fadin, "Ho! Zainabu, ai irinku daban ne cikin mata, na sami kamarki ai sai ma nayi da gaske zan fito, ki dubi yallabai fa (chairman) irin matan da yake mu'amala da su, amman a kanki duk ya susuce, rannan da ya sanya aka kira ni kamar yayi mini kuka wallahi." Ta kuma kulewa da Oga Bala irin shakiyyan mutanen nan ne marasa mutunci da kamun kai ga almundahana, duk wata cuwa- cuwa da ake yi a karamar hukuma shine sila dan shedani ne, ya iya rubuta bocha ta bogi har akwai ta 'yan kwadin sakateriya da ta kadangaru da karnukan dake gadi. Dan haka ta mike a kule ta dauki jakarta tana fadin, "Kai dai wallahi dan iska ne, gwara na bar ofis din, da man zagayowa nayi gwara na tafi tun bata kaini da cuccusa maka zagi ba." Maimakon yaji haushi sai ma ya kuma fashewa da dariya yana fadin, "Dan Allah kiyi hakuri wallahi har na tura a sanar da yallabai DPM kin shigo kada ya zaci karya nake yi....." Sallamar DPM din ce ta katse shi, ya kumshe baki yana dariya, DPM ya kalli Zainabu da wani duba tamkar ya cinyeta ya ce, "Zainabu idon ki kenan ko, to ki taddani a ofis."Ya juya ya fita yana kannewa oga Bala ido, oga Bala ya fashe da dariya yana fadin, "Yallabai kenan, da girman kujerarka." Ta kuma gallawa Oga Bala harara tana fadin, "Wallahi oga ka shiga uku, Allah ya shiyeka, ka kuma sani abinda kake zaton zaka samu ba zaka samu din ba, domin na rantse da girman Allah ba zai samu abinda yake so din ba, ko da maye ne kuwa shi,ya toshe baki a tsorace kamar zai zubo da gudawa a wando ya mike tsaye yana fadin, "Don girman Allah ki yi hakuri Zainabu ki rufa mini asiri har na sanya ran zan samu 'yan canji da alfarma....." Bata kuma cewa komai ba ta kada kanta ta bar masa Ofis din da yanayin ta na jan hankali. Ya dafe kai gami da komawa jagwab ya zauna yana fadin, "Kai wannan yarinya anyi shaidaniya, yanda take yawo da hankalin maza kamar wata ibilishiya, gata da shegen shiga rai, balle a ce mutun ya dandani zumarta ya shiga uku Inji DPM." Sai kuma ya fashe da muguwar dariyarsa da ya tuno yanda DPM ya mutu akan son Zainabu har ya kan ce masa, Bala ka san Allah tunda nake ban taba gamsuwa da mace irin Zainabu ba, wallahi tana da wani irin maganadisu a jikinta dake jan mutum gunta. Ta shiga ofis din babu ko sallama, ya mike jikinsa yana rawa zai tarota ta dakatar da shi tana fadin, "Ka ga yallabai kada ka taba ni don Istibira'i nake yi aure zan yi ma, yanzu kuma Allah ya shirya ni." Ya ware idanuwa waje cike da fargaba yana fadin, "Ki yiwa Allah Zainabu ka da kiyi mini haka, ki amince ki aure ni, ni na yadda komai kike so zan miki, idan kuma ba zaki aure ni ba to mu cigaba da mu'amalarmu a boye, tunda dai ai kinsan shi mijin da zaki aura ba waliyyi bane da zai hakura da ke kadai ba." "Yallabai ka tsaya na sanar da kai, zan yi aure da kyakykyawar zuciya, ka dubeni da kyau zaka san na bambanta da Zainabun da ka sani can baya, dan haka ina baka hakuri sai an jima....." Ta juya ta nufi kofar fita. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Da sauri ya sha gabanta yana fadin, "Haba Zainabu, kada mu yi haka da ke, kin san dai aikin nan naki ba zuwa kike yi ba, dan haka idan kika ki amincewa da ni zan sanya a baki (quarry) ko ma na sanya a kore ki, kin san dai babu sama da ni a Local government din nan, ko chairaman karya yake, tunda dai shi dan siyasa ne zai iya tafiya ya barni da ke." Ta ja tsaki cike da nuna rashin damuwa ta ce, "Yallabai kenan, ko ka barni ko kada ka barni wannan matsalarka ce, domin dai kasan neman aiki ba abu ne mai wahala a gurina ba, sai anjima." Ta kada kai ta fice. Ya bita da sauri yana kira "Zainabu! Zainabu!" Amman ko waige bata yi ba ta fice daga ofis din, ya dawo ranshi a tsananin bace ya dafe goshi, lallai yarinyar nan muguwar 'yar rainin hankali ce wallahi, yanda yake jinta kamar ya zace ta, amman babu komai zai bita har gida, dole ne ya san yanda zai yi ya ruguza maganar auren ta. Tana kokarin fita daga sakateriyar motar chairaman ta ci birki a gefenta yana kokarin shiga, ya leko ta windo babu kunyar direban dake jansa, balle jama'ar da ke tare da shi (ko da yake ai sun san hali). "Zainabu kace nake gani ko idona ne ke mini gizo." Ta kuma hade rai tamkar zata fasa kuka, ya langabar da kai yana magana, "Kai Zainabu alkawari wallahi baice haka ba, fafur kin gujeni, gashi babu damar naje kofar gidanku saboda 'yan saka ido, na yi waya kin ki dagawa, Don Allah ki koma zanyi magana da ke.ta kalli agogo dake hannunta ta ce, "Mai girma ka yi hakuri, wallahi yanzu akwai inda zani, amman ai oga Bala ya bani address din inda zan same ka, zan zo kada ka damu." (Ta yi masa haka ne domin ya kyale ta). "Kada fa ki jirgani Zainabu don nasan halinki, sau nawa na aika da mota gidanku kika ki zuwa?" Ta rangwadar da kai cike da yaudara ta ce, "Haba Yallabai nifa nayi maka alkawari, "Za ki zo yau na jira ki?" Ta ce, "Amman dai sai dare zan zo, domin yanzu unguwa zani." Ya ce, "Shike nan zan jiraki, bani lambar wayarki." Ta gaya masa lambar bogi, ya saka a wayarsa, sannan ya baiwa direban umurnin su wuce yana fadin, "Ina jiranki Zainabu." Ta ce masa "To." Kawai ta wuce da sauri, domin dai tana zancen zuci, "Wai me wadannan mutane suke maida ta ne? Sai kace wata tsinanniya kowa Zainabu kowa Zainabu?, to zata gwada musu ba karya ba ce ita, banzaye duk babu wata soyayya da suka iya ko su gyara matansu, sai dai su fito suna kashewa kadangarun bariki kudi, amman idan kaje kaga matansu sai ka zubda yawu, da anyi magana su ce matansu kazamai ne, to ita mace ai dole sai an bata zata gyara kanta." Ta ja tsaki dai-dai sanda take tsaida wani mai a daidai ta sahu. Mustafa da yayi parking tun dazu yana jiran fitowarta ya bi bayansu dan ganin inda zata kuma, sanda ya ga ta shiga gida sai yaji ransa ya yi sanyi, lallai ya yadda Zainabu da gaske take zata kare kanta zata yi tsarkakakken aure, ya aminta ta gyara zuciyarta. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 ***************** Rayuwa mai sauyi, lallai Ma'aikin Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya yi gaskiya, da yace idan zuciya ta gyaru dukkan jiki ya gyaru, idan kuma ta baci dukkan jiki ya baci, to haka ce ta faru ga Zainabu. Domin dai gyaruwar zuciyarta sai ta gyara dukkanin al'amuranta, domin dai yanzu Zainabu ta daina fita ko ina in dai ba da dalili ba, gurin aiki ma tun ranar da abin ya faru bata kara zuwa ba, da wata ya kare ma aka turo masinjan ofishinsu ya kawo mata albashi ta yi mamaki matuka, domin tayi zaton zasu koreta ne, amman har lokacin maza basu daina sintiri a kofar gidansu ba, domin dai a sati na biyu da fara istibira'in nata Mustafa ya amshi wayarta har layin (sim card) ya bata sabuwa da sabon layi, don haka ba kowa ne ya san layin da ta sake ba, don haka duk wanda ya kira tsohon layinta sai ace masa a kulle take dan haka wasu suka hakura, wasu kuma basu gaji ba suka cigaba da zuwa kofar gidan su suna naci. Sala kam tamkar ta shake Zainabu don takaici, amman ita ko a jikinta, domin dai ta saba da mitar Sala, idan ta ji Mustafa ya zo tayi ta surfa zagi, wani lokacin yana jiyota amman sai ya ke nuna kamar bai san tana yi ba, domin dai bai taba yiwa Zainabu zancen ba. Ita kam Sala tayi fadan a banza, domin dai Zainabu ba ta ce mata ko uffan, domin daman duk iyakacin rashin kunyarta bata yiwa Sala da Babanta, domin a duniya tana ganin darajar iyayenta, kuma ko waye kai ka taba mata su zaka gane kuren ka. Da Sala taga fada ba ci bane sai ta koma ta asiri, shima dai a banza domin dai duk 'yankudaden ta sun kare, daman Zainabu ce mai bata kudi na banza, Sadiku kam sai dai ya jibge mata kayan abinci komai da komai,Idan ta ce ya bata kudi sai ya ce mai take bukata ya siyo mata? Sai ta hau mita da dole sai ya ji abinda za tayi da kudin, idan yaji haka sai ya ajiye mata kadan ya wuce. Karimatu kuwa ta bi mijinta can Aba domin can aka yi masa canjin aiki (transfer). Shi kam Mustafa ya yarda da Zainabu dari bisa dari, domin duk wata hanya da ya san zai kamata da laifi yabi amman bai sameta da laifin komai ba, yana kuma sane da mutanen da ke zuwa gurinta bata fita sai dai Sala ta fito tana basu hakuri, har takan ce asiri aka yiwa diyar ta su taya ta da addu'a. (Ku ji fa irin wannan azzalumar uwa wacce bata tsoron haduwarta da Allah). Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 ************ Cikin hukuncin Allah ta kammala Istibira'inta ta tsarkaka daga fushin Allah da kazantar zina, ranar jinta take yi kamar wacce aka yiwa albishir din gidan aljanna, tun da ranan Mustafa yayo mata waya, irin kalaman da ya gaya mata su suka sanyaya mata rai domin dai har ta fara zargin anya kuwa Mustafan ta bai sake ba?, domin dai duk wadannan kalaman na soyayya da kallon da yake mata yanzu duk ya daina, da ya zo ya bata abinda zai bata sai yayi mata sallama ya wucewarsa kamar bai wani damu da ita ba, gashi sai yayi sati bai zo ba sai dai yayi mata waya ya tambayi lafiyarta ya kashe. Tunda suka gama waya take murna ta fada kicin da sauri tana kokarin shirya masa abinda zai ci don yace mata a nan zai yi dinner (abincin dare) yau, ta kirawo kaninta Ila ta rubuta masa duk abinda take bukata ya siyo mata. Sala kallonta kawai take yi cike da mamaki amman bata ce komai ba, da ta kammala girkin ta yi wanka ta shirya kanta cikin wani riga da siket na leshi wanda ya amshi jikinta, ta gyara gashinta ya sha mai tai parking dinsa, duk da ba wani tsaho ne da shi ba, tayi wata kwalliya ta daukar hankali. Rabon Zainabu da irin wannan kwalliyar tun ranar da ta fara zaman Istibira'i, Sala ta fara washe baki cike da murna domin tayi zaton ko asirinta ne ya kama Zainabu, domin ta baiwa kawarta Asma wani magani ta ce ta zuba mata cikin nono don idan itace ta bata ba zata sha ba, Asma din tayi dariya kawai ta karba, sai da suka hadu da Zainabu take gaya mata suka yi dariya kawai suka watsar da maganin. Karfe shida saura wayarta ta fara kira, ko bata gani ba ta san Mustafa ne don haka ta mike ta kara fesa turaruka a jikinta ta yafa dan yalolon gyalanta ta nufi kofar gida, daman ta karbi makullin dakin Sadiku don haka can ta bude musu tace da Ila ya shigo da shi. Sai da ya shiga ya zauna a dakin sannan ta shiga, babu laifi dakin gado ne karami sai loka mai cike da littafai da kayan kallo bisa (TV stand) abin dora tibi, sai kujera guda daya mai taushi, an malale dakin da kafet, sai wani irin hanga da kayansa a sakale kanana. Ta shiga dakin da sallama idonta yana kasa, Mustafa ya zuba mata ido tamkar zai lasheta, rabonsa da yayi mata irin wannan kallon har ya manta, ya lumshe ido saboda kanshin turaren ta dake dukan hancinsa. Ta zauna bisa kafet ta tankwashe kafafunta, ta dube shi da yanayin salonta na jan hankali muryarta mai taushi ta ratsa dodon kunnensa, "Mustafa honey ya gida?"ya yi murmushi ya ce, "Zainabu irin wannan kwalliya da kika yi ai sai ki maida mu ruwa, lallai dole na bude wuta a yi bikin nan nan da sati daya." Ta kalleshi tana wani kashe ido ta ce, "Haba dai, kamar bikin wata 'yar tsana? Ka dai bari ayi ko wata hudu ne ma ko biyar....." "What, me? Wallahi ba zan iya wata guda ba tare da na mallake ki ba, Zainabu kin san yanda nake jinki a raina kuwa?, Zainabu kina wasa da irin son da nake miki, ban san yaya rayuwata zata kasance ba." Ta rangwadar da kai tana dariya mai dauke hankali, ya taso tsam ya matso kusa da ita ya kwantar da kai kamar wani maraya. Ya kwantar da murya ya ce, "Zainabu kamshinki yana da dadi ko na dan shaka ne....." Ta mike tsaye tana dariya ta koma can nesa da shi ta ce, "Haba nawan, kada muyi tuban muzuru mana, kasan ance sharuddan tuba da nadama da kuma daina aikata aikin sabon." Ya koma ya jingina da kujerar yana dariya ya ce, "Ho! Zainabu wayo, daman gwada ki nake yi, ni yaushe zan yadda na kuma shan azabar da na sha na rashinki?" Kiran sallah ne ya katse musu hirar tasu, ya mike ya ce bari ya je masallaci ya dawo, ta ce shi kenan sai ya dawo, ta shiga itama zata gabatar da tata Sallar. Duk da bata da wani wadataccen ilimi na addini tana da kokarin yin sallah a kan lokaci. Tana shiga Sala ta rike haba tana dubanta ta ce, "Oh ni Abula kin hada kanki da wahala, yanzu kina nufin duk uwar kwalliyar nan domin yaron nan Mustafa kika yi? Da nayi zaton kin gano gaskiya ne, ke ba kya ganin yanda kawarki Asma'u take fantamawa, ina jin jiya kuna hirar tana kasar waje da saurayinta." Zainabu ta kulu iyakacin kuluwa, yau kam ta gaza jure maganganun Sala, ta dubi Sala da takaici a fuskarta ta ce, "Haba Sala, wai kin fi so nayi ta karuwanci ina kawo miki kudi Allah yana tsine mini da jama'ar gari? Yanzu ba zai zama abin alfahari a gurinki ace nayi aure ba, duk fa abinda mutane suke fada akan mu gaskiya ne, ba kya tsoron fushin Allah akan mu balle cutukan zamani da azabar da ake sha gurin karuwanci, ki gaya mini karuwar da kika taba ganin ta ci riba a rayuwarta, karshen su dai tallan taba ko hauka ko bara, ko kuma mutuwar wulakanci a tsakiyar titi, don haka na tsarkake zuciya ta zanyi aure da kyakykyawar niyya, idan zaki sanyawa aurena albarka shi kenan idan kuma ba zaki sanya ba Allah yana gani." Sala ta hau salati tana tafa hannu, "La'ilaha illallahu, yau ni kike zagi a gidan nan Abula? To tsaya na gaya miki har abada ban son auranki da Mustafa, idan auran za kiyi ga masu kudi shahararru da ke sonki har da gwabnoni amman ki tsaya ga wannan karamin alhaki, wallahi kinji kunya." Ita dai Zainabu bandaki ta shige ta bar Sala tana mitarta. Kiran da wayarta tayi mata ne ya sanya ta mike domin ta san Mustafa ya dawo kenan, ta dauki abincin da ta shirya masa ta nufi shagon Sadiku. Tana shiga ya mike ya tarota ya amshi tiren abincin yana tsokanar ta "A'a 'yan mata ban yarda da daukar irin wannan kayan ba, ai sai kirjinki ya bude."Ta yi dariya tana masa wani duba ta ce, "Kai honey wallahi kana shagwaba ni." Ta jawo tiren ta zuba masa abinci a faranti ta mika masa. Ya kanne mata ido yana kallon abincin ya ce, "Lallai ashe amaryar tawa ta iya girki, ina sane nace a shirya mini abinci, taso to mu ci." "Ka yi hakuri wata rana za mu ci kaji honey." Ya manne kafada kamar wani yaro yana fadin, "Na ki wayon, in ko ba zaki ci ba nima ba zan ci ba, kin manta da da kike bani a baki ma." Ta ce, "Shi kenan bari na taso." Ta zauna daga gefensa suna ci suna hirarsu mai tsarki, sai da zai tafi ya sanar da ita jibi mutanen gidan su za su zo neman aure. Ta ce shike nan zata sanarwa da Yayanta Sadiku domin dai a gidan Malam za'a kai komai, da kyar suka rabu kamar kada su rabu. KARSHEN TIKA-TIKA-TIK. Ranar Juma'a da daddare kanin mahaifin Mustafa da wansa da abokinsa suka kawo kudin zance har da sadakinsu gidan Malam, Sadiku da Malam da wani dan uwan Malam din ne suka karbe su, aka gaisa a mutunce da daraja juna. Sun yanke sati hudu ne bikin daidai da na Sadiku, su kam iyayen Mustafa sati biyu suka soo, domin haka angon ya ce musu, amman jin so ake a hada guda biyu ya sanya suka hakura, suka yi sallama a mutunce da ganin darajar juna. Bayan sun tafi Malam ya kuma kirga kudin kamar yanda suka kawo, dubu Hamsin na sadaki, dubu hamsin na kayan sanya rana, sai dubu Ashirin na gaisuwar uwa da uba. Da fari Malam ya ce yayi yawa, suka ce yayi hakuri ya karba, domin da kudin jimlarsu dubu dari biyu ne Mustafa ya bada suka rage ya koma haka, domin auren da ba'a tsawwala ba yafi daraja. Sun rabu akan a bar kudin gurin Malamin duk da ya so Sadiku ya tafi da su yace a'a ya rike a gurinsa. Sai dai wajen karfe goma da rabi Baba Abbakar ya dira a gidan Malam akan ya zo ya karbi kudin nan sun yanke shawarar da su za'a cika a yi mata kayan daki. Malam yayi jim kamar ba zai ce komai ba, can dai ya shiga gida ya fito da dubu saba'in ya baiwa Baba Abbakar yana fadin, "Wannan zan iya baka, amman sadakin Zainabu a hannunta zan bata domin hakkinta ne, duk ranar da aka daura mata aure." Baba Abbakar yace, "Shike nan Malam babu komai." Ya amshi saba'in din ya sanya a aljihunsa, suka yi sallama ya nufi gida. Sai da ya yiwa kudin kyakykyawan boyo sannan ya shiga cikin gidan yana muzurai, da yake Sala a kule take domin har gidan Malam ya zo yayi mata bayanin duk abinda ya faru, tsananin kwarjininsa ya sanya ta kasa cewa komai sai da ya tafi tayi ta mita tana cewa, daman tasan bakin ciki ake yi diyarta ta sami gidan hutu, shi ya sanya aka yi mata asiri ta auri wannan da ba wani bane, don haka koda ya shigo ko kallon tsiya bai isheta ba balle na arziki, dan haka ya wuce ya kwanta yana kuma makale da kudinsa. Washegari da sassafe ya ficewarsa ya baiwa Sala naira dari biyar yace a siyawa yara koko,ta karba tana mamaki, ta kasa jurewa ta ce, "Lallai yau anyi abin kai, ina jin dai Abbakar tsintuwa kayi, rabon da ka bada kudin abincin 'ya'yanka ai kusan shekara ashirin da biyar kenan, lallai zan dorar yau." Yayi murmushi kawai ya fice, domin dai baya son ta ja su da nisa don kada ta dagoshi, ya ce zai kashe kudin domin dai ai diyarsa ce, komai ta fanjama-fanjam, domin dai a doke dai ba zai doku ba. Can gurin mai shayi ya nufa ya sanya aka hada masa shayi da wainar kwai da biredi da bota na dari biyar, ya gyara zama ya kwashi gara yayi gyatsarsa ya koma majalisarsu, ranar wuni suka yi yana sai musu gyada da ruwa zuwa tsire da balangu, duk wanda ke wucewa ta gabansu su kansu ranar sun san Baba Abbakar yayi samu, da rana ta yi kuma otal (hotel) ya tafi ya ci abinci har da kazarsa. Sati uku cif suka wuce, shirye-shiryen biki ya kankama domin dai gidan su Mustafa sun kawo kayansu na lefe, duk da sai da aka yi bacin rai domin dai Hajiya Kubra tace babu wani daga danginta da zai sanya hannunsa cikin wannan bikin, dan haka ba zasu je kai kayan lefen ba. Ran Alhaji Abdullahi ya baci amman sai ya danne zuciyarsa ya dinga lallashinta, da yake bata iya ketare maganar mijinta sai ta hakura ta sanarwa da kanwarta Hajiya Saratu da kuma Yayarta, tun gurin duban kayan Hajiya Saratu ta fara korafi kayan sun yi yawa, yarinyar da aka ce 'yar talla ce za'a kaiwa wannan dukiya? Ai dole a rage, Hajiya Kubra ta ce, "Hakane kin kawo shawara gaskiya." Dan haka suka fara kwashe manyan atamfofi su exclusive da super da aura, suka bar holland, vlisco da england, ghana da shaddodi da lesuna kanana. Hajiya Saratu 'yar duniya ce, sam ba halinsu daya da yayarta ba, Ma'aikaciyar banki ce, irin matan nan ne masu isa da izgili da hassada, yayarta ma ba kyaleta tayi ba don dai ba biye mata take yi ba, don haka ta dubi Alhaji Abdullahi ta ce, "Haba Alhaji wannan yarinyar da 'yar talla ce, diyar matsiyata jahilai za'a kaiwa wannan dukiyar? Ai ba za ta iya amfani da su ba, ko da yake ta danyi yawon....." "Ke Saratu ni sa'anki ne da zaki dinga gaya mini wannan maganar? To wallahi zan saba muku gaba dayanku, koma me cece shi ya ga abarsa yace yana so, kuma kuna da 'ya'ya mata baku san me zasu zama ba, fata na gari lamiri."Ya yi fada sosai sannan ya fice. Tsananin kwarjini da rashin hayaniyarsa da rashin shiga abinda ba nasa ba ya sanya kowa ke shakkarsa, don haka kowa yayi tsit, sai da ya fita ne sannan Hajiya Saratu ta dauki jakarta tana fadin, "Lallai Kubra an dauko miki ruwan dahuwarki, kinga sai bala'i yake, akan wannan kucakar yarinyar Alhaji yake mana wannan cin mutuncin har da yiwa 'ya'yanmu baki, to ba dani ba, babu hannuna cikin wannan sha'anin." Ta nufi kofa a kufule. Hajiya Kubra ta rikota ta ce, "Haba 'yar uwa kada kiyi mini haka, kin san dai yanda naki jinin mutuwa ta haka naki jinin auran nan da yarinyar nan karuwa, idan kika ce kin zame hannunku waye zai taimaka mini mu ga bayanta? Ki yi hakuri ki rabu da Alhaji a ruwan sanyi zan shawo kansa, wuyarta dai a yi auren." Da haka ta samu ta lallaba Hajiya Saratu suka tafi kai kayan. Sun so su tata rashin mutunci sai dai da yake a gidan Malam ne yayi musu kwarjini, saboda ganin mata masu mutunci da sanin darajar kansu, 'ya'yan Malam kyawawa ne masu ilmi don haka duk manya suke aure, duk ya sanar da su maganar biki, sune kuma kamar dangin uban su Zainabu, don haka suka gaza iskancinsu, amman duk da haka sun yada maganganu. Sanda Mustafa ya ji an rage kaya daga bakin Sumayya ransa ya baci, amman ya bar abun a ransa ya tafi ya siya kayan da suka cire ya baiwa Zainabu yace ta sanya cikin kayan lefen, za tayi magana ya hanata yace tayi kawai yanda yace din, sai lokacin ta gane abinda ya faru don tayi mamakin ganin kayan sun ragu amman dai tayi shiru ne kawai. Saura sati guda Sadiku yayi kiran Zainabu dakinsa ransa a tsananin bace kamar wanda aka aikowa da sakon mutuwa. Ita kanta da taga yanayin fuskarsa sai da gabanta ya fadi, ta dubeshi a tsorace ta ce, "Yaya Sadiku lafiya ko?" Ya ja tsaki kana ya ce ta zauna, sai da ta zauna sannan ya ce mata, "Zainabu akwai wadanda suka kai mu takaicin rashin iyaye na gari a zamanin nan? babu su tabbas, ba muyi dace da iyaye na gari ba, sai dai Allah ya shirya mu ba wai don tarbiyyarsu ba."Gabanta yana faduwa domin ta san tunda yake fadin wannan magana akwai wani mummunan abu da ke shirin faruwa, ta ce masa, "Wai me ya faru ne?" Ya yi kwafa sannan ya fara zayyana mata, "Kamar yanda kika sani Sala ta ci alwashin ko cokali ba zata yi miki ba, ta fada a gabana ta fada a gaban ki, kuma ko bikin Karima ma haka tayi duk da irin tallan da kuka sha yi mata, balle Baba da daman ba a zancensa gwara kowa da shi. To jiya da daddare na yanke shawarar na sami Malam mu yi magana akan kayan da za'a siya miki, kin san nima da hidima a kaina gashi ba wasu wadatattun kudi nake da su ba, wanda nake dan tarawa ne a banki, sai na dauki dubu tamanin a ciki da zummar na bawa Malam a hada da kudin zance da dukiyar uwa da uba ya zamana dubu dari da hamsin a yi kayan gado da kujeru, dubu hamsin dinki ta sadaki a baki abarki a hannunki, idan ya so kayan daki kya san yadda za kiyi ki hada na jere. Da na jewa da Malam da maganar sai ya cika da mamaki ya ce mini, "Sadiku wanne kudi kuma, bayan tun ranar da aka kawo Mahaifinku ya zo na bashi duka, sai nace a'a dubu Saba'in zan bashi dubu hamsin sai an daura aure zan baki a hannunki, domin sadaki hakkin mace ne, sai ya ce mini ai kun yanke shawara da su zaku cika kuyi kayan daki." "Ina jin haka raina yayi masifar baci don na san Baba ya kashe kudin nan, baya jin kunya balle tsoron Allah, bai sauke nauyinsa namu da ke kansa ba wanda Allah ya dora masa ba, amman ya koma yake karbar hakkinmu, domin kada na bada mu na watsawa Mahaifinmu kasa a ido, don nasan duk lalacewarsa shine ubanmu, ya sanya na dannen fushi na na rufa masa asiri na ce da Malam, shi kenan zanje mu yi maganar da shi naji ina kudin, Malam ya bini da to kawai, amman daga irin kallon da yake mini na san ya san ba za'a sami kudin nan a hannun Baba ba, domin ya fimu sanin halinsa." "Don haka na yanke hukunci da kaina yau na zauna naki yin bacci, na dinga karance-karance har karfe biyu da rabi sanda Baba ya shigo gida, ina jinsa yana kokarin kulle kofa ya sanya na leka, shi kansa yayi mamakin ganina, ya ce lafiya Sadiku baka yi bacci ba?" Na ce "Baba ka shigo daga daki na ina son yin magana da kai bana son Sala ta ji, babu musu ya biyo ni ya tsaya daga bakin kofa yana wani muzurai ya ce, "Lafiya dai ko?" "Na zayyane masa yanda muka yi da Malam, na dora da cewar, yanzu ya bada kudin gurin nasa a cika a yi miki kayan daki." "Na gaya miki sai gashi ya kama gumi jikinsa ya dauki rawa ya kama inda-inda, daga karshe sai ya ce wai ya karbi kudin yana tahowa a hanya 'yan sane suka yanke masa aljihu, to yasan idan ya fada ba za'a yadda ba ne shi ya sanya yayi shiru, yanzu haka neman kudi yake ido rufe ya biya." "Daga yanda yake maganar zaki tabbatar bashi da gaskiya, raina ya baci na ce, Haba Baba mai yasa ka karbi kudin nan, tun da muka taso baka san cinmu ba balle shan mu, duk wani fadi tashi Mahaifiyarmu ce ke yi, don haka duk wani hali da 'ya'yanka suka shiga kai ne ja gaba, mun kyale ka don babu yanda za muyi amman yanzu ace an kawo kudin auren diyarka ka bi ka amshe bayan kai ko tsinke ba zaka yi mata ba? Wanne abin gori kake son bar mana, yanzu idan sirikan Zainabu suka ji wannan zancen da yaya kake ganin zasu kalle ta?." "Maimakon yayi nadama, a'a sai ma ya kama fada, ta inda ya shiga ba ta nan yake fita ba yana fadin, ai nasan Babarku ce ta sanya kuka raina ni, amman banda haka ta yaya zan fadi magana ka karyata ni, duk lalacewata ai nine ubanku dai ba a sakewa tuwo suna....." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 "Fada dai babu makama, kamar an tashi Sala sai muka jiyo muryarta daga cikin gida tana fadin, Wai waye ke mana hayaniya a daran nan, kin san ita ba lokaci take dubawa ba ta zaci dare ne sosai, ta iso zauren ta ga Baba a kofar dakina a tsaye, shi kuwa jikinsa sai rawa yake. Da mamaki ta ce, Abbakar lafiya na ganka a nan, me ya faru?" Da in-ina yake fada, "Fada nake masa ya bar kofar gida bai kara ba, kada awaki su shigo su yi miki barna." Yana magana yana kanne mini ido wai kada na fada, da yake ranar babu 'yan magana a kanta sai ta yamutsa fuska ta juya kawai, ya bita da sauri, shine duk na ji raina ya kuma baci, wallahi bacci sai dai barawo jiya ya sace ni."Ran Zainabu idan yayi dubu ya baci, ta dafe kai tana fadin, "Oh ni Zainabu mun shiga uku, yaushe zuciyar iyayenmu zata gyaru su san Annabi ya faku? Sadiku duk fa wani iskanci da yawon tallan da nayi Baba ya sani, amman a matsayinsa na Mahaifina bai taba kirana yayi mini fada ba, Balle Sala da ke kuma tinzirani, shin suna zaton Allah zai barsu haka ne? Addu'a kawai zamu cigaba da yi musu sannan mu binne wannan maganar a tsakaninmu." "Domin ka san idan Sala taji wani bala'in ne zai tashi, don nasan ko ruwa ba zai sha a gidan nan ba, kuma sai ta sanar da kowa, daga karshe dai mu ne da abin kunya domin su ko a jikinsu, daman dangin Mustafa musamman Babarsa ba auren nan take so ba, balle haka ta faru taji ai na shiga uku da gori, dan haka kawai mu ja bakinmu mu yi shiru, Allah ya sanya ina da kudi a account dina, kada ka damu idan anjima zan fito maka da dubu dari biyu, duk abinda ka ga ya dace daga kujeru zuwa gado ka siya, amman ni na sayi komai na jere da na kicin zuwa labule, kayan katako ne kawai ban siya ba, ka bar kudinka kawai tunda kai ma kana da taka hidimar, na gode." Ya ce, "A'a, nayi niyyar baki dan haka sai a sayi kayan gadon da su. Ta ce, "Shi kenan na gode,Ta fice daga dakin nasa amman har lokacin zuciyarta tafasa take yi, ina ma wani ne can yayi mata haka da yau ya gane kurensa wallahi, ita da take neman fada da kudinta balle ya zo?, don dai Mahaifin ta ne, ta kuma yi alkawarin ba zata yi masa magana ba, ta barshi da kansa zai gane bai kyauta ba komai daren dadewa. Mustafa kam idan ka ganshi tamkar wanda aka yiwa albishir da gidan Aljanna, duk da irin maganganun da Hajiyarsa ke gaya masa yayi kunnen uwar shegu kamar baya jin ta, hidima yake yi sosai, an shirya biki na garari. Ranar kamu ma a central hotel aka shirya za'a yi, an yiwa gurin kamun kwalliya mai kayatarwa, Mahmud Nagudu yana cashewa, amarya ta shigo cikin wani irin Sari na Indiya (Golden colour) kalar kyalli, har da irin sarkar nan tasu ta goshi ta yi kyau matuka, da yake Zainabu akwai iya tsara kwalliya, nan fa aka fara cashe rawa, sam ta manta ita amarya ce, domin yanda ka san mazari haka take gurin rawa, sai da Asma tayi mata rada a kunne sannan ta tuna ta koma ta zauna tana dariya, kawayenta kuwa suka yi mata ca da liki, gaskiya sunyi mata kara. Sanda dangin mijin suka iso sai da gabanta ya fadi don ganin irin kallon da Hajiya Saratu ke mata, tabbas a halitta bata da makusa duk iyakacin hassadar mutum, dan haka ne ma ya sanya ta dinga kallonta a wulakance, Rungumar da Sumayya kanwar Mustafa ta yi mata ne ya sanyaya mata rai, nan fa Anti Binta ta fara fesa mata turare (Diyar Malam ce tana koyarwa a makarantar Legal), nan fa kida ya kuma barkewa, sai karfe takwas aka tashi. A motar Asma suka zo gurin kamun dan haka bayan an watse ma suka fita da zummar hawa, sai dai sakon da ya shigo wayarta ya tsaidata tana karantawa, ta yi murmushi ta leka ta windo tana fadin, "To ke an hutar da ke domin dai ga ango na can yana jirana a mota au haka za kiyi mini 'yar iska zan rama wallahi." Tana dariya ta nufi gurin motar Mustafa domin ya gaya mata inda yake a tsaye. Tunda ta nufo shi yake kallonta ta hasken fitilar da ta haske kofar hotel din, ji yake kamar ya fita da gudu ya taro ta, amman dai ya dake ta karaso, ita kuma har wani sauya salon tafiya take yi. Ta shiga motar tana murmushin jan hankali, ya riko hannunta yana fadin, "Kai Zainabu wannan wane irin kunshi ne sai kace na indiyawa?" Ta kanne ido tana dariya ta ce, "Kai dai kawai kace yayi kyau wace ni nayi irin na Indiyawa?" Ya dinga murza hannun nata yana murmushi ya ce, "Ai ni a guna yafi na Aishwarya Rai da Pretty Zinta da Kajol da duk wata macen indiya da ke tashe, domin yanda nake jinki tamkar mafi kyan duniya." Ta yi dariya sosai domin jin dadin kalamansa, amman sai ta canja maganar tana cewa, "Wai yaushe ne kazo nan nema? Na yi mamaki da na ji kace kana kallona na zo ka maidani gida." Ya kishingida da kujera har lokacin yana rike da hannunta ya ce, "Kina fitowa daga gida na isa aka ce kun wuce a motar Asma'u, shine na biyo bayanki, komai akan idona aka yi, can baya na labe inda ba zaku ganni ba, amman sanda naga kina taka rawa dauriya ta ta kusa karewa na fito na hanaki, domin sai naga kamar mai kidan da yaransa ke kawai suke kallo, sai Asma'u tayi maki gata tayi miki rada a kunnen kika daina.""Tuba nake ba zan kuma ba, kasan ni da rawa....." "Mu bar wannan caftar, yanzu ina muka nufa?" Ya tambaye ta. "Gida zan koma, don mai yi mini dilka da halawa tana jirana." Ya tada motar yana fadin, "A'a ai dole na kai ki a gyara mini jikin nan, ki duba tun yau yanda kika fara zama, fatarki ta zama wata mai taushi da kyalli." Yana magana yana cigaba da murza hannunta dayan kuma yana tuki da shi. Ta janye hannunta tana fadin, "Kada ka sanya mu yi hatsari." Amman bai saki din ba dole ta hakura tana tsokanarsa har suka isa gida. Zainabu tana da wani sirri da ke sanya maza matowa a kanta, wato gyaran jiki, na farko dai duk nacinka ba zaka taba ganin gashi ko kwaya guda a gabanta ko a hammatarta ba, kullum cikin askewa take da (shaving powder), domin a cewarta sune gidan tsami dake sanya jikin mace wari duk irin turaren da ta sanya, sannan na gaban kan rike kwayoyin cuta wanda ke hassadawa mace cutuka kala- kala, baya ga tauye mata ni'ima da yake yi, sannan ba ta da sanya gurin shan magunguna 'yan gaske ba irin na macuta ba, don haka yanzu da zata kwanta sai da tayi hadin ta ta sha kamar haka. Hadin nikakkiyar aya wacce aka jikata ta jiku aka markado da dabino jikakke, bayan an surfa ayar a hadin aka markado da kanumfari kadan sai a sanya madara ko nono da suga ta sha, sannan ta kuma dauko wani dakakkan garin hadi wanda aka hada garin kanumfar da dakakkiyar 'ya'yan kankana da dabino da garin aya tankadadde da kirfa da gero da hakin daka da mazarkwaila da sassaken banna aka dakesu lukwi ta sha da yoghot na roba. Sannan ta dauko wata buta can bayan gadonta wacce take jike da ruwan bagaruwa din-din-din, ta zagaya bandaki ta yo tsarki dashi da ruwan dumi a cikin flask da ta kara, bayan ta dawo ta dauko auduga ta dangwali garin fas da ta kwabashi da man zaitun da itacen asuwaki ta matsa shi a gabanta, yayi kamar minti biyar sannan ta cire ta koma ta feshe jikinta da turaruka ta sanyo rigar bacci ta kwanta. Zainabu kam tana da sirrikan da take siye zuciyar maza da shi a banza ma balle mijinta abin son ta Mustafa, don haka tayi alwashin zata yi gyaran da zata gigita shi. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Gurin Dina ma tayi kyau matuka tamkar itace tayi kanta, Mustafa duk ya wani rude ga wani irin kamshi da take yi, domin dai idan ta yi wanka takan shafa mai mai hade da turare sannan ta sanya turare mai maiko, ta kawo (body spray) turaren jiki ta shafa sannan bayan ta sanya kaya ta kanyi amfani da turare kusan kala shida, don haka sai ka rasa gane wanne irin turare ta sanya. Ranar Asabar 20 ga watan Shida 2004 aka daura aure mai cike da tarihi na Mustafa Abdullahi da Zainabu Abbakar, jama'a kam tamkar ana bikin sallah, gaskiya daurin auran yayi jama''aA kuma ranar aka je aka yi mata jere, Zainabu kam ta fidda kanta kunya, domin tayi kaya na gani na fada, duk girman gidan Mustafa an jere ko ina, ga gara da aka jibga mata komai da komai, abin dai gwanin sha'awa, su Malam kan sunyi mata kara, sun zame mata gata da 'yar uwarta Karimatu wacce itace ke tsaye akan komai na bikin na su, tun da Sala tace babu ruwanta, sunyi sa'a dai Sala bata yi bala'i ba faran-faran da kowa ta ci kwalliyarta kamar gaske. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Zaharaddeen Shomar whatsapp 08168575100 Idan Zuciya Tagyaru2-03 Posted by ANaM Dorayi on 08:07 AM, 11-Feb-16 Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU _______________ Na _________Fauziyya D Sulaiman____ Amman har lokacin tana nan kan bakanta na sai ta raba auran, duk da babu wani abu na kushewa da zata iya cewa daga Mustafa, Kayan lefen Zainabu duk kawayenta babu wacce ta samu kamarsu, ita dai tafi son Zainabu ta cigaba da bin maza tana kawo mata kudi, babu tsoron Allah a zuciyar ta balle nadama. Ranar lahadi da misalin karfe goma sha daya da mintuna aka shigar da Zainabu dankareren gidanta na masoyinta, gidan kam ya hadu duk hassadar mai hassada. 'Yan kai amarya sun watse cike da tsegumin gidan, har wata a cikin matan na fadin, "Oh ni Maryam, zamani ya canza, ki ga mace ta gama iskancinta da watsewarta amman daga karshe sai kiga mai kudi ya aureta, nawa muka gani a wannan zamani? Ki dubi gidan da Zainabu ta shigo, haka nan wata a bayan layinmu Ummi Caransi ka da ki so kiga iskancin da tayi, karshe na gaya miki wani minista ne ya aure ta, yanzu baki ga arniyar motar da take murzawa ba wallahi." Abokiyar maganar tata tayi kwafa tana fadin, "Ki ji Maryam da wani zance, to menenen abin mamaki a ciki? Ko kin manta ayar Allah ta cewar (Mazinaci baya aure sai mazinaciya ko fasika)? don haka idan kika bincika za ki ga wata kila daman can abokin fasikancin ta ne ta aura, ko kuma shima yana yi a can itama tana yi a can Allah ya hadasu, su kuma matan kwarai da basu auran manya Allah ya ga zuciyarsu don haka sai ya hadasu da salihan bayi 'yan uwansu talakawa, ko kuma masu kudin na gari, wanda yanzu sai kinyi da gaske za ki samo su." "Idan kuma kika yi nazari zaki ga 'yan iskan da ke auran masu kudin suna ganin sunci riba, gaba zasu girbi abinsu ko da akan 'ya'yansu ne, idan Allah ya sosu da rahama idan kuma basu da rabo sai Allah yayi musu talala sai a can, dan haka shi iskanci bashi da wata riba ga mace ko namiji, fatanmu dai Allah ya shirya mana zuri'a, sannan mu dage da tarbiyyar yara, domin amana ce Allah ya ba mu komai dadewa za mu yi wa Allah bayanin yanda muka yi kiwonsu, idan sun zama na gari su zame nana sadakatu jariya bayan ranmu, duk aikin da suka yi na lada mu samu rabo, idan kuma mun watsa su zamu yi wa Allah bayanin sakacin da muka yi da kiwon da ya bamu." Maryam ta yi ajiyar zuciya ta ce, "Haka ne kuma, a yanzu dai sai mu baza kunnen mu ji abinda zai biyo baya kenan da auran Zainabu.......a'a ki daina fadin haka, ai shi Ubangiji Gafurur Rahim ne, kuma da zuciya yake amfani, idan zuciyar Zainabu ta gyaru sai Allah ya saka mata da mafi alkhairi, tun da dai shi sarki ne mai yafiya, kuma idan ka gorantawa dan uwanka wani aiki na sabo da yayi, ko zina ko sata da dai sauransu, sai kiga Allah kaima ya dora maka, tunda abin jarabawar ce, kuma muma ba wayonmu ko dabararmu bace ya sanya Allah ya shirye mu ba illah Rahamarsa, don haka sai a yiwa wadanda suka kauce addu'ar shiriya." Maryam ta ce, "Haka ne kam, Allah na tuba." Suka rufe zancen nasu domin jin motar da zata mai da 'yan kawo amarya ta dawo. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 BURIN MASOYA..... Burin masoya lallai bai wuce ganin su tare ba, bisa aminci na aure ba, lallai haka ce ta faru ga Mustafa da Zainabu, domin dai ko wasu 'yan siyan baki bai zo da su ba, sai abokinsa kuma amininsa Alkasim, shima daga kofar gida suka rabu yana zolayarsa. Yana shiga ya kukkulle ko ina na gidan ya nufi dakin amaryarsa cike da doki da murna. Ita kam tana zaune bisa tafkeken gadonta wanda ya sha kayan shimfidu na alfarma, ta sha wani hadadden leshi da kudinsa ya tasamman dubu hamsin, bashi da nauyi sai dankaran taushi, light purple ne ya sha duwatsu da cin baki da fari, ya amshi jikin Zainabu, sai sarka da dan kunne na zallar daimond kirar dubai da ta sanya da zabba da awarwaro, an kuma nadeta da wata laffaya wacce ta sha turaruka kala-kala, kamshi ne kawai ke tashi kala-kala daga jikinta, gashin nan ya sha gyara duk da ba ma'abociyar sanya gashi bace a wannan karon an mata kitso da shi, ta yi kyau das tamkar amaryar larabawa, domin Zainabu tana da kyau matuka, duk da fatarta bata fiye haske ba, hancinta da idonta ya kara fito da kyawunta, sam bata shafa man bilicin domin tana son kalar fatarta kalar alawa, sai dai fa akwai ta da amfani da mayukan gyaran fata. Sai ta hada mayuka na dubu sittin har fiye da haka, don haka kullum ka ganta tamkar diyar tarwada tana sheki da sulbi, balle ka taba jikinta, wani silbi yake yi da taushi, ta yadda ta kashewa jikinta ko nawa ne, don haka ba a banza take siye zuciyar 'yan maza ba. Da gaggawa ya isa gabanta ya zauna sosai bisa gadon saboda kamshin dake shiga hancinsa, ya daga laffayar a hankali, ta dago tana masa murmushinta mai kyau kumatunta ya lotsa (beauty point), ta kwantar da murya da kissa ta ce, "Mustafa honey yaya gajiyar biki?" Ya lumshe ido cikin wani salo da kallon da ya saba sace zuciyarta, da wata irin murya wacce shi kansa bai san yana da ita ba ya ce, "Zainabu yau kin zama tawa ni kadai, yau wane farin ciki kike zaton zanyi? Bana jin wata gajiya sam, ki cire wannan laffayar na ga adon naki." Ya kama warware mata laffayar, shigar da ke jikinta ta fito ya kuma rudewa. Da kyar ya iya dauko fresh milk da nama ya ce su ci domin kada su ji yunwa, babu musu ta ci amman tana jikinsa a makale kamar zata gudu, ita da kanta ta san tayi rashin zumarta Mustafa. Ba su kammala cin abincin ba komai ya kacame, domin ba zai iya hakuri da Zainabu ba, wani salo take nuna masa da yake haukatar da shi, tana daga cikin mata ajin farko da suka amsa sunansu,Sai dai wani abu da ma'auratan basu yi ba shine, sallar da Ma'aiki ya koyar da mu ta samun tsaftatacciyar zuri'a da samun zaman lafiya a aure ba, saboda sun kwadaitu da juna kamar basu san juna ba. Da kyar suka iya rabuwa da juna da safe, amman sun yadda lallai aure yafi komai dadi, domin babu fargaba a zuciyarsu ta wani zai gansu ko kuma ta suna aikata sabo, dan haka suka sakata suka wala. Karfe goma na safe suka fito babban falonsu suna sakale da hannun juna, kananan kaya ne a jikinta, duk sanda ta taka kafarta sai jikinta yayi rawa, wata irin halitta ce da Zainabu ta daukar hankali, bata dai ta tsaho sosai amman tana da siffa irin mai daukar hankalin nan, don haka idan ta saka kananan kaya sai ka ganta tamkar wacce da su aka halicce ta.shima Mustafa ba baya ba, yana da tsaho da kirar karfi, yana da faffadan kirji da yake birge mata da su, yana da kyan fuska irin ta maza ajin farko hancinsa dogo ne, shi kam yana da duhun fata sai dai ba can ba, yana da saje dan siriri wanda ya fito da kyan fuskarsa sosai, gashinsa yana da taushi saboda gyara da yake samu. Suka fito rike da hannun juna cikin nishadi da soyayya, kafin su karaso kukunsu Emmanuel ya kammala shirya komai, domin tun yana saurayi shi ke shirya masa abinci a can gidansa na shakatawa, ya iya girki matuka domin abinda ya karanta kenan. Ya zauna ya zaunar da ita bisa cinyarsa, ta kalli abincin da mamaki ta ce, "Honey waye ya dafa....kai Zainabu har kin manta da mutumin naki Ema?, ai da shi na taho nan gidan ma, don ya dinga taimaka miki gurin aikinki." Ta yi murmushi ta ce, "Ba mantawa nayi da shi ba, gani na yi ban gane shi ba, ka sanshi da shakiyanci, nasan idan ya gama abinci ya kan zauna a gurin har mu fito yana mana shakiyanci." Ya ce, "Ai da kika ce yanzu ya san da bambanci, na gargade shi da kada na ganshi a cikin gida idan ba lokacin aikinsa ba ne, da zarar kuma ya kammala ya fita, domin kin san ina da tsananin kishi musamman a kanki, ba zan so ya dinga kalle mini ke ba." Ta yi murmushi sannan ta ce, "Ai dole zai tafi ma don ban yadda wani yayi mini girkin mijina ba." Sannan ta debo abinci a cokali ta sanya masa a bakinsa, ya lumshe ido yana dariya ya amsa, haka nan suka dinga ciyar da juna. Sai wajajen karfe goma sha biyu yayi shirin tafiya gaida su Hajiyarsa, ta ce masa ya dace ya raba kayan gara biyu ya kai musu nasu. Ya dube ta ya ce, "Haba dai me za su yi da wani kayan abinci, ai suna da shi da yawa a sito (store)." Ta kwantar da kai tana masa wani duba ta ce, "Honey haka ne ka'idar ai, dole idan aka kawo kayan gara sai an kai gidan iyayen miji, suma ba ci zasu yi ba zasu rabawa 'yan uwa ne maganin gori ga matar, domin kasan mutananmu sun dauki garar nan da girma."ya yamutsa fuska ya ce, "Kin san Allah? Wallahi da an yi shawara da ni da babu wata gara da za'a kawo, domin ni ke nake aure ba gara ba, duk namijin da kika ji yana gori ko habaici don gara to lallai matsiyace ne na karshe, su kansu masu goranta garar daga dangin angon suma zuciyar talauci ce da su duk arzikinsu, domin mai wadatacciyar zuciya a gurin Allah yake nema bai saka rai da na wani ba." Ta ce "Haka ne ga wanda ya gane, mu je mu raba kawai lokaci yana kurewa baka je ka gaida su ba." Kusan komai daidai suka raba ta sanya gyalanta ta taya shi shigarwa a mota, wasu kuma sai da Ema ya sanya musu, bayan but din ya cika taf da kaya, tana kallonsa tana daga masa hannu ya fice daga gidan. Ta koma falo ta zauna zugum tana kallo, sai taji kewar maigidan nata, sai kuma ta tuno da shandy dinta, da ma tayo guzurin abinta domin ta lura kamar Mustafa yanzu ya daina shan komai sai taba, don haka ta shige daki ta dauko ta tana zuka tana lumshe idanunta kamar mai cin naman kaza, sai da ta ishe ta sannan ta fadi jagwab a gado tana ramuwar baccin daran jiya. Shi kuwa sanda ya isa gidansu ya tadda kanwarsa Sumayya da Zainab 'yan matan Hajiyarsa suna kallo, da girmamawa suka gaishe shi, ya zauna bisa kujerar yana amsawa da sakin fuska. Zainab ce ta mike ta ce, "Ya Mustafa bari a kawo maka abinci da ruwa ko?"Ya ce, "A'a Zainab ki barshi a koshe nake." (Da yake suna dasawa da Zainabu, duk cikin 'yan matan gidansu tafi kowa tarbiyya, gashi tana da sunan masoyiyarsa, lokuta da dama yakan tsokane ta da mai sunan darling su yi dariya). Ya kuma dubansu ya ce, "Yaya dai 'yan matan gidan mu ina Momin taku take naji shiru babu motsinta?" Ta ce, "Wallahi gajiyar bikin nan ce bata sake ta ba, amman ta tashi bari na kirawo maka ita." Ta mike ta nufi sashin Momin nasu. Ya kalli Zainab wacce gaba daya hankalinta yana kan kallon fim din da suke kallo na wani Indiya mai suna Ghajini, ya ce, "Yaya dai mai sunan darling, ke fa akwai ki da son indiya dan naji wani lokaci har fassarawa kike, a bani labarin wannan fim din." Ta yi dariya ta ce, "Ya Mustafa ai wannan fim din labarinsa ba zai badu ba domin ya hadu karshe wallahi, sai dai mu baka aro ka gani." Ya yi dariya ya ce, "A'a bani da lokacin kallo sai dai na baiwa takwararki ta kalla, domin naga ita ma tana son kallon, idan yaso sai ta bani labarin naji." Ta yi dariya ta ce, "Yaya kenan, kana son Yayar nan tamu da yawa wallahi, zan so muje mu gaishe ta kuwa." Ya ji dadin abinda ta ce har ransa, shi ya sanya hirarsu take tsaho da Zainab, domin tana son Zainabunsa ya ce, "Lallai yarinya zaki ga Zainabu kuwa, za kuma ki san ba a banza nake sonta ba, domin tana cikin mata sahun farko, ke ni fa a iyakacin yawo na da nayi a duniya har yau ban ci karo da macen da ta hada qualities din Zainabu ba." Zainab ta sanya dariya cike da mamakin irin son da Yayan na su ke yiwa Zainabu, tun da take bata taba jin ko labarin irin soyayyar su ba, shima dariyar ya kama yi a haka su Hajiya Kubra suka tadda su. Dadi ya kama ta domin a rayuwarta tana son taga ya saki jiki da 'yan uwansa yana hira, amman shi miskili ne sai ya so, sai dai ta lura suna dasawa da Zainab ko don sunan 'yar mulkin tashi ne da ita Oho? Ya tsagaita dariyar yana duban ta ya ce, "Momi barka da safiya, na shigo ban ganki ba na ke tambayar 'yan matanki suka ce kina ciki." Ta yi murmushi ta ce, "Lallai kam ka yi sa'a yau basu da lakca ta safe shi ya sanya aka zauna kallo." Zainab ta mike da zummar barin falon, Hajiya Kubra ta ce, "A'a ina zaki Zainab? Zauna ku cigaba da kallonku, ai hirar da ku za'a yi." Ta koma ta zauna amman hankalinta yana kan fim din gaba daya, hira suke yi sosai shi da Hajiyar tasa kamar babu wani abu a tsakaninsu, har kusan awa guda, can ya mike ya ce zaije ya gaida abokansa yayi musu ban gajiya. Sai a sannan Zainabu ta fado mata, ta hade rai ta ce, "A gaida su." Kamar kada ya fita ganin yanda ta sauya lokaci guda, amman gudun kada ya tsokanowa kansa fitina sai ya sanya yayi shiru ya juya ya nufi kofa, Zainab da Sumayya suna yi masa a gaida Antinsu, ta galla musu harara basu kula da ita ba. Sai da ya fita sannan ya tuna da kayan garar dake cikin motarsa, ya kirawo mai gadi ya ce ya shiga da su ciki, shi kuma yana saukowa da su. An shiga da buhu biyu maigadin ya ce, "Wai Hajiya ta ce ka shiga tana son ganinka, a daina shiga da kayan."gabansa ya yanke ya fadi amman ya dake ya shiga yana addu'a a zuciyarsa. Tana zaune inda ya barta, sai dai tayi kicin-kicin kamar ba ita ba, har lokacin su Zainab suna nan suna kallonsu. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 "Momi gani maigadi ya ce kina kira." Ta yamutsa fuska tana kallonsa ta ce, "Na ga ana shigo da kayan abinci shine na ce bari naji daga wa, don naga har da dubulan da alkaki?" Gabansa ya cigaba da faduwa, ya daure yayi ta maza ya ce, "Momi daman kayan gara ne Zainabu ta ce a kawo......" "Kai!" Ta doka masa tsawa, ta dora da cewar, "Kaga munyi kama da wadanda za su ci kaya daga hannun matsiyaciyar matarka? Me take da shi da zata bamu? Bana raba daya biyu wannan kayan garar da kudin haram aka siye su, don haka yau ce rana ta karshe da zaka kuma kawo mini wani abu da ya shafi matarka, kada ka manta na sha sanar da kai bani kaunarta na tsane ta, domin na santa na san wacece ita, kai ne aka linke a bai-bai, don haka ka hada kayanka ka fice da su, tun basu sanya jini na ya hau ba, zan kuma sanar da kai kashedi na karshe, ko da wasa kada ka yi gigin kawota gidan nan, domin wallahi sai ta gwammace bata taba gani na ba balle ta auri jini na, domin kasan sirrinta kaf yana tafin hannuna, idan kunne ya ji jiki ya tsira." Sororo yayi tsaye yana jinta cike da tashin hankali, bai taba zaton kiyayyar da Mominsa ke yiwa Zainabu ta kai nan ba, amman yaya ya iya dole ya fara kinkimar kayan yana fita da su. Zainab da Sumayya dake zaune jikinsu yayi sanyi, domin basu son abinda Momin ke yiwa Yayan nasu akan matarsa sam, amman basu da ta cewa don haka suka ja bakinsu suka yi shiru. Shi kuwa da ya gama jidewa ya dawo ya durkusa a gabanta ya ce, "Ki yi hakuri Momi ba zan kuma yin abinda zai bata miki rai ba da sani na Insha Allah, na barki lafiya." Ya mike ya nufi kofa. Ta yi tsaki cike da kuncin zuciya ta ce, "Bacin rai kuwa ai yanzu ka fara gani tun da ka kwaso kara da kiyashi ka ajiye a gidanka, koren juji wanda Manzon Allah ya hori sahabbai da su guje shi, wato kyakykyawar mace a gida mara tarbiyya." Kanwarsa Sumayya ta ce, "Haba Momi ya dace ki yi hakuri zuwa yanzu tunda dai Allah ya kaddara sai anyi auren nan....." "Ke rufe mini baki, ni zaki yiwa wa'azi? Da ban yarda da kaddara ba zan amince ya aure ta ne? Ai na sani ita din mummunar kaddara ce a gare mu, amman nasan babu alkhairi ga Zainabu har abada."Ta mike ta nufi dakinta tana mita. Zainab ta dubi Sumayya ta ce, "Kin ga da Momi tana fadan nan sai naji duk hankalina ya tashi, abinda ba halinta ba ne, na rasa irin laifin da Anti Zainabu ta yi mata haka da zafi ta tsane ta." Ta yi ajiyar zuciya ta ce, "Kin san tsohuwar dalibarta ce, kuma ta san halinta sarai, gashi munafukai sun kawo mata labarin gidansu gaba daya, mu da ba shiga harkar 'yan unguwar nan da muka tashi nake ba sai da aka so ayi mini tseguminta, na ce ina ruwana meye nawa a ciki, wanda yace yana sonta yafi kowa sanin halinta kuma shine zai zauna da ita meye nawa a ciki, ita kanta Momi na so ace ta kauda kanta." Haka nan suka dinga tattauna matsalar, su kansu ba su son wannan sabanin tsakanin Momi da Yayansu. Shi kuwa Mustafa da kyar ya iya fita daga gidan da motarsa, yaje ya yi parking can gefen hanya, ya dora kansa bisa sitiyarin ya runtse idonsa zuciyarsa tana zafi, ya rasa wacce irin kiyayya Momi ke yiwa Zainabu, ya dace ace zuwa yanzu da ta zama matarsa ta sassauta. Amman ina saima karuwa da tayi, domin matakin da ta dauka yana nuna alamun ba za ta yi wata mu'amala da ita a matsayin sirikarta ba, tunda ta ce ko gidan bata kaunar tazo balle kuma ace ta zo wata sabgar, shi kam bai san inda zai tsoma rayuwarsa ba, Zainabu kam wani ginshiki ce na rayuwarsa da ba zai iya rabuwa da ita ba, sai dai kawai ya cigaba da addu'a Allah ya daidaita tsakaninsu da Mominsa, domin wannan kiyayyar tana ci masa tuwo a kwarya. Rayuwa ce mafi dadi da soyayya suka gudanar a cikin sati biyu da suka yi na hutunsu na amarci, dukkaninsu sun yadda ba suyi zaben tumin dare ba. Domin Zainabu ta bada kaimi sosai gurin ganin ta faranta ran maigidan nata, tayi sa'a kuwa lallai ta gama da zuciyarsa kaf, bai ganin kowacce mace da gashi, don haka bini-bini yana gida har abokansa suna masa tsiya. Ranar lahadi da daddare suna falo a zaune, ita tana zaune bisa kafet ta mike kafafunta shi kuma ya dora kansa bisa cinyarta tana wasa da gashinsa, har kitso take masa suna dariya, domin ji yake kamar tana masa susa. Ya ce, "Zainabu na gobe fa zan koma Ofis dan kin san hutun sati biyu kacal suka bani." Ta sha kunun karya ta ce, "Kai honey har hutun ya kare? Ai kamata yayi su baka wata guda gaskiya." Cikin shagwaba da jan rai take maganar tata. Ya rungumota jikinsa yana hada hancinsa da nata ya ce, "Haba my honey ki yi dariya mana, dole ce nima ta sanya zan koma, kin san aikin gwabnati babu daga kafa, amman kin san duk inda nake kina raina." Ta ce, "Shi kenan nima goben na fara zuwa aikina tun da zaman kadaici zai dame ni....." "What, me? Aiki Zainabu? A'a babu ke babu zuwa aiki." Ya katse mata magana. Ta ji maganar tasa a bazata don haka ta ce, "Haba dai, da wasa kake kaima kasan ba zaka rabani da aikina ba, kai da iyayenka suke kirana da 'yar matsiyata suka ga na kuma share gindi na zauna a gidanka bana nemo na kaina ai sai su zaci kwadayi ne ya sanya na aureka, kuma kasan sarai iyayena ba wasu bane dole zan dinga taimakawa 'yan uwana, don haka kama sake batu aiki kamar da kasa zan koma gobe ni ma domin ba muyi da kai zaka hana ni aiki ba." Ya tashi zaune yana mata wani duba tamkar wanda aka aikowa da sallahun mutuwa, sai wani hura hanci yake yi da zafin rai ya ce, "Kin san Allah Zainabu, ba zaki kuma zuwa wannan matsiyaciyar Sakateriyar da sunan aiki ba, ko kina zaton bani da labarin samarinki a can? To ki bude kunnanki da kyau ki ji, duk wani ko wasu da kike mu'amala da su can da to yanzu na yanke ta."Yanda yake maganar da gadara da isa itama ya hasala ta, don haka da tsiwa ta ce, "Au kace daman ka aure ni da wata manufa daban ne, to tsaya na sanar da kai Zainabu kaifi daya ce, wallahi da ina da niyyar kuma kusantar wani namiji da wallahi baka isa na aure ka ba har na zauna wata uku cur ina Istibira'i ba, don haka ka ji da kunnenka Zan koma aikina, duk abinda zuciyarka zata sanar da kai kai ka sani." Tana gama fadin haka ta nufi cikin dakinta ranta yana suya. Shi ma nashi ya kuma suya ya kama lallai ya sani Zainabu fitsararriya ce, amman ya yi zaton a matsayinsa na mijinta kuma wanda take so zata rangwantawa, ya koma ya jingina da kujera ya lumshe ido zuciyarsa na cigaba da suya, wallahi komai zai faru sai dai ya faru amman ba zai taba yadda ace yana nan sake da baki matarsa na mu'amala da wasu 'yan iska ba, ya fi kowa sanin halin shegen DPM din nan da chairman din da kuma sauran ma'aikatan dake sakateriyar, domin yayi bincike mai kyau a kansu, don haka komai Zainabu za tayi ba zai barta ta koma aikin nan ba, idan ta so tayi (resignation letter) takardar barin aiki shi kenan idan kuma bata yi ba ita ta sani. Haka nan ya yi ta zama a falon har kusan karfe sha biyu na dare, ga dai TV a kunne amman hankalinsa ba ya kan kallon, ya dai gaji ya kulle ko ina ya nufi dakin baccin na su,tana kwance a gadon da alama ta dade da yin bacci, tamkar mai bacci a cikin ruwa haka nan fuskarta tayi kyau, sanye take da wata yaloluwar rigar bacci duk iyakacin surarta a bayyane take, ga wani kamshi da ke tashi daga jikinta, yayi saurin kashe fitilar dakin wai don idonsa ya daina gano masa surar Zainabu domin yayi fushi da ita yana son ta gane yayi fushin,can karshen gado ya kwanta nesa da ita, sai dai kamshin Zainabu ya addabe shi da kewar lallausar fatarta, ya runtse idonsa wai bacci ya dauke shi dole, amman da kyar ya samu bacci ya iya daukarsa, domin dai cikin kwanakin nan ya shagwabe da kwana jikin Zainabu, ko tana kwance lamo bisa kirjinsa kamshinta yana dukan hancinsa. Da wurwuri ya tashi domin dai baccinsa rabi da rabi ne, sashinsa kawai ya nufa don shiryawa a can. Sai da ya kammala shiryawa ya fito ya zauna a tebur din cin abinci shiru yana tunani, domin ya saba da cin abincin Zainabu a 'yan kwanakin nan tana bisa cinyarsa tana masa shagwaba tana sanya masa a baki, a haka sai ya ci mai yawa ya koshi. Ya dafe kai kamar ba zai ci ba, can ya daure ya hada shayin kadan ya sha da soyayyar wainar kwai da soyayyan dankali. Ya dauki brief case jakar zuwa aiki ya nufi sashin Zainabu domin ya san halinta tun da ta dage sai ta fita lallai zata iya din. Ya duba falonta bata nan don haka ya wuce dakin baccinta kai tsaye, can gaban madubi ya hangota, daga ita sai dan micicin tawul iyakacin cinyarta da alama daga wanka ta fito, cinyoyinta sun fito sambal masu sulbi gwanin sha'awa, tana shafa mai, ta cikin madubi ta hango shi amman sai tayi kamar bata ganshi ba. Yanda ya ganta sai yaji wani abu ya tsirga masa, ya daure ya kauda kansa gefe ya kirawo sunanta, bata dube shi ba balle ta amsa masa ba, ya kulu matuka don haka da zafin rai ya ce, "Ke! Zainabu kina jina ina kiranki kin mini banza ko, to daman kashedi na zo nayi miki, wallahi ko da wasa kada ki fita gurin aikin nan, idan kina son zaman lafiya.....Idan bana so kuma fa?" Ta tambaya sanda ta mike tsaye tana kada kugu, wato komai ta fanjama fanjam kenan.Ya kawo iyakacin wuya, ya nunata da yatsa ya ce, "Kada ki yi mini rashin kunya don naga baki da mutunci, ni kike yiwa wannan tsiwar? To ki nutsu ki sani mijinki nake ba dadiro ba, in dai kuma ina da daraja irin ta miji wacce Allah ya bani to ban yarda ki fita ba, idan kuma kece ke iko da kanki to Bismilla....." Yanda yayi maganar ta sa ya sanya taji ba zata iya masa musu ba, don haka har ya fita bata kuma cewa komai ba, tana jin alamun tashin motarsa ta leka ta windo da sauri, da gudu ya figi motar tamkar mai shirin tashi sama, shi kansa maigadin tsaye yayi yana kallonsa cike da mamaki, domin ya san ba hakan ubangidan nasa yake ba. Ta koma ta zauna jabar gefen gado ranta yana suya da zafi, anya kuwa zata yadda wannan mutumin ya raina mata hankali? Ta ayyana a ranta, wato daman akwai abinda yake tunani a ransa shi ya sanya yayi mata lambo bai taba maganar zai hana ta aiki ba, lallai bai san ta bane labarinta yake ji, amman dai lallai ya ci darajar aure, don wallahi ba don hakan ba babu abinda zai hanata fita yau. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Tayi kwafa gami da nufar jakarta ta kayan cakunta, domin yanda take jin zuciyarta idan bata busa hayaki ta tsotsi ruwan shandy ba sam ba zata ji dadi ba. Tabar shaidan din ta fara kunnawa ta dinga bulbula hayaki kamar mai shirin hada hadari, sai da taji ta caku sannan ta hakura, ta dauko kwalbar shandy ta tsotsa iyakacin son ranta tayi dif abinta sannan ta baje a gado, idanuwanta suka yi mata nauyi don haka dole ta lumshe su, sam ba bacci take yi ba sai dai sake-sake na karya da zuciyarta ke mata wai gata can cikin hazo tana yawo cikin fararan kaya da kambu a kanta, Mustafa na rungume da ita bisa faffadan kirjinsa, ta yi tsaki gami da mai da kanta gefe don bata son tayi tunaninsa, amman ina banda shi babu abinda ranta ke iya gane mata.Sai da tayi kusan awa daya da wani abu sannan ta ji dan dama dama, ga wata azababbiyar yunwa, domin duk mai yin shaye- shaye yana da saurin jin yunwa, shi ya sanya wadanda basu da kudi irin 'yan iskan titi suke saurin haukacewa saboda yunwa ga buguwa sunyi. Wani dan wando three quarter iyakar gwiwa ta sanya, da riga iyakacin cibiya mara hannu, bata daura komai a kanta ba, haka nan bata yi wata kwalliya ba, amman da yake tana da kyau sai ta fito fes da ita. Kai tsaye ta nufi tebur din cin abincin su, tayi zaune shiru kamar ba zata ci ba, domin dai kewar Mustafa ta fara taba ta, musamman kirjinsa faffada da yake mata filo ko bargo da shi, ta lumshe manyan idanuwanta wadanda ke yi mata luu kamar ba zasu budu ba, sannan ta bude da kyar idonta ya kai kan wani hotonsa da ya dauka yana murmushi, tamkar ka kirashi ya amsa, ta zubawa hoton ido kewar mijinta ta dameta, haka nan ta danne ta yafini abinci ta ci kadan sannan ta koma doguwar kujera ta kunna TV wai ko ta rage kewa. Shi kam daga nasa bangaren kasa hasala komai yayi a Ofis din sa sai faduwar gaba yake yi domin yana fargabar kada Zainabu ta fita, domin dai ya san halinta da kafiya gami da taurin zuciya. Ya kasa samun nutsuwa, don haka dole ya mike da zummar zaije ya ci abinci ya dawo, sanda yayi hon maigadin ya leko cike da mamaki domin yasan da kam idan maigidan ya tafi aiki sai karfe shida yake dawowa amman sai ya wangale kofar da azama, ya shiga yayi fakin can rumfar da aka tanada don ita.ya nufi gidan kai tsaye da saurinsa, bisa doguwar kujera ya hangota da remote a hannunta bacci ya dauke ta. Yayi ajiyar zuciya cike da jin dadi bata ki jin maganarsa ba, wani son ta ya kuma shiga ransa. Ya lumshe ido cike da jin dadi sannan ya nufi firji ya dauki lemo mai sanyi ya fincine kan ya kafa baki yana sha, sai yaji gaba daya ya huce daga fushin da yayi da ita, ya kuma amince da lallai zai shawo kanta ta hakura da aikin cikin ruwan sanyi. Ya kuma dubanta, shigarta tayi masa kyau matuka, ya karasa gabanta ya durkusa ya kai hannunsa kamar zai taba ta amman sai ya fasa domin bai son ta san ya dawo, don haka ya mike ya fice ya nufi Ofis din nasa can Deport na hotoro. Karfe shida saura ya dawo gidan, bai ji motsinta ba bai kuma nemeta ba, domin yana sauri ya tafi masallaci daga can ya biya ya gaida da iyayensa don kada yaki zuwa yayi laifi gurin Hajiya, domin ka'ida ne kullum sai yaje ya gaishe ta, sam kuma ya manta bai sanar da ita yau zai koma aiki ba. Ya dan jima a gidan nasu suna hira da Hajiyar tasa har ya ci abincin dare a can, sai wajen karfe goma ya iso gidan. Zainabu kam ta cika fam domin a tunaninta wani sabon salon wulakanci ne ya tsiro da shi, tana zaune a falo sanye take da wata doguwar riga ta shadda wacce ta kamata tsam daga kirjin ta, ta dora dauri tamkar gwargwaro, ga wani dankunne masu kyau da ta sanya sai kamshi take yi, kallo take yi amman hankalinta ba a can yake ba. Ya shigo da sallama da saurinsa don ya san yayi laifi, ta dago dara-daran idanuwanta tana kallonsa, sai kuma ta dauke idonta ta maidasu bisa TV, duk da akwai gajiya a tattare da shi sai da ya zauna kusa da ita.ya dubeta yana dan murmushi ya ce, "Madam tuba nake na yo dare, tun wajen shida na shigo banji motsinki ba, gashi ana ta kiraye-kirayen sallah don haka na wuce masallaci, da na fito kuma naje na gaida Hajiya don bata san na koma aiki yau ba, na san kin sha kadaici ko?" Ta yamutsa fuska gami da wani kada ido, abinda ya kuma kara mata kyau, ya mike, "Bari naje nayo wanka, ko zaki taya ni?" Ya dubeta yana dariya. Ta kauda kanta gefe cike da takaici, lallai ma ya raina mata wayo. Ya iso gabanta ya tsugunna ya kwantar da kai. "Haba zuma ta ki tayani wanka mana, kin shagwabani ba zan iya cuda bayana ba yanzu kinji ko?" Ta dubeshi kamar ta kwada masa mari yanda yake wani narke mata ta ce, "Don Allah Mustafa ka rabu da ni kada ka sanya zuciyata ta buga." Ta janye hannunta daga rikon da yayi mata. Ya kuma sanya dariya kana ya ce, "Shi kenan, bari na je na yo wankan don jikina har wani danko yake yi, sai na fito na lallashi zuciyar don idan ta buga nima tawa bugawa za ta yi." Ya nufi sashinsa yana murmushi, ta bishi da harara domin haushinsa take ji. Can ta mike ta shige dakinta ta fada wanka ta fito ta shirya kan ta kamar yanda ta saba, kamshi kamar a jikinta aka yi shi, ta sanya wata yaloluwar rigar bacci mai hade da diras, iyakacin mazaunanta ta tsaya, don haka kana ganin komai na jikinta, ta haye gadonta ta lumshe idanuwa har lokacin zuciyarta cike take da takaicin Mustafa.Ya shiga dakin yana duban ta, gaba daya sai ya ji dauriyarsa da fushinsa sun kare, daman shi fadan ya ishe shi don jiya bai yi baccin kirki ba, ba zai so yauma a kwata ba. Ya hau gadon yana mata magana "Sleeping beauty ba dai har kinyi bacci ba, kai zumata kada ki zamo raguwa mana, yanzu fa ko sha daya bata yi ba." Tana jinsa amman tayi masa bakam taki tankawa, domin ta lura rainin hankali zai mata irin na 'yan maza, sai sun gama kunsa maka bakin ciki da rana idan dare yayi kuma suce suna neman wani abu, kamar ba shine ya rufe ido dazu yayi mata rashin mutunci ba. Ya jawota jikinsa yana mata wani salo da yake tsokano ta da shi yana fadin, "Haba Zainabu kada muyi haka da ke, na zo kaina bisa wuya tuba nake." Ta hankade shi gefe tana fadin, "Don Allah ka rabu dani, wai me ka maida ni ne? Ko ka manta abinda ka yi min dazu ne, ka kyaleni kawai kowa yayi harkarsa." Ya kuma matsawa jikinta yana mata salonsa da yake sace zuciyarta tun a can baya, cikin kunnenta yake magana, "Haba Zainabu, ki yi hakuri tawan mu bar fadan haka ya isa, dauriya ta wallahi ta kare da kyar na iya bacci daran jiya, ni dai na yadda makaman, ki bari daga baya mayi maganar aikin." Yanda yake maganar kamar rada da kuma salon da yake mata ya sanya ta gaza hankade shi, don haka cikin shagwaba take magana, "Ni dai gaskiya ka rabu dani, bayan kasan kai ne mai laifi sai kace ba ni ba dazu kamar zaka doke ni.....Haba dai duka, ni na isa na doki mai raina? Don Allah kiyi hakuri kaina bisa wuya, haba honey sweet din Musty." Yanda yake maganar gaba daya ya gama kashe mata jiki, don haka dole ta share ta fara gwada masa lallai itama tayi kewar sa, nan suka lalace. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 ************** Da wayo da dabara Mustafa ya hana Zainabu aiki, sai dai bai rageta da komai ba, don tafi wata mai yin aikin ma, sannan ya bude mata katuwar super market da sunanta, haka nan ya bata jari mai dama ta fara kasuwanci. Don haka ta kwantar da hankalinta tayi zaman ta a gida domin ta lura sam bai kaunar ta fita ko ina, sai dai kawayenta dake sintiri a gidan, don Asma kusan kullum tana gidan har tana sha'awar inama ace ita ce ta sami irin wannan rayuwar ta Zainabu. Ranar wata Juma'a da asuba suna kwance makale da juna wayar Mustafa ta fara kira, da azama ya dauka domin ya san kiran Momin sa ne, ai kuwa ita ce din, hankalinsa a tashe ya ce, "Yaya dai Momi lafiya ko?" "Ka hanzarta zuwa Alhaji ba shi da lafiya, ciwonsa ya tashi don jiya ba mu yi bacci ba....Innalillahi wa inna ilaihi raji'un." Kawai ya ce sannan ya ajiye wayar ya hau saka kayansa. Zainabu da ta tashi firgigit don jin salatinsa ta yi kansa tana tambayarsa abinda ya faru. Cikin tashin hankali ya ce mata, "Zainabu ciwon Alhajin mu ne ya tashi don dama yana da ciwon hanta." Ita ma ta shiga firgici sosai, har harabar da ake ajiye motoci ta raka shi, sai da taga ya fita daga gate din gidan sannan ta dawo cikin gida cike da fargaba. Shi kuwa yana isa suka sanya Baban nasa a mota sai asibitin Malam Aminu Kano, kai tsaye A & E dakin gaggawa aka shigar da shi,sanda suka yi hoton cikin abin ya tsorata likitocin, domin hantar ta shi ta kuma kamuwa fiye da da can, nan fa suka fara kokarin samo kan ciwon, sai da suka ga ya samu bacci sannan suka kyale shi. Hajiya Kubra da Mustafa dai suna waje hankalinsu ya kai kololuwar ta shi, sai da aka tabbatar musu ya samu bacci sannan suka sami kwanciyar hankali, daga nan aka sake masa daki zuwa Aminity, aka bashi kwanciya. Wajejen karfe tara asibitin ya cika da 'ya'ya da 'yan uwa, duk da an hana kowa shiga gurinsa, Mustafa ya samu ya koma gida domin yayo wanka. Ya samu Zainabu har lokacin bata cire kayan baccin ta ba, yana shiga ta tashi da sauri ta tare shi ta rike shi gam a jikinta tana tambayarsa jikin Alhajin nasu. Har ransa ya ji dadin kulawarta ga mahaifinsa, cikin kwantar da hankali ya sanar da ita ya sami sauki, ya ce wanka ma ya dawo ya yi. Bata sake shi ba ta ce, "Bari naje na taimaka maka sai mu wuce asibitin tare." Wajen karfe goma sha daya suka nufi asibitin, Zainabu tayi dan girkinta na dubiya, sai dai kirjinta yana ta bugawa, domin yau ne zasu yi ido biyu da Hajiya Kubra tun bayan da ta auri danta. Sun isa asibitin cike yake har lokacin da jama'a, duk yawanci suna waje gindin bishiya sun shimfida kafet, ya isa tana biye da shi a baya. Tun da Hajiya Kubra ta hango Zainabu ranta yayi mummunan baci, ta bata rai matuka don haka ko da ta karaso gurin ta gaisheta bata ko kalleta ba balle ta amsa, su Hajiya Saratu kuwa har sun fita hade rai, don har tsaki ta saki ta kauda kai gefe. Ran Zainabu yayi matukar baci, don ta manta rabon da ayi mata wulakanci irin wannan, shi da kansa Mustafa kunya ta kama shi kamar kasa ta tsage ya shiga ciki yake ji, amman yaya ya iya tunda dai iyayansa ne. Kanwarsa Sumayya ce ta ce, "Anti ga guri ki zauna mana." Domin dai ko gurin zama ba'a bata ba. Su Hajiya Saratu sai aka sake babin hira tana ta aibata mata wai masu bin maza don talauci, kowa a gurin ya fuskanci inda zancen nata ya sanya gaba, don haka babu wanda ya kulata illa Hajiya Kubra da taji ranta yayi wasai domin dai ta san da Zainabu take. Ita kam Zainabu ji take yi kamar ta tashi tayi musu rashin mutunci, sai dai darajar Mustafa zata iya hakuri da duk wani cin kashi da za'a yi mata, don haka ta dukar da kanta kawai tana wasa da yatsunta, shi kuwa Mustafa gurin likitan ya wuce domin yaji yaya jikin Baban nasa yake, amman dai daurewa kawai yayi ya tafi ya bar Zainabu a nan gurin. Sai da suka yi awa uku babu wanda yace da kowa kala sai dai 'yan matan Hajiya dake jan Zainabu da hira domin su janye hankalinta daga kan su Hajiya Saratu. Ta yi kokarin biye musu amman hankalinta gaba daya yana kan su Hajiyan, domin dai duk abinda Hajiya Saratu ke fadi ta san da ita take. Dawowarsa ya sanya taji dan dama-dama, domin cewa yayi ta tashi ya maidata gida ya dawo, kamar wacce ke kan kaya don haka ta mike da saurinta ta ce, "To Hajiya mun tafi Allah ya kara sauki." Ba su tanka mata ba har lokacin, har sun dan fara tafiya Hajiya Kubra ta kirawo Mustafa ya dawo ya durkusa a gabanta.Da daga murya ta kama yi masa fada, "Bance maka kada ka sake ka kawo matar ka duk inda nake ba? Ko ka manta da kashedi na ne, eye? To tsaya kaji na gaya maka har yanzu wannan dokar tana nan, don haka bana bukatar na kara ganinta a asibitin nan, idan kuma ka kuma zuwa da ita to kai ka jawa kanka ko me nayi mata." Ya mike jikinsa babu kwari ransa idan yayi dubu duk ya baci, domin dai yasan sarai Zainabu taji duk abinda Hajiyar ke fada, da kyar yake iya daga kafarsa, takunsa na uku ya kuma jiyo maganarta. "Kai, wannan warmers din wa kuka kawo wa? To ka dauki abincin ka domin wallahi ba zamu ci ba, sai dai mu zubawa karnuka." Ya juyo ya durkusa ya dauki warmers din ya nufi mota, ta ja tsaki tana fadin, "Gayyar tsiya arna da idi, haka kawai ina fama da ciwon mijina yazo ya kuma bata mini rai." Har suka isa gida babu wanda ya ce da dan uwansa kala, shi ya rasa me zai ce mata, dama ba a gabanta ta fadi maganganun ba to da sauki, domin sai yasan dabarar da zai yi ya hanata zuwa asibitin amman yanzu aikin gama ya riga ya gama, domin anyi a gabanta taji, don haka bashi da sauran hanyar kariya ko wani boye-boye, shi kunyarta ma yake ji wallahi. Sanda suka isa gida tun bai gama fakin ba ta balle murfin motar ta fice, ya bita da kallo kamar ya kirawota amman sai ya fasa ya kifa kansa kawai bisa sitiyarin yayi shiru yana sake- sake, kusan minti ashirin yayi a haka sannan ya nufi cikin gida.Shiru falon babu kowa don haka kai tsaye ya wuce cikin daki, sai ya taddata ta kunna taba tana sha, duk tayi facali da kayan jikinta daga ita sai dan siket iyakar cinya da rigar mama, sai busa hayaki take yi tamkar wacce ke shirin tada karamin hadari ko ta sami tabin hankali. Gabansa ya yanke ya fadi domin dai yayi zaton ta daina shan taba, amman sai gashi yau ya gani da idonsa. Hankalinsa ya tashi matuka, don haka yana isa ya kwace tabar dake hannunta ya sanya bisa (ash tray) ya kashe. Ta dago idonta da ya sauya kala ta dalla masa harara kana ta zaro tabar ibilis (wiwi) a jakarta ta kunnan ta fara zuka. Ya kuma hasala ainun domin dai bai san ta inda ta samo wadannan abubuwa ba. "Ke Zainabu kinyi hauka ne?" Ya fada a hasale. Ta daga ido ta kuma wurga masa harara, ya kai hannu zai kwace tabar shaidan din amman bata yadda ba sai ma daga masa hannu da tayi tana fadin, "Enough, ya ishe ka haka." "Akan me zan yadda ki sha abinda zai cutar da ke, ke ko kunya ba zaki ji ba ki zo tsakiyar dakinki na aure kina shaye-shaye, eye?" Ta mike a kufule tana nuna shi da yatsa tana fadin, "Malam ya ishe ka ka rabu dani, dame kake so naji ne, eye? Iyayenka sun bata mini rai kace ba zan sha abinda zai sanyaya mini zuciya ba?" "Wallahi ka sani, wannan matar Hajiya Saratu naji suna fada ko wa, taci darajar aure da wallahi yau san nayi mata rashin mutunci, shegiya matsiyaciya, ko ta zaci ban san ta bane, ai duk wasu manyan gwamnati samarinta ne duk da tana takama da aure, kuma duk wanda zai bata kwangila sai ta bashi kanta, ko diyar ta ba tana can kasar waje tana karatu da karuwanci ba.....ya ishe ki Zainabu, kina son ki bata mini rai da yawa ne eye?" Ya katseta cikin hargowa. Ta rike kugu tana girgiza gami da fadin, "Lallai ka dade ranka bai baci ba, domin ni ai daga bola aka tsintoni shi ya sanya da ta zageni baka rama mini ba, banza karuwar gida wacce ke bin maza da aurenta da 'ya'yan ta.....Ya dauketa da wani wawan mari wanda ya sanya ta zube bisa gado, ta mike da azama tana kokarin kamo rigarsa, ya kuma hanbareta ta fadi bisa tsakiyar gado, ya kuma hasala sosai. Cikin bacin rai yake fadin, "Duk lalacewar dangina ina sonsu, don haka idan kinga zaki iya hakura da abinda suka yi miki to idan ba zaki iya ba kiyi abinda kika ga dama amman ba zan lamunci cin mutunci ba wallahi." Ta dago da jan ido tana dubansa ta ce, "Wallahi Mustafa zaka san ka mareni, kuma ko zaka kashe ni ba zan daina cewa Hajiya Saratu karuwar gida da aure ba, sannan kai ma da suke zagina a kanka ai dan iskan ne, kuma taba da wiwi yanzu na fara sha domin dai kai ne ka koya mini, idan ka kuma tabani kuma wallahi ka doki aurenka domin baka auri jaka 'yar iska ba." (Fauza tace tsiyar auren bariki kenan babu daraja balle mutunta juna). Maganarta ta karshe ce ta sanya ya tsaya sororo ya kasa aiwatar da komai a kanta, sai dai jikinsa sai kyarma yake yi, kawai sai ya juya ya bar dakin ya shige dakinsa ya fada bisa gado ransa na suya, gaba daya yau sun bata masa rai, wai shin da me zaiji ne da rashin lafiyar mahaifinsa ko kuma da fitinarsu? Da kyar ya iya yin wanka ya ci abincin dake cikin warmer din ya fita daga gidan. Ita kuwa kullo kanta tai cikin daki ta fara cakewarta abinta. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Har dare da ya dawo bai ganta ba, bai neme ta ba domin ransa a bace yake har lokacin, sai da safe ne ma da ya tashi yaji yana kewarta don haka ya leka dakinta ya taddata ta ci kwalliya da wani wando fela da half vest tayi kyau matuka, kamar ya shareta sai ya takalo zance. "Ina breakfast, karin kumallo na?" Ta daga idonta wanda ke gigitashi idan tayi masa dubanta na yauki, idanuwan Zainabu na daya daga cikin abinda ke kashe masa lakar jikinsa, gasu da girma da kyau tsakiyarsu kamar an diga zaiba, musamman idan bata kora shandy ko ta sha tabar shaidan ba sunyi kyau matuka. Ta karkace kai gami da murguda dan karamin bakinta ta ce, "Ban yi ba ko da magana?" Abin ya bashi dariya domin ya lura masifa kawai take ji, shi kansa ya san ba karamin karfin hali tayi jiya ba dan sam bata tankawa Hajiya Saratu ba, shi abinda tafi bashi haushi tabar da ya tadda tana sha, domin da niyyar rarrashinta ya shigo daki, ta kuma kara da zagin kanwar mahaifiyarsa. Sai yayi dariya kawai ya ce, "Shi kenan naje na ci a hotel tun da ban da matsayin da za'a dafa mini a gidana." Bata tanka masa ba illa cigaba da tayi da sauya tashoshin tauraron dan Adam, ya juya ya ce, "Sai na dawo." Sai da yayi nisa ya jiyo muryarta tana cewa, "A yiwa Baba sannu da jiki." Ya ji dadi har ransa domin yasan lallai ta damu da ciwon tsohon nasa, don haka ya ce, "Zai ji Insha Allahi in dai ya farka zan sanar da shi." Sanda ya isa asibitin yayi sa'a jikin na sa yayi kyau don har yana gane mutane, ya isa ya zauna a gefen gadon yana gaishe shi.Alhaji Abdullahi yayi murmushi yana amsa gaisuwar dan nasa har yana tambayarsa Zainabu. Ya yi murmushi jin Alhajin na ambaton Zainabu, ya ce, "Ta ce ma a gaisheka jiya ai da ita muka zo lokacin kana bacci." Cikin ikon Allah da hukuncinsa randa ya cika sati guda a asibitin aka sallame shi, jiki yayi kyau sai dai an kafa masa tsauraran matakai na daina cin duk wani protein abinci mai gina jiki, kamar nama da kaza ka kwai soyayye da madara da hanta har sai ciwon ya lafa sosai. Gaba daya iyalansa sun sami kwanciyar hankali don ganin jikin Mahaifinsu yayi sauki, sai dai Mustafa wanda har lokacin Zainabu fushi take yi da shi, yayi yayi ya shawo kanta amman ya gaza. Yauma da kyar ya rarrafa ya kai karfe hudu a Ofis, kome yake yi Zainabu yake gani, sai yake ganin kamar ya shekara bai tare da ita ma, don haka ya hada komatsansa ya nufi gida. Tana zaune a falo sanye da wata doguwar shimi iyakacin gwiwa mai hannu irin siririn nan, ta kama ta tsam a kirjinta kamar rigar mama, kugun nan ya matsu tsam sai kuma ta bada fadi daga kasa, kan nan ya sha gyara ta yi parking dinsa da ribon duk da ba wani yawa ne da shi ba, sai wani kamshi ke tashi a falon na ta. Ya ajiye brief case dinsa ya fada kujera yana fadin, "Washi, na gaji wallahi." Ko kallonsa bata yi ba balle ya sanya ran zata yi masa magana, sai wani taunar cingam take kas- kas, wanda ke kuma tsokano shi. Ya dubeta sanda yaji wani abu ya tsaya masa a wuya ya ce, "Zainabu manyan mata, har yanzu ba'a huce bane? Tuba nake." Bata ce komai ba sai murguda baki kawai da ta yi, tana wani fari da ido abin da ya kara mata kyau. Ya ce lallai wannan yarinyar 'yar rainin wayo ce ke, kina nufin haka za muyi ta zama bari nazo nayi maganinki. Ya mike da azama tayi zaton zolayarta yake sai da taji ya makureta tayi tayi ta ture ta gaza, har mintsininsa tayi amman ko gezau, don haka ta kama yi masa kukan shagwaba wanda ya kuma tsokano shi, dole dai ta saki jiki ta nuna masa Zainabu tayi missing dinsa itama, wannan ne ya sanya suka shirya dole, don ya san ta yanda yake samo lagonta Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 *****BAYAN SHEKARU BIYU***** Aurensu yayi shekaru biyu har da wani abun amman ko batan wata Zainabu bata yi ba, abin har ya fara damunta, domin yanzu 'ya'yan Karimatu kanwarta guda uku, ga 'ya'yan gwanin sha'awa, sannan matar Sadiku ma ta haihu yaron har yayi wayo. Shi kansa Mustafa ya fara damuwa don haka ne ma suka fara yawon ziyartar likitoci, sai dai iyakacin gwaje-gwajen da aka yi musu ance shi kam bai da matsala sai dai ita ce ke da matsala amman an bata magunguna ta sha da zummar duk abinda ta gani ta koma. Duk da Hajiya bata shiga zancan sa da Zainabu yanzu ta fara yi masa gori, wai ya auro wacce ta karar da kwayoyin haihuwarta a titi gurin zubar da ciki, don haka ya shirya aure don ta kusa aura masa diyar mutunci wasu abubuwa ne kawai suka tsaida ta, don haka hankalinsa ya kuma tashi suka bazama neman haihuwa ido rufe. Ranar wata asabar ya tashi da wani mugun ciwon ciki, ya dinga kwara amai kamar ba zai yi ba, Zainabu tace a kai shi asibiti ya ce, A'a a yiwa likitansa waya kawai. Ai kuwa haka aka yi, yana zuwa ya sanya masa drip karin ruwa, sannan ya sanya masa allurar amai. Tana nan zaune tana gadin ruwan Sumayya ta yo mata waya akan tana neman wayar Mustafa, ko ya manta yau ne birthday din Zubaida diyar Hajiya Saratu da ya ce zasu je tare. Zainabu ta ce, "Ayya kin ganshi nan kwance babu lafiya ana masa karin ruwa." Hankalin Sumayya ya tashi tace gata nan zuwa. Suna gama wayar ta sanar da Hajiyarsu, duk da gabanta ya fadi amman sai ta tabe baki ta ce, "Allah ya sauwake" kawai. Ita kam Sumayya mota ta shiga ta taho dubasa. Sanda taje dubashi jikin nasa yayi dan dama- dama, don haka daga nan gurin birthday din ta wuce, a can take sanarwa da 'yan uwa abinda ya sami Mustafa. Ai kuwa ana tashi daga fati aka yo gayya zuwa duba Mustafa, ita ce motar karshe da Hajiya Saratu da suka taho da diyarta Zubaida, sanda suka iso sauran sun komawarsu gida. Suka zauna suna masa sannu, yana amsawa don lokacin ya farka. Zainabu ta shigo don daman tana kicin ne, tana sanye da atamfa super tayi mata wani dinki na daukar magana, ko mahassadi ya ga Zainabu sai ta burge shi, domin siket din ya zauna daram a kugun ta kamar sai da aka gwadata aka yi, wuyanta da kunnenta white gold ne kirar dubai ga warwaro kirar Saudiyya da ta sanya da zobuna, tayi kyau matuka sai kamshin nan nata take yi tamkar fure.Ta shigo dakin da sallama, ta dube su ta ce, "A'a sannunku da zuwa." Sumayya ce kawai ta amsa, Hajiya Saratu da Zubaida yamutsa fuska kawai suka yi. Ta zauna gefen Mustafa ta tallabo shi tana bashi fresh milk don ya ce ta bashi, bayan ta kashe ruwan sosai ta rungumeshi a jikinta ba da niyyar komai ba. Amman sai Hajiya Saratu ta kulu, domin ganin yanda Zainabu ta koma tamkar diyar sarki ya hasalata, babu wanda zai kalleta yace Abu ce diyar Sala da Baba Abbakar, don haka taja tsaki tana fadin, "Kai har yanzu Allah bai kawo 'yan dugwi-dugwi a gidanka ba, sai dai a cika maka masai da kashi." Zubaida tayi dariya ta ce, "To ke Momi banda rigima irin taki, yaushe uterus mahaifar da tayi condemn ta lalace zata iya haihuwa?, naji fa ance matar tasa sai da ta gama sheke ayarta sannan suka yi aure, kinga ai babu zancen haihuwa sai dai a hole kawai." Ran Zainabu idan yayi dubu ya baci, don haka ta janye fresh milk daga bakin Mustafa don kada ya kware bata gani ba, ta kwantar da shi ta saita karin ruwan kamar yanda likita ya nuna sannan ta gyara zama ta ce, "Kinsan shi gwano ai baya jin warin jikinsa, gwara wanda ya nemi 'yan uwansa bakar fata da wanda yake iskanci da turawa wadanda kowa ya sani duniya sune ke da kanjamau, kinga ni ai haihuwa ce kawai zan rasa, wata kuwa bayan rashin haihuwar har kanjamau ce da ita, don jiki ya nuna kiga mace tamkar sillan kara babu dan abin yanga, ai da gani da magana. Ran Hajiya Saratu da Zubaida ya baci matuka, ita kuwa Sumayya ji tayi Zainabu tayi mata daidai domin dai ta tsani Zubaida da halayenta daman, su kuwa sam basu taba sanin Zainabu ta san sirrin su ba, don haka Hajiya ta kuma hasala. Ta mike tsaye tana nuna Zainabu da yatsa tana surfa mata ruwan bala'i da gori tana fadin, "Ke wallahi hawainiyarki ta kiyayi rama ta, shegiya 'yar matsiyata 'yar tallan shinkafa da wake. Ke banda kaddara me Mustafa zai yi dake, an gama yawan gantali bin tasha-tasha tallan goro da rogo, duk samarin kasuwa sun gama kwakularki, wallahi idan kika yi wasa zan miki abinda har ki mutu ba zaki manta ba, ko kina zaton bamu san asalin balbela bane, su tsoho ana can gindin bishiya ana maula da bara, su Inna kuma ana gindin murhu suyar gyada da wake da shinkafa ana dorawa kanne su ma ana kwakulesu a shaguna, an dai yi asara." Ran Zainabu idan yayi dubu ya baci, hankalinta ya tashi, Mustafa dake kwance cewa yake, "Zainabu don girman Allah kiyi hakuri ki rabu dasu, zan sanar da Baba duk abinda suka yi miki." Amman ina shi kansa ya san ko kusa ba zata kyale ba, don haka ta mike tsaye tana huci ta ce, "Kaga Malam babu ruwanka ai Uba baifi Uba ba, kuma uwa bata fi uwa ba, balle kai kanwar Uwarka ce." Ta maida dubanta ga Hajiya Saratu tana fadin "Alhamdulillah, don duk wanda zaice Zainabu tayi iskanci sai dai yace tayi kafin aure, amman a yanzu ina zaune zaman aure sunna zuciyata da gangar jikina sun gyaru, ke kuwa da waye bai san abinda kike yi ba da yawon siyasarki da ake kwana dake a hotel da kuma yawon kwangilarki da sai anyi fasikanci dake sannan za'a baki kwangila da aurenki kuma, wa ma ya sani ko duk 'ya'yan naki na kwangilar nema.....""Kan ubancan, dan abu ta kazar ubanki ni zaki yiwa sharri? wallahi yau sai kinci ubanki." Ta ci damara ta nufi Zainabu gadan-gadan. Mustafa da yaga abin zai baci ya fincike karin ruwan ya shiga tsakani yana baiwa Hajiya Saratu hakuri wacce tunda take ba'a taba mata irin wannan cin mutuncin ba, bata san yanda aka yi Zainabu ta san sirrinsu haka ba. Ita ma Zubaida da ta kama zage-zage tana fadin wallahi yau sai sunci uban Zainabu, Sumayya ce ke janyeta, ita ma Zainabu bakinta bai mutu ba, sai da Mustafa ya turata a daki ya kulle sannan su Hajiya Saratu suka fice tana fadin wallahi ba zata yadda ba don tasan shine ya sanar da matarsa sirrinta har take mata gori. Ya bita yana rantsuwa har yana fadin, "Hajiya yanda kika samo sirrinta ban sani ba itama haka ta samo naki babu hannuna, don wallahi ni ban taba jin wannan zancen ba ma sai yau." Bata bi ta kansa ba suka shige mota Sumayya na tuka su. Kai tsaye gidan Hajiya Kubra suka shiga ta fasa ihu tana fadin Wallahi kotu ce zata raba ta da Zainabu matar Mustafa, tunda tace duk 'ya'yanta har wadanda suka mutu shegu ne basu da uba, bayan kowa ya san Ubansu. Hajiya Kubra ta tareta hankalinta a tashe, domin dai sam bata fahimci abinda take nufi ba. Nan ka kwashe karya da gaskiya ta fadi, sannan ta ce wai kawai dan sunje dubashi basu kulata ba ta kama gaya mata wadannan maganganu, tana fadi tana kuka, domin abin yayi mata ciwo matuka, daman 'yan magana na cewa idan baki ya san abinda zai fada bai san abinda za'a mai da masa ba. Sumayya da aka yi komai a gabanta ta ce, "A'a Anti Saratu gaskiya ba haka aka yi ba, Momi wallahi ita ce ta fara....." "Au! Kema kina bayansu? Daman nasan daman Kubra kece kike sanya 'ya'yanki su yi mini rashin kunya." Hajiya Saratu ta katse ta, itama ta ce "A'a Hajiya ba haka....." "Rufe mini baki, kina nufin 'yar iskar yarinyar nan ba zata yi abinda aka ce tayi ba?" Ta kalli Hajiya Saratu tana cigaba da fadin, "Saratu ko me aka ce matar Baba tayi wallahi zan yadda, tun da bake ba ni kaina yarinyar nan ta zageni, yanzu ma abinda ya sanya take rangwanta mini don taga tana auren dana ne, sai dai wallahi ba zan kyaleta ta ci miki mutunci ba, don ke 'yar uwata ce uwa daya uba daya, ki zo muje gidan ki ga abinda zan yi, zan rama miki abinda tayi miki." Sumayya ta dafe kai cike da tashin hankali, don bata san abinda zai faru ba. Shi kuwa Mustafa da ya ga su Hajiya Saratu sun fice ya nufi dakin da ya kulle Zainabu ya bude ya tadda ta tsaye tana huci tamkar kumurci. Ya galla mata harara yana fadin, "Kin kyauta Zainabu, yanzu ko don ganin halin da nake ciki ba zai sanya ki yi hakuri ba? Yanzu na tabbatar lallai baki so na.....In dai a zagi iyayena na kyale shine so to ban sonka kai tsaye kaji na gaya maka Mustafa. Wallahi don na zauna da kai ba zan yadda a ciwa iyayena mutunci ba don duk lalacewarsu sune suka haife ni, na kuma gaya maka duk shegiyar matar da ta kuma zagin iyayena a gidan nan ko gemunta na jan kasa don girma sai na dake ta, aure hauka ne? Nayi kama da wacce zan zauna akan namiji ana gasa ni, ka sani zan iya rabuwa da kai in dai akan Baba Abbakar ne da Sala,domin su ne suka kawo ni duniyar da har ka ganni ka aura. Don haka idan har kana son zama da ni dole ka kare darajar Iyaye na, Ni Zainabu ka aura don haka wanda ya ga dama ya zageni yace mini karuwa zan iya hakura idan na so, sai dai duk wanda ya zagi Sala da Baba Abbakar sai inda karfina ya kare wallahi." Maganganunta suka kashe masa jiki, ya sani tun can baya Zainabu mai son iyayenta ce, kuma bata yadda da duk abinda zai taba mutuncin iyayen nata ba, don haka yaga bashi da abinda zai kuma cewa illa ya fice daga dakin, don kansa ya soma juyawa. Yana zama a falo ya jiyo shigowar mutane, kafin ya ankara har sun bayyana a falon. Hajiya Kubra da Hajiya Saratu da Zubaida ne, hankalinsa ya kai kololuwar tashi. Ko zama basu yi ba Hajiya Kubra ta fara surfa fada, "To sallamamme wanda aka asirce, to tsaya kaji idan Zainabu ta asirce ka ka kasa katabus a kanta ni wallahi sam baka isa ba, domin ban hada 'yan uwana da kowa ba." Hargowar Hajiya ta jawo hankalin Zainabu ta fito falon. Ko dar bata ji a jikinta ba don dai tasan karshen abin dai bai wuce ace ya sake ta ba. Muryar Hajiya Kubra ta cigaba da karade falon, "Don haka in dai ni ce Hadiza Kubra na haifeka to yanzu ka rabu da yarinyar nan!" Gumi ya fara karyowa Mustafa, ya ma rasa mai zai ce yaji dadi a zuciyarsa, ya kalli ina Zainabu ke tsaye yaga ko a jikinta itama, ya kalli iyayan nasa da suka tsare shi da ido, kawai sai ya dauko biro da wata (jotter) dake kan TV ya rubutawa Zainabu saki daya ya mika mata. Ta amsa shekeke tana fadi, "Wallahi tafi nono fari. Su Hajiya Saratu zasu kuma yin magana Hajiya Kubra ta ce, "Kinga magana ta kare ku wuce mu tafi." Babu musu suka wuce domin dai ta nunawa Zainabu sun isa. Zainabu ta hada kayanta a trolley ta zuba a motarta ta nufi gidan Asma, don da kunya ta nufi gidansu ta ce Mustafa ya sake ta. Shi kuwa daki ya shige ya dafe kansa tamkar wanda wani na shi ya mutu, ji yake kamar jin dadin rayuwarsa ya kare tunda ya rabu da Zainabu, ya rasa wane irin so yake yiwa Zainabu a rayuwarsa ma. Rabon da ya sha wani abin maye har ya manta, baya ga taba yanzu babu abinda yake sha tun da Mahaifinsa ya taba kama shi dumu-dumu da kayan maye, ya ga bacin rai wanda bai taba gani daga gurin Mahaifin nasa ba tunda ya zo duniya, daga karshe ya ce yayi masa alkawarin ba zai kuma shan wani abu na sanya maye ba ya yi masa alkawarin, amman banda haka babu abinda zai hana shi yau ya kora shandy ko wisky, don haka taba kawai ya dauko ya dinga sha kamar wanda aka yiwa gorin ta. Su Sumayya da Zainab kam suna gida hankalinsu a tashe yake, domin sun san ba za'a yi mai dadi a gidan Yayan nasu ba, ai kuwa da su Hajiya suka dawo suka ji abinda ya faru sun girgiza, sai da suka kebe a daki ne ma Zainab ta kalli Zubaida tana fadin, "Zubaida kin san wani abu? Wallahi wannan sakin auran da yaya Mustafa ya yiwa Anti Zainabu kunyi aikin banza, don wallahi komai dadewa sai sun koma, domin na dade ban ji irin soyayyar su ba ko da a film ko a littafi balle a gaske." Zubaida ta kuma hasala, gashi daman basa shiri da Zainab, domin ita diyar kanin Alhaji Abdullahi ce uwa daya uba daya, kuma halinsu sam bai zo daya ba, don haka ta rike kugu tana fadin, "Oho dai su suka sani koma meye, tunda dai an bata red card ai ni burina ya cika wallahi, kune daman ai 'yan kanzaginta." Sumayya ta ce, "Gaskiya Zainab ta gaya miki, kije ki rubuta cikin diary dinki zaki sha mamaki wata rana." Zubaida tayi tsaki kawai ta bar dakin don daman ta san halinsu daya da Zainab da Sumayya, babu wanda ya isa ya shiga tsakaninsu. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Sanda ta isa gidan Asma tana falo a kwance bisa doguwar kujera tana waya da wani saurayinta. Ta shiga gami da wurgar da jakarta can gefe guda ta kayan. Asma ta mike cike da mamaki a fuskarta, tayi kokarin sallamar wanda suke hirar sannan ta ce, "Zainabu me ya faru, kin ganki kamar wacce aka koro." Ta ja tsaki gami da mika mata takardar sakin da Mustafa ya bata. Asma ta karba da sauri tana karantawa, ta dago kai a razane ta ce, "Zainabu da gaske kike Mustafa ya baki saki? Kai ban yarda ba, kina son kice mini duk son da yake gwada miki ya kare?" Ta lumshe ido kamar ba za ta ce komai ba, can dai ta tasahi zaune sosai ta kwashe duk abinda ya faru ta sanarwa da Asma. Asma ta banka wani zagi tana fadin, "Lallai wadannan mutanen basu da mutunci, wato gwano baya jin warin jikinsa, yarinyar da kike fada Zubaida ba bu iskancin da bata yi a garin nan, duk gayun garin nan sun san da zamanta, don daran jiya ma sai da na ganta a night club wai ana birthday dinta, lallai na sani Mustafa zai kawo kanshi ki kwantar da hankalinki 'yar uwa. Zainabu ta yamutsa fuska gami da yin kwafa sannan ta ce, "Asma kin san Allah tun da aka zagi iyayena naji auran Mustafa ya fita daga raina, domin nasan da haka kawai ya sake ni sai nayi ciwon zuciya saboda son sa da nake yi amman yanzu ko dar ban ji ba, kawai zan gyara gidan da na siya kwanaki na koma can da zama don ba zan koma gidanmu ba sai Sala tayi mini dariya da gori." Asma ta ce, "Haba Zainabu ki bar fadin haka ma don nasan dole Mustafa zai nemeki ki bashi one week sati guda ki gani......." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Zaharaddeen Shomar whatsapp 08168575100 Idan Zuciya Tagyaru2-04 Posted by ANaM Dorayi on 07:37 AM, 12-Feb-16 Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU ______________ Na ________Fauziyya D Sulaiman_____ Book 2 page 4 "Kinga barni da zancen nan Asma, idan kina da shandy bani na tsotsa ko na rage bacin raina. Kwanaki biyu suka yi Mustafa bai cikin hayyacinsa, don bai san yana son Zainabu ba ma sai yansu, gashi Alhajinsu bai nan da zai shawo masa kan Hajiyarsa don ta dauki zafi da yawa, daman yaya lafiyar kura balle tayi hakua, don daman Zainabu a wuyan ta take. Ranar da ta cika kwanaki uku ya gaza hakuri sai gashi a kofar gidansu da karfe takwas na dare, Ya yi sa'a yana yin parking kaninta Ilu na fitowa daga gidan, don haka ya kirawo shi. Yaron ya taho da gudu don ya gane ko waye, tun bai kai ga magana ba Ila ya fara magana "Laa yanzu Anti Karima ta dawo daga gidanku ance Anti bata nan wai ta tafi unguwa kwanaki biyu." Ya ji maganar wani iri don haka ya ce da Ila "Bata zo nan ba kenan yau?Ya ce "Eh ta dade bata zo gidan mu ba ma, kuma naji Anti Karima tayi mata waya ma tace wayar ta a rufe take." Yayi shiru yana tunanin inda Zainabu ta tafi, amman sai ya tuno da gidan Asma don haka ya raya lallai tana can don haka kai tsaye ya nufi gidan Asma din. Kai tsaye ya shiga da motarsa har cikin gidan yayi parkinga saboda mai gadin nata ya san shi daman, ya nufi falon kai tsaye ya bude ya shiga, a falo ya ganta zaune ita kadai sanye da dogon siket da riga da ta kama jikinta ya shiga da sallamarsa. Ta daga kai tana kallonsa ta tsaya da shan fate din da take yi da cokali, ko me ta tuna kuma sai ta kauda kanta gefe ta cigaba da kallonta. Ya isa ya zauna a gefenta ta kuma matsawa gefe, ya kuma matsawa har suka dangana da karshen kujera, yayi murmushi ya ce, "To mun kai karshe sai yaya Zainabu." Sai kuwa ta mike ta bar masa kujerar ta koma wata, ya kuma tashi ya bita, ta hasala matuka don haka ta kuma mikewa da zummar barin falon, ya riko hannunta gam, tayi- tayi ta kwace amman ta kasa, ta juya fuskarta tana harararsa, yayin da shi kuma yake mata murmushi gami da mayataccen kallon nasa. Ta kuma hasala don tana ganin rainin wayo ma yake shirin yi mata, da zafin rai ta ce, "Malam ka sake ni ko ka manta ni ba matar ka bace yanzu, ka fita daga harkata." Ya saki dariya gami da jawota ta fada jikinsa, sai ta kama kokarin kwacewa amman ta kasa, cikin kunnenta yake magana "Zainabu har yanzu ai ke matata ce, tun da dai saki daya nayi miki, sannan baki kammala idda ba, yanzu haka ma na maida ke dakinki, kinga magana ta kare kenan.""Ba zai yiwu ba Mustafa kama janye wannan magana, domin dai na gama auranka har abada, haka kawai zan zauna ana wulakanta mini iyaye? Da kuma kake cewa ka maidani yaya zaka yi da Mahaifiyarka tunda ita ce ta baka umurni ka sakeni?, kasan ta ji wannan maganar ma ba za ta yadda ba." "Zainabu abin da ya kawo ni kenan, don Allah ki fahimce ni, wallahi kina da girma a zuciyata ba zan iya rabuwa da ke ba, ki dubi kwanaki uku kacal yanda na koma, balle ace rabuwa ce ta din-din- din, na yanke shawarar zan mai dake dakinki ki zauna a gidana na farm center, idan Baba ya dawo zan sanar da shi kuma nasan shi zai shawo kanta Insha Allah, please Zainabu kada kice a'a, kin san ina sonki da yawa." Yanda yake maganar cikin kunnenta da sanyi da taushi da kuma salon da yake gwada mata ya sanya ta kasa kwacewa, jikinta ya mutu amman har lokacin bata yadda da batun sa ba, shi da kansa ya lura da hakan. Ya kuma riketa gam yana cigaba da fadin, "Haba zuma (honey), ki na gani zamu yadda mahassada su yi galaba a kanmu? Wallahi tun can daman Hajiya Saratu bata kaunata, ita kanta Momi ba sonta take yi ba, banda hassada da kyashi babu komai cikin ranta, don ba sosai suke shiri da Momi ba, abin ne aka yi shi kan gaba don Momi daman bata son aurenmu, idan kika yadda muka rabu za su yi mana dariya don sunyi galaba a kanmu kenan, kada ki ce a'a Zainabu." Kalaman nasa sunyi tasiri a zuciyarta, don haka ta kwanta lamo a jikinsa yana shafata tamkar diyar mage. Ya kuma kai bakinsa daidai kunnenta yana fadin, "Please Zainabu say something, ki yi hakuri Zainabu ki ce wani abu. Muryarta da sanyi ta fara magana, "Mustafa ka sani bana son wulakanci ko kadan, da ace Mahaifiyarka ce ta yi mini wannan cin mutuncin zan iya hakura, domin nasan ita ta kamani da laifuka da na cancanta haka a gunta, sannan ita mace ce kamila dole zata kyamaci irinmu, amman wata can Hajiya Saratu wacce ta fini iskanci daga ita har diyar ta....." Ya toshe mata baki yana fadin, "Ya wuce don Allah ki manta da ita, zan dauki mataki mai kyau a kanta Insha Allah." Bata ce komai ba tayi shiru domin dai ta huce din, don itama cikin kwanakin nan uku tayi rashin zumarta Musty, daurewa kawai take yi, musamman idan Asma ta tafi tabar mata gidan sai taji yayi mata fadi, ta yi kallo har ta gaji, ko abinci take ci sai Mustafa ya fado mata. Da dai ya lura ta sakko din ya fara nuna mata lallai yayi rashin ta din da gaske, bata yi sanya ba don ya san Zainabu babu wasa, ta shiga mai da masa martaninsa, a nan gidan ya kwana domin Asma bata nan. Da safe ne da ya gama shiri bayan ya karya ya ce ta shirya da yamma idan ya taso daga Ofis zai zo su wuce gidan na sa, zai sanya a gyara shi kafin yamma, tana makale da shi har jikin mota tana masa salon dake kokarin hana shi fita, sun dade a jikin mota can ya ce, "Anya kuwa Zainabu ba zan fasa zuwa Ofis din nan ba kuwa yau?" Ta kwantar da kai tana dariya ta ce, "Haba dai, ina nan ina jiranka har ka dawo, babu mai gutsirar maka ni, zaka same ni guda." Suka yi dariya gaba dayansu, ta bude masa motar ta tura shi tana fadin, "A dawo lafiya mai rai na."Ya yi dariya ya ce, "Zainabu kin gama da ni, sai na dawo." Sai da motar ta bacewa ganinta sannan ta koma cikin gidan, wani nishadi da soyayyar Mustafa ke bijiro mata, sai take ganin tayi wauta da can da take cewa zata rabu da shi, ta san ko ta baru da shi son sa da soyayyarsa ba zasu bari tayi wata mu'amala da wani namiji ba, domin shi ne namiji kwallin kwal da ya santa ya iya tafiyar da ita da soyayyarsa da lallashi. Haka nan ta wuni har rana ta yi tana tunanin Mustafa da soyayyarsa har Asma ta shigo daga yawonta. Zainabu ta galla mata harara don ganinta a wani birkice ta ce, "Kai Asma Allah ya shirya ki, ya dace wallahi ki hakura da iskanci ki yi aure, duk lalacewar aure yafi wannan iskanci da kike yi wallahi." Asma ta yadda jaka bisa kujera tana fadin, "Wash Allah na, wallahi duk jikina ciwo yake." "Ba dole ki yi ciwon jiki ba kinje katon banza ya lugwigwita ki kwana da yini....." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Asma ta fashe da dariya tana fadin, "Shegiya don Allah ya tsamar dake zaki dinga mini gori, wa kike zaton zai aure ni da gaskiya yanzu kamar yanda kika samu? Kuma ni ba abunda kike nufi ne ya gajiyar da ni ba illa damben da muka ci da shegen dan iskan, ke yanzu har kin manta da naki iskancin da kika yi ko?" Zainabu ta kuta ta ce, "Wallahi kin san ko da nayi yawo babu shegen namijin da ya isa na zauna yayi ta lugwigwita ni kwana da yini, kin san sai na ga dama, kuma lokacina a kayyade yake, idan kuma na washeka ko dubu nawa zaka bani baka isa na kuma mu'amala da kai ba, ya dace ki yiwa kanki fada ki zama International karuwa ba local ba shine za kiyi daraja, ki duba yanda kika wani birkice kamar wacce tayi kwanaki tana jinya, mutum daya kacal ya more ki a banza da wofi." Ta ja tsaki gami da yarfe hannu ta ce, "Malama na fa gaya miki ba wannan ne ya wahalar da ni ba, dokuwa muka yi da shege dan rainin wayo, kai karuwanci masifa ne, shege dan akuya da matarsa ce yayi mata haka? Ashe na gaya miki ba ni kadai ce a gidan ba da wata a wani daki, idan ya fita daga guna sai ya shiga gurinta, a dare daya fa don jaraba da masifa, daga karshe da ya fice nace bari na leka naga me yake yi ne yace mini wai wisky yake shawowa kawai, sai naga ya shiga wani daki ina shiga na ganshi da wata shegiya, kishi da haushi ya cika ni don ban sani ba ko tana da shegiyar HIV, don irin kucakan nan ne wallahi baki ganta ba sai kin zubda yawu, shine fa da na kulu na kwala masa wata flower vase a gaban goshinsa. Bai ji ciwo ba amman dan jaraba sai yayi kaina da duka yana kuma dura mini zagi, nan fa ya kama duka na kamar ya sami jaka, da naga zai halaka ni na daga wani glass na maka masa a kansa sai ga jini ya tsinke, ashe shegiyyar da taga muna fada ta kirawo police 'yan sanda don kin san lambarsu yanzu available take, sai ta gudu abinta, suna zuwa suka taddamu a haka shine fa suka kwashe mu a daran nan sai police station. Daga can aka kaishi chemist dakin bada magani, har dinki aka yi masa sannan aka dawo da shi muka kwana a bayan kanta...""Shi yafi damuwa domin dan iskan yana gudun kada iyalansa su ji don haka ya dinga roko 'yan sandan su kashe case din anan kada su kaimu kotu kamar yanda suka ce, ni kuwa wallahi ko a jikina tunda na san bariki na fito ba karatun allo ba balle ace nayi abun kunya. Daga karshe dai sai da suka caje shi dubu dari, jiki yana rawa ya bada, da suka dawo kaina nace a'a nan fa daya ni ko kudina ma bai biyani ba, da dai suka ga zan musu tijara don sun san kar ta san kar ne suma din shegune suka sake mu tare. Shine na koma gidansa muka kama wata rigimar wai ba zai bani komai ba don naji masa ciwo, yanzu shi bai san me zaice da iyalansa ba. Da na lura munafuki ne mai tsoron matansa na ce wallahi idan bai bani ba kuwa har tsakar gidansa zanje nayi masa tijara, shine dan iskan ya wurgo mini dubu ashirin, kamar kada na karba amman ganin yamma ta yi ga yunwa ina ji ya sanya na kyale shi shege dan akuya, kinga gobe ai ba zai kara ba." Zainabu tayi tsaki tana fadin, "To don Allah meye abin riba anan yanzu? Kin san Allah ni yanzu ko rabuwa nayi da Mustafa wallahi ba zan kuma wannan mummunar harkar ba, don kina ganin Tinda da Zara yanda kanjamau ta maidasu yanzu ko a gidansu babu mai kulasu balle bariki da bata da amana, kowa gudunsu yake yi har da wadanda suka gwagwada musu don su suna da kudi suna cin kaji da choculate ta kanjamau gasu nan jikinsu kamar basu da ita, wallahi sai dai na koma business Allah, ke ni yanzu ma dan kaina nake son gani kada ka mutu baka da mai maka addu'a." Asma tayi dariya ta ce, "Lallai kawata kinji duniya, mu kan a taya mu da addu'a, yanzu yaya za'a yi da mutumin namu Mustafa babu waya ba zuwa, ko binsa Ofis za muyi? Zainab ta galla mata harara tana fadin, "Haba dai ajinmu ya wuce nan, ki dube ni da kyau bani da makusa ko siffar da zanyi kwantai, ko Mustafa ya kini ina da masoya balle shi yayi kadan ya rabu da ni don yau anan muka kwana......." "Shegiyar, Zainabu kina sha'aninki wallahi, yanzu har Mustafa ya kawo kan shi?" Ta mike ta koma kusa da ita ta dafa gwiwarta ta kwantar da murya tana fadin, "Ki yiwa Allah ki bani sirrin nan naki Zainabu da ya sanya duk namijin da ya kusance ki bai iya hakura, wallahi har yau samarinki na bariki na kwalaficinki, akwai wanda ya ce muddin na lallaba kika cigaba da mu'amala da shi zai bani miliyan guda, ya ce shi babu ruwansa da aurenki, to nasan ko baki da aure yanzu baki san mu'amala da kowa sai Musty balle da aurenki, don haka na bashi hakuri, na dinga hillatarsa da gwalangwaso ko zai kyasa ni, daga karshe dai na samu shiga, sai dai tun daga sannan bai kuma kirana ba, ya ce Zainabu daban ce." "Ki yiwa Allah ki gaya mini sirrin nan Zainabu." Zainabu ta yi dariya gami da mikewa tsaye tana fadin, "Ai kinfi kowa sanin sirrin nawa, kawai gyara ne da iya kwanciya, sannan da baiwa daga Allah, ki dubi dan karamin bakina kin san akwai abu a nan." Suka yi shewa gami da tafawa. Zainabu ta ce, "Ba zaki bata mini lokaci Mustafa ya taddani a haka ba tun kwalliyar safe ba, sai na fito daga wanka." Ta nufi bandaki. Ita ma ta mike ta ce, "Nima din ai wankan zan yi don duk jikina ciwo ya ke, shegen wallahi ya jibgeni da yawa, koda yake nima na yi masa tabo"Zainabu ta shiryo cikin wani wando gajere ne sosai da wata 'yar makalalliyar riga, kugunta ya fito das, shape dinta kuwa tamkar zai tsinke da siranta, tayi parking gashinta, fatarta tayi likwi-likwi gwanin sha'awa tamkar jikin jariri, Zainabu tana da kyau da iya kwalliya da ke kuma sanyata shiga zuciyar duk wanda ke tare da ita. Tana nan a falo tana kallo Asma na ciki tana shiri ya shigo falon, da saurinta ta mike da gudu ta fada jikinsa tana masa abinda ta saba, ya daga ta cak kamar wata 'yar tsana sannan ya manneta a jikinsa. Cikin kwantar da murya ya ce, "I miss you Zainabu." Ta kwantar da kanta a jikinsa tana fadin, "Me too Zumana." Suka yi dariya gami da fadawa kujera. Can ya ce, "Maza ki hado kayanki mu wuce kada dare yayi ina jin yunwa da yawa." Ta mike ta shige ciki don hado kayanta, doguwar (after dress) ta sako akan kayanta ta fito janye da troley dinta, Asma na biye da ita a baya. Bakinta cike da fara'a ta ce, "Da girman kujerarka yallabai, ni dai na san tsakaninka da Zainabu bata baci ko kadan, duk wanda ya shiga tsakaninku zai sha haushi da kunya.'' Dadi ya cika shi ya dubeta yana wani washe baki ya ce, "Lallai Asma kin gano lagonmu, kawar taki ce ba a wasa ba, irinsu a wannan zamanin kadan suka rage, idan na rabu da ita zan dade ina lalube ban sami rabinta ba." Dadi ya cika Zainabu da yabon da mijinta ke mata, ta kwanta a kirjinsa tana tsunkulinsa kamar wani dan yaro. Ya yi dariya yana fadin, "Asma kin gani ko?" Ta ce, "Zainabu tafi gaban nan, ni dai a taimaka a karasa gida don Allah Zainabu kada ki sanya ya manta hanyar."Suka yi dariya gaba dayansu sannan ya kama troley din suka fice Asma na biye da su, sai da ya shiga mota ya ciro kudi naira dubu hamsin ya mikawa Asma ya ce, "Gashi nan ladan rike mini zumata da aka yi." Ta amsa da sauri tana fadin, "Yallabai ina godiya, a sha soyayya lafiya." Ta juya ta koma cikin gida. Ya juya yana kallon Zainabu da ta kwanto da jikinta rabi jikinsa tana masa wani duba, Yayi murmushi kawai ya tada motar ya nufi gidansa na farm center. Dan babba ne amman bai kai wancan gidan nasu ba, don shi ko maigadi babu, shi ya fita ya bude musu sannan ya shiga da motar ciki ya faka suka fice, suna rike da juna kamar daya zai gudu ya bar dayan. Washegari ta kirawo kanwarta Karima ta ce tana gidan Mustafa na farm center, don ya sanar da ita taje can bata same ta ba, ta ce gata nan zuwa kuwa don tana son ganinta magana ce mai muhimmanci. Ai kuwa ta gane kwatancen da tayi mata ta iso har nan, maigidan ta ne ya sauketa ta tura gate din ta shiga, yace da yamma zai dawo ya dauketa. 'Ya'yan ta Jidda da Sulaiman suna makaranta sai na bayanta Salim, ta shiga falon da Sallama ta tadda yayar tata tana kallon dish. Bayan sun gaisa ta mike ta ce, "Anti yunwa fa nake ji haka na koma kamar rumbu, Dadinsu Jidda har tsokanata yake yi, bari na samo abinci a kicin dinki." Zainabu ta yi dariya tana fadin, "Ke dai fadi gaskiya ko dai kin harbu, don cikin ku babu wuya, tun da dai Salim yayi wata goma ai magana ta kare kila an gamu." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Ta dan tsaya tana dariya ta ce, "Au Anti ke ma haka zaki ce, ai wannan karon kam sai na huta Insha Allah, ulcer ce kawai ke damu na." "To Allah ya sawake, kije ki gani ina jin farfesu kawai ya rage wanda ya siyo jiya, baki ne mu a gidan babu komai sai yau zai shigo da su." Ta fito dauke da farfesun a plate da biredi da lemon gwangwani ta zauna gefenta, suna ci suna hira. Sai da ta kammala sannan ta fara maganar da ta kawo ta. "Anti maganar yaran nan ce, ya dace irin rayuwar da muka yi ta wahala da talla a ce kannanmu basu yi ba, tunda dai Allah ya hore mana, ki duba yanda Lubabatu ta girma amman wai fada suke yi da Sala dole sai tayi talla tunda taki kula samari ta samu kudi, ita kuma Jamila ba ki ga iskancin shigar da take yi ba sai zaginta ake yi a layin, ga samari 'yan iska na rashin mutunci, to yanzu da ita Sala ke shiri, idan kika ga yanda take kyarar Lubabatu tamkar 'yar riko, ga yaran nan da kyau, maimakon ta goya musu baya su yi karatu a'a nema take ta watsa rayuwarsu, Yaya Sadiku ne ya zo gidana yana sanar da ni nace zan sameki mu san yanda zamu bullowa al'amarin." Zainabu ta yi kwafa gami da fara magana cikin zafin rai, "Sala sai dai addu'a, har yau taki tayi nadama ta san Annabi ya faku, meye bamu yi mata ba? Dan da tace rashi ne yanzu kuma menene, tunda dai kayan abinci wani har tadda wani yake yi, ga kudi ana bata, sannan har gida ake zuwa siyan abinci da waina da safe, ai ya dace ace ta saduda haka, wato so take suje su kwaso mana ciki ko?" (Wanzami bai son jarfa, ance daman duk mai iskanci baya son ace wani na shi nayi) Don haka ran Zainabu ya baci sosai, ta dinga fada babu ji babu gani, daga karshe ta ce da Karimatu, "Ki kyale ni da ita, don nice maganinta don tasan halina, su kuma zan gaya musu irin abinda ake ji a karuwancin don wallahi wahalarsa tafi dadinsa yawa, musamman yanzu da kanjamau tayi yawa." Da wannan shawara suka rufe zancan Sala suka fada wani, Karimatu ke sanar da Zainabu mijinta ya biya musu kudin Hajji don haka bana tare zasu tafi. Zainabu ta ce, "Lallai ina murna, idan kin tashi tafiya in dai Mustafa bai biya mana ba sai ki kawo Salim na yaye shi, don kewa da rashin haihuwa sun fara damuna ki tayani da addu'a Karima, nasan abinda nayi can baya ne Allah ya nuna mini iyakata tun a nan duniya." Fuskarta ta sauya zuwa damuwa karara. Karimatu ta lallashe ta, sai da yamma maigidanta ya zo daukarta ta hada mata kayan kwalliya da jakunkuna guda biyu irin wanda take saidawa. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 *** *** *** *** Kwanasu goma sha uku a gidan su (Farm center) Alhaji Abudllahi ya dawo, Mustafa ya fi kowa farin ciki da dawowar tasa, ita kuwa Hajiya Kubra ta yi zaton ko ya hakura da Zainabu domin ta sanya ana masa rokon Allah a kanta, bata san suna tare ba ma, don haka idan ya zo gidan take nan-nan da shi. Sai da Alhaji ya kwana biyu sannan ya same shi a falonsa da zancan na su, cikin ladabi ya kwashe duk abinda ya faru da shi da Zainabu da Hajiya Saratu har zuwa sakin da Mominsa ta sanya ya yi mata, bai boye komai ba Sai kai ta gidan sa na (farm center) kawai ya boye bai sanarwa da Alhajin ba. Ran Alhaji yayi mugun baci musamman da yaji abin akan Hajiya Saratu ne, daman shi sam baya shiri da ita musamman da ya san halinta da abinda take yi, musamman harkar siyasa da take yi da auranta tana kuma bin maza a titi, don ta mallake mijin nata, don haka sam baya son ta haushinta yake ji. Don haka ya kirawo layin wayar Hajiya Kubra wacce daman tana shirin zuwan ne, ta shigo dauke da faranti na abinci ta ajiye a gefe sannan ta zauna tana fadin, "Yanzu nake shirin kawo maka daman." Sam bata lura da Mustafa ba sai da ya ce, "Barka da yamma Momi." Ta kalli inda yake, sai jikinta ya bata da wani abun ganin yanda Alhaji yayi kicin-kicin, ta amsa kawai sannan ta mai da hankalinta ga maigidan wanda yake kallonta, can yayi gyaran murya ya fara magana.Khadija yaya kuka yi da yaron nan ne? Yanzu sai da kika san yanda kika yi kika raba auran nan, ina ce kinfi kowa sanin fitinar 'yar uwarki eye? Idan da gaskiya ai sai ki tsaya ki saurari bayanin kowa, wai ni me kuka dauki aure ne? Daga wannan 'yar magana shi kenan sai saki kin sani fa da shine halak din da Allah baya so, wato saki dan haka kin farantawa shaidan rai, kinyi abu ba da tunani ba." Duk da taji haushin kawo kararta da Mustafa yayi, amman ta gano itama bata kyauta ba, don haka ta kwantar da murya don ganin mai gidan nata ya dauki zafi abinda yakan dade bai yi ba ta ce, "A yi hakuri nayi kuskure, amman raina ne ya baci a lokacin....."don idan da daraja matar Mustafa ba zata rama ko me Saratu tayi mata ba tunda dai 'yar uwa ta ce uwa daya uba daya." "Haba Khadija iyaye ai sun fi gaban komai, duk iyakacin hakurin ka aka zagi iyayenka da cin mutuncinsu in dai kai dan halak ne ka tanka, balle har da diyarta suka je suka yi mata cin mutunci, don Allah ki dinga adalci akan yarinyar nan, kada kiyayyar da kike mata ta sanya ki jawowa kanki fushin Allah." "Shi kenan Alhaji ya wuce ba zan kuma ba, sai dai ya kwabeta wallahi ta iya bakinta." Da sauri Mustafa ya ce, "Ita ma kanta ta gano bata kyauta ba yanzu tace a baki hakuri ma." Ta galla masa harara cike da jin haushi, a ranta tana fadin ashe yana tare da ita har yanzu, kai wannan yarinya ta zama matar jaraba, shi kuwa ganin irin kallon da take masa ya sanya shi sunkuyar da kanshi jikinsa na rawa. Alhaji ne ya ce, "Ka tashi ka tafi ya wuce sai dai a kiyayi gaba." Bai tashi ba kansa yana kasa ya ce, "Ka nemar mini izini gurin Momi na mai da Zainabu, ko har yanzu tana kan bakanta....." "Neman izinin me za'a yi nawa abinda kana tare da ita kaje kayi ta yi, ai kowa rai ya yiwa dadi baya ga mai shi ne." Hajiya Kubra ta katse shi. Alhaji Abdullahi yayi dariya don ya lura har yanzu bata huce ba ya ce, "To ai cewa yayi na nemar masa alfarma, don haka na nemar masa alfarma, don haka na durkusa a gabanki Khadija ina neman alfarmar Mustafa ya mai da matarsa Zainabu dakinta na sunnar Ma'aiki.Yanda yake maganar ya bata dariya don kamar wani danta ya koma, don haka fuskarta a sake ta ce, "Komai ya wuce ya maida ta, sai dai kuma ina da magana nima da muka yi can baya ta auran da zan ba shi, domin yarinyar tana karatu ne yanzu kuma ta kammala digirinta don haka nima ina so mu tsaida magana yanzu ta biki." Gaban Mustafa ya fadi amman sai ya dake don kada ya tsokanowa kansa, sai dai gumi kawai yake hadawa duk da sanyin AC da fankar dake kadawa a dakin. Alhaji Abdullahi ya ce, "Ina jinki Khadija wacce yarinya kika zaba masa don idan ba aurawa Mustafa wacce ranki ke so aka yi ba rigimar ba zata kare ba." Ta yi murmushi gami da gyara zama ta ce, "Ba wata bace illa diya ta Zainab, don daman tuntuni nake masa tanadinta don yarinyar mai tarbiyya ce wacce muka rene ta da tarbiyya da tsantse ni." Hankalin Mustafa idan yayi dubu ya tashi, a ransa ya dinga maimaita Zainab! Zainab! Sai yaji inama ace mafarki yake yi ba gaske ba, tunda yake bai taba kawo wa zai auri Zainab ba yarinyar da ya dauke ta tamkar kanwarsa yake ganinta, kai Momi ta baro masa jidali lallai, don Allah ya sani ba zai iya son wata mace kamar Zainabu ba, don haka sai yake ji kamar ya ce ba zai aura ba. Ran Alhaji Abdullahi yayi dadi domin dai yana son shima ace an hada zumunci tsakaninsa da Dan uwansa wanda su biyu ne kacal a duniya, gashi kuma daman yarinyar yana matukar kaunarta kamar shi ya haifeta, don tun da ya daukota gidansa bai taba jin wani abu na aibu a tattare da ita ba, yarinya ce mai matukar hakuri da kawaici ga biyayya, don haka da fara'arsa ya ce, "Kai tsohuwar nan rigimarki bata karewa, amman ai kece uwarta don haka ba zamu watsa miki kasa a ido ba, zan sami Salisu (Mahaifin Zainab) mu tattauna."Ya maida dubansa ga Mustafa yana fadin, "To kai ka zama na Zainabu da Zainab, mata masu suna iri daya, don haka sai ka rike amana don 'yar uwarka mai halin kwarai ce." Jikinsa sanyi kalau ya ce, "Ba damuwa Baba na gode." Ya mike yana musu sallama kamar wanda aka bigewa kwauri, jinsa yake wani iri daban, amman ya sani ko ya sha giyar wake bai isa ya ja da maganar auran nan ba don wanda ke goya masa bayan ma ya bada goyon baya (100%) dari bisa dari, don haka sallamawa ce kawai tashi. Haka nan ya shiga motarsa cike da tunanin abinda zai biyo baya duk randa Zainabu ta ji wannan zancan, Zainabu mai shegen kishi ko sunan mace ta gani a wayarsa in dai ba 'yar uwarsa bace rannan sai sun kwashi adashin tsiya, balle ace wai shine zai yi aure, kuma ma kanwarsa Zainab, kai abinda kamar wuya fa gurguwa da auren nesa, hakan nan ya isa gida da taimakon Allah don bai san da yanda yaje ba. Sanda ya isa ya tadda Zainabu ta ci kwalliya tamkar 'yar tsana, sai ya ji damuwarsa kashi saba'in ta ragu, ta taho da gudu da dafe shi, yayi wani taga-taga kamar zai fadi amman da yake dirarran namiji ne ya tsaya kyam, ya daga ta yana wani wulwulata kamar Bebi. Sai da suka shiga daki sannan ta kula da yanayinsa, duk yanda Mustafa ke cikin damuwa Zainabu na lakanta saboda yanda take ji dashi a ranta, don haka ta kama tambayarsa abinda ya dame shi. Kamar ya sanar da ita gaskiya, amman bai san yanda zata dauki maganar ba, don haka ya wayance kawai ya ce kansa ke ciwo, nan fa ta bazama ta samo masa magani tana wani lelensa kamar 'yar bebi har bacci ya dauke shi. Cikin kankanin lokaci Iyayansu suka gama komai na sanya rana da biki gaba daya, wata biyu kacal aka sanya, kowa yaji dadi a dangin musamman dangin mijinta wadanda suke sonta sai ta kuma samun wani matsayi don tana kyautata musu matuka domin macece mai kirki da kyauta, illar ta daya akwai ta da saurin fushi kuma sam bata son raini balle wargi. Sai da aka sanya rana sannan Zainab ta ji labari, jin abin tayi kamar mafarki kamar kuma wasa, don haka ta tadda Sumayya daki ta zauna gefenta hankalinta a matukar tashe ta ce, "Sumayya wai don Allah da gaske ne an sanya ranar aure na da Yaya Mustafa ko zolayata Fatima ke yi?" (Wata 'yar uwar Babanta da ke gidan). Sumayya ta kalleta cike da tausayi don ita kanta bata so aka yiwa Zainabu haka ba don sunyi alkawarin ba zasu auri namijin da son su yafi nashi ba duk son da suke masa kuwa, sai sun sami namijin da son sa yafi nasu, sai gashi yanzu za'a aura mata wanda bai sonta kwata-kwata hankalinsa yana kan watanta. Sumayya ta dafa ta idonta itama cike da kwalla ta ce, "Zainab wallahi ni kaina sai yau nake jin wannan labarin, wai kuma Momi ce ta hada auren, don daman tace sai Mustafa ya auri wata cikin 'yan uwa, wallahi ban taba zaton ke Momi zata ce ba nayi zaton Zubaida zata bashi don naga ita ce ke son sa da Babarta suke son ya aureta tuntuni, dalilin da ya sanya suka tsani Anti Zainabu ma kenan." Zainab ta fasa kuka mai ciwo ta ce, "Yanzu Sumayya babu wani taimako da zaki yi mini a janye maganar nan, ba zan ce miki bana son Yaya Mustafa ba don yayi haduwar da duk wata mace zata so shi, sai dai muddin na yadda na shiga gidansa zan zamo mace mara daraja da samun kulawar mijinta, ki taimake ni gwara a hadani da ko waye da ace Yaya Mustafa zan aura, don yayi nisa a son Anti Zainabu." Ita ma Sumayya idon ta ya ciko da kwalla ta rungume Zainab tana lallashinta gami da yin magana, "Zainab ki kwantar da hankalinki, Insha Allahu zanyi iyakar kokari na naga na shawo kan Momi, amman idan Allah ya kaddara ke matar Yaya Mustafa ce babu tsumi babu dabara sai kin aure shi, sai dai muyi addu'ar Allah ya zaba abinda yafi zama alkhairi." Sun jima suna jimamin su har gari ya waye, suka shirya suka tafi camp, domin sun fito bautar kasa suna camp ba'a yi posting dinsu ba. Shi kam Mustafa ya fi kowa shiga tashin hankali da sanya ranar nan, har ya zama ko kaunar ganin Zainab bai son yi, don haka sun jima sam basu hadu ba, sai dai daga karshe zuciyarsa ta bashi shawarar abinda ya dace ya yi, dole ita Zainab din zata sami Momin na su ta ce a fasa auren, don haka bai shirya gayawa Zainabu ba har sai ya aiwatar da abinda ke ransa tukunna. Su kam bayin Allah basu san abinda ake ciki ba, da yamma suka dawo gida domin su Babansu ne ya ce bai yadda su zauna a camp din ba, aka yi sa'a kuma yana da abokai daga sama, daman Nigeria wa ka sani ne wa ya sanka, don haka ya sami yanda suke so. Tun da suka doso falon gidan suke jin hayaniya, suka kalli juna cike da tashin hankali sannan suka shiga da sauri, sun tadda 'yan matan gidan kowacce tayi tsuru-tsuru, sai Zubaida da ke wata kujera a zaune tana matsar ido ga kuma Hajiya Saratu tana surfa bala'i."Kubra ko kin fadi ko baki fadi ba aikin ki ya nuna baki kaunata balle zuri'ata, domin tun karon farko na auran Mustafa na nuna bana son hadin nan kika watsa mini kasa a ido, sannan kullun kina kurin sai kin raba auren ki masa auren zumunci, sai gashi yarinyar nan Zainabu ta zageni tatas kina kallo ta dawo gidan Mustafa, sannan don cin fuska da kika tashi nemar masa aure kika samo a dangin mijinki saboda kinfi kaunarsu da mu, idan abin naki gaskiya ne ai da Zubaida ya dace ki hada su tun da dai kin san ita yake so tunda farko, ko kuma nace ta nuna alamun tana son shi, taki kula kowa saboda Mustafa amman ki mini irin wannan cin mutuncin." Hajiya Kubra dake zaune ta yi murmushi da nuna rashin damuwa da maganar 'yar uwar ta sannan ta fara magana, "Saratu ina ce da Zainab da Zubaida duk 'ya'yana ne, kuma idan da gaskiya a duniya ba zan fifita Zainab akan Zubaida ba, ki yadda Allah da Zainab ya kaddara auran don wallahi ban taba sanin Zubaida na son yaron nan ba, kuma ita kanta Zainab din sai da aka sanya rana ta sani don haka kinga bai dace ki zargeni ba ko ki kullace ni ba....." Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 "Kullata da zargi kam har abada ba zai rabu a tsakaninmu ba, don dai da arziki a garinsu gwara naki kuma a gidanku a dakinku a karkashin gadonku, kuma in dai har kamar yanda kikace ba zaki fifita Zainab akan Zubaida da gaske ne to ki san yadda za kiyi ki warware sanya ranar da aka yi musu ki maida ta da Zubaida, don yanda Zubaida ke fadi tunda ta rasa Mustafa karo na biyu ita da aure har abada, kinga kin dirar mani rayuwar diya da ka......Hajiya Kubra ta dubi Hajiya Saratu da mamaki ta ce, "Haba Saratu ai imanin dayanku bai cika har sai ya so wa dan uwansa abinda ya so wa kansa, yanzu kina ganin idan aka yi haka anyi adalci? Sannan da wane idon zan kalli Babansu na ce wai a warware sanya ranar nan, kema kin san ba abu ne mai yiwu wa ba zan jawa kaina abin magana ne da gori ga....." "Shi kenan kin gama magana kin gama nuna mini kinfi kaunar Zainab da jininki Zubaida, sai dai yau ce rana ta karshe da zaki kuma ganin kafarmu a cikin gidanki, kuma daga yau ki cire ni a jerin 'yan uwanki balle wata sabgarki ta tashi ki sanya ni a ciki." Ta maida dubanta ga Zubaida ta ce, "Ta so muje, ki kwantar da hankalinki Allah zai musanya miki da miji na gari, su dai su yi mu gani don wallahi nasan karuwar matarsa ba zata barshi ya zauna da Zainab din ba, daman kece daidai ita." Suka fice daga falon a fusace. Ran Hajiya Kubra idan yayi dubu ya baci, ta yi tagumi cike da damuwa ta rasa abinda ya sanya Saratu ke bakin ciki da duk wani abu da ya kasance na farin ciki ko na cigabanta, idan ta ce bata son Zainabu don mugun halinta ita kuma Zainab meye laifinta, kuma tunda take bata taba mata maganar hada auren Zubaida da Mustafa ba sai yau don tsokano fitina, tun suna yara haka take mata gashi dai uwarsu daya ubansu daya amman tana bakin ciki da duk wani ci gaba ko farin ciki a rayuwarta. Su kam 'yan matan gidan tsuru-tsuru suka yi, Itama Zainab ji tayi kamar ta sanya hannu a kanta tayi ta zunduma ihu, musamman irin bangazar da Zubaida tayi mata da gayya da zata wuce gami da ja mata dogon tsaki har da mutsitsike dan yatsa, daman can bata jituwa da Zubaida balle wannan abin ya biyo baya,Sumayya ce ta jata suka yi dakinsu itama Hajiya Kubra ta shige dakin baccinta domin ta daura alwala ta bada farali amman har lokacin hankalinta a tashe yake. Karfe takwas da minti hudu Zainab taji wayarta ta fara ruri na neman agaji, ta dauko ta da sauri, sunan Mustafa ta gani baro-baro Ya Mustafa, gabanta ya yanke ya fadi, sai jikinta ya hau tsuma don bata san mai zai ce mata ba. Tayi dai ta maza ta danna madannin amsa kira ta kara a kunnenta gami da yin sallama. Da kyar ya iya amsawa sannan ya ce, "Ke kina jina? Ina falon boys quarters ki zo yansu, kuma bance kizo da wata ba ko ki sanar da wata nazo ba, don nasan halinki." Yana kaiwa nan ya kashe wayar. Ta yi tsumu-tsumu tana kallon wayar, kamar ta tsaya ta sanarwa da Sumayya wacce ke wanka amman sai ta tuna da gargadin da yayi mata don haka ta mike jikinta na rawa ta nufi sashin yaran, daman tana shirye tsaf gyale kawai ta dauka. Yana zaune bisa kujera ya hade hannuwa, fuskar nan ta sa babu alamun fara'a, ta yi sallama ta shigo har lokacin jikinta rawa yake. Tunda ta shigo ya zuba mata ido, yau ce rana ta farko da ya tsaya yayi mata kallon tsaf, doguwa ce amman ba can ba kuma itama fara ce ba tas ba, tana da kyau daidai misali don duk inda mace take ji da kanta ta kai nan, tana da gashi mai tsaho sannan tana da kirar mata ta burgewa, sai dai ko kusa bata kamo Zainabu a kyan kira da jiki ba. Har ta zauna bai dauke idonsa daga kanta ba, abinda ya kara tsurar da ita, shi kam so yake yaga abinda zai kushe Zainab da shi a ransa amman har ya karaci kallon kurillah nashi bai gano ba sai dai yace Zainabun sa ta fita.Ita kam sai rawar jikinta ya kuma karuwa don ganin duban da yake mata babu ko kunya, ta daure ta zauna kamar wacce zata zauna bisa garwashi. Yayi shiru bai ce mata kala ba, ita kam tsoro ne ya hanata cewa komai, amman don kada ta kara laifi sai ta daure da kyar kamar mai yin rada ta ce, "Ya Mustafa ina wuni.....Kinga ba wannan ce ta kawo ni ba kina ji ko? Zuwa nayi naji dahir daga bakinki, shin ke ce kika ce kina sona har aka hada auran nan?" Ranta ya dan sosu, sai taji dauriya tazo mata, don ba zata lamunci yayi mata cin fuska ba, don haka ta danne ta ce, "Kai ma ka san hakan ba zata faru ba, ni a matsayin Yayana na dauke ka, don haka kama daina tunanin nice naje na ce ina son ka aureni." "Wonderful, haka nake son ji daman, don haka yarinya kin kwaci kanki muddin kika sanar da Momi baki sona, ni bance bani sonki ba sai dai soyayyar mu bata aure bace, ina ganin ke 'yar uwata ce daman..... don haka ina son ki sanar da Momi baki sona a janye maganar auran nan, idan kika yi haka kin kwaci kanki, don kin sani Zainabu ce kadai macen da nake so har abada, raina ba zai iya rayuwa da wata can ba bayan Zainabu." Ita kam tunda ya fara maganar bata ce ko kala ba har yayi ya gama, sai da yaga bata da niyyar cewa komai sannan ya kuma cewa, "Banji kince komai ba, don bana son asan na zo gurinki ma balle ayi zaton ko ni na sanar da ke, ki nuna ba kya sona ne kawai don kanki, hakan ma zai fiddani daga zargin Momi. Ta kuma daurewa kashi na biyu ta ce, "Hakan ba mai yiwuwa bane, yanda kake tsoron bacin ran Momi nima haka nake tsoro, kuma yanda kake gudun zargi nima haka nake gudu, don haka wallahi da bakina ba zance da Momi bana sonka ba, sai dai kai kaje ka fada idan ba haka ba kuwa sai dai a yi auran....Kinga Malama kina wata maganar ba zaki je ki fada ba ni ke nake tausayawa, domin idan kika sake aka yi auran nan kin san ke ce a hannu don zan sanar da ke ba zan iya shiga dakinki da sunan kwana ko auratayya ba, hasalima ba zan iya miki duban da na kewa Zainabu ba, don haka idan kin fada kanki kika ceta, idan kuma kika yi sakaci har aka daura kin shiga rayuwa mara ma'ana da daraja, don kin san har abada ba zan iya sakinki ba hakan kamar na yanki tikitin salwantar da zaman lafiya da Momi ne na har abada, don haka zan zauna dake wani irin zama ne da ba zan iya bashi suna ba." Idanuwanta suka ciko da kwalla, hankalinta yayi mugun tashi da jin kalaman Mustafa, amman ta san ko da zata koma matsayin da har abada bata da 'yanci ne a gidan sa ba zata iya cewa da Momi bata son danta ba gaba da gaba, "Zaka iya yin komai kaga dama, amman wallahi har abada Momi ba zata ji kalmar kin ka daga bakina ba, na shirya zama baiwa a gidanka, domin shege shi ke manta alkhairi ba dan halak ba, Momi tayi mini abinda har na mutu ba zan manta ba....." "Shut up, rufe mini baki!" Ya fadi a fusace san da ya mike tsaye don ganin hakarsa bata tadda ruwa ba, wannan itace dabara da ta rage masa ta karshe, don haka ya gama saddakarwa da lallai auran nan babu fashi, amman zai nunawa yarinyar nan namijin duniya ne shi da ba'a isa a yi masa auran dole ba.Ya nuna ta da yatsa ya ce, "Ki shirya fuskantar bakar rayuwa mara fasali a gidan Mustafa da Zainabu....." Yana kaiwa nan ya fice daga falon yana wata irin tafiya kamar zai balla tayal din da ya malale falon. Sai da ya fice taji kuka ya kwace mata, ta hada kai da gwiwa tana kuka sosai, haka nan Allah ke tsarawa bawa abinda ya so ko da son ransa ko babu, ita kam ko a mafarki bata taba zaton zata zama matar Mustafa ba don ta riga ta san yayi nisa a son Zainabu, ita kanta ta san Zainabu macece da kishi da ita zai iya zama bala'i da masifa domin babu ta inda ta rago ga mijinta, daga fannin girki har fannin kwalliya, balle kissa da iya tarairayar miji, takanas suke zuwa gidan daukar kwas kuma duk sanda suka je sai sun ga wani sabon salon da zai basu mamaki da sha'awa. Ita kam ta yadda rayuwarta a gidan Mustafa rayuwa ce zata yi mara 'yanci da cigaba ma, ta mika al'amarinta ga Allah tunda shine ya tsara mata wannan rayuwa ta san zai bata mafita, don Allah ya ce, "Baya dorawa rai abinda yafi karfinsa." To tasan zai kai mata dauki, ta yaya ne bai bata sani ba za dai ta mika kukanta gareshi. Sai da taci kukanta ta koshi sannan ta mike kamar wacce aka yiwa duka da kyar take takawa duk jikinta ya mutu murus ta nufi gida tana jan kafafu. A tsakar daki ta tadda Sumayya ta zauna tana kallo, tana shigowa ta dubeta da sauri, daga gani babu tambaya kuka take don farin idonta ya rune zuwa ja har wani kumbura kuma idanun nata suka yi, fuskar nan duk tayi wani luhu-luhu abinka da farar mace. Sumayya ta mike da sauri tana tambayar ta, "Zainab me ya faru? Ina kika je? Tun dazu nake nemanki ga wayarki kin barta a daki, Ko Ya Mustafa ne....."Ta daga kai ta kalleta da sauri saboda tambayarta ta karshe amman ta gaza cewa komai. "Na ma san shine, Me yayi miki? Me yace miki? Yace baya son ki ko? Zan sanar da Momi yanzu kuwa....." Ta rike ta sanda ta ga ta nufi kofa da sauri. "Kada ki fada mata na sani zata kirashi tayi masa fada ne, shi kuma zai yi zaton nice na sanar da ita don daman yace ko me aka yi mini sai na sanar dake, don Allah ki bari kada ki gaya mata ni baice mini komai ba, bai ma zo ba fa." Tana maganar tana sheshshekar kuka. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 Sumayya..... ta ce, "Haba Zainab naga Ya Mustafa da idona wallahi, don na fita amso sako gurin Baba Maigadi dana aike shi na ganshi ya fito daga boys quarters ransa a bace, yana wata tafiya kamar tunzirarre har ya fice a motarsa bai ganni ba, ni kuma na kyale shi don naga kwana biyu kamar haushina yake ji." "Ni dai don Allah kada ki gayawa Momi, ki rabu da shi kawai Allah yana sane da ni." Sumayya ta warce hannunta tana fadin, "Wallahi sai na yi mata maganar akan auran nan ko da banyi mata ta Ya Mustafa ba, kina ganin irin cin mutuncin da Anty Saratu ma ta tayi dazu, Zubaida kuma har da bangazarki da taka miki kafa, ina kallo don kada nayi magana ne ace ina goya miki baya ne, shi ya sanya nayi shiru, me yayi zafi haka kawai kina rayuwarki a zo a matsa miki bayan baki sanya a ka ba, dame zaki ji da kin da Ya Mustafa ke miki ko da kiyayyar Zubaida ko kuma da kishi da Aunty Zainabu, gwara yaje ya auri Zubaidar sa tantance tsakaninta da Anty Zainabun, bani waje na sami Momi din." Ta nufi dakin Momin nasu.Zainab ta fada gado ta kuma fashewa da kuka mai cin rai, lallai kam tana cikin matsala babba, wanne ne baya cikin wadannan matsaloli guda uku, dama ace ta samu Ya Mustafan yana sonta da sauki amman mutumin da yake ganin ina wuta ya jefa ta. Sanda ta isa dakin ta tadda Momi da wasu fayal a gabanta tana cikewa, tana sanye da (medical glass) dinta, ta isa ta zauna gefenta Momin ta ce, "Ya dai aka yi na ganki duk ranki a bace." Ta kuma hade girar sama da ta kasa ta ce, "Momi akan maganar Ya Mustafa da Zainab ne tunda kinga ita bata son shi shi baya sonta gwara a hakura, ga kuma Anty Zainabu a gida kinga ba zai ga wata mace da daraja ba tunda yana ganin Anty Zainabu, ni a ganina gwara a maida auran kan Zubaida tunda ita tana son shi, kinga ita zata iya da ita, kar ce ta san kar." Hajiya Kubra ta zare glass dinta gami da rufe fayal din tayi murmushi sannan ta ce, "Sumayya tunda aka yi maganar auran nan naga take-takenku ke da Zainabu na san lallai Zainab bata son Mustafa, ba wai kuma bata son sa don komai ba ne illa don tana tsoron matarsa, lallai kam matarsa abar tsoro ce, sai dai kiyayyar da nake mata ba zata sanya na rufe ido na yi mata sharri ba, a iyakacin binciken da nayi a kanta babu wanda ya ce mini tana mu'amala da malamai ko bokaye, don haka zargin da nake yi da na cewar asiri tayi masa ya kau a zuciya ta. Yanzu na gano tsantsar iya duniyanci ne da kissa ya sanya Zainabu ta tafi da Zuciyar Baba, don haka Zainab macece itama zata iya duk abinda Zainabu tayi ko ma tayi sama da nata din, don duk mace tana da kissa da nata wayon nasan wata rana zai yi alfahari da auranta Insha Allah,wannan ne ma ya sanya na jajirce naga anyi auran nan, don da can na zaci asiri take yi naji tsoron kada na hada auran a nakasa mini diya, amman tunda kissa ce da iya zama da miji to itama zata iya wuyarta dai a yi auran. Maganar Zubaida kuma kada ki kuma tunanin zan amince Mustafa ya aureta, don idan na bari ya auri Zubaida ba a rabu da bukar bane an haifi Habu, don wallahi gwara Zainabu sau dubu da Zubaida, ita din da har neman mata take yi, sannan duk irin rayuwar da tayi a makaranta ina sane da ita, sai dai tun da na fara sanar da Mahaifiyarta ta nuna bata son gaskiya na zuba musu ido. Ki sani ina son yayi auran mace salaha kuma ta gari ne, wacce ko bayan ransa zata iye rike masa zuri'arsa da tarbiyya, amma daga Zubaida har Zainabu zuaciyarsu bata gyaru ba balle gangar jikinsu ta gyaru su gyara wani ba, kuma Allah ya sani ba wai ina kin Zainabu don sunanta ko don gidansu ba, ina kinta don halinta na banza ne, don haka ina neman kema ki taimaka dan uwanki ya ajiye salihar mace mai gyararriyar zuciya a gidansa, wacce zata haifa masa zuri'a dayyiba masu nagarta. Jikin Sumayya yayi sanyi ta kuma gamsu da bayanin Momi, sai dai tana ganin kamar Momi tayi son kai, don tana son danta ya sami zuri'a dayyiba sai ta aura masa mace ta gari bayan shi din zuciyarsa bata gyaru ba, tunda kowa ya san yanda ya auri Zainabu ita Momin din ce bata san komai ba, idan har akayi wannan aure lallai an tauye Zainab mai kamala da kamun kai, amman babu yanda za ta iya sanarwa da Mominta wannan maganar, don haka ta mike kawai ta nufi kofa. Momin ta ce, "Ki dinga tausar Zainab, gobe kuma zanje kasuwa zan siyo mata wasu littafai da zasu taimaka mata, ki bata hakuri don ni yanzu kunyarta nake ji don na san naso kaina, amman Insha Allahu yanda tayi mana biyayya Allah ba zai kunyata ta ba komai dadewa." Sanda Sumayya ta isa dakin ta tadda Zainab bisa sallaya ta yi sujjada tana ta addu'a, duk da bata jin abinda take fadi tasan kukanta take kaiwa rabbi don haka itama tayi alwala ta fara taya ta neman yardar Allah Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C737012347 . *** *** *** *** *** kwanaki sun fara ja na biki sai shirye-shirye ake yi a ko ina daga bangarorin iyayan amarya da na ango, amma ango gaba daya a birkice yake, Zainabu ta shiga damuwa kwarai ganin halin da ya shiga, don haka ta yiwa kanta alkawarin ganin ta magance masa abinda ke damunsa. Ya dawo gidan yau karfe tara na dare, don yayi mata waya ba zai dawo da wuri ba, wani inji ne ya tsaya na zuba mai, don haka shi yake gyara shi don kananan injiniyoyin duk sun gaza. Tana zaune a falo tana kallon tashar Zee Aflam ya shigo, tana sanye da dogon wando fela da ya kama ta tsam ta sanya wata riga mai huda-huda wacce ana hango kalar rigar kayan sun yi mata kyau matuka, sai wani kamshi take yi mara fasaltuwa. Tana jin shigowarsa ta nufeshi da gudu, ya daga ta kamar kullum ya manne a jikinsa, ta shiga aiwatar masa da abinda ta saba, ya shagala matuka don Zainabu ta san kansa da kyar ta jashi zuwa bandaki, ita ce ta kusa yi masa rabin wanka suka fito nannade da tawul yana dauke da ita kamar wata 'yar tsana, don da yaga dama zai dauketa tsaf yana tsokanarta, yace kamar roba take babu wani nauyi da yake shi din kakkarfa ne, musamman da yake yana aikin karfi.,sunyi shiru a kan gado, ya rasa ajin da zai ajiye Zainabu don ta gama masa komai, gaba daya kusan rayuwarta gurin kyautata masa kwanciyarsa take karewa bata taba gazawa da shi ba, duk sanda yazo da bukatarsa ta gamsar da shi ko da tana al'ada ne ta kan san yanda za tayi ta biya masa bukatarsa ba tare da ya kusance ta ba, Zainabunsa zuma ce. Sai da ta tabbata ta gamsar da shi sannan tayi lamo a kirjinsa tana wasa da cikin salonta na kuma sace zuciyarsa ta ce, "Zuma yau dole ka sanar da ni abinda ke damunka, idan ka shigo sai na ganka duk ranka a bace, ko Ofis ake taba mini kai ne?, nifa ban son abinda zai dinga tsunkulinka, ka sanar da ni kaji ko kana so nayi kuka?" Ta karasa maganar da kissa da wani salo da ya sanya shi kusan shidewa, sai dai duk da haka kirjinsa yana bugawa kamar zai fito waje. Ya tashi zaune har lokacin tana jikinsa kamar zata koma cikinsa ko kuma a maida halittarsu tare, don haka ne ma duk sanda suka raba shimfida (idan sunyi fada) ya shiga damuwa matuka, don muddin yana gida Zainabu na makale da shi tana goga masa lallausar fatarta, abinda ke kara mata martaba a idonsa, don yana son hakan da take masa, kai duk wani abu da yake so ma Zainabu nayi masa. Ta kuma narkewa tana shagwaba ta ce, "Allah ka sanar da zanyi zanyi kuka, ko kana son nima na fara damuwa kamar yanda kake.....ya toshe mata bakinta kirjinsa hr lokacin yana bugawa, ya ga gwara ma ya sanar da ita tunda yanzu bikin saura sati biyu kacal kada ta ji a wani gurin ta zarge shi, sai dai ya san yau kam zai gamu da tashin hankali. Ya daure yayi ta 'yan maza ya ce, "Zainabu tuntuni nake son sanar da ke abinda ke damuna, sai dai ban san yanda zaki dauki lamarin ba, ke din mutum ce mai muhimmanci a rayuwata wacce har nake ganin da na rasa ki gwara na rasa raina, kuma wallahi har abada ko kina raye ko baki raye ko muna tare ko bamu tare ba zan iya son wata sama da ke ba don ke din rayuwa ce ta jin dadi, sai dai akwai wani matsayi da mutum yakan kai da duka mai neman cikawa da imani ba zai bijirewa maganarsu ba, ma'ana ina nufin uwa kenan." Tana jin ya ambaci haka taji gabanta ya yanke ya fadi don jin ya ambaci Mahaifiyarsa, don tana zaton ko cewa tayi sai ya sake ta, tana ganin in dai haka din ne ta shiga uku don kamar yanda yace itace rayuwarsa shima din shine rayuwarta, amman sai ta gaza cewa komai illa bugawa da kirjinta ya kama yi ta kuma kankameshi tamkar za'a rabasu da karfin tsiya. Ya cigaba da magana a hankali cikin mafi taushin lafazi da zaben kalmomi, "Don haka Zainabu, ko me zance ina son ki fahimceni don kinsan ke ce kadai nake so zan kuma cigaba da so har daukewar numfashi na. Ba wata magana bace illa Momi ta ce lallai sai na auri kanwata Zainab har ma an sanya rana bikin saura sati biyu, tun daga sannan ban kuma samun kwanciyar hankali ba......" "Kai! Ya isheka haka Malam." Ta fadi da karfi da zafin zuciya sanda take janyewa daga jikinsa tana masa wani duba da tsana da jin haushi. Ta dora da cewar, "Ni zaka rainawa wayo ka maidani 'yar iska? To baka isa ba nafi karfin ka hada ni da wata saboda ban aureka dan kudi ko wani abu ba illa so, da na so auran kudi da sai naje na auri mai mata, don haka sai dai ka zaba ko ni ko wacce zaka aura, kazo kana mini wani rainin hankali, mtsw!" Ta ja tsaki gami da fadawa kujerar da ke dakin ta dafe kai,Hankalinsa ya kai kololuwar tashi, ya san haka zata faru daman don haka ya so ya yakice maganar auran nan ko ta halin kaka amman sai da ta tabbata, yanzu yaya zai yi da rayuwarsa da rigimar Zainabu? Ya daure ya kuma kwantar da murya ya ce, "Haba Zainabu ya dace ki fahimce ni, kin san dai bayan ke ba ni da abar so, wallahi ki yadda wannan auran zan yi ne don biyayya ga iyayena amman ba don ina son yarinyar ba, hasalima ita kanta yarinyar ta san ke ce dai kadai nake so, don Allah ki kwantar da hankalinki mu fahimci juna." Ta galla masa harara gami da kauda kai gefe, zuciyarta sai wani irin tukuki take yi, ji take kamar ta rufe shi da duka, ita ko sanda tana bariki namiji bai isa ya hada ta da wata ba balle ace wai mijinta da take so ta ware shi daban a ranta fiye da kowa. Saboda tsabar takaici ma sai ta kasa cewa komai illa idanuwanta da ke zubda hawaye tamkar famfo. Jin ta yi shiru ya sanya shi mikewa ya isa gabanta ya tsugunna ya kuma kwantar da murya ya ce, "Zainabu ki yiwa Allah ki dauki abin nan da sauki, ki kuma zira ido ki ga irin zaman da zan yi da yarinyar nan don na gaya mata ta sani ba zan taba sonta ba....." "Ka rabu da ni malam ka ji ko!" Ta fadi da tsawa gami da mikewa tsaye tana huci tamkar wacce tayi tseren gudu, ta dora da cewar, "Ka na ji ko? Ba ka isa na zauna da kai kana tare da wata 'yar iska ba, don haka na gaya maka sai dai ka zabi daya. Da me zan ji? da kiyayyar da danginka ke mini ko da kakaba maka diyarsu da suka yi? Don haka sai ka zauna da wacce aka zaba maka ake son ka zauna da ita amma ba ni ba." Tana kaiwa nan ta fice daga dakin da gudunta don kuka ya ci karfinta.....Tofa,karshen tika tiki tik..Labari ya dakko gakums takaddunsa sunkare,yaya za'ayi kenan, saidai ko muhadu a littafi nagaba kuma na karshe........(KO INA LABARIN SALA DA BABA ABBAKAR DA KUMA SADIKU DA KANNENSA? KO SALA TA GANE KUSKURENTA KO KUMA TA KARA ZURFI CIKIN BATAR TA? KO WANNAN AUREN ZAI YIWU KUWA? DON JIN AMSAR WADANNAN TAMBAYOYI SAI MU HADU A LITTAFIN NA UKU Mai kaunarku da yi muku fatan alkhairi a kullum. FAUZANKU CE! Mrs Q for Q, adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *